← Book details Imara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 5

Gabatarwa

Imara Part 1 Complete Hausa Novel · about 120 min read

 *IMARA💋💋*


© AMINA I IBRAHIM

*Nanameera*


*SADAUKARWA*
*This book na Dedicated to yhu SALMA AHMAD ISAH, Tabbas ke ta dabance a wajena ina matuƙar jin daɗin kasancewar mu tare, Ubangiji ya saka maki da mafificin Alkhairi ya ɗaukaka min ke my graphics designer😍 yasa kifi haka rabbi ya wadataki da farin ciki mara yankewa 🤲 Really appreciate 🍬 tarh 🥺😍 ur stubborn friend Nanameera 🥰.*


*BOOK 1*

*Page 1*


BISMILLAHI RAHMANIR RAHEEM✍️.


*DOHA (QATAR)*


*Al-Udaid Kingdom*

*7:30 pm*


A nutse yake taka ƙasa, duk inda ya taka sai wajen ya amsa dalilin takalmin dake ƙafafunsa, hannayensa zube cikin aljihun wandon dake jikinsa yanayin yanda yake tafiyar zai tabbatar maka da ba ƙaramin mutum bane domin tafiya yake cikin isa da taƙama. Yanda yake ɗaga ƙafartasa zuwa gaba haka itama take janye tata ƙafar zuwa baya, yayin da mabayyanin tashin hankali ya wanzu akan fuskarta, ɗaga ƙafarta tayi da niyyar yin baya taji ta maƙale jikin bango wanda hakan ke nuni da tazo ƙarshen bathroom ɗin, fararen hannayenta ta sanya ta rufe fuskarta har sannan jikinta rawa yake na tsananin tsoron da take ciki a hankali ya furzar da wani zazzafan numfashi yana zare glasses ɗin dake maƙale kan farar fuskarsa ya zuba mata kyawawan idanunsa yana kallonta frm head to toe wani irin yar-yar haka taji abu na bin jikinta wanda ya samo asali dalilin kallon da yake mata kokari take tasamu zarafin ɗago fuskarta amma ta gagara sai sauke numfashi take da sauri da sauri. Hannunsa ya sanya ya shafi fuskarta dashi da sauri ta janye fuskar daga kallonsa wasu zafafan hawaye suka shiga sintiri akan kuncinta girgiza kansa ya yi cikin wata kamilalliyar murya yake furta


"My Baby girl meyasa kike son wahalar da zuciyar wanda yake sonki da gaskiya?, Meyasa baki sona? kinsan irin yanda nakejin sonki cikin raina kuwa? Haba Imara ya kamata ace kina tausayawa wannan zuciyar ki soni nikuma zan fitar dake daga cikin wannan halin ƙuncin da kike ciki"


Wani raunataccen kuka ne ya kwace mata tana girgiza kanta ta haɗe hannayenta waje ɗaya alamar roƙo tana kallonsa da idanunta wanda suka rine cikin wata iriyar murya mai matuƙar rauni ta shiga furta


"Dan Allah dan Annabi ka rufamin asiri Ameer kaifa tamkar uba haka kake a gareni ko ka manta matsayina ne? Ni ce fa Imara matar ɗanka Maheer dan Allah yallaɓai kadaina furta wannan maganar wlh zan iya mutuwa dan Allah..." Ta ƙarashe maganar tana fashewa da wani sabon kukan, ɗan murmushi Ameer ya yi ya juya yana takawa a hankali har yaje gaban mirror ɗin dake maƙale jikin sink ya ƙurawa fuskarsa idanu babban mutum ne dan aƙalla zai iya kaiwa 60-65yrs da haihuwa kana ganinsa kaga mutum mai tarin kamala da haiba gameda kwarjini above 30s sannan ya juyo ya zuba mata idanu ganin yanda take kuka idanunta a rufe kamar wacce aka ce an yiwa mutuwa kallon shigar jikinta ya shiga yi wata doguwar riga ce Abaya black colour a jikinta kanta babu ɗankwali gashinta duk ya barbare a fuskarta yarinya ce qarama dan bazata shige 18-19yrs ba sai rawar jiki take har sannan tana sake ɗauke fuskarta daga inda takejin alamun yana kallonta. Gabanta ya ƙaraso ya kama hannunta tayi saurin janyewa tana girgiza kanta murmushinsa mai kyau ya yi ya ce"shikenan Imara amma ki sani ni Sheykh Fahad bin saleem al-kuwari bazan taɓa daina sonki ba kuma nayi miki alƙawarin saina mallakeki ta kowace hanya Ma'assalama(Sai anjima)" yana gama faɗin hakan ya fice daga bathroom ɗin, a hankali ta sulale ƙasa kan tiles ta fashe da wani irin matsanancin kuka inna'lil lahi wa ina ilayhi raji'uun shine kawai abinda bakinta ke iya furtawa wace irin masifa ce wannan ke neman shigowa rayuwarta bayan wacce take ciki? Meyasa Ameer ke neman tarwatsa mata ragowar rayuwar data rage mata rashin sanin wanda zai bata amsa ya sanya ta haɗe kanta tsakanin cinyoyinta tana cigaba da kukanta wanda batasan ranar dainawarsa ba.


"Katalina!! Katalina!! Katalina!!..."


Turus ya yi bakin bathroom ɗin yana kallonta ganin yanda ta cure waje ɗaya tana kuka wani tsaki yaja sannan ya ƙarasa cikin zafin nama yana zuwa ya jawo kanta wanda hakan ya sanya ta fashe da wani sabon kukan tana riƙe hannunsa fincikota ya yi yana janta a ƙasa har suka baro bathroom ɗin yana tafe da ita tana kuka ya buɗe wani babban ɗaki ya jefata ciki rufe ɗakin ya yi ya juyo yana kallonta da idanunsa wanda suka rine saboda ɓacin rai sai huci yake ya gaza furta komai Ita kuwa maƙale jikinta tayi tana cigaba da rera kukanta


"Wai ke me kika ɗauki kanki a gidan nan? Gani kike kamar ke wata abar damuwa ce? Ko kuma kina tunanin yanda ake cemiki Gimbiya haka abun yake? To bari kiji ke bakomai bace face Dolly wacce za'a yi amfani dake wajen cimma burin wannan masarautar saboda haka ki wani daina ɗaukan kanki wata ki dinga tunawa dake ƴar matsiyata ce wacce aka ɗauko ki cikin wahala kuma zaki ƙare cikinta!"


"Keeeeee!"


Da sauri ta ɗago kanta tana kallonsa ganin yanda ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan table ɗin dake gefenta yana kallonta sai kuma ya yatsine fuska ya ce"kidaina wannan koke-koken da babu inda zai kaiki ki maida hankali kan abubuwan dana faɗa miki idan har baki maida hankalinki kin koyi komai ba zakisha baƙar wahala cikin Al-Udaid" goge idanunta tayi tana kallonsa sai kuma ta ce"me kuma kakeson nayi? nagaji yallaɓai kawai ka mayar dani gida inda ka ɗaukoni na huta da wannan masifar wacce kuke neman jefani ciki ni bansan komai gameda rayuwarku ba kuma wlh bana fatan na sani dan girman Allah kamayar dani gida dan Allah..." Ta ƙarashe maganar tana kuka taɓe bakinsa ya yi ya miƙe tsaye ya dafa table ɗin gabansa yana mata wani shegen kallo ya ce" ya sunanki?"


"IMARA!"


Ta bashi amsa itama tana kallonsa, da wani irin ƙarfi ya daki table ɗin gabansa nan take ya tsage ya ɗago idanunsa yana kallonta sauke nata idanun tayi ganin yanda ya haɗe fuska kamar hadari cikeda masifa yake faɗin


"Koda wasa idan na sake jin kin ambaci wannan sunan saina yi miki abinda zaki daɗe baki manta ba a rayuwarki KATALINA shine sunan dana zaɓa miki kuma da haka nakeson a kiraki daga rana mai irinta yau ki manta da sunanki IMARA ki sanya a ranki ke KATALINA ce idan ba haka ba..." Ya cije lips ɗinsa wanda suka jiƙe saboda masifar da yake


"Idan ban amsa wannan sunan ba me zakayi?"


Cakk ya tsaya a bakin ƙofar hannayensa zube cikin aljihu amma bai juyo ba tasowa tayi tazo har gabansa tana kallon bayansa ta cigaba da faɗin "Zaka kasheni ne? Koko zaka mayar dani wajen iyayena? Ko kuma sakina zakayi? Ni ba Katalina ba ce kuma bazan amsa sunan da banawa ba koda kuwa a ce hakan na nufin rasa rayuwata ni IMARA shine sunana!".


Murmushi kawai ya yi bai ce mata komai ba kuma ya cigaba da tafiyarsa da idanu Imara ta bishi sai kuma ta dawo gefen royal bed ɗinta ta zauna tana sake rushewa da wani sabon kukan na zallar baƙin cikin irin abubuwan da Maheer yake mata.


Zaune ya samesu suna magana ƙasa-ƙasa yana zuwa ya kara kunnensa a bayansu juyowa sukayi duka ta dungure masa kai


"Ochh! Shamma akwai zafi fa" ya faɗa yana kwaɓe fuska harararsa Shamma tayi ta ce"gulma babu kyau Maheer" "shuu Ummi" ya faɗa yana zama gefenta kansa ya ɗora bisa cinyarta tashiga shafa masa cikeda so da ƙauna take faɗin" ka dinga rufe kanka kaga akwai sanyi" gyaɗa mata kai ya yi yana lumshe idanunsa saboda daɗin shafar kan da yakeji gan haka yasa Ameer wanda tun ɗazu ke binsu da idanu ya ce a nutse


"Ya maganar Companyn Udaid Maheer?" Tashi zaune ya yi yana fuskantar mahaifin nasa cikin girmamawa ya ce"muna iya bakin ƙoƙari Ameer komai yana tafiya yanda ya kamata da yardar Allah" jinjina kai ya yi ya miƙe yana gyara zaman alkyabbar jikinsa ya ce"Allah ya taimaka" Ameen Maheer ya ce shi kuma Ameer ya yi waje yana tafiya cikeda nutsuwa wacce tagama ratsa shi.


A hankali take buɗe idanunta wanda suka yi mata nauyi da mamaki ta ƙarasa buɗesu tana murza idanun ganin inda tayi baccin jiki babu kwari Imara ta tashi kai tsaye kuma wankan daya kawota ta fara tana gamawa ta fito cikin towel tana tsane jikinta jikin mirror ɗin wajen ta tsaya tana kallon fuskarta gaba ɗaya ta sake ramewa kamar ba ita ba fuska ta sakeyi ƴar ƙarama da ita kyakkyawar saƙar dake maƙale a wuyanta ta zubawa idanu


Yammacin Alhamis ne yanayin garin lokacin sanyi ne hakan yasa ko'ina na ɗan ƙaramin ƙauyen ya ɗauki sanyi irin mai shiga jikin nan, a hankali ta kamo hannunta ta riƙe cikin nata bakinta na rawa take furta


"IMARA ki kula da rayuwa ki yarda da duk ƙaddarar data zo miki ba lallai yanzu ki fahimci abinda yake akwai ba amma tabbas watarana zaki gane abinda nake yawan gaya miki idan kinada rabo zaki iya haɗuwa da iyayenki idan kuma ubangiji bai ƙadarta ba to shikenan ke dasu har abada, hannunta ta sanya cikin samirar dake gefenta ta xaro wata kyakkyawar sarƙa sai kyalli take cikin kakkarwar hannu ta danƙa mata cikin nata siririn hannun tana kallonta da idanunta wanda suka fara rufewa ta ce"wannan ita kaɗai ce ragowar abinda yake mallakinki ki kula da ita karki bari tabar wuyanki IMARA domin ita ɗin ƙaddararki ce ki kul..." Tsit ɗan ƙaramin ɗakin ya ɗauki shiru na wasu sakwanni kafin Imara ta mayar da idanunta kan mahaifiyar tata ta kalleta da son sanin abinda ya sanya tayi shiru saidai yanda taga idanunta sun ƙafe ya sanya ta saki wani razanannen ihu


"Ummaaaaaaaa!"


Da sauri ta dafe ƙirjinta tana sake taɓa wuyanta har sannan sarƙar tana nan wasu hawaye Masu kamada na kewa suka shiga zirarowa kan kyakkyawar fuskanta a hankali ta sanya hannayenta ta share hawayen sannan ta ɗauki rigar dake maƙale jikin ƙarfen ta dinga binta da kallo yama za'a yi ta sanya irin wadannan kayan? akanme za'a mayar da ita wata can daban wacce ba ita ba? menene dalilin daya sanyama take kamada Katalinan tasu? Wace ma KATALINAN?, Taɓe bakinta ta yi rashin sanin amsar tambayoyin nata ta ɗaga rigar tana sake juyata kamar zatayi kuka haka ta sanya rigar.


A babban kitchen ɗin masarautar suke tsaye kowa da abinda yake yi ganin sunyi sauri sun kammala abinda za'a ci da daddare, shigowa tayi tana sanye da wata riga t-shirt fara sai wani jeans trouser wanda ya matseta sosai gashin kanta wanda yasha gyara ya zubo har gadon bayanta cikeda ladabi suka sunkuya dukansu suka gaisheta da idanu ta bisu sai kuma ta nufi wajen carbinet ta ɗauko wani glass cup da idanu suka shiga binta sanin halinta kuma yasa babu wanda ya yi yunƙurin karɓar aikin da take


"A'a mene haka nake gani?" Da sauri Joda da ɗago manyan idanunta tana kallon Immi da tashi kitchen ɗin cikin faɗa take kallon maids ɗin tana cewa" mene amfaninku kuna ganinta babu wanda zai yi tunanin karɓar aikin da take ko kun manta matsayinta ne cikin wannan fadar? naga..."


"Hyyyy Immi ni ce ban saka su kinsan banason ƙazanta so ban yarda da tsaftarsu ba kwata-kwata calm down" kallonta Immi tayi sai kuma ta jinjina kai ta ce"nayi zaton wani abun suke son fitowa dashi a cikin fadar nan, na fuskanci ba ƙaunarmu ake a gidan nan ba kawai dan babu yanda aka iya damu ne kuma nan bada jimawa ba fadar zata dawo hannunmu" taɓe baki Joda tayi bata sake cewa komai ba ta juya ta fice daga kitchen ɗin dan ba kasafai ta fiye son hayaniya ba saida Immi ta gama sababinta sannan ta fice daga kitchen ɗin tana tafiya cikeda izza da ƙasaita.


A hankali take tafiya tana jan rigar jikinta a ƙoƙarinta naganin rigar ta saukar mata ƙasa wata irin riga ce wacce ta tsaya iya gwuiwarta fararen ƙafafunta sun bayyana daga saman riga mai irin half shoulder ɗin nan ce hakan yasa har saida tudun breast ɗinta ya fito ta cikin rigar, sosai necklace ɗin wuyanta ta ƙarawa kwalliyar tata kyau tayi kamar wata ƴar tsana gwanin ban sha'awa saidai gaba ɗaya ba daɗin jikinta take jiba dan bata saba irin wannan sheɗancin shigar ba a hankali take taka ƙasa saboda hills ɗin takalman dake ƙafarta wanda suke neman kayar da ita, tunda ta tawo yake zuba mata lulu eyes ɗinsa yana kallonta frm head to toe ganin yanda take tafiya tana wani cure jikinta ya sanya ya taɓe baki cikin takunsa na isa ya ƙaraso gabanta sunkuyar da kanta tayi tana wasada fingers ɗinta hannun nata ya kalla ganinsu zara-zara sai kuma ya mayar da idanunsa fuskarta wacce ta faɗa sosai hannunsa ya sanya ya ɗago fuskarta ɗauke kanta tayi tana kallon gefe ya riko fuskar tata ya yi copping face ɗinsu suna shaƙar ƙamshin juna ya ce"...*


*****Tunda suka fara taka stairs ɗin haɗɗaɗen benen fadar ake binsu da kallo yanayin yanda suke tafiya a hankali kuma cikin nutsuwa ba ƙaramin kyau ya yi musu ba, kowa na parlon akwai abinda yake saƙawa acikin ransa ganin irin kallon da ake musu ya sanya Maheer sake matse hannunta cikin nasa fuskarsa a haɗe babu alamar fara'a suka ƙarasa sakkowa, wata ɓoyayyiyar ajiyar zuciya Dameer ya sauke sai kuma ya ɗauke kansa murmushi Shamma tayi tana kallon Imara ta ce" wow dear kinyi kyau Masha Allah, allahumma bareek" ɗan murmushi Imara ta saki tana kallon Shamma sai kuma ta juyar da kanta wanda kai tsaye ya faɗa cikin idanun Ameer, wata irin bugawa zuciyoyinsu sukayi a tare kowa da kalar nasa tashin hankali a nutse yake bin shigar jikinta da kallo sai kuma yaja idanunsa ya lumshe jin yanda kansa ke barazanar tsagewa bai ce komai ba ya miƙe yana dogara sandarsa da mamaki Shamma ta ce" a'a Ameer ina zaka kuma bayan bakaci abinci ba?" Batareda ya juyo ba ya ce" Alhamdulillah" da idanu kawai mutanen wajen suka bi shi har ya haye saman fadar kai tsaye kuma apartment ɗinsa ya nufa.


Yana shiga ya zare alkyabbar jikinsa ya rage daga shi sai Jallabiya ya shige toilet, a jikin sink ya tsaya yana kallon kyakkyawar fuskarsa a mudubi kafin a hankali kuma wani gudan jini ya fito daga bakinsa hancinsa ya fara zubar da jini yana cikin wannan yanayin na wasu mintuna kafin ya buÉ—e idanunsa wanda suke rine na tsananin azaba famfo ya kunna ya tari ruwa ya wanke bakinsa da fuskarsa gemunsa na É—igar ruwa ya sanya tafin hannunsa ya goge fuskar tasa sannan ya juya ya fita.


Cikin dare tana kwance ya shigo yana sanye cikin wasu pyjamas white colour ya ɗora hula akansa tsayawa ya yi jikin ƙarfen gadon ya zuba mata idanu ganin yanda take baccinta a hankali lumshe idanunsa ya yi ganin yanda tayi masa wani irin kyau kamar ya ɗauketa ya mayar da ita nasa ɗakin ya kwantar da ita gefensa yana shafa kanta haka yaji, wata iskace ta kaɗa wacce ta sanyata juyawa da niyyar sauya ɓari idanunta ya sauka cikin nasa da sauri ta miƙe zaune tana ja baya cikin tashin hankali murya can ƙasa take faɗin


"Nashiga uku Ameer dan Allah dan Annabi ka koma ɗaki kar wani yazo ya ganka wlh nashiga uku, kaifa sirikina ne matsayin mahaifi nake kallonka Ameer dan Allah karka karyamin zuciya kaji tausayina wlh idan Maheer ya gano wannan alaƙar bazai yafe mana ba dagani har kai Ameer ni ƴarka ce wacce zaka yiwa faɗa idan kaga ina shirin aikata ba daidai ba bai kamata ace kaine wanda zaka nemi aikata irin wannan mummunan abun gareni ba" ta ƙarashe maganar tana sakin wani marayan kuka, murmushi ya yi ya tako har inda take ya zauna gefen gadon ya kama hannunta yana murzawa a hankali cikin nutsuwa yake cewa


"Babyn Ameer ya kamata ki tausayawa Ameer É—inki ina cikin matsala zuciyata zafi takemin a duk sanda na ganki da Maheer inajin kamar na kwaceki daga hannunsa ki yarda da Ameer zai baki farin ciki mara yankewa zan zame miki garkuwa zan mayar dake Sarauniyar Udaid kinji Lolona"


Girgiza kanta ta shiga yi cikin tashin hankali take faÉ—in".


*©AMEENA I IBRAHIM*


*Nanameera#*
*Fashion gurl#*
*IMARA💋#*. *IMARA 💋💋*


*© AMEENA I IBRAHIM*

*Nanameera ✍️*


*Page 2*


"A'a Ameer dan Allah ka rufamin asiri wlh zuciyata zata iya tarwatsewa idan har ka cigaba da yimin irin wadannan abubuwa..." Cak maganar tata ta tsaya ganin hawaye na sintiri kan fuskarsa baki buɗe Imara tashiga kallonsa sai kuma tashiga girgiza kanta hawaye na bin kuncinta, Ameer bai sake cewa komai ba ya miƙe tsaye yana riƙe da sandarsa ya fice daga ɗakin hannayenta biyu ta ɗora aka ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi wace irin masifa ce haka?. A hankali ta tashi daga kan gadon tana tafiya kamar wacce kwai ya fashewa a jiki ta fice daga bedroom ɗin nata, tafiya take tana leƙe-leƙe amma babu wanda taci karo dashi har ta ƙaraso wajen swimming pool ɗin haskene a wajen tamkar rana a hankali ta ƙarasa wajen kujerar daya saba zama saidai kuma babu shi babu alamunsa ba ƙaramin mamaki hakan ya bawa Imara ba above 5mins tana tsaye gaban kujerar kafin tabar wajen cikeda zulumi kai tsaye kuma bedroom ɗinsa ta nufa tana zuwa ta tura ƙofar a hankali gabanta na faɗuwa saidai ga mamakinta nanma baya nan da alama ma kwata-kwata bai shigo ɗakin ba, jingina tayi da jikin ƙofar tana tunanin inda Maheer ya tafi da wannan tsohon daren ganin lokaci na shigewa yasa tabar ɗakin ta koma nata kwanciya tayi ta lullaɓa da duvet saidai bacci ya gagari idanunta tana nan kwance har ta jiyo kamilalliyar muryarsa yana kiran sallar farko hakan yasa kawai ta tashi ta shiga toilet dan ɗauro alwala.


*6:45am*

A harabar fadar motarsa tayi parking ya fito yana sanye da wasu English wears ya É—ora p-cap akansa yana tafe ana gaisheshi wani ya amsa wani kuma ya É—aga musu hannu har ya shigo cikin fadar zaune ya sameta tana sanye da wata t-shirt milk colour sai wani mini skirt data sanya irin mai kama jikin nan tana operating system É—in dake gabanta kallo É—aya ya yi mata ya É—auke kai


"Barka Akii"


Sautin muryarta ta daki kunnensa lokacin da yake shirin hayewa sama ɗan juyowa ya yi ya kalleta sai kuma ya saki fuskarsa ya ce" saukar yaushe Joda?" rufe system ɗin tayi ta tashi tana tafiya cikin isa ta ƙaraso gabansa a jikin handle ɗin benen ta ɗora kanta tana kallonsa ta ce" jiya nazo nd kuma ban ganka ba sai yanzu fatan kana lpy" jinjina kansa ya yi ya ce" ina klao y mutanen Turkey ɗin" murmushi tayi wanda ya fito da zallar kyanta ta ce" suna jiran ranar komawarka" samun kansa ya yi da yin dariya ya shafa kansa ya ce" yep lemme take shower zamu yi magana" okay ta ce sannan ya juya yabar wajen, da idanu Joda ta bisa har ya kammala hawa stairs ɗin sannan tabar wajen tana zuwa ta ɗauki system ɗinta zata bar wajen


"Joda!"


Batareda ta juyo ba ta tsaya ya ƙaraso inda take yana murmushi ya ce" ni Meyasa baki kulani" ɗago daradaran idanunta tayi ta watsa masa sai kuma ta ce"kana lpy" bata jira amsar dazai bata ba tabar wajen, kwafa Dameer ya yi ya zauna kan kujera ya yi crossing legs ɗinsa cikeda annashuwa yake faɗin


"Karki damu yarinya soon zanyi gyara komai zan tabbatar da cewa Udaid ta dawo ƙarƙashin ikona!".


Tura ƙofar bedroom ɗin ya yi ya hangota zaune kan stool tana ƙoƙarin gyara gashin kanta taɓe baki ya yi sannan ƙaraso gabanta yana kallon fuskarta ta jikin mirror ɗin gabanta ya ce"idan kin gama akwai kaya a bedroom an ajiye miki kije ki ɗauka su zaki saka" yana faɗin hakan ya juya zai tafi


"Wait!"


Cak ya tsaya ya juyo yana kallonta ya ce"akwai wani abun ne?" Tasowa tayi tana kallonsa ta ce"inada kayan da zan saka anan beside ma kuma ina kaje da daddare banganka ba" wani banzan kallo Maheer ya watsa mata baice komai ba kuma ya yi ficewarsa. Da idanu Imara ta bishi sai kuma takoma ta cigaba da abinda take, fitowa tayi cikin wata doguwar riga milk colour ga gyara gashinta rabi ya sauka gadon bayanta rabi kuma yana ta gefen kafaɗarta a main parlor na fadar tasamu duk family ɗin kowa yana harkar gabansa cikin sanyin jiki ta ƙaraso tana zuwa ta tsuguna gaban Shamma

"Barka da safiya"

Shafa kanta Shamma tayi tana murmushi ta ce"how was ur night?" kanta a ƙasa tana wasada fingers ɗinta ta ce"Alhamdulillah" jinjina kai Shamma tayi sannan ta ɗaga idanunta tana kallonsa sanye yake da wasu suit black colour gashin kansa ya sha gyara ya yi wani irin sihirtaccen kyau da hannu tayi masa alama da yazo ya ƙaraso yana zuwa ya zauna gefenta ya ɗora kansa gefen kafaɗarta tana sauke ajiyar zuciya shafa kansa tayi cikin taushin murya ta ce" Maheer what's wrong with you?" shiru ya yi bai ce komai ba sai ajiyar zuciya da yake saukewa a jere a jere, fitowa ya yi cikin hanzari yana gyara maɓallin hannunsa murmushi Immi tayi ta ce"magaji ka fito?" gyaɗa mata kai ya yi ya ce"Eh Immi zani Company ne, Sabahul khair Shamma" ya faɗa yana kallonta jinjina masa kai tayi fuskarta ɗauke da murmushi kamar koda yaushe ta ce"ka tashi lpy Dameer?" "Alhamdulillah" ya bata amsa yana ƙoƙarin fita daga fadar, da idanu Immi ta bishi sai kuma ta tashi tabi bayansa.


*** Tsaye yake gaban motarsa hannayensa naɗe cikin aljihu ya zuba mata ido yana kallonta, "baka jina ne Dameer?" ɗan mirmushin gefen baki yayi sai kuma ya ce"nafaɗa miki ki bar komai a hannuna Immi zan kula da komai amma sai kina neman dagulan lissafi" ɗan juyawa tayi tana kallon ma'aikatan da suke ta kai komo a compound ɗin sai kuma ta jawo gefen rigarsa tana kallonsa cikin ido ta ce"kai baka gane abinda nake nuna maka idan har bamuyi komai a yanzu ba zamu faɗa cikin danasani Udaid zata kwace daga hannunmu" hannunsa ya sanya ya hargitsa gashin kansa wanda yake a gyara sai kuma ya furzar da wani zazzafan numfashi ya ce"shikenan naji na kuma san abinda zanyi da fari dole mu janye wannan yarinyar dan ita ce babbar matsalarmu a halin yanzu" "nasani kuma ina goyan bayanka duk abinda zaka aikata dan ganin ka kwaci abinda yake mallakinka" jinjina mata kai ya yi sannan ya juya ya shige mota yayi mata key not too long ya bar fadar. Tunda ta shiga kitchen ɗin take kai komo tama rasa abinda zatayi jingina tayi da jikin carbinet tana sanya ɗan yatsanta ɗaya a baki tana tsotsa kamar yanda tasaba, shigowa yayi yana kallonta bai ce mata komai ba ya kama hannunta suka bar kitchen ɗin ɗan taɓe baki Joda tayi tana gyara zaman Bluetooth ɗin dake kunneta a hankali ta ajiye cup ɗin hannunta ta fita, kai tsaye ɗakinta tashiga tana zuwa ta zauna gefen royal bed ɗinta ta jawo wayarta ta shiga danna wasu nambobi tana jin wayar ta fara ringing ta tashi ta shige toilet ta rufe ƙofar


"Akwai buƙatar ka dawo Al-Udaid Damisa abubuwa na gab da lalacewa a tanan Al-Udaid na buƙatar magaji!" Joda ta faɗa cikin tsantsar nutsuwa da kwantar da murya shiru taji yayi kuma daman tanada tabbacin bazai magana ba tana ji ya katse kiran. Jingina tayi da jikin bango tana sauke ajiyar zuciya.


*** Kallonsa take da manyan idanunta wanda sukayi jajur dasu sun kumbura ganin yanda ta zuba masa idanu ya sanya ya matso kusada ita hannunsa ya sanya ya dungure mata kai tayi saurin dafe kanta hawaye na biyo kuncinta hannunsa ya sanya ya kama haɓarta yana kallon fuskarta ya ce"idan ina miki magana kina kafeni da idanu ranki zai dinga ɓaci" turo baki tayi tana ƙoƙarin kwace fuskarta ta ce" daman akwai watarana wacce raina yake ba a ɓace ba a gidan nan?" Baki buɗe Maheer ke kallonta sai kuma ya yi kwafa ya janyo rigar dake maƙale jikin hanger ya wulla mata ya ce"yanzu ba sai anjima ba ki sanyata ki fito karki bari nadawo kiranki"


"Amma..." Maganar ta tsaya cak ganin ya rufo mata ƙofar bathroom ɗin wasu zazzafan hawaye suka fara sintiri kan fuskarta a hankali ta sulale a ƙasa gefen sink ta haɗe gwuiwarta tana rushewa da wani kuka mai cin rai kwata-kwata lamarin Maheer ya fara ɗaga mata hankali nema yake ya tarwatsa zuciyarta kullum tunaninta ɗaya wacece KATALINA? Meyasa Maheer ya zaɓi ya mayar da ita KATALINA?!.


Tana fitowa ta ganshi tsaye hannayensa zube cikin aljihu da alama waya yake hakan yasa taja ta tsaya a wajen saida ya kammala sannan ya kalleta ya ɗan taɓe baki ya ce" ki saki jikinki ki daina wannan abun da kike ki sani ke yanzu matsayin Gimbiyar Udaid kike dole ki koyi komai kuma ki ganeshi kamar yanda nafaɗa miki zan mayar dake Katalina to bazan sare ba har sai naga kin zama kamar tan saboda haka ki shirya!" Da idanu kawai Imara ke binsa sai kuma ta buɗe bakinta wanda takejin ya yi mata nauyi ta ce"dan Allah zan iya tambayarka abu guda ɗaya?" yana kallon wani wajen daban ya ce"tambayi" "Meyasa ka aureni? Kuma wacece KATALINA?" Kallonta ya yi sai kuma ya yi murmushi ya ce" idan lokacin ki sani ya yi xaki sani" kafin tayi magana taga ya juya ya bar wajen hakan yasa ta bisa da kallo sai kuma ta juya da niyyar tafiya.


"So kike kisan wacece KATALINA?"

Cak! Imara ta tsaya tana tunanin muryar dan bata taɓa jin mai irinta cikin fadar ba cikin takunta na isa ta ƙaraso gabanta tana sanye da riga da wando as usual ta raba gashinta gida biyu rabi ya zuba bayanta rabi kuma gefen kafaɗarta da idanu Imara ta bita kallo irin na mamaki kyakkyawace irin ajin farko ɗin nan tanada manyan idanu masu ɗaukan hankali, cikin sanyin murya Imara ta ce"Eh inaso nasani inason sanin dalilin daya sanya Maheer ya aureni meyasa kuma yakeson mayar dani wata daban kuma..."


"Hyyyy what's wrong with you?, Kina ta magana baki gajiya I'm just asked u a single question amma kina neman fasamin kai da hayaniya kinsan matsayinki a gidan nan kuwa? kinsan me zama matar Maheer yake nufi? Stupid!" Da idanu Imara tashiga bin Joda har ta ɓacewa ganinta

"Ko wace ita take yiwa mutane masifa ohho!" Imara ta faÉ—a tana yin gaba abinta.


*** Tunda ya shiga yake zagaye office É—in yana girgiza kai tamkar wani mahaukaci kallonsa Ahlan ya yi sai kuma ya ce" wannan fa duk ba mafita bace Dameer idan har kanason ganin ka kwaci Udaid dolene ka saita zuciyarka ka rage fushinka" kallonsa Dameer ya yi da idanunsa wanda suka sauya launi sai ya ce"me zanyi Ahlan? Akanme za'a dinga bawa Maheer abu ni ana banza dani? Maheer ya yimin abubuwa dayawa yasha hanani samun abu shiyasa this time around billah sai naga bayansa yanda ko babu ran Ameer ni ne Magaji!" Dafashi Ahlan ya yi ya ce"kayi komai abokina ka tsaya tsayin daka ka kwatarwa kanka yanci kaima É—an Ameer ne saboda haka kanada kowace dama tazama shugaban Udaid".


Shamma na zaune kan ɗaya daga cikin kujerun dake zagaye da fadar ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya wanda ke nuni da irin tata isar fitowa Immi tayi tana kallonta kamar zata shige sai kuma ta ce"Barka da hutawa Shamma" jingina mata kai tayi ta ce" ykk?" Yanda ta bata amsa ba ƙaramin ƙona mata rai ya yi ba amma kawai ta dake ta juya ta fice daga fadar taɓe baki Shamma tayi tana cigaba da kallonta, da gudu Joda ta fito tana zuwa ta zauna gefen Ameer tana dariya ta ce"Ameer dan Allah kalli kaga" karɓar system ɗin tata ya yi sai kuma ya kalleta ya yi murmushi ya ce"yanzu kinyi farin ciki?" gyaɗa masa kai tayi tana murmushinta mai kyau dafa kanta ya yi ya ce"Allah ya sanya albarka" "Ameen ya rabbi Shukran Ameer" jan kumatunta ya yi ya ce"haza wajib" tashi tayi ta shige ciki da idanu Shamma ta bita sai kuma ta girgiza kai shi kansa Ameer bai ji daɗi yanda ta rasheta ba amma ya ya zai yi haka ƙaddara ta zaɓar musu.


Zaune take gefen swimming pool ɗin ta zubawa ruwan idanu yanayin yana tuna mata da wasu shekaru da suka shuɗe cikin rayuwarta lokuta wanda bazata manta dasu ba duk da batada wayo amma hakan bai hanata kasa tuna wani abu daga ciki ba duk da bata ganin fuskarsa amma tana jin bugun zuciyarta na sauyawa a duk Lokacin da taga surarsa. Tsugune take bakin Kogin tana ƙoƙarin ɗiban ruwa tanajin sanda yazo ya tsaya a bayanta hakan yasa ta miƙe tana kallon fuskarsa da take a rufe ta ce" yauma ka sake zuwa ko?, wai ya sunanka?" da idanu kawai taga yana binta hakan yasa ta tura baki gaba tana harararsa ta ce"wannan kaman kurma baya magana, kai kana jina? Yayane sunanka?" Shiru nan ma taji ya yi mata ta galla masa harara ta ɗora tulunta aka tashige ta gefensa saida tayi nisa sannan ta tsaya ita kaɗai take cewa" to kodai nayi masa turanci inaga baya jin Hausa" da wannan tunanin ta koma inda yake tsaye har sannan tana kallonsa ta ce" kai what's ur name? Kanajin turanci? Ni sunana Imara gurin granny na nazo wannan ƙauyen kai ya sunanka? ko kai bature ne? nima mama ta ce inada kyau kai kaga kyan?" Ganin har sannan bai ce mata komai ba kuma bai buɗe fuskarsa ba ya sanya ta haɗe rai tana ƙoƙarin fashewa da kuka ta sanya hannunta a baki cikeda shagwaɓa take cewa"sai kai ta tsaiwa nonse kawai ni babu ruwana ma dakai aljani kawai".


"Keeee!"

A ɗan firgice ta ɗago idanunta sai kuma ta sunkuyar da kanta "what are you thinking?" Girgiza masa kai tayi tana ƙoƙarin tashi tsaye cikin rawar murya ta ce"bab.bb.bakomai" taɓe baki ya yi ya ce"koma mene bai dameni ba kije Ameer na kiranki" dafe ƙirjinta tayi tana gwalalo ido ta ce" Ameer kuma ni?" Da mamaki yake kallonta ya ce"akwai matsala ne? ya ce kin masa laifi to kije yanzu ba sai anjima ba ki kuma shirya gobe zaki fara zuwa school karki manta da sunanki KATALINA!" Cikeda tsiwa ta ce" nifa wlh sunana IMARA!" haɓarta ya kama yana mata wani banzan kallo ya ce" ba roƙonki nake ba idan har kinajin zaki iya to gobe idan kin fita daga Udaid kice sunanki IMARA a sannan zaki gane kuskurenki sannan zan nuna miki wane Maheer!" yana gama faɗin hakan ya juya ya bar wajen yana wuci. Dafe kanta tayi tana sakin kuka ta ce"nashiga ukuna Allah ka taimakeni bazan iya ba" tafaɗa tana fashewa da wani sabon kukan.


*** Around 10pm tana tsaye jikin mirror tana gyara kanta ya turo kofar ya shigo batasan sanda ta saki comb ɗin hannunta ba tana girgiza kanta a hankali yake tafe cikin nutsuwa ya ƙaraso gabanta ja da baya tafara bakinta na rawa ta kasa magana

"Lolo narh"


Ameer ya furta cikin wani iriyar murya mai rauni gaba ɗaya ya rame kamar bashi ba manya-manyan idanunsa sun janye kaɗan kuma sun sauya launi daga farare zuwa ja damuwa tagama bayyana akan fuskarsa, tsayawa yayi ya zuba mata idanu yana kallonta ƙasa tayi da nata idanun wanda hawaye ya gama cikashi cikin sanyin murya take cewa" dan darajar Annabi Ameer kayi haƙuri kabar wannan tunanin a cikin ranka wlh nasan shaiɗan ne kayi yaƙi dashi kamar yanda kake faɗa a masallaci ka taimaki rayuwata kada ka jefani halin da bazan iya ba ka taimaka Ameer" tafaɗa tana haɗe hannayenta waje ɗaya alamar roƙo, numfasawa ya yi cikin taushin murya yake cewa"Lolo nafi kowa son na ganki cikin farin ciki nafi kowa damuwa dake a cikin fadar nan wlh nafi kowa sonki nine na dace dake ba Maheer ba ki taimaka ki fahimci Ameer ɗinki zan shiga wani hali idan har kika cigaba da watsar da buƙatata koda yaushe zuciyata zafi takemin inaji kamar zan mutu dan Allah Lolo ki taimaki Ameer" girgiza kanta tayi tana ƙunshe bakinta gudun kada kukanta ya fito ta ce" inna'lil lahi wa ina ilayhi raji'uun Auzubillahi minna shaiɗanin rajeem astgfirullah ya Allah dan Allah Ameer kadaina faɗar wannan maganar wlh zuciyata zata buga nashiga uku ni IMARA!" Shiru Ameer ya yi ya zuba mata ido yana kallon yanda take kuka kamar ranta zai fita above 5mins sannan ya yi murmushi yana kallonta ya ce"kina iya kirana da duk sunan da kikaso Lolo naji nine shaiɗani amma inason ki sani bazan taɓa iya daina sonki ba IMARA koda kuwa a ce soyayyarki zatayi ajalina Ni Fahad ke nakeso kuma zan cigaba da sonki har zuwa ƙarshen numfashina a duniya nasan koda bana raye watarana zaki so ni" banda kuka babu abinda IMARA keyi gaba ɗaya ta birkita kanta tashi ya yi yana dogara sandarsa ya yi waje daidai nan Maheer ya shigo ɗakin da sauri ta juya masa baya ta goge hawayen fuskarta sannan ta juyo tana cigaba da taje kanta


"Lafiyarki?"

Girgiza masa kai tayi tana ƙoƙarin ɓoye hawayen dake shirin sauka kan fuskarta ɗaga kafaɗarsa ya yi irin i don't care ɗin nan ya ce" anyway ga kayana an kawo maki ki tabbata gobe kin shirya kamar yanda na nuna miki kafin ki fito" yana gama faɗin hakan ya bar ɗakin da idanu Imara ta bishi zuciyarta na mata suya wane irin miji ne Maheer????.


Tana gama gyara kanta ta ɗauki wata sleeping dress ma ɗan kauri ta sanya a jikinta ta haɗe gashinta waje guda ta ɗaure gudun kar ya dameta ta shafa turare sannan ta ɗauki wata hula ta rufe gashin kanta, agogon gefenta ta kalla taga kusan 11pm hakan yasa kawai ta fice daga ɗakin kai tsaye kuma apartment ɗin Maheer ta nufa tana zuwa without knocking ta tura ƙofar ɗakin turus tayi tana kallonsu ganin yanda take zaune ta ɗora kanta akan cinyarsa tana masa hira sai dariya yake yana ganinta ya haɗe rai Joda ta miƙe tsaye tana kallonta sai kuma ta taɓe baki ta kalleshi ta ce"saida safe Akii" miƙewa tsaye ya yi shima ya sumbaci goshinta ya ce"laylatan sa'eedan" murmushi tayi sannan ta ratsa ta gefen Imara ta fita, Maheer bai sake kallon inda take ba ya shige toilet jiki a sanyaye ta ƙarasa gefen gadon ta zauna lokaci ɗaya hawaye ya kawo kan fuskarta. Kusan 30mins kafin ya fito sanye da bathrobe sai ɗan ƙaramin towel yana goge gashin kansa tana kallonsa har ya kammala duk abinda yake ya shirya cikin pyjamas maroon colour wanda sukayi masa kyau cikin takunsa na isa ya ƙaraso gefen gadon ya zauna yana kallonta ya ce" keeee!" ɗago idanunta tayi ta kalleshi sai kuma ta sunkuyar da kanta tana wasada fingers ɗinta. "Me kike anan?" Cikin sanyin jiki ta ce" ni tsoro nakeji bazan iya kwana ni kaɗai ba anan zan kwana" a fusace ya juyo yana kallonta ya ce".


*Nanameera#*
*Fashion gurl 🥰#*
*IMARA 💋#*
*LOLO#*
*Writer ✍️#**Chapter 3:*


"Get out!" Abinda kawai ya furta kenan yana kafeta da manyan idanunsa ɗan turo baki tayi sai kuma ta ce"ni bazan iya kwana ni kaɗai ba wlh saidai na kwanta a nan a ƙasa" buɗe idanunsa ya yi a kanta yana yi mata wani mugun kallo cikin kakkausar murya ya ce"idan nayi kamada abokin wasanki to ki cigaba da zama anan" da haka ya juya mata baya yana rufe gaba ɗaya jikinsa da duvet, bayansa Imara tabi da kallo hawaye na zubowa kan fuskarta me Maheer yake nufi da ita?, Wane irin mutum ne shi?.


***A nutse ya turo kofar ɗakin yana sanye cikin wasu suit black colour as usual idanunsa maƙale da glasses, lumshe idanunsa ya yi saboda ƙamshin turaren daya daki hancinsa kusan 2mins kafin ya buɗe idanunsa akanta sanye take cikin wata Abaya black colour ta yi rolling veil ɗin abayar a fuskarta ƴar ƙaramar round face ɗinta ta fito sosai gwanin sha'awa ɗauke idanunta tayi daga kallonsa fuskanta a haɗe babu walwala bai ce mata komai ba ya kamo hannunta ya matse cikin nasa ya tallafi fuskarta akan tafin hannunsa yana bin ta da kallo hannunsa ya sanya ya gyara mata gashinta wanda yake kwance gefen fuskarta ta yi saurin lumshe idanunta tana ƙamƙame jikinta waje guda batayi aune ba taji dungure mata kai tayi baya zata fadi ya sanya ƙafa ya tareta yana yi mata wani irin kallo ya ce"ke har abada bazaki ji magana ba ko?" Ɗago idanunta wanda suka sauya kala tayi tana kallonsa da rashin fahimta ta ce"me kuma nayi maka?" Ta faɗa tana dafe goshinta, harararta ya yi bai sake ce mata komai ba ya juya ya bar ɗakin. A dinning area ya samesu duka kowa na cin abincinsa cikeda nutsuwa wajen Shamma ya ƙarasa ya rungumeta yana murmushi ya ce" Barka da safiya Shamma" murmushi ta yi ta ce" ka tashi lpy?" "Alhamdulillah" ya ƙarasa wajen Ameer sunkuyawa ya yi a gabansa ya ɗora kansa bisa cinyarsa yana sakin wata ajiyar zuciya wani yalwataccen murmushi Ameer ya yi yana shafa sumar wacce tasha gyara ya ce"Ka tashi lpy?" ɗago kansa ya yi yana murmushi ya ce"Alhamdulillah Ameer" jinjina kai Ameer ya yi yana zamesa daga jikinsa ya mike tsaye dai-dai lokacin da ta shigo dinning area ɗin kallo ɗaya Ameer ya yi mata ya ɗauke kansa yabar parlon zuciyarsa na ayyana masa abubuwa dayawa da idanu kawai Imara ta bisa sai kuma ta sunkuyar da kanta ta ƙaraso wajensu Shamma ta gaishesu kamar yanda ta saba. Kujerar gefensa ta zauna sai juya abincin gabanta take ta gagara kai shi bakinta kallonta Shamma ta yi ta ce" ki ci abinci mana daughter ko bakison school ɗin?" ɗan murmushi ta yi tana girgiza kanta ta kai abincin bakinta,


"Maybe bata saba irin wannan rayuwar ba shiyasa ta fito daga ƙabilar matsiyata dole ta dinga kasa cin abinci"


Cak! Imara ta tsaya da tauna abincin da takeyi ta zubawa Immi idanu wanda suka gama sauya kala ba ita kaɗai ba kowa ma na wajen kallon Immi yake, ajiye spoon ɗin hannunsa ya yi ya miƙe tsaye bai kalli kowa ba ya kama hannunta suka bar wajen da idanu Joda ta bisu sai kuma ta taɓe baki.


*Education City, Doha, Qatar*
_DOHA INSTITUTE OF GRADUATE STUDIES (DI)_


Fitowa ya yi daga office ɗin yana kallonta ya ce"idan har kika aikata wani abu wanda za'a gane ke ba Katalina ba ce wlh sai na saki dana sani" kallonsa kawai tayi sai kuma ta taɓe baki tana kallon wani wajen bai sake ce mata komai ba ya fice daga wajen ita kuma tabi wanda zai nuna mata class ɗin nasu. Babban class mai matukar kyau da ɗaukan hankali komai na amfanin student an tanada a cikinsa a hankali take wara idanunta tana kallon tsirarun mutanen dake cikinsa wanda basu fi 20 ba suna ganinta suka tashi suna ihu sai murna suke


"Welcome back friend kin dawo?" juyawa Imara tayi tana kallon wacce take mata magana ganin yanda take dariya yasa ta yi murmushi itama wanda yake iya laɓɓanta ta gyaɗa mata kai dukda bata gane inda ta dosa ba hannunta taji an kama ta juya tana kallonta bata ce komai ta zaunar da ita gefenta tana kallonta ta ce"munyi kewarki sosai Katalina yanzu kin ji sauƙi?" da idanu kawai Imara ke bin ta tama rasa abin da zata ce gaba ɗaya ƙwaƙwalwarta ta gaza gane abin da suke nufi shin wa ce Katalina? Meyasa suke zaton ita Katalina ce? kuma ina Katalinan?, Jijjigatan da akayi ya sanya ta ɗago manyan idanunta tana kallonta ta ce"Eh I'm fine" murmushi tayi ta ce"Allah ya ƙara lafiya Ina Maheer?" " Ya tafi" Imara ta ce da sauri tana sunkuyar da kanta, da gudu ta ƙaraso zata ta ɓata tayi saurin riketa ganin yanda ta ɗora kanta kan desk idanunta a rufe ta ce"bari Nora inaga bata jin daɗi na ganta wani iri" kwaɓe fuska ta yi ta ce"Rania na ƙagu nayi magana da Katalina wlh nayi kewarta ki barni ko sau ɗaya ne nayi mata magana" girgiza kai Rania tayi tana gyara gashinta da ya rufe mata fuska ta ce" ki bari sai anjima please" numfasawa tayi ta ce"shikenan Allah ya kaimu" "Ameen".


*** Tunda ta shigo gidan take zaune a fadar tayi shiru tunani ne kala-kala cikin zuciyarta jira take Maheer ya dawo ta tambayeshi amma har yanzu shiru bai shigo fadar ba, fitowa tayi tana sanya da wata riga iya gwuiwa ta gyara gashin kanta sai sheƙi yake hannunta riƙe da wayarta tana dannawa hankali kwance tana zuwa ta nemi waje ta zauna a kujera ta ɗora ƙafarta saman kujerar tana cigaba da danna wayarta da kallo Imara ta bita sai kuma tayi tunanin ta tambayeta tunda taji rannan ta fara maganar da wannan tunanin ta daga ta kalleta sai kuma ta ce"daman kince za ki faɗamin wace Katalina to ki faɗamin yanzu" tayi maganar tana langwaɓar da kanta gefe ɗaya, tamkar tana magana da kujerar gabanta haka Joda tayi mata bazaka taɓa cewa da ita take maganar ba ganin tayi mata banza ya sanya Imara ta harareta tana ala wadan hali irin nata. Tana ƙoƙarin tashi ya shigo hannunsa riƙe da wata kwalba ƴar ƙarama sai tangaɗi yake a matuƙar tsorace Imara ke kallonsa ganin yanda ya yo kanta tashi Joda tayi tana kallonsa sai kuma ta girgiza kanta da gudu Imara ta nufi stairs ganin yanda yake ƙoƙarin cimmata da sauri shima ya hau saman duk inda tayi yana bin ta, karo tayi da Ameer da yake ƙoƙarin shiga nasa apartment ɗin yana dogara sandarsa cikeda nutsuwa bayansa tashige tana kuka cikin tashin hankali take faɗin


"Dan Allah Ameer ka taimaka mini wayyo Ummana zai kasheni dan Allah Ameer!" Cikin wata murya irinta bugaggu Dameer ya ce" babu wanda ya isa ya hanani gamawa dake a wannan daren dole sai kin mutu ni ne zanyi ajalinki..." Ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin yin inda take. Ƙara ta saki tana riƙe alkyabbar jikin Ameer ba tareda tasan tayi hakan ba, wata irin ajiyar zuciya Ameer ya sauke jin yanda jikinta ya haɗu da nasa ya runtse idanunsa yana jin wani abu na taso masa tun daga ƙafafunsa, baisan sanda Dameer ya fincikota daga jikinsa ba ya haɗata da jikin bango ya shaƙe mata wuya tuni idanun Imara suka firfito waje sai miƙa hannunta take hawaye na zuba daga idanun da gudu Joda tazo ta dinga dukansa amma hakan bai sa ya saketa ba saima sake shaƙeta da yayi yana wani irin cije leɓe ihun da Joda keyi ne ya sanya mutanen fadar suka jiyo da gudu kuma suka ƙaraso wajen ana masa magana amma kamar ma ba dashi ake ba.


Hannu ɗaya ya sanya ya fincikeshi daga jikinta ta faɗi ƙasa nan sumammiya ya juyo da fuskarsa ya wanke shi da mari har biyu bai gama buɗe idanun ba ya sake masa wani ya shaƙe masa wuya yana kallonsa da idanunsa wanda sukayi jajur dasu ganin yana ƙaƙarin mutuwa ya sanya Immi ta ƙaraso gabansu tana kallonsa cikin kwantar da murya ta ce"yi haƙuri magaji ka rabu dashi kaga ƙaninka ne sake shi" tamkar tana magana da dutse haka Maheer ya yi mata madadin ya sake shi sai ma sake shaƙesa da ya yi above 5mins kafin Ameer ya ƙaraso gabansa ya kama hannunsa bai ce masa komai ba suka bar wajen.


***A hankali ta shiga buɗe idanunta wanda suka yi mata nauyi kallon inda take a kwance tayi sai kuma ta miƙe zaune tana shafa wuyanta saboda wani raɗaɗi da taji yana yi mata ɗan turo bakinta tayi tana tuno yanda ya shaƙe mata wuya kwaɓe fuska ta yi ta ce"mugu kawai" ta faɗa tana tura baki gaba, shigowa ya yi hannayensa zube a aljihun trouser ɗin jikinsa ya tsaya a kanta yana kallonta kwaɓe fuska ta yi ta "kaga abinda ya yimin ko?" jin ya yi shiru yasa ta sake cewa "kuma da zafi sosai kamar zan mutu wayyo Allahna..." sakar baki Maheer ya yi yana kallonta ganin yanda take abu kamar ƙaramar yarinya girgiza kansa ya yi bai ce komai ba ya juya zai fita. Da sauri ta miƙe tsaye tana kallonsa ta ce

"Yawwa daman ina ta jiranka xan tambayeka" tsayawa ya yi ba tareda ya juyo ba tana wasada fingers É—inta ta ce"daman yau a school ne aka dinga cemin Katalina kuma wai ya jikina? Daman ita Katalina kamar mu É—aya? kuma itama fara ce? Tana ina yanzu? Wai batada lafiya nag..."


"Hyyyyy yimin shiru aku kawai kin fiye surutu karki sake tambayata wani abu kawai duk wanda ya ce miki Katalina ki amsa sannan koda wasa idan kika ce ba sunanki bane sai ranki ya ɓaci!" Ya fice daga ɗakin cikin tafiyarsa ta isa, buga ƙafarta tayi a ƙasa kamar za tayi kuka ta ce" kullum baya bani amsa wai ni ce aku?" Sai kuma tayi murmushi tana gyada kanta tuna wasu lokuta da suka shuɗe, komawa tayi ta kwanta kan gadon idanunta a buɗe tayi nisa cikin tunanin da take taga mutum tsaye a kanta cikin sauri ta tashi tana ja da baya akan gadon fuskarta a kwaɓe kamar zatayi kuka tana kallonsa zama ya yi gefen gadon har sannan idanunsa na kanta kusan 2mins kafin ya numfasa cikeda nutsuwa ya fara magana"Lolo narh! Ya jikin naki?" cikin rawar murya ta ce"naji sauƙi Ameer" jinjina kansa ya yi yana ƙoƙarin ɓoye abin da yake cikin ransa ya ce" har yanzu ina nan akan bakata ki yarda da Ameer bazai cutar dake ba, ba sai kin faɗa min ba nasan ba daɗin zama da Maheer kike ba saboda haka ki bani dama zan fitar dake daga cikin halin da kika shiga..." Ya ƙarashe maganar yana kallon fuskarta to see her reaction. Ɗan turo baki Imara tayi tana langwaɓar da kanta gefe ta ce"ka rufamin asiri Ameer wannan maganar ka daina yin ta dan Allah..."


"Wace magana?", Maheer ya faɗa yana shigowa ɗakin hannunsa riƙe da system, a ɗan razane Imara ta ce"bab...ba komai kawai akan abin da Dameer ya yimin ne" ajiye system ɗin hannunsa ya yi a kan wani table ya zauna gefen Ameer yana murmushi ya ce" karka damu Ameer babu abinda ya sameta ai" murmushinsa mai kyau ya yi yana kallonta ya ce"haka tace min ai" sunkuyar da kanta tayi jin zuciyarta tayi wata kyakkyawar bugawa bai sake cewa komai ba ya miƙe tsaye yana dogara sandarsa ya yi hanyar waje.


"Maheer ka bata shawara taso wanda ya ke sonta a rayuwa karta wulaƙantashi yin hakan babban zunubi ne" Ameer ya faɗa yana ƙoƙarin barin ɗakin, murmushi Maheer ya yi ya ce"In sha Allah Ameer".


***Tana danna masa kansa da towel ta ce"koda wasa karka sake yin irin abin da kayi yau Dameer akan me kasan ka bugu zaka shigo gida? Sannan mene haÉ—in ka da ita da har kake neman kasheta? kuma dan rashin hankali a gaban kowa" ture hannunta ya yi daga kansa yana wuci ya ce"Ni Immi ki daina wani yimin faÉ—a dole sai ta mutu dan banason ganinta a cikin fadar nan kuma babu wanda ya isa ya dakatar dani!, sannan..."


Wasu lafiyayyun maruka Immi ta sauke masa a fuska tana kallonsa fuskarta a haÉ—e babu alamar fara'a ta ce"to kasani kanayin wani kuskure Udaid zata kwace maka shashasha!" Dafe kuncinsa ya yi yana kafeta da idanunsa sai kuma ya yi kwafa ya tashi ya fice daga bedroom É—in kamar zai tashi sama.


JODA.

***Tsaye take jikin motarta tana sanye da English wears riga da wando ta tufke gashinta waje guda tana danna wayarta, tun daga nesa yake kallonta yana murmushi har ya ƙaraso gabanta kallonsa ta yi bata ce komai ba ta shige motar ganin haka ya sa shima ya shige ɗaya site ɗin da wani irin speed taja motar suka bar wajen, a wani restaurant tayi parking suka fito a tare ya kalleta sai kuma ya yi murmushi harararsa tayi bata ce komai ba tashige ciki hakan yasa shima ya bita sai da ta zauna sannan ta kalleshi cikin nutsuwa ta ce"ka daina yawan dariya dan Allah haba!" murmushi ya sake yi yana kallonta ya ce"oh tanan kuma kika ɓullo?" ɗan ƙaramin tsaki tayi tana kallonsa ta ce"bar wannan maganar akwai abinda yasa na kiraka kuma yanada amfani saboda haka ka saurara kaji abinda zan ce please" ganin ya bata full attention nasa ya sa tayi murmushi a karo na farko wanda ya yi matuƙar ƙara mata kyau cikin siririyar muryarta ta fara magana

".


*Chapter 4*


"Nan da ƴan kwanaki zai dawo ƙasar nan kuma shigarsa Udaid na nufin abubuwa masu yawa, saboda haka na shirya komai kuma ina buƙatar taimakon ka, Rasheed!" Gyara zaman glasses ɗin fuskarsa ya yi yana kallonta ya ce"ina tare dake a kowane lokaci kawai ki sanar dani abin da kika shirya" wani cute smile tayi ta cigaba da magana.


***A hankali take taka stairs din benan dan gaba ɗaya a tsorace take, "Habibty" a dan firgice ta juyo ta saki wata ajiyar zuciya tana dafe ƙirjinta ta ce"Sabahul khair Shamma (Barka da safiya Shamma), murmushi Shamma tayi tana kama hannunta ta ce"why are you scared?" Ta marairaice fuska tana kallon Shamma bata ce komai ba, a gefenta ta zaunar da ita bayan itama ta zauna tana kallonta ta ce"kar ki saka damuwa a ranki babu abinda Dameer zai yi miki, ki cire incident din jiya a ranki kinji baby" jinjina kanta tayi hawaye na kawo idanun nata ta ce" in sha Allah Shamma" shafa kanta tayi tana murmushi ta ce"good girl" murmushin Imara ta mayar mata sannan ta tashi tsaye tana kallonta ta ce"zan tafi school" "Allah ya kiyaye" Ameen ta ce tana gyara zaman veil ɗin ta. Sound ɗin takalminsa ya sanya ta ɗago kanta tana duban inda hannayensa zube cikin aljihun trouser ɗin jikinsa ya sakko fuska babu wata walwala yana zuwa ya gaisheda Shamma ta amsa cikeda fara'a bai cewa Imara komai ba ya yi waje ta bi bayansa tana murguɗa masa baki.


Yana ƙoƙarin shiga motarsa yaga shigowar wata baƙuwar mota hakan yasa ya tsaya yana kallon motar har tayi parking, waro idanunsa waje yayi ganin wacce ta fito daga motar sanye take da wata riga irin mai kama jikin nan wacce ta tsaya iya cinyarta fararen cinyoyinta duk sun fito waje sai gyara gashin kanta wanda ya ke ƙoƙarin rufe mata fuska take tana ganinsa ta washe baki ta tawo da gudu da niyyar shigewa jikinsa saurin matsawa ya yi yana kallonta hakan yasa ta dakata tana tsuke fuska ta ce cikin wata siririyar murya


"Haba Akhii yaushe rabon dana ganka baka missing ɗina?" tabe bakinsa ya yi yana ƙoƙarin buɗe motarsa ya ce"wane ya baki shawarar ki dawo?" watsa hannayenta tayi alamar bata sani ba ya kalleta sai kuma ya shige motarsa, Imara tabi da kallo sai kuma ta juya tabar wajen. Sun yi nisa da gida ta kalleshi ganin yanda yake tuƙinsa cikeda nutsuwa ta tura baki gaba ta ce" kuma yau idan suka min magana me zan ce?" Jin bai ce komai ba yasa ta ci-gaba da faɗin"ni wlh zan ce musu ba sunana Katalina ba kuma ni ba ƴar ƙasar nan ba ce har ƙasarmu kaje ka ce aurena zaka yi ashe kai mugu n..." Cak taji ya tsayar da motar ya juyo a fusace ya shaƙe wuyanta yana kallonta da idanunsa wanda suka gama sauya kala ya ce" kina iya aikata duk abin da kikaso a sanda kikaga dama amma ki sani Maheer bazai taɓa lamuntar tunon asiri ba dole ki ɓoye sirrin sannan kiyi abin da na ce miki ki manta da cewa ke Imara ce! Ki manta da cewa ke ba ƴar ƙasar nan ba ce! Ki manta da wata rayuwa ki sanya a ranki ke Katalina ce!! Idan kuma ba haka ba..." Ya cije laɓɓansa sannan ya hankaɗata tsananin azaba ya hana Imara furta wata kalma ta riƙe wuyanta wanda takejin kamar har yanzu hannunsa yana kai wasu zafafan hawaye ne suka shiga sakkowa kan kuncinta lokaci ɗaya kuma wani irin tari na azaba ya ziyarceta, tsawon lokacin data ɗauka a haka Maheer bai kalli inda take ba har ya yi parking a compound ɗin makarantar


"Get down!"


Abinda ya furta kenan ba tareda ya kalleta ba, cikin sanyin jiki Imara ta sauka daga motar ta shiga tafiya toward direction ɗin class ɗin su har sannan bata daina jin zafin shaƙewar da Maheer ya yi mata ba. Koda ta shiga class ta tarar har lecturer ɗinsu ya shiga hakan yasa kawai ta zauna tana sauraran abin da yake cewa duk da rabin zaman nata tunani take har ya kammala lecturen ya fita Rania ce ta kalleta tana murmushi ta ce"yau kin makara meyasa?" kallonta Imara tayi sai kuma ta kwabe fuska ta ce"bansan lokaci ya tafi haka ba" jinjina kai Rania ta yi ta ce"yanzu ya kike jin jikin naki?" lumshe idanunta tayi nan take hawayen da yake kwance cikin idanun ya zubo kan kyakkyawar fuskarta da mamaki Rania ta ce"ya Ilahi, meke damunki? ko ciwon ne? Ina ne ke miki zafi?" hannunta ta sanya ta goge hawayen sai kuma ta kalli Rania tayi murmushi cikin sanyin murya ta ce"ba komai fa I'm fine kawai wani abu na tuna" girgiza kai Rania tayi ta ce"wannan ba halin ki bane Katalina, bamu ɓoyewa juna komai dan Allah ki sanar dani abin da yake damunki kinji" ta ƙarashe maganar cikin rauni shiru Imara tayi tana kallon Rania tabbas tana buƙatar wanda zata faɗawa damuwarta, tana buƙatar wanda zata kwanta jikinsa tayi kuka amma ba Rania ba! "Imara think idan kika ce zaki faɗa mata abin da ke zuciyarki to tabbas zaki fallasa kan ki kuma Maheer ba zai kyale ki ba dole ki danne abin da kike ji kiyi kamar yanda ya umarce ki" wani ɓangare na zuciyar Imara ta faɗa mata haka, da sauri ta dafe saitin zuciyar tata jin yanda take bugawa da ƙarfi.


"Katalina!", Rania ta kirayi sunanta a ɗan firgice ta kalleta sai kuma tayi murmushi tana kokarin ɓoye damuwarta ta ce"karki damu friend ina lafiya kinji babu komai" shiru Rania tayi badan ta gamsu da abin da Katalina ta ce ba.


****


*LONDON*

*Royal Brompton and harefield hospital specialist care*

*7:30pm*

Kwance take akan gadon marasa lafiyar, a hankali take jan cazbahar hannunta. Wata mata farar tsohuwar mata ce kana ganinta kansa ta manyanta amma kuma da gwarinta yanda take komai a nutse ne zai tabbatar da hakan, turo ƙofar ɗakin akai wanda yasa ta maida hankalinta ga ƙofar tana ganin wanda zai shigo likita ta gani hakan yasa ta ɗan tsuke fuska tana ɗauke kai murmushi kawai likitan ya yi sanin halinta ya ƙaraso gabanta cikin fara'a ya ce" how are you feeling maa?" kallonsa ta yi sai kuma ta sake ɗauke kanta tana kallon gefe, girgiza kansa ya yi ya ce cikin harshen turanci" zan miki allurar yanzu" da sauri ta kalleshi sai kuma ta galla masa harara cikin wata kamilalliyar murya ta fara magana da larabci

"Ya Ilahy, wane ya ce maka bani da lafiya? A'a ni nasamu sauƙi Ana-bikhair Shukran laak" ta haɗe hannayenta alamar godiya. Daman ya rigada yasan haka zata yi yasa ya yi murmushi kawai ya ce"I'm sorry maa dole a miki kodan lafiyarki" wangale baki tayi tana kallonsa sai kuma ta ce" yau naga abin da ya isheni to na ce na warke ai sai a barni haka ko kuma..." Shiru ta yi da maganar ganin ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo jin takun tafiyarsa ya sanya doctorn yin murmushi ya juya ya kalleshi, sanye yake da wata riga t-shirt fara jikinta da stickern hoton Damisa sai wani cargon 3-quater black colour sai canvas fari a ƙafarsa yanada tsayi sosai haka kuma yanada faɗi yanayin jikinsa zaka kalla kasan ma'abocin gym ne saboda yanda duk wani ƙashi na jikinsa yake a murɗe kallo ɗaya ya yi musu ta tsakanin gashin da ya rufe fuskarsa sai kuma ya ɗauke kai yana gyara zaman Bluetooth ɗin kunnensa ya shiga takawa har wajen window ɗin ɗakin da alama waya yake da wani. Ganin ya juya musu baya yasa ta yafito likitan da hannu cikin ƙasa da murya ta ce"kaga wannan azababben ya zo dan Allah ka tafi idan ya fita zan nemeka da kaina kaji"


"Min Fadlhik(Excuse me)"


Tsit tayi shiru da bakinta tana kallonsa ganin har sannan wayarsa yake yasa ta sake kallon likitan ta ce"ka ji yaro" jinjina mata kai ya yi sannan ya juya zai fita, "wait" ya faɗa yana juyowa murmushi doctorn ya yi yana kallonsa ya ce"sir You need something?" bai ce masa komai ba ya zauna gefen gadon yana ƙarewa hannunta kallo above 2mins kafin ya buɗe bakinsa cikin cool voice ɗinsa ya ce" zo ka mata injection ɗin" da sauri ta kalleshi sai kuma ta hade ranta tana huci ganin haka yasa likitan ya dawo har ya yi mata allurar ba ta ce komai ba sai kallo da ido tana ganin ya fita ta bisa da harara.


"Da kin daina harararsa Jadda tunda bashi ya sa kansa ba" a fusace ta ce"koma wane ya saka shi ya je shi da Allah babu wanda zai dinga cutata yana azabtar dani wlh" jin ya yi mata shiru yasa ta yi kwafa ta ce"tunda ga mahaukaciya na magana dole ayi min shiru to uwarka Fateymarh ita ka yiwa shiru ba ni ba" tamkar tana magana da gadon da take kai haka ya yi mata daga ƙarshe ma ya tashi ya fice daga ɗakin, girgiza kanta ta yi cikin faɗa ta cigaba da magana " yaro sai shegen miskilanci da jin kai wai shi wani wannan matarsa ta shiga uku a wajensa wai KA SAUYA HALI!" Jadda ta faɗa tana cigaba da jan cazbahar hannunta.


Kai tsaye office ɗin likitan ya shiga bayan ya zauna doctorn ya kalleshi fuskarsa ɗauke da fara'a ya ce cikin harshen turanci" she's getting better yanayin jikinta ya nuna tana samun sauki sosai" shiru ya yi for some second sai kuma ya numfasa "zuwa yaushe za'a iya discharging nata?" Ya faɗa yana miƙewa tsaye, "maybe by next week" jinjina kai ya yi ya juya ya fice daga office ɗin yana wata irin tafiya mai nuni da isa.


*UDAID*


Murmushi Shamma tayi tana kallonta ta ce"shine kika dawo?" kwaɓe fuska tayi ta ce"wlh Shamma na gaji akwai wahala sosai acan shiyasa na dawo kuma wai ina Ameer?" bata rufe bakinta ba ya shigo gidan bakinsa ɗauke da sallama, da gudu ta tashi tana zuwa ta shige jikinsa tana dariya shafa kanta ya yi da murmushi a fuskarsa ya ce"kaifa-al-hal?(ya ya kike?)" tana sake riƙe shi ta ce" Ana-bikhair Ameer" jinjina kansa ya yi sannan ya janye ta daga jikinsa, akan royal cushion ɗin dake parlon ya zauna ya lumshe idanunsa, kallon Shamma tayi sai kuma ta sake kallonsa ta zauna gefensa da mamaki ta ce"Shamma Ameer bashida lafiya ne?" numfasawa Shamma tayi tana kallonta ta ce"nima bana ce ba Maha haka kullum yake yanzu kamar akwai abin da yake damunsa" hannunta na dama ta ɗora akan fuskarsa ya yi saurin sakin ajiyar zuciya yana buɗe idanu, sosai ta ji zafi a jikinsa hakan yasa ta kwaɓe fuska tana kallonsa ta ce"Ameer ka je asibiti kuwa?" jin ya yi shiru yana kallonta yasa ta cigaba"ka ji jikinka akwai zazzaɓi please ka je asibiti ko a kira doctor ya duba ka?" tayi maganar tana sake kallonsa. Ɗan murmushi ya yi yana jan kumatunta ya ce" ina lafiya fa" turo baki tayi tana kallonsa ta ce"a'a ni dai ka shirya gobe muje asibiti" jinjina mata kai ya yi bai sake cewa komai ba ya tashi ya bar parlon. Da kallo ta bishi har ya shige apartment ɗinsa sannan ta kalli Shamma dake zaune har sannan ta ce"Shamma wai ina Akhii?" murmushi ta yi ta ce" bai shigo ba har yanzu" taɓe baki tayi ta ce"wacce na gansu tare ita ce matar tasa?" gyaɗa mata kai Shamma ta yi, tayi murmushi ta ce"she's beautiful" girgiza kai Shamma ta yi saboda sanin surutun Maha kawai ta tashi ta bar wajen. Tana tashi Joda ta fito hannunta riƙe da system ɗin ta as usual kallo ɗaya Maha ta yi mata ta ɗauke kai dan ko kaɗan basa shiri itama Jodan zamanta tayi wajen kamar batasan da mutum a gurin ba, above 5mins kafin Maha ta tashi zata bar wajen har tayi gaba sai kuma ta dawo tana kallon Joda ta ce cikin harshen larabci

"Ina mai baki shawara ki gyara ɗabi'unki tun kafin lokaci ya ƙure miki, akwai lokuta da dama da bamu gane masoyanmu da kuma maƙiyanmu musamman idan mutum ya kasance yana rangwamin sanin ya kamata kamar dai ke ɗin nan. Ki sani lokaci na nan da za kiyi danasanin abubuwan da kika aikata kuma danasani mara amfani, it's better for you to change your attitude or else..." Ta juya fuu ta haye sama. Sai a sannan Joda ta ɗago idanunta wanda suka kaɗa sukayi jajur tabi bayanta da kallo wani irin tafarfasa zuciyarta ke yi tashi tsaye tana sake duban inda Maha ta yi sai kuma ta daki glass table ɗin dake gabanta nan take ya tawarwatse hannunta ya fashe kallon fararen hannunta wanda suka jiƙe da jini tayi sai kuma ta fasa wata irin ƙara ta zube a wajen sumammiya.


***Zaune ta sameshi a gefen gado ya jingina da jikin fuskar gadon idanunsa a rufe amma ba bacci yake ba, zama tayi gefensa ta kama hannunsa ta riƙe, buɗe runannun idanun nasa ya yi yana kallonta sosai abun ya bata mamaki dan ta daɗe bata ga Ameer cikin irin wannan yanayin ba, cikin sanyin murya ta ce"yallaɓai idan da abin da ke damunka ka sanar damu ko zamu iya maka maganinsa, idan kuma ba zamu iya ba mu tayaka da addu'a amma wannan damuwar bata dace da mai irin Shekarunka ba" da idanu kawai Ameer ya bita ganin hawaye na zuba a idanunta, hannunsa ɗaya ya sanya ya jawota gefensa ya riƙe haɓarta yana kallonta sai kuma ya yi murmushi yana girgiza mata kai da sauri ta shige jikinsa tana fashewa da kuka, shiru Ameer ya yi mata yana jin yanda take kukan. Saida tayi shiru dan kanta sannan ya ɗago fuskarta ya goge mata hawayen cikin kamilalliyar muryarsa ya fara magana

"Zan so a ce kunada damar warwaren matsalata da nafi kowa son na sanar daku, saidai abin da ke cikin raina ya shige tunanin mai tunani. Saboda haka ku tayani da addu'a kawai" kallonsa Shamma tayi sai kuma ta girgiza kanta tana kallonsa ta ce".


# *Imara*
# *Lolo*
# *Joda*
# *Nanameera*
# *Fashion gurl**Chapter 5*


"Wace irin matsala ce da har zata gagara sanar da iyalinka?, Ameer kodan lafiyarka ka daure ka sanar mana, kowa ya damu a fadar nan, ka daina walwala kullum saidai kana ɗaki why?" Ta ƙarashe maganar cikin rauni. Bai ce komai ba ya sanya hannunsa ya janyeta daga jikinsa ya tashi ya fice daga ɗakin hannunsa goye a bayansa, baki buɗe ta bisa da kallo har ya ɓacewa ganinta a hankali ta miƙe tsaye ta shiga zagaye ɗakin tana saƙe-saƙen wasu abubuwa a ranta. Library ɗinsa ya nufa dan akwai muhimman abubuwan da yakeson gabatarwa duk da baya jin daɗin jikinsa. Akan wata royal cushion dake gefensa ya zauna hannunsa riƙe da Alqur'ani mai girma, a hankali fuskarta ke yi masa gizo akan idanunsa yana hango ɗan siririn bakinta wanda take masa tsiwa dashi, saurin runtse idanunsa ya yi a hankali ya ɗora hannunsa bisa ƙirjinsa yana jin yanda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi.


"Astgfirullah!"


Shine abin da ya samu damar furtawa yana sake rufe idanunsa a karo na babu adadi, above 10mins yana zaune a wajen ba tare da ya samu damar aiwatar da abin da ya kawo shi ba, kwakwalwarsa gabaÉ—aya ba a wajen take ba, tunaninsa da zuciyarsa sun karkarta zuwa gare ta.


****

*Al-Udaid Kingdom, North part, backyard*

*9:30pm*

JODA

Tsaye take ta jingina da jikin wani bango, sanye take da wata riga t-shirt milk colour sai wandon jeans Blue colour gashinta ya zubo ta gefen kafaɗarta, idanunta maƙale cikin glasses black colour mai ɗan faɗi, yanayin wajen ya taimaka wajen ƙarawa backyard ɗin kyau. Furzar da iska ya yi daga bakinsa yana kallonta cikin harshen larabci ya ce" ?Limadha tanẓur ilayya (Meyasa kike kallona?". Finger ɗinta ta sanya ta ɗan janye glasses ɗin fuskarta ya dawo kan tsinin hancinta tana kallonsa da sexy eyes ɗinta ta ce cikin harshen turanci" like how? (Kamar yaya kenan?" ɗan basarwa ya yi sanin halinta ya yi murmushi har saida beauty point ɗinsu suka loma ya ce" just move on " jin tayi shiru yasa ya ce"yanzu mene ne plan A?" Kyakkyawan murmushi Joda tayi ta ɗan cije lips ɗinta ta ce"zan tura maka later " jin jina kansa ya yi yana kallonta ya ce" shikenan ina jiranki " . Juyawa yayi ya fara tafiya hannayensa zube cikin aljihu.


"Rasheed!"


Juyowa ya yi yaga bashi take kallo ba sai ya zuba mata idanu, "Kun hadhiran (Ka kula)", É—an murmushi ya yi wanda ya fito da zallar kyansa ya ce "then you care about me?" Wani kallo ta watsa masa sai kuma ta juya tabar wajen, girgiza kansa ya yi yana jinjina hali irin na Joda kafin ya juya ya tafi shima.


*** Zaune take gefen gadon ta zuba uban tagumi, tunani ne kala-kala cikin ranta gaba ɗaya ƙwaƙwalwarta nema take ta gaza ɗaukan abubuwan dake tunkaro ta, dole ta nemawa kanta mafita. Agogon dake maƙale jikin kusurwar ɗakin ta kalla, 9:45 ta gani a jiki ta sauke idanunta ƙasa tana tunanin wani abu, mene makomar aurenta?, me Maheer yake nufi da ita?, wacece ita a wajensa?. Rashin sanin amshoshin tambayarta ya sanya ta fashe da wani raunataccen kuka ta kwanta kan gadon ta ƙanƙame pillow tana wani irin kuka mai tsuma zuciya, kuka ne wanda yake fitowa tun daga ƙasan zuciyarta, kuka ne wanda yake fassara how sad she is, kuka ne irin kukan komai ya ƙare mata. Meyasa sai ita?, Meyasa ƙaddararta ta zaɓa mata haka? Yaushe zata yi farin ciki?


"Sanda kika aminta da Ameer matsayin mai sonki, sanda kika yarda da soyayya da kuma ƙaunar da nake nuna miki, sanda kika buɗe zuciyarki har ta karɓi saƙon da Fahad ke aiko mata a kowace rana, ki yarda dani Lolo, ki ƙaunaceni kamar yanda nima nake ƙaunarki na faɗa kuma zan sake faɗa, billahil-azeem nafi Maheer sonki, ni ne na dace dake ba Maheer ba, ki karbi soyayya ta hannu bibbiyu nayi miki alƙawarin farin ciki mara yankewa, zan zame miki garkuwa, zan baki farin ciki, zan kula da lamuranki, zan tsaya miki. Ki karbi ƙaddarar ki yanda take, ni ne ƙaddarar ki IMARA!"

Ameer ya faɗa yana ƙarasa shigowa ɗakin hannunsa riƙe da sandarsa as usual, a firgice ta ɗago tana kallonsa da idanunta wanda suka yi jajur, ta miƙe tsaye tana goge hawayen da suka mata caɓa-caɓa a fuska ta fara magana;


"Eh, tabbas!, tabbas kai ƙaddararta ne, irin ƙaddarar da kowane bawa yake rokon ubangiji ya kareshi daga gareta, irin ƙaddarar da idan ta gaba to ka take hanaka bacci, ka zame mini ƙarfen ƙafa Ameer!, wlh zuciyata gab take da bugawa idan har ka cigaba da furta irin waɗannan kalaman masu muni a gareni, kanada ilimi, sanin ya kamata, nutsuwa ta zuci data zahiri amma shaiɗan ya rinjayi zuciyarka, ka kasa gane abun da yake daidai da kuma wanda yake ba daidai ba." Durƙusawa ƙasa tayi ta haɗe hannayenta waje ɗaya alamar roƙo tana kuka ta cigaba da faɗin;


"Dan girman Allah, dan darajar Annabi, dan alfarmar iyayenka ka manta dani cikin rayuwarka, ka cire wannan tunanin daga cikin ranka, wlh babu kyau ko kaɗan nifa matar Maheer ce, sirika nake a gurinka. Ka taimaka Ameer! Ka taimaka min. Ta zube a ƙasa tana sake rushewa da wani sabon kukan kamar ranta zai fita, tun da ta fara magana Ameer ke kallonta a hankali kuma yake lumshe idanunsa, gefen gadon ya zauna ya dafe saitin zuciyarsa jin yanda take bugawa da ƙarfi. Above 5mins babu wanda ya ce wani abu a cikinsu, a hankali kuma ta fara rage sound ɗin kukan nata sai ajiyar zuciya da take ta saukewa, miƙewa tsaye ya yi ya fara takawa cikin tafiyarsa ta isa ya ƙaraso gabanta. Sunkuyawa ya yi yana kallonta for some seconds sai kuma ya sakar mata kyakkyawan murmushi, saurin ɗauke idanunta tayi tana runtse su saboda yanda taga ya yi mata wani irin kwarjini. Ya ɗauki mintuna akanta kafin ya tashi ya fice daga ɗakin ba tare da ta sani ba.


Washegari.


Tana ƙoƙarin sanya takalmin ta ya shigo ɗakin, fuskarsa a ɗaure babu alamar fara'a, kallo ɗaya Imara tayi masa ta cigaba da abin da take. Saida ta kammala sanya takalmin wanda yake canvas white colour sannan ta tashi tsaye, hang bag ɗinta ta ɗauka ta ratsa ta gefensa zata fita taji ya janyota, gabansa ya dawo da ita fuskarsa dab da tata, kallonta ya shiga yi frm head to toe sai kuma ya wani yatsine fuska bai ce komai ba ya kama hannunta suka fita daga ɗakin.


***Gaba ɗaya jama'ar gidan sun hallara wajen cin abinci, babu abin da ke tashi sai ƙarar spoons da knives, "Ayn Jūdā? (Ina Joda?)," Immi ta faɗa tana sake ɗaga kanta, murmushi Dameer ya yi ya ce" Maybe akwai mutanen da bata son gani yasa bata fito ba.", duk suka ɗago suka kalleshi, Shamma ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba ta ture plate ɗin hannunta ta tashi ta bar wajen.


"Dameer!"


Cikeda ladabi ya kalli Ameer ya ce" Na'am Ameer"


" La tuḥāwilu abadan mā faʿaltahu al-ān (Karka sake irin haka)" cewar Ameer yana tashi tsaye, cikeda ladabi Dameer ya ce " in sha Allah". Bai sake kallon kowa ba ya bar wajen. Miƙewa Immi tayi tana kallonsa ta ce"ka sameni a ɗaki" okay ya ce sannan y tashi yabi bayanta. Tsaye ya sameta tana kai kawo cikin ƙaton parlon dake cikin part ɗinta, da idanu ya bita ganin kamar hankalinta ba a kwance yake ba yasa ya ce "what's going on Immi?" dafe kanta tayi ta ce"Dameer abubuwa na gab da lalacewa, UDAID na gab da barin hannun mu, sirrin da na daɗe ina ɓoyewa nason fitowa fili." Ɗan murmushi ya yi yana girgiza kansa ya kamo hannunta ya riƙe cikin nasa cikin son kwantar mata da hankali ya fara magana

"Haba Immi, wannan ba abu bane mai yiwuwa, nayi miki alƙawarin yin duk wani abin da ya kamata wajen ganin na cika burinki, saboda haka ki kwantar da hankalinki". Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke ta gyaɗa masa kai ba tareda ta ce komai ba.


*SHAMMA*.


"Ƴaƴana?, Ƴaƴana?, ku ba Yarana bane!, wlh dana riƙe ku matsayin ya'ya gara na mutu na bar duniyar, koda wasa bana ƙaunarku, tunda har kun zaɓeta matsayin uwa to nima na haƙura na sallama mata ku, ta raine ku, ta baku kulawa, amma har abada babu ni babu ku!"


"Shamma dan Allah kar kiyi haka, ke uwace nasan kina son mu, karki bari a rabamu dake, ki jiƙanmu a matsayin mu na yayanki, dan Allah Shamma, karki ji mata ciwo ki taimaka Shamma!" A fusace ta riƙo hannun ƙaramar yarinyar da bazata shige 4-5yrs ba ta hankaɗata, wata razananniyar ƙara yarinyar ta saki dalilin tafasasshen ruwan heatern data zubo a jikinta, da gudu yaron ya saki hannunta ya ƙarasa wajen yarinyar ya shiga jijjigata saidai duk inda ya cire hannunsa sai fatarta ta biyo hannunsa ganin haka yasa ya saki wata irin ƙara, nan take idanunsa suka kaɗa suka yi jajur tamkar gauta, jijiyoyin kansa suka firfito. Tamkar wanda aka zabura haka ya miƙe tsaye naman jikinsa na wani irin rawa wacce ke nuni da ɓacin ran da yake ciki, hannunsa ɗaya ya sanya ya tattare gashin da ya rufe fuskarsa ya maƙaleshi gefen kunnensa, ya kafeta da manyan idanunsa bakinsa na rawa.


"Shamma! Shamma!", girgiza kai Maha tayi ta ƙaraso gabanta ta dafata, a firgice Shamma ta ɗago kanta tana kallonta, sai kuma ta ɗauke idanunta tana ƙoƙarin ɓoye hawayen dake cikin idanun. Zama Maha tayi gefenta cikeda damuwa ta ce "Shamma something went wrong with you but you couldn't tell anyone why?" Kyakkyawar fuskarta ta larabawa Shamma ta kalla sai kuma tayi murmushi ta ce cikin harshen larabci " karki damu baby, ina lafiya" girgiza kai Maha tayi ta ce"shikenan Allah yasa haka ne" "Ameen ya rabbi" Shamma ta faɗa tana kaƙalo murmushi. Tashi Maha tayi ta ce"daman fita zanyi shine nazo na faɗa miki saina dawo bye" hannu kawai Shamma ta ɗaga mata dan batajin zata iya cewa wani abu ta fice daga ɗakin. Tana fita Shamma ta ɗora kanta gefen pillow ta fashe da wani sabon kukan mai cin rai tana nadamar abubuwan da suka faru a baya.


*Education City, Doha, Qatar*
_DOHA INSTITUTE OF GRADUATE STUDIES (DI)_


3:30pm.


Zaune suke cikin capteria kowa na duba abinda zai yi order, ganin hankalinta gaba ɗaya baya wajen yasa Rania ta taɓa ta, a ɗan firgice ta kalleta sai kuma ta sakar mata murmushi tana murza idanunta wanda yayi jajur dashi, ajiye Menu book ɗin Rania tayi ta juyo tana fuskantar ta ta ce cikin harshen larabci "Katalina meke damunki?, tunanin me kike?, me yake hanaki bacci naga idanunki sun koma haka?" Rania ta jero mata tambayar tana kafeta da manyan idanunta, kasa cewa komai Imara tayi kawai sai ta faɗa jikinta ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi. Dafa kanta Rania tayi bata ce komai ba, saida ta barta tayi kukan mai isarta sannan ta fara sakin ajiyar zuciya a hankali tana shassheƙar kuka, ɗago fuskarta Rania tayi tana kallonta ta ce"now tell me what wrong with you?" Ɗan murmushi Imara tayi tana goge hawayen idanunta ta ce"babu komai fa, kawai na tuna wani abu ne shikenan." Baki buɗe Rania take kallonta sai kuma ta girgiza kai


"Me kika tuna da yake sanya ki kuka?, ko shikenan Allah yasa hakane abinda kika faÉ—a"
Jinjina mata kai Imara tayi ta ce"hakane ma" ta faÉ—a tana lumshe idanunta. Shiru suka É—auka na wasu sakkani kafin Imara ta sake kallonta ta ce"can I ask you friend?" "Why not?" Rania ta bata amsa tana kallonta with full attention. Numfasawa Imara ta yi sai kuma ta ce cikin harshen larabci" inada wata friend so tana cikin matsala nikuma na kasa bata shawara shine nake neman taimakon ki ki bani shawara " jinjina kai Rania ta yi, Imara ta cigaba da faÉ—in"zan baki É—an labarin abin da ke damunta sai ki bani shawara Please".


Tunda Imara ta fara magana Rania ke bin ta da kallo irin na mamaki, da daɗe bataji abin da ya gigita mata lissafi ba irin wannan, wane irin son zuciya ne wannan?, wace irin duniya muke ciki ne? Inna'lil lahi wa ina ilayhi raji'uun, shine kawai abin da take iya furtawa gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi. Ganin yanda tayi yasa Imara tayi murmushi tana taɓa ta ta ce " karki damu kanki fa, kawai shawara nakeson ki bata" numfasawa Rania tayi tana kallonta ta ce


"Imara na daÉ—e ban ji abin da ya bani tsoro ba irin wannan, kuma da gaske nufi yake ta rabu da É—ansa?" Jinjina mata kai Imara ta yi ta cigaba da faÉ—in;


"Shawara anan shine kawai ta cigaba da addu'a even through nasan tanayi but ta ƙara, na biyu kuma tana iya using wannan opportunity ɗin wajen ganin ta samu amsar tambayar da take nema, I mean ta tambaye shi wasu abubuwa game da mijinta da kuma matar da yake magana akai, ta nan ne zata gane abin da mijin ke ɓoye mata da kuma wanda ya faru a baya. Idan tayi haka zata iya gano bakin zaren daga nan sai ta yankewa rayuwarta hukunci dan wannan ba ƙaramin al-amari bane!"


Murmushi Imara tayi ta ce"yawwa Friend Nagode sosai in sha Allah nima zan sanar da ita Allah yasa a dace" Ameen ya rabbi Rania ta ce sannan suka cigaba da duba abincin.


***Zaune yake gefen gadonsa idanunsa maƙale akan wani Enlargement na hoto ya zuba mata idanu, fuskar dake jikin hoton sak Imara babu abin da ya raba su. Yanayin shigar dake jikinta ne kawai ya bambanta domin ita wannan ƙananun kaya ne a jikinta gashin kanta kuma a buɗe babu veil.


Da gudu ya ƙarasa sauka daga saman yana tafe yana ture mutane, can ya hango su suna tsaye kana ganinsu kaga ɗalibai, ajiyar zuciya ya sauke sanda ya hangeta fuskanta a sake sai murmushi take, tana ganinsa ta saki murmushi da gudu ta tawo ta shige jikinsa, murmushin shima yake ya riƙeta gam, sun jima a haka kafin ta sake shi tana kallonsa ta ce cikin cool voice ɗinta "you kept me waiting" ta faɗa tana tura baki gaba, hannunta ya kama ya riƙe cikin nasa yana dariya ya ce "I'm sorry na tsaya duba patient ne" langwaɓar da kai tayi ta ce" shikenan kaje sai mun haɗu anjima"


"Really?"


Jinjina masa kai tayi ya bata peck a goshi sannan ya juya zai bar wajen.


"Maheer!"


Juyowa ya yi jin tayi kiran sunansa abin da ya daÉ—e bai ji ba a rayuwarsa, É—aga mata gira ya yi ya ce"what?" Murmushi tayi har saida beauty point É—inta ya loma ta ce" don't forget with me, I love you" yanda tayi maganar jiki a sanyaye ya sanya yayi murmushi ya gyaÉ—a mata kai


"Har abada Peanut", murmushi ta saki ta É—aga masa hannu alamar bye shima ya mayar mata sannan ya juya ya shige motarsa.


"PEANUTTTTT..."

Ya faɗa a fili yana shafa hoton, ɗumin da yaji a fuskarsa ya tabbatar masa da cewa kuka yake kuma daman ya cancanci ya yi kukan, he missed her, ƙaunar da yakewa Katalina daban take a cikin zuciyarsa amma ta tafi, she left him without even say goodbye to him, why? Why???.


"Saboda baka yi deserving rayuwa da ita ba, kanada son kanka, kana fifita buƙatarka akan ta wani, kana iya salwantar da wani abu matuƙar kai zaka samu biyan buƙata, you are too selfish Maheer!"


# *Bestnovel
# *Nanameera
# *Imara
# *2025.

*Chapter 4*


"Nan da ƴan kwanaki zai dawo ƙasar nan kuma shigarsa Udaid na nufin abubuwa masu yawa, saboda haka na shirya komai kuma ina buƙatar taimakon ka, Rasheed!" Gyara zaman glasses ɗin fuskarsa ya yi yana kallonta ya ce"ina tare dake a kowane lokaci kawai ki sanar dani abin da kika shirya" wani cute smile tayi ta cigaba da magana.


***A hankali take taka stairs din benan dan gaba ɗaya a tsorace take, "Habibty" a dan firgice ta juyo ta saki wata ajiyar zuciya tana dafe ƙirjinta ta ce"Sabahul khair Shamma (Barka da safiya Shamma), murmushi Shamma tayi tana kama hannunta ta ce"why are you scared?" Ta marairaice fuska tana kallon Shamma bata ce komai ba, a gefenta ta zaunar da ita bayan itama ta zauna tana kallonta ta ce"kar ki saka damuwa a ranki babu abinda Dameer zai yi miki, ki cire incident din jiya a ranki kinji baby" jinjina kanta tayi hawaye na kawo idanun nata ta ce" in sha Allah Shamma" shafa kanta tayi tana murmushi ta ce"good girl" murmushin Imara ta mayar mata sannan ta tashi tsaye tana kallonta ta ce"zan tafi school" "Allah ya kiyaye" Ameen ta ce tana gyara zaman veil ɗin ta. Sound ɗin takalminsa ya sanya ta ɗago kanta tana duban inda hannayensa zube cikin aljihun trouser ɗin jikinsa ya sakko fuska babu wata walwala yana zuwa ya gaisheda Shamma ta amsa cikeda fara'a bai cewa Imara komai ba ya yi waje ta bi bayansa tana murguɗa masa baki.


Yana ƙoƙarin shiga motarsa yaga shigowar wata baƙuwar mota hakan yasa ya tsaya yana kallon motar har tayi parking, waro idanunsa waje yayi ganin wacce ta fito daga motar sanye take da wata riga irin mai kama jikin nan wacce ta tsaya iya cinyarta fararen cinyoyinta duk sun fito waje sai gyara gashin kanta wanda ya ke ƙoƙarin rufe mata fuska take tana ganinsa ta washe baki ta tawo da gudu da niyyar shigewa jikinsa saurin matsawa ya yi yana kallonta hakan yasa ta dakata tana tsuke fuska ta ce cikin wata siririyar murya


"Haba Akhii yaushe rabon dana ganka baka missing ɗina?" tabe bakinsa ya yi yana ƙoƙarin buɗe motarsa ya ce"wane ya baki shawarar ki dawo?" watsa hannayenta tayi alamar bata sani ba ya kalleta sai kuma ya shige motarsa, Imara tabi da kallo sai kuma ta juya tabar wajen. Sun yi nisa da gida ta kalleshi ganin yanda yake tuƙinsa cikeda nutsuwa ta tura baki gaba ta ce" kuma yau idan suka min magana me zan ce?" Jin bai ce komai ba yasa ta ci-gaba da faɗin"ni wlh zan ce musu ba sunana Katalina ba kuma ni ba ƴar ƙasar nan ba ce har ƙasarmu kaje ka ce aurena zaka yi ashe kai mugu n..." Cak taji ya tsayar da motar ya juyo a fusace ya shaƙe wuyanta yana kallonta da idanunsa wanda suka gama sauya kala ya ce" kina iya aikata duk abin da kikaso a sanda kikaga dama amma ki sani Maheer bazai taɓa lamuntar tunon asiri ba dole ki ɓoye sirrin sannan kiyi abin da na ce miki ki manta da cewa ke Imara ce! Ki manta da cewa ke ba ƴar ƙasar nan ba ce! Ki manta da wata rayuwa ki sanya a ranki ke Katalina ce!! Idan kuma ba haka ba..." Ya cije laɓɓansa sannan ya hankaɗata tsananin azaba ya hana Imara furta wata kalma ta riƙe wuyanta wanda takejin kamar har yanzu hannunsa yana kai wasu zafafan hawaye ne suka shiga sakkowa kan kuncinta lokaci ɗaya kuma wani irin tari na azaba ya ziyarceta, tsawon lokacin data ɗauka a haka Maheer bai kalli inda take ba har ya yi parking a compound ɗin makarantar


"Get down!"


Abinda ya furta kenan ba tareda ya kalleta ba, cikin sanyin jiki Imara ta sauka daga motar ta shiga tafiya toward direction ɗin class ɗin su har sannan bata daina jin zafin shaƙewar da Maheer ya yi mata ba. Koda ta shiga class ta tarar har lecturer ɗinsu ya shiga hakan yasa kawai ta zauna tana sauraran abin da yake cewa duk da rabin zaman nata tunani take har ya kammala lecturen ya fita Rania ce ta kalleta tana murmushi ta ce"yau kin makara meyasa?" kallonta Imara tayi sai kuma ta kwabe fuska ta ce"bansan lokaci ya tafi haka ba" jinjina kai Rania ta yi ta ce"yanzu ya kike jin jikin naki?" lumshe idanunta tayi nan take hawayen da yake kwance cikin idanun ya zubo kan kyakkyawar fuskarta da mamaki Rania ta ce"ya Ilahi, meke damunki? ko ciwon ne? Ina ne ke miki zafi?" hannunta ta sanya ta goge hawayen sai kuma ta kalli Rania tayi murmushi cikin sanyin murya ta ce"ba komai fa I'm fine kawai wani abu na tuna" girgiza kai Rania tayi ta ce"wannan ba halin ki bane Katalina, bamu ɓoyewa juna komai dan Allah ki sanar dani abin da yake damunki kinji" ta ƙarashe maganar cikin rauni shiru Imara tayi tana kallon Rania tabbas tana buƙatar wanda zata faɗawa damuwarta, tana buƙatar wanda zata kwanta jikinsa tayi kuka amma ba Rania ba! "Imara think idan kika ce zaki faɗa mata abin da ke zuciyarki to tabbas zaki fallasa kan ki kuma Maheer ba zai kyale ki ba dole ki danne abin da kike ji kiyi kamar yanda ya umarce ki" wani ɓangare na zuciyar Imara ta faɗa mata haka, da sauri ta dafe saitin zuciyar tata jin yanda take bugawa da ƙarfi.


"Katalina!", Rania ta kirayi sunanta a ɗan firgice ta kalleta sai kuma tayi murmushi tana kokarin ɓoye damuwarta ta ce"karki damu friend ina lafiya kinji babu komai" shiru Rania tayi badan ta gamsu da abin da Katalina ta ce ba.


****


*LONDON*

*Royal Brompton and harefield hospital specialist care*

*7:30pm*

Kwance take akan gadon marasa lafiyar, a hankali take jan cazbahar hannunta. Wata mata farar tsohuwar mata ce kana ganinta kansa ta manyanta amma kuma da gwarinta yanda take komai a nutse ne zai tabbatar da hakan, turo ƙofar ɗakin akai wanda yasa ta maida hankalinta ga ƙofar tana ganin wanda zai shigo likita ta gani hakan yasa ta ɗan tsuke fuska tana ɗauke kai murmushi kawai likitan ya yi sanin halinta ya ƙaraso gabanta cikin fara'a ya ce" how are you feeling maa?" kallonsa ta yi sai kuma ta sake ɗauke kanta tana kallon gefe, girgiza kansa ya yi ya ce cikin harshen turanci" zan miki allurar yanzu" da sauri ta kalleshi sai kuma ta galla masa harara cikin wata kamilalliyar murya ta fara magana da larabci

"Ya Ilahy, wane ya ce maka bani da lafiya? A'a ni nasamu sauƙi Ana-bikhair Shukran laak" ta haɗe hannayenta alamar godiya. Daman ya rigada yasan haka zata yi yasa ya yi murmushi kawai ya ce"I'm sorry maa dole a miki kodan lafiyarki" wangale baki tayi tana kallonsa sai kuma ta ce" yau naga abin da ya isheni to na ce na warke ai sai a barni haka ko kuma..." Shiru ta yi da maganar ganin ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo jin takun tafiyarsa ya sanya doctorn yin murmushi ya juya ya kalleshi, sanye yake da wata riga t-shirt fara jikinta da stickern hoton Damisa sai wani cargon 3-quater black colour sai canvas fari a ƙafarsa yanada tsayi sosai haka kuma yanada faɗi yanayin jikinsa zaka kalla kasan ma'abocin gym ne saboda yanda duk wani ƙashi na jikinsa yake a murɗe kallo ɗaya ya yi musu ta tsakanin gashin da ya rufe fuskarsa sai kuma ya ɗauke kai yana gyara zaman Bluetooth ɗin kunnensa ya shiga takawa har wajen window ɗin ɗakin da alama waya yake da wani. Ganin ya juya musu baya yasa ta yafito likitan da hannu cikin ƙasa da murya ta ce"kaga wannan azababben ya zo dan Allah ka tafi idan ya fita zan nemeka da kaina kaji"


"Min Fadlhik(Excuse me)"


Tsit tayi shiru da bakinta tana kallonsa ganin har sannan wayarsa yake yasa ta sake kallon likitan ta ce"ka ji yaro" jinjina mata kai ya yi sannan ya juya zai fita, "wait" ya faɗa yana juyowa murmushi doctorn ya yi yana kallonsa ya ce"sir You need something?" bai ce masa komai ba ya zauna gefen gadon yana ƙarewa hannunta kallo above 2mins kafin ya buɗe bakinsa cikin cool voice ɗinsa ya ce" zo ka mata injection ɗin" da sauri ta kalleshi sai kuma ta hade ranta tana huci ganin haka yasa likitan ya dawo har ya yi mata allurar ba ta ce komai ba sai kallo da ido tana ganin ya fita ta bisa da harara.


"Da kin daina harararsa Jadda tunda bashi ya sa kansa ba" a fusace ta ce"koma wane ya saka shi ya je shi da Allah babu wanda zai dinga cutata yana azabtar dani wlh" jin ya yi mata shiru yasa ta yi kwafa ta ce"tunda ga mahaukaciya na magana dole ayi min shiru to uwarka Fateymarh ita ka yiwa shiru ba ni ba" tamkar tana magana da gadon da take kai haka ya yi mata daga ƙarshe ma ya tashi ya fice daga ɗakin, girgiza kanta ta yi cikin faɗa ta cigaba da magana " yaro sai shegen miskilanci da jin kai wai shi wani wannan matarsa ta shiga uku a wajensa wai KA SAUYA HALI!" Jadda ta faɗa tana cigaba da jan cazbahar hannunta.


Kai tsaye office ɗin likitan ya shiga bayan ya zauna doctorn ya kalleshi fuskarsa ɗauke da fara'a ya ce cikin harshen turanci" she's getting better yanayin jikinta ya nuna tana samun sauki sosai" shiru ya yi for some second sai kuma ya numfasa "zuwa yaushe za'a iya discharging nata?" Ya faɗa yana miƙewa tsaye, "maybe by next week" jinjina kai ya yi ya juya ya fice daga office ɗin yana wata irin tafiya mai nuni da isa.


*UDAID*


Murmushi Shamma tayi tana kallonta ta ce"shine kika dawo?" kwaɓe fuska tayi ta ce"wlh Shamma na gaji akwai wahala sosai acan shiyasa na dawo kuma wai ina Ameer?" bata rufe bakinta ba ya shigo gidan bakinsa ɗauke da sallama, da gudu ta tashi tana zuwa ta shige jikinsa tana dariya shafa kanta ya yi da murmushi a fuskarsa ya ce"kaifa-al-hal?(ya ya kike?)" tana sake riƙe shi ta ce" Ana-bikhair Ameer" jinjina kansa ya yi sannan ya janye ta daga jikinsa, akan royal cushion ɗin dake parlon ya zauna ya lumshe idanunsa, kallon Shamma tayi sai kuma ta sake kallonsa ta zauna gefensa da mamaki ta ce"Shamma Ameer bashida lafiya ne?" numfasawa Shamma tayi tana kallonta ta ce"nima bana ce ba Maha haka kullum yake yanzu kamar akwai abin da yake damunsa" hannunta na dama ta ɗora akan fuskarsa ya yi saurin sakin ajiyar zuciya yana buɗe idanu, sosai ta ji zafi a jikinsa hakan yasa ta kwaɓe fuska tana kallonsa ta ce"Ameer ka je asibiti kuwa?" jin ya yi shiru yana kallonta yasa ta cigaba"ka ji jikinka akwai zazzaɓi please ka je asibiti ko a kira doctor ya duba ka?" tayi maganar tana sake kallonsa. Ɗan murmushi ya yi yana jan kumatunta ya ce" ina lafiya fa" turo baki tayi tana kallonsa ta ce"a'a ni dai ka shirya gobe muje asibiti" jinjina mata kai ya yi bai sake cewa komai ba ya tashi ya bar parlon. Da kallo ta bishi har ya shige apartment ɗinsa sannan ta kalli Shamma dake zaune har sannan ta ce"Shamma wai ina Akhii?" murmushi ta yi ta ce" bai shigo ba har yanzu" taɓe baki tayi ta ce"wacce na gansu tare ita ce matar tasa?" gyaɗa mata kai Shamma ta yi, tayi murmushi ta ce"she's beautiful" girgiza kai Shamma ta yi saboda sanin surutun Maha kawai ta tashi ta bar wajen. Tana tashi Joda ta fito hannunta riƙe da system ɗin ta as usual kallo ɗaya Maha ta yi mata ta ɗauke kai dan ko kaɗan basa shiri itama Jodan zamanta tayi wajen kamar batasan da mutum a gurin ba, above 5mins kafin Maha ta tashi zata bar wajen har tayi gaba sai kuma ta dawo tana kallon Joda ta ce cikin harshen larabci

"Ina mai baki shawara ki gyara ɗabi'unki tun kafin lokaci ya ƙure miki, akwai lokuta da dama da bamu gane masoyanmu da kuma maƙiyanmu musamman idan mutum ya kasance yana rangwamin sanin ya kamata kamar dai ke ɗin nan. Ki sani lokaci na nan da za kiyi danasanin abubuwan da kika aikata kuma danasani mara amfani, it's better for you to change your attitude or else..." Ta juya fuu ta haye sama. Sai a sannan Joda ta ɗago idanunta wanda suka kaɗa sukayi jajur tabi bayanta da kallo wani irin tafarfasa zuciyarta ke yi tashi tsaye tana sake duban inda Maha ta yi sai kuma ta daki glass table ɗin dake gabanta nan take ya tawarwatse hannunta ya fashe kallon fararen hannunta wanda suka jiƙe da jini tayi sai kuma ta fasa wata irin ƙara ta zube a wajen sumammiya.


***Zaune ta sameshi a gefen gado ya jingina da jikin fuskar gadon idanunsa a rufe amma ba bacci yake ba, zama tayi gefensa ta kama hannunsa ta riƙe, buɗe runannun idanun nasa ya yi yana kallonta sosai abun ya bata mamaki dan ta daɗe bata ga Ameer cikin irin wannan yanayin ba, cikin sanyin murya ta ce"yallaɓai idan da abin da ke damunka ka sanar damu ko zamu iya maka maganinsa, idan kuma ba zamu iya ba mu tayaka da addu'a amma wannan damuwar bata dace da mai irin Shekarunka ba" da idanu kawai Ameer ya bita ganin hawaye na zuba a idanunta, hannunsa ɗaya ya sanya ya jawota gefensa ya riƙe haɓarta yana kallonta sai kuma ya yi murmushi yana girgiza mata kai da sauri ta shige jikinsa tana fashewa da kuka, shiru Ameer ya yi mata yana jin yanda take kukan. Saida tayi shiru dan kanta sannan ya ɗago fuskarta ya goge mata hawayen cikin kamilalliyar muryarsa ya fara magana

"Zan so a ce kunada damar warwaren matsalata da nafi kowa son na sanar daku, saidai abin da ke cikin raina ya shige tunanin mai tunani. Saboda haka ku tayani da addu'a kawai" kallonsa Shamma tayi sai kuma ta girgiza kanta tana kallonsa ta ce".


# *Imara*
# *Lolo*
# *Joda*
# *Nanameera*
# *Fashion gurl*


*Chapter 06*


Da mamaki Maheer ke kallonta yayinda take ƙoƙarin shigowa ɗakin, ajiye hoton hannunsa ya yi ya miƙe tsaye yana nunata da yatsa ya ce"You...!" Gyaɗa masa kai tayi tana murmushi ta ce " ko nayi ƙarye ne?, ba halin ka bane?," girgiza kanta tayi jin yayi shiru ta cigaba da faɗin "halinka kenan, kanada son kanka, baka damuwa da damuwar waɗanda suke kusa da kai, idan kuma har abin da na faɗa ba gaskiya bane to Inason ka nunamin gaskiyar, ka bani kunya, ka barni na tafi inda na fito dan girman Allah" ta ƙarashe maganar tana haɗe hannayenta alamar roƙo. Da idanu kawai Maheer ya bita sai kuma ya bi ta gefenta ya fice daga ɗakin ba tareda y ce mata komai ba, zaman daɓaro Imara ta yi akan tiles ɗin ɗakin da fashe da kuka tana kallon ƙofa, above 5mins kafin ta tashi ta shiga goge idanunta sai kuma ta koma inda ya ajiye enlargement ɗin hoton ta ɗaukeshi. Daskarewa Imara ta yi ganin mai kama da ita sak jikin hoton, hannunta na rawa ta taɓa hoton nan take taji wasu hawaye sun fara sakko mata wanda batasan na menene ba, wacece wannan?,


"KATALINA!"


Wani ɓangare na zuciyarta ya bata amsar, runtse idanunta tayi sai kuma ta sake buɗe su kan hoton, kenan wannan shine dalilin daya sanya Maheer ya ɗaukota?, meyasa suke kama?, wace ita?, mene ne ya rabata da Maheer?, ina take yanzu?. Shiru tayi na ɗan lokaci ƙwaƙwalwarta na ayyana mata abubuwa dayawa, maganar Rania ce ta faɗo mata hakan yasa ta miƙe tsaye kamar wacce aka tsikara ta fice daga ɗakin da sauri.


***Zaune take kan kujerar dake gefen gadonta hannunta riƙe da wayarta tana danna cikeda nutsuwa, wata long sleeve ɗin riga ce a jikinta wacce ta ɗan matseta sosai, ta tukfe gashin kanta waje guda. Wata number ta yi dialing ta zubawa screen ɗin wayar tata idanu har ta katse ba'a ɗauka ba, kwaɓe fuska ta yi ta sake dialing amma kamar ɗazu har ta kashe ba'a yi picking ba. Cilli tayi da wayar kan gadonta ta tashi ta fice daga ɗakin, apartment ɗin Immi ta nufa tana shiga ta isketa zaune suna magana da Shamma, kallo ɗaya ta yi mata ta kalli Immi cikin cool voice ɗinta ta ce"idan kin gama zamuyi magana" murmushi Immi ta yi ta ce"Tom daughter" ganin ta juya zata fita yasa ta kalli Shamma sai kuma ta ce


"Daughter bakiga Shamma ba?" Tana ƙoƙarin fita daga ɗakin ta ce"naganta mana" kafin Immi tayi magana ta fice daga ɗakin tana buga ƙofar, shiru Shamma tayi tana jin wani irin zafi can ƙasan zuciyarta.


"Ki ƙara hakuri kinsan har yanzu yarinya ce" Immi ta faɗa tana dafa Shamma, murmushin yaƙe Shamma ta yi ta miƙe ta ce"anjima ma ƙarasa" jinjina mata kai Immi tayi Shamma ta gyara zaman rigar jikinta ta fice daga ɗakin, wani murmushi Immi ta saki tana bin bayanta da kallo sai kuma ta tashi ta fita domin haɗuwa da Joda.


*8:30pm*


Turo ƙofar ɗakin ta yi ta shigo, wani sassanyan ƙamshi ne ya daki hancinta tayi saurin lumshe idanunta, zaune ta hangesa kan carpet ya tankwashe ƙafafunsa gabansa wani littafi ne yana rubutu akai, a hankali ta shiga takawa har gabansa, sai a sannan ya ɗago dara-daran idanunsa, kai tsaye kuma suka shige cikin nata. Sunkuyar da kanta tayi tana wasada fingers ɗinta, rufe littafin hannunsa ya yi ya ajiye shi gefe yana kallonta ya ce" Marhaban biki" jinjina masa kai ta yi ya yi mata nuni da ta zauna, zama ta yi tana gyaran veil ɗin kanta, kallo ɗaya Ameer ya yi mata ya ɗauke kai cikin daddaɗar muryasa ya fara mata magana


"Yau kuma tsiwar aka biyo ni har ɗaki a yimin?" Kallonsa ta yi taga ya kalleta tayi saurin sauke idanunta ƙasa, murmushinsa mai kyau ya yi ya ce "then me ya kawo ki?, ko zuwa kika yi ki gaida Ameer?" da sauri ta gyaɗa masa kai, waro idanunsa ya yi ya ce "really?" Ta sake jinjina masa kai. Numfasawa ya yi ya ce"Allah ya yi miki albarka Lolo" cikin sakin fuska ta ce"Ameen Nagode Ameer, saida safe"


"Laylatan sa'eedan"


Cewar Ameer, bata sake cewa komai ba ta tashi ta fice daga É—akin, girgiza kansa ya yi sai kuma ya É—auko littafin ya cigaba da rubutunsa.


*London*
*Royal Brompton and harefield hospital specialist care*


*9:30am*


Turo ƙofar ɗakin ya yi ya shigo, turus ya yi ganin yanda take haɗa kayanta dake cikin drawer. Girgiza kansa ya yi bai ce komai ba ya ƙarasa shiga ciki, zama ya yi kusada ita yana kallonta fuskarsa ɗauke da murmushi ba kamar wancen lokacin ba, ɗago kai tayi ta kalleshi ta galla masa harara ta cigaba da abin da take, gyara zamansa yayi yana murmushi ya ce"matar wa ya ɓata miki kai?" Yanda ya yi maganar cikin zolaya ya ƙara fusata ta ta kalleshi kamar zatayi kuka ta fara magana cikin harshen larabci


"A'a kar ka fara wlh, tunda an san ni aka cuta dole ka ce wa ya taɓa ni, to wlh bazai yiwu ba kuma ni yau bazan sake kwana ƙasar nan ba kaji na faɗa maka" shafa kansa ya yi wanda yasha gyara yana murmushi ya kamo hannunta cikin kwantar da murya ya fara magana"haba matar me ya yi zafi haka?, kiyi haƙuri nan da 3days za'a yi discharging naki" janye hannunta ta yi tana watsa masa wani kallo ta ce"a'a, inaaaa, ni zaka yiwa siyasa?, wlh baka isa ba!. Ni yau nakeson barin ƙasar nan haba!, nagaji" ganin yanda take masifa ya sanya ya tsuke fuska kamar ba shi ba ya kalleta cikin wata husky voice ya ce" to tashi ki tafi mana" juyowa ta yi ta kalleshi ganin yanda ya haɗe rai ya saka ta fasa faɗar abin da tayi niyya ta cigaba da haɗa kayanta tana cewa"mutum sai baƙar zuciya, Ka sauya hali!".


*Al-Udaid Kingdom*
*10:00am*

Zaune take gefen gado tana linke kayanta kasancewar yau Saturday babu lecture, gaba daya hankalinta baya jikinta, ƙwaƙwalwarta tayi nisa cikin tunanin da take, tana da buƙatar sanin abubuwa masu yawa game da mijinta da kuma Udaid gaba ɗaya, amma wa zata tunkara?, wane wanda zai warware mata wannan al'amarin ta fahimceshi?


"Ameer!"


Wani bangare na zuciyarta ya bata amsa, girgiza kanta tayi ta ce a fili"amma zai sanar dani komai?, ta yaya?" Ajiye rigar hannunta tayi ta kwaɓe fuska kamar ƴar baby ta zuba uban tagumi, above 5mins kafin ta miƙe tsaye ta sanya ɗan ƙaramin hijab kan Abayar jikinta ta fice daga ɗakin da sauri.


A hankali ta tura ƙofar ɗakin bakinta ɗauke da sallama, babu kowa a ciki sai ƙamshin turarensa mai matuƙar daɗi wanda ya haɗe da sanyin ɗakin ya bada wani irin yanayin mai daɗin gaske, tamkar mayen ƙarfe haka Imara taji ana janta zuwa cikin ɗakin kai tsaye kuma inda royal bed ɗinsa yake ta nufa. Zama tayi gefensa tana shafa katifar tana jin wata nutsuwa na saukar mata, kalle-kalle ta shiga yi a ɗakin, komai tsaf yake tamkar ba babba mutum bane a ɗakin ko ba'a faɗa ba Ameer ɗan gayu ne ajin farko. Tashi tayi ta ƙarasa gaban dressing mirror ɗin dake kallonta ta ƙurawa kanta idanu tabbas ta rame sosai kuma hakan nada alaƙa da halin data tsinci kanta a ciki, sarƙar dake maƙale a wuyanta ta kalla, ta kai hannu ta shafi sarƙar wacce ke tuna mata rayuwarta ta baya, inama da ta dawo mata, inama ranakun farin cikin da suka shige su sake maimaita kansu, ɗumin da taji akan fuskarta ya tabbatar mata da kuka take, hannunta ta sanya ta goge hawayen nata nan da nan fuskarta tayi jajur.


"Lolona"

A ɗan firgice ta juya sai kuma ta sunkuyar da kanta ganin ya zuba mata idanu, taku biyu yayi ya ƙaraso gabanta ya harɗe hannayensa a ƙirji yana kallonta ya ce "why are you crying?" girgiza masa kai tayi alamar babu komai, murmushi ya yi cikin nutsuwar da ta gama ratsa shi ya ce"ajiye ina sonki a gefe, daga yau na zama friend ɗinki, a good friend saboda haka feel free and tell me what's wrong with you, I'm here with you" kallonsa tayi a karo na farko, kallo na tsanaki ta ce cikin muryar kuka

"Are you sure?"


"Absolutely sure"


Ya bata amsa, goge hawayen fuskanta tayi ta gyaɗa masa kai, ya miƙa mata hannunsa kallonsa tayi sai kuma ta kalli hannun da ya miƙa mata kafin ta ɗora nata a kai, bai ce mata komai ba ya fara tafiya da ita, Library ɗinsa ya nufa da ita, suna shiga ta zauna kan kujera shi kuma ya nufi inda fridge yake, ruwa mai sanyi ya ɗauko mata da cup ya dawo ya zauna kujerar dake facing tata ya ɓalle bottle ɗin sannan ya miƙa mata, ko kallon cup ɗin bata yi ba ta kafa bakinta jikin bottle ɗin ta fara shan ruwan, cikin sakkanin da basu shige uku ba ta ajiye empty na robar ya kalleta ganin yanda take sauke numfashi a hankali. Tana matuƙar bashi tausayi, yana ɗaya daga dalilan daya sanya yake sake jin sonta cikin zuciyarsa. Sun ɗauki mintuna kafin yaga ta dawo cikin nutsuwarta, ya gyara zamansa yana facing ɗinta sosai ya ce"now tell me" numfasawa tayi cikin sanyin murya ta ce "Ameer"


"Lolona"


"Kome na tambayeka zaka bani amsa?" Jinjina mata kai ya yi, ta cigaba da faÉ—in

"To dan Allah Ameer waye Maheer?, meyasa ya aureni?, wace Katalina?, meyasa nake ganin komai ba daidai bane?, meyasa Maheer ya tsaneni?, meyasa kake sona?" Tunda ta fara magana Ameer ke kallonta fuskarsa fal da tausayinta. Jin ya yi shiru yasa ta fashe da kuka tana rufe bakinta da hannunta take faÉ—in


"Ba zaka faɗa min ba ko?, ba zaka iya ba ko Ameer?, kace kai abokina ne, kenan bazaka iya taimakona ba?, kafison na cigaba da zama cikin fadar nan har baƙin ciki ya kasheni?." Sakkowa tayi daga kan kujerar ta tsuguna kan gwuiwarta ta haɗe hannayenta waje ɗaya alamar roƙo ta cigaba da faɗin "dan Allah dan Annabi Ameer ka taimakeni, ka sanar dani waɗannan abubuwan ko nasamu wani tudu da zan kama wajen ganin na sauya rayuwata, ka zame mini aboki nagari kaji dan Allah karka bari na rasa rayuwata saboda wannan takaicin dan Allah Ameer dan All...Allah...dan..." Ta kasa cigabawa saboda kukan da yaci ƙarfinta. Shiru Ameer ya yi yana sauraren kukan nata wnada yake jinsa har ƙasan zuciyarsa,


"IMARA!"


Ɗago jajayen idanunta tayi ta kalleshi cikin shassheƙar kuka ta ce "Na'am" "stop crying!" Daina kukan tayi ta shiga sauke ajiyar zuciya da sauri da sauri. Numfasawa Ameer ya yi ya haɗe hannayensa biyu waje guda idanunsa bisa carpet ɗin ɗakin ya fara magana cikin tsaftaccen harshen larabci;.


"Zan sanar dake abin da kika buƙaci ki sani, wanda kuma bayan ke babu wanda ya san da hakan, kema kuma zan sanar dake ne domin na wanke kaina daga zargin da kike mini, tabbas Imara ina sonki, kuma naji ina ƙaunarki, saidai bansan dalili ba har yau, ina ji kamar na taɓa rayuwa dake a baya, mun saba kuma mun shaƙu sosai, tun ranar da Maheer ya kawo ki gidan nan naji sonki ya ɗarsu cikin zuciyata, bansan wane kalar so bane, ban san dalilin samuwarsa ba, amma naji inason ki kasance a gefena har na ƙarshen rayuwata. Amma na rantse miki da Allah ban taɓa miki so wanda yake bana daidai ba, kuma nasan abinda na aikata ba laifi bane dan na furta ina sonki, ko a wajen Allah ban aikata abin da yake haramun ba" kallonsa tayi kawai ba tareda ta ce komai ba ya cigaba da faɗin


"Maheer, ya kasance ɗa a wajena, ina kuma matuƙar alfahari da hakan, Maheer mutum ne mai sauƙin kai saidai idan ba'a fahimceshi ba, amma yana da sauƙin mu'amala. Rayuwarsa ta shiga wani hali shekaru biyu da suka shige, ya faɗa cikin wani mawuyacin hali, ya maida damuwa abokiyar rayuwarsa, shin kinsan dalili?"


Girgiza masa kai Imara ta yi ya jinjina kansa ya cigaba da faÉ—in


"Katalina! Saboda Katalina, ta kasance budurwa a wajensa, yana ɗaya daga cikin masu yi mata lecture a school, two years back ta shirya yin tafiya, a ranar sun haɗu da Maheer a makaranta bayan ya dawo gida aka kira shi aka faɗa masa ta yi hatsari ta rasu, Maheer bai yarda ba saida ya je har gidansu, amma iyayenta suka ƙi bashi damar shiga ya ganta, tun daga sannan rayuwarsa ta canja sabon da yayi da Katalina ba ƙarami bane takai ta kawo kowa ya gani sunanta yake kira, daga nan muka kai shi asibiti, anyi iya bakin ƙoƙari kafin a samu kan Maheer lokacin Katalina ta yi shekara da rasuwa. Bayan ya dawo hankalinsa ne aka tura shi aikin kwangila ƙasar ku, tun ranar daya fara ganinki ya kirani a waya hankalinsa a tashe ya ce ya ga Katalina, Ni kaina sanda ya turan hotonki saida na gazgata cewa ita ce, nan yaƙi yarda yace sai ya tawo dake shine dalilin da aka ɗaura muku aure, saidai tun da kuka dawo ƙasar nan ya fuskanci ke daban Katalina daban shikenan ya shiga muzguna miki, duk a tunanin Maheer ke Katalina ce kawai kin rabu dashi ne saboda daman can iyayenki Basu san alaƙarku, amma ni tun ranar dana ganki na tabbatar da ke ba Katalina ba ce! Kuma na yarda da ke, nake sonki nake ƙaunarki. Ruwa ya ɗauka yasha sannan ya cigaba da faɗin "maganar UDAID kuma bazan iya baki labarinta ba domin nasan ba zaki taɓa fahimta ba, amma idan har kina cikinta watarana zaki gane abinda ta ƙunsa."


Wata nannauyar ajiyar zuciya Imara ta sauke kafin ta ɗago ta kalleshi cikin sanyin murya ta ce "yaushe zan koma gidan mu?" Kyakkyawan murmushi ya yi yana girgiza kansa ya ce "bansani ba nima" kwalla ce ta kawo idanunta ta ce "zan nemi Maheer ya sakeni na koma gidanmu, tunda ba ni ce wacce yake so ba, duk da zan so sanin dalilin daya sanya muke kama amma zan bar wa Allah komi zan koma Nigeria na cigaba da rayuwata kamar yanda nafara ta" shiru Ameer ya yi bai ce mata komai ba, badan bai ji abin da ta ce ɗin ba, sai dan bai san amsar da zai bata ba dukda yasan abune mawuyaci barinta da Udaid. Ganin bai ce komai ba ya sanya ta miƙe tayi hanyar waje tana tafiya jikinta a sanyaye ba kamar yanda ta shigo ba. Saida ta kai bakin ƙofar sannan ta juyo ta kalleshi taga ita ya ke kallon muryarta na rawa ta ce "Nagode sosai Ameer, nagode da kulawa" lumshe idanunsa ya yi bai ce komai ba ta juya ta fita. Da mamaki Shamma ke kallonta har ta shige nata apartment ɗin, me ya kaita wajen Ameer?, yaushe ma Ameer ya fara magana da ita?, me suke tattaunawa da har ta daɗe haka a ciki?.


"Shamma!"


Firgigit ta juya tana kallonsa sai kuma tayi murmushi ta ce "Lafiya son?" Girgiza kansa ya yi ya ce "sorry I scared you" murmushi ta yi ta ce "ba komai, ka ci abinci?" Shafa cikin nasa ya yi ya ce "I'm not hungry Shamma, so you don't have to be worry" harararsa tayi ta ce "hakane" ganin ta dauke idanunta ya sanya ya saƙalo hannayensa a wuyanta yana murmushi ya ce "I'm sorry to zan ci in sha Allah"


"Promise?"


Jinjina mata kai ya yi ta ce"oya Maza kaje ka ci nima zani wajen Ameer ne" shiru ya yi sai kuma ya ce"kin gano meke damun nasa?" girgiza kai tayi ya ce " amma why Shamma?" Numfasawa tayi ta ce "Maheer kasan halinsa yana da kafiya akan abu, nayi nayi ya sanar dani meke damunsa yaƙi" girgiza kai ya yi ya ce"let me talk to him" jinjina masa kai tayi, ya yi gaba tana biye a bayansa.


***Tunda ta shiga É—akin take kai kawo ta kasa zama guri É—aya, me kunnuwanta suka jiye mata? Ameer yana son Imara? Inna'lil lahi wa ina ilayhi raji'uun, wane irin abu ne wannan kamar a Film ko a littafai? Maha ta tambayi kanta. Kasa jurewa tayi ta É—auki wayarta ta shiga dialing numbern Joda sai kuma ta katse kiran tana girgiza kanta a fili ta ce


"No bai kamata ba, babu wanda zan sanarwa, zan cigaba da riƙe abun a raina tunda babu wanda ya sani"


"Me zaki cigaba da riƙewa a ranki?"


Daga bakin ƙofa taji an wullo mata tambayar, Shamma ce ta shigo hannunta riƙe da mug sai tiriri yake, murmushin yaƙe tayi dukda yanda ƙirjinta ke bugawa na tsananin tashin hankali ta ce "babu komai Shamma, akan wasu coursemates ɗina ne suke soyayya shine basu san kowa ya sani Ni kuma na sani shine da nake tunanin na faɗawa sauran" mug ɗin hannunta ta ajiye ta kama hannun Maha tana murmushi ta ce"kul, karki zama mai tonawa mutane asiri, duk abin da kikaga Allah ya rufe shi to babu shakka ya kasance a rufen shine mafi Alkhairi, a duk sanda kikaga wani ɗan uwanki musulmi na cikin matsala ki taimakeshi, idan yana neman rufin asiri ki rufa masa sai kiga kema Allah ya rufa miki asiri ranar gobe ƙiyama"


Wasu zafafan hawayene suka shiga sintiri kan fuskarta, na tsananin tausayin Shamma, koda wasa batayi tunanin Ameer zai iya furta irin wannan kalaman ba, sai gashi yana furta yana son wata, watar ma kuma matar É—ansa. Ganin kamar tunani take ya sanya Shamma ta shiga goge mata hawayen fuskarta


"Daga yi miki faÉ—a sai kuka kuma Maha?"


Murmushi tayi tana share hawayen ta ce"thank you Shamma, Ana ahubbuki( ina sonki)" murmushi tayi tana jan kumatunta ta ce" nima haka".


A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga bakinta ɗauke da sallama, hangensa tayi kan gadon ya rufe jikinsa da duvet da alama bacci yake, around 12am ne tasan ba ƙaramin al'amari bane zai sanya ya kwanta a wannan lokacin, ƙarasawa tayi ta zauna gefen gadon ta zubawa kyakkyawar fuskarsa idanu, Allah sarki haka rayuwa take dama, a lokacin da kake muradin rayuwa da wani abu a lokacin yake barinka, watarana ayi farin ciki watarana ayi baƙin ciki, a duk halin da mutum ya tsinci kansa ya godewa Allah shine kawai abin da ya fi masa, daga sanda ka kasance mai godiya ga Allah, daga sannan matsalolinka zasu zama tarihi. Ajiyar zuciya ta sauke tana sake tunano abin da Ameer ya ce mata, da gaske Maheer baya sonta, da gaske Katalina yake so, amma meyasa ita kullum take jin sonsa cikin zuciyarta?, meyasa take jin kamar shine abokin rayuwarta?, meyasa take kasa jin zafinsa?


"Soyayya!".


08106608363.

# *IMARA*
# *Bestnovel*
# *2025*
# *Nanameera.**Chapter 7&8*


Taji Maheer ya furta yana buɗe idanunsa, sunkuyar da kanta tayi ba tace komai ba ta miƙe zata fita, hannunta ya riƙe cikin nasa tayi saurin sauke idanunta ƙasa tana goge hawayen dake zuba a idanunta da hannu ɗaya. Miƙewa zaune ya yi har sannan yana riƙe da hannunta, jawota ya yi ya zaunar da ita kusada shi ya zuba mata idanu yana kallonta, shiru Imara ta yi tana wasada fingers ɗinta sun ɗauki wasu mintuna kafin ya numfasawa cikin sanyin murya wanda bai san yanada shi ba ya ce


"Saboda kina sona kuma kin yarda dani"


Janye hannunta tayi tana girgiza kanta ta ce"hakane amma yanzu na cire wannan yardar da nayi maka, kai ɗin ba abun yarda bane, ka cutar da rayuwata, a lokacin da nake tunanin matsalolina sun zo ƙarshe sai ka shigo cikin rayuwata ka hanani zama lafiya, ka shiga bijiromin da abubuwa waɗanda suka fi ƙarfina. Kakeson ka cimma wata manufarka ta hanyar amfani dani, bazan taɓa mantawa da wannan ba Maheer, bazan manta ba, zan cigaba da tuna irin yanda ka kula dani a baya kafin ka nuna ƙudirinka na aurena!" Tana gama faɗin haka ta fice daga ɗakin kamar zata tashi sama. Ajiyar zuciya ya sauke deep down nasa yana jin babu daɗi abin da ya yi mata domin tabbas ta riƙe shi masoyi kuma abun dogaronta bata taɓa tunanin haka daga gare shi ba, da wannan tunanin Maheer ya ƙarasa yinin ranar dan ko babban parlon bai sake fitowa ba.


Washegari.


Da wuri tagama shirin makarantar ta dan akwai abin da takeson faɗawa Rania kafin su fara lecture, tana ƙoƙarin fita daga ɗakin ya shigo kallonsa ta yi sai kuma ta saki murmushi ta tsuguna har ƙasa ta gaisheshi, amsawa ya yi da fara'a a fuskarsa ta tashi tana sunkuyar da kanta ƙasa


"Makaranta za ki?"


GyaÉ—a masa kai Imara ta yi, ya jinjina kansa shima ya ce "ki zo mu fita tare sai driver ya ajiye ki" har zata ce a'a sai kuma ta gyaÉ—a masa kai ko babu komai zata samu damar kasancewa tare dashi har ta sake fahimtar wasu abubuwan da ya shafi Udaid. Da wannan tunanin ta bi bayansa suka fice daga apartment É—in,


Tunda suka fara sakkowa ta zuba musu idanu tana kallonsu, wani irin abu taji ya zo ya tsaya mata a ƙirji nan da nan fuskarta tayi jaa na tsananin baƙin ciki, ita kaɗai ce a parlon hannunta riƙe da mug na tea. Imara ce ta kalleta cikin sakin fuska ta ce "Sabahul khair Maha" mayar mata da murmushin tayi ta ce "kin tashi lpy?" "Alhamdulillah" cewar Imara,


"Barka da fitowa Ameer" Maha ta faɗa tana ƙoƙarin barin parlon, jinjina mata kai Ameer ya yi bai ce komai ba ya fice daga fadar, Imara tabi bayansa.


*London*
10:00am.


Tamkar wacce ke magana da statue haka ya yi mata, daga ƙarshe ma ya sanya Bluetooth a kunnensa yana jin karatu, baki Jadda ta saka ganin ya yi mata shiru sai kuma ta kama gefen hijab ɗin dake jikinta ta fara goge kwalla. Gajiya ya yi da zaman ya miƙe hannayensa zube a aljihu ya ce "idan kin gama kukan ki sameni a waje, if not wlh zan tafi na barki ƙasar nan" da harara Jadda ta bisa, sai kuma ta cigaba da haɗa kayan nata tana magana cikin masifa


"Yaro ba mutunci gare shi ba yanzu sai ya tafi ya barni, sallamamme".


***Suna fitowa daga lecture Imara ta kalleta ta ce"kinsan me kuwa?" Girgiza mata kai Rania ta yi ta ce"zo muje zan baki labari" da sauri Rania ta kama hannunta tana dariya ta ce"nidai wlh ki faɗamin anan kawai" murmushi Imara tayi bayan ta zauna kan wata kujera ta kalli Rania tana nuna mata gefenta ta ce"zo ki zauna" babu musu Rania ta zauna ta yi tagumi ta ce"oya ina jinki Maza-Maza" numfasawa ta yi ta ce"ƙawata ta kirani ta cemin taji daɗi shawararki har tafara sanin wasu abubuwan na dangin mijin nata" murmushi Rania ta yi ta ce"To Masha Allah, ta cigaba da kaiwa Allah kukanta in sha Allah komai zai zame mata tarihi" dafata Imara ta yi ta ce"zan faɗa mata in sha Allah, kema kuma ina godiya" harararta Rania ta yi ta ce"banson hauka fa" tuntsirewa sukayi da dariya a tare.


MAHEER.


Zaune yake cikin office ɗinsa sai juyi yake kam kujerar tasa, abubuwa dayawa suna neman shigowa rayuwarsa, tunani yake wani hukunci zai yanke akan Imara tunda dai yanzu ya gano ba ita ce wacce yake muradin yin rayuwa da ita ba, kodai ya maidata garinsu?, ko dai ya sanar da ita gaskiyar daya daɗe yana ɓoye mata?, amma wane kallo zata yi masa?


"Calm down Maheer, calm down!" Ya faɗa yana dukan kansa, ganin tunani na neman hargitsa ƙwaƙwalwarsa yasa ya miƙe ya ɗauki car key ɗinsa ya fice daga Companyn gaba ɗaya.


***Fitowa Joda tayi daga motar tana ƙarewa wajen kallo kafin ta saki handle ɗin motar ta fito tana tafiya cikeda taƙama, hango shi tayi zaune idanunsa maƙale cikin glasses baƙi ta ƙarasa wajen tana murmushi, zama tayi gefensa cikin fara'ar da batasan tana da shi ba ta ce "welcome yallaɓai" murmushi ya sakar mata shima cikin jin daɗi ya ce "thank you beauty" murmushi tayi har saida beauty point ɗinta ya loma sannan ta ce"ka yar dani ko?" Waro idanunsa ya yi ya ce "ni ɗin?" ta gyaɗa masa kai tana kwaɓe fuska, girgiza kansa ya yi ya ce "nikam karki min sharri, tunda kika baro turkey baki nemeni ba sannan ni yanzu ki ce na watsar dake?" rufe bakinta tayi tana dariya ta ce "kawai a bar maganar, tunda naga ƴar tone tone ce" dariyar shima ya yi ya ce "kinsan ai kece bakida gaskiya kawai" murmushi ta yi ta ce"shikenan naji let bygone be bygone, yanzu me zaka ci?".


Wani banzan kallo Maheer ya watsa masa ya miƙe ya ce"kai naga ba'a abun arziki dakai nayi ta nan" tuntsirewa ya yi da dariya yana riƙe rigarsa ya ce"haba friend wlh wasa nake zo kaji" doke hannunsa ya yi ya ce" just leave me " shafa kansa Asad ya yi yana dariya ya ce"zama ka dawo ne yaro".


6:00pm.

Tafiya suke a tare suna ɗan taɓa hira gaba ɗaya sun gaji kasancewar yau sai yammaci suka tashi daga lecture, ganin yanda take ta kwaɓe fuska yasa Rania ta ce "wai yaushe kika zama haka ne?, ke da bakida son jiki amma ji yanda kike yi yanzu haba!" kallonta Imara tayi sai kuma ta yi murmushi tana sake ƙanƙame books ɗin hannunta ta ce "to ai da kika sani" shiru Rania tayi ganin kamar ba son maganar take ba, waro idanu Imara tayi ganin wanda yake gabato inda take, gaba ɗaya guards sun zagaye shi ko ba'a faɗa maka ba kasan babban mutum ne wanda ƙasar ke ji dashi. Murmushi Ameer ya sakar mata daidai lokacin da yazo dab da ita, baki buɗe Imara ke kallonsa kafin ta haɗiye yawun bakinta cikin sanyin murya ta ce "ba dai laifi nayi ba?" girgiza mata kai ya yi ya ce " zuwa nayi tafiya dake" baki buɗe Imara ke kallonsa sai kuma ta ce"ai da baka zo ba bama yanzu zan tafi, kuma..." shiru tayi ganin yanda Ameer ya kafeta da idanunsa, da hannunsa ya yi mata nuni da ta shige ta tura baki gaba sannan tayi gaba tana ɗagawa Rania hannu, murmushi Rania tayi itama tana ɗaga mata hannun. A back seat ta zauna tana sake ƙanƙame books ɗin hannunta haka kawai take jin ta uncomfortable musamman da daga Ameer na zaune gefenta duk da ba ita yake kallo ba ɗan ƙaramin azkar ɗin hannunsa yake ja. Har suka ƙarasa gida babu wanda yace komai a cikinsu kowanne da abin da yake saƙawa cikin zuciyarsa, tana ganin motar tayi parking ta kama handle ɗin zata buɗe amma ta ji shi ƙam da alama lock aka sakawa motar, gyran murya ya yi driving ya fice daga motar Imara ta juyo ta kalleshi tana rarraba idanu, ganin har sannan bai ɗago kansa ba yasa kamar zatayi kuka ta ce " zan sauka" ɗago kansa ya yi ya kalleta, saurin runtse idanu Imara tayi ganin yanda idanunsa suka sauya launi sunyi jajur dasu sun ƙara fitowa. Cikin rawar murya ta ce


"Am...Ameer lafiya?, wani abu yana damunka?, ko bakada lafiya?" Ta jera masa tambayoyin lokaci guda, lumshe idanunsa ya yi kawai nan take wani ruwa ya kwanta cikin idanun, hannunta ta kai zata taɓa shi ko me ta tuna kuma sai ta janye jiki a sanyaye ta ce


"Mene ne yake maka ciwo?, ko na faɗawa Maheer?, bari na kira Shamma" ta juya tana kama handle ɗin ƙofar a karo na biyu, tattausan hannunsa ya sanya ya riƙe nata hannun tana juyowa ya girgiza mata kai, kwaɓe fuska tayi ta ce"to kuma kai bakada lafiya ba za'a faɗawa kowa ba, ko so kake ka mutu?" Wani murmushi ne ya suɓuce masa, Imara sakar baki tayi tana kallonsa ganin yanda ya yi wani irin kyau tamkar ba tsoho ba, ganin kamar tayi nisa cikin tunani ya sanya ya ɗan girgiza ta kallonsa tayi ta ce "ni ka saukeni"


"Baki son Ameer É—in?"


Ta tsinkayi daddaɗar muryasa, kallonsa tayi taga kamar ba shine ya yi maganar ba dan kwata-kwata ma ba ita yake kallo ba, langwaɓar da kai ta yi ta ce "ayyah Ameer magrib yana yi kuma zaka je masallaci" ta faɗa ba tare da tabi ta kan waccen maganar ba, shiru ya yi mata bai bata amsa ba yasa ta haɗe rai cikeda ta tsiwa ta ce " ni ka buɗe motar na fita, haba!" Murmushi ya yi ya ce "rigima kuma za'a min?" shiru ta masa dan gaba ɗaya ya fara fusatata ya ce "tom ji ke saida safe" kafin ya rufe bakinsa ta buɗe ƙofar motar tayi waje tana yarfe hannu.


Ajiyar zuciya Maha ta sauke tana sakin window É—in, da gaske ne Ameer neman Imara yake!, yaushe Ameer ya zama haka?, me yake damunsa da har zai iya aikata irin wannan É—anyan aikin?, kenan da gaske cin amanar Shamma yake?.


"No, bazai yiwu ba!, bazan bari ba, dole sai nayi maganin wannan matsalar" Maha ta faÉ—a cikin É—aga murya, cikin hanzari ta fita daga É—akin nata tana tafe kamar wata zararriya.


***

Tunda suka shiga cikin jirgin bata sake ganin gilmawarsa ba, ta zuba uban tagumi tana tunanin inda ya shige ya barta, ƙofar VIPn ya buɗe ya fito yana sanye da wasu English wears t-shirt milk colour sai three-quarter coffee gashin kansa wanda yasha gyara sai sheƙi yake ya zubo har wajen kafaɗarsa, tafiya yake kamar baya so sai yamutse fuska yake har ya ƙaraso gabanta. Wani nannauyar ajiyar zuciya Jadda ta sauke kafin ta kalleshi ta galla masa harara cikin faɗa take faɗin


"Kai dai wannan yaro ka sauya hali!, banda kai sallamamme ne ka yi tafiyar ka ka barni cikin jimamin inda ka shiga, saboda rashin imani irin naka, to wlh kaida Allah, kaje idan ka zalunceni ni na yafe maka dan bazan maka baki ba, amma dai ka sauya hali!" Ta ƙarashe maganar tana nuna shi da yatsa, wani kallo ya yi mata wanda ya sanyata sauke idanunta ƙasa cikin kwantar da murya ba kamar ɗazu ba ta ce


"Haba mijin sai ka tafi ka barni bayan kasan yanda na damu dakai, banason na mutu banga aurenka ba" ta kama gefen mayafin jikinta tana goge hawaye, ji ya yi jikinsa ya yi sanyi ya kamo hannunta ya riƙe cikin nasa yana murmushi ya ce


"Ke da zakiyi shigar amare ranar bikin ai kina nan ma, ko amaryar na tabbata ba zata faÉ—a miki kyau ba" washe baki tayi tana kallonsa cikeda fara'a ta ce "to to Masha Allahu, wa ya ganni bikin mijin ai baza'a gane ni ba" murmushi kawai ya yi ganin hankalinta ya kwanta kuma daman abin da yakeso kenan.


Maƙalewa Jadda tayi jikin matattakalar jirgin tana ƙarewa garin kallo ganin ba inda ya dace su kasance ba, zuwa ya yi ya shige ta gabanta tayi saurin figoshi tana kallonsa ta ce "kai ina ne nan ka kawo ni?" Bai ce mata komai ba ya zare hannunta daga jikinsa ya ƙarasa sauka daga jirgi, cikin saurin ta irin na tsoffi ta ƙaraso gabansa ta ce a fusace


"Hala da Fatima kake magana da kayi shiru ko?" A fusace shima ya juyo ya ɗora hannayensa a ƙugu kamar mace yana zazzare mata idanu ya ce" me kika ce?"


"To ni kuwa me zance É—an nan?, kawai tambaya nake ina ne nan?"


"Ƙasarku na kawo ki ki gani!".*IMARA💋💋*


*Chapter 9&10*


Waro idanu Jadda tayi sai kuma ta shiga tafa hannu, tsabar baƙin ciki ya sanya ta rushe da kuka tana kallonsa ta ce "Wlh Muhammadu zan nuna maka ɓacin raina da baka taɓa ganin irinsa ba, kayi gaggawar sauya wannan maganar taka" tunda ta fara magana yake kallonta, duk abinda ta faɗa daga cikin zuciyarta yake, da gaske batasan zuwa wajen danginta, ta guji yan 'uwanta, yaushe wannan gabar zata ƙare?. Ganin yanda ta haɗe rai kamar ba ita ba ya sanya ya kamo hannunta cikin sanyin murya ya fara magana


"Jadda dan Allah kiyi haƙuri, mene rayuwar?, abin da ya faru ya shige mana, ki dawo cikin dangin ki, ki daina gudun 'ya'yanki, uhm" kafeshi tayi da idanu bata ce komai ba, ganin yanda idanunta ya fara sauya launi ya sanya ya girgiza kai ya ce"shikenan yanzu ki yi haƙuri zan yi mana booking flight ko zuwa dare ne, kafin nan muje gidan ku gaisa"


"Abaan!"


Yaji ta kira sunansa cikin wata murya mai nuna asalin fushin da take ciki,


"Karka kuskura ka sake furtamin maganar su anan, idan ba haka ba wlh zan saɓa maka, sannan kuma ni bazan je inda suke ba, har abada!" Shafa kansa kawai ya yi sanin halin gaddamar Jadda, cikin sanyin murya ya ce"shikenan bari muje hotel sai nayi mana booking flight"


"Da ka nemawa kanka salama"

Bai sake bi ta kanta ba ya yi gaba tana biye dashi.


*UDAID*
7:35pm.

A hankali ta tura ƙofar ɗakin tana wulla idanunta ciki, babu kowa a ciki sai ƙamshi dake tashi ko'ina an gyara shi tsaf, ƙarar zubar ruwan da taji yasa ta kalli toilet ɗin, sai kuma ta yi tsaki ta ƙarasa gaban madubin hannunta ta ɗora kan drawern ta zubawa fuskarta idanu, abubuwa dayawa zuciyarta ke raya mata.


"Lafiya Maha?"

Ta tsinkayi muryar Imara tana mata magana, wani irin abu taji ya tsaya mata a ƙirji nan da nan fuskarta tayi jaa, ta juya yana watsa mata wani shegen kallo ta ce" lafiyar ce ta kawo haka munafuka!" Baki buɗe Imara ke kallonta, Maha ta cigaba da faɗin


"Saboda ke mahauciya ce baki san me kike ba, shashasha, dabba, me bakin iyaye har zaki nemi ubanmu ko?, saboda ke daƙiƙiya ce bakisan abinda yake daidai da wanda ba daidai ba ko?, saboda ke matsiyaciya ce ƴar matsiyata ko?, kin bani mamaki!, nayi tunanin ke mutuniyar kirki ce ashe ba haka bane, no wonder naga kowa na gudunki a gidan nan ashe su suka san da wacce suke zaune. Ki rasa wa zaki nema ma sai uban mijinki, surukinki!,"


ÆŠora hannu Imara tayi aka tuni hawaye suka gama wanke mata fuska cikin rawar murya ta ce

"Wl...wlh...Mah... Wane ya faÉ—a miki?"


"Sai an faɗa min?, daman kun sanar da wani ne wanda kuke tunanin zai faɗawa wasu?, abin da kuke tattaunawa a cikin ɗaki, nima Allah ne ya yi nufin tonon asirin ku yasa naji kuna maganar, kinyi asara wlh kuma na rantse miki da Allah ba zan bar maganar nan iya haka ba saina tona idan yaso kuwa yaji abin da kuke aikatawa!" Ta ƙarashe maganar cikin ƙaraji sannan ta fice daga ɗakin. Zubewa Imara tayi kan tiles ɗin saidai zuwa sannan ko kukan ma ta kasa samun damar yi, sai wata irin rawa da jikinta ke yi, ta jure jikinta waje guda tana sauke ajiyar zuciya akai-akai.


***Zaune yake gefen gadon nasa sai juya takardar dake hannunsa yake, tunani yake idan abin da ya yi shine abin da ya kamata, amma ya mutane zasu ɗauki maganar tasa?, Allah yasa kowa ya fahimceshi. Wani zazzafan numfashi Maheer ya sauke kafin ya tashi tsaye ya linke takardar ya zura a aljihun trouser ɗinsa sannan ya yi waje, a bakin stairs ɗin ya hangi Joda tana danna wayarta, ƙarasawa gabanta ya yi without making any sound yana zuwa ya rufe mata idanu da hannunsa, ɗan murmushin gefen baki tayi tana riƙe hannayen nasa ta ce


"Wai ka mantani, tun daga nesa na ganka fa"


Waro idanu ya yi yana juyo da ita gabansa ya ce" oh shit!" Tuntsirewa tayi da dariya ta ce "ina zuwa ne na ga kasha kwalliya?" Harararta ya yi ya ce "inda kika aikeni" rufe bakinta tayi da hannunta tana dariya ta ce"au nafa manta ba'a tambayarka inda zaka" girgiza kansa ya yi yana murmushi ya sauka daga Benen.


*DAMEER*

Tunda ya shiga yake kai kawo a cikin ɗakin yana jin ransa babu daɗi, tamkar zuciyarsa zata fito haka yake ji, turo ƙofar ɗakin tayi ta shigo tana kallonsa ta ce"Dameer lafiya?" juyowa ya yi ya kalleta idanunsa sun kaɗa sun yi jajur dasu, yanda ya kafeta da idanu yasa Immi ta ce "ka tsareni da ido, ka sanar dani abin da ke faruwa" wani zazzafan numfashi ya furzar daga bakinsa ya zuba hannayensa a aljihu yana kallonta ya ce


"Immi raina ya fara ɓaci da wannan al'amarin, abubuwa sun fara fin ƙarfinmu, ƙaramar magana na nema ta zama babba, Udaid zata bar hannun mu ki fahimta!" Ya faɗa yana dafa kafaɗarta. Girgiza kai Immi tayi tana janye shi daga jikinta ta ce" wai meke damunka Dameer?, ta ya ya?, bazan bari haka ta faru ba!, dole sai nasan yanda nayi mulkin Udaid ya dawo hannunka, koda kuwa bakada gadonta".


"Immi kin sani na sani ni ba jinin gidan nan bane, ban raɓi Udaid ba!, kin kawo ni a matsayin Dameer wanda ya mutu tun bayan kwana biyu da haihuwarsa, nasha gwagwarmaya sosai a cikin fadar nan, har na girma cikinta ina faɗi tashi na yanda zan samu wani matsayi a cikinta, amma ace har yanzu ban cimma matsaya ba?, banida wani abun dogaro?, ba zai yiwu ba!, wlh ba zai yiwu ba Immi!"


Kamo hannun tayi ta zaunar dashi kan kujera ta dafa table É—in dake gabansa tana kallonsa ido cikin ido ta ce


"Me kake nufi da wannan maganar taka?, meyasa ka sakota cikin zancenmu?, juyan baya ka shirya yi ne?, so kake wani yaji abin da kake cewa?, karka sake Dameer!, kar ka kuskura ka sake furta irin waÉ—annan kalaman ko da kuwa dani ne, kai Dameer ne wanda aka haifa cikin fadar nan, so you have to be careful!"


Yanda Immi tayi maganar cikin ɓacin rai ya sanya shi yin shiru, bai ce komai ba ya tashi ya fice daga ɗakin sai sauke ajiyar zuciya yake. Wani gumi ne ya shiga keto mata wanda batasan na mene ne ba, kodan abun da Dameer ya faɗa ne?, kada watarana asirinta ya tonu.


"Never!"

Ta faÉ—a a fili,


"Ke dawa?"


A firgice Immi ta juyo tana kallon Joda wacce ke tsaye kanta hannunta riƙe da system, doguwar rigar Turkey Abaya ce a jikinta ta ɗaura veil ɗin abayar a kanta, sosai farinta ya ƙara fitowa kasancewar abayar Black colour. A ɗan daburce Immi ta ce


"Aaa...Joda yaushe kika shigo?"


Taɓe baki ta yi ta zauna gefen gadon tana kallonta ta ce"kina can zancen zuci" murmushi Immi tayi tana hamdala aranta da bataji abin da Dameer ya ce ba, ta kalleta ta ce"zancen zucin me zanyi nida babu abin da ke damuna sai naga kin yi aure" kallonta Joda tayi sai kuma ta kwaɓe fuska ta ce"aure kuma Immi taɓ!, nidai a'a wlh" dariya Immi tayi ta ce"ai aure ya zama dole Joda mu duk ba auren muka yi muka haife ku ba?" Yamutse fuska tayi daidai lokacin wayar hannunta ta fara ƙara, sunan da tagani akan screen ɗin wayarta ya sanya ta miƙe tsaye da mamaki Immi ta kalleta ta ce"lafiya dai?" girgiza kai Joda tayi bata samu damar bata amsa ba tayi waje da sauri. A babban parlon ta tsaya tana sake kallon wayar kafin ta ɗaga kiran ya katse.


"I'm outside"

Taga text message É—in ya shigo wayarta, tamkar wacce aka cirewa laka haka taji, ta kasa gaba ta kasa baya. Nan da nan hawaye ya kawo idanunta, ganin lokaci na shigewa ya sanya tayi waje da sauri,


Duba gabaɗaya farfajiyar gidan tayi bata hangi kowa ba sai masu aiki da kowa ke abin da ke gabansa, mayafin kanta ta saki ta yafa sannan ta fice daga gidan da sauri, daga can tsallake ta hangeshi tsaye ya juya baya kwantaccen gashin kansa mai kama da na mata ya zubo wajan kafaɗarsa, da gudu ta tsallaka ba tare da ta kalli titin ba dukda motoci na shigewa tana zuwa ta ƙanƙameshi ta baya tana sakin wani raunataccen kuka, wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana ɗan jan numfashinsa, hannunsa ya sanya ya jawota gabansa ta sake shigewa jikinta tana cigaba da kukan, numfashinta har ɗaukewa yake hannunsa ya sanya ya rungumeta sosai ya shiga shafa kanta ba tareda ya ce mata komai ba, sun ɗauki lokaci a haka kafin ta fara sauke ajiyar zuciya tana jan numfashi, ɗago kanta tayi tana kallonsa ta shiga shafa fuskarsa hannunta na rawa


"Ak...Akhi...Akhee!"


Hannunsa ya ɗora akan nata yana ɗan murmushi ya shafi kanta ya ce"kina lafiya?" Kasa magana tayi ta sake fashewa da kuka tana rungumeshi ta shiga girgiza kanta, ɗago fuskarta ya yi ya zuba mata idanu gaba ɗaya fuskarta tayi jajur da ita idanunta sunyi jaa, ko ba'a faɗa maka ba daga ganinta kasan y'ar uwarsa ce dan har kamar tasu ta ɓaci. Saida yaga ta sami nutsuwa sannan ya janye hannunsa cikin sanyin murya ya ce


"Duk sanda na sake zuwa kikayi kuka bazan kuma dawowa ba!" Girgiza kanta ta shiga yi tana rufe bakinta gudun kada kukan nata ya fito ta ce "to kayi haƙuri bazan ƙara ba" yanda tayi maganar Cikin shagwaɓa ya sanya ya harareta ya ce"yaushe zaki girma Joda?" Turo bakinta tayi gaba ya yi murmushi wanda ya fito da zallar kyansa ya ce "shikenan ki koma ciki, duk sanda kike buƙatar wani abu just let me know kinji" rau-rau tayi da idanunta kamar zata yi kuka ta ce "tafiya za kayi?" Gyaɗa mata kai ya yi yana ɓame bakinsa kamar yaro ƙarami, wasu sabbin hawayen ne suka fara sintiri kan fuskarta ya waro idanunsa yana murmushi ya ce"ɓaure sarkin kuka, zo nan" ƙarasawa tayi ta shige jikinsa ya shafa kanta yana murmushi ya ce"ki fito da miji nayi miki aure" fashewa tayi da kuka tana dukansa s ƙirji ta ce cikin wata shagwaɓaɓɓiyar murya


"A'aaaa ni banaso!"


Dariya ya yi ya ce"ai ko dole kiyi aure yarinya" ɗago kanta tayi ta hararesa ta ce "to kai ma kayi auran" murmushi ya yi ya ce"ai daman na kusa watarana zan nuna miki matata" murmushi ta yi ta ce"tom Allah ya kaimu" janyeta ya yi a jikinsa ya ce"I'm coming" jinjina masa kai tayi ya juya inda ya yi parking motarsa ya buɗe, wasu ledoji ya ɗebo sannan ya dawo wajenta yana murmushi ya ce"guess what?" Lumshe idanunta tayi ta bude ta ce"chocolate?" dungure mata kai ya yi ya ce"kwaɗayi" turo baki tayi tana shafa goshinta ta ce"wollah da zafi yaya" "to bari na ƙara miki" ya faɗa yana kawo hannunsa, saurin yin baya tayi tana tuntsirewa da dariya ta ce"ni dai a'a" murmushi ya yi ya ce"nidai riƙe zan shige" shiru tayi tana kallonsa ta karɓi ledojin kamar zatayi kuka ta ce

"Yayaaa!"


Kama hannunta ya yi yana murmushi ya ce"ƴar ƙaramar kanwata " rungumeshi tayi tana fashewa da kuka ta ce"ni karka tafii, karka barni dan Allah" shafa kanta ya yi yana sakin ajiyar zuciya ya ce cikin sigar rarrashi


"Kin fi so raina ya ɓaci Joda?" Girgiza masa kai ta yi ya ce"good, saboda haka ki koma ciki nayi mikin alƙawarin zuwa na tafi dake kinji" sanin halinsa ya sanya ta gyaɗa masa kai kawai tana sake tusa kanta cikin ƙirjinsa, ɗago fuskarta ya yi ya shiga goge mata hawayen yana murmushi ya ce"ki daina rigima Joda" murmushi tayi masa ta ce"to yaya" peck ya yi mata a goshi sannan ya saketa


"Tafi"


Ya faɗa yana kallonta, kallonsa tayi sai kuma ta juya tafara tafiya toward direction ɗin gidan, tana zuwa ƙofar ta sake juyowa ta kalleshi taga ya ɗaga mata hannu. Ɗaga masa itama tayi sannan ta shige cikin gidan, wani zazzafan numfashi ya sauke sannan ya shige motarsa ya bar unguwar.


***Around 9pm ya shigo É—akin bakinsa É—auke da sallama, amsa masa tayi idanunta ya kumbura, da mamaki yake kallonta ya zauna gefenta sake goge idanunta ta yi tana murmushi ta ce "sannu da zuwa"


"Mene ya saka ki kuka?


Girgiza kai tayi tana goge idanunta ta ce "abu ne ya faɗa min idona" hannunsa ya ɗora akanta ya ce" yanzu fa?" "Ya fita" ta faɗa da sauri, jinjina mata kai ya yi sannan ya zaro wata box a bayansa yana murmushi ya ce "gashi nan" karɓa tayi ta ce"mene ne?" Yunkurin buɗewa tayi ya yi saurin riƙe hannunta yana murmushi ya ce"no ki bari ba yanzu ba" murmushi tayi ta ce "Nagode"


"Saida safe"


Jinjina masa kai tayi ya tashi ya fice daga ɗakin, a ƙofar ɗakin ya tsaya ya jingina da bango ya yi shiru kamar wanda wani abu ke damunsa.


"Akhii me kake anan?"


Juyowa ya yi ya kalleta sai kuma ya yi murmushi ya ce"Maha rigima" murmushi kawai tayi ta ce"meke damunka?" "Me kika gani?" Shima ya bata amsa, girgiza kai tayi ta ce"shikenan kawai" tayi gaba bata sake cewa komai ba, da kallo ya bi bayanta sannan shima ya bar wajen.


A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga, zaune ta hangeshi gefen gado yana jan cazbahar hannunsa, sallama ta yi ya amsa ba tareda ya kalleta ba, ƙarasawa tayi ta tsuguna a gabansa cikeda ladabi ta ce "Barka da hutawa Ameer" kallonta ya yi fuskarsa a sake ya ce"Maha" "na'am Abbiey" murmushi Ameer ya yi ya ce"Masha Allah" shiru suka yi na wani lokaci, magana takeson tayi masa amma kuma nauyinsa da take ji ya hanata, kwarjinin Ameer ya hanata amayar da abinda ta ƙunso, ganin bata ce komai ba ya sanya ya yi gyaran murya. A ɗan firgice ta kalleshi sai kuma ta yi murmushi ta ce"daman zuwa nayi zan faɗa maka wata magana" gyara zamansa ya yi yana kallonta ya ce " Tom inaji" cikin sanyin murya ta fara magana a harshen larabci


"Ameer naga wani abu ne ko na ce naji wata magana ne wacce ta sanya naji tsoro, naji babu daɗi, na shiga ruɗani, hankalina kuma ya tashi,koda wasa ban taɓa tunanin hakan ba, meyasa Ameer?, meyasa?, why?, why??. Meyasa sai ita?, idan kace wata kakeso wlh babu wanda zai hanaka aure, tunda ba haramun bane, amma wai IMARA! IMARA!, IMARA matar Maheer, ita kakeso Ameer?, matar auren matar kuma ɗanka, why Ameer?, why? Wlh zuciyata gab take da bugawa, naji kamar na gudu na bar gidan nan, wane irin saɓon Allah ne Ameer?, da girmanka da mutuncinka, ka aikata irin wannan abun, me Shamma da Immi suka rageka dashi?, dame TA FI SU?(Upcoming novel) Yarinyar da ba kowan kowa ba, naji ba daɗi Ameer, kuma Wlh wannan abun ba daidai bane, na zaɓi nayi maganar da kai ne saboda naji ta bakinka, idan har ya tabbata kuma hakane wlh sai nafaɗa kowa yaji a fadar nan, gwara ayi duk abin da za'a yi da ku cigaba da wannan rayuwar, bazan bar maganar ba!, wlh bazan bari ba! Ka bani kunya Ameer!, ka ruguza soyayyar dake tsakanin mu, ka sanya shakku cikin zuciyata, wlh bana son ganinka! Banason ganinka Ameer!, banaso...bana...b"


Maganar ta maƙale saboda kukan da yaci ƙarfinta, tunda ta fara magana Ameer ke kallonta bazaka taɓa cewa dashi take ba yanayin nutsuwarsa bai sauya sai idanunsa da suka kaɗa sukayi jajur, jijiyoyin kansa sun firfito, ganin tayi shiru ya sanya ya kama hannunta jikinsa na rawa ya fara magana


"Karki yimin mummunar fahimta Maha, babu abin da ke tsakanina da IMARA, kawai dai nasan ina sonta, son da bansan dalilinsa ba!, tabbas ina ƙaunarta, inajinta har cikin raina, kuma wlh nafi Maheer sonta, nasan zaki fahimci Ameer ɗin ki, ina nan a matsayina na masoyinku, bazan taɓa canzaku ba dan Allah kuma karku canzani"


"Dole mu sauyaka domin bazamu cigaba da rayuwa da mahaifi irinka ba!, ba kada imani Ameer! Wlh bakada Imani!, bazan taɓa barin wannan cin amanar ba saboda haka zaka ga abin da zan aikata!, zan yiwa tufkar hanci, zan tabbatar ban bar wata alama wacce za'a gane ka ba, zan rufe maka sirrinka har abada" wata ajiyar zuciya ya sauke ta samun sauƙi ya miƙe yana kallonta ya ce" daman nasani ba zaki juyamin baya ba Maha, nasan kina tare da Ameer ɗinki" fashewa tayi da kuka ta shige cikinsa tana rawar murya ta ce"kayi haƙuri Ameer, wlh bazan jure ba, bazan iya yafe cin amana ba, ka yafeni Ameer, ka yafeni...wlh ina sonka..ina sonkaa..." Tayi baya tana cire jikinta daga nasa. Kallonta Ameer ya yi sai kuma ya kalli cikinsa wanda ke zubar jini kamar an buɗe famfo dafa cikin nasa ya yi ya ɗago yana ƙoƙarin yi mata magana daidai lokacin Imara ta shigo ɗakin, sandarewa tayi ganin Ameer cikin jini ya durƙusa da gudu ta tafi ta riƙe shi tana jijjigashi cikin tashin hankali take faɗin


"Ameer, Ameer!!!! Ameer!! Ka tashi kaji kada ka rufe idanunka, zan kira Maheer ya kai ka asibiti, karka rufe idanun Ameer, karka rufe don Allah!!!!" Ɗago idanunta tayi da niyyar yiwa Maha magana taga babu kowa a tsaye, a hankali kuma ta kalli gefenta taga wuƙar da aka kashe shi da ita, an ajiye mata jikinta kuma duk jinin Ameer ɗin, hannunta na rawa ta ɗauki wuƙar ta shiga juyata daidai nan kuma Shamma ta bude ɗakin ta shigo. Sakin wuƙar tayi ta sake riƙe shi tana jijjigashi cikin tsananin tashin hankali take faɗin


"Dan Allah Ameer karka tafi ka barni, ka tashi kaji, kasan me? Ina sonka wlh inama ina sonka ka tashi kaji!, zan dinga dafa maka abinci mai daɗi ka tashi kajii" gaba ɗaya ta fice a hayyacinta banda kiran sunansa babu abin da take, wani ihu Shamma ta saki wanda ya yi sanadiyar shigowar mutane ɗakin da gudu suka ƙaraso wajensa suna kallonsa


"Kika kashe shi?"


A razane Imara ta ɗago idanunta tana kallon Maha, kafin tayi magana Immi ta ce"inna'lil lahi wa ina ilayhi raji'uun, ta kashe shi, wlh ta kashe shi, shikenan ta kashe Ameer" bin su kawai Imara ta shiga yi da kallo kafin ta miƙe tsaye daidai nan Maheer ya shigo dakin, da gudu ya ƙarasa wajen Ameer ɗin ya rungumeshi yana jijjigashi ya ce"Buddy, ka buɗe idanun, stay still, zan kai ka asibiti" hannun Ameer na rawa ya ɗora kan fuskar Maheer yana ƙoƙarin goge masa hawayen fuskarsa. Maha ce ta riƙe Imara cikin faɗa take faɗin"me mahaifin mu ya yi miki da zaki kashe shi?, saboda kina gudun ya tona miki asiri?, ke wace irin mara imani ce?, me ya yi miki IMARA! Me ya yi miki?" Girgiza kai Imara ta shiga yi tama kasa furta koda kalma guda ɗaya, hannunta ta kalla taga duk jinin Ameer tamkar ita ce wacce tayi kisan da gaske, wani irin sarawa kanta ya yi tayi saurin ɗora hannunta aka tana sakin wani firgitaccen ihu kafin ta juya da gudu ta fice daga ɗakin.


ÆŠakinta ta koma ta shiga tana dube-dube kamar mahaukaciya, wajen dressing mirror taje ta barbazo da kayan dake wajen, juyawa tayi zata fita sai kuma ta dawo da sauri ta buÉ—e wardrobe É—in ta daidai nan Maheer ya shigo É—akin. Akwatin daya bata ta É—auko da sauri ta fara ja da baya tana kallonsa cikin tashin hankali take cewa


"Wlh bani ba ce!, wlh bani ba ce!, ban kashe Ameer ba!, bani ba ce wlh!, tafiya ma zanyi" kallonta kawai Maheer ya yi bai ce mata komai ba ya ɗauki car key ɗinsa ya yi waje da sauri, da gudu ta tafi daga ɗakin ta sauka ƙasa bata ko ganin gabanta, fita tayi daga fadar har sannan bata daina gudun ba, da mamaki Maids ɗin fadar ke kallonta ganin kamar bata hayyacinta ta fice daga gidan gaba ɗaya.


***Tunda ya fito yake yawo ba tareda ya samu inda ake sayarda irin abincin ba, shi kaɗai yake jan tsaki yana dukan sitiyarin motar, tun daga nesa ya hangota tana gudu kamar wata mahaukaciya taɓe bakinsa ya yi a ransa ya furta


"Nonsense!"


Kamar wasa yaga tana ƙara yo inda yake duk ƙoƙarinsa na son ganin ya taka burki kasawa ya yi bai yi aune ba sai gani ya yi ta faɗi ƙasa, sai a sannan yaja wani dogon birki ya fito yana hargitsa sumar kansa wacce ta barbareje. Gabanta ya ƙaraso ya tsaya ya riƙe ƙugunsa wanda ya zamar masa jiki, ɗan siririn tsaki yaja sannan ya sunkuya dan ganin ko tana numfashi, da sauri ya kalleta ganin ta riƙe hannunsa bakinta na rawa ta furta


"Papaa..."


Sake kallon fuskarta ya yi jin sunan data ambace shi dashi da kuma muryarta, a ɗan razane ya durƙusa gabanta ya ɗago kanta waro idanunsa ya yi cikin wani irin yanayi ya furta


"*IMARA*"


*End of free pages 🤪💃*


*Wacece IMARA?*
*Da gaske Maheer ya mutu?*
*Wace rayuwa Imara zata faÉ—a bayan faruwar wannan al'amari?*
*Akwatin me Maheer ya bata?*
*Wacece Jadda kuma mene alaƙarta da Qatar?*
*Wane ne Abaan?, mene alaƙarsa da Joda?*
*Mene ne alaƙar Abaan da IMARA da har ya furta sunanta?*
*Idan Dameer ba É—an Ameer bane to É—an wane!?*
*Wacece Katalina kuma mene alaƙarta da IMARA!?*
*Mene ne abin da ya raba Shamma da Æ´aÆ´anta?*
*Shin za'a kama Maha ko kuwa ba za'a ganeta ba?*
*Me IMARA ta rasa a rayuwarta da har ta faɗa wannan ƙangin?*
*IMARA💋*


*Domin samun amshoshin waɗannan tambayoyin ki biya Naira ɗari biyar kacal ₦500 via 7041901078 Hauwa Adamu lawan opay sai a turo da shaida ta 08106608363 Nanameera, masu Arewabooks kuyi following ɗina Nanameera08 zan dinga posting a can a matsayin VIP*


*Note:*
*Littafin nan ₦500 ne idan zaki biya ki biya dan Allah 🙏 Ba zanyi ragi ba!, ki biya ki karanta cikin salama da kwanciyar hankali.*


# *Bestnovel*
# *2025*
# *Ameenatou*
# *IMARA💋💋*


08106608363
Chat me to subscribe yours.


*IMARA 💋💋*

*Chapter 11*


*No.106 Nassarawa G.R.A, Sultan road, Kano state, Nigeria.*

*6:10pm*


A hankali ta turo ƙofar ɗakin tana kallonta, bacci take har sannan da batasan ma an shigo ba, tsayawa tayi a kanta ta zuba mata idanu tana kallonta cikeda tausayawa. Girgiza kai tayi sai kuma ta juya ta fice daga ɗakin tana sauke ajiyar zuciya, a hankali ta shiga buɗe idanunta tana jujjuyasu saida ta ƙarewa ɗakin kallo tsaf sannan ta tashi zaune bakinta na rawa tsoro ya bayyana a kan fuskarta, wata iriyar ƙara ta saki tana ƙoƙarin cire drip ɗin dake hannunta, cikin hanzari ta shigo ɗakin ta ƙaraso gabanta tana kallonta hankali tashe ta ce


"Daughter wani abun ke miki ciwo?, mene ya baki tsoro?" Kallonta Imara tayi sai kuma ta sake sakin wata ƙarar tana sauka daga kan gadon daidai lokacin ya buɗe ɗakin ya shigo, tsayawa ya yi jikin ƙofa ya zuba mata idanu yana kallonta, ganin tayo bakin ƙofar yasa ta furta


"Abaan tare ta mana"


Tamkar da statue ake magana saboda yanda ya yi banza da lamarin sai ma ciro wayarsa da ya yi daga aljihu ya shiga dannawa, ta gabansa tazo zata shige har sannan kuma bata daina ƙarar da take ba. Ƙafarsa ya sanya ya taɗeta ta juyo tana neman faɗuwa ya tallafeta, tsura masa idanu Imara tayi tana kallonsa har sannan jikinta rawa yake sai ƙifta idanu take, ɗauke kansa ya yi daga kanta ya saketa ƙasa ba tare da tayi tsammanin haka ba. Fashewa tayi da kuka saboda yanda kanta ya bugu da tiles ɗin ɗakin ta riƙe kan tana shafawa.


"Mene haka Abaan?"

Kwaɓe fuska ya yi yana kallonta ya ce "Mom meya faru?" sanin halin rainin hankalinsa ya sanya ta girgiza kai kawai ta ƙaraso ta kama hannunta ta miƙe tsaye tana shafa mata kan ta ce"sorry muje na shafa miki man zafi" kallonta Imara ta yi sai kuma ta gyaɗa mata kai tana goge hawayen kan fuskarta. Da idanu ya bisu har suka fice sai kuma ya taɓe baki yana girgiza kansa ya juya ya fice daga ɗakin shi ma. Ƙarar tafiyar da taji a stairs ya sanya ta daga idanunta tana kallonsa, ganin yana shirin fita yasa ta ce"to sallamamme saboda zaman kafurci muke a gidan nan shine ka shirya zaka fice ko sanar dani baka yi ba ko?" da wani irin expression ya juyo yana kallonta tsabar takaici ma ya hanasa magana, ganin bai ce komai ba yasa ta cigaba da cewa "to Uwarka Fatuu ita ka yiwa haka ba ni ba" idanunsa ne suka sauya kala ya juyo yana kallonta cikin wata kakkausar murya ya fara magana


"Daman sharaɗi aka kafamin na cewa idan zan fita sai na sanar dake?, ko uwata ce ke?, mene haɗin ki da fita ta?, ki daina yimin irin wannan to!, banason ana shiga sabgata ki daina wlh!" Bai tsaya sauraren abin da zata ce ba ya juya ya fice daga parlon yana banko ƙofa. Harara ta galla masa cikin takaici ta yi kwafa ta ce"zaka san dani kake wlh!"


***A hankali ta fito daga cikin motar tana ɗan ya mutse fuska, gaba ɗaya a gajiye take ko ta kan jakarta bata bi ba ballantana good flask ɗinta tayi cikin gidan tana tafiya kamar zata faɗi, babu ko sallama ta shiga ciki ta hango Jadda zaune sai surfa masifa take ita ɗaya, ƙarasawa tayi ta zauna ƙasanta ta ɗora kanta a cinyarta kamar zata yi kuka ta ce


"Jaddaaa!"


A shagwabe tayi maganar tana jan ƙarshen sunan, shafa kanta Jadda tayi tana sakin wata ajiyar zuciya ta musamman ta ce"Shalele kin dawo?" gyaɗa mata kai tayi ta ce "dan Allah Jadda ki cewa yaya ya cireni a school ɗin nan wlh sun fiye tsanani ni nafison waccen wlh" kama haɓa Jadda tayi ta ce "keee rufamin asiri wannan yayan naku mai kamada samudawa sai baƙar zuciya ina zan iya masa, kin san kuwa yanda muka ƙarke dashi a asibiti, ɗan nan so ya yi ya yi ajalina, ko kaɗan baya ƙaunar zaman lafiya sai son tashin hankali da kayi magana ya fara ɗaɗɗaga maka ƙirji wai shi namiji, dan ma dai ni ba tsoransa nake ji ba. Ki dai yi haƙuri kawai ki ƙarasa makarantar ki huta" bubbuga ƙafa ta shiga yi daidai nan tayi sallama ta shigo, ƙarasowa tayi ta tsuguna gaban Jadda cikin girmamawa ta ce"Barka da rana Jadda" kallonta kawai Jadda ta yi sai kuma ta ce "ke wai yaushe zaki waye ne?, kullum yarinyar kamar wacce ake yiwa baki, ke Ki sauya hali!" turo baki tayi ta ce"to kuma me nayi miki?, kawai ki dinga yiwa mutane faɗa, ni wlh ki daina zagina kuma na rantse sai na faɗawa yaya duk abin da kuke" harararta Nana tayi kafin tayi magana Jadda ta amshe;


"Kee fita a idona na rufe, wato ni kike faÉ—awa magana ko?, to bari shi uban naku ya dawo duk zakuyi bayani wlh" tashi Umaima tayi ta É—auki jakarta tayi sama ba tareda ta sake cewa komai ba.


"Na rantse Jadda Umaima munafuka ce, ki faɗawa Abbiey ya yi maganinsu wlh kuma ki ce har zaginki sun yi" rufe mata baki Jadda tayi ta ce"har sai kin faɗa min ai yanda suka ɓata miki rai yau suma duk sai nasu ran ya ɓaci.


"To! To! To..."


Ɗago idanu suka yi a tare, tsaye yake a kansu yana sanye cikin wata dakkakiyar shadda ash colour ya ɗora hula zanna akai, farar fatarsa sai sheƙi take, zama ya yi kusada ita yana kallonta cikin zolaya ya ce"kullum aka shigo gidan nan kina magana, ki dinga yin shiru Jadda" karkace baki tayi tana harararsa tace "to ɗan nema uban kwainane kamarya na dinga shiru?, Allah ya tsagamim bakin magana sannan ace nayi shiru ai uban kuturu ma ya yi kaɗan" tuntsirewa ya yi da dariya yana miƙewa tsaye ya ce"ai sai ki bada himma" harararsa tayi ta ce "kaji dashi nidai a daina shiga sabgata sai na kula mutum yawwa!" Girgiza kansa ya yi yana murmushi ya ce "Allah ya huci zuciyarki Hajiya Jadda" washe baki tayi tana murmushi ta ce"ko kai fa, yanzu daga ina kake kaci wannan kwalliyar?" Waro idanunsa ya yi yana shafa gemunsa ya ce "zance naje" wani kallon up and down tayi masa wanda ya sanya ya tuntsire da dariya ya ce"irin wannan kallo haka Jaddarmu?" Kallon Nanah ta yi ta ce"ke tashi muje ciki mu bar wannan" murmushi kawai ya yi ya haye sama dan ɗauro alwala.


***Kallonta Tayi tana murmushi ta ce"yawwa daughter Kinga yanda kikayi kyau kuwa?" Kallonta IMARA tayi sai kuma ta kalli kanta a mudubi, wata farar atampa mai adon baƙi Mamah ta bata, ta ɗaura mata ɗankwali ya zauna kamar ba ita ba, sosai farinta da kuma zallar kyanta ya sake fitowa, hannunta Mamah ta kama tana murmushi ta ce "muje kici abinci" bin bayanta Imara tayi ba tareda ta ce mata komai ba. Babu kowa a parlon sai sautin karatun Alkur'ani dake tashi, lumshe idanunta tayi saboda wani sanyi da taji yana ratsa duk gaɓɓan jikinta. Zaunar da ita Mamah tayi a parlon ta shiga jera mata abinci kala-kala, tea tafara zuba mata tana murmushi ta ce "ki fara gasa cikinki sai kici abincin, zanje nadawo" gyaɗa mata kai kawai Imara tayi dan batada bakin magana har sannan, tana ganin Mamah ta hau sama ta ɗora kanta akan dinning table ɗin wasu hawaye suka shiga sakko mata kan kuncinta. Inuwar mutum data gani ya sanya ta ɗago idanunta tana kallonta, kallo ɗaya Nanah tayi mata ta bar wajen tana taɓe baki, batasan wace ba dan bata taɓa ganinta ba amma haka kawai taji ko kaɗan bata kwanta mata ba!. Fasa zama cin abincin tayi ta juya ta bar wajen tana danna laptop ɗinta hankali kwance, horn ɗin da taji ya sanya ta ajiye laptop ɗin hannunta tayi waje da gudu, tana ƙarasawa compound ɗin yana fitowa daga motar da gudu ta rungumeshi tana dariya ta ce


"Welcome back Abbiey"


Shafa kanta ya yi yana murmushi ya ce cikin wata murya mai daɗi "ƴar Auta ta dawo daga school?" Jakar hannunsa ta karɓa tana gyaɗa masa kai ta ce" wlh Abbiey bana son school ɗin ka cewa yaya a cireni please" kallonta ya yi yana tafiya cikeda nutsuwa ya ce"menene baki so a school ɗin?, karatun?" Girgiza masa kai tayi ya ce "then what?" turo baki tayi sanin halinsa ta ce "kawai nafison waccen" "to kiyi magana dashi sai ya cire ki" shiru tayi bata sake cewa komai ba har suka shiga gidan. Zaune suka tarar dasu Jadda na ganinsa ta shiga share hawaye da tissue tana kallon Mamah ta ce "ina faɗa miki yaron nan kamar zai kai mini duka saboda fusata ko yarsa ba zai yiwa abun da ya yi mini ba" numfasawa Mamah tayi jiki a sanyaye ta ce "dan Allah Jadda kiyi haƙuri kinsan halin Abaan daman"


"What happened?"


Abbiey ya tambaya daga tsaye, kafin Mamah tayi magana Jadda ta fara bashi labarin abin da ya faru da ma wanda bai faru ba tana yi tana sharce majina da tissue kaman gaske, sosai ran Abbiey ya ɓaci yana kallon Mamah ya ce"ina Muhammad?" cikin sanyin murya ta ce"ya fita bai dawo ba yallaɓai" ƙarasawa wajen Jadda ya yi ya ce"I'm sorry Jadda, idan ya dawo zan masa magana in sha Allahu" goge hawayen ta shiga yi tace "tom sai kuma yarinyar nan Umaima itama bakaga abin da tayi mini ba" jinjina mata kai ya yi ya ce" a gabanki zan hukunta su Jadda, let me take shower first" gyaɗa masa kai Jadda tayi cikin shassheƙar kuka ta ce "Allah ya yi maka albarka" murmushi ya yi ya ce"Ameen Jadda".


***A hankali take driven É—in idanunsa a lumshe gabaÉ—aya a gajiye yake, kallonsa tayi ta jikin mudubin ta ce"wai Adeel meke damunka ne?" É—an buÉ—e idanunsa ya yi ya ce" wlh Mom nagaji ne, wai meyasa baku tawo da driver ba?" Harararsa tayi ta ce"saboda haka mukayi niyya kai zaka kaimu" ta glass É—in ya kalleta ganin yanda ta haÉ—e rai ya saka yayi murmushi ya ce"Allah ya huci zuciyarki Mom" banza ta yi masa tana kallon gefenta. Girgiza kai tayi ganin yanda ta kwanto akan kafaÉ—arta tana baccinta hankali kwance.


*8:30pm*

Zaune suke gaba dayansu sakamakon kiran da Abbiey ya yi musu, shiru kowannensu ya yi ganin yanda Abbieyn ke musu faÉ—a abin da ya daÉ—e bai yi ba Jadda kuma sai hura hanci take yi. Can ciki ya yi sallama ya shigo parlon yana kallon mahaifin nasa ya ce "Abbiey gani" da hannu ya yi masa nuni daya zauna, zama Abaan ya yi yana kallonsa da mamaki


"Muhammad daman Jadda abokiyar wasanka ce ban sani ba?, ko kuma Sa'ar ka ce bamu sani ba?" cikin sanyin murya ya ce "Abba akwai matsala ne?, wani abun ta ce maka nayi mata?, me nayi miki Jadda!" Ya ƙarashe maganar yana kallonta, harararsa tayi ta ɗauke idanunta ba tace komai ba. Abbiey ne ya cigaba da faɗin


"Da ina kake magana ko dani?, na tambayeka kana mayar min da tambaya. Koda wasa idan na sake jin haka ya faru sai ranka ya ɓaci Muhammad kuma ba kai kaɗai ba da gaba ɗayanku nake" ya ƙarashe maganar yana kallonsu duka, sunkuyar da kai suka yi ya ce"ku bata hakuri" ya faɗa yana kallon Abaan


"Kiyi haƙuri Jadda" Abaan ɗin ya faɗa yana tashi daga wajen ya haye sama a fusace, da harara Jadda ta bishi tana taɓe baki, kallon Umaima ya yi ya daka mata tsawa ya ce"duk ranar dana sake jin makamancin haka ya faru idan ranki ya yi dubu sai ya ɓaci, ɓacemin daga gani!" Da gudu ta tashi ta bar parlon tana kuka. Tsaki Abbiey ya yi yana kallon Ammar ya ce"ina Ibrahim ne?"


"Bai dawo ba Abbiey"


Ammar ya faɗa kansa a ƙasa, jinjina kai Abbiey ya yi yana kallon Jadda ya ce"kiyi haƙuri Jadda" murmushi ta yi ta ce"babu komai daman ni ban riƙe su ba" jinjina kansa ya yi kafin ya yi mata sallama ya tashi ya fita daga apartment din nata.


***Tunda ta ɗauko box ɗin take jujjuyata tana tuna incident daya faru na ƙarshe, gaba ɗaya batada nutsuwa, gaba ɗaya ta rasa kuzari tunaninta ɗaya halin da Ameer yake ciki, ko ya mutu ko kuma yana raye bata sani ba. A hankali ta buɗe box, waro idanunta tayi ganin wani haɗaɗɗen ring ko ba'a faɗa ba kasan da kuɗi aka siye shi. Ɗago zoben tayi ta juya shi sai kuma ta saki murmushi mai sauti ta zura a hannunta tamkar saboda hannun nata aka yi zoben haka ya yi mata. Tana ƙoƙarin rufe box ɗin idanunta ya sauka kan wata farar welfolded paper ciro papern ta yi ta warwareta ta shiga karanta rubutun jiki kamar haka


_Nasan zakiyi mamakin wannan takardar dana rubuta miki, amma kuma zaki ji dadin ta ta wani ɓangaren, na aureki IMARA da niyyar zan kula dake kuma zan so ki, saidai na yaudareki na kai ki ƙasarmu domin cika wani muradi nawa, a yanzu kuma nagane illar aikata haka. Kullum kina burin komawa ƙasar ku domin ki cigaba da rayuwarki kamar yanda kika fara, saboda haka na yanke shawarar rabuwa dake domin na samar miki da farin ciki. Ni Maheer bin Fahad al-kuwari na sake ki matata IMARA saki uku, Kinga daman babu idda akan ki, zan tabbatar da na mayar dake ƙasar ku domin ki cigaba da rayuwarki, ki yafeni na abin da na aikata miki, a sanda zaki iske wannan takardar nayi miki nisan da ba zaki iya magana dani ba a saboda haka nake neman gafarar ki, ki yafemin duk abubuwan da nayi miki. Maheer_


*#Bestnovel*
# *IMARA 💋 💋*
# *2025*
# *Nanameera*.


08106608363.


*IMARA 💋 💋*

Mikiya writers asso...
Chapter 1 · 0% Book details