← Book details Zuciya Da Kwanji Book 4 End Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 5 OF 5

fara

Zuciya Da Kwanji Book 4 End Complete Hausa Novel · about 15 min read

da neman gafararka bisa laifuffukan da na
dinga
yi maka abdul,zuciyata da kwanjina, wato
niyyoyina da abin da na aikata,wanda ka
sani da
wanda baka sani ba, don girman Allah ina
neman
gafararka" Yanzu mazantakarsa ta

dawo,dan
cikin dakewa ya tare ta "Za ki fi birgeni
idan kika
fada min wanda ban sani ba din, duk
muninsu na
yi miki alkawarin zan fahimce ki". Kai tsaye
ta
amsa. "Yunkurin zubar maka da ciki". Ya yi
ajiyar
zuciya ya yi murmushi ya ce. "Na yafe miki
dukkan laifin da kika yi min". Ta kada kai
kanta
na sunkuye sannan ta kuma nisawa. "A yau
zan
dawo da wuta magana da ka fada min in
nuna
maka gamsuwata a kanta,wato ka taba ce
min ko
ya ya akwai digon sonka a raina na
karyata,ban
kuma taba saka ran hakan za ta yiwu ba sai
dab
da za ka bata,wato lokacin da nake yunkurin
zubar da cikin yadda ka rika fishi dani kana
min

fada yadda kake so. Sai na dinga jin gaba
daya
duniyar ta yi min zafi fiye da yadda kake
tsammani a wannan lokacin,na dinga jin ka
bar
fishi dani mu zauna lafiya kamar shine
matsalata
kadai a duniya. Magana ta gaskiya tun a
wannan
lokacin na fara tunanin ya kamata na zauna
a
gidan nan saboda haka ba dole malam ya yi
min
ba, ya yi min nasiha ya kuma ba ni
zabi,dama
abin da ya kamace ni ke nan. Ko bana sonka
ina
zan tafi in. Kai maka da ko 'ya?" Ya yi
dariya
kawai yana kallon ta,sai ta yi fuska sosai ta
dora.
"Sai dai akwai sharadin gaskiya wanda nake
so
ka fahimce ni a kansa ba zan iya zaman
cikin

gidan nan ba abdul,dalilan da nake jin ni
dai
masu karfi ne a wajena. Ya tare ta shi ma
cikin
yin fuska. "Kamar kin taba fada min kuwa
mun
gama zube sharuda tun a waje". Ta dube shi
da
kyau ta ce. "Au abdul a kan wadancan
sharudan
kake so mu dore?" Ya girgiza kai. "In na
fada
maka dalilan na yanzu idan kana da neman
shawara kana iya tuntubar malam,in ma ba
za ka
tuntube shi ba ni ka bani dama in tuntube
shi".
Ya yi shiru yana kallon ta ita ma ta yi shiru
tana
kallon sa har sai da ya tabbatar ba ta niyyar
magana sannan ya ce mata. "Ina jin ki
mana
fatima". A raunane ta ce. "Wallahi da gaske
ba
zan iya zaman gidan nan ba sai dai a canja

min
gida,ina da kishi ba zan iya jure in dinga
ganinka
da wasu matan ba, ina son rayuwar walwala
da
abin hannuna. Hakan ba zai samu ba kila in
na yi
ya zama rigima,ban iya hayaniya ba,ba
kuma na
son in dore cikin balle har'ya 'ya su taso su
dauki samfur. A cikin gidan nan kuwa laifi
ba sai
ka yi niyyar yinsa yake zama naka ba.Abu na
karshe shine,ban yiwa kaina tanadin mutuwa
yanzu ba gaskiya,nima gara in zauna in yi
rayuwa
mai dadi a gidan aure,amma na tabbatar
sadiya
za ta iya kawo mu harin kisa ba tare da na
cancanci haka ba...." Ya tare ta fuskarsa
babu
yabo babu fallasa. "Haba fatima,kar kishin
ya.
Sanya ki wuce gona da iri mana....." Ita ma
ta yi

saurin tare shi. "To ina ma kishin yake,ai
ban fara
shi ba tukunna.ina fada maka ne bisa abin
da ya
faru,bana son munafinci da kumbiya
kumbiya da
al'amura alhalimn ba za su amfane ni ba.
In
sadiya ta yi nasarar kashe ni duk yadda
kake
sona ba za ka iya dawo dani ba Abudl,sai
dai a
yiwa iyayena asara ta..." Ya tare ta da
tuntsura
dariya. "Haba fadima,ban da mayar da
allura
garma mana, a fadace fadacen a kike da
sadiya
ta taba ikirarin kashe ki? Kai tsaye ta amsa.
"Ranar da ka bata hankalina a tashe saboda
ina
ta jiran shigowar ka,sai na tashi na tafi in
tambaye hindatu ko ka sanar da ita za ka je
wani
gurin. Wallahi sai na sami sadiya a dakin da

galan da ashana tana hankoron sai ta zo ta
kone
mu saboda tana zaton ka dawo kana cikin
dakina
hindatu tana ta fama hana ta. Amma ka
fahimce
ni, ba na fada maka ba ne dan na bata ta a
wajenka, na fada maka ne dan shine dalilin
da
yake bukatar karin bayani,sai dai ko babu
shi da
gaske nake ina son a canja min gida,in kuma
zaman katya kake so mu yi sai in janye
gaskiyar
tawa". Ta dinga jan fasali saboda ya rasa
ta inda
zai bullo mata, ya tabbatar ba ya son bacin
ranta,musamman da ta ambato zaman
karya.
Amma batun canji gida wani gingimemen aiki
ne
a wajensa. Sai ya kamo hannunta ya janyo
ta
dawo kusa da shi ta zauna, ya dafa
kafadarta a

tausashe ya ce. "Kin karade lissafinki kuwa
a kan
canja miki gida fadima? Misali ko ina da
gidan
fadima? Misali ko ina da gidan da zan canja
miki
don Allah ni ba ki tawaye ni ba a matsayina
na
mayen kallon fuskarki kullum? Kuma
yaranmu ki
jaza mana wata dangantaka ta nesa dan
suifi
son ki da ni? Ta koma hannunsa ta rike tana
girgiza kai. "Abdul kana son kallon fuskata
tasa
ka farin ciki? Kana son ganin 'ya'yan naka
cikin
walwala? To in dai a cikin gidan nan muke
na
rantse maka da Allah ba zai samu ba. Ba
zan rufe
ka ba,nice tushen farin ciki,ni kuma na
tabbatar in
dai a cikin gidan nan ne ba zan yi shi ba".
Bai

taba tsammanin fatima tana da jayayya ba
sai
yau, kuma ya kusa yin jan ido ta bari,sai
ma ya
kuma bullo da wata lallabawar. "Na
yarda,amma
za ki bani dan lokaci na samar da gidan ko?
Bani
da sha'awar biyan haya", Cikin kyautata
murya ta
ce. "Gidan ba matsala bane ina dasu,sai ka
zaba
a ciki. Ya yi saurin tare ta. "Ba zan laminci
hakan
ba,ke nake so ba tare da kudinki ba,kuma
duk
wani abu na sarayar da hakki ba na cikinsa
fadima". Ta dan ja fasali sannan ta dube
shi.
"Wanne tsari za ka bi wajen sama min
gidan?"
Shima ya jima yana tunani sannan ya ce.
"Zan
nemi bashi sayan gida a ma'aikatarmu,na
zan ba

za su isa sayen gidan da za ki zauna ba,
saboda
haka zan yi tunani hanyoyin da za su kawo
wasu
kudin". A nutse ta ce. "To idan kyauta na
baka
gidan fa? Nan ma ya girgiza kai. "Bana so".
Yana
rufe baki ta karbe. "To maimakon ka je
ma'aikata
neman bashi ni ka zo gurina na baka mana,
sai
ka fadi tsarin da kake son ka biyani". Nan
ma ya
girgiza kai amma bai tanka ba. Ta jima cikin
tsura masa ido sannan ta sauke numfashi ta
ce.
"Abdul cikin biyun nan fa dole ka dau daya
wallahi, ko ka karbi gida kyauta ko kuma ka
karbe shi bashi, ban lamunci fita waje ciwo
bashi
ba. Kuma ni ko haihuwa bana so na yi a
gidan
nan".
2 · Like · React · Report · May 21, 2015

Amierah S-Man
Zuciya d kwanji 4
13"Kin fiye rigima". Abin da ya iya ce mata
ke nan.
Ya koma a hankali ya kwanta. Ta mike ta
nufi
wardrobe tana cewa. "Ba rigima ba ce ina
son mu
mutu tare kuma bana son mu rayu cikin
kunci da
tashe tashen hankula, kuma ina son mu
dinga
fuskantar juna da abin da yake zuciyoyinmu
kai
tsaye. Wallahi da gaske nake ba zan iya
zaman
farin cikin da nake so ba a gidan nan ba.
Misali.
Idan na dauki masu aiki ina daukar nauyin
su
babu me yarda nice,hasalima babu gurin da
za su
zauna. Kai wasu daga waje ma sai sun zo sun
zage ni, in kai za ka dauki nauyinsu abin ya
yi

maka yaw,ni kuma in na hakura ba zan iya
abin
da 'yan aikin za su yi ba". Shi dai kallon ta
kawai
yake,sai da ta gama shirin kwanciyarta
tsab,ta
kashe fitila sai dunlight ta zo ta kwanta ta ja
bargo ta juya masa baya. Ya yi gyara murya
ya
ce. "Yaushe zamu asibiti?" Ta amsa kai
tsaye.
"Tunda ba siyen gida bane sai mu tashi mu
tafi
yanzu". Ya tuntsure da dariya ya ce.
"Maganar
ba ta mutu ba ke nan". Ta ce,"bana
tsammanin
za ta mutu abdul". Ya sauke ajiyar zuciya
ya ce.
"Allah ya huci zuciyarki,gobe sai mu shirya
muje
asibiti ko? Muje wajen malam kai masa
takardar
sakin Alh da kudadensa,in ya so sai ki yi
masa

maganar gidan,idan ya fahimce ki shi ke
nan ni
bakon sauki ne,tunda na jingina farin ciki
da
ke...." Da sauri ta juyo ta rungume shi tana
tsananin bayyana murna,tana cewa. "Malam
zai
fahimce ni abdul". Farin cikin duniyar nan
ya rufe
shi,tun kafin ta gama rikicewa ya lalubi
kunnenta
ya rada mata. "Ba ki bani dama na nemi
afuwarki
da taki yafiyar ba kika rude mu da maganar
gida
fadima. Nima ina neman ki yafe min dukkan
kurakuran da na yi miki, sannan ina rokon ki
yi
hakuri da kuncina,na yi alkwarin kyautata
miki
iyakar karfina,ki ci gaba da yi min afuwa a
abin
da na gaza don Allah.
4 · Like · React · Report · May 21, 2015
Amierah S-Man

Zuciya d kwanji 4
14****************************
*************** Bayan
wata daya Alh ya dawo nigeria tare da
sabuwar
Fatima da ya canja wato matarsa da ya
auro a
astana mai suna merian,kyakkyawar mace
mai
kama da madubi ko ma fiye da fadiman da
ya
rasa. Tun kafin ya samu labarin an saki
abdullahi
ya hadu da marian ya ji kuma a ransa za ta
iya
maye gurbin fatima ko ma fiye,kasancewar
yana
ganin ita tana son sa. Ya kashe makudan
kudi a
kanta ya auro ta ya nufo nigeria,saboda
haka
malam na samun labarin saukarsa bai yi
kasa
gwiwa ba suka yi kwamba shi da sagiru da
abdulwahab suka je wajensa da neman sulhu.

Tun kafin a kai ruwa rana ma ya nuna musu
shi
tuni ya manta da wata fatima. Kudin ma bai
karba ba ya ce a mayarwa Abdullahi,komai
dai ya
zo da sauki,aka fahimci juna aka yiwa juna
godaiya suka yi sallam suka barshi da
mariansa,kila ita ma idan aka tabo ta a
sami
wani zuciya da kwanjin. ***************
*************************** Gaba daya
rayuwar
gidan abdullahi ta canja fiye da yadda
Abdullahi
ya yi tsammani,fatima mace ce mai saukin
kai da
sadaukarwa. Ko sonta ne ya rufe masa ido
shi
dai ya kasa ganewa akan tsaurin ra'ayinta
na
tabbatar da abin da ta ke so da dalilai da
hujjoji
kiri kiri a kan maganar gidan nan sai da ta
yi
nasara a kansa ta hanyar malam. Ta ma kai

wa
malam din takardun katon gidan a unguwar
tarauni da sunan ta mallaka masa ya ba shi
da
hannunsa. Malam kuma ya nuna ya
gamsu,ya
kwantar masa da hankali da cewa. Dama
idan dai
zai samu,to mafi a'ala ka rabawa matanka
gida
zai fi, sannan bana so mu ci gaba da
kuntatawa
yarinyar nan. Idan dai baka hangen wani
aibu a
cikin ware mata gida ita kadai sannan za ka
iya
adalci,to ka daure ka barta.sai ku yi
sharadin in
ka ga ba dai dai ba za a rushe maganar.
Abdullahi bai so ba dai ya sami nutsuwa
saboda
amincin da tsakaninsa da mahaifinsa. Amma
rayuwar da ya yi da fatima cikin sati uku da
ta
yarda ta karbe shi,sai ya sakankance da

girman
sha'aninta,zama da ita aminci ne da
nishadantarwa da zuciya. Tana da kawaici
da
biyayya kamar hindatu, sannan tana da
wayewar
faranta zuciya da soyayya irin nata da yake
zaton
ta a shi duk kuwa da tsohon cikin da take ja.
Saboda haka fatima ta ci gaba da kasancewa
tauraruwar zuciyarsa sai dai ya yi kokarin
boyewa ta ko wace fuska a idon hindatu da
sadiya domin duk wani abu da ya biyo ta kan
fatima wanda ya kirkire shi domin ita ba ya
ware
su ciki. Haka zalika bangaren hidima, in ka
dauke
tata da ta kebanta a bangaren cikinta.
Hindatu
dama ba ta matsala duk abin da ya zo mata
tana
karbarsa da godiyar Allah,ballantana a
yanzu da
Abdullahi ke yawan kyautata mata yana
yabonta.

Sadiya ma ta yi kokarn zubar da makaman
ta,musamman tun daga ranar Abdullahi ya
nuna
mata matsayin hindatu da fatima a
zuciyarsa,da
kuma abin da ya samar musu matsayin. Sai
ta
shawarci kanta karatun ta nutsu,sai kuma a
yanzu ne ta gane karatun da ta yi shine
mafi
a'ala a tare da ita,domin yanzu ne fatima
ta fito
sosai take nuna wace ce ita. Facakar kudi ta
dangi da ta kasaita sai ka ce matar
gwamna.An
cika musu gida da motoci da shige da ficen
'yan
'uwa da kayan kudi makudai. Sai kawai ma
fatiman ta fara ba ta shakka,dan haka da
abdullahi ya hada su ita da hindatu ya
sanar da
su cewa fatima za ta koma gidan ta ba
karamin
farin ciki sadiya ta yi ba, dan ta tabbatar
har

abada ba za ta daina kishin fatima ba,in ta
zafafa
kishin kuma ta tabo da abu turab! In kuwa
ta yi
nisa shi ke nan. An kammala gyaran gida
tsab,
amma an kulle shi da zummar sai ranar da
fatima
ta haihu daga asibiti sai a wuce sabon gida.
******************************
*********** Laraba
ashirin ga wata uku na shekara subu biyu da
sha
uku dai dai fatima ta haifo kyakkyawar
'yarta mai
kama da ita kamar ta yi kaki ta ajiye.
Saboda
yadda dangi suka cika asibitin lokacin da
fatima
ke labour,yarinyar na zuwa duniya nurse din
da ta
dago tana dariya ta ce. "Dangin nan kamar
sun
san kyakkyawar baby za su haifo suka
tanada

mata gata haka. Fatima ta cika da farin ciki
tana
biyo yarinyar da kallo cike da wata irin
kauna
wadda ba ta ta ba tsammanin ana samar da
irin
ta a cikin al'uma ba,sai doki take. Abdul ya
shigo
ta ga yadda su kare wanda ta fahimci kama
.......
Tuni ya san da irin wannan kaunar kuma
tanadarwa yarinyar tun kafin zo. Cikin awa
daya
maijego da 'yarta suka kammala cikin shiri
tsab,abin sha'awa. Sannan aka bude kofar
ganinsu. Dangi suka cika dakin dole aka bar
abdullahi da raragefe,aka kuma bar fatima
da
dokin a watse a basu guri a bar Abdullahi da
'yarsa ya dauka. Amma hakan ba ta samu
ba sai
da sha dayan dare ta yi,abdullahi ya kai su
hindatu gida ya dawo,ya kara raka kawu da
momi
wajen mota. Yana dawowa likita ya shigo

dakin,duk da haka fatima ba ta fasa abin
da ta yi
niyya ba, wato tashi zaune tana duban
abdullahi.
"Abdul rufo mana kofar nan wallahi kowa ya
zo
mun yi bacci". Abdullahi bai fahimce ta ba,
kuma
kafin ya nemi haske likita ya riga shi. "Ku yi
me
in kun rufe kofar?" Ta amsa cikin zolaya da
dariya. "To kaunar ku muka taru muka
haifawa
'yar ko daukar arziki kun hana mu yi mata
balle
mu kalle ta,kai ma dubi dan Allah yadda ka
bi ka
kankame ta" Suka tuntsure da dariya su
duka.
Abdullahi ya dago yane cewa. "Ashe kin gane
nima mitar da na gama yi ke nan...." Dr ya
tare
shi. "Amma dai ko za ku yiwa kowa Rashin
mutunci a kan 'yar nan ai ina tsammanin ya
kamata a tsallake ni......" Babu ko shakka

fatima
ta tare shi. "Haba likita duk abin da ka yi a
kallon
da ka yiwa yarinyar nan dazu da yanzu ba
ka
fanshe ba? Karbo ta don Allah abdul......"
Suka
kuma tuntsurewa da dariya. Abdullahi kuma
ya
kima hannu a basu 'yarsu,dole likita ya ba
shi ya
juya ya fita yana musu dariya cike da farin
ciki
yadda ya yi ceton ran da ba za a manta da
shi
ba. Suka sa'yar nan a tsakiya suna ta faman
kallo,duk motsi sai Abdullahi ya sanya mata
albarka,har fatiman ta dauki samfur ita ma
ta
dinga nemar mata albarkar ubangiji. Can
fatima
ta dago ta dube shi "Abdul wanne suna zamu
sa
mata? Ya kasa dago kai ya kalle ta saboda
fargabar yadda za ta karbi abin da zai

fada,amma
dai haka ya daure ya fito a shi sai dai ta
sigar
hikima. "Ki zabar mata sunan daya tsakanin
sunanki da hindatu,ina sonki haka kawai ba
tare
da na san abin da ya sani sonki ba, kullum
ina
wayar gari da sababbin sonki marasa adadi
kamar yadda nake wayar gari da tausayin
hindatu
saboda sna da take tsakani da Allah da
kuma irin
hakuri da kawaicinta. Fatima ta mayar da
kanta
ga jaririyar fuskarta ta canja,sai kallon
yarinyar
take. Ta jima ba ta tanka ba,sai faman
kallon ta
yake cikin dukan zuciya,ya san kuluwa ta yi
amma bai yi zargin danyen hukunci cikin
zargi.
Bai nemi jin ta bakinta ba sai da dan kanta
ta
kuma dagowa ta dube shi fuskarta a bace.

Wata
shekarar kuma sai na haifo sadiya ko? Ya
kara
dagewa da tausasa murya ya ce. "Ni ban ce
ba,
ba ki gamsu da dalilan da na gabatar miki
ba ne?
Kuma zabi na baki. Ko ba ke kika haifi 'yar
ba ai
ba zan miki dole ba fadima,kawai dan na za
ki
fahimce ni ne shi yasa ban yi shakkar in
nemi
alfarmarki ba". Ta kuma daukar shiru tana
kallon
yarinyar,sai dai babu bacin rai a fuskarta.
Sannan
ta nisa ba tare da ta dube shi ba ta ce.
"Idan
girma za a bi,sadiya ba za ta ji dadi ba
idan ka
tsallake ta ka dauko hindatu,ka ture tawa ni
ka ji
dani ma kafin ka haifo wata. Ta kare da
dariya.

Ya ji wani sanyi ya ratsa zuciyarsa,kaunar
fatiman ta kara mamaye ransa,yana kallon
idonta
kai tsaye ya amsa.
3 · Like · React · Report · May 21, 2015
Amierah S-Man
Karshe......
Zuciya d kwanji 4
15)"Na gode Allah ya yi miki albarka,sai dai
ba girma
bane, ai kin ji dalilin da na baki za a iya
samun
sadiyar nan gaba ko a waje su hindatu ta
haifo
ko ita ta haifa. Musamman idan ta kara
gyara
halinta.batun haihuwar fatima kuma kin san
Allah? In zan haifi fatima goma ba za su
ishe ni
ba,duk wani abu da ya yi kama da ke ban
taba jin
ya gundure ni ba". Ta dago suka yiwa juna
wani
kallo,sannan ta kawar da kai tana cewa.
"Na

sani,da kuma za ka haifi fadima goma sha
biyu ni
duka,bani da shakkun za su gagari zuciya da
kwanjinka, za ka iya komai namu,sonmu da
tsayawa a kan tarbiyarmu. Him! Ina yiwa
hindatu
murnar samun uba na gari. Ta kare da
sunkuyawa ta sumbaci kuncin yarinyar.tana
dagowa shima ya mayar da nasa sumbar
inda ta
sumbata,sannan ya dago ya sumbaci fatima.
Ya
ce cikin karsashi da kuma ji. "Ina son ku
fadima".
Ta yi sukuri tana kallon sa, sannan ta kada
kai.
"Muma haka".
******************************
*****************
Alhamdulillah ina godiya d fatan alkhairin d
kuke min nagode
Compelled by hauwee jidderh abdulkadir AKA mss jidderh
Chapter 5 · 0% Book details