Sashe 9
Matar Shege Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya ce"a'a,shikenan an bar shi". Mu ka d'an yi fira,har ya nuna min gidanshi,wanda za mu zauna a ciki,na kalla na ce ya yi kyau,ya tambayeni komai ya yi min,ko da wani gyaran? Na ce ai gidanshi ne,kar ya biyewa ra'ayina,bai jima ba ya tafi,don dama daga wurin aiki ya zo gidan namu.
Ya na tafiya nima na k'ara gaba,wurin Anas na je na ari wayarsa,na saka lambata a ciki na danna kira,ban yi zaton za a d'aga ba,don duk a zatona har yanzu ta na d'akin babu wanda ganta,ga mamaki na sai na ji muryar mace ta d'aga da sallama, na amsa ina nazarin muryar,mu ka yi shiru na y'an sakanni kafin ta ce"waye me magana?"
"Me wayar ce" Na bata amsa
Ta ce"Zinatu ce?"
Na ce"e,sai na ji muryar kamar ta Baby"
Ta ce"e ni ce,wayarki ta na hannuna,ki kwatanta min gidanku zan zo na kawo miki yanzu".
Na d'an yi jim! Ina tunanin ta yanda wayar ta je hannunta,sannan na kwatanta mata tiryan-tiryan,ta yi min godiya ta ce ga ta nan zuwa.
Na bawa Anas wayarsa,sai da na siyi ruwa da lemo sannan na koma gida,na d'an k'ara kimtsa d'akina na kunna turaren tsinke,har tsakar gidan nan share,duk da na ga Mama ta share da safe,Allah ma ya taimakeni ma su siyan waina sun watse,na koma d'akina ina zaman jiranta
Ina kwance ina sak'a da warwara na ji muryarta ta na rangad'a sallama na tashi na tareta da fara'a,Allah ya taimaka Mama ba ta nan,bare ta sa mana ido,bayan ta zauna mu ka gaisa,na ba ta ruwa
Ba ta sha ba ma,ta mik'o min jakata sannan ta nisa ta ce"Zinatu zan tambayeki,ki fad'a min gaskiya don Allah".
Na d'an ji dam! Na ce"to in sha Allah".
Ta ce"menene ya had'aku da Salim har ki ka je d'akinsa ki ka manta jaka?"
Na yi shiru ina tunanin na fad'a mata gaskiya,ko na yi k'aryar da za ta shigar da ni rayuwar Salim.Ban gama yanke shawara ba na ji muryarta "don Allah ke ki fad'a min gaskiya, shi ina kokwanto akan abin da ya fad'a min".
Cikin y'an sakanni dabara ta zo min,na ce" zan fad'a miki gaskiya, amma da sharad'i".
Da d'an mamaki ta ce"sharad'i kuma? Na meye?"
Na gyara zama na ce"ina son ki ba ni labarin soyayyar Salim da Junaina,da kuma abin da ya rabasu,sannan ki samo min lambar ita Junainan,ko kuma adireshin ta".
Baby ta tsaya kallona kamar me nazari,cikin so tabbatar mata na ce"wannan shi ne sharad'in,amma idan ba zai yiwu ba babu dole fa,za ki iya auna k'aryar da Salim ya yi miki".
Ta nisa kafin ta ce"amma ke me yasa ki ke son jin labarin?"
Na ce"ina da babban dalili,ke dai ki sanar min daga baya kya ji dalilin"
Ta ce"to shikenan,amma dai kin san ba zai yiwu na san komai ba,saboda haka iya wanda na sani zan sanar dake".
Na gyad'a kai alamar gamsuwa.Ta fara ba ni labari "Junaina y'ar jihar Katsina ce,a Manumfashi,gidansu su na da yawa,amma ita k'ad'aice mace,ta na da kyau babu laifi,ina tunanin za ta kai shekara ashirin da biyar.Wani yayanta ne abokin Salim,wanda su ka yi makaranta tare a Egypt.Wata rana Salim ya kai masa ziyara Katsina,saboda ya duba shi,sakamakon rashin lafiya da ya ke yi,a ranar ne suka had'u da Junaina,Yaya ya ce ya na ganinta ya ji k'aunar ta,amma ya dake har ya baro garin bai nuna ba,ashe ita ma haka ta kamu da son shi,ta samu lambar shi a wurin yayanta,ta yi ta damunsa da kira da sak'onni har dai ta bayyana masa son shi take,ya amince da ita,ya na mugun son ta sosai,lokaci d'aya duka dangi kowa ya sani saboda yawan zuwa Katsina da yake yi,in dai ka na son ganin Salim a farinciki to ka yi masa firar Junaina.Ganin da gaske suke soyayyar, ya sa Abbanmu ya ce ai kawai gwara ayi auren kowa ya samu nutsuwa,sai dai ana zuwa da zancen aure Junaina ta ce ta amince,amma ba yanzu ba,sai ta yi digiri"
Baby ta sauke numfashi,ta tab'e baki ta ce"saboda babu gaskiya, tun da me take yi ba ta yi digirin ba?"
"Gaskiya kam!" Na fad'a ina gyara zama.
Ta cigaba "kuma ta ce ita a Kano take son yin karatun,Yaya ya fi kowa jin dad'in hakan,saboda ya dinga ganinta akai-akai,admission ma shi ne ya sama mata,kuma ya d'auki nauyin karatun ta da duk wasu buk'atun ta,mahaifinta shi dai godiya ce kawai aikinsa,B U K ta fara zuwa,da farko ta na karatun kamar abin arzik'i,Salim ya na ta hidima da ita,sai daga baya wasu mazan suka fara d'auke mata hankali,mutane da yawa sun so ankarar da Salim,amma ya k'i yarda,saboda tsabar k'aunarta.Haka ake ta tafiya,abun Junaina ya na k'ara gaba,shi kuma ya na k'ara rufe idonsa,har dai ta kai ga ta daina b'oye masa komai, ta na kula samari a gabansa,ya sha zuwa ya tarar da ita da saurayi sai ta ce masa abokinta ne,idan ya ga abun bai yi masa ba zai iya canza shek'a,haka ya yi ta hak'uri ya na daurewa,saboda ba ya so ya rasa ta"
"Kin san wani abun takaici?". Ta dakata,tare da tambaya ta.
Na girgiza kai alamar a'a.Ta d'ora" daga k'arshe dai Junaina sai da ta yarda da samarin shaho,suka d'auke mata hankali,tun ta na yiwa makaranta asha ruwan tsuntsaye har ta daina karatun duka,wani saurayin ta ya kama mata gida a 'Dorayi,yanzu haka ta na can da zama".
"Subhanallah! Zaman kanta take yi kenan?" Na tambaye ta da mamaki.
Ba ta bani amsa ba ta d'ora"lokacin da ya ankara kar ki so ki ga yanda ya shiga tashin hankali,sai da ya kusa shafe wata d'aya a kwance,ya na daga kwancen yana kiran wayarta,amma wallahi ba ta zo ta duba shi ba.Da k'yar mu ka samo kan shi,ya dawo cikin hayyacin sa,amma duk da haka sai ya cigaba da bibiyarta,ita kuma ta na yi masa wulak'anci son ranta,amma wai a hakan ta ce masa shi za ta aura idan zai jirata,kuma kud'i ko nawa ne idan tana bukata shi take tambaya ya tura mata ko ya kai mata".
Na jinjina kai na ce"tabb! Amma wannan ta cika y'ar rainin hankali!".
Baby ta ce"ai duk ba ma wannan bane abin haushin,kin san kuwa y'an'uwanta shi suke zargi da lalata musu y'arsu?"
Na zaro ido cikin mamaki na ce"rainin hankali! Ai sai su zo su gani"
Baby ta ce"su ga me!? Shi fa suka kira,kuma ya tabbatar musu da shi ne ,kawai saboda ya kareta. Ke so fa k'addara ne!"
Na ce "tabbas! Lallai wannan Junaina ta cika mara rabo".
Ta cigaba"to daga baya ta dawo ta ce masa ta daina komai,ya ba ta jari za ta fara sana'a,saboda mahaifinta ya gargad'e ta k'ar ta kuskura ta koma Katsina,jiki na rawa ya d'auki kud'i masu yawa ya bata,ta bud'e wani wurin sai da kayan sawa,na maza da mata,amma duk da haka dai ta k'i yarda da auren su.Ba mu san lokacin da ya fara shaye-shaye ba,ba mu san dalili ba,amma gaskiya duk mun fi danganta abun da halin da Junaina ta saka shi ne ya jefa shi a harkar".
Ta d'ora " kuma ya ce shi zai jira har lokacin da za ta nutsu,ta amince da aurensa,ba zai tab'a yin aure ba,saboda ta ce muddin ya yi aure to ta rabu da shi har abada! A cewar shi dai yanzu ya rabu da ita,amma duk ba mu yarda ba,sai dai daga lokacin da na ga jakarki a d'akinsa na fara zargin wani abun kuma na da ban.Wannan shi ne labarin Junaina,sai ki cika alk'awari ki fad'a min gaskiyar tsakanin ki da Yaya".
Hawayen da ban tantance ko na meye ba suka shiga zubo min,tun ina gogewa har na fashe da kuka sosai.Wata k'aunar Salim da tausayin shi suka yiwa zuciyata dirar mikiya,har na ji idan ba shi na aura ba ni ma har abada ba zan yi auren ba.
Baby ta tsaya ta na kallona da alamun mamaki,sannan ta ce"Allah yasa dai ba zatona bane ya ke shirin tabbata!".
Na yi shiru ina saita kaina,na ce"ko kad'an,Baby kar ki zargeni ko d'an'uwanki,yanda ya fad'a miki d'in na san gaskiya ne...". Na kwashe labarin tun farkon had'uwarmu har izuwa ranar da na bar jakata na fad'a mata.
Ta yi shiru kamar me tunani,sannan ta kalleni ta ce"Zinatu tsakanin ki da Allah da gaske ki ke son Salim?"
Na yi saurin fad'in"wallahi har zuciyata nake k'aunar Salim,tunda na yi masa kallo d'aya,idan so ya na zama k'addara to son Salim shi ne tawa k'addarar". Na fashe da kuka
Cikin sanyin murya ta ce"ayya! Ki bar kukan haka,ba zan yi miki alk'awarin auren Salim ba,amma zan yi iya yi na ganin na had'a alak'ar ku,ke ma sai ki had'a da addu'a, da kuma y'an dabarun ki".
Na ce"na gode sosai y'ar'uwa,amma a ganina me zai hana na shiga jikin Junaina,na karanci halaye da d'abi'unta,ko koyi da ita zai sa Salim ya maye gurbinta da ni?"
Baby ta yi murmushi ta ce"Zinatu gurbin ido ba ido bane,kuma shi so babu ruwan shi da halayya,tunda ita d'in yake so,to fa ko za ki yi birgima a tab'o ki koma kamarta sak,bai zama lallai ya so ki ba".
Na jinjina kai na ce"hakane,amma duk da haka ina son ganin ta dai,ki taimakeni da lambarta don Allah".
Ta ce"wa!? Ni kam me zan yi da lambarta,kin san yanda na tsaneta kuwa? Zan dai kwatanta miki wurin sana'arta idan ki na so".
"Ina so!" Na fad'a da sauri.
Ta kwatanta min,babu nisa ma sosai,a zoo road ne wurin,kuma siffanta min kamannin ta
Na rakata har bakin titi ina ta kwarara mata godiya kamar ba gobe.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 11
Ina dawowa daga rakiyar Baby,na zauna na kira lambar Salim,har ta katse bai d'auka ba,sai da na kira sau uku sannan ya d'aga cikin fushi ya ce"ke! Lafiya kike kira na?"
Na d'an ji fad'uwar gaba,amma na dake na ce"lafiya lau,na kira ne kawai na gaishe ka,kuma na ji lafiyarka".
Bai bani amsa ba,kawai ya kashe wayar.Na had'a kai da gwuiwa,hawaye suka min sallama,na jima a haka ina nazari kafin na tashi cikin sauri,kamar an tsikare ni
Ya na tafiya nima na k'ara gaba,wurin Anas na je na ari wayarsa,na saka lambata a ciki na danna kira,ban yi zaton za a d'aga ba,don duk a zatona har yanzu ta na d'akin babu wanda ganta,ga mamaki na sai na ji muryar mace ta d'aga da sallama, na amsa ina nazarin muryar,mu ka yi shiru na y'an sakanni kafin ta ce"waye me magana?"
"Me wayar ce" Na bata amsa
Ta ce"Zinatu ce?"
Na ce"e,sai na ji muryar kamar ta Baby"
Ta ce"e ni ce,wayarki ta na hannuna,ki kwatanta min gidanku zan zo na kawo miki yanzu".
Na d'an yi jim! Ina tunanin ta yanda wayar ta je hannunta,sannan na kwatanta mata tiryan-tiryan,ta yi min godiya ta ce ga ta nan zuwa.
Na bawa Anas wayarsa,sai da na siyi ruwa da lemo sannan na koma gida,na d'an k'ara kimtsa d'akina na kunna turaren tsinke,har tsakar gidan nan share,duk da na ga Mama ta share da safe,Allah ma ya taimakeni ma su siyan waina sun watse,na koma d'akina ina zaman jiranta
Ina kwance ina sak'a da warwara na ji muryarta ta na rangad'a sallama na tashi na tareta da fara'a,Allah ya taimaka Mama ba ta nan,bare ta sa mana ido,bayan ta zauna mu ka gaisa,na ba ta ruwa
Ba ta sha ba ma,ta mik'o min jakata sannan ta nisa ta ce"Zinatu zan tambayeki,ki fad'a min gaskiya don Allah".
Na d'an ji dam! Na ce"to in sha Allah".
Ta ce"menene ya had'aku da Salim har ki ka je d'akinsa ki ka manta jaka?"
Na yi shiru ina tunanin na fad'a mata gaskiya,ko na yi k'aryar da za ta shigar da ni rayuwar Salim.Ban gama yanke shawara ba na ji muryarta "don Allah ke ki fad'a min gaskiya, shi ina kokwanto akan abin da ya fad'a min".
Cikin y'an sakanni dabara ta zo min,na ce" zan fad'a miki gaskiya, amma da sharad'i".
Da d'an mamaki ta ce"sharad'i kuma? Na meye?"
Na gyara zama na ce"ina son ki ba ni labarin soyayyar Salim da Junaina,da kuma abin da ya rabasu,sannan ki samo min lambar ita Junainan,ko kuma adireshin ta".
Baby ta tsaya kallona kamar me nazari,cikin so tabbatar mata na ce"wannan shi ne sharad'in,amma idan ba zai yiwu ba babu dole fa,za ki iya auna k'aryar da Salim ya yi miki".
Ta nisa kafin ta ce"amma ke me yasa ki ke son jin labarin?"
Na ce"ina da babban dalili,ke dai ki sanar min daga baya kya ji dalilin"
Ta ce"to shikenan,amma dai kin san ba zai yiwu na san komai ba,saboda haka iya wanda na sani zan sanar dake".
Na gyad'a kai alamar gamsuwa.Ta fara ba ni labari "Junaina y'ar jihar Katsina ce,a Manumfashi,gidansu su na da yawa,amma ita k'ad'aice mace,ta na da kyau babu laifi,ina tunanin za ta kai shekara ashirin da biyar.Wani yayanta ne abokin Salim,wanda su ka yi makaranta tare a Egypt.Wata rana Salim ya kai masa ziyara Katsina,saboda ya duba shi,sakamakon rashin lafiya da ya ke yi,a ranar ne suka had'u da Junaina,Yaya ya ce ya na ganinta ya ji k'aunar ta,amma ya dake har ya baro garin bai nuna ba,ashe ita ma haka ta kamu da son shi,ta samu lambar shi a wurin yayanta,ta yi ta damunsa da kira da sak'onni har dai ta bayyana masa son shi take,ya amince da ita,ya na mugun son ta sosai,lokaci d'aya duka dangi kowa ya sani saboda yawan zuwa Katsina da yake yi,in dai ka na son ganin Salim a farinciki to ka yi masa firar Junaina.Ganin da gaske suke soyayyar, ya sa Abbanmu ya ce ai kawai gwara ayi auren kowa ya samu nutsuwa,sai dai ana zuwa da zancen aure Junaina ta ce ta amince,amma ba yanzu ba,sai ta yi digiri"
Baby ta sauke numfashi,ta tab'e baki ta ce"saboda babu gaskiya, tun da me take yi ba ta yi digirin ba?"
"Gaskiya kam!" Na fad'a ina gyara zama.
Ta cigaba "kuma ta ce ita a Kano take son yin karatun,Yaya ya fi kowa jin dad'in hakan,saboda ya dinga ganinta akai-akai,admission ma shi ne ya sama mata,kuma ya d'auki nauyin karatun ta da duk wasu buk'atun ta,mahaifinta shi dai godiya ce kawai aikinsa,B U K ta fara zuwa,da farko ta na karatun kamar abin arzik'i,Salim ya na ta hidima da ita,sai daga baya wasu mazan suka fara d'auke mata hankali,mutane da yawa sun so ankarar da Salim,amma ya k'i yarda,saboda tsabar k'aunarta.Haka ake ta tafiya,abun Junaina ya na k'ara gaba,shi kuma ya na k'ara rufe idonsa,har dai ta kai ga ta daina b'oye masa komai, ta na kula samari a gabansa,ya sha zuwa ya tarar da ita da saurayi sai ta ce masa abokinta ne,idan ya ga abun bai yi masa ba zai iya canza shek'a,haka ya yi ta hak'uri ya na daurewa,saboda ba ya so ya rasa ta"
"Kin san wani abun takaici?". Ta dakata,tare da tambaya ta.
Na girgiza kai alamar a'a.Ta d'ora" daga k'arshe dai Junaina sai da ta yarda da samarin shaho,suka d'auke mata hankali,tun ta na yiwa makaranta asha ruwan tsuntsaye har ta daina karatun duka,wani saurayin ta ya kama mata gida a 'Dorayi,yanzu haka ta na can da zama".
"Subhanallah! Zaman kanta take yi kenan?" Na tambaye ta da mamaki.
Ba ta bani amsa ba ta d'ora"lokacin da ya ankara kar ki so ki ga yanda ya shiga tashin hankali,sai da ya kusa shafe wata d'aya a kwance,ya na daga kwancen yana kiran wayarta,amma wallahi ba ta zo ta duba shi ba.Da k'yar mu ka samo kan shi,ya dawo cikin hayyacin sa,amma duk da haka sai ya cigaba da bibiyarta,ita kuma ta na yi masa wulak'anci son ranta,amma wai a hakan ta ce masa shi za ta aura idan zai jirata,kuma kud'i ko nawa ne idan tana bukata shi take tambaya ya tura mata ko ya kai mata".
Na jinjina kai na ce"tabb! Amma wannan ta cika y'ar rainin hankali!".
Baby ta ce"ai duk ba ma wannan bane abin haushin,kin san kuwa y'an'uwanta shi suke zargi da lalata musu y'arsu?"
Na zaro ido cikin mamaki na ce"rainin hankali! Ai sai su zo su gani"
Baby ta ce"su ga me!? Shi fa suka kira,kuma ya tabbatar musu da shi ne ,kawai saboda ya kareta. Ke so fa k'addara ne!"
Na ce "tabbas! Lallai wannan Junaina ta cika mara rabo".
Ta cigaba"to daga baya ta dawo ta ce masa ta daina komai,ya ba ta jari za ta fara sana'a,saboda mahaifinta ya gargad'e ta k'ar ta kuskura ta koma Katsina,jiki na rawa ya d'auki kud'i masu yawa ya bata,ta bud'e wani wurin sai da kayan sawa,na maza da mata,amma duk da haka dai ta k'i yarda da auren su.Ba mu san lokacin da ya fara shaye-shaye ba,ba mu san dalili ba,amma gaskiya duk mun fi danganta abun da halin da Junaina ta saka shi ne ya jefa shi a harkar".
Ta d'ora " kuma ya ce shi zai jira har lokacin da za ta nutsu,ta amince da aurensa,ba zai tab'a yin aure ba,saboda ta ce muddin ya yi aure to ta rabu da shi har abada! A cewar shi dai yanzu ya rabu da ita,amma duk ba mu yarda ba,sai dai daga lokacin da na ga jakarki a d'akinsa na fara zargin wani abun kuma na da ban.Wannan shi ne labarin Junaina,sai ki cika alk'awari ki fad'a min gaskiyar tsakanin ki da Yaya".
Hawayen da ban tantance ko na meye ba suka shiga zubo min,tun ina gogewa har na fashe da kuka sosai.Wata k'aunar Salim da tausayin shi suka yiwa zuciyata dirar mikiya,har na ji idan ba shi na aura ba ni ma har abada ba zan yi auren ba.
Baby ta tsaya ta na kallona da alamun mamaki,sannan ta ce"Allah yasa dai ba zatona bane ya ke shirin tabbata!".
Na yi shiru ina saita kaina,na ce"ko kad'an,Baby kar ki zargeni ko d'an'uwanki,yanda ya fad'a miki d'in na san gaskiya ne...". Na kwashe labarin tun farkon had'uwarmu har izuwa ranar da na bar jakata na fad'a mata.
Ta yi shiru kamar me tunani,sannan ta kalleni ta ce"Zinatu tsakanin ki da Allah da gaske ki ke son Salim?"
Na yi saurin fad'in"wallahi har zuciyata nake k'aunar Salim,tunda na yi masa kallo d'aya,idan so ya na zama k'addara to son Salim shi ne tawa k'addarar". Na fashe da kuka
Cikin sanyin murya ta ce"ayya! Ki bar kukan haka,ba zan yi miki alk'awarin auren Salim ba,amma zan yi iya yi na ganin na had'a alak'ar ku,ke ma sai ki had'a da addu'a, da kuma y'an dabarun ki".
Na ce"na gode sosai y'ar'uwa,amma a ganina me zai hana na shiga jikin Junaina,na karanci halaye da d'abi'unta,ko koyi da ita zai sa Salim ya maye gurbinta da ni?"
Baby ta yi murmushi ta ce"Zinatu gurbin ido ba ido bane,kuma shi so babu ruwan shi da halayya,tunda ita d'in yake so,to fa ko za ki yi birgima a tab'o ki koma kamarta sak,bai zama lallai ya so ki ba".
Na jinjina kai na ce"hakane,amma duk da haka ina son ganin ta dai,ki taimakeni da lambarta don Allah".
Ta ce"wa!? Ni kam me zan yi da lambarta,kin san yanda na tsaneta kuwa? Zan dai kwatanta miki wurin sana'arta idan ki na so".
"Ina so!" Na fad'a da sauri.
Ta kwatanta min,babu nisa ma sosai,a zoo road ne wurin,kuma siffanta min kamannin ta
Na rakata har bakin titi ina ta kwarara mata godiya kamar ba gobe.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 11
Ina dawowa daga rakiyar Baby,na zauna na kira lambar Salim,har ta katse bai d'auka ba,sai da na kira sau uku sannan ya d'aga cikin fushi ya ce"ke! Lafiya kike kira na?"
Na d'an ji fad'uwar gaba,amma na dake na ce"lafiya lau,na kira ne kawai na gaishe ka,kuma na ji lafiyarka".
Bai bani amsa ba,kawai ya kashe wayar.Na had'a kai da gwuiwa,hawaye suka min sallama,na jima a haka ina nazari kafin na tashi cikin sauri,kamar an tsikare ni