Sashe 8
Bintu Diyar Bayice Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘’Mungode kwarai hak’ik’a mun yi dana sanin abin da ya wakana a Masarautar mu, hallo mu na fatan hakan ya zama alkhairi a gare ki. Ki tsaya tsayin daka domin tabbatar da rufin asirin mu, shakka babu kin mana abin da ‘ya’yan mu ba su ma na ba. Tashi ki tafi d’iyar arziki, mu na addu’a albarkar Allah ya bi ki duk in da za ki kasance’’
Jiki na rawa, amma Bintu ta kasa tashi ta kuma kasa magana. Jakadiya ce ta lek’o, ganin yanayin da Bintu ta ke ya sa ta yiwa Dattijan nan magana su shigo su tafi da Bintu Sarki ya gama ganawa da ita.
A 6angaran Hajja Kilishi su ka tadda Dattijiwar Fabarusa wato Uwalanze. Nan aka damk'a hannun Bintu gare ta bisa alada da amana. Bintu fuska k’udundune cikin alkyabba kuka har da majina, Uwalanze ta ja hannun ta, biye da su d’aya daga cikin wannan dattijan ne da su ka kai ta ga Sarki, dama kuma ita d’in ce cikin su ta san gaskiyar lamarin wato Gwaggo Munari. Kai tsaye motocin Fabarusa su ka numfa.
Motoci ne na gani na fad’a wanda ke tashe wannan k’arnin. Mota ta farki cike fal da dogaran Fabarusa, sai ta biyu wacce ke rufe ruf da bakin gilashi, ita ce motar da su Yarima Barde ke ciki. A ta ukun Bintu ke zaune tsakiyar Uwalanze da Gwaggo Munari. Sai ta hud'in kuma bayin da aka bawa Bintu ne, wanda idan ka d'auke Maman Cangwi ko wacce daga cikin su tafe ta ke da na ta kullalliyar akan Bintu. Mota ta biyar ma dogaran Fabarusa ne ciki. Nan su ka d'auki hanyar Fabarusa.
A hankali Bintu ta ji ana ta6a kafad'ar ta, maimakon ta tashi sai ma dad'a lumshe idanu ta yi ta na mai murmushi, kasancewar mafarkin da ta ke mai dad'i, wai ga ta a makarantar su, tare da Aisar su na zantawa ya sa ta ji sam ba ta so ta farka. Gwaggo Munari ce ta katse mata jin dad'i ta hanyar jijjaga kafad'ar ta, wannan karan da d'an karfi domin kuwa sun jima da isa Masarautar Fabarusa, yanzun haka kofar fada su ke, Uwalanze har ta fice daga motar amma Bintu na nan ta na baccin asara.
A firgice Bintu ta tashi jin jijjigar ta wuce hankali, ga busar algaita da ke tashi, har da hayaniya da wak'e dake tashi daga bakin mutan Fabarusa da su ka cika kofar fada domin ganin isowar amaryar Yerima Barde.
Ganin alamar Bintu ta tashi, Gwaggo Munari ta shiga gyara ma ta alkyabba yanda fuskar ta zai rufu da kyau, ta na fad'in
"Ko ke fa Gimbiya d'iyar Sarki mai dole, ai ke kuwa bacci be same ki ba"
Kalmar nan ta Gimbiya da jama'a ke kiran Bintu da shi sam ba ya mata dad'i, gani ta ke tamkar ana raina mata iyayen ta, ya ga wanda su ka haife ta amma fin k'arfi zai sa a raba ta da su? In dai haka zama Gimbiya ya ke Allah wadar da irin na Sa'ayrasa.
Ta na kan wannan tunani ne gilashin motar ya sauka, yayinda Jakadiyar Fabarusa ta bayyana a gare su, kana ta ce
"Gide mutan Fabarusa, na cikin gari hallo da na fada, kwan mu da kwarkwatar mu, mun hito domin tarbar amaryar zaki, Yariman mu abin alfaharin mu. Mu na neman alfarmar bayyanar wagga Gimbiya ta Sa'ayarasa, da ta kasance Gimbiyar Fabarusa da ga ranar jiya har illa MashaAllahu"
Gwaggo Munari na mai murmushi ta amsa mata da
"Gimbiyar ta mu, wacce ta kasance fure a gare mu, wacce babu shakka za ta wadata ku da kyawu gami da kamshi da ke tattare da ita, Gimbiya Fatima ta Sa'ayrasa ta amsa kiran mutan Fabarusa"
Jakadiya ta rangwad'a gud'a, tuni waje ya kaure da hayaniya,yayinda mata da yara su ka hau wak'a su na tafi, fad'i su ke
"Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!"
🐪🐫🐪🐫🐪🐫[8/29, 9:27 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
7⃣
Sidiya ce...✍🏼
Jakadiya ta bud’e kofar motar ta in da Bintu ta ke. Bayi mata guda goma shabiyu, wanda su ka kasu gida biyu sahu su ma jere kan sa sunkuye gaban motar su na jiran fitowar Bintu domin taka mata baya. Idan Bintu ta motsa toh dutse ma ya motsa, sai da Gwaggo Munri ta fito sannan ta zagayo gare ta, hannun Bintu ta lalabu cikin alkyabba, sannu a hankali, cikin azanci kai ka ce Gimbiyar ce da gaske ta fito da Bintu. Tuni bayin nan su ka zube gwiwowin su biyu a k’asa cike da girmamawa. Mata da yara masu waka ba su fasa ba. Cewa su ke
‘’Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!!’’
Jakadiya kuwa ba ta fasa gud’a ba. Tuni hayaniya da sowar jama’a ya rud’a Bintu, har sai da Gwaggo Munari ta fahimta ganin yanda ta cize waje d’aya ta kasa tafiya. Cikin rad’a Gwaggo Munari ta ce da Bintu
‘’yo to ki ka cize nan Gimbiya kya iya wad’uwa ba ki sani ba, gide rufa mana asiri mu tai, ke kawai ki ta salati, hallo ka da ki kuskura ki kai kallan ki ga jama’a, hakan ka iya rud’a ki, maza soma ambaton Allah’’
Nan da nan Bintu ta tsinci kan ta ta na mai ambaton Ubangiji. Tsakiyar Uwanlenze da Gwaggo Munari, Jakadiya daga baya, biye da ita bayi goma shabiyu ne, su ka kutsa ta hanyar da aka tanada na musammam domin wucewar Gimbiya. Ba su zame koina ba sai cikin fadar Fabarusa.
Kansencewar Masarautar Fabarusa ta yi biyun ta Sa’ayrasa a girma da tsari, ba su Ladiyo ba, hatta Gwaggo Munari sai da ta yi da gaske wajan 6oye shawa’an ta ga Masarautar domin kuwa lokacin da su saka k'afar su a katafariyar fadar Fabarusa, sun ga abin mamakin gaske, wato bayan girman fadar na da ban al’ajabi, kuma yadda aka fasalta ko tsara ginin ta shi ma abin mamaki ne. A tak’aice sai da su ka zamo tankamar k’auyawan da su ka shigo birni. Gini ne irin na gargajiya wanda aka kafa harsashin ginin da manyan duwatsu ma su tsada, wad'an su kamu takwas wasu goma. Tsakanin kowace katanga akwai duwatsu masu tsada wad’anda aka yanka su bisa ga ma’auni san’annan aka dasa itacen al’ul daga gefan su. Tsuntsayen fada iri iri ke shawagi, musammam d’awisu da jin su ne su ka fi yawa.
Sai da su kusta sauro gomasha biyu kan su kai ga shiga cikin gidan Sarki, kowanne da na sa irin adon da kayan k’awa, wanda idan su ka shiga wannan su ka shiga na gaban sa sai su ka ashe na baya ba komai ba ne idan aka had’a sa da na gaban sa. 'Bangarn uwar gidan Sarki Abdulrahman, wacce ake kira Goggon nan aka sauke su. In da aka zaunar da Bintu bisa shimfid’a na musammam da aka ta na dar mata daga tsakiyar falo, yayinda su Ladiyo, Hansai, Lanta da Maman Cangwai su ka yi zaune daga gefe matsayin su na bayin Gimbiya.
Tuni Barori da Bayi su ka shiga kai kawo da hidima domin tarbar baki cikin aminci ta hanyar tabbatar da ba su bawa Masarautar su kunya ba. Kayan marmari na daga ‘ya’yan itace ne, nama na k’arama da babban dabba kai har da ma na d’awisu, su dubulan ne, caccabe, alkaki da nakiya komai bajau sai wanda jama'ar Sa’ayrasa su ka za6a. Gwaggo Munari na mai jinjina kai cikin ran ta take fad’in
‘’ma su abu da abun sa, gaskiya dukiya cikin wanga masarauta ba a cewa komai! D’iyar bayi ke kuwa Allah ya yankewa kakar saka, amre cikin wanga Masarauta shi an baiwa’’
Ciki su ka bud'e su ka ci su ka yi nak. Amma ita ko Bintu ruwa ma kasa sha ta yi bare ta kai ga cin abinci duk da kuwa azababban yunwa ne ya addabi cikin ta. Bayan an tabbatar su huta ne wata baiwa ta zo ta ce da su idan sun shirya za ta kai su ga masauk’in su domin Gimbiya Fatima ta shirya ta sami fitowa zuwa taron wankan amarya wanda za a yi nan ba da jimawa ba.
🐫🐪🐫🐪🐫🐫
[8/29, 9:30 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
8⃣
Sidiya ce.....✍🏼
Shiryayyan d’aki mai had’e da 6and'aki aka aje su Ladiyo, su Bintu kuwa d’aya daga cikin d’akunan Goggon nan a matsayin ta na uwar gida aka sauke su kan a gama wankan amarya a mik’a ta ga na ta 6angaran.
Su na shiga masaukin na su ba da jimawa ba, wata baiwa ta sake dawowa d’auke da kaya, gaban Bintu wacce ke zaune bisa gado har lokacin ba ta bud’e fuskarta ba baiwa ta zu6e, ta na mai aje kayan gaban ta, ta ce
‘’ an gaida Gimbiya Fatima, wagga kaya tsaraba ne da ga Goggo nan, ta ce a shedawa Gimbiya Fatima ta sanya su yayinda za ta hito wajan wankan amarya nan ba da jimawa ba’’
‘’Gimbiya Fatima ta amsa, ta na godiya’’
Cewar Gwaggo Munari. Bayan fitar baiwar Gwaggo Munari ta yaye alkyabbar Bintu, sai ga ta ta yi wuri wuri da ido.
‘’Gimbiya yanzun ga ba lokacin tuntuntuni ba ne, kin dai san dalilin da ya sa ki wanga Masarauta da kuma a gurbin wacce ki ka zo, gwara dai ki sake shawara ki nutsu in har ba so ki ke ki rasa ran ki sa’annan ki haddasa yaki da gaba wanda ka iya halaka ta mu Masarauta gaba d’aya’’
Jiki na rawa, amma Bintu ta kasa tashi ta kuma kasa magana. Jakadiya ce ta lek’o, ganin yanayin da Bintu ta ke ya sa ta yiwa Dattijan nan magana su shigo su tafi da Bintu Sarki ya gama ganawa da ita.
A 6angaran Hajja Kilishi su ka tadda Dattijiwar Fabarusa wato Uwalanze. Nan aka damk'a hannun Bintu gare ta bisa alada da amana. Bintu fuska k’udundune cikin alkyabba kuka har da majina, Uwalanze ta ja hannun ta, biye da su d’aya daga cikin wannan dattijan ne da su ka kai ta ga Sarki, dama kuma ita d’in ce cikin su ta san gaskiyar lamarin wato Gwaggo Munari. Kai tsaye motocin Fabarusa su ka numfa.
Motoci ne na gani na fad’a wanda ke tashe wannan k’arnin. Mota ta farki cike fal da dogaran Fabarusa, sai ta biyu wacce ke rufe ruf da bakin gilashi, ita ce motar da su Yarima Barde ke ciki. A ta ukun Bintu ke zaune tsakiyar Uwalanze da Gwaggo Munari. Sai ta hud'in kuma bayin da aka bawa Bintu ne, wanda idan ka d'auke Maman Cangwi ko wacce daga cikin su tafe ta ke da na ta kullalliyar akan Bintu. Mota ta biyar ma dogaran Fabarusa ne ciki. Nan su ka d'auki hanyar Fabarusa.
A hankali Bintu ta ji ana ta6a kafad'ar ta, maimakon ta tashi sai ma dad'a lumshe idanu ta yi ta na mai murmushi, kasancewar mafarkin da ta ke mai dad'i, wai ga ta a makarantar su, tare da Aisar su na zantawa ya sa ta ji sam ba ta so ta farka. Gwaggo Munari ce ta katse mata jin dad'i ta hanyar jijjaga kafad'ar ta, wannan karan da d'an karfi domin kuwa sun jima da isa Masarautar Fabarusa, yanzun haka kofar fada su ke, Uwalanze har ta fice daga motar amma Bintu na nan ta na baccin asara.
A firgice Bintu ta tashi jin jijjigar ta wuce hankali, ga busar algaita da ke tashi, har da hayaniya da wak'e dake tashi daga bakin mutan Fabarusa da su ka cika kofar fada domin ganin isowar amaryar Yerima Barde.
Ganin alamar Bintu ta tashi, Gwaggo Munari ta shiga gyara ma ta alkyabba yanda fuskar ta zai rufu da kyau, ta na fad'in
"Ko ke fa Gimbiya d'iyar Sarki mai dole, ai ke kuwa bacci be same ki ba"
Kalmar nan ta Gimbiya da jama'a ke kiran Bintu da shi sam ba ya mata dad'i, gani ta ke tamkar ana raina mata iyayen ta, ya ga wanda su ka haife ta amma fin k'arfi zai sa a raba ta da su? In dai haka zama Gimbiya ya ke Allah wadar da irin na Sa'ayrasa.
Ta na kan wannan tunani ne gilashin motar ya sauka, yayinda Jakadiyar Fabarusa ta bayyana a gare su, kana ta ce
"Gide mutan Fabarusa, na cikin gari hallo da na fada, kwan mu da kwarkwatar mu, mun hito domin tarbar amaryar zaki, Yariman mu abin alfaharin mu. Mu na neman alfarmar bayyanar wagga Gimbiya ta Sa'ayarasa, da ta kasance Gimbiyar Fabarusa da ga ranar jiya har illa MashaAllahu"
Gwaggo Munari na mai murmushi ta amsa mata da
"Gimbiyar ta mu, wacce ta kasance fure a gare mu, wacce babu shakka za ta wadata ku da kyawu gami da kamshi da ke tattare da ita, Gimbiya Fatima ta Sa'ayrasa ta amsa kiran mutan Fabarusa"
Jakadiya ta rangwad'a gud'a, tuni waje ya kaure da hayaniya,yayinda mata da yara su ka hau wak'a su na tafi, fad'i su ke
"Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!"
🐪🐫🐪🐫🐪🐫[8/29, 9:27 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
7⃣
Sidiya ce...✍🏼
Jakadiya ta bud’e kofar motar ta in da Bintu ta ke. Bayi mata guda goma shabiyu, wanda su ka kasu gida biyu sahu su ma jere kan sa sunkuye gaban motar su na jiran fitowar Bintu domin taka mata baya. Idan Bintu ta motsa toh dutse ma ya motsa, sai da Gwaggo Munri ta fito sannan ta zagayo gare ta, hannun Bintu ta lalabu cikin alkyabba, sannu a hankali, cikin azanci kai ka ce Gimbiyar ce da gaske ta fito da Bintu. Tuni bayin nan su ka zube gwiwowin su biyu a k’asa cike da girmamawa. Mata da yara masu waka ba su fasa ba. Cewa su ke
‘’Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!!’’
Jakadiya kuwa ba ta fasa gud’a ba. Tuni hayaniya da sowar jama’a ya rud’a Bintu, har sai da Gwaggo Munari ta fahimta ganin yanda ta cize waje d’aya ta kasa tafiya. Cikin rad’a Gwaggo Munari ta ce da Bintu
‘’yo to ki ka cize nan Gimbiya kya iya wad’uwa ba ki sani ba, gide rufa mana asiri mu tai, ke kawai ki ta salati, hallo ka da ki kuskura ki kai kallan ki ga jama’a, hakan ka iya rud’a ki, maza soma ambaton Allah’’
Nan da nan Bintu ta tsinci kan ta ta na mai ambaton Ubangiji. Tsakiyar Uwanlenze da Gwaggo Munari, Jakadiya daga baya, biye da ita bayi goma shabiyu ne, su ka kutsa ta hanyar da aka tanada na musammam domin wucewar Gimbiya. Ba su zame koina ba sai cikin fadar Fabarusa.
Kansencewar Masarautar Fabarusa ta yi biyun ta Sa’ayrasa a girma da tsari, ba su Ladiyo ba, hatta Gwaggo Munari sai da ta yi da gaske wajan 6oye shawa’an ta ga Masarautar domin kuwa lokacin da su saka k'afar su a katafariyar fadar Fabarusa, sun ga abin mamakin gaske, wato bayan girman fadar na da ban al’ajabi, kuma yadda aka fasalta ko tsara ginin ta shi ma abin mamaki ne. A tak’aice sai da su ka zamo tankamar k’auyawan da su ka shigo birni. Gini ne irin na gargajiya wanda aka kafa harsashin ginin da manyan duwatsu ma su tsada, wad'an su kamu takwas wasu goma. Tsakanin kowace katanga akwai duwatsu masu tsada wad’anda aka yanka su bisa ga ma’auni san’annan aka dasa itacen al’ul daga gefan su. Tsuntsayen fada iri iri ke shawagi, musammam d’awisu da jin su ne su ka fi yawa.
Sai da su kusta sauro gomasha biyu kan su kai ga shiga cikin gidan Sarki, kowanne da na sa irin adon da kayan k’awa, wanda idan su ka shiga wannan su ka shiga na gaban sa sai su ka ashe na baya ba komai ba ne idan aka had’a sa da na gaban sa. 'Bangarn uwar gidan Sarki Abdulrahman, wacce ake kira Goggon nan aka sauke su. In da aka zaunar da Bintu bisa shimfid’a na musammam da aka ta na dar mata daga tsakiyar falo, yayinda su Ladiyo, Hansai, Lanta da Maman Cangwai su ka yi zaune daga gefe matsayin su na bayin Gimbiya.
Tuni Barori da Bayi su ka shiga kai kawo da hidima domin tarbar baki cikin aminci ta hanyar tabbatar da ba su bawa Masarautar su kunya ba. Kayan marmari na daga ‘ya’yan itace ne, nama na k’arama da babban dabba kai har da ma na d’awisu, su dubulan ne, caccabe, alkaki da nakiya komai bajau sai wanda jama'ar Sa’ayrasa su ka za6a. Gwaggo Munari na mai jinjina kai cikin ran ta take fad’in
‘’ma su abu da abun sa, gaskiya dukiya cikin wanga masarauta ba a cewa komai! D’iyar bayi ke kuwa Allah ya yankewa kakar saka, amre cikin wanga Masarauta shi an baiwa’’
Ciki su ka bud'e su ka ci su ka yi nak. Amma ita ko Bintu ruwa ma kasa sha ta yi bare ta kai ga cin abinci duk da kuwa azababban yunwa ne ya addabi cikin ta. Bayan an tabbatar su huta ne wata baiwa ta zo ta ce da su idan sun shirya za ta kai su ga masauk’in su domin Gimbiya Fatima ta shirya ta sami fitowa zuwa taron wankan amarya wanda za a yi nan ba da jimawa ba.
🐫🐪🐫🐪🐫🐫
[8/29, 9:30 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
8⃣
Sidiya ce.....✍🏼
Shiryayyan d’aki mai had’e da 6and'aki aka aje su Ladiyo, su Bintu kuwa d’aya daga cikin d’akunan Goggon nan a matsayin ta na uwar gida aka sauke su kan a gama wankan amarya a mik’a ta ga na ta 6angaran.
Su na shiga masaukin na su ba da jimawa ba, wata baiwa ta sake dawowa d’auke da kaya, gaban Bintu wacce ke zaune bisa gado har lokacin ba ta bud’e fuskarta ba baiwa ta zu6e, ta na mai aje kayan gaban ta, ta ce
‘’ an gaida Gimbiya Fatima, wagga kaya tsaraba ne da ga Goggo nan, ta ce a shedawa Gimbiya Fatima ta sanya su yayinda za ta hito wajan wankan amarya nan ba da jimawa ba’’
‘’Gimbiya Fatima ta amsa, ta na godiya’’
Cewar Gwaggo Munari. Bayan fitar baiwar Gwaggo Munari ta yaye alkyabbar Bintu, sai ga ta ta yi wuri wuri da ido.
‘’Gimbiya yanzun ga ba lokacin tuntuntuni ba ne, kin dai san dalilin da ya sa ki wanga Masarauta da kuma a gurbin wacce ki ka zo, gwara dai ki sake shawara ki nutsu in har ba so ki ke ki rasa ran ki sa’annan ki haddasa yaki da gaba wanda ka iya halaka ta mu Masarauta gaba d’aya’’