Sashe 2
Me Zanyi Da Ita Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shatu ma hawayen take “yanzu innaji da gatanki muke ta yawo bama nan garin bama can mune har nan niger 🇳🇪 ashe asalinmu yan nigeria 🇳🇬 ne “. Innaji ta dafa kanta tace “kaddarar haihuwarki ne shatu da ta wannan cikin fatana idan kin sadu da dangina kice su yafe min na mutu ina tsananin kewarsu “. Share hawayenta tayi tace “insha Allah innaji ba zaki mutu ba da ‘kafarki zaki ga danginki “.
[8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-
2
Sumul suka farka innaji ranar ta d’an ji sau’ki, har yamma shatu na tare da ita Ta kasa motsawa ko nan da can ranar kam jikinta a sanyaye yake duk tsiwar da masifat ta zubar tana gefen innaji a zaune kan tabarmar karauni. Innajin Ta tsefe mata kanta Ta wanke tas da kanwa da karkashi sai ‘kyalli gashin yake yasha man kwakwa kasancewar shatu mai gashi na ban mamaki tamkar mutanen ‘kasar hindu don ma bata son gyarashi da ‘kyar take barin innajin ta ta’ba mata kai shima sai tayi mata jan ido.
Har aka gama tana kwance lamo ba mai magana tsakaninsu ita innaji tana karatun suratu maryama ita kuwa shatu ta lula duniyar tunani gaba d’aya ta rasa sukuni.har la’asar tayi kafin ta mi’ke tayi alwala ta kuma zubawa innajin ruwan alwala innaji ta kar’ba tana murmushi “ Allah yayi miki albarka shatu yasa ki cimma duk burin da nake miki fata a rayuwarki “. “Ameen “ shatu ta fad’a murya a sha’ke. Suna idarwa innajin ta aiketa gidan modibbo kar’bo rubutu.
Duk tsokanar da yara suke mata a hanya ranar banza tayi dasu burinta taje ta dawo ta iske innaji lafiya sumul, don haka take ta sauri kamar zata tashi sama.
Ko mintuna biyu bata yi ba a gidan moddibon ta juyo a sukwane ko saurarar gwaggoji ( salame) da take ‘kwala mata kira ba tayi ba.
Kamar an cillota haka ta afka tsakargidan da sauri ta saki ajiyar zuciya had’e da cewa Alhamdulillah Allah innaji na d’auka kafin na dawo kin mutu” murmushi innaji tayi kafin ta furta “mutuwa ai sai lokaci yayi ayshatu” da sauri ta dubeta jin sunan da ta kira ta dashi innaji ta waro ido tace “lafiya “ ta hau girgiza kai “ ji nayi kin kira ni da sunan da baki Ta’ba kira na ba “ dariya kawai tayi tana shan rubutun ta had’e da kallon shatu kallo mai nuna tsananin ‘kaunar da take mata.
Cikin dare innaji ta fara jin ciwon na’kuda tun tana daurewa har abin yaci ‘karfinta ta mi’ke da ‘kyar ta bud’e wata adaka ta zaro wasu hotuna da biro ta rubuta address din family house d’insu ta nad’e a takarda ko bakomai bata san ya ta Allah zata kasance ba.
Da ‘karfi ciwon yazo mata har bata san lokacin data fara tashin shatu ba a razane shatu ta tashi saboda wani mummunan mafarki da take a wannan lokacin, ganin innaji cikin wani mawuyacin hali bata san sanda ta zunduma ihu ba tana ru’kun’kumeta “ bana so innaaji bana son mafarkin da nayi ya tabbata “. Da kyar innaji ta’ka’kalo wani murmushi tana mi’ka mata takarda “ ayshatu ban san ya ta Allah zata kasance ba amma koma dai yayane bayan raina ki nemi dangi na idan mahaifana suna raye ki basu wannan takardar da wannan hoton suna gani sun san ke jini nace Ayshatu idan babanki ya dawo kice masa ya yafe ni Allah ya yanke ganawarmu “. Hawaye take yi sosai na tsananin azabar na’kuda. Ayshatu kuwa ta zama kamar mutum mutumi ta rasa ma mai zatayi abinka da’kan’kantar shekaru. Sai jijjiga innaji take ba bakin magana har zuwa sanda taji innajin ta saki kalmar shahada jikinta gaba d’aya ya saki ji kake d’if lamarin Alhakamu ya tabbata. Ita kuwa a nata tunanin barci innaji tayi bata san mutuwa ba bata san ya ake mutuwa ba gashi ana fad’a musu zafin fitar rai a yanda kuwa ake kwatantawa tabbas wannan ba mutuwa bace barcine ta ayyana hakan a ranta, don haka hankalinta kwance ita ma ta kwanta a gefen innajin barci ya kwasheta barcin da shine ya kaita har’karfe goma na safe.
Tana farkawa ta tashi a razane tana kallon hasken d’akin tare da tunanin me yasa innaji yau bata tashesu sallahr asuba ba. dubanta ta kai inda innajin take da sauri ta zare ido ganin idonta a kakkafe ya kalli sama ai bata san sanda ta hau jijjigata ba jin bata motsi yasa ta runtuma waje a guje tana Kiran jama’a “kuzo ku duba min innata tayi barcin zomo na tasheta ta’ki tashi “ ma’kota suka shiga gidan sai gani tayi suna fitowa jiki a salu’be ga kallon tausayi suna mata . Kalmar da taji wata ta fad’a ne Allah yaji’kanki maryamu halinki na gari ya biki yasa ta farka daga tunanin da take na cewa innaji barci take.aiko zuba hannu aka ta ‘kwalla’kara sai ganinta a kayi a zube ba numfashi.
Allahu akbar kabeeran Ubangiji kenan mai yin yarda yaso a lokacin da yaga dama Allah yaji’kan iyayenmu.
A safiyar juma’ar misalin ‘karfe sha d’aya na safe aka sada innaji zuwa gidanta na gaskiya hawaye sai zarya yake a fuskar abokan arziki kowa ya shaida innaji bata da abokin rigima to ita maganar ma bata dameta ba balle har ta samu abokin rigima. Shatu zube a cinyar gwaggoji sai mayar da ajiyar zuciya take da razana har sai da moddibo ya sake mata rubutu aka bata. To haka dama rayuwa take.
A hankali shatu ta fara sabawa da rashin innaji kullum kuwa ma’kale da takarda da hotunannan take kwana tayi al’kawarin sai ta sadu da dangin mahaifinta. Gidansu gwaggoji ta koma ta daina wanka ta daina komai wai ita ta gama jin dad’in duniya tunda innaji ta tafi ta barta. Yaran mutane kuwa a lokacin ta ‘kara takura musu musammam masu uwa raye shatu bata da ‘kiba sam amma sai ‘karfi ta gallabi mutanen garin tun ana d’aga mata’kafa saboda rashin uwa har tausayin ya kau aka fara kawo ‘kararta wajen gwaggoji. Gwaggoji bata da fad’a sam don haka shatu take’kara sangarcewa kullum da rashin jin da zata rakito ta kai yanzu har manya shiga shirginsu take musamman masu gonaki da suke kuka da ita.
Makaranta kuwa tuni tayi sallama da ita ta allo kawai take yi itama don moddibo yana cin gidansu ne da batayi ba. Gashi yanzu shi bashi da cikakkiyar lafiya yau fari gobe tsumma.
BAYAN WATA SHIDDA
Da rasuwar innaji jikin moddibo ya ‘kara tsananta, hakan yasa shi fara had’a komatsansa baya so ya mutu anan ya fito ya mutu cikin ahalinsa da suke garin yola. Itama gwaggoji hankalinta yafi kwanciya su tafi musamman saboda shatu ko bakomai a can dangi da yawa za’a samu mai tayasu kula da ita.
Safiyar wata asabar suka fito da ‘yan ‘kullin kayansu suka fara sallama da mutanen garin da suka yi dandazo a ‘kofar gida, duk jikinsu yayi sanyi musamman yara da suke kallon shatu Idanunsu fal ‘kwalla. Shatun ma kuka take ta kalli yaran tana murmushi “kuyi min tsokanar’karshe don Allah ko bakomai zan dinga tuna ku.” Shiru su kayi mata, murya na rawa ta fara binsu d’aya bayan d’aya tana cewa “ku fad’a mujiya mai idonta a loko....” Ai kuwa yara suka fara har ita suna kuka kuka, dariya- dariya a haka suka rakasu har inda mai amalanke yazo ya d’ebesu tana d’aga musu hannu suna bin amalanke , rayuwa kenan ba mamaki shikkenan tayi sallama da garin nijar. Amma ta’kudirce insha Allah zata dawo.
Kwanansu kusan biyu suna tafiya, kafin Allah ya kawo su garin yola nan suka hau motar garinsu demsa, daga demsa suka shiga wata’kur’kura ta isar dasu cikin ‘kauyensu gwamba. Ai kuwa mutanen garin suna ganinsu suka shiga fitowa ana murnar ganinsu.
Bayan sun shiga cikin gidan mai girman gaske ginin’kasa suka fara yiwa juna gaisuwa anan suke jin labarin mutuwar muji mahaifin shatu. Ashe da ya taho hatsari yayi a garin yola hakan yasa ya bada address din family house d’insu na nan kafin a kawo shi kuma rai yayi halinsa. Su kuma basu san inda zasu samesu ba. hankalin shatu ya tashi ta zube wajen har iskokanta suka ziyarceta, kowa a wajen ya tausaya mata musamman da suka ji labarin rasuwar maryamu ma. Moddibo kuwa innalillahi wa inna ilaihir raji’una yake ja kansa yana juyawa sai gani a kayi shima luuuuu ya kifa. Ai ko ana d’ago shi aka ga rai yayi halinsa. Nan kuwa koke- koke ya ‘karu shatu kuwa kuka take aljannun Na sake bugeta. Gwaggoji kuwa kasa magana tayi tana taajjabin lamarin Ubangiji ashe haka mutuwa take lokaci d’aya taji mutuwar d’anta ‘kwaya guda da rage bata dawo daga razanin ba shima mijin ya mutu, ai ji tayi ina ma ita ma ubangiji ya d’au ranta.
Moddibo kam ya dace ya mutu ranar juma’a aka sadashi da gidansa Na gaskiya. Haka rayuwa take Allah yasa mu cika da imani .
Gwaggoji daga ranar bata sake samun lafiya ba. sai dai a kwantar a tayar, hankalin shatu ya matu’kar tashi duk ta sake firgai firgai ko wanka batayi, bata so ta rasa gwaggoji a karo na hud’u Ta san idan ta rasa gwaggoji gatanta ya gama zubewa warwas. Mutanen nan taga basu da zumunci ko a yanzu haka ita take yiwa gwaggojin komai hatta da gyara jiki idan ta’bata. Iyakacinsu da su abinci shima ko yaro’karami zai iya cinyeshi.
[8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-
2
Sumul suka farka innaji ranar ta d’an ji sau’ki, har yamma shatu na tare da ita Ta kasa motsawa ko nan da can ranar kam jikinta a sanyaye yake duk tsiwar da masifat ta zubar tana gefen innaji a zaune kan tabarmar karauni. Innajin Ta tsefe mata kanta Ta wanke tas da kanwa da karkashi sai ‘kyalli gashin yake yasha man kwakwa kasancewar shatu mai gashi na ban mamaki tamkar mutanen ‘kasar hindu don ma bata son gyarashi da ‘kyar take barin innajin ta ta’ba mata kai shima sai tayi mata jan ido.
Har aka gama tana kwance lamo ba mai magana tsakaninsu ita innaji tana karatun suratu maryama ita kuwa shatu ta lula duniyar tunani gaba d’aya ta rasa sukuni.har la’asar tayi kafin ta mi’ke tayi alwala ta kuma zubawa innajin ruwan alwala innaji ta kar’ba tana murmushi “ Allah yayi miki albarka shatu yasa ki cimma duk burin da nake miki fata a rayuwarki “. “Ameen “ shatu ta fad’a murya a sha’ke. Suna idarwa innajin ta aiketa gidan modibbo kar’bo rubutu.
Duk tsokanar da yara suke mata a hanya ranar banza tayi dasu burinta taje ta dawo ta iske innaji lafiya sumul, don haka take ta sauri kamar zata tashi sama.
Ko mintuna biyu bata yi ba a gidan moddibon ta juyo a sukwane ko saurarar gwaggoji ( salame) da take ‘kwala mata kira ba tayi ba.
Kamar an cillota haka ta afka tsakargidan da sauri ta saki ajiyar zuciya had’e da cewa Alhamdulillah Allah innaji na d’auka kafin na dawo kin mutu” murmushi innaji tayi kafin ta furta “mutuwa ai sai lokaci yayi ayshatu” da sauri ta dubeta jin sunan da ta kira ta dashi innaji ta waro ido tace “lafiya “ ta hau girgiza kai “ ji nayi kin kira ni da sunan da baki Ta’ba kira na ba “ dariya kawai tayi tana shan rubutun ta had’e da kallon shatu kallo mai nuna tsananin ‘kaunar da take mata.
Cikin dare innaji ta fara jin ciwon na’kuda tun tana daurewa har abin yaci ‘karfinta ta mi’ke da ‘kyar ta bud’e wata adaka ta zaro wasu hotuna da biro ta rubuta address din family house d’insu ta nad’e a takarda ko bakomai bata san ya ta Allah zata kasance ba.
Da ‘karfi ciwon yazo mata har bata san lokacin data fara tashin shatu ba a razane shatu ta tashi saboda wani mummunan mafarki da take a wannan lokacin, ganin innaji cikin wani mawuyacin hali bata san sanda ta zunduma ihu ba tana ru’kun’kumeta “ bana so innaaji bana son mafarkin da nayi ya tabbata “. Da kyar innaji ta’ka’kalo wani murmushi tana mi’ka mata takarda “ ayshatu ban san ya ta Allah zata kasance ba amma koma dai yayane bayan raina ki nemi dangi na idan mahaifana suna raye ki basu wannan takardar da wannan hoton suna gani sun san ke jini nace Ayshatu idan babanki ya dawo kice masa ya yafe ni Allah ya yanke ganawarmu “. Hawaye take yi sosai na tsananin azabar na’kuda. Ayshatu kuwa ta zama kamar mutum mutumi ta rasa ma mai zatayi abinka da’kan’kantar shekaru. Sai jijjiga innaji take ba bakin magana har zuwa sanda taji innajin ta saki kalmar shahada jikinta gaba d’aya ya saki ji kake d’if lamarin Alhakamu ya tabbata. Ita kuwa a nata tunanin barci innaji tayi bata san mutuwa ba bata san ya ake mutuwa ba gashi ana fad’a musu zafin fitar rai a yanda kuwa ake kwatantawa tabbas wannan ba mutuwa bace barcine ta ayyana hakan a ranta, don haka hankalinta kwance ita ma ta kwanta a gefen innajin barci ya kwasheta barcin da shine ya kaita har’karfe goma na safe.
Tana farkawa ta tashi a razane tana kallon hasken d’akin tare da tunanin me yasa innaji yau bata tashesu sallahr asuba ba. dubanta ta kai inda innajin take da sauri ta zare ido ganin idonta a kakkafe ya kalli sama ai bata san sanda ta hau jijjigata ba jin bata motsi yasa ta runtuma waje a guje tana Kiran jama’a “kuzo ku duba min innata tayi barcin zomo na tasheta ta’ki tashi “ ma’kota suka shiga gidan sai gani tayi suna fitowa jiki a salu’be ga kallon tausayi suna mata . Kalmar da taji wata ta fad’a ne Allah yaji’kanki maryamu halinki na gari ya biki yasa ta farka daga tunanin da take na cewa innaji barci take.aiko zuba hannu aka ta ‘kwalla’kara sai ganinta a kayi a zube ba numfashi.
Allahu akbar kabeeran Ubangiji kenan mai yin yarda yaso a lokacin da yaga dama Allah yaji’kan iyayenmu.
A safiyar juma’ar misalin ‘karfe sha d’aya na safe aka sada innaji zuwa gidanta na gaskiya hawaye sai zarya yake a fuskar abokan arziki kowa ya shaida innaji bata da abokin rigima to ita maganar ma bata dameta ba balle har ta samu abokin rigima. Shatu zube a cinyar gwaggoji sai mayar da ajiyar zuciya take da razana har sai da moddibo ya sake mata rubutu aka bata. To haka dama rayuwa take.
A hankali shatu ta fara sabawa da rashin innaji kullum kuwa ma’kale da takarda da hotunannan take kwana tayi al’kawarin sai ta sadu da dangin mahaifinta. Gidansu gwaggoji ta koma ta daina wanka ta daina komai wai ita ta gama jin dad’in duniya tunda innaji ta tafi ta barta. Yaran mutane kuwa a lokacin ta ‘kara takura musu musammam masu uwa raye shatu bata da ‘kiba sam amma sai ‘karfi ta gallabi mutanen garin tun ana d’aga mata’kafa saboda rashin uwa har tausayin ya kau aka fara kawo ‘kararta wajen gwaggoji. Gwaggoji bata da fad’a sam don haka shatu take’kara sangarcewa kullum da rashin jin da zata rakito ta kai yanzu har manya shiga shirginsu take musamman masu gonaki da suke kuka da ita.
Makaranta kuwa tuni tayi sallama da ita ta allo kawai take yi itama don moddibo yana cin gidansu ne da batayi ba. Gashi yanzu shi bashi da cikakkiyar lafiya yau fari gobe tsumma.
BAYAN WATA SHIDDA
Da rasuwar innaji jikin moddibo ya ‘kara tsananta, hakan yasa shi fara had’a komatsansa baya so ya mutu anan ya fito ya mutu cikin ahalinsa da suke garin yola. Itama gwaggoji hankalinta yafi kwanciya su tafi musamman saboda shatu ko bakomai a can dangi da yawa za’a samu mai tayasu kula da ita.
Safiyar wata asabar suka fito da ‘yan ‘kullin kayansu suka fara sallama da mutanen garin da suka yi dandazo a ‘kofar gida, duk jikinsu yayi sanyi musamman yara da suke kallon shatu Idanunsu fal ‘kwalla. Shatun ma kuka take ta kalli yaran tana murmushi “kuyi min tsokanar’karshe don Allah ko bakomai zan dinga tuna ku.” Shiru su kayi mata, murya na rawa ta fara binsu d’aya bayan d’aya tana cewa “ku fad’a mujiya mai idonta a loko....” Ai kuwa yara suka fara har ita suna kuka kuka, dariya- dariya a haka suka rakasu har inda mai amalanke yazo ya d’ebesu tana d’aga musu hannu suna bin amalanke , rayuwa kenan ba mamaki shikkenan tayi sallama da garin nijar. Amma ta’kudirce insha Allah zata dawo.
Kwanansu kusan biyu suna tafiya, kafin Allah ya kawo su garin yola nan suka hau motar garinsu demsa, daga demsa suka shiga wata’kur’kura ta isar dasu cikin ‘kauyensu gwamba. Ai kuwa mutanen garin suna ganinsu suka shiga fitowa ana murnar ganinsu.
Bayan sun shiga cikin gidan mai girman gaske ginin’kasa suka fara yiwa juna gaisuwa anan suke jin labarin mutuwar muji mahaifin shatu. Ashe da ya taho hatsari yayi a garin yola hakan yasa ya bada address din family house d’insu na nan kafin a kawo shi kuma rai yayi halinsa. Su kuma basu san inda zasu samesu ba. hankalin shatu ya tashi ta zube wajen har iskokanta suka ziyarceta, kowa a wajen ya tausaya mata musamman da suka ji labarin rasuwar maryamu ma. Moddibo kuwa innalillahi wa inna ilaihir raji’una yake ja kansa yana juyawa sai gani a kayi shima luuuuu ya kifa. Ai ko ana d’ago shi aka ga rai yayi halinsa. Nan kuwa koke- koke ya ‘karu shatu kuwa kuka take aljannun Na sake bugeta. Gwaggoji kuwa kasa magana tayi tana taajjabin lamarin Ubangiji ashe haka mutuwa take lokaci d’aya taji mutuwar d’anta ‘kwaya guda da rage bata dawo daga razanin ba shima mijin ya mutu, ai ji tayi ina ma ita ma ubangiji ya d’au ranta.
Moddibo kam ya dace ya mutu ranar juma’a aka sadashi da gidansa Na gaskiya. Haka rayuwa take Allah yasa mu cika da imani .
Gwaggoji daga ranar bata sake samun lafiya ba. sai dai a kwantar a tayar, hankalin shatu ya matu’kar tashi duk ta sake firgai firgai ko wanka batayi, bata so ta rasa gwaggoji a karo na hud’u Ta san idan ta rasa gwaggoji gatanta ya gama zubewa warwas. Mutanen nan taga basu da zumunci ko a yanzu haka ita take yiwa gwaggojin komai hatta da gyara jiki idan ta’bata. Iyakacinsu da su abinci shima ko yaro’karami zai iya cinyeshi.