Gabatarwa
Laifin Boye Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 172 min read
DOCUMENT MADE BY
ESHATT SMILER HOM OF HAUSA NOVLS
DOCUMNTS
WASAPP 08066360176 FOR MORE
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 馃挕
Writing by Ayshat Dansabo lemu 馃枈
*1*
Alhaji shu'aib Abba aji zaune akatafaran falon gdn sa, hannunsa rikeda waya samfurin iPhone x , waya yake kuma bisa dukkanin alamu yana cikin matukar farinciki.
Hajiya kubrace ke sakkowa daga stairs, cikin takunta na kasaitattun mata, kallo daya zakai matan kasan hutu da jin dadi sunyi zaman dirshan ajikinta
Shiganta kadai ya isa yatabbatar maka da cewa itadin hamshakiya ce, kuma gogaggiyar mace wanda ilimi da wayewa taxamani ya matukar takarawa acikin rayuwanta
Ahnkl take takowa fuskanta dauke da murmushin da tasan yana matukar tasiri axuciyan gogan nata,
Byn ta zauna kusa dashi har jikinsu na gugan juna,wani qamshi mai matukar sanyin dadi ne ya doki hancin Alhaji shu'aib , hakan yasashi gyara zama yana mai aje wayan hannunsa, fuskanta yake kallo wanda yasha light make up tamkar ba babbar mace ba, kafin ya furta
"Madam kenan sai yanxu kike sakkowa ina shirin fita " murmushin ta mai tsada tasake saki kafin ta furta
"To ai dadyn su yusrah gani yanxu ko , af waishin ya mgn zuwa dakko , yusrah kasanfa jirginsu zai sauka karfe 5 ne bakuma lallai ne shushu yadakko taba, ksan kuma mutuniyar bataso driver kadai yaje dakkota"
Kallon ta yayi kafin yayi mgn wani hadadden aamshi yafara kaikawo , cikin hancinansu kafin wata murya mai matukar dadin amo tayi sallama, cikin falon dukansu dubansu suka mayar ga kofan falon,
Wani hadadden matashi ne yake sallama, yaci ado cikin kananan kaya da sukai matukar fito da kyawunsa,
Tareda tsantsan kuruciyar sa, ahnkl yake takowa cikin falon fuskan sa dauke da murmushi,
Daga hajiya kubra har alhaji shu'aib suma murmushin ne akan fuskar su,
Kai tsaye kusada kafan dadyn nasa ya tsuguna yana fadin, dady gud morning shafa suman kansa dadyn yayi wnda yake kwance luff , kafin ya amsa morning my son
Ya gajiyan tafiya ?
Murmushi matashin saurayin yayi yana fadin
"Gajiya tabi lfy dady "
Karisawa kusada hajiya kubrah yayi , har yana kwantar da kansa acinyan ta kafin ya furta
"Momy antashi lfy ?
Shafa kansa tayi tana murmushi take fadin, " my son anfito lfy ya gajiya ?
Ahnkl ya furta momy tabi lfy , mikewa yayi yana shafa cikin sa dayake alafe , kafin yakai dubansa ga dining area yana fadin
"Am very hungry mom bari inyi kalaci inzo musha hira "
Mikewa Alhaji Shu'aib yayi yana fadin
"Kazo dai kai shagwabar taka ta fama ba tunda jinka kake tamkar dan yaye idn karabi jikin mumy "
Hajiya kubrah kefadin
"Bakomi dai dadyn yusrah kaidai jeka sai ka dawo , karfe 5 shureim sai ya dakko yusrah idn ta sauka koni da kaina driver yakaini intaro abata "
Dining yawuce yana cin chips , tareda pepesoup na naman rago, yanayin taunansa cikin natsuwa da aji kadai xai birge ka
Kusan mintina akalla 30 yashafe kafin ya mike , yana aje cup din daya shanye ruwan tea din
Kafin ya nufi cikin falon inda momyn sa ke hakimce , hannunta rikeda jaridar daily trust,
Isowan shureim cikin falon yasata aje jaridar tana dubansa, kafin tafurta
" my shushu harka kammala ? Ya amsa da eh momy yana zama kusa da ita "
Hira sukeyi tamkar wasu sa'anin juna da momyn, rabin hiran suna yinsa akan tafiyan daya dawo , daga kasar london wanda ya shafe kusan watanni 2 acan,
Yana gudanar da seminar da aka turashi , kafin ya kammala yadawo gd
Cikin hiran ya dubi hajiya kubrah yana fadin
"Momy naji kina fadin yau baby yusy zata dawo kice yau kunnuwana sai sunyi ciwo , sbd surutunta daxata ishe mutane dashi"
Murmushi sosai mumyn tayi kafin tace kai shushu 'yar autan nawa akewa sharri
Mikewa yayi yana fadin "momy bari intafi gurin sudais inason ganinsa kafin ya wuce hospital"
Adawo lfy tace dashi kafin ta dauki jaridarta tai sama , shikuma ya fice kai tsaye katon parking lot ya nufa, wanda motoci ne na alfarma girke acikinta ,
Wata hadaddiyar mota baka wuluk ya bude , sabuwace kar ga dukkan alamu bata jima da kawota ba,
Dukkanin ma'aikatan dake kai kawo aharaban gdn , mika gaisuwa sukeyi gurin shalelan gdn kuma uban gdn su shureim,
Suna matukar girmamashi , da ganin mutuncinsa kasancewan s a mai saukin kai matuka , dayi musu alkhairy akai akai ,
Tuki yake cikin natsuwa da gwanancewa, kai tsaye garki ya nufa , byn yakira Dr. Sudais ya shaida masa yana bisa hanya
Byn ya baro gurin Dr. Sudais dinne yaji kawai guess house din dady yakeson zuwa,
Domin lokuta da daman yakanso kebewa aguri guda ya huta, sosai yake jin dadin kasancewa cikin katon gurin hutawan dake guess house din ,
Koda ya isa mai gadi ya bude ya kwashi gaisuwa, ganin motan dady dana Alhaji Adam yaba shureim mamaki , sbd baiyi tunanin ganin dady a Irin lokacin yazo hutawa ba
Sai dai ganin motar Alhaji adam ne yadan danne mamakinsa, yake tunanin watakil zasu tattauna harkokin kwangilolin sune da sauran business da sukeyi tare,
Koda shureim yai parking sai kaitsaye yanufi katafaren garden din dake gdn , wanda duk wanda yakasance ciki dole ne kasami natsuwa da nishadi ,
Gurin yanada matukar niimah shuke shukene birjik , ga resting chairs nan na hutawa banda kukan tsintsaye dake kai kawo cikin kunnuwan mutum,
Teburyn buga snooker ya nufa wanda shiyasa aka kafa , yana bugawa ahnkl byn ya gajine ya sami guri ya kwanta yana danne danne awayansa
Shine shiga snap, shiga IG , shiga Facebook har lokaci yaja,
Ahnkl Ya mike ya nufi cikin gdn , har xuwa lokacin motacin su dady nanan alamun basu tafiba
A katon falon ya xube byn ya dauki ruwa cikin frige , yana sha sanyin ruwan naratsa makoshinsa,
Aje goran ruwan yayi ya nufi up stairs, atunanin sa zaisami su dady afalon dake saman , sai dai babu motsin kowa
Hakan yasashi tunanin ko su bedroom din dadyne , inda yafi zama ciki ya huta domin bayaune kadai shushu yasaba zuwa hutawa , a guess house din ya tadda dadyn yaxoba shima
Saidai kowa yanada bedroom dinsa , hakan yasa shureim ya nufi dakin dayake mallakinsane
Murda kofan yayi tareda sanya kansa ciki , lokaci guda numfashinsa yafara barazanan daukewa
Janyo kofan yayi da saury hannuwansa duka biyune dafe da goshinsa,
Tunda yake aduniya bai taba mummunan gani irin na yauba, tuni yakeji xuciyansa na barazanan fadowa kasa,
Ahnkl yanufi bedroom din dadyn danufin shiga yazauna , kozaiji yafarka daga mummunan farkin dayake ganin yafada
Sai dai kash koda yabude dakin wani kara yasaki , tareda zubewa agurin yana salati tareda hawaye masu zafi dasuka fara sintiry afuskan sa ahnkl ya sulale kasa ,
Salatin dayake ya ankarar da Alhaji shu'aib cewa wani ya shigo cikin bedroom,
Cikin sauri yake kokarin rufe tsiraicinsa , yayinda yamakaro domin aikin gama yagama , turesu yayi daga kansa yana kokarin ganin kowaye mai wannan kasadan ,
Koda sukai ido hudu da shureim , wani kara shima yasaki dukkanin jikinsa rawa yake , murya asheke yake fadin shu shu rei m, da kyar yahado sunan ya furta cikin tsananin firgici da tashin hnkl,
Yagama sadakarwa yau azal tafada masa , asirinsa daya dade yana binnewa yau dansa mafi soyuwa aransa yaganshi
Yana aikata mummunan barna, wanda kunya kadai ta isheshi , da kuma yadda mutuncinsa zai zube a idon tilon dan nasa
Wani zazzafan hawaye kebiyo fusknsa, yayin da
Shureim ya dade da shidewa , baimasan abnd yacigaba da faruwaba
Ayshat Dansabo lemu 馃憣馃徎
LAIFIN BOYE
*_Haske writers_* *_association_* 妫e啯瀵�
Writing by Ayshat Dansabo lemu 妫e啯鐎�
*2*
Aysha kiyi hanzary ki fito mana , nikam banison yanayin sanyin jikinki ace mutum tun daxu bai gama shiry ba
Wata kyakykyawar macece ke wannan mgn , tana zaune cikin kayataccen parlonta , yayin da Aysha ke room dinta tana shiri mgn da umman ta tayine yasata , rataya jakanta ta fito cikin takunta na natsuwa da birgewa
Aysha kyakykyawar macece matuka, tana da matsakaicin tsayi bakuma xaka kirata mare tsayi kai tsayeba, Allah yabata baiwa na structure din jiki ,wanda ake kirada kirar kalangu , ko ina ajikinta acike yake tap akwai baiwan kugu da na fulani tubarkalla,
Wanda hakan kejanyo maza zuwa gareta , choculate color ce fatarta wanda yahadu da hutu yasa fatar yaiwani irin fresh , Aysha natsatsiyar macece tanada kamun kai matuka , sai dai awani lokutan miskilace matuka
Fitowanta kai tsaye kusada ummanta ta nufa , tana fadin
"Umma to bagashi yanzu nafitoba kumama banda abnki umma zuwa gurin saloon harwani saury ake masa"
Umman ta dubi Aysha tana cewa to saikije bedroom dina ki dauki 5k , sannan inaso idn kindawo kiceda bala kutsaya gdn hajiya kubrah , munyi waya akwai sako daxaki karbo min
To kawai tace ta nufi bedroom din umman , kudin ta dauka ta fito tana ma umma saita dawo tafice
Bala naganin fitowanta yayi saurin gyara parking, back sit tashige suka bar gdn kai tsaye a hadadden gurin saloon din yai parking Aysha ta fito ta shige
Kaman yadda tayi tunani hakan ne yakasance, ta tadda mutane balaifi hakan yasa saida ta bata lokaci , kafin aimata straiching da wankin kafa ta baro gurin ba, kaman yadda umma tace hakan akayi daga salon din kai tsaye gdn hajiya kubrah dake maitama suka nufa
*******
Farkawa shureim yayi yagansa kawai a falon dake nan up stairs , dadynsa da Alhaji Adam ne akansa , kallo daya zakai musu kasan dukkaninsu suna cikin tashin hnkl
Ahnkl yake kara bude idanunsa akan dadynsa, abubuwan dasuka faru yake dawomasa , sake rufe idanunsa yayi ya bude xuwa yanxu dayake ganin iyayen nasa tsaye akansa ya tabbatar badaga mafarki yatashi ba
Wasu hawaye masu zafi suke sintiry a fuskarsa, hakan yasa zuciyan Alhaji shu'aib sake tsinkewa, cikin karfin hali da dakiya ya tsugunna yana kokaryn kama hannun shureim din, yayin da shushun yayi saurin janye hannuwansa , yana watsawa dadyn wani kallo mai cikeda nuna tsana , wanda hakan bakaramin sake tsinkar da zuciyan dadyn hakan yayiba
Tashi zaune yayi yana duban Alhaji Adam , wanda yayi karfin halin fadin
"Shureim kada kazargi mahaifinka akan abnd idanuwanka sukagani, wlh sharrin shaidan ne da kuma son xuciya , hakika yau nidashi munyi matukar nadaman wannan mummunar harkan da muka jefa kanmu ciki"
Ahnkl shureim yasamu ya mike tsaye duk da jirin dake dibansa haka yake , takawa ahnkl ya nufi hanyar stairs batareda ya tsaya jin abnd alhaji adamu ke kokaryn sanar dashiba, sbd aganinsa basuda wani hujjan dazai gamsar dashi akan abnd adanunsa suka gane masa,
Allah ne kadai yakai shureim gd tundaga irin mahaukacin horn din dayake saki , mai gadin yasan babu lfy aguje yashige xuwa parking lot, yayi parking kai tsaye part dinsa yanufa ko takalmin kafansa bai cireba ya kwanta akan 3 seather , idanunsa ya lumshe yana juya duk wani abnd yafaru a yinin yau , hakika tunda yake bai taba mugun ganin daya firgitashi irin nayau ba,
Bai taba tunanin mahaifinsa daya bashi ingantacciyar tarbiya, zai kasance mai aikata sabo irin hakaba,
Bai taba tunanin mahaifinsa yana aikata boyayyen LAIFI irin wannan ba, ahnkl haushi da jin wani irin tsanar mahaifinsa ke kokaryn mamaye zuciyansa
Abnd bai taba tunani ko amafarki zaiji hakan game da ddynsa ba, sosai shureim yadafe kasan tareda fashewa da kuka tamkar karamin yaro, afili yake furta why? Dady meyasa kasauya halayyanka kyawawa zuwa aikata k'azamin LAIFIN BOYE irin wannan ba
Wayansa ne ya dauki rury hakan yasashi dauka , cwt mum abnd ke yawo akan screen din kenan ahnkl ya kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa, karfe 5 harta gota Sai alokacin yatuna da zance dauko yusrah daga airport dazaiyi
Jin muryansa kawai mum tayi tasan akwai matsala , cikin tashin hnkl ta furta shushu lfy kuwa ? Murynsa can kasa ya furta mumy vanjin dadine zazzabi da ciwan kai kedamuna
Salati tadauka tana fadin kana inane yanzu , ganin hnkln ta yatashi yasashi fadin" mum ina gurin Dr. Sudai yabani magani zan huta zuwa anjima sai indawo lokacin naji karfin jikina
Mgn dakko yusy asa driver yadakko ta plx mum, hajiya kubrah ta amsa dafadin hakan yazama dole shushun mumy , dakaina nida driver zamu dakkota nidai fatana Allah yasa jikin naka da sauki ?
Da kyar ya amsa da mumy karkidamu da sauki sosai , yanxu haka kaina ne kadai ke sarawa magani nasha , inaso danayi bacci natashi kila inji dadi sosai
Maza kwanta to my son ka huta momy tafadi tana katse wayan, hakan yaiwa shureim dadi ahnkl yake takawa zuwa bedroom dinsa kai tsaye tiolet yawuce
Yajima sosai kafin yafito sallolin da yawuceshi yayi , ya dade yana addua Allah kada yasa abnd yakeji gameda mahaifin shi yadore , domin kuwa wata zazzafan tsana yakeji nasa aransa
*****
Aysha ce take takawa cikin takunta mai cikeda natsuwa, xuwa cikin gdn hajiya kubrah byn driver yayi parking, sallama tayi cikin muryanta mai matukar sanyi da dadin amoh, jin shiru yasata samarma kanta mazauni
Mintina kusan 10 ta share azaune kafin tafara jiyo karan takun takalmi , ana sakkowa daga stairs daga kanta tayi cikin saa sukai ido 4 da hajiya kubrah
Cikin faraa da sakin fuska take fadin lale da Ayshatu , aitun daxu hajiya safiya tace gaki bisa hanya naji shiru
Takai karshen mgn ne tana karisowa cikin falon , tazauna hakan yaba Aisha daman zamowa kadan tana gaida hajiya kubran
Cikin matukar sakin fuska take amsa gaisuwar tata, kafin ta dora da fadin kinga yanxu haka autata zanje dakkowa yau zata sauka, farin cikin Aysha yakasa boyuwa hakan yada tasaki murmushi , tana fadin wow mumy kice gobe nan zan yini dani zaa kwance tsaraban Cairo
Sakon da zataba Aysha ta dakko tareda hado mata turaruka tabata , tare suka fito Aysha suka dauki hanyan gd yayinda motar hajiya kubrah suka nufi airport domin dakko autan ta wacce zata duro Daga kasar cairo , ta kammala karatunta gaba daya tazama cikakkiyar 'yar jarida
Ayshat Dansabo lemu 妫e啯鍟犳#鍐ㄧ法
[7:50PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*3*
Alhaji shu'aib da Alhaji Adam kuwa tun byn ficewan shureim, suka zube anan falon suna kallon_ kallon , da kyar Alhaji shu'aib ya iya furta
"Adamu yanxu menene mafita kakoga irin kallan tsanan da shushu kemin? Wlh tsanata nake hangowa karara afuskan sa, zan iya jure komi amma banda hango kiyayyata karara afuskan my son, inama shureim wani irin so dani kaina bansan yadda zan fassara shiba, hakan kuma baya rasa nasaba da irin nutsuwa da kamun kansa , uwa uba tsananin biyayyan dayake min, ina tsoran shureim ya juyamin baya Adam, tir da wannan mummunan sana'a tamu "
Ya kareshe mgn yana sauke ajiyan xuciya mai zafin gske , burinsa kawai kada shureim ya fallasa asirinsa agaban hajiya kubrah, duk da yasan zai wuya yayi hakan
Alhaji Adam wanda shima yarasa mafita , jiyake azuciyansa shima tamkar salman dansa ne yakamashi yana aikata abnd shureim yagani , da kyar ya iya duban aminin nasa kuma abokin gudanar da wannan business din tasu , dake janyo musu kazaman miliyoyin kudi tareda kwangiloli masu tsoka , daga manyan kasa , kafin ya furta
"Abokina kayi kokaryn ganin ayau basai gobe ba kazaunar da shureim , kafadamasa gskyn abnd yajefamu ga fara wannan harka , nasani shushu mai hnklne zai fahimcemu duk nasan bamuda wata hujja ,
Wanda zamu dogara dashi yasa shureim yagamsu ba son zuciyan mu daneman Tara kazaman dukiya yajanyo mana fadawa wannan harka Muna aikata LAIFIN BOYE tareda kawar da hnkln mutane akanmu ba , wacce tayi sanadiyyan bata rayuwanmu gaba daya"
Sosai suke tattauna yadda Alhaji shu'aib zai shawo kan shureim din, daga karshe shawaran Alhaji Adam yadauka
Shureim wanda yake kwance yanajin zazzabi mai zafi na neman rufeshi, wayansa yajanyo yayi dialing number Dr. Sudais , buga biyu ya Daga wayan yana fadin
"Guy yane ? "
Da kyar shureim ya iya furta
"Plxx guy kayi sauri kazo wlh zazzabi mai zafi yakeson rufeni , gara kazo kayimin allura tunkan nakaiga rafke muku cikin daki"
Da mamaki sosai sudai kejin wai shureim baida lfy lallai yanzu yanzu sai Allah, kaman ba dazu suka rabu suna ma juna shakiyanci ba,
Hakan yasashi furta
"Kaganin dama yanzu zan baro hospital din, "
*****
Tafiya sukeyi bisa titi zukekiyar budurwa mai kimanin shekaru 18 ne , kwance akafadun hajiya kubrah sai zuba ruwan shagwaba take , ita adole tayi missing mumyn tasu a lot yayinda hajiya kubran ke biye mata
Cikin shagwabar take fadin
"Mum wai ya shushu ciwan me yake ne ? "
Hajiya kubrah tashafa byn ta tana fadin
"Hmmn wlh baby hnkln yana kan shushu cewa yayi zazzabi ne , nikuma yadda nasanshi da juriyan cuta , muryansa yadaga hnkln amma bari mujira dawowansa aga halin dayake ciki"
Koda suka iso gd suna shigowa compound din mumy tahango motar Dr. Sudais, hakan yasa ta dubi yusrah tana fadin
"Yawwa yusy kinga motar sudais inaga yadawo da shushune , bari muje part din nasa muga yanayin jikin nasa"
Atare suka nufi part din shureim itada momyn yayinda driver ke kwasan kayanta xuwa cikin gd
Kwance yake sunadan mgn da Dr. Sudai wanda yagama yimasa injection,sudais na tambayan shureim din yadda akai ciwo yazo da gaggawa haka , gashi koda ya gwadasa yadda yaji bugun zuciyansa, yakaru almun yana cikin tashin hnkl tambayan shureim damuwansa yake da abnd yajanyo hakan agaresa amma yayi biris dashi
Ahaka hajiya kubrah sukai sallama itada yusrah , sudais ya amsa sallaman fusknsa fes akan yusrah wanda girmanta da kyawun data kara yai matukar bashi mamaki
Yusrah da gudu ta isaga shureim dake ta saukemata smiling , ta zube kasa tareda kama hannuwansa tai kising
Tana fadin "my ya shushu I miss u ya jikin naka "?
Sake damke hannuwanta yayi yana tashi zaune ahnkl ya furta
" my baby doll jiki dasauki zazzabi cefa kuma kinga guy dinnan yamin injection harna farajin sauki so ya hanya babyn mumy"
Hajiya kubrah data zuba musu idanu taji dadi sosai ganin shureim din jikin nasa dasauki bayadda tayi zato ba
Karisawa tayi tareda da shafa kansa kafin ta furta
"My son ya jikin ? Murmushi yai yana fadin momy nama warke fa ni dama nafada miki ba wani ciwo bane sosai, "
Sudais ne ya dubi yusrah yana fadin babyn mumy baki ganni bane bako mgn , ko duk zumudin ganin shushu ne ya rufe idanun?
Yadda yayi mgn sai yasa yusrah jin kunya hakan yasa ta rufe idanunta tana fadin
"Laah ya sudais sorry wlh dokin ganin my cwt bro yarufen idanu "
Shima murmushi yayi yana tambayanta ya karatu tareda tayata murnan kammalawa , da fatan alkhairy sun dan jima kafin subar part din shureim din , har suka fice idanun sudais nakan yusrah wacce gaba daya ganinta yasashi cikin jin wani yanayi atattare dashi
Ya kasa boye mamakinsa saida ya dubi shureim yana fadin
"Guy kaga yadda baby yusy tazama big gal kuwa gsky nidai inajin 'yar gd zaai indai mumy zata bani "
Wani harara shureim ya aika masa kafin yace kaifa dan world ne sudais , kanwar bayanka zaka kalla da sunan luv don Allah karka janyo mana raini
Karfe 9pm iyalan ne duka zaune ana cin dinner , momy dady and yusrah banda shureim wanda sam yaki shigowa part din, domin bayi kaunar sake dora idanunsa akan dadyn ,
Momy ce ta daga waya takirashi bugu daya ya dauka , yana fadin mumy takatse sa da fadin son lfy bakashigo yin dinner ba duk gamu mun hadu ,
Ahnkl ya furta mumy kinmanta jikin babu dadine , kisa yusrah tadan kawomin part dina , ruwan tea kawai saidan abu mara nauyi yakareshe mgn da shagwaba sosai
Hanging up tayi tana kallon dady take fadin, dadyn yusrah shushu fa baijin dadi , cikeda firgici da tashin hnkl yake furta
"Meya samesa kubrah kuma kika kasa sanar dani tun shigowata gdn , "
Hajiya kubrah tayi murmushinta mai kayatarwa , kafin ta furta
"easy dadyn yusrah jikin
aida sauki fever ne kuma yasamu sauki sosai yanxuma shagwabar ce tamotsa wai yusrah takai masa abncin part dinsa"
Ajiyan zuciya Alhaji shu'aib ya sauke , tuni ya harbo girgin shureim din, sam bayason haduwansu ne shiyasa zai fara gujewa duk wata hanya dazai sa suhadu , sosai hnkln sa yatashi sai dai yazama dole ya koyi danne damuwansa gaban momyn , tun kafin tafara fahimtar wani abu
12 o'clock nadare Alhaji shu'aib ne ke zare jikinsa ahnkl daga hajiya kubrah, wacce tayi nisa sosai cikin baccin ta kai komo yafara cikin tafkeken bedroom din nasa , kafin daga bisani ya lallaba ya fice
Kaitsaye part din shureim ya nufa koda yakai kofar part din , waya yazaro yayi kiransa sai dai hartagama ringing bai daga ba
Cikeda mamaki yasake dialing sai jin wayan yayi is switch off , hakan yai matukar bashi mamaki
Ahnkl yafara knocking kofar shureim wanda ke kwance aparlon sa , yana kallon wani American film domin yasan koya kwanta damuwa, bazata barshi ya iyama bacci ba yaji shigowan kirn dadyn
Jin ana knocking yabashi mamaki waye zaizo part dinsa a wannan tym din
Cikeda fargaba ya mike jin haryanxu ba abar knocking din ba, bude kofar yayi ahnkl ganin dady yasa gabanshi faduwa, lokaci guda yahade fusknsa tamau fuuu ya juya xuwa cikin parlon
Alhaji shu'aib ya rufa masa baya , zama shureim yayi tareda runtse idanunsa , dady nabinsa da kallon mamakin sauyawar shureim din lokaci guda
Ahnkl ya zauna kusada son din nasa tareda dafa kafadunsa , kafin yafara kokarin yadda zaiyi shureim ya sauraresa
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[7:58PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*4*
Kiran sunansa yayi ahnkl shureim, yadda yakirasa da sunan shureim yasan tabbas dadyn mgn mai muhimmanci zaiyi dashi , hakan yasa shi amsawa da na'am dady
Dady yacigaba da fadin"shureim inaso kabani hnkln ka da nutsuwarka nan , abnd yasa nazabi wannan lokacin sbd inaso abnd zamu tattauna yazama sirri
Ina nufin ko mumyn ko ban yadda taji wannan sirrin nawaba, nasani ayanzu kanajin tsanata shureim, kanaji inama banine mahaifinka ba ayanzu, domin duk da mai tarbiya irinka , bazai so nazama uba agaresa ba "
Hawaye masu zafi suka sauka akan kafadun shureim, wanda harzuwa lokacin idanun sa aruntse suke , jin digon hawyen yasashi bude idanunsa yana kallon mahaifinsa na zubda hawaye
Kallon sa yayi tareda sauka kasa ya kwantar da kanshi kan kafafun dadyn, ahnkl ya furta dady ina jinka
Dadyn ma kasa yazauna shureim ya zuba masa idanuwa , yana sauraren yaji menene dadyn yazo dashi adai dai wannan lokacin, kafin dadyn yafara mgn dacewa
"Shureim tunda aka haifeka kataso kaganka cikin arziki ne, bakata taba sanin miye babu ba, duk abnd kanema kana samu har zuwa lokacin Dama zama mutum
Nabaka dukkanin kulawa tareda gata nayi kokaryn
Ganin na inganta tarbiyanka, cikin hukuncin Allah kazamo cikin yaron da duk wani uba zaiyi alfaharin kasancewan ka da agaresa"
"Shureim kaman yadda kataso kasani nidin , hamshakin Dan kwangilane kuma dan kasuwa , da wadannan sana'a biyu natara duk wani arziki daka sani shureim"
Tunkafin na aury kubrah ina cikin mazajen da zaa lissfa cikin masu rufin asiry sosai ,
Wannan mummunan harka da muka fara shureim , tasamo asaline wani lokaci da muka nemi wata kwangila mai tsoka , nida abokina Alhaji Adamu sai aka hadamu da wani minister , amatsayin na manyan 'yan kwangiloli bamusha wahalan ganawa dashi ba
Sai dai koda muka sami ganinsa yabamu address din gueshouse din sane , inda wata Sunday ban mancewa misalin 4 na yamma muka samesa nida Adamu
Koda muka isa akai mana iso zuwa cikin falon , abn mamaki munsamesa ne tareda 'yan mata kusan guda uku , bayaga wata gogaggiyar hajiya wacce alamu yanuna tareda wadannan matan suke
Ganinmu yasa yasallami wannan hajiyar tareda wadannan 'yan matan ya basu umurnin shigewa ciki , yanayin shigansu da tafiyansu kadai zai shedamaka cikakkun 'yan barikine
Byn shegewansu ne minister ya dubemu byn mungaisa cikin aminci da mutunci , mukasake shaida masa mune dai masu nemn abamu kwangilolin da sanata ya shaida musa
Daga lokacin yafara shaida mana tsarinsu shida sanata, na indai munason wannan kwangila dolene mucika sharuddan dazasu bamu , sharadi nafarko kodai suyi lalata damu sannan ayi signing sannan kwangila tazo garemu , ko kuma mu amince zamu dinga kawo musu abokan harka maza da mata domin su rika hutawa dasu ,
Idn kuma har bamu amince da hakanba to sai dai mu hakura da wannan kwangila , wanda hakan na nufin zamuyi asaran riba ta miliyoyin kudi ba kadan ba
Sai dai nan take nashaida ma minister bamu aminta da wadannan sharuda ba, sai dariyan da yayi da kuma kashedin daya biyo bayane yasa muka aminta dashi da kuma dukkanin abnd ya bukata
Domin yashaida mana cewa tunda yafallasa asirinsa , dole mu muzaba cikin abu 2 daya lissafo mana , bijirewa hakan yana nufin toshewar duk wata kafa dazamu iya samin kwangila koda ko ta taroce , hakan yadaga hnkln mu kwarai da gske
Batareda dogon nazari ba muka aminta da kudirinsa na 2, wato mudinga kawo musu mata da kuma matasa suna holewa dasu , "
Cikin tsananin tashin hnkl shushu ya kalli mahaifinsa , tuni yafaraji kansa na sarawa wannan wace irin kazamar sana'ace ?
Sai dai Alhaji shu'aib yakatse tunanin shureim ta hanyar cigaba da mgn yana fadin
"Shureim bamu baro gurin minister ba saida muka tabbatar masa dacewa mun amince da kudurinsa, Adamu shine yasake ba minister tabbacin cikin satin zaiga manyan kaya "
Nasan alokuta da dama kanaji idn ina waya , ina yawan cewa ansami manyan kaya , to ba kaya nake nufi irin nabusiness dina daka sani ba , alokuta da daman manyan kayan danake fadin suna nufin mata da kuma matasa ,
Tundaga lokacin muka zama tamkar masu safaran , yan mata da matasa muna rabasu hotel -hotel ga manyan kasannan , mukuma muna samun manyan kudade da kwangiloli naban mamaki ,
Kafin kace haka munzama manyan kawalai , kudi kota ina muke samu duk wata kwangila da zata fito , daga state ko federal mune kan gaba ,
Tunda muka fara wannan harkan shureim , ban taba sama zuciyata zan iya lalata da 'ya mace ba , hasalima idn aka kawosu bakasafai hakan bukaci ganin su ba, sai dai mubada umurni arabasu hotels byn mun tabbatar da kayayyakin sun wanku , zakuma ayaba dasu matuka Alhaji Adamu shine mutumin da Azal yafara fadawa kansa
Watarana ankawo mana manyan kaya , masu matukar kyau da daukan hnkl , wadanda idn mutum bai yi da gske ba to tabbas shaidan zai iya nasara akansa,
Lokacin da aka basu kaya domin gyarasu kaman yadda akeyi , kafin ayi posting ma senatocin mu da ministers ne , shaidan yayi nasara akansa , harya keta mutuncin daya Daga ciki wacce take sabuwace baa taba komi da itba
Kasancewar yawancin kayan da ake bukata sunfi son sabbi fil aledansu ne, tunda ga lokacin Admu yafara harka duk kayan da zaa kawo sai sauki daya ciki , sai dai bai taba shaawar neman jinsin saba sai dai mata ,
Sannu ahnkl kasancewar sa abokin tafiya , amini kuma abokin harka yasa yau da gobe dayake kwadaitar dani , irin dadin zumar dayake lasa yasa tun ina masa fada har nadaina nafara sha'awan nima inlashi gardin zuman dayake kwadaitar dani
Wata rana nima ankawo wasu 'yan mata kyawawa, sai dai Irin gogaggun yarane da idanunsu ya bude da harkan sosai , daya Daga cikinsu da kanta tai shaawan kasancewa dani , Alhaji ta tunkara da mgn domin shine nasu alokacin yasanr da jta nisam bana wannan hakan
Sai dai dayake ance mace shaidaniyace , hakan yasa suka sakamun magani acikin lemu , awannan rana komi yafaru aranan nakara sanin zumar wata mace wacce ba kubrah ba, yanayin data tafi dani ya kara jefani cikin wani hali
Daga ranan shedan yaci gaba dajan ragamanmu , dazaran ankawo mata saimun huta dasu kafin mu aikasu inda yakamata , sosai suke bamu hadin kai kasancewar mu masu arziki komi najin dadin rayuwa muna tanadar musu ,
Sai dai bamu taba shawa'awar kusanta jinsinmu na mazaba sam , sai mu nemosu murabasu gasu minister da manyan kasa
Ko kadan bantaba bude wata kofa ko kafan da kubrah zata gane ina mu'amala da wasu mataba, sai dai ance rana dubu ta barawo ne rana daya tak namai kaya, sai gashi tsayin shekaru muna sheke ayarmu tareda da kawar da hnkln mutane damuke , da harkan business wacce aboye harkan damuke gudanarwa yafi komi kawomana arziki , wlh shureim wannan kasar tamu lalacewarta yawuce inda kake tunani
Manyan sun baci ta yadda ko aiki kake neman karin girma ko wani mukami mai tsoka , sai kabi hanyan lalata ko fasadi kafin subaka dama kakai inda kakeso, sai dai wanda Allah ya tsallakar dakuma wanda bai biyewa son zuciya da kuma kwadayin tara dukiyaba ,
Shureim inaso kayafemin ka kuma rufe sirrina , baniso kubrah taji wannan mummunar lbryn , idn kaimin hakan tabbas zan san kai cikakken dane nagary agareni , kuma daga yau nayima alkawarin daina wannan harkan , zan rungumi kasuwanci na zan hakura da naiman duk wata kazamiyar kwangila , matukar saina sabi Allah kona kauce hanya zan sameta ,
Sosai shushu ke kuka tamkar karamin yaro, da kyar ya iya duban dadyn sa kafin yafara mgn
"Dady hakika kun aikata mafi mummunan fasadi adoran kasa , kun zabi ku tsuda dukiyanku da kazantacciyar arziki , ayau ina kyamatar duk wani abu daka mallakamin koka ciyar dani da kudin kazan tacciyar kwangilan da kuke samu
Dady meyasa kuka biyema son zuciyoyinku da neman tara dinbin dukiya , ta hanyar kaucewa hanya?
Ayau inajin nadaman kasancewa ta jininka , ina ji inama nafito cikin talakawa wanda suke nema da kyar sannan suci susha, da irin wannan kazamar dukiyan daka hada halas da haram kana ciyar damu ka shayar damu
Meyasa dady zabi aikata LAIFUKAN BOYE ? don kawai katara arziki , dady ina mai bakin cikin kasan cewata jininka wlh dady, kasani cewa wannan abnd kuke aikatawa , zakubar mana mummunan tabone da bazai taba gogewa ba
idn ni ban tona sirrin ka ba tabbas Allah zai tona dady ,
Alhaji shu'aib gaba daya yagama muzanta agaban dan nasa, jiyake yi tamkar ya ga cewa komi cikin mafarki yake kasancewa ba gaske bane,
Sai dai muryan shureim ne yadawo dashi hayyacinsa jin yana fadin
"Dady inaso nai maka nasiha daka sadaukar da duk wata dukiya daka tarasa ta wannan harkan, kayi gaggawar sadaukar dasu domin tsarkake dukiyankata halas ,
Ka rungumi dukiyar ka ta halas kacigaba da juyata , koda ko hakan na nufin karayar arxiki ne agareka, "
Duk wani kaddara da kasan kabani cikin wannan kazamar dukiyan daka tara , kajanyeta daga gareni dady ,
Yana kaiwa nan yayi gaggawar tashi xuwa bedroom dinsa, yayinda yarufo kofan da karfin gske , fadawa gado yayi yana kuka sosai yasan yanason mahaifinsa, amma yazama dole yajuyamai baya , hakan kadai shizaisa ya saduda yakuma tuba daga wannan mummunan fasadin dasuke aikatawa"
Cikeda mutuwan jiki tareda damuwa matuka dady ya mike yabar part din shureim ,yana mai nadaman duk abnd ya aikata arayuwansa,
Gashi farin cikinsa na nema ya ruguje , domin bayaji zai iya jure juya bayan shushu daga garesa ,gashi yasan tabbas barin wannan harka itace rufin asirinsa
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[8:02PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*5*
Cikin mutuwan jiki dady yafice daga part din shureim, ahankali ya sadada zuwa bedroom dinsa , har zuwa lokacin hajiya kubrah bacci take
Kwanciya yayi tareda raba jikinsa da nata , idanunsa arufe yake ruf yayinda zuciyansa ke cikeda tunani da damuwa,
Bayaji adaren yau zai iya rintsawa Sam hakan yasashi tunanin mikewa ya dauro alwala, sallah yayi yana adduan Allah ya yafemasa , yakuma bashi ikon nesanta kanshi daga mummunan laifukan da suke aikatawa na BOYE
Misalin 9am na safe iyalan gdn ne zaune a dining suna kalaci , yusrah wacce ke sanye cikin shigan rigada wando na bacci , wanda yai mata matukar kyau domin itadin kyakykyawace sahun farko
Kowa yayi nisa cikin cin abncinsa shushu ne kadai har zuwa lokacin bai shigoba, hajiya kubrah na kokaryn daga waya ta kirashi
Sukaji bude kofa tareda hadadden qamshinsa yafara cika hancinansu, yana sanye cikin shirin zuwa office yaci suit wanda yai matukar yimasa kyau, tareda fito da kuruciyansa zallah
Hnkl yake karisowa cikin falon har ya iso dining area din, yusrah da murnanta take fadin ya shureim gud morning byn yaja kujeran kusa da ita yazauna
Shima kokarin wadata fuskansa da murmushi yakeyi , alokacin dayake shafa kanta yana fadin
"Morning my yusy ya gajiyan tafiya ko ince yagajiyan zaman flight? "
Cikeda murmushi da shagwaba take fadin "babu gajiya my big bros "
Dady yafara gaisarwa amma sam bai yadda sun hada idanunsu ba, saiya juya gurin mumy wanda zuciyansa ke cikeda fal da tausayinta,
Domin yasani idn hartaji abnd dady suke aikatawa a boye, zataji bakin ciki tareda kaurace masa domin kullin nasihanta akansu baya wuce, yatsaya ma halas ya guji aikata duk wata sabo, tana yawan kwadaitar dashi gameda aje iyali,
Domin gujewa fadawa halaka
Yazataji idn taji wai dadyne yake kawalcin mata harda matasa , bai tsaya anan ba shima yana aikata zina dasu ,
Sosai wani takaicin mahaifin nasa yasake kamashi, kadan ya iyashan ruwan shayi ya wuce office , yana aiki da National Health Insurance dake nan Abuja
******
Jakan hannun ta ajiye tareda zubewa bisa kujera , tana fadin wash ummah nagaji wlh yadda kikasan a motar kasuwa nayi fitannan
Ayshace take wannan mgn byn tadawo tana mikawa ummanta sakon , data amso daga gurin hajiya kubrah ta dora da fadin
"Wlh umma kinsan muna gaisawa bamu jimaba itama tace zata dakko yusrah , yau zata dawo harta kammala karatunta nikam karatun yusy yayi sauri sosai
Hajiya safiya ta dubi tilon 'yar tata tana fadin" ai haka karatun yake idn bakai kakeba mussamman idn katafi waje nan da nan saikiga kadawo ka kammala"
Aysha wacce tamike tana fadin "wlh kuwa umma muma dai Alhamdulillh tunda mun kammala asa'a, services kadai ya rage mana tana karisa mgn ne tareda daukan hand bag dinta , ta nufi room dinta yayin da tabar ummah na bude sakon ta data amso daga gdn hajiya kubrah
****
Matashiyar budurwa ce da bazata wuce shekaru 19 aduniya ba, duk da hijab ne sanye ajikinta hakan bai boye kyawunta ba, farace tas da ita da alamu kuma Allah yayi mata baiwan halitta mai daukar hnkl
Tafiya takeyi cikin natsuwa wanda duk namijin daya dora idanunsa akanta, zaiyi zaton wata natsatsiyar macece mai matukar kamun kai
Koda ta iso wani katon gd wanda kai tsaye bazaka kirashi da gdn talakawaba, zaka lissafashi ajerin gidaje na masu rufin asiry
Tura kofar gate din shiga tayi tasanya kanta ciki kaman jira akeyi tashigo gdn, wayanta yafara rury zaro sayar tayi daga cikin jakan ta byn taja tatsaya
Cikin rawan jiki ta amsa wayan tana fadin" hello bakin rai bakin fama banji abnd me kiran take fadiba , nadaiji wannan budurwan nafadin "karki damu dole gobe mukasance tare nima din nayi kewarki matuka aminiya, daurewa kawai nakeyi kinsan halin Abba h bayi kaunan yawan fitata, dama skull kesawa kaji koda yaushe kana free to yanzu mungama, banida wani sakewa yanxu amma karki damu nasan yadda zanyi
Suna gama wayan tayi shigewarta cikin gdn , tana rikeda wayanta samfuryn iphone 8 kai tsaye falon tashiga tana kwada sallama
Mahaifiyarta na kwance da alamu kaman bata lfy ne , domin kuwa tana kwance bisa 3 seather ne ta rufa da bargo,
Jin sallama yasata bude fuskarta tana duban kofa , take fadin Aneesa sai yanxu ? Yi maza ki aje jaka kishiga kitchen
Aneesa tana kokaryn shiga dakinta take fadin, to ummah ya jikin toh,?
Umman ta amsa da dasauki sosai Aneesah kawai dai haryanzu , jikinane bakarfi sosai shiyasa kiyi maza kidaura girki kinga haryanxu lantana, bata dawo ba idn tadawo din saiku karisa tare
Aneesa ta amsada toh ummah karki damu bari in sauya kaya, tana shiga room dinta tacire pitted gown din dake jikinta, byn tacire hijab din Aneesa tanada matukar diri mai daukan hnkl , kyakkykyawace matuka wacce ta mallaki duk wani abu da mace zatai dagawa dashi
Wata riga mara nauyi tasaka tareda daura zani akai ta fito tanufi kitchen domin daura girkin rana, kaman yadda umman tabata umurni
Washegary Aneesa ce ke shiri domin tanaso yau duk yadda zaai sukance da Rufaida , wata riga da wando tasaka wadanda basuda maraba da tsirara, sai ta dakko wani hadadden after dress ta daura akai
Light make up taima face dinta tayi kyau tamkar kasaceta ka gudu,
Safan kafa tasaka byn tadakko hijab cream tasaka wanda yasauka guiwanta, tafito sak cikin shiga takamala gaduk wanda yaga Aneesa , zaimata kallo na mace kamila tagaske
Around 11 tafito ummanta wacce tayi garas, tana kai kawo tsakanin kitchen da kuma falon Abban na Aneesa, dayake weekend ne yana gd bakasafai yafaye fitaba
Kallon Aneesa tayi tana fadin harkin fito , saiki je kisake sanarda Abban naki , duk da nasanar dashi zaki dubiyan Rufaida ne ba lfy
Aneesa tasauke murmushi tana fadin "to ummah tana shigewa bangaren Abban nata , zaune yake afalon nasa yana kallon CNN ya amsa sallaman Aneesah
Sake gaidashi tayi tareda shaida masa zata gdn su Rufaida ne domin duba jikinta , Abban nata ya dubeta tareda kallon shiganta wanda baiga makusaba, illah sake yaba natsuwan yarinyar taska dayake gani
1k yazaro yabata yana fadin Aneesah karbi wannan,kitabbatar karfe 5 na yamma yamiki acikin gdn nan, kinsani sarai banason yawon banza
Kasada kanta tasake yi tana fadin " to Abba insha Allah tadauki kudin tayi gaba
Bawani tafiya mai tsawo sukayi ba suka isa gdn su Rufaida wanda yake anguwan Rimi Kaduna, katon gd ne sosai wanda kana kallo kasan mai kudin gaske ne mamallakin sa
Koda mai gadi ya bude yaga Aneesah ce gaisuwa yashiga mika mata, domin duk wanda ya kwana yatashi cikin gdn su Rufaida yasan matsayin datake dashi aguryn shalelen gdn wato Rufy
Gaidashi tayi cikin girmamawa kaman yadda tasaba, kasancewansa dattijo datake ganin mutuncin sa, jaka taballe tabashi 500 sabuwa kal cikin irin kudaden datake samu daga abokan harkanta , da kuma Rufy wacce bata kyashin kashe mata kudi ko mallaka mata
Koda tashige katon main parlor na gdn babu motsin kowa, hakan yasata kai tsaye ta nufi bedroom dinn hajiya khairiyya
Sallama takeyi cikin sanyin muryanta hajiya khairiyya da suke kirada momy , ta amsa tana fadin "barkadai Aneesa ai tun jiya Rufaida ke shelan zuwanki "
Cikin girmamawa tagaida momyn kafin ta fito , tanufi wani corridor wanda zai kaita dakin Rufaida
Tunkafin takarisa kofar room din tafara kwallah mata kira, bakin rai bakin fama kifito mana, aguje wata budurwa da tagaji da haduwa tayo waje suka rungume juna
Sosai Rufaida tasake kwakume Aneesah tana shakan hadaddan qamshin dake fita ajikinta, yayinda hannusanta ke kokarin kama wadataccen kugun Aneesah
Aneesah ne tajanye jikinta tana fadin shegiya tawan aikya baridai mushiga daga ciki ko , dukansu dariya suka saka kafin su shige dakin Rufaida , wanda bashida maraba da dakin mace mai aure domin babu abnd baa zuba najin dadin rayuwa acikinsaba
Basu tsaya a karamin falonba kai tsaye bedroom dinta suka yada zango
Wanda suna shiga takai hannu tacire hijab din dake jikin Aneesa, tareda after dress din daya boye asalin shigan dake jikin Aneey din
Wani mayen kallon take binta dashi tamkar zata cinyeta danya
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[8:16PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*6*
Alhaji Adam zaune ababban falon sa , gefensa matarsa ce hajiya safeeya wayansa yadauki rury, hannu takai tadauki wayan tareda mika masa
Amsa yayi ya kara akunni byn ya latsa ok, Alhaji shu'aib ne hakan yasashi kokarin mikewa , yanufi hanyar bedroom dinsa domin kebewa
Daga bangaren Alhaji shu'aib kuwa yasanar da Alhaji Adam din cewa , gashinan bisa hanya yanaso sutattauna mgn akan abnd yafaru ne
Hakan yasa Alhaji Adam din sanar dashi su hadu a farm house ne nashi Alhaji Adam, domin kokadan bayason su tattauna matsalan a gdn sa
Cikin sauri yadauki hula da car key dinsa byn yasake feshe jikinsa da turare, yafito yana duban hajiya safeeya yake fadin
"Umman Aysha zanje farm house munada meeting ne dazamu gabatar yanxu "
Adawo lfy taimai suka hero tare har zuwa babban main parlor na gdn, Ayshat ce kwance cikin shigan wata hadaddiyar gown ta boyel , tayi kyau harta gaji ganin Abban ta yafito cikin shirin fita , yasata mikewa ta iso garesa kaitsaye kanta ta kwantar akafadunsa tana fadin
"Abba fita zakai dayanzu nake shirin zuwa maka hira ,"
Shafa kanta yayi yana fadin "Aysha meeting garemu yanzu haka su dadynki Alhaji shu'aib sunacan suna jirana, "
Shagwabe face tayi tana fadin "shikenan Abba adawo lfy nima zuwa anjima nakeso inje gurin yusrah kasan jiya tadwo gara inje a kwance tsaraba dani"
Murmushi yayi yana fadin gud gal to adawo lfy yafice abnsa
Ita kuma Ayshat ta nufi room dinta domin gyara face dinta kafin ta fito don zuwa gurin yusrah
*****
Farm house Alhaji shu'aib da Alhaji Adam ne zaune , suna hira akan abnd yashafi harkokin business dinsu , na shigo da kayan gini zuwa motoci da sauransu daga kasashen ke'tare
Kafin daga bisani Alhaji shu'aib ya dubi Alhaji Adam yana fadin
"Wato Adamu duk yadda nake tunanin shushu zai fahimceni abn yaci tura, hasalima tsanata nake hangowa daga idanunsa karara, hakika nayi nadaman aikata LAIFIN BOYE, gashi yanzu natra dukiyan sai dai asanadiyyan tonan asirinmu gashi shushu na nema ya juyan baya "
Alhaji Adam ya nisa kafin ya furta "ka kwantr da hnklnk shu'aib shureim bazai taba iya juyama bayaba, kasani duk dana kwarai dole yaji zafin abnd muke aikatawa , amma ina tabbatr maka zai sakko ne "
Alhaji shu'aib ya karbi mgn yana fadin"to Allah yasa hakan ni yanzu abnd nakeso kasani shine bani ba duk wata harka damukeyi ada
Bazan cigaba da amsar duk wata kazamar kwangila ba, hasalima duk wani dukiyata danasan ta hanyar kazamar kwangila nasameta , na yanke shawaran sadaukar da ita ga marayu , zan gina musu gd inkuma basu tallafi
Zan cigaba da juya dukiyata ta kasuwanci ita kadai ta wadatar dani , domin banga anfanin inci gaba da wannan mummunar sana'ar ba , alhali jinina tilo namiji dana mallaka na neman ya juyan baya , Adamu na kunyata jiya agaban shushu
Nasani ban masa adalci ba idn har zan cigaba da aikata LAIFIN BOYE , domin tara kazamar dukiya sukuma injefasu cikin bakin ciki
Shureim yasanar dani bayason duk wani abu dana mallaka dominsa , matukar da dukiyan wannan harka nasameshi , kai takaima yana fadin yana kyamatar duk wani abu dana ciyar dashi da wannan dukiya ta kawalci da barna
Adamu to miye riban wannan harka tamu gara mutuba mubi tafarkin tsira , ko yaranmu zasu yafemana mummunan tabon damukai musu, domin wannan kadai ya isa abn gory agaresu "
Nikam tundaga ranan da shushu yaganmu cikin mummunan yanayi, naji natsani wannan fasadi damuke aikatawa , na tsani su minister da duk wasu manyan kasan nan , masu aikata laifuka irin namu zanbar wannan harkan koda zai zama sanadiyar karayar arzikina "
Jikin Alhaji Adam gaba daya yagama yin sanyi, tabbas yasani maganganun aminin nashi sune zallan gsky , yazama dole su tuba domin Allah da kuma kare nutuncin yaransu , duk da cewa sun riga sun musu tabon da bazai goguwa ba, domin komin dadewa sai ankira yaransu da cewa iyayensu kawalai ne mazinata , tir da biyewa son zuciyan dasuka yi abaya "
Sun dade sosai suna tattauna yadda zasu bullowa su minister , domin surabu lfy dasu da kuma yadda zasu gina gidajen marayu , da dukiyan dasuka tara da wannan harka tasu , daga karshe suka watse ko wannan su driver yajashi zuwa gd domin hutawa cikin iyalansa
******
Aneesa basuyi masauki a ko inaba sai akan makeken gadon Rufaida , samfurin Turkish bed wanda yagaji da haduwa
Babu abnd baa zuba na more jin dadin rayuwa cikin bedroom dinba, kaikace dakin wata babbar macece mai miji
Irin kallon datakebin jikin Aneesan dashi yasa Aneesan kokarin saka hijab domin tsokanar Rufin, cikin azama takai hannu ta fisge tana fadin plzz karki rufemin kayan dadina, waishin wani tsari kikaiwa su umma suka barki fitowa da wury haka?
Dariya Aneesa tasa tana fadin"cewa nayi bakida lfy sosai kina kwance nadai tsatstsara umma , ta tambayanmun Abba shinefa yau nasake sanar dashi shikuma harda bani kudin mota "
Takarishe mgn tana dariya sosai kafin daga bisani ta tsuke fuska, damuwace karara ta bayyana afuskanta , kafin tasake dora idanunta akan Rufaida wacce ta shagala akallon dukiyan fulanin Aneesa , wadanda suka cika kirjin taf atsaye suke cak tamkar basushan murza
Kafin tacigaba da fadin"zumata wlh natsani Abba na tsani halayyan sa nason kai da kuma son zuciya
A kullum natuna shine silar jefani a halin danake ciki sainaji natsanesa"
Zuwa lokacin idanunta sunyi ja alamun bacin rai, Rufaida ce tamike ta fice batareda tace komiba , bata jima ba tasake shigowa cikin bedroom din , Rabeca mai aiki tana biye da ita hannunta dauke da katon tray
Wanda aka shakoshi da juices da kayan lashe-lashe, ta dire tareda juyawa byn tamika gaisuwa ga Anee babe
Tana fita Rufaida na kulle bedroom din kafin ta dawo , ta dauki cup din juice mai sanyin gske ta tsiyaya , tamatsa dabda Aneesa ta kai cup din bakinta
Babu musu tashiga shan ruwan juice din sanyinsa naratsa makoshinta , saida tashanyeshi tas sannan Rufaida tasauke cup din
Wani kallo take bin Aneesan dashi gani tayi tasake fresh da kyau , ahnkl takai hannu tazare karamar rigan da batada maraba da babu dake jikin Aneesan,
Nashanunta suka fito muraran hakan yasa Rufaida kai hannunta kansu , ta fara murzasu ahnkl jikinta Aneeysosai tashiga , kafin takai bakinta kunnin Aneesan tana fadin
"Kiyi hakury zumata nasan zafin dakike ji azuciyanki , inaso kisama ranki zaki sami abnd kikeso , kinsan ina kishin wannan jikin plzz kada kiyarda kice zaki mallakawa wani shi ,
Wlh nida ke munrigada munzama bakin rai bakin fama, aurema zan barki sbd cikan burinki nason kidandani dadin namiji ,da kuma son kihaihu amma kisani bazan iya rabuwa dakeba zumata "
Duk wannan mgn da Rufaida keyi hannunta nakan kirjin Aneesa , tana murzasu son ranta kafin Aneesan tafara maida martani cikin kwarewa da sanin kan harkan
Kafin kace me sun tube junansu tareda fadawa wata duniya , ta aikata LAIFIN BOYE wanda dukkaninsu babu wacce iyayenta sukai nasaran gano halin da take ciki , sudai kawai sunsan irin zazzafan soyayyan darayan nasu kewa juna
Sun dauki shawon lokaci suna gamsar da junansu , kafin su sami natsuwa inda Aneesan byn tagama samin natsuwanta , take hawaye sosai wanda narasa dalilin yinshi
Shin natsananin dadine da gamsuwa ? Koko akwai dalilin zubansu ?
To amsar dai nagareni sai kucigaba da bina don jin yazata kaya
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[8:29PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writer's_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*7*
Rufaida ko tana kwance dai-dai ne haihuwar uwarta, wani irin nishadi takeji domin Aneesa tasan kan yadda takeyi tagamsar da ita,
Shiyasa duk cikin yan matan da take tarayya dasu tafisonta, tareda matsanancin kishinta ganin irin hawayen dake ambaliya afuskan Aneey
Yasa Rufaida mikewa tana jan tsaki ta nufi toilet , domin yin wanka don kuwa inda sabo tarigada tasaba ganin Aneesa na wannan kukan
Sai dai basuji dadin juna ba dazaran sun kammala mashaar su xata farah kuka, wanda sam batajin lallashi sai tayi mai isanta sannan take rarrashin kanta,
Ganin Rufaida tashigene yasa Aneesa cigaba da zubda hawayenta masu zafi, hawayan datakeyi tana zubdasune domin takaicin irin laifin datake aikatawa a BOYE, sam wannan harkan tanayinsane bada son ranta ba illah tsabar shaawa datai mata yawa
Wanda Abban ta yaki fahimtar hakan, yazabi kore mata samari tareda dora burin lallai saita hado masa degree, kafin ya aurar da ita wanda ita Aneesa sam ba burinta kenan ba, aure takeso atsarinta tafison tayi aure kafin kammala karatunta, amma fir abban nata yaki
Adalilin hakan yajawo mata fadawa wannan harkan, wanda take ganin shine kadai zai dinga kawar mata da sha'awarta, batareda iyayenta sun farga ba domin tana tsoron fishinsu da kuma aikata zina , amma tasawa zuciyanta dazaran tasami miji dole ne tayi aure
Bakaman Rufaida datayi muguwar nisa aharkan ba, sam bata shawan tayi aure sai dai takan bi maza wadanda sukai mata, kuma sosai samari ke kashe mata dukiya ita kuma tana wadata Aneesa da duk wani abu na jin dadin rayuwa
Fitowan Rufaida ya katse ma Aneesa tunani ta mike da kyar tafada bathroom din ,
Tsayin mintuna ta fito daureda karamin towel iyakacinsa kugunta , kanta sharkaf yake da ruwa kai tsaye inda Rufy take gaban mirrow tana busar da gashinta ta nufa
Wata handrayer Aneey tadauka tareda jonashi awuta , tafara busar dakanta gashi gareta na asalin fulanin domin ummanta fulani ce
Cikin mintuna 15 Aneesa tagama kintsa kanta tas sai qamshi ketashi ajikinta, shiganta tamayar kamar yadda ta fito gaban iyayenta
4:30pm dot suka fito daga room din Rufaida xuwa main parlour na gdn, inda hajiya khairy da bakuwarta ke xaune suna hira
Har kasa Aneesa tagaida bakuwar momy wato hajiya marwa, ta amsa cikin sakin fuska tana jinjina natsuwa irin ta Aneesa
Sallama taiwa momy suka fice zuwa compound din gdn , inda driver ke zaman jiran fitowansu domin maida Aneesa gd
Katon ledane shake da cosmetics xuwa ubansun perfumes, ke jibge ciki jakan hannun Aneesa Rufaida ta amsa tareda zuba mata kudade Wanda bansan adadinsu ba , byn ta mika mata ne tana Mirza yatsun hannunta take dadi
"My surgar sainazo ki kularmin da kanki plxx , "
Wani kallo na shaidanci Aneey ta aimata kafin ta furta angama Bakin rai
Driver yaja motar suka bar haraban gdn , yayinda Rufaida ta juya tanajin kewan Aneesa sosai cikin xuciya da gangar jikinta
******
Shureim shu'aib Abba aji ne ke tuki ahnkl cikin gwanancewa, tasowansa daga office kenan yana hanyan komawa gd ne, agajiye yake liss amma hakan bai hanashi biyawa, ya jido ice cream da meatbag ba domin yasan yana isa gd yusrah zata ce ina tsaraba
Koda ya iso gd kai tsaye part dinsa ya nufa domin watsa ruwa, byn yafito yasake shiryawa cikin bakin wandon jeans da shirt fara mai ratsin sky blue , yayi kyau matuka gashin nan akwance luff
Roba 2 na ice cream yasaka a frige dinsa , kafin ya kwashi sauran da meat bag din yayi part din momy
Yusrah da Aysha ne zaune sunata hira ana kwasan dariya , Ayshat na sanye cikin riga da skat na swiss boyel, sosai dinkin ya amshi jikinta tareda fito kyawunta, dan kwalin kanta yazame hakan yasa kake ganin jelan kananan calaban dake kanta na kwance abayanta
Hajiya kubrah sam hnkln ta nskan TV tana kallo , sallaman shushu da kuma azababben qamshinsa ya sanar dasu shigowan sa cikin parlon
Momy ce ta amsa sallaman tna fadin my son harka dawo, karisawa kusada ita yayi yana fadin momy nadawo
Jikawai yayi anrungumesa ta baya yana kokarin zama, yusrah ce kefadin oyoyo ya shushu , hannu yasa ya dungureta yana fadin my baby doll kedai bakya girmako ,
Dariya tayi sosai tana fadin sorry ya shureim ganin ledan hannunka ne naji gaba daya yawuna ya ya tsunke
Murmushi yayi yasakar mata ledan yana fadin"gashinan saiki je kitasha ai "
Momy dai nasauraransu bata tankaba, Ayshat ko idanu ta zuba musu ta dade sosai bata sanya shushun a idanunta ba, kasancewar bawai tafaye xuwa gdn bane tunda yusy ta tafi karatu
Shikuma bamai xaman part din momy bane sosai , koka xo balallai ko yana gdn kaganshi ba shiyasa tadade bata Gandhi ba saidai taji suna waya da yayanta salman
Sosai taga yasake wani mugun kyau da fresh , ita aduniya shureim yana birgeta, ahnkl cikin muryanta mai sanyi da dadin amo take gaidashi
"Ya shureim ina yini "
Sai da ya kalli side din kafin ya ansa gaisuwan fuskansa ba yabo ba fallasa, shisam bai kula da itama cikin parlon ba saida ta gaidashi
Daga haka bai sake kallonta ba ya fuskanci momy suna ngn, yusrah ta dauki ledan ice cream din suka wuce xuwa bedroom dinta
Karfe 7pm ana magrib driver yazo daukan Ayshat , har gurin mota yusrah tarakata da katuwar leda mai dauke da tsaraba
Koda dare tayi aka hadu domin yin dinner shushu kin shigowa yayi, sai yusrah ce takai masa part dinsa,
Tundaga ranan shureim ya canza gaba daya yadaina cin abnci tareda su apart din momy kaman yadda aka saba matukar dady yana gari , gaisuwa kadai kehadasu da dadyn shima ba cikin sakin fuska ba
Sam irin zaman hiran dasuke da dadyn yana shagwaba, suna tattauna abnd yashafesu ya janyeshi, sam daga gaisuwa shikenan zai tashi ya fice
Idn kaga shureim yasaki face to da momy ne ko yusrah, hakan bakaramin cin zuciyan dadyn yake ba
Yau takama weekend saty 2 kenan da faruwan abnd shushu yaga iyayen nasa na aikatawa,
Misalin karfe 10am shureim ya fito daga part dinsa , yana sanye cikin rigada wando na da'nyar gezna kalan sky blue , sosai yayi masifar kyau cikin kayan kasncewan sa mai farin fata , sai dai farinsa ba irin tau dinnan bane fresh ne sosai
Shureim yakaiduk wani level dazaa lissfashi cikin jerin kyawawan maza, dasukanyi karancin samu ya hadu takowani fanni,
Kaduna yake shirin xuwa inda zai shafe tsawon 1 week , yana gudanar da wani aiki da aka turashi a branch din dake nan kd
Da sallama ya shiga part din momy saidai falon tsit yake, yana kokaryn zama momy na fitowa daga part din dady
Hakan yasashi karisawa tareda rungume ta yana gaidata, itama rungumeshi tayi tana fadin kai my son wannan wanka haka, kodai surukar tasamu ne ?
Sosai ya shagwabe fuska yana fadin "kai momy kinfaye zolaya nikam bansami kowaba, ni sam haryau banga yarinyar data kwantamin ba, inajin dai saikin zabomin mata donni nagaza samu"
Murmushine ya kwace a fuskan momy cikin matukar farin ciki take fadin , da gske kakeyi my son kai amma naji dadi zanko yima zabin dazakai alfary dshi shushu,
Shureim ganin farin ciki kwance fuskan momy hakan yasa yaji , lallai awannan karon dole yayi hakury yabata dama domin cikan burin ta nataga yayi aure, zai zauna da duk zabinda zatayimai domin yasan bazata taba zabamai abnd zai cutar dashi ba
Alhaji shu'aib ne ya fito daga part dinsa yana gyara babban rigarsa da alamu fita zaiyi shima,
Yaji duk abnd su momyn ke tattaunawa da shushun, hakan yasa cikin fara'a yakariso cikin falon yana fadin kubrah keda dan lelen nakine kuke zantawa,?
Cikin farin ciki take kokaryn yimasa bayanin abnd suke mgn akai , ya dakatar da ita ga fadin naji duk abnd kuka tattauna kubrah Allah yai zabi nagari
Shureim wanda tun fitowan dady ya tsuke fuskan sa tamkar bai taba dariyaba, batareda yabari idanunsu sun hadu ba ya furta "gud morning dady "
dadyn ya amsa da "morning my son sai ina naga ansha wanka haka"
Shushu yasaci kallonsa kadan kafin ya furta , "kd zani dady akwai aikin dazan gudanar na saty guda "
Alhaji shu'aib ya dubesa yana fadin"to Allah yabada nasara idn kadawo inaso mu tattauna muhimmiyar mgn dakai son "
Shushu ya amsa da to dady saina dawo din, yusrah ce tasakko daga stairs tagama hadewa cikin bubu na wani lace mai azabar kyau , tayi kyau harta gaji qamshi kawai kefita ajikinta
Bata dubi kowaba saida ta isa ga dady tashige jikinsa , rungumeta yayi yana fadin autan dady anfito , cikin shagwaba take fadin
"Eh dady shushu taduba tana fadin ya shushu gud morning tun 9nake jiran shigowanka kaki tashi dawury yauko, takarishe mgn tana shagwaba "
Shureim ya sakar mata murmushi yana fadin dubeta batasan ta girmaba, wai mantawa kike yanzu kinzama big gal ne degree fa gareki ba yar primary kikeba , kike wannan sangarta baby doll
Dady ne yace babu dai ruwanka da auta kaima naga haryanxu bawai kagirma da shagwabar bane,
Ganin dady na neman samin kafan jansa da hiran da suka dade basuyi ba, yasa shureim yimusu sallama domin tafiya
Tafiyan 1hour da mintuna 40 yakai shushu garin na gwanma , kai tsaye a hotel yayi masauki sai da yahuta yai wanka yasauya kaya , sannan yafito domin zaga gari
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[5:50PM, 3/22/2018] 閳ワ拷+233 50 348 1936閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*8*
Bayan kwana biyu da zuwan shureim kaduna, misalin 4 na yamma tasowan sa daga office dinsu kenan, yayi wasu interview tuki yakeyi ahnkl ksancewan yagaji
Hanyan dazai kaishi Mangal plaza yadauka, domin yanason siyan cable na iphone ya manta nashi a Abuja
Parking dinsa kenan ya fito daga cikin motan , yana kokaryn shiga sukuma suna kokaryn fitowa
'Yan matane su biyu kyawawan gaske daya nasanye cikin after dress tasha rolling, takalmi ne mai tudu akafarta yayinda ta rufe face din da katon bakin eyes glass
Dayan nasanye cikin wani hadadden laces riga da skat , kafanta sanye da bakin safa yayinda jikinta ke rufe da hijab wanda tsayinsa ya wuce guiwarta kadan, fuskanta sanye da farin eyes glass wanda yai matukar yimata kyau ba kadan ba
Tunda shushu yasauke idanunsa akan wannan matashiyar budurwan yaji, wani abu wanda vaisan komiyeba ya tsirga mishi a kahon zuci, da karfi bugun zuciyansa ya karu idanunsa kyam akansu , har suka kawo dabdashi suna kokarin wucesa, sam su basuma kula da shiba hnkln su kwance suke kokaryn wucesa
Hakan yasa shureim sauke wata Irin ajiyan xuciya, byn sun nufi wata katuwar mota suna kokaryn shiga back seat,
Karfin hali hali yayi yaja kafafunsa domin xuwa garesu , don abnd zuciyansa ke tunzurasa kenan
Aneesa takai hannu domin rufe kofan motar saiji tayi anrike murfin motan, tunkan takaiga mgn wani fitinannen qamshine yacika hancinta
Leko da kanta tayi domin ganin wani mai karanbanin ne wannan, idanuwanta ne sukayi arba da hadadde kuma kyakykyawan matashin saurayin
Rass taji gabanta yayi mummunan fadi bata taba cin karo da handsome guy irin wannan dake tsaye gabanta ba
Sai dai cikin karfin hali idanunta akansa tamkar yadda shima idonsa ke kanta, tayi mgn cikin muryanta mai matukar taushi da dadin amoh take fadin
"Mallam lfy yada haka? zakazo ka kama kofarmota ka rike "
Murmushin dabaisan sadda yasubuce aface dinsaba yasakar mata, kafin yafurta "uhumm 'yan mata sorry ko don Allah inba damuwa inason ganin 2 minit plxx"
Rufaida data fara kosawa Aneesa taduba kafin tamaida dubanta ga shureim tana fadin"kana iya tambayan aminiya idn tabaka dama babu damuwa"
Rufaida ce takatse Aneesa da fadin "plxx baby fita kisallamesa mu wuce sam Rufaida batama tsaya kallon shushun ba idanunta nakan wayan hannunta , datake chart da saurayinta salman Adam
Ahnkl ta fito daga cikin motar ta jingina jikinta, kafin ta saci kallon sa wanda idanunsa nakanta
Shureim yafara da fadin" sunana shureim ni mazaunin garin Abujane , Nazo gudanar da wani aikine anan garin, shigowata kenan na hango ku mgn gsky farat daya naji kin birgeni , abnd ban tabaji akan wata 'ya maceba hakan yasa nayi karfin halin isowa gareki inba damuwa inaso kibani Phone number dinki, naga alama saury kuke karna bata muku lokaci"
Aneesa gaba daya jinta take cikin wani yanayi , shushu yagama tafiya da zuciyanta farat daya , mgn sa ma kadai bakaramin sake kashe jikinta yayi ba , ba musu tashiga karanto masa digit dinta yana sawa cikin phone dinsa
Saida ya kammala yasake kallonta yana fadin"to malamar bata fadamin sunan ta ba "
Saida tasaki murmushi wanda har dimple dinta suka lob'a , kafin tafurta "kayi saving da Aneesah "
Aneesahh yaja sunan kafin ya furta nice name , saikin jini zuwa anjima baijira jin komiva yayi gaba abnsa,ya barta da shakan fitinannan qamshinsa, sai bin byn sa tayi da kallo tana yaba class dinsa , uwa uba kyau da muryansa mai matukar dadi take sake jiyo amonsu cikin kunnuwanta, kiran sunanta da yayi kuwa jitayi duk duniya babu wanda ya iya fadin tamkar shushu
Koda tashiga mota Rufaida tacika tayi fam, cikin masifa take watsa mata wani irin kallo, kafin ta furta" zumata wai waye wannan da kika tsaya saurara haka ? "
Aneesa tadubeta tana kashe mata idanu take fadin"Bakin rai wlh wani handsome guy ne nayi kamu, nikam fitowanmu tayau tabiyani don gsky farat daya naji gayen yayimin"
Wani irin kallo Rufaida kebinta dashi yayinda zuciyanta ya buga da karfi, me Aneesa ke nufi da hakan ? tabbas tanaso tajanyo wa kanta, don sam bata kaunar ranan da zataji Aneey ta furta kalman so gawani da namiji, domin hakan na nuni da barazanan cewa zatayi aure wanda bata fatan hakan, tafiso su dawwama ahaka suna sheke ayarsu , kaji son kai dai irin na Rufaida hmm
Batace da ita komiba driver yaja motar suka fice daga plaza din , kai tsaye gdn su Rufaidan suka yada zango ,
Yauma kaman koyaushe swida suka murji juna sosai, kafin su sami natsuwa Aneesa na kwance akan kirjin Rufaida , yauma kuka takeyi tamkar koda yaushe hawaye nasauka bisa kirjin Rufaida
Ahnkl Rufi tasa hannunta tana murza kirjin Aneesa , daya hannun na lalubarta ta kasa muryanta adishe yake , alamun tana son kary amma sai dai Aneesan ne tajanye jikinta , murya can kasa take fadin My surgar plzz stop it marata ciwo take , kinsan karshen month yayi period na keson zuwa
Rufy sam bata saurara mata ba saida suka sake aikata tsiyarsu , domin jarababbun matane ajin karshe
Rufaida ta mike tafada tiolet domin gyara jinkinta , yayinda Aneesa tacigaba da hasko fuskan shushu na mata yawo , duk ta kosa tasake sauraron voice dinsa mai matukar dadi
Koda ta gyara jikinta bata dauki dogon lokaci ba ta bukaci wucewa gd , domin tasan halin Abba idn yadawo bai sameta a gdn ba, dama kuma donyayi asubancin zuwa zaria ne hartasamu da kyar umma tabata daman fitowa daga gdn
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[5:50PM, 3/22/2018] 閳ワ拷+233 50 348 1936閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writer's_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*9*
Hajiya kubrah ce zaune itada yusrah , sun baje uban kaya tundaga kan handbags takalma zuwa fashions jewelries , hadaddun gske wanda aka turo mata Daga kasar China
Yusrah ke zaban set guda akowanne ciki tana yin gefe guda dashi , zuwa can tadubi hajiya kubrah tana fadin momy waini kam yaushe , zaki bude plaza ne domin kasuwancin nan yakarbeki Sosai
Hajiya kubrah tayi murmushi tana fadin"wlh auta abnd nake bury kenan bary shushu yadawo ayi shawarah, domin ko dady surprise zamuyi masa sai abn yatabbata zaiji lbry
Wasu hadaddun hand bags da takalma , momy taware su wanda kudinsu zaikai 50k , ta dubi yusrah tana fadin auta aje wannan tareda naki na Aysha ne
Yusrah ta janyesu tana fadin"lallai Ayshat takice momy nasan zataji dadi sosai da wannan kyautan"
Masu aikin hajiya kubrah ne ke kwashe kayan zuwa wani daki na daban, kafin zuwa anjima afara zuwa duba kayan, sosai take ciniki matan manya da student rabi kuma tasararwa 'yan kasuwa
Yusrah ma nata dana Ayshat ta kwasa zuwa upstairs , koda ta sakko momyn nazaune wannan lokacin waya takeyi , tana sanar da aminanta kaya sun iso
Koda tagama wayan kallon yusrah dake faman latsa waya tayi, tana fadin"yusy kinsan abnd nake shiryawa araina kuwa gameda shushu?
Yusrah ta aje wayan hannunta tana fadin"saikin fadi momy me kike shiryawa big brother din nawa ne"
Momy take fadin"dazu nakemai mgn aure shine yace yabani zabi , duk wacce naga tadace dashi zai amshe ta hannu biyu, to nikam gsky babu yarinyar danake ganin tadace da shureim sai Aysha,
Aysha itace yarinyar da takwanta min arai nadade ina shaawar shureim ya aureta, inadai kauda kaine sbd banaso insashi ya aury abnd bashida raayi , da kuma ganin sam bayama shiga sabganta
Amma tunda yabani dama ayanzu to itace yarinyar dana zaba mai tazama abokiyar rayuwansa"
Yusrah wani ihun murna tasaki tana fadin gsky momy kinyi tunani mai kyau, Aysha tanada nutsuwa da kuma kamun kai ga ilimin addini daidai gwargwado tasan abnd takeyi, zakuma sudace da juna"
Gasky momy nayi farin ciki dama ya shushu yadade yana birge Aysha, nasani tana sonshi kawai dai kunya da zurfin cikin tane yasa takasa bayyana hakan
Sosai momy taji dadin mgn da yusrah tayi , tareda jin kwaryn guiwan dazata tinkary hajiya safiya da mgn , domin sam bataso a aje lokaci sbd gudun kar shushun yasauya mgn
*********
Washegaryn ranan hajiya kubrah da kuma yusrah suka isa gdn , aminin mijin nata wato Alhaji Adam, rungume juna sukayi tsakanin momy da kuma hajiya safeeya , wadanda suke aminan junane,
Aysha da yusrah sukai masauki adakin Ayshan, cikin murnan wannan ziyara da suka kawo ,Aysha nasanye cikin wandon jeans daya fito da hips dinta , sai karamar top data kamata tareda fito da surar kirjinta dake cikeda dukiyar fulani, kasan cewan garin da zafi shiyasa sanyin Air condition yacika dakin ta ko'ina,
Yusrah ce take fadin shegiya Ayshat kinga yadda kike sake cikane , kinyi wani kiba sbd angama skul sai zaman hutawa ko, kafin musha biki mukaiki dakin miji
Aysha takai mata duka tana fadin wlh yusy bakida kyau , nikam ban shirya aureba hasalima bani sauraren kowa, mutum daya nakeso amma sam baimasan ina dakon sonsaba, nakuma san dawuya insamesa yusy , zancigaba da dakon sonsa domin banaji zan iya cire sonsa araina ,
Tuni har idanunta sun canza launi , yusrah ta dafa kafadunta tana fadin"miye abn damuwa Ayshat shiko wannan waye daya sami babban gurbi axuciyanki haka "?
Any way ko waye kiyi addua kawai idn har rabonkine zaki sameshi cikin ruwan sanyi
Amma zanso inji wanene wannan wanda kika mato kansa haka
Aysha ta jinjina kai tana fadin"hmm hakane yusrah shiyasa addua kadai narike inayi , batareda na fallasawa kowa sirrin dake raina ba"
Plxx kuyi maneji da wannan ina busy ne , zakujini soon insha Allah , tnx 4 d luv and support 棣冩
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[5:50PM, 3/22/2018] 閳ワ拷+233 50 348 1936閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*10*
Hajiya safeeya da hajiya kubrah ne zaune cikin bedroom din ummah hajiya safeeyan,
Momy ta dubi hajiya safeeyan tana fadin"umman Aysha wato wata muhimmiyar mgn nakeso mutattauna , daga haka takwashe yadda sukayi da shushu tafadama hajiya safeeyan,
Ta kare mgn tana fadin shiyasa nataso domin mutattauna, sbd nina yanke shawaran muhada Aysha da shureim , domin dorewan zumuncin mu nayaba da nutsuwan Aysha , amma ki tattauna da ita idn har bata da raayinsa, bazamuyi mata doleba"
Hajiya safeeyan wacce farin ciki ya lullube ta ke fadin"karki damu momyn yusy wannan abune mai sauki nikaina nadade ina tunanin hakan, amma kinsan halin yaran zamni bakasafai suke yadda da hade hade ba, amma tunda shiyabada xabin anemamai, zanyi mgn da Ayshat abnd mukayi zakiji feedback ayau da dare basai gobe ba"
Koda su momy suka tashi tafiya gurin mota Aysha tarakasu, tanata godia akan kayan da momyn ta kawo mata,
*******
Aneesa kwance tayi ale-ale akan bed dinta chart takeyi itada Rufaida , da sauran friends dinta sai dai gabaki daya hnkln ta da tunaninta nakan shureim
Sauraren kiran shushu kawai takeyi amma taji shiru, daga kanta tayi tana sake kallon agogo karfe 10 harda kusan rabi,
Kashe data tayi ta jefar da wayan kan bed din, tarasa meyasa shushu yayi karan tsaye cikin zuciyanta farat daya, bata taba haduwa da saurayin dayayi saurin sace xuciyanta irin shureim ba
Tayi samary da dama abaya wadanda tasosu amma sam , bata tabajin abnd takeji akansu yadda takeji akan shushun ba,
Karan wayanta ne yakatse tunaninta cikin hanzari tadaga wayan , byn tasake narke murya tayi sallama
Daga bangaren shushu wanda ke kwance bisa makaken bed din dake dakin hotel din daya sauka, jin muryanta kawai dayayi yasa shi sake gyara kwanciyan shi kafin ya amsa sallaman da fadin
"Wa'alaikumussalam pretty malama Aneesah kinji ni shiru , sorry ayyukane sukasha kaina sai yanxu nasami lokaci, Allah dai yasa ban katse ma malamar bacci ba"
Aneesa wacce tayi lamo tana sauraren muryan shushun, wanda yake saukar mata da wani irin kasala , ta amsa da fadin"no baka katsemin bacci ba dafatan kana lfy "
Shureim ya amsa da fadin"lfy nake Aneey sai dai kinmin wata irin sata wacce baa taba yimin irin ta ba"
Aneesa tazaro idanu tamkar shushu naganinta , kafin tashagwabe murya tareda sake narke muryan take fadin"sata kuma shureim wani iri kenan? "
Dakyar ya saita kansa domin kuwa yaji wannan shagwabar ta Aneey har cikin gangar jikin sa,
Cikin karfin hali yayi mgn yana fadin "satan zuciyata kikai Aneesa bada wasaba kinyi nasaran sace zuciyata farat daya,
Abnd bantabaji akan kowace mace ba , gsky Aneesa nafada tarkon sonki , wanda nakeji idn har bansameki amatsayin mata ba , bani da sauran nutsuwa ina fata wani baiyi nasaran sace hrt dinki ba?
Ya karishe mgn cike da karyewan zuciya "
Aneesa wacce kejin wani farin ciki wanda tadade bataji irin shi ba, cikin muryanta mai dadi tasake narkesa sosai kafin ta furta, "babu wanda ya sace zuciyan shureim , kuma ina maka albishir da cewa Aneesa takamu da soonka tamkar yadda ka kamu da nata , "
Wani dadine ya ziyarci zuciyan shushu tareda wani nishadi , cikin dansa yake fadin dama haka so yake , gasky bai taba tsintan kansa cikin yanayin dayakejin zuciyansa ayanxu ba
Sosai hira ya tsinke tsakaninsu Rabin hiran Aneey ce ke kirkiransa, domin shushu rasa abnd cewa yake abnka dafarin shiga wanda baisan kan soyayya ba, sun dade suna musayn muryoyinsu tsakanin juna
Sunajin nishadi nadaban atattare dasu har xuwa 11 nadare kafin suyi sallama, ko wannan su najinsa cikin farin ciki mara misaltuwa
Wanda shureim baccin sa na ranan gaba daya yayisane cikeda mafarkin ya mallaki Aneesan
****
Hajiya safeeya ce tareda Aysha cikin bedroom din umman , kafin ta dubi Ayshat din tana fadin"shatu kisaurareni mgn muhimmiya ce zamuyi dake
Dazu momyn shushu tazomin da mgn son ayi hadin zumunci tsakaninki da shureim din, tazabeki amatsayin kizama suruka agareta, banaso ki cuci kanki ko kiyi kawaici akan abnd bakida raayi akai
Hakan yasa mukace saimunji ta bakinki kafin muyanke shawara, domin shushu shiyaba momyn sa dama tazabamai mata , hakan yasa itakuma tazabeki bisa yaba nutsuwa da hnklnki
Don haka idn kinada wanda kikeso karki boyemin komi kisanar dani , ni uwace bazan so kitauye farin cikin ki domin cikar burin wani ba, momy wayayyan macece wacce zata fahimceki "
Jikin Aysha ne yayi sanyi yayinda takejin wani farin ciki na ziyartan zuciyanta, tabbas shureim shine kadai namijin datakejin sonsa har cikin jininta, shine namijin datakejin bazata iya yakiceshi cikin ranta ba, sai dai tana boyewane sbd hakan shine rufin asirinta ,
Sai dai ayanxu datake sauraren ummanta jitayi tsohon mikin sonsa datake dannewa yataso gabaki daya
Cikin karfin hali ta dago tadubi umman kafin tafara mgn ahnkl tana fadin
"Umma nikam banida wani wanda natsayar inaso , don haka duk hukunci da kuka yanke zan amsheshi hannu biyu, domin nasan bazaku taba yanke hukuncin abnd zai cutar dani ba
Sai dai fatan Allah yasa shidin yakarbeni amatsayin zabin momyn, takarishe mgn ahnkl tana hawaye , wanda azahiri na farin cikin xata mallaki abnd zuciyanta kesone, duk da batasan shi shureim din ko aya zai karbeta ba idn yaji itace zabin momy
Sai dai tanaji koma aya zai karbeta zata zauna dashi, tacigaba daraya sonsa cikin zuciyanta koda ko shi zai nuna rashin so agareta
Hannu taji na ummanta bisa kafadunta tana fadin" yawwa Aysha Allah yai miki albarka kuma ina mai tabbatar miki bazakiyi nadamn auren shureim ba, domin shushu yaron kirkine wanda zamuyi alfari idn wannan abu yatabbata
Tashi kije zanyi mgn da hajiya kubrah infada mata yadda mukayi , Allah yai mana zabi na alkhairy kinji ko
Ameen Aysha ta furta tana ficewa daga bed room din momyn zuwa nata, gado tafada tana sauke ajiyan zuciya mai dadin gaske
Ahnkl ta lalubo wayanta tareda zakulo pic din shushun , wanda awayar yusrah tatura batareda ita yusyn tasani ba
Yayi masifar kyau a pic din wwnda yadaukeshi awani hadaddan gurin shak'atawa a garin Miami dake kasar America, yayi kyau harya gaji shafa pic din takeyi da hannuwanta yayinda , takejin soyayyan shureim Abba Aji nasake bin jinin jikinta
Ta dauki lokaci mai tsawon gske kafin bacci yai nasaran saceta ,cikeda mafarkai barkatai duk na shushun
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[5:51PM, 3/22/2018] 閳ワ拷+233 50 348 1936閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*11*
Hajiya safeeya bata sami kiran hajiya kubrah ba, sai washegary byn sun tattauna mgn da Alhaji Adam, wanda haryaso yafita farin ciki dajin wannan tunani dasukayi , nason hada auren tilon yar sa mace Aysha
Da shureim wanda zaiyi matukar alfary da hakan ,domin yasan waye shushu yasan Irin nutsuwan da kamun kansa, yanajin Allah yasa shi shushun ya amince idn yaji wacece zabin momyn tasa
Coz shi kanshi shaidane akan cewa ayanxu babu wanda shushu yake ganin bakinsu , tamkar shida mahaifinsa sai dai Alhaji Adam yadanne damuwansa yayi fatan alkhairy
Koda hajiya safeeya tasnar da momy yadda sukayi da Aysha, bakaramin farin ciki tayiba fatanta shushu yadawo agabatar da baiko batare da wani jinkiri ba,
Karfe 10 nadare hajiya kubrah ce sanye cikin nighties masu azaban kyau , irin nasu na manyan mata sosai take zabga qamshi mai matukar saukar ma mai shakansa da nutsuwa
Bedroom din Alhaji shu'aib aji ta tura tashige, wanda tasameshi kwance bisa gado , gefenshi cup ne daya shanye ruwan ganyen shayi na green tea , wanda tagabatar mai kafin ta tayi kintso kanta
Kusada shi taje takwanta kafadunsu na gugan najuna, qamshin daya shaqa nata ne yasashi sake shigewa jikinta
Ahnkl take furta "dadyn yusy mgn nakeso muyi gameda hadin auren shushu da Aysha , "
Tashi yayi zaune kaman yadda momyn itama tazauna , saidai haryanzu jikinsu nahade dana junane ,
Kallonta yayi kafin ya furta "Aysha yarinyar Adam kike nufi wai? "
Gyada kai tayi tana fadin"kwarai kuwa itace yarinyar dana zabamai domin zasu dace da juna, kuma zumuncin mu zaifi dorewa yana naga kaman fuskar ka tanuna akamun damuwa? "
Dady wanda yai kokaryn boye damuwansa ya zakulo murmushi , yana fadin"haba momyn yusy kema kinsan saina fi kowa farin ciki , kawai dai muyi fatan zabin yaiwa shi shureim din , kinsan bazan Goya baya ayimai abnd baida raayi ba
Duk da cewa shiyabada goyan baya ayimai zabin daya dace dashi, Allah yashige gaba yatabbatar da alkhairy"
Momy ta amsa da ameen karka damu ninasan shushu bazai taba bani kunyaba, kuma kai shaidane kullum yana mana biyayya, kuma Aysha natsatstsace wacce zaiyi alfari da aurenta , ahnkl zasu so junansu insha Allah "
Daganan suka cigaba da tattaunawa akan yadda komi zaitafi batare da anbata lokaciba
********
Bada bata lokaciba soyayya mai karfi ta kullu tsakanin shushu da Aneesa, wacce takejin ayanxu xata iya batawa da duk wani wanda zai mata shamaki da mallakan shureim
Tundaga randa suka fara waya akalla kullum sai shushu yakirata fin sau 5 arana, da dare kuma zasu dauki dogon lokaci suna chart , ana musayan kalaman soyayya mai tsafta
Gaba daya shushu yagama sallamawa yayi dace da irin macen daya dade yana mafarkin mallaka, domin Aneesa bata taba anfani da wata kalma da zai nuna mai itadin tanada wani aibu ba,
Saima nunamai datake itadin fa cikakkar mai kamun kaice , Sbd Aneesa daidai gwargwado anbata ilimin addini mai zurfi , hakan yasa Abba ke ganin bazata iya aikata wani abn ashsha ba,
Yau yakama 1 week da xuwan shureim kd kenan, kuma ayau din yake son wucewa Abuja hakan yasa tun safe yashaidawa Aneesa yanaso su gana kafin yawuce
Domin bazai iya wucewa baiyi tozali da itaba , duk da cewa kullum cikin turamasa pics take , amma sam bata yarda tayi pic din dazaiga aibunsa
Tunda shureim yasanar da Aneey zancen zuwansa gdn su , hnkln ta yai kololuwa gurin tashi domin tasan , kotasha giyan wake ne bazaa barta fita ba bare tayi dabaran kaishi gdn su Rufy
Kwance take akan bed tarasa wani dabarace zatayi , wanda zaisa abarta tafita domin bataji zata iya sabawa shushu kota bata ransa
Muryan Abbanta ne yakatse tunaninta yana kwalla mata kira , cikin hanzari ta yo waje zuwa parlo inda takejin amon muryansa
Tsaye tasameshi cikin shirin fita yaci babbar riga , rusunawa tayi tana fadin gani Abba
Kallonta yayi yana fadin "Aneesa inaso karfe 6 ku shirya abncin da mutum 5 zasuci , keda mai aiki kuyi komi akan tsari zani zaria indawo , ban amince kifita ko ina ba inafatan kingane tashi kije "
Aneesa ta amsa da cewa "to Abbas adawo lfy "
Ameen ya amsa yana binta da kallo yayinda sonta ke karuwa azuciyansa, yanason Aneesa sosai tareda yaba hnklnta da nutsuwan dayake gani tattare da ita , sbd baisan tana aikata *LAIFIN BOYE* ba
Shigewa tayi bedroom dinta tabarshi da umman ta , bata wani jimaba tasake fitowa byn taji tashin motansa alamun yafita
Dakin ummanta ta nufa wacce tasameta tana sake saka turaren wuta abedroom din nata, qamshi kawai ketashi bakin gadon tazauna tana zare idanu
Umma tadubeta tana fadin "Aneesa lfy daiko ? "
Neesa tadubi ummanta tana fdin "wlh umma wani alfarma nazo nema dama wani sabon saurayi nayi , to shine yau yakeson xuwa musake ganawa sbd Abuja yake , aiki ya kawoshi nan kd nan dai takwashe komi gameda shureim tasanar da ummanta
Wanda takarishe mgn tana fadin " wlh umma shureim natsatstsan mutum ne kuma dagske sona yake da aure, kuma nima nakamu da sonsa wlh Allah ummah
Ke mahaifiyace agareni bazan iya boye miki komiba, kibani goyan baya na saurari shureim domin wlh umma ayanxu aure shine cikar bury na
Kuma bantavaji na kamu dason wani namiji kaman yadda nakejin shushu araina ba, Amma nasani idn Abba yaji koransa xaiyi kaman yadda yashayi abaya
Narasa meya Abba ke koremin samary, ayanxu nsgama degree wlh aure nakeso umma , kitaimakeni awannan karon kinunawa Abba cewa aurene araina ba boko ba"
Umma kiyi hakury dani domin Abba yafara kaini bango , har inajin nafara jin tsanansa akan son zuciyansa dayakebi yana neman tauye rayuwata
Wlh umma natsani Abba domin nikadai nasan irin halin daya jefani ciki asanadin son zuciyan.....
Batakare mgn taba taji saukan wani lafiyayyen mary akan fuskanta, wanda yasa ganinta yadauke na wucin gadi kafin cikin fada umman tafara fadin
"Aneesa kina haukane mahaifinki kike fadin kin tsanesa, shikike fadiwa munanan kalamai irin haka? , tobari kiji kiyi gaggawan saita bakinki ko intsinke harshen ki , sha sha sha kawai insake jin irin wadannan kalaman nafita abakinki"
Aneesa durkushe wa tayi kan bed din tana kuka sosai, tasani umma bazata taba fahimtar metakeji cikin zuciya da gangar jikinta ba, bazata taba gane illan da son zuciyan Abba yajefa rayuwanta ba, sbd bata fito da *LAIFIN BOYE* fili ba, tabbas wannan karon dole tabijire wa Abba matukar bazai bata goyan baya akan shushu ba
Bazata taba dora wani masters dayake bury ba, aure takeso ba karatu ba , tagaji da aikata **LAIFIN BOYE* duk adalilin son zuciyansa
Idanunta tasauke masu zubar hawaye akan ummanta, wacce take kallonta wannan karon jikinta yayi sanyi ganin yadda Aneesa ke kuka sosai
Tabbas tasani Aneesa takai munzilin dazata bukaci aure, kuma daidai gargwado tayi biyayya gurin cika burin Abba nasamin ilimin boko mai zurfi
Ita kanta tafi shaawar Aneesa tayi aure amma Abba yakauda kai
Aneesa ahnkl taje kusada umma takwantar dakanta akan cinyarta, har zuwa lokacin kuka take tana fadin"umma kiyi hakury nadaina wlh zuciyata ne ke matukar zafi , nasanar dake gskyn abnd ke raina ne sbd hakury na yakare awannan karon "
Inason shureim shima yanasona umma kibani goyan baya nasaurari mutumin dayazo da niyyan aure gareni , plzz umma kiji tausayina kinji takarishe mgn cikin karyewan zuciya"
Jikin umma gaba daya yagama yin sanyi tausayin d'iyanta yakarya zuciyanta, ahnkl take patting bayanta tana fadin"na fahimceki Aneesa awannan karon nima bazan goyi bayan son ran abbanki ba, tunda har kika furta aure kikeso to shizakiyi da izinin Allah , nabaki dama yazo kugana kafin yawuce inyaso nida kaina zantinkary Abba da mgn "
Ki kwantar da hnklnki kiyi ta addua kinji maza tashi kije kisama masa abnd zaici , kafin ya iso amma kiyi komi cikin lokaci banaso abbanki yadawo yafahimci wani abu
Kina sane kuma da umurnin sa don haka kiyi hanzari "
Cikin murna sosai Aneesa ta tashi tana ma ummah godia , kafin tafice tana share ragowan hawayen fuskanta
Umma tabita da kallo yayinda tausayi da tsoro yadarsu cikin ranta, tabbas tunda har Aneesa ta iya furta wadannan kalaman, yazama dole sumata auren don gudun abnd zaije yadwo , sai yau take sake Allah wadai dason xuciya irin na abban Aneesa
Yaushe awannan zamanin 'yar ka zata nuna son aure , kai kuma kadage saitayi boko sosai takejin lallai wannan karon dole tagoyi byn Aneesa , bazata amince dawani batuba inbana ya aurar mata da d'iyaba
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*12*
Aneesa ce ke kaikawo tsakan dakin da Abba ke sauke baki da kuma kitchen , tana shirya abncin datayi don tarban shureim Aji
Tasha wanka tashirya kanta cikin hadadden after dreess mai azaban kyau da tsada, Rufy tasai musu atafiyar datayi kasar Dubai, tasha light makeup a faces dinta, tareda yin rolling akanta sai tashin fitinannen qamshi kakeji ajikinta
Saida taga komi yayi yadda takeso ta koma cikin gd , kaman jira ake tana shiga room dinta wayanta na tsuwwa, shushun natane ke kira hakan yasa ta dauki wayan cikin kashe murya
Sanar da ita yayi gashi nan awaje hakan yasa tana rike da wayan , take xira flat shoe dinta tayi waje , karo sukaci da ummanta dake kokaryn shigowa dakin, hakan yasa Neesa kashe wayan tana duban umma take fadin "sorry umma ga shureim nan ya iso zan shigo dashi "
Umma tabita da kallo tana fadin"to maza shigo dashi "
Aneesa tafice tana takunta cikin nutsuwa da yauki, umma tabita da kallo aranta take fadin lallai da gske Aneesa tna qaunar shureim
Domin bata taba ganin d'iyartata na irin wannan rawan jikin akan namiji ba
Bakar mota tahango ta parka hakan yabata tabbacin shushu ne, tana kokarin dialing number dinsa sai gani tayi ya fito,
Yana tunkarota sake karemai kallo take tundaga sama har kasa, ayau sai sake gani tayi yayi mata kyauma fiyeda ganinta nafarko dashi, yayi kyau sosai cikin shigan qananan kaya , wanda yai masa kyau idan sa rufe cikin farin eye glass
Koda yakariso kusada ita saitayi saurin dauke idonta akansa, murmushin sa mai tsada ya sake mata,
Juyawa tayi yana biye da ita abaya har xuwa dakin bak'i, duk wani motsi da takunta akan idanunsa yana sake karema surar jikinta kallo
Bakaramin kyau Aneesa tai masa cikin shigan datayiba , sosai yake sakejin sonta cikin zuciya da ilahirin jikinsa
Tana jifansa da murmushi take nuna masa daya cikin kujerun dake parlon, ya zauna itama tazauna awacce ke facing dinsa
Kafin ta surusuna kadan tana fadin"barka da zuwa dafatan ka iso lfy"
Saida yasanya idanunsa cikin nata kafin yafurta"lfy lau pretty ya gajiyan wahal da zuciyata "
Dariya tayi kasa -kasa kafin ta furta "hmm shureim kenan kaidai akwaika da zolaya "
Mikewa tayi ta zubo masa juice mai sanyi cikin cup, ta miko masa hannu yasa ya amsa yana karewa yatsunta kallo , wanda sukasha jan lalle sosai ya birgeshi , gawani qamshinta daya cika hancinsa, tas ya shanye ya dire cup din kafin ya fuskanceta sosai , yana fadin
"Aneesa gani gareki akaro na 2 ina mai sake jaddada qaunata zuwa gareki, banzo da niyyan wasa ko yaudara ba aurenki nakeson yin, domin azahirin gsky yadda nakejin kaunarki cikin zuciyata bazai misaltu ba
Don haka inaso kisanar dani gskyn abnd ke ranki gamedani , banaso adauki dogon lokaci batare da iyaye sun shigo cikin mgn ba
Don haka nakeson kisanar dani cikakkiyar ke wacece, domin dana isa Abuja ayau nakeson sanar da momy cewa nasami matar aure
Don harnayi kasadan bata zabi amma nasan tunda narigata samun zabin zuciyata shikenan, don haka ina sauraranki pretty"
Aneesa ta dubeshi kafin tafara da fadin "kaman yadda kaji sunana Aneesa , iyayena dukkaninsu haifaffun zariane , Abba yafitone a anguwan juma dake cikin birnin zazzau, yayin da umma ya Aurota daga samaru
Abba na aiki yakawoshi garin kd anan aka haifemu nida yayana wanda yarasu yanada shekaru 6 , yakasance ayanxu nice daya tak da suka mallaka
Hakan yasa Abba yadaura dogon buri akaina naganin , sainayi karatu mai zurfin gske a fannin boko , duk da cewa vanida raayin karatun aure nakeso , amma saina dinga yimasa biyayya domin ganin nacika burinsa
Nayi samari sosan gske amma duk wanda yakawo kansa , gdn mu dasunan neman aurena Abba zai koreshi yasanar dashi karatu zanyi ba aureba
Duk dacewa abn nadamuna amma sai nake boye damuwata , har zuwa yanzu dana kammala state university , services kadai yarage min sosai fuskan Aneesa ya bayyana zallan damuwa
Shureim wanda ya tsuramata idanu yana sauraran ta, ya jinjina kai yana fadin " ehem ina sauraronki pretty"
Aneesa tacigaba da fadin"shureim har kawo yanzu danake maka wannan mgn Abba burinshi ayanzu ina kammala services Indora masters, sam baya mgn infito da miji nasara wani dogon burine yake dashi akaina, bana burin zurfafa boko arayuwata shureim, zuciya da gangar jikina tun da dadewa aure suke muradi, amma narasa yadda zanyi Abba yafahimci cewa aure nakeso ba karatu ba
Sai dai inamaka albishir da cewa Aneesa na sonka , sonda ban taba yima kowani namiji irin saba, awannan karon inaji nizanyi nasara insha Allah kaine mijina shushu
Takarishe mgn tana rufe idanunta da hannu alamun kunya"
Shureim wanda jikinsa yafara sanyi mgn Aneesa nakarshe yabashi kwarin guiwa, tareda jin sabon sonta kominta nabirgeshi , cikin murmushi yake fadin
"Gud Aneesa naji dadin yadda nasami gurbi cikin zuciyanki, mgn Abba kuma kisa aranki lokacin auren ne baizoba adacan , amma ayanxu kam kisama zuciyanki da ikon Allah shureim shine zai mallakeki, so addua kurum zamuyi tayi kinji
Oya open ur eyes , kinwani rufemin fuskan dake sani cikin nishadi
Yakai karshen mgn cikeda xolaya , yana mai sake fadin but baki sanar dani aikin da Abba yakeba pretty"
Aneesa ta furta "Abba yayi retare daga aikin gwamnati yana harkokin business dinsane da kuma harkan noma da kiwo "
Jinjina kai shureim yayi cikeda gamsuwa kafin ya furta"gud pretty to nidai
Sunana shureim shu'aib Abba Aji
Dady na fitaccen dan kwangilane kuma rikakken dan business sosai,
Mu haifaffun garin gombe ne saidai a Abuja muka tashi , dady da momy dukkaninsu 'yan bokone , hakan yasa muka tashi cikin gata da wayewa, hakan baihanamu samun ingantacciyar tarbiya ta addini ba, nine babba kuma namiji daya tak dasuka mallaka, sai auta yusrah sam Abba bai taba shaawar aikin gwamnati ba
Nayi karatuna akasar Turkey inda nakaranta business administration, yanzu ina aikine da National Health insurance dake Abuja, ina kuma taba harkokin business daya shafi shigo da motoci daga kasashen ketare
Momyna cikakkiyar fulanin garin gombene , yayinda dady kuma hausa Fulani,"
Aneesa ta jinjina kai tana fadin"Allah ya shige mana gaba "
Shushu ya amsa da Ameen baby pretty I luv u
Wlh Aneey idn bansameki ba bansan ya rayuwata zata kasanceba, plxx ki rikeni amana kinga ni first luv ne bantaba so ba sai dai asoni, sai yanxu rana tsaka kikai nasaran mamaye zuciyan baki daya
Aneesa tayi dariya kafin ta jefeshi da wani kallon luv take fadin"karka damu my shushu Aneesa takace insha Allah "
Abnci ta xubamai basmati rice with patotoa source , sai pepe meat wanda yake tashin qamshi
Plate din ta tura gabanshi kafin ta zuba banana smoothie a cup ta tura mai, tareda ruwan Faro duk wannan abn idanun shureim nakanta
Komi takeyi birgeshi takeyi komi tanayinsane cikin nutsuwa, komawa tayi ta zauna tana fadin oya bismillah
Sosai yaci abncin jin cewa dakanta tashirya dominsa, yakuma yaba sosai da kwarewanta afannin girki , daga haka suka taba hiransu ta masoya kowa na fadawa d'an uwansa yadda yake jinsa aransa
Daga karshe shushun yamike don kama hanyan Abuja, har gurin mota tarakshi tana xubamai shagwaban dake susuta shi , fadi takeyi zatayi missing dinsa kai kace sun shekara dasanin junane , hmm soyayya kenan inji Ayshat
Rafan 20k ya mika mata hadeda leda mai daukeda turaruka masu tsadan gske, wanda yatsaya yasiya domin ta
Ja baya tayi tana girgiza kai take fadin"no shureim bazan karba ba "
Shureim wanda ranshi yagama baci cikin hade faces yake fadin"sbd bakyaso sona ko pretty shiya bazaki karbi abnd yafito daga gareni ba"
Ganin yadda ranshi yabaci yasa Aneesa daukan ledan turarukan , tareda yimai godia da fatan sauka lfy , ta juya zuwa cikin gd tabar shushun nabin bayanta da kallo harta bacewa ganinsa
Kafin yasauke ajiyan zuciya ya shiga mota yanajin sonta nasake game dukkanin zuciyansa
Fatanshi kawai yakai gd lfy domin gabatarwa momy da albishir din , yasamu macen dayakeso wacce bayaji idn baisameta zai cigaba da rayuwa mai kyau
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*13*
Fuskar Aneesa yakasa boye farin cikin datake ciki, domin har wani extra nishadi takeji, gawani soyayyan shureim din dake sake zaman dirshan cikin zuciyanta
Haka tashiga parlour babu kowa jin tashin qamshi dake fitowa daga site din kitchen, ya tabbatar mata da cewa ummah natare da mai aiki suna shirya abncin da Abba yasa ayi kenan
Kai tsaye hanyan kitchen din ta dosa fuskanta dauke da murmushi , lantana dake facing kofar kitchen din tana shirya salad da umma tagama hadawa, ta dubi Aneesa tana fadin
"Yar gd na sai yanxu gashi har hajiya ta shigo munkammala komi, "
Neesa tayi dariya tana "fadin wlh lantana sai yanzu yatafi ta dubi umma tana fadin ummah sannu da aiki nabarki da wahala wlh sai yanxu ya tafi"
Ummah ta dubeta tana fadin"bakomi Aneesa yanzu dai yimaza kizo kifara shirya abncin adakin baki , kinga har 6 takusa ba abn mamaki bane kiji shigowan su yanzu "
Aiko Aneesa kai tsaye tawuce room din ta kayan jikin ta tasauya , ta fito suka fara kai abncin suna ajewa harsuka kammala,
Koda tadawo ledan turaran da shushun yakawo tadauka, tayi bedroom ummah domin nuna mata kyauta daga masoyinta shureim
Ganin bata cikin dakin yasata juyawa tabar turaren bisa bed din, Rufaida takira tana shaida mata yaufa masoyinta yazo , domin rufin tun haduwan Aneesa da shushu kullum cikin yamata zancensa datake
Wanda hakan bakaramin kona ran Rufaida yakeba, sai dai sam bata nunawa Aneesan , domin tana ganin bayanzu bane lokacin daya dace tafito da kishin shureim da takeji ba , domin duk wani wanda zai rabi Neesa tofa Rufaida ta tsaneshi kenan
*********
Shigan yamma shureim yayiwa Abuja hakan yasa koda ya isa gd, kai tsaye part dinsa ya wuce sai dayayi wanka ya huta , kafin ya fito zuwa part dinsu momy
Da yusrah yafara cin karo cikin parlon ganinsa yasata rugowa da gudu tana fadin"oyoyo ya shushu shikuma ya rungumeta yana fadin baby ya gdn "
Sakinsa tayi tana fadin wlh munyi missing dinka ya shushu, hannu yakai ya dungure goshinta yana fadin"to aigani nadawo wai ina cwt mom ne ? Da hannu yusrah ta nunamasa bedroom din momy alamun tana ciki
Hakan yasa yakama hanyar bedroom din yana fadin"momy am back yana tura kofar ya tadda tana waya ne ashe, hakan yasashi janyo stool yazauna yana zabga mata murmushi, shushu bakaramin son mumy yakeba sosai
Saida ta kammala wayan ya isa ya kwantar da kansa akafadunta kafin ya furta"momy I miss u nasameku lfy ? "
Mom ta shafa kansa tana fadin lfy qalau my son , ya gajiyan hanya ?
Shushu ya amsa da Alhamdulillh mom sai dai nagaji , fura kawai nakeson sha hope akwaishi cikin frige,
Mom tayi murmushi tana nuna masa side din da karamin frige dinta ke aje cikin bedroom din, tana fadin"kaga ga furacan cikin frige dazu nadama shi don nasan Saika nemeshi
Tashi yayi yana fadin wlh momy nayi missing dinsa tunda naje banshaba sam, dakko jug din kacokan yayi yana dauki cup dake jere saman frige din, ya zuba yafara sha sanyin furan da gardin coconut da aka dama furan dashi yana ratsashi
Kusada ita yadawo yazauna tamkar zai shige ciki, kafin ya furta "momy yau akwai fa daddadan albishir dazan miki , wanda zai saki farin ciki da jinshi"
Momy tayi murmushi tana fadin "kaman kasan nima jira kawai nake kadawo nima insanar dakai wata muhimmiyar mgn
Shureim wanda bai kawo komi cikin ransaba ya furta " mom to mubary zuwa anjima sai infara gabatar da nawa domin duk na kisa , dady yayi tafiyane? Yayi tambayar yana kallon momy wacce taji tambayar tazo mata abzata
A tunaninta shureim shine nafarko dazaisan dady yayi tafiyane imma yayi byn ita,
Towai meke faruwa tsakanin dady da shushu , domin tafara ganin canji daga yadda shureim din yarage walwala matukar suna tareda dadyn
Kauda kai tayi tana fadin dady nagary babu inda yaje , bakuyi wayabane tunda katafi?
Shureim ya amsa da munyi momy amma sau daya , Naso sake nemansa ayyuka sun min yawane ,
Kiran sallah da ake kwadawa yakatse hiran nasu , shushu yatashi yana fadin"momy time 4 pray bari indawo masallaci saimu tattauna mgn ko yafice abnsa"
Momy ta nufi toilet domin dauro alwala
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*14*
Shureim da momy da Aneesa ne zaune a falo , byn sun kammala dinner har zuwa lokacin kuma dady bai shigo gdn ba
Momy ta dubi shureim dake cin Apple ahnkl tana fadin ,"my son ina jinka wani albishir ne kataho dashi ? "
Shushu ya dauki wayan shi batare da yafara cewa komiba, pic din Aneesa ya danno wacce tadauke shi tana sanye da doguwar riga xubin Indian design,
Tasha rolling tayi kyau sosan gske mikama momy wayan yayi yana cewa"momy duba pic dinnan kiga tayi kuwa
Allah yayi nayi mata wlh momy son Aneesa yayiwa zuciyata mummunan kamu , 7 days da haduwan mu kenan amma inajinta cikin zuciyata , tayadda bazan iya cikakkiya rayuwa mai nagarta ba inban mallaki Aneesa ba mom"
Ya karisa mgn yana dariya sosai kana kallon fuskansa zakasan, yana fadin komine with full confidence dinsa,
Yusrah da momy ya bary da baki bude xuciyoyinsu cikeda tsananin mamakin shureim din, hannun momy har rawa yake da kyar tanemo nutsuwan ta , yusrah ce tadawo dab da ita domin ganin wata mai sa'an ce shureim kefadin wadannan kalaman akanta
Dukkaninsu suka xubama pic din idanu suna kallon hoton Aneesa, sai dai atake zuciyan momy taji batai na'am da Aneesa ba , sbd bataga abnd Aneesa zata nunawa Ayshat ba daya wuce farin fata data fita
Yusrah tafara mgn tana fadin "big bros gsky tayi but zabin da momy taima wlh tafita haduwa ya shushu"
Wani uban harara yajefi yusrah dashi yana duban momy dake miko masa wayan
Fuskanta kadai daya kalla yanuna bata yaba da Aneesa ba , zuciyan shureim takarye ya zubama momy idanu yana sauraron jin mezai fito abakinta
Momy ta mika masa wayan tana fadin "shureim naga hoto takumayi batada makusa sai dai zabin danaima tafita komi , uwa uba ita munsanta munsan halayyan ta don haka kamakaro ,
Sai dai ka jingine mgn wannan yarinyan ka amshi zabin mu kaman yadda kabani izinin nemo maka mata , to aranan nayanke shawaran hadaka da Ayshat yarinyar dadynku Alhaji Adam"
Tuni shureim kejin wani xufa na keto masa idanunsa sun kada sunyi jajir, cikin tsananin tashin hnkl yake fadin
"Wat momy Ayshat fa kikace qanwar salman , no momy karki min haka wlh bantaba son ta ba bakuma naji zan sota , hasalima ina mata kallo ne tamkar yusrah kinko ga zancen ma nasota bai tasoba
Momy Aneesa itace kadai zuciyata keso ban taba soba sai akanta , plxx momy kijanye zancen tunkafin ma yaje kunninta tafara rainani, nacene kizaban mata arashin sanin zan hadu da Aneesa , tunda nahadu da wacce zuciyata keso plxx momy kijanye zancen Aysha"
Ya karishe mgn tamkar zai rushe da kuka , yayin da momy tai mugun shan kunu domin bataji akwai wanda ya isa yatada zancen auren shushu da Aysha
Hakan yasa takirayi sunanshi"shureim ka saurareni da kyau kaji mgn injanye zancen hadin aurenku da Ayshat ma baitasoba, domin bazaka maisheni karaman maceba, naje har gd nasanar da momynku hajiya safiya, takumayi na'am sannan dadynka da shi Adamun sun tattauna mgn , yarinya harta Amince batareda datayi gardama ba saikai danake ganin na isadakai
To bary kaji wlh kaji narantse Ayshat itace zabina, sai dai idn zakayi mata biyu saikayi byn kacika burina , saika aury zabin naka daga baya , amma mgn wata Aneesa kama ajeshi agefe "
Bata sake bashi daman mgn ba tamike tai hanyar bedroom dinta, tare da rufe kofan jikake baaamn...
Tabar shushun dafe da kansa wanda kejuyawa tamkar zai tarwatse, gaba daya jinsa yake cikin wani yanayi dabai taba tsinta kansa cikiba, na tsananin tashin hnkl da rudani
Yusrah ce ta matso kusadashi tana fadin "plxx ya shushu kayi hakury ka amshi zabin momy wlh Ayshat bata da makusa, ga nutsuwa ta mallaki komi da ake nema ga cikakkar mace, kuma na tabbatar idn akai auren.............. Wani tsawa yadaka mata cikin hargowa yake fadin leave idiot kawai, ni kike fadawa wannan banzar mgn ?
Aguje yusrah tayi hanyar bedroom dinta tana kunshe dariyan dake son taho mata, gefe guda kuma tausayin shushun na Neman karya zuciyanta, sai dai sam tafisonsa da qawarta ace wanta gd naso mezaisa akai dawa, sannan sanin kantane Ayshat macece da kowani namiji zaiyi alfary da samunta
Shureim mikewa yayi yanajin wani mugun jiri nafisgansa , da kyar yakai kansa part dinsa kafin ya zube kan sofa , yana sauke numfashi mai zafin gske gaba daya brain dinsa cushewa yai
Meke shirin faruwa dashine? Meyasa momy zata juyamasa baya alokacin dayake matukar bukatan tallafinta , domin samun cikar burinsa wato Aneesa yarinyar dayake jin sonta nakaruwa akowace dak'ika, why ? Why?
Meyasa momy zata zabi hadashi da yarinyar dabai taba mafarkin wani abu yashiga tsakaninsa da ita daya wuce gaisuwaba ,
Yarinyar dayakejin zafin mahaifinta cikin zuciyansa , tuni zuciyansa ke hasko masa yanayin daya tsinci Alhaji Adam da mahaifinsa suna aikata mummunan *LAIFIN* *BOYE*
rintse idanunsa yayi yanajin saukan wasu zafafan hawaye , wadanda suke zibowa tareda wani matsanan ciyar tsanan Alhaji Adam da Aysha"
Aneesa kadai yake ji aransa itake yake kallo amatsayin natsatstsiyr mace , wacce idn yasameta yayi babban dace Meyasa momy xatamai haka ?
Tunowa yai da mgn momyn"sai dai kayi mata biyu byn kacika burina "
Dafe zuciyansa yai dake masa zafi shine akewa zancen yayi mata 2? Anyako momy nason sa tana son farin cikinsa?
Wayansane yashiga rury a wahalce ya daukota yana kallon sunan dake yawo akan screen din
My luv shine sunan dake yawo bisa screen din wayan, amma shushu yakasa daga wayan, hartagaji ta tsinke bai sami daman receiving ba
*********
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*15*
A bangaren Aneesa kuwa jin takira har 2 misscall bai daga wayanba, tayi tunanin ko ya kwantane sbd gajiyan tafiya, hakan yasata ta tura masa text na fatan ya isa gd lfy, tareda kalamn soyayya da tasan xaiji dadinsu
Kiran dataji ummah namata ne yasata aje wayan ta nufi bedroom din umman,
Xama tayi bakin bed din tana kallon ummanta dake rikeda ledan, turarukan da shureim yabata tana fadin"umma gani "
Umman ta dubi Aneesa tana fadin "wannan kuma daga ina? "
Aneesa tayi murmushi tana fadin"umma shureim ne yabani nashigo dazu kinshiga wanka, saina ajeshi bisa bed ta karike mgn tana kallon umma"
Umma tayi murmushi tana "fadin to angode amma ki kula da amsan kayan samary ,niban fayason irin wadannan kyaututtukan ba "
Aneesa ta ja numfashi tana fadin "wlh umma ban amsaba saida naga ransa yabaci , da harda kudi masu yawa wlh kin amsa nayi"
Umma ta tsuke fuska tana fadin" to akul dinki da amsar ko kwandalansa , nafada miki wannan din ma saiki adana har dues lokacin da xamuga yadda xata kasance , Allah yazaba abnd yafi alkhairy"
Ameen Aneesa ta furta tana mikewa rikeda ledan xuwa dakinta, wardrobe ta bude ta aje ledan tareda sauya kayan jikinta xuwa na bacci, ta kwanta xuciyanta fal tunanin shureim tareda jin son taji voice dinsa, ahaka bacci yai awan gaba da ita
Washegary Alhaji Mahmud wato Abban Aneesa da umma habeeba ke zaune afalon Abban, byn kammala kalacinsu Aneesa tayi sallama cikin falon
Tana sanye cikin doguwar riga ta bubu wacce tai mata kyau , karamin gyale tayafa bisa kanta yasakko kafadunta, durkusawa tayi ta gaida Abban nata, ya amsa cikin sakin fuska byn fitanta ne
Umma ta dubi Abban tana fadin"yawwa Alhaji dama inaso muyi mgn akan wannan yarinyar Aneesa, jiya take sanar dani tasami tsayayyen saurayin daya fito yana sonta da aure, harma ya biyo nan ajiyan sun gana kafin ya wuce Abuja,
Domin can yake dazama
Anturoshi wani aiki ne anan kd suka hadu da Aneesa, kuma bisa dukkanin alamu tayi naam dashi tashaida min yana nutsuwa sosai , shine nace zan tunkareka da mgn don azahirin gsky hnkl yayi kwanciya da mgn auren Aneesa, tunda dai gwargwado tayima ka biyayya , tacika burinka naganin tayi degree duk da cewa nadade da lakantan yrinyar nan tafi bukatar aure akan karatun, amma hakanan tadanne don ganin tabi abnd kake so
Don haka awannan karon tanuna auren takeso da gske , kaga ko gara muyi mata don gudun zubewan mutuncin mu , ina tsoron zamanin nan damuke ciki Abban Aneesa "
Tunda tafara mgn ya zuba mata idanu yayinda ya bata fuska sosan gske, ganin tasa aya a mgn ta yabashi daman sake sanya idanunsa cikin nata , kafin yafara fadin
"Naji mgn ki Habiba wato har kene zaki bata daman kawo saurayi cikin gdn nan , batareda an nemi izini nabako? To naji tasami meso kuma ta shaida miki aure takeso, to naji awannan karon bazan tauye taba zanbata dama tayi aure amma da sharadin, sai munyi yarjejeniya da yaron byn auren zai barta ta dora masters dinta "
Umma wani sanyi ya ziyarci zzuciyanta,yanzu tasake gasgata duk wanda yarike addua bazai ga rashin nasaraba , tasan addua datakeyi dare da rana ne yafara tasiri , ta kumaji shureim yasake kwanciya aranta , da alama shi alkhairy ga Aneesa tunda gashi atashin farko sunyi nasara Abba bai kushe mgn ba
Kallon ta yayi yaga yadda farin cikinta yakasa boyuwa, hakan yasashi fadin"kiramin Aneesa yanzu inason mgn da ita "
Aneesa durkushe gaban Abba kanta akasa, Abban ya dubeta yana fadin Aneesa waye shureim? Gabanta ne ya yanke yafadi domin tana matukar tsoran mahaifinta , sam bata shaku dashi yadda tashaku da ummanta ba, hakan kuma yasamu ne sbd sm shiko irin yajata ajiki bayayi , saida tasaci kallonsa taga fuskansa asake yake sannan taji tasami nutsuwa
Ahnkl ta sanar da Abba waye shureim har yadda suka hadu bata boye masa komi ba,
Jin jina kai yayi yana fadin kina nufin kicemin shi yaron Alhaji Abba aji ne fitaccen dan kwangilan nan, kuma dan kasuwa lallai kin dakko mana dan babban gd ,ai mahaifinsa ba boyayye bane yayi fice sosai
To badamuwa Allah yazaba mafi alkhairy , amma inaso kisani bazan amince dashiba harsai munyi yarjejeniya zai barki kicikamin burina , naganin kinyi masters wannan kadai zai sa in amince ki aureshi , kisanar dashi randa zai sake zuwa inason ganawa dashi , kafin bashi izinin cigaba da mgn dake tashi kibani waje
Sum sum Aneesa tayi waje zuwa dakinta kan bed dinta tafada tasaki ihun murna, yai Abban tane yayi naam da mgn shureim batareda fada da hantaranta ba, wani nishadi takeji tareda matsananciyan soyayyan shushun dake sake mamaye zuciyanta
*********
Karfe 11am shureim ya fito daga part dinsa, yana sanye cikin bakin wandon jeans da blue din shirt, yayi kyau sosan gske sai fitinannen qamshinsa ketashi, kana kallon fuskansa zakasan baya cikin walwala
Kai tsaye part din su momy taiwa tsinke koda yashiga falon , da yusrah yaci karo tasha wanka cikin shigan gown ta laces siririn veil tarufe dogon gashinta dashi, tana rataye da jaka akafadan ta sai wayanta rike ahannu, da alamu fita zatai kallo daya yai mata yadauke kansa , domin har ita haushin ta yakeji yusrah ce kafadin
"Ya shushu ina kwana tana sauke masa smile ganin yadda yahada face,tasani haushin kalamanta na jiya ya yaji"
Bai tanka mataba Sai ma harara daya watsa mata wanda yasa yusrah sakin dariyan datake kunshewa, aiko hakan ya tunzura shushun cikin tsawa yake fadin
"Will u get out kosai nataso natakaki? nikike wa dariya baby alright zanyi maganinki "
Allah yahuci zuciyan yayana haka yusrah ta furta tana kokarin fita , ta kuma cewa bye ya shushu momy na bedroom saina dawo "
Ko tanka mata baiba illah wani dogon tsaki dayaja, ya nufi dining area din bude warmas yashigayi yana tabe baki kafin ya dauki cup ya hada oat , sai fraid egg sukenan abnd yasaka acikinsa , shima da kyar domin sam zuciyan sa babu dadi
Kaman wanda kwai yafashewa aciki ya nufi bedroom din momy, zuciyansa na bugawa d a karfi domin baisan yadda zasu kwashe da momy ba
Koda yatura kofan da sallama ya shiga tana hakimce akan bed waya takeyi ,
Guri yasamu yazauna ya zuba mata idanu bai jima ba ta aje wayan , tana kokarin tashi da Sauri shushu ya isa tareda kai hannu yariko hannunta , yana adin "morning momy "
Hajiya kubrah takoma ta zauna tana fadin "morning son"
Shureim ya kwantar da kasan a cinyanta yana fadin"plzz momy karkice zaki fishi dani akan mgn Aneesa , wlh momy nima natsince kaina cikin sontane dumu -dumu, ki tausayamin insami abnd zuciyata takeso momy , nasan kina sona bazakiso in tagayyara ba "
Hannu takai tana shafa suman kansa tana fadin"my son bawai banason ka da wannan yarinyar bane , illah inaso kagane cewa zabin danai maka abn kadubane , Aysha yarinyar kirkice tana da kyau da nutsuwan dazakai alfahari da samunta, shushu kaikanka zaka bada shaidan cewa Aysha bata da makusan dazakace zaka bijirewa aurenta, sai dai idn kanason ka tozartani ka jefa zuciyata cikin damuwa, dama masu iya mgn since amafi yawan lokuta d'anda kake nunawa so yafi wahal dakai "
Cikin damuwa shureim ya dubi momy yana fadin"no Allah yahuci zuciyanki bana fatan nasaba umurninki matukar auren Aysha shizai saki farin ciki na amince dashi , sai dai sam banajin zan sota momy , Aneesa nekadai cikin zuciyata yakai karshen mgn yana hawaye "
Tausayinsa yakama momy amma ta danne , hannu tasa tana wifing tears din kafin tafara mgn tana fadin "shushu calm down plxx ka kwantar da hnklnka so ahnkl yake shigan bawa,na tabbatar itama zaka sota ngd da goyan bayan daka bani
Kuma ina maka albishir da cewa zaka aury Aneesa amma byn ka cikamin buryna na auren Ayshat , wanda nakeso ayi komi nanda 2 month kacal
Allah yai maka albarka zaiyi mgn ta hanashi tareda fadin" shishh..... tashi jeka my son Allah maka albarka "
Tamkar zai rushe da ihu yabar dakin yana rangaji, yayinda kansa ke sarawa banda sonjin voice din Neesa baya jin komi cikin ransa, yarasa meyasa yakejinta har cikin jininsa,
Wayansa da ke aljihun wandon sane yafara ringing, duk atunaninsa Neesa ce hakan yasa yazaro cikin zakuwa
Sai sunan dady yagani yana yawo a screen din, wani takaici yarufesa kaman bazai daga kiranba, sai gab da zata tsinke ya daga ko kafin yayi mgn yaji muryan dady nafadin
"Kasameni a guess House dina dake wuse 2"
Ya katse wayan batareda yaba shureim din daman mgn ba
Shushu jiyai kaman ya tarwatsa phone din don takaici , ahaka yakarisa part dinsa zubewa a sofa yayi , yana sauke numfashi
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*16*
Gueshouse din Alhaji shu'aib shine zaune tareda amininsa Alhaji Adam , suna tattaunawa akan gine ginen gidajen marayu, da islamiyun da ake ginawa da dukiyan dasuka sadukar dashi , wanda suka samesa tahanyar banza
Wanda saura kiris kammala komi hakan yasa dady yakira shureim din domin , ya fayyace masa komi tareda nuna masa yadda komi yake
Shushun sai da yashafe tsayin lokaci har iyayen nasa sunfara fidda rai da zai zo , sannan ya shigo cikin katon falon dake down stairs
Kana kallon fuskansa zakasan yana cike da matsananciyar damuwa, har kasa ya gaidasu kafin yasami guri yazauna
Dady ya dubi tilon dan nasa wanda yakaranci damuwa kwance a fuskar sa kafin yafara mgn da fadin
"Shureim bawani abu yasa nakiraka nan ba gani gaka ga kuma dadynka Adam , sai don mutattauna mgn akan *LAIFUKAN BOYE*da mukai ta aikatawa muna samin kazaman kwangiloli da tarin dukiya, kaman yadda nashaidama zan sadaukar da duk wata dukiya dana sameta ko ince muka sameta , to Alhamdulillh nida Adam muka zauna muka tattauna abnd yakamata
Mun nisa gurin gine gine na gidajen marayu da islamiyu da masallatai, muna yi akaduna , nan Abuja mun gina a gombe mahaifata sannan sai katsina da yola
Wanda saura kiris ayyukan su kammala, mac book ya janyo yana nuna masa kaf gine gine wadanda suka tsaru , kana kallo kasan bakaramar dukiya bace take kuka gurin aikata wadannan ayyuka,
Shureim cikeda gamsuwa da tsantsan farin ciki yake kallon komi, har cikin zuciyansa yaji dadin yadda iyayen nasa sukai saurin nadama, tareda sadaukarwa suka zabi anfani da nasiharsa da kuma kokarin bijerewarsa ga dady duk don yaga cewa sun dawo kan hanya
Ahnkl ya dubi dady yana fadin" Alhamdulillh dady naji dadin yadda komi yakasance ina kuma addua Allah yasa kunyi tuba na gsky , Allah ya shiryarvda duk wani Musulmi mai aikata laifuka Irin naku ,
Zan kuma rufe sirrinku amatsayina na danku wanda bazaiso adinga nunaku amatsayin ,masu aikata *laifukan boye* ba
Sosai yasaki ji dasu sunata tattauna batutuwan dasuka shafesu , har lokaci yaja sosai Alhaji Adam shine yafara tafiya , yabar dady da shushun suna cigaba da hiransu
Byn tafiyansu ne dady yakama hannun shureim din , yana kallnsa sosai yake fadin
"My son tunda kashigo nake karantar damuwa atare dakai , kasanar dani meke damunka ? "
Shureim yawani shagwabe fuska yana fadin"Abba byn nadawo daga kd ne momy ke sanar dani kun yake shawarn hada aurena da Aysha , nikuma mgn gsky dady banason Ayshat ban taba mata kallo nadaban daya wuce na qanwa taba
Kuma atafiyan danayi
Allah yahadani da yarinyar data shiga xuciyata farat daya, ina tsananin son ta dady
Nan ya kwashe yadda sukayi kaf da momy har mgn matsayan dasuke kai ayanxu, na cewan saiya fara cika burin momy na auren Aysha kafin daga bisani ya aury Aneesa "
Dady yadafa kafadunsa yana fadin"kazama jarumi mana son kada soyayya tayi saurin saka ka susuce ehem,
Mgn da kubrah tayi tabbas ina byn ta nima domin ko yanzu kafin kazonan saida muka tattauna mgn da Adamu, Aysha ta amsa tana sonka anriga anyi mgn bagirman mubane ace andawo anfasa , kai mijin mace hudune shureim don haka zaka aury Aneesa amma saika fara auren qanwarka wacce mukafi gamsuwa da tarbiyanta ,
Don haka ka kwantar da hnkln ka sannan mgn soyayya ahnkl zaka sota shushu, ita yarinyar da kakeso din waye mahaifinta ?
Shureim ya dubi dady kafin yasanar dashi abnd Aneesa tasanar mai , tundaga mahaifansu zuwa aiyukan da mahaifin nata yake kai ayanzu, cikeda gamsuwa dady kefadin ok Allah ya tabbatar da alkhairy "
Mgn Ayshat kuwa cikin week dinnan zaa saka rana saikai kokaryn zuwa ku fuskanci juna ,
Idn yaso zansa afara gyaran gd na dake sun city sai kayi anfani dashi , tunda katon gurine da zaka iya aje mata ko ukune batareda takura ba
shidai shureim bin dady da kallo kawai yakeyi amma sam zuciyan sa batayi na'am daya fara auren Ayshat ba, inama laifin sufara aura masa zabin zuciyansa kafin nasu , sai dai vayaso yasabama mahaifansa mussamman momy dayake ganin tadauki lamarin da zafi "
Jiki asanyaye ya mike yana fadin shikenan dady zanyi yadda kukeso, shima dady mikewan yayi suka fito atare, driver dinsa yajashi shureim kuma yashiga nasa ya fice daga gdn
Yayi tafiya mai nisa kafin yasami gefen hanya ya parka,
Wayansa ya ciro yayi dialing number din Aneesa, wanda buga biyu yayi kaman tana jira ta daga wayan, byn tasake narke murya take amsa sallaman sa
Jin muryanta yasa shureim sake lafewa tareda sauke ajiyan zuciya,hira sosai suka yi mai cikeda kalaman soyayya kafin suyi sallama da juna
Shureim bai nufi gd ba sai hospital din da Dr. sudais yanufa, kasancewar sunday ce shi shushun yana hutun weekend ne
*********
Rufaida ce kwance adakin wata frnd dinta kuma abokiyar watsewarsu Aymana , wacce itama budurwace amma gogaggiyar barikice, wacce take mu'amala da mata da maza , daga ita har Rufaida iyayensu masu kudin gskene , wadanda ake damawa dasu a gwamnati,
Domin dukansu iyayensu narikeda mukamai masu kaurin gske , shiyasa suke yadda sukeso ba kwaba bare saka idanu daga iyayen nasu , wannan yabasu damar sheke ayarsu yadda sukeso
Aymana ce take kallon Rufaida wacce keta faman huci , cikeda bacin ran takira Aneesa ganajin number busy ,
Tsaki taja tana fadin"wlh Aneesa kibi asannu domin ina tsananin kishinki "
Wani uban harara Aymana ta zabgawa Rufaida tana fadin "andaiji kunya wai kaman Aneesa ce zaki mato akanta , narasa jarabar data sameki ki rasa wacce zaki zaba tazama dadironki sai wannan yarinyar, wacce bawani class ke garetaba , inbanda keda kike haskata wlh ni kallo bata isheni ba
Bafa wani wuta ahannun ubanta sai rufin asiry , babe ana harka da manyan babies ke kina biye da wacce batada 'yan ci , har yau Aneesa da dabara fa take fitowa kuhade inba kinje gdn su bane
Rufaida tadubi Aymana tana fadin "Aymana bazaki gane bane Aneesa tadabance ina samin gamsuwa da ita fiyeda tunaninki, tasan takan yadda ake harkannan wlh shiyasa naki yadda nasata akungiya , nafiso nikadai inmory abata
Keni yanxu matsalata baiwuce guy din data jajibo tanaso ba, kinsan shegiyan duk da goge wanta a less wlh auretakeso , nikuma bani bukatan abnd zai rabamu
Amma ayadda take nunamin bakaramin matowa tayi akan gayenba, kuma kinsan me wlh tacemin sonda takemai kadan ne akan yadda yakesonta
Yanxu hanyar daxan tarwatsasu nake nema cikin sauki , kunnin Aymana takai bakinta
Tana mata rada , kafin su kwashe da dariya Aymana nafadin bakifa da kyau tawan
Saida suka sheke ayarsu kafin Rufy tabar gdn su Aymana, itakadai kejan motanta kiran Vibe cikin gwanancewa,
Kai tsaye anguwan su Aneesa ta nufa domin tanakewanta 2 days , sannan tana bukatan samin information akan shureim Aji , namijin datake jin kishinsa tunkan tasan koshi waye takumayi tozali da kyakykyawar fuskansa
Bata dauki dogon lokaci ba ta parka motarta akofar gdn su Neesa , kafin tafito cikin takunta na gogaggun mata tayiwa cikin gidan tsinke
********
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*17*
Koda Rufaida tai sallama a parlor umman Aneesa ce zzaune,tana kallon tashar manara hnklnta nakan wa'azin da ake yi
Amsa sallaman tayi tana fadin"maraba da Rufaida kece da rana haka"
Rufaida ta dan durkusa tana gaida umman cikin mutuntawa, tamkar d'iyar kirki ita kuma umma na amsawa baki bude da murmushi
Aneesa ce tafito aguje tana fadin "oyoyo my bakin rai "
Harara Rufaida ta watsa mata tana fadin "dallah can byn tun daxu nake kiranki line busy koda uban wa kike waya oho"
Dariya sosai Aneey tasa tana fadin"kedai kincika daukr zafi shureim nefa muke waya dashi "
Umma ta dubesu tana fadin ehem zaku fara ba , dariya sukayi duka yayinda Aneesa takama hannun Rufaida suka nufi dakinta
Fitowa tasakeyi ta nufi kitchen karamin tray ta dauka , ta dora jug mai cike da kunun farar shinkafa wanda tasha coconut da madara sai milk flavour
Tahado da goran cway da ruwa ta nufi dakinta dashi kafin lantana ta sauke launch, akasa ta aje tray din tana fadin "bakin rai bakin fama ga mutuminki nan kunun rice kaman nasan kina tace, tana mgn ne tana tsiyaya kunun cikin cup , ta mikama Rufaida wacce takafe Aneesa da idanu "
Sanye Aneesan take cikin skat da riga na English wears , marasa nauyi kasncewar zafin da ake zabgawa , rigar takamata matuka tareda fito da surar kirjinta , sai skat din wanda yataimaka wajen fito da hips dinta
Byn Rufaida ta amshi cup din ne tafara kurban kunun, wanda sanyinsa da gardinsa ya ratsa makoshinta , tasha kaman Rabin cup din sannan ta aje tana fuskantan Aneesa
Take fadin"waike baby intambayeki man wayene wannan shureim din , dake neman yafara sace zuciyanki koma ince yasace, a ina yake impact dai inason sanin cikakken wayeshi "
Aneesa ta dubi Rufaida duba mai cikeda nazary , tasani sarai Rufaida batada kyau duk yadda akai wani kulli takeson hada mata , hakan yasa ta sake sanya idanunta cikin na Rufin
Kafin ta furta "cikakken sunansa shureim Abba aji mazaunin Abuja ,nan dai tasanar da ita komi kaman yadda shushun yasanar mata "
Rufaida ta jinjina kai tana nanata sunan cikin zuciyarta , tabbas tasan wannan sunan abakin salman, kaddai ace shine wanda salman keyawan sanar da ita abokinsane , kuma iyayensu aminan junane yana sanar da ita qualities din shureim aji , sam guy din shi baruwansa da rudin duniya
Tabba inko hakane dole Aneesa tamato kansa, ko sbd arzikin mahaifinsa ya isa tasosa, cikin dabara take fadin nice baby but natabajin sunan abakin salman I think kaman abokan junane nema
Aneesa ta dubeta tana fadin bari kiga pic din wlh gayen ya hadu over, kuma kinsan abn karin farin ciki Abba ya yi na'am da mgn duk da yace saisun yarjejeniya akan zai barni nayi karatu ko byn auren "
Wani harara Rufaida tasauke ma Aneesa afaikace afili kuwa dariya tayi , tana fadin"wow kice abn da gske akeyi yanzu babe hrwani rawan kafa kike zakiyi aure , amma inafatan yasan wacece zai aura , domin yasan yadda zai rika sharing dinki dani , dama sauran wadanda kike kulawa, domin inada lbryn kina muamala da seeyama qawar Aymana"
Aneesa saida taji gabanta yai mummunar faduwa,shikenan Rufaida tadakko hanyar da zata tarwatsa rayuwanta, don indai zatai kokaryn anfani da *LAIFIN BOYE* tanemi rabata da shushu to tabbas tana shirin tarwatsa rayuwanta ne
Cikin matsanancin tsoro take duban Rufaida tana fadin"haba Rufaida ya kike tunanin zan bude baki insanar da shureim cewa nidin 'yar lesbian ce , guy din dayake min kallon ustaziya natsatstsiyar mace,
Kumama keda kanki kinsani dukanmu babu wanda iyayenmu sukasan muna aikata *LAIFIN BOYE*
Plxx Rufy murufe wannan babin wlh ina matukar son shushu, son da bantama wani da namijiba, idn ban aury shureim ba bansan halin dazan fadaba, kda kiyi yunkurin rabani da rayuwata , nayi miki alqawarin cigaba da kasancewa dake har zuwa lokacin da zamuyi aure da shushu, daga lokacin zan killace kaina zan rabu da wannan harkan
Takai karshen mgn tana mikama Rufaida phone dinta "
Rufy wacce takejin dukkanin kalaman Aneesa tamkar zuban ruwan zafine cikin ranta, ta amshi wayan tana kokarin boye bacin ranta , zuciyan tane ya buga dakarfin gske sakamakon ganin kyakykyawar fuskar shureim shu'aib aji
Tabba dole Aneesa tamato akansa domin guy din yagama haduwa, zaiyi matukar wahala yataya ma mace kansa takasa amsar sa, stake kishin kasanvewansa da Aneesa yasake mamye ranta
Tabbas tasan idn hartayi saken da Aneesa ta aureshi tasan , zai matukar wahala tasame kulasu domin daman arashin yin auren ne yajefata wannan harkan
Inko hartasami kaman shureim bataji zata sake sauraren jinsinta , nan a nan ta tura pic din zuwa wayanta kafin tasaita kanta sosai
Tana duban Aneesa da keman kallon yanayin da Rufaida ke ciki , kafin ta furta "gsky qawata gayen ya hadu banga laifin zuciyanki data mato akansaba
Irinsu mnyan mata ke kwadayin samu keko a arha yazo miki , kinga dole kigigice mussamman dayazo akan gaban , kin matsu kikasance da namiji domin kigane banbancin ababen biyu kikuma cika burinki nasamin kids,
Wani makirin smiling tasake jifan Aneesa dashi kafin ta dora maganarta" ina miki fatan shureim yazama mallakinki bakin rai
Yanxu dai bari inji duminki baby na ta kai hannu tana rungumo Aneesa zuwa kirjinta ,
Aneey tamike dasauri tasaka ma kofar dakin ta lock , kafin tadawo ga Rufaida wacce harta tafara cire kayan jikinta
Badawasaba suka fara laluban junansu kafin su fda duniyarsu ta masha'a , sosai Rufaida ta murji Aneesa kafin sufawo natsuwansu
Mai da kayanta takeyi ajikinta tana duban Aneesa dake kwance babu komi ajikinta , illah hawayen dake sauka nisa bedsheet din dake shinfide akan bed din
Wanda suka tumurmusheshi yanxu zuciyanta na mata kuna kaman ko yaushe, tanajin haushin mahaifinta tasani dole Allah ya kamashi da laifi , domin duk abnd take aikatawa shine sila da ace yaimata aure da bata fata ga wannan mummunar harkanba
Sai da Rufaida ta gama maida kayanta tsaf domin bata bukatan yin wanka saita je gd,
Kallon Aneesa tayi tana tabe baki kafin ta furta "to mrs shureim atashi agyara jiki nizan wuce zuwa gd sainajiki "
Aneesa ta tashi zaune tana share hawayenta rigan ta zura yasauka guiwa , dogon hijab tasaka mai kaury yarufe jikinta
Ahaka suka fito domin yiwa Rufaida rakiya , wacce kejinta cikin farin ciki domin jefi tsuntsu biyu da dutse daya
Nafarko ta sami biyan bukanta 100%daga jikin Aneesa shiyasa take qaunar yarinyar over, na biyu kuma gashi tasami information akan shureim abnd yai saura tasake bincike akansa sosai kafin ta d'ana tarkonta
~~~~
Wannan shafin kyauta ce agareki Anty mejidda musa, sosai nakejin dadin yadda kike bibiyan buk dina , tareda bada courage plzz duk inda akaga munyi kuskure ina bukatan gyara , Allah yabar qauna 閴傦拷
**********
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*18*
Shureim ne zaune a offices din Dr sudais sanyin Ac naratsashi , hakan yabashi daman kwanciya bisa kujeran dake offices din
Cox sudais din yabarshi ne sun shiga theather , idanunsa alumshe suke ya fada duniyan tunanin yadda zaiyi ya aury mata 2, wannan wani irin lamari ne zai kasance dashi
Meyasa su momy bazasu janye mgn wannan yarinyar ba, wani kwafa yayi yana ayyana irin wulakancin da Aysha zata fuskanta, watoma itace tace tana sonsa
Ahnkl yasake zaro wayansa yana kallon pic din Aneesa wanda ayanxu itace ta mamaye screen din wayansa
Ahaka Dr. Sudais ya sameshi yayi nisa yana kallon pic din Aneesa, shamma tansa Dr sudais yayi ya warce wayan , yana kallon pic din wacce ke bisa screen din, kafin ya kwashe da dariya yana fadin
"Huuhh guy kace kafada system din luv ne haka, amma fa kayi babban kamu , domin yarinyar tayi ba karya yana mgn ne tareda zama bisa kujera"
Shushu ya tashi zaune yana yasina fuska kafin ya furta"dallah Mallam bani wayata ubanwa yace idanunka sudinga kallemin mata "
Wani dariyan sudais yasake dauka yana mika masa phone din
Kafin ya furta"Allah yabaka hakury lover boy din momy yanzu dai miye lbry ne? "
Shureim yasake bata rai alamun damuwa ya wanzu akan fuskansa, kafin ya fuskanci sudais din yana fadin "wlh guy ina cikin matsala bansan ya akeso nayi da raina ba ahnkl ya kwashe komi yasanar dashi
Ya kare mgn yana fadin amma nafi ganin laifin wancen yarinyar data Basu goyon baya , amma zatasan tayi kasadan shiga rayuwata "
Dr. Sudais shima yatausaya ma aminin nasa , domin yasan yadda so yake mussamman ma shi shushun da baitaba fadawa tarkon son wata mace ba sai yanzu, sannan bazai bashi goyan bayan ya bijirema umurnin iyayeba, ko bakomi shi shaidace akan cewa Aysha yarinya ce natsatstsiya , kuma tana da kyau da qualities din da kowani namiji zai so takasance mallakin sa, amma ayanxu yasani shushu bazai fahimci hakan ba , sbd yafada tarkon son abnd zuciyansa keso
Dafa kafadun shushun yayi yana fadin"shureim kayi hakury kai haka naka kaddaran yazo ,ka amshesu duka amatsayin zabin rankane bawai kaware Aneesa kadai don itace kakejin sonta aranka ba, kobakomi Ayshat qanwace agareka kuma ko don salman baikamata ace muna tare tsawon lokaci , ka aury qanwansa kace zaka wulakantata ba, so inabaka shawara don Allah shushu kada kawulakanta Ayshat , domin bakasan wacece zata zamema alkhairy cikin rayuwanka ba, "
Dakatardashi shushun yayi tahanyar daga masa hannu yana fadin"enough sudais domin na fuskanci kaima baka qaunata tunda har kake goyan bayan nafara auren abnd banso , narasa meyasa kowa baya goyan byn Aneesa sai wannan stupid gal din, ohh yanzu atakaice kaima bakasona da Neesa ko? "
Dariya sudais yayi yana fadin "calm down my frnd nibance Neesa batayi ba , bankuma ce bana sonka da itaba domin kagama samun tabbacin indai itace matarka zaka sameta , ina maka nasiha ne sbd ita wacce kake kurarin bakaso itace zata fara zama first wife din taka , wannan kawai shine amma ni inason duk abnd kakeso shushun momy angon Aysha angon Aneesa , gsky abokina kai mai sa'a ne wadannan zuk'a-zuk'an mata haka
Yakai karshen mgn cikeda zolaya hadida dariyan shak'iyanci "
Shureim ya mike yana daukan car key dinsa yake fadin"kai dai Dan world ne wlh ka koreni tunda baka supporting my precious dina
Don haka bye zani gd inhuta idn kagama iskancin naka by next week nakeso ka rakani kd, ohhh nafa manta kafin nan ance inje inga waccan yarinyar "
Dariya sosai sudais keyi harda rike ciki kafin yafurta"alryt duk yadda kace haka za'ai angon nan da 2 month "
Wani uban tsaki shushu yaja yana ficewa daga offices din ,
Koda shureim ya koma gd gurin 2 narana kai tsaye part din momy ya nufa, domin yunwa yakeji sosai hakan yasa koda yashiga kai tsaye dining ya nufa , ya zuba abnci yafarci yayi nisa dafaraci momy ta fito
Sanye take cikin doguwar rigan bubu wanda yazauna ajikinta sosai, kana kallonta kaga manyan mata babu mai cewa ta ajiye kaman shushu sbd tsananin gyara da kulawa da jikinta ke samu
Fuskanta asake take fadin dama kashigo nida inatajin motsi , nakumasan yusrah ta fita ashe kaine kashigo koka nemeni , sbd kana fishi dani ko? Hmm yaro kenan atunaninka shushu kana zaton , zan iya zabama abnd zai cutar dakaine ? Hmm kumama banda abnka aiba cewa akai kwata-kwata bazaka aury sarauniyar zuciyan taka ba , cewa nayi saika fara auren zabin mu kafin naka "
Shureim wanda ya aje spoon domin yakare cin abncin ya dubi momy yana fadin"haba momy nifa ba fushi nake dakeba kawai dai tunanin yadda zanyi da mata 2 nake , domin bantaba koda mafarkin faruwan hakan agareni ba"
Wani harara momyn ta sauke masa kafin ta furta "to ai saika fara yanzu domin nan da 2 month zaka angonce da daughter na inyaso duk lokacin daka yanke asa rananka da ita Aneesa sai asa, don haka gara kazama jarumi tun yanzu , inaso kuma kasa tsoran Allah azuciyanka ka rike Ayshat da amana , koda bakajin sonta hakan bayana nufin ka wulakantata bane , idn kuma burin dake ranka kenan tokasani matukar ka zalince ta koka wulakanta ta wlh kaji na rantse bazan yafemaka ba "
A firgice ya dubi fuskan momy wanda sam babu alamun wasa atattare da mgn daya fito bakinta, jinjina kai yayi yana ayyana wai yaushe Ayshat tasami wannan matsayin azuciyan momy , har shine yau momy ke fadin bazata yafe masa ba idn ya wulakanta Ayshat?
Wani tsanan Ayshan yaji yasake mamaye ransa, da kyar ya saita bacin ransa yana fadin"Allah yahuci zuciyanki momy insha Allah ma babu abnd zai faru , ai Ayshat qanwata ce babu yadda zaai incutar da ita "
Ya kare mgn yana kallon fuskar momy wanda ayanxu tasaki wani murmushi, najin dadin kalaman da shureim yayi ,
Kafin ta furta gud my son kokaifa harnaji dadin mgn ka, ina tabbatar ma dacewan zakayi alfary da zabina zuwa gaba, Allah yai muku albarka kaida ita kai dama Aneesan gaba daya
Domin duk abnd kakeso nima inaso shushu matukar zai zame maka alkhairy ne ,
Sosai shureim yaji dadin kalaman momy , tunda aka fara wannan cecekucen sai yanzu momy tayi mgn daya faranta ransa,
Haka suka dinga hira sosai shushu yasaki ransa, wanda hakan ne burin momy shiyasama tasako mgn Aneesa don ya gane cewa bawai suna k'inta bane , sam sunadaiso yagane muhimmncin zabin dasukai mai ne
*********
Wednesday in the evening.........
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*19*
Wednesday in the evening Aysha ce kwance bisa cinyan umma , tana game din candy crush manyan calaban dake kanta umman ke warware mata , tana sharce mata dogon tashin ta da tsayinsa yasauka gadon bayanta
Wayan ummace tadauki rury hakan yasa ta tsaida abnd takeyi ta dauki wayan, ganin sunan hajiya kubrah ne yasa ta daga wayan tana fadin"barka da warhaka hajiya kubrah ya gdn ya yusrah "
Daga bangaren hajiya kubarah ta amsa tana shaidawa hajiya safiyan cewa, ga shureim nan bisa hanya zaizo su fara fuskantan juna da d'iyar tata Aysha
Sosai umma tayi farin ciki tana fadin"to shikenan hajiya babu damuwa gani ga Ayshan ma yanzu zan sanar mata sallama sukayi da juna "
Umma tadubi Ayshat tana fadin"oya saiki maza ki kintsa ga yayanki shureim nan zuwa ku gana "
Aysha kallon umma tayi alokaci guda kuma kirjinta yabuga , samun kanta tayi dajin fargaban yadda zasu hadu da shureim din, batasan yadda haduwan nasu zai kasance ba
Jiki asanyaye ta mike zuwa room din ta gashinta tafara gyarawa, tashafe shi damayuka masu qamshin gske , kafin ta isa ga sif dinta wanda yake shak'e da situru
Ta dade tsaye tana nazarin shigan daya dace tayi , kafin ta yanke shawaran zaro wata hadaddiyar gown ta atamfa , dinkin yayi asalin zama ajikinta sosan gske abnka da kwararrun Tailor suka tabi kayan
Light make-up tayiwa fuskarta tadauki designers perfumes ta shiga feshe jikinta dasu , axababben qamshine yagauraye dakin baki daya
Batayi tunanin daura dan kwaliba illah karamin veil data dauka wanda yadace da shigan jikinta, tayane gashinta dashi zuwa kafadunta
Juyi tayi agaban mirrow din tana furta masha Allah domin ita kanta tasan Allah yayi mata baiwan wani abu waishi kyau da diri
Phone dinta tadauka ta fito daga dakin kai tsaye kitchen tanufa , rabice keta faman shirya abncin dinner umurni Aysha tabata akan cewa , ta hado ruwa da juice zuwa su danbun nama with snacks takai dakin baki tashirya , cikin ladabi ta amsa da to anty
Ficewa tayi takoma dakinta sam tarasa dalilin datakeji bugun zuciyanta nakaruwa , number din yusrah tayi dialing bugu biyu ta daga wayan , cikeda zolaya take fadin "ran matan yaya shushu ya dade, ya akayine ? "
Ajiyan zuciya Aysha tasauke tana fadin kedai wlh baki rabo da wasa, ni dakisan ma yadda zuciyata ke bari dakin tausayamin plxx qawata kibiyosa kuzo tareman, wlh tsoran haduwanmu dashi nake yusrah, ke shaidace yaya shushu bawani jituwa muka fayeyiba illah gaisuwa dake hadamu, gashi yanzu mgn daya shigo tsakaninmu wlh nasan tsanata zaiyi tunda bashi yafurta yana sona ba, takai karshen mgn cikeda karyewan zuciya, wanda hakan yasa gaba daga yusrah taji tausayinta yarufeta , "
Cikin karfafa mata guiwa tayi dariya tana fadin"common karki bada mata mana miye haka da saurin karaya haka, babu wani abu qawata ki dake xuciyanki aikema bakece kika nemi ahadaku ba beside kinama da wanda zuciyanki keso , amma kika danne kika amince dashi , so inaso kicire duk wani tsoro aranki karma yafara gane weakness dinki akansa tunyanxu kinganeko , duk abnd kuka tattauna ki kirani zuwa anjima , yanxu dai kitabbatar kin wanku yadda yadace ehem bye "
Takashe wayan tabar Aysha jigum tana nanata mgn yusrah, dafa kanta tayi tana fadin ohh ashefa nikadai nasan sirrin dake raina game dashi , tabbas yazama dole incigaba da boyewa har zuwa inga yadda ya shushun zai karbeni
Tunaninta ya tsayane alokacin dataji umma na kwalla mata kira , hakan yasata mikewa dasauri ta fice still tayi tana zare idanu, ganin zaratan matasan biyu zaune suna kwasan gaisuwa
Sam batayi tsammanin sun isoba sai da umma taharareta sannan takariso cikin falon, daga nesa dasu kadan ta tsuguna gaidasu , wanda Dr. Sudais kadai ya amsa gaisuwan amma shi gogan baima da niyyan dagowa yadubi side din datake
Duk dacewa tinda ta tinkaro falon fitinannen qamshinta yafara cika hancinsa, umma ce kefadin "to shureim ku karisa dakin baki gatanan fitowa ko "
Kaman jira yake shiya fara mikewa yayinda yabar Aysha da karema shigan jikinsa kallo, yana sanyene cikin wata d'anyar yadi mai ubansun tsada , dinkin halpjanfer akai masa bakaramin kyau yayiba kansa ba hula illah gashinsa dake kwance luff sai shek'i yake, ya boye idon sa cikin bakin eye glass wanda dawuya kagane zahirin halin da fuskarsa ke ciki
Saida ta tabbatar sun isa parlon bakin kafin tabiyo byn su , tana shirin shiga tajiyo mgn sudais yana fadin"wai kai guy dinnan wani irin dan iskane kai , tunda muka fito kaketa faman wani cin magani , wlh kaji narantse idn yarinyar nan tafito ka wulakantata kaman agaban momy kayi ,
Kila anfada maka rashin so haukane kuma inbanda abnka itadin budan baki tayi tacemaka sonka take , ok don ta yi biyayya ta amince shine zakayi tunanin ko sonka takeko , lallai bakasan mata ba kasan dai Aysha bakaramar yarinya bace dayazama dole tayi tolerating wannan bad habit din daka dakko nunawa ko?
Sosai zuciyanta yashiga bugawa shikenan abnd take hasashe yatabbata , ya shushu ya tsaneta bayasonta lallai tayi gangancin furta amincema aurensa ,
Jikinta amatukar sanyaye tayi sallama domin takawo karshen maganganun datakeji , tun kafin gogan nata yafara furta wasu kalaman akanta
Sudais ya amsa sallaman yana fadin shigo mana amaryan mu , cikin jin kunya da mutuwan jiki tashiga tasami mazauni , sake gaisawa sukai da sudais cikin sakin fuska sai tsokananta yake yi
Shiko shureim ko gigin kallon inda take baiyiba gaba daya hnkln sa nakan wayansa , sai faman danne- danne yakeyi shirune yaratsa parlon tsayin mintuna
Daga bisani Aysha ta tashi tagabatar musu da lemu da danbun nama, sudais tafara turawa gabanshi kafin ta dauki na shureim ta isa kusadashi ta aje
Tana fadin "bismillanku ya shushu kusha lemu plxx"
Tamkar tayi mgn da gunki haka shureim yai mata , ko kallon inda take baiba jikinta har rawa yafara sbd bacin rai abnka damai saurin kuka , nantake hawaye suka cika idanunta tana maidasu
Komawa tayi tazauna tana wasa da zoben gold dake yatsun hannunta, mgn take cikin zuciyanta take fadin"oni Ayshat to yanzu miye laifina anan dahar ya shushu zai fara wulakantani don kawai na amince da bukatar mahaifiyansa ,?
Tabbas dole taboye duk wani sonsa datakeyi kodan gudun wulakanci , domin bazata jura wulakanci ba dole tanunawa shureim itama bawai tana raayinsa bane tamkar yadda yakejin ta aransa haka zata nuna itama tana jinsa
Mikewan da Dr sudais yayi rikeda plate ahannunsa yana fadin"amaryan mu bari inyi waje inbaku daman zantawa da angon naki ko? "
Yayi mgn cikeda zolaya hakan yadawo da hnkln Ayshan kansa , tayi kokarin zakalo murmushi tana fadin kai ya sudais aida kazauna miye aciki
Dafe kirji yayi tareda zaro ido cikin sigan zolaya yake fadin kirifamin asiry waneni dajin hiran masoya ina dai jiran yallabai din daga compound
Sosai mgn shi yaba Ayshat din dariya hakan yasata murmusawa har kumatunta suko lotsa ,
Byn fitan sudais shiru yasake ratsawa tsakaninsu har zuwa lokacin shureim nata faman danna waya, tamkar baisan dazaman wata halitta afalon ba haka yayi
Zuciyanta ne yacigaba da baci da irin salon wulakancin ya shureim din
Hakan yasata yanke shawaran kawo karshen shirun tahanyar dubansa tana fadin ...............
**********
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*20*
Ya shureim inaso kagafarceni abisa kuskuren danayi na amincewa da bukatan momy, danasan hakan zai jefa zuciuanka cikin tsanata wlh dana bijerema bukatansu
Nasan irin zafin dakakeji acikin zuciyanka, tamkar yadda nima nakejine dukkanin bamu son juna , amma kasani zabin iyaye ba abn yardawa bane , domin sun cancanci muyi musu biyayya, kaman yadda nida kai shaidane akan irin son da iyayenmu ke nunamana , bazasu taba zabamana abnd zai cutar damu ba
Ya shureim nasha kai dakake namiji kuma babba agareni zaka fini nuna jarumta gurin ganin muncika burin iyayenmu, atunani ne nice abn tausayi domin akwai wanda zuciyata keso , amma nasaudakar da abnd nakeso domin infaranta ran iyayenmu
Amma ina rokan ka dakayi hakury ka cire tsanata acikin zuciyanka,ni haryanzu ina kallonka amatsayin ya salman ne, wanda bazan so ganinsa cikin damuwaba, idn har kana da zabin zuciyanka ya shushu kasanar da momy tayi hakury ajanye batun auren mu amma bazan iya juran wulakanci ba
Takai karshen mgn tana kokarin maida hawayen dake shirin zobo mata , dukkanin maganganun datakeyi tanayinsu ne bisa karfin hali, juriya dakuma dakewa "
Shureim wanda tunda tasoma magana yake kallonta yana sauraran duk abnd ke fitowa abakinta, sai dai yarasa mai yasa maganganun nata suka fara karya zuciyansa, ashe dama bata sonsa itama biyayya take kokarin yi ?
Sam saiyaji zuciyansa baiso jin cewa bata sonsan ba , yaso yayi anfani da son datake mai ne ahasashensa yaji dadin wulakantata , amma kash.... Sai gashi tana furta masa cewa yadda yakeji gameda ita haka itama takeji , kenan ta tsanesa cikin jin zafin mgn ta yafara furta
"Ayshat inaso kisani tunda nake bantaba koda kwatanta son wata mace cikin zuciyata ba, hasalima sam ni babu soyayya atsarin rayuwata salman shaidane akan hakan,
Ganin cewa na isa aje iyali kuma burin su momy ne nayi aure , hakan yasa nabata daman zabomin mata wanda shine babban kuskuren dana fara nadaman furtashi rayuwata
Aranan dana bata zabi aranan nabar garin nan xuwa kd , awashegari na hadu da yarinyar data sace zuciyata ta ruguxa duk wani plan dina,
Itace macen datai nasaran mamaye zuciyata , Aneesa ita kadai zuciyata keso ayanxu ita kadai nake mafarkin inbude ido inganta agd na amatsayin mata ,
Aysha bantaba miki kallo nadaban daya wuce yadda nake kallon yusrah ba, nayi kokaryn momy tagane cewa ayanxu nasami wacce zuciyata ke tsananin so , amma kash takasa gane hakan hasalima ahalin da ake ciki yanzu mata 2 akeso inkasance dasu
Momy tace saidai infara aurenki kafin daga baya in auro zabin zuciyata , don haka ina shawartanki idn har kinsan kinada wanda kikeso kiyi gaggawan ganin baa kawoki gd na ba, domin babu abnd zaki fuskanata sai wulakanci sbd zuciyata bata kaunarki
Na tabbatar idn kika sanar da momy kina da zabin ranki zata hakura , idn kuma kin shirya xama da kishiya da mutumin da baki aransa kofa abude take
Yakarisa mgn yana wani yatsina tareda karemata kallo yadda hawaye ke gudu afuskanta"
Ayshat wacce takejin maganganun shureim tamkar zuban ruwan dalmane cikin zuciyanta, dago idanunta masu zubar da hawaye tayi tana dubansa , takasa dauke idanunta akansa wani irin masifan son sa da kishinsa ke sake narke zuciyanta, mai yasa zuciyanta takasa cire son shureim ? Meyasa shureim bazai yi naam da itaba ? Gashi yanzu yana sanar da ita wacce yakeso haryana fadin baya kaunarta , tabbas zuciya bataimata adalci akan so ba
Cikin muryan kuka take fadin "ya shureim naji dukkanin abnd kace sai dai inaso kasani , bazan taba iya bude baki insanar da momy cewa banason jininta ba
Bazan iya rusa farin cikin danake hange a idanun iyayena nason ganin zumuncin su yadore ba, ya shushu bazan iyaba nabaka dama kai dakake namiji kafadawa iyayena baka sona da bakinka , nasan zasu fi gamsuwa sukuma janye batun aurenmu , subaka zabin ranka karayu da ita kadai basai an hadaka da wacce katsanaba
Sai dai nasani matukar aurena dakai rubutacce ne ya shureim, duk da bamu son juna bazamu iya kaucewa rubutacciyar kaddaranmu ba, don haka inanan akan bakata zanyi musu biyayya
Amma kanada daman ka sakeni saki uku byn ankawoni cikin gdn ka , daga karshe inamaka fatan samun cikar burinka Aneesa "
Cikin sassarfa tabar parlon tana xubar da hawaye , jitakeyi inama zata iya cire son shureim dake kassara zuciyanta , data yarda kwallon mangoro kodan ta huta da kuda
Sai dai hakan ya faskara duk wadannan maganganun data fadamai , tafadesu ne cikeda karfin hali amma wlh tanajin sonsa nakaruwane cikin ranta
Koda tashiga parlor tayi saa ummanta batanan, hakan yabata daman wucewa room dinta , kan hado ta kwanta tasaki kukan datake rikewa kotaji sanyi cikin ranta
Abangaren shureim kuwa jiyayi tamkar andasashi agurin , maganganun Ayshat kadai kemasa yawo cikin kwakwalwan kansa, meyasa yarinyar tafishi xurfin tunani ne, tabbas idn har aurensu rubutaccen kaddara ne yasani bazasu iya gujewa hakanba
Sai dai yarasa meyasa zuciyansa ke azalzalansa dajin haushin yarinyar ne ? Ganin bashida amsan tambayan yasashi mikewa ya fice
Amota yasami sudais yana waya hakan yasashi , zagayawa bangaren driver yatashi motar suka fice daga gdn , byn mai gadi yabude musu gate aguje shushun kejan motn tamkar zasu tashi sama
Sunyi nisa kafin sudais yagama wayan dayakeyi yana fadin"waikan don ubanka lfy kake irin wannan tukin waima meyafarune tsakaninka da gimbiyar taka , yakarishe mgn yana kunshe dariyan dake son taho masa
Wani matsiyacin tsaki shureim yaja kafin yasami gefen hanya yayi parking, batareda yace uffan ba yafito tareda jefama sudais car key din
Zagayowa yayi yai tsaye yana jiran sudais din yafito, dariya sosai sudais din yakeyi harda hawaye kafin yafito ya koma inda shureim din yataso , shikuma yashiga yazauna seat din mai zaman banza yanata faman tsaki
Saida suka fara tafiya bisa titi sannan sudais yafara mgn"waikai guy dinnan meyafarune kaketa jan tsaki ? "
Kaman shushu bazai kulasaba sai dai yafara fadin"hmmm wai harnine yarinyar nan zata dinga gasawa mgn harda cewa itama bata kaunata yadda nakejinta araina itama haka takeji tanada wanda takeso, to don ubanta wani shegen yace ta amince da mgn tun farko
Wlh kaji narantse saina wulakanta yarinyar nan , inbanda ma anjanyomin raini harta isa gani gata tadinga furta kalaman da taga dama agare ni? Kwafa yayi yana fadin amma duk laifin momyne data dage akan wannan mgn
Sudais yatsaida dariyansa yana fadin "wow ammafa Ayshat
tabiyani wlh nagode mata dabatayi shakkan sanardakai bata son kaba,
Abnd nake fadama kenan kayi ahnkl domin amincewan ta bashi kenuna wai tana sonkaba, sai gashi tana sanar dakai kaga kenan tafika hnklne data zabi faranta ran iyayenmu , sabanin kai da soyayya take neman rufe idanunka , wlh kayi ahnkl matukar kace wulaknta yarinyar nan kazaba tofa kasani , wataran zakayi nadaman hakan domin kiyayya yana saurin juyewa yakoma matsananciyar soyayya , musamman idn yakance daya bashida hakki akan dan uwansa, don haka kataka asannu wlh ka kumayi hnkl da fushin momy ehe"
Shureim ya maka masa harara yana fadin kai dai dama ai ba'a abn kirki dakai , idn sonta kake why not amaida batun kanka , yakare mgn yanajan tsaki gaba daya haushi da tsanan Aysha yacika ransa,
Amma yazaiyi hakanan xai faranta ran momy ya aureta sai dai yana tausaya mata wulakancin dazata fuskanta daga gareshi byn anyi
Haka suka cigaba da tafiya babu wanda yasake kula wani , har Dr sudais yayi dropping shushun ya dauki motarsa yabar gdn
Akuma washegari aka kai duk wani abu da ake bukata nasaka ranan aure, inda aka tsaida 2 month kacal, byn iyayen sun tattauna batun shushun dana Aneesa wanda zai aura byn anyi bikinsu da Ayshat din,
Alhaji Adam bai nuna damuwa ko wani abuba yayi fatan alkhairy acewansa ai shureim yana da daman yin mata daga daya har 4 ne, umman ce dai taji tausayin diyar tata amma ganin yadda Ayshat din taboye damu wanta yasa itama take karfafa mata guiwa
Yau yakama weekend ayau dinne kuma shureim keson zuwa gurin precious dinsa, shida Dr sudai wanda zai masa rakiya
Tun 12 suka dauki hanyan kd byn yasanar da ita gasunan bisa hanya
********
Kd.......
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*22*
Yusrah zuciyata ta dade dakamuwa dason maso wani , wanda hausawa ke kirada koshin wahala,
Wlh yusrah nikaran kaina bazan cemiki ga sanda nafada son sa ba, fangar da sonsa nakeba sai da zuciyata tayi mummunan kamuwa da kaunarsa,
Tun inasaka rai zan iya samun soyayyan sa harna fara fidda tsammani, bansake fidda ran ba saida na fahimci nikadai ce zuciya da ruhina ke azabtuwa da soyayyar da, shi zuciyan sa tayi nisa gurin son wata shiyasa nazabi binne son axuciyata batareda nasanar da kowa sirrin dake rainaba
Yusrah ayau zan tona miki abnd nadade ina boyewa, wlh bakowa zuciyata ke azabtuwa dasinsa ba illah shureim , ya shushu shine kadai namijin dana rayu da sonsa cikin zuciyata ba, tunban san so ba harna fahimci sonsa nake
Hakan yasa da momy tazo da bukatan hadamu aure nayi saurin amincewa, a tunani ya shushu bazai tsaneni ba sai dai kash nayi kuskuren danake nadama ayanxu
Domin bana hango komi akwayar idanunsa sai zallan kiyayyata yusy , kifadamin yazanyi inciresa daga cikin mind dina? Shureim baya sona yusrah ayanxu ba wacce yatsana Irina , kallona yake amatsayin bakar katanga dazatai masa shamaki wajan hanashi samun cikan burinsa alokacin dayake bukata "
Aysha takai karshen mgn tana zubar da hawaye masu zafin gske ,
Yusrah baki bude take kallon Ayshat wacce tausayinta yagama cika zuciyarta, a hnkl ta matsa tareda rungume Ayshat din tana patting byn ta ahnkl
Take fadin "sorry my frnd kiyi hakury kikuma cire damuwa aranki , ina baki tabbacin ya shushu zai zama naki ya shushu zai soki fiyema da kike sonsa insha Allah ,
Banaso ki karaya kuma naji dadin yadda kika iya danne soyayyansa baki bary ya gane hakan ba, kicigaba da boyewa har zuwa lokacin da zai shigo hannu wlh kinji na rantse bana fatan ki raga masa ,
Ahnkl yusrah ke tsaida kukanta byn ta koma ta zauna, take duban yusrah tana fadin yusy yanxu baki tausayin ya shushu ,
Yusrah tayi dariya tana fadin yusrah kenan, kedai kawai kibi abnd nace , ki rabi dashi yaje yaita son wacce take gabansa ayanxu , komi yana zuwa da lokacin sane , nan suka cigaba da hiransu na aminan juna , anan ne kuma yusrah ke tseguntawa Aysha cewa ya sudais ke sonta
**********
Salman da Rufaida ne kwance akan bed cikin dakin hotel din dasukai masauki , byn yakawo mata ziyara daga garinna Abuja,
Salman shine namiji daya tilo da zuciyan Rufaida ta amince dashi , har take mallaka masa jikinta yayi yadda yaga dama ,
Sun hadu dashi ne agarin Abuja wani bikin dasukayi na qawarta , dasuka kaita birnin tarayyan , tunda salman yaganta ya like mata har dai yasami kanta ,
Suka fara soyayya har yagane cewa Rufaida cikakkiya kuma gaggiyar 'yar less ce wacce take harka da mata kala da daban -daban
Cike salo da iya jan hnklnsa yafara yaudaranta harta fara sallama masa kanta , shine namijin daya fara shigan ta byn tagama rabama mata kanta ,
Saidai yadda ta yafi dashi taba gamsuwa jiyayi bazai iya rabuwa da itaba, domin tagama gogewa a iya wasannin dake gigita mutum gata jarumace karshe gurin samar mishi da nutsuwa,
Tasha jin lbryn shureim aji abakinsa , yana kuma yawan fadan kyawawan halayensa , shiyasa ayanzu taci burin sake samun information akan sa daga salman din
Kanta na kwance bisa kirjin salman dinne bayan sungama sheke ayarsu , wasa yake da kirjinta yanda yakeso
Wayanta ta dauka tareda hasko pic din shureim aji , kafin tazare jikinta ahnkl tana sanya idanunta cikin na salman din take fadin
"My bobo inason kasanar dani waye guy dinnan , tana mgn ne tareda mika masa phone din nata "
Salman ya amsa yana dora idanunsa akan screen din wwayan,xunbur yayi yatashi zaune yana tsareta da manyan idanunsa masu firgitata,
Ganinpic din shureim awayanta yamatukar tsoratashi , sbd yasan Rufaida shaidaniyar yarinyar ce me kuma yakawo pic shureim wayanta?
Cikin tsare gida yake fadin uban me yahadaki da Pic din shushu? O akuyancin naki yafara dawowa kan mazane ba matan da akasaba biba
To barikiji shureim ba irin guys din da kukebi bane , wannan baya ciki da tambadaddun bariki kinaji ko , imma wani buri ko kwadayi kike dashi akansa u have 2 be very careful Rufaida ,
Sosai mgn salman yabata mata rai amma tashanye domin tasan yafita hauka , yanzu saisu samu matsala idn tace zata kawo masa zafin kai
Ganin ransa yabaci ne yasata komawa jikinsa tana kokarin hada bakinta danashi , wanda yaki bata daman hakan sai tabige ga shafa gashin dake kwance akirjinsa
Ahnkl take fadin "easy mana my sugar bobo nibabu abnd yahadani da shi illah information danake nema akansa
Domin qawata yakeso suna matukar son juna shine tasani inmata bincike akansa , wannan shine kawai amma kasan ni ai bakuwani dameni ba , nafi ganewa innemi mata kai ne kadai kake making love dani kaima shaidane bobo , takai karshen mgn tana lasan lips dinsa
Kafin sufada dukiyar kissing din juna , cikin dabara da lallami tadinga tambayan salman gameda shureim din har tasami abnd take nema ,
Yayi juyin duniya tasanar dashi wace yarinyar ce shushu kema azabar so haka, har yazabi yayi kata 2 don kawai yacika burinsa akan mallakanta
Sam sai hnklnshi yakasa kwanciya tausayin qanwar shi yasake kamashi , domin yasan shureim baya son Ayshat yagani akwayar idanunsa , domin shi mutum ne dabai iya boye abnd ke ransaba
Sai dai duk yadda yaso Rufaida tabashi haske akan yarinyar da shushun keso ttaki,domin baya fata takasance cikin jerin matan da Rufaida ke harka dasu , inko har hakan ne lallai shushu yayi zaben tumun dare
Hakadai sukagama tanvadewan su suka rabu da Rufy batareda yasami cikakkiyar shaidan cewa , yar less irinsu Rufaida shushu yafada tarkon sontaba
********
Alhaji wlh kaji narantse idn har baka yanke shawara akan bukatata na muyi aureba , saina tona maka asiri saina fallasa LAIFIN BOYE da kake shukawa kana boyema matanka ba
Nagaji da wannan rayuwan na rashin 'yanci kamaidani tamkar wata matar ka , sainayi mgn aure kafinga kaucewa
Byn kaine kafara bata budurcina to wlh nagaji dole ka aure inkuma ka kiya wlh saikayi nadaman sanina,
Wata matashiyar budurwace da bazata wuce shekaru 20 ba , black beauty ce ajikin karshe , tana mgn ne tana maida kayan jikinta byn tagama kintsawa,
Alhaji shu'aib Wanda ke kwance ya tsura ma maryam idanu , yana mamakin wai shine karamar yarinya, kaman yusrah zata tasa tana gaya masa mgn hartana masa barazana da zata tona masa asiry gaban iyalansa?
Lallai gaba daya zina baiyi ba yana sake nadaman jefa kansa cikin wannan masifa dayayi, gashi yakasa daina mu'amala da mata ,
Dagashi har aminin nasa garama shi kan adamun , wanda saima abnd yakaru azahiri dai sundaina safaran matasa da 'yan mata suna rabawa manyan kasa
Wannan sun tuba zinarce dai suka kasa dainawa ,shikam yakasa rabuwa da maryam ne sbd irin natsuwar datake samar masa
Tabbas lokaci yayi dazai yakice zina ya aury dadiron tasa wato maryam, yarinyar dayamaida ta tamkar matansa , kuma shine yafara sanin ta amace
Hakan yasa yake kara jin tausayinta , kallonta yayi byn tagama gyara zaman veil akafadunta , tana wani kada jiki take fadin toni zan wuce saika sallameni ka kuma je kayanke shawara, nabaka nan da 2weeks kayanke mgn 1
Rafar 40k ya dire mata tadauka cikeda yatsina tawatsa cikin jaka, kafin tafice tabarsa da fitinan qamshinta
Lumshe idanu yayi yakasa kwakwkwaran motsi , tunani ne yacika kwanyasa ta yadda zai tinkaray hajiya kubrah da zancen auren yarinyar cikinsa , domin sai dai suxo shekaru daya da yusrah ,
Sosai kansa yadauki zafi sai dai bashi da mafitan daya wuce hakan , tun kafin ta tona masa asiri agabansu ta fito da LAIFIN suke aikatawa a BOYE fili , gara ya aureta kawai cikin rufin asiry
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*24*
Koda maryam ta aje wayan duban qawarta nabila tayi , tana fadin baby nida wannan dittijon banzan ne fa , wlh saina shayar da Alhaji shu'aib mamaki
Matukar bai amince da aurena ba wai yana sanar dani inmasa uxuri ya aurar da babban yaronsa , tukunna saiyasan yadda zai bullowa matansa dabatun aurena
Ke kijimin fa nifa wlh tausayin ma matar nasa nake , domin da alamu bata da masaniya akan Duk irin ta'asar dayake aikatawa a BOYE
Nabila ta sheke da dariya tana fadin ai wlh maryam , nikaina mamakin halayyan wadannan bayin Allah nake idn kingansu cikin manyan kaya , saiki rantse mutanan kirkine , amma kibisa a hnkl mana tunda dai kinsan yana qaunarki
Tunda dai harya amince ai anyi mai wuyar , dariya sukeyi sosai yayinda gaba daya jikin yusrah yai mugun sanyi , haka kawai zuciyar ta ke kwadaitar da ita son jin waye wannan, dasuke yanka haka mai sunan dadyn ta
Cikin karfin hali da dakiya tadubi maryam din byn ta kirkiro murmushi , take fadin "umm nikam qawata aure zakiyi ne muzo musha biki ,
Maryam tayi dariya tana fadin hmn kedai qawata bari kawai , wani Alahji ne kewahal da zuciyata wlh , sosai nake azabtuwa da sonsa amma danayi mgn aure Sai yafara kwalo -kwalo
Kuma abn shi shina fara sallama ma budurci na , takarishe mgn tana fasa kwai da cingum din dake bakin
Baki sake Ayshat da yusrah ke duban maryam , xuwa yanzu dukansu sun amince dazargin su akan maryam din , cewa 'yar barikice
Yusrah ce tayi karfin halin fadin , o niko zanso sanin wannan mutumin gashi naji kin anbaci sunansa daya dana dady na , kinsan ina girmma masu wannan sunan
Amma ko inhakane bai kyauta ba shiyafi cancanta daya aureki tunda dai shiya fara saninki ,
Zuwa yanxu fuskan maryam yabayya alamun damuwa kadan , kafin ta dubi yusrah tana fadin " kedai bari qawata ai bariki baiyiba matsalan mace tafara saida mutuncinta atiti kenan
Wlh ina ragawa Alhaji shu'aib ne ganin shidin bakaramin mutum bane, kuma koda shiyafara sanina ba cikin dole yaminba , nice na sallama kaina sbd ganin akwai wuta ahannunsa sosai
Kafin tasake wani mgn wayanta yasake daukan rury , saida taja tsaki tana fadin kunga shinefa mai kiran , kaman bayanxu muka gama waya ba hmm bari kuji bai wuce yace muhadu a guess house dinsaba,
Tana mgn ne tareda receiving call din byn tadanna hands free , muryan Alhaji shu'aib ne yafito baro-baro yana fadin babyna , nifa amatse nake dake gsky duk yanda zaai kixo kisameni a guess house, haba jan ran ya isa haka nan rabona da inmory ni'imarki 1 week kenan
Tashin hnkl wanda baa saka masa rana shine yasami yusrah da Aysha alokaci guda , jin muryan dady nasakin wannan zance gaba daya jikin yusrah rawa yakeyi
Jitakeyi tamkar amafarki hakan ke faruwa , muryan maryam ne yadawo dasu daga duniyan dasuka lula na tashin hnkl
Tana fadin "shikenan Alahji na karka damu nima nayi kewanka daurewa kawai nakeyi "
Kit ta kashe wayan batareda tasake bashi daman mgn ba ,
Ta dubesu tana fadin kunji garanko dama ninasan zancen kenan ,
Nabila da sauran ne kawai suka iya mgn , amma yusrah da Ayshat ko tamkar an dasasu agurin haka suka kasance, yusrah ko motsi takasa tana ji inama mafarki takeyi ,
Saidai jin Ayshat na zhngurinta yasata gane afarke take , da kyar ta iya duban Ayshat wacce idanunta harsun fara canza kala tsabar tashin bnkl ,
Mikewa sukayi suna duban maryam cikin karfin hali Ayshat kefadin , sis plzz idn badamuwa munaso mudan kebe dake awaje , akwai mgn damukeso mutattauna
Mikewa maryam tayi tana gyara zaman mayafinta , kafin ta furta "ok babu damuwa mujeko "
Can waje suka fita direct gurin motansu suka nufa , yusrah ta bude back seat ta shiga byn ta kwanta yaraf , kaman jira take sukadaice tasaki kukan datake rikewa , hawaye masu zafin gske suka fara mata ambaliya
Ayshat ce budewa maryam front seat ta zauna , yayinda ita tazauna a seat din driver
Gaba daya sautin kukan yusrah akeji cikin motar , yayinda Ayshat ma batasan sanda tafara xubda hawaye ba
Maryam zuwa lokacin zuciyarta tafara sanar da ita akwai babbar matsala , hakan yasata bude baki tana fadin
"Bayin Allah lfy kuwa kun kirani kun tasani gaba kuna kuka kuma "
Ayshat tashare hawayen fuskanta tana fadin "maryam don Allah kisanar damu waye Alhaji shu'aib dinki , waye kuma kukai waya dashi yanxu , gaba daya kinjefamu cikin tashin hnkl
Domin muryan wannan damukaji ba muryan kowa bane illah na dadin mu , I mean mahaifin yusrah kuma aminin mahaifina , wanda kuma yake shirin zama surukina nan da 2 month
Takarishe mgn tana wani sabon hawayen "
Jikin maryam ne yai sanyi zuciyanta yashiga bugawa da karfi , no wonder tunda taga yusrah take ganin mugun kamansu da Alahji shu'aib, ashe 'yar sace ta cikinsa
Cikin tashin hnkl take fadin "Ayshat sai dai kuyi hakury amma wannan mutumin da kukaji shine wanda nake nufin ina tarayya dashi , shiya fara bareni aledata wanda ayanxu haka nakeda burin zama matarsa domin shiyafi cancanta daya aureni
Alahji banice kadai yafara tarayya da itaba yadade yana hulda da matan banza, ke amgn danaji akansa shida amininsa Alahji Adam, har rabawa manyan sanatoci zuwa minister mata sukeyi da matasa ana anfani dasu , amma sudai bantaba ji ance suna neman jinsin junaba
Alahji Adam yafi Alahji na harka da mata , domin xan iya cewa tasanadin farkansa afrah nahadu da Alahji shu'aib ,
Inamai baku hakury dacewa addua itace kadai mafita , amma iyayenku sunyi nisa a aikata LAIFIN BOYE
wani irin ihu yusrah tasaki tana fadin " wayyo Allah na Allah kasa inbude ido inga cewa duk abnd kunnuwana keji mafarkine , duk wannan abn idanun yusrah arufe suke kam
Sai dai jin sautin kukan Ayshat daya cika kunninta yatabbatar mata ba mafarki takeba, bude idanun tayi tajin gina jikin seat din , kanta da zuciyan tane suka dauki ciwo alokaci guda
Cikin disashewan muraya take fadin "tashi kije maryam mungode amma kisani bantaba tsanar wata 'ya mace sama dakeba aduniya , domin ke kika fara jifan dady da munanan kalamai agabana , bani kuma da hurumin hukuntaki domin shiya yada girmansa ,
Ina rokonki dakiyi gaggawar cireshi aranki domin ko kin aury dady bazaki taba daraja a idanun Muba , kaico dady yagama damu why why !
Dafe kirjinta tayi dake barazanar tarwatsewa , dariyan da maryam tasaki irin na marasa mutuncine yasake jefa yusrah cikin tashin hnkl
Kafin maryam din tafara mgn cikin gadara darashin kunya take fadin
" o sannu mai uba so inaso kibude kunnuwanki dakyau kiji , maryam ba shegiya bace nasan dadin mahaifi kaman yadda kikasani , banbanci na dake nibansami gata daga nawa iyayenba , wanda adalilin hakan harna jefa kaina halin danake ciki ayanxu
Tunda mahaifinki yai nasaran keta haddina wlh bani da mijin aure saishi kodako banasonsa , bare inasonsa sbd akwai wuta ahannunsa , idn na auresa zan fantama
Mgn rashin daraja bana fatan samunsa agareku , don haka abu daya zanbaku shawara ku binne wannan sirrin dakukasani na iyayenku , domin fallasashi nanufin rashin kwanciyan hnkl ne da iyayenku mata zasu shiga
Kucigaba da asirta LAIFIN BOYE da iyayenku ke aikatawa ,
Nabarku lfy takarishe mgn tana ficewa batareda ko waiwayensu ba "
Hakan kuma yayi dai dai da rushewan dasu yusrah sukayi , babu mai lallashin wani Ayshat har kanta take bugawa bisa kanbun motar ,
Yadda takejin zuciyanta tamkar zata yo waje haka takeji ,
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*25*
Ayshat ce tagaji da kukan ta lallashi kanta , juyawa tayi ga yusrah wanda idanunta harsun fara tasawa sbd kuka
Cikin dusassar murya Aysha kefadin "sis saidai fa muyi hakury kuka ayanxu bashine mafita ba, iyayenmu sun riga sun cucemu yusy bazamu taba goge tabon dasukai mana ba "
Ganin yusrah bata zimmar kulata yasa Aysha taiwa motar key , haka sukabar gdn bikin Zahrah saraki batare da amarya tasake sakasu cikin idanunta ba
Aysha gdn su ta nufa koda sukai parkin sun dade cikin motar batare da dayansu yayi yunkurin fitowaba, itadai yusrah gaba daya tazama kurma yayinda Ayshat tunanin yadda zasu shiga cikin gd ayanayin dasuke ciki kawai take
Fatanta Allah yasa karsu tadda umma aparlor , cikin karfin hali take fadin"yusrah mujeko amma kishare wannan fuskar taki , kinsan dai umma saita tambayi dalilin wannan hawayen ko"
Batare datace uffanba tamika hannu ga hand bag dinta , tissue tazaro tana goge fuskanta tareda shafa powder tadaiyi kwaskwarima , duk da hakan kallo daya zaka mata kasan taci kuka takoshi
Aysha kwaskwariman taiwa face dinta suka fito xuwa cikin gdn , cikin lucky suka tadda parlon shiru babu motsin ko TV hakan yaba Ayshat daman sauke ajiyan zuciya
Dakin suka nufa suka zube a sofa yusrah tayi jifa da veil dinta , tareda zare dankwalin kanta
Aysha ce tadubeta tana fadin "yusrah inaso kiyi hakury ki lallashi zuciyanki , kirufe wannan mgn atsakanin mu kada kice ko ya shushu zaki tinkara dashi nasan wautan ki baby
Kisani fallasa wannan sirrin tamkar tarwatsewan farin cikin su momy ne, mudai kawai muyi addua Allah yashiryar dasu , kuma mgn maryam da dady indai har auran ta zai zamo silar kintsuwansa waje guda , plxx baby yusy kubashi dama ya aureta
Inama Abba ne dadiron sa takike masa wlh zangoyi byn aurensa da ita matukar zai daina bin mata , yusrah zuciyata zafi takeyi inajin tsanan mahaifina tareda jin ciwan yadda yazubar da mutuncinsa , meyasa basu zabi sukaro ma iyayenmu kishihoyi uku alokaci guda akan su zabi mafi munin aikata LAIFIN BOYE ba?
Tunda Aysha tafara mgn yusrah tafara sharan hawaye, kafin tafara mgn tana fadin" Ayshat duk yadda kikejin tsanan Abba baikaiga yadda nakejin na dady ba , sannan wlh kinji na rantse saina sanar daya shushu wannan mgn
Domin shikadai ne zai iya ma Abba mgn kada ya aury maryam, bazan sanar da momy ba sbd ayanzu ina tausayin ta Aysha , idn kinga yadda take kokary akan dady da yadda kulkum yake tarairayanta , har abn yana bani sha'awa nasha adduan Allah yabani mijin dazamu gina rayuwa tamkar yadda su dady suke , basa taba nuna ma juna cewa sunfara manyan ta
Aysha bazaki taba tunanin dady xai iyacin amanan momy ba , momy ta yadda da mijinta bazan iya tinkaranta da wannan mummunan lbryn ba, amma ya shureim namijine yafimu kaifin tunani xan sanar dashi ko zuciyata xataji sanyi
Shiru Ayshat tayi tana jinjina mgn yusrah aranta, to ko itama zata tinkary ya salman da mgn ne? Wata zuciyan tace to aishima duk shegiyan darince
Wani takaicine yazirce zuciyanta itadai batai sa'an samin kamilin uba da yayaba, gara yusrah ya shureim natsatstsane wanda yasan ciwan kansa
Cikin karfi hali tadubi yusrh wacce itama idanunta nakan Ayshat din tana fadin "shikenan baby tunda kinyi rantsuwa "
Karfe 6pm na yamma yusrah ce tafito domin tafiya gd , Ayshat ce tarakota byn sunyi sallama da umman, wacce sam bata fahimci komiba kasancewar tunda suka dawo , suka kule adakin Ayshat basu fitoba sai da yusrah ta tashi tafiya gd , hakan yasa umma tunanin koma shigowansu kenan yusrah tasauke Ayshat din ita kuma zata wuce gd
*********
Karfe 9pm yusrah ce sanye da karamin hijab wanda ta dora akan doguwar rigan baccin dake jikinta
Saidata tabbatar momy na part din dady sannan tafice zuwa part din ya shureim , wanda cikin sa'a kofar abude take sallama tayi akofar falon nasa
Yana kwance sungama waya da Neesa kenan yafara kallon news , atashar NTA yaji sallaman yusrah
Yes come in yafadi idanunsa nakan TV shigowa tayi tana fadin ya shushu kallo akene,
Kallonta yayi yana fadin baby lfy daiko naganki kaman byn zu muka rabuba,
Nan da nan ta bata fuska alamun damuwa ya bayya afuskan ta , cikin damuwa take fadin ya shushu mgn nakeso muyi akan wani lamari daya firgita tunanina, tareda jefa zuciyata cikin tsananin rudu da takaici
Rage volume din TV yayi yana fuskantan ta sosai , yake fadin"inajinki baby sanar dani damuwanki domin bakida wani dan uwan dazai saurari matsalanki daya wuceni "
Ya shushu kataba sanin dady mazinaci ne ? Kataba sanin yana cin amanan momy yana harka da matan banza awaje, sannan katabajin mgn da akeyi akansu na kawalancin matasa da 'yan mata ga manyan kasa?
Tun yaushe dady yafara aikata wadannan munanan ayyukan a BOYE ? meyasa yazabi cin amanan mu yaxubar da kima da mutuncinsa don kawai yasami arxiki?
Ya shureim natsani dady wlh ayanxu natsanesa , kafadamin taya zan iya danne zuciyanta akan wannan mummunan lbryn daya ziyarci zuciyoyinmu nida Ayshat, dukanmu iyayenmu sun kasance masu aikata LAIFUKAN BOYE
Takarike mgn tana kuka mai taba zuciya , wani irin mummunan tashin hnkl ne yazirci zuciyan shureim,
A ina baby taji wannan lbryn ? Cikin son danne zuciyansa yariko hannunta yana fadin "baby a ina kikaji wannan lbryn ? "
Cikin muryan kuka take sanar dashi duk abnd yafaru yau har wayan da dady sukayi da maryam bata boyemai komiba ,
Wani irin takaicine yaziyarci shureim , yanzu dady dama basubar neman mataba , wannan wata irin masiface ?
Lallashinta yakeyi yana fadin duk abnd kikaji baby babu karya aciki, domin ranan wanka baa boyon cibi nan shureim yasanar da ita abnd yafaru abaya har kawo lokacin da su dadyn suka kirashi , suka nunamai sun tuba sai ashe mutuban bana daina neman matabane
Yacigaba da fadin yusrah dole kinatsu ki koyi danne damuwa da bacin rai , sbd kar momy tagano halin da akeci kinji ko , yanzu adduan mu dady yake bukata bawai fishi da bacin ran dazamu nunaba
Sannan mgn maryam sam batada laifi don tadage saita auri dady , don shiyafara keta mutuncinta batareda tsoran Allah ,ya tuna yanada budurwa kaman ki ba , yasaki ji alokacin da kika rasa budurcinki kuma wanda kikavawa kanki yagujeki alokacin dakike tsaka dason kasancewa tareda shi baby?
Don haka matukar dady yaxoda batun kara aure zai auri yarinyar , to yazama dole mubashi goyan baya yusrah hakan shine kadai gatan dazamuyi ma momy , mu ceto dady da ita yarinyar daga fasadin da suke aikatawa,
Kukan yusrah ne yakaru cikin rishin kukan take fadin "yanxu ya shushu muna kallo dady zai aurowa momy karuwa wlh ya shushu natsani maryam "
Wani tsawa yadaka mata cikin bacin rai da fishi yake fadin
"Eh haka nake nufi baby idn bamu barshi ya aureta ba mubarsu sucigaba da aikata sabo? Look yusrah duk yadda kike taya momy jin zafin kishi nafiki son kasancewanta cikin farin ciki
Auren maryam da dady shine kadai mafita , don haka ki boye duk wani damuwa dazai janyo hnkln momy tafahimci akwai wani abu da kike boyewa
Zamu xuba masa idanun har lokacin dazai tinkary momy da zancen sake auren sa , daga lokacin mune zamu karfafa zuciyanta harta bashi goyan baya , natabbatar idn taga mun amince zata amince itama "
Yacigaba da rarrashin yusrah yaana karfafa zuciyanta sai da yatabbatar tagamsu da maganganunsa kafin yadora dafadin
"Baby yusy wannan halayyan nasu dady yana daya daga abnd yasa nasakejin tsanan aurena da wancan yarinyar, domin sam nadaina ganin mutuncin Abba Adam"
Yusrah bata bari shureim ya ida fadin mgn dayakeson fadiba , tayi saurin rufe bakinsa tana fadin
"No ya shushu kada kabary laifin Abba yashafi Ayshat wlh Ayshat yarinyar kirkice, da kaga halin datashiga asanadin jin halayyan dasu dady ke aikatawa sai ka tausaya mata , kada ka tsaneta akan hakan ya shushu don Allah kaso Ayshat kodon darajan yadda umma keyabon halayenka nagari ,
Wlh ya shureim zakaji dadin zama da Ayshat domin she's very simple bata da matsala , nasani so ahnkl yake shiga amma kayi kokary kasanmata wani gurbi koda kadan ne cikin zuciyanka
Nasan Anty Aneesa tayi zaman durshan but ya shushu muma asanmana ko gurbi kadan ne plxx kajiii.. "
Takarishe mgn cikeda shagwaba tana langabar dakai , sosai taba shureim din dariya yana fadin
"Wlh baby bakida dama wannan irin kamfen haka toko dai itace ta turoki ? "
Zaro idanu yusrah tayi tana fadin "tabdi karifan asiry da Ayshat wlh sam ba itabace nice dai nake ganin tadace tasami gurbi a hrt dinta ,
Aysha tanada wanda zuciyanta kematukar so ya shushu kawai dai tazabi tasadaukar da abnd zuciyanta kesone donta faranta ran momy , ko wannan kadai ya isa karaga mata ya shushu ka kaunaceta kodan kaima nafaranta ran momy , takarishe mgn cikeda damuwa a fuskanta tmkar gske "
Jikin shushu yayi sanyi yana jinjina karfin hali irin na Ayshat , wanda shikam ayadda yakejin Aneesa aransa baya tunanin zai iya sadaukar da son donya faranta ran wani ,
"Hmm baby kenan zan duba dacewan hakan but ni Neesa ita nakeji araina , amma kicigaba damin addau Allah yabani ikon yima kawarki adalci
Haka shureim yafurta yana mai duban agogo , ganin har 10 yawuce yasashi mikewa domin raka yusrah part din momy"
Byn yasake kwantar mata da hnkl akan batun su dady ,
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*27*
********
Rana bata karya ayaune za'a daura auren shureim shu'aib Abba aji da Ayshat Adam
Tun safe Ayshat keta faman zubda hawaye wadanda suke zuba da ma'anoni biyu , nafarko tana murnan zata mallaki namijin da sonsa yaima zuciyanta mummunan kamu
Na biyun ko natausayin kanta da irin zaman dazasuyi da shureim wanda ta tabbatar balallai zaman yazama mai dadi ba, sai dai zamn fuskanta hakury da juriya kawai
Yusrah kadai tasan ma'anan kukan da Ayshat din keyi hakan yasa , ba matsa akan lallai tayi shiruba tabarta tayi mai isanta , yayinda su sury karofi kezaton kukan rabuwa da gd ne Aysha keyi tun farin safe
********
Abangaren ango shushu kuwa tun safe misalin 10 yake aikin lalllashin Aneesa , wacce take tafaman yimasa kuka da shagwaban wai zaa kai masa Aysha ,
Magiya takemai kada yaci amanan soyayya yajuya mata baya , idn ankai masa amarya gaba daya tagama susuta shureim da salon kukanta da shagwabar da take mai
Wanda kesake jefa zuciyansa cikin wani haki , baisami kan gimbiyar tasaba sai gurin 12 suka rabu awaya
Shureim yai shiru yana jin yadda zuciyansa kebugawa , tareda so da kaunar Aneesa
Agefe guda kuma wani yanayi yake tsintan kansa ciki nabacin ran auren Ayshat da za'a lika masa yau , wanda yake jin inama da cikar burinsa ne Aneesa , dabazai iya misalta halin farin cikin dazai shiga ayau dinba
Lokaci nata tafiya batare da shushun yayi yunkurin koda motsawa daga kwancen dayake ba , bare asaka ran zai tashi yashiga wanka
Wayoyinsa dayasan zaa damesa gaba daya yayi switching off din su ,
Already baima bude kofar part dinsa ba , sai yanzu datakeji anata knocking tamkar zaa balla kofar
Afusace yamike ya bude kofan 4 eyes sukayi da Dr sudais , wanda yasha wanka cikin fararan manyan kaya , sosai yayi kyau sai zabga qamshi yake
Still yayi yana karewa shushun kallo ganin singlet da boxer kadaine ajikinsa , da alaman ko wanka baida shirin shiga gashi harsun fara samin baki masu zuwa daurin auren kasancewar 2 ne
Gashi har 1 tayi wani uban harara ya zabgawa shureim din , kafin yaraba ta gefensa yawuce batare dayace dashi cikanka ba
Kai tsaye bathroom din cikin bedroom din shushun Dr sudais ya nufa , byn ya zare babbar rigan dake jikinsa ya aje
Ruwan wanka yatara masa kafin yafito yana fadin "dallah Mallam katashi kashiga wanka lokaci natafiya , banson iskancin banza tun dazu uwar me katsayayi , inata kiran line danake da hope din samunka tunda ka kulle wadancan amma line busy
Bai wuce kana waya da wancen yarinyar bako , tana batama lokaci da kissarsu ta mata kamance uban mutanen dazaka tara ko "
Da shushu yaje yai wankan yana fitowa ya tadda har Dr sudai yafito masa da kayan dazai sa , wanda sak iri daya suka dinka banbancin zaren da akai dinkin ne kawai
Sosai shureim yai masifar kyau cikin manyan kayan , kyawunsa yake fitowa agogon zallan azurfa ya daura a hannunsa
Kafin yafara feshe jikinsa da turaruka masu qamshin gske , kallon sa kawai sudais keyi yadda yake komi cikin basarwa
Koda suka fito nan mosque na jikin gdn sukai sallah , kafin yaja hannun shushun zuwa gurin momy
Gd yacika dankam da mutane da dakarn mata 'yan uwa da abokan arxiki , haka sukai ta ketawa duk inda suka wuce sai ansake kallon shureim aji domin yayi kyau naban mamaki, yafito angon sak cikin karfin hali yake ma kowa murmushi domin danne damuwar dake zuciyansa , kodon momy tayi farin ciki
A bedroom dinsa suka sameta taci ado tamkar yarinya karama, babu mai dubanta yasha itace tahaifi shushun sai dai ace ko kaninta ne
Cikin sauri tawaremai hannuwanta yakariso ta rungume abnta , qawayen ta su hajiya rahma suka dauki tafi
Kafin asakar musu ruwan flash bakin momy yaki rufuwa , Dr sudais shima kallon sha'awa yakebinsu dashi dashi
Sosai shureim ya nuna farin cikin sa ajikin momy sai smiling yake faman zabgawa ana daukansu pic
Kafin daga bisani su fito domin saura baifi mintuna 30 ashafa fatiha ba ,
Karfe 2 dot dubban mutane manyan kasa da hanshakan 'yan kasuwa suka shaida daurin auren shureim da Aysha cikin sadaki 500k
Daganan nan kuma aka rankaya zuwa babban hotel din da za'a gabatar da reception ,
Duk wanda yadubi manyan aminin junan Alhaji shu'aib da Alhaji Adam zai tabbatar da irin farancikin dasuke ciki awannan rana
Byn daura aurene aka gabatar da gagarumar walima ta mata zallah a gdn su Ayshat din
Hazikar malamar da aka gayyato wato malama ummy shatu , tayi matukar kokari guriin fadakar da mata yadda zamantakewan aure akeso yakasance ga ma'aurata cikin dinbin ilimi da wayewa
Ta tabo dukkanin muhimman bangarory da mace yakamata takula dasu , agdn aurenta mussaman bangaren tsafta da kula dakai , kulada shinfidar miji tareda muhimmancin biyayya ga mijin dakuma girmama iyayensa
Kulada tsaftar gd , jiki dana shinfida zuwa tsaftar abnci , dole mace tasami cikakkiyar kwarewa da wayewa akan wadannan,
Ummy Aysha tacigaba zabga wa'azi mai kashe jiki wanda yasa Amarya Aysha keta faman kuka , a lokacin ne tasake jin cewa ashe jan aikine akanta wanda dole saita saka hakury da juriya sannan tafiyar zata yiwu
zuwa yamma ne aka gama shirya amarya cikin shiga ta alfarma , zuwa bangaren Abba dimin yimata nasiha kafin awuce da ita gdn ta
Sosai yai mata fada da nasiha masu ratsa zuciya daga karshe yasamata albarka
Gurin umman ta aka maidota wacce takasa cewa komi suka qanqame juna suna kuka gunin tausayi
Sai 'yan uwantane sukai ma Ayshan nasiha da kyar aka zare Ayshat daga jikin momy
Yusrah wacce tagaji da haduwa cikin ashoebin laces dasukayi na qawaye itace ta taho tarike hannun Ayshan tana rarrashi har gurin da convoy na motocin daukan amaren suke
Nan aka saka Ayshat atsakiya wata qanwar umma na gefe guda , yayinda yusrah ke rikeda Ayshat din wacce har zuwa lokacin kuka takeyi mai taba zuciya
Gaba daya tagama karyar da zuciyan yusrah wacce lokaci by lokaci take dauke hawayen dake fita a idanunta
Har aka isa maitama inda zaa fara damka Ayshan hannun momy , sai andawo daga gurin gagarumar Dinner da momy tashirya kafin za'a kaita gdn angonta dake sun city
Sosai aka karbi amarya cikin karramawa da mutuntawa , momy rasa inda zata saka Ayshan tayi sbd matukar farin cikin datake ciki
Karfe 8 aka fara tafiya gurin dinner din
Amarya Aysha tasha make up daga kwararriyan mai make-up din da momy tadakko ,
Yayinda tafito taiwani irin kyau cikin weeding gown da THE CICADA suka fito da ita fadin irin kyan datayi abn sai wanda yagani
Qamshi kuwa dake fita ajikinta abn sai wanda yashaka , waya sudais yaiwa cwtyn sa yusrah akan gasu awaje kasancewa duk angama kwashe qawaye
Sukadai suka rage da Amarya sai momy da qawayenta dasuketa shirin fita suma
Hannun Ayshan cikin na yusrah wacce itama tagaji dayin kyau suka fito , kallo daya shureim yai musu wanda yake sanye cikin manyan kaya white anyi aiki daxaren dinki light brown
Color din wedding gown din Amarya wacce akayi anfani da cream an light brown , sosai kuma ya amshi fatarta
Tunda ya dauke kai baisake waiwaye inda suke ba , illah ma wayansa daya zaro yana latsawa shiko sudais Gaba daya ya shagala akallon yusrah wacce shiganta yagama tafiya da zuciyanta
Shiyayi saurin fitowa yabude back seat Aysha ta shiga , kafin yusrah takoma front seat ta kame idanun sahibin nata nakanta
Yayinda bugun zuciyan Ayshat yakaru wani irin qamshinta dana shushun ne yahadu guri guda yabada wani irin qamshi mai masifan dadi
Saidai takasa sakewa tanaso ta kalli fuskansa amma tana tsoran suhada idanu , babu wanda yatankawa juna tsakanin shida ita
Sunyi nisa suna tafiya inbanda yusrah da sudai daketa soyewansu babu bai cewa uffan cikin Amarya da angon
Kiran Aneesan sane yashigo wayansa cikin zumudi ya daga wayan yana fadin "hello my pretty daga bangaren Aneesa tafara zubamai shagwaba waiya turo mata pic dinsa taga wankan da yayi na zuwa dinner din
Hade face yayi cikeda narke murya tamkar wani karamin yaro yayi mgn" haba my precious wai harkin daina kishinane kike fadin wannan mgn , ni inanan xuciyata nagareki amma harda wani cewa inturomiki pic "
Ko meta fadi masa oho sai wani dariya shushun yayi yana fadin , I luv u my pretty oya tell me mgn dazai kwantar min da mind dina inta recalling har zuwa muyi waya anjima
Kometa fadi masa yai kissing wayan kafin ya aje yana kokarin juyawa ya kalli fuskan Ayshan yaga yanayin datake ciki
Kaman tasan nufin sa taki dagowa da kanta wanda ke kasa , zuciyanta tamkar zai faso kirjinta haka takeji
Wani masifan kishi da tsanar Aneesa ke mamaye zuciyanta , yayinda datake tausayin kanta nahalin dazata shiga naganin wulakanci a gdn shushu
Tun yau yafara waya da ita agabanta babu ko karan ganin yau aka daura musu aure, tabbas ta amince ya shureim bayi kaunarta
Wasu hawayene takeji suna kokarin taho mata tana dannesu don gudun bata kwalliyan fuskanta , sai dai duk iya yadda tayi kokarin ganin basukaiga xubowa saida suka xubo
Batare datayi yunkurin sa tissue din dake hannunta ta daukesu ba , Daga yusrah har sudais basuji dadin yadda sudais ya amsa wayan Aneesa ba
Domin duk wanda yaga yanayin yadda akai wayan yasan don aci fuskan Ayshan ne , sam yusrah tadauke wuta jitakeyi tamkar itace akama wannan cin fuskar , tabbas dolene qawarta saitayi hakury takoyi danne zuciyanta matukar salon da ya shushun zai dauka kenan naci mata fuska don ya nuna bata gabansa kome?
Har suka isa gurin babu wanda yasake cewa uffan cikin yusrah da Dr sudais da zuciyoyinsu yagama baci da abnd shushun yayi
Sudais da yusrah suka fara fita suna jiran fitowan ya shushun da Ayshat, wanda kaman jira shureim yake su fita Ayshat na kokarin fita sai jitayi yajawo hannunta
Tareda matse yatsun hanunta da karfi cikeda mugunta, hakan yasa Ayshat sakin wani wahalallan kara
Tana mai duban fuskansa tuni wasu hawayen sun zubo mata , wani makirin smiling yasakar mata kafin yakai bakinsa saitin kunninta har kuma zuwa lokacin bai daine murje mata yatsuba
Kirjin Ayshat tamkar zai fado sbd bugawa , gawani rawa dajikinta yake tamkar mazari ,
Jin saukan voice dinsa tayi yana fadin"hey Amarya ina miki murna da shigowa rayuwan shureim , biyayyan ki da jajircewanki wajan ganin kin cika burin iyayenmu abune xa za'a jinjina miki
Saidai inaso kisani bazaki taba sauya zuciyan shureim ba , shureim Aneesa kadaice cikin xuciyanshi
Don haka saiki shiryama zama da mutumin dazuyansa kefarautan samin cikar burinsa wato my pretty ,
Sannan wannan hawayen dakike xubarwa donnayi waya da rabin raina , kadan kikagani wannan somin tabine so karki wani far a damuwa kinji ko qanwata"
Yakarishe mgn yana sake mata yatsu byn ya murzasu dakarfin gske , awahalce tayi wani kara kafin tayi kokarin ficewa daga motan , tanajin zuciyanta na mata zafi yusrah ce yakariso da sauri tana fadin
"Sorry Ayshat kada kibari bakaken maganganunsa sufara tasiri akanki tunyanzu , dole saikin jure ahnkl ta dauke hawayen dake fuskan Ayshan , batare da tabari kwalliyan yabaci ba
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu棣冩瀳
*28*
Karisowan shushu kusada su ne ya tsaida mgn da yusrah keson sake fadi, batare da yace komiba yariko hannunta
Suka fara takawa har suka isa inda qawaye ke jira wanda zasu shiga da Amarya, duk wanda yaga yadda shushu ke zabga smiling da yadda itama Ayshan take smiling zaiyi zaton wasu masoya ne masu tsananin kaunar juna
Bakin momy yakasa rufuwa sanda tayi tozali da tilon d'an nata , da Ayshan wacce akullum zuciyanta ke kara natsuwa da ita amatsayin surukan datake tunanin zata kula mata da shushun ta
Gury yayi gury antara matan manyan mutane , sosai dinner din yaqayatar da duk wanda ya halarci gurin
Koda aka fito filin rausayawa karkuso kuga yadda abokan ango dashi kanshi suke ma Ayshan barin kudi ,
Wanda shi shushun yanayi ne don yafaranta ran momy , yakore duk wani shakku cikin zuciyanta ,
Sbd yagama tsara Irin zaman pretending din dazasuyi da Ayshan, wanda momy bazata taba gano komi game dashi ba, har zuwa lokacin dazai mallaki abar kaunarsa Aneesa
Koda aka tashi dinner sosai Aysha ta dage akan saidai sudais yafara komawa da ya shushu , domin bazata sake shiga motar dayake cikiba
Tun suna ganin kaman wasa take har suka fahimci abn nata dagaske takeyi , duk kuma wannan darun da akeyi ya shureim din yadade dashiga mota sukadai yake jira
Sunacan suna ba Ayshan baki akan tayi hakury amma fir taki , ganin shirun yayi yawa yasa shushun fitowa ahnkl yake takawa har zuwa inda suke tsaye
Yusrah na ganin sa tafara fadin "yawwa ya shushu kazo ka lallashi amaryan mu wai cewa tayi bazata shiga mota mukoma kamar yadda mukazo ba
Bai jira komi ba kawai gani sukayi ya fincikota yana ja , yayinda Aysha tsananin takaici yasata fashewa da kuka , tarasa miye yasami brain din ya shureim yake mata wulaknci irin hakan
Ganin yadda take neman tirjewa yasashi daukanta cak zuwa motan , yusrah da sudais dariya sukeyi sosai suna mamakin halin shureim
Koda yadireta a motan wani tsawa yadaka mata yana fadin , will u shut up kosaina bige bakin , uban waye bawanki dazaiyi sahu biyo gurin daukanki?
Ok sbd kinga suna lallabaki shine kike samin daman kawoma mutane raini ko , dacen wani gulman yasa kika biyo mu aida tunda fari kinyo motanki daban ne , yakarishe mgn yana jan wani dogon tsaki
Hannunta daya damke ta fisge dakarfin gske , kafin tasanya idanunta cikin nasa wanda suke zubar da hawaye tana fadin" enough ya shushu maganganun sun isheni hakanan ,
Wlh bawai kafini baki bane ko kuma tsoronka nakeba, sai dai ina baka girmane amatsayinka na yaya kuma miji agareni , wanda Allah yasanya aljannata akarkashin kafanka , bacin haka wlh ya shushu dana gwadama kaima baka gabna kaman yadda nasan zuciyanka tayi nisa akan wata can daban
Kasani nima zuciyata namiji daya nariga na mallakawa ita , wanda banajin har adauki numfashina zan iya daina kaunarsa ,
Takai karshen mgn tana murguda baki cikeda tsiwa tamkar ba Ayshan danasani mai kawaici da kauda kai ba ,
Baki sake cikin tsananin mamaki shureim ke kallonta , gaba daya yakasa furta komi lallai shi anriga angama jawo masa raini , gawani masifan jin dacin mgn ta dayaji nacewan dason wani zata mutu , haka kawai yakeson sanin to waye wannan din ?
Sai dai kozai mutu dason jin haske akan hakan bayajin zai iya budan baki yasake mgn ayanxu , da zuciyansa tagama baci dajin zafin kalamanta
Shigowan su yusrah yasake rufe bakin shushun batareda dayayin yunkurin maida raddi ba ,
Tunda suka tafara tafiya banda yusrah da sudais dake hiransu kasa -kasa , babu mai cewa uffan saima lokaci -lokaci da Ayshan kesakin tsaki wanda hakan bakaramin kona zuciyan shureim yakeba,
Gani yake gaba daya tagama rainashi shizata tasa tanama tsaki , duk ya kosa su sauka don tsananin zafin da zuciyansa kemasa
Direct unguwar sun city suka nufa gdn shushun , Wanda katon gd ne nagske yamallaka masa halak malak ne yazauna da iyalinsa
Koda sukayi parking yusrah tafara fita yayinda tazagayo ta budema Ayshan kofa domin tafito
Sai wani harara daya shureim din yaimata yasata saurin ja baya , tana danne dariyan dake son kwace mata
Gaba sukayi can da sudais suna hiransu tamasoya , yayinda Ayshat tayi yunkurin ficewa daga motar tana jan tsaki
Hannu yasa yajango riganta da karfin gske wanda saura kadan yafada bisa kirjinsa, idanunsa harsun sauya kala sbd bacin rai yake mgn
"Ke wai waye tsaranki dazaki tasa kinama tsaki byn kingama rashin kunyanki ban kulaki bako, to kisani yanzu kina karkashin ikonane zan kumayi maganin rashin kunyanki , kuma mgn kina son wani wannan keya shafa domin kinfi kowa sanin bakya gabana , inada wacce nake tsananin so
Wani tsakin tasake ja batare data ce uffan ba , takaicine ya ciyoshi har baisan sadda yajuyo da fuskanta yana jifan ta da mugun kalloba
Kafin yasa hannu ya bige bakinta yana fadin " idn kika sakemin tsaki wlh sainayi miki abnd bazaki sake yunkurin yimin tsaki agabana ba , nonsense kawai
Aiko yana sakin ta tasake jan wani dogon tsakin tana fadin , kayi duk abnd kaga dama ya shushu domin nagaji da salon wulakncin ka
Da karfi yasake janyota wannan karon saida tafado bisa kirjinsa ,ga mamakinta bakinsa yake kokarin hadewa danata
Duk yadda taso kwace kanta tagaza yin hakan domin karfin ba daya bane, sosai yashiga tsotsan bakinta cikeda mugunta kafin ya lalubi harshenta yaciza da karfi
Wanda yasa Ayshan kusan sakin fitsarin tsabar azaban daya xiyarci kwanyan ta , tuni hawaye sunfara gudu Kafin yasake yana fadin
"Kisake gwada yimintsaki kigani inban tsinke harshen ba mara kunyar karya kawai oya get out tun banyi ball dake cikin motar ba"
Wannan karon jikin Ayshan gaba daya rawa yakeyi , tagama tsorata da ya shushun gawani radadi da harshenta kemata
Cikin saurin kaman zata kifa tafice amotan tana share hawayen fuskanta , gashi rigan jikinta tahanata saury da kyar ta isa inda take hango su Dr sudais da yusrah atsaye
Hangota da baby yusy tayi yasata saurin tahowa ta kwashe mata rigan tabaya suka fara takawa xuwa cikin gdn
Da bismillah tasaka kafarta ta dama cikin dakinta , harxuwa bedroom dinta yusrah takaita , sauran frnds ne suka cika dakin dawasu 'yan uwan Abba da momy
Su shukrah dange ne suka shiga tsokanarta , wanda har suka gama Aysha babu bakin mgn , domin shushu yakasheshi murus dasalon muguntarsa
Yusrah ce tazame tayi waje domin suyi sallama da hubbynta kafin su wuce
Koda tashigo ta tadda Ayshan ne bisa pray mat tana gabatar da shafa'i da wutury , koda ta idah kan gado ta dare tayi kwanciyarta
Batare data shiga cikin hiran da qawayen nata keyiba , wanda rabin hiran zancen haduwan shushun da dacewan da sukayi da Ayshan su surayya keyi
Lumshe idanunta Ayshat tayi tamkar bacci tafara , wanda azahirin gsky zuciyanta tayi nisa gurin tunanin wace irin zama zatayi da ya shushun
Duk sanda sunan Aneesa yafado ranta sai gabanta yafadi , yayinda wani kishi kan rufe zuciyanta kaman ayanxu kaf wayan da shureim din yadingayi da Aneesan kedawo cikin brain dinta
Tamkar ayanzu yake amsa wayar haka takeji cikin zuciyanta , tabbas tagama amincewa Aneesa tagama sace zuciyan ya shureim
Wasu siraran hawayene ke fita daga idanunta , daxata iya yakice shushu cikin zuciyanta tabbas datayi hakan kodan tahuta
Sai dai duk irin abnd yake mata sonsa ma karuwa yake cikin ranta , mussamman ayanxu da takeda tabbacin yaxama mallakinta
Gaba daya Ayshat awannan Daren tayi baccine cikeda mafarkan ya shushun wanda tana rasa gane kan gadon mafarkin
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*29*
Washegary ne budan kai around 9pm anwatse tas daga gdn amarya, Daga ita sai yusrah itama din momy ce tace tazauna idn angwayen sun shigo saita koma gd
Hakan yasa yusrah kama hannun Ayshat suna zagaya dakunan, wanda kusan 4 bedrooms ne da parlour har kala 3, banda part din shushun wanda basuyi ma karanbanin zuwa ba
Aysha tajinjina wa Abban ta takuma hakikance itadin 'yar gatace, domin ankashe mata dukiya fiyeda tunanin mai karatu ,
Byn sungama ne sukai masauki anan falon dayake dagashi sai bedroom din Ayshan, hira sukeyi da yusrah wanda rabin hiran tana karfafa guiwan Ayshat din ne akan , takasance mai hakury da kauda kai sannan tayi iya kokarinta gurin ganin ta kyautata ma ya shushun
Basu shigo ba sai around 10 su biyune kacal daga shi sai Dr sudais , koda suka shigo tun akofa suke jin tashin qamshin turarukan wuta masu azabar qamshi
Har suka danna kansu a katon main parlor din wanda yagaji da haduwa , anan sudais yayi masauki bisa 2 seater
Yana duban shushun dake wani faman yatsina , yana fadin "to mallam saika fito da amarya musayi baki ko
Wani harara shureim din ya aika masa kafin yafurta " saika kira babyn ka ai don inajin suna tare domin momy tace kaine zaka sauke mata ita gd , das y ma nayi kokari muka shigo yanzu "
Sudais baisake furta ko kalma 1 ba ya ciro wayansa yana kiran line din yusy, Daga wayan tayi tana narke murya
Bata dauki lokaci ba sai gata afalon dasuke zaune , duban ya shushun tayi tana fadin
"Ya shushu ina yini "
Harara yabita dashi batare da ya amsa gaisuwan taba , ganin hakan yasa ta dubi hubbyn nata tana gayar dashi
Wanda yake binta dawani mayen kallo yake amsa gaisuwan , tareda fadin "my cwt ina amaryan tamune plxx taho da ita mugaisa tunda wannan dan iskan bashida niyan tashi "
Murmushi tayi tajuya zuwa taho da Ayshan wacce tayi mirsisi tace babu inda zata fito , hakan yasa yusrah yin zuciya tadauki jakarta tana fadin"ok toni nayi nan Allah bada zama lfy yahada kanku akularmin da big brother na plxx"
Ganin da gske yusrah tafiya zatai yasa Aysha mikewa cikin sauri byn tagyara lullubin jikinta ,
Aparlor tacin musu tsaye da sudais da alamu sallama sukeda gogan nata , wanda ya hakimce cikin kujera
Kallo daya tai masa tadauke kai yana sanye cikin riga da wando na wani hadaddan material wanda yasha dinki , yayi kyau harya gaji sai dai fuskan nan sam babu walwala
Ahnkl taja kafa ta isa inda yusrah ke tsaye , sunkuyar dakai tayi tana gaida Dr sudais ya amsa yana tsokanar ta ,
Rafar 50k ya aje mata wai nasayan baki kafin suyi mata sallama , tana rikeda hannun yusrah suna hawayen rabuwa da juna , da kyar suka rabu Aysha ta juya zato koma zuwa bedroom dinta
Batare data sake kokarin koda kallon side din daya shureim din yake ba , wanda keta faman danna waya abnsa
Keh! Taji ya ambata hakan yasata cigaba da tafiyanta, tana gab da wuce cikin parlon taji yafurta"keh Aysha bakiranki nakeba "
Cak ta tsaya tana tunanin tajene kota yi tafiyarta , jim kadan tayanke shawaran komawa cikin parlorn
Guri tasamu tazauna batareda datace uffan ba, hakan yasa shima ya cigaba da danna wayansa , sun share tsayin mintuna kafin ya aje wayan yana fadin
"Ke har rashin kunyan taki yakai ana kira kinajin mutane ko, alryt toki sani ni anan gdn bazan dauki raini ba kijina ,
Zaman aure kikazo yi dolene ki aje duk wani jin kai naki da rashin kunya , sannan kishirya yadda zaman zai kasance domin kinfi kowa sanin inada wacce nakeso ke baki gabana,
Inaso kisani a idanun momy da 'yan uwanki kadai zan iya daurewa in nuna musu cewan kedin matata ce , basai nayi miki bayani mai zurfiba nasan kinfahimci abnd nake nufi
Sannan ko yusrah ban yarda tasan sirrin zaman da zamuyi ba , inkuma kika sanr mata wannan damuwanki ne
Sai mgn my one and only dina wato my pretty inaso cikin next month agama mgn komi domin insami cikar burina ,
Ina fata zaki bani hadin kai ki kuma jure zama da mutumin da zuciyansa sam baya kallonki amatsayin mata , kaman yadda kike fadin kema wani banzan ne cikin mind dinki ko "
Yakarishe mgn yana mikewa domin zuwa part dinsa ya watsa ruwa , gaba daya muryan Aneesa kawai yakeson ji kozai sami natsuwa ,
Harya kai bakin kofan ficewa daga parlorn ya juyo yana fadin , "o ki kwashe wadannan kayan nakine idn bakya bukata kuma saikisan abnyi dasu "
Aysha wacce takejin tamkar zuciyanta tafado don takaici , da kyar ta iya mikewa batare data bi takan ledojin dake zube bisa center table din dake parlon ba sai kudin da Dr sudais ya aje tadauke
Tayi bedroom dinta kai tsaye bisa bed tayi masauki , tanajin wani zafi cikin zuciyanta , ko yaushe ya shushun zai daina gasa mata mgn akan wata banza can oho ,
Wannan karon bata yarda tazubar da hawayeba sam , sai dai zuciyanta namata zafi matuka tareda jin kishin Aneesa sosai cikin zuciyanta
Kayan jikinta tacire zuwa na bacci tayi kwanciyanta , byn tayi addua ta shafa tayi light off
Sai dai sam baccin yaki yazo illah tunane -tunane dake addaban zuciyanta , tana jin dayanzu auren soyayya sukai da shureim da yananan yana tarairayanta ,
Amma gashi yanzu ita kadai kwance saima jinyar kalamansa masu zafi da zuciyanta keyi , hakika auren maso wani babu komi cikinsa illah bakin ciki da takaici
Sai dai babu yadda ta iya domin bakin alkalami yariga yabushe , tunda har gata cikin gdn sa amatsayin mata , ranan dai sai bacci barawo yasace Ayshan
Washegary saida ta makara sallan asuba, byn ta idar tagama su azkar dinta da karatun qur'an ne , tasake komawa ta kwanta bata farkaba sai around 11
Hakan yasa cikin sauri ta fada bathroom tayo wanka , byn tagama ne ta dauro alwala ta fito
Saida tagabatar da salatul Dhuha kafin ta nufi gaban mirror domin kintsa kanta
Kwalliya sosai tayi byn tasake shafe dogon gashin kanta da mayuka masu azabar qamshi, sosai take shafe jikinta da turaruka masu sanyin qamshi
Kafin ta nufi qaton sif dinta wanda already yusrah dasu sury sungama shirya mata kayanta ciki , wadanda dukansu sabbi ne fil kama daga English wears zuwa dinkakkun kaya
Hannunta yakai kan wani shegen lace ne mara nauyi , wanda akai masa pitted gown sosai rigan yazauna ajikinta tamkar dama ajikin aka dinka kayan
Tayi kyau harta gaji batayi yunkurin daura dankwalin ba, saita rikoshi ahannu hadeda phone dinta
Yunwa takeji sosan gske tana fitowa babban falon , kallon dazatai center din dining ta hango mutum nata faman kora ruwan tea , ga kulolin anbci nan zube da alamu momy ce ta aiko da breakfast
Hakan yasa Ayshat itama kai tsaye ta nufi wajan cikin takunta na nutsuwa,koda ta isa kujeran dake facing dinsa taja tazauna
Kafin tadubesa tana fadin"ya shushu gud morning"
Bata damu daya amsaba ta dauki plate tafara bude kulas din data gani , abncine har kala 3 chips ne da Pepe soup din kayan ciki, sai waina da miyan taushe wanda yaji naman kaza
Sai flask mai dauke da ruwan zafi da kayan tea difference color, hakan yasata xuba chips din hadida pepe soup din tanaci ahnkl
Sam bata kuma koda kallon inda yakeba cin abncinta take cikeda nutsuwa , shikam shureim kaman yadda bai amsa gaisuwanta ba haka baiko kalli inda takeba
Illah qamshinta dayake shaka wanda yakejin sa harcikin ransa, kasance wansa ma'aboci son qamshine shi
Saida yagama shanye tea dinsa kaf sannan yayi yunkurin tashi , wayansa ne yayi kuka hakan yasashi kara wayan akunni byn ya koma ya zauna
Yake fadin "hello my cwt mom gud morning"
Banji me ake fadi adaya bangarenba illah shushun dake fadin
Yes momy lafiya lau muke gamata kusa dani muna break , wani shagwaba yake xubama momyn wanda yajawo hnkln Ayshat kansa
Tana dubansa bakaramin sha'awa yabataba sai yanzu takaremai kallo, yana sanye cikin farar shirt sai ash din wandon jeans gashinnan ya kwanta luff sosai yaimata kyau bakadanba
Saitaji wani sabon sonsa yanasake mamaye zuciyanta ,
Ganin yana kokarin maido dubansa garetane yasata saurin dauke kanta , tana kurban ruwan shayinta ahnkl
Wayan hannunsa yake mika mata yana fadin "ga mom zaku gaisa abnd yace kenan"
Ahnkl Aysha ta kallesa sukai 4 eyes harara yasauke mata kafin takai hannunta daya sha lalle ta amshi wayan , tana wani smiling takara wayan akunni tabar shureim da kallonta
Gaida momy takeyi cikeda girmamawa , kafin tacigaba da mgn cikin shagwaba tana fadin"bakomi momy saidai kadaici plxz momy kice ma baby tazo muyi hira , kome momyn tasanar da ita tawani sake narke murya tana fadin"kai momy Allah bakomi nidai kawai tazo "
Shureim takaicine da mamakin Ayshan yadda take wanima momyn shagwaba ko kunyan idonsa yacikasa gashi abn haushi momyn saiwani biye mata takeyi
Mikomai wayan tayi byn sungama mgn da momyn , inda suka rabu zuwa anjima momyn zata turo driver da yaran dazasu dinga mata aikace -aikace
Karban wayan sa yayi yana jan tsaki yabar dining din , yayinda Ayshan tabishi da kallo tana kada kanta
Ita takwashe komi zuwa kitchen ta wanke kayan dasuka bata , ta fito zuwa parlor ledojin kajin jiya da tarkacen su fresh milk din takwashe tazuba a frige
Ledan kajin ta kwasa zuwa kitchen oven ta kunna tayi warming kajin , ta juye a tray ta fitodashi mayafi ta dauka tanufi waje
Mai gadi ta hango hakan yasa tai masa alamun yataho da hannu, cikin sauri yataho tareda xubewa yana gaidata
Sam sai Aysha taji wani iri domin dattijone wanda saidai suxo tsara daya da Abban ta, hakan yasata saurin fadin"haba baba aini yakamata indurkusa nagaidaka daga yau kada kasake hakan , ga wannan baba kuci kaida sauran ma'aikatan ko"
Mallam garba yadubi Ayshat cikeda farin ciki yayi godia byn yakarbi karamin tray din hannunta , yacigaba da fadin "Allah yai miki albarka yabaku zaman lfy hajiya "
Har Aysha tajuya mallam garba bai daina yabon kyawun halinnta da saukin kanta ba , ya yaba da tarbiyan data samu da sam bata kasance cikin yaran masu kudin dake wulaknta nakasa dasu ba"
Koda takoma sake saka turarukan wuta tayi a burner , ko wani lungu da sako yadauki qamshi , bedroom dinta takoma ta gyara shima tawadata shi da qamshi mai ratsa zuciya
Asalin main parlour din tadawo ta kunna kallo tanayi byn tayi ale-ale bisa 3 seater, kallonta takeyi hnklnta kwance
Sam bataji fitowansa ba illah ganin mutum datayi akanta , fuskansa ahade yake fadin"hey gal kitashi kije part dina akwai kayana cikin trolley's ki shiryamin su cikin sip
And u make sure kinyi yadda yadace domin bazaman kallo kikazo yiba Right? "
Yana mgn ne cikeda gadara dakuma bada umurni , yana kuma gama fadi yayi gaba abinsa yabar Aysha sake da baki , tana mamakin ya shureim , wato duk wannan abn yanayi ne donta gane bayi kaunarta kome?
Imma hakan ne aransa zata shayar dashi mamaki , imma yanayi donya bata ranta ne zata nunamai hakan baya gabanta ,
Jin tashin motansa da fice wansa yabata kwarin guiwan mikewa , tanufi kofar dazai kaita part din nasa
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu棣冩瀳
*30*
*********
Rufaida da Neesa ne suke hira adakin Aneesan around 11am kenan, zuwan bazata taima Aneesan domin kwana kusan 10 kenan rabonsu da juna
Don haka Rufy tayi kewan Neesa sosai Rufaida ce ke duban Aneesan wacce kesanye cikin riga body hug wanda yakama matuka , sai skat shima yamatseta tareda fitar da suranta muraran
Kafin tayi mgn tana fadin"bakin fama ya kuke ciki da ango ko ince shushunki ne, "
Sosai Aneesa tabata rai tana fadin "hmm kedai bari bakin rai idn zuciyana natuna my luv angon watane ayanxu sam sai inji ko ruwa nakasa sha sbd tsananin kishi ,
Amma idn natuna shushuna nikadai ce aransa sai indanji sanyi, wlh my bakin rai sam shureim bayason yarinyar na kara gasgata hakan ne ajiya
Domin kusan raba dare mukai muna taredashi through phone , kinga mai sabuwar amarya guda inda tana gabansa kema kinsan hakan bazai faruba,
Kuma wani abn dadi sam bayiso idn muna tarema ina masa zancenta , kedai kitayani addua Allah yasa ayi namu auren cikin gaggawa wlh na matsu mukasance da my shushu"
Tunda tafara mgn Rufy ke jefa mata harara afakaice, cikin zuciyanta tayi kwafa tana fadin zaki fadi shushunki yarinya
Afili kuwa wani kafirin dariya tayi tana fadin woo tawan kice dai ke keda zuciyan shureim aji gsky kefa mai sa'a ce sugar na
Takarisa mgn tana daura hannu akan kirjin Aneesan , lokaci guda tasake matsawa suka manne da juna cikin salonta na kwararru aharkan tafara laluban bakin Aneesa
Wacce sam batayi gardaman mika wuya ba domin itadin ma abukace take da Rufaida, kankace miye sunfada wata duniya na faranta ran junansu
Byn sungama sheke ayarsu ne sundawo cikin hayyacinsu , Aneesa tafara yin wanka ta gyara jikinta , yayinda ita Rufy kayan kawai tamaida ,
Sam bata son yin wanka inba taje gd tanutsu bane , kiran Aneesa akeyi a phone dinta hakan yasata daga wayan cikin zumudi domin ko shushunta ne
Yadda takashe murya tareda narketa suna waya cikin musayan kalaman luv , yasake turnuke zuciyan Rufaida duk da bayaune karon farko da Aneesa tasaba amsa wayan shureim agabanta ba
Amma salon ansa wayan tayau tasha banban da wanda tasaba gani , domin yadda takewa shushun ji Rufy take dama ita take ma hakan akan shinfida da tafi kayatar da ita
Tana mamakin wani irin so Aneesa kewa shureim daya cancanci irin kalamn datake narka masa , dolene ya matk akanta yadda bata iya boye masa tsananin kaunar datake mai
Sun dauki lokaci mai tsayi suna wayan kafin Aneesa tayi hanging up byn tayi kissing phone , lumshe idanunta tayi tsawon some seconds kafin tabudesu akan Rufy
Wacce idanunta kekan Aneesan tana mata wani duba mai cikeda zaki gane bakida wayau
Mikewa tayi tana rataya katuwar jakanta byn tadire ma Aneesa katuwar ledan data shigo dashi wanda Aneesa batayi zaton ita aka kawoma wa ba
Har gurin motanta Aneesa taiwa Rufy rakiya byn tayiwa umma sallama , wacce kefadin"kigaida su umman taki Rufaida "
Kayan data kawomata ta kwasa byn tadawo yimata rakiya takaiwa umma domin tagani, dogayen riguna ne 'yan Dubai da mayafansu , sai turaruka da akamu duk cikin irin kayan da rufin kesamu tsaraba daga iyayentane ta debo mata , domin su kullum cikin tafiya suke iyayen rufin
Godia sosai umma kefaman yi tana fadin"o ni idn kika tashi aure ko ya zaku iya rabuwa da Rufaida wannan irin shakuwa da kukai dajuna "
Dariya Aneesa keyi tana fadin "umma kenan nima kullum cikin tunanin hakan nake domin munriga munzama bakin rai bakin fama"
Takarishe mgn tana kwashe kayan xuwa dakinta wayan dasukayi da shureim yasata jinta cikin nishadi da walwala
Sbd ayanzu zuciyanta tagama aminta shureim nata ne ita daya, bakaman da datake gudun yajuya mata baya domin yasami sabuwar amarya ba
***********
*2* *weeks later*
Cikin sati biyun nan babu abnd ke shiga tsakanin Aysha da shureim illah gaisuwa , wanda saiyayi raayine sannan zai amsa gaisuwan tata ma
Akuma wannan week dinne yakoma aiki hakan yasa Ayshat ketashi tun wury tahada break fast , ta shirya komi bisa dining
Duk da cewa akwai sabon kuku da shureim din yakawo 2 days kenan, wanda sam Aysha bata yarda yayi abnci da ita , ita take dafa abncin daxataci hade dana shushun wanda ta gargadi kukun dacewa koda wasa kada yasake shureim yafahimci ita keyin abncin dayake xama yakwashi gara yana yaba iya abncin kukun batare dayasan oganniya Aysha ke sarrafawa ba
Duk atunaninsa breakfast kadai Ayshan ke hadawa yaci
Yauma kaman kullum tagama hada komi bisa dining already tariga tayi wanka , tana Sanye cikin riga da wando na english wears wanda sukai asalin fito da surarta
Duk yadda ta motsa qamshine ke tashi ajikinta kuma yau dinne karon farko data fara fito da wannan salon
Fuskanta sosai yasha light make up, kara kallon dining tayi komi ta aje yadda yadace illah cups nashan shayine kawai tamanta bata kwaso ba
Hakan yasata juyawa xuwa kitchen din domin ta kwaso , daidai kuma da fitowan ya shushun yana Sanye cikin shigan fita office , axababben qamshinsa duk yagama cika falon
Agogon zallan axurfa dake daure a tsintsiyan hannunsa yaduba quarter to 9 cikin sauri yakarisa zuwa dining
Zamansa yayi dai-dai dajin karan takun takalman da Ayshat tasa, wanda tana taka tiles din suna kara shiya kai hnkln shushu dakallon sashen dayake jiyo takun tafiyan
Idanunsa ne suka sauka akan Ayshat wanda saida yaji wani yam ajikinsa, sakamakon bai taba tunanin zata iya shiga irin wanda kejikinta acikin gdn sa
Ya shagala sosai da kallon suranta wanda baitaba tsayawa yakalla ba , ashe dama haka yarinyar keda jiki tamkar ita tayi kanta? ,
Kirjinta dake tsaye cak cike da dukiyan fulani yafi komi tsole idanunsa , yayi nisa cikin kallon suranta takariso gurin dining din
Hakan yasashi wayancewa yana wani jan tsaki yake fadin"oya kiyi sauri kibani cup mana kobaki ganin nakusa yin late ne yakarisa mgn cikin tsawa"
Ayshat datuni tagane borin kunyan taga irin kallon dayake binta dashi yake , yasata sakin smiling tana fadin"sorry ya shushu aigashi na aje bari intaya ka xubawa tunda ka kusakayi late yayanmu "
Furucinta nakarshe yasashi saurin dubanta , suna hada eyes tayi saurin dauke kanta tamkar ba itayi mgn ba , cigaba da hada masa tea din tayi ta tura gabansa
Yayinda shikuma yake cin soyayyen plantain da egg , tana turamasa cup din gabansa ta mike domin bashi guri byn ta gama tabbatar dacewa qamshinta yacika wajen
Tafiyatake tana juya jikinta cikeda gayya kallo daya yabita dashi , yana kwafa cikin zuciyansa yake fadin "hmm lallai yarinyar nan wannan kuma sabon salon na menene"?
Ganin tana kokarin wuce dining area din tashiga parlor yasashi , daga murya yana fadin" keeh! Ayshat zonan "
Hakan yasa Ayshat juyowa tadawo kusa dashi kadan ta tsaya tana duban yadda yawane hade face, danne dariyan dake taho mata tayi tana fadin "gani yaya shureim "
Aje fork din hannunsa yayi yana fadin"look Ayshat wannan wace iriyar shigan rashin mutuncine wannan kika tsirfo dashi , ko anfada miki nan din gdn kafiraine , ko kina tunanin don kin bayyana wannan banzar surar taki shizaija hnkl na xuwa gareki ?
To dagayau banason kisake maimaita kwatan kwacin irin wannan banzar shigan Right?
Yakarishe mgn cikeda tsawa
Ga mamakinsa dariya Ayshat ta kwashe dashi , cikin dariyan take fadin "Allah sarki ya shushu aibansan shigan danai zai bata ranka ba wlh da banyi
Nima yau kadai natashi inajin mararin sakasu domin nadade ban waiwayi shiga irin wannan ba
Kuma atunanina ba haramun bane don qanwa tasanya irin wadannan kayan a gdn yayanta , mussaman nida nake cin tudu 2 agurinka na matsayin qanwa kuma mata agareka
Kuma koda wasa bantabajin baby tace kataba hanata irin wannan shiganba , kasancewan ta ma'abociya ta ammuli dasaka irin wadannan kayan
Ya shushu kadaina mgn wainayi shigannan ne don inja hnkl ka gareni , koka manta matsayin danake dashi baiwuce nakanwa bace zallah,
Kumama mai mace kamar Aneesa data gana sace dukkanin zuciyanka ya shushu, ai banaji wata mace xata iya janyo hnklnk gareta , so ya shureim kayi hakury kada kahanani saka favourite dina alokacin danake bukata tunda ko anture zancen ni matace to amatsayin qanwa nake tamkar baby agurinka "
Takarishe mgn tana tsaresa da manyan idanunta , gaba daya sai shureim yaji tamkar tarufe masa bakine , yakasa furta komi illah kallonta dayakeyi sam yakasa dauke idanunsa akan mazaunanta wanda hips dinta suka fito tamkar zasuyi mgn
Ganin yashagala akan dubanta yasata yin tafi tana fadin "plxx ya shushu kayi hakury kaji"
Wani uban harara yasauke mata yana fadin "leave plxx"
Hakan yasata juyawa da dan gudunta mazaunanta na kadawa, har shureim baisan sanda yarintse idanunsaba
Yazaiyi da wannan yarinyar karta sake masa wannan shigan cikin gdn sa? Saidai tariga takashe bakinsa baida wani hujja imma yace xai matsa karfa yarinyar tafara tunanin ko tarkonta xai kamashine
Mikewa yayi yafice tana mai adawo lfy ko kallonta baiba illah uban tsakin dayaja , yana fita takwashe da dariya ta nufi dining domin yin breakfast ,
Haka kawai takejin nishadi tana kuma tunanin wani irin wanka zata dauka da yamma ,
Waya tazaro tana dailing number din yusrah , domin tunjiya take samata rai zatazo taji shiru
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*31*
Karfe 4pm na yamma yusrah da Aysha ne a kitchen sungama abnci suna kwashewa a food flask , yusrah dake juye pineapple and strawberry milk shake cikin jug, tana saka ice ta dubi Aysha tana fadin
"Matan ya shushu kina bani lbry sai yayi yaya Dakika gama gayamasa mgn? "
Dariya Aysha tayi sosai tana fadin "wlh baby yakasa fadin komi illah dogon tsakin danasha kafin yabarmin gdn
Kumafa sai kallona yake ke zakiyi zaton baitaba ganina bane, hmmm namiji kenan wlh kuma yanzu nasa kafan saka kananun kaya daganan har shegiyan tashigo ,
Cire kunya zanyi inkoyi tsiwan karfi da yaji tunda nafara dago weakness dinsa"
Yusrah sosai take kwasan dariya harda hawaye kafin ta furta, "badai zaman pretending yace zakuyi ba agaban mutane ku nuna ku ma'aurtane amma da zaran kun kadaice akoma 'yar gdn jiya to aike gaba takaiki tawan
Da wannan daman zaki sami ki shege jikinsa kindai gane ai , Aysha takai hannu suka tafa suna kwasan dariya "
Sun shirya komi bisa dining yayinda kukun yake nasu na gd shida ma'aikata , iyatu Aysha ta kwadama kira daya cikin masu aikin da momy takawo mata , domin ta gyara kitchen din
Itakuma kai tsaye bathroom tashige domin yin wanka, byn ta fito daureda alwala sallah tafara gabatarwa kafin
Ta shafa lotion tananan zaune gaban mirrow yusrah ta shigo tana waya, bakin gado tazauna idanunta akan Aysha dake ta faman shafe-shafe tana yaba kyawun jikinta da irin laushin fatarta,
Cikin zuciyata tana takaicin yadda ya shushu ke wulakanta Ayshan , towai koshi baya dubanta da kyaune , ita a iya hangenta bataga aibun Ayshan ba dahar ya shureim zai kasa karbanta yabata gurbi cikin zuciyanta , domin babu abnd ita Aneesan daya matk kanta zata nunawa Ayshan daya wuce farin fata datafi Ayshan dashi
Itadai Ayshat kokarin fesa roll on take a hammata taji muryan yusrah nacewa"matar ya shushu kinga kayan dana fito miki kisaka muga karyan iskancin wani "
Takarishe mgn tana dagama Ayshan wani fingilwan riga , wanda tsayinsa bazai wuce iya guiwaba idn Ayshan tasakashi
Kuma gaba daya transperant ce rigan wanda komi naka zai zama abayyane yake, yana hade dawani shegen skin tight wandone
Rigan red ne sai wandon yazo black colour, Aysha ta tsurawa kayan idanu tana mamakin yusrah , domin ita a iya abnta bazata iya saka kayan ta tinkari inda ya shushu yakeba,
Kafin tagaika mgn har yusy ta kariso tana mika mata kayan take fadin"dallah ni amshi kinwani saki baki kinkasa mgn miye najin kunyan sakawa ashema bason jawo mijinki kikeba "
Kina sanedai watace zai kawo kuma wacce kikasan tasace zuciyansa , don haka yanzu bakida lokacin wata kunya , lokacine dazakiyi anfani dashi ki sami kidasa wani abu azuciyansa kozaki sami gurbi acikin ransa
Allah yabaki duk wani makaman aiki a hannunki sai dai kawai kiyi addu'a Allah yasaka kaunarki cikin zuciyansa Aysha"
Gaba daya Sai Aysha taji yusrah tabata kwarin guiwa , mgn datayi tabbas itace iyakan gsky kuma dole ne ta aje duk wata kunya tayi abnd zai janyo hnkln shureim kanta,
Domin ayanzu shi halalinta ne babu wani kunya atsakaninsu ,zuciyanta shushu takeso shikadaine namijin daya sace zuciyanta , dolene tayi anfani da damanta ta yadda zata cusa sonta aransa
Karban kayan tayi tasaka tundaga sama har kasa take karema kanta kallo, bakaramin kyau tayi cikin kayan ba
Wanda gaba daya ya fallasa asirin suran jikinta , bama kaman saman rigan inda yafito da kirjinta sosai ,
Red janbaki tasa tayi kyau sosai sai tashin qamshi dake fita ajikinta tako ina, yusrah ta dubeta tasake duba kafin ta furta "masha Allah ta ya shushu wlh kingama hadewa yau banbarin gdn nan batare danaga yadda game din zai tashi , takarishe mgn tana kwasan dariya
Falo sukayi masauki byn Aysha ta tabbatar gdn ta yagama zama tsaf sai tashin qamshi kefita akowani kusurwa,
Kallo sukeyi nawani Nigerian film mai kyau , sosai hnkln su yakoma kan kallon dasukeyi sam basuji shigowansa ba
Saida qamshinsa yafara musu sallama tukun , yusrah ce ta mike da gudu ta kankameshi tana fadin " oyoyo ya shushu"
Shima rungumeta yayi yana fadin "oyoyo baby yaushe kikazo "
Murmushi tayi tana fadin "tun dazu nake ya shushu yau nazo taya amaryanmu hirane"
Peck yabata yana fadin "kin kyauta babyn momy"
Aysha wacce idanunta ke kansu ganin yasaki baby , yasata tashi tsaye sai dai tasami kanta cikin jin matsananciyan kunya
Tamkar takoma tazauna sai kuma tayi namaza , ganin yadda yusrah kemata signing
da ido
Shureim wanda
Sai yanzu yadaura ido akanta , baki sake yake karemata kallo tundaga sama har kasa,
Bai gama shiga cikin mamakin Aysha ba yaga tana tinkaroshi , fuskanta dauke da kafirin smiling wanda har dimple dinta saida suka lotsa
Cikin tsananin dauriya da karfin hali ta rungumeshi tana fadin "welcome my ya shushu tareda manne jikinta anashi "
Saura kadan yasaki jakan hannunsa da wayansa , sbd wani irin hanayi daya ziyarcesa abazata , gawani fitinannen qamshi daya doki hancinsa ,sam taki yadda idanunsu yahadu guri guda
Wannan ne karon farko da mace tafara sanya jikinta cikin nasa, hakan yataka rawa gurin jefa zuciyansa cikin wani yanayi wanda bazai fassaruba
Sai yanzu yatuno da plan din yanda zaman nasu zai kasance, hakan yasashi karfin halin saita kansa
Sake rungumeta yayi yana fadin"my wifey ya gdn nabarki cikin kewata ko ? "
Kokaryn yakiceta yakeyi kozai sami natsuwan zuciya amma sai Ayshan tasake shigewa jikinsa tana fadin"kai ya shushu baga baby tazo tayani hiraba amma duk da haka nayi kewanka my king"
Wani miyau ya hadiye dakarfin gske tareda rintse idanunsa , sakamakon yadda ta manne kirjinta da jikinsa, wani irin shock ne ya ziyarci zuciyansu baki daya ,
Hakan yasa Aysha saurin janyewa daga jikinsa , Sai dai amaimakon ta barshi sai kama hannunsa tayi tana fadin"oya muje kai wanka saika fito ga abnci can Peter ya kammala komi bisa dining"
Kallon side din da yusrah take shureim yayi , gani yayi ta tsura musu idanu hakan yasashi sakin smiling yana fadin "alryt my wifey let's go kinga yadda baby ta kafemu da ido "
Yayi mgn cike da karfin hali gaba daya shi yanzu Aysha tafara bashi tsoronema , sosai ya jinjina ma karfin halinta
Yadda suka jera tana rikeda hannunsa xakayi tunanin irin masoyan ma'auratane masu tsananin son junansu
Dai-dai corridor din dazai kaisu part dinsa tasaki hannunsa, tareda sanya idanunta cikin nasa kafin ta furta "ina fata yadda nayi yayi dai-dai da game din dakakeso afara bugashi ya shushu ?
Kaga wannan kadai zai fara cire duk wani kokwanto azuciyar qanwarka , ina fatan banzake dayawaba? "
Shidai shureim gaba daya komawa yayi tamkar wani gunki , kallon ta kawai yake yana mamakin duk wani acting datakeyi , cikeda confedence dinta sam babu ko digon tsoransa dayake hangowa cikin idanunta "
Bata bashi daman mgn ba ta juya tana kada mai jikinta tabarshi da shakan fitinannen qamshinta daya manne ajikinsa,
Tsaye tayi a corridor din dazai sadata da parlor tana sauke ajiyan zuciya, da shureim zai taba kirjinta a tym din shine zai tabbatar komi tayishine cikin matsanancin karfin hali ,
Shiko sam yakasa motsawa sannan suran Ayshan yakasa fita daga eyes dinsa, ganin komi yake daya faru tamkar amafarki ne yakasance , ahnkl yaja kafa zuwa bedroom dinsa inda yayi saurin tubewa yafada bath room , ruwa ya dinga sakarwa kansa Kafin ya iyayin wanka
Itako Aysha tana isa falon yusrah ta taho da gudu ta rungumeta tana fadin"gsky qawata kinbiyani nasiya wannan scene din domin acting din yayi bakarya "
Dariya suka kwashe dashi Kafin yusrah
Ta rufe bakinta tana fadin"hmm bariga in lallaba inyi gd don idn yafito yasaman hararace zansha shi tamkar nina kar zomon "
Har gurin mota Aysha taraka yusrah kafin tadawo tayi shigewanta daki , lock ta dannawa kofar gudun karma shureim din yayi gigin zuwa yasauke mata wulakanci
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*32*
Byn shushu ya gama kintsawa ne yafito zuwa dining domin cin abnci, cikin zuciyansa yake addua Allah yasa ya tadda Ayshan zaune
Sai dai koda ya fito zuwa parlor TV kawai ya tadda kunne yana aiki, hakan yabashi daman karisawa zuwa dining area din
Abnci ne har kala 3 ya tadda anjera kular farko ya bude mai daukeda jallof din macaroni wanda yaji kayan lanbu,
Sai tuwan semo miyan danyar kubewa, kular karshe Pepe chicken ne wanda ketashin qamshin spices masu matukar dadi
Lemun coconut da lemun zobo ya tadda cikin jug duk ansaka ice aciki, gakuma juice nan duk an aje , sosai yadda aka tsara dining din yau ya birgesa, har yanaji dole yaga peter domin yasake yaba irin kokarin dayake yi , don yana jin dadin girkinsa sosan gske
Tuwan semo din shiya zuba yanaci yana hasko surar Ayshat din cikin shigan daya gigitashi, sam bai taba tunanin yarinyar ta mallaki irin surar dayake so ajikin maceba , musamman abnd yafi birgesa ajikin mace wato breast wanda yake ganin hartafi rabin ran nasa , wadatansu gasu atsaye cak babu alamun rankwafawa,
Samun kansa yayi dason sake dora idanunsa akanta , harya gama cikin abncin bai daina mamakin yadda akayi Ayshat harta iya rungumarsa ba ,
Wani yarr yasake ji ajikinsa Tamkar alokacin abn yake faruwa, bakaramin santin xobo drink din da abncin yayiba, wanda har yakeji dolene yaima peter mgn kullum yadinga hada masa wannan hadin xobon
Koda ya kammala cin abncin waya yazaro ya kira layin peter, yana bashi umurnin yasamesa a main parlor , koda peter yashigo yana zare idanu can ya hango ogan nasa bisa a dining area, hakan yasashi nufan bangaren
Cikin sauri ya zube yana gaida shushun cikin harshen nasara, nan shureim yasake yabamai tareda sanar dashi yacigaba da aiki kaman yadda yakeyi , sannan lemun xobo din yayi mai don haka kullum yana bukatansa matukar zaici abnci a gd
Sosai peter ke ansawa ogan nasa xakayi tsammanin shiyake sarrafa duk abubuwan da ubangidan nasa keyabawa,
Koda shureim yakoma parlor yayi tunanin zai sami Ayshat ta fito , sai dai wayam babu ita hakan yasashi kwanciya tareda canza channel zuwa inda yake bukata yana kallo, jefi -jefi yakan kalli kofan side dinta ko zaiga fitowanta , domin yanason mata kashedi akan irin rungumar datai masa, wanda yajefa shi cikin wani yanayi wanda bazai fassaruba,
Wanda baitabajin hakan ba gefe guda idanunsa na kwadayin sake , ganin kyakykyar suranta domin bakarya shigan datayi yataboshi
Lumshe idanu yayi yana sake hasko yanayin dasuka shiga dazun, hannunsa yarintse wanda Ayshan tarike alokacin datake jansa zuwa part dinsa
Yana tuno irin laushin hannun dayaji wanda alokaci har wani abu kemasa yawo cikin jininsa , tabbas ya amince mace duk yarintarta shu'umah ce 棣冦亙
Ko awashegary sam Ayshat bata yarda sun hadu da shushun ba , tana gama shirya breakfast tayi shigewanta daki ,
Saida ta tabbatar yabar mata gdn sannan tafito tawataya abnta
************
Salman ne da shureim a office din shushun yakai masa ziyara , hira sukeyi sosai kafin salman ya dubi shushu yana fadin
"Waikai ango naga kodan fresh dinnan da ake karawa idn anyi aure kai babu lbry ne"
Nan da nan ya shushun ya hade face yana fadin"to banda abnka ka taba ganin mutum ya angwance da macen da bayaso ? ni haryau bansan dadin auren ba bare har inyi wani fresh din, "
Salman wanda yakafe shushun da ido sam baiji dadin mgn da shureim din yayiba , hakan yasa shima yadaure fuska yana fadin
"Waikai shureim yaushe zaka koyi yima mutum karane ?
Karfa kamance Aysha qanwace agareni , mikake tsammani zanji cikin zuciyata idn kana furta kalman rashin so agareta ,
Haba shushu da anyi mgn kace baka sonta baka ra'ayinta , bakasan naji haushinka alokacin bikin nan ba ko
Duk wasu frnds dinmu saida suka fahimci yadda bakason wannan auren, don girman Allah na rokeka da ka rike Aysha amana shureim, nasan wata tariga ta samin gurbi cikin zuciyanka , amma baidace ko dan darajan amintan dake tsakanin iyayenmu damu kanmu kadinga furta kalman rashin so agareta ba , wannan shirmene wlh guy kakeyi
Kadinga imagining nine akabawa auren yusrah nake wulakantata , ina furta cewa bana ra'ayinta agabanka yazakaji cikin zuciyanka shushu?
Nasani baa ma mutum dole aharkan soyayya but tunda har aure ya shiga tsakani plxx an plxx karka cutar min da qanwa ,
Allah yanuna mana lokacin aurenka da gimbiyar taka Neesa , duk da haryau ni ankimin cikakken bayani gameda ita ,
Salman yakai karshen mgn cikeda zolayan shushun , wanda gaba daya jikinsa yayi sanyi "
Saiyaji kunyan salman yarufeshi tabbas baya kyautawa akan abnd yakema Ayshan, yakuma tabbatar da shi salman din aka aurawa yusrah bazai iya masa wannan cin fuskan akanta ba
Dafa kafadun salman yayi yana fadin"sorry abokina kagafarceni tabbas bana kyautawa , kuma nayi alqawari daga yau koma gaban waye bazan sake furta kalman rashin son Aysha ba ,
Wlh salman laifin xuciyata ce dahar yau takasa aminta da qanwar tamu amatsayin masoyiya , soyayyan Aneesa yarigada yayi zaman durshan cikin mind dina
Amma nayi maka alqawarin rike Ayshat amana kodan infaranta ran momy , yakai karshen mgn yana sakin ma salman din similing"
Salman dinma murmushi yayi yana fadin "kokaifa boss dadai yafi wlh har tausayi Aysha kebani , sbd nasan yadda kake fadi baka sonta har agabanta haka kake fadi, kuma Nasan dole tarika jin dacin hakan cikin zuciyanta
Domin ita macece kasan kuma mata sun tsani namiji yadinga furta musu kalman rashin so karara, don haka kayi ahnkl shureim kada wata rana Allah yajarabeka da kaunarta cikin zuciyanka ,
Aysha she's very innocent tana da hnkl ina fadama wannan badon wai inyabeta don tana qanwata ba, kasan ni kasan halina idn har abu bai minba kowaye nawa bazan boye aibinsa ba, haka duk yadda bansan mutum matukar yanada halin kirki dazan fada tofa bazan boyeba
Da ace tanada wani hali narashin kirki am d first person da zan nuna rashin son aurenku , sbd nasan halin miskilancin ka , so plxx ka riketa da amana karka cire ran wataran zaka iya jin sonta fiyema da yadda kakejin Neesa aranka am telling u wlh
Any way mubar wannan mgn akwai damuwan daya kawoni gurinka mu tattauna , ina cikin matsala shureim"
Shushu wanda gaba daya kalaman salman sun kashe jikinsa, mgn da mom ta taba yimasa take kuma jaddada masa akullum akan Ayshan shine yafado ransa
Fadi yake aransa yazama dole ya koyi boye rashin sonta cikin ransa, yayi kokarin kula da ita kodon momy tunda dai nan gaba kadan zai auro abar sonsa Aneesa, sai dai yana tunanin yadda hakan zai kasance domin sam bayajin ko alamun son Ayshan cikin ransa,
Fuskantan salman shushun yayi yana fadin "matsala kuma tame kenan Allah dai yasa bagurin biye-biyen matanka ne wata taimaka wani abn ba , nifa ina rabaka da neman mata amma haryau kaki ka tuba "
Wani murmushin takaici salman yayi yana fadin.................
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo 棣冩瀳
*33*
Salman ya kwashe kaf abnd yafaru tundaga haduwansa da Afrah harzuwa abnd yashiga tsakaninsu, da alakan dake tsakaninta da Abban sa bai boyewa shureim komaiba
Yakarishe mgn yana fadin "shushu narasa yaushe Abba yazama tantirin mazinaci , har da aje dadiro wlh nikadai nasan yadda nakejin tsanansa cikin zuciyata,
Idn natuna irin nasihan dayakemin akan illan zina , amma gashi yana aikatawa hakan bakaramin sake jefa zuciyata cikin rudani hakan yake ba
Wlh shushu saina kawo karshen alakan dake tsakanin Abba da Afrah, nikadai nasan yadda nakejin yarinyar araina
Shureim wanda idanunsa kekan salman jikinsa yayi sanyi , tausayin salman yarufeshi tabbas yana cikin fitina , ace mutum yafada son dadiron mahaifinsa
Sai dai sam baiyi mamakin alakan dake tsakanin Alhaji Adam da Afrah ba, sbd yafi kowa sanin waye mahaifan su ,
Hakan yasa shushun dafa kafadun salman yana fadin" frnd kaine bakasan suwaye iyayenmu da LAIFUKAN dasuke aikatawa a BOYE ba , bazan taba ganin laifinka donka furta tsanan Abba dakakeji ba, domin natsinci kaina cikin matsananciyar tsanansu dajin zafinsu
Har zuwa lokacin da suka nunamin nadamansu da tuban su karara ba, Ashe sunrage wani kasone cikin LAIFIN BOYE dasuke aikatawa amma basubar wani kason ba"
Ahnkl shureim ya warware ma salman duk Irin abnd yasan iyayensu nayi a BOYE, har zuwa mummunan ganin dayai musu a guess house din dady
Harkawo kan alakan dake tsakanin dady da maryam ayanxu, wanda yake shirin aurowa momy ita amatsayin abokiyan zama , bayan sungama tanbadewan su dashi
Salman gaba daya jikinsa harwani tsuma yake tabbas iyayensu , basu kyauta musu ba bakuma suyiwa kansu adalci ba , basuyi musu ba suma duk da cewan shima baikasance cikin kamilan mutane ba
Nan suka shiga tattaunawa akan yadda zasu bullowa iyayen nasu , tareda yimusu fatan shiriya cikin saury
Kafin salman yamike yaiwa shushun sallama yafice zuciyansa naraya masa yadda zai datse alakan Afrah da mahaifinsa
Baitaba jin son wata mace har yakejin zai iya aurenta irin Afrah ba, tunda ya dandani zumarta ya gigice don haka tunda har mahaifinsa yarigashi lasan wannan zazzakar zumar ,da yazamamai shamaki akan aurenta
Toya zama dole shima yatsinke masa jin dadi da ni'imar dayake kwasa ajikinta, zuciyansa har wani turiri yakeyi na kishin Abban sa da Afrah yakeji,
*********
Shushu koda yabar offices bai wuce gd ba kai tsaye gdn momy ya wuce , domin yanason su tattauna akan mgn wasu kayan ta da zaizo
Ya dade agn momyn kafin yabaro momy tabashi wata leda mai dauke dakayan mata , masu kyan gske wata aminiyanta tazo dashi daga Ghana, tamikamai tana fadin"gashi kakaiwai daughter na taduba ciki akwai takarda maidauke da bayanin komi "
Shureim ya amshi ledan yafice yana murmushi , zuciyansa nakara mamakin yadda momyke kaunar Aysha din
Ana kiran magrib ya isa gd hakan yasashi wucewa masallaci kai tsaye ,saida aka idar da sallan kafin yashiga cikin gdn rikeda ledan sakon momy
ESHATT SMILER HOM OF HAUSA NOVLS
DOCUMNTS
WASAPP 08066360176 FOR MORE
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 馃挕
Writing by Ayshat Dansabo lemu 馃枈
*1*
Alhaji shu'aib Abba aji zaune akatafaran falon gdn sa, hannunsa rikeda waya samfurin iPhone x , waya yake kuma bisa dukkanin alamu yana cikin matukar farinciki.
Hajiya kubrace ke sakkowa daga stairs, cikin takunta na kasaitattun mata, kallo daya zakai matan kasan hutu da jin dadi sunyi zaman dirshan ajikinta
Shiganta kadai ya isa yatabbatar maka da cewa itadin hamshakiya ce, kuma gogaggiyar mace wanda ilimi da wayewa taxamani ya matukar takarawa acikin rayuwanta
Ahnkl take takowa fuskanta dauke da murmushin da tasan yana matukar tasiri axuciyan gogan nata,
Byn ta zauna kusa dashi har jikinsu na gugan juna,wani qamshi mai matukar sanyin dadi ne ya doki hancin Alhaji shu'aib , hakan yasashi gyara zama yana mai aje wayan hannunsa, fuskanta yake kallo wanda yasha light make up tamkar ba babbar mace ba, kafin ya furta
"Madam kenan sai yanxu kike sakkowa ina shirin fita " murmushin ta mai tsada tasake saki kafin ta furta
"To ai dadyn su yusrah gani yanxu ko , af waishin ya mgn zuwa dakko , yusrah kasanfa jirginsu zai sauka karfe 5 ne bakuma lallai ne shushu yadakko taba, ksan kuma mutuniyar bataso driver kadai yaje dakkota"
Kallon ta yayi kafin yayi mgn wani hadadden aamshi yafara kaikawo , cikin hancinansu kafin wata murya mai matukar dadin amo tayi sallama, cikin falon dukansu dubansu suka mayar ga kofan falon,
Wani hadadden matashi ne yake sallama, yaci ado cikin kananan kaya da sukai matukar fito da kyawunsa,
Tareda tsantsan kuruciyar sa, ahnkl yake takowa cikin falon fuskan sa dauke da murmushi,
Daga hajiya kubra har alhaji shu'aib suma murmushin ne akan fuskar su,
Kai tsaye kusada kafan dadyn nasa ya tsuguna yana fadin, dady gud morning shafa suman kansa dadyn yayi wnda yake kwance luff , kafin ya amsa morning my son
Ya gajiyan tafiya ?
Murmushi matashin saurayin yayi yana fadin
"Gajiya tabi lfy dady "
Karisawa kusada hajiya kubrah yayi , har yana kwantar da kansa acinyan ta kafin ya furta
"Momy antashi lfy ?
Shafa kansa tayi tana murmushi take fadin, " my son anfito lfy ya gajiya ?
Ahnkl ya furta momy tabi lfy , mikewa yayi yana shafa cikin sa dayake alafe , kafin yakai dubansa ga dining area yana fadin
"Am very hungry mom bari inyi kalaci inzo musha hira "
Mikewa Alhaji Shu'aib yayi yana fadin
"Kazo dai kai shagwabar taka ta fama ba tunda jinka kake tamkar dan yaye idn karabi jikin mumy "
Hajiya kubrah kefadin
"Bakomi dai dadyn yusrah kaidai jeka sai ka dawo , karfe 5 shureim sai ya dakko yusrah idn ta sauka koni da kaina driver yakaini intaro abata "
Dining yawuce yana cin chips , tareda pepesoup na naman rago, yanayin taunansa cikin natsuwa da aji kadai xai birge ka
Kusan mintina akalla 30 yashafe kafin ya mike , yana aje cup din daya shanye ruwan tea din
Kafin ya nufi cikin falon inda momyn sa ke hakimce , hannunta rikeda jaridar daily trust,
Isowan shureim cikin falon yasata aje jaridar tana dubansa, kafin tafurta
" my shushu harka kammala ? Ya amsa da eh momy yana zama kusa da ita "
Hira sukeyi tamkar wasu sa'anin juna da momyn, rabin hiran suna yinsa akan tafiyan daya dawo , daga kasar london wanda ya shafe kusan watanni 2 acan,
Yana gudanar da seminar da aka turashi , kafin ya kammala yadawo gd
Cikin hiran ya dubi hajiya kubrah yana fadin
"Momy naji kina fadin yau baby yusy zata dawo kice yau kunnuwana sai sunyi ciwo , sbd surutunta daxata ishe mutane dashi"
Murmushi sosai mumyn tayi kafin tace kai shushu 'yar autan nawa akewa sharri
Mikewa yayi yana fadin "momy bari intafi gurin sudais inason ganinsa kafin ya wuce hospital"
Adawo lfy tace dashi kafin ta dauki jaridarta tai sama , shikuma ya fice kai tsaye katon parking lot ya nufa, wanda motoci ne na alfarma girke acikinta ,
Wata hadaddiyar mota baka wuluk ya bude , sabuwace kar ga dukkan alamu bata jima da kawota ba,
Dukkanin ma'aikatan dake kai kawo aharaban gdn , mika gaisuwa sukeyi gurin shalelan gdn kuma uban gdn su shureim,
Suna matukar girmamashi , da ganin mutuncinsa kasancewan s a mai saukin kai matuka , dayi musu alkhairy akai akai ,
Tuki yake cikin natsuwa da gwanancewa, kai tsaye garki ya nufa , byn yakira Dr. Sudais ya shaida masa yana bisa hanya
Byn ya baro gurin Dr. Sudais dinne yaji kawai guess house din dady yakeson zuwa,
Domin lokuta da daman yakanso kebewa aguri guda ya huta, sosai yake jin dadin kasancewa cikin katon gurin hutawan dake guess house din ,
Koda ya isa mai gadi ya bude ya kwashi gaisuwa, ganin motan dady dana Alhaji Adam yaba shureim mamaki , sbd baiyi tunanin ganin dady a Irin lokacin yazo hutawa ba
Sai dai ganin motar Alhaji adam ne yadan danne mamakinsa, yake tunanin watakil zasu tattauna harkokin kwangilolin sune da sauran business da sukeyi tare,
Koda shureim yai parking sai kaitsaye yanufi katafaren garden din dake gdn , wanda duk wanda yakasance ciki dole ne kasami natsuwa da nishadi ,
Gurin yanada matukar niimah shuke shukene birjik , ga resting chairs nan na hutawa banda kukan tsintsaye dake kai kawo cikin kunnuwan mutum,
Teburyn buga snooker ya nufa wanda shiyasa aka kafa , yana bugawa ahnkl byn ya gajine ya sami guri ya kwanta yana danne danne awayansa
Shine shiga snap, shiga IG , shiga Facebook har lokaci yaja,
Ahnkl Ya mike ya nufi cikin gdn , har xuwa lokacin motacin su dady nanan alamun basu tafiba
A katon falon ya xube byn ya dauki ruwa cikin frige , yana sha sanyin ruwan naratsa makoshinsa,
Aje goran ruwan yayi ya nufi up stairs, atunanin sa zaisami su dady afalon dake saman , sai dai babu motsin kowa
Hakan yasashi tunanin ko su bedroom din dadyne , inda yafi zama ciki ya huta domin bayaune kadai shushu yasaba zuwa hutawa , a guess house din ya tadda dadyn yaxoba shima
Saidai kowa yanada bedroom dinsa , hakan yasa shureim ya nufi dakin dayake mallakinsane
Murda kofan yayi tareda sanya kansa ciki , lokaci guda numfashinsa yafara barazanan daukewa
Janyo kofan yayi da saury hannuwansa duka biyune dafe da goshinsa,
Tunda yake aduniya bai taba mummunan gani irin na yauba, tuni yakeji xuciyansa na barazanan fadowa kasa,
Ahnkl yanufi bedroom din dadyn danufin shiga yazauna , kozaiji yafarka daga mummunan farkin dayake ganin yafada
Sai dai kash koda yabude dakin wani kara yasaki , tareda zubewa agurin yana salati tareda hawaye masu zafi dasuka fara sintiry afuskan sa ahnkl ya sulale kasa ,
Salatin dayake ya ankarar da Alhaji shu'aib cewa wani ya shigo cikin bedroom,
Cikin sauri yake kokarin rufe tsiraicinsa , yayinda yamakaro domin aikin gama yagama , turesu yayi daga kansa yana kokarin ganin kowaye mai wannan kasadan ,
Koda sukai ido hudu da shureim , wani kara shima yasaki dukkanin jikinsa rawa yake , murya asheke yake fadin shu shu rei m, da kyar yahado sunan ya furta cikin tsananin firgici da tashin hnkl,
Yagama sadakarwa yau azal tafada masa , asirinsa daya dade yana binnewa yau dansa mafi soyuwa aransa yaganshi
Yana aikata mummunan barna, wanda kunya kadai ta isheshi , da kuma yadda mutuncinsa zai zube a idon tilon dan nasa
Wani zazzafan hawaye kebiyo fusknsa, yayin da
Shureim ya dade da shidewa , baimasan abnd yacigaba da faruwaba
Ayshat Dansabo lemu 馃憣馃徎
LAIFIN BOYE
*_Haske writers_* *_association_* 妫e啯瀵�
Writing by Ayshat Dansabo lemu 妫e啯鐎�
*2*
Aysha kiyi hanzary ki fito mana , nikam banison yanayin sanyin jikinki ace mutum tun daxu bai gama shiry ba
Wata kyakykyawar macece ke wannan mgn , tana zaune cikin kayataccen parlonta , yayin da Aysha ke room dinta tana shiri mgn da umman ta tayine yasata , rataya jakanta ta fito cikin takunta na natsuwa da birgewa
Aysha kyakykyawar macece matuka, tana da matsakaicin tsayi bakuma xaka kirata mare tsayi kai tsayeba, Allah yabata baiwa na structure din jiki ,wanda ake kirada kirar kalangu , ko ina ajikinta acike yake tap akwai baiwan kugu da na fulani tubarkalla,
Wanda hakan kejanyo maza zuwa gareta , choculate color ce fatarta wanda yahadu da hutu yasa fatar yaiwani irin fresh , Aysha natsatsiyar macece tanada kamun kai matuka , sai dai awani lokutan miskilace matuka
Fitowanta kai tsaye kusada ummanta ta nufa , tana fadin
"Umma to bagashi yanzu nafitoba kumama banda abnki umma zuwa gurin saloon harwani saury ake masa"
Umman ta dubi Aysha tana cewa to saikije bedroom dina ki dauki 5k , sannan inaso idn kindawo kiceda bala kutsaya gdn hajiya kubrah , munyi waya akwai sako daxaki karbo min
To kawai tace ta nufi bedroom din umman , kudin ta dauka ta fito tana ma umma saita dawo tafice
Bala naganin fitowanta yayi saurin gyara parking, back sit tashige suka bar gdn kai tsaye a hadadden gurin saloon din yai parking Aysha ta fito ta shige
Kaman yadda tayi tunani hakan ne yakasance, ta tadda mutane balaifi hakan yasa saida ta bata lokaci , kafin aimata straiching da wankin kafa ta baro gurin ba, kaman yadda umma tace hakan akayi daga salon din kai tsaye gdn hajiya kubrah dake maitama suka nufa
*******
Farkawa shureim yayi yagansa kawai a falon dake nan up stairs , dadynsa da Alhaji Adam ne akansa , kallo daya zakai musu kasan dukkaninsu suna cikin tashin hnkl
Ahnkl yake kara bude idanunsa akan dadynsa, abubuwan dasuka faru yake dawomasa , sake rufe idanunsa yayi ya bude xuwa yanxu dayake ganin iyayen nasa tsaye akansa ya tabbatar badaga mafarki yatashi ba
Wasu hawaye masu zafi suke sintiry a fuskarsa, hakan yasa zuciyan Alhaji shu'aib sake tsinkewa, cikin karfin hali da dakiya ya tsugunna yana kokaryn kama hannun shureim din, yayin da shushun yayi saurin janye hannuwansa , yana watsawa dadyn wani kallo mai cikeda nuna tsana , wanda hakan bakaramin sake tsinkar da zuciyan dadyn hakan yayiba
Tashi zaune yayi yana duban Alhaji Adam , wanda yayi karfin halin fadin
"Shureim kada kazargi mahaifinka akan abnd idanuwanka sukagani, wlh sharrin shaidan ne da kuma son xuciya , hakika yau nidashi munyi matukar nadaman wannan mummunar harkan da muka jefa kanmu ciki"
Ahnkl shureim yasamu ya mike tsaye duk da jirin dake dibansa haka yake , takawa ahnkl ya nufi hanyar stairs batareda ya tsaya jin abnd alhaji adamu ke kokaryn sanar dashiba, sbd aganinsa basuda wani hujjan dazai gamsar dashi akan abnd adanunsa suka gane masa,
Allah ne kadai yakai shureim gd tundaga irin mahaukacin horn din dayake saki , mai gadin yasan babu lfy aguje yashige xuwa parking lot, yayi parking kai tsaye part dinsa yanufa ko takalmin kafansa bai cireba ya kwanta akan 3 seather , idanunsa ya lumshe yana juya duk wani abnd yafaru a yinin yau , hakika tunda yake bai taba mugun ganin daya firgitashi irin nayau ba,
Bai taba tunanin mahaifinsa daya bashi ingantacciyar tarbiya, zai kasance mai aikata sabo irin hakaba,
Bai taba tunanin mahaifinsa yana aikata boyayyen LAIFI irin wannan ba, ahnkl haushi da jin wani irin tsanar mahaifinsa ke kokaryn mamaye zuciyansa
Abnd bai taba tunani ko amafarki zaiji hakan game da ddynsa ba, sosai shureim yadafe kasan tareda fashewa da kuka tamkar karamin yaro, afili yake furta why? Dady meyasa kasauya halayyanka kyawawa zuwa aikata k'azamin LAIFIN BOYE irin wannan ba
Wayansa ne ya dauki rury hakan yasashi dauka , cwt mum abnd ke yawo akan screen din kenan ahnkl ya kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa, karfe 5 harta gota Sai alokacin yatuna da zance dauko yusrah daga airport dazaiyi
Jin muryansa kawai mum tayi tasan akwai matsala , cikin tashin hnkl ta furta shushu lfy kuwa ? Murynsa can kasa ya furta mumy vanjin dadine zazzabi da ciwan kai kedamuna
Salati tadauka tana fadin kana inane yanzu , ganin hnkln ta yatashi yasashi fadin" mum ina gurin Dr. Sudai yabani magani zan huta zuwa anjima sai indawo lokacin naji karfin jikina
Mgn dakko yusy asa driver yadakko ta plx mum, hajiya kubrah ta amsa dafadin hakan yazama dole shushun mumy , dakaina nida driver zamu dakkota nidai fatana Allah yasa jikin naka da sauki ?
Da kyar ya amsa da mumy karkidamu da sauki sosai , yanxu haka kaina ne kadai ke sarawa magani nasha , inaso danayi bacci natashi kila inji dadi sosai
Maza kwanta to my son ka huta momy tafadi tana katse wayan, hakan yaiwa shureim dadi ahnkl yake takawa zuwa bedroom dinsa kai tsaye tiolet yawuce
Yajima sosai kafin yafito sallolin da yawuceshi yayi , ya dade yana addua Allah kada yasa abnd yakeji gameda mahaifin shi yadore , domin kuwa wata zazzafan tsana yakeji nasa aransa
*****
Aysha ce take takawa cikin takunta mai cikeda natsuwa, xuwa cikin gdn hajiya kubrah byn driver yayi parking, sallama tayi cikin muryanta mai matukar sanyi da dadin amoh, jin shiru yasata samarma kanta mazauni
Mintina kusan 10 ta share azaune kafin tafara jiyo karan takun takalmi , ana sakkowa daga stairs daga kanta tayi cikin saa sukai ido 4 da hajiya kubrah
Cikin faraa da sakin fuska take fadin lale da Ayshatu , aitun daxu hajiya safiya tace gaki bisa hanya naji shiru
Takai karshen mgn ne tana karisowa cikin falon , tazauna hakan yaba Aisha daman zamowa kadan tana gaida hajiya kubran
Cikin matukar sakin fuska take amsa gaisuwar tata, kafin ta dora da fadin kinga yanxu haka autata zanje dakkowa yau zata sauka, farin cikin Aysha yakasa boyuwa hakan yada tasaki murmushi , tana fadin wow mumy kice gobe nan zan yini dani zaa kwance tsaraban Cairo
Sakon da zataba Aysha ta dakko tareda hado mata turaruka tabata , tare suka fito Aysha suka dauki hanyan gd yayinda motar hajiya kubrah suka nufi airport domin dakko autan ta wacce zata duro Daga kasar cairo , ta kammala karatunta gaba daya tazama cikakkiyar 'yar jarida
Ayshat Dansabo lemu 妫e啯鍟犳#鍐ㄧ法
[7:50PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*3*
Alhaji shu'aib da Alhaji Adam kuwa tun byn ficewan shureim, suka zube anan falon suna kallon_ kallon , da kyar Alhaji shu'aib ya iya furta
"Adamu yanxu menene mafita kakoga irin kallan tsanan da shushu kemin? Wlh tsanata nake hangowa karara afuskan sa, zan iya jure komi amma banda hango kiyayyata karara afuskan my son, inama shureim wani irin so dani kaina bansan yadda zan fassara shiba, hakan kuma baya rasa nasaba da irin nutsuwa da kamun kansa , uwa uba tsananin biyayyan dayake min, ina tsoran shureim ya juyamin baya Adam, tir da wannan mummunan sana'a tamu "
Ya kareshe mgn yana sauke ajiyan xuciya mai zafin gske , burinsa kawai kada shureim ya fallasa asirinsa agaban hajiya kubrah, duk da yasan zai wuya yayi hakan
Alhaji Adam wanda shima yarasa mafita , jiyake azuciyansa shima tamkar salman dansa ne yakamashi yana aikata abnd shureim yagani , da kyar ya iya duban aminin nasa kuma abokin gudanar da wannan business din tasu , dake janyo musu kazaman miliyoyin kudi tareda kwangiloli masu tsoka , daga manyan kasa , kafin ya furta
"Abokina kayi kokaryn ganin ayau basai gobe ba kazaunar da shureim , kafadamasa gskyn abnd yajefamu ga fara wannan harka , nasani shushu mai hnklne zai fahimcemu duk nasan bamuda wata hujja ,
Wanda zamu dogara dashi yasa shureim yagamsu ba son zuciyan mu daneman Tara kazaman dukiya yajanyo mana fadawa wannan harka Muna aikata LAIFIN BOYE tareda kawar da hnkln mutane akanmu ba , wacce tayi sanadiyyan bata rayuwanmu gaba daya"
Sosai suke tattauna yadda Alhaji shu'aib zai shawo kan shureim din, daga karshe shawaran Alhaji Adam yadauka
Shureim wanda yake kwance yanajin zazzabi mai zafi na neman rufeshi, wayansa yajanyo yayi dialing number Dr. Sudais , buga biyu ya Daga wayan yana fadin
"Guy yane ? "
Da kyar shureim ya iya furta
"Plxx guy kayi sauri kazo wlh zazzabi mai zafi yakeson rufeni , gara kazo kayimin allura tunkan nakaiga rafke muku cikin daki"
Da mamaki sosai sudai kejin wai shureim baida lfy lallai yanzu yanzu sai Allah, kaman ba dazu suka rabu suna ma juna shakiyanci ba,
Hakan yasashi furta
"Kaganin dama yanzu zan baro hospital din, "
*****
Tafiya sukeyi bisa titi zukekiyar budurwa mai kimanin shekaru 18 ne , kwance akafadun hajiya kubrah sai zuba ruwan shagwaba take , ita adole tayi missing mumyn tasu a lot yayinda hajiya kubran ke biye mata
Cikin shagwabar take fadin
"Mum wai ya shushu ciwan me yake ne ? "
Hajiya kubrah tashafa byn ta tana fadin
"Hmmn wlh baby hnkln yana kan shushu cewa yayi zazzabi ne , nikuma yadda nasanshi da juriyan cuta , muryansa yadaga hnkln amma bari mujira dawowansa aga halin dayake ciki"
Koda suka iso gd suna shigowa compound din mumy tahango motar Dr. Sudais, hakan yasa ta dubi yusrah tana fadin
"Yawwa yusy kinga motar sudais inaga yadawo da shushune , bari muje part din nasa muga yanayin jikin nasa"
Atare suka nufi part din shureim itada momyn yayinda driver ke kwasan kayanta xuwa cikin gd
Kwance yake sunadan mgn da Dr. Sudai wanda yagama yimasa injection,sudais na tambayan shureim din yadda akai ciwo yazo da gaggawa haka , gashi koda ya gwadasa yadda yaji bugun zuciyansa, yakaru almun yana cikin tashin hnkl tambayan shureim damuwansa yake da abnd yajanyo hakan agaresa amma yayi biris dashi
Ahaka hajiya kubrah sukai sallama itada yusrah , sudais ya amsa sallaman fusknsa fes akan yusrah wanda girmanta da kyawun data kara yai matukar bashi mamaki
Yusrah da gudu ta isaga shureim dake ta saukemata smiling , ta zube kasa tareda kama hannuwansa tai kising
Tana fadin "my ya shushu I miss u ya jikin naka "?
Sake damke hannuwanta yayi yana tashi zaune ahnkl ya furta
" my baby doll jiki dasauki zazzabi cefa kuma kinga guy dinnan yamin injection harna farajin sauki so ya hanya babyn mumy"
Hajiya kubrah data zuba musu idanu taji dadi sosai ganin shureim din jikin nasa dasauki bayadda tayi zato ba
Karisawa tayi tareda da shafa kansa kafin ta furta
"My son ya jikin ? Murmushi yai yana fadin momy nama warke fa ni dama nafada miki ba wani ciwo bane sosai, "
Sudais ne ya dubi yusrah yana fadin babyn mumy baki ganni bane bako mgn , ko duk zumudin ganin shushu ne ya rufe idanun?
Yadda yayi mgn sai yasa yusrah jin kunya hakan yasa ta rufe idanunta tana fadin
"Laah ya sudais sorry wlh dokin ganin my cwt bro yarufen idanu "
Shima murmushi yayi yana tambayanta ya karatu tareda tayata murnan kammalawa , da fatan alkhairy sun dan jima kafin subar part din shureim din , har suka fice idanun sudais nakan yusrah wacce gaba daya ganinta yasashi cikin jin wani yanayi atattare dashi
Ya kasa boye mamakinsa saida ya dubi shureim yana fadin
"Guy kaga yadda baby yusy tazama big gal kuwa gsky nidai inajin 'yar gd zaai indai mumy zata bani "
Wani harara shureim ya aika masa kafin yace kaifa dan world ne sudais , kanwar bayanka zaka kalla da sunan luv don Allah karka janyo mana raini
Karfe 9pm iyalan ne duka zaune ana cin dinner , momy dady and yusrah banda shureim wanda sam yaki shigowa part din, domin bayi kaunar sake dora idanunsa akan dadyn ,
Momy ce ta daga waya takirashi bugu daya ya dauka , yana fadin mumy takatse sa da fadin son lfy bakashigo yin dinner ba duk gamu mun hadu ,
Ahnkl ya furta mumy kinmanta jikin babu dadine , kisa yusrah tadan kawomin part dina , ruwan tea kawai saidan abu mara nauyi yakareshe mgn da shagwaba sosai
Hanging up tayi tana kallon dady take fadin, dadyn yusrah shushu fa baijin dadi , cikeda firgici da tashin hnkl yake furta
"Meya samesa kubrah kuma kika kasa sanar dani tun shigowata gdn , "
Hajiya kubrah tayi murmushinta mai kayatarwa , kafin ta furta
"easy dadyn yusrah jikin
aida sauki fever ne kuma yasamu sauki sosai yanxuma shagwabar ce tamotsa wai yusrah takai masa abncin part dinsa"
Ajiyan zuciya Alhaji shu'aib ya sauke , tuni ya harbo girgin shureim din, sam bayason haduwansu ne shiyasa zai fara gujewa duk wata hanya dazai sa suhadu , sosai hnkln sa yatashi sai dai yazama dole ya koyi danne damuwansa gaban momyn , tun kafin tafara fahimtar wani abu
12 o'clock nadare Alhaji shu'aib ne ke zare jikinsa ahnkl daga hajiya kubrah, wacce tayi nisa sosai cikin baccin ta kai komo yafara cikin tafkeken bedroom din nasa , kafin daga bisani ya lallaba ya fice
Kaitsaye part din shureim ya nufa koda yakai kofar part din , waya yazaro yayi kiransa sai dai hartagama ringing bai daga ba
Cikeda mamaki yasake dialing sai jin wayan yayi is switch off , hakan yai matukar bashi mamaki
Ahnkl yafara knocking kofar shureim wanda ke kwance aparlon sa , yana kallon wani American film domin yasan koya kwanta damuwa, bazata barshi ya iyama bacci ba yaji shigowan kirn dadyn
Jin ana knocking yabashi mamaki waye zaizo part dinsa a wannan tym din
Cikeda fargaba ya mike jin haryanxu ba abar knocking din ba, bude kofar yayi ahnkl ganin dady yasa gabanshi faduwa, lokaci guda yahade fusknsa tamau fuuu ya juya xuwa cikin parlon
Alhaji shu'aib ya rufa masa baya , zama shureim yayi tareda runtse idanunsa , dady nabinsa da kallon mamakin sauyawar shureim din lokaci guda
Ahnkl ya zauna kusada son din nasa tareda dafa kafadunsa , kafin yafara kokarin yadda zaiyi shureim ya sauraresa
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[7:58PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*4*
Kiran sunansa yayi ahnkl shureim, yadda yakirasa da sunan shureim yasan tabbas dadyn mgn mai muhimmanci zaiyi dashi , hakan yasa shi amsawa da na'am dady
Dady yacigaba da fadin"shureim inaso kabani hnkln ka da nutsuwarka nan , abnd yasa nazabi wannan lokacin sbd inaso abnd zamu tattauna yazama sirri
Ina nufin ko mumyn ko ban yadda taji wannan sirrin nawaba, nasani ayanzu kanajin tsanata shureim, kanaji inama banine mahaifinka ba ayanzu, domin duk da mai tarbiya irinka , bazai so nazama uba agaresa ba "
Hawaye masu zafi suka sauka akan kafadun shureim, wanda harzuwa lokacin idanun sa aruntse suke , jin digon hawyen yasashi bude idanunsa yana kallon mahaifinsa na zubda hawaye
Kallon sa yayi tareda sauka kasa ya kwantar da kanshi kan kafafun dadyn, ahnkl ya furta dady ina jinka
Dadyn ma kasa yazauna shureim ya zuba masa idanuwa , yana sauraren yaji menene dadyn yazo dashi adai dai wannan lokacin, kafin dadyn yafara mgn dacewa
"Shureim tunda aka haifeka kataso kaganka cikin arziki ne, bakata taba sanin miye babu ba, duk abnd kanema kana samu har zuwa lokacin Dama zama mutum
Nabaka dukkanin kulawa tareda gata nayi kokaryn
Ganin na inganta tarbiyanka, cikin hukuncin Allah kazamo cikin yaron da duk wani uba zaiyi alfaharin kasancewan ka da agaresa"
"Shureim kaman yadda kataso kasani nidin , hamshakin Dan kwangilane kuma dan kasuwa , da wadannan sana'a biyu natara duk wani arziki daka sani shureim"
Tunkafin na aury kubrah ina cikin mazajen da zaa lissfa cikin masu rufin asiry sosai ,
Wannan mummunan harka da muka fara shureim , tasamo asaline wani lokaci da muka nemi wata kwangila mai tsoka , nida abokina Alhaji Adamu sai aka hadamu da wani minister , amatsayin na manyan 'yan kwangiloli bamusha wahalan ganawa dashi ba
Sai dai koda muka sami ganinsa yabamu address din gueshouse din sane , inda wata Sunday ban mancewa misalin 4 na yamma muka samesa nida Adamu
Koda muka isa akai mana iso zuwa cikin falon , abn mamaki munsamesa ne tareda 'yan mata kusan guda uku , bayaga wata gogaggiyar hajiya wacce alamu yanuna tareda wadannan matan suke
Ganinmu yasa yasallami wannan hajiyar tareda wadannan 'yan matan ya basu umurnin shigewa ciki , yanayin shigansu da tafiyansu kadai zai shedamaka cikakkun 'yan barikine
Byn shegewansu ne minister ya dubemu byn mungaisa cikin aminci da mutunci , mukasake shaida masa mune dai masu nemn abamu kwangilolin da sanata ya shaida musa
Daga lokacin yafara shaida mana tsarinsu shida sanata, na indai munason wannan kwangila dolene mucika sharuddan dazasu bamu , sharadi nafarko kodai suyi lalata damu sannan ayi signing sannan kwangila tazo garemu , ko kuma mu amince zamu dinga kawo musu abokan harka maza da mata domin su rika hutawa dasu ,
Idn kuma har bamu amince da hakanba to sai dai mu hakura da wannan kwangila , wanda hakan na nufin zamuyi asaran riba ta miliyoyin kudi ba kadan ba
Sai dai nan take nashaida ma minister bamu aminta da wadannan sharuda ba, sai dariyan da yayi da kuma kashedin daya biyo bayane yasa muka aminta dashi da kuma dukkanin abnd ya bukata
Domin yashaida mana cewa tunda yafallasa asirinsa , dole mu muzaba cikin abu 2 daya lissafo mana , bijirewa hakan yana nufin toshewar duk wata kafa dazamu iya samin kwangila koda ko ta taroce , hakan yadaga hnkln mu kwarai da gske
Batareda dogon nazari ba muka aminta da kudirinsa na 2, wato mudinga kawo musu mata da kuma matasa suna holewa dasu , "
Cikin tsananin tashin hnkl shushu ya kalli mahaifinsa , tuni yafaraji kansa na sarawa wannan wace irin kazamar sana'ace ?
Sai dai Alhaji shu'aib yakatse tunanin shureim ta hanyar cigaba da mgn yana fadin
"Shureim bamu baro gurin minister ba saida muka tabbatar masa dacewa mun amince da kudurinsa, Adamu shine yasake ba minister tabbacin cikin satin zaiga manyan kaya "
Nasan alokuta da dama kanaji idn ina waya , ina yawan cewa ansami manyan kaya , to ba kaya nake nufi irin nabusiness dina daka sani ba , alokuta da daman manyan kayan danake fadin suna nufin mata da kuma matasa ,
Tundaga lokacin muka zama tamkar masu safaran , yan mata da matasa muna rabasu hotel -hotel ga manyan kasannan , mukuma muna samun manyan kudade da kwangiloli naban mamaki ,
Kafin kace haka munzama manyan kawalai , kudi kota ina muke samu duk wata kwangila da zata fito , daga state ko federal mune kan gaba ,
Tunda muka fara wannan harkan shureim , ban taba sama zuciyata zan iya lalata da 'ya mace ba , hasalima idn aka kawosu bakasafai hakan bukaci ganin su ba, sai dai mubada umurni arabasu hotels byn mun tabbatar da kayayyakin sun wanku , zakuma ayaba dasu matuka Alhaji Adamu shine mutumin da Azal yafara fadawa kansa
Watarana ankawo mana manyan kaya , masu matukar kyau da daukan hnkl , wadanda idn mutum bai yi da gske ba to tabbas shaidan zai iya nasara akansa,
Lokacin da aka basu kaya domin gyarasu kaman yadda akeyi , kafin ayi posting ma senatocin mu da ministers ne , shaidan yayi nasara akansa , harya keta mutuncin daya Daga ciki wacce take sabuwace baa taba komi da itba
Kasancewar yawancin kayan da ake bukata sunfi son sabbi fil aledansu ne, tunda ga lokacin Admu yafara harka duk kayan da zaa kawo sai sauki daya ciki , sai dai bai taba shaawar neman jinsin saba sai dai mata ,
Sannu ahnkl kasancewar sa abokin tafiya , amini kuma abokin harka yasa yau da gobe dayake kwadaitar dani , irin dadin zumar dayake lasa yasa tun ina masa fada har nadaina nafara sha'awan nima inlashi gardin zuman dayake kwadaitar dani
Wata rana nima ankawo wasu 'yan mata kyawawa, sai dai Irin gogaggun yarane da idanunsu ya bude da harkan sosai , daya Daga cikinsu da kanta tai shaawan kasancewa dani , Alhaji ta tunkara da mgn domin shine nasu alokacin yasanr da jta nisam bana wannan hakan
Sai dai dayake ance mace shaidaniyace , hakan yasa suka sakamun magani acikin lemu , awannan rana komi yafaru aranan nakara sanin zumar wata mace wacce ba kubrah ba, yanayin data tafi dani ya kara jefani cikin wani hali
Daga ranan shedan yaci gaba dajan ragamanmu , dazaran ankawo mata saimun huta dasu kafin mu aikasu inda yakamata , sosai suke bamu hadin kai kasancewar mu masu arziki komi najin dadin rayuwa muna tanadar musu ,
Sai dai bamu taba shawa'awar kusanta jinsinmu na mazaba sam , sai mu nemosu murabasu gasu minister da manyan kasa
Ko kadan bantaba bude wata kofa ko kafan da kubrah zata gane ina mu'amala da wasu mataba, sai dai ance rana dubu ta barawo ne rana daya tak namai kaya, sai gashi tsayin shekaru muna sheke ayarmu tareda da kawar da hnkln mutane damuke , da harkan business wacce aboye harkan damuke gudanarwa yafi komi kawomana arziki , wlh shureim wannan kasar tamu lalacewarta yawuce inda kake tunani
Manyan sun baci ta yadda ko aiki kake neman karin girma ko wani mukami mai tsoka , sai kabi hanyan lalata ko fasadi kafin subaka dama kakai inda kakeso, sai dai wanda Allah ya tsallakar dakuma wanda bai biyewa son zuciya da kuma kwadayin tara dukiyaba ,
Shureim inaso kayafemin ka kuma rufe sirrina , baniso kubrah taji wannan mummunar lbryn , idn kaimin hakan tabbas zan san kai cikakken dane nagary agareni , kuma daga yau nayima alkawarin daina wannan harkan , zan rungumi kasuwanci na zan hakura da naiman duk wata kazamiyar kwangila , matukar saina sabi Allah kona kauce hanya zan sameta ,
Sosai shushu ke kuka tamkar karamin yaro, da kyar ya iya duban dadyn sa kafin yafara mgn
"Dady hakika kun aikata mafi mummunan fasadi adoran kasa , kun zabi ku tsuda dukiyanku da kazantacciyar arziki , ayau ina kyamatar duk wani abu daka mallakamin koka ciyar dani da kudin kazan tacciyar kwangilan da kuke samu
Dady meyasa kuka biyema son zuciyoyinku da neman tara dinbin dukiya , ta hanyar kaucewa hanya?
Ayau inajin nadaman kasancewa ta jininka , ina ji inama nafito cikin talakawa wanda suke nema da kyar sannan suci susha, da irin wannan kazamar dukiyan daka hada halas da haram kana ciyar damu ka shayar damu
Meyasa dady zabi aikata LAIFUKAN BOYE ? don kawai katara arziki , dady ina mai bakin cikin kasan cewata jininka wlh dady, kasani cewa wannan abnd kuke aikatawa , zakubar mana mummunan tabone da bazai taba gogewa ba
idn ni ban tona sirrin ka ba tabbas Allah zai tona dady ,
Alhaji shu'aib gaba daya yagama muzanta agaban dan nasa, jiyake yi tamkar ya ga cewa komi cikin mafarki yake kasancewa ba gaske bane,
Sai dai muryan shureim ne yadawo dashi hayyacinsa jin yana fadin
"Dady inaso nai maka nasiha daka sadaukar da duk wata dukiya daka tarasa ta wannan harkan, kayi gaggawar sadaukar dasu domin tsarkake dukiyankata halas ,
Ka rungumi dukiyar ka ta halas kacigaba da juyata , koda ko hakan na nufin karayar arxiki ne agareka, "
Duk wani kaddara da kasan kabani cikin wannan kazamar dukiyan daka tara , kajanyeta daga gareni dady ,
Yana kaiwa nan yayi gaggawar tashi xuwa bedroom dinsa, yayinda yarufo kofan da karfin gske , fadawa gado yayi yana kuka sosai yasan yanason mahaifinsa, amma yazama dole yajuyamai baya , hakan kadai shizaisa ya saduda yakuma tuba daga wannan mummunan fasadin dasuke aikatawa"
Cikeda mutuwan jiki tareda damuwa matuka dady ya mike yabar part din shureim ,yana mai nadaman duk abnd ya aikata arayuwansa,
Gashi farin cikinsa na nema ya ruguje , domin bayaji zai iya jure juya bayan shushu daga garesa ,gashi yasan tabbas barin wannan harka itace rufin asirinsa
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[8:02PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*5*
Cikin mutuwan jiki dady yafice daga part din shureim, ahankali ya sadada zuwa bedroom dinsa , har zuwa lokacin hajiya kubrah bacci take
Kwanciya yayi tareda raba jikinsa da nata , idanunsa arufe yake ruf yayinda zuciyansa ke cikeda tunani da damuwa,
Bayaji adaren yau zai iya rintsawa Sam hakan yasashi tunanin mikewa ya dauro alwala, sallah yayi yana adduan Allah ya yafemasa , yakuma bashi ikon nesanta kanshi daga mummunan laifukan da suke aikatawa na BOYE
Misalin 9am na safe iyalan gdn ne zaune a dining suna kalaci , yusrah wacce ke sanye cikin shigan rigada wando na bacci , wanda yai mata matukar kyau domin itadin kyakykyawace sahun farko
Kowa yayi nisa cikin cin abncinsa shushu ne kadai har zuwa lokacin bai shigoba, hajiya kubrah na kokaryn daga waya ta kirashi
Sukaji bude kofa tareda hadadden qamshinsa yafara cika hancinansu, yana sanye cikin shirin zuwa office yaci suit wanda yai matukar yimasa kyau, tareda fito da kuruciyansa zallah
Hnkl yake karisowa cikin falon har ya iso dining area din, yusrah da murnanta take fadin ya shureim gud morning byn yaja kujeran kusa da ita yazauna
Shima kokarin wadata fuskansa da murmushi yakeyi , alokacin dayake shafa kanta yana fadin
"Morning my yusy ya gajiyan tafiya ko ince yagajiyan zaman flight? "
Cikeda murmushi da shagwaba take fadin "babu gajiya my big bros "
Dady yafara gaisarwa amma sam bai yadda sun hada idanunsu ba, saiya juya gurin mumy wanda zuciyansa ke cikeda fal da tausayinta,
Domin yasani idn hartaji abnd dady suke aikatawa a boye, zataji bakin ciki tareda kaurace masa domin kullin nasihanta akansu baya wuce, yatsaya ma halas ya guji aikata duk wata sabo, tana yawan kwadaitar dashi gameda aje iyali,
Domin gujewa fadawa halaka
Yazataji idn taji wai dadyne yake kawalcin mata harda matasa , bai tsaya anan ba shima yana aikata zina dasu ,
Sosai wani takaicin mahaifin nasa yasake kamashi, kadan ya iyashan ruwan shayi ya wuce office , yana aiki da National Health Insurance dake nan Abuja
******
Jakan hannun ta ajiye tareda zubewa bisa kujera , tana fadin wash ummah nagaji wlh yadda kikasan a motar kasuwa nayi fitannan
Ayshace take wannan mgn byn tadawo tana mikawa ummanta sakon , data amso daga gurin hajiya kubrah ta dora da fadin
"Wlh umma kinsan muna gaisawa bamu jimaba itama tace zata dakko yusrah , yau zata dawo harta kammala karatunta nikam karatun yusy yayi sauri sosai
Hajiya safiya ta dubi tilon 'yar tata tana fadin" ai haka karatun yake idn bakai kakeba mussamman idn katafi waje nan da nan saikiga kadawo ka kammala"
Aysha wacce tamike tana fadin "wlh kuwa umma muma dai Alhamdulillh tunda mun kammala asa'a, services kadai ya rage mana tana karisa mgn ne tareda daukan hand bag dinta , ta nufi room dinta yayin da tabar ummah na bude sakon ta data amso daga gdn hajiya kubrah
****
Matashiyar budurwa ce da bazata wuce shekaru 19 aduniya ba, duk da hijab ne sanye ajikinta hakan bai boye kyawunta ba, farace tas da ita da alamu kuma Allah yayi mata baiwan halitta mai daukar hnkl
Tafiya takeyi cikin natsuwa wanda duk namijin daya dora idanunsa akanta, zaiyi zaton wata natsatsiyar macece mai matukar kamun kai
Koda ta iso wani katon gd wanda kai tsaye bazaka kirashi da gdn talakawaba, zaka lissafashi ajerin gidaje na masu rufin asiry
Tura kofar gate din shiga tayi tasanya kanta ciki kaman jira akeyi tashigo gdn, wayanta yafara rury zaro sayar tayi daga cikin jakan ta byn taja tatsaya
Cikin rawan jiki ta amsa wayan tana fadin" hello bakin rai bakin fama banji abnd me kiran take fadiba , nadaiji wannan budurwan nafadin "karki damu dole gobe mukasance tare nima din nayi kewarki matuka aminiya, daurewa kawai nakeyi kinsan halin Abba h bayi kaunan yawan fitata, dama skull kesawa kaji koda yaushe kana free to yanzu mungama, banida wani sakewa yanxu amma karki damu nasan yadda zanyi
Suna gama wayan tayi shigewarta cikin gdn , tana rikeda wayanta samfuryn iphone 8 kai tsaye falon tashiga tana kwada sallama
Mahaifiyarta na kwance da alamu kaman bata lfy ne , domin kuwa tana kwance bisa 3 seather ne ta rufa da bargo,
Jin sallama yasata bude fuskarta tana duban kofa , take fadin Aneesa sai yanxu ? Yi maza ki aje jaka kishiga kitchen
Aneesa tana kokaryn shiga dakinta take fadin, to ummah ya jikin toh,?
Umman ta amsa da dasauki sosai Aneesah kawai dai haryanzu , jikinane bakarfi sosai shiyasa kiyi maza kidaura girki kinga haryanxu lantana, bata dawo ba idn tadawo din saiku karisa tare
Aneesa ta amsada toh ummah karki damu bari in sauya kaya, tana shiga room dinta tacire pitted gown din dake jikinta, byn tacire hijab din Aneesa tanada matukar diri mai daukan hnkl , kyakkykyawace matuka wacce ta mallaki duk wani abu da mace zatai dagawa dashi
Wata riga mara nauyi tasaka tareda daura zani akai ta fito tanufi kitchen domin daura girkin rana, kaman yadda umman tabata umurni
Washegary Aneesa ce ke shiri domin tanaso yau duk yadda zaai sukance da Rufaida , wata riga da wando tasaka wadanda basuda maraba da tsirara, sai ta dakko wani hadadden after dress ta daura akai
Light make up taima face dinta tayi kyau tamkar kasaceta ka gudu,
Safan kafa tasaka byn tadakko hijab cream tasaka wanda yasauka guiwanta, tafito sak cikin shiga takamala gaduk wanda yaga Aneesa , zaimata kallo na mace kamila tagaske
Around 11 tafito ummanta wacce tayi garas, tana kai kawo tsakanin kitchen da kuma falon Abban na Aneesa, dayake weekend ne yana gd bakasafai yafaye fitaba
Kallon Aneesa tayi tana fadin harkin fito , saiki je kisake sanarda Abban naki , duk da nasanar dashi zaki dubiyan Rufaida ne ba lfy
Aneesa tasauke murmushi tana fadin "to ummah tana shigewa bangaren Abban nata , zaune yake afalon nasa yana kallon CNN ya amsa sallaman Aneesah
Sake gaidashi tayi tareda shaida masa zata gdn su Rufaida ne domin duba jikinta , Abban nata ya dubeta tareda kallon shiganta wanda baiga makusaba, illah sake yaba natsuwan yarinyar taska dayake gani
1k yazaro yabata yana fadin Aneesah karbi wannan,kitabbatar karfe 5 na yamma yamiki acikin gdn nan, kinsani sarai banason yawon banza
Kasada kanta tasake yi tana fadin " to Abba insha Allah tadauki kudin tayi gaba
Bawani tafiya mai tsawo sukayi ba suka isa gdn su Rufaida wanda yake anguwan Rimi Kaduna, katon gd ne sosai wanda kana kallo kasan mai kudin gaske ne mamallakin sa
Koda mai gadi ya bude yaga Aneesah ce gaisuwa yashiga mika mata, domin duk wanda ya kwana yatashi cikin gdn su Rufaida yasan matsayin datake dashi aguryn shalelen gdn wato Rufy
Gaidashi tayi cikin girmamawa kaman yadda tasaba, kasancewansa dattijo datake ganin mutuncin sa, jaka taballe tabashi 500 sabuwa kal cikin irin kudaden datake samu daga abokan harkanta , da kuma Rufy wacce bata kyashin kashe mata kudi ko mallaka mata
Koda tashige katon main parlor na gdn babu motsin kowa, hakan yasata kai tsaye ta nufi bedroom dinn hajiya khairiyya
Sallama takeyi cikin sanyin muryanta hajiya khairiyya da suke kirada momy , ta amsa tana fadin "barkadai Aneesa ai tun jiya Rufaida ke shelan zuwanki "
Cikin girmamawa tagaida momyn kafin ta fito , tanufi wani corridor wanda zai kaita dakin Rufaida
Tunkafin takarisa kofar room din tafara kwallah mata kira, bakin rai bakin fama kifito mana, aguje wata budurwa da tagaji da haduwa tayo waje suka rungume juna
Sosai Rufaida tasake kwakume Aneesah tana shakan hadaddan qamshin dake fita ajikinta, yayinda hannusanta ke kokarin kama wadataccen kugun Aneesah
Aneesah ne tajanye jikinta tana fadin shegiya tawan aikya baridai mushiga daga ciki ko , dukansu dariya suka saka kafin su shige dakin Rufaida , wanda bashida maraba da dakin mace mai aure domin babu abnd baa zuba najin dadin rayuwa acikinsaba
Basu tsaya a karamin falonba kai tsaye bedroom dinta suka yada zango
Wanda suna shiga takai hannu tacire hijab din dake jikin Aneesa, tareda after dress din daya boye asalin shigan dake jikin Aneey din
Wani mayen kallon take binta dashi tamkar zata cinyeta danya
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[8:16PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*6*
Alhaji Adam zaune ababban falon sa , gefensa matarsa ce hajiya safeeya wayansa yadauki rury, hannu takai tadauki wayan tareda mika masa
Amsa yayi ya kara akunni byn ya latsa ok, Alhaji shu'aib ne hakan yasashi kokarin mikewa , yanufi hanyar bedroom dinsa domin kebewa
Daga bangaren Alhaji shu'aib kuwa yasanar da Alhaji Adam din cewa , gashinan bisa hanya yanaso sutattauna mgn akan abnd yafaru ne
Hakan yasa Alhaji Adam din sanar dashi su hadu a farm house ne nashi Alhaji Adam, domin kokadan bayason su tattauna matsalan a gdn sa
Cikin sauri yadauki hula da car key dinsa byn yasake feshe jikinsa da turare, yafito yana duban hajiya safeeya yake fadin
"Umman Aysha zanje farm house munada meeting ne dazamu gabatar yanxu "
Adawo lfy taimai suka hero tare har zuwa babban main parlor na gdn, Ayshat ce kwance cikin shigan wata hadaddiyar gown ta boyel , tayi kyau harta gaji ganin Abban ta yafito cikin shirin fita , yasata mikewa ta iso garesa kaitsaye kanta ta kwantar akafadunsa tana fadin
"Abba fita zakai dayanzu nake shirin zuwa maka hira ,"
Shafa kanta yayi yana fadin "Aysha meeting garemu yanzu haka su dadynki Alhaji shu'aib sunacan suna jirana, "
Shagwabe face tayi tana fadin "shikenan Abba adawo lfy nima zuwa anjima nakeso inje gurin yusrah kasan jiya tadwo gara inje a kwance tsaraba dani"
Murmushi yayi yana fadin gud gal to adawo lfy yafice abnsa
Ita kuma Ayshat ta nufi room dinta domin gyara face dinta kafin ta fito don zuwa gurin yusrah
*****
Farm house Alhaji shu'aib da Alhaji Adam ne zaune , suna hira akan abnd yashafi harkokin business dinsu , na shigo da kayan gini zuwa motoci da sauransu daga kasashen ke'tare
Kafin daga bisani Alhaji shu'aib ya dubi Alhaji Adam yana fadin
"Wato Adamu duk yadda nake tunanin shushu zai fahimceni abn yaci tura, hasalima tsanata nake hangowa daga idanunsa karara, hakika nayi nadaman aikata LAIFIN BOYE, gashi yanzu natra dukiyan sai dai asanadiyyan tonan asirinmu gashi shushu na nema ya juyan baya "
Alhaji Adam ya nisa kafin ya furta "ka kwantr da hnklnk shu'aib shureim bazai taba iya juyama bayaba, kasani duk dana kwarai dole yaji zafin abnd muke aikatawa , amma ina tabbatr maka zai sakko ne "
Alhaji shu'aib ya karbi mgn yana fadin"to Allah yasa hakan ni yanzu abnd nakeso kasani shine bani ba duk wata harka damukeyi ada
Bazan cigaba da amsar duk wata kazamar kwangila ba, hasalima duk wani dukiyata danasan ta hanyar kazamar kwangila nasameta , na yanke shawaran sadaukar da ita ga marayu , zan gina musu gd inkuma basu tallafi
Zan cigaba da juya dukiyata ta kasuwanci ita kadai ta wadatar dani , domin banga anfanin inci gaba da wannan mummunar sana'ar ba , alhali jinina tilo namiji dana mallaka na neman ya juyan baya , Adamu na kunyata jiya agaban shushu
Nasani ban masa adalci ba idn har zan cigaba da aikata LAIFIN BOYE , domin tara kazamar dukiya sukuma injefasu cikin bakin ciki
Shureim yasanar dani bayason duk wani abu dana mallaka dominsa , matukar da dukiyan wannan harka nasameshi , kai takaima yana fadin yana kyamatar duk wani abu dana ciyar dashi da wannan dukiya ta kawalci da barna
Adamu to miye riban wannan harka tamu gara mutuba mubi tafarkin tsira , ko yaranmu zasu yafemana mummunan tabon damukai musu, domin wannan kadai ya isa abn gory agaresu "
Nikam tundaga ranan da shushu yaganmu cikin mummunan yanayi, naji natsani wannan fasadi damuke aikatawa , na tsani su minister da duk wasu manyan kasan nan , masu aikata laifuka irin namu zanbar wannan harkan koda zai zama sanadiyar karayar arzikina "
Jikin Alhaji Adam gaba daya yagama yin sanyi, tabbas yasani maganganun aminin nashi sune zallan gsky , yazama dole su tuba domin Allah da kuma kare nutuncin yaransu , duk da cewa sun riga sun musu tabon da bazai goguwa ba, domin komin dadewa sai ankira yaransu da cewa iyayensu kawalai ne mazinata , tir da biyewa son zuciyan dasuka yi abaya "
Sun dade sosai suna tattauna yadda zasu bullowa su minister , domin surabu lfy dasu da kuma yadda zasu gina gidajen marayu , da dukiyan dasuka tara da wannan harka tasu , daga karshe suka watse ko wannan su driver yajashi zuwa gd domin hutawa cikin iyalansa
******
Aneesa basuyi masauki a ko inaba sai akan makeken gadon Rufaida , samfurin Turkish bed wanda yagaji da haduwa
Babu abnd baa zuba na more jin dadin rayuwa cikin bedroom dinba, kaikace dakin wata babbar macece mai miji
Irin kallon datakebin jikin Aneesan dashi yasa Aneesan kokarin saka hijab domin tsokanar Rufin, cikin azama takai hannu ta fisge tana fadin plzz karki rufemin kayan dadina, waishin wani tsari kikaiwa su umma suka barki fitowa da wury haka?
Dariya Aneesa tasa tana fadin"cewa nayi bakida lfy sosai kina kwance nadai tsatstsara umma , ta tambayanmun Abba shinefa yau nasake sanar dashi shikuma harda bani kudin mota "
Takarishe mgn tana dariya sosai kafin daga bisani ta tsuke fuska, damuwace karara ta bayyana afuskanta , kafin tasake dora idanunta akan Rufaida wacce ta shagala akallon dukiyan fulanin Aneesa , wadanda suka cika kirjin taf atsaye suke cak tamkar basushan murza
Kafin tacigaba da fadin"zumata wlh natsani Abba na tsani halayyan sa nason kai da kuma son zuciya
A kullum natuna shine silar jefani a halin danake ciki sainaji natsanesa"
Zuwa lokacin idanunta sunyi ja alamun bacin rai, Rufaida ce tamike ta fice batareda tace komiba , bata jima ba tasake shigowa cikin bedroom din , Rabeca mai aiki tana biye da ita hannunta dauke da katon tray
Wanda aka shakoshi da juices da kayan lashe-lashe, ta dire tareda juyawa byn tamika gaisuwa ga Anee babe
Tana fita Rufaida na kulle bedroom din kafin ta dawo , ta dauki cup din juice mai sanyin gske ta tsiyaya , tamatsa dabda Aneesa ta kai cup din bakinta
Babu musu tashiga shan ruwan juice din sanyinsa naratsa makoshinta , saida tashanyeshi tas sannan Rufaida tasauke cup din
Wani kallo take bin Aneesan dashi gani tayi tasake fresh da kyau , ahnkl takai hannu tazare karamar rigan da batada maraba da babu dake jikin Aneesan,
Nashanunta suka fito muraran hakan yasa Rufaida kai hannunta kansu , ta fara murzasu ahnkl jikinta Aneeysosai tashiga , kafin takai bakinta kunnin Aneesan tana fadin
"Kiyi hakury zumata nasan zafin dakike ji azuciyanki , inaso kisama ranki zaki sami abnd kikeso , kinsan ina kishin wannan jikin plzz kada kiyarda kice zaki mallakawa wani shi ,
Wlh nida ke munrigada munzama bakin rai bakin fama, aurema zan barki sbd cikan burinki nason kidandani dadin namiji ,da kuma son kihaihu amma kisani bazan iya rabuwa dakeba zumata "
Duk wannan mgn da Rufaida keyi hannunta nakan kirjin Aneesa , tana murzasu son ranta kafin Aneesan tafara maida martani cikin kwarewa da sanin kan harkan
Kafin kace me sun tube junansu tareda fadawa wata duniya , ta aikata LAIFIN BOYE wanda dukkaninsu babu wacce iyayenta sukai nasaran gano halin da take ciki , sudai kawai sunsan irin zazzafan soyayyan darayan nasu kewa juna
Sun dauki shawon lokaci suna gamsar da junansu , kafin su sami natsuwa inda Aneesan byn tagama samin natsuwanta , take hawaye sosai wanda narasa dalilin yinshi
Shin natsananin dadine da gamsuwa ? Koko akwai dalilin zubansu ?
To amsar dai nagareni sai kucigaba da bina don jin yazata kaya
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[8:29PM, 4/12/2018] 閳ワ拷+234 806 060 4338閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writer's_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*7*
Rufaida ko tana kwance dai-dai ne haihuwar uwarta, wani irin nishadi takeji domin Aneesa tasan kan yadda takeyi tagamsar da ita,
Shiyasa duk cikin yan matan da take tarayya dasu tafisonta, tareda matsanancin kishinta ganin irin hawayen dake ambaliya afuskan Aneey
Yasa Rufaida mikewa tana jan tsaki ta nufi toilet , domin yin wanka don kuwa inda sabo tarigada tasaba ganin Aneesa na wannan kukan
Sai dai basuji dadin juna ba dazaran sun kammala mashaar su xata farah kuka, wanda sam batajin lallashi sai tayi mai isanta sannan take rarrashin kanta,
Ganin Rufaida tashigene yasa Aneesa cigaba da zubda hawayenta masu zafi, hawayan datakeyi tana zubdasune domin takaicin irin laifin datake aikatawa a BOYE, sam wannan harkan tanayinsane bada son ranta ba illah tsabar shaawa datai mata yawa
Wanda Abban ta yaki fahimtar hakan, yazabi kore mata samari tareda dora burin lallai saita hado masa degree, kafin ya aurar da ita wanda ita Aneesa sam ba burinta kenan ba, aure takeso atsarinta tafison tayi aure kafin kammala karatunta, amma fir abban nata yaki
Adalilin hakan yajawo mata fadawa wannan harkan, wanda take ganin shine kadai zai dinga kawar mata da sha'awarta, batareda iyayenta sun farga ba domin tana tsoron fishinsu da kuma aikata zina , amma tasawa zuciyanta dazaran tasami miji dole ne tayi aure
Bakaman Rufaida datayi muguwar nisa aharkan ba, sam bata shawan tayi aure sai dai takan bi maza wadanda sukai mata, kuma sosai samari ke kashe mata dukiya ita kuma tana wadata Aneesa da duk wani abu na jin dadin rayuwa
Fitowan Rufaida ya katse ma Aneesa tunani ta mike da kyar tafada bathroom din ,
Tsayin mintuna ta fito daureda karamin towel iyakacinsa kugunta , kanta sharkaf yake da ruwa kai tsaye inda Rufy take gaban mirrow tana busar da gashinta ta nufa
Wata handrayer Aneey tadauka tareda jonashi awuta , tafara busar dakanta gashi gareta na asalin fulanin domin ummanta fulani ce
Cikin mintuna 15 Aneesa tagama kintsa kanta tas sai qamshi ketashi ajikinta, shiganta tamayar kamar yadda ta fito gaban iyayenta
4:30pm dot suka fito daga room din Rufaida xuwa main parlour na gdn, inda hajiya khairy da bakuwarta ke xaune suna hira
Har kasa Aneesa tagaida bakuwar momy wato hajiya marwa, ta amsa cikin sakin fuska tana jinjina natsuwa irin ta Aneesa
Sallama taiwa momy suka fice zuwa compound din gdn , inda driver ke zaman jiran fitowansu domin maida Aneesa gd
Katon ledane shake da cosmetics xuwa ubansun perfumes, ke jibge ciki jakan hannun Aneesa Rufaida ta amsa tareda zuba mata kudade Wanda bansan adadinsu ba , byn ta mika mata ne tana Mirza yatsun hannunta take dadi
"My surgar sainazo ki kularmin da kanki plxx , "
Wani kallo na shaidanci Aneey ta aimata kafin ta furta angama Bakin rai
Driver yaja motar suka bar haraban gdn , yayinda Rufaida ta juya tanajin kewan Aneesa sosai cikin xuciya da gangar jikinta
******
Shureim shu'aib Abba aji ne ke tuki ahnkl cikin gwanancewa, tasowansa daga office kenan yana hanyan komawa gd ne, agajiye yake liss amma hakan bai hanashi biyawa, ya jido ice cream da meatbag ba domin yasan yana isa gd yusrah zata ce ina tsaraba
Koda ya iso gd kai tsaye part dinsa ya nufa domin watsa ruwa, byn yafito yasake shiryawa cikin bakin wandon jeans da shirt fara mai ratsin sky blue , yayi kyau matuka gashin nan akwance luff
Roba 2 na ice cream yasaka a frige dinsa , kafin ya kwashi sauran da meat bag din yayi part din momy
Yusrah da Aysha ne zaune sunata hira ana kwasan dariya , Ayshat na sanye cikin riga da skat na swiss boyel, sosai dinkin ya amshi jikinta tareda fito kyawunta, dan kwalin kanta yazame hakan yasa kake ganin jelan kananan calaban dake kanta na kwance abayanta
Hajiya kubrah sam hnkln ta nskan TV tana kallo , sallaman shushu da kuma azababben qamshinsa ya sanar dasu shigowan sa cikin parlon
Momy ce ta amsa sallaman tna fadin my son harka dawo, karisawa kusada ita yayi yana fadin momy nadawo
Jikawai yayi anrungumesa ta baya yana kokarin zama, yusrah ce kefadin oyoyo ya shushu , hannu yasa ya dungureta yana fadin my baby doll kedai bakya girmako ,
Dariya tayi sosai tana fadin sorry ya shureim ganin ledan hannunka ne naji gaba daya yawuna ya ya tsunke
Murmushi yayi yasakar mata ledan yana fadin"gashinan saiki je kitasha ai "
Momy dai nasauraransu bata tankaba, Ayshat ko idanu ta zuba musu ta dade sosai bata sanya shushun a idanunta ba, kasancewar bawai tafaye xuwa gdn bane tunda yusy ta tafi karatu
Shikuma bamai xaman part din momy bane sosai , koka xo balallai ko yana gdn kaganshi ba shiyasa tadade bata Gandhi ba saidai taji suna waya da yayanta salman
Sosai taga yasake wani mugun kyau da fresh , ita aduniya shureim yana birgeta, ahnkl cikin muryanta mai sanyi da dadin amo take gaidashi
"Ya shureim ina yini "
Sai da ya kalli side din kafin ya ansa gaisuwan fuskansa ba yabo ba fallasa, shisam bai kula da itama cikin parlon ba saida ta gaidashi
Daga haka bai sake kallonta ba ya fuskanci momy suna ngn, yusrah ta dauki ledan ice cream din suka wuce xuwa bedroom dinta
Karfe 7pm ana magrib driver yazo daukan Ayshat , har gurin mota yusrah tarakata da katuwar leda mai dauke da tsaraba
Koda dare tayi aka hadu domin yin dinner shushu kin shigowa yayi, sai yusrah ce takai masa part dinsa,
Tundaga ranan shureim ya canza gaba daya yadaina cin abnci tareda su apart din momy kaman yadda aka saba matukar dady yana gari , gaisuwa kadai kehadasu da dadyn shima ba cikin sakin fuska ba
Sam irin zaman hiran dasuke da dadyn yana shagwaba, suna tattauna abnd yashafesu ya janyeshi, sam daga gaisuwa shikenan zai tashi ya fice
Idn kaga shureim yasaki face to da momy ne ko yusrah, hakan bakaramin cin zuciyan dadyn yake ba
Yau takama weekend saty 2 kenan da faruwan abnd shushu yaga iyayen nasa na aikatawa,
Misalin karfe 10am shureim ya fito daga part dinsa , yana sanye cikin rigada wando na da'nyar gezna kalan sky blue , sosai yayi masifar kyau cikin kayan kasncewan sa mai farin fata , sai dai farinsa ba irin tau dinnan bane fresh ne sosai
Shureim yakaiduk wani level dazaa lissfashi cikin jerin kyawawan maza, dasukanyi karancin samu ya hadu takowani fanni,
Kaduna yake shirin xuwa inda zai shafe tsawon 1 week , yana gudanar da wani aiki da aka turashi a branch din dake nan kd
Da sallama ya shiga part din momy saidai falon tsit yake, yana kokaryn zama momy na fitowa daga part din dady
Hakan yasashi karisawa tareda rungume ta yana gaidata, itama rungumeshi tayi tana fadin kai my son wannan wanka haka, kodai surukar tasamu ne ?
Sosai ya shagwabe fuska yana fadin "kai momy kinfaye zolaya nikam bansami kowaba, ni sam haryau banga yarinyar data kwantamin ba, inajin dai saikin zabomin mata donni nagaza samu"
Murmushine ya kwace a fuskan momy cikin matukar farin ciki take fadin , da gske kakeyi my son kai amma naji dadi zanko yima zabin dazakai alfary dshi shushu,
Shureim ganin farin ciki kwance fuskan momy hakan yasa yaji , lallai awannan karon dole yayi hakury yabata dama domin cikan burin ta nataga yayi aure, zai zauna da duk zabinda zatayimai domin yasan bazata taba zabamai abnd zai cutar dashi ba
Alhaji shu'aib ne ya fito daga part dinsa yana gyara babban rigarsa da alamu fita zaiyi shima,
Yaji duk abnd su momyn ke tattaunawa da shushun, hakan yasa cikin fara'a yakariso cikin falon yana fadin kubrah keda dan lelen nakine kuke zantawa,?
Cikin farin ciki take kokaryn yimasa bayanin abnd suke mgn akai , ya dakatar da ita ga fadin naji duk abnd kuka tattauna kubrah Allah yai zabi nagari
Shureim wanda tun fitowan dady ya tsuke fuskan sa tamkar bai taba dariyaba, batareda yabari idanunsu sun hadu ba ya furta "gud morning dady "
dadyn ya amsa da "morning my son sai ina naga ansha wanka haka"
Shushu yasaci kallonsa kadan kafin ya furta , "kd zani dady akwai aikin dazan gudanar na saty guda "
Alhaji shu'aib ya dubesa yana fadin"to Allah yabada nasara idn kadawo inaso mu tattauna muhimmiyar mgn dakai son "
Shushu ya amsa da to dady saina dawo din, yusrah ce tasakko daga stairs tagama hadewa cikin bubu na wani lace mai azabar kyau , tayi kyau harta gaji qamshi kawai kefita ajikinta
Bata dubi kowaba saida ta isa ga dady tashige jikinsa , rungumeta yayi yana fadin autan dady anfito , cikin shagwaba take fadin
"Eh dady shushu taduba tana fadin ya shushu gud morning tun 9nake jiran shigowanka kaki tashi dawury yauko, takarishe mgn tana shagwaba "
Shureim ya sakar mata murmushi yana fadin dubeta batasan ta girmaba, wai mantawa kike yanzu kinzama big gal ne degree fa gareki ba yar primary kikeba , kike wannan sangarta baby doll
Dady ne yace babu dai ruwanka da auta kaima naga haryanxu bawai kagirma da shagwabar bane,
Ganin dady na neman samin kafan jansa da hiran da suka dade basuyi ba, yasa shureim yimusu sallama domin tafiya
Tafiyan 1hour da mintuna 40 yakai shushu garin na gwanma , kai tsaye a hotel yayi masauki sai da yahuta yai wanka yasauya kaya , sannan yafito domin zaga gari
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[5:50PM, 3/22/2018] 閳ワ拷+233 50 348 1936閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*8*
Bayan kwana biyu da zuwan shureim kaduna, misalin 4 na yamma tasowan sa daga office dinsu kenan, yayi wasu interview tuki yakeyi ahnkl ksancewan yagaji
Hanyan dazai kaishi Mangal plaza yadauka, domin yanason siyan cable na iphone ya manta nashi a Abuja
Parking dinsa kenan ya fito daga cikin motan , yana kokaryn shiga sukuma suna kokaryn fitowa
'Yan matane su biyu kyawawan gaske daya nasanye cikin after dress tasha rolling, takalmi ne mai tudu akafarta yayinda ta rufe face din da katon bakin eyes glass
Dayan nasanye cikin wani hadadden laces riga da skat , kafanta sanye da bakin safa yayinda jikinta ke rufe da hijab wanda tsayinsa ya wuce guiwarta kadan, fuskanta sanye da farin eyes glass wanda yai matukar yimata kyau ba kadan ba
Tunda shushu yasauke idanunsa akan wannan matashiyar budurwan yaji, wani abu wanda vaisan komiyeba ya tsirga mishi a kahon zuci, da karfi bugun zuciyansa ya karu idanunsa kyam akansu , har suka kawo dabdashi suna kokarin wucesa, sam su basuma kula da shiba hnkln su kwance suke kokaryn wucesa
Hakan yasa shureim sauke wata Irin ajiyan xuciya, byn sun nufi wata katuwar mota suna kokaryn shiga back seat,
Karfin hali hali yayi yaja kafafunsa domin xuwa garesu , don abnd zuciyansa ke tunzurasa kenan
Aneesa takai hannu domin rufe kofan motar saiji tayi anrike murfin motan, tunkan takaiga mgn wani fitinannen qamshine yacika hancinta
Leko da kanta tayi domin ganin wani mai karanbanin ne wannan, idanuwanta ne sukayi arba da hadadde kuma kyakykyawan matashin saurayin
Rass taji gabanta yayi mummunan fadi bata taba cin karo da handsome guy irin wannan dake tsaye gabanta ba
Sai dai cikin karfin hali idanunta akansa tamkar yadda shima idonsa ke kanta, tayi mgn cikin muryanta mai matukar taushi da dadin amoh take fadin
"Mallam lfy yada haka? zakazo ka kama kofarmota ka rike "
Murmushin dabaisan sadda yasubuce aface dinsaba yasakar mata, kafin yafurta "uhumm 'yan mata sorry ko don Allah inba damuwa inason ganin 2 minit plxx"
Rufaida data fara kosawa Aneesa taduba kafin tamaida dubanta ga shureim tana fadin"kana iya tambayan aminiya idn tabaka dama babu damuwa"
Rufaida ce takatse Aneesa da fadin "plxx baby fita kisallamesa mu wuce sam Rufaida batama tsaya kallon shushun ba idanunta nakan wayan hannunta , datake chart da saurayinta salman Adam
Ahnkl ta fito daga cikin motar ta jingina jikinta, kafin ta saci kallon sa wanda idanunsa nakanta
Shureim yafara da fadin" sunana shureim ni mazaunin garin Abujane , Nazo gudanar da wani aikine anan garin, shigowata kenan na hango ku mgn gsky farat daya naji kin birgeni , abnd ban tabaji akan wata 'ya maceba hakan yasa nayi karfin halin isowa gareki inba damuwa inaso kibani Phone number dinki, naga alama saury kuke karna bata muku lokaci"
Aneesa gaba daya jinta take cikin wani yanayi , shushu yagama tafiya da zuciyanta farat daya , mgn sa ma kadai bakaramin sake kashe jikinta yayi ba , ba musu tashiga karanto masa digit dinta yana sawa cikin phone dinsa
Saida ya kammala yasake kallonta yana fadin"to malamar bata fadamin sunan ta ba "
Saida tasaki murmushi wanda har dimple dinta suka lob'a , kafin tafurta "kayi saving da Aneesah "
Aneesahh yaja sunan kafin ya furta nice name , saikin jini zuwa anjima baijira jin komiva yayi gaba abnsa,ya barta da shakan fitinannan qamshinsa, sai bin byn sa tayi da kallo tana yaba class dinsa , uwa uba kyau da muryansa mai matukar dadi take sake jiyo amonsu cikin kunnuwanta, kiran sunanta da yayi kuwa jitayi duk duniya babu wanda ya iya fadin tamkar shushu
Koda tashiga mota Rufaida tacika tayi fam, cikin masifa take watsa mata wani irin kallo, kafin ta furta" zumata wai waye wannan da kika tsaya saurara haka ? "
Aneesa tadubeta tana kashe mata idanu take fadin"Bakin rai wlh wani handsome guy ne nayi kamu, nikam fitowanmu tayau tabiyani don gsky farat daya naji gayen yayimin"
Wani irin kallo Rufaida kebinta dashi yayinda zuciyanta ya buga da karfi, me Aneesa ke nufi da hakan ? tabbas tanaso tajanyo wa kanta, don sam bata kaunar ranan da zataji Aneey ta furta kalman so gawani da namiji, domin hakan na nuni da barazanan cewa zatayi aure wanda bata fatan hakan, tafiso su dawwama ahaka suna sheke ayarsu , kaji son kai dai irin na Rufaida hmm
Batace da ita komiba driver yaja motar suka fice daga plaza din , kai tsaye gdn su Rufaidan suka yada zango ,
Yauma kaman koyaushe swida suka murji juna sosai, kafin su sami natsuwa Aneesa na kwance akan kirjin Rufaida , yauma kuka takeyi tamkar koda yaushe hawaye nasauka bisa kirjin Rufaida
Ahnkl Rufi tasa hannunta tana murza kirjin Aneesa , daya hannun na lalubarta ta kasa muryanta adishe yake , alamun tana son kary amma sai dai Aneesan ne tajanye jikinta , murya can kasa take fadin My surgar plzz stop it marata ciwo take , kinsan karshen month yayi period na keson zuwa
Rufy sam bata saurara mata ba saida suka sake aikata tsiyarsu , domin jarababbun matane ajin karshe
Rufaida ta mike tafada tiolet domin gyara jinkinta , yayinda Aneesa tacigaba da hasko fuskan shushu na mata yawo , duk ta kosa tasake sauraron voice dinsa mai matukar dadi
Koda ta gyara jikinta bata dauki dogon lokaci ba ta bukaci wucewa gd , domin tasan halin Abba idn yadawo bai sameta a gdn ba, dama kuma donyayi asubancin zuwa zaria ne hartasamu da kyar umma tabata daman fitowa daga gdn
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[5:50PM, 3/22/2018] 閳ワ拷+233 50 348 1936閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writer's_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*9*
Hajiya kubrah ce zaune itada yusrah , sun baje uban kaya tundaga kan handbags takalma zuwa fashions jewelries , hadaddun gske wanda aka turo mata Daga kasar China
Yusrah ke zaban set guda akowanne ciki tana yin gefe guda dashi , zuwa can tadubi hajiya kubrah tana fadin momy waini kam yaushe , zaki bude plaza ne domin kasuwancin nan yakarbeki Sosai
Hajiya kubrah tayi murmushi tana fadin"wlh auta abnd nake bury kenan bary shushu yadawo ayi shawarah, domin ko dady surprise zamuyi masa sai abn yatabbata zaiji lbry
Wasu hadaddun hand bags da takalma , momy taware su wanda kudinsu zaikai 50k , ta dubi yusrah tana fadin auta aje wannan tareda naki na Aysha ne
Yusrah ta janyesu tana fadin"lallai Ayshat takice momy nasan zataji dadi sosai da wannan kyautan"
Masu aikin hajiya kubrah ne ke kwashe kayan zuwa wani daki na daban, kafin zuwa anjima afara zuwa duba kayan, sosai take ciniki matan manya da student rabi kuma tasararwa 'yan kasuwa
Yusrah ma nata dana Ayshat ta kwasa zuwa upstairs , koda ta sakko momyn nazaune wannan lokacin waya takeyi , tana sanar da aminanta kaya sun iso
Koda tagama wayan kallon yusrah dake faman latsa waya tayi, tana fadin"yusy kinsan abnd nake shiryawa araina kuwa gameda shushu?
Yusrah ta aje wayan hannunta tana fadin"saikin fadi momy me kike shiryawa big brother din nawa ne"
Momy take fadin"dazu nakemai mgn aure shine yace yabani zabi , duk wacce naga tadace dashi zai amshe ta hannu biyu, to nikam gsky babu yarinyar danake ganin tadace da shureim sai Aysha,
Aysha itace yarinyar da takwanta min arai nadade ina shaawar shureim ya aureta, inadai kauda kaine sbd banaso insashi ya aury abnd bashida raayi , da kuma ganin sam bayama shiga sabganta
Amma tunda yabani dama ayanzu to itace yarinyar dana zaba mai tazama abokiyar rayuwansa"
Yusrah wani ihun murna tasaki tana fadin gsky momy kinyi tunani mai kyau, Aysha tanada nutsuwa da kuma kamun kai ga ilimin addini daidai gwargwado tasan abnd takeyi, zakuma sudace da juna"
Gasky momy nayi farin ciki dama ya shushu yadade yana birge Aysha, nasani tana sonshi kawai dai kunya da zurfin cikin tane yasa takasa bayyana hakan
Sosai momy taji dadin mgn da yusrah tayi , tareda jin kwaryn guiwan dazata tinkary hajiya safiya da mgn , domin sam bataso a aje lokaci sbd gudun kar shushun yasauya mgn
*********
Washegaryn ranan hajiya kubrah da kuma yusrah suka isa gdn , aminin mijin nata wato Alhaji Adam, rungume juna sukayi tsakanin momy da kuma hajiya safeeya , wadanda suke aminan junane,
Aysha da yusrah sukai masauki adakin Ayshan, cikin murnan wannan ziyara da suka kawo ,Aysha nasanye cikin wandon jeans daya fito da hips dinta , sai karamar top data kamata tareda fito da surar kirjinta dake cikeda dukiyar fulani, kasan cewan garin da zafi shiyasa sanyin Air condition yacika dakin ta ko'ina,
Yusrah ce take fadin shegiya Ayshat kinga yadda kike sake cikane , kinyi wani kiba sbd angama skul sai zaman hutawa ko, kafin musha biki mukaiki dakin miji
Aysha takai mata duka tana fadin wlh yusy bakida kyau , nikam ban shirya aureba hasalima bani sauraren kowa, mutum daya nakeso amma sam baimasan ina dakon sonsaba, nakuma san dawuya insamesa yusy , zancigaba da dakon sonsa domin banaji zan iya cire sonsa araina ,
Tuni har idanunta sun canza launi , yusrah ta dafa kafadunta tana fadin"miye abn damuwa Ayshat shiko wannan waye daya sami babban gurbi axuciyanki haka "?
Any way ko waye kiyi addua kawai idn har rabonkine zaki sameshi cikin ruwan sanyi
Amma zanso inji wanene wannan wanda kika mato kansa haka
Aysha ta jinjina kai tana fadin"hmm hakane yusrah shiyasa addua kadai narike inayi , batareda na fallasawa kowa sirrin dake raina ba"
Plxx kuyi maneji da wannan ina busy ne , zakujini soon insha Allah , tnx 4 d luv and support 棣冩
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[5:50PM, 3/22/2018] 閳ワ拷+233 50 348 1936閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*10*
Hajiya safeeya da hajiya kubrah ne zaune cikin bedroom din ummah hajiya safeeyan,
Momy ta dubi hajiya safeeyan tana fadin"umman Aysha wato wata muhimmiyar mgn nakeso mutattauna , daga haka takwashe yadda sukayi da shushu tafadama hajiya safeeyan,
Ta kare mgn tana fadin shiyasa nataso domin mutattauna, sbd nina yanke shawaran muhada Aysha da shureim , domin dorewan zumuncin mu nayaba da nutsuwan Aysha , amma ki tattauna da ita idn har bata da raayinsa, bazamuyi mata doleba"
Hajiya safeeyan wacce farin ciki ya lullube ta ke fadin"karki damu momyn yusy wannan abune mai sauki nikaina nadade ina tunanin hakan, amma kinsan halin yaran zamni bakasafai suke yadda da hade hade ba, amma tunda shiyabada xabin anemamai, zanyi mgn da Ayshat abnd mukayi zakiji feedback ayau da dare basai gobe ba"
Koda su momy suka tashi tafiya gurin mota Aysha tarakasu, tanata godia akan kayan da momyn ta kawo mata,
*******
Aneesa kwance tayi ale-ale akan bed dinta chart takeyi itada Rufaida , da sauran friends dinta sai dai gabaki daya hnkln ta da tunaninta nakan shureim
Sauraren kiran shushu kawai takeyi amma taji shiru, daga kanta tayi tana sake kallon agogo karfe 10 harda kusan rabi,
Kashe data tayi ta jefar da wayan kan bed din, tarasa meyasa shushu yayi karan tsaye cikin zuciyanta farat daya, bata taba haduwa da saurayin dayayi saurin sace xuciyanta irin shureim ba
Tayi samary da dama abaya wadanda tasosu amma sam , bata tabajin abnd takeji akansu yadda takeji akan shushun ba,
Karan wayanta ne yakatse tunaninta cikin hanzari tadaga wayan , byn tasake narke murya tayi sallama
Daga bangaren shushu wanda ke kwance bisa makaken bed din dake dakin hotel din daya sauka, jin muryanta kawai dayayi yasa shi sake gyara kwanciyan shi kafin ya amsa sallaman da fadin
"Wa'alaikumussalam pretty malama Aneesah kinji ni shiru , sorry ayyukane sukasha kaina sai yanxu nasami lokaci, Allah dai yasa ban katse ma malamar bacci ba"
Aneesa wacce tayi lamo tana sauraren muryan shushun, wanda yake saukar mata da wani irin kasala , ta amsa da fadin"no baka katsemin bacci ba dafatan kana lfy "
Shureim ya amsa da fadin"lfy nake Aneey sai dai kinmin wata irin sata wacce baa taba yimin irin ta ba"
Aneesa tazaro idanu tamkar shushu naganinta , kafin tashagwabe murya tareda sake narke muryan take fadin"sata kuma shureim wani iri kenan? "
Dakyar ya saita kansa domin kuwa yaji wannan shagwabar ta Aneey har cikin gangar jikin sa,
Cikin karfin hali yayi mgn yana fadin "satan zuciyata kikai Aneesa bada wasaba kinyi nasaran sace zuciyata farat daya,
Abnd bantabaji akan kowace mace ba , gsky Aneesa nafada tarkon sonki , wanda nakeji idn har bansameki amatsayin mata ba , bani da sauran nutsuwa ina fata wani baiyi nasaran sace hrt dinki ba?
Ya karishe mgn cike da karyewan zuciya "
Aneesa wacce kejin wani farin ciki wanda tadade bataji irin shi ba, cikin muryanta mai dadi tasake narkesa sosai kafin ta furta, "babu wanda ya sace zuciyan shureim , kuma ina maka albishir da cewa Aneesa takamu da soonka tamkar yadda ka kamu da nata , "
Wani dadine ya ziyarci zuciyan shushu tareda wani nishadi , cikin dansa yake fadin dama haka so yake , gasky bai taba tsintan kansa cikin yanayin dayakejin zuciyansa ayanxu ba
Sosai hira ya tsinke tsakaninsu Rabin hiran Aneey ce ke kirkiransa, domin shushu rasa abnd cewa yake abnka dafarin shiga wanda baisan kan soyayya ba, sun dade suna musayn muryoyinsu tsakanin juna
Sunajin nishadi nadaban atattare dasu har xuwa 11 nadare kafin suyi sallama, ko wannan su najinsa cikin farin ciki mara misaltuwa
Wanda shureim baccin sa na ranan gaba daya yayisane cikeda mafarkin ya mallaki Aneesan
****
Hajiya safeeya ce tareda Aysha cikin bedroom din umman , kafin ta dubi Ayshat din tana fadin"shatu kisaurareni mgn muhimmiya ce zamuyi dake
Dazu momyn shushu tazomin da mgn son ayi hadin zumunci tsakaninki da shureim din, tazabeki amatsayin kizama suruka agareta, banaso ki cuci kanki ko kiyi kawaici akan abnd bakida raayi akai
Hakan yasa mukace saimunji ta bakinki kafin muyanke shawara, domin shushu shiyaba momyn sa dama tazabamai mata , hakan yasa itakuma tazabeki bisa yaba nutsuwa da hnklnki
Don haka idn kinada wanda kikeso karki boyemin komi kisanar dani , ni uwace bazan so kitauye farin cikin ki domin cikar burin wani ba, momy wayayyan macece wacce zata fahimceki "
Jikin Aysha ne yayi sanyi yayinda takejin wani farin ciki na ziyartan zuciyanta, tabbas shureim shine kadai namijin datakejin sonsa har cikin jininta, shine namijin datakejin bazata iya yakiceshi cikin ranta ba, sai dai tana boyewane sbd hakan shine rufin asirinta ,
Sai dai ayanxu datake sauraren ummanta jitayi tsohon mikin sonsa datake dannewa yataso gabaki daya
Cikin karfin hali ta dago tadubi umman kafin tafara mgn ahnkl tana fadin
"Umma nikam banida wani wanda natsayar inaso , don haka duk hukunci da kuka yanke zan amsheshi hannu biyu, domin nasan bazaku taba yanke hukuncin abnd zai cutar dani ba
Sai dai fatan Allah yasa shidin yakarbeni amatsayin zabin momyn, takarishe mgn ahnkl tana hawaye , wanda azahiri na farin cikin xata mallaki abnd zuciyanta kesone, duk da batasan shi shureim din ko aya zai karbeta ba idn yaji itace zabin momy
Sai dai tanaji koma aya zai karbeta zata zauna dashi, tacigaba daraya sonsa cikin zuciyanta koda ko shi zai nuna rashin so agareta
Hannu taji na ummanta bisa kafadunta tana fadin" yawwa Aysha Allah yai miki albarka kuma ina mai tabbatar miki bazakiyi nadamn auren shureim ba, domin shushu yaron kirkine wanda zamuyi alfari idn wannan abu yatabbata
Tashi kije zanyi mgn da hajiya kubrah infada mata yadda mukayi , Allah yai mana zabi na alkhairy kinji ko
Ameen Aysha ta furta tana ficewa daga bed room din momyn zuwa nata, gado tafada tana sauke ajiyan zuciya mai dadin gaske
Ahnkl ta lalubo wayanta tareda zakulo pic din shushun , wanda awayar yusrah tatura batareda ita yusyn tasani ba
Yayi masifar kyau a pic din wwnda yadaukeshi awani hadaddan gurin shak'atawa a garin Miami dake kasar America, yayi kyau harya gaji shafa pic din takeyi da hannuwanta yayinda , takejin soyayyan shureim Abba Aji nasake bin jinin jikinta
Ta dauki lokaci mai tsawon gske kafin bacci yai nasaran saceta ,cikeda mafarkai barkatai duk na shushun
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
[5:51PM, 3/22/2018] 閳ワ拷+233 50 348 1936閳ワ拷: *LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*11*
Hajiya safeeya bata sami kiran hajiya kubrah ba, sai washegary byn sun tattauna mgn da Alhaji Adam, wanda haryaso yafita farin ciki dajin wannan tunani dasukayi , nason hada auren tilon yar sa mace Aysha
Da shureim wanda zaiyi matukar alfary da hakan ,domin yasan waye shushu yasan Irin nutsuwan da kamun kansa, yanajin Allah yasa shi shushun ya amince idn yaji wacece zabin momyn tasa
Coz shi kanshi shaidane akan cewa ayanxu babu wanda shushu yake ganin bakinsu , tamkar shida mahaifinsa sai dai Alhaji Adam yadanne damuwansa yayi fatan alkhairy
Koda hajiya safeeya tasnar da momy yadda sukayi da Aysha, bakaramin farin ciki tayiba fatanta shushu yadawo agabatar da baiko batare da wani jinkiri ba,
Karfe 10 nadare hajiya kubrah ce sanye cikin nighties masu azaban kyau , irin nasu na manyan mata sosai take zabga qamshi mai matukar saukar ma mai shakansa da nutsuwa
Bedroom din Alhaji shu'aib aji ta tura tashige, wanda tasameshi kwance bisa gado , gefenshi cup ne daya shanye ruwan ganyen shayi na green tea , wanda tagabatar mai kafin ta tayi kintso kanta
Kusada shi taje takwanta kafadunsu na gugan najuna, qamshin daya shaqa nata ne yasashi sake shigewa jikinta
Ahnkl take furta "dadyn yusy mgn nakeso muyi gameda hadin auren shushu da Aysha , "
Tashi yayi zaune kaman yadda momyn itama tazauna , saidai haryanzu jikinsu nahade dana junane ,
Kallonta yayi kafin ya furta "Aysha yarinyar Adam kike nufi wai? "
Gyada kai tayi tana fadin"kwarai kuwa itace yarinyar dana zabamai domin zasu dace da juna, kuma zumuncin mu zaifi dorewa yana naga kaman fuskar ka tanuna akamun damuwa? "
Dady wanda yai kokaryn boye damuwansa ya zakulo murmushi , yana fadin"haba momyn yusy kema kinsan saina fi kowa farin ciki , kawai dai muyi fatan zabin yaiwa shi shureim din , kinsan bazan Goya baya ayimai abnd baida raayi ba
Duk da cewa shiyabada goyan baya ayimai zabin daya dace dashi, Allah yashige gaba yatabbatar da alkhairy"
Momy ta amsa da ameen karka damu ninasan shushu bazai taba bani kunyaba, kuma kai shaidane kullum yana mana biyayya, kuma Aysha natsatstsace wacce zaiyi alfari da aurenta , ahnkl zasu so junansu insha Allah "
Daganan suka cigaba da tattaunawa akan yadda komi zaitafi batare da anbata lokaciba
********
Bada bata lokaciba soyayya mai karfi ta kullu tsakanin shushu da Aneesa, wacce takejin ayanxu xata iya batawa da duk wani wanda zai mata shamaki da mallakan shureim
Tundaga randa suka fara waya akalla kullum sai shushu yakirata fin sau 5 arana, da dare kuma zasu dauki dogon lokaci suna chart , ana musayan kalaman soyayya mai tsafta
Gaba daya shushu yagama sallamawa yayi dace da irin macen daya dade yana mafarkin mallaka, domin Aneesa bata taba anfani da wata kalma da zai nuna mai itadin tanada wani aibu ba,
Saima nunamai datake itadin fa cikakkar mai kamun kaice , Sbd Aneesa daidai gwargwado anbata ilimin addini mai zurfi , hakan yasa Abba ke ganin bazata iya aikata wani abn ashsha ba,
Yau yakama 1 week da xuwan shureim kd kenan, kuma ayau din yake son wucewa Abuja hakan yasa tun safe yashaidawa Aneesa yanaso su gana kafin yawuce
Domin bazai iya wucewa baiyi tozali da itaba , duk da cewa kullum cikin turamasa pics take , amma sam bata yarda tayi pic din dazaiga aibunsa
Tunda shureim yasanar da Aneey zancen zuwansa gdn su , hnkln ta yai kololuwa gurin tashi domin tasan , kotasha giyan wake ne bazaa barta fita ba bare tayi dabaran kaishi gdn su Rufy
Kwance take akan bed tarasa wani dabarace zatayi , wanda zaisa abarta tafita domin bataji zata iya sabawa shushu kota bata ransa
Muryan Abbanta ne yakatse tunaninta yana kwalla mata kira , cikin hanzari ta yo waje zuwa parlo inda takejin amon muryansa
Tsaye tasameshi cikin shirin fita yaci babbar riga , rusunawa tayi tana fadin gani Abba
Kallonta yayi yana fadin "Aneesa inaso karfe 6 ku shirya abncin da mutum 5 zasuci , keda mai aiki kuyi komi akan tsari zani zaria indawo , ban amince kifita ko ina ba inafatan kingane tashi kije "
Aneesa ta amsa da cewa "to Abbas adawo lfy "
Ameen ya amsa yana binta da kallo yayinda sonta ke karuwa azuciyansa, yanason Aneesa sosai tareda yaba hnklnta da nutsuwan dayake gani tattare da ita , sbd baisan tana aikata *LAIFIN BOYE* ba
Shigewa tayi bedroom dinta tabarshi da umman ta , bata wani jimaba tasake fitowa byn taji tashin motansa alamun yafita
Dakin ummanta ta nufa wacce tasameta tana sake saka turaren wuta abedroom din nata, qamshi kawai ketashi bakin gadon tazauna tana zare idanu
Umma tadubeta tana fadin "Aneesa lfy daiko ? "
Neesa tadubi ummanta tana fdin "wlh umma wani alfarma nazo nema dama wani sabon saurayi nayi , to shine yau yakeson xuwa musake ganawa sbd Abuja yake , aiki ya kawoshi nan kd nan dai takwashe komi gameda shureim tasanar da ummanta
Wanda takarishe mgn tana fadin " wlh umma shureim natsatstsan mutum ne kuma dagske sona yake da aure, kuma nima nakamu da sonsa wlh Allah ummah
Ke mahaifiyace agareni bazan iya boye miki komiba, kibani goyan baya na saurari shureim domin wlh umma ayanxu aure shine cikar bury na
Kuma bantavaji na kamu dason wani namiji kaman yadda nakejin shushu araina ba, Amma nasani idn Abba yaji koransa xaiyi kaman yadda yashayi abaya
Narasa meya Abba ke koremin samary, ayanxu nsgama degree wlh aure nakeso umma , kitaimakeni awannan karon kinunawa Abba cewa aurene araina ba boko ba"
Umma kiyi hakury dani domin Abba yafara kaini bango , har inajin nafara jin tsanansa akan son zuciyansa dayakebi yana neman tauye rayuwata
Wlh umma natsani Abba domin nikadai nasan irin halin daya jefani ciki asanadin son zuciyan.....
Batakare mgn taba taji saukan wani lafiyayyen mary akan fuskanta, wanda yasa ganinta yadauke na wucin gadi kafin cikin fada umman tafara fadin
"Aneesa kina haukane mahaifinki kike fadin kin tsanesa, shikike fadiwa munanan kalamai irin haka? , tobari kiji kiyi gaggawan saita bakinki ko intsinke harshen ki , sha sha sha kawai insake jin irin wadannan kalaman nafita abakinki"
Aneesa durkushe wa tayi kan bed din tana kuka sosai, tasani umma bazata taba fahimtar metakeji cikin zuciya da gangar jikinta ba, bazata taba gane illan da son zuciyan Abba yajefa rayuwanta ba, sbd bata fito da *LAIFIN BOYE* fili ba, tabbas wannan karon dole tabijire wa Abba matukar bazai bata goyan baya akan shushu ba
Bazata taba dora wani masters dayake bury ba, aure takeso ba karatu ba , tagaji da aikata **LAIFIN BOYE* duk adalilin son zuciyansa
Idanunta tasauke masu zubar hawaye akan ummanta, wacce take kallonta wannan karon jikinta yayi sanyi ganin yadda Aneesa ke kuka sosai
Tabbas tasani Aneesa takai munzilin dazata bukaci aure, kuma daidai gargwado tayi biyayya gurin cika burin Abba nasamin ilimin boko mai zurfi
Ita kanta tafi shaawar Aneesa tayi aure amma Abba yakauda kai
Aneesa ahnkl taje kusada umma takwantar dakanta akan cinyarta, har zuwa lokacin kuka take tana fadin"umma kiyi hakury nadaina wlh zuciyata ne ke matukar zafi , nasanar dake gskyn abnd ke raina ne sbd hakury na yakare awannan karon "
Inason shureim shima yanasona umma kibani goyan baya nasaurari mutumin dayazo da niyyan aure gareni , plzz umma kiji tausayina kinji takarishe mgn cikin karyewan zuciya"
Jikin umma gaba daya yagama yin sanyi tausayin d'iyanta yakarya zuciyanta, ahnkl take patting bayanta tana fadin"na fahimceki Aneesa awannan karon nima bazan goyi bayan son ran abbanki ba, tunda har kika furta aure kikeso to shizakiyi da izinin Allah , nabaki dama yazo kugana kafin yawuce inyaso nida kaina zantinkary Abba da mgn "
Ki kwantar da hnklnki kiyi ta addua kinji maza tashi kije kisama masa abnd zaici , kafin ya iso amma kiyi komi cikin lokaci banaso abbanki yadawo yafahimci wani abu
Kina sane kuma da umurnin sa don haka kiyi hanzari "
Cikin murna sosai Aneesa ta tashi tana ma ummah godia , kafin tafice tana share ragowan hawayen fuskanta
Umma tabita da kallo yayinda tausayi da tsoro yadarsu cikin ranta, tabbas tunda har Aneesa ta iya furta wadannan kalaman, yazama dole sumata auren don gudun abnd zaije yadwo , sai yau take sake Allah wadai dason xuciya irin na abban Aneesa
Yaushe awannan zamanin 'yar ka zata nuna son aure , kai kuma kadage saitayi boko sosai takejin lallai wannan karon dole tagoyi byn Aneesa , bazata amince dawani batuba inbana ya aurar mata da d'iyaba
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*12*
Aneesa ce ke kaikawo tsakan dakin da Abba ke sauke baki da kuma kitchen , tana shirya abncin datayi don tarban shureim Aji
Tasha wanka tashirya kanta cikin hadadden after dreess mai azaban kyau da tsada, Rufy tasai musu atafiyar datayi kasar Dubai, tasha light makeup a faces dinta, tareda yin rolling akanta sai tashin fitinannen qamshi kakeji ajikinta
Saida taga komi yayi yadda takeso ta koma cikin gd , kaman jira ake tana shiga room dinta wayanta na tsuwwa, shushun natane ke kira hakan yasa ta dauki wayan cikin kashe murya
Sanar da ita yayi gashi nan awaje hakan yasa tana rike da wayan , take xira flat shoe dinta tayi waje , karo sukaci da ummanta dake kokaryn shigowa dakin, hakan yasa Neesa kashe wayan tana duban umma take fadin "sorry umma ga shureim nan ya iso zan shigo dashi "
Umma tabita da kallo tana fadin"to maza shigo dashi "
Aneesa tafice tana takunta cikin nutsuwa da yauki, umma tabita da kallo aranta take fadin lallai da gske Aneesa tna qaunar shureim
Domin bata taba ganin d'iyartata na irin wannan rawan jikin akan namiji ba
Bakar mota tahango ta parka hakan yabata tabbacin shushu ne, tana kokarin dialing number dinsa sai gani tayi ya fito,
Yana tunkarota sake karemai kallo take tundaga sama har kasa, ayau sai sake gani tayi yayi mata kyauma fiyeda ganinta nafarko dashi, yayi kyau sosai cikin shigan qananan kaya , wanda yai masa kyau idan sa rufe cikin farin eye glass
Koda yakariso kusada ita saitayi saurin dauke idonta akansa, murmushin sa mai tsada ya sake mata,
Juyawa tayi yana biye da ita abaya har xuwa dakin bak'i, duk wani motsi da takunta akan idanunsa yana sake karema surar jikinta kallo
Bakaramin kyau Aneesa tai masa cikin shigan datayiba , sosai yake sakejin sonta cikin zuciya da ilahirin jikinsa
Tana jifansa da murmushi take nuna masa daya cikin kujerun dake parlon, ya zauna itama tazauna awacce ke facing dinsa
Kafin ta surusuna kadan tana fadin"barka da zuwa dafatan ka iso lfy"
Saida yasanya idanunsa cikin nata kafin yafurta"lfy lau pretty ya gajiyan wahal da zuciyata "
Dariya tayi kasa -kasa kafin ta furta "hmm shureim kenan kaidai akwaika da zolaya "
Mikewa tayi ta zubo masa juice mai sanyi cikin cup, ta miko masa hannu yasa ya amsa yana karewa yatsunta kallo , wanda sukasha jan lalle sosai ya birgeshi , gawani qamshinta daya cika hancinsa, tas ya shanye ya dire cup din kafin ya fuskanceta sosai , yana fadin
"Aneesa gani gareki akaro na 2 ina mai sake jaddada qaunata zuwa gareki, banzo da niyyan wasa ko yaudara ba aurenki nakeson yin, domin azahirin gsky yadda nakejin kaunarki cikin zuciyata bazai misaltu ba
Don haka inaso kisanar dani gskyn abnd ke ranki gamedani , banaso adauki dogon lokaci batare da iyaye sun shigo cikin mgn ba
Don haka nakeson kisanar dani cikakkiyar ke wacece, domin dana isa Abuja ayau nakeson sanar da momy cewa nasami matar aure
Don harnayi kasadan bata zabi amma nasan tunda narigata samun zabin zuciyata shikenan, don haka ina sauraranki pretty"
Aneesa ta dubeshi kafin tafara da fadin "kaman yadda kaji sunana Aneesa , iyayena dukkaninsu haifaffun zariane , Abba yafitone a anguwan juma dake cikin birnin zazzau, yayin da umma ya Aurota daga samaru
Abba na aiki yakawoshi garin kd anan aka haifemu nida yayana wanda yarasu yanada shekaru 6 , yakasance ayanxu nice daya tak da suka mallaka
Hakan yasa Abba yadaura dogon buri akaina naganin , sainayi karatu mai zurfin gske a fannin boko , duk da cewa vanida raayin karatun aure nakeso , amma saina dinga yimasa biyayya domin ganin nacika burinsa
Nayi samari sosan gske amma duk wanda yakawo kansa , gdn mu dasunan neman aurena Abba zai koreshi yasanar dashi karatu zanyi ba aureba
Duk dacewa abn nadamuna amma sai nake boye damuwata , har zuwa yanzu dana kammala state university , services kadai yarage min sosai fuskan Aneesa ya bayyana zallan damuwa
Shureim wanda ya tsuramata idanu yana sauraran ta, ya jinjina kai yana fadin " ehem ina sauraronki pretty"
Aneesa tacigaba da fadin"shureim har kawo yanzu danake maka wannan mgn Abba burinshi ayanzu ina kammala services Indora masters, sam baya mgn infito da miji nasara wani dogon burine yake dashi akaina, bana burin zurfafa boko arayuwata shureim, zuciya da gangar jikina tun da dadewa aure suke muradi, amma narasa yadda zanyi Abba yafahimci cewa aure nakeso ba karatu ba
Sai dai inamaka albishir da cewa Aneesa na sonka , sonda ban taba yima kowani namiji irin saba, awannan karon inaji nizanyi nasara insha Allah kaine mijina shushu
Takarishe mgn tana rufe idanunta da hannu alamun kunya"
Shureim wanda jikinsa yafara sanyi mgn Aneesa nakarshe yabashi kwarin guiwa, tareda jin sabon sonta kominta nabirgeshi , cikin murmushi yake fadin
"Gud Aneesa naji dadin yadda nasami gurbi cikin zuciyanki, mgn Abba kuma kisa aranki lokacin auren ne baizoba adacan , amma ayanxu kam kisama zuciyanki da ikon Allah shureim shine zai mallakeki, so addua kurum zamuyi tayi kinji
Oya open ur eyes , kinwani rufemin fuskan dake sani cikin nishadi
Yakai karshen mgn cikeda xolaya , yana mai sake fadin but baki sanar dani aikin da Abba yakeba pretty"
Aneesa ta furta "Abba yayi retare daga aikin gwamnati yana harkokin business dinsane da kuma harkan noma da kiwo "
Jinjina kai shureim yayi cikeda gamsuwa kafin ya furta"gud pretty to nidai
Sunana shureim shu'aib Abba Aji
Dady na fitaccen dan kwangilane kuma rikakken dan business sosai,
Mu haifaffun garin gombe ne saidai a Abuja muka tashi , dady da momy dukkaninsu 'yan bokone , hakan yasa muka tashi cikin gata da wayewa, hakan baihanamu samun ingantacciyar tarbiya ta addini ba, nine babba kuma namiji daya tak dasuka mallaka, sai auta yusrah sam Abba bai taba shaawar aikin gwamnati ba
Nayi karatuna akasar Turkey inda nakaranta business administration, yanzu ina aikine da National Health insurance dake Abuja, ina kuma taba harkokin business daya shafi shigo da motoci daga kasashen ketare
Momyna cikakkiyar fulanin garin gombene , yayinda dady kuma hausa Fulani,"
Aneesa ta jinjina kai tana fadin"Allah ya shige mana gaba "
Shushu ya amsa da Ameen baby pretty I luv u
Wlh Aneey idn bansameki ba bansan ya rayuwata zata kasanceba, plxx ki rikeni amana kinga ni first luv ne bantaba so ba sai dai asoni, sai yanxu rana tsaka kikai nasaran mamaye zuciyan baki daya
Aneesa tayi dariya kafin ta jefeshi da wani kallon luv take fadin"karka damu my shushu Aneesa takace insha Allah "
Abnci ta xubamai basmati rice with patotoa source , sai pepe meat wanda yake tashin qamshi
Plate din ta tura gabanshi kafin ta zuba banana smoothie a cup ta tura mai, tareda ruwan Faro duk wannan abn idanun shureim nakanta
Komi takeyi birgeshi takeyi komi tanayinsane cikin nutsuwa, komawa tayi ta zauna tana fadin oya bismillah
Sosai yaci abncin jin cewa dakanta tashirya dominsa, yakuma yaba sosai da kwarewanta afannin girki , daga haka suka taba hiransu ta masoya kowa na fadawa d'an uwansa yadda yake jinsa aransa
Daga karshe shushun yamike don kama hanyan Abuja, har gurin mota tarakshi tana xubamai shagwaban dake susuta shi , fadi takeyi zatayi missing dinsa kai kace sun shekara dasanin junane , hmm soyayya kenan inji Ayshat
Rafan 20k ya mika mata hadeda leda mai daukeda turaruka masu tsadan gske, wanda yatsaya yasiya domin ta
Ja baya tayi tana girgiza kai take fadin"no shureim bazan karba ba "
Shureim wanda ranshi yagama baci cikin hade faces yake fadin"sbd bakyaso sona ko pretty shiya bazaki karbi abnd yafito daga gareni ba"
Ganin yadda ranshi yabaci yasa Aneesa daukan ledan turarukan , tareda yimai godia da fatan sauka lfy , ta juya zuwa cikin gd tabar shushun nabin bayanta da kallo harta bacewa ganinsa
Kafin yasauke ajiyan zuciya ya shiga mota yanajin sonta nasake game dukkanin zuciyansa
Fatanshi kawai yakai gd lfy domin gabatarwa momy da albishir din , yasamu macen dayakeso wacce bayaji idn baisameta zai cigaba da rayuwa mai kyau
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*13*
Fuskar Aneesa yakasa boye farin cikin datake ciki, domin har wani extra nishadi takeji, gawani soyayyan shureim din dake sake zaman dirshan cikin zuciyanta
Haka tashiga parlour babu kowa jin tashin qamshi dake fitowa daga site din kitchen, ya tabbatar mata da cewa ummah natare da mai aiki suna shirya abncin da Abba yasa ayi kenan
Kai tsaye hanyan kitchen din ta dosa fuskanta dauke da murmushi , lantana dake facing kofar kitchen din tana shirya salad da umma tagama hadawa, ta dubi Aneesa tana fadin
"Yar gd na sai yanxu gashi har hajiya ta shigo munkammala komi, "
Neesa tayi dariya tana "fadin wlh lantana sai yanzu yatafi ta dubi umma tana fadin ummah sannu da aiki nabarki da wahala wlh sai yanxu ya tafi"
Ummah ta dubeta tana fadin"bakomi Aneesa yanzu dai yimaza kizo kifara shirya abncin adakin baki , kinga har 6 takusa ba abn mamaki bane kiji shigowan su yanzu "
Aiko Aneesa kai tsaye tawuce room din ta kayan jikin ta tasauya , ta fito suka fara kai abncin suna ajewa harsuka kammala,
Koda tadawo ledan turaran da shushun yakawo tadauka, tayi bedroom ummah domin nuna mata kyauta daga masoyinta shureim
Ganin bata cikin dakin yasata juyawa tabar turaren bisa bed din, Rufaida takira tana shaida mata yaufa masoyinta yazo , domin rufin tun haduwan Aneesa da shushu kullum cikin yamata zancensa datake
Wanda hakan bakaramin kona ran Rufaida yakeba, sai dai sam bata nunawa Aneesan , domin tana ganin bayanzu bane lokacin daya dace tafito da kishin shureim da takeji ba , domin duk wani wanda zai rabi Neesa tofa Rufaida ta tsaneshi kenan
*********
Shigan yamma shureim yayiwa Abuja hakan yasa koda ya isa gd, kai tsaye part dinsa ya wuce sai dayayi wanka ya huta , kafin ya fito zuwa part dinsu momy
Da yusrah yafara cin karo cikin parlon ganinsa yasata rugowa da gudu tana fadin"oyoyo ya shushu shikuma ya rungumeta yana fadin baby ya gdn "
Sakinsa tayi tana fadin wlh munyi missing dinka ya shushu, hannu yakai ya dungure goshinta yana fadin"to aigani nadawo wai ina cwt mom ne ? Da hannu yusrah ta nunamasa bedroom din momy alamun tana ciki
Hakan yasa yakama hanyar bedroom din yana fadin"momy am back yana tura kofar ya tadda tana waya ne ashe, hakan yasashi janyo stool yazauna yana zabga mata murmushi, shushu bakaramin son mumy yakeba sosai
Saida ta kammala wayan ya isa ya kwantar da kansa akafadunta kafin ya furta"momy I miss u nasameku lfy ? "
Mom ta shafa kansa tana fadin lfy qalau my son , ya gajiyan hanya ?
Shushu ya amsa da Alhamdulillh mom sai dai nagaji , fura kawai nakeson sha hope akwaishi cikin frige,
Mom tayi murmushi tana nuna masa side din da karamin frige dinta ke aje cikin bedroom din, tana fadin"kaga ga furacan cikin frige dazu nadama shi don nasan Saika nemeshi
Tashi yayi yana fadin wlh momy nayi missing dinsa tunda naje banshaba sam, dakko jug din kacokan yayi yana dauki cup dake jere saman frige din, ya zuba yafara sha sanyin furan da gardin coconut da aka dama furan dashi yana ratsashi
Kusada ita yadawo yazauna tamkar zai shige ciki, kafin ya furta "momy yau akwai fa daddadan albishir dazan miki , wanda zai saki farin ciki da jinshi"
Momy tayi murmushi tana fadin "kaman kasan nima jira kawai nake kadawo nima insanar dakai wata muhimmiyar mgn
Shureim wanda bai kawo komi cikin ransaba ya furta " mom to mubary zuwa anjima sai infara gabatar da nawa domin duk na kisa , dady yayi tafiyane? Yayi tambayar yana kallon momy wacce taji tambayar tazo mata abzata
A tunaninta shureim shine nafarko dazaisan dady yayi tafiyane imma yayi byn ita,
Towai meke faruwa tsakanin dady da shushu , domin tafara ganin canji daga yadda shureim din yarage walwala matukar suna tareda dadyn
Kauda kai tayi tana fadin dady nagary babu inda yaje , bakuyi wayabane tunda katafi?
Shureim ya amsa da munyi momy amma sau daya , Naso sake nemansa ayyuka sun min yawane ,
Kiran sallah da ake kwadawa yakatse hiran nasu , shushu yatashi yana fadin"momy time 4 pray bari indawo masallaci saimu tattauna mgn ko yafice abnsa"
Momy ta nufi toilet domin dauro alwala
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*14*
Shureim da momy da Aneesa ne zaune a falo , byn sun kammala dinner har zuwa lokacin kuma dady bai shigo gdn ba
Momy ta dubi shureim dake cin Apple ahnkl tana fadin ,"my son ina jinka wani albishir ne kataho dashi ? "
Shushu ya dauki wayan shi batare da yafara cewa komiba, pic din Aneesa ya danno wacce tadauke shi tana sanye da doguwar riga xubin Indian design,
Tasha rolling tayi kyau sosan gske mikama momy wayan yayi yana cewa"momy duba pic dinnan kiga tayi kuwa
Allah yayi nayi mata wlh momy son Aneesa yayiwa zuciyata mummunan kamu , 7 days da haduwan mu kenan amma inajinta cikin zuciyata , tayadda bazan iya cikakkiya rayuwa mai nagarta ba inban mallaki Aneesa ba mom"
Ya karisa mgn yana dariya sosai kana kallon fuskansa zakasan, yana fadin komine with full confidence dinsa,
Yusrah da momy ya bary da baki bude xuciyoyinsu cikeda tsananin mamakin shureim din, hannun momy har rawa yake da kyar tanemo nutsuwan ta , yusrah ce tadawo dab da ita domin ganin wata mai sa'an ce shureim kefadin wadannan kalaman akanta
Dukkaninsu suka xubama pic din idanu suna kallon hoton Aneesa, sai dai atake zuciyan momy taji batai na'am da Aneesa ba , sbd bataga abnd Aneesa zata nunawa Ayshat ba daya wuce farin fata data fita
Yusrah tafara mgn tana fadin "big bros gsky tayi but zabin da momy taima wlh tafita haduwa ya shushu"
Wani uban harara yajefi yusrah dashi yana duban momy dake miko masa wayan
Fuskanta kadai daya kalla yanuna bata yaba da Aneesa ba , zuciyan shureim takarye ya zubama momy idanu yana sauraron jin mezai fito abakinta
Momy ta mika masa wayan tana fadin "shureim naga hoto takumayi batada makusa sai dai zabin danaima tafita komi , uwa uba ita munsanta munsan halayyan ta don haka kamakaro ,
Sai dai ka jingine mgn wannan yarinyan ka amshi zabin mu kaman yadda kabani izinin nemo maka mata , to aranan nayanke shawaran hadaka da Ayshat yarinyar dadynku Alhaji Adam"
Tuni shureim kejin wani xufa na keto masa idanunsa sun kada sunyi jajir, cikin tsananin tashin hnkl yake fadin
"Wat momy Ayshat fa kikace qanwar salman , no momy karki min haka wlh bantaba son ta ba bakuma naji zan sota , hasalima ina mata kallo ne tamkar yusrah kinko ga zancen ma nasota bai tasoba
Momy Aneesa itace kadai zuciyata keso ban taba soba sai akanta , plxx momy kijanye zancen tunkafin ma yaje kunninta tafara rainani, nacene kizaban mata arashin sanin zan hadu da Aneesa , tunda nahadu da wacce zuciyata keso plxx momy kijanye zancen Aysha"
Ya karishe mgn tamkar zai rushe da kuka , yayin da momy tai mugun shan kunu domin bataji akwai wanda ya isa yatada zancen auren shushu da Aysha
Hakan yasa takirayi sunanshi"shureim ka saurareni da kyau kaji mgn injanye zancen hadin aurenku da Ayshat ma baitasoba, domin bazaka maisheni karaman maceba, naje har gd nasanar da momynku hajiya safiya, takumayi na'am sannan dadynka da shi Adamun sun tattauna mgn , yarinya harta Amince batareda datayi gardama ba saikai danake ganin na isadakai
To bary kaji wlh kaji narantse Ayshat itace zabina, sai dai idn zakayi mata biyu saikayi byn kacika burina , saika aury zabin naka daga baya , amma mgn wata Aneesa kama ajeshi agefe "
Bata sake bashi daman mgn ba tamike tai hanyar bedroom dinta, tare da rufe kofan jikake baaamn...
Tabar shushun dafe da kansa wanda kejuyawa tamkar zai tarwatse, gaba daya jinsa yake cikin wani yanayi dabai taba tsinta kansa cikiba, na tsananin tashin hnkl da rudani
Yusrah ce ta matso kusadashi tana fadin "plxx ya shushu kayi hakury ka amshi zabin momy wlh Ayshat bata da makusa, ga nutsuwa ta mallaki komi da ake nema ga cikakkar mace, kuma na tabbatar idn akai auren.............. Wani tsawa yadaka mata cikin hargowa yake fadin leave idiot kawai, ni kike fadawa wannan banzar mgn ?
Aguje yusrah tayi hanyar bedroom dinta tana kunshe dariyan dake son taho mata, gefe guda kuma tausayin shushun na Neman karya zuciyanta, sai dai sam tafisonsa da qawarta ace wanta gd naso mezaisa akai dawa, sannan sanin kantane Ayshat macece da kowani namiji zaiyi alfary da samunta
Shureim mikewa yayi yanajin wani mugun jiri nafisgansa , da kyar yakai kansa part dinsa kafin ya zube kan sofa , yana sauke numfashi mai zafin gske gaba daya brain dinsa cushewa yai
Meke shirin faruwa dashine? Meyasa momy zata juyamasa baya alokacin dayake matukar bukatan tallafinta , domin samun cikar burinsa wato Aneesa yarinyar dayake jin sonta nakaruwa akowace dak'ika, why ? Why?
Meyasa momy zata zabi hadashi da yarinyar dabai taba mafarkin wani abu yashiga tsakaninsa da ita daya wuce gaisuwaba ,
Yarinyar dayakejin zafin mahaifinta cikin zuciyansa , tuni zuciyansa ke hasko masa yanayin daya tsinci Alhaji Adam da mahaifinsa suna aikata mummunan *LAIFIN* *BOYE*
rintse idanunsa yayi yanajin saukan wasu zafafan hawaye , wadanda suke zibowa tareda wani matsanan ciyar tsanan Alhaji Adam da Aysha"
Aneesa kadai yake ji aransa itake yake kallo amatsayin natsatstsiyr mace , wacce idn yasameta yayi babban dace Meyasa momy xatamai haka ?
Tunowa yai da mgn momyn"sai dai kayi mata biyu byn kacika burina "
Dafe zuciyansa yai dake masa zafi shine akewa zancen yayi mata 2? Anyako momy nason sa tana son farin cikinsa?
Wayansane yashiga rury a wahalce ya daukota yana kallon sunan dake yawo akan screen din
My luv shine sunan dake yawo bisa screen din wayan, amma shushu yakasa daga wayan, hartagaji ta tsinke bai sami daman receiving ba
*********
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*15*
A bangaren Aneesa kuwa jin takira har 2 misscall bai daga wayanba, tayi tunanin ko ya kwantane sbd gajiyan tafiya, hakan yasata ta tura masa text na fatan ya isa gd lfy, tareda kalamn soyayya da tasan xaiji dadinsu
Kiran dataji ummah namata ne yasata aje wayan ta nufi bedroom din umman,
Xama tayi bakin bed din tana kallon ummanta dake rikeda ledan, turarukan da shureim yabata tana fadin"umma gani "
Umman ta dubi Aneesa tana fadin "wannan kuma daga ina? "
Aneesa tayi murmushi tana fadin"umma shureim ne yabani nashigo dazu kinshiga wanka, saina ajeshi bisa bed ta karike mgn tana kallon umma"
Umma tayi murmushi tana "fadin to angode amma ki kula da amsan kayan samary ,niban fayason irin wadannan kyaututtukan ba "
Aneesa ta ja numfashi tana fadin "wlh umma ban amsaba saida naga ransa yabaci , da harda kudi masu yawa wlh kin amsa nayi"
Umma ta tsuke fuska tana fadin" to akul dinki da amsar ko kwandalansa , nafada miki wannan din ma saiki adana har dues lokacin da xamuga yadda xata kasance , Allah yazaba abnd yafi alkhairy"
Ameen Aneesa ta furta tana mikewa rikeda ledan xuwa dakinta, wardrobe ta bude ta aje ledan tareda sauya kayan jikinta xuwa na bacci, ta kwanta xuciyanta fal tunanin shureim tareda jin son taji voice dinsa, ahaka bacci yai awan gaba da ita
Washegary Alhaji Mahmud wato Abban Aneesa da umma habeeba ke zaune afalon Abban, byn kammala kalacinsu Aneesa tayi sallama cikin falon
Tana sanye cikin doguwar riga ta bubu wacce tai mata kyau , karamin gyale tayafa bisa kanta yasakko kafadunta, durkusawa tayi ta gaida Abban nata, ya amsa cikin sakin fuska byn fitanta ne
Umma ta dubi Abban tana fadin"yawwa Alhaji dama inaso muyi mgn akan wannan yarinyar Aneesa, jiya take sanar dani tasami tsayayyen saurayin daya fito yana sonta da aure, harma ya biyo nan ajiyan sun gana kafin ya wuce Abuja,
Domin can yake dazama
Anturoshi wani aiki ne anan kd suka hadu da Aneesa, kuma bisa dukkanin alamu tayi naam dashi tashaida min yana nutsuwa sosai , shine nace zan tunkareka da mgn don azahirin gsky hnkl yayi kwanciya da mgn auren Aneesa, tunda dai gwargwado tayima ka biyayya , tacika burinka naganin tayi degree duk da cewa nadade da lakantan yrinyar nan tafi bukatar aure akan karatun, amma hakanan tadanne don ganin tabi abnd kake so
Don haka awannan karon tanuna auren takeso da gske , kaga ko gara muyi mata don gudun zubewan mutuncin mu , ina tsoron zamanin nan damuke ciki Abban Aneesa "
Tunda tafara mgn ya zuba mata idanu yayinda ya bata fuska sosan gske, ganin tasa aya a mgn ta yabashi daman sake sanya idanunsa cikin nata , kafin yafara fadin
"Naji mgn ki Habiba wato har kene zaki bata daman kawo saurayi cikin gdn nan , batareda an nemi izini nabako? To naji tasami meso kuma ta shaida miki aure takeso, to naji awannan karon bazan tauye taba zanbata dama tayi aure amma da sharadin, sai munyi yarjejeniya da yaron byn auren zai barta ta dora masters dinta "
Umma wani sanyi ya ziyarci zzuciyanta,yanzu tasake gasgata duk wanda yarike addua bazai ga rashin nasaraba , tasan addua datakeyi dare da rana ne yafara tasiri , ta kumaji shureim yasake kwanciya aranta , da alama shi alkhairy ga Aneesa tunda gashi atashin farko sunyi nasara Abba bai kushe mgn ba
Kallon ta yayi yaga yadda farin cikinta yakasa boyuwa, hakan yasashi fadin"kiramin Aneesa yanzu inason mgn da ita "
Aneesa durkushe gaban Abba kanta akasa, Abban ya dubeta yana fadin Aneesa waye shureim? Gabanta ne ya yanke yafadi domin tana matukar tsoran mahaifinta , sam bata shaku dashi yadda tashaku da ummanta ba, hakan kuma yasamu ne sbd sm shiko irin yajata ajiki bayayi , saida tasaci kallonsa taga fuskansa asake yake sannan taji tasami nutsuwa
Ahnkl ta sanar da Abba waye shureim har yadda suka hadu bata boye masa komi ba,
Jin jina kai yayi yana fadin kina nufin kicemin shi yaron Alhaji Abba aji ne fitaccen dan kwangilan nan, kuma dan kasuwa lallai kin dakko mana dan babban gd ,ai mahaifinsa ba boyayye bane yayi fice sosai
To badamuwa Allah yazaba mafi alkhairy , amma inaso kisani bazan amince dashiba harsai munyi yarjejeniya zai barki kicikamin burina , naganin kinyi masters wannan kadai zai sa in amince ki aureshi , kisanar dashi randa zai sake zuwa inason ganawa dashi , kafin bashi izinin cigaba da mgn dake tashi kibani waje
Sum sum Aneesa tayi waje zuwa dakinta kan bed dinta tafada tasaki ihun murna, yai Abban tane yayi naam da mgn shureim batareda fada da hantaranta ba, wani nishadi takeji tareda matsananciyan soyayyan shushun dake sake mamaye zuciyanta
*********
Karfe 11am shureim ya fito daga part dinsa, yana sanye cikin bakin wandon jeans da blue din shirt, yayi kyau sosan gske sai fitinannen qamshinsa ketashi, kana kallon fuskansa zakasan baya cikin walwala
Kai tsaye part din su momy taiwa tsinke koda yashiga falon , da yusrah yaci karo tasha wanka cikin shigan gown ta laces siririn veil tarufe dogon gashinta dashi, tana rataye da jaka akafadan ta sai wayanta rike ahannu, da alamu fita zatai kallo daya yai mata yadauke kansa , domin har ita haushin ta yakeji yusrah ce kafadin
"Ya shushu ina kwana tana sauke masa smile ganin yadda yahada face,tasani haushin kalamanta na jiya ya yaji"
Bai tanka mataba Sai ma harara daya watsa mata wanda yasa yusrah sakin dariyan datake kunshewa, aiko hakan ya tunzura shushun cikin tsawa yake fadin
"Will u get out kosai nataso natakaki? nikike wa dariya baby alright zanyi maganinki "
Allah yahuci zuciyan yayana haka yusrah ta furta tana kokarin fita , ta kuma cewa bye ya shushu momy na bedroom saina dawo "
Ko tanka mata baiba illah wani dogon tsaki dayaja, ya nufi dining area din bude warmas yashigayi yana tabe baki kafin ya dauki cup ya hada oat , sai fraid egg sukenan abnd yasaka acikinsa , shima da kyar domin sam zuciyan sa babu dadi
Kaman wanda kwai yafashewa aciki ya nufi bedroom din momy, zuciyansa na bugawa d a karfi domin baisan yadda zasu kwashe da momy ba
Koda yatura kofan da sallama ya shiga tana hakimce akan bed waya takeyi ,
Guri yasamu yazauna ya zuba mata idanu bai jima ba ta aje wayan , tana kokarin tashi da Sauri shushu ya isa tareda kai hannu yariko hannunta , yana adin "morning momy "
Hajiya kubrah takoma ta zauna tana fadin "morning son"
Shureim ya kwantar da kasan a cinyanta yana fadin"plzz momy karkice zaki fishi dani akan mgn Aneesa , wlh momy nima natsince kaina cikin sontane dumu -dumu, ki tausayamin insami abnd zuciyata takeso momy , nasan kina sona bazakiso in tagayyara ba "
Hannu takai tana shafa suman kansa tana fadin"my son bawai banason ka da wannan yarinyar bane , illah inaso kagane cewa zabin danai maka abn kadubane , Aysha yarinyar kirkice tana da kyau da nutsuwan dazakai alfahari da samunta, shushu kaikanka zaka bada shaidan cewa Aysha bata da makusan dazakace zaka bijirewa aurenta, sai dai idn kanason ka tozartani ka jefa zuciyata cikin damuwa, dama masu iya mgn since amafi yawan lokuta d'anda kake nunawa so yafi wahal dakai "
Cikin damuwa shureim ya dubi momy yana fadin"no Allah yahuci zuciyanki bana fatan nasaba umurninki matukar auren Aysha shizai saki farin ciki na amince dashi , sai dai sam banajin zan sota momy , Aneesa nekadai cikin zuciyata yakai karshen mgn yana hawaye "
Tausayinsa yakama momy amma ta danne , hannu tasa tana wifing tears din kafin tafara mgn tana fadin "shushu calm down plxx ka kwantar da hnklnka so ahnkl yake shigan bawa,na tabbatar itama zaka sota ngd da goyan bayan daka bani
Kuma ina maka albishir da cewa zaka aury Aneesa amma byn ka cikamin buryna na auren Ayshat , wanda nakeso ayi komi nanda 2 month kacal
Allah yai maka albarka zaiyi mgn ta hanashi tareda fadin" shishh..... tashi jeka my son Allah maka albarka "
Tamkar zai rushe da ihu yabar dakin yana rangaji, yayinda kansa ke sarawa banda sonjin voice din Neesa baya jin komi cikin ransa, yarasa meyasa yakejinta har cikin jininsa,
Wayansa da ke aljihun wandon sane yafara ringing, duk atunaninsa Neesa ce hakan yasa yazaro cikin zakuwa
Sai sunan dady yagani yana yawo a screen din, wani takaici yarufesa kaman bazai daga kiranba, sai gab da zata tsinke ya daga ko kafin yayi mgn yaji muryan dady nafadin
"Kasameni a guess House dina dake wuse 2"
Ya katse wayan batareda yaba shureim din daman mgn ba
Shushu jiyai kaman ya tarwatsa phone din don takaici , ahaka yakarisa part dinsa zubewa a sofa yayi , yana sauke numfashi
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*16*
Gueshouse din Alhaji shu'aib shine zaune tareda amininsa Alhaji Adam , suna tattaunawa akan gine ginen gidajen marayu, da islamiyun da ake ginawa da dukiyan dasuka sadukar dashi , wanda suka samesa tahanyar banza
Wanda saura kiris kammala komi hakan yasa dady yakira shureim din domin , ya fayyace masa komi tareda nuna masa yadda komi yake
Shushun sai da yashafe tsayin lokaci har iyayen nasa sunfara fidda rai da zai zo , sannan ya shigo cikin katon falon dake down stairs
Kana kallon fuskansa zakasan yana cike da matsananciyar damuwa, har kasa ya gaidasu kafin yasami guri yazauna
Dady ya dubi tilon dan nasa wanda yakaranci damuwa kwance a fuskar sa kafin yafara mgn da fadin
"Shureim bawani abu yasa nakiraka nan ba gani gaka ga kuma dadynka Adam , sai don mutattauna mgn akan *LAIFUKAN BOYE*da mukai ta aikatawa muna samin kazaman kwangiloli da tarin dukiya, kaman yadda nashaidama zan sadaukar da duk wata dukiya dana sameta ko ince muka sameta , to Alhamdulillh nida Adam muka zauna muka tattauna abnd yakamata
Mun nisa gurin gine gine na gidajen marayu da islamiyu da masallatai, muna yi akaduna , nan Abuja mun gina a gombe mahaifata sannan sai katsina da yola
Wanda saura kiris ayyukan su kammala, mac book ya janyo yana nuna masa kaf gine gine wadanda suka tsaru , kana kallo kasan bakaramar dukiya bace take kuka gurin aikata wadannan ayyuka,
Shureim cikeda gamsuwa da tsantsan farin ciki yake kallon komi, har cikin zuciyansa yaji dadin yadda iyayen nasa sukai saurin nadama, tareda sadaukarwa suka zabi anfani da nasiharsa da kuma kokarin bijerewarsa ga dady duk don yaga cewa sun dawo kan hanya
Ahnkl ya dubi dady yana fadin" Alhamdulillh dady naji dadin yadda komi yakasance ina kuma addua Allah yasa kunyi tuba na gsky , Allah ya shiryarvda duk wani Musulmi mai aikata laifuka Irin naku ,
Zan kuma rufe sirrinku amatsayina na danku wanda bazaiso adinga nunaku amatsayin ,masu aikata *laifukan boye* ba
Sosai yasaki ji dasu sunata tattauna batutuwan dasuka shafesu , har lokaci yaja sosai Alhaji Adam shine yafara tafiya , yabar dady da shushun suna cigaba da hiransu
Byn tafiyansu ne dady yakama hannun shureim din , yana kallnsa sosai yake fadin
"My son tunda kashigo nake karantar damuwa atare dakai , kasanar dani meke damunka ? "
Shureim yawani shagwabe fuska yana fadin"Abba byn nadawo daga kd ne momy ke sanar dani kun yake shawarn hada aurena da Aysha , nikuma mgn gsky dady banason Ayshat ban taba mata kallo nadaban daya wuce na qanwa taba
Kuma atafiyan danayi
Allah yahadani da yarinyar data shiga xuciyata farat daya, ina tsananin son ta dady
Nan ya kwashe yadda sukayi kaf da momy har mgn matsayan dasuke kai ayanxu, na cewan saiya fara cika burin momy na auren Aysha kafin daga bisani ya aury Aneesa "
Dady yadafa kafadunsa yana fadin"kazama jarumi mana son kada soyayya tayi saurin saka ka susuce ehem,
Mgn da kubrah tayi tabbas ina byn ta nima domin ko yanzu kafin kazonan saida muka tattauna mgn da Adamu, Aysha ta amsa tana sonka anriga anyi mgn bagirman mubane ace andawo anfasa , kai mijin mace hudune shureim don haka zaka aury Aneesa amma saika fara auren qanwarka wacce mukafi gamsuwa da tarbiyanta ,
Don haka ka kwantar da hnkln ka sannan mgn soyayya ahnkl zaka sota shushu, ita yarinyar da kakeso din waye mahaifinta ?
Shureim ya dubi dady kafin yasanar dashi abnd Aneesa tasanar mai , tundaga mahaifansu zuwa aiyukan da mahaifin nata yake kai ayanzu, cikeda gamsuwa dady kefadin ok Allah ya tabbatar da alkhairy "
Mgn Ayshat kuwa cikin week dinnan zaa saka rana saikai kokaryn zuwa ku fuskanci juna ,
Idn yaso zansa afara gyaran gd na dake sun city sai kayi anfani dashi , tunda katon gurine da zaka iya aje mata ko ukune batareda takura ba
shidai shureim bin dady da kallo kawai yakeyi amma sam zuciyan sa batayi na'am daya fara auren Ayshat ba, inama laifin sufara aura masa zabin zuciyansa kafin nasu , sai dai vayaso yasabama mahaifansa mussamman momy dayake ganin tadauki lamarin da zafi "
Jiki asanyaye ya mike yana fadin shikenan dady zanyi yadda kukeso, shima dady mikewan yayi suka fito atare, driver dinsa yajashi shureim kuma yashiga nasa ya fice daga gdn
Yayi tafiya mai nisa kafin yasami gefen hanya ya parka,
Wayansa ya ciro yayi dialing number din Aneesa, wanda buga biyu yayi kaman tana jira ta daga wayan, byn tasake narke murya take amsa sallaman sa
Jin muryanta yasa shureim sake lafewa tareda sauke ajiyan zuciya,hira sosai suka yi mai cikeda kalaman soyayya kafin suyi sallama da juna
Shureim bai nufi gd ba sai hospital din da Dr. sudais yanufa, kasancewar sunday ce shi shushun yana hutun weekend ne
*********
Rufaida ce kwance adakin wata frnd dinta kuma abokiyar watsewarsu Aymana , wacce itama budurwace amma gogaggiyar barikice, wacce take mu'amala da mata da maza , daga ita har Rufaida iyayensu masu kudin gskene , wadanda ake damawa dasu a gwamnati,
Domin dukansu iyayensu narikeda mukamai masu kaurin gske , shiyasa suke yadda sukeso ba kwaba bare saka idanu daga iyayen nasu , wannan yabasu damar sheke ayarsu yadda sukeso
Aymana ce take kallon Rufaida wacce keta faman huci , cikeda bacin ran takira Aneesa ganajin number busy ,
Tsaki taja tana fadin"wlh Aneesa kibi asannu domin ina tsananin kishinki "
Wani uban harara Aymana ta zabgawa Rufaida tana fadin "andaiji kunya wai kaman Aneesa ce zaki mato akanta , narasa jarabar data sameki ki rasa wacce zaki zaba tazama dadironki sai wannan yarinyar, wacce bawani class ke garetaba , inbanda keda kike haskata wlh ni kallo bata isheni ba
Bafa wani wuta ahannun ubanta sai rufin asiry , babe ana harka da manyan babies ke kina biye da wacce batada 'yan ci , har yau Aneesa da dabara fa take fitowa kuhade inba kinje gdn su bane
Rufaida tadubi Aymana tana fadin "Aymana bazaki gane bane Aneesa tadabance ina samin gamsuwa da ita fiyeda tunaninki, tasan takan yadda ake harkannan wlh shiyasa naki yadda nasata akungiya , nafiso nikadai inmory abata
Keni yanxu matsalata baiwuce guy din data jajibo tanaso ba, kinsan shegiyan duk da goge wanta a less wlh auretakeso , nikuma bani bukatan abnd zai rabamu
Amma ayadda take nunamin bakaramin matowa tayi akan gayenba, kuma kinsan me wlh tacemin sonda takemai kadan ne akan yadda yakesonta
Yanxu hanyar daxan tarwatsasu nake nema cikin sauki , kunnin Aymana takai bakinta
Tana mata rada , kafin su kwashe da dariya Aymana nafadin bakifa da kyau tawan
Saida suka sheke ayarsu kafin Rufy tabar gdn su Aymana, itakadai kejan motanta kiran Vibe cikin gwanancewa,
Kai tsaye anguwan su Aneesa ta nufa domin tanakewanta 2 days , sannan tana bukatan samin information akan shureim Aji , namijin datake jin kishinsa tunkan tasan koshi waye takumayi tozali da kyakykyawar fuskansa
Bata dauki dogon lokaci ba ta parka motarta akofar gdn su Neesa , kafin tafito cikin takunta na gogaggun mata tayiwa cikin gidan tsinke
********
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*17*
Koda Rufaida tai sallama a parlor umman Aneesa ce zzaune,tana kallon tashar manara hnklnta nakan wa'azin da ake yi
Amsa sallaman tayi tana fadin"maraba da Rufaida kece da rana haka"
Rufaida ta dan durkusa tana gaida umman cikin mutuntawa, tamkar d'iyar kirki ita kuma umma na amsawa baki bude da murmushi
Aneesa ce tafito aguje tana fadin "oyoyo my bakin rai "
Harara Rufaida ta watsa mata tana fadin "dallah can byn tun daxu nake kiranki line busy koda uban wa kike waya oho"
Dariya sosai Aneey tasa tana fadin"kedai kincika daukr zafi shureim nefa muke waya dashi "
Umma ta dubesu tana fadin ehem zaku fara ba , dariya sukayi duka yayinda Aneesa takama hannun Rufaida suka nufi dakinta
Fitowa tasakeyi ta nufi kitchen karamin tray ta dauka , ta dora jug mai cike da kunun farar shinkafa wanda tasha coconut da madara sai milk flavour
Tahado da goran cway da ruwa ta nufi dakinta dashi kafin lantana ta sauke launch, akasa ta aje tray din tana fadin "bakin rai bakin fama ga mutuminki nan kunun rice kaman nasan kina tace, tana mgn ne tana tsiyaya kunun cikin cup , ta mikama Rufaida wacce takafe Aneesa da idanu "
Sanye Aneesan take cikin skat da riga na English wears , marasa nauyi kasncewar zafin da ake zabgawa , rigar takamata matuka tareda fito da surar kirjinta , sai skat din wanda yataimaka wajen fito da hips dinta
Byn Rufaida ta amshi cup din ne tafara kurban kunun, wanda sanyinsa da gardinsa ya ratsa makoshinta , tasha kaman Rabin cup din sannan ta aje tana fuskantan Aneesa
Take fadin"waike baby intambayeki man wayene wannan shureim din , dake neman yafara sace zuciyanki koma ince yasace, a ina yake impact dai inason sanin cikakken wayeshi "
Aneesa ta dubi Rufaida duba mai cikeda nazary , tasani sarai Rufaida batada kyau duk yadda akai wani kulli takeson hada mata , hakan yasa ta sake sanya idanunta cikin na Rufin
Kafin ta furta "cikakken sunansa shureim Abba aji mazaunin Abuja ,nan dai tasanar da ita komi kaman yadda shushun yasanar mata "
Rufaida ta jinjina kai tana nanata sunan cikin zuciyarta , tabbas tasan wannan sunan abakin salman, kaddai ace shine wanda salman keyawan sanar da ita abokinsane , kuma iyayensu aminan junane yana sanar da ita qualities din shureim aji , sam guy din shi baruwansa da rudin duniya
Tabba inko hakane dole Aneesa tamato kansa, ko sbd arzikin mahaifinsa ya isa tasosa, cikin dabara take fadin nice baby but natabajin sunan abakin salman I think kaman abokan junane nema
Aneesa ta dubeta tana fadin bari kiga pic din wlh gayen ya hadu over, kuma kinsan abn karin farin ciki Abba ya yi na'am da mgn duk da yace saisun yarjejeniya akan zai barni nayi karatu ko byn auren "
Wani harara Rufaida tasauke ma Aneesa afaikace afili kuwa dariya tayi , tana fadin"wow kice abn da gske akeyi yanzu babe hrwani rawan kafa kike zakiyi aure , amma inafatan yasan wacece zai aura , domin yasan yadda zai rika sharing dinki dani , dama sauran wadanda kike kulawa, domin inada lbryn kina muamala da seeyama qawar Aymana"
Aneesa saida taji gabanta yai mummunar faduwa,shikenan Rufaida tadakko hanyar da zata tarwatsa rayuwanta, don indai zatai kokaryn anfani da *LAIFIN BOYE* tanemi rabata da shushu to tabbas tana shirin tarwatsa rayuwanta ne
Cikin matsanancin tsoro take duban Rufaida tana fadin"haba Rufaida ya kike tunanin zan bude baki insanar da shureim cewa nidin 'yar lesbian ce , guy din dayake min kallon ustaziya natsatstsiyar mace,
Kumama keda kanki kinsani dukanmu babu wanda iyayenmu sukasan muna aikata *LAIFIN BOYE*
Plxx Rufy murufe wannan babin wlh ina matukar son shushu, son da bantama wani da namijiba, idn ban aury shureim ba bansan halin dazan fadaba, kda kiyi yunkurin rabani da rayuwata , nayi miki alqawarin cigaba da kasancewa dake har zuwa lokacin da zamuyi aure da shushu, daga lokacin zan killace kaina zan rabu da wannan harkan
Takai karshen mgn tana mikama Rufaida phone dinta "
Rufy wacce takejin dukkanin kalaman Aneesa tamkar zuban ruwan zafine cikin ranta, ta amshi wayan tana kokarin boye bacin ranta , zuciyan tane ya buga dakarfin gske sakamakon ganin kyakykyawar fuskar shureim shu'aib aji
Tabba dole Aneesa tamato akansa domin guy din yagama haduwa, zaiyi matukar wahala yataya ma mace kansa takasa amsar sa, stake kishin kasanvewansa da Aneesa yasake mamye ranta
Tabbas tasan idn hartayi saken da Aneesa ta aureshi tasan , zai matukar wahala tasame kulasu domin daman arashin yin auren ne yajefata wannan harkan
Inko hartasami kaman shureim bataji zata sake sauraren jinsinta , nan a nan ta tura pic din zuwa wayanta kafin tasaita kanta sosai
Tana duban Aneesa da keman kallon yanayin da Rufaida ke ciki , kafin ta furta "gsky qawata gayen ya hadu banga laifin zuciyanki data mato akansaba
Irinsu mnyan mata ke kwadayin samu keko a arha yazo miki , kinga dole kigigice mussamman dayazo akan gaban , kin matsu kikasance da namiji domin kigane banbancin ababen biyu kikuma cika burinki nasamin kids,
Wani makirin smiling tasake jifan Aneesa dashi kafin ta dora maganarta" ina miki fatan shureim yazama mallakinki bakin rai
Yanxu dai bari inji duminki baby na ta kai hannu tana rungumo Aneesa zuwa kirjinta ,
Aneey tamike dasauri tasaka ma kofar dakin ta lock , kafin tadawo ga Rufaida wacce harta tafara cire kayan jikinta
Badawasaba suka fara laluban junansu kafin su fda duniyarsu ta masha'a , sosai Rufaida ta murji Aneesa kafin sufawo natsuwansu
Mai da kayanta takeyi ajikinta tana duban Aneesa dake kwance babu komi ajikinta , illah hawayen dake sauka nisa bedsheet din dake shinfide akan bed din
Wanda suka tumurmusheshi yanxu zuciyanta na mata kuna kaman ko yaushe, tanajin haushin mahaifinta tasani dole Allah ya kamashi da laifi , domin duk abnd take aikatawa shine sila da ace yaimata aure da bata fata ga wannan mummunar harkanba
Sai da Rufaida ta gama maida kayanta tsaf domin bata bukatan yin wanka saita je gd,
Kallon Aneesa tayi tana tabe baki kafin ta furta "to mrs shureim atashi agyara jiki nizan wuce zuwa gd sainajiki "
Aneesa ta tashi zaune tana share hawayenta rigan ta zura yasauka guiwa , dogon hijab tasaka mai kaury yarufe jikinta
Ahaka suka fito domin yiwa Rufaida rakiya , wacce kejinta cikin farin ciki domin jefi tsuntsu biyu da dutse daya
Nafarko ta sami biyan bukanta 100%daga jikin Aneesa shiyasa take qaunar yarinyar over, na biyu kuma gashi tasami information akan shureim abnd yai saura tasake bincike akansa sosai kafin ta d'ana tarkonta
~~~~
Wannan shafin kyauta ce agareki Anty mejidda musa, sosai nakejin dadin yadda kike bibiyan buk dina , tareda bada courage plzz duk inda akaga munyi kuskure ina bukatan gyara , Allah yabar qauna 閴傦拷
**********
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*18*
Shureim ne zaune a offices din Dr sudais sanyin Ac naratsashi , hakan yabashi daman kwanciya bisa kujeran dake offices din
Cox sudais din yabarshi ne sun shiga theather , idanunsa alumshe suke ya fada duniyan tunanin yadda zaiyi ya aury mata 2, wannan wani irin lamari ne zai kasance dashi
Meyasa su momy bazasu janye mgn wannan yarinyar ba, wani kwafa yayi yana ayyana irin wulakancin da Aysha zata fuskanta, watoma itace tace tana sonsa
Ahnkl yasake zaro wayansa yana kallon pic din Aneesa wanda ayanxu itace ta mamaye screen din wayansa
Ahaka Dr. Sudais ya sameshi yayi nisa yana kallon pic din Aneesa, shamma tansa Dr sudais yayi ya warce wayan , yana kallon pic din wacce ke bisa screen din, kafin ya kwashe da dariya yana fadin
"Huuhh guy kace kafada system din luv ne haka, amma fa kayi babban kamu , domin yarinyar tayi ba karya yana mgn ne tareda zama bisa kujera"
Shushu ya tashi zaune yana yasina fuska kafin ya furta"dallah Mallam bani wayata ubanwa yace idanunka sudinga kallemin mata "
Wani dariyan sudais yasake dauka yana mika masa phone din
Kafin ya furta"Allah yabaka hakury lover boy din momy yanzu dai miye lbry ne? "
Shureim yasake bata rai alamun damuwa ya wanzu akan fuskansa, kafin ya fuskanci sudais din yana fadin "wlh guy ina cikin matsala bansan ya akeso nayi da raina ba ahnkl ya kwashe komi yasanar dashi
Ya kare mgn yana fadin amma nafi ganin laifin wancen yarinyar data Basu goyon baya , amma zatasan tayi kasadan shiga rayuwata "
Dr. Sudais shima yatausaya ma aminin nasa , domin yasan yadda so yake mussamman ma shi shushun da baitaba fadawa tarkon son wata mace ba sai yanzu, sannan bazai bashi goyan bayan ya bijirema umurnin iyayeba, ko bakomi shi shaidace akan cewa Aysha yarinya ce natsatstsiya , kuma tana da kyau da qualities din da kowani namiji zai so takasance mallakin sa, amma ayanxu yasani shushu bazai fahimci hakan ba , sbd yafada tarkon son abnd zuciyansa keso
Dafa kafadun shushun yayi yana fadin"shureim kayi hakury kai haka naka kaddaran yazo ,ka amshesu duka amatsayin zabin rankane bawai kaware Aneesa kadai don itace kakejin sonta aranka ba, kobakomi Ayshat qanwace agareka kuma ko don salman baikamata ace muna tare tsawon lokaci , ka aury qanwansa kace zaka wulakantata ba, so inabaka shawara don Allah shushu kada kawulakanta Ayshat , domin bakasan wacece zata zamema alkhairy cikin rayuwanka ba, "
Dakatardashi shushun yayi tahanyar daga masa hannu yana fadin"enough sudais domin na fuskanci kaima baka qaunata tunda har kake goyan bayan nafara auren abnd banso , narasa meyasa kowa baya goyan byn Aneesa sai wannan stupid gal din, ohh yanzu atakaice kaima bakasona da Neesa ko? "
Dariya sudais yayi yana fadin "calm down my frnd nibance Neesa batayi ba , bankuma ce bana sonka da itaba domin kagama samun tabbacin indai itace matarka zaka sameta , ina maka nasiha ne sbd ita wacce kake kurarin bakaso itace zata fara zama first wife din taka , wannan kawai shine amma ni inason duk abnd kakeso shushun momy angon Aysha angon Aneesa , gsky abokina kai mai sa'a ne wadannan zuk'a-zuk'an mata haka
Yakai karshen mgn cikeda zolaya hadida dariyan shak'iyanci "
Shureim ya mike yana daukan car key dinsa yake fadin"kai dai Dan world ne wlh ka koreni tunda baka supporting my precious dina
Don haka bye zani gd inhuta idn kagama iskancin naka by next week nakeso ka rakani kd, ohhh nafa manta kafin nan ance inje inga waccan yarinyar "
Dariya sosai sudais keyi harda rike ciki kafin yafurta"alryt duk yadda kace haka za'ai angon nan da 2 month "
Wani uban tsaki shushu yaja yana ficewa daga offices din ,
Koda shureim ya koma gd gurin 2 narana kai tsaye part din momy ya nufa, domin yunwa yakeji sosai hakan yasa koda yashiga kai tsaye dining ya nufa , ya zuba abnci yafarci yayi nisa dafaraci momy ta fito
Sanye take cikin doguwar rigan bubu wanda yazauna ajikinta sosai, kana kallonta kaga manyan mata babu mai cewa ta ajiye kaman shushu sbd tsananin gyara da kulawa da jikinta ke samu
Fuskanta asake take fadin dama kashigo nida inatajin motsi , nakumasan yusrah ta fita ashe kaine kashigo koka nemeni , sbd kana fishi dani ko? Hmm yaro kenan atunaninka shushu kana zaton , zan iya zabama abnd zai cutar dakaine ? Hmm kumama banda abnka aiba cewa akai kwata-kwata bazaka aury sarauniyar zuciyan taka ba , cewa nayi saika fara auren zabin mu kafin naka "
Shureim wanda ya aje spoon domin yakare cin abncin ya dubi momy yana fadin"haba momy nifa ba fushi nake dakeba kawai dai tunanin yadda zanyi da mata 2 nake , domin bantaba koda mafarkin faruwan hakan agareni ba"
Wani harara momyn ta sauke masa kafin ta furta "to ai saika fara yanzu domin nan da 2 month zaka angonce da daughter na inyaso duk lokacin daka yanke asa rananka da ita Aneesa sai asa, don haka gara kazama jarumi tun yanzu , inaso kuma kasa tsoran Allah azuciyanka ka rike Ayshat da amana , koda bakajin sonta hakan bayana nufin ka wulakantata bane , idn kuma burin dake ranka kenan tokasani matukar ka zalince ta koka wulakanta ta wlh kaji na rantse bazan yafemaka ba "
A firgice ya dubi fuskan momy wanda sam babu alamun wasa atattare da mgn daya fito bakinta, jinjina kai yayi yana ayyana wai yaushe Ayshat tasami wannan matsayin azuciyan momy , har shine yau momy ke fadin bazata yafe masa ba idn ya wulakanta Ayshat?
Wani tsanan Ayshan yaji yasake mamaye ransa, da kyar ya saita bacin ransa yana fadin"Allah yahuci zuciyanki momy insha Allah ma babu abnd zai faru , ai Ayshat qanwata ce babu yadda zaai incutar da ita "
Ya kare mgn yana kallon fuskar momy wanda ayanxu tasaki wani murmushi, najin dadin kalaman da shureim yayi ,
Kafin ta furta gud my son kokaifa harnaji dadin mgn ka, ina tabbatar ma dacewan zakayi alfary da zabina zuwa gaba, Allah yai muku albarka kaida ita kai dama Aneesan gaba daya
Domin duk abnd kakeso nima inaso shushu matukar zai zame maka alkhairy ne ,
Sosai shureim yaji dadin kalaman momy , tunda aka fara wannan cecekucen sai yanzu momy tayi mgn daya faranta ransa,
Haka suka dinga hira sosai shushu yasaki ransa, wanda hakan ne burin momy shiyasama tasako mgn Aneesa don ya gane cewa bawai suna k'inta bane , sam sunadaiso yagane muhimmncin zabin dasukai mai ne
*********
Wednesday in the evening.........
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*19*
Wednesday in the evening Aysha ce kwance bisa cinyan umma , tana game din candy crush manyan calaban dake kanta umman ke warware mata , tana sharce mata dogon tashin ta da tsayinsa yasauka gadon bayanta
Wayan ummace tadauki rury hakan yasa ta tsaida abnd takeyi ta dauki wayan, ganin sunan hajiya kubrah ne yasa ta daga wayan tana fadin"barka da warhaka hajiya kubrah ya gdn ya yusrah "
Daga bangaren hajiya kubarah ta amsa tana shaidawa hajiya safiyan cewa, ga shureim nan bisa hanya zaizo su fara fuskantan juna da d'iyar tata Aysha
Sosai umma tayi farin ciki tana fadin"to shikenan hajiya babu damuwa gani ga Ayshan ma yanzu zan sanar mata sallama sukayi da juna "
Umma tadubi Ayshat tana fadin"oya saiki maza ki kintsa ga yayanki shureim nan zuwa ku gana "
Aysha kallon umma tayi alokaci guda kuma kirjinta yabuga , samun kanta tayi dajin fargaban yadda zasu hadu da shureim din, batasan yadda haduwan nasu zai kasance ba
Jiki asanyaye ta mike zuwa room din ta gashinta tafara gyarawa, tashafe shi damayuka masu qamshin gske , kafin ta isa ga sif dinta wanda yake shak'e da situru
Ta dade tsaye tana nazarin shigan daya dace tayi , kafin ta yanke shawaran zaro wata hadaddiyar gown ta atamfa , dinkin yayi asalin zama ajikinta sosan gske abnka da kwararrun Tailor suka tabi kayan
Light make-up tayiwa fuskarta tadauki designers perfumes ta shiga feshe jikinta dasu , axababben qamshine yagauraye dakin baki daya
Batayi tunanin daura dan kwaliba illah karamin veil data dauka wanda yadace da shigan jikinta, tayane gashinta dashi zuwa kafadunta
Juyi tayi agaban mirrow din tana furta masha Allah domin ita kanta tasan Allah yayi mata baiwan wani abu waishi kyau da diri
Phone dinta tadauka ta fito daga dakin kai tsaye kitchen tanufa , rabice keta faman shirya abncin dinner umurni Aysha tabata akan cewa , ta hado ruwa da juice zuwa su danbun nama with snacks takai dakin baki tashirya , cikin ladabi ta amsa da to anty
Ficewa tayi takoma dakinta sam tarasa dalilin datakeji bugun zuciyanta nakaruwa , number din yusrah tayi dialing bugu biyu ta daga wayan , cikeda zolaya take fadin "ran matan yaya shushu ya dade, ya akayine ? "
Ajiyan zuciya Aysha tasauke tana fadin kedai wlh baki rabo da wasa, ni dakisan ma yadda zuciyata ke bari dakin tausayamin plxx qawata kibiyosa kuzo tareman, wlh tsoran haduwanmu dashi nake yusrah, ke shaidace yaya shushu bawani jituwa muka fayeyiba illah gaisuwa dake hadamu, gashi yanzu mgn daya shigo tsakaninmu wlh nasan tsanata zaiyi tunda bashi yafurta yana sona ba, takai karshen mgn cikeda karyewan zuciya, wanda hakan yasa gaba daga yusrah taji tausayinta yarufeta , "
Cikin karfafa mata guiwa tayi dariya tana fadin"common karki bada mata mana miye haka da saurin karaya haka, babu wani abu qawata ki dake xuciyanki aikema bakece kika nemi ahadaku ba beside kinama da wanda zuciyanki keso , amma kika danne kika amince dashi , so inaso kicire duk wani tsoro aranki karma yafara gane weakness dinki akansa tunyanxu kinganeko , duk abnd kuka tattauna ki kirani zuwa anjima , yanxu dai kitabbatar kin wanku yadda yadace ehem bye "
Takashe wayan tabar Aysha jigum tana nanata mgn yusrah, dafa kanta tayi tana fadin ohh ashefa nikadai nasan sirrin dake raina game dashi , tabbas yazama dole incigaba da boyewa har zuwa inga yadda ya shushun zai karbeni
Tunaninta ya tsayane alokacin dataji umma na kwalla mata kira , hakan yasata mikewa dasauri ta fice still tayi tana zare idanu, ganin zaratan matasan biyu zaune suna kwasan gaisuwa
Sam batayi tsammanin sun isoba sai da umma taharareta sannan takariso cikin falon, daga nesa dasu kadan ta tsuguna gaidasu , wanda Dr. Sudais kadai ya amsa gaisuwan amma shi gogan baima da niyyan dagowa yadubi side din datake
Duk dacewa tinda ta tinkaro falon fitinannen qamshinta yafara cika hancinsa, umma ce kefadin "to shureim ku karisa dakin baki gatanan fitowa ko "
Kaman jira yake shiya fara mikewa yayinda yabar Aysha da karema shigan jikinsa kallo, yana sanyene cikin wata d'anyar yadi mai ubansun tsada , dinkin halpjanfer akai masa bakaramin kyau yayiba kansa ba hula illah gashinsa dake kwance luff sai shek'i yake, ya boye idon sa cikin bakin eye glass wanda dawuya kagane zahirin halin da fuskarsa ke ciki
Saida ta tabbatar sun isa parlon bakin kafin tabiyo byn su , tana shirin shiga tajiyo mgn sudais yana fadin"wai kai guy dinnan wani irin dan iskane kai , tunda muka fito kaketa faman wani cin magani , wlh kaji narantse idn yarinyar nan tafito ka wulakantata kaman agaban momy kayi ,
Kila anfada maka rashin so haukane kuma inbanda abnka itadin budan baki tayi tacemaka sonka take , ok don ta yi biyayya ta amince shine zakayi tunanin ko sonka takeko , lallai bakasan mata ba kasan dai Aysha bakaramar yarinya bace dayazama dole tayi tolerating wannan bad habit din daka dakko nunawa ko?
Sosai zuciyanta yashiga bugawa shikenan abnd take hasashe yatabbata , ya shushu ya tsaneta bayasonta lallai tayi gangancin furta amincema aurensa ,
Jikinta amatukar sanyaye tayi sallama domin takawo karshen maganganun datakeji , tun kafin gogan nata yafara furta wasu kalaman akanta
Sudais ya amsa sallaman yana fadin shigo mana amaryan mu , cikin jin kunya da mutuwan jiki tashiga tasami mazauni , sake gaisawa sukai da sudais cikin sakin fuska sai tsokananta yake yi
Shiko shureim ko gigin kallon inda take baiyiba gaba daya hnkln sa nakan wayansa , sai faman danne- danne yakeyi shirune yaratsa parlon tsayin mintuna
Daga bisani Aysha ta tashi tagabatar musu da lemu da danbun nama, sudais tafara turawa gabanshi kafin ta dauki na shureim ta isa kusadashi ta aje
Tana fadin "bismillanku ya shushu kusha lemu plxx"
Tamkar tayi mgn da gunki haka shureim yai mata , ko kallon inda take baiba jikinta har rawa yafara sbd bacin rai abnka damai saurin kuka , nantake hawaye suka cika idanunta tana maidasu
Komawa tayi tazauna tana wasa da zoben gold dake yatsun hannunta, mgn take cikin zuciyanta take fadin"oni Ayshat to yanzu miye laifina anan dahar ya shushu zai fara wulakantani don kawai na amince da bukatar mahaifiyansa ,?
Tabbas dole taboye duk wani sonsa datakeyi kodan gudun wulakanci , domin bazata jura wulakanci ba dole tanunawa shureim itama bawai tana raayinsa bane tamkar yadda yakejin ta aransa haka zata nuna itama tana jinsa
Mikewan da Dr sudais yayi rikeda plate ahannunsa yana fadin"amaryan mu bari inyi waje inbaku daman zantawa da angon naki ko? "
Yayi mgn cikeda zolaya hakan yadawo da hnkln Ayshan kansa , tayi kokarin zakalo murmushi tana fadin kai ya sudais aida kazauna miye aciki
Dafe kirji yayi tareda zaro ido cikin sigan zolaya yake fadin kirifamin asiry waneni dajin hiran masoya ina dai jiran yallabai din daga compound
Sosai mgn shi yaba Ayshat din dariya hakan yasata murmusawa har kumatunta suko lotsa ,
Byn fitan sudais shiru yasake ratsawa tsakaninsu har zuwa lokacin shureim nata faman danna waya, tamkar baisan dazaman wata halitta afalon ba haka yayi
Zuciyanta ne yacigaba da baci da irin salon wulakancin ya shureim din
Hakan yasata yanke shawaran kawo karshen shirun tahanyar dubansa tana fadin ...............
**********
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*20*
Ya shureim inaso kagafarceni abisa kuskuren danayi na amincewa da bukatan momy, danasan hakan zai jefa zuciuanka cikin tsanata wlh dana bijerema bukatansu
Nasan irin zafin dakakeji acikin zuciyanka, tamkar yadda nima nakejine dukkanin bamu son juna , amma kasani zabin iyaye ba abn yardawa bane , domin sun cancanci muyi musu biyayya, kaman yadda nida kai shaidane akan irin son da iyayenmu ke nunamana , bazasu taba zabamana abnd zai cutar damu ba
Ya shureim nasha kai dakake namiji kuma babba agareni zaka fini nuna jarumta gurin ganin muncika burin iyayenmu, atunani ne nice abn tausayi domin akwai wanda zuciyata keso , amma nasaudakar da abnd nakeso domin infaranta ran iyayenmu
Amma ina rokan ka dakayi hakury ka cire tsanata acikin zuciyanka,ni haryanzu ina kallonka amatsayin ya salman ne, wanda bazan so ganinsa cikin damuwaba, idn har kana da zabin zuciyanka ya shushu kasanar da momy tayi hakury ajanye batun auren mu amma bazan iya juran wulakanci ba
Takai karshen mgn tana kokarin maida hawayen dake shirin zobo mata , dukkanin maganganun datakeyi tanayinsu ne bisa karfin hali, juriya dakuma dakewa "
Shureim wanda tunda tasoma magana yake kallonta yana sauraran duk abnd ke fitowa abakinta, sai dai yarasa mai yasa maganganun nata suka fara karya zuciyansa, ashe dama bata sonsa itama biyayya take kokarin yi ?
Sam saiyaji zuciyansa baiso jin cewa bata sonsan ba , yaso yayi anfani da son datake mai ne ahasashensa yaji dadin wulakantata , amma kash.... Sai gashi tana furta masa cewa yadda yakeji gameda ita haka itama takeji , kenan ta tsanesa cikin jin zafin mgn ta yafara furta
"Ayshat inaso kisani tunda nake bantaba koda kwatanta son wata mace cikin zuciyata ba, hasalima sam ni babu soyayya atsarin rayuwata salman shaidane akan hakan,
Ganin cewa na isa aje iyali kuma burin su momy ne nayi aure , hakan yasa nabata daman zabomin mata wanda shine babban kuskuren dana fara nadaman furtashi rayuwata
Aranan dana bata zabi aranan nabar garin nan xuwa kd , awashegari na hadu da yarinyar data sace zuciyata ta ruguxa duk wani plan dina,
Itace macen datai nasaran mamaye zuciyata , Aneesa ita kadai zuciyata keso ayanxu ita kadai nake mafarkin inbude ido inganta agd na amatsayin mata ,
Aysha bantaba miki kallo nadaban daya wuce yadda nake kallon yusrah ba, nayi kokaryn momy tagane cewa ayanxu nasami wacce zuciyata ke tsananin so , amma kash takasa gane hakan hasalima ahalin da ake ciki yanzu mata 2 akeso inkasance dasu
Momy tace saidai infara aurenki kafin daga baya in auro zabin zuciyata , don haka ina shawartanki idn har kinsan kinada wanda kikeso kiyi gaggawan ganin baa kawoki gd na ba, domin babu abnd zaki fuskanata sai wulakanci sbd zuciyata bata kaunarki
Na tabbatar idn kika sanar da momy kina da zabin ranki zata hakura , idn kuma kin shirya xama da kishiya da mutumin da baki aransa kofa abude take
Yakarisa mgn yana wani yatsina tareda karemata kallo yadda hawaye ke gudu afuskanta"
Ayshat wacce takejin maganganun shureim tamkar zuban ruwan dalmane cikin zuciyanta, dago idanunta masu zubar da hawaye tayi tana dubansa , takasa dauke idanunta akansa wani irin masifan son sa da kishinsa ke sake narke zuciyanta, mai yasa zuciyanta takasa cire son shureim ? Meyasa shureim bazai yi naam da itaba ? Gashi yanzu yana sanar da ita wacce yakeso haryana fadin baya kaunarta , tabbas zuciya bataimata adalci akan so ba
Cikin muryan kuka take fadin "ya shureim naji dukkanin abnd kace sai dai inaso kasani , bazan taba iya bude baki insanar da momy cewa banason jininta ba
Bazan iya rusa farin cikin danake hange a idanun iyayena nason ganin zumuncin su yadore ba, ya shushu bazan iyaba nabaka dama kai dakake namiji kafadawa iyayena baka sona da bakinka , nasan zasu fi gamsuwa sukuma janye batun aurenmu , subaka zabin ranka karayu da ita kadai basai an hadaka da wacce katsanaba
Sai dai nasani matukar aurena dakai rubutacce ne ya shureim, duk da bamu son juna bazamu iya kaucewa rubutacciyar kaddaranmu ba, don haka inanan akan bakata zanyi musu biyayya
Amma kanada daman ka sakeni saki uku byn ankawoni cikin gdn ka , daga karshe inamaka fatan samun cikar burinka Aneesa "
Cikin sassarfa tabar parlon tana xubar da hawaye , jitakeyi inama zata iya cire son shureim dake kassara zuciyanta , data yarda kwallon mangoro kodan ta huta da kuda
Sai dai hakan ya faskara duk wadannan maganganun data fadamai , tafadesu ne cikeda karfin hali amma wlh tanajin sonsa nakaruwane cikin ranta
Koda tashiga parlor tayi saa ummanta batanan, hakan yabata daman wucewa room dinta , kan hado ta kwanta tasaki kukan datake rikewa kotaji sanyi cikin ranta
Abangaren shureim kuwa jiyayi tamkar andasashi agurin , maganganun Ayshat kadai kemasa yawo cikin kwakwalwan kansa, meyasa yarinyar tafishi xurfin tunani ne, tabbas idn har aurensu rubutaccen kaddara ne yasani bazasu iya gujewa hakanba
Sai dai yarasa meyasa zuciyansa ke azalzalansa dajin haushin yarinyar ne ? Ganin bashida amsan tambayan yasashi mikewa ya fice
Amota yasami sudais yana waya hakan yasashi , zagayawa bangaren driver yatashi motar suka fice daga gdn , byn mai gadi yabude musu gate aguje shushun kejan motn tamkar zasu tashi sama
Sunyi nisa kafin sudais yagama wayan dayakeyi yana fadin"waikan don ubanka lfy kake irin wannan tukin waima meyafarune tsakaninka da gimbiyar taka , yakarishe mgn yana kunshe dariyan dake son taho masa
Wani matsiyacin tsaki shureim yaja kafin yasami gefen hanya yayi parking, batareda yace uffan ba yafito tareda jefama sudais car key din
Zagayowa yayi yai tsaye yana jiran sudais din yafito, dariya sosai sudais din yakeyi harda hawaye kafin yafito ya koma inda shureim din yataso , shikuma yashiga yazauna seat din mai zaman banza yanata faman tsaki
Saida suka fara tafiya bisa titi sannan sudais yafara mgn"waikai guy dinnan meyafarune kaketa jan tsaki ? "
Kaman shushu bazai kulasaba sai dai yafara fadin"hmmm wai harnine yarinyar nan zata dinga gasawa mgn harda cewa itama bata kaunata yadda nakejinta araina itama haka takeji tanada wanda takeso, to don ubanta wani shegen yace ta amince da mgn tun farko
Wlh kaji narantse saina wulakanta yarinyar nan , inbanda ma anjanyomin raini harta isa gani gata tadinga furta kalaman da taga dama agare ni? Kwafa yayi yana fadin amma duk laifin momyne data dage akan wannan mgn
Sudais yatsaida dariyansa yana fadin "wow ammafa Ayshat
tabiyani wlh nagode mata dabatayi shakkan sanardakai bata son kaba,
Abnd nake fadama kenan kayi ahnkl domin amincewan ta bashi kenuna wai tana sonkaba, sai gashi tana sanar dakai kaga kenan tafika hnklne data zabi faranta ran iyayenmu , sabanin kai da soyayya take neman rufe idanunka , wlh kayi ahnkl matukar kace wulaknta yarinyar nan kazaba tofa kasani , wataran zakayi nadaman hakan domin kiyayya yana saurin juyewa yakoma matsananciyar soyayya , musamman idn yakance daya bashida hakki akan dan uwansa, don haka kataka asannu wlh ka kumayi hnkl da fushin momy ehe"
Shureim ya maka masa harara yana fadin kai dai dama ai ba'a abn kirki dakai , idn sonta kake why not amaida batun kanka , yakare mgn yanajan tsaki gaba daya haushi da tsanan Aysha yacika ransa,
Amma yazaiyi hakanan xai faranta ran momy ya aureta sai dai yana tausaya mata wulakancin dazata fuskanta daga gareshi byn anyi
Haka suka cigaba da tafiya babu wanda yasake kula wani , har Dr sudais yayi dropping shushun ya dauki motarsa yabar gdn
Akuma washegari aka kai duk wani abu da ake bukata nasaka ranan aure, inda aka tsaida 2 month kacal, byn iyayen sun tattauna batun shushun dana Aneesa wanda zai aura byn anyi bikinsu da Ayshat din,
Alhaji Adam bai nuna damuwa ko wani abuba yayi fatan alkhairy acewansa ai shureim yana da daman yin mata daga daya har 4 ne, umman ce dai taji tausayin diyar tata amma ganin yadda Ayshat din taboye damu wanta yasa itama take karfafa mata guiwa
Yau yakama weekend ayau dinne kuma shureim keson zuwa gurin precious dinsa, shida Dr sudai wanda zai masa rakiya
Tun 12 suka dauki hanyan kd byn yasanar da ita gasunan bisa hanya
********
Kd.......
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*22*
Yusrah zuciyata ta dade dakamuwa dason maso wani , wanda hausawa ke kirada koshin wahala,
Wlh yusrah nikaran kaina bazan cemiki ga sanda nafada son sa ba, fangar da sonsa nakeba sai da zuciyata tayi mummunan kamuwa da kaunarsa,
Tun inasaka rai zan iya samun soyayyan sa harna fara fidda tsammani, bansake fidda ran ba saida na fahimci nikadai ce zuciya da ruhina ke azabtuwa da soyayyar da, shi zuciyan sa tayi nisa gurin son wata shiyasa nazabi binne son axuciyata batareda nasanar da kowa sirrin dake rainaba
Yusrah ayau zan tona miki abnd nadade ina boyewa, wlh bakowa zuciyata ke azabtuwa dasinsa ba illah shureim , ya shushu shine kadai namijin dana rayu da sonsa cikin zuciyata ba, tunban san so ba harna fahimci sonsa nake
Hakan yasa da momy tazo da bukatan hadamu aure nayi saurin amincewa, a tunani ya shushu bazai tsaneni ba sai dai kash nayi kuskuren danake nadama ayanxu
Domin bana hango komi akwayar idanunsa sai zallan kiyayyata yusy , kifadamin yazanyi inciresa daga cikin mind dina? Shureim baya sona yusrah ayanxu ba wacce yatsana Irina , kallona yake amatsayin bakar katanga dazatai masa shamaki wajan hanashi samun cikan burinsa alokacin dayake bukata "
Aysha takai karshen mgn tana zubar da hawaye masu zafin gske ,
Yusrah baki bude take kallon Ayshat wacce tausayinta yagama cika zuciyarta, a hnkl ta matsa tareda rungume Ayshat din tana patting byn ta ahnkl
Take fadin "sorry my frnd kiyi hakury kikuma cire damuwa aranki , ina baki tabbacin ya shushu zai zama naki ya shushu zai soki fiyema da kike sonsa insha Allah ,
Banaso ki karaya kuma naji dadin yadda kika iya danne soyayyansa baki bary ya gane hakan ba, kicigaba da boyewa har zuwa lokacin da zai shigo hannu wlh kinji na rantse bana fatan ki raga masa ,
Ahnkl yusrah ke tsaida kukanta byn ta koma ta zauna, take duban yusrah tana fadin yusy yanxu baki tausayin ya shushu ,
Yusrah tayi dariya tana fadin yusrah kenan, kedai kawai kibi abnd nace , ki rabi dashi yaje yaita son wacce take gabansa ayanxu , komi yana zuwa da lokacin sane , nan suka cigaba da hiransu na aminan juna , anan ne kuma yusrah ke tseguntawa Aysha cewa ya sudais ke sonta
**********
Salman da Rufaida ne kwance akan bed cikin dakin hotel din dasukai masauki , byn yakawo mata ziyara daga garinna Abuja,
Salman shine namiji daya tilo da zuciyan Rufaida ta amince dashi , har take mallaka masa jikinta yayi yadda yaga dama ,
Sun hadu dashi ne agarin Abuja wani bikin dasukayi na qawarta , dasuka kaita birnin tarayyan , tunda salman yaganta ya like mata har dai yasami kanta ,
Suka fara soyayya har yagane cewa Rufaida cikakkiya kuma gaggiyar 'yar less ce wacce take harka da mata kala da daban -daban
Cike salo da iya jan hnklnsa yafara yaudaranta harta fara sallama masa kanta , shine namijin daya fara shigan ta byn tagama rabama mata kanta ,
Saidai yadda ta yafi dashi taba gamsuwa jiyayi bazai iya rabuwa da itaba, domin tagama gogewa a iya wasannin dake gigita mutum gata jarumace karshe gurin samar mishi da nutsuwa,
Tasha jin lbryn shureim aji abakinsa , yana kuma yawan fadan kyawawan halayensa , shiyasa ayanzu taci burin sake samun information akan sa daga salman din
Kanta na kwance bisa kirjin salman dinne bayan sungama sheke ayarsu , wasa yake da kirjinta yanda yakeso
Wayanta ta dauka tareda hasko pic din shureim aji , kafin tazare jikinta ahnkl tana sanya idanunta cikin na salman din take fadin
"My bobo inason kasanar dani waye guy dinnan , tana mgn ne tareda mika masa phone din nata "
Salman ya amsa yana dora idanunsa akan screen din wwayan,xunbur yayi yatashi zaune yana tsareta da manyan idanunsa masu firgitata,
Ganinpic din shureim awayanta yamatukar tsoratashi , sbd yasan Rufaida shaidaniyar yarinyar ce me kuma yakawo pic shureim wayanta?
Cikin tsare gida yake fadin uban me yahadaki da Pic din shushu? O akuyancin naki yafara dawowa kan mazane ba matan da akasaba biba
To barikiji shureim ba irin guys din da kukebi bane , wannan baya ciki da tambadaddun bariki kinaji ko , imma wani buri ko kwadayi kike dashi akansa u have 2 be very careful Rufaida ,
Sosai mgn salman yabata mata rai amma tashanye domin tasan yafita hauka , yanzu saisu samu matsala idn tace zata kawo masa zafin kai
Ganin ransa yabaci ne yasata komawa jikinsa tana kokarin hada bakinta danashi , wanda yaki bata daman hakan sai tabige ga shafa gashin dake kwance akirjinsa
Ahnkl take fadin "easy mana my sugar bobo nibabu abnd yahadani da shi illah information danake nema akansa
Domin qawata yakeso suna matukar son juna shine tasani inmata bincike akansa , wannan shine kawai amma kasan ni ai bakuwani dameni ba , nafi ganewa innemi mata kai ne kadai kake making love dani kaima shaidane bobo , takai karshen mgn tana lasan lips dinsa
Kafin sufada dukiyar kissing din juna , cikin dabara da lallami tadinga tambayan salman gameda shureim din har tasami abnd take nema ,
Yayi juyin duniya tasanar dashi wace yarinyar ce shushu kema azabar so haka, har yazabi yayi kata 2 don kawai yacika burinsa akan mallakanta
Sam sai hnklnshi yakasa kwanciya tausayin qanwar shi yasake kamashi , domin yasan shureim baya son Ayshat yagani akwayar idanunsa , domin shi mutum ne dabai iya boye abnd ke ransaba
Sai dai duk yadda yaso Rufaida tabashi haske akan yarinyar da shushun keso ttaki,domin baya fata takasance cikin jerin matan da Rufaida ke harka dasu , inko har hakan ne lallai shushu yayi zaben tumun dare
Hakadai sukagama tanvadewan su suka rabu da Rufy batareda yasami cikakkiyar shaidan cewa , yar less irinsu Rufaida shushu yafada tarkon sontaba
********
Alhaji wlh kaji narantse idn har baka yanke shawara akan bukatata na muyi aureba , saina tona maka asiri saina fallasa LAIFIN BOYE da kake shukawa kana boyema matanka ba
Nagaji da wannan rayuwan na rashin 'yanci kamaidani tamkar wata matar ka , sainayi mgn aure kafinga kaucewa
Byn kaine kafara bata budurcina to wlh nagaji dole ka aure inkuma ka kiya wlh saikayi nadaman sanina,
Wata matashiyar budurwace da bazata wuce shekaru 20 ba , black beauty ce ajikin karshe , tana mgn ne tana maida kayan jikinta byn tagama kintsawa,
Alhaji shu'aib Wanda ke kwance ya tsura ma maryam idanu , yana mamakin wai shine karamar yarinya, kaman yusrah zata tasa tana gaya masa mgn hartana masa barazana da zata tona masa asiry gaban iyalansa?
Lallai gaba daya zina baiyi ba yana sake nadaman jefa kansa cikin wannan masifa dayayi, gashi yakasa daina mu'amala da mata ,
Dagashi har aminin nasa garama shi kan adamun , wanda saima abnd yakaru azahiri dai sundaina safaran matasa da 'yan mata suna rabawa manyan kasa
Wannan sun tuba zinarce dai suka kasa dainawa ,shikam yakasa rabuwa da maryam ne sbd irin natsuwar datake samar masa
Tabbas lokaci yayi dazai yakice zina ya aury dadiron tasa wato maryam, yarinyar dayamaida ta tamkar matansa , kuma shine yafara sanin ta amace
Hakan yasa yake kara jin tausayinta , kallonta yayi byn tagama gyara zaman veil akafadunta , tana wani kada jiki take fadin toni zan wuce saika sallameni ka kuma je kayanke shawara, nabaka nan da 2weeks kayanke mgn 1
Rafar 40k ya dire mata tadauka cikeda yatsina tawatsa cikin jaka, kafin tafice tabarsa da fitinan qamshinta
Lumshe idanu yayi yakasa kwakwkwaran motsi , tunani ne yacika kwanyasa ta yadda zai tinkaray hajiya kubrah da zancen auren yarinyar cikinsa , domin sai dai suxo shekaru daya da yusrah ,
Sosai kansa yadauki zafi sai dai bashi da mafitan daya wuce hakan , tun kafin ta tona masa asiri agabansu ta fito da LAIFIN suke aikatawa a BOYE fili , gara ya aureta kawai cikin rufin asiry
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*24*
Koda maryam ta aje wayan duban qawarta nabila tayi , tana fadin baby nida wannan dittijon banzan ne fa , wlh saina shayar da Alhaji shu'aib mamaki
Matukar bai amince da aurena ba wai yana sanar dani inmasa uxuri ya aurar da babban yaronsa , tukunna saiyasan yadda zai bullowa matansa dabatun aurena
Ke kijimin fa nifa wlh tausayin ma matar nasa nake , domin da alamu bata da masaniya akan Duk irin ta'asar dayake aikatawa a BOYE
Nabila ta sheke da dariya tana fadin ai wlh maryam , nikaina mamakin halayyan wadannan bayin Allah nake idn kingansu cikin manyan kaya , saiki rantse mutanan kirkine , amma kibisa a hnkl mana tunda dai kinsan yana qaunarki
Tunda dai harya amince ai anyi mai wuyar , dariya sukeyi sosai yayinda gaba daya jikin yusrah yai mugun sanyi , haka kawai zuciyar ta ke kwadaitar da ita son jin waye wannan, dasuke yanka haka mai sunan dadyn ta
Cikin karfin hali da dakiya tadubi maryam din byn ta kirkiro murmushi , take fadin "umm nikam qawata aure zakiyi ne muzo musha biki ,
Maryam tayi dariya tana fadin hmn kedai qawata bari kawai , wani Alahji ne kewahal da zuciyata wlh , sosai nake azabtuwa da sonsa amma danayi mgn aure Sai yafara kwalo -kwalo
Kuma abn shi shina fara sallama ma budurci na , takarishe mgn tana fasa kwai da cingum din dake bakin
Baki sake Ayshat da yusrah ke duban maryam , xuwa yanzu dukansu sun amince dazargin su akan maryam din , cewa 'yar barikice
Yusrah ce tayi karfin halin fadin , o niko zanso sanin wannan mutumin gashi naji kin anbaci sunansa daya dana dady na , kinsan ina girmma masu wannan sunan
Amma ko inhakane bai kyauta ba shiyafi cancanta daya aureki tunda dai shiya fara saninki ,
Zuwa yanxu fuskan maryam yabayya alamun damuwa kadan , kafin ta dubi yusrah tana fadin " kedai bari qawata ai bariki baiyiba matsalan mace tafara saida mutuncinta atiti kenan
Wlh ina ragawa Alhaji shu'aib ne ganin shidin bakaramin mutum bane, kuma koda shiyafara sanina ba cikin dole yaminba , nice na sallama kaina sbd ganin akwai wuta ahannunsa sosai
Kafin tasake wani mgn wayanta yasake daukan rury , saida taja tsaki tana fadin kunga shinefa mai kiran , kaman bayanxu muka gama waya ba hmm bari kuji bai wuce yace muhadu a guess house dinsaba,
Tana mgn ne tareda receiving call din byn tadanna hands free , muryan Alhaji shu'aib ne yafito baro-baro yana fadin babyna , nifa amatse nake dake gsky duk yanda zaai kixo kisameni a guess house, haba jan ran ya isa haka nan rabona da inmory ni'imarki 1 week kenan
Tashin hnkl wanda baa saka masa rana shine yasami yusrah da Aysha alokaci guda , jin muryan dady nasakin wannan zance gaba daya jikin yusrah rawa yakeyi
Jitakeyi tamkar amafarki hakan ke faruwa , muryan maryam ne yadawo dasu daga duniyan dasuka lula na tashin hnkl
Tana fadin "shikenan Alahji na karka damu nima nayi kewanka daurewa kawai nakeyi "
Kit ta kashe wayan batareda tasake bashi daman mgn ba ,
Ta dubesu tana fadin kunji garanko dama ninasan zancen kenan ,
Nabila da sauran ne kawai suka iya mgn , amma yusrah da Ayshat ko tamkar an dasasu agurin haka suka kasance, yusrah ko motsi takasa tana ji inama mafarki takeyi ,
Saidai jin Ayshat na zhngurinta yasata gane afarke take , da kyar ta iya duban Ayshat wacce idanunta harsun fara canza kala tsabar tashin bnkl ,
Mikewa sukayi suna duban maryam cikin karfin hali Ayshat kefadin , sis plzz idn badamuwa munaso mudan kebe dake awaje , akwai mgn damukeso mutattauna
Mikewa maryam tayi tana gyara zaman mayafinta , kafin ta furta "ok babu damuwa mujeko "
Can waje suka fita direct gurin motansu suka nufa , yusrah ta bude back seat ta shiga byn ta kwanta yaraf , kaman jira take sukadaice tasaki kukan datake rikewa , hawaye masu zafin gske suka fara mata ambaliya
Ayshat ce budewa maryam front seat ta zauna , yayinda ita tazauna a seat din driver
Gaba daya sautin kukan yusrah akeji cikin motar , yayinda Ayshat ma batasan sanda tafara xubda hawaye ba
Maryam zuwa lokacin zuciyarta tafara sanar da ita akwai babbar matsala , hakan yasata bude baki tana fadin
"Bayin Allah lfy kuwa kun kirani kun tasani gaba kuna kuka kuma "
Ayshat tashare hawayen fuskanta tana fadin "maryam don Allah kisanar damu waye Alhaji shu'aib dinki , waye kuma kukai waya dashi yanxu , gaba daya kinjefamu cikin tashin hnkl
Domin muryan wannan damukaji ba muryan kowa bane illah na dadin mu , I mean mahaifin yusrah kuma aminin mahaifina , wanda kuma yake shirin zama surukina nan da 2 month
Takarishe mgn tana wani sabon hawayen "
Jikin maryam ne yai sanyi zuciyanta yashiga bugawa da karfi , no wonder tunda taga yusrah take ganin mugun kamansu da Alahji shu'aib, ashe 'yar sace ta cikinsa
Cikin tashin hnkl take fadin "Ayshat sai dai kuyi hakury amma wannan mutumin da kukaji shine wanda nake nufin ina tarayya dashi , shiya fara bareni aledata wanda ayanxu haka nakeda burin zama matarsa domin shiyafi cancanta daya aureni
Alahji banice kadai yafara tarayya da itaba yadade yana hulda da matan banza, ke amgn danaji akansa shida amininsa Alahji Adam, har rabawa manyan sanatoci zuwa minister mata sukeyi da matasa ana anfani dasu , amma sudai bantaba ji ance suna neman jinsin junaba
Alahji Adam yafi Alahji na harka da mata , domin xan iya cewa tasanadin farkansa afrah nahadu da Alahji shu'aib ,
Inamai baku hakury dacewa addua itace kadai mafita , amma iyayenku sunyi nisa a aikata LAIFIN BOYE
wani irin ihu yusrah tasaki tana fadin " wayyo Allah na Allah kasa inbude ido inga cewa duk abnd kunnuwana keji mafarkine , duk wannan abn idanun yusrah arufe suke kam
Sai dai jin sautin kukan Ayshat daya cika kunninta yatabbatar mata ba mafarki takeba, bude idanun tayi tajin gina jikin seat din , kanta da zuciyan tane suka dauki ciwo alokaci guda
Cikin disashewan muraya take fadin "tashi kije maryam mungode amma kisani bantaba tsanar wata 'ya mace sama dakeba aduniya , domin ke kika fara jifan dady da munanan kalamai agabana , bani kuma da hurumin hukuntaki domin shiya yada girmansa ,
Ina rokonki dakiyi gaggawar cireshi aranki domin ko kin aury dady bazaki taba daraja a idanun Muba , kaico dady yagama damu why why !
Dafe kirjinta tayi dake barazanar tarwatsewa , dariyan da maryam tasaki irin na marasa mutuncine yasake jefa yusrah cikin tashin hnkl
Kafin maryam din tafara mgn cikin gadara darashin kunya take fadin
" o sannu mai uba so inaso kibude kunnuwanki dakyau kiji , maryam ba shegiya bace nasan dadin mahaifi kaman yadda kikasani , banbanci na dake nibansami gata daga nawa iyayenba , wanda adalilin hakan harna jefa kaina halin danake ciki ayanxu
Tunda mahaifinki yai nasaran keta haddina wlh bani da mijin aure saishi kodako banasonsa , bare inasonsa sbd akwai wuta ahannunsa , idn na auresa zan fantama
Mgn rashin daraja bana fatan samunsa agareku , don haka abu daya zanbaku shawara ku binne wannan sirrin dakukasani na iyayenku , domin fallasashi nanufin rashin kwanciyan hnkl ne da iyayenku mata zasu shiga
Kucigaba da asirta LAIFIN BOYE da iyayenku ke aikatawa ,
Nabarku lfy takarishe mgn tana ficewa batareda ko waiwayensu ba "
Hakan kuma yayi dai dai da rushewan dasu yusrah sukayi , babu mai lallashin wani Ayshat har kanta take bugawa bisa kanbun motar ,
Yadda takejin zuciyanta tamkar zata yo waje haka takeji ,
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*25*
Ayshat ce tagaji da kukan ta lallashi kanta , juyawa tayi ga yusrah wanda idanunta harsun fara tasawa sbd kuka
Cikin dusassar murya Aysha kefadin "sis saidai fa muyi hakury kuka ayanxu bashine mafita ba, iyayenmu sun riga sun cucemu yusy bazamu taba goge tabon dasukai mana ba "
Ganin yusrah bata zimmar kulata yasa Aysha taiwa motar key , haka sukabar gdn bikin Zahrah saraki batare da amarya tasake sakasu cikin idanunta ba
Aysha gdn su ta nufa koda sukai parkin sun dade cikin motar batare da dayansu yayi yunkurin fitowaba, itadai yusrah gaba daya tazama kurma yayinda Ayshat tunanin yadda zasu shiga cikin gd ayanayin dasuke ciki kawai take
Fatanta Allah yasa karsu tadda umma aparlor , cikin karfin hali take fadin"yusrah mujeko amma kishare wannan fuskar taki , kinsan dai umma saita tambayi dalilin wannan hawayen ko"
Batare datace uffanba tamika hannu ga hand bag dinta , tissue tazaro tana goge fuskanta tareda shafa powder tadaiyi kwaskwarima , duk da hakan kallo daya zaka mata kasan taci kuka takoshi
Aysha kwaskwariman taiwa face dinta suka fito xuwa cikin gdn , cikin lucky suka tadda parlon shiru babu motsin ko TV hakan yaba Ayshat daman sauke ajiyan zuciya
Dakin suka nufa suka zube a sofa yusrah tayi jifa da veil dinta , tareda zare dankwalin kanta
Aysha ce tadubeta tana fadin "yusrah inaso kiyi hakury ki lallashi zuciyanki , kirufe wannan mgn atsakanin mu kada kice ko ya shushu zaki tinkara dashi nasan wautan ki baby
Kisani fallasa wannan sirrin tamkar tarwatsewan farin cikin su momy ne, mudai kawai muyi addua Allah yashiryar dasu , kuma mgn maryam da dady indai har auran ta zai zamo silar kintsuwansa waje guda , plxx baby yusy kubashi dama ya aureta
Inama Abba ne dadiron sa takike masa wlh zangoyi byn aurensa da ita matukar zai daina bin mata , yusrah zuciyata zafi takeyi inajin tsanan mahaifina tareda jin ciwan yadda yazubar da mutuncinsa , meyasa basu zabi sukaro ma iyayenmu kishihoyi uku alokaci guda akan su zabi mafi munin aikata LAIFIN BOYE ba?
Tunda Aysha tafara mgn yusrah tafara sharan hawaye, kafin tafara mgn tana fadin" Ayshat duk yadda kikejin tsanan Abba baikaiga yadda nakejin na dady ba , sannan wlh kinji na rantse saina sanar daya shushu wannan mgn
Domin shikadai ne zai iya ma Abba mgn kada ya aury maryam, bazan sanar da momy ba sbd ayanzu ina tausayin ta Aysha , idn kinga yadda take kokary akan dady da yadda kulkum yake tarairayanta , har abn yana bani sha'awa nasha adduan Allah yabani mijin dazamu gina rayuwa tamkar yadda su dady suke , basa taba nuna ma juna cewa sunfara manyan ta
Aysha bazaki taba tunanin dady xai iyacin amanan momy ba , momy ta yadda da mijinta bazan iya tinkaranta da wannan mummunan lbryn ba, amma ya shureim namijine yafimu kaifin tunani xan sanar dashi ko zuciyata xataji sanyi
Shiru Ayshat tayi tana jinjina mgn yusrah aranta, to ko itama zata tinkary ya salman da mgn ne? Wata zuciyan tace to aishima duk shegiyan darince
Wani takaicine yazirce zuciyanta itadai batai sa'an samin kamilin uba da yayaba, gara yusrah ya shureim natsatstsane wanda yasan ciwan kansa
Cikin karfi hali tadubi yusrh wacce itama idanunta nakan Ayshat din tana fadin "shikenan baby tunda kinyi rantsuwa "
Karfe 6pm na yamma yusrah ce tafito domin tafiya gd , Ayshat ce tarakota byn sunyi sallama da umman, wacce sam bata fahimci komiba kasancewar tunda suka dawo , suka kule adakin Ayshat basu fitoba sai da yusrah ta tashi tafiya gd , hakan yasa umma tunanin koma shigowansu kenan yusrah tasauke Ayshat din ita kuma zata wuce gd
*********
Karfe 9pm yusrah ce sanye da karamin hijab wanda ta dora akan doguwar rigan baccin dake jikinta
Saidata tabbatar momy na part din dady sannan tafice zuwa part din ya shureim , wanda cikin sa'a kofar abude take sallama tayi akofar falon nasa
Yana kwance sungama waya da Neesa kenan yafara kallon news , atashar NTA yaji sallaman yusrah
Yes come in yafadi idanunsa nakan TV shigowa tayi tana fadin ya shushu kallo akene,
Kallonta yayi yana fadin baby lfy daiko naganki kaman byn zu muka rabuba,
Nan da nan ta bata fuska alamun damuwa ya bayya afuskan ta , cikin damuwa take fadin ya shushu mgn nakeso muyi akan wani lamari daya firgita tunanina, tareda jefa zuciyata cikin tsananin rudu da takaici
Rage volume din TV yayi yana fuskantan ta sosai , yake fadin"inajinki baby sanar dani damuwanki domin bakida wani dan uwan dazai saurari matsalanki daya wuceni "
Ya shushu kataba sanin dady mazinaci ne ? Kataba sanin yana cin amanan momy yana harka da matan banza awaje, sannan katabajin mgn da akeyi akansu na kawalancin matasa da 'yan mata ga manyan kasa?
Tun yaushe dady yafara aikata wadannan munanan ayyukan a BOYE ? meyasa yazabi cin amanan mu yaxubar da kima da mutuncinsa don kawai yasami arxiki?
Ya shureim natsani dady wlh ayanxu natsanesa , kafadamin taya zan iya danne zuciyanta akan wannan mummunan lbryn daya ziyarci zuciyoyinmu nida Ayshat, dukanmu iyayenmu sun kasance masu aikata LAIFUKAN BOYE
Takarike mgn tana kuka mai taba zuciya , wani irin mummunan tashin hnkl ne yazirci zuciyan shureim,
A ina baby taji wannan lbryn ? Cikin son danne zuciyansa yariko hannunta yana fadin "baby a ina kikaji wannan lbryn ? "
Cikin muryan kuka take sanar dashi duk abnd yafaru yau har wayan da dady sukayi da maryam bata boyemai komiba ,
Wani irin takaicine yaziyarci shureim , yanzu dady dama basubar neman mataba , wannan wata irin masiface ?
Lallashinta yakeyi yana fadin duk abnd kikaji baby babu karya aciki, domin ranan wanka baa boyon cibi nan shureim yasanar da ita abnd yafaru abaya har kawo lokacin da su dadyn suka kirashi , suka nunamai sun tuba sai ashe mutuban bana daina neman matabane
Yacigaba da fadin yusrah dole kinatsu ki koyi danne damuwa da bacin rai , sbd kar momy tagano halin da akeci kinji ko , yanzu adduan mu dady yake bukata bawai fishi da bacin ran dazamu nunaba
Sannan mgn maryam sam batada laifi don tadage saita auri dady , don shiyafara keta mutuncinta batareda tsoran Allah ,ya tuna yanada budurwa kaman ki ba , yasaki ji alokacin da kika rasa budurcinki kuma wanda kikavawa kanki yagujeki alokacin dakike tsaka dason kasancewa tareda shi baby?
Don haka matukar dady yaxoda batun kara aure zai auri yarinyar , to yazama dole mubashi goyan baya yusrah hakan shine kadai gatan dazamuyi ma momy , mu ceto dady da ita yarinyar daga fasadin da suke aikatawa,
Kukan yusrah ne yakaru cikin rishin kukan take fadin "yanxu ya shushu muna kallo dady zai aurowa momy karuwa wlh ya shushu natsani maryam "
Wani tsawa yadaka mata cikin bacin rai da fishi yake fadin
"Eh haka nake nufi baby idn bamu barshi ya aureta ba mubarsu sucigaba da aikata sabo? Look yusrah duk yadda kike taya momy jin zafin kishi nafiki son kasancewanta cikin farin ciki
Auren maryam da dady shine kadai mafita , don haka ki boye duk wani damuwa dazai janyo hnkln momy tafahimci akwai wani abu da kike boyewa
Zamu xuba masa idanun har lokacin dazai tinkary momy da zancen sake auren sa , daga lokacin mune zamu karfafa zuciyanta harta bashi goyan baya , natabbatar idn taga mun amince zata amince itama "
Yacigaba da rarrashin yusrah yaana karfafa zuciyanta sai da yatabbatar tagamsu da maganganunsa kafin yadora dafadin
"Baby yusy wannan halayyan nasu dady yana daya daga abnd yasa nasakejin tsanan aurena da wancan yarinyar, domin sam nadaina ganin mutuncin Abba Adam"
Yusrah bata bari shureim ya ida fadin mgn dayakeson fadiba , tayi saurin rufe bakinsa tana fadin
"No ya shushu kada kabary laifin Abba yashafi Ayshat wlh Ayshat yarinyar kirkice, da kaga halin datashiga asanadin jin halayyan dasu dady ke aikatawa sai ka tausaya mata , kada ka tsaneta akan hakan ya shushu don Allah kaso Ayshat kodon darajan yadda umma keyabon halayenka nagari ,
Wlh ya shureim zakaji dadin zama da Ayshat domin she's very simple bata da matsala , nasani so ahnkl yake shiga amma kayi kokary kasanmata wani gurbi koda kadan ne cikin zuciyanka
Nasan Anty Aneesa tayi zaman durshan but ya shushu muma asanmana ko gurbi kadan ne plxx kajiii.. "
Takarishe mgn cikeda shagwaba tana langabar dakai , sosai taba shureim din dariya yana fadin
"Wlh baby bakida dama wannan irin kamfen haka toko dai itace ta turoki ? "
Zaro idanu yusrah tayi tana fadin "tabdi karifan asiry da Ayshat wlh sam ba itabace nice dai nake ganin tadace tasami gurbi a hrt dinta ,
Aysha tanada wanda zuciyanta kematukar so ya shushu kawai dai tazabi tasadaukar da abnd zuciyanta kesone donta faranta ran momy , ko wannan kadai ya isa karaga mata ya shushu ka kaunaceta kodan kaima nafaranta ran momy , takarishe mgn cikeda damuwa a fuskanta tmkar gske "
Jikin shushu yayi sanyi yana jinjina karfin hali irin na Ayshat , wanda shikam ayadda yakejin Aneesa aransa baya tunanin zai iya sadaukar da son donya faranta ran wani ,
"Hmm baby kenan zan duba dacewan hakan but ni Neesa ita nakeji araina , amma kicigaba damin addau Allah yabani ikon yima kawarki adalci
Haka shureim yafurta yana mai duban agogo , ganin har 10 yawuce yasashi mikewa domin raka yusrah part din momy"
Byn yasake kwantar mata da hnkl akan batun su dady ,
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*27*
********
Rana bata karya ayaune za'a daura auren shureim shu'aib Abba aji da Ayshat Adam
Tun safe Ayshat keta faman zubda hawaye wadanda suke zuba da ma'anoni biyu , nafarko tana murnan zata mallaki namijin da sonsa yaima zuciyanta mummunan kamu
Na biyun ko natausayin kanta da irin zaman dazasuyi da shureim wanda ta tabbatar balallai zaman yazama mai dadi ba, sai dai zamn fuskanta hakury da juriya kawai
Yusrah kadai tasan ma'anan kukan da Ayshat din keyi hakan yasa , ba matsa akan lallai tayi shiruba tabarta tayi mai isanta , yayinda su sury karofi kezaton kukan rabuwa da gd ne Aysha keyi tun farin safe
********
Abangaren ango shushu kuwa tun safe misalin 10 yake aikin lalllashin Aneesa , wacce take tafaman yimasa kuka da shagwaban wai zaa kai masa Aysha ,
Magiya takemai kada yaci amanan soyayya yajuya mata baya , idn ankai masa amarya gaba daya tagama susuta shureim da salon kukanta da shagwabar da take mai
Wanda kesake jefa zuciyansa cikin wani haki , baisami kan gimbiyar tasaba sai gurin 12 suka rabu awaya
Shureim yai shiru yana jin yadda zuciyansa kebugawa , tareda so da kaunar Aneesa
Agefe guda kuma wani yanayi yake tsintan kansa ciki nabacin ran auren Ayshat da za'a lika masa yau , wanda yake jin inama da cikar burinsa ne Aneesa , dabazai iya misalta halin farin cikin dazai shiga ayau dinba
Lokaci nata tafiya batare da shushun yayi yunkurin koda motsawa daga kwancen dayake ba , bare asaka ran zai tashi yashiga wanka
Wayoyinsa dayasan zaa damesa gaba daya yayi switching off din su ,
Already baima bude kofar part dinsa ba , sai yanzu datakeji anata knocking tamkar zaa balla kofar
Afusace yamike ya bude kofan 4 eyes sukayi da Dr sudais , wanda yasha wanka cikin fararan manyan kaya , sosai yayi kyau sai zabga qamshi yake
Still yayi yana karewa shushun kallo ganin singlet da boxer kadaine ajikinsa , da alaman ko wanka baida shirin shiga gashi harsun fara samin baki masu zuwa daurin auren kasancewar 2 ne
Gashi har 1 tayi wani uban harara ya zabgawa shureim din , kafin yaraba ta gefensa yawuce batare dayace dashi cikanka ba
Kai tsaye bathroom din cikin bedroom din shushun Dr sudais ya nufa , byn ya zare babbar rigan dake jikinsa ya aje
Ruwan wanka yatara masa kafin yafito yana fadin "dallah Mallam katashi kashiga wanka lokaci natafiya , banson iskancin banza tun dazu uwar me katsayayi , inata kiran line danake da hope din samunka tunda ka kulle wadancan amma line busy
Bai wuce kana waya da wancen yarinyar bako , tana batama lokaci da kissarsu ta mata kamance uban mutanen dazaka tara ko "
Da shushu yaje yai wankan yana fitowa ya tadda har Dr sudai yafito masa da kayan dazai sa , wanda sak iri daya suka dinka banbancin zaren da akai dinkin ne kawai
Sosai shureim yai masifar kyau cikin manyan kayan , kyawunsa yake fitowa agogon zallan azurfa ya daura a hannunsa
Kafin yafara feshe jikinsa da turaruka masu qamshin gske , kallon sa kawai sudais keyi yadda yake komi cikin basarwa
Koda suka fito nan mosque na jikin gdn sukai sallah , kafin yaja hannun shushun zuwa gurin momy
Gd yacika dankam da mutane da dakarn mata 'yan uwa da abokan arxiki , haka sukai ta ketawa duk inda suka wuce sai ansake kallon shureim aji domin yayi kyau naban mamaki, yafito angon sak cikin karfin hali yake ma kowa murmushi domin danne damuwar dake zuciyansa , kodon momy tayi farin ciki
A bedroom dinsa suka sameta taci ado tamkar yarinya karama, babu mai dubanta yasha itace tahaifi shushun sai dai ace ko kaninta ne
Cikin sauri tawaremai hannuwanta yakariso ta rungume abnta , qawayen ta su hajiya rahma suka dauki tafi
Kafin asakar musu ruwan flash bakin momy yaki rufuwa , Dr sudais shima kallon sha'awa yakebinsu dashi dashi
Sosai shureim ya nuna farin cikin sa ajikin momy sai smiling yake faman zabgawa ana daukansu pic
Kafin daga bisani su fito domin saura baifi mintuna 30 ashafa fatiha ba ,
Karfe 2 dot dubban mutane manyan kasa da hanshakan 'yan kasuwa suka shaida daurin auren shureim da Aysha cikin sadaki 500k
Daganan nan kuma aka rankaya zuwa babban hotel din da za'a gabatar da reception ,
Duk wanda yadubi manyan aminin junan Alhaji shu'aib da Alhaji Adam zai tabbatar da irin farancikin dasuke ciki awannan rana
Byn daura aurene aka gabatar da gagarumar walima ta mata zallah a gdn su Ayshat din
Hazikar malamar da aka gayyato wato malama ummy shatu , tayi matukar kokari guriin fadakar da mata yadda zamantakewan aure akeso yakasance ga ma'aurata cikin dinbin ilimi da wayewa
Ta tabo dukkanin muhimman bangarory da mace yakamata takula dasu , agdn aurenta mussaman bangaren tsafta da kula dakai , kulada shinfidar miji tareda muhimmancin biyayya ga mijin dakuma girmama iyayensa
Kulada tsaftar gd , jiki dana shinfida zuwa tsaftar abnci , dole mace tasami cikakkiyar kwarewa da wayewa akan wadannan,
Ummy Aysha tacigaba zabga wa'azi mai kashe jiki wanda yasa Amarya Aysha keta faman kuka , a lokacin ne tasake jin cewa ashe jan aikine akanta wanda dole saita saka hakury da juriya sannan tafiyar zata yiwu
zuwa yamma ne aka gama shirya amarya cikin shiga ta alfarma , zuwa bangaren Abba dimin yimata nasiha kafin awuce da ita gdn ta
Sosai yai mata fada da nasiha masu ratsa zuciya daga karshe yasamata albarka
Gurin umman ta aka maidota wacce takasa cewa komi suka qanqame juna suna kuka gunin tausayi
Sai 'yan uwantane sukai ma Ayshan nasiha da kyar aka zare Ayshat daga jikin momy
Yusrah wacce tagaji da haduwa cikin ashoebin laces dasukayi na qawaye itace ta taho tarike hannun Ayshan tana rarrashi har gurin da convoy na motocin daukan amaren suke
Nan aka saka Ayshat atsakiya wata qanwar umma na gefe guda , yayinda yusrah ke rikeda Ayshat din wacce har zuwa lokacin kuka takeyi mai taba zuciya
Gaba daya tagama karyar da zuciyan yusrah wacce lokaci by lokaci take dauke hawayen dake fita a idanunta
Har aka isa maitama inda zaa fara damka Ayshan hannun momy , sai andawo daga gurin gagarumar Dinner da momy tashirya kafin za'a kaita gdn angonta dake sun city
Sosai aka karbi amarya cikin karramawa da mutuntawa , momy rasa inda zata saka Ayshan tayi sbd matukar farin cikin datake ciki
Karfe 8 aka fara tafiya gurin dinner din
Amarya Aysha tasha make up daga kwararriyan mai make-up din da momy tadakko ,
Yayinda tafito taiwani irin kyau cikin weeding gown da THE CICADA suka fito da ita fadin irin kyan datayi abn sai wanda yagani
Qamshi kuwa dake fita ajikinta abn sai wanda yashaka , waya sudais yaiwa cwtyn sa yusrah akan gasu awaje kasancewa duk angama kwashe qawaye
Sukadai suka rage da Amarya sai momy da qawayenta dasuketa shirin fita suma
Hannun Ayshan cikin na yusrah wacce itama tagaji dayin kyau suka fito , kallo daya shureim yai musu wanda yake sanye cikin manyan kaya white anyi aiki daxaren dinki light brown
Color din wedding gown din Amarya wacce akayi anfani da cream an light brown , sosai kuma ya amshi fatarta
Tunda ya dauke kai baisake waiwaye inda suke ba , illah ma wayansa daya zaro yana latsawa shiko sudais Gaba daya ya shagala akallon yusrah wacce shiganta yagama tafiya da zuciyanta
Shiyayi saurin fitowa yabude back seat Aysha ta shiga , kafin yusrah takoma front seat ta kame idanun sahibin nata nakanta
Yayinda bugun zuciyan Ayshat yakaru wani irin qamshinta dana shushun ne yahadu guri guda yabada wani irin qamshi mai masifan dadi
Saidai takasa sakewa tanaso ta kalli fuskansa amma tana tsoran suhada idanu , babu wanda yatankawa juna tsakanin shida ita
Sunyi nisa suna tafiya inbanda yusrah da sudai daketa soyewansu babu bai cewa uffan cikin Amarya da angon
Kiran Aneesan sane yashigo wayansa cikin zumudi ya daga wayan yana fadin "hello my pretty daga bangaren Aneesa tafara zubamai shagwaba waiya turo mata pic dinsa taga wankan da yayi na zuwa dinner din
Hade face yayi cikeda narke murya tamkar wani karamin yaro yayi mgn" haba my precious wai harkin daina kishinane kike fadin wannan mgn , ni inanan xuciyata nagareki amma harda wani cewa inturomiki pic "
Ko meta fadi masa oho sai wani dariya shushun yayi yana fadin , I luv u my pretty oya tell me mgn dazai kwantar min da mind dina inta recalling har zuwa muyi waya anjima
Kometa fadi masa yai kissing wayan kafin ya aje yana kokarin juyawa ya kalli fuskan Ayshan yaga yanayin datake ciki
Kaman tasan nufin sa taki dagowa da kanta wanda ke kasa , zuciyanta tamkar zai faso kirjinta haka takeji
Wani masifan kishi da tsanar Aneesa ke mamaye zuciyanta , yayinda datake tausayin kanta nahalin dazata shiga naganin wulakanci a gdn shushu
Tun yau yafara waya da ita agabanta babu ko karan ganin yau aka daura musu aure, tabbas ta amince ya shureim bayi kaunarta
Wasu hawayene takeji suna kokarin taho mata tana dannesu don gudun bata kwalliyan fuskanta , sai dai duk iya yadda tayi kokarin ganin basukaiga xubowa saida suka xubo
Batare datayi yunkurin sa tissue din dake hannunta ta daukesu ba , Daga yusrah har sudais basuji dadin yadda sudais ya amsa wayan Aneesa ba
Domin duk wanda yaga yanayin yadda akai wayan yasan don aci fuskan Ayshan ne , sam yusrah tadauke wuta jitakeyi tamkar itace akama wannan cin fuskar , tabbas dolene qawarta saitayi hakury takoyi danne zuciyanta matukar salon da ya shushun zai dauka kenan naci mata fuska don ya nuna bata gabansa kome?
Har suka isa gurin babu wanda yasake cewa uffan cikin yusrah da Dr sudais da zuciyoyinsu yagama baci da abnd shushun yayi
Sudais da yusrah suka fara fita suna jiran fitowan ya shushun da Ayshat, wanda kaman jira shureim yake su fita Ayshat na kokarin fita sai jitayi yajawo hannunta
Tareda matse yatsun hanunta da karfi cikeda mugunta, hakan yasa Ayshat sakin wani wahalallan kara
Tana mai duban fuskansa tuni wasu hawayen sun zubo mata , wani makirin smiling yasakar mata kafin yakai bakinsa saitin kunninta har kuma zuwa lokacin bai daine murje mata yatsuba
Kirjin Ayshat tamkar zai fado sbd bugawa , gawani rawa dajikinta yake tamkar mazari ,
Jin saukan voice dinsa tayi yana fadin"hey Amarya ina miki murna da shigowa rayuwan shureim , biyayyan ki da jajircewanki wajan ganin kin cika burin iyayenmu abune xa za'a jinjina miki
Saidai inaso kisani bazaki taba sauya zuciyan shureim ba , shureim Aneesa kadaice cikin xuciyanshi
Don haka saiki shiryama zama da mutumin dazuyansa kefarautan samin cikar burinsa wato my pretty ,
Sannan wannan hawayen dakike xubarwa donnayi waya da rabin raina , kadan kikagani wannan somin tabine so karki wani far a damuwa kinji ko qanwata"
Yakarishe mgn yana sake mata yatsu byn ya murzasu dakarfin gske , awahalce tayi wani kara kafin tayi kokarin ficewa daga motan , tanajin zuciyanta na mata zafi yusrah ce yakariso da sauri tana fadin
"Sorry Ayshat kada kibari bakaken maganganunsa sufara tasiri akanki tunyanzu , dole saikin jure ahnkl ta dauke hawayen dake fuskan Ayshan , batare da tabari kwalliyan yabaci ba
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu棣冩瀳
*28*
Karisowan shushu kusada su ne ya tsaida mgn da yusrah keson sake fadi, batare da yace komiba yariko hannunta
Suka fara takawa har suka isa inda qawaye ke jira wanda zasu shiga da Amarya, duk wanda yaga yadda shushu ke zabga smiling da yadda itama Ayshan take smiling zaiyi zaton wasu masoya ne masu tsananin kaunar juna
Bakin momy yakasa rufuwa sanda tayi tozali da tilon d'an nata , da Ayshan wacce akullum zuciyanta ke kara natsuwa da ita amatsayin surukan datake tunanin zata kula mata da shushun ta
Gury yayi gury antara matan manyan mutane , sosai dinner din yaqayatar da duk wanda ya halarci gurin
Koda aka fito filin rausayawa karkuso kuga yadda abokan ango dashi kanshi suke ma Ayshan barin kudi ,
Wanda shi shushun yanayi ne don yafaranta ran momy , yakore duk wani shakku cikin zuciyanta ,
Sbd yagama tsara Irin zaman pretending din dazasuyi da Ayshan, wanda momy bazata taba gano komi game dashi ba, har zuwa lokacin dazai mallaki abar kaunarsa Aneesa
Koda aka tashi dinner sosai Aysha ta dage akan saidai sudais yafara komawa da ya shushu , domin bazata sake shiga motar dayake cikiba
Tun suna ganin kaman wasa take har suka fahimci abn nata dagaske takeyi , duk kuma wannan darun da akeyi ya shureim din yadade dashiga mota sukadai yake jira
Sunacan suna ba Ayshan baki akan tayi hakury amma fir taki , ganin shirun yayi yawa yasa shushun fitowa ahnkl yake takawa har zuwa inda suke tsaye
Yusrah na ganin sa tafara fadin "yawwa ya shushu kazo ka lallashi amaryan mu wai cewa tayi bazata shiga mota mukoma kamar yadda mukazo ba
Bai jira komi ba kawai gani sukayi ya fincikota yana ja , yayinda Aysha tsananin takaici yasata fashewa da kuka , tarasa miye yasami brain din ya shureim yake mata wulaknci irin hakan
Ganin yadda take neman tirjewa yasashi daukanta cak zuwa motan , yusrah da sudais dariya sukeyi sosai suna mamakin halin shureim
Koda yadireta a motan wani tsawa yadaka mata yana fadin , will u shut up kosaina bige bakin , uban waye bawanki dazaiyi sahu biyo gurin daukanki?
Ok sbd kinga suna lallabaki shine kike samin daman kawoma mutane raini ko , dacen wani gulman yasa kika biyo mu aida tunda fari kinyo motanki daban ne , yakarishe mgn yana jan wani dogon tsaki
Hannunta daya damke ta fisge dakarfin gske , kafin tasanya idanunta cikin nasa wanda suke zubar da hawaye tana fadin" enough ya shushu maganganun sun isheni hakanan ,
Wlh bawai kafini baki bane ko kuma tsoronka nakeba, sai dai ina baka girmane amatsayinka na yaya kuma miji agareni , wanda Allah yasanya aljannata akarkashin kafanka , bacin haka wlh ya shushu dana gwadama kaima baka gabna kaman yadda nasan zuciyanka tayi nisa akan wata can daban
Kasani nima zuciyata namiji daya nariga na mallakawa ita , wanda banajin har adauki numfashina zan iya daina kaunarsa ,
Takai karshen mgn tana murguda baki cikeda tsiwa tamkar ba Ayshan danasani mai kawaici da kauda kai ba ,
Baki sake cikin tsananin mamaki shureim ke kallonta , gaba daya yakasa furta komi lallai shi anriga angama jawo masa raini , gawani masifan jin dacin mgn ta dayaji nacewan dason wani zata mutu , haka kawai yakeson sanin to waye wannan din ?
Sai dai kozai mutu dason jin haske akan hakan bayajin zai iya budan baki yasake mgn ayanxu , da zuciyansa tagama baci dajin zafin kalamanta
Shigowan su yusrah yasake rufe bakin shushun batareda dayayin yunkurin maida raddi ba ,
Tunda suka tafara tafiya banda yusrah da sudais dake hiransu kasa -kasa , babu mai cewa uffan saima lokaci -lokaci da Ayshan kesakin tsaki wanda hakan bakaramin kona zuciyan shureim yakeba,
Gani yake gaba daya tagama rainashi shizata tasa tanama tsaki , duk ya kosa su sauka don tsananin zafin da zuciyansa kemasa
Direct unguwar sun city suka nufa gdn shushun , Wanda katon gd ne nagske yamallaka masa halak malak ne yazauna da iyalinsa
Koda sukayi parking yusrah tafara fita yayinda tazagayo ta budema Ayshan kofa domin tafito
Sai wani harara daya shureim din yaimata yasata saurin ja baya , tana danne dariyan dake son kwace mata
Gaba sukayi can da sudais suna hiransu tamasoya , yayinda Ayshat tayi yunkurin ficewa daga motar tana jan tsaki
Hannu yasa yajango riganta da karfin gske wanda saura kadan yafada bisa kirjinsa, idanunsa harsun sauya kala sbd bacin rai yake mgn
"Ke wai waye tsaranki dazaki tasa kinama tsaki byn kingama rashin kunyanki ban kulaki bako, to kisani yanzu kina karkashin ikonane zan kumayi maganin rashin kunyanki , kuma mgn kina son wani wannan keya shafa domin kinfi kowa sanin bakya gabana , inada wacce nake tsananin so
Wani tsakin tasake ja batare data ce uffan ba , takaicine ya ciyoshi har baisan sadda yajuyo da fuskanta yana jifan ta da mugun kalloba
Kafin yasa hannu ya bige bakinta yana fadin " idn kika sakemin tsaki wlh sainayi miki abnd bazaki sake yunkurin yimin tsaki agabana ba , nonsense kawai
Aiko yana sakin ta tasake jan wani dogon tsakin tana fadin , kayi duk abnd kaga dama ya shushu domin nagaji da salon wulakncin ka
Da karfi yasake janyota wannan karon saida tafado bisa kirjinsa ,ga mamakinta bakinsa yake kokarin hadewa danata
Duk yadda taso kwace kanta tagaza yin hakan domin karfin ba daya bane, sosai yashiga tsotsan bakinta cikeda mugunta kafin ya lalubi harshenta yaciza da karfi
Wanda yasa Ayshan kusan sakin fitsarin tsabar azaban daya xiyarci kwanyan ta , tuni hawaye sunfara gudu Kafin yasake yana fadin
"Kisake gwada yimintsaki kigani inban tsinke harshen ba mara kunyar karya kawai oya get out tun banyi ball dake cikin motar ba"
Wannan karon jikin Ayshan gaba daya rawa yakeyi , tagama tsorata da ya shushun gawani radadi da harshenta kemata
Cikin saurin kaman zata kifa tafice amotan tana share hawayen fuskanta , gashi rigan jikinta tahanata saury da kyar ta isa inda take hango su Dr sudais da yusrah atsaye
Hangota da baby yusy tayi yasata saurin tahowa ta kwashe mata rigan tabaya suka fara takawa xuwa cikin gdn
Da bismillah tasaka kafarta ta dama cikin dakinta , harxuwa bedroom dinta yusrah takaita , sauran frnds ne suka cika dakin dawasu 'yan uwan Abba da momy
Su shukrah dange ne suka shiga tsokanarta , wanda har suka gama Aysha babu bakin mgn , domin shushu yakasheshi murus dasalon muguntarsa
Yusrah ce tazame tayi waje domin suyi sallama da hubbynta kafin su wuce
Koda tashigo ta tadda Ayshan ne bisa pray mat tana gabatar da shafa'i da wutury , koda ta idah kan gado ta dare tayi kwanciyarta
Batare data shiga cikin hiran da qawayen nata keyiba , wanda rabin hiran zancen haduwan shushun da dacewan da sukayi da Ayshan su surayya keyi
Lumshe idanunta Ayshat tayi tamkar bacci tafara , wanda azahirin gsky zuciyanta tayi nisa gurin tunanin wace irin zama zatayi da ya shushun
Duk sanda sunan Aneesa yafado ranta sai gabanta yafadi , yayinda wani kishi kan rufe zuciyanta kaman ayanxu kaf wayan da shureim din yadingayi da Aneesan kedawo cikin brain dinta
Tamkar ayanzu yake amsa wayar haka takeji cikin zuciyanta , tabbas tagama amincewa Aneesa tagama sace zuciyan ya shureim
Wasu siraran hawayene ke fita daga idanunta , daxata iya yakice shushu cikin zuciyanta tabbas datayi hakan kodan tahuta
Sai dai duk irin abnd yake mata sonsa ma karuwa yake cikin ranta , mussamman ayanxu da takeda tabbacin yaxama mallakinta
Gaba daya Ayshat awannan Daren tayi baccine cikeda mafarkan ya shushun wanda tana rasa gane kan gadon mafarkin
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*29*
Washegary ne budan kai around 9pm anwatse tas daga gdn amarya, Daga ita sai yusrah itama din momy ce tace tazauna idn angwayen sun shigo saita koma gd
Hakan yasa yusrah kama hannun Ayshat suna zagaya dakunan, wanda kusan 4 bedrooms ne da parlour har kala 3, banda part din shushun wanda basuyi ma karanbanin zuwa ba
Aysha tajinjina wa Abban ta takuma hakikance itadin 'yar gatace, domin ankashe mata dukiya fiyeda tunanin mai karatu ,
Byn sungama ne sukai masauki anan falon dayake dagashi sai bedroom din Ayshan, hira sukeyi da yusrah wanda rabin hiran tana karfafa guiwan Ayshat din ne akan , takasance mai hakury da kauda kai sannan tayi iya kokarinta gurin ganin ta kyautata ma ya shushun
Basu shigo ba sai around 10 su biyune kacal daga shi sai Dr sudais , koda suka shigo tun akofa suke jin tashin qamshin turarukan wuta masu azabar qamshi
Har suka danna kansu a katon main parlor din wanda yagaji da haduwa , anan sudais yayi masauki bisa 2 seater
Yana duban shushun dake wani faman yatsina , yana fadin "to mallam saika fito da amarya musayi baki ko
Wani harara shureim din ya aika masa kafin yafurta " saika kira babyn ka ai don inajin suna tare domin momy tace kaine zaka sauke mata ita gd , das y ma nayi kokari muka shigo yanzu "
Sudais baisake furta ko kalma 1 ba ya ciro wayansa yana kiran line din yusy, Daga wayan tayi tana narke murya
Bata dauki lokaci ba sai gata afalon dasuke zaune , duban ya shushun tayi tana fadin
"Ya shushu ina yini "
Harara yabita dashi batare da ya amsa gaisuwan taba , ganin hakan yasa ta dubi hubbyn nata tana gayar dashi
Wanda yake binta dawani mayen kallo yake amsa gaisuwan , tareda fadin "my cwt ina amaryan tamune plxx taho da ita mugaisa tunda wannan dan iskan bashida niyan tashi "
Murmushi tayi tajuya zuwa taho da Ayshan wacce tayi mirsisi tace babu inda zata fito , hakan yasa yusrah yin zuciya tadauki jakarta tana fadin"ok toni nayi nan Allah bada zama lfy yahada kanku akularmin da big brother na plxx"
Ganin da gske yusrah tafiya zatai yasa Aysha mikewa cikin sauri byn tagyara lullubin jikinta ,
Aparlor tacin musu tsaye da sudais da alamu sallama sukeda gogan nata , wanda ya hakimce cikin kujera
Kallo daya tai masa tadauke kai yana sanye cikin riga da wando na wani hadaddan material wanda yasha dinki , yayi kyau harya gaji sai dai fuskan nan sam babu walwala
Ahnkl taja kafa ta isa inda yusrah ke tsaye , sunkuyar dakai tayi tana gaida Dr sudais ya amsa yana tsokanar ta ,
Rafar 50k ya aje mata wai nasayan baki kafin suyi mata sallama , tana rikeda hannun yusrah suna hawayen rabuwa da juna , da kyar suka rabu Aysha ta juya zato koma zuwa bedroom dinta
Batare data sake kokarin koda kallon side din daya shureim din yake ba , wanda keta faman danna waya abnsa
Keh! Taji ya ambata hakan yasata cigaba da tafiyanta, tana gab da wuce cikin parlon taji yafurta"keh Aysha bakiranki nakeba "
Cak ta tsaya tana tunanin tajene kota yi tafiyarta , jim kadan tayanke shawaran komawa cikin parlorn
Guri tasamu tazauna batareda datace uffan ba, hakan yasa shima ya cigaba da danna wayansa , sun share tsayin mintuna kafin ya aje wayan yana fadin
"Ke har rashin kunyan taki yakai ana kira kinajin mutane ko, alryt toki sani ni anan gdn bazan dauki raini ba kijina ,
Zaman aure kikazo yi dolene ki aje duk wani jin kai naki da rashin kunya , sannan kishirya yadda zaman zai kasance domin kinfi kowa sanin inada wacce nakeso ke baki gabana,
Inaso kisani a idanun momy da 'yan uwanki kadai zan iya daurewa in nuna musu cewan kedin matata ce , basai nayi miki bayani mai zurfiba nasan kinfahimci abnd nake nufi
Sannan ko yusrah ban yarda tasan sirrin zaman da zamuyi ba , inkuma kika sanr mata wannan damuwanki ne
Sai mgn my one and only dina wato my pretty inaso cikin next month agama mgn komi domin insami cikar burina ,
Ina fata zaki bani hadin kai ki kuma jure zama da mutumin da zuciyansa sam baya kallonki amatsayin mata , kaman yadda kike fadin kema wani banzan ne cikin mind dinki ko "
Yakarishe mgn yana mikewa domin zuwa part dinsa ya watsa ruwa , gaba daya muryan Aneesa kawai yakeson ji kozai sami natsuwa ,
Harya kai bakin kofan ficewa daga parlorn ya juyo yana fadin , "o ki kwashe wadannan kayan nakine idn bakya bukata kuma saikisan abnyi dasu "
Aysha wacce takejin tamkar zuciyanta tafado don takaici , da kyar ta iya mikewa batare data bi takan ledojin dake zube bisa center table din dake parlon ba sai kudin da Dr sudais ya aje tadauke
Tayi bedroom dinta kai tsaye bisa bed tayi masauki , tanajin wani zafi cikin zuciyanta , ko yaushe ya shushun zai daina gasa mata mgn akan wata banza can oho ,
Wannan karon bata yarda tazubar da hawayeba sam , sai dai zuciyanta namata zafi matuka tareda jin kishin Aneesa sosai cikin zuciyanta
Kayan jikinta tacire zuwa na bacci tayi kwanciyanta , byn tayi addua ta shafa tayi light off
Sai dai sam baccin yaki yazo illah tunane -tunane dake addaban zuciyanta , tana jin dayanzu auren soyayya sukai da shureim da yananan yana tarairayanta ,
Amma gashi yanzu ita kadai kwance saima jinyar kalamansa masu zafi da zuciyanta keyi , hakika auren maso wani babu komi cikinsa illah bakin ciki da takaici
Sai dai babu yadda ta iya domin bakin alkalami yariga yabushe , tunda har gata cikin gdn sa amatsayin mata , ranan dai sai bacci barawo yasace Ayshan
Washegary saida ta makara sallan asuba, byn ta idar tagama su azkar dinta da karatun qur'an ne , tasake komawa ta kwanta bata farkaba sai around 11
Hakan yasa cikin sauri ta fada bathroom tayo wanka , byn tagama ne ta dauro alwala ta fito
Saida tagabatar da salatul Dhuha kafin ta nufi gaban mirror domin kintsa kanta
Kwalliya sosai tayi byn tasake shafe dogon gashin kanta da mayuka masu azabar qamshi, sosai take shafe jikinta da turaruka masu sanyin qamshi
Kafin ta nufi qaton sif dinta wanda already yusrah dasu sury sungama shirya mata kayanta ciki , wadanda dukansu sabbi ne fil kama daga English wears zuwa dinkakkun kaya
Hannunta yakai kan wani shegen lace ne mara nauyi , wanda akai masa pitted gown sosai rigan yazauna ajikinta tamkar dama ajikin aka dinka kayan
Tayi kyau harta gaji batayi yunkurin daura dankwalin ba, saita rikoshi ahannu hadeda phone dinta
Yunwa takeji sosan gske tana fitowa babban falon , kallon dazatai center din dining ta hango mutum nata faman kora ruwan tea , ga kulolin anbci nan zube da alamu momy ce ta aiko da breakfast
Hakan yasa Ayshat itama kai tsaye ta nufi wajan cikin takunta na nutsuwa,koda ta isa kujeran dake facing dinsa taja tazauna
Kafin tadubesa tana fadin"ya shushu gud morning"
Bata damu daya amsaba ta dauki plate tafara bude kulas din data gani , abncine har kala 3 chips ne da Pepe soup din kayan ciki, sai waina da miyan taushe wanda yaji naman kaza
Sai flask mai dauke da ruwan zafi da kayan tea difference color, hakan yasata xuba chips din hadida pepe soup din tanaci ahnkl
Sam bata kuma koda kallon inda yakeba cin abncinta take cikeda nutsuwa , shikam shureim kaman yadda bai amsa gaisuwanta ba haka baiko kalli inda takeba
Illah qamshinta dayake shaka wanda yakejin sa harcikin ransa, kasance wansa ma'aboci son qamshine shi
Saida yagama shanye tea dinsa kaf sannan yayi yunkurin tashi , wayansa ne yayi kuka hakan yasashi kara wayan akunni byn ya koma ya zauna
Yake fadin "hello my cwt mom gud morning"
Banji me ake fadi adaya bangarenba illah shushun dake fadin
Yes momy lafiya lau muke gamata kusa dani muna break , wani shagwaba yake xubama momyn wanda yajawo hnkln Ayshat kansa
Tana dubansa bakaramin sha'awa yabataba sai yanzu takaremai kallo, yana sanye cikin farar shirt sai ash din wandon jeans gashinnan ya kwanta luff sosai yaimata kyau bakadanba
Saitaji wani sabon sonsa yanasake mamaye zuciyanta ,
Ganin yana kokarin maido dubansa garetane yasata saurin dauke kanta , tana kurban ruwan shayinta ahnkl
Wayan hannunsa yake mika mata yana fadin "ga mom zaku gaisa abnd yace kenan"
Ahnkl Aysha ta kallesa sukai 4 eyes harara yasauke mata kafin takai hannunta daya sha lalle ta amshi wayan , tana wani smiling takara wayan akunni tabar shureim da kallonta
Gaida momy takeyi cikeda girmamawa , kafin tacigaba da mgn cikin shagwaba tana fadin"bakomi momy saidai kadaici plxz momy kice ma baby tazo muyi hira , kome momyn tasanar da ita tawani sake narke murya tana fadin"kai momy Allah bakomi nidai kawai tazo "
Shureim takaicine da mamakin Ayshan yadda take wanima momyn shagwaba ko kunyan idonsa yacikasa gashi abn haushi momyn saiwani biye mata takeyi
Mikomai wayan tayi byn sungama mgn da momyn , inda suka rabu zuwa anjima momyn zata turo driver da yaran dazasu dinga mata aikace -aikace
Karban wayan sa yayi yana jan tsaki yabar dining din , yayinda Ayshan tabishi da kallo tana kada kanta
Ita takwashe komi zuwa kitchen ta wanke kayan dasuka bata , ta fito zuwa parlor ledojin kajin jiya da tarkacen su fresh milk din takwashe tazuba a frige
Ledan kajin ta kwasa zuwa kitchen oven ta kunna tayi warming kajin , ta juye a tray ta fitodashi mayafi ta dauka tanufi waje
Mai gadi ta hango hakan yasa tai masa alamun yataho da hannu, cikin sauri yataho tareda xubewa yana gaidata
Sam sai Aysha taji wani iri domin dattijone wanda saidai suxo tsara daya da Abban ta, hakan yasata saurin fadin"haba baba aini yakamata indurkusa nagaidaka daga yau kada kasake hakan , ga wannan baba kuci kaida sauran ma'aikatan ko"
Mallam garba yadubi Ayshat cikeda farin ciki yayi godia byn yakarbi karamin tray din hannunta , yacigaba da fadin "Allah yai miki albarka yabaku zaman lfy hajiya "
Har Aysha tajuya mallam garba bai daina yabon kyawun halinnta da saukin kanta ba , ya yaba da tarbiyan data samu da sam bata kasance cikin yaran masu kudin dake wulaknta nakasa dasu ba"
Koda takoma sake saka turarukan wuta tayi a burner , ko wani lungu da sako yadauki qamshi , bedroom dinta takoma ta gyara shima tawadata shi da qamshi mai ratsa zuciya
Asalin main parlour din tadawo ta kunna kallo tanayi byn tayi ale-ale bisa 3 seater, kallonta takeyi hnklnta kwance
Sam bataji fitowansa ba illah ganin mutum datayi akanta , fuskansa ahade yake fadin"hey gal kitashi kije part dina akwai kayana cikin trolley's ki shiryamin su cikin sip
And u make sure kinyi yadda yadace domin bazaman kallo kikazo yiba Right? "
Yana mgn ne cikeda gadara dakuma bada umurni , yana kuma gama fadi yayi gaba abinsa yabar Aysha sake da baki , tana mamakin ya shureim , wato duk wannan abn yanayi ne donta gane bayi kaunarta kome?
Imma hakan ne aransa zata shayar dashi mamaki , imma yanayi donya bata ranta ne zata nunamai hakan baya gabanta ,
Jin tashin motansa da fice wansa yabata kwarin guiwan mikewa , tanufi kofar dazai kaita part din nasa
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu棣冩瀳
*30*
*********
Rufaida da Neesa ne suke hira adakin Aneesan around 11am kenan, zuwan bazata taima Aneesan domin kwana kusan 10 kenan rabonsu da juna
Don haka Rufy tayi kewan Neesa sosai Rufaida ce ke duban Aneesan wacce kesanye cikin riga body hug wanda yakama matuka , sai skat shima yamatseta tareda fitar da suranta muraran
Kafin tayi mgn tana fadin"bakin fama ya kuke ciki da ango ko ince shushunki ne, "
Sosai Aneesa tabata rai tana fadin "hmm kedai bari bakin rai idn zuciyana natuna my luv angon watane ayanxu sam sai inji ko ruwa nakasa sha sbd tsananin kishi ,
Amma idn natuna shushuna nikadai ce aransa sai indanji sanyi, wlh my bakin rai sam shureim bayason yarinyar na kara gasgata hakan ne ajiya
Domin kusan raba dare mukai muna taredashi through phone , kinga mai sabuwar amarya guda inda tana gabansa kema kinsan hakan bazai faruba,
Kuma wani abn dadi sam bayiso idn muna tarema ina masa zancenta , kedai kitayani addua Allah yasa ayi namu auren cikin gaggawa wlh na matsu mukasance da my shushu"
Tunda tafara mgn Rufy ke jefa mata harara afakaice, cikin zuciyanta tayi kwafa tana fadin zaki fadi shushunki yarinya
Afili kuwa wani kafirin dariya tayi tana fadin woo tawan kice dai ke keda zuciyan shureim aji gsky kefa mai sa'a ce sugar na
Takarisa mgn tana daura hannu akan kirjin Aneesan , lokaci guda tasake matsawa suka manne da juna cikin salonta na kwararru aharkan tafara laluban bakin Aneesa
Wacce sam batayi gardaman mika wuya ba domin itadin ma abukace take da Rufaida, kankace miye sunfada wata duniya na faranta ran junansu
Byn sungama sheke ayarsu ne sundawo cikin hayyacinsu , Aneesa tafara yin wanka ta gyara jikinta , yayinda ita Rufy kayan kawai tamaida ,
Sam bata son yin wanka inba taje gd tanutsu bane , kiran Aneesa akeyi a phone dinta hakan yasata daga wayan cikin zumudi domin ko shushunta ne
Yadda takashe murya tareda narketa suna waya cikin musayan kalaman luv , yasake turnuke zuciyan Rufaida duk da bayaune karon farko da Aneesa tasaba amsa wayan shureim agabanta ba
Amma salon ansa wayan tayau tasha banban da wanda tasaba gani , domin yadda takewa shushun ji Rufy take dama ita take ma hakan akan shinfida da tafi kayatar da ita
Tana mamakin wani irin so Aneesa kewa shureim daya cancanci irin kalamn datake narka masa , dolene ya matk akanta yadda bata iya boye masa tsananin kaunar datake mai
Sun dauki lokaci mai tsayi suna wayan kafin Aneesa tayi hanging up byn tayi kissing phone , lumshe idanunta tayi tsawon some seconds kafin tabudesu akan Rufy
Wacce idanunta kekan Aneesan tana mata wani duba mai cikeda zaki gane bakida wayau
Mikewa tayi tana rataya katuwar jakanta byn tadire ma Aneesa katuwar ledan data shigo dashi wanda Aneesa batayi zaton ita aka kawoma wa ba
Har gurin motanta Aneesa taiwa Rufy rakiya byn tayiwa umma sallama , wacce kefadin"kigaida su umman taki Rufaida "
Kayan data kawomata ta kwasa byn tadawo yimata rakiya takaiwa umma domin tagani, dogayen riguna ne 'yan Dubai da mayafansu , sai turaruka da akamu duk cikin irin kayan da rufin kesamu tsaraba daga iyayentane ta debo mata , domin su kullum cikin tafiya suke iyayen rufin
Godia sosai umma kefaman yi tana fadin"o ni idn kika tashi aure ko ya zaku iya rabuwa da Rufaida wannan irin shakuwa da kukai dajuna "
Dariya Aneesa keyi tana fadin "umma kenan nima kullum cikin tunanin hakan nake domin munriga munzama bakin rai bakin fama"
Takarishe mgn tana kwashe kayan xuwa dakinta wayan dasukayi da shureim yasata jinta cikin nishadi da walwala
Sbd ayanzu zuciyanta tagama aminta shureim nata ne ita daya, bakaman da datake gudun yajuya mata baya domin yasami sabuwar amarya ba
***********
*2* *weeks later*
Cikin sati biyun nan babu abnd ke shiga tsakanin Aysha da shureim illah gaisuwa , wanda saiyayi raayine sannan zai amsa gaisuwan tata ma
Akuma wannan week dinne yakoma aiki hakan yasa Ayshat ketashi tun wury tahada break fast , ta shirya komi bisa dining
Duk da cewa akwai sabon kuku da shureim din yakawo 2 days kenan, wanda sam Aysha bata yarda yayi abnci da ita , ita take dafa abncin daxataci hade dana shushun wanda ta gargadi kukun dacewa koda wasa kada yasake shureim yafahimci ita keyin abncin dayake xama yakwashi gara yana yaba iya abncin kukun batare dayasan oganniya Aysha ke sarrafawa ba
Duk atunaninsa breakfast kadai Ayshan ke hadawa yaci
Yauma kaman kullum tagama hada komi bisa dining already tariga tayi wanka , tana Sanye cikin riga da wando na english wears wanda sukai asalin fito da surarta
Duk yadda ta motsa qamshine ke tashi ajikinta kuma yau dinne karon farko data fara fito da wannan salon
Fuskanta sosai yasha light make up, kara kallon dining tayi komi ta aje yadda yadace illah cups nashan shayine kawai tamanta bata kwaso ba
Hakan yasata juyawa xuwa kitchen din domin ta kwaso , daidai kuma da fitowan ya shushun yana Sanye cikin shigan fita office , axababben qamshinsa duk yagama cika falon
Agogon zallan axurfa dake daure a tsintsiyan hannunsa yaduba quarter to 9 cikin sauri yakarisa zuwa dining
Zamansa yayi dai-dai dajin karan takun takalman da Ayshat tasa, wanda tana taka tiles din suna kara shiya kai hnkln shushu dakallon sashen dayake jiyo takun tafiyan
Idanunsa ne suka sauka akan Ayshat wanda saida yaji wani yam ajikinsa, sakamakon bai taba tunanin zata iya shiga irin wanda kejikinta acikin gdn sa
Ya shagala sosai da kallon suranta wanda baitaba tsayawa yakalla ba , ashe dama haka yarinyar keda jiki tamkar ita tayi kanta? ,
Kirjinta dake tsaye cak cike da dukiyan fulani yafi komi tsole idanunsa , yayi nisa cikin kallon suranta takariso gurin dining din
Hakan yasashi wayancewa yana wani jan tsaki yake fadin"oya kiyi sauri kibani cup mana kobaki ganin nakusa yin late ne yakarisa mgn cikin tsawa"
Ayshat datuni tagane borin kunyan taga irin kallon dayake binta dashi yake , yasata sakin smiling tana fadin"sorry ya shushu aigashi na aje bari intaya ka xubawa tunda ka kusakayi late yayanmu "
Furucinta nakarshe yasashi saurin dubanta , suna hada eyes tayi saurin dauke kanta tamkar ba itayi mgn ba , cigaba da hada masa tea din tayi ta tura gabansa
Yayinda shikuma yake cin soyayyen plantain da egg , tana turamasa cup din gabansa ta mike domin bashi guri byn ta gama tabbatar dacewa qamshinta yacika wajen
Tafiyatake tana juya jikinta cikeda gayya kallo daya yabita dashi , yana kwafa cikin zuciyansa yake fadin "hmm lallai yarinyar nan wannan kuma sabon salon na menene"?
Ganin tana kokarin wuce dining area din tashiga parlor yasashi , daga murya yana fadin" keeh! Ayshat zonan "
Hakan yasa Ayshat juyowa tadawo kusa dashi kadan ta tsaya tana duban yadda yawane hade face, danne dariyan dake taho mata tayi tana fadin "gani yaya shureim "
Aje fork din hannunsa yayi yana fadin"look Ayshat wannan wace iriyar shigan rashin mutuncine wannan kika tsirfo dashi , ko anfada miki nan din gdn kafiraine , ko kina tunanin don kin bayyana wannan banzar surar taki shizaija hnkl na xuwa gareki ?
To dagayau banason kisake maimaita kwatan kwacin irin wannan banzar shigan Right?
Yakarishe mgn cikeda tsawa
Ga mamakinsa dariya Ayshat ta kwashe dashi , cikin dariyan take fadin "Allah sarki ya shushu aibansan shigan danai zai bata ranka ba wlh da banyi
Nima yau kadai natashi inajin mararin sakasu domin nadade ban waiwayi shiga irin wannan ba
Kuma atunanina ba haramun bane don qanwa tasanya irin wadannan kayan a gdn yayanta , mussaman nida nake cin tudu 2 agurinka na matsayin qanwa kuma mata agareka
Kuma koda wasa bantabajin baby tace kataba hanata irin wannan shiganba , kasancewan ta ma'abociya ta ammuli dasaka irin wadannan kayan
Ya shushu kadaina mgn wainayi shigannan ne don inja hnkl ka gareni , koka manta matsayin danake dashi baiwuce nakanwa bace zallah,
Kumama mai mace kamar Aneesa data gana sace dukkanin zuciyanka ya shushu, ai banaji wata mace xata iya janyo hnklnk gareta , so ya shureim kayi hakury kada kahanani saka favourite dina alokacin danake bukata tunda ko anture zancen ni matace to amatsayin qanwa nake tamkar baby agurinka "
Takarishe mgn tana tsaresa da manyan idanunta , gaba daya sai shureim yaji tamkar tarufe masa bakine , yakasa furta komi illah kallonta dayakeyi sam yakasa dauke idanunsa akan mazaunanta wanda hips dinta suka fito tamkar zasuyi mgn
Ganin yashagala akan dubanta yasata yin tafi tana fadin "plxx ya shushu kayi hakury kaji"
Wani uban harara yasauke mata yana fadin "leave plxx"
Hakan yasata juyawa da dan gudunta mazaunanta na kadawa, har shureim baisan sanda yarintse idanunsaba
Yazaiyi da wannan yarinyar karta sake masa wannan shigan cikin gdn sa? Saidai tariga takashe bakinsa baida wani hujja imma yace xai matsa karfa yarinyar tafara tunanin ko tarkonta xai kamashine
Mikewa yayi yafice tana mai adawo lfy ko kallonta baiba illah uban tsakin dayaja , yana fita takwashe da dariya ta nufi dining domin yin breakfast ,
Haka kawai takejin nishadi tana kuma tunanin wani irin wanka zata dauka da yamma ,
Waya tazaro tana dailing number din yusrah , domin tunjiya take samata rai zatazo taji shiru
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*31*
Karfe 4pm na yamma yusrah da Aysha ne a kitchen sungama abnci suna kwashewa a food flask , yusrah dake juye pineapple and strawberry milk shake cikin jug, tana saka ice ta dubi Aysha tana fadin
"Matan ya shushu kina bani lbry sai yayi yaya Dakika gama gayamasa mgn? "
Dariya Aysha tayi sosai tana fadin "wlh baby yakasa fadin komi illah dogon tsakin danasha kafin yabarmin gdn
Kumafa sai kallona yake ke zakiyi zaton baitaba ganina bane, hmmm namiji kenan wlh kuma yanzu nasa kafan saka kananun kaya daganan har shegiyan tashigo ,
Cire kunya zanyi inkoyi tsiwan karfi da yaji tunda nafara dago weakness dinsa"
Yusrah sosai take kwasan dariya harda hawaye kafin ta furta, "badai zaman pretending yace zakuyi ba agaban mutane ku nuna ku ma'aurtane amma da zaran kun kadaice akoma 'yar gdn jiya to aike gaba takaiki tawan
Da wannan daman zaki sami ki shege jikinsa kindai gane ai , Aysha takai hannu suka tafa suna kwasan dariya "
Sun shirya komi bisa dining yayinda kukun yake nasu na gd shida ma'aikata , iyatu Aysha ta kwadama kira daya cikin masu aikin da momy takawo mata , domin ta gyara kitchen din
Itakuma kai tsaye bathroom tashige domin yin wanka, byn ta fito daureda alwala sallah tafara gabatarwa kafin
Ta shafa lotion tananan zaune gaban mirrow yusrah ta shigo tana waya, bakin gado tazauna idanunta akan Aysha dake ta faman shafe-shafe tana yaba kyawun jikinta da irin laushin fatarta,
Cikin zuciyata tana takaicin yadda ya shushu ke wulakanta Ayshan , towai koshi baya dubanta da kyaune , ita a iya hangenta bataga aibun Ayshan ba dahar ya shureim zai kasa karbanta yabata gurbi cikin zuciyanta , domin babu abnd ita Aneesan daya matk kanta zata nunawa Ayshan daya wuce farin fata datafi Ayshan dashi
Itadai Ayshat kokarin fesa roll on take a hammata taji muryan yusrah nacewa"matar ya shushu kinga kayan dana fito miki kisaka muga karyan iskancin wani "
Takarishe mgn tana dagama Ayshan wani fingilwan riga , wanda tsayinsa bazai wuce iya guiwaba idn Ayshan tasakashi
Kuma gaba daya transperant ce rigan wanda komi naka zai zama abayyane yake, yana hade dawani shegen skin tight wandone
Rigan red ne sai wandon yazo black colour, Aysha ta tsurawa kayan idanu tana mamakin yusrah , domin ita a iya abnta bazata iya saka kayan ta tinkari inda ya shushu yakeba,
Kafin tagaika mgn har yusy ta kariso tana mika mata kayan take fadin"dallah ni amshi kinwani saki baki kinkasa mgn miye najin kunyan sakawa ashema bason jawo mijinki kikeba "
Kina sanedai watace zai kawo kuma wacce kikasan tasace zuciyansa , don haka yanzu bakida lokacin wata kunya , lokacine dazakiyi anfani dashi ki sami kidasa wani abu azuciyansa kozaki sami gurbi acikin ransa
Allah yabaki duk wani makaman aiki a hannunki sai dai kawai kiyi addu'a Allah yasaka kaunarki cikin zuciyansa Aysha"
Gaba daya Sai Aysha taji yusrah tabata kwarin guiwa , mgn datayi tabbas itace iyakan gsky kuma dole ne ta aje duk wata kunya tayi abnd zai janyo hnkln shureim kanta,
Domin ayanzu shi halalinta ne babu wani kunya atsakaninsu ,zuciyanta shushu takeso shikadaine namijin daya sace zuciyanta , dolene tayi anfani da damanta ta yadda zata cusa sonta aransa
Karban kayan tayi tasaka tundaga sama har kasa take karema kanta kallo, bakaramin kyau tayi cikin kayan ba
Wanda gaba daya ya fallasa asirin suran jikinta , bama kaman saman rigan inda yafito da kirjinta sosai ,
Red janbaki tasa tayi kyau sosai sai tashin qamshi dake fita ajikinta tako ina, yusrah ta dubeta tasake duba kafin ta furta "masha Allah ta ya shushu wlh kingama hadewa yau banbarin gdn nan batare danaga yadda game din zai tashi , takarishe mgn tana kwasan dariya
Falo sukayi masauki byn Aysha ta tabbatar gdn ta yagama zama tsaf sai tashin qamshi kefita akowani kusurwa,
Kallo sukeyi nawani Nigerian film mai kyau , sosai hnkln su yakoma kan kallon dasukeyi sam basuji shigowansa ba
Saida qamshinsa yafara musu sallama tukun , yusrah ce ta mike da gudu ta kankameshi tana fadin " oyoyo ya shushu"
Shima rungumeta yayi yana fadin "oyoyo baby yaushe kikazo "
Murmushi tayi tana fadin "tun dazu nake ya shushu yau nazo taya amaryanmu hirane"
Peck yabata yana fadin "kin kyauta babyn momy"
Aysha wacce idanunta ke kansu ganin yasaki baby , yasata tashi tsaye sai dai tasami kanta cikin jin matsananciyan kunya
Tamkar takoma tazauna sai kuma tayi namaza , ganin yadda yusrah kemata signing
da ido
Shureim wanda
Sai yanzu yadaura ido akanta , baki sake yake karemata kallo tundaga sama har kasa,
Bai gama shiga cikin mamakin Aysha ba yaga tana tinkaroshi , fuskanta dauke da kafirin smiling wanda har dimple dinta saida suka lotsa
Cikin tsananin dauriya da karfin hali ta rungumeshi tana fadin "welcome my ya shushu tareda manne jikinta anashi "
Saura kadan yasaki jakan hannunsa da wayansa , sbd wani irin hanayi daya ziyarcesa abazata , gawani fitinannen qamshi daya doki hancinsa ,sam taki yadda idanunsu yahadu guri guda
Wannan ne karon farko da mace tafara sanya jikinta cikin nasa, hakan yataka rawa gurin jefa zuciyansa cikin wani yanayi wanda bazai fassaruba
Sai yanzu yatuno da plan din yanda zaman nasu zai kasance, hakan yasashi karfin halin saita kansa
Sake rungumeta yayi yana fadin"my wifey ya gdn nabarki cikin kewata ko ? "
Kokaryn yakiceta yakeyi kozai sami natsuwan zuciya amma sai Ayshan tasake shigewa jikinsa tana fadin"kai ya shushu baga baby tazo tayani hiraba amma duk da haka nayi kewanka my king"
Wani miyau ya hadiye dakarfin gske tareda rintse idanunsa , sakamakon yadda ta manne kirjinta da jikinsa, wani irin shock ne ya ziyarci zuciyansu baki daya ,
Hakan yasa Aysha saurin janyewa daga jikinsa , Sai dai amaimakon ta barshi sai kama hannunsa tayi tana fadin"oya muje kai wanka saika fito ga abnci can Peter ya kammala komi bisa dining"
Kallon side din da yusrah take shureim yayi , gani yayi ta tsura musu idanu hakan yasashi sakin smiling yana fadin "alryt my wifey let's go kinga yadda baby ta kafemu da ido "
Yayi mgn cike da karfin hali gaba daya shi yanzu Aysha tafara bashi tsoronema , sosai ya jinjina ma karfin halinta
Yadda suka jera tana rikeda hannunsa xakayi tunanin irin masoyan ma'auratane masu tsananin son junansu
Dai-dai corridor din dazai kaisu part dinsa tasaki hannunsa, tareda sanya idanunta cikin nasa kafin ta furta "ina fata yadda nayi yayi dai-dai da game din dakakeso afara bugashi ya shushu ?
Kaga wannan kadai zai fara cire duk wani kokwanto azuciyar qanwarka , ina fatan banzake dayawaba? "
Shidai shureim gaba daya komawa yayi tamkar wani gunki , kallon ta kawai yake yana mamakin duk wani acting datakeyi , cikeda confedence dinta sam babu ko digon tsoransa dayake hangowa cikin idanunta "
Bata bashi daman mgn ba ta juya tana kada mai jikinta tabarshi da shakan fitinannen qamshinta daya manne ajikinsa,
Tsaye tayi a corridor din dazai sadata da parlor tana sauke ajiyan zuciya, da shureim zai taba kirjinta a tym din shine zai tabbatar komi tayishine cikin matsanancin karfin hali ,
Shiko sam yakasa motsawa sannan suran Ayshan yakasa fita daga eyes dinsa, ganin komi yake daya faru tamkar amafarki ne yakasance , ahnkl yaja kafa zuwa bedroom dinsa inda yayi saurin tubewa yafada bath room , ruwa ya dinga sakarwa kansa Kafin ya iyayin wanka
Itako Aysha tana isa falon yusrah ta taho da gudu ta rungumeta tana fadin"gsky qawata kinbiyani nasiya wannan scene din domin acting din yayi bakarya "
Dariya suka kwashe dashi Kafin yusrah
Ta rufe bakinta tana fadin"hmm bariga in lallaba inyi gd don idn yafito yasaman hararace zansha shi tamkar nina kar zomon "
Har gurin mota Aysha taraka yusrah kafin tadawo tayi shigewanta daki , lock ta dannawa kofar gudun karma shureim din yayi gigin zuwa yasauke mata wulakanci
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo lemu 棣冩瀳
*32*
Byn shushu ya gama kintsawa ne yafito zuwa dining domin cin abnci, cikin zuciyansa yake addua Allah yasa ya tadda Ayshan zaune
Sai dai koda ya fito zuwa parlor TV kawai ya tadda kunne yana aiki, hakan yabashi daman karisawa zuwa dining area din
Abnci ne har kala 3 ya tadda anjera kular farko ya bude mai daukeda jallof din macaroni wanda yaji kayan lanbu,
Sai tuwan semo miyan danyar kubewa, kular karshe Pepe chicken ne wanda ketashin qamshin spices masu matukar dadi
Lemun coconut da lemun zobo ya tadda cikin jug duk ansaka ice aciki, gakuma juice nan duk an aje , sosai yadda aka tsara dining din yau ya birgesa, har yanaji dole yaga peter domin yasake yaba irin kokarin dayake yi , don yana jin dadin girkinsa sosan gske
Tuwan semo din shiya zuba yanaci yana hasko surar Ayshat din cikin shigan daya gigitashi, sam bai taba tunanin yarinyar ta mallaki irin surar dayake so ajikin maceba , musamman abnd yafi birgesa ajikin mace wato breast wanda yake ganin hartafi rabin ran nasa , wadatansu gasu atsaye cak babu alamun rankwafawa,
Samun kansa yayi dason sake dora idanunsa akanta , harya gama cikin abncin bai daina mamakin yadda akayi Ayshat harta iya rungumarsa ba ,
Wani yarr yasake ji ajikinsa Tamkar alokacin abn yake faruwa, bakaramin santin xobo drink din da abncin yayiba, wanda har yakeji dolene yaima peter mgn kullum yadinga hada masa wannan hadin xobon
Koda ya kammala cin abncin waya yazaro ya kira layin peter, yana bashi umurnin yasamesa a main parlor , koda peter yashigo yana zare idanu can ya hango ogan nasa bisa a dining area, hakan yasashi nufan bangaren
Cikin sauri ya zube yana gaida shushun cikin harshen nasara, nan shureim yasake yabamai tareda sanar dashi yacigaba da aiki kaman yadda yakeyi , sannan lemun xobo din yayi mai don haka kullum yana bukatansa matukar zaici abnci a gd
Sosai peter ke ansawa ogan nasa xakayi tsammanin shiyake sarrafa duk abubuwan da ubangidan nasa keyabawa,
Koda shureim yakoma parlor yayi tunanin zai sami Ayshat ta fito , sai dai wayam babu ita hakan yasashi kwanciya tareda canza channel zuwa inda yake bukata yana kallo, jefi -jefi yakan kalli kofan side dinta ko zaiga fitowanta , domin yanason mata kashedi akan irin rungumar datai masa, wanda yajefa shi cikin wani yanayi wanda bazai fassaruba,
Wanda baitabajin hakan ba gefe guda idanunsa na kwadayin sake , ganin kyakykyar suranta domin bakarya shigan datayi yataboshi
Lumshe idanu yayi yana sake hasko yanayin dasuka shiga dazun, hannunsa yarintse wanda Ayshan tarike alokacin datake jansa zuwa part dinsa
Yana tuno irin laushin hannun dayaji wanda alokaci har wani abu kemasa yawo cikin jininsa , tabbas ya amince mace duk yarintarta shu'umah ce 棣冦亙
Ko awashegary sam Ayshat bata yarda sun hadu da shushun ba , tana gama shirya breakfast tayi shigewanta daki ,
Saida ta tabbatar yabar mata gdn sannan tafito tawataya abnta
************
Salman ne da shureim a office din shushun yakai masa ziyara , hira sukeyi sosai kafin salman ya dubi shushu yana fadin
"Waikai ango naga kodan fresh dinnan da ake karawa idn anyi aure kai babu lbry ne"
Nan da nan ya shushun ya hade face yana fadin"to banda abnka ka taba ganin mutum ya angwance da macen da bayaso ? ni haryau bansan dadin auren ba bare har inyi wani fresh din, "
Salman wanda yakafe shushun da ido sam baiji dadin mgn da shureim din yayiba , hakan yasa shima yadaure fuska yana fadin
"Waikai shureim yaushe zaka koyi yima mutum karane ?
Karfa kamance Aysha qanwace agareni , mikake tsammani zanji cikin zuciyata idn kana furta kalman rashin so agareta ,
Haba shushu da anyi mgn kace baka sonta baka ra'ayinta , bakasan naji haushinka alokacin bikin nan ba ko
Duk wasu frnds dinmu saida suka fahimci yadda bakason wannan auren, don girman Allah na rokeka da ka rike Aysha amana shureim, nasan wata tariga ta samin gurbi cikin zuciyanka , amma baidace ko dan darajan amintan dake tsakanin iyayenmu damu kanmu kadinga furta kalman rashin so agareta ba , wannan shirmene wlh guy kakeyi
Kadinga imagining nine akabawa auren yusrah nake wulakantata , ina furta cewa bana ra'ayinta agabanka yazakaji cikin zuciyanka shushu?
Nasani baa ma mutum dole aharkan soyayya but tunda har aure ya shiga tsakani plxx an plxx karka cutar min da qanwa ,
Allah yanuna mana lokacin aurenka da gimbiyar taka Neesa , duk da haryau ni ankimin cikakken bayani gameda ita ,
Salman yakai karshen mgn cikeda zolayan shushun , wanda gaba daya jikinsa yayi sanyi "
Saiyaji kunyan salman yarufeshi tabbas baya kyautawa akan abnd yakema Ayshan, yakuma tabbatar da shi salman din aka aurawa yusrah bazai iya masa wannan cin fuskan akanta ba
Dafa kafadun salman yayi yana fadin"sorry abokina kagafarceni tabbas bana kyautawa , kuma nayi alqawari daga yau koma gaban waye bazan sake furta kalman rashin son Aysha ba ,
Wlh salman laifin xuciyata ce dahar yau takasa aminta da qanwar tamu amatsayin masoyiya , soyayyan Aneesa yarigada yayi zaman durshan cikin mind dina
Amma nayi maka alqawarin rike Ayshat amana kodan infaranta ran momy , yakai karshen mgn yana sakin ma salman din similing"
Salman dinma murmushi yayi yana fadin "kokaifa boss dadai yafi wlh har tausayi Aysha kebani , sbd nasan yadda kake fadi baka sonta har agabanta haka kake fadi, kuma Nasan dole tarika jin dacin hakan cikin zuciyanta
Domin ita macece kasan kuma mata sun tsani namiji yadinga furta musu kalman rashin so karara, don haka kayi ahnkl shureim kada wata rana Allah yajarabeka da kaunarta cikin zuciyanka ,
Aysha she's very innocent tana da hnkl ina fadama wannan badon wai inyabeta don tana qanwata ba, kasan ni kasan halina idn har abu bai minba kowaye nawa bazan boye aibinsa ba, haka duk yadda bansan mutum matukar yanada halin kirki dazan fada tofa bazan boyeba
Da ace tanada wani hali narashin kirki am d first person da zan nuna rashin son aurenku , sbd nasan halin miskilancin ka , so plxx ka riketa da amana karka cire ran wataran zaka iya jin sonta fiyema da yadda kakejin Neesa aranka am telling u wlh
Any way mubar wannan mgn akwai damuwan daya kawoni gurinka mu tattauna , ina cikin matsala shureim"
Shushu wanda gaba daya kalaman salman sun kashe jikinsa, mgn da mom ta taba yimasa take kuma jaddada masa akullum akan Ayshan shine yafado ransa
Fadi yake aransa yazama dole ya koyi boye rashin sonta cikin ransa, yayi kokarin kula da ita kodon momy tunda dai nan gaba kadan zai auro abar sonsa Aneesa, sai dai yana tunanin yadda hakan zai kasance domin sam bayajin ko alamun son Ayshan cikin ransa,
Fuskantan salman shushun yayi yana fadin "matsala kuma tame kenan Allah dai yasa bagurin biye-biyen matanka ne wata taimaka wani abn ba , nifa ina rabaka da neman mata amma haryau kaki ka tuba "
Wani murmushin takaici salman yayi yana fadin.................
Ayshat Dansabo lemu 棣冩啠棣冨編
*LAIFIN BOYE*
*_Haske writers_* *_association_* 棣冩寱
Writing by Ayshat Dansabo 棣冩瀳
*33*
Salman ya kwashe kaf abnd yafaru tundaga haduwansa da Afrah harzuwa abnd yashiga tsakaninsu, da alakan dake tsakaninta da Abban sa bai boyewa shureim komaiba
Yakarishe mgn yana fadin "shushu narasa yaushe Abba yazama tantirin mazinaci , har da aje dadiro wlh nikadai nasan yadda nakejin tsanansa cikin zuciyata,
Idn natuna irin nasihan dayakemin akan illan zina , amma gashi yana aikatawa hakan bakaramin sake jefa zuciyata cikin rudani hakan yake ba
Wlh shushu saina kawo karshen alakan dake tsakanin Abba da Afrah, nikadai nasan yadda nakejin yarinyar araina
Shureim wanda idanunsa kekan salman jikinsa yayi sanyi , tausayin salman yarufeshi tabbas yana cikin fitina , ace mutum yafada son dadiron mahaifinsa
Sai dai sam baiyi mamakin alakan dake tsakanin Alhaji Adam da Afrah ba, sbd yafi kowa sanin waye mahaifan su ,
Hakan yasa shushun dafa kafadun salman yana fadin" frnd kaine bakasan suwaye iyayenmu da LAIFUKAN dasuke aikatawa a BOYE ba , bazan taba ganin laifinka donka furta tsanan Abba dakakeji ba, domin natsinci kaina cikin matsananciyar tsanansu dajin zafinsu
Har zuwa lokacin da suka nunamin nadamansu da tuban su karara ba, Ashe sunrage wani kasone cikin LAIFIN BOYE dasuke aikatawa amma basubar wani kason ba"
Ahnkl shureim ya warware ma salman duk Irin abnd yasan iyayensu nayi a BOYE, har zuwa mummunan ganin dayai musu a guess house din dady
Harkawo kan alakan dake tsakanin dady da maryam ayanxu, wanda yake shirin aurowa momy ita amatsayin abokiyan zama , bayan sungama tanbadewan su dashi
Salman gaba daya jikinsa harwani tsuma yake tabbas iyayensu , basu kyauta musu ba bakuma suyiwa kansu adalci ba , basuyi musu ba suma duk da cewan shima baikasance cikin kamilan mutane ba
Nan suka shiga tattaunawa akan yadda zasu bullowa iyayen nasu , tareda yimusu fatan shiriya cikin saury
Kafin salman yamike yaiwa shushun sallama yafice zuciyansa naraya masa yadda zai datse alakan Afrah da mahaifinsa
Baitaba jin son wata mace har yakejin zai iya aurenta irin Afrah ba, tunda ya dandani zumarta ya gigice don haka tunda har mahaifinsa yarigashi lasan wannan zazzakar zumar ,da yazamamai shamaki akan aurenta
Toya zama dole shima yatsinke masa jin dadi da ni'imar dayake kwasa ajikinta, zuciyansa har wani turiri yakeyi na kishin Abban sa da Afrah yakeji,
*********
Shushu koda yabar offices bai wuce gd ba kai tsaye gdn momy ya wuce , domin yanason su tattauna akan mgn wasu kayan ta da zaizo
Ya dade agn momyn kafin yabaro momy tabashi wata leda mai dauke dakayan mata , masu kyan gske wata aminiyanta tazo dashi daga Ghana, tamikamai tana fadin"gashi kakaiwai daughter na taduba ciki akwai takarda maidauke da bayanin komi "
Shureim ya amshi ledan yafice yana murmushi , zuciyansa nakara mamakin yadda momyke kaunar Aysha din
Ana kiran magrib ya isa gd hakan yasashi wucewa masallaci kai tsaye ,saida aka idar da sallan kafin yashiga cikin gdn rikeda ledan sakon momy