Gabatarwa
Dakarun Musulunci Part 5 Complete Hausa Novel · about 25 min read
[12/14, 6:53 PM] INSTRUCTOR⚓: **DAKARUN MUSULUNCI**
LITTAFI NA BIYAR 5
PART A ✍️ ✍️ ✍️
NA ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI👮
TYPING:-UMAR FAROUQ ZANGO✍️✍️
POSTING:- NAJIBULLAH MUHAMMAD 🥷🥷
ASLM, bayan tsokacin da dakatawar posting din Dakarun Musulunci insha Allah a yau zamuci gaba, Muna fatan Allah ya taimakemu 🙏🥰♥️♥️
Duk sa'adda Huzaifa ya sami nasarar saran jikin katon mutumin ko ya sokeshi da takobinsa sai yaji kamar dutse ya doka ko kwarzanewa jikinsa baya yi sai dai kaga tartsatsin wuta na tashi.
Wannan barandami na mutumin kuwa, duk abinda ya sama dashi sai ya rabe gida biyu walau dutse ko karfe.
Duk irin zafin naman Huzaifa da tsananin jarumtakarsa sai yaga duk sun zama na banza domin katon ya ninkashi a komai.
In ba don ma yana da mutukar kwarewa ba da iya yaki da tuni katon yayi masa kwaf daya.
Suna cikin wannan bakin gumurzu ne katon ya shammaci Huzaifa ya gabza masa naushi fuska.
Saboda karfin naushi sai da Huzaifa yayi sama ya gwaru da jikin bango a lokacin da wani gudan jini yayi fitar burgu daga cikin bakinsa ya fado kasa a mutukar galabaice takobinsa ma sai ta subuce daga hannunsa ta fado kasa.
Koda ganin abinda ya faru sai aljani huraisul Marwas ya fusata ainun ya bude fuka fukansa ya kawowa katon mutumin suka a kirji da wani mashinsa na yaki.
Kawai sai katon ya tare sukar da tafin hannunsa.
Take mashin ya narke ya kama diga kasa tamkar ya kwana dari a cikin wuta yana damuwa.
Cikin zafin nama katon ya kaiwa hurusul Marwas mangari da hannunsa guda, ai kuwa sai yayi Saar samunsa a fuka fukinsa na hagu.
Kamar an cilla tsakuwa haka hurusul Marwas ya fada can baya ya gwaru da bango ya fado kasa sumamme sakamakon karyewar fuka fukinsa.
Koda katon ya ga wannan nasara da ya samu sai ya bushe da dariya mugunta sannan ya juya izuwa kan yarima Huzaifa yaje kansa ya tsaya ya raba kafafunsa kuma ya sunkuyo da nufin ya kama kan Huzaifa ya murde masa wuya.
Ashe a dai dai wannan lokaci hunzalu na ta yiwa Allah kirari yana neman ya karfafeshi da karfin da zai iya taimakon su Huzaifa.
Ai kuwa nan take yaji wani gagrumin karfi ya shiga jikinsa, kawai sai gani yayi ya daka tsalle daga inda yake ya dira akan wannan garjejen kato.
Kafin katon ya kamo kan Huzaifa da hannayensa tuni hunzalu ya naushi gadon bayansa.
Saboda tsananin karfin naushi take gadon bayan katon ya burme, sai ga hannun hunzalu ya Faso ta cikin katon.
Yana zare hannunsa sai katon ya sulale kasa matacce, ji kake Tim! Tamkar giwa ce ta fadi.
Shi kansa hunzalu bai san saadda ya kame ba kamar gunki saboda tsananin mamaki bisa ganin wannan gagarumar jarumta da yayi. Kawai sai yaji tsoron Allah da kaunarsa sun karu ainun a cikin ransa, bai san saadda idanunsa suka ciko da kwallah ba suka fara zubar da hawayen murna.
Huzaifa da aljani hurusul Marwas kuwa, kasa motsawa sukayi saboda tsananin alajabi sai bayan yan dakiku sannan Huzaifa ya mike tsaye ya dubi hunzalu cikin murmushi yace, ya kai hunzalu kayi sani cewa wanda duk ya yi imani da Allah kuna ya dogara da shi bisa dukkan lamuransa to fa babu abinda zai gagareshi a doron kasa.
Tabbas imaninka da tsoronka ga Allah ne suka sa ka sami wannan gagarumin karfi har ka sami nasarar kashe wannan katon ka ceto rayuwarmu.
Ni da hurusul Marwas kuwa ajizanci ne irin na dan Adam yasa muka shaafa da ci gaba da neman taimakon Allah, a lokacin da muke yin yaki da wannan kato, shi yasa muka masa samun nasara a kansa.
Koda Huzaifa yazo nan a zancensa sai yaji ana ta kiran sunansa a bayansa.
Koda ya waiga da sauri sai yaga ashe ba wasu bane face dakarun garinsu wadanda ke cikin wannan daki a kulle, su duka sun zo bakin kofar dakin sun tsaitsaya wacce take a kulle da katon kwado kuma an yi tane da sandunan karfe mai kauri.
Nan take Huzaifa ya sunkuya ya dauki takobinsa ya tofa mata wata addua sannan ya dagata sama ya sare kwadon mukullin da aka rufe kofar da shi.
Take kwadon ya fadi kasa kofar ta bude, sai dakarun suka fito waje gaba dayansu cikin tsananin farinciki suna yiwa Allah godiya gami da yiwa Huzaifa jinjina.
Nan dai aka dunguma da nufin a fice daga cikin kurkukun gaba daya amma sai Huzaifa ya tsaya cak! Sakamakon aljani hurusul Marwas a kwance yana nishi ya kasa tashi.
Cikin kaduwa Huzaifa ya ruga gareshi ya durkusa a gabansa yace, ya kai dan uwanavv menene ya sameka ka kasa tashi kana ta nishi haka?
Hurusul Marwas ya budi baki da kyar yace, shi baka ganin yadda fuka fukina na hagu ya kumbura bane?
Ai na karye ne kuma ba zan iya koda motsawa ba daga nan face an gyara mini wannan karaya.
Koda Huzaifa ya dubi fuka fukin ya ga yadda ya karye kuma ya kumbura sumtum! Sai hankalinsa ya dugunzuma domin bai san yadda ake DOA aljanu ba yayin da suka karye.
Huzaifa ya dubi aljani hurusul Marwas yace, yanzu menene abinyi?
Kaga dai inda zamu taru mu duka nan ni da dakarun nan da muka ceto rayuwarsu ba za mu iya daukarka ba sannan kuma bamu san yadda ake gyara karaya ba irin taku ta aljanu.
Koda jin wannan batu sai aljani hurusul Marwas yayi murmushin karfin haki yace, ai batun gyaran karayarmu iri dayane da naku, kawai yanzu ku garzaya ku samo itatuwan bishiya masu kauri gami da danyar jijiyar bishiya kuzo ku gyara karayar da sauri kafin abokan gaba su zo su afka mana domin na san cewa nan da zuwa wani lokaci akilin sarki shaaran zai iya samun labarin halin da kurkuku ke ciki aboda tsegumi irin na yan uwana aljanu. Yanzu ma karfin addu'armu ne ya hana aljanun dake yaso munafunci zuwa kusa da nan bare su san halin da ake ciki.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa ya umarci wasu daga cikin dakarun na musulunci da su ruga suje u samo manyan itatuwa da danyar jijiyar bishiya.
Nan da nan kuwa dakarun suka cika umarni. Lokacin da aka zo da abubuwa biyun sai aljani hurusul Marwas ya dubi yarima Huzaifa yace, ina mai baku shawara daku samo murtukekiyar sarkar karfe ku fara daure hannayena, kafafuna da wuyana kasa cikin dirkoki in ba haka ba kuwa gyaran karayar nan ba zai yiwu ba.
Koda jin wannan batu sai yarima Huzaifa yayi murmushi yace, hakika aikin mai shawara baya baci.
Aaje a samo irin sarkokin da ake daure fursunonin aljanu a gidan nan, sannan vkuma ina son muci gaba da yin adduoi gaba dayanmu domin Allah ya hana abokan gabarmu zuwa nan harmu kammala duk abinda muka zo yi.
Nan take kuwa akayi amfani da wannan umarni.
Bayan an samo wata murtukekiyar sarkar karfe an daure hanaye, kafafu da wuyan aljani hurusul Marwas a jikin wadan su manyan dirkokin gini, sai hurusul Marwas ya sake bayar da shawara a toshe bakinsa da tsummokara a daureshi tamau.
Wannan shawara ma ba ayi biris da ita ba,, koda aka fara gyara karayar fuka fukin nasa kuwa yaji wani irin mugun radadi da zugi sai ya yunkura cikin azabbaben karfi, ya kwarara uban ihu.
Da yake bakinsa a toshe yake sai ihun ya zamo kamar an busa bututun algaita, amma duk da haka sai da karar sautin ta cika birnin shumbul gaba daya ta firgita komai da kowa.
Motsawar da yayi kuwa, sai da gaba dayan ginin gidan kurkukun yayi girgiza kamar zai rushe.
Cikin hanzari Huzaifa da sauran jamaarsa suka daka tsalle suka dira akan hurusul Marwas suna kokarin danneshi.
Duk da haka sai suka kasa ladaftar da shi domin da zarar ya yunkura sakamakon zafin da yake ji na gyaran karayar sai kaga ya watsar da su kasa tamkar busassun ganyayen bishiya na zubowa kasa.
* * * * * *
A can gidan sarautar sarki shaaran kuwa, lokacin da wakilin sarki da sauran jamaar asa suka jiyo sautin ihun aljani hurusul Marwas dai suka rude kuma suka cika da tsananin mamaki domin basu taba jin wani sauti ba makamancinsa a cikin garin.
Nan take wani babban badakare ya dubi wakilin sarki yace, ya shugabana anya kuwa ba abokan gabarmu mune suka shigo cikin garin nan bamu sani ba suka fara yi mana yakin sunkuru?
Koda jin wannan tambaya sai wakilin sarki shaaran ya dakawa badakaren tsawa yace, hana wannan wacce irin maganar banza kakeyi ne haka?
Ta yaya abokan gaba zasu iya shigowa cikin garin nan ba tare da mun sani ba alhalin ka san cewa a ko ina kuma dare da rana aljannunmu masu gadin birnin nan suna sintiri suna kewaya garin?
Badakaren ya numfasa yace, ya shugabana ni fa alamarin mutanen nan maabota addinin musulunci yana bani tsoro saboda suna da matukar karfin sihiri.
Ka tuna cewar bamu taba jin irin wannan sauti ba a garin nan sai wannan karon, kuma mutum ba zai iya fitar da wannan sauti ba sai dai gawurtaccen jarumin aljani kamar irin aljanun da suje gadin kurkukun sarki da gidan gonarsa.
Ni dai ina mai bayar da shawara ka tura dakaru suje su gano halin da kurkukun yake cikin da kuma gidan gona don kada makiya su zo su shammacemu.
Saadda wakilin sarki yaji wannan batu sai ya gyada kai yace, hakika aikin mai shawara baya baci, amma ai na san cewa babu ta yadda za'ayi makiya su iya shigowa cikin garin nan ba tar da asirinsu ya tonu ba saboda irin kwararan matakan tsaron da sarki ya dauka.
Koda gama fadin hakan sai wakilin sarki ya dubi wannan badakaren yace dashi yayi sauri ya hau dokinsa ya tafi izuwa kurkuku ya gano halin da yake ciki, sannan kuma ya wuce izuwa can gidan gonar sarki can ma ya gan ko akwai wata matsala.
Nan take kuwa badakaren ya hau dokinsa ya zabureshi da gudu ya nufi hanyar da zata kaishi kurkukun.
* * * * * *
A can kurkuku kuwa, cikin gaggawa su Huzaifa suka gama gyaran karayar aljani hurusul Marwas sannan Huzaifa ya bayar da wata addua ta musamman yace kowa yayi ta biyata a cikin zuciyarta sannan ya umarci humzalu da yayi musu jagora izuwa gidan gonar sarki.
Nan take kuwa suka hau dawakansu su duka suka fice daga cikin gidan kurkukun suna ta karanta wannan assay addua da Huzaifa ya basu suna ta wuce gawarwakin dakarun dake tsaro gaba daya.
Sai a wannan lokacine ragowar dakarun kurkukun da ke can kofofin farko na shigowa suka ankara da abinda ke faruwa, suka ruga da gudu izuwa kan su yarima Huzaifa da nufin su kashe su.
Nanfa aka rugumtsume da sabon azabbaben yaki.
Da yake wannan karon su Huzaifa na tare da dakarun musulunci sai nan da nan suka sami nasarar yakin.
Koda tsirarun dakarun suka ga saura su yan kadan sai suka zubar da makamansu suka fara yunkurin guduwa.
Cikin daga murya Huzaifa ya bayar da umarnin kada a bari dayansu ya tsira ya gudu daga cikin kurkukun.
Aikuwa sai dakarun musulunci suka rinka kurewa dakarun kurkukun gudu suna rafkesu.
Nan da nan aka karar dasu gaba daya. Faruwar haka ke da wuya sai aka sake hawa dawakai da nufin a tafi izuwa gidan gonar sarki. Har an iso baki kofar fita daga kurkukun sai wani tunani ya fadowa Huzaifa kawai sai yaja linzamin dokinsa ya tsaya cak sannan ya dubi hunzalu da sauran dakaru na musulunci ya ce, ba zamu iya tafiya ba izuwa gidan gonar sarki a haka ba dole ne mu yi bad da kama muyi shiga irin ta dakarun sarki shaaran yadda ko akan hanya babu mai taremu.
Wasu daga cikinmu kuma dole ne su yi shiga ta bayi sannan ina son mutum hudu daga cikinku wadanda zasu iya kundunbala su tsaya a bakin kofar kurkukun nan a matsayin masu gadi a cikin shigar masu gadin domin jikina ya bani cewa a ko Yaushe wakilin sarki shaaran zai iya turo mutanensa domin su zo su ga halin da kurkukun nan ke ciki.
Yanzu su waye zasu iya yin wannan kundunbala mu barsu anan kofar kirkir koda dai sun mutu sun san cewa shahada sukayi?
Kafin Huzaifa ya rufe bakinsa tuni gaba daya dakarun sun budi baki cikin hadin murya kowa dacewa shi ya amince.
Koda jin haka sai Farin ciki ya kama Huzaifa ya dubesu yace, hakika duka imaninku ya inganta domin dukka musulmi na gari yana da burin shahada.
Koda gana fadin hakan sai nan da nan aka shiga shirye shiryen sauya tufafi.
Cikin kankanin lokaci kowa ya gama komtsawa. Aljani hurusul Marwas ne kadai bai yi shiga irin ta dakarun shaaran ba a matsayinsa na aljani.
Take aka bar mutum hudu a bakin kofar kurkukun suka yi tsayuwa irin wacce masu gadin kurkukun ke yi koda Yaushe.
A sannane Huzaifa da sauran dakarun suka tusa keyar dakarunsu da suka yi shigar bayi suka gaba, hunzalu ne akan gaba cikin shigar dakarun birnin yana yi musu jagora, Huzaifa na daga can bayan karshe.
Suna cikin wannan tafiya ne suka yi kicibus da wannan badakare wanda wakilin sarki shaaran ya turo shi kurkukun domin yaga halin da kurkukun ke ciki.
Koda ganinsa sai wani daga cikin dakarun musulunci ya yunkura zai zare wuka ya kasheshi, amma sai Huzaifa ya yi masa inkiyar ya kyaleshi.
Lokacin da badakaren ya karaso dag da su ya ga ashe hunzalu ne ke jagorantar wadannan bayi sai ya risina cikin girmamawa ya gaisheshi yace, ya shugabana daga ina kuke haka, kuma ina zaku kai da wadannan bayi haka?
Koda jin wannan tambaya sai hunzalu ya dubi badakaren yace, daga kurkuku muke kuma gidan gonar sarki zamu kai wadannan fursunoni domin su canji maaiakatan can kamar yadda aka sabayi kullum.
Koda jin wannan batu sai mamaki ya kama badakaren yace, haba ya shugabana ta yaya zaka debo fursunoni daga kurkuku ka kaisu can gidan gonar sarki alhalin kafin sarki ya taci yaki ya kafa doka mai tsauri cewar babu mahalukin da zai sake shiga ko fita daga cikin kurkuku da gidan gonarsa?
Yanzu haka ma wakilin sarki ne yace na zo na ga halin da kurkukun ke ciki sannan na wuce izuwa can gidan gonar tasa, can ma na ga lafiyar sa.
Saadda badakaren yazo nan a zancensa sai yaji hunzalu ya bushe da dariya.
Lokaci guda kuma ya turbine fuskarsa ya daka masa tsawa yace, ina hankalinka ya taci ne?
Shin kana zaton zan aikata abinda zai bata ran sarki ne alhalin na san cewa ko yaya nayi wani kuskure sawa zaiyi a kashe dana guda daya dake tare a inda ban sani ba?
Ka sani cewa ni ne mai kula da aiyukan gidan gonar sarki idan aikin gonar sarki ya tsaya ko aka sami wata matsala yana dawowa zai hukuntani.
Ka ga ni yanzu kana bata mini lokaci kuma kana batawa kanka lokaci gwara ka tafi izuwa Aiken da aka yi maka.
Koda gama fadin hakan sai hunzalu ya bangaje wannan badakaren ya wuce gaba ayarin su Huzaifa suka take masa baya.
Da yake duk u Huzaifa suna sanye ne hulunan karfe ne badakaren bai ga fuskar dayansu ba bare ya gane cewar ba dakarun kasar bane, amma sai ya tafi yana waigensu cikin alamun mamaki da rashin yarda.
A wannan lokaci aljani hurusul Marwas na can sama cikin gajimare yana bin su Huzaifa kuma yana karanta dduar da Huzaifa ya bayar dalilin da ya sa sauran aljanun dake shawagi a sararin saman garin suka kasa ganinsa ke nan kuma suka kasa ganin su Huzaifa.
Lokacin da su Huzaifa suka ci gaba da tafiya sai wani badakare dake kusa da Huzaifa ya dubeshi cikin girmamawa yace, ya shugabana me yasa ba ka barni na kashe wancan badakaren ba dazu?
Kayi sani cewa barinsa a da rai a garemu ba karamin ganganci bane domin ga dukkan alamu bai yarda da mu ba, kuma zai iya zuwa ya kai labarin mu ga wakilin sarki shaaran can fada a turo mana mayaka masu yawa su kawo mana hari.
Saadda Huzaifa yaji wannan batu sai yayi ajiyar zuciya sannan yace, tabbas abinda ka fada gaskiya ne, to amma kuma kashe shin shine abu mafi hadari a garemu domin idan wakilin sarki ya ga ya dade bai koma ba zai turo abu sawunsa kuma idan aka zo aka ga gawarsa za'a gane cewar mun shigo cikin garin sai abi sawunmu har can gidan gonar a tarfa mu.
Yanzu kuwa idan yaje kofar kurkukun yaga dakarunsu a tsaye babu alamar wata matsala zai juyo ne ya biyomu izuwa can gidan gonar sarki, kafin ya riskemu kuma tuni mu munje mun dauko luhaira.
Koda Huzaifa yazo nan a zancensa sai gaba daya dakarun suka gamsu da bayaninsa kuma suka cika da tsananin mamakin irin basirarsa da yadda akayi ya shirya wannan dabara.
Alhamdulillahi nan zan da kata sai Allah ya kaimu sati mai zuwa zaku jini dauke da ci gaban wannan labari.
Sunana Umar Farouq Zango nake muku Fatan alkhairi sai mun hadu a ranar jumaa idan Allah ya kaimu.🙏🙏🙏🙏
[12/14, 6:53 PM] INSTRUCTOR⚓: **DAKARUN MUSULUNCI**
LITTAFI NA BIYAR 5
Part B ❤️ ♥️
NA ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI👮👮
Typing:- UMAR FAROUQ ZANGO.✍️
Posting:- Najibullahi Muhammad 🥷🥷
Haka dai suka ci gaba da tafiya har tsawon kusan rabin sa'a sannan suka iso kofar gidan gonar sarki.
Tun daga mesa gabansu ya fadi sakamakon hango irin tsananin tsaron da ke gidan gonar, wanda ya ninka na kurkukun sau goma.
Nan take zuciyoyinsu suka karaya suka tabbar da cewar babu yadda za'ayi su shiga cikin wannan gidan gona cikin irin Saar da nasarar da suka samu a can kurkuku kuma komai zai iya faruwa ko dai su rasa rayuwarsu ko kuma a dade ana gumurzu har wakilin sarki ya san da zuwan su azo ayi musu rubdugu.
Koda yarima Huzaifa ya gama aiyana wannan alamari sai hankalinsa ya dugunzuma ya rasa abinda ke masa dadi ya fara shawara da zuciyar sa.
Abin da ya fado masa a rai shine, idan har basu sami damar shiga cikin gidan gonar ba kai tsaye har su gano inda Luhaira take a cikin kankanin lokaci ba duk shirin su ya wargatse.
Har suka karasa daf da kofar gidan gonar Huzaifa bai sami wata mafita ba.
Da isowarsu sai dakarun dake tsaron kofar suka dakatar dasu.
Shugaban masu gadin ya dubi Hunzalu a fusace yace, menene ya kawoka nan tare da bayi kalilan da kuma dakaru masu yawa haka?
Koda jin wannan tambaya sai zuciyar sa ta buga da karfi, tsoro ya baibayeshi ya firgita ainun domin yana ganin cewa asirinsa ya tonu amma sai ya yi ta maza ya dakawa shugaban masu gadin tsawa yace, shin ka manta da wanda kake maganane?
Ka manta da cewar nine mai kula da dukkanin bayin dake aiki a cikin gidan gonar nan fiye da shekaru talatin baya har ma sai da dana yazo ya gajeni?
Koda jin wannan batu sai shugaban masu gadin ya bushe da dariyar mugunta, lokaci guda kuma ya turbune fuskarsa yace, ai duk maganar da kake yi alamarin ne na da wanda ya wuce.
Shin ka manta ne da cewar dan naka daya gajeka Yanzu haka baya kan aikinsa kuma an sare masa hannuwansa da kafafunsa kuma antsire idamunsa sakamakon laifin da ya aikata na kusantar amaryar da sarki zai aura.
Kai kanka yaushe rabonka da shiga cikin gidan gonar nan, a kallah ankai sati guda.
Kuma sarkine da kansa ya dakatar da kai don tabbatar da tsaro a gidan gonar gaba daya bisa barazanar abokan gaba.
Ina mai tabbatar maka da cewa idan ba sarki shaaran bane ya zo da kansa nan yace mu bude maka kofa ku shiga ba babu yadda za'ayi ku shiga cikin gidan nan.
Koda jin wannan batu sai hankali su yarima Huzaifa ya dugunzuma ainun suka rasa abin da ke musu dadi.
Shugaban masu gadin ya sake duban hunzalu ya daka masa tsawa yace, ya kai hunzalu ina mai shawartarka da ka gaggauta janye gidan gonar nan kafin cikar dakika dari ko Yanzu nan na umarci dakaruna dake kan ganuwa suyi musu ruwan kibau.
Yana gama fadin hakan sai ya juya ya koma can bakin kofar gidan gonar inda sauran yan uwansa masu gadi suke.
Nan take hunzalu ya karaso gaban yarima Huzaifa ya dubeshi cikin tsananin damuwa yace, ya shugabana yanzu menene abinyi?
Kawai sai Huzaifa yace, ku zo mu koma da baya izuwa can cikin duhuwar dajin can.
Ba tare da bata lokaciba suka bi wannan umarni suka shige izuwa cikin duhuwar ciyayi da bishiyoyi wadanda ke nesa kadan da kofar gidan gonar inda ba a iya hangosu.
Da shigar su wannan wuri sai suka sauko daga kan damakansu kowa ya zauna a kasa dirshan cikin alamun karayar zuciya aka yi tsit tamkar babu mai laka a jikinsu.
Tsawon yan dakiku dayansu baice uffan ba kowa yana tunani, a sannane hunzalu ya dubi yarima Huzaifa yace, ya shugabana yanzu kana da wata dabara ne wacce kake ganin zamu iya amfani da ita wajen samun nasarar dauko Luhaira kuma mu fito a raye ba tare da mun fuskanci wata matsala ba?
Lokacin da hunzalu ya zo nan a zancensa sai Huzaifa yayi ajiyar zuciya sannan yace, a rayuwata ban taba samun karayar zuciya ba irin ta yanzu bisa duk abinda nasa a gabana.
Ina da yakinin cewa Allah zai iya bamu nasarar shiga cikin wannan gidan gona bisa taimakonsa, to amma bani da tabbacin cewar da yawan mu bazamu rasa rayuwarmu ba.
Abu na biyu shine, duk a cikinmu babu wanda yasan ainahin dai dai gurin da Luhaira take bare da zarar mun shiga ciki mu wuce kai tsaye izuwa wajen dole sai mun bata lokaci mai yawa wajen gano wajen ko kuwa hunzalu ka san inda aka ajiye Luhaira?
Humzalu ya gyada kai yace,ai kullum ai an sauyawa Luhaira dakin kwana a cikin gidan gonar nan, kuma a kallah dakunan sun fi guda dari uku, sannan kowanne daki tsakaninsa da wank akwai tazara ta a kalla tafiyar rabin saa.
Koda jin wannan batu sai zuciyar yarima Huzaifa ta sake karaya fiye da ko yaushe yaji kamar ya fashe da kuka saboda takaici, kawai sai ya dubi gaba daya dakarun yace, ku tashi muyi kokarin barin garin nan ba zamu iya shiga cikin gidan gonar nan ba har mu iya dauko Luhaira.
Tunda dai Allah ya sa ni da su aljani hurusul Marwas mun sami nasarar ceto rayuwarku ai mun sami gagarumar nasara ta farko.
Koda gama fadin hakan sai kowa ya mike da nufin a hau dawakai abi wata barauniyar hanya wacce zata kutsa dasu izuwa cikin daji.
Kwatsam! Sai suka hango badakaren nan wanda wakilin sarki ya tura can kurkuku domin yaga abinda ke faruwa bisa doki a sukwane ya durfafi kofar gidan gonar. Koda ganin haka sai hankalin su Huzaifa ya sake dugunzuma ainun domin sun san cewa da zarar ya iso bakin kofar gidan gonar ya tambayi labarin su asirinsu ya tonu kenan.
Ba zato ba tsammani sai kuma suka sake hango aljani hurusul Marwas ya sauko daga sama ya sure shi da dokinsa gaba daya yayi sama da su kamar shawo ya suri dantsako kuna dai ya lullubesu da fuka fukansa ya luluka da su izuwa can kololuwar sama.
Kafin kiftawar ido ya bace bat! Bayan yan dakiku sai gashi ya sake bayyana tsulum! A gaban Huzaifa.
Kawai sai ya dubeshi yace, ya shugabana ka yi mini izini ni kadai zan shiga cikin gidan gonar nan na dauko Luhaira cikin ikon Allah batare da asirina ya tonu ba.
Kuma a cikin dakiku kadan zan hattama wannan aiki.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yayi murmushi sannan yace, Yanzu ina kakai wannan badakaren da dokinsa?
Hurusul Marwas najin wannan tambaya sai ya mai da masa da martanin musmushin sannan yace ai tuni nayi aikin namu na aljanu.
Cikin jikinsa na shiga na komar da shi izuwa can wajen wakilin sarki ya shaida masa cewar yaje kurkuku da gidan gona ya tabbatar da babu wata matsala.
Bayan wakilin sarki ya sallameshi ya koma cikin yan uwansa bayi kuma sai na shafeshi na sa masa barci mai nauyi saboda ina tsoro cewar bayan na fita daga jikinsa zai iya dawowa cikin hayyacinsa ya koma wajen wakilin sarki ya sanar da shi ainahin gaskiyar alamari.
Koda aljani hurusul Marwas yazo nan a jawabinsa sai murna ta kama yarima Huzaifa da su Humzalu kuma suka Sam cikakken kwanciyar hankali.
Cikin faraa Huzaifa ya dubi aljani hurusul Marwas yace, tabbas Yanzu ne na dada tabbatarda cewa ni da kai duk muna bukatar juna kuma idan dayanmu baya tare da dayan to babu yadda za'ayi ya sami nasarar cika aikin da yazo yi a kasarnan.
Ya kai hurusul Marwas nayi maka izini maza ka shiga cikin gidan gonar nan ka dauko mini Luhaira.
Hurusul Marwas ya risina yace, an gama ya shugabana.
Kafin ya budi baki yace wani abu tuni aljani hurusul Marwas ya bace bat daga gabansa.
Nan fa tunanin zuci yace fadowa Huzaifa ya tambayi zuciyar sa yana mai cewa, menene dalilin da yasa aljani hurusul Marwas ya kirani da matsayin shugabansa a wannan karon alhalin tun daga lokacin da muka hadu dashi abokina yake kirana dashi?
Amsar da Huzaifa ya kasa baiwa kansa kenan, amma sai ya kudure a cikin ramsa cewar idan suka sami nutsuwa dai ya yi masa wannan tambayar.
Huzaifa na cikin yin wannan tunani ne kawai yaga aljani hurusul Marwas ya sake baiyana tsulum! A gabansa goge da Luhaira gadon bayansa amma ko ina a jikin hurusul Marwas sara ne na takobi sai jinine ke kwarara daga jikinsa.
Da rub da ciki aljani hurusul Marwas ya kife kasa yana numfashi sama sama, ita kuwa Luhaira dake kwance a bayansa, barci take ta faman sharara bata ma san abinda ke faruwa ba.
A dimauce, cikin tsananin firgici yarima Huzaifa ya dauke Luhaira daga kan bayansa. Hurusul Marwas ya shimfide akan ciyawa gefe daya sannan suka taru akan aljani hurusul Marwas suna yi masa magani gami da tofa masa adduoi domin su ceto rayuwarsa.
Sai da lokaci mai dan tsawo ya shafe sannan numfashin aljani hurusu Marwas ya dawo dai dai har ya iya bude idanunsa.
Koda ya tsinci kansa a gabansu Huzaifa kuma yaga Luhaira kwance a cana gefe daya tana ta shara barcinta sai ya yi kabbara cikin tsananin Farin ciki kuma yayi godiya ga Allah, sannan ya mike zaune ya dubi Huzaifa yace, ya shugabana burina na farko ya cika tunda har bukatunka sun biya bisa abinda kazo nema a garin nan.
Ka kubutar da dakarunku wadanda aka tsare a kurkuku sannan kuma ka dauko Luhaira.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yayi murmushi a gareshi yace, a'a gyara maganar ka, ba nine na dauko Luhaira ba kaine, kuma in ba don kai na da babu yadda za'ayi na iya daukota.
Gama fadin hakan ke da wuya sai hankalin kowa ya koma kan Luhaira wacce ke kwance akan ciyawa.
Nan fa su duka suka dimauce bisa ganin irin tsananin kyawun da Allah ya bata domin inda za'a hada kyawun gimbiya Lafirta dana yar uwarta Sazirat a waje guda bazai kai rabin ma Luhaira ba.
A wannan lokaci wata doguwar riga ce fara kal mai shara shara a jikinta, don haka duk surar jikinta a fili take, musamman ma idan iska ta kada rigar.
Cikin gaggawa Huzaifa ya cire alkyabbar jikinsa ya lullubeta da ita sanna ya dubi aljani hurusul Marwas yace, ya kai dan uwana yanzu menene abinyi?
Koda jin wannan tambaya sai hurusul Marwas yayi murmushi yace, babu abinyi face muyi sauri mu bar garin nan mu durfafi birninku na Darul husuf domin muje mu ga halin da ake ciki, walau anci nasarar yakin da ake yi ko ba'a ci ba.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yaji gaba daya hankalinsa ya koma kan birnin Darul Husuf.
Nan take ya sake daukar Luhaira ya dorata a gadon bayan aljani Hurusul Marwas sannan shima ya kama dokinsa ya hau, suma su Humzalu sai suka yi koyi da shi.
Nan take aka ci gaba da tafiya ana karanta wannan addua wacce yarima Huzaifa ya bayar tun da farko.
*wannan shine abinda ya faru ga su Huzaifa, bayan sun sami nasarar debo fursunoninsu daga kurkukun sarki shaaran kuma sun dauko Luhaira daga gidan gonar sa bayan sun sha bakar wahala da bakin gumurzu*
* * * * * *
Al'markin su sarki shaaran kuwa, bayan ya gama sanar da mahaifiyar ukashat duk abinda ya faru da kuma hukuncin da zai dauka na gaba wato neman taimakon dakarun yaki daga sauran kasashen kafirai na nahiyar don aje a yiwa birnin Darul Husuf rubdugu a gama da shi farat daya, sai ta kyalkyale da dariyar Fatin ciki sannan kuma ta tashe da kukan bakin ciki tace, tabbas dana ukashat ya ci amanata a matsayina na mahaifiyarsa, kuma ya bani kunya.
Lallai da hannayena zan kashe shi, amma kuma nayi matukar Farin ciki daka sami nasarar cin wannan birni namu da yaki cikin BAZATO!
Shawarar da zan baka itace, ka gaggauta shirin tafiya izuwa kasashen makwabtaka domin nemo dakarun gudunmawa na yaki amma kafin ka tafi ka bar jiran gari nan a hannuna.
Nayi maka alkawarin cewar kafin ma a sake yin yakin karshe zan kama sarki Uwaisul Karni da duk mukarrabansa sai dai ka dawo ka iskesu a cikin kurkuku a tsare.
Koda jin wannan batu sai sarki shaaran da yarda Sazirat suka kalli junan su sannan suka kalli mahaifiyar ukashat cikin alamun rashin yadda da gamsuwa, kawai sai suka koma gefe daya sukayi dan kuskuks.
Sarki shaaran ya dawo wajena ya dubeta yace, yake matar babban maki yina, kiyi sani cewa na yi shawara da yata Sazirat kuma mun yanke hukuncin cewar zamu bar Miki jiran birnin Darul Husuf a hannunki, amm bisa sharadi guda.
Sharadin kuwa shine, idan har da gaske zaki iya kama sarki uwaisul karni shi da mukarrabansa har ki tsaresu a kurkuku to mu dawo mu iske kan danki ukashat a tsire a jikin ice akan ganuwar garin nan.
Idan kuwa muka dawo muka ga babu wannan kai na Danko, to mun san cewa yaudararmu kikayi don haka zamu shigo cikin birnin ne da karfin tsiya mu sake yakarku kuma mu kashe kowa da komai ko kaza guda daya bazamu barta da rai ba.
Koda jin wannan sharadi sai hankalin mahaifiyar ukashat ya dugunzuma ainun saboda ta san cewa bazata iya kashe danta ba ko kuma ta sa wani ya kashe shi komai tsanar da take yi masa a rayuwarta.
Nan take ta nuna cewa zata cika wannan umarni, amma tan bukatar a bar mata kamar dakaru dubu dari wadanda zasu karta ta sami ikon tafiyar d komai kamar yadda ya kamata, sarki shaaran yayi murmushi yace, shikenan na amince da hakan.
Nan take ya ware dakaru dubu dari aka barsua birnin Darul Husuf sannan sarki shaaran, Sazirat da sauran dakarunsu suka yi shiri suka hau dawakansu suka fice daga cikin birnin suka nausa cikin daji a guje suka durfafi hanyar da zata kaisu birninsu na shumbul.
* * * * * *
Bayan kamar rabin sa'a da bacewar sarki shaaran a cikin daji, sai tawagar su sarki uwaisul karni ta bullo daga wata hanya daban ta durfafi birnin Darul Husuf.
Sarki uwaisul karni ne akan gaba tare da yarima ukashat.
Su da dukkanin dakarun dake biye da su sun yi shigar yaki ne dauke da makamai.
A wanann lokaci rana bata fadi ba amma magriba ta kawo kai.
Kafin a isa inda za'a iya hango kofar birnin sai sarki uwaisul karni ya ja linzamin dokinsa ya tsaya cak! Kuma ya bayar da umarnin a tsaya a wajen a kafa tantuna.
Alamarin da ya baiwa kowa mamaki ke nan, saboda bai kamata a tsaya a daji ba dag da magriba tunda ana dag da shia gari.
Alhamdulillahi, anan zan dakata kuma sai Allah ya kuma ara mana rana irin ta yau zaku jini dauke da ci gaban wannan Littafi.
[12/14, 6:53 PM] INSTRUCTOR⚓: **DAKARUN MUSULUNCI**
LITTAFI NA BIYAR 5
LITTAFI NA BIYAR 5
PART A ✍️ ✍️ ✍️
NA ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI👮
TYPING:-UMAR FAROUQ ZANGO✍️✍️
POSTING:- NAJIBULLAH MUHAMMAD 🥷🥷
ASLM, bayan tsokacin da dakatawar posting din Dakarun Musulunci insha Allah a yau zamuci gaba, Muna fatan Allah ya taimakemu 🙏🥰♥️♥️
Duk sa'adda Huzaifa ya sami nasarar saran jikin katon mutumin ko ya sokeshi da takobinsa sai yaji kamar dutse ya doka ko kwarzanewa jikinsa baya yi sai dai kaga tartsatsin wuta na tashi.
Wannan barandami na mutumin kuwa, duk abinda ya sama dashi sai ya rabe gida biyu walau dutse ko karfe.
Duk irin zafin naman Huzaifa da tsananin jarumtakarsa sai yaga duk sun zama na banza domin katon ya ninkashi a komai.
In ba don ma yana da mutukar kwarewa ba da iya yaki da tuni katon yayi masa kwaf daya.
Suna cikin wannan bakin gumurzu ne katon ya shammaci Huzaifa ya gabza masa naushi fuska.
Saboda karfin naushi sai da Huzaifa yayi sama ya gwaru da jikin bango a lokacin da wani gudan jini yayi fitar burgu daga cikin bakinsa ya fado kasa a mutukar galabaice takobinsa ma sai ta subuce daga hannunsa ta fado kasa.
Koda ganin abinda ya faru sai aljani huraisul Marwas ya fusata ainun ya bude fuka fukansa ya kawowa katon mutumin suka a kirji da wani mashinsa na yaki.
Kawai sai katon ya tare sukar da tafin hannunsa.
Take mashin ya narke ya kama diga kasa tamkar ya kwana dari a cikin wuta yana damuwa.
Cikin zafin nama katon ya kaiwa hurusul Marwas mangari da hannunsa guda, ai kuwa sai yayi Saar samunsa a fuka fukinsa na hagu.
Kamar an cilla tsakuwa haka hurusul Marwas ya fada can baya ya gwaru da bango ya fado kasa sumamme sakamakon karyewar fuka fukinsa.
Koda katon ya ga wannan nasara da ya samu sai ya bushe da dariya mugunta sannan ya juya izuwa kan yarima Huzaifa yaje kansa ya tsaya ya raba kafafunsa kuma ya sunkuyo da nufin ya kama kan Huzaifa ya murde masa wuya.
Ashe a dai dai wannan lokaci hunzalu na ta yiwa Allah kirari yana neman ya karfafeshi da karfin da zai iya taimakon su Huzaifa.
Ai kuwa nan take yaji wani gagrumin karfi ya shiga jikinsa, kawai sai gani yayi ya daka tsalle daga inda yake ya dira akan wannan garjejen kato.
Kafin katon ya kamo kan Huzaifa da hannayensa tuni hunzalu ya naushi gadon bayansa.
Saboda tsananin karfin naushi take gadon bayan katon ya burme, sai ga hannun hunzalu ya Faso ta cikin katon.
Yana zare hannunsa sai katon ya sulale kasa matacce, ji kake Tim! Tamkar giwa ce ta fadi.
Shi kansa hunzalu bai san saadda ya kame ba kamar gunki saboda tsananin mamaki bisa ganin wannan gagarumar jarumta da yayi. Kawai sai yaji tsoron Allah da kaunarsa sun karu ainun a cikin ransa, bai san saadda idanunsa suka ciko da kwallah ba suka fara zubar da hawayen murna.
Huzaifa da aljani hurusul Marwas kuwa, kasa motsawa sukayi saboda tsananin alajabi sai bayan yan dakiku sannan Huzaifa ya mike tsaye ya dubi hunzalu cikin murmushi yace, ya kai hunzalu kayi sani cewa wanda duk ya yi imani da Allah kuna ya dogara da shi bisa dukkan lamuransa to fa babu abinda zai gagareshi a doron kasa.
Tabbas imaninka da tsoronka ga Allah ne suka sa ka sami wannan gagarumin karfi har ka sami nasarar kashe wannan katon ka ceto rayuwarmu.
Ni da hurusul Marwas kuwa ajizanci ne irin na dan Adam yasa muka shaafa da ci gaba da neman taimakon Allah, a lokacin da muke yin yaki da wannan kato, shi yasa muka masa samun nasara a kansa.
Koda Huzaifa yazo nan a zancensa sai yaji ana ta kiran sunansa a bayansa.
Koda ya waiga da sauri sai yaga ashe ba wasu bane face dakarun garinsu wadanda ke cikin wannan daki a kulle, su duka sun zo bakin kofar dakin sun tsaitsaya wacce take a kulle da katon kwado kuma an yi tane da sandunan karfe mai kauri.
Nan take Huzaifa ya sunkuya ya dauki takobinsa ya tofa mata wata addua sannan ya dagata sama ya sare kwadon mukullin da aka rufe kofar da shi.
Take kwadon ya fadi kasa kofar ta bude, sai dakarun suka fito waje gaba dayansu cikin tsananin farinciki suna yiwa Allah godiya gami da yiwa Huzaifa jinjina.
Nan dai aka dunguma da nufin a fice daga cikin kurkukun gaba daya amma sai Huzaifa ya tsaya cak! Sakamakon aljani hurusul Marwas a kwance yana nishi ya kasa tashi.
Cikin kaduwa Huzaifa ya ruga gareshi ya durkusa a gabansa yace, ya kai dan uwanavv menene ya sameka ka kasa tashi kana ta nishi haka?
Hurusul Marwas ya budi baki da kyar yace, shi baka ganin yadda fuka fukina na hagu ya kumbura bane?
Ai na karye ne kuma ba zan iya koda motsawa ba daga nan face an gyara mini wannan karaya.
Koda Huzaifa ya dubi fuka fukin ya ga yadda ya karye kuma ya kumbura sumtum! Sai hankalinsa ya dugunzuma domin bai san yadda ake DOA aljanu ba yayin da suka karye.
Huzaifa ya dubi aljani hurusul Marwas yace, yanzu menene abinyi?
Kaga dai inda zamu taru mu duka nan ni da dakarun nan da muka ceto rayuwarsu ba za mu iya daukarka ba sannan kuma bamu san yadda ake gyara karaya ba irin taku ta aljanu.
Koda jin wannan batu sai aljani hurusul Marwas yayi murmushin karfin haki yace, ai batun gyaran karayarmu iri dayane da naku, kawai yanzu ku garzaya ku samo itatuwan bishiya masu kauri gami da danyar jijiyar bishiya kuzo ku gyara karayar da sauri kafin abokan gaba su zo su afka mana domin na san cewa nan da zuwa wani lokaci akilin sarki shaaran zai iya samun labarin halin da kurkuku ke ciki aboda tsegumi irin na yan uwana aljanu. Yanzu ma karfin addu'armu ne ya hana aljanun dake yaso munafunci zuwa kusa da nan bare su san halin da ake ciki.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa ya umarci wasu daga cikin dakarun na musulunci da su ruga suje u samo manyan itatuwa da danyar jijiyar bishiya.
Nan da nan kuwa dakarun suka cika umarni. Lokacin da aka zo da abubuwa biyun sai aljani hurusul Marwas ya dubi yarima Huzaifa yace, ina mai baku shawara daku samo murtukekiyar sarkar karfe ku fara daure hannayena, kafafuna da wuyana kasa cikin dirkoki in ba haka ba kuwa gyaran karayar nan ba zai yiwu ba.
Koda jin wannan batu sai yarima Huzaifa yayi murmushi yace, hakika aikin mai shawara baya baci.
Aaje a samo irin sarkokin da ake daure fursunonin aljanu a gidan nan, sannan vkuma ina son muci gaba da yin adduoi gaba dayanmu domin Allah ya hana abokan gabarmu zuwa nan harmu kammala duk abinda muka zo yi.
Nan take kuwa akayi amfani da wannan umarni.
Bayan an samo wata murtukekiyar sarkar karfe an daure hanaye, kafafu da wuyan aljani hurusul Marwas a jikin wadan su manyan dirkokin gini, sai hurusul Marwas ya sake bayar da shawara a toshe bakinsa da tsummokara a daureshi tamau.
Wannan shawara ma ba ayi biris da ita ba,, koda aka fara gyara karayar fuka fukin nasa kuwa yaji wani irin mugun radadi da zugi sai ya yunkura cikin azabbaben karfi, ya kwarara uban ihu.
Da yake bakinsa a toshe yake sai ihun ya zamo kamar an busa bututun algaita, amma duk da haka sai da karar sautin ta cika birnin shumbul gaba daya ta firgita komai da kowa.
Motsawar da yayi kuwa, sai da gaba dayan ginin gidan kurkukun yayi girgiza kamar zai rushe.
Cikin hanzari Huzaifa da sauran jamaarsa suka daka tsalle suka dira akan hurusul Marwas suna kokarin danneshi.
Duk da haka sai suka kasa ladaftar da shi domin da zarar ya yunkura sakamakon zafin da yake ji na gyaran karayar sai kaga ya watsar da su kasa tamkar busassun ganyayen bishiya na zubowa kasa.
* * * * * *
A can gidan sarautar sarki shaaran kuwa, lokacin da wakilin sarki da sauran jamaar asa suka jiyo sautin ihun aljani hurusul Marwas dai suka rude kuma suka cika da tsananin mamaki domin basu taba jin wani sauti ba makamancinsa a cikin garin.
Nan take wani babban badakare ya dubi wakilin sarki yace, ya shugabana anya kuwa ba abokan gabarmu mune suka shigo cikin garin nan bamu sani ba suka fara yi mana yakin sunkuru?
Koda jin wannan tambaya sai wakilin sarki shaaran ya dakawa badakaren tsawa yace, hana wannan wacce irin maganar banza kakeyi ne haka?
Ta yaya abokan gaba zasu iya shigowa cikin garin nan ba tare da mun sani ba alhalin ka san cewa a ko ina kuma dare da rana aljannunmu masu gadin birnin nan suna sintiri suna kewaya garin?
Badakaren ya numfasa yace, ya shugabana ni fa alamarin mutanen nan maabota addinin musulunci yana bani tsoro saboda suna da matukar karfin sihiri.
Ka tuna cewar bamu taba jin irin wannan sauti ba a garin nan sai wannan karon, kuma mutum ba zai iya fitar da wannan sauti ba sai dai gawurtaccen jarumin aljani kamar irin aljanun da suje gadin kurkukun sarki da gidan gonarsa.
Ni dai ina mai bayar da shawara ka tura dakaru suje su gano halin da kurkukun yake cikin da kuma gidan gona don kada makiya su zo su shammacemu.
Saadda wakilin sarki yaji wannan batu sai ya gyada kai yace, hakika aikin mai shawara baya baci, amma ai na san cewa babu ta yadda za'ayi makiya su iya shigowa cikin garin nan ba tar da asirinsu ya tonu ba saboda irin kwararan matakan tsaron da sarki ya dauka.
Koda gama fadin hakan sai wakilin sarki ya dubi wannan badakaren yace dashi yayi sauri ya hau dokinsa ya tafi izuwa kurkuku ya gano halin da yake ciki, sannan kuma ya wuce izuwa can gidan gonar sarki can ma ya gan ko akwai wata matsala.
Nan take kuwa badakaren ya hau dokinsa ya zabureshi da gudu ya nufi hanyar da zata kaishi kurkukun.
* * * * * *
A can kurkuku kuwa, cikin gaggawa su Huzaifa suka gama gyaran karayar aljani hurusul Marwas sannan Huzaifa ya bayar da wata addua ta musamman yace kowa yayi ta biyata a cikin zuciyarta sannan ya umarci humzalu da yayi musu jagora izuwa gidan gonar sarki.
Nan take kuwa suka hau dawakansu su duka suka fice daga cikin gidan kurkukun suna ta karanta wannan assay addua da Huzaifa ya basu suna ta wuce gawarwakin dakarun dake tsaro gaba daya.
Sai a wannan lokacine ragowar dakarun kurkukun da ke can kofofin farko na shigowa suka ankara da abinda ke faruwa, suka ruga da gudu izuwa kan su yarima Huzaifa da nufin su kashe su.
Nanfa aka rugumtsume da sabon azabbaben yaki.
Da yake wannan karon su Huzaifa na tare da dakarun musulunci sai nan da nan suka sami nasarar yakin.
Koda tsirarun dakarun suka ga saura su yan kadan sai suka zubar da makamansu suka fara yunkurin guduwa.
Cikin daga murya Huzaifa ya bayar da umarnin kada a bari dayansu ya tsira ya gudu daga cikin kurkukun.
Aikuwa sai dakarun musulunci suka rinka kurewa dakarun kurkukun gudu suna rafkesu.
Nan da nan aka karar dasu gaba daya. Faruwar haka ke da wuya sai aka sake hawa dawakai da nufin a tafi izuwa gidan gonar sarki. Har an iso baki kofar fita daga kurkukun sai wani tunani ya fadowa Huzaifa kawai sai yaja linzamin dokinsa ya tsaya cak sannan ya dubi hunzalu da sauran dakaru na musulunci ya ce, ba zamu iya tafiya ba izuwa gidan gonar sarki a haka ba dole ne mu yi bad da kama muyi shiga irin ta dakarun sarki shaaran yadda ko akan hanya babu mai taremu.
Wasu daga cikinmu kuma dole ne su yi shiga ta bayi sannan ina son mutum hudu daga cikinku wadanda zasu iya kundunbala su tsaya a bakin kofar kurkukun nan a matsayin masu gadi a cikin shigar masu gadin domin jikina ya bani cewa a ko Yaushe wakilin sarki shaaran zai iya turo mutanensa domin su zo su ga halin da kurkukun nan ke ciki.
Yanzu su waye zasu iya yin wannan kundunbala mu barsu anan kofar kirkir koda dai sun mutu sun san cewa shahada sukayi?
Kafin Huzaifa ya rufe bakinsa tuni gaba daya dakarun sun budi baki cikin hadin murya kowa dacewa shi ya amince.
Koda jin haka sai Farin ciki ya kama Huzaifa ya dubesu yace, hakika duka imaninku ya inganta domin dukka musulmi na gari yana da burin shahada.
Koda gana fadin hakan sai nan da nan aka shiga shirye shiryen sauya tufafi.
Cikin kankanin lokaci kowa ya gama komtsawa. Aljani hurusul Marwas ne kadai bai yi shiga irin ta dakarun shaaran ba a matsayinsa na aljani.
Take aka bar mutum hudu a bakin kofar kurkukun suka yi tsayuwa irin wacce masu gadin kurkukun ke yi koda Yaushe.
A sannane Huzaifa da sauran dakarun suka tusa keyar dakarunsu da suka yi shigar bayi suka gaba, hunzalu ne akan gaba cikin shigar dakarun birnin yana yi musu jagora, Huzaifa na daga can bayan karshe.
Suna cikin wannan tafiya ne suka yi kicibus da wannan badakare wanda wakilin sarki shaaran ya turo shi kurkukun domin yaga halin da kurkukun ke ciki.
Koda ganinsa sai wani daga cikin dakarun musulunci ya yunkura zai zare wuka ya kasheshi, amma sai Huzaifa ya yi masa inkiyar ya kyaleshi.
Lokacin da badakaren ya karaso dag da su ya ga ashe hunzalu ne ke jagorantar wadannan bayi sai ya risina cikin girmamawa ya gaisheshi yace, ya shugabana daga ina kuke haka, kuma ina zaku kai da wadannan bayi haka?
Koda jin wannan tambaya sai hunzalu ya dubi badakaren yace, daga kurkuku muke kuma gidan gonar sarki zamu kai wadannan fursunoni domin su canji maaiakatan can kamar yadda aka sabayi kullum.
Koda jin wannan batu sai mamaki ya kama badakaren yace, haba ya shugabana ta yaya zaka debo fursunoni daga kurkuku ka kaisu can gidan gonar sarki alhalin kafin sarki ya taci yaki ya kafa doka mai tsauri cewar babu mahalukin da zai sake shiga ko fita daga cikin kurkuku da gidan gonarsa?
Yanzu haka ma wakilin sarki ne yace na zo na ga halin da kurkukun ke ciki sannan na wuce izuwa can gidan gonar tasa, can ma na ga lafiyar sa.
Saadda badakaren yazo nan a zancensa sai yaji hunzalu ya bushe da dariya.
Lokaci guda kuma ya turbine fuskarsa ya daka masa tsawa yace, ina hankalinka ya taci ne?
Shin kana zaton zan aikata abinda zai bata ran sarki ne alhalin na san cewa ko yaya nayi wani kuskure sawa zaiyi a kashe dana guda daya dake tare a inda ban sani ba?
Ka sani cewa ni ne mai kula da aiyukan gidan gonar sarki idan aikin gonar sarki ya tsaya ko aka sami wata matsala yana dawowa zai hukuntani.
Ka ga ni yanzu kana bata mini lokaci kuma kana batawa kanka lokaci gwara ka tafi izuwa Aiken da aka yi maka.
Koda gama fadin hakan sai hunzalu ya bangaje wannan badakaren ya wuce gaba ayarin su Huzaifa suka take masa baya.
Da yake duk u Huzaifa suna sanye ne hulunan karfe ne badakaren bai ga fuskar dayansu ba bare ya gane cewar ba dakarun kasar bane, amma sai ya tafi yana waigensu cikin alamun mamaki da rashin yarda.
A wannan lokaci aljani hurusul Marwas na can sama cikin gajimare yana bin su Huzaifa kuma yana karanta dduar da Huzaifa ya bayar dalilin da ya sa sauran aljanun dake shawagi a sararin saman garin suka kasa ganinsa ke nan kuma suka kasa ganin su Huzaifa.
Lokacin da su Huzaifa suka ci gaba da tafiya sai wani badakare dake kusa da Huzaifa ya dubeshi cikin girmamawa yace, ya shugabana me yasa ba ka barni na kashe wancan badakaren ba dazu?
Kayi sani cewa barinsa a da rai a garemu ba karamin ganganci bane domin ga dukkan alamu bai yarda da mu ba, kuma zai iya zuwa ya kai labarin mu ga wakilin sarki shaaran can fada a turo mana mayaka masu yawa su kawo mana hari.
Saadda Huzaifa yaji wannan batu sai yayi ajiyar zuciya sannan yace, tabbas abinda ka fada gaskiya ne, to amma kuma kashe shin shine abu mafi hadari a garemu domin idan wakilin sarki ya ga ya dade bai koma ba zai turo abu sawunsa kuma idan aka zo aka ga gawarsa za'a gane cewar mun shigo cikin garin sai abi sawunmu har can gidan gonar a tarfa mu.
Yanzu kuwa idan yaje kofar kurkukun yaga dakarunsu a tsaye babu alamar wata matsala zai juyo ne ya biyomu izuwa can gidan gonar sarki, kafin ya riskemu kuma tuni mu munje mun dauko luhaira.
Koda Huzaifa yazo nan a zancensa sai gaba daya dakarun suka gamsu da bayaninsa kuma suka cika da tsananin mamakin irin basirarsa da yadda akayi ya shirya wannan dabara.
Alhamdulillahi nan zan da kata sai Allah ya kaimu sati mai zuwa zaku jini dauke da ci gaban wannan labari.
Sunana Umar Farouq Zango nake muku Fatan alkhairi sai mun hadu a ranar jumaa idan Allah ya kaimu.🙏🙏🙏🙏
[12/14, 6:53 PM] INSTRUCTOR⚓: **DAKARUN MUSULUNCI**
LITTAFI NA BIYAR 5
Part B ❤️ ♥️
NA ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI👮👮
Typing:- UMAR FAROUQ ZANGO.✍️
Posting:- Najibullahi Muhammad 🥷🥷
Haka dai suka ci gaba da tafiya har tsawon kusan rabin sa'a sannan suka iso kofar gidan gonar sarki.
Tun daga mesa gabansu ya fadi sakamakon hango irin tsananin tsaron da ke gidan gonar, wanda ya ninka na kurkukun sau goma.
Nan take zuciyoyinsu suka karaya suka tabbar da cewar babu yadda za'ayi su shiga cikin wannan gidan gona cikin irin Saar da nasarar da suka samu a can kurkuku kuma komai zai iya faruwa ko dai su rasa rayuwarsu ko kuma a dade ana gumurzu har wakilin sarki ya san da zuwan su azo ayi musu rubdugu.
Koda yarima Huzaifa ya gama aiyana wannan alamari sai hankalinsa ya dugunzuma ya rasa abinda ke masa dadi ya fara shawara da zuciyar sa.
Abin da ya fado masa a rai shine, idan har basu sami damar shiga cikin gidan gonar ba kai tsaye har su gano inda Luhaira take a cikin kankanin lokaci ba duk shirin su ya wargatse.
Har suka karasa daf da kofar gidan gonar Huzaifa bai sami wata mafita ba.
Da isowarsu sai dakarun dake tsaron kofar suka dakatar dasu.
Shugaban masu gadin ya dubi Hunzalu a fusace yace, menene ya kawoka nan tare da bayi kalilan da kuma dakaru masu yawa haka?
Koda jin wannan tambaya sai zuciyar sa ta buga da karfi, tsoro ya baibayeshi ya firgita ainun domin yana ganin cewa asirinsa ya tonu amma sai ya yi ta maza ya dakawa shugaban masu gadin tsawa yace, shin ka manta da wanda kake maganane?
Ka manta da cewar nine mai kula da dukkanin bayin dake aiki a cikin gidan gonar nan fiye da shekaru talatin baya har ma sai da dana yazo ya gajeni?
Koda jin wannan batu sai shugaban masu gadin ya bushe da dariyar mugunta, lokaci guda kuma ya turbune fuskarsa yace, ai duk maganar da kake yi alamarin ne na da wanda ya wuce.
Shin ka manta ne da cewar dan naka daya gajeka Yanzu haka baya kan aikinsa kuma an sare masa hannuwansa da kafafunsa kuma antsire idamunsa sakamakon laifin da ya aikata na kusantar amaryar da sarki zai aura.
Kai kanka yaushe rabonka da shiga cikin gidan gonar nan, a kallah ankai sati guda.
Kuma sarkine da kansa ya dakatar da kai don tabbatar da tsaro a gidan gonar gaba daya bisa barazanar abokan gaba.
Ina mai tabbatar maka da cewa idan ba sarki shaaran bane ya zo da kansa nan yace mu bude maka kofa ku shiga ba babu yadda za'ayi ku shiga cikin gidan nan.
Koda jin wannan batu sai hankali su yarima Huzaifa ya dugunzuma ainun suka rasa abin da ke musu dadi.
Shugaban masu gadin ya sake duban hunzalu ya daka masa tsawa yace, ya kai hunzalu ina mai shawartarka da ka gaggauta janye gidan gonar nan kafin cikar dakika dari ko Yanzu nan na umarci dakaruna dake kan ganuwa suyi musu ruwan kibau.
Yana gama fadin hakan sai ya juya ya koma can bakin kofar gidan gonar inda sauran yan uwansa masu gadi suke.
Nan take hunzalu ya karaso gaban yarima Huzaifa ya dubeshi cikin tsananin damuwa yace, ya shugabana yanzu menene abinyi?
Kawai sai Huzaifa yace, ku zo mu koma da baya izuwa can cikin duhuwar dajin can.
Ba tare da bata lokaciba suka bi wannan umarni suka shige izuwa cikin duhuwar ciyayi da bishiyoyi wadanda ke nesa kadan da kofar gidan gonar inda ba a iya hangosu.
Da shigar su wannan wuri sai suka sauko daga kan damakansu kowa ya zauna a kasa dirshan cikin alamun karayar zuciya aka yi tsit tamkar babu mai laka a jikinsu.
Tsawon yan dakiku dayansu baice uffan ba kowa yana tunani, a sannane hunzalu ya dubi yarima Huzaifa yace, ya shugabana yanzu kana da wata dabara ne wacce kake ganin zamu iya amfani da ita wajen samun nasarar dauko Luhaira kuma mu fito a raye ba tare da mun fuskanci wata matsala ba?
Lokacin da hunzalu ya zo nan a zancensa sai Huzaifa yayi ajiyar zuciya sannan yace, a rayuwata ban taba samun karayar zuciya ba irin ta yanzu bisa duk abinda nasa a gabana.
Ina da yakinin cewa Allah zai iya bamu nasarar shiga cikin wannan gidan gona bisa taimakonsa, to amma bani da tabbacin cewar da yawan mu bazamu rasa rayuwarmu ba.
Abu na biyu shine, duk a cikinmu babu wanda yasan ainahin dai dai gurin da Luhaira take bare da zarar mun shiga ciki mu wuce kai tsaye izuwa wajen dole sai mun bata lokaci mai yawa wajen gano wajen ko kuwa hunzalu ka san inda aka ajiye Luhaira?
Humzalu ya gyada kai yace,ai kullum ai an sauyawa Luhaira dakin kwana a cikin gidan gonar nan, kuma a kallah dakunan sun fi guda dari uku, sannan kowanne daki tsakaninsa da wank akwai tazara ta a kalla tafiyar rabin saa.
Koda jin wannan batu sai zuciyar yarima Huzaifa ta sake karaya fiye da ko yaushe yaji kamar ya fashe da kuka saboda takaici, kawai sai ya dubi gaba daya dakarun yace, ku tashi muyi kokarin barin garin nan ba zamu iya shiga cikin gidan gonar nan ba har mu iya dauko Luhaira.
Tunda dai Allah ya sa ni da su aljani hurusul Marwas mun sami nasarar ceto rayuwarku ai mun sami gagarumar nasara ta farko.
Koda gama fadin hakan sai kowa ya mike da nufin a hau dawakai abi wata barauniyar hanya wacce zata kutsa dasu izuwa cikin daji.
Kwatsam! Sai suka hango badakaren nan wanda wakilin sarki ya tura can kurkuku domin yaga abinda ke faruwa bisa doki a sukwane ya durfafi kofar gidan gonar. Koda ganin haka sai hankalin su Huzaifa ya sake dugunzuma ainun domin sun san cewa da zarar ya iso bakin kofar gidan gonar ya tambayi labarin su asirinsu ya tonu kenan.
Ba zato ba tsammani sai kuma suka sake hango aljani hurusul Marwas ya sauko daga sama ya sure shi da dokinsa gaba daya yayi sama da su kamar shawo ya suri dantsako kuna dai ya lullubesu da fuka fukansa ya luluka da su izuwa can kololuwar sama.
Kafin kiftawar ido ya bace bat! Bayan yan dakiku sai gashi ya sake bayyana tsulum! A gaban Huzaifa.
Kawai sai ya dubeshi yace, ya shugabana ka yi mini izini ni kadai zan shiga cikin gidan gonar nan na dauko Luhaira cikin ikon Allah batare da asirina ya tonu ba.
Kuma a cikin dakiku kadan zan hattama wannan aiki.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yayi murmushi sannan yace, Yanzu ina kakai wannan badakaren da dokinsa?
Hurusul Marwas najin wannan tambaya sai ya mai da masa da martanin musmushin sannan yace ai tuni nayi aikin namu na aljanu.
Cikin jikinsa na shiga na komar da shi izuwa can wajen wakilin sarki ya shaida masa cewar yaje kurkuku da gidan gona ya tabbatar da babu wata matsala.
Bayan wakilin sarki ya sallameshi ya koma cikin yan uwansa bayi kuma sai na shafeshi na sa masa barci mai nauyi saboda ina tsoro cewar bayan na fita daga jikinsa zai iya dawowa cikin hayyacinsa ya koma wajen wakilin sarki ya sanar da shi ainahin gaskiyar alamari.
Koda aljani hurusul Marwas yazo nan a jawabinsa sai murna ta kama yarima Huzaifa da su Humzalu kuma suka Sam cikakken kwanciyar hankali.
Cikin faraa Huzaifa ya dubi aljani hurusul Marwas yace, tabbas Yanzu ne na dada tabbatarda cewa ni da kai duk muna bukatar juna kuma idan dayanmu baya tare da dayan to babu yadda za'ayi ya sami nasarar cika aikin da yazo yi a kasarnan.
Ya kai hurusul Marwas nayi maka izini maza ka shiga cikin gidan gonar nan ka dauko mini Luhaira.
Hurusul Marwas ya risina yace, an gama ya shugabana.
Kafin ya budi baki yace wani abu tuni aljani hurusul Marwas ya bace bat daga gabansa.
Nan fa tunanin zuci yace fadowa Huzaifa ya tambayi zuciyar sa yana mai cewa, menene dalilin da yasa aljani hurusul Marwas ya kirani da matsayin shugabansa a wannan karon alhalin tun daga lokacin da muka hadu dashi abokina yake kirana dashi?
Amsar da Huzaifa ya kasa baiwa kansa kenan, amma sai ya kudure a cikin ramsa cewar idan suka sami nutsuwa dai ya yi masa wannan tambayar.
Huzaifa na cikin yin wannan tunani ne kawai yaga aljani hurusul Marwas ya sake baiyana tsulum! A gabansa goge da Luhaira gadon bayansa amma ko ina a jikin hurusul Marwas sara ne na takobi sai jinine ke kwarara daga jikinsa.
Da rub da ciki aljani hurusul Marwas ya kife kasa yana numfashi sama sama, ita kuwa Luhaira dake kwance a bayansa, barci take ta faman sharara bata ma san abinda ke faruwa ba.
A dimauce, cikin tsananin firgici yarima Huzaifa ya dauke Luhaira daga kan bayansa. Hurusul Marwas ya shimfide akan ciyawa gefe daya sannan suka taru akan aljani hurusul Marwas suna yi masa magani gami da tofa masa adduoi domin su ceto rayuwarsa.
Sai da lokaci mai dan tsawo ya shafe sannan numfashin aljani hurusu Marwas ya dawo dai dai har ya iya bude idanunsa.
Koda ya tsinci kansa a gabansu Huzaifa kuma yaga Luhaira kwance a cana gefe daya tana ta shara barcinta sai ya yi kabbara cikin tsananin Farin ciki kuma yayi godiya ga Allah, sannan ya mike zaune ya dubi Huzaifa yace, ya shugabana burina na farko ya cika tunda har bukatunka sun biya bisa abinda kazo nema a garin nan.
Ka kubutar da dakarunku wadanda aka tsare a kurkuku sannan kuma ka dauko Luhaira.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yayi murmushi a gareshi yace, a'a gyara maganar ka, ba nine na dauko Luhaira ba kaine, kuma in ba don kai na da babu yadda za'ayi na iya daukota.
Gama fadin hakan ke da wuya sai hankalin kowa ya koma kan Luhaira wacce ke kwance akan ciyawa.
Nan fa su duka suka dimauce bisa ganin irin tsananin kyawun da Allah ya bata domin inda za'a hada kyawun gimbiya Lafirta dana yar uwarta Sazirat a waje guda bazai kai rabin ma Luhaira ba.
A wannan lokaci wata doguwar riga ce fara kal mai shara shara a jikinta, don haka duk surar jikinta a fili take, musamman ma idan iska ta kada rigar.
Cikin gaggawa Huzaifa ya cire alkyabbar jikinsa ya lullubeta da ita sanna ya dubi aljani hurusul Marwas yace, ya kai dan uwana yanzu menene abinyi?
Koda jin wannan tambaya sai hurusul Marwas yayi murmushi yace, babu abinyi face muyi sauri mu bar garin nan mu durfafi birninku na Darul husuf domin muje mu ga halin da ake ciki, walau anci nasarar yakin da ake yi ko ba'a ci ba.
Koda jin wannan batu sai Huzaifa yaji gaba daya hankalinsa ya koma kan birnin Darul Husuf.
Nan take ya sake daukar Luhaira ya dorata a gadon bayan aljani Hurusul Marwas sannan shima ya kama dokinsa ya hau, suma su Humzalu sai suka yi koyi da shi.
Nan take aka ci gaba da tafiya ana karanta wannan addua wacce yarima Huzaifa ya bayar tun da farko.
*wannan shine abinda ya faru ga su Huzaifa, bayan sun sami nasarar debo fursunoninsu daga kurkukun sarki shaaran kuma sun dauko Luhaira daga gidan gonar sa bayan sun sha bakar wahala da bakin gumurzu*
* * * * * *
Al'markin su sarki shaaran kuwa, bayan ya gama sanar da mahaifiyar ukashat duk abinda ya faru da kuma hukuncin da zai dauka na gaba wato neman taimakon dakarun yaki daga sauran kasashen kafirai na nahiyar don aje a yiwa birnin Darul Husuf rubdugu a gama da shi farat daya, sai ta kyalkyale da dariyar Fatin ciki sannan kuma ta tashe da kukan bakin ciki tace, tabbas dana ukashat ya ci amanata a matsayina na mahaifiyarsa, kuma ya bani kunya.
Lallai da hannayena zan kashe shi, amma kuma nayi matukar Farin ciki daka sami nasarar cin wannan birni namu da yaki cikin BAZATO!
Shawarar da zan baka itace, ka gaggauta shirin tafiya izuwa kasashen makwabtaka domin nemo dakarun gudunmawa na yaki amma kafin ka tafi ka bar jiran gari nan a hannuna.
Nayi maka alkawarin cewar kafin ma a sake yin yakin karshe zan kama sarki Uwaisul Karni da duk mukarrabansa sai dai ka dawo ka iskesu a cikin kurkuku a tsare.
Koda jin wannan batu sai sarki shaaran da yarda Sazirat suka kalli junan su sannan suka kalli mahaifiyar ukashat cikin alamun rashin yadda da gamsuwa, kawai sai suka koma gefe daya sukayi dan kuskuks.
Sarki shaaran ya dawo wajena ya dubeta yace, yake matar babban maki yina, kiyi sani cewa na yi shawara da yata Sazirat kuma mun yanke hukuncin cewar zamu bar Miki jiran birnin Darul Husuf a hannunki, amm bisa sharadi guda.
Sharadin kuwa shine, idan har da gaske zaki iya kama sarki uwaisul karni shi da mukarrabansa har ki tsaresu a kurkuku to mu dawo mu iske kan danki ukashat a tsire a jikin ice akan ganuwar garin nan.
Idan kuwa muka dawo muka ga babu wannan kai na Danko, to mun san cewa yaudararmu kikayi don haka zamu shigo cikin birnin ne da karfin tsiya mu sake yakarku kuma mu kashe kowa da komai ko kaza guda daya bazamu barta da rai ba.
Koda jin wannan sharadi sai hankalin mahaifiyar ukashat ya dugunzuma ainun saboda ta san cewa bazata iya kashe danta ba ko kuma ta sa wani ya kashe shi komai tsanar da take yi masa a rayuwarta.
Nan take ta nuna cewa zata cika wannan umarni, amma tan bukatar a bar mata kamar dakaru dubu dari wadanda zasu karta ta sami ikon tafiyar d komai kamar yadda ya kamata, sarki shaaran yayi murmushi yace, shikenan na amince da hakan.
Nan take ya ware dakaru dubu dari aka barsua birnin Darul Husuf sannan sarki shaaran, Sazirat da sauran dakarunsu suka yi shiri suka hau dawakansu suka fice daga cikin birnin suka nausa cikin daji a guje suka durfafi hanyar da zata kaisu birninsu na shumbul.
* * * * * *
Bayan kamar rabin sa'a da bacewar sarki shaaran a cikin daji, sai tawagar su sarki uwaisul karni ta bullo daga wata hanya daban ta durfafi birnin Darul Husuf.
Sarki uwaisul karni ne akan gaba tare da yarima ukashat.
Su da dukkanin dakarun dake biye da su sun yi shigar yaki ne dauke da makamai.
A wanann lokaci rana bata fadi ba amma magriba ta kawo kai.
Kafin a isa inda za'a iya hango kofar birnin sai sarki uwaisul karni ya ja linzamin dokinsa ya tsaya cak! Kuma ya bayar da umarnin a tsaya a wajen a kafa tantuna.
Alamarin da ya baiwa kowa mamaki ke nan, saboda bai kamata a tsaya a daji ba dag da magriba tunda ana dag da shia gari.
Alhamdulillahi, anan zan dakata kuma sai Allah ya kuma ara mana rana irin ta yau zaku jini dauke da ci gaban wannan Littafi.
[12/14, 6:53 PM] INSTRUCTOR⚓: **DAKARUN MUSULUNCI**
LITTAFI NA BIYAR 5