Sashe 2
Mailaah Part 1 Complete Hausa Novel. · about 7 min read
Zazzaune suke agaban wanda daga gani babbane ko me faɗa aji, nasiha yake musu me ratsa jiki, fuskar kowanensu aɗan maraurace, amma banda shi, zaune yake a tsakiyarsu baice komi ba, kuma ko kaɗa kai alamun amsawa bayayi kamar yanda sauran suke, aduƙe yake ba'a iya ganin ainahin fuskarshi, saboda baƙi wuluk ɗin gashin kanshi daya zubo har gaban fuskarshi, ganin sauran sun miƙe ya saka shima ya miƙe, ba tare daya ko kalli kowa ba ya saka kai gaba ya juya ya kama tafiya, tafiya yake cike da sadaukantaka kuma cikin isa da ƙasaita kamar wani jinin sarauta, matasane biye dashi a baya har suka zo daidai inda ya tsaya a ƙofar wani ɗan ƙaramin gida, gidanda a ido zaka iya hango ƙanƙantar da zaiyi a ciki, tsayawa yai saitin ƙofar daya buɗe, ya juyo da baya yana kallon matasan da birkitattun idanuwansa waɗanda suke sheƙi a cikin hasken farin watan, ganin yanda ya tsaresu da ido yana kallo, sai kawai suka juya suka tafi, sai da sukai mashi nisa a ido sannan ya juya ya shiga gidan ya kulle.
Kanshi tsaye ya nufi kwalli ɗayan ɗakin da ke gidan ya shiga, ɗan turus yayi ganin yanda duhu ya mamaye ko ina, ba tare da jinkiri ba yashiga laluben makunin fitilar ɗakin dake jikin bango, bai yi aune ba ya ji ya sauke ƙafarshi akan wani abu lallausa kuma me ɗumi, da hanzari ya ja da baya, sai yai rashin sa'a ƙafarshi ta zame, ki kake timm ya faɗa akan wani abu me laushi kuma tattausa wanda ke fitar da lumfashi da alama hallitace me rai a wajen.
Tun shigowarshi ina iya ganinshi, musamman da yake sanye cikin farare tas ɗin tufafi masu haske, naga sanda ya ke ta laluben bango da alama abu yake nema, ban motsa daga inda nike zaune ba, sai de na ɗaga kaina acikin duhun na dubi wajen da swetch ɗin ya ke, ban sa'ilin da ya ƙaraso inda nike ba, daidai saitin ƙafata, juyowar da zanyi dai kawai naji lallausa tafi me tsananin taushi ya taka ƙafata, ba halina bane zabura ko tsorata aduk lokacin da naga wani abu wanda zai cutar da ni, sam ni bana tsorata kamar sauran mutane, sai de in shiga wani yanayi me wuyar fassara, yanayin da ke tsorata du wanda ya raɓe ni.
Second ɗaya, biyu, uku, har zuwa sakannin goma banji abin da ya tausheni me taushi da tsananin nauyi ya ɗagani ba, can cikin maƙoshi na furta sauti, "auch" saboda ji danayi zuciyata na zullo har tana ƙoƙari fucewa ta maƙogarona, wani irin luguden duka take min lokcin da naji hannunshi na laluben jikina kamar meson tantance wani abu, saurin tallafe hannunshi na yi ina girgiza kai kamar yana gani na, ina jin yanda ya sauke wa ta ƙaƙƙarfar ajiyar, sai kuma ya janye jikinshi gefe ya kwanta a ƙasa, wani irin shiru marar hayaniya ne ya mamaye ɗakin yayinda sautin komi ya ɗauke saina shaƙa da fesarwar iskar numfarfashinmu, mu kanmu bamusan iya adadin tsawon lokacin da muka kwashe a haka ba.....✍️
SOMIN TAƁI KENAN A CIKIN LABARI ME TAKEN MAILAAH KU BIYO NI DAN JIN YANDA ZATA ƘARKE
Follow the 🌹MARYAM STAR⭐⭐⭐ HAUSA NOVELS AND MORE 𝐶𝐻𝐴𝑁𝑁𝐸𝐿✍️📚📙✏️ channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb5xdoy2975BcTM5m133
🥀🌹𝑴𝑨𝑰𝑳𝑨𝑨𝑯🌹🥀
𝑾𝑹𝑰𝑻𝑬 𝑩𝒀
𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑨𝑹⭐⭐
𝒀𝑨𝑹 𝑩𝑨𝑰𝑾𝑨𝑹 𝑱𝑨𝑱𝑰𝑹𝑻𝑨𝑻𝑻𝑼.
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
PAID BOOK
FREE PAGES
BOOK ONE
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الْحَمْدُ لِلَّهِ نَحْمَدُهُ وَنَسْتَعِينُهُ وَنَسْتَغْفِرُهُ وَنَعُوذُ بِاللَّهِ مِنْ شُرُورِ أَنْفُسِنَا وَمِنْ سَيِّئَاتِ أَعْمَالِنَا مَنْ يَهْدِهِ اللَّهُ فَلَا مُضِلَّ لَهُ وَمَنْ يُضْلِلْ فَلَا هَادِيَ لَهُ وَأَشْهَدُ أَنْ لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيكَ لَهُ وَأَنَّ مُحَمَّدًا صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ
---------Chapter 3 & 4
Ban saniba ko ƙosawa yai da yanayin sai jin motsinshi nayi ya tashi, fita yayi zuwa waje kafin ya dawo hannunshi riƙe da wani abu me haske, banyi aune ba sai ji nayi anhaske saitin inda nike a zaune, a mugun zabure na miƙe tsaye jikina na karkarwa, cikin ƴan sakanni ƙalila du nabi na ruɗe inata faman kare farar fuskata da hasken ke neman nakasa min ido, ja da baya na yi ganin yanda yake sake tunkaro ni da hasken, yaraf na faɗa akan gado inata faman shesheka, lokaci ɗaya hasken ya fitilar da yasamu damar kunnawa ya bibaye ɗakin, direct ya sauke birkitattun idanuwansa akaina, sai wasu maganganu suka shiga yi mashi amsa kuwa cikin kunne.
"Haske!!!, ka kiyaye kunna haske kai tsaye a inda ta ke, bata son haske, yana kassara zaman lafiyarta, kuma yana zautar da ƙaramar ƙwaƙwalwarta, haske ne matakin farko da ke fara rikita tunaninta, takan shiga tsoro da firgici a lokacin da haske ya haskata kai tsaye ba tare da dabara ba."
Ƙaramar ajiyar zuciya ya sauke, kafin a hankali ya shiga taka dogayen ƙafafuwansa har ya ƙaraso inda nike zaune dafe da kaina inata faman shesheka idanuwana a warwaje, wani itin tartsatsin haske ya gilma ta cikin kaina lokacin da na ɗago da fuskata wacce tafara tirewa zuwa kalar jah, saukar idanuwa a cikin nashi birkitattun idanuwa wanda nike hango sheƙi da walwali wani kalar rauni, raunine irina na tsoro da fargabar faruwar wani abu, ban gama tantace inda kaina yake ba kawau naji na tafi luuuu duniyar na juya min, daga nan ban sake sanin komi ba, duhun da yake lulluɓe cikin ƙaddarar rayuwata ya ratsa da masarrafar tunani da ganina, shirun da ke cutar da tuhina ya ziyarceni ba tare dana shiryawa hakanba.
Jijiyoyine ruɗu-ruɗu duka firfito a gaban goshi da kanshi, yayinda gumi ke tsatstsafo mashi ta kowace hudar gashi dake jikin fatarshi, da iya ƙarfin da Allah ya azurtashi yake riƙe da kafaɗuna yana jijjigani da tsananin ƙarfi ko zan dawo hayyacina, amma ina, a maimakon ihu da gurnani me ban tsoro da nacika gidan da shi, sai kaina ya shiga lauyewa gefe da gefe, wani irin fari tas ɗin yawu ya dinga gangarowa daga bakina, nan take jikina ya saki sautina ya ɗauke dif jikina yai wani irin sanyi ƙalau, a mugun tsorace ya sake ni nai baya bakinshi a buɗe idanuwan a waje ya dafe kanshi da ƙarfi sannan ya furta. "MAILAAHHHHHHHHHH!!!!!!!."
Da wani irin hanzari magidancin da ke zaune akan sallaya yana tasbihi ya miƙe, lokaci ɗaya shaƙuwa ta kama shi, cikin sarkewar murya ya ke faɗi bayan ya dafe saitin zuciyarshi dake barazanr tarwatsewa.
"MAILAAH, innalillahi wa'inna ilaihi raju'un, hasbunallahu wani'imal wakil, yah Rahaman." sai kuma ya duƙe a wajen wasu irin zafafan hawaye na ɓalle mashi, ga kuka da zafin zuciya sannan ga shaƙuwar data addabeshi.
Wannan shine karo na babu adadi datai juyi kamar me barci, ranta a mugun ɓace bayan ta buɗe ido kaɗan ta ga har lokacin zaune ya ke yana tasbihi, ji take kamar ta tashi ta shaƙoshi ta kwantar a gefenta, sai babu adadi take baƙin ciki da zagayowar ranar a matsayin ranar girkinta, da tasan haka abin zai juye da bata yi wannan tafiyarba, ta na tsaka da tunani mahita sai ta ji sallatinshi, ba tare da ɓata lokaci ba har tana mancewa da ashe barci take ta miƙe zumbur tare da ƙarasawa zuwa inda yake a durƙushe yana saƙuwa, hannunshi a saitin zuciyarshi, idan ta ce batai farin ciki da hakan ba to ta gillara ƙarya, cike da kwarewa da sanin makamar aiki tashiga bashi taimakon gaugawa, bayan ta bashi ruwa me matsakaicin sanyi ta kwantar dashi akan gado da kyar, sannan ta dallara mashi allurar barci me tsananin ƙarfi, bai haura ƴan sakanni ba barci yai awon gaba da shi, cike da murna ta fice ta na jin daɗin yanda ta samu wannan damar, kanta tsaye ta haura samman dogon stirs ɗin dake fitar da dum light a gefen matattakalarshi, bayan ta shiga sai da ta tabbatar da ta rufe ko ina, sannan ta sunkuya a ƙasan gaɗo ta janyo wani ɗan ƙaramin jan akwati, nan take sarka me tsananin tsada ta bayyana, cike da nishaɗi ta shafa bayan sarƙar sai sarƙar ta fara rikiɗewa tana sauyawa yayinda hayaƙi fari fat ya cike ɗakin ta yanda ba'a iya ganin komi, can bayan wasu ƴan mintuna hayaƙin ya soma raguwa ahankali har ya ɓace ɓat, abin mamaki sai wannan matar ta bayyana zaune, farar fuskarta ta ƙara haske, yayinda hancinta ya ƙara tsayi kamar anja shi, laɓanta suka sake rinewa zuwan dark pink, sai ɗaukar ido ta ke, ga wani gwarjini na bala'i dake bayyane akan fuskarta, cikin ƙanƙanin lokaci kyawunta ya linku sosai fiye da yanda ta shigo ɗakin.
Kanshi tsaye ya nufi kwalli ɗayan ɗakin da ke gidan ya shiga, ɗan turus yayi ganin yanda duhu ya mamaye ko ina, ba tare da jinkiri ba yashiga laluben makunin fitilar ɗakin dake jikin bango, bai yi aune ba ya ji ya sauke ƙafarshi akan wani abu lallausa kuma me ɗumi, da hanzari ya ja da baya, sai yai rashin sa'a ƙafarshi ta zame, ki kake timm ya faɗa akan wani abu me laushi kuma tattausa wanda ke fitar da lumfashi da alama hallitace me rai a wajen.
Tun shigowarshi ina iya ganinshi, musamman da yake sanye cikin farare tas ɗin tufafi masu haske, naga sanda ya ke ta laluben bango da alama abu yake nema, ban motsa daga inda nike zaune ba, sai de na ɗaga kaina acikin duhun na dubi wajen da swetch ɗin ya ke, ban sa'ilin da ya ƙaraso inda nike ba, daidai saitin ƙafata, juyowar da zanyi dai kawai naji lallausa tafi me tsananin taushi ya taka ƙafata, ba halina bane zabura ko tsorata aduk lokacin da naga wani abu wanda zai cutar da ni, sam ni bana tsorata kamar sauran mutane, sai de in shiga wani yanayi me wuyar fassara, yanayin da ke tsorata du wanda ya raɓe ni.
Second ɗaya, biyu, uku, har zuwa sakannin goma banji abin da ya tausheni me taushi da tsananin nauyi ya ɗagani ba, can cikin maƙoshi na furta sauti, "auch" saboda ji danayi zuciyata na zullo har tana ƙoƙari fucewa ta maƙogarona, wani irin luguden duka take min lokcin da naji hannunshi na laluben jikina kamar meson tantance wani abu, saurin tallafe hannunshi na yi ina girgiza kai kamar yana gani na, ina jin yanda ya sauke wa ta ƙaƙƙarfar ajiyar, sai kuma ya janye jikinshi gefe ya kwanta a ƙasa, wani irin shiru marar hayaniya ne ya mamaye ɗakin yayinda sautin komi ya ɗauke saina shaƙa da fesarwar iskar numfarfashinmu, mu kanmu bamusan iya adadin tsawon lokacin da muka kwashe a haka ba.....✍️
SOMIN TAƁI KENAN A CIKIN LABARI ME TAKEN MAILAAH KU BIYO NI DAN JIN YANDA ZATA ƘARKE
Follow the 🌹MARYAM STAR⭐⭐⭐ HAUSA NOVELS AND MORE 𝐶𝐻𝐴𝑁𝑁𝐸𝐿✍️📚📙✏️ channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb5xdoy2975BcTM5m133
🥀🌹𝑴𝑨𝑰𝑳𝑨𝑨𝑯🌹🥀
𝑾𝑹𝑰𝑻𝑬 𝑩𝒀
𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑨𝑹⭐⭐
𝒀𝑨𝑹 𝑩𝑨𝑰𝑾𝑨𝑹 𝑱𝑨𝑱𝑰𝑹𝑻𝑨𝑻𝑻𝑼.
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
PAID BOOK
FREE PAGES
BOOK ONE
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الْحَمْدُ لِلَّهِ نَحْمَدُهُ وَنَسْتَعِينُهُ وَنَسْتَغْفِرُهُ وَنَعُوذُ بِاللَّهِ مِنْ شُرُورِ أَنْفُسِنَا وَمِنْ سَيِّئَاتِ أَعْمَالِنَا مَنْ يَهْدِهِ اللَّهُ فَلَا مُضِلَّ لَهُ وَمَنْ يُضْلِلْ فَلَا هَادِيَ لَهُ وَأَشْهَدُ أَنْ لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيكَ لَهُ وَأَنَّ مُحَمَّدًا صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ
---------Chapter 3 & 4
Ban saniba ko ƙosawa yai da yanayin sai jin motsinshi nayi ya tashi, fita yayi zuwa waje kafin ya dawo hannunshi riƙe da wani abu me haske, banyi aune ba sai ji nayi anhaske saitin inda nike a zaune, a mugun zabure na miƙe tsaye jikina na karkarwa, cikin ƴan sakanni ƙalila du nabi na ruɗe inata faman kare farar fuskata da hasken ke neman nakasa min ido, ja da baya na yi ganin yanda yake sake tunkaro ni da hasken, yaraf na faɗa akan gado inata faman shesheka, lokaci ɗaya hasken ya fitilar da yasamu damar kunnawa ya bibaye ɗakin, direct ya sauke birkitattun idanuwansa akaina, sai wasu maganganu suka shiga yi mashi amsa kuwa cikin kunne.
"Haske!!!, ka kiyaye kunna haske kai tsaye a inda ta ke, bata son haske, yana kassara zaman lafiyarta, kuma yana zautar da ƙaramar ƙwaƙwalwarta, haske ne matakin farko da ke fara rikita tunaninta, takan shiga tsoro da firgici a lokacin da haske ya haskata kai tsaye ba tare da dabara ba."
Ƙaramar ajiyar zuciya ya sauke, kafin a hankali ya shiga taka dogayen ƙafafuwansa har ya ƙaraso inda nike zaune dafe da kaina inata faman shesheka idanuwana a warwaje, wani itin tartsatsin haske ya gilma ta cikin kaina lokacin da na ɗago da fuskata wacce tafara tirewa zuwa kalar jah, saukar idanuwa a cikin nashi birkitattun idanuwa wanda nike hango sheƙi da walwali wani kalar rauni, raunine irina na tsoro da fargabar faruwar wani abu, ban gama tantace inda kaina yake ba kawau naji na tafi luuuu duniyar na juya min, daga nan ban sake sanin komi ba, duhun da yake lulluɓe cikin ƙaddarar rayuwata ya ratsa da masarrafar tunani da ganina, shirun da ke cutar da tuhina ya ziyarceni ba tare dana shiryawa hakanba.
Jijiyoyine ruɗu-ruɗu duka firfito a gaban goshi da kanshi, yayinda gumi ke tsatstsafo mashi ta kowace hudar gashi dake jikin fatarshi, da iya ƙarfin da Allah ya azurtashi yake riƙe da kafaɗuna yana jijjigani da tsananin ƙarfi ko zan dawo hayyacina, amma ina, a maimakon ihu da gurnani me ban tsoro da nacika gidan da shi, sai kaina ya shiga lauyewa gefe da gefe, wani irin fari tas ɗin yawu ya dinga gangarowa daga bakina, nan take jikina ya saki sautina ya ɗauke dif jikina yai wani irin sanyi ƙalau, a mugun tsorace ya sake ni nai baya bakinshi a buɗe idanuwan a waje ya dafe kanshi da ƙarfi sannan ya furta. "MAILAAHHHHHHHHHH!!!!!!!."
Da wani irin hanzari magidancin da ke zaune akan sallaya yana tasbihi ya miƙe, lokaci ɗaya shaƙuwa ta kama shi, cikin sarkewar murya ya ke faɗi bayan ya dafe saitin zuciyarshi dake barazanr tarwatsewa.
"MAILAAH, innalillahi wa'inna ilaihi raju'un, hasbunallahu wani'imal wakil, yah Rahaman." sai kuma ya duƙe a wajen wasu irin zafafan hawaye na ɓalle mashi, ga kuka da zafin zuciya sannan ga shaƙuwar data addabeshi.
Wannan shine karo na babu adadi datai juyi kamar me barci, ranta a mugun ɓace bayan ta buɗe ido kaɗan ta ga har lokacin zaune ya ke yana tasbihi, ji take kamar ta tashi ta shaƙoshi ta kwantar a gefenta, sai babu adadi take baƙin ciki da zagayowar ranar a matsayin ranar girkinta, da tasan haka abin zai juye da bata yi wannan tafiyarba, ta na tsaka da tunani mahita sai ta ji sallatinshi, ba tare da ɓata lokaci ba har tana mancewa da ashe barci take ta miƙe zumbur tare da ƙarasawa zuwa inda yake a durƙushe yana saƙuwa, hannunshi a saitin zuciyarshi, idan ta ce batai farin ciki da hakan ba to ta gillara ƙarya, cike da kwarewa da sanin makamar aiki tashiga bashi taimakon gaugawa, bayan ta bashi ruwa me matsakaicin sanyi ta kwantar dashi akan gado da kyar, sannan ta dallara mashi allurar barci me tsananin ƙarfi, bai haura ƴan sakanni ba barci yai awon gaba da shi, cike da murna ta fice ta na jin daɗin yanda ta samu wannan damar, kanta tsaye ta haura samman dogon stirs ɗin dake fitar da dum light a gefen matattakalarshi, bayan ta shiga sai da ta tabbatar da ta rufe ko ina, sannan ta sunkuya a ƙasan gaɗo ta janyo wani ɗan ƙaramin jan akwati, nan take sarka me tsananin tsada ta bayyana, cike da nishaɗi ta shafa bayan sarƙar sai sarƙar ta fara rikiɗewa tana sauyawa yayinda hayaƙi fari fat ya cike ɗakin ta yanda ba'a iya ganin komi, can bayan wasu ƴan mintuna hayaƙin ya soma raguwa ahankali har ya ɓace ɓat, abin mamaki sai wannan matar ta bayyana zaune, farar fuskarta ta ƙara haske, yayinda hancinta ya ƙara tsayi kamar anja shi, laɓanta suka sake rinewa zuwan dark pink, sai ɗaukar ido ta ke, ga wani gwarjini na bala'i dake bayyane akan fuskarta, cikin ƙanƙanin lokaci kyawunta ya linku sosai fiye da yanda ta shigo ɗakin.