← Book details A Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 80

Sashe 41

A Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Mazan bariki dama suna auren macen da suka hadu da ita a bariki?,ai saidai su tsotseta tas.....su musaya wannan zaqin da gardin da suka samu daga gareta da 'yan kudaden da zasuyita mata barinsa......daga sanda buqata kuma ta biya su tattarata su watsar su qara gaba zu zabi wata". Sai ta tuna maganar da sukayi taba yi da bibo wadda ke kamaceceniya da kalmomin maleeka roommate dinta. Juyi tayi kadan saman gadon,tana da burika masu tarin yawa akan karatunta,wannan ya sanya ta sadaukar da rayuwarka akanshi. Tana so ta ganta tana fantamawa,tanason ta ganta tana haskawa tamkar sabreen da dukkan wani alatu da jin dadi......tanaso taga maza suna mutuwa a kanta sama da sabreen......amma dukka ta hanyar karatunta da kyawun sura da Allah ya bata. Tana cikin sahun jerin farko farko da 'ya'ya masu kyau a gidan......ta tabbata ko wannan ya isheta jari wajen zaben kalar mijin da take buri da muradi idan aka qara da karatunta da takesa ran kammalashi ta kuma riqi kyakkyawan certificate mafi girman daraja a idanun mutane.

Ta samesu a zaune sun gama shiryawa sanda ta koma dakin. Kai tsaye ta wuce can ciki ta jawo rigarta ta sama ta zura,ta hada igiyoyin ta daureta ta zauna dai dai jikinta,abinda ya bawa rigar daman fidda kyakkyawan shape din nan nata da ba kasafai ya fiya bayyana ba saboda ita din ba ma'abociyar sanya damammun kaya bace. Sai data sake goge jikinta da sassanyan oil perfume dinta sannan ta fara rolling dan kwalinta saman kanta idanunta akan fuskarta data bayyana tarwai ta cikin madubin.

Maganganunsu taketa tattaunawa ita da zuciyarta. Dabiar kawun dama bibo gaba daya. Yadda tsahon lokaci da zamani bai sanya kowannensu ya sauya ba. Ranta da zuciyarta duka ba dadi. Ta iya rigima tuburan idan taso......ta iya surutu har kayi zaton ma ba ita bace......hakanan ta iya fada musu da kuma taurin kai......amma daga sanda rayuwa ta soma Karantar da ita wasu darussa sai ta gane basu take buqata ba,don haka ta tattarasu ta aje a gefe.

Jakar da zata dace da shigar da kuma yanayin ta dauko. Kaman yadda ta saba duba jaka kafin takai ga fita da ita haka ma wanna,a nan taci karo da kudaden da mashkur ya bata. Maidasu jakar tayi da zummar damqawa suraj su,daidai lokacin haneefa ta shigo tana kiranta

"Kizo inji kawu sule"

"Kawu kuma?" Ta tambayi haneefan tana duban idanunta

"Eh" Kamar ba zata mata komai ba,sai ta fesar da iska daga bakinta. Tasan dukkan abinda zai sanyashi shigowa wajenta baya taba zame mata abun alkhairi face tarin matsaloli fadace fadace da fadin maganganu barkatai da zasu yamutsa DUNIYARTA tana zaune salin alin

"Kice masa gani nan" Ta bata amsa tana juyawa sashen ajiye takalmanta ta fara dubawa. Takalma ne kala kala masu mabanbantan shape kudi da kuma kaloli. Wani adadi ne me yawa ma'ajiyar takalman taci,wanda dukkansu idan ka kalla babu takalmin qasa sa dubu goma.

A duk sanda ta kalli sashen suturar data mallaka a yanzu,a karan kanta mamakinta yana sake ninkuwa ne. Suturu na alfarmar da yaran masu hannu da shuni ke taqamar mallaka ko jin isar cewa sun kai. Daya daga ciki ta zaro,ta aje a qasa ta zura a qafafunta sannan ta debi wayoyinta ta jefa a jaka tayi hanyar fita tana ji a ranta ko sisi a yau din bazai samu daga wajenta ba muddin abinda ya shigo dashi kenan.

*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*

*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*

*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*

*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*

*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*

*ZAFAFA BIYAR*

*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*

*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*

_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_

_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_

_K'ALBIM Mamuhghee_

_AJIYA A DUHU Billynabdul_

_DUNIYATA Huguma_

_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_

*hudu 2k*

*uku 1500*

*Biyu 1k*

*Daya 500*

_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_

*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*

*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*

*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*

*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*

*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*

*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪

89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf

*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*

*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 43
___________________________
GROUP 1
https://chat.whatsapp.com/DT97XBDyEfyEwniN0a09Cz

*_assalamu alaikum warahmatullah_*

*_kina ta ganin kaya kala kala online?,kinason siya amma kina tsoron damfara?,tsada ko rashin ingancin kaya?_*

*_wannan tsoro da taraddadi ya yanke miki indai da HUGUMA CLOSET_*

*_muna da nau'ikan kaya kala daban daban bisa farashin da ba kowanne dan kasuwa ke iya bada kayansa akan hakan ba_*

Shadda
Laces
Atamfa
Kayan yara English wears dana jarirai
Qawatattun handbags
Mayafai
Abayas da jallabiyas
Inner wears
Huluna na maza da mata yara da manya socks
Takalma na maza da mata yara da manya
Lafayas
Sarqoqi agoguna banguls da rings

_kai komai daya danganci kayan ado na fita kunya wa dan adam_

_bisa farashin da zaiyi daidai da buqatarka_

*_Me kike jira sallah na gabatowa?,ana can ana ruwan suturu daidai da qarfin kowa?_*

*_masu manyan qarfi da matsakaita?_*

*_ki dinga siya da kadan kadan kina saka kudin kina tara abinki har sukai sanda zaki karba?,ko ki siya lokaci daya a kai miki_*

*_muna aika kaya ko ina a duniya in sha Allah_*

*MUNA BONONZA LOKACI LOKACI NA DUKA ABINDA RABO YA TSAGA*

*_MASU REPOSTING DA MASU SARI DUKA BA'A BARSU A BAYA BA,KI SIYA KI SAIDA KI SAMU RIBARKI HANKALI KWANCE,BA TARADDADIN INGANCIN KAYA KO WANDA KIKA BAIWA KUDINKI_*

*_KIYI JOINING KI TURAWA 'YAN UWA DA ABOKAN ARZIQI_*

*_INGANCI RAHUSA GASKIYA DA AMANA SHINE TAKENMU_*🫶🏽🫶🏽✌🏽✌🏽✌🏽✌🏽

GROUP 2LINK

https://chat.whatsapp.com/CKY0xZDtpby6MTkGrPkXLr
_________________________

Samunsa tayi zaune dirshan saman carfet yana karakaina da kwanukan da suka gama breakfast. Ya buda flask din da suka zuba dafaffen naman kai wanda sukaci suka bar sauran sai zuwa dare. Yana cikin ire iren siyayyar da take musu lokaci bayan lokaci dukka a qoqarinta na ganin basu rasa komai ba......basu nema komai sun rasa ba......hakanan komai din bai gagaresu ba. Tana da buri me yawa akansu,tana da mafarki mai fadi......tana kuma fata da sanya ran wataran zata basu rayuwa fiye da wadda sukeyi a yanzu haka.

Daga kai yayi yana dubanta sanda yake tauna naman,zaqin maggi yana ratsashi.

"To zauna mana banda abinki,kikayi wani dogogo saman hannun kujera?" Ya fadi saboda yadda ta kame a hannun kujerar rungume da hannayenta. Sam batason ya bata mata lokaci ta kuma fahimci zuwa yayi yaci mata lokacin

"Kawu ai ina tunanin wancan maganan mun gama da ita ko?,fita nakeso nayi ne ana jira na" Ta fada tana duba agogon hannunta.

"Kefa kin fiya tsiya da hurwar banza da wofi,ayita tattaroki kina wargajewa?,har sai kin jawo magauta sun jimu?" Shuruuuu tayi tana me zuba masa idanu tare da mamakin fitar kalamin daga bakinsa. Wai magauta,ji kuma na nawa?,ko yana tunanin cikin gidan yana da wani magauci a tsakaninsu da ya wuce shi karan kansa?.

"Tunda sauri kike bari nayi a gaggauce" Ya fada yana sude hannunsa daya nado romon naman kan,ya gyara zamansa sosai yana kallonta.

"Kinsan hausawa sunce ko kana gudu haifi ka yar.....kuma ita haihuwa rana gareta" Yayi maganar cikin sigar kwantar da murya da jan hankali. Bata ce masa ta tafasa ya sauke ba,tadai ci gaba da kallonsa yana bayanansa tare da son jin inda zantukansa zasu tuqe

"Wato wata gwaggwabar mu'amala ce ta taso mana,wadda cikin ikon Allah take buqatar adam zuba wasu kudade kuma a kwashe da riba me tarin yawa.......to kinsam harka ta samu dai ba'a wasa da ita a lokaci irin wannan,duba da yadda al'amuran qasa suka yamutse....to na duba na dubo......na laluba na lalubo kaf 'yan uwa na kusa dana nesa......ba wanda zai rufan sittira ya bani kudin nan aro ko bashi banda ke diyar albarka" Ya qarasa maganar yana addu'a qasan ransa. Ya santa sarai.....yasan aikinta,yasan kuma abinda zata aikata da wanda ba zata yi din ba. Ya jima baiga yarinya mai zubin matsorata ba,wadda kuma a zahiri zuciyarta a tsaye take carrr babu tsoro ba irin sabreen din.

Tsam ta miqe abinta bayan data fahimci cewa yakai aya a maganarsa

"Bani da wasu kudade kawu.....zan fita sai na dawo" Ta fada kanta tsaye tana gyara chain din hand bag dinta. Daga zaunen ya tada kai yana dubanta

"Wai baki fahimci abinda nake magana bane akai sabreen?" Qaramin murmushi ta saki. Ta sani,idan tayi rantsuwa ko kaffara ba zatayi ba,zaije yayi caca ne.....abar da ya jima yana tabawa da taimakon mahaifinta ta soma sakinsa,sai gashi a yanzu gushewar me masa saiti ta sanya ya dawo da dukka wasu tsaffin dabi'unsa da ake sanya ran yayi adabo dasu. Duk da hanyar da take samar da kudadenta.....amma tayi imanin ba zata iya diba ta bashi ya buga caca ba. Inda wajen wata lalurar dabanne,ita a karan kanta lokaci bayan lokaci tana miqa mass,shi kansa yasan tana sahun mutane na farko farko da hannunsa ke yawan amsa daga garesu koda bataso haka ba.

"Naji kawu...kayi haquri bani dasu" Ta sake fada hankalinta kwance,don sam case dinta bai daga mata hankali ba,don abu daya data sani shine,ko sama da qasa zasu hadu ba zata iya bada silai tata ya sanya a caca ba,bayan tarin buqatu da lalurori dake zayyane cikin littafin ayyukanta da takeson wanzarwa. Tana da babban mafarki akan mutanen da take rayuwa dasu,tana son kowanne ta daukeshi ta dora rayuwarsa bisa wani gurbi ko matakin da koda bayan ta gushe tasan tayi dashen daya baza rassa sassa da kuma jijiyoyi masu inganci da qarko.
Chapter 41 · 0% Book details