← Book details A Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 80

Sashe 44

A Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shadda
Laces
Atamfa
Kayan yara English wears dana jarirai
Qawatattun handbags
Mayafai
Abayas da jallabiyas
Inner wears
Huluna na maza da mata yara da manya socks
Takalma na maza da mata yara da manya
Lafayas
Sarqoqi agoguna banguls da rings

_kai komai daya danganci kayan ado na fita kunya wa dan adam_

_bisa farashin da zaiyi daidai da buqatarka_

*_Me kike jira sallah na gabatowa?,ana can ana ruwan suturu daidai da qarfin kowa?_*

*_masu manyan qarfi da matsakaita?_*

*_ki dinga siya da kadan kadan kina saka kudin kina tara abinki har sukai sanda zaki karba?,ko ki siya lokaci daya a kai miki_*

*_muna aika kaya ko ina a duniya in sha Allah_*

*MUNA BONONZA LOKACI LOKACI NA DUKA ABINDA RABO YA TSAGA*

*_MASU REPOSTING DA MASU SARI DUKA BA'A BARSU A BAYA BA,KI SIYA KI SAIDA KI SAMU RIBARKI HANKALI KWANCE,BA TARADDADIN INGANCIN KAYA KO WANDA KIKA BAIWA KUDINKI_*

*_KIYI JOINING KI TURAWA 'YAN UWA DA ABOKAN ARZIQI_*

*_INGANCI RAHUSA GASKIYA DA AMANA SHINE TAKENMU_*🫶🏽🫶🏽✌🏽✌🏽✌🏽✌🏽
__________________________

Yana da matuqar karsashi da qarfin zuciya......da kuma fuskantar dukkan wani goal nashi har sai ya cimmasa ya kaishi qasa. Baya taba bari buri tsoro ko fargaba suyi masa iyaka ko shamaki......faduwa kuma bata sanyashi yayi giving up,wannan shine sirrin nasarar da kullum yake dada samu.

Za'a iya cewa kai tsaye farouq hannun damanshi ne,don haka ba wani motsi ko mission nasu da dayan bai ganewa koda bai gayawa daya ba,duk da cewa ma babu boye boye gaba daya a tsakaninsu. Wannan ta sanya farouq ya jima da fuskantar fu'ad,idan magana kake ta aure ko soyayya to kada ma ka fara kiran sunanshi a ciki,domin baya gane komai ta wannan bangaren. Yakan jima yana dubansa cikin mamaki,ya bawa kasuwancinsa lokacinsa da rayuwarsa fiye da komai baya ga familynsa,wato shi sadiq musaddiq anni da abba,kullum lissafinsa da target dinsa moving forward.....moving to the next step. A hankali ya fara zolayarsa don gane gejin yadda idanunsa basa gane kowacce halitta da ake kira da DIYA MACE,sai ya sake karatun nasa da kyau yadda ya kamata,har daga qarshe ranar yakai kusan biyu na dare saman system yana duba wasu sabbin diamond da aka samu nasarar cirowa,yadda zasu sarrafashi da kuma kamfani mafi dacewa da zasu kai.

Shi kam har yayi bacci ma kai na biyu ne,ya fito main parlor na sassansu ya sameshi zaune dungurgur saman sofa yana fama da zazzafan coffee don hana idanunsa kamuwa da bacci. Farouq din da mamaki yake kallonsa,saidai baice masa komai ba har sai da yaje fridge ya ciro ruwa me sanyi ya dawo gefansa ya zauna

"Sannu bawan kasuwanci" Ya fada cikin gatse,gatsen da bai damu fu'ad ba saima maida idanunsa kan ruwan hannun farouq din da yayi. Har ya dauke idanunsa kamar bazai magana ba cikin dabi'ar nan tasa ta shariya da banzatar da abu,sai kuma ya dawo da dubansa kanshi.

"Kana da jarabar son aure.....amma kana kashe kanka da abubuwan banza da wofi.....kana namiji me yake hadaka da kayan zaqi da sanyi?" Yayi masa tambayar fuskarsa a hade yana duban idanunshi.

Qaramar dariya farouq din ya saki yana qoqarin bude gorar hannunsa

"Kasan me?,nifa bazan iya rayuwar da kakeyi ba,duk wani abu me dadi ka haramtawa kanka ci sai d'ai d'aiku,ka tattaro abubuwan da sam basu da dadi ko dandano a harshe kullum dasu kake mu'amala......yanzu kalla don Allah" Ya fada yana nuna tray din gaban fu'ad da awannin baya kadan ya gama amfani dashi.

"Gasashen zaitun.....hadin salad me man zaitoon,shayin ginseng,wolf Berry smoothie.....meye mai dadi a ciki?" Ya fada yana yamutsa fuska.

Idanu kawai fu'ad ya zuba masa har yakai qarshen zancan. A nutse ya saki wani qaramin murmushi da bai bayyana ba yana dauke idonsa daga kan farouq

"Dukka abinda ka lissafa yanxun kaje kayi binciken amfaninsa ga jiki da lafiya" Ya amsa masa yana jawo wata takarda dake aje a gefansa yana son hadesu waje daya da stapler.

Kai ya girgiza yana tabe baki

"Wanne amfani zan tsaya dubawa abinda basu da dandano ko kada......kaifa a taqaice ko?,bakasan meye dadi ba kwata kwata wallahi"

"Tashi don Allah ka tafi mr ciye ciye karka cikamin kai da bayanai.....kaci gaba da ciye ciyenka yadda kake da hazaqar son kayi aure,auren zai baka amsarka". Dariya ta kubcewa farouq din harda buga qafa tamkar ba dare ba

" To mijin aljana.....don dai na tabbatar zaiyi wahala kaidai idan aka kira me ruqiyya yayi maka ruqiyya inajin mata hudu gareka cikin jinsin aljanu".

Duk yadda yakai ga pressure dinsa hade rai ko salon miskilancinsa farouq kadai ke saukeshi. Ya addabeshi wasu lokutan har yaji kamar ya makeshi amma ba yadda ya iya dashi,don kaf duniya baya gashi ba wanda yake masa karan tsayen da yake masa irin haka. Ko a yanzun ma sai da yayi silar fitar murmushi daga kyakyawar fuskarsan nan ma'abociyar tsukewa da ba kasafai ta fiya fidda fara'a

"Kaga bakina alaikum na huta ai.....don wadannan matan na bil'adama......." Sai kuma yayi shuru ba tare da ya qarasa fade ba. Ba kasafai ya fiya son tona abinda ke danqare a zuciyarsa ba,baisani ba ko Allah ya nufeshi da rahama daya zare son aure ko son mallakar mace kwata kwata daga zuciyarsa ba?.

Dan kadan farouq ya kalleshi ta gefan idanu ganin ya dauko magana ya kuma katseta,sai shima yayi shuru kawai bai sake cewa dashi komai ba.

Tun daga wannan lokaci idan yaso masa tsiya da shaqiyanci yakan kirashi da mijin aljana. Anni tayi tayi ya daina amma ina,lamarin farouq sai a hankali,mugun shakiyyi ne idan yaso,idan kuma ya sakaka a gaba ka saku kenan......amma kuma tamkar hawainiya yake,idan yaso canzawa zaka rantse da Allah bashi bane matsokanin nan ba.

Kusan a tare suka amsa sallamar farouq din

"Kana nan dama?" Farouq din ya fada sanda ya qaraso dining din yaja kujera dake tsakiyarsu ya zauna yana tattare long sleeve din shirt din jikinsa sama.

"Yana nan sunatayi shi da mutuniyar" Anni ta bashi amsa tana dariya qasa qasa.

Baki ya tabe yana bubbude warmer din dake jere kan dining din

"Wannan autar taki anni taci kai wallahi.....wai ita an gaya mata zama zamuyita yi da ita a gidan nan?,baka gaya mata gaskiya wallahi" Ya qarasa maganar yana duban fuskar musaddiq cikin salo na harara.

Dariyar ta kubcewa musaddiq ya kalleshi da kyau yana daidaita zamansa idonsa akan farouq

"Yanzu don Allah BB(big brother suke masa abbreviation),so kake ayita kada mata hanjin ciki?,duka duka amna nawa take?"

"Allaaaaahu akhbar.....kaga masuyi don Allah,dama kana cikin masu lalatata a gidan nan......don Allah kayita gaya mata damu zata rayu.....Allah ka sakata ne kawai a keken bera......itafa har yanxu bata da hankali na lura......na godewa abba ma da yace sai taje ta raka nanna......tafiya duka duka sati biyu kawai amma ta cika mutane da qorafin yhan yhan yhan......itafa gida zata dawo waye ya mutu waye ya tashi.....shi kuma wancan mijin aljanar yana can yana sake daure mata qarqashi...."

"Farouq?" Anni ta tsaidashi tana dubansa

"Sunan nan bazai fita a bakinka ba ko?" Ta sake jefa masa tambayar tana dubansa.

Gyara zamansa yayi yana wani tsuke gira,shi ala dole yana son zama serous.

"Allah dai ya bada haquri anni......amma shima ai anni ba sunan da yafi dacewa dashi sai wannan.....banga alamar lafiyarsa qalau ba" Ya qarasa fada qasa yana fara serving kanshi da abincin da yafi so. Idanu anni kawai ta tsura masa tana kallonsa ba tare da tace komai ba,ita kanta yadda fu'ad keyi da lamarin yana tabata,ko a fuska ko kuma a aikace bai taba damuwa da ganin dukansu su ukun suna shirin yin aure ne su barshi ba,yana shiga dashi akayi dukka maganganun da zaayi da iyayen yara,amma shi yana zaune ba wani damuwa a gabanshi,saima lissafin yadda zaici gaba da juya kwabo ta koma dari.

"Kaga MAN.....ka koma gaya mata gaskiya,aurar da ita zamuyi da wurwuri.....ba zancan yin PHD a gidan nan.....munason ganin jikokin 'yar uwarmu mace". Daga anni har musaddiq ba wanda farouq din bai bawa dariya ba ganin yadda yayi maganar da gasken gaske har yana tabo hannun musaddiq din don ya jishi da kyau,ya kuma basar ya soma cin abincinsa.

Na anni kawai idanu,tana tsarkake girman ubangiji da yadda yake halittar bayinsa da mabanbantan dabi'u da kuma halaye. Yara hudu,mace cikon ta biyar amma kowanne da nasa halin da dabi'ar. Ta sauke boyayyar ajiyar zuciya kunnuwanta suna sauraren hirarrakinsu. Bahaushe yayi gaskiya da yake cewa DA D'A DA DUKIYA BA'A YI MUSU MUGUNTA,DON BA'ASAN ME MORARSU BA SAI ALLAH. tana tuna wani lokaci can baya.....shekaru da suka shude,sanda ta tsoma qafafunta da sunan kome gidan tsohon mijinta alhaji hamza. Yadda tasha baqar wuya kafin ta daidaita lamuran gidan ta kuma maida kowa cikin hayyacinsa. Me babban suna tafi shan wuya akansa akan kowa,tasha gwagwarmaya kafin ta samu nasarar cire wannan fushin baqin rai da kuma mummunan fenti da ya yiwa kusan kowa da yake kewaye dashi idan ka dauke 'yan gidan nasu. Rashin yarda da rashin sakewa da jama'a wanda har yanzu tana fuskantar ragowa da kuma tasirin wannan dabi'ar tattare dashi da bata gama barin jikinss ba. Wani irin yanayi me ban tausayi da har yaso taba karatunshi.....boyayyen kuka duk dare da rashin bacci. Ta dauki dogon zango cikin musu addu'a da neman daidaitar rayuwarsu. Tofi rubutu da addu'a dukka kafin lamuransa su fara daidaita. Sai ta fuskanci kyara tsangwama ga duk macen da zata dososhi koda qanqanuwar yarinya ce. Bata fuskanci yadda abun yayi musu!mugun tasiri ba sai bayan wasu shakaru data haifa musu Aminatu amna me sunanta kenan.....haihuwar data tabbatar matsanancin rabo ne,don ko a wasa bata taba tunanin wai zata sake wata aba wai ita haihuwa ba.

Da fari tsakaninsa da amna idanu ne kawai,baya ma zama.inda take bare daukarta,ta fahimci kaman wata kakkaifar gaba ce tsakaninsa da jinsin mata,ita kadaice mace cikin miliyoyin mata da take samun kulawa da qauna daga gareshi wanda ita dinma sai da suka debi shekaru yana dari dari da ita. Bata tsananta tuhuma ba,tasan incident din daya faru dashi a baya akan mariya da mariya sune suke hunting dinsa.
Chapter 44 · 0% Book details