Sashe 8
Canjin Rayuwa Part 4 Complete Hausa Novel · about 4 min read
2⃣5⃣Daidai lokacin kuma Alhaji ya shigo, yana jiyo hayaniya, yace, Hama lfy kuke min hayaniya da farar magriba? Tace, Zainabu ce zatayi min rashin kunya, don yara sunce ba zasu iya cin abincinta ba. Alhaji yace, sbd me? Tace, to abincin bai ciyo don bata iyaba. Alhaji mutum ne wanda komai qanqantar magana, sai ya ririta ta. Don haka sai yace, yanason duk 'yan gidan su hallara. Ya tara su har zainabun. Yace, su fada masa da gske ne girkin Zainabu babu dadi? Maman bushira tace, injiwa? To kai da zaka tambayemu baka ta6a ci bane? Yace, to iya magana, jikar zance, ban dake, don na kula kinfi son yarinyarnan da iyalina. Ya dinga bin yaran da sauran matan yana tambayarsu ko ta iya? Suka dinga cewa babu dadi. Sai 'ya'yan Maman bushira ne kurum Sukace sudai suna ci. Alhaji yace, ban ta6a cin abincinta ba amma yau zanci, in har baiyi dadi ba, kamar yadda kuka ce, to zan dauki mataki. Don bazan dinga fita da sassafe neman abinci ba, sannan kizo kina girka shi son ranki, a kasa ci ana zubar dashi. Zainabu dai shiru tayi, sbd ba tada ta cewa, amma fatanta shine Allah yasa ya yanke mata hukuncin saki.
Shi Alhaji ba mutum bane maicin abincin gidansa, yafi zuwa Gidan abinci shagunan masu indomie koko gurin masu tsire. Dakinsa ya kira Zainabu yace, ta bude abincin ya gani. Jikinta sai 6ari yake, ta bude, qauri ya cika dakin. Yace, eh lallai dole yara su kasa cin abinci, tun kafin in kaishi baka ne wannan qaurin yake tashi? Ta kalleshi cikin tsananin tsoro, yace, uwarki bata koya miki girki bane? Tace, ni ban iya yin girki da babbar tukunya ba, kuma gashi a murhu. Yace, da Allah rufe min baki! Nine zaki fadawa baki iya girki a murhu ba. Ubanki baya iya ci da gidanku. Ni nake riqe da gidanku, da har zakice min baki iya girki da murhu ba. Wa zaki gaya ma kokai dan uban waye. Da dai kince sakaryar uwarki bata koya miki ba, sai yawon talla da nafi yarda. Ran Zainabu yakai maqura gurin 6aci, tace nidai gsky duk abinda za'ayi, ayi, amma a daina zagin iyayena. Kuma ai duk yaushe muka hadu da zaka ce kai ne kake ci da gidanmu? Ashe Zainabu ta tafka kuskure daya fada ta fada. Domin ba'a fadi yana fadi. Nan take ya tashi a fusace, ya hau kilarta. Maman bushira tana zaune Zugum tana jiyo ihun Zainabu, baqin ciki fal a zuciyarta, domin tana tsoron kar wannan halin da mijinta keyi ya juye kan 'ya'yanta, sbd in ka cutar da dan wani, sai an cutar da naka don kaima kaji. Haka yayi ta kilarta har ya gaji, yabarta don ba zuwa ceto.
2⃣6⃣Tun Zainabu tana kuka har ta kasa. Yace, tashi ki fitarmin a daki! Kasa tashi tayi, domin data yunqura, sai ta koma ta zube. Sai kuma ga jini ya soma zuba. Idanu ya zaro yana kallonta. Sai kuma ya soma kiran Maman bushira. Ta shigo ranta 6ace, yace, kamata zuwa daki, naga jini yana zuba, ko dai al'ada takeyi? Maman bushira tace, wace al'ada kuma? Yarinyarnan ciki gareta, saidai inka sake doko cikin. Yace, ni ban doketa a ciki ba. Maman bushira ta dago ta tana kiran sunanta "Zainabu! Zainabu! Cikin tsoro tace, Alhaji yarinyarnan tana da rai kuwa? Da sauri yasa takalmi yace dauke ta zuwa dakinta, bari in kira danladi Mai chemist. Tace, ka dauketa dai, ni ai bazan iyaba. Cikin tsawa yace, kama ta muje mana. Kan gadonta suka dora ta, duk jini ya 6ata hanyar da kuma dakinsa da nata. Ya fita da sauri. Maman bushira tace, maganinka kenan! Allah yasa ya zamar maka ishara. Zainabu dai tanaji, ba suma tayi ba, amma tana cikin mawuyacin hali. Sake yin lamo tayi tare da sakin jiki sbd jin rudewar da Alhaji yayi. Ko da danladi mai chemist yazo, dauke Numfashinta tayi. Dama shi ba wai ilimin gareshi ba, ya ta6a yin shara ne a asibitin Gwamnati, shine yazo ya bude chemist mutane suke ta tururuwa. Danladi yana ta6a ta, sai yace wai, wai, Alhaji! Gsky kuje asibiti, don gsky ba zan iya ba. Dubi jinin fa kamar an yanka qaramar dabba. Alhaji ya zaro ido cikin fargaba, to ni yanxu wane asibiti zamuje? Banason zuwa wannan asibitin Gwamnatin. baba yace bari in kwatanta maka wani na kudi ka kaita bakinka alaikum.
Sun kaita, an amsheta, amma yayi kashin kudi masu yawa, sannan kuma cikin yananan bai fita ba. Bayan tafiyarsa Gida, gurin qarfe sha daya Nurse din da ta taya likitan aiki lokacin da ake qoqarin tsaida jinin, ta samu maman bushira a zaune kan kujerar dake kusa da gadon da Zainabu take kai kwance, tace, sannu mama. Maman bushira tace, yauwa 'yan mata sannu da aiki. Mun gode fa. Tace, yauwa dan Allah mama, wannan 'yarki ce? Maman bushira tace, a'a kishiya ta ce. Nurse din ta zaro ido. "Kishiyarki kuma? Kina nufin wancan daya fita mijinku ne?" tace, eh.
[17/09 9:56 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
Shi Alhaji ba mutum bane maicin abincin gidansa, yafi zuwa Gidan abinci shagunan masu indomie koko gurin masu tsire. Dakinsa ya kira Zainabu yace, ta bude abincin ya gani. Jikinta sai 6ari yake, ta bude, qauri ya cika dakin. Yace, eh lallai dole yara su kasa cin abinci, tun kafin in kaishi baka ne wannan qaurin yake tashi? Ta kalleshi cikin tsananin tsoro, yace, uwarki bata koya miki girki bane? Tace, ni ban iya yin girki da babbar tukunya ba, kuma gashi a murhu. Yace, da Allah rufe min baki! Nine zaki fadawa baki iya girki a murhu ba. Ubanki baya iya ci da gidanku. Ni nake riqe da gidanku, da har zakice min baki iya girki da murhu ba. Wa zaki gaya ma kokai dan uban waye. Da dai kince sakaryar uwarki bata koya miki ba, sai yawon talla da nafi yarda. Ran Zainabu yakai maqura gurin 6aci, tace nidai gsky duk abinda za'ayi, ayi, amma a daina zagin iyayena. Kuma ai duk yaushe muka hadu da zaka ce kai ne kake ci da gidanmu? Ashe Zainabu ta tafka kuskure daya fada ta fada. Domin ba'a fadi yana fadi. Nan take ya tashi a fusace, ya hau kilarta. Maman bushira tana zaune Zugum tana jiyo ihun Zainabu, baqin ciki fal a zuciyarta, domin tana tsoron kar wannan halin da mijinta keyi ya juye kan 'ya'yanta, sbd in ka cutar da dan wani, sai an cutar da naka don kaima kaji. Haka yayi ta kilarta har ya gaji, yabarta don ba zuwa ceto.
2⃣6⃣Tun Zainabu tana kuka har ta kasa. Yace, tashi ki fitarmin a daki! Kasa tashi tayi, domin data yunqura, sai ta koma ta zube. Sai kuma ga jini ya soma zuba. Idanu ya zaro yana kallonta. Sai kuma ya soma kiran Maman bushira. Ta shigo ranta 6ace, yace, kamata zuwa daki, naga jini yana zuba, ko dai al'ada takeyi? Maman bushira tace, wace al'ada kuma? Yarinyarnan ciki gareta, saidai inka sake doko cikin. Yace, ni ban doketa a ciki ba. Maman bushira ta dago ta tana kiran sunanta "Zainabu! Zainabu! Cikin tsoro tace, Alhaji yarinyarnan tana da rai kuwa? Da sauri yasa takalmi yace dauke ta zuwa dakinta, bari in kira danladi Mai chemist. Tace, ka dauketa dai, ni ai bazan iyaba. Cikin tsawa yace, kama ta muje mana. Kan gadonta suka dora ta, duk jini ya 6ata hanyar da kuma dakinsa da nata. Ya fita da sauri. Maman bushira tace, maganinka kenan! Allah yasa ya zamar maka ishara. Zainabu dai tanaji, ba suma tayi ba, amma tana cikin mawuyacin hali. Sake yin lamo tayi tare da sakin jiki sbd jin rudewar da Alhaji yayi. Ko da danladi mai chemist yazo, dauke Numfashinta tayi. Dama shi ba wai ilimin gareshi ba, ya ta6a yin shara ne a asibitin Gwamnati, shine yazo ya bude chemist mutane suke ta tururuwa. Danladi yana ta6a ta, sai yace wai, wai, Alhaji! Gsky kuje asibiti, don gsky ba zan iya ba. Dubi jinin fa kamar an yanka qaramar dabba. Alhaji ya zaro ido cikin fargaba, to ni yanxu wane asibiti zamuje? Banason zuwa wannan asibitin Gwamnatin. baba yace bari in kwatanta maka wani na kudi ka kaita bakinka alaikum.
Sun kaita, an amsheta, amma yayi kashin kudi masu yawa, sannan kuma cikin yananan bai fita ba. Bayan tafiyarsa Gida, gurin qarfe sha daya Nurse din da ta taya likitan aiki lokacin da ake qoqarin tsaida jinin, ta samu maman bushira a zaune kan kujerar dake kusa da gadon da Zainabu take kai kwance, tace, sannu mama. Maman bushira tace, yauwa 'yan mata sannu da aiki. Mun gode fa. Tace, yauwa dan Allah mama, wannan 'yarki ce? Maman bushira tace, a'a kishiya ta ce. Nurse din ta zaro ido. "Kishiyarki kuma? Kina nufin wancan daya fita mijinku ne?" tace, eh.
[17/09 9:56 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa