← Book details Bintu Diyar Bayice Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 16

Sashe 7

Bintu Diyar Bayice Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya sake kiran sunan ta a karo na biyu, maimakon ta amsa, kawai sai ta sa ma sa kuka, ya rasa yanda zai yi da ita dan kuwa Barde sam be iya rarrashi ba. Ta d’au lokaci mai tsayi ta na rera kuka gaban sa, tin ya na iya ba ta baki, har ya mata shiru dan kuwa shi dama Magana wahala ta ke masa. Sai da ta yi shiru dan kan ta, sannan ya dube ta, kana ya ce

‘’ban san kud’irin mahaifina ba, sai bayan da bakin alk’alami ya bushe, sai da aka d’aura min amre da kauna gun ki Fatima….’’

Jin haka Gimbiya K’amariyya ta kai duban ta gare shi, ta ga ya k’ara ma ta kyau da kwarjini na kwaran gaske, wai kuma an d’aura ma sa Bintu! Bintu dai d’iyar bayi! Ji ta yi kamar ta bud’e baki ta fad’a masa gaskiya komai ta fanjama fanjam, tunawa da ta yi da na ta Mahaifin ya sa ta a dole ta na ji ta na gani ta yi shiru, babu mamaki shi ya na da wani shiri ne na daban. Murya na rawa ta ce

‘’ina cikin damuwa Yarima, ina mafita?’’

Kallan ta yake na wasu dak’ikai, kafin daga bisani ya saki ajiyar zuciya mai karfi gami da sauke kafad’a, kana ya ce

‘’Allah shi ne mafita, shi za mu kai kukan mu gare shi, hallo bana yiwa Mahaifina musu, ban ta6a ba K’amariyya shi ya sa ma ki gaya aiwatar da wanga lamari ba tare da ya tuntu6e niba, yanzu ban da tsumi hallo ba dabara, amma ina so ki sani ina son ki, kwaran gaske’’

Cikin hawaye K’amariyya ta ce

"me zai hana ka sanar da Mahaifin ka gaskiya kamar yanda na sanar da nawa Mahaifin?’’

‘’ban da wannan ikon K’amariyya, da ina da shi da tuni na aiwatar da hakan’’

Cewar Yarima Barde ya na amai girgiza kai. Nan Gimbiya K’amariyya ta fusata, ta tashi da sauri za ta fita. Yarima Barde ma tashin ya yi, ya dakatar da ita ta hanyar fad’in

‘’kar ki yi fushi K’amariyya, kunar za ta min yawa, badan wacce aka d’aura min jinin ki ba ce kuma kauna gun ki da na ce duk duniya babu wacce na tsana face ita, sam ba za ta sami kulawa bare wani abu wai soyayya daga gare ni ba saboda soyayyar ki, hallo babu yanda zan yi dole haka zan zauna da ita har Allah ya kawo karshen zaman, dan darajar Mahaifan mu da Masarautun mu’’

Kallan sa ta ke yayinda hawaye ke gudana daga idanun ta, a hankali ta furta
‘’ina ma ka fatan alkhairi Yarima Badde’’

Sannan ta juya a hankali ta na ficewa. Tsayawa yayi ya na kallan ta yayinda ta ke ficewa daga rayuwar sa, idanun sa sun yi jajur, ji yayi k’afafun sa sun kasa d’aukar gangan jikin sa, a hankali ya zauna zuciyar sa cike da tunanin yanda rayuwar sa ta sauya a wuni d’aya. Shi ba mutum ba ne mai san mata, mata ne ma ke san sa da bibiyan sa. Tin da Allah ya had’a shi da Gimbiya K’amariyya, ita ce mace ta fari da ya ji ya na kauna zai kuma iya aura. Amma yau gashi an ma sa Katanga da ita ta hanyar aura ma sa kanwar ta. Yatsun sa ya tusa cikin sumar kan sa sanadiyar sarawa da ya ji kan sa na yi, ya na fad’in

‘’lahaula walakuwata illa billah!’’

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

Khadija Sidi..✍🏼

6⃣

Ko da Gimbiya K’amariyya ta koma d'akin ta, sai ta sallami bayin ta gaba d’aya sannan ta kulle d’akin ta haye tsakiyar gado ta na rusa kuka. Bintu kuwa d’akin Hajja Kilishi bayi ke jera kaya da aka d’inka ma ta na alfarma, yayinda Hajja Kilishi ta sa ta gaba sai bayani iri-iri ta ke mata akan kayan da kuma yanda za ta na amfani da su, da yanda ake son zaman na ta ya kasance a fadar Fabarusa kasancewar Sarki ya janye makwanin biyun da ya kamata a kai Bintu ga Masarautar Fabarusa.

Bintu da ba cikin hayyacin ta ta ke ba, babu abun da ta gane kawai dai amsa ma ta ‘’um’’ ta ke. Da wuri Hajja Kilishi ta bawa Bintu umarnin kwanciya saboda sammakon da za su yi a washagari. Yanda ta ga rana haka ta ga dare, haka ta kwana cikin zulumi sai da asuba wani bacci mai nauyi ya sace ta.

Ba ta jima ta na bacci ba, Hajja Kilishi ta aiko d’aya daga cikin Bayin da aka bawa Bintu, wato Ladiyo ta tada ita gudun kada su makara. Nan ta ke tseguntawa Bintu cewar Gimbiya Binta har ta wuce Nigeria makaranta bisa ga umarnin Takawa. Kuka Bintu ta saka ta na mai fad’in

‘’Na shiga uku ni Bintu, wallahi ni Bintu na ke ba Binta ba, d’iyar bayi na ke ba d’iyar Sarki ba, ashe dai ba zan kammala makaranta ta ba, wayyo Inna ki zo ki taimake ni na shiga uku na lalace!’’

Da ladiyo ta ga haka, kawai sai ta fice, jim kad’an sai ga ta dawo biye da ita Hajja Kilishi ce rai 6ace. Tuni ta hau Bintu da fad’a, ta na fad’in

‘’Wai ashe ba ki da tawassali Fatima? Ba ki yarda da k’addara ba? Idan ba ki fasa kuka ba ba ba ki nuna mana ba a isa da ke ba’’

Jin wanna kalame na Hajja Kilishi tuni Bintu ta shiga taitayin ta, sai ajiyar zuciya ta ke kawai. Hajja Kilishi ba ta gushe ba ta cigaba da maganar ta kamar haka

‘’Ki d’au kaddara ki yi fata Allah ya sa hakan shi an alhairi gare ki, yoto ai alkhairin ne ma. Ina ke ladiyo ?’’
Ladiyo ta matso kusa tare da fad’in

‘’Ran ki shi dad’e’’

‘’Maza ku shiga bayan gida ku had’o mata ruwan wankan amare’’

Cewar Hajja Kilishi.
‘’An gama ran ki shi dad’e’’

‘’Ke kuma Hansai maza shirya kayan Gimbiyar ta ku, Ina Maman Cangwai ne? maza ku sheda mata ta ta kawo maganin d’ar nan da lalle domin yiwa amarya wankan lalle’’

Hansai na mai duk’ar da kai ta ce

‘’Ranki shi dad’e ai tuni Maman Cangwai na can rariya, fitowar Bintu kawai ake jira......’’

‘’Bintu ki ka ce!!’’

Hajja Kilishi ta daka ma sa tsawa. Hansai ta zube k’asa jiki na 6ari ta ke fad’in

‘’Tuba na ke ranki shi dad’e, na tuba ran ki shi dad’e ki min rai aradu na tuba’’

‘’Kwarankwatsi ki na rasa ran ki muddi ki ka kuskure asirin Masarautar ga tonu sanadiyar kuskure irin wang, shasha kawai, me an sunan Gimbiyar ga?’’

Hajja Kilishi na magana ne a hasala kamar mai shirin bugun Hansai. Ita kuwa Hansai idanun ta ke kawo ruwa.

‘’Gimbiya Bintu.....’’

‘’Gimbiya Fatima, ban yarda kin kira ta Bintu ko Binta ba!’’

‘’An gama ran ki shi dad’e, godiya na ke’’

Cewar Hansai. Allah Allah ta ke Hajja Kilishi ta sallame ta ko ta sami sarari. Jin Hajja Kilishi ta ce ta yi maza ta idda umarnin da aka ba ta, Hansai ta tashi da sauri ta fice. Kan ace me? Tuni aka shiga hidimar shirya Bintu, sai ga ta ta fito tsaf da ita cikin fararan tufa tun daga sama har k’asa. Hajja Kilishi ce ta d’auko wani dank'areriyar sark’a na gwal tare da yari da warwaro ta ce a sanyawa Bintu na ta gudunmawar kenan. Haka ma Inna Salti ta turowa Bintu goma ta arziki, ciki har da farrar god'iya. Sauran matan Sarkin ma suma ba a bar su baya ma, sai da su ka yi tattaki domin
nuna bacintar su dan kuwa abu na kishiyoyi sai da ya so ya zama gasa.

Rana ba ta k’arya, sai ga shi ana fitar da kayan Bintu zuwa motocin da ke jere domin kai amarya ga Masarautar Fabarusa, yayinda dattijiwar da ta zo amsar amarya, me suna Uwalanze ke zaune ta na jira. Wasu dattijai mata guda biyu, wanda su ke tamkar kakanni wajan su Gimbiya K'amariyya ne bisa ga al’ada su ka zo raka Bintu wajan Sarki domin su yi sallama a matsayin Mahaifin ta, sannan su damk’a ta ga mutan Fabarusa.

Bintu na ji ta na gani su ka sa ta tsakiya, gud’a ke tashi su kuwa tsofi fad’i su ke

‘’Allah Ya ba da sa’ar tafiya Gimbiya Binta, Allah ya sa a dace d’iyar arziki’’

Ba su zame ko ina ba sai turakar Sarki, in da su ka tadda Jakadiya tsaye bakin k’ofa ta na jira. Da isar su ta mu su iso zuwa gaban Sarki da ke daman abun da ta ke jira kenan. Gaban Sarki su ka aje Bintu dan idan aka d'auke dattijiya mai suna Gwaggo Munari cikin su, duk a na su zatan Gimbiya Binta ce. Sai da su ka kai gaisuwar su ga Sarki sannan su ka juya su ka bawa Sarki waje domin su gana da d’iyar sa.

Murya na rawa Bintu ta furta

‘’Barka da safiya ran ka shi dad’e’’

Shiru be iya amsawa ba, tsabagen tausayin Bintu da ya ji ya lullu6e shi, gami da nadamar hukuncin da ya aikata bisa ga san zuciya. Daga bisani ya nisa tare da fad’in

‘’Da wata murya za mu amsa mi ki Fatima? Da wata murya za mu amsa mi ki d’iyar arziki? Da wani baki za mu amsa mi ki wanga d’iya da ke gaban mu? Yau mun yi kad’an mu amsa gaisuwar wagga d’iya, wacca jama’a su ka ku6uta da ga yunwa saboda ita. Sanadiyyar wagga d’iya, mutan Sa’ayrasa na godiya gare mu, mu kuma godiyar mu gare ki ya ke, Allah ya saka mi ki da alkhairi sa’’

Shiru ya yi na d’an wani lokaci sannan ya cigaba
Chapter 7 · 0% Book details