Sashe 15
Matar Shege Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar haka na wuni ina ta tunanin ta inda zan samu wannan kud'in,to ni kam indai ba kayan lefena zan siyar ba ta ina kud'in za su fito? Ga shi sai hanya-hanya ya ke min,ya k'i sanar min yanda aikin ya ke,da dubu hamsin ne ma da tsaf zan shafawa idona toka na tambayi Habib,don na tabbata zai bani,amma gaskiya dubu d'ari biyu ya yi yawa,da me zai ji? Ga duka ga tsinka jaka!
Dab da magriba na tambayi Anti zan je gida na d'akko wasu kayana,sai da ta yi min fad'a kafin ta bar ni,wai meyasa tun safe ban je ba sai da magriba? Haka dai na shirya na tafi shagon Baby,sai dai ina zuwa na tarar ba ta nan,wai lokacin tafiyarta gida ya yi.Na kirata a waya na sanar mata na zo mata nan,ta ce sai dai na k'araso gidansu tunda babu nisa,ta kwatanta min na kama hanya.
WANI KUSKURE...
Ban san zuwa na gidan su Salim a lokacin kuskure bane sai daga baya,da na je na tarar da megadi,amma bai hana ni shiga ba,ina dai tunanin Baby ta sanar masa za ta yi bak'uwa,lokacin har an shiga masallaci ana sallar magriba,a tsakar gida na tadda Baby,ta tareni da farinciki,mu ka k'arasa ciki,ta na ta murna
Mu na zama sai ga wata matashiya ta zo ta kawo min abun motsa baki,na tambayi Baby wace ita? Ta fad'a min me taya su aiki ce,sunanta Habiba.
Na sha lemon da ta kawo min,sannan mu ka gaisa da Baby na ce"yi sauri ki d'akko min,kin ga magriba ta yi".
Ta ce"Tabb! Ai ki tashi ki yi sallarki,yau sai kin ci abincin dare a gidan nan".
Na ce"rufa min asiri Baby,kunyar Ammi na ke ji wallahi".
Ta kwashe da dariya,har da rik'e ciki ta ce"wato ga surukarki ko? Aikuwa dole sai kun gaisa,don ta san da zuwanki,sallah take yi shiyasa ba ta fito ba"
Na tashi tsaye na ce"don Allah Baby ki rufa min asiri,wallahi sauri na ke yi".
Ta yi murmushi ta ce"to bari na nuna miki abun d'ebe kewa".
Kafin na yi magana ta ja hannuna,ta nufi wani d'aki da ni,ta tura k'ofar ta bud'e mu ka shiga,ni na yi zaton ma d'akinta ne,amma ina shiga sai na ji irin k'amshin da nake ji a jikin Salim ya daki hanci na,ga wani k'aton hotonsa a bangon d'akin,ya yi kyau sosai yana sanye da k'ananun kaya,a d'ayan bangon kuma na shi ne,shi da Baby,ta rirrik'e shi su na dariya,sun yi kyau sosai,kamar rak'umi da akala haka ta ja ni har kan gadonsa.
Ta ce"ga d'akin angon ki nan,na san ba za ki gaji da jiran Ammi ba ".
Na zauna a bakin gadon,kamar wata amarya,tuni na ji wata kasala ta rufeni,k'amshin sa duk ya cika d'akin,har na fara zargin ko dai ya na ciki?
Na kalli Baby na ce" k'amshin Salim duka ya cika d'akin,ko dai ya na nan?"
Ta yi dariya ta ce"turarukan shi dai su na nan,ko na ba ki d'aya?"
Na zare ido na ce"rufa min asiri,idan ya tambaye ki Wanda ya d'auka fa?"
"Sai na ce ke ce" Ta fad'a ta na d'age kafad'a.Na yi murmushi na tashi, na ce,
"Don Allah mu fita,ni dai gida zan koma".
Ta d'akko wani turare a gaban mudubi ta damk'a min a hannu ta ce" ni ce na ba ki kyauta".
Na karb'a na ce"na gode".
Da mu ka fito ba Ammi ba ta dawi falon ba,sai ta ce bari ta kira ta mu gaisa,ni dai duk sai na ji kunyar matar tun kafin na ganta,haka dai na zauna don kar Baby ta ji babu dad'i
Wayata ta fara ringing na ga Nazifi ne me kira,kamar kar na d'aga sai dai na d'aga,get fas ne ya ke tambaya ta,na ce ya ba ni mintuna ina cikin gidan
Ina gama wayar Ammi ta na k'arasowa tare da Baby,babbar mace ce y'ar gayu,fara ce tass! Don da gani ma hasken ta Salim ya yi
Ta k'araso da murumushi a fuskarta ta zauna a d'aya daga cikin kujerun
Na ji ta yi min wani kwarjini,na sakko na zauna a k'asa,kaina a duk'e na gaishe ta
"Lafiya lau Zinatu,ta shi ki koma kujerar" Ammin ta fad'a
Bam koma ba,kuma ban d'ago na kalle ta ba
Baby ta ce"Ammi sauri take yi,bari na raka ta".
Ta ce"to! Rowa za ki ma k'awar taki,ba za ta ci abinci ba?"
Na yi saurin fad'in"na k'oshi Ammi,na gode". Na tashi na yi hanyar fita,ina ta wasa da kwalbar turaren ta cikin hijjabina.
Kafin Baby ta fito daga d'akinta har na fice tsakar gida,bayan na yi wa Ammi sai da safe.Baby ta fito hannunta rik'e da leda,ta mik'o min,sannan ta ba ni get fas d'in guda biyu.
Na amsa na ce"ke! Wannan ledar ta meye?"
Ta ce"Ammi ta ba ki".
Na ce"to ki taya ni godiya,Allah ya saka".
"Ameen" Ta fad'a, ta na murmushi.Sai da ta raka ni har k'ofar gida sannan ta koma
Ina tsaye a bakin titi ina jiran adaidaita sahu,na ga hango wani mashin tun daga nesa ya dalle min fuska da hanke,ni ma shi na ke kallo don ina son sanin ko waye,amma hasken ya kashe min ido har na kasa gane shi,ya zo ya wuce ni.Na shiga adaidaita,bayan na zauna na bud'e ledar,da kud'i na fara cin karo,na yi mamaki don haka na yi saurin d'akko su,na k'irga dubu biyar ne cif,sai wata atamfa me kyau,da mayafi,sai wani saitin turare a kwali,na ji dad'in kyautar sosai,na kai kwalbar turaren Salim hancina,na shak'a har da lumshe idona,sai na ji kamar ina tare da shi ne,na jefa shi jakata tare da kud'in,na kuma fara tunanin yanda zan yi idan Anti ta tambaye ni wanda ya ba ni.
Ina shiga gida mu ka had'u da Nazifi,ya tare ni da fad'in"yawwa kin samu abun?"
Na ce"an samu" Na d'akko get fas d'in na ba shi duka,sannan na yi masa bayanin kayan da Ammi ta ba ni
Ya ce"tab! Aikuwa Anti ta na falo, don yanzu haka daga can na ke".
Na ce"yanzu me zan ce mata?"
Ya yi dariya ya ce"ai kawai ki bar min,dama yau zan je zance,kin ga sai ayi kyauta akan kyauta,ita ta ba ki,ke kin ba ni,ni kuma na bawa wata".
Na harare shi na ce"kyautar surukar tawa? Ina so ni ma"
Allah ya taimake ni hijjabi ne a jikina,na saka saitin turaren cikin jakata,na soke sauran kayan a jikina,na shiga d'akin.
Washegari da safe sai ga sak'on Salim a wayata,hannu na rawa na bud'e,duk da na san ba ya nema na sai na yi masa wani laifin,ko sallama babu a sak'on,tambaya ta kawai ya ke yi,wai da fatan dai jiya ba gidansu na je ba.
Na maida masa da amsa _"idan na je gidanku zai zama matsaka ne?_
Ina ta jiran amsa na ji shiru,na tashi na d'akko turaren da daga jiya zuwa yau na shinshina shi ya fi sau shurin masak'i.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 16
*O'o! Fans😂,ni fa ba matar shege sunan littafin nan ba🤦🏻♀️Matar shige ne,(shi)na ke sakawa ba (she) ba,matar shige ba ta daraja,ni na isa na ce matar shege ba ta daraja? Shi ma shegen ai ba shi ya zab'awa kansa kasancewa a haka ba*
Yau kwanaki uku kawai suka rage min na biyan kud'in da za a yi min aikin nan,kuma har yanzu dubu goma sha uku ne a hannuna,ni da nake buk'atar dubu d'ari biyu,duk iya tunanina na kasa gano ta yanda wannan kud'i za su shigo min,har wata rama na yi a y'an kwanakin.Tun Nazifi na yi min magiyar na kawo har ya gaji ya daina yi min zancen
Kuma har yanzu Habib bai kira ni ba,bai kuma zo gidan Antin ba,bare na saka ran wani abun daga wurin sa.Kullum sai na yi sana'ar tawa,ta kiran Salim amma sam! Ba ya d'agawa.Junaina ta kira ni jiya take tambaya ta ya batun bayanan Salim d'in? Don haushi ban san lokacin da na k'unduma mata zagi ba,na dinga surfa mata ruwan ashar kamar zan ari baki,kuma na ce idan ba ta yi recoding ta kunnawa Salim ba, ba ta haifu ba! Ba ta tanka ni ba dai, ta katse kiran,na danna shegiya a blacklist na yi wurgi da wayar.
Ranar Asabar ne ya kama birthday d'in,don haka ranar Juma'ar nan duk wanda ya kalleni sai ya gane ina cikin damuwa,Anti kuwa tun kwana biyu da suka wuce ta zaunar da ni ta tambaye ni,na yi mata k'aryar babu komai,ko d'azu mun yi waya da Baby ta sake tambaya ta,na tabbatar mata da zuwa na goben.
Da yamma mu ka keb'e da Nazifi a k'ofar gida,ya kalle ni da kyau ya ce "Zinatu! Yau ce fa rana ta k'arshe da ya kamata a kammala duk wani shiri! Kuma kin ga dole sai da kud'i, wanda za mu yi aikin tare ya na da wasu uzururrukan fa".
Na yi huci me zafi,ina kalmashe hannayena a k'irji,na ma rasa abun fad'a
Ya ce"kin yi shiru".
Na yi jim! Sannan cikin sanyi na ce" Nazifi a bar shi kawai na hak'ura,idan Salim rabo na ne zai aure ni".
"Wai duk saboda kud'in ki ka hak'ura?" Ya tambaye ni
Na ce"e! Tunda na yi duk yi na,ban samu hanyar samu ba,kuma lokaci ya k'ure".
Nazifi ya yi shiru kamar me nazari,can ya jinjina kai ya ce"ina zuwa". Ya ja gefe can nesa da ni,ya ciro wayarsa a aljihu ya kara a kunne
Wallahi ban san da wanda ya yi waya ba,ba na jiyo muryarsa bare na fahimci wayar,kuma ya juya baya bare motsin bakinsa ya d'an yi min k'arin haske,wajan minti biyar ya na waya,sannan ya dawo inda nake ya na fara'a,har abun ya so bani mamaki.
Na ce"kuma murmushin na meye?"
Ya washe baki ya ce"ke na ke tayawa".
"Ni kuma?" Na tambaye shi
Ya gyara wuyan rigarsa ya ce"wanda za mu yi aikin tare ne ya ce ki bar kud'in kawai,dayake na yi masa bayanin ba ki da kud'i, shi ne ya ce tunda ya na da shi kawai zai taimake ki.Yanzu dai aiki zai yiwu gobe in sha Allah!".
Dab da magriba na tambayi Anti zan je gida na d'akko wasu kayana,sai da ta yi min fad'a kafin ta bar ni,wai meyasa tun safe ban je ba sai da magriba? Haka dai na shirya na tafi shagon Baby,sai dai ina zuwa na tarar ba ta nan,wai lokacin tafiyarta gida ya yi.Na kirata a waya na sanar mata na zo mata nan,ta ce sai dai na k'araso gidansu tunda babu nisa,ta kwatanta min na kama hanya.
WANI KUSKURE...
Ban san zuwa na gidan su Salim a lokacin kuskure bane sai daga baya,da na je na tarar da megadi,amma bai hana ni shiga ba,ina dai tunanin Baby ta sanar masa za ta yi bak'uwa,lokacin har an shiga masallaci ana sallar magriba,a tsakar gida na tadda Baby,ta tareni da farinciki,mu ka k'arasa ciki,ta na ta murna
Mu na zama sai ga wata matashiya ta zo ta kawo min abun motsa baki,na tambayi Baby wace ita? Ta fad'a min me taya su aiki ce,sunanta Habiba.
Na sha lemon da ta kawo min,sannan mu ka gaisa da Baby na ce"yi sauri ki d'akko min,kin ga magriba ta yi".
Ta ce"Tabb! Ai ki tashi ki yi sallarki,yau sai kin ci abincin dare a gidan nan".
Na ce"rufa min asiri Baby,kunyar Ammi na ke ji wallahi".
Ta kwashe da dariya,har da rik'e ciki ta ce"wato ga surukarki ko? Aikuwa dole sai kun gaisa,don ta san da zuwanki,sallah take yi shiyasa ba ta fito ba"
Na tashi tsaye na ce"don Allah Baby ki rufa min asiri,wallahi sauri na ke yi".
Ta yi murmushi ta ce"to bari na nuna miki abun d'ebe kewa".
Kafin na yi magana ta ja hannuna,ta nufi wani d'aki da ni,ta tura k'ofar ta bud'e mu ka shiga,ni na yi zaton ma d'akinta ne,amma ina shiga sai na ji irin k'amshin da nake ji a jikin Salim ya daki hanci na,ga wani k'aton hotonsa a bangon d'akin,ya yi kyau sosai yana sanye da k'ananun kaya,a d'ayan bangon kuma na shi ne,shi da Baby,ta rirrik'e shi su na dariya,sun yi kyau sosai,kamar rak'umi da akala haka ta ja ni har kan gadonsa.
Ta ce"ga d'akin angon ki nan,na san ba za ki gaji da jiran Ammi ba ".
Na zauna a bakin gadon,kamar wata amarya,tuni na ji wata kasala ta rufeni,k'amshin sa duk ya cika d'akin,har na fara zargin ko dai ya na ciki?
Na kalli Baby na ce" k'amshin Salim duka ya cika d'akin,ko dai ya na nan?"
Ta yi dariya ta ce"turarukan shi dai su na nan,ko na ba ki d'aya?"
Na zare ido na ce"rufa min asiri,idan ya tambaye ki Wanda ya d'auka fa?"
"Sai na ce ke ce" Ta fad'a ta na d'age kafad'a.Na yi murmushi na tashi, na ce,
"Don Allah mu fita,ni dai gida zan koma".
Ta d'akko wani turare a gaban mudubi ta damk'a min a hannu ta ce" ni ce na ba ki kyauta".
Na karb'a na ce"na gode".
Da mu ka fito ba Ammi ba ta dawi falon ba,sai ta ce bari ta kira ta mu gaisa,ni dai duk sai na ji kunyar matar tun kafin na ganta,haka dai na zauna don kar Baby ta ji babu dad'i
Wayata ta fara ringing na ga Nazifi ne me kira,kamar kar na d'aga sai dai na d'aga,get fas ne ya ke tambaya ta,na ce ya ba ni mintuna ina cikin gidan
Ina gama wayar Ammi ta na k'arasowa tare da Baby,babbar mace ce y'ar gayu,fara ce tass! Don da gani ma hasken ta Salim ya yi
Ta k'araso da murumushi a fuskarta ta zauna a d'aya daga cikin kujerun
Na ji ta yi min wani kwarjini,na sakko na zauna a k'asa,kaina a duk'e na gaishe ta
"Lafiya lau Zinatu,ta shi ki koma kujerar" Ammin ta fad'a
Bam koma ba,kuma ban d'ago na kalle ta ba
Baby ta ce"Ammi sauri take yi,bari na raka ta".
Ta ce"to! Rowa za ki ma k'awar taki,ba za ta ci abinci ba?"
Na yi saurin fad'in"na k'oshi Ammi,na gode". Na tashi na yi hanyar fita,ina ta wasa da kwalbar turaren ta cikin hijjabina.
Kafin Baby ta fito daga d'akinta har na fice tsakar gida,bayan na yi wa Ammi sai da safe.Baby ta fito hannunta rik'e da leda,ta mik'o min,sannan ta ba ni get fas d'in guda biyu.
Na amsa na ce"ke! Wannan ledar ta meye?"
Ta ce"Ammi ta ba ki".
Na ce"to ki taya ni godiya,Allah ya saka".
"Ameen" Ta fad'a, ta na murmushi.Sai da ta raka ni har k'ofar gida sannan ta koma
Ina tsaye a bakin titi ina jiran adaidaita sahu,na ga hango wani mashin tun daga nesa ya dalle min fuska da hanke,ni ma shi na ke kallo don ina son sanin ko waye,amma hasken ya kashe min ido har na kasa gane shi,ya zo ya wuce ni.Na shiga adaidaita,bayan na zauna na bud'e ledar,da kud'i na fara cin karo,na yi mamaki don haka na yi saurin d'akko su,na k'irga dubu biyar ne cif,sai wata atamfa me kyau,da mayafi,sai wani saitin turare a kwali,na ji dad'in kyautar sosai,na kai kwalbar turaren Salim hancina,na shak'a har da lumshe idona,sai na ji kamar ina tare da shi ne,na jefa shi jakata tare da kud'in,na kuma fara tunanin yanda zan yi idan Anti ta tambaye ni wanda ya ba ni.
Ina shiga gida mu ka had'u da Nazifi,ya tare ni da fad'in"yawwa kin samu abun?"
Na ce"an samu" Na d'akko get fas d'in na ba shi duka,sannan na yi masa bayanin kayan da Ammi ta ba ni
Ya ce"tab! Aikuwa Anti ta na falo, don yanzu haka daga can na ke".
Na ce"yanzu me zan ce mata?"
Ya yi dariya ya ce"ai kawai ki bar min,dama yau zan je zance,kin ga sai ayi kyauta akan kyauta,ita ta ba ki,ke kin ba ni,ni kuma na bawa wata".
Na harare shi na ce"kyautar surukar tawa? Ina so ni ma"
Allah ya taimake ni hijjabi ne a jikina,na saka saitin turaren cikin jakata,na soke sauran kayan a jikina,na shiga d'akin.
Washegari da safe sai ga sak'on Salim a wayata,hannu na rawa na bud'e,duk da na san ba ya nema na sai na yi masa wani laifin,ko sallama babu a sak'on,tambaya ta kawai ya ke yi,wai da fatan dai jiya ba gidansu na je ba.
Na maida masa da amsa _"idan na je gidanku zai zama matsaka ne?_
Ina ta jiran amsa na ji shiru,na tashi na d'akko turaren da daga jiya zuwa yau na shinshina shi ya fi sau shurin masak'i.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 16
*O'o! Fans😂,ni fa ba matar shege sunan littafin nan ba🤦🏻♀️Matar shige ne,(shi)na ke sakawa ba (she) ba,matar shige ba ta daraja,ni na isa na ce matar shege ba ta daraja? Shi ma shegen ai ba shi ya zab'awa kansa kasancewa a haka ba*
Yau kwanaki uku kawai suka rage min na biyan kud'in da za a yi min aikin nan,kuma har yanzu dubu goma sha uku ne a hannuna,ni da nake buk'atar dubu d'ari biyu,duk iya tunanina na kasa gano ta yanda wannan kud'i za su shigo min,har wata rama na yi a y'an kwanakin.Tun Nazifi na yi min magiyar na kawo har ya gaji ya daina yi min zancen
Kuma har yanzu Habib bai kira ni ba,bai kuma zo gidan Antin ba,bare na saka ran wani abun daga wurin sa.Kullum sai na yi sana'ar tawa,ta kiran Salim amma sam! Ba ya d'agawa.Junaina ta kira ni jiya take tambaya ta ya batun bayanan Salim d'in? Don haushi ban san lokacin da na k'unduma mata zagi ba,na dinga surfa mata ruwan ashar kamar zan ari baki,kuma na ce idan ba ta yi recoding ta kunnawa Salim ba, ba ta haifu ba! Ba ta tanka ni ba dai, ta katse kiran,na danna shegiya a blacklist na yi wurgi da wayar.
Ranar Asabar ne ya kama birthday d'in,don haka ranar Juma'ar nan duk wanda ya kalleni sai ya gane ina cikin damuwa,Anti kuwa tun kwana biyu da suka wuce ta zaunar da ni ta tambaye ni,na yi mata k'aryar babu komai,ko d'azu mun yi waya da Baby ta sake tambaya ta,na tabbatar mata da zuwa na goben.
Da yamma mu ka keb'e da Nazifi a k'ofar gida,ya kalle ni da kyau ya ce "Zinatu! Yau ce fa rana ta k'arshe da ya kamata a kammala duk wani shiri! Kuma kin ga dole sai da kud'i, wanda za mu yi aikin tare ya na da wasu uzururrukan fa".
Na yi huci me zafi,ina kalmashe hannayena a k'irji,na ma rasa abun fad'a
Ya ce"kin yi shiru".
Na yi jim! Sannan cikin sanyi na ce" Nazifi a bar shi kawai na hak'ura,idan Salim rabo na ne zai aure ni".
"Wai duk saboda kud'in ki ka hak'ura?" Ya tambaye ni
Na ce"e! Tunda na yi duk yi na,ban samu hanyar samu ba,kuma lokaci ya k'ure".
Nazifi ya yi shiru kamar me nazari,can ya jinjina kai ya ce"ina zuwa". Ya ja gefe can nesa da ni,ya ciro wayarsa a aljihu ya kara a kunne
Wallahi ban san da wanda ya yi waya ba,ba na jiyo muryarsa bare na fahimci wayar,kuma ya juya baya bare motsin bakinsa ya d'an yi min k'arin haske,wajan minti biyar ya na waya,sannan ya dawo inda nake ya na fara'a,har abun ya so bani mamaki.
Na ce"kuma murmushin na meye?"
Ya washe baki ya ce"ke na ke tayawa".
"Ni kuma?" Na tambaye shi
Ya gyara wuyan rigarsa ya ce"wanda za mu yi aikin tare ne ya ce ki bar kud'in kawai,dayake na yi masa bayanin ba ki da kud'i, shi ne ya ce tunda ya na da shi kawai zai taimake ki.Yanzu dai aiki zai yiwu gobe in sha Allah!".