Sashe 13
Daurin Goro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dariya nayi na tura baki gaba, kallo na naga ya tsaya yanayi sosai, babu ko giftawa, hannu nasa naja gashin idon sa cika da tsokana.
"Ouch, kai kika min haka?" Ya tambaya yana taba idon nasa
"Abu zan cire maka fah."
"Karya ne."
"Da gaske." Na saka dariya ina matsawa. Riko ni yayi ya dawo dani kusa dashi.
"Kina son kiyi karatu ko?"
Da sauri na daga masa kai na
"Good... Zan saki a makaranta. Kina so?"
"Ina so wallahi." Na faɗa cike da murna
"Ok Tam, zan saki amma sai kinyi min alƙawarin zaki yi karatu sosai, sosai."
"Zanyi Allah."
"Good."
"Toh yaushe zaka sani, kuma aina makarantar take."
Shafa kansa yayi alamar tunani kafin yace
"Yau zan fara zuwa neman makarantar, in Sha Allah zanyi kokarin ganin an samu, duk da ma anci term daya amma hakan zaki shiga ciki, sai kiyi kokari sosai ki kamo su."
Murna na hau yi sosai kamar zanyi rawa, hannun sa ya rataye a saman kirjin sa yana kallo na, sauka nayi na jawo littafan da muke karatu dasu na fara jera su daya bayan daya. Be yi magana ba, sai murmushi kawai yake. Chan ya mike da sauri yana dafa kai, shaf yaso mantawa da tafiyar Mummy, abinda ma ya tashe shi da wurwuri kenan. Fita yayi yaja min kofar na cigaba da hada littafan cike da farin ciki.
***Har airport ya rakata, ba zatayi tafiyar mota ba wannan karon wai Lagos zata wuce akan wani kasuwancin ta, dole sai dai driver nata yabi bayan ta a mota ya koma gida, sanda suka isa ta kara jaddada masa alkawarin su, amsa mata yayi da toh da haka sukayi sallama. Be koma gidan ba, sai kawai ya bazama neman makarantar da zatayi daidai da Aminatun sa, makaranta yake so me kyau me tsada wadda zata taimaka mata kwarai wajen cikar burin ta, be damu da ko nawa za'a kashe ba, kudin da ya karba wajen Mummy da wanda yake dashi dana Daddy zasu ishe shi komai. Shi dai kawai ya samu ya tabbatar yayi wa dukkan su abinda suke so ba tare da ya fifita daya ba. Sai yamma sannan ya samu ya gama wasu abubuwan, duk da ba dukka ya gama ba amma yaci karfin komai, ya samu makarantar da tayi masa, har ma sun bashi damar ya kawo ta interview. A gajiye ya shiga gida, sallah kawai yayi yaci abinci ya sake shiryawa ya fita, gidan su ya wuce kai tsaye dan yana so su sake magana da mahaifiyar ta, a kafa ya taka a hankali kunnen sa sakale da earpiece suna magana da Ja'afar, har ya kusa karasawa gidan suna magana yana fada mishi yadda komai yake tafiya a gida. Daga nesa kadan yaga ta fito, cikin zulumi, kallo daya zakayi mata kasan ba a nutse take ba, da sauri ya kashe wayar yana kokarin tsaida ta yaga ta kara sauri, har zai juya sai kuma yayi tunanin ko babu lafiya, da sauri yabi bayan ta don tabbatar da babu wata matsala dan yanayin ta kawai ya nuna ba kalou ba. Tafiya take tayi hakan kuma shima be fasa bin nata ba, kamar daga sama ta hango Harira tana nufo ta, ja tayi ta tsaya jikin wata bishiya har ta ƙaraso, ganin haka yasa yayi kokarin juyawa, sai dai kalmar da yaji yasa shi dakatawa yana kokarin ganin yaji komai
"Wai Menene wannan kiran haka, kinga fa shiyasa kawai na yanke shawarar fitowa mu hadu a hanya dan yan gidan ma har sun fara zargin wani abu. " Hariran ta fada tana karasowa.
"Maganar Aminatu ce kin sani ai, fisabilillah bayan kin min alƙawarin ko wata biyu ba za'a yi ba zai sauta ta dawo gida, shiru kake ji gashi ana maganar watanni biyar, kinsan me hakan zai haifar nan gaba."
"Toh nidai bansan ina matsalar take ba, a gabanki na dauki kudin na bawa malam Tsalha da zauren gidan mu, ya tabbatar mana da ba za'a dau lokaci ba, toh ni bansan ina matsalar kuma take ba."
"Ni duk ba wannan ba, yanzu gaba daya bani da kwanciyar hankali wallahi, ni idan zai yiwu kawai ki nemo Hajiyar nan, ayi magana, ta in da ake hawa ta nan ake sauka, na fasa wallahi gwara su karbi yar su."
"Kamar ya? Abinda aka yi yarjejeniya, da zarar yaron nan ya kai matsayin da ake so ya kai din, sai ayi komai cikin sauki, amma yanzu daga farawa kice kin gaji, me ma akayi?"
"Ba zaki gane ba, dalilin baki san yadda yaya suke a zuciyar iyayensu ba, ni kam gaskiya ba zan iya ba, nayi nadamar abinda kika sani na aikata, yanzu zuwa zakiyi ki bani addireshin su, na je na same su a warware komai, na maida musu da yar su, tun kafin ranar da nadama ta ba zatayi min amfani ba."
Wani banzan kallo Harira tayi mata
"Amma dai kamar ba a hayyacin ki kike ba ko? Kar ki manta su waye mutanen da kike cewa zaki je, kina tunanin zasu tsaya sauraren ki? Bayan haka ma wacce hujja kike da ita da zaki nuna musu?"
"Jini ba karya bane Harira, wallahi suna ganin Aminatu ko ba'a fada ba zasu gane tasu ce, bayan haka kinsan dai ina da hoton mijin dana matar da muka dauka a saman file din asibitin su."
Dariya Harira ta saka sosai hadda tafa hannu
"Lallai Innaro, bansan ma kwata kwata tunanin ki baya ja ba sai yau, kinsan kuwa me kike shirin yi? Ina tabbatar miki da kina zuwa zasu kamaki su rufe ki, daga ke har zuri'ar ki kuwa babu wanda zai tsira."
"Ki fuskance ni, akwai matsala ne idan aka cigaba a haka, wadda zamu shiga sai tafi ya yanzu wallahi, idan muka samu yaron nan ya tsinke igiyar auren, sai mu tattara mu mayar musu da yar su, in yaso ita matar data tsara komai sai su kare chan, nidai Buri na d'ana ya dawo, rashin sa ya fara tabani. Nayi nadamar komai wallahi."
"Da kika gama kafa kanki da kudin da kika karba ba, ke fa wallahi san kanki yayi yawa, wato kinci moriyar ganga ko, toh bari kiji in fada miki gaskiyar magana, bansan in da suke ba, bansan aina za'a same su ba, rabona da su tun sanda muka rabu a asibiti, na yagi rabona, bayan wannan bansan komai akan su ba, ke wallahi ko sunan su ban sani ba, na sai tuna sanda Hajiyar take fada mana sunan da take so a sawa jaririyar, Aminatu MD. Daga wannan bansan komai akan su ba."
Wani irin kukan kura Inno tayi ta damki wuyan Harira, tuni kokawa ta rikice tsakanin su. Farouk dake tsaye a gefe yayi mutuwar tsaye tun sanda ya fara jin komai har zuwa sanda abubuwan suka dau zafi. Sosai maganar ta taɓa shi, wani irin mugun tausayin ta ya kara dirar masa fiye da wanda yake ji a baya, an cuci rayuwar ta, an raba ta da gatan ta, sai dai ya kasa gane dalilin daya sa suka aikata hakan, kenan babu sanin mahaifanta, toh wacece wannan data zabi rayuwar yarinyar ta lalace akan wani banzan burin ta mara tushe. Ya kasa gano hakan sai dai ya dau alwashin sai ya tabbatar da duk ya warware wannan daurin, ko da kuwa hakan na nufin....
Jin yadda suke abu kamar yara ne yasa shi magana cikin tsawa dan ba karamin bata masa rai sukayi ba.
"Ku dakata!"
A firgice suka juyo, wani irin bugawa kirjin Inno yayi, ta ɗora hannu a kanta kamar zata fasa ihu
"Yanzu kune kuke kiran kanku matsayin iyaye? Masu tarbiyyar yayan su? Tir daku wallahi."
"Faruku... Tsaya kaji, duk ba abinda kake tunani bane wallahi, yaudara ta akayi..." Katse ta yayi cikin tsananin bacin rai
"Babu sauran girmamawa ko mutuntawa a tsakanin mu. A dah ina miki kallon uwa ne, wadda tasan ciwon kanta dana ya'yan ta, ina ganin girman ki,a matsayin wadda ta kawo Aminatu duniya. Sai dai a yanzu babu ɗaya daga cikin wannan da zai sa na cigaba da ganin girman naki, ki sani a yau ni Farouk, ni zan zame wa Aminatu uwa, uba da dukkan gatan ta, har zuwa lokacin da zan hada ta da iyayen ta, babu kuma daya daga cikin ku da ya isa ya raba auren mu, ƙaddara ce ta haɗa mu, kuma babu wani mutum da ya isa ya raba."
Yana kaiwa nan ya juya a zafafe ya bar wajen, kwala masa kira take cike da tashin hankali, amma babu alamun zai tsaya balle ya saurare ta,kallo Harira tayi cike da tsana tace
"Sai kin yi dana sanin abinda kika aikata min."
Dariya ta saka harda tafa hannu tace
"Ko ke kiyi dana sani ba, uwar yan son zuciya ai nice maganin irin ku."
RanoHafsat Rano
(10)
***
Rai a bace ya shigo gidan, muka bishi da kallo nida Dada, be tanka ba, dan ko sallama a ciki ciki yayi ta yayi saurin wucewa dakin sa, yana zuwa ya maida mukullin kofar ya rufe, shiru mukayi baki daya babu wanda yayi motsi, ni a raina mamakin abinda ya sashi wannan tsananin fushin haka nake, ita kuwa Dadah ina kyautata zaton tasan tabbas koma menene akayi mishi ba karami bane. Har dare be fito ba, naje na buga dakin nasa yafi sau nawa baya budewa, duk na rasa ina zaka saka raina. Komawa nayi na shige cikin kujera nayi lamo na kasa ko cin abinci. Ina kwance na fara kuka kasa kasa, bansan dalilin kukan nawa ba, kila hakan na da na saba da yunwar da ke nukurkusata ne, jin karar bude dakin sa yasa nayi saurin tashi, shi dinne ya fito cikin shigar kananan kaya, fuskar sa tayi fayau kamar wanda yayi ciwo, tashi nayi na zauna sosai ban bar hawayen dake zuba a fuskata ba ya karasa sauka. Da sauri ya ƙaraso gareni ya zauna yana leka fuska ta
"Kuka?" Ya tambaya yana mamaki.
Daga masa kai nayi ina sake matsar kwallar.
"Menene?" Ya furta yana matsar da hannu na daga fuskar tawa, goge min hawayen ya shiga yi yana girgiza min kai.
"Karki kara kuka kinji? Babu abinda zai sake faruwa."
"Ouch, kai kika min haka?" Ya tambaya yana taba idon nasa
"Abu zan cire maka fah."
"Karya ne."
"Da gaske." Na saka dariya ina matsawa. Riko ni yayi ya dawo dani kusa dashi.
"Kina son kiyi karatu ko?"
Da sauri na daga masa kai na
"Good... Zan saki a makaranta. Kina so?"
"Ina so wallahi." Na faɗa cike da murna
"Ok Tam, zan saki amma sai kinyi min alƙawarin zaki yi karatu sosai, sosai."
"Zanyi Allah."
"Good."
"Toh yaushe zaka sani, kuma aina makarantar take."
Shafa kansa yayi alamar tunani kafin yace
"Yau zan fara zuwa neman makarantar, in Sha Allah zanyi kokarin ganin an samu, duk da ma anci term daya amma hakan zaki shiga ciki, sai kiyi kokari sosai ki kamo su."
Murna na hau yi sosai kamar zanyi rawa, hannun sa ya rataye a saman kirjin sa yana kallo na, sauka nayi na jawo littafan da muke karatu dasu na fara jera su daya bayan daya. Be yi magana ba, sai murmushi kawai yake. Chan ya mike da sauri yana dafa kai, shaf yaso mantawa da tafiyar Mummy, abinda ma ya tashe shi da wurwuri kenan. Fita yayi yaja min kofar na cigaba da hada littafan cike da farin ciki.
***Har airport ya rakata, ba zatayi tafiyar mota ba wannan karon wai Lagos zata wuce akan wani kasuwancin ta, dole sai dai driver nata yabi bayan ta a mota ya koma gida, sanda suka isa ta kara jaddada masa alkawarin su, amsa mata yayi da toh da haka sukayi sallama. Be koma gidan ba, sai kawai ya bazama neman makarantar da zatayi daidai da Aminatun sa, makaranta yake so me kyau me tsada wadda zata taimaka mata kwarai wajen cikar burin ta, be damu da ko nawa za'a kashe ba, kudin da ya karba wajen Mummy da wanda yake dashi dana Daddy zasu ishe shi komai. Shi dai kawai ya samu ya tabbatar yayi wa dukkan su abinda suke so ba tare da ya fifita daya ba. Sai yamma sannan ya samu ya gama wasu abubuwan, duk da ba dukka ya gama ba amma yaci karfin komai, ya samu makarantar da tayi masa, har ma sun bashi damar ya kawo ta interview. A gajiye ya shiga gida, sallah kawai yayi yaci abinci ya sake shiryawa ya fita, gidan su ya wuce kai tsaye dan yana so su sake magana da mahaifiyar ta, a kafa ya taka a hankali kunnen sa sakale da earpiece suna magana da Ja'afar, har ya kusa karasawa gidan suna magana yana fada mishi yadda komai yake tafiya a gida. Daga nesa kadan yaga ta fito, cikin zulumi, kallo daya zakayi mata kasan ba a nutse take ba, da sauri ya kashe wayar yana kokarin tsaida ta yaga ta kara sauri, har zai juya sai kuma yayi tunanin ko babu lafiya, da sauri yabi bayan ta don tabbatar da babu wata matsala dan yanayin ta kawai ya nuna ba kalou ba. Tafiya take tayi hakan kuma shima be fasa bin nata ba, kamar daga sama ta hango Harira tana nufo ta, ja tayi ta tsaya jikin wata bishiya har ta ƙaraso, ganin haka yasa yayi kokarin juyawa, sai dai kalmar da yaji yasa shi dakatawa yana kokarin ganin yaji komai
"Wai Menene wannan kiran haka, kinga fa shiyasa kawai na yanke shawarar fitowa mu hadu a hanya dan yan gidan ma har sun fara zargin wani abu. " Hariran ta fada tana karasowa.
"Maganar Aminatu ce kin sani ai, fisabilillah bayan kin min alƙawarin ko wata biyu ba za'a yi ba zai sauta ta dawo gida, shiru kake ji gashi ana maganar watanni biyar, kinsan me hakan zai haifar nan gaba."
"Toh nidai bansan ina matsalar take ba, a gabanki na dauki kudin na bawa malam Tsalha da zauren gidan mu, ya tabbatar mana da ba za'a dau lokaci ba, toh ni bansan ina matsalar kuma take ba."
"Ni duk ba wannan ba, yanzu gaba daya bani da kwanciyar hankali wallahi, ni idan zai yiwu kawai ki nemo Hajiyar nan, ayi magana, ta in da ake hawa ta nan ake sauka, na fasa wallahi gwara su karbi yar su."
"Kamar ya? Abinda aka yi yarjejeniya, da zarar yaron nan ya kai matsayin da ake so ya kai din, sai ayi komai cikin sauki, amma yanzu daga farawa kice kin gaji, me ma akayi?"
"Ba zaki gane ba, dalilin baki san yadda yaya suke a zuciyar iyayensu ba, ni kam gaskiya ba zan iya ba, nayi nadamar abinda kika sani na aikata, yanzu zuwa zakiyi ki bani addireshin su, na je na same su a warware komai, na maida musu da yar su, tun kafin ranar da nadama ta ba zatayi min amfani ba."
Wani banzan kallo Harira tayi mata
"Amma dai kamar ba a hayyacin ki kike ba ko? Kar ki manta su waye mutanen da kike cewa zaki je, kina tunanin zasu tsaya sauraren ki? Bayan haka ma wacce hujja kike da ita da zaki nuna musu?"
"Jini ba karya bane Harira, wallahi suna ganin Aminatu ko ba'a fada ba zasu gane tasu ce, bayan haka kinsan dai ina da hoton mijin dana matar da muka dauka a saman file din asibitin su."
Dariya Harira ta saka sosai hadda tafa hannu
"Lallai Innaro, bansan ma kwata kwata tunanin ki baya ja ba sai yau, kinsan kuwa me kike shirin yi? Ina tabbatar miki da kina zuwa zasu kamaki su rufe ki, daga ke har zuri'ar ki kuwa babu wanda zai tsira."
"Ki fuskance ni, akwai matsala ne idan aka cigaba a haka, wadda zamu shiga sai tafi ya yanzu wallahi, idan muka samu yaron nan ya tsinke igiyar auren, sai mu tattara mu mayar musu da yar su, in yaso ita matar data tsara komai sai su kare chan, nidai Buri na d'ana ya dawo, rashin sa ya fara tabani. Nayi nadamar komai wallahi."
"Da kika gama kafa kanki da kudin da kika karba ba, ke fa wallahi san kanki yayi yawa, wato kinci moriyar ganga ko, toh bari kiji in fada miki gaskiyar magana, bansan in da suke ba, bansan aina za'a same su ba, rabona da su tun sanda muka rabu a asibiti, na yagi rabona, bayan wannan bansan komai akan su ba, ke wallahi ko sunan su ban sani ba, na sai tuna sanda Hajiyar take fada mana sunan da take so a sawa jaririyar, Aminatu MD. Daga wannan bansan komai akan su ba."
Wani irin kukan kura Inno tayi ta damki wuyan Harira, tuni kokawa ta rikice tsakanin su. Farouk dake tsaye a gefe yayi mutuwar tsaye tun sanda ya fara jin komai har zuwa sanda abubuwan suka dau zafi. Sosai maganar ta taɓa shi, wani irin mugun tausayin ta ya kara dirar masa fiye da wanda yake ji a baya, an cuci rayuwar ta, an raba ta da gatan ta, sai dai ya kasa gane dalilin daya sa suka aikata hakan, kenan babu sanin mahaifanta, toh wacece wannan data zabi rayuwar yarinyar ta lalace akan wani banzan burin ta mara tushe. Ya kasa gano hakan sai dai ya dau alwashin sai ya tabbatar da duk ya warware wannan daurin, ko da kuwa hakan na nufin....
Jin yadda suke abu kamar yara ne yasa shi magana cikin tsawa dan ba karamin bata masa rai sukayi ba.
"Ku dakata!"
A firgice suka juyo, wani irin bugawa kirjin Inno yayi, ta ɗora hannu a kanta kamar zata fasa ihu
"Yanzu kune kuke kiran kanku matsayin iyaye? Masu tarbiyyar yayan su? Tir daku wallahi."
"Faruku... Tsaya kaji, duk ba abinda kake tunani bane wallahi, yaudara ta akayi..." Katse ta yayi cikin tsananin bacin rai
"Babu sauran girmamawa ko mutuntawa a tsakanin mu. A dah ina miki kallon uwa ne, wadda tasan ciwon kanta dana ya'yan ta, ina ganin girman ki,a matsayin wadda ta kawo Aminatu duniya. Sai dai a yanzu babu ɗaya daga cikin wannan da zai sa na cigaba da ganin girman naki, ki sani a yau ni Farouk, ni zan zame wa Aminatu uwa, uba da dukkan gatan ta, har zuwa lokacin da zan hada ta da iyayen ta, babu kuma daya daga cikin ku da ya isa ya raba auren mu, ƙaddara ce ta haɗa mu, kuma babu wani mutum da ya isa ya raba."
Yana kaiwa nan ya juya a zafafe ya bar wajen, kwala masa kira take cike da tashin hankali, amma babu alamun zai tsaya balle ya saurare ta,kallo Harira tayi cike da tsana tace
"Sai kin yi dana sanin abinda kika aikata min."
Dariya ta saka harda tafa hannu tace
"Ko ke kiyi dana sani ba, uwar yan son zuciya ai nice maganin irin ku."
RanoHafsat Rano
(10)
***
Rai a bace ya shigo gidan, muka bishi da kallo nida Dada, be tanka ba, dan ko sallama a ciki ciki yayi ta yayi saurin wucewa dakin sa, yana zuwa ya maida mukullin kofar ya rufe, shiru mukayi baki daya babu wanda yayi motsi, ni a raina mamakin abinda ya sashi wannan tsananin fushin haka nake, ita kuwa Dadah ina kyautata zaton tasan tabbas koma menene akayi mishi ba karami bane. Har dare be fito ba, naje na buga dakin nasa yafi sau nawa baya budewa, duk na rasa ina zaka saka raina. Komawa nayi na shige cikin kujera nayi lamo na kasa ko cin abinci. Ina kwance na fara kuka kasa kasa, bansan dalilin kukan nawa ba, kila hakan na da na saba da yunwar da ke nukurkusata ne, jin karar bude dakin sa yasa nayi saurin tashi, shi dinne ya fito cikin shigar kananan kaya, fuskar sa tayi fayau kamar wanda yayi ciwo, tashi nayi na zauna sosai ban bar hawayen dake zuba a fuskata ba ya karasa sauka. Da sauri ya ƙaraso gareni ya zauna yana leka fuska ta
"Kuka?" Ya tambaya yana mamaki.
Daga masa kai nayi ina sake matsar kwallar.
"Menene?" Ya furta yana matsar da hannu na daga fuskar tawa, goge min hawayen ya shiga yi yana girgiza min kai.
"Karki kara kuka kinji? Babu abinda zai sake faruwa."