Sashe 1
Mailaah Part 1 Complete Hausa Novel. · about 6 min read
🥀🌹MAILAAH🌹🥀
Follow the 🌹MARYAM STAR⭐⭐⭐ HAUSA NOVELS AND MORE 𝐶𝐻𝐴𝑁𝑁𝐸𝐿✍️📚📙✏️ channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb5xdoy2975BcTM5m133
🥀🌹𝑴𝑨𝑰𝑳𝑨𝑨𝑯🌹🥀
𝑳𝑨𝑩𝑨𝑹𝑰 𝑴𝑬 𝑪𝑰𝑲𝑬 𝑫𝑨
𝑭𝑨𝑫𝑨𝑲𝑨𝑹𝑾𝑨
𝒁𝑨𝑳𝑳𝑨𝑹 𝑪𝑨𝑲𝑾𝑨𝑲𝑰𝒀𝑨
𝑫𝑨 𝒁𝑨𝒁𝒁𝑨𝑭𝑨𝑹 𝑺𝑶𝒀𝑨𝒀𝒀𝑨 𝑴𝑬 𝑻𝑺𝑨𝒀𝑨𝑾𝑨 𝑨𝑲𝑶𝑲𝑶𝑵 𝑲𝑨𝑰
𝑾𝑹𝑰𝑻𝑬 𝑩𝒀
𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑨𝑹⭐⭐
𝒀𝑨𝑹 𝑩𝑨𝑰𝑾𝑨𝑹 𝑱𝑨𝑱𝑰𝑹𝑻𝑨𝑻𝑻𝑼.
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚
PAID BOOK
FREE PAGES
BOOK ONE
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الْحَمْدُ لِلَّهِ نَحْمَدُهُ وَنَسْتَعِينُهُ وَنَسْتَغْفِرُهُ وَنَعُوذُ بِاللَّهِ مِنْ شُرُورِ أَنْفُسِنَا وَمِنْ سَيِّئَاتِ أَعْمَالِنَا مَنْ يَهْدِهِ اللَّهُ فَلَا مُضِلَّ لَهُ وَمَنْ يُضْلِلْ فَلَا هَادِيَ لَهُ وَأَشْهَدُ أَنْ لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيكَ لَهُ وَأَنَّ مُحَمَّدًا صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ
---------Chapter 1 & 2
Miƙa na yi tare saka hannuna na rufe bakina da wa ta iriyar waskekiyar hamma ta kwace min ba tare dana shirya ba, ahankali na fara warware ƙafafuwana daga tankwasar da nai musu ta tsawon awanni, sai na ji sunyi min tsami har wa ta ƙara suke saki ƙas-ƙas, amma ahaka na daure na miƙe su a zaune, zura hannuna na yi tare da shafo daga dokin wuyana zuwa wuya, ina jin yanda ƙashin wajen kemin wanu iri saboda tsabar gajiya da duƙiyar da nayi, yawata idanuwa na nike a ko wane saƙo da lungu na ɗakin ina mamakin sanda har duhun dare ya mamaye ko ina ba tare dana ankara ba, sai na koma baya ina tariyo abin da ya faru.
Hayaniyar muryoyi mabanbanta ke tashi, kowace murya da abin da take faɗi, sai na girgiza kaina da naji yayimin wani irin nauyi kamar dutse, na tariye wurin hayaniyar da koma daidai inda najiyo muryar wacce nikewa kallon bango abar jinginata ke faɗin.
"Yo maraici hauka ne da za'a gallabi rayuwar baiwar Allah wacce bata ji ba bata gani ba, dan anga bata da wani zaɓi sai yanda rayuwa ta juyata shine za'abiyewa son zuciya acutar da ita, dan anga tana nuna kamar batason farin ciki ba shine za'a kashe ma ta rayuwa a tsaye, na rantse da girman Allah babu inda zanje imbar MAILAAH a wannan baƙin gidan me kama da akurkin kaji, dan kawai Allah ya jarabceta da ciwo sai a maidata kamar kamar mujiya a cikin mutane, wallahi ba zata zauna agidannan da sunan aure ba, sai na tafi da ita inda babu me sake jin ɗuriyarta.
Kyakkyawar fara tas ɗin matar da hutu da naira suka nuna jikinsu akanta ta faɗi tare da warware mayafinta ta ci ɗamara dashi a ƙugu ta na jijjiga jiki.
"Haba Hajiya Munubiya, dan Allah ki kyale musu yarinyarsu suyi yanda suke so da ita, Allah yasan zuciyarki da niyyar taimakonta da kike tun tana ƙanƙanuwa, yanzu ba lokacin tada jijiyoyin wuya ko yin faɗa bane, kawai kibita da fatan alkairi da addu'ai Allah yasa auren ya zama silar canzawar ƙaddararta, dan Allah kiyi haƙuri kowa yasan kina tsananin son MAILAAH kuma kin ɗauketa kamar ƴar cikinki, yanzu kiyi ma ta nasiha da huɗuba akan abin da ya shafi zaman aure."
"Hajiya Umma ba za ki gane yanda nike ji ba, ba za ki gane yanda nike tsananin tausayin MAILAAH ba, ina jin rashin dacewa akan banzatar da ita da ake yi dan kawai an ganta a haka, yarinya tun tana ƙarama take shan wahalar rayuwa har girmanta haka, sannan ace abiyewa son zuciya ayi ma ta irin wannan auren, ki kalli gidan da ke amsa sunan gidan mijinta, wallahi ko me gadin gidnsu yafi ƙarfin zama a irin wannan gidan bare ita." tana magana tana kuka, idanuwanta suka kaɗa sukai jawur, cikin hanshaƙan matan da ke tsaitsaye su na yatsine fuska wa ta taja dogon tsaki tare da faɗin.
"Mtswwwww aikin banza da wofi, kinsan kina jin tausayinta har haka kika gagara aura ma ta ɗaya daga cikin jiga-jigan ƴaƴanki, sai yanzu da waɗanɗa keda ita suka aurar za ki zo da guntuwar gulmarki kina kuka munafurci wai ke gamai tausayi." maganar da matar ta yi ta sake tunzura tunzurarra, wato Hajiya Munubiya, nan ta koma kanta ta fara gaggasa ma ta magana, matar itama ba daga baya ba, sai ta zage ta dinga macifa tare da zagin Hajiya Munubiya, nan take ɗan ƙaramin ɗakin amarya ya hauci aka hau faɗa.
Ina zaune akan ɗan ƙaramin madaidaicin gadon ɗakin, tun da aka zaunar da ni akai na duƙe ina kallon farin zanin da aka shimfiɗa, jin hayaniyarsu nike tana zaman lafiyar kwanyata, nan take jikina yahau tsuma, hannayena da ƙafafuwa suka hau karkarwa kamar wacce aka jonawa shocking, iya yanda hayaniyarsu ke ƙara yawa iya haka nike sake birkicewa, nan take da kwarara wa ta iriyar ƙara me shiga har tsakiyar kwanyar du wanda yaji ta, lokaci ɗaya na miƙe tsaye tare da soma neman guduwa ina kwarara ihu, kafin kace me, tuni rabi da kwatar mutanen ɗakin sunyi waje a mugun kiɗime, ina shirin fitowa naji anfizgeni baya tare da ɗagani saka sannan aka sake ni ƙasa na faɗi timmm, nan take kaina ya bugu da ƙasa, sai nayi wani shiru ya gifta, hayaniyar da nike ji anamin a cikin kai ta daina, sai duhu daya lulluɓe ganina duniyar tai min tsif kamar babu kowa acikinta.
Ban san tsawon wane lokaci na ɗauka bana hayyacina ba, sai farkawa na yi naga wacce muke kira da Anty Ummie riƙe da ƙaramar fanka a saitina tana yimin tofi, kamar kullum bance komi ba sai tashi da nayi na zauna inabin saura da kallo, wasu suce min sannu wasu kuma su kalleni su taɓe baki, sai da marice yayi sannan kowa yayimin sallama suka watse bayan sun lulluɓemin fuskata da farin mayafi, daga inda nike zaune ina iya jin yanda motocinsu ke tafiya ɗaya bayan ɗaya, duƙar da kaina na yi na shiga tunanin iska dan babu abin da nike iya tunawa sai de inyi shiru ko inyi kamar na zurfafa a tunani, haka nike kaina babu komi sai fanko.
A hankali na sauke ƙafafuwa zuwa ƙasan gado, sai nayi saurin janyesu jin na taka wani abu me sulɓi, haka nike inada wuyar sabo musamman da sababbin abubuwa, rayuwa tafi yi min sauƙi a ɗakina na gidanmu, du bayan lokaci ana yin aiki da sauye-sauyen abubuwa, amma bani yarda ayi a ɗakina, du randa aka sauyamin wani abu sai na daɗe ban sake a ɗakinba, haka zanta zama a takure kamar raƙumi a keji.
Har nakoma na sake jingina sai kuma na sake tashi tunowa da ai Sallah nike so inyi, ahankali na sauko duka ƙafafuwa tare da yunƙura kamar me tsoron taka ƙasa na miƙe tsaye akan ƙafafuwana da nike jinsu kamar ba ajikina suke ba saboda tsami da ciwon da suke yi, ahankali na shiga takasu harna fice daga cikin ɗakin wanda duhu ya mamaye babu haske ko kaɗan, tsayawa nayi ina ƙarewa tsakar gidan kallon badan komi ba sai dan tap da nike nema, wani ɗan ƙaramin tanki na gani a kusa dashi ga famfo shima ƙarami, sai na tsugunna nayi fitsarin da cika min mara, sannan nai tsarki tare da ɗauro alwala, du sai da na jiƙe farar lafayar da ka naɗamin, a haka na koma ɗaki ina jina wani daban, sai tin da Anty Ummie ta nuna inda makunin haske yake kafin tafiyarsu na kalla, sai na miƙa hannuna bayan na rintse idanuwa gam na kunna haske, da sauri nakai zaune ina shesheka lokacin da nike ji a jikina farin hasken ya gauraye ko ina, kuma da alama hasken me ƙarfi ne sosai, nakai kusan mintuna arba'in ahaka ba tare dana tashi kona buɗe idona ba, sai da hasken yabi jikina, du wani gashi daya miƙe sai da ya kwanta sannan na tashi, jakar da nike aje kayan sallahta a ciki na gani agefe tare da wasu sabbin akwatinan, ban tsaya kallon komi dake wajen ba na kwalle kayana na saka rigar sallah da abayata.
Follow the 🌹MARYAM STAR⭐⭐⭐ HAUSA NOVELS AND MORE 𝐶𝐻𝐴𝑁𝑁𝐸𝐿✍️📚📙✏️ channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb5xdoy2975BcTM5m133
🥀🌹𝑴𝑨𝑰𝑳𝑨𝑨𝑯🌹🥀
𝑳𝑨𝑩𝑨𝑹𝑰 𝑴𝑬 𝑪𝑰𝑲𝑬 𝑫𝑨
𝑭𝑨𝑫𝑨𝑲𝑨𝑹𝑾𝑨
𝒁𝑨𝑳𝑳𝑨𝑹 𝑪𝑨𝑲𝑾𝑨𝑲𝑰𝒀𝑨
𝑫𝑨 𝒁𝑨𝒁𝒁𝑨𝑭𝑨𝑹 𝑺𝑶𝒀𝑨𝒀𝒀𝑨 𝑴𝑬 𝑻𝑺𝑨𝒀𝑨𝑾𝑨 𝑨𝑲𝑶𝑲𝑶𝑵 𝑲𝑨𝑰
𝑾𝑹𝑰𝑻𝑬 𝑩𝒀
𝑴𝑨𝑹𝒀𝑨𝑴 𝑺𝑻𝑨𝑹⭐⭐
𝒀𝑨𝑹 𝑩𝑨𝑰𝑾𝑨𝑹 𝑱𝑨𝑱𝑰𝑹𝑻𝑨𝑻𝑻𝑼.
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚
PAID BOOK
FREE PAGES
BOOK ONE
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الْحَمْدُ لِلَّهِ نَحْمَدُهُ وَنَسْتَعِينُهُ وَنَسْتَغْفِرُهُ وَنَعُوذُ بِاللَّهِ مِنْ شُرُورِ أَنْفُسِنَا وَمِنْ سَيِّئَاتِ أَعْمَالِنَا مَنْ يَهْدِهِ اللَّهُ فَلَا مُضِلَّ لَهُ وَمَنْ يُضْلِلْ فَلَا هَادِيَ لَهُ وَأَشْهَدُ أَنْ لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيكَ لَهُ وَأَنَّ مُحَمَّدًا صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ
---------Chapter 1 & 2
Miƙa na yi tare saka hannuna na rufe bakina da wa ta iriyar waskekiyar hamma ta kwace min ba tare dana shirya ba, ahankali na fara warware ƙafafuwana daga tankwasar da nai musu ta tsawon awanni, sai na ji sunyi min tsami har wa ta ƙara suke saki ƙas-ƙas, amma ahaka na daure na miƙe su a zaune, zura hannuna na yi tare da shafo daga dokin wuyana zuwa wuya, ina jin yanda ƙashin wajen kemin wanu iri saboda tsabar gajiya da duƙiyar da nayi, yawata idanuwa na nike a ko wane saƙo da lungu na ɗakin ina mamakin sanda har duhun dare ya mamaye ko ina ba tare dana ankara ba, sai na koma baya ina tariyo abin da ya faru.
Hayaniyar muryoyi mabanbanta ke tashi, kowace murya da abin da take faɗi, sai na girgiza kaina da naji yayimin wani irin nauyi kamar dutse, na tariye wurin hayaniyar da koma daidai inda najiyo muryar wacce nikewa kallon bango abar jinginata ke faɗin.
"Yo maraici hauka ne da za'a gallabi rayuwar baiwar Allah wacce bata ji ba bata gani ba, dan anga bata da wani zaɓi sai yanda rayuwa ta juyata shine za'abiyewa son zuciya acutar da ita, dan anga tana nuna kamar batason farin ciki ba shine za'a kashe ma ta rayuwa a tsaye, na rantse da girman Allah babu inda zanje imbar MAILAAH a wannan baƙin gidan me kama da akurkin kaji, dan kawai Allah ya jarabceta da ciwo sai a maidata kamar kamar mujiya a cikin mutane, wallahi ba zata zauna agidannan da sunan aure ba, sai na tafi da ita inda babu me sake jin ɗuriyarta.
Kyakkyawar fara tas ɗin matar da hutu da naira suka nuna jikinsu akanta ta faɗi tare da warware mayafinta ta ci ɗamara dashi a ƙugu ta na jijjiga jiki.
"Haba Hajiya Munubiya, dan Allah ki kyale musu yarinyarsu suyi yanda suke so da ita, Allah yasan zuciyarki da niyyar taimakonta da kike tun tana ƙanƙanuwa, yanzu ba lokacin tada jijiyoyin wuya ko yin faɗa bane, kawai kibita da fatan alkairi da addu'ai Allah yasa auren ya zama silar canzawar ƙaddararta, dan Allah kiyi haƙuri kowa yasan kina tsananin son MAILAAH kuma kin ɗauketa kamar ƴar cikinki, yanzu kiyi ma ta nasiha da huɗuba akan abin da ya shafi zaman aure."
"Hajiya Umma ba za ki gane yanda nike ji ba, ba za ki gane yanda nike tsananin tausayin MAILAAH ba, ina jin rashin dacewa akan banzatar da ita da ake yi dan kawai an ganta a haka, yarinya tun tana ƙarama take shan wahalar rayuwa har girmanta haka, sannan ace abiyewa son zuciya ayi ma ta irin wannan auren, ki kalli gidan da ke amsa sunan gidan mijinta, wallahi ko me gadin gidnsu yafi ƙarfin zama a irin wannan gidan bare ita." tana magana tana kuka, idanuwanta suka kaɗa sukai jawur, cikin hanshaƙan matan da ke tsaitsaye su na yatsine fuska wa ta taja dogon tsaki tare da faɗin.
"Mtswwwww aikin banza da wofi, kinsan kina jin tausayinta har haka kika gagara aura ma ta ɗaya daga cikin jiga-jigan ƴaƴanki, sai yanzu da waɗanɗa keda ita suka aurar za ki zo da guntuwar gulmarki kina kuka munafurci wai ke gamai tausayi." maganar da matar ta yi ta sake tunzura tunzurarra, wato Hajiya Munubiya, nan ta koma kanta ta fara gaggasa ma ta magana, matar itama ba daga baya ba, sai ta zage ta dinga macifa tare da zagin Hajiya Munubiya, nan take ɗan ƙaramin ɗakin amarya ya hauci aka hau faɗa.
Ina zaune akan ɗan ƙaramin madaidaicin gadon ɗakin, tun da aka zaunar da ni akai na duƙe ina kallon farin zanin da aka shimfiɗa, jin hayaniyarsu nike tana zaman lafiyar kwanyata, nan take jikina yahau tsuma, hannayena da ƙafafuwa suka hau karkarwa kamar wacce aka jonawa shocking, iya yanda hayaniyarsu ke ƙara yawa iya haka nike sake birkicewa, nan take da kwarara wa ta iriyar ƙara me shiga har tsakiyar kwanyar du wanda yaji ta, lokaci ɗaya na miƙe tsaye tare da soma neman guduwa ina kwarara ihu, kafin kace me, tuni rabi da kwatar mutanen ɗakin sunyi waje a mugun kiɗime, ina shirin fitowa naji anfizgeni baya tare da ɗagani saka sannan aka sake ni ƙasa na faɗi timmm, nan take kaina ya bugu da ƙasa, sai nayi wani shiru ya gifta, hayaniyar da nike ji anamin a cikin kai ta daina, sai duhu daya lulluɓe ganina duniyar tai min tsif kamar babu kowa acikinta.
Ban san tsawon wane lokaci na ɗauka bana hayyacina ba, sai farkawa na yi naga wacce muke kira da Anty Ummie riƙe da ƙaramar fanka a saitina tana yimin tofi, kamar kullum bance komi ba sai tashi da nayi na zauna inabin saura da kallo, wasu suce min sannu wasu kuma su kalleni su taɓe baki, sai da marice yayi sannan kowa yayimin sallama suka watse bayan sun lulluɓemin fuskata da farin mayafi, daga inda nike zaune ina iya jin yanda motocinsu ke tafiya ɗaya bayan ɗaya, duƙar da kaina na yi na shiga tunanin iska dan babu abin da nike iya tunawa sai de inyi shiru ko inyi kamar na zurfafa a tunani, haka nike kaina babu komi sai fanko.
A hankali na sauke ƙafafuwa zuwa ƙasan gado, sai nayi saurin janyesu jin na taka wani abu me sulɓi, haka nike inada wuyar sabo musamman da sababbin abubuwa, rayuwa tafi yi min sauƙi a ɗakina na gidanmu, du bayan lokaci ana yin aiki da sauye-sauyen abubuwa, amma bani yarda ayi a ɗakina, du randa aka sauyamin wani abu sai na daɗe ban sake a ɗakinba, haka zanta zama a takure kamar raƙumi a keji.
Har nakoma na sake jingina sai kuma na sake tashi tunowa da ai Sallah nike so inyi, ahankali na sauko duka ƙafafuwa tare da yunƙura kamar me tsoron taka ƙasa na miƙe tsaye akan ƙafafuwana da nike jinsu kamar ba ajikina suke ba saboda tsami da ciwon da suke yi, ahankali na shiga takasu harna fice daga cikin ɗakin wanda duhu ya mamaye babu haske ko kaɗan, tsayawa nayi ina ƙarewa tsakar gidan kallon badan komi ba sai dan tap da nike nema, wani ɗan ƙaramin tanki na gani a kusa dashi ga famfo shima ƙarami, sai na tsugunna nayi fitsarin da cika min mara, sannan nai tsarki tare da ɗauro alwala, du sai da na jiƙe farar lafayar da ka naɗamin, a haka na koma ɗaki ina jina wani daban, sai tin da Anty Ummie ta nuna inda makunin haske yake kafin tafiyarsu na kalla, sai na miƙa hannuna bayan na rintse idanuwa gam na kunna haske, da sauri nakai zaune ina shesheka lokacin da nike ji a jikina farin hasken ya gauraye ko ina, kuma da alama hasken me ƙarfi ne sosai, nakai kusan mintuna arba'in ahaka ba tare dana tashi kona buɗe idona ba, sai da hasken yabi jikina, du wani gashi daya miƙe sai da ya kwanta sannan na tashi, jakar da nike aje kayan sallahta a ciki na gani agefe tare da wasu sabbin akwatinan, ban tsaya kallon komi dake wajen ba na kwalle kayana na saka rigar sallah da abayata.