Sashe 2
Bintu Diyar Bayice Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘’Makara kam an riga an makara, saidai fa a jira bayan komai ya lafa a yiwa Takawa magana watakil shi bai zai rasa dabara ba.’’
Cewar Hajja Kilishi yayin da tashi tsaye jiki sanyaye, tak’ara da fadin.
‘’Kunsan mu na da baki, duk abinda za ku yi kada ku manta da martabar Takawa, ku kula ku kame kanku kada ku jawo mana abun da zai halaka yankin ga gaba d'aya’’
Ta na gama Magana ta juya abun ta ta fice, ta bar Inna Salti tare da Jakadiya cikin al’ajabi. Gimbiya Kamariyya gani ta ke sam Hajja Kilishi ba ta damu ba saboda ita dama ba ta ta6a haihuwa ba shi ya sa sam ba ta damu da lamarinsu ba. Ita kuwa Gimbiya Binta abinda ya tsaya mata a rai bai wuce na ta na murnar raba Bintu da masoyin a Aisar, sai gashi ta zama matar wanda har ta gama rayuwar ta a doran k’asa ba za ta sami kamar shi ba, abun takaici ta yiwa yar uwarta asarar masoyi, duk akan wanda sam be ma san ta nayi ba.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[8/14, 9:33 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
2⃣
Daga cikin masallacin Sa’ayrasa, ko da bawa ya tsinci kansa gaban Aisar, hannunsa damke cikin na sa yayinda yake jero masa tambayar da shi kansa bai ta6a jin ko da makamancin sunan ba a matsayinsa na bawan barga da kwananan ya dawo cikin sawun bayin da ke kula da lambu. Zufa ne ya shiga keto masa, cikin kame-kame da in’ina ya ce
‘’Eye? Na’am lillahi warasulihi wanga zoben tsintarsa na ka yi, idan kuwa na yi karya aratta kashe ni….’’
Maimaikon Aisar ya saki bawa sai dad’a damke hannu bawa yayi. Cikin neman d’auki bawa ya kai dubansa ga sauran yan tawagar na shugaban k’asa ya na mai neman d’oki. Hakan yasa Junaidu tausaya ma bawan duk da ko shakka babu ya san zoben hannun bawa mallakin d’an uwansa ne. Kana ya na mai shiga tsakanin bawa da Aisar ta hanyar ciro hannun Aisar daga cikin na bawa yayinda yayiwa bawa nuni da ya ciro zoben, nan da nan bawa ya ciro zoben, ya mik'awa Junaidu kai durkushe ya na mai fad’in
‘’Tuba na ke, aradun Allah tsinta na kai, ku min rai……’’
Nan bawa ya fashe da kuka, wanda hakan ba k’aramin dad’a kular da Aisar ya yi ba, ji yake kamar ya shek’eshi har sai ya matso gaskiya daga bakin bawan.
‘’Ka ga ba kuka za ka yi ba, babu abun da zai ma muddin ka fad’a masa gaskiya, shin in aka sami wanga zoben?’’
Cewar Junaidu ya na mai kok’arin saka idanunsa cikin na Bawa don gano inda bawa ya dosa. Shi kuwa bawa ya gama rikicewa sai rantse rantse kawai yake, fad’i yake
‘’Tsinta na ka yi, kwankwasi tsinta na ka yi a lambu, aradu tsinta na ka yi.’’
Jin an furta
‘’Ko shakka babu gaskiya ya ka fad’i, don na shedi wanga bawa mai gaskiya ne.’’
Gaba d’aya hankalinsu ya koma ga mai maganar. Sanye ya yake cikin bakar jamfa wanda aka masa ado da bakin zare, idan ka d’auke rawaninsa da yake fari komai na jikinsa bak'i ya sanya, kai kace wani taron bakin ciki ya halarta, ko da shike a nasa 6angaran hakan ta ke. Kallo d’aya Aisar ya masa ya d’auke kai ya na fad’in
'’A matsayinka na wa za mu k’ar6i shedanka?’’
‘’A matsayinsa na Yarima Nuhun Sa’ayrsa ranka shi dad’e.’’
Fad’in bawan da ke tafe da Yarima Nuhu kenan, ganin idan ba a yi dagaske ba yanda ran Yarima Nuhu ya ke a dak’ule komai mai afkuwa ne. Jin haka Junaidu ya bawa Yarima Nuhu hannu suka gaisa haka sauran yan tawagar amma ban da Aisar wanda idan ransa yayi dubu ya 6aci, don haka a kusa ya ke. Sanin hakan ne ya sa Junaidu yin saurin yiwa Yarima Nuhu bayani, ya na mai nuna ma sa zoben. Ganin zoben da kuma jin wanda Aisar ya ke tambaya Yerima Nuhu ya san ko shakka babu Bintunsa ta arziki a ke nema, zoben nan shine zoben da ya kar6a daga hannunta ya wulgar. Wato wannan shi ne Aisar d’in da yake soyayya da Bintunsa….
Bawan nan dai da ke tafe da Yarima Nuhu ne cike da ladabi ya furta
‘’A hakik’anin gaskiya wanga bawa ada bawan barga ne, be dad’e da dawowa sahun bayinmu masu kula da lambu ba, saboda haka ina mai tabbatar maka ba zai san wagga d’iyar bayi da ku ke magana akai ba, dan yanda alama ya nuna ko shakka babu ta na daga cikin bayin cikin babban gida tun da har aka iya tsintar zoben hannunta cikin lambu, haka nima da na ke bawan kofar gabas, ba mai yiyuwa ba ne na santa, domin kuwa ba mu da wata alak’a da zai had’amu da bayin cikin babban gida’’
‘’Shin ina za mu sami wagga d’iya?’’
Aisar ya tambaya ya na mai fatan samin mafita daga bakin bawa. Nan take bawa ya masa alk’awarin tayashi cigiyar Bintu nan ba da dad’ewa ba, sannan su ka sallami wannan bawa da zoben Bintu ke gareshi. Yarima Nuhu ya shaida mu su abinda ya kawo shi gare su, wato sheda ma su ana buk’atar su d’akin taro. Ya na gama shaida mu su yayi gaba dan kuwa yanzun da ya gane Aisar shi an samrayin da ya kwace zuciyar Bintu ya fi ma sa d’aci akan auren da aka d’aurawa Bintu a yau, dan wannan ya san ba mai d’orewa ba ne musammam idan aka yi la'akari da wanda aka d’aura mata.
Dakyar Junaidu ya lalla6i Aisar, sai da ya masa tuni da ba fa su kad’ai ba ne, akwai manya cikinsu, sun zo d’aurin aure ne bisa wakilcin shugaban k’asa ba wai hakan nan bak’akatan su ka zo ba, sannan ya samu ya d’an shawo kansa, ta hanyar masa alk’awarin bayan komai ya lafa Junaidu da kansa zai tsaya har sai sun samo Bintu kafin su juya gida, ko da kuwa hakan ya na nufin raba tafiya da tawagar ta su. Da wannan su ka yi tattaki zuwa d’akin taro ba tare da sun bari manya daga cikinsu sun fahimci abinda ke faruwa ba.
Yarima Barde kuwa da dabara Yarima Jafar da Khalil su ka ja shi mota, gaba d’aya ya zame mu su tamkar mutum mutumi, ya d’auke mu su wuta. Cikin mota sai da su ka d’au kusan rabin awa babu wanda ya iya furta komai.
Dogarin Masarautar Fabarusa ya zo ya buga musu kofa, nan ya zube ya na mai sheda mu su umarnin Sarki Abdulrahman na a ma su iso gareshi.
‘’Su na cikin masallacin ne?’’
Yarima Jafar ya tambaya, in da Dogari ya ba shi amsa da
‘’A'a, sun wuce ga d’akin taron masarauta tunda jimawa, Yarima kad’ai ake tsimayi ranka shi dad’e.’’
‘’Mu na nan tafe.’’
Cewar Khalil, yayinda Dogari ya tashi da sauri ya na fad’in
‘’A iso lafiya.’’
Yarima Jafar na duban Yarima Barde ya ce
‘’Ka bawa zuciyarka hakuri mu amsa kiran Mai Martaba’’
Ko kallonsa be yi ba bare ma ya nuna alamar ya san da shi ake, kamar an aje dutse. Ganin haka Khali ya ce da Yarima Jafar.
‘’Ka san halin Barde a sama ya ke, ina zaifi mu lalla6a mu je a dai ga fuskarshi, in ya so sai mu nemi izinin tafiya ta hanyar ba da uzirinmu ga Mai Martaba.’’
Da wannan shawara su ka fito daga motar, amma Yarima Barde fitowa ta ma sa wuya, sai da Yarima Jafar ya ma sa tuni akan wanda ya sa a yi kiransa sannan ya fito cike da k’asaita, dama shi idan ransa ya 6aci nan fa sarautar ta sa ke bunk’asa. Ko da dogarawan da ke tsimayinsu su ka ga fitowarsa tuni su ka rufa musu baya, zuwa d’akin taro, kai kace Sarki Abdulrahman na Fabarusa ne da kansa ke tafe.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
3⃣
Dakin taron ya cika fal da jama’a, tawagar Aisar da shigowar su ke nan, na su 6angaran na shugaban k’asa su ka zauna. Haka ma hakiman Sa’ayra da Fabarusa, Agadez, Diffa da sauran Hakiman yanki da sassa na jamhuriyar Nijar wajan su na musammam su ka zauna. Haka kuma yankin Sarakuna wanda Sarkin Sa’ayrasa mai gayya mai taro ya hakimce, kusa da shi kuma Sarkin Fabarusa ne zaune cikin aminci. Hakan ba k’aramin farantawa jama’a rai yayi ba, wai ashe dai akwai ranar k’arshen gaba tsakanin Sa’ayrasa da Fabarusa? Shin dama akwai rana irin ta yau da za a ga Sarakunan wanga yanki zaune cikin aminci?
Busa na alkgaita ke tashi daga waje, jama’ar Sa’ayrasa kwan su da kwarkwatar su sun yi dandazo cikin d’akin taro, murna gun su ba a cewa komai domin kuwa a yau yunwa zai kau a k’asar su. Ganin shigowar su Yarima Barde tuni dogarai su ka hau yiwa ango kirari. Shi kuwa Yarima Barde sam ba cikin hayyacin sa ya ke ba, amma in aka d’auke Yarima Jafar da Khalil wanda dama sun san halin da abokin na su ya ke ciki babu wanda zai kalle shi ya ce ya na cikin wani hali, sai dai ma ayi tsammanin tsabar sarauta da miskilanci ne yake d’ibar sa.
Cewar Hajja Kilishi yayin da tashi tsaye jiki sanyaye, tak’ara da fadin.
‘’Kunsan mu na da baki, duk abinda za ku yi kada ku manta da martabar Takawa, ku kula ku kame kanku kada ku jawo mana abun da zai halaka yankin ga gaba d'aya’’
Ta na gama Magana ta juya abun ta ta fice, ta bar Inna Salti tare da Jakadiya cikin al’ajabi. Gimbiya Kamariyya gani ta ke sam Hajja Kilishi ba ta damu ba saboda ita dama ba ta ta6a haihuwa ba shi ya sa sam ba ta damu da lamarinsu ba. Ita kuwa Gimbiya Binta abinda ya tsaya mata a rai bai wuce na ta na murnar raba Bintu da masoyin a Aisar, sai gashi ta zama matar wanda har ta gama rayuwar ta a doran k’asa ba za ta sami kamar shi ba, abun takaici ta yiwa yar uwarta asarar masoyi, duk akan wanda sam be ma san ta nayi ba.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[8/14, 9:33 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
2⃣
Daga cikin masallacin Sa’ayrasa, ko da bawa ya tsinci kansa gaban Aisar, hannunsa damke cikin na sa yayinda yake jero masa tambayar da shi kansa bai ta6a jin ko da makamancin sunan ba a matsayinsa na bawan barga da kwananan ya dawo cikin sawun bayin da ke kula da lambu. Zufa ne ya shiga keto masa, cikin kame-kame da in’ina ya ce
‘’Eye? Na’am lillahi warasulihi wanga zoben tsintarsa na ka yi, idan kuwa na yi karya aratta kashe ni….’’
Maimaikon Aisar ya saki bawa sai dad’a damke hannu bawa yayi. Cikin neman d’auki bawa ya kai dubansa ga sauran yan tawagar na shugaban k’asa ya na mai neman d’oki. Hakan yasa Junaidu tausaya ma bawan duk da ko shakka babu ya san zoben hannun bawa mallakin d’an uwansa ne. Kana ya na mai shiga tsakanin bawa da Aisar ta hanyar ciro hannun Aisar daga cikin na bawa yayinda yayiwa bawa nuni da ya ciro zoben, nan da nan bawa ya ciro zoben, ya mik'awa Junaidu kai durkushe ya na mai fad’in
‘’Tuba na ke, aradun Allah tsinta na kai, ku min rai……’’
Nan bawa ya fashe da kuka, wanda hakan ba k’aramin dad’a kular da Aisar ya yi ba, ji yake kamar ya shek’eshi har sai ya matso gaskiya daga bakin bawan.
‘’Ka ga ba kuka za ka yi ba, babu abun da zai ma muddin ka fad’a masa gaskiya, shin in aka sami wanga zoben?’’
Cewar Junaidu ya na mai kok’arin saka idanunsa cikin na Bawa don gano inda bawa ya dosa. Shi kuwa bawa ya gama rikicewa sai rantse rantse kawai yake, fad’i yake
‘’Tsinta na ka yi, kwankwasi tsinta na ka yi a lambu, aradu tsinta na ka yi.’’
Jin an furta
‘’Ko shakka babu gaskiya ya ka fad’i, don na shedi wanga bawa mai gaskiya ne.’’
Gaba d’aya hankalinsu ya koma ga mai maganar. Sanye ya yake cikin bakar jamfa wanda aka masa ado da bakin zare, idan ka d’auke rawaninsa da yake fari komai na jikinsa bak'i ya sanya, kai kace wani taron bakin ciki ya halarta, ko da shike a nasa 6angaran hakan ta ke. Kallo d’aya Aisar ya masa ya d’auke kai ya na fad’in
'’A matsayinka na wa za mu k’ar6i shedanka?’’
‘’A matsayinsa na Yarima Nuhun Sa’ayrsa ranka shi dad’e.’’
Fad’in bawan da ke tafe da Yarima Nuhu kenan, ganin idan ba a yi dagaske ba yanda ran Yarima Nuhu ya ke a dak’ule komai mai afkuwa ne. Jin haka Junaidu ya bawa Yarima Nuhu hannu suka gaisa haka sauran yan tawagar amma ban da Aisar wanda idan ransa yayi dubu ya 6aci, don haka a kusa ya ke. Sanin hakan ne ya sa Junaidu yin saurin yiwa Yarima Nuhu bayani, ya na mai nuna ma sa zoben. Ganin zoben da kuma jin wanda Aisar ya ke tambaya Yerima Nuhu ya san ko shakka babu Bintunsa ta arziki a ke nema, zoben nan shine zoben da ya kar6a daga hannunta ya wulgar. Wato wannan shi ne Aisar d’in da yake soyayya da Bintunsa….
Bawan nan dai da ke tafe da Yarima Nuhu ne cike da ladabi ya furta
‘’A hakik’anin gaskiya wanga bawa ada bawan barga ne, be dad’e da dawowa sahun bayinmu masu kula da lambu ba, saboda haka ina mai tabbatar maka ba zai san wagga d’iyar bayi da ku ke magana akai ba, dan yanda alama ya nuna ko shakka babu ta na daga cikin bayin cikin babban gida tun da har aka iya tsintar zoben hannunta cikin lambu, haka nima da na ke bawan kofar gabas, ba mai yiyuwa ba ne na santa, domin kuwa ba mu da wata alak’a da zai had’amu da bayin cikin babban gida’’
‘’Shin ina za mu sami wagga d’iya?’’
Aisar ya tambaya ya na mai fatan samin mafita daga bakin bawa. Nan take bawa ya masa alk’awarin tayashi cigiyar Bintu nan ba da dad’ewa ba, sannan su ka sallami wannan bawa da zoben Bintu ke gareshi. Yarima Nuhu ya shaida mu su abinda ya kawo shi gare su, wato sheda ma su ana buk’atar su d’akin taro. Ya na gama shaida mu su yayi gaba dan kuwa yanzun da ya gane Aisar shi an samrayin da ya kwace zuciyar Bintu ya fi ma sa d’aci akan auren da aka d’aurawa Bintu a yau, dan wannan ya san ba mai d’orewa ba ne musammam idan aka yi la'akari da wanda aka d’aura mata.
Dakyar Junaidu ya lalla6i Aisar, sai da ya masa tuni da ba fa su kad’ai ba ne, akwai manya cikinsu, sun zo d’aurin aure ne bisa wakilcin shugaban k’asa ba wai hakan nan bak’akatan su ka zo ba, sannan ya samu ya d’an shawo kansa, ta hanyar masa alk’awarin bayan komai ya lafa Junaidu da kansa zai tsaya har sai sun samo Bintu kafin su juya gida, ko da kuwa hakan ya na nufin raba tafiya da tawagar ta su. Da wannan su ka yi tattaki zuwa d’akin taro ba tare da sun bari manya daga cikinsu sun fahimci abinda ke faruwa ba.
Yarima Barde kuwa da dabara Yarima Jafar da Khalil su ka ja shi mota, gaba d’aya ya zame mu su tamkar mutum mutumi, ya d’auke mu su wuta. Cikin mota sai da su ka d’au kusan rabin awa babu wanda ya iya furta komai.
Dogarin Masarautar Fabarusa ya zo ya buga musu kofa, nan ya zube ya na mai sheda mu su umarnin Sarki Abdulrahman na a ma su iso gareshi.
‘’Su na cikin masallacin ne?’’
Yarima Jafar ya tambaya, in da Dogari ya ba shi amsa da
‘’A'a, sun wuce ga d’akin taron masarauta tunda jimawa, Yarima kad’ai ake tsimayi ranka shi dad’e.’’
‘’Mu na nan tafe.’’
Cewar Khalil, yayinda Dogari ya tashi da sauri ya na fad’in
‘’A iso lafiya.’’
Yarima Jafar na duban Yarima Barde ya ce
‘’Ka bawa zuciyarka hakuri mu amsa kiran Mai Martaba’’
Ko kallonsa be yi ba bare ma ya nuna alamar ya san da shi ake, kamar an aje dutse. Ganin haka Khali ya ce da Yarima Jafar.
‘’Ka san halin Barde a sama ya ke, ina zaifi mu lalla6a mu je a dai ga fuskarshi, in ya so sai mu nemi izinin tafiya ta hanyar ba da uzirinmu ga Mai Martaba.’’
Da wannan shawara su ka fito daga motar, amma Yarima Barde fitowa ta ma sa wuya, sai da Yarima Jafar ya ma sa tuni akan wanda ya sa a yi kiransa sannan ya fito cike da k’asaita, dama shi idan ransa ya 6aci nan fa sarautar ta sa ke bunk’asa. Ko da dogarawan da ke tsimayinsu su ka ga fitowarsa tuni su ka rufa musu baya, zuwa d’akin taro, kai kace Sarki Abdulrahman na Fabarusa ne da kansa ke tafe.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
3⃣
Dakin taron ya cika fal da jama’a, tawagar Aisar da shigowar su ke nan, na su 6angaran na shugaban k’asa su ka zauna. Haka ma hakiman Sa’ayra da Fabarusa, Agadez, Diffa da sauran Hakiman yanki da sassa na jamhuriyar Nijar wajan su na musammam su ka zauna. Haka kuma yankin Sarakuna wanda Sarkin Sa’ayrasa mai gayya mai taro ya hakimce, kusa da shi kuma Sarkin Fabarusa ne zaune cikin aminci. Hakan ba k’aramin farantawa jama’a rai yayi ba, wai ashe dai akwai ranar k’arshen gaba tsakanin Sa’ayrasa da Fabarusa? Shin dama akwai rana irin ta yau da za a ga Sarakunan wanga yanki zaune cikin aminci?
Busa na alkgaita ke tashi daga waje, jama’ar Sa’ayrasa kwan su da kwarkwatar su sun yi dandazo cikin d’akin taro, murna gun su ba a cewa komai domin kuwa a yau yunwa zai kau a k’asar su. Ganin shigowar su Yarima Barde tuni dogarai su ka hau yiwa ango kirari. Shi kuwa Yarima Barde sam ba cikin hayyacin sa ya ke ba, amma in aka d’auke Yarima Jafar da Khalil wanda dama sun san halin da abokin na su ya ke ciki babu wanda zai kalle shi ya ce ya na cikin wani hali, sai dai ma ayi tsammanin tsabar sarauta da miskilanci ne yake d’ibar sa.