Sashe 34
Canjin Rayuwa Part 4 Complete Hausa Novel · about 4 min read
1⃣1⃣1⃣Zantukansa ta hada dana Mahaifiyarta data sake kiranta a waya ta nana ta mata. Dole ta haqura, kuma ta yarda cewa, mijinta fa ba laifi yayi ba don ya qara aure. Sunna ya raya. Ba taji haushin kanta ba, sai ranar daya kawo mata zainabu, gaba daya sai taji ba taga abin kishi ba. Ita kuwa Zainabu sai taji tana shakkar Mimi. Ga wani qwarjini da Mimin tayi mata, har ita kanta Mimin ta lurabda haka. Don haka sai ita Mimin tace, kar fa kiji komai, nan gidan mijinki ne. Zainabu ta yarda Allah ne kawai ya bata Malam, domin mai kamar Mimi ba zai kalleta ba.
Mimi ta sauka, wannan ma Namiji ne, sai yaci sunan Alhaji. An sha suna, sannan itama zainabu ta kama nata laulayin. Lokacin Ismail baya qasa. Sun tafi Africa ta kudu. Shine ya kira Mimi ya fada mata cewa Zainabu babu lafiya, don Allah ta dubata. Mimi ta tausaya mata halin da ta sameta. Ita ce takai ta Asibiti. Bayan gwaje-gwaje an gano ciki wata biyu. Mimi ta wuce da ita Gidanta kafin mijin ya dawo. Dakin su Al'amin ta sauketa. Da yake ynxu tanada masu aiki, yarinya da tsohuwa, sannan sunada Mai gadi. Mimi tsakani da Allah take kula da Zainabu, kwana biyar ya dawo, samun Zainabu danyayi gurin Mimi tana samun kula, sai ya sake daga darajar Mimi. Harma ya fada mata cewa, My Dija, na jima da yarda cewa ko dabba na daure zaki kula da ita, bare Mutum. Hakan ya qara mata qaimi gurin zama zama da kishiyarta lfy. Zainabu ta haihu ta samu 'ya mace. Ga mamakin Mimi sai Zainabu tace ya sama 'yar sunan Mimi wato Khadija. 'ya kuwa taga kaya gurin Mimi.
1⃣1⃣2⃣Mimi cikin motarta tare da yaranta, a Abuja sunje bikin Na'ima ne ta auri wani maqwafcinsu da matarsa ta rasu gurin haihuwar danta na biyu. Bayan biki ya watse da ranar da zata tafi tace, bata barin Abuja, saita nemo mina qawarta. Gidan iyayen mina taje neman labarin. Har gidanta qanin mina ya raka Mimi anan cikin Abuja. Sun rungume juna sunata murna, kafin suka 6arke da labari. Mina tasha mamakin jin cewa, sheikh Ismail Abdurrahman shine Malaminta da mahaifinta ya bata. Tace, ta san shi domin yana daya daga cikin malaman da take nutsuwa da wa'azin su. Sai mallon mimi takeyi tana Mamakin ta. Tace dubeki kamar matar shugaban qasa, wai matar Malami. Mimi tayi dariya, tace kinsan Allah duk wadda mijinta ba Malami bane, ina mai jajanta mata, domin ta rasa abubuwa da dama. Me zanyi da wani shugaban qasa da ba zai samu lokacina ba sai na mutan qasa? Barni da mijina mai kasheni da kalolin soyayyarsa. Mina tace, qwarai na yarda dake, domin wata lakcarsa da naji yana yiwa mata da maza, saida nace, Allah yasa haka yakewa iyalinsa. Mimi tana dariya, tace yana min. Suna cikin haka saiga wayarsa. Mina kallon mimi takeyi tanata zuba shagwa6a a waya. Wai gobe zata dawo, shi kuma yace idanunsa aun qosa su ganta. Ta bashi mina sun gaisa, suka yi bankwana tare da amsar lambar juna. Rayuwar su mimi abin koyi ce ga mutane na qwarai.
Bayan shekara uku Ginin Ismail yayi nisa, na jami'a, lokacin Mimi tana goyon Abdurrahman sunan mahaifin ismail. Sannan sun tare a sabon gidan su dake nan layin, ita kuma Zainabu ya gyara mata inda suka tashi. Kwanciyar hankali da qaruwar arziki kullum suna cikinta. Yaran ta uku duk maza, Hajiya sauda tace, qila irin tawa zakiyi, sai na hudu ki samu mace. Ta dauko Ummi tana zama gurinta, kuma ta saka ta makaranta mai kyau. Ita ma kuma ta koma makaranta don ta samu digiri dinta ko ba za tayi aiki ba, ta aje kwalinta don wata rana. Mimi ta fito wanka tana zaune a gaban madubi tana ta shafe-shafen jiki da turarruka masu qamshi. Yau Malaminta ya dawo daga tafiyar da sukayi ta sati biyu qasashe biyar, suka zagaya shi da manyan Malamai don yin da'awa. Dakinsa ta nufa don daukar darasi. Fatanta Allah yasa ta samu rumaisa a yau. Yana cikin bandaki, sai ta shige. Ni kuma sai na dawo baya tare da fadin Allah ya qara danqon soyayya. QARSHE.......
Mu hadu a sabbin littafai na, SANADIN FURUCI...da RUDI KO BURI....Taku a kullum Halimarku K/Mashi. Sai na jiku a 08081165107 don jin ta bakinku.
Nima Abdu pro mlf (Abdurrahman) da na rubuta muku, ina yima kowa fatan alkhairi, da fatan Allah ya amfanar damu darussan dake cikin labarin Ameen.
Ma'assalam👏🏼👏🏼👏🏼
sai inna Habiba wace take muku post a whatsapp nace mu
Ma'assalam👏🏼👏🏼👏🏼
Mimi ta sauka, wannan ma Namiji ne, sai yaci sunan Alhaji. An sha suna, sannan itama zainabu ta kama nata laulayin. Lokacin Ismail baya qasa. Sun tafi Africa ta kudu. Shine ya kira Mimi ya fada mata cewa Zainabu babu lafiya, don Allah ta dubata. Mimi ta tausaya mata halin da ta sameta. Ita ce takai ta Asibiti. Bayan gwaje-gwaje an gano ciki wata biyu. Mimi ta wuce da ita Gidanta kafin mijin ya dawo. Dakin su Al'amin ta sauketa. Da yake ynxu tanada masu aiki, yarinya da tsohuwa, sannan sunada Mai gadi. Mimi tsakani da Allah take kula da Zainabu, kwana biyar ya dawo, samun Zainabu danyayi gurin Mimi tana samun kula, sai ya sake daga darajar Mimi. Harma ya fada mata cewa, My Dija, na jima da yarda cewa ko dabba na daure zaki kula da ita, bare Mutum. Hakan ya qara mata qaimi gurin zama zama da kishiyarta lfy. Zainabu ta haihu ta samu 'ya mace. Ga mamakin Mimi sai Zainabu tace ya sama 'yar sunan Mimi wato Khadija. 'ya kuwa taga kaya gurin Mimi.
1⃣1⃣2⃣Mimi cikin motarta tare da yaranta, a Abuja sunje bikin Na'ima ne ta auri wani maqwafcinsu da matarsa ta rasu gurin haihuwar danta na biyu. Bayan biki ya watse da ranar da zata tafi tace, bata barin Abuja, saita nemo mina qawarta. Gidan iyayen mina taje neman labarin. Har gidanta qanin mina ya raka Mimi anan cikin Abuja. Sun rungume juna sunata murna, kafin suka 6arke da labari. Mina tasha mamakin jin cewa, sheikh Ismail Abdurrahman shine Malaminta da mahaifinta ya bata. Tace, ta san shi domin yana daya daga cikin malaman da take nutsuwa da wa'azin su. Sai mallon mimi takeyi tana Mamakin ta. Tace dubeki kamar matar shugaban qasa, wai matar Malami. Mimi tayi dariya, tace kinsan Allah duk wadda mijinta ba Malami bane, ina mai jajanta mata, domin ta rasa abubuwa da dama. Me zanyi da wani shugaban qasa da ba zai samu lokacina ba sai na mutan qasa? Barni da mijina mai kasheni da kalolin soyayyarsa. Mina tace, qwarai na yarda dake, domin wata lakcarsa da naji yana yiwa mata da maza, saida nace, Allah yasa haka yakewa iyalinsa. Mimi tana dariya, tace yana min. Suna cikin haka saiga wayarsa. Mina kallon mimi takeyi tanata zuba shagwa6a a waya. Wai gobe zata dawo, shi kuma yace idanunsa aun qosa su ganta. Ta bashi mina sun gaisa, suka yi bankwana tare da amsar lambar juna. Rayuwar su mimi abin koyi ce ga mutane na qwarai.
Bayan shekara uku Ginin Ismail yayi nisa, na jami'a, lokacin Mimi tana goyon Abdurrahman sunan mahaifin ismail. Sannan sun tare a sabon gidan su dake nan layin, ita kuma Zainabu ya gyara mata inda suka tashi. Kwanciyar hankali da qaruwar arziki kullum suna cikinta. Yaran ta uku duk maza, Hajiya sauda tace, qila irin tawa zakiyi, sai na hudu ki samu mace. Ta dauko Ummi tana zama gurinta, kuma ta saka ta makaranta mai kyau. Ita ma kuma ta koma makaranta don ta samu digiri dinta ko ba za tayi aiki ba, ta aje kwalinta don wata rana. Mimi ta fito wanka tana zaune a gaban madubi tana ta shafe-shafen jiki da turarruka masu qamshi. Yau Malaminta ya dawo daga tafiyar da sukayi ta sati biyu qasashe biyar, suka zagaya shi da manyan Malamai don yin da'awa. Dakinsa ta nufa don daukar darasi. Fatanta Allah yasa ta samu rumaisa a yau. Yana cikin bandaki, sai ta shige. Ni kuma sai na dawo baya tare da fadin Allah ya qara danqon soyayya. QARSHE.......
Mu hadu a sabbin littafai na, SANADIN FURUCI...da RUDI KO BURI....Taku a kullum Halimarku K/Mashi. Sai na jiku a 08081165107 don jin ta bakinku.
Nima Abdu pro mlf (Abdurrahman) da na rubuta muku, ina yima kowa fatan alkhairi, da fatan Allah ya amfanar damu darussan dake cikin labarin Ameen.
Ma'assalam👏🏼👏🏼👏🏼
sai inna Habiba wace take muku post a whatsapp nace mu
Ma'assalam👏🏼👏🏼👏🏼