Sashe 4
Darasi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata shaƙa babban nasu ya kawo min tare da duka na akai nan da nan na daina ganin komai sai duhu,saurin ɗaukata suka yi da ya ke dare ne babu wanda ya gansu suka shiga dani wani kango.
"Kai ba-ba ya zamuyi da wannan yarinyar kada fa a kamamu".?
"au tsoron kamen ka
Ke kai" ?,kawai mu ƙwashi rabonmu mu mu wuce mu bar ƴar talla masu son kuɗin jaraba ai daman ƙarshen son kuɗi kenan",ya faɗi hakan yana lashe bakinsa.
"Haba Amma ta ya ya zaki ƙwanta ki yi ta bacci amman kuma ƴarki bata dawo ba har yanzu?ki duba agogo ƙarfe goma na dare fa?gaskiya Amma wannan mummunar ɗabi'ar da ki ka ɗakko ba za ta haifa miki ɗa mai ido ba",yana faɗar hakan ya yi hanyar waje yana cigaba da mitarsa kamar zai cinye ta,amman matar nan Ƙara juyawarta ta yi tana baccinta har da minshari,Haruna ma da ya ke ƙarami kuka ya dinga kuka ganin Fahima bata dawo ba,don ya saba ita ke kaishi ya yi fitsari.
A hankali ya ke tafiya yana ɗan duba lungu2 na layinsu,ƙwatsam ya hango wani lungu,ci ke da ƴan daba suna shawarwari a tsakaninsu akan su aikata mata ko kada suyi.
Shahada ya yi yaje wajen ya haskosu da babbar fitilarsa,da sauri suka jiyo dukkansu kana ganinsa kasan shine mahaifin yarinyar nan don har hasken da ƙyau irin na fulani duk na shi ne.
"Aha kace kazo ne ka karɓi ƴar ka ko"?.
sai suka tuntsire da wata mahaukaciyar dariya suna nuna baban Fahima.
Kukan kura ya yi ya bige mutum biyu Alokaci guda da ya ke sun bugu sosai suka zube a wajen,saura mutum biyu,da sauri ya yo kansu suma suka fita da gudu,ya tsugunna yana hawaye har sun fara yagawa Fahima kayanta abin tausayi.
Kawai sai yaji saukar wani abu a bayansa tun daga nan bai ƙara sanin inda ya ke ba.
*** *** ***
Da wuri Sakinat ta dira a garin yola babban birnin adamawa,tana sanye da glass baƙi no respect wanda ya gaji da haɗuwa yana sheƙi da walwali.
Ta saka ƙananun kaya komai na jikinta ana gani ita daman ƙirar slindium ne da ita babu cinya babu sharaɓa sai fari wanda har yawa ya yi mata saboda bleaching.
Chewin gum ne abakinta tana taunarsa yana ƙara ƙara ras-ƙara ras,alamar za ta yi rashin mutunci kenan .
Bata sha wahalar gane gidansu Ammar ba don rabonta da zuwa shekara shida kenan,kallon gidan ta ke tana ya mutsa fuskarta,taja trolley ɗinta tana wani yauƙi da yanga kamar mutanen gidan suna kallonta.
Hanan tana sama tana hango ta,da sauri ta sauko don ba ta son Ammi tasan abinda zai faru don wallahi ba za ta bari wannan matar ta shigo musu gida ba,suna cikin farin cikinsu ta kawo musu baƙin ciki.
"Ke makira ina zaki"?.
Hanan ta faɗi hakan tana ɗaga mata gira tare da tare hanya.
Wani banzan kallo Sakinat ta yi mata ta cire gilashinta tana kallonta ta ƙasan glass ɗin, sannan ta ce"Hmm Hanno ki ke ko wa?to ma dai ko me ye sunanki?,ko wannan siririyar bafulata na bata isa ta ce za ta hanani shiga wannan ruɓaɓɓan gidanba wanda ko albarkacin fenti ba ya samu.
Idanun Hanan suka yi jawur jin zagin rashin mutuncin da Sakinat ta ke musu,da sauri ta nuna Sakinat da hannu ta ce"Hmm da ba asan asalin balbela ba da sai ta ce daga misra ta ke,ke kin manta gidan na ki uban ko albarkacin siminti bana tunanin ya samu"?.
"kuma kinga gidannan kaf babu siriri sai wannan makauniyar uwar ta ki wacce har ta mutu bata gani saboda baƙin cikinki dana wannan baƙin basa muden uban na ki,kuma kaf gidan na mu babu wanda ya fito ba ta hanya ta halak ba,wani kuwa sai da a kayi cikinsa sannan aka yi aure. . .
Cikin matsanancin fushi Sakinat ta kaiwa Hanan wani mari,Hanan ta shafa wajen da hannunta ta ce"ko yanzu Sakinat na fiki cin ribar zance tunda gashi har kinyi mari saboda fusata,amman fa baki mari banza ba don ba a marin wannan ƙyaƙyawar fuskar tawa a zauna lafiya ko mijinki ne kuwa ballan tana ma ke."
wani mari Hanan ta kaiwa Sakinat wanda sai da yasa ta riƙe hannun ƙofar shiga farlon,wata shaƙa Sakinat ta kaiwa Hanan,ta kama maƙogoron ta Hanan ta kama kararin mutuwa,Ammi ta fito za ta gidan barka ta hango abinda ya ke faruwa.
Da sauri ta ƙaraso tana rabasu tana mamakin ƙarfin hali irin na Sakinat,sa ƙer Ammi ta ɓanɓare Hanan ta ƙwanta luf a hannun Ammi kamar ba ta numfashi.
Sakinat tayo kan Ammi za ta haɗasu duka,suka jiyo sallama Ammi na kallon tsinanniyar shigar da Sakinat ta yi wai a matsayin matar Aure matar ɗanta tilo.
Amir ne da matarsa har da ƴaƴansa biyu,sosai sukayi mamakin ganin Sakinat a gidansu Ammar don sun san takun saƙar da ke tsakaninsu.
Amir ya ce"Ammi lfy me ya samu Hanan ɗin?wani abu ne ya same ta?."
gaba ki ɗaya ya tambayeta,Ammi ta shaida masa duk abinda ta gani a lokacin da tazo,bata gama ƙarasawa ba me gayya me aiki ya fito yana sanye da kayan motsa jiki don bai san abinda ya ke faruwa ba,yana zuwa Sakinat ta saki kuka ta faɗa jikinsa kamar ƴar yarinya.
*** *** ***
A wajen mahaifin Fahima ya faɗi baya motsi,ƴan patrol suka zo wucewa suka hango ƴan daban nan suna Ɗaukar Fahima,da sauri suka zo wajen suna zuwa suka arce da gudu amman an kama guda ɗaya.
Aka kai su Fahima asibiti aka fara yi musu taimakon gaggawa,sai dai mahaifin Fahima har yanzu bai farfaɗo ba amman Fahima ta farfaɗo.
Allah sai kun fara comments zan fara yin sa da yawa.
*Miss green ce*
*DARASI!!*
Free page 8/9
Rabiatu Bashir
(ummu maher)miss green.
*Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu ta online zasu biya 2k*
08/09
. . . . .har yanzu mahaifina bai farfaƊo daga suman da ya yi ba,sai dai yana numfashi,hankali na ya tashi sosai don likitoci sun faɗamin Mu biyu aka kawo mu ni da mahaifina,kuma tunda aka kawo mu ƴan sintirin da suka kawo mu sune suke biyan kuɗin.
Amma tana gidan goggo mahaifiyarta sai faɗa ta ke mata na rashin mutuncin da ke yi,gashi yanzu daga ni har mahaifina babu mu babu labarinmu,sharce hawaye ta yi da majina ta ce"wallahi Goggo ni fa ban san yadda a kayi yarinyar na neme ta na rasa ba,daga tura ta talla tun jiya bata dawo ba,idan zubarda kuɗin tallan ta yi ta dawo mana,shi kuma Malam da karan baninsa ya tafi nemo ta,gashi yanzu babu labarinsu su duka".sai ta cigaba da kukanta.
Tun da ta fara maganar Goggo ke yi mata wani banzan kallo,sai da ta gama sannan ta ce"wai ni kuwa Amaturrahman kina da kirki kuwa?"cewa fa ki ka yi wai mahaifinta ya yi karanbani?shi da ƴarsa sai yaƙi fita nemanta saboda sakaci da kuma rashin hankali?,ke irin wannan riƙon na yi miki a rayuwarki?tambayar ki na ke yi?".kamar za ta daki Amma ranar ta yi suna cikin wannan halin ne a kayi sallama a ƙofar gida.
Kallon banza Goggo ta yiwa Amma sannan ta ce"w/kslm waye?".ta ɗauki mayafinta ta leƙa.
Salati ta fara yi tana kiran sunan Allah tana cewa"to shikken Mlm Bashir yanzu zamu taho insha Allah",da sauri ta dawo tana faɗawa Amma wai ƴan sintiri ne jiya suka kai su Fahima da mahaifinta asibiti,kuma tunda safe akaje cen gidan Amma ba a sameta ba,shine Bashir ya ce yasan kina nan gidan.
Bakin Amma bai mutu ba da abinda ya faru da mijinta da ƴar ta ba sai cewa ta yi"Hmm su Bashir an riƙa wajen iya gulma yanzu har yasan nan na taho?".
lokacin har Goggo ta saka hijabi ta ɗakko kuɗi ta ɗaure a bakin zaninta"ta ce to maras tunani idan kin gama gulmar mutane ki tashi mu tafi?wa wiya kawai mara tunani,har a wannan halin da ake ciki bakin ki bai mutu ba".
*** *** ***
abin mamaki Sakinat tana fara kuka hankalin Ammar ya tashi,ya kalli Khalisat da ke jikin Mahaifiyarsa tana kuka ya daka mata wata uwar tsawa ya ce"shut up!ki yiwa mutane shiru munafuka wato daman bakya son matata ko?to wallahi ko waye zai ƙi matata ko waye wallahi tallahi saina rabu dashi".ya faɗi hakan cikin yaran fillanci ya riƙe hannun Sakinat suka yi wuce warsu,Sakinat harda wani la fewa ajikin Mijinta tana yiwa su Ammi gwalo.
Ni kuwa na ce oh Sakinat kamar abin arziƙi haɗa ɗa da uwa,Duniya ina zaki damu😭.ya Allah ka haɗa mu da surukan arziƙi Amin.
Sororo Ammi ta yi tana kallon bayan ɗanta Ammar,shi kuma tasa ƙaddarar kenan mace,jiya i yanzu yana tare da ƙanwarsa suna hira kamar abin arziƙi,amman yau daga zuwan matarsa har komai ya watse.
Wasu zafafan hawaye ne ya fara zubowa Ammi a ƙwarmin idanunta, bata san sanda Khalisat ta saka hannu ta fara share mata hawaye ba,ita ma Khalisat ɗin kuka ta ke na tausayin kansu"Ammi ki yi haƙuri don Allah kinji,komai ya yi farko yana da ƙarshe kada ki saka wannan abin a ranki kinji?".rungume junansu sukayi suna tausayin kansu dana Ammar.
Har sun manta da tsayuwar Amir sai da sukaji yana cewa"haƙiƙa Sakinat ba ƙaramar butulu ba ce da ta manta,da duk abin arziƙin da ki ka yi mata ta butulce miki,ta zaɓi taci miki mutunci ta kassara miki rayuwaɓ,ta zaɓi hanyar musguna miki ta hanyar mallake miki ɗanki,amman babu komai aƙwai Allah."
Matar Amir ma har kuka ta yi don ganin abinda ya faru,tana yawan ji a littafin hausa da sauran kafofi yadda ƴaƴa suke wulaƙanta iyayensu, amman bata taɓa gani da idanun ta ba sai yau.
a ranar Sakinat ta saka mijinta a gaba kamar mayya suka tafi Abuja,shi kuwa Amir saboda haushi daman alokacin ya tafi gida,saboda takaicin hali irin na Ammar ace ka rasa wanda zaka ƙunta tawa a rayuwarka sai mahaifiyarka wacce tasha wahala a rayuwarta don rayuwarka ta ginu?gaskiya abin aƙwai lauje cikin naɗi.
Ranar gidan Ammi kamar ana zaman makoki,gidan shiru don ɗan wannan zuwan da Ammar ya yi komai sun ƙara shaƙuwa sosai,ranar kusan raba dare Ammi da Khaisat sukayi suna kaiwa Allah kukansu ta hanyar yin nafilfilu.
"Kai ba-ba ya zamuyi da wannan yarinyar kada fa a kamamu".?
"au tsoron kamen ka
Ke kai" ?,kawai mu ƙwashi rabonmu mu mu wuce mu bar ƴar talla masu son kuɗin jaraba ai daman ƙarshen son kuɗi kenan",ya faɗi hakan yana lashe bakinsa.
"Haba Amma ta ya ya zaki ƙwanta ki yi ta bacci amman kuma ƴarki bata dawo ba har yanzu?ki duba agogo ƙarfe goma na dare fa?gaskiya Amma wannan mummunar ɗabi'ar da ki ka ɗakko ba za ta haifa miki ɗa mai ido ba",yana faɗar hakan ya yi hanyar waje yana cigaba da mitarsa kamar zai cinye ta,amman matar nan Ƙara juyawarta ta yi tana baccinta har da minshari,Haruna ma da ya ke ƙarami kuka ya dinga kuka ganin Fahima bata dawo ba,don ya saba ita ke kaishi ya yi fitsari.
A hankali ya ke tafiya yana ɗan duba lungu2 na layinsu,ƙwatsam ya hango wani lungu,ci ke da ƴan daba suna shawarwari a tsakaninsu akan su aikata mata ko kada suyi.
Shahada ya yi yaje wajen ya haskosu da babbar fitilarsa,da sauri suka jiyo dukkansu kana ganinsa kasan shine mahaifin yarinyar nan don har hasken da ƙyau irin na fulani duk na shi ne.
"Aha kace kazo ne ka karɓi ƴar ka ko"?.
sai suka tuntsire da wata mahaukaciyar dariya suna nuna baban Fahima.
Kukan kura ya yi ya bige mutum biyu Alokaci guda da ya ke sun bugu sosai suka zube a wajen,saura mutum biyu,da sauri ya yo kansu suma suka fita da gudu,ya tsugunna yana hawaye har sun fara yagawa Fahima kayanta abin tausayi.
Kawai sai yaji saukar wani abu a bayansa tun daga nan bai ƙara sanin inda ya ke ba.
*** *** ***
Da wuri Sakinat ta dira a garin yola babban birnin adamawa,tana sanye da glass baƙi no respect wanda ya gaji da haɗuwa yana sheƙi da walwali.
Ta saka ƙananun kaya komai na jikinta ana gani ita daman ƙirar slindium ne da ita babu cinya babu sharaɓa sai fari wanda har yawa ya yi mata saboda bleaching.
Chewin gum ne abakinta tana taunarsa yana ƙara ƙara ras-ƙara ras,alamar za ta yi rashin mutunci kenan .
Bata sha wahalar gane gidansu Ammar ba don rabonta da zuwa shekara shida kenan,kallon gidan ta ke tana ya mutsa fuskarta,taja trolley ɗinta tana wani yauƙi da yanga kamar mutanen gidan suna kallonta.
Hanan tana sama tana hango ta,da sauri ta sauko don ba ta son Ammi tasan abinda zai faru don wallahi ba za ta bari wannan matar ta shigo musu gida ba,suna cikin farin cikinsu ta kawo musu baƙin ciki.
"Ke makira ina zaki"?.
Hanan ta faɗi hakan tana ɗaga mata gira tare da tare hanya.
Wani banzan kallo Sakinat ta yi mata ta cire gilashinta tana kallonta ta ƙasan glass ɗin, sannan ta ce"Hmm Hanno ki ke ko wa?to ma dai ko me ye sunanki?,ko wannan siririyar bafulata na bata isa ta ce za ta hanani shiga wannan ruɓaɓɓan gidanba wanda ko albarkacin fenti ba ya samu.
Idanun Hanan suka yi jawur jin zagin rashin mutuncin da Sakinat ta ke musu,da sauri ta nuna Sakinat da hannu ta ce"Hmm da ba asan asalin balbela ba da sai ta ce daga misra ta ke,ke kin manta gidan na ki uban ko albarkacin siminti bana tunanin ya samu"?.
"kuma kinga gidannan kaf babu siriri sai wannan makauniyar uwar ta ki wacce har ta mutu bata gani saboda baƙin cikinki dana wannan baƙin basa muden uban na ki,kuma kaf gidan na mu babu wanda ya fito ba ta hanya ta halak ba,wani kuwa sai da a kayi cikinsa sannan aka yi aure. . .
Cikin matsanancin fushi Sakinat ta kaiwa Hanan wani mari,Hanan ta shafa wajen da hannunta ta ce"ko yanzu Sakinat na fiki cin ribar zance tunda gashi har kinyi mari saboda fusata,amman fa baki mari banza ba don ba a marin wannan ƙyaƙyawar fuskar tawa a zauna lafiya ko mijinki ne kuwa ballan tana ma ke."
wani mari Hanan ta kaiwa Sakinat wanda sai da yasa ta riƙe hannun ƙofar shiga farlon,wata shaƙa Sakinat ta kaiwa Hanan,ta kama maƙogoron ta Hanan ta kama kararin mutuwa,Ammi ta fito za ta gidan barka ta hango abinda ya ke faruwa.
Da sauri ta ƙaraso tana rabasu tana mamakin ƙarfin hali irin na Sakinat,sa ƙer Ammi ta ɓanɓare Hanan ta ƙwanta luf a hannun Ammi kamar ba ta numfashi.
Sakinat tayo kan Ammi za ta haɗasu duka,suka jiyo sallama Ammi na kallon tsinanniyar shigar da Sakinat ta yi wai a matsayin matar Aure matar ɗanta tilo.
Amir ne da matarsa har da ƴaƴansa biyu,sosai sukayi mamakin ganin Sakinat a gidansu Ammar don sun san takun saƙar da ke tsakaninsu.
Amir ya ce"Ammi lfy me ya samu Hanan ɗin?wani abu ne ya same ta?."
gaba ki ɗaya ya tambayeta,Ammi ta shaida masa duk abinda ta gani a lokacin da tazo,bata gama ƙarasawa ba me gayya me aiki ya fito yana sanye da kayan motsa jiki don bai san abinda ya ke faruwa ba,yana zuwa Sakinat ta saki kuka ta faɗa jikinsa kamar ƴar yarinya.
*** *** ***
A wajen mahaifin Fahima ya faɗi baya motsi,ƴan patrol suka zo wucewa suka hango ƴan daban nan suna Ɗaukar Fahima,da sauri suka zo wajen suna zuwa suka arce da gudu amman an kama guda ɗaya.
Aka kai su Fahima asibiti aka fara yi musu taimakon gaggawa,sai dai mahaifin Fahima har yanzu bai farfaɗo ba amman Fahima ta farfaɗo.
Allah sai kun fara comments zan fara yin sa da yawa.
*Miss green ce*
*DARASI!!*
Free page 8/9
Rabiatu Bashir
(ummu maher)miss green.
*Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu ta online zasu biya 2k*
08/09
. . . . .har yanzu mahaifina bai farfaƊo daga suman da ya yi ba,sai dai yana numfashi,hankali na ya tashi sosai don likitoci sun faɗamin Mu biyu aka kawo mu ni da mahaifina,kuma tunda aka kawo mu ƴan sintirin da suka kawo mu sune suke biyan kuɗin.
Amma tana gidan goggo mahaifiyarta sai faɗa ta ke mata na rashin mutuncin da ke yi,gashi yanzu daga ni har mahaifina babu mu babu labarinmu,sharce hawaye ta yi da majina ta ce"wallahi Goggo ni fa ban san yadda a kayi yarinyar na neme ta na rasa ba,daga tura ta talla tun jiya bata dawo ba,idan zubarda kuɗin tallan ta yi ta dawo mana,shi kuma Malam da karan baninsa ya tafi nemo ta,gashi yanzu babu labarinsu su duka".sai ta cigaba da kukanta.
Tun da ta fara maganar Goggo ke yi mata wani banzan kallo,sai da ta gama sannan ta ce"wai ni kuwa Amaturrahman kina da kirki kuwa?"cewa fa ki ka yi wai mahaifinta ya yi karanbani?shi da ƴarsa sai yaƙi fita nemanta saboda sakaci da kuma rashin hankali?,ke irin wannan riƙon na yi miki a rayuwarki?tambayar ki na ke yi?".kamar za ta daki Amma ranar ta yi suna cikin wannan halin ne a kayi sallama a ƙofar gida.
Kallon banza Goggo ta yiwa Amma sannan ta ce"w/kslm waye?".ta ɗauki mayafinta ta leƙa.
Salati ta fara yi tana kiran sunan Allah tana cewa"to shikken Mlm Bashir yanzu zamu taho insha Allah",da sauri ta dawo tana faɗawa Amma wai ƴan sintiri ne jiya suka kai su Fahima da mahaifinta asibiti,kuma tunda safe akaje cen gidan Amma ba a sameta ba,shine Bashir ya ce yasan kina nan gidan.
Bakin Amma bai mutu ba da abinda ya faru da mijinta da ƴar ta ba sai cewa ta yi"Hmm su Bashir an riƙa wajen iya gulma yanzu har yasan nan na taho?".
lokacin har Goggo ta saka hijabi ta ɗakko kuɗi ta ɗaure a bakin zaninta"ta ce to maras tunani idan kin gama gulmar mutane ki tashi mu tafi?wa wiya kawai mara tunani,har a wannan halin da ake ciki bakin ki bai mutu ba".
*** *** ***
abin mamaki Sakinat tana fara kuka hankalin Ammar ya tashi,ya kalli Khalisat da ke jikin Mahaifiyarsa tana kuka ya daka mata wata uwar tsawa ya ce"shut up!ki yiwa mutane shiru munafuka wato daman bakya son matata ko?to wallahi ko waye zai ƙi matata ko waye wallahi tallahi saina rabu dashi".ya faɗi hakan cikin yaran fillanci ya riƙe hannun Sakinat suka yi wuce warsu,Sakinat harda wani la fewa ajikin Mijinta tana yiwa su Ammi gwalo.
Ni kuwa na ce oh Sakinat kamar abin arziƙi haɗa ɗa da uwa,Duniya ina zaki damu😭.ya Allah ka haɗa mu da surukan arziƙi Amin.
Sororo Ammi ta yi tana kallon bayan ɗanta Ammar,shi kuma tasa ƙaddarar kenan mace,jiya i yanzu yana tare da ƙanwarsa suna hira kamar abin arziƙi,amman yau daga zuwan matarsa har komai ya watse.
Wasu zafafan hawaye ne ya fara zubowa Ammi a ƙwarmin idanunta, bata san sanda Khalisat ta saka hannu ta fara share mata hawaye ba,ita ma Khalisat ɗin kuka ta ke na tausayin kansu"Ammi ki yi haƙuri don Allah kinji,komai ya yi farko yana da ƙarshe kada ki saka wannan abin a ranki kinji?".rungume junansu sukayi suna tausayin kansu dana Ammar.
Har sun manta da tsayuwar Amir sai da sukaji yana cewa"haƙiƙa Sakinat ba ƙaramar butulu ba ce da ta manta,da duk abin arziƙin da ki ka yi mata ta butulce miki,ta zaɓi taci miki mutunci ta kassara miki rayuwaɓ,ta zaɓi hanyar musguna miki ta hanyar mallake miki ɗanki,amman babu komai aƙwai Allah."
Matar Amir ma har kuka ta yi don ganin abinda ya faru,tana yawan ji a littafin hausa da sauran kafofi yadda ƴaƴa suke wulaƙanta iyayensu, amman bata taɓa gani da idanun ta ba sai yau.
a ranar Sakinat ta saka mijinta a gaba kamar mayya suka tafi Abuja,shi kuwa Amir saboda haushi daman alokacin ya tafi gida,saboda takaicin hali irin na Ammar ace ka rasa wanda zaka ƙunta tawa a rayuwarka sai mahaifiyarka wacce tasha wahala a rayuwarta don rayuwarka ta ginu?gaskiya abin aƙwai lauje cikin naɗi.
Ranar gidan Ammi kamar ana zaman makoki,gidan shiru don ɗan wannan zuwan da Ammar ya yi komai sun ƙara shaƙuwa sosai,ranar kusan raba dare Ammi da Khaisat sukayi suna kaiwa Allah kukansu ta hanyar yin nafilfilu.