Sashe 16
Daurin Goro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"I can't wait ranar nan tazo, duk plans d'ina na ranar ne, Allah dai ya kaimu, zaki yi mamaki sosai."
Bude baki nayi zanyi magana yayi saurin katse ni
"Karma ki tambayi me zai faru ranar, kedai kawai ki shirya mata, it's going to be the biggest day of our lives."
"Shikenan." Nace ina matsawa gaba.
"Ba sallama?" Ya marairaice murya yana bude min hannayenku sa, sarai na gane me yake nufi, dariya nayi, na kara yin gaba, sosa kansa ya shiga yi yana kallo na, sai dana tabbatar nayi nisa daga in da yake sannan na daga mishi hannu ina masa gwalo, da hannu yayi min alamar zai kamani ne.
***
Washegari tun da wuri na tashi, ina nan da d'abi'ata ta dauki idan zanyi abu na tashi da duku-duku na hau shiri, ina ji aka kad'a kararrawar assembly da ake yi a duk ranar da za'a rufe makaranta, a gurguje aka gabatar da komai da ranar da za'a dawo makaranta, kasancewar akwai sauran wajen sati uku kafin a fara Waec yasa aka bawa yan Ss3 hutun sati daya, sai kuma a dawo a fara karatun jarabawar kafin lokacin ta ya zo. Da haka kowa ya hau watse wa cike da farin ciki zuwa gida. Ina tsaye a saman barander classes dinmu na kafa wa gate ido naga shigowar shi, ji nayi kamar zan zame, haka dai na daure na nufi wajen motar, ina zuwa yana fitowa, idanun mu suka sarke waje daya, da sauri na janye nawa na hau gaishe shi, murmushi kawai yayi ya wuce wajen da aka signing, a gaggauce yayi signing din ya taimaka min na dau yan kaya na muka dau hanyar kauyen mu. Sanyin Ac da kamshin turaren da ya bulbula ne suka cika motar, lamo nayi jikin kujera ina jin wani yanayi ne wuyar fassara, magana yake min kasa kasa wanda zaka rantse ba dani ɗin yake ba, idon sa na kan titi sai dai hannun sa daya na rike da nawa yana murzawa a hankali. Har muka isa gida na kasa sakat, shi kuwa babu abinda ya dame shi, sha'anin gaban sa kawai yake cike da tsantsar farin ciki da ya kasa boyuwa a saman fuskar sa.
A kasalance na fito daga motar bayan ya tsaya, gaba nayi kawai dan Allah Allah nake na isa ciki na samu sauƙin abinda nake ji, ina shiga daki yana turo kofar, tsaye yayi kamar yadda ya saba a wanchan lokacin, hannayen sa jingina da makarin kofar, idanun sa na zagaya wa lungu da sak'o na dakin.
"Garin sauri kin manta kayanki Madam."
"Na manta wallahi."
"Dole ki manta ai, kina gudu na, duk kin chanja Aminatu, what's wrong with you?"
Ya fada yana takowa cikin dakin, saurin kasa nayi da kaina ina jin sanda yazo daf dani
"Look at me." Ya furta a chan kasan makoshinsa, a dan darare na dago na kalle shin, sai naga ya cika gaba daya wajen. Tallafo fuska ta yayi ya dago ni
"Kinsan matsayi na wajen ki ko? Kinsan dai ba zan cutar dake ba, then why are you behaving like this? Kamar kin ga bako."
"Ni kawai kunyar ka nake ji Allah."
Na faɗa kai tsaye. Dariya yayi ya saki fuskar tawa ya fada saman gadon dakin, tsaye nayi ina tunanin abin yi, ji nayi ya finciko ni na fado gadon kusa dashi, har saman keyata na buguwa da sangalalin hannun sa, matsowa yayi sosai yana kura min ido
"Shekarar ki 17 if i'm not mistaken, ni kuma i'm 29, nasan abinda ya dace da wanda be dace ba, karki damu, babu wani abu da zan miki da nasan zaiyi hurting dinki, ki daina tsoro na ko kunya ta, ki dauke ni kamar dah, Ya Farouk dinki, ni a waje na,har yanzu yar karamar Aminene nake kallon ki."
Dariya na saka, na kai masa dukan wasa, da sauri ya tare yana hade hannaye na waje daya ya murde su, yar kara nayi kamar zanyi kuka na shiga magiyar yayi hakuri, da kyar na samu ya hakuran, amma sam yaki barin dakin, ni kuma na matsu ya fita dan na samu na watsa ruwa na cire kayan jiki na, kiran wayar da akayi masa ce ta taimake ni, da sauri naga ya daga wayar yana kokarin fita daga dakin baki daya, da haka na samu damar saka key a dakin na aiwatar da abubuwan da nake so.
***Har dare be sake waiwayo ni ba, ina zaune a dakin ban fita falo ba, gidan tsit babu motsin kowa, kaina ke dan saramin saboda yunwar da ta fara addabata, ban dauko komai cikin provision dina ba, gashi naje Kitchen ɗin babu komai balle na samu abinda zan dan taba. Zamewa nayi na kwanta a saman tiles din dakin hannu na rike da wani story book ina karantawa saboda rage kadaita, turo kofar akayi, hannun sa dauke da ledoji manya guda biyu, tashi nayi da sauri na zauna. Ajiye ledojin yayi a gabana ya zauna.
"Ya Farouk yunwa." Nace ina bata fuska.
Tura min ledojin yayi
"Kiyi hakuri abu ne urgent ya fitar dani."
Matsawa nayi na bude na dudduba, kafin na tashi dan zuwa dauko abinda zan juye a ciki.
Bayan mun gama ci na tattare komai na maida na dawo dakin, ban tarar dashi a ciki ba, na shirin bacci na kashe wutar, ina cikin addu'a akayi knocking, tashi nayi na bude, yana tsaye cikin shigar bacci shima, rabawa yayi ta gefe na ya wuce ciki, tsaye nayi a jikin kofar ina kallon sa, har ya haye gadon nawa yana jan dubet zuwa saman kafadarshi.
"Idan kin gama tsaiwar, ki rufe kofar kizo ki kwanta."
Muryar sa ta daki kunne na, jim nayi kamar ba zan motsa ba, sai kuma na shigaa jan kafata da kyar kamar wadda kwai ya fashe wa na isa dayan bangaren, a darare na hau gadon na kwanta gefe daya, ina jin sa ya mirgino zuwa bangaren da nake, ya dora kansa saman pillow na yana saka ni cikin jikin sa. Jiki na ne ya hau rawa kamar mazari, a hankali ya dora bakin sa saman kunne na ya furta
"Let sleep princess, Goodnight."
Manage pls nayi typing ya goge 😥😥😢😓🙏
Comments yana taimakawa sosai wajen motivating writer🙏 Thanks All Jazakumullah bhi khair*ONAR TASFAH*
*OROG NIRUAD*
*RIYAB AFAFAZ*
*EGAP (12)*
***
Kamar tsohuwar munafuka haka nayi ya raba idanu, gaba daya na rasa yadda zanyi, duk na takura,kasa koda kwakkwaran motsi nayi ina jin shi yana karanta mana addu'ar bacci. Bani da kuzarin da zan iya bude baki na, nayi addu'ar nima, haka nayi shiru ina tunanin abinda ke faruwa.
"Princess."
Ya kira ni da sabon sunan da ban san yaushe na same shi ba.
"Uhum ." Nace kamar me ciwon hakori,.
"Please ki saki jikin sa, bacci nake ji nasan kema haka, beside ni mijinki ne, mata da miji basa raba daki sai da kwakkwaran dalili, so kawai ki saki jikin ki dan ba fita zan ba, ina nan anan zan kwana atau."
Ban tanka ba, ina jin sa yana ta kokarin ganin sai na saki jikina, wanda ni kuwa har ga Allah ba iya wa zanyi ba, a yadda nake ji ma yanzun Allah sa nayi runtsawa, yadda yabi ya kanainayeyi, bana jin zai barni na shaki iska me dadi yau kuwa. Har ya gama surutan sa ya fara jan numfashi sannan na sauke ajiyar zuciya, gaba daya bani da sukuni balle nutsuwa da zan iya runtsawa. Sake sake na shiga yi ina tuna wani Novel dana taba karantawa. Da haka bacci barawo yayi awun gaba dani ba tare da na shirya masa ba.
***
Kira wayar sa ce ta farkar dani, baya dakin, na kai duba na wajen wayar, sunan da na gani yana yawo a saman wayar na kura wa ido, har ta gama ta katse wani kiran ya sake shigowa, ita ɗin ce dai, tsam na mike nayi hanyar toilet ba tare da na sake bi takan wayar ba. Tsawon mintuna talatin na dauka a toilet din, gaba daya na hado har da wanka na fito, a gurguje na hau shiryawa ina kallon kofa kar ya shigo, har na gama ɗin kuwa be shigo ba, sai a lokacin na lura ya dau wayar tasa kenan ya shigo ina toilet, ban shafa komai ba sai yar powder da wetlips, na dora hijabi na a saman sabuwar atamfar da na saka ta sau daya a makaranta, blue ce da adon baki anyi mata zanen ganye. Half covered shoe d'ina black na jawo a cikin kayan dana zo dasu na zura na yo waje. Yana zaune a saman kujerar falon, hannun sa rike da mug yana fitar da tururi alamun abu me zafi ne a ciki, shi dinma yayi wanka ya shirya cikin ƙananan kaya black top da wandon su na sojoji, kallo ya hau bina dashi har na karasa ina zama a kasan carpet daidai wajen da kafafun sa suke. Zamowa yayi ya zauna kusa dani kafadarsa na gogar tawa yayi saurin cewa
"Good morning princess."
Murmushi nayi na gaishe shi da ina kwana? Amsawa yayi yana mika min mug din hannun nasa
"Tayani sha wallahi cikana a cunkushe yanke."
Mika hannu nayi zan karba ya girgiza min kai, hanyar bakina yayo dashi a kunya ce na bude ya kafe min cup din, a hankali na shiga kurbar kunun gyadar daya sha madara da sugar, ina sha ina tunanin in da ya samo shi, tas na shanye, ya jawo tissue ya mika min yana tashi
"Anji dadi an shanye min."
Dariya nayi ina karba shi
"Ni kawai dan ka takura ne nasha, amma ba dadi."
"Really!" Yace yana rike kugun sa.
"Umm."
"Ai shikenan, gobe ma rana ce, za'a kawo min ne ba zan baki ba."
"Waya kawo maka?" Nayi saurin tambayar shi dan dama ina son sani. Make kafadar shi yayi ya juya hannun shi
"Ba sai kinji ba."
Murmushi kawai nayi ina ayyana a raina wanda ya kawo mishin, ganin zan bata wa kaina lokaci da tunani yasa na wuce Kitchen ɗin, na wanke mug din na gyara wajen na fito. A tsaye na tarar dashi yana kokarin saka p-cap a kansa
Bude baki nayi zanyi magana yayi saurin katse ni
"Karma ki tambayi me zai faru ranar, kedai kawai ki shirya mata, it's going to be the biggest day of our lives."
"Shikenan." Nace ina matsawa gaba.
"Ba sallama?" Ya marairaice murya yana bude min hannayenku sa, sarai na gane me yake nufi, dariya nayi, na kara yin gaba, sosa kansa ya shiga yi yana kallo na, sai dana tabbatar nayi nisa daga in da yake sannan na daga mishi hannu ina masa gwalo, da hannu yayi min alamar zai kamani ne.
***
Washegari tun da wuri na tashi, ina nan da d'abi'ata ta dauki idan zanyi abu na tashi da duku-duku na hau shiri, ina ji aka kad'a kararrawar assembly da ake yi a duk ranar da za'a rufe makaranta, a gurguje aka gabatar da komai da ranar da za'a dawo makaranta, kasancewar akwai sauran wajen sati uku kafin a fara Waec yasa aka bawa yan Ss3 hutun sati daya, sai kuma a dawo a fara karatun jarabawar kafin lokacin ta ya zo. Da haka kowa ya hau watse wa cike da farin ciki zuwa gida. Ina tsaye a saman barander classes dinmu na kafa wa gate ido naga shigowar shi, ji nayi kamar zan zame, haka dai na daure na nufi wajen motar, ina zuwa yana fitowa, idanun mu suka sarke waje daya, da sauri na janye nawa na hau gaishe shi, murmushi kawai yayi ya wuce wajen da aka signing, a gaggauce yayi signing din ya taimaka min na dau yan kaya na muka dau hanyar kauyen mu. Sanyin Ac da kamshin turaren da ya bulbula ne suka cika motar, lamo nayi jikin kujera ina jin wani yanayi ne wuyar fassara, magana yake min kasa kasa wanda zaka rantse ba dani ɗin yake ba, idon sa na kan titi sai dai hannun sa daya na rike da nawa yana murzawa a hankali. Har muka isa gida na kasa sakat, shi kuwa babu abinda ya dame shi, sha'anin gaban sa kawai yake cike da tsantsar farin ciki da ya kasa boyuwa a saman fuskar sa.
A kasalance na fito daga motar bayan ya tsaya, gaba nayi kawai dan Allah Allah nake na isa ciki na samu sauƙin abinda nake ji, ina shiga daki yana turo kofar, tsaye yayi kamar yadda ya saba a wanchan lokacin, hannayen sa jingina da makarin kofar, idanun sa na zagaya wa lungu da sak'o na dakin.
"Garin sauri kin manta kayanki Madam."
"Na manta wallahi."
"Dole ki manta ai, kina gudu na, duk kin chanja Aminatu, what's wrong with you?"
Ya fada yana takowa cikin dakin, saurin kasa nayi da kaina ina jin sanda yazo daf dani
"Look at me." Ya furta a chan kasan makoshinsa, a dan darare na dago na kalle shin, sai naga ya cika gaba daya wajen. Tallafo fuska ta yayi ya dago ni
"Kinsan matsayi na wajen ki ko? Kinsan dai ba zan cutar dake ba, then why are you behaving like this? Kamar kin ga bako."
"Ni kawai kunyar ka nake ji Allah."
Na faɗa kai tsaye. Dariya yayi ya saki fuskar tawa ya fada saman gadon dakin, tsaye nayi ina tunanin abin yi, ji nayi ya finciko ni na fado gadon kusa dashi, har saman keyata na buguwa da sangalalin hannun sa, matsowa yayi sosai yana kura min ido
"Shekarar ki 17 if i'm not mistaken, ni kuma i'm 29, nasan abinda ya dace da wanda be dace ba, karki damu, babu wani abu da zan miki da nasan zaiyi hurting dinki, ki daina tsoro na ko kunya ta, ki dauke ni kamar dah, Ya Farouk dinki, ni a waje na,har yanzu yar karamar Aminene nake kallon ki."
Dariya na saka, na kai masa dukan wasa, da sauri ya tare yana hade hannaye na waje daya ya murde su, yar kara nayi kamar zanyi kuka na shiga magiyar yayi hakuri, da kyar na samu ya hakuran, amma sam yaki barin dakin, ni kuma na matsu ya fita dan na samu na watsa ruwa na cire kayan jiki na, kiran wayar da akayi masa ce ta taimake ni, da sauri naga ya daga wayar yana kokarin fita daga dakin baki daya, da haka na samu damar saka key a dakin na aiwatar da abubuwan da nake so.
***Har dare be sake waiwayo ni ba, ina zaune a dakin ban fita falo ba, gidan tsit babu motsin kowa, kaina ke dan saramin saboda yunwar da ta fara addabata, ban dauko komai cikin provision dina ba, gashi naje Kitchen ɗin babu komai balle na samu abinda zan dan taba. Zamewa nayi na kwanta a saman tiles din dakin hannu na rike da wani story book ina karantawa saboda rage kadaita, turo kofar akayi, hannun sa dauke da ledoji manya guda biyu, tashi nayi da sauri na zauna. Ajiye ledojin yayi a gabana ya zauna.
"Ya Farouk yunwa." Nace ina bata fuska.
Tura min ledojin yayi
"Kiyi hakuri abu ne urgent ya fitar dani."
Matsawa nayi na bude na dudduba, kafin na tashi dan zuwa dauko abinda zan juye a ciki.
Bayan mun gama ci na tattare komai na maida na dawo dakin, ban tarar dashi a ciki ba, na shirin bacci na kashe wutar, ina cikin addu'a akayi knocking, tashi nayi na bude, yana tsaye cikin shigar bacci shima, rabawa yayi ta gefe na ya wuce ciki, tsaye nayi a jikin kofar ina kallon sa, har ya haye gadon nawa yana jan dubet zuwa saman kafadarshi.
"Idan kin gama tsaiwar, ki rufe kofar kizo ki kwanta."
Muryar sa ta daki kunne na, jim nayi kamar ba zan motsa ba, sai kuma na shigaa jan kafata da kyar kamar wadda kwai ya fashe wa na isa dayan bangaren, a darare na hau gadon na kwanta gefe daya, ina jin sa ya mirgino zuwa bangaren da nake, ya dora kansa saman pillow na yana saka ni cikin jikin sa. Jiki na ne ya hau rawa kamar mazari, a hankali ya dora bakin sa saman kunne na ya furta
"Let sleep princess, Goodnight."
Manage pls nayi typing ya goge 😥😥😢😓🙏
Comments yana taimakawa sosai wajen motivating writer🙏 Thanks All Jazakumullah bhi khair*ONAR TASFAH*
*OROG NIRUAD*
*RIYAB AFAFAZ*
*EGAP (12)*
***
Kamar tsohuwar munafuka haka nayi ya raba idanu, gaba daya na rasa yadda zanyi, duk na takura,kasa koda kwakkwaran motsi nayi ina jin shi yana karanta mana addu'ar bacci. Bani da kuzarin da zan iya bude baki na, nayi addu'ar nima, haka nayi shiru ina tunanin abinda ke faruwa.
"Princess."
Ya kira ni da sabon sunan da ban san yaushe na same shi ba.
"Uhum ." Nace kamar me ciwon hakori,.
"Please ki saki jikin sa, bacci nake ji nasan kema haka, beside ni mijinki ne, mata da miji basa raba daki sai da kwakkwaran dalili, so kawai ki saki jikin ki dan ba fita zan ba, ina nan anan zan kwana atau."
Ban tanka ba, ina jin sa yana ta kokarin ganin sai na saki jikina, wanda ni kuwa har ga Allah ba iya wa zanyi ba, a yadda nake ji ma yanzun Allah sa nayi runtsawa, yadda yabi ya kanainayeyi, bana jin zai barni na shaki iska me dadi yau kuwa. Har ya gama surutan sa ya fara jan numfashi sannan na sauke ajiyar zuciya, gaba daya bani da sukuni balle nutsuwa da zan iya runtsawa. Sake sake na shiga yi ina tuna wani Novel dana taba karantawa. Da haka bacci barawo yayi awun gaba dani ba tare da na shirya masa ba.
***
Kira wayar sa ce ta farkar dani, baya dakin, na kai duba na wajen wayar, sunan da na gani yana yawo a saman wayar na kura wa ido, har ta gama ta katse wani kiran ya sake shigowa, ita ɗin ce dai, tsam na mike nayi hanyar toilet ba tare da na sake bi takan wayar ba. Tsawon mintuna talatin na dauka a toilet din, gaba daya na hado har da wanka na fito, a gurguje na hau shiryawa ina kallon kofa kar ya shigo, har na gama ɗin kuwa be shigo ba, sai a lokacin na lura ya dau wayar tasa kenan ya shigo ina toilet, ban shafa komai ba sai yar powder da wetlips, na dora hijabi na a saman sabuwar atamfar da na saka ta sau daya a makaranta, blue ce da adon baki anyi mata zanen ganye. Half covered shoe d'ina black na jawo a cikin kayan dana zo dasu na zura na yo waje. Yana zaune a saman kujerar falon, hannun sa rike da mug yana fitar da tururi alamun abu me zafi ne a ciki, shi dinma yayi wanka ya shirya cikin ƙananan kaya black top da wandon su na sojoji, kallo ya hau bina dashi har na karasa ina zama a kasan carpet daidai wajen da kafafun sa suke. Zamowa yayi ya zauna kusa dani kafadarsa na gogar tawa yayi saurin cewa
"Good morning princess."
Murmushi nayi na gaishe shi da ina kwana? Amsawa yayi yana mika min mug din hannun nasa
"Tayani sha wallahi cikana a cunkushe yanke."
Mika hannu nayi zan karba ya girgiza min kai, hanyar bakina yayo dashi a kunya ce na bude ya kafe min cup din, a hankali na shiga kurbar kunun gyadar daya sha madara da sugar, ina sha ina tunanin in da ya samo shi, tas na shanye, ya jawo tissue ya mika min yana tashi
"Anji dadi an shanye min."
Dariya nayi ina karba shi
"Ni kawai dan ka takura ne nasha, amma ba dadi."
"Really!" Yace yana rike kugun sa.
"Umm."
"Ai shikenan, gobe ma rana ce, za'a kawo min ne ba zan baki ba."
"Waya kawo maka?" Nayi saurin tambayar shi dan dama ina son sani. Make kafadar shi yayi ya juya hannun shi
"Ba sai kinji ba."
Murmushi kawai nayi ina ayyana a raina wanda ya kawo mishin, ganin zan bata wa kaina lokaci da tunani yasa na wuce Kitchen ɗin, na wanke mug din na gyara wajen na fito. A tsaye na tarar dashi yana kokarin saka p-cap a kansa