Sashe 34
A Duniya Ta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idanu ta zuba mata kamar yadda itama ta zuba mata nata idanun. Babu komai cikin tambayar annin face zallar rainin wayo da kuma rainin hankali. Tana cewa yanzu yanzu tayi mata tambayar amma buqatar maimaici takeyi kenan?.
Tattara dukka nutsuwarta tayi da kuma tarin kalaman dake cike fal a bakinta,tanaso a yau ko yaya ta fanshe haushi da takaicin anni dake kwance a ranta.....haushi baqinciki da kuma Takaicin da suka jima suna ci mata rai.
"Zuwa yanzu ya kamata ace kinsan cewa da Muhammadu da musaddiq nice na haifi abuna ba kece kika haifamin su ba......zuwa yanzu ya kamata ace kin warware duk wani qulli da kikayi a kansu....kibarmin yara na na moresu kamar yadda kowacce uwa ke morar 'ya'yanta......yanzu har takai matsayin da ni zan daga kira na kira fu'ad yaqi dagamin kira saboda baqin kilbibinki da qullinki ameena?" Qaramin murmushi anni ta saki tana dan motsa idanunta sannan ta waresu akan maama. Tana mamakin maama din sosai a yadda take da qarfin halin lissafo abubuwa irin haka. Kamar ma dai ta manta ita din WACECE. Kamar ta manta su waye yaran da take ikirari gami da!kiransu da sunan 'YA'YANTA.
A dukka zancanta babu wani abu daya dameta ko ya bata mata rai,don bawai yau ko jiya tasan mariya ba,ba kuma shekaran jiya ko waccan shekaran jiya ta gama fahimtar duk wani karkataccen saqo shagube da jirwaye da kamar wanka da mariya ke aike mata a fakaice ba. Saidai ko da wasa bata taba daga mata hankali kota dadata da qasa ba,tunda ta sani cewa tun ran gini tun ran zane......hakanan mariya din ta riga tabar kari tun ran tubani,duk wani da zatayi a yanzu bazai zame mata damuwa ba,don akwai idanun data sanya take kallonta dasu.
Abu daya ne da taji bataji dadinsa ba shine abinda fu'ad din yayi. Qin daga kiranta,wanda ita kanta ba zata daga masa qafa ba akan hakan,kuskure ne babba wanda yana daya daga cikin abubuwan da take yaqi dasu da son canzasu akai zuwa wani abu na daban,saidai akance mahori ya riga mabada hali.
"Wannan tsohon zance ne da duniya ta riga ta shaidashi......meye abun daga hankali,tada jijiyar wuya ko wahalar da baki wajen maimaitamin shi mariya?,fu'ad danki ne halak malak da ya fito daga tsatsonki,haka ma musaddiq.......qaddara ta jefosu hannuwana da taimakon salon taki rawar da kika taka,shin meye laifin ameenatu a ciki?,rubutacce ne wannan,duk wanda yayi lissafinsa ba daidai ba dole idan yazo kwashewa ya diba ba daidai ba......ba wanda ya tayaki lissafin bare kiyi tunanin shi ya miki dungushe" Sosai martanin anni ya tabata. Ta sani magana ce take maida mata a kaikaice wadda bata buqatar dogon bayani ko kuma fashin baqi.
Murmushi maaman ta saki tana kada qafarta
"Shi lissafi idan akayishi ba daidai ba......akwai hanyoyin gyaransa don a samu a diba yadda ya kamata,akwai rance akwai ciko akwai kuma bashi.......mariya nake har yau har gobe ameena" Idanunta anni ta janye daga kanta tana sakin murmushi. Mariya na daya daga cikin halittun dake bata mamaki a rayuwarta kaf.....saidai ta wani fannin sai taga lamarinta ba abune daya cancanci a tsaya ana masa mamaki ba. Landline dake kusa da ita ta jawo ta soma latsa wasu lambobi wanda bugu biyu kawai aka daga.
"Kiyimin kiran amna kice ta kiramin yayansu tace ya kirani yanzu yanzu"
"An gama" Aka bata amsa a gaggauce cikin zaquwa da son isar da buqatarta.
Kife wayar tayi tana duban maama hankali kwance
"Kada ki tsananta sanya damuwa a ranki mariya......komai juyin lokaci da zamani fu'ad da farouq ba zasu taba canzawa daga sunan 'ya'yanki ba......"
".....na jima da sanin hakan" Ta katsi numfashin anni tana miqewa
"Kada ki tsammaci cewa gazawa kasawa ko kuma rashin isa ta sanyani bi ta hannunki don nayi magana da fu'ad......a'ah.....nayi hakanne don ki sani.......daga rana irin ta yau hakan ba zata sake faruwa ba.....don zaki rasa dama irin wannan ne har abada.........a sannu zaki manta da cewa kin taba sanin wani me suna fu'ad ko musaddiq......wannan saqon nakeson isar miki".
Yadda bata motsa ba hakanan bata ce da ita komai ba,har zuwa sanda ta juya tana ficewa zuwaira tana biye da ita a baya.
Duk da ranta baqiqqirin yake amma ta wani fannin tana jin wani farinciki yana shigarta. Ko banza,ko kuma yaya ne ta amayar mata da wani sashe na maganganun da suke cizo zuciyarta. Cikin miliyoyin maganganun da take buri da fatan amayar mata yau din ta fesar mata da kadan daga ciki,saidai kuma ta kasa samun salama ko qanqani cikin ranta,musamman sanda take ratsa stairs tana saukowa tana ratsa falon farko na anni din.
Bata da wani buri a rayuwa daya wuce dukka wannan daula dukiya da kuma mulki su dawo qarqashin kulawarta,su dawo qarqashin mulkinta,su dawo qarqashin umarninta.
Tunda ya sauko ya kasa wucewa yabar gidan kamar yadda anni ta umarceshi,kawai sai ya samu kansa da samun waje ya zauna saman tsadaddu kuma lafiyayyun sofas din da suka zamo ado wa falon. Kujeru ne na musamman kaman yadda kowanne falo na gidan ke qawace da nashi kalar kujerun.
Ba komai yakeyi ba,kawai yana zaune ne hakanan,saidai kuma zuciyarsa tayi nisa da gangar jikinsa. Tun yana da shekaru biyu a duniya yasan wacece ita,yasan abune me matuqar wahala ta iya zama da anni ta sauko lafiya qalau ba tare data gasa mata maganganu masu ciwo ba. Damuwar anni damuwarsu ce,sukan gwammace ciwo bacin rai damuwa ko jarrabawa ta samesu amma tabar musu anninsu ta zauna lafiya.
Motsi da alamun takun mutum da yaji yaja hankalinsa,ya waiwaya da sauri daidai sanda ta kammala sauka daga stairs din take doso ainihin falon ta yadda zata cimma qofar fita waje.
Da idanu ta kafeshi har zuwa sanda ta cimmasa a inda yake tsaye goye da hannayensa.
"Ka gaza tafiya ko saboda kada kabar wajen na bata ran qanwa ko yayar ubanka!" Ta furta a zafafe. Kadan zuwaira ta matsa hannuwanta
"Da ruwan sanyi ma saika dafa dutse......kiyi a hankali" Ta furta mata qasa qasa. Kalamanta sun samu gurbi a zuciyarta saidai basu samu damar sauketa daga fushinta ba gaba daya,don haka taci gaba da kallonsa a sanda yake tsaye a gabanta ba tare da yace komai ba. Kimanin mintuna biyu kafin ta furxar da iska daga bakinta sannan ta juya tana barin falon zuwairan na biye da ita.
Sanda suke ratsa farfajiyar farko ta gidan zuwa na biyu.....duk da maganganu da zuwaira keyi wanda duka akan abinda ya faru cikin gidanne amma hakan bai dauke hankalinta daga tarin zalla zalla kuma galla gallan motocin dake ajiye qarqashin sashen ajiyar motoci na gidan ba.
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 35
Ta sauke wata qatuwar ajiyar zuciya me nauyin gaske
"Bugatti,rolls Royce,Lamborghini Aventado,Brabus G_wagon,Mercedes Benz,BMW......zuwaira?" Ta qarashe lissafin jerin motocin da idanunta suka gani din tana waiwaya ga zuwairan
"Na'am?"
"Kinsan adadin lissafi da qiyasin kudaden wadannan motocin kuwa?,kinsan waye da waye matsayi da matakin rayuwa suke cillashi zuwa ga mallakarsu?,kinsan wanne me tsananin sa'ar ne cikin duniya yake da rabon samun wadannan motocin?.....zuwaira ace d'ana keda su amma ya rasa a gidan da zaya barni sai a wannan wulaqantaccen gidan?" Ta fadi da mugun zafi tana nuna gidan da suke tsaye a gabansa da yatsa.
Kamar yau ne zuwairan ta saba ganin gidan,kamar ba cikinsa take kwana take tashi ba,ta daga kai tana duban gidan da maama din ke kira da wulaqantacce.
Kyakkyawan gini ne da aka yishi madaidaici me dauke da madaidaiciyar harabar dake dauke da mota qirar range Rover guda biyu duka don biyan buqatar matar gidan. Wadatacciyar haraba dake dauke da dogayen katangu da kuma yalwataccen gate dake qarqashin kulawar mutum daya wato malam saidu. Akwai qaton kitchen da aka zuba masa dukka kayan tasarrufin girki kamar kitchen din 'yar bana bakwai,kitchen din dake maqale da store dake danqare da kayan abincin da yafi qarfin cikin mutum ashirin da zasu shekara kullum suna ci kuma ana kyauta dasu.
Babban falo me dauke da dining area......bedrooms guda hudu da kowanne aka qawatashi da kayan gado 'yan turkey masu asalin kyau da tsada,kaman yadda aka qawata falon da kayan turkey din hatta da curtains da carpet kuwa. Wuta 24hrs,engine wanki dana guga,Ac hade da fanka,me aiki guda daya a cikin gida,da kuma me kula da farfajiyar gidan namiji baya ga me gadi malam saidu. Albashin naira dubu dari duk wata ga mamallakiyar gidan.
Nisan buri......zurfafa da kuma zarmewa a son zuciya.....take laifuka,dannesu da manta abinda baya ta haifar ya lullube idanunsu su dukka biyun
"Indai zaa yi qiyasi bisa irin nau'in arziqin fu'ad.....idan dai zaa yi duba da gidan daya sanya wadancan mutanen wanda idan aka sanya gidanki cikin nasu baifi matsayin boys quarters na gidan ba......tabbas ya wulaqanta haqqin haihuwa......hakanan ire iren wadannan gidajen kinfi qarfin zama a cikinsa saidai kiyi kyautarsa ga irinmu"
"Zuwaira" Ta kira sunanta cikin jaddadawa
"Na'am"
"Ki rubuta ki ajiye.....muddin ban raba tsakaninsa da aminatu ba tabbas ban haifu 'yar halak ba...." Maganarta ta qarshe kenan da tayi ta kutsa kanta cikin gidan tana jin gaba daya gidan tafi qarfin wanzuwa a ciki.
"Subhanallah......innalillahi wa'inna ilaihi rajiun" Malam saidu ya furta yana dire qaramar radio din dake hannunsa yanata kokawar kunnata.
Tattara dukka nutsuwarta tayi da kuma tarin kalaman dake cike fal a bakinta,tanaso a yau ko yaya ta fanshe haushi da takaicin anni dake kwance a ranta.....haushi baqinciki da kuma Takaicin da suka jima suna ci mata rai.
"Zuwa yanzu ya kamata ace kinsan cewa da Muhammadu da musaddiq nice na haifi abuna ba kece kika haifamin su ba......zuwa yanzu ya kamata ace kin warware duk wani qulli da kikayi a kansu....kibarmin yara na na moresu kamar yadda kowacce uwa ke morar 'ya'yanta......yanzu har takai matsayin da ni zan daga kira na kira fu'ad yaqi dagamin kira saboda baqin kilbibinki da qullinki ameena?" Qaramin murmushi anni ta saki tana dan motsa idanunta sannan ta waresu akan maama. Tana mamakin maama din sosai a yadda take da qarfin halin lissafo abubuwa irin haka. Kamar ma dai ta manta ita din WACECE. Kamar ta manta su waye yaran da take ikirari gami da!kiransu da sunan 'YA'YANTA.
A dukka zancanta babu wani abu daya dameta ko ya bata mata rai,don bawai yau ko jiya tasan mariya ba,ba kuma shekaran jiya ko waccan shekaran jiya ta gama fahimtar duk wani karkataccen saqo shagube da jirwaye da kamar wanka da mariya ke aike mata a fakaice ba. Saidai ko da wasa bata taba daga mata hankali kota dadata da qasa ba,tunda ta sani cewa tun ran gini tun ran zane......hakanan mariya din ta riga tabar kari tun ran tubani,duk wani da zatayi a yanzu bazai zame mata damuwa ba,don akwai idanun data sanya take kallonta dasu.
Abu daya ne da taji bataji dadinsa ba shine abinda fu'ad din yayi. Qin daga kiranta,wanda ita kanta ba zata daga masa qafa ba akan hakan,kuskure ne babba wanda yana daya daga cikin abubuwan da take yaqi dasu da son canzasu akai zuwa wani abu na daban,saidai akance mahori ya riga mabada hali.
"Wannan tsohon zance ne da duniya ta riga ta shaidashi......meye abun daga hankali,tada jijiyar wuya ko wahalar da baki wajen maimaitamin shi mariya?,fu'ad danki ne halak malak da ya fito daga tsatsonki,haka ma musaddiq.......qaddara ta jefosu hannuwana da taimakon salon taki rawar da kika taka,shin meye laifin ameenatu a ciki?,rubutacce ne wannan,duk wanda yayi lissafinsa ba daidai ba dole idan yazo kwashewa ya diba ba daidai ba......ba wanda ya tayaki lissafin bare kiyi tunanin shi ya miki dungushe" Sosai martanin anni ya tabata. Ta sani magana ce take maida mata a kaikaice wadda bata buqatar dogon bayani ko kuma fashin baqi.
Murmushi maaman ta saki tana kada qafarta
"Shi lissafi idan akayishi ba daidai ba......akwai hanyoyin gyaransa don a samu a diba yadda ya kamata,akwai rance akwai ciko akwai kuma bashi.......mariya nake har yau har gobe ameena" Idanunta anni ta janye daga kanta tana sakin murmushi. Mariya na daya daga cikin halittun dake bata mamaki a rayuwarta kaf.....saidai ta wani fannin sai taga lamarinta ba abune daya cancanci a tsaya ana masa mamaki ba. Landline dake kusa da ita ta jawo ta soma latsa wasu lambobi wanda bugu biyu kawai aka daga.
"Kiyimin kiran amna kice ta kiramin yayansu tace ya kirani yanzu yanzu"
"An gama" Aka bata amsa a gaggauce cikin zaquwa da son isar da buqatarta.
Kife wayar tayi tana duban maama hankali kwance
"Kada ki tsananta sanya damuwa a ranki mariya......komai juyin lokaci da zamani fu'ad da farouq ba zasu taba canzawa daga sunan 'ya'yanki ba......"
".....na jima da sanin hakan" Ta katsi numfashin anni tana miqewa
"Kada ki tsammaci cewa gazawa kasawa ko kuma rashin isa ta sanyani bi ta hannunki don nayi magana da fu'ad......a'ah.....nayi hakanne don ki sani.......daga rana irin ta yau hakan ba zata sake faruwa ba.....don zaki rasa dama irin wannan ne har abada.........a sannu zaki manta da cewa kin taba sanin wani me suna fu'ad ko musaddiq......wannan saqon nakeson isar miki".
Yadda bata motsa ba hakanan bata ce da ita komai ba,har zuwa sanda ta juya tana ficewa zuwaira tana biye da ita a baya.
Duk da ranta baqiqqirin yake amma ta wani fannin tana jin wani farinciki yana shigarta. Ko banza,ko kuma yaya ne ta amayar mata da wani sashe na maganganun da suke cizo zuciyarta. Cikin miliyoyin maganganun da take buri da fatan amayar mata yau din ta fesar mata da kadan daga ciki,saidai kuma ta kasa samun salama ko qanqani cikin ranta,musamman sanda take ratsa stairs tana saukowa tana ratsa falon farko na anni din.
Bata da wani buri a rayuwa daya wuce dukka wannan daula dukiya da kuma mulki su dawo qarqashin kulawarta,su dawo qarqashin mulkinta,su dawo qarqashin umarninta.
Tunda ya sauko ya kasa wucewa yabar gidan kamar yadda anni ta umarceshi,kawai sai ya samu kansa da samun waje ya zauna saman tsadaddu kuma lafiyayyun sofas din da suka zamo ado wa falon. Kujeru ne na musamman kaman yadda kowanne falo na gidan ke qawace da nashi kalar kujerun.
Ba komai yakeyi ba,kawai yana zaune ne hakanan,saidai kuma zuciyarsa tayi nisa da gangar jikinsa. Tun yana da shekaru biyu a duniya yasan wacece ita,yasan abune me matuqar wahala ta iya zama da anni ta sauko lafiya qalau ba tare data gasa mata maganganu masu ciwo ba. Damuwar anni damuwarsu ce,sukan gwammace ciwo bacin rai damuwa ko jarrabawa ta samesu amma tabar musu anninsu ta zauna lafiya.
Motsi da alamun takun mutum da yaji yaja hankalinsa,ya waiwaya da sauri daidai sanda ta kammala sauka daga stairs din take doso ainihin falon ta yadda zata cimma qofar fita waje.
Da idanu ta kafeshi har zuwa sanda ta cimmasa a inda yake tsaye goye da hannayensa.
"Ka gaza tafiya ko saboda kada kabar wajen na bata ran qanwa ko yayar ubanka!" Ta furta a zafafe. Kadan zuwaira ta matsa hannuwanta
"Da ruwan sanyi ma saika dafa dutse......kiyi a hankali" Ta furta mata qasa qasa. Kalamanta sun samu gurbi a zuciyarta saidai basu samu damar sauketa daga fushinta ba gaba daya,don haka taci gaba da kallonsa a sanda yake tsaye a gabanta ba tare da yace komai ba. Kimanin mintuna biyu kafin ta furxar da iska daga bakinta sannan ta juya tana barin falon zuwairan na biye da ita.
Sanda suke ratsa farfajiyar farko ta gidan zuwa na biyu.....duk da maganganu da zuwaira keyi wanda duka akan abinda ya faru cikin gidanne amma hakan bai dauke hankalinta daga tarin zalla zalla kuma galla gallan motocin dake ajiye qarqashin sashen ajiyar motoci na gidan ba.
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*🇳🇪🇳🇪
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*🥰🥰
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
PAGE 35
Ta sauke wata qatuwar ajiyar zuciya me nauyin gaske
"Bugatti,rolls Royce,Lamborghini Aventado,Brabus G_wagon,Mercedes Benz,BMW......zuwaira?" Ta qarashe lissafin jerin motocin da idanunta suka gani din tana waiwaya ga zuwairan
"Na'am?"
"Kinsan adadin lissafi da qiyasin kudaden wadannan motocin kuwa?,kinsan waye da waye matsayi da matakin rayuwa suke cillashi zuwa ga mallakarsu?,kinsan wanne me tsananin sa'ar ne cikin duniya yake da rabon samun wadannan motocin?.....zuwaira ace d'ana keda su amma ya rasa a gidan da zaya barni sai a wannan wulaqantaccen gidan?" Ta fadi da mugun zafi tana nuna gidan da suke tsaye a gabansa da yatsa.
Kamar yau ne zuwairan ta saba ganin gidan,kamar ba cikinsa take kwana take tashi ba,ta daga kai tana duban gidan da maama din ke kira da wulaqantacce.
Kyakkyawan gini ne da aka yishi madaidaici me dauke da madaidaiciyar harabar dake dauke da mota qirar range Rover guda biyu duka don biyan buqatar matar gidan. Wadatacciyar haraba dake dauke da dogayen katangu da kuma yalwataccen gate dake qarqashin kulawar mutum daya wato malam saidu. Akwai qaton kitchen da aka zuba masa dukka kayan tasarrufin girki kamar kitchen din 'yar bana bakwai,kitchen din dake maqale da store dake danqare da kayan abincin da yafi qarfin cikin mutum ashirin da zasu shekara kullum suna ci kuma ana kyauta dasu.
Babban falo me dauke da dining area......bedrooms guda hudu da kowanne aka qawatashi da kayan gado 'yan turkey masu asalin kyau da tsada,kaman yadda aka qawata falon da kayan turkey din hatta da curtains da carpet kuwa. Wuta 24hrs,engine wanki dana guga,Ac hade da fanka,me aiki guda daya a cikin gida,da kuma me kula da farfajiyar gidan namiji baya ga me gadi malam saidu. Albashin naira dubu dari duk wata ga mamallakiyar gidan.
Nisan buri......zurfafa da kuma zarmewa a son zuciya.....take laifuka,dannesu da manta abinda baya ta haifar ya lullube idanunsu su dukka biyun
"Indai zaa yi qiyasi bisa irin nau'in arziqin fu'ad.....idan dai zaa yi duba da gidan daya sanya wadancan mutanen wanda idan aka sanya gidanki cikin nasu baifi matsayin boys quarters na gidan ba......tabbas ya wulaqanta haqqin haihuwa......hakanan ire iren wadannan gidajen kinfi qarfin zama a cikinsa saidai kiyi kyautarsa ga irinmu"
"Zuwaira" Ta kira sunanta cikin jaddadawa
"Na'am"
"Ki rubuta ki ajiye.....muddin ban raba tsakaninsa da aminatu ba tabbas ban haifu 'yar halak ba...." Maganarta ta qarshe kenan da tayi ta kutsa kanta cikin gidan tana jin gaba daya gidan tafi qarfin wanzuwa a ciki.
"Subhanallah......innalillahi wa'inna ilaihi rajiun" Malam saidu ya furta yana dire qaramar radio din dake hannunsa yanata kokawar kunnata.