← Book details Canjin Rayuwa Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 34

Sashe 2

Canjin Rayuwa Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

3⃣Mimi, wadda ake turawa tana jinsu, duk qarma-qarmar da yakeyi tana jinsu, kuma ta sani. A zaton ta ma da kudinta akeyi mata komai, har suka qare ya shiiga nasa. Tace, to yaya Amina su sallamemu mana tunda dai babu kudi. Yaya ta kalli Ismail, "Nima nawa tunanin kenan, ko ya ka gani? Ismail yace, bari dai ayi hoton mu gani. Allah yasa dai kudin babu yawa. Ynxun ma tunanina ko zan barku anan inje in amso ragowar na hannun Mahmud. Yaya tace, muje dai, in kaji kudin, sai ka tafi. Dubu shida da dari shida ne kudin hoton, don haka dole ne ya tafi ya amso ragowar kudin, kafin ya isa, saida ya kira layin Mahmud din, don haka mai acha6ar da ya kaishi, shine ya dawo dashi. Don haka suka biya akayi musu, sannan suka amshi sakamako suka koma. Sai sha biyu sannan likitan ya dawo ya duba, yace Alhmdlh, kuma tana da jiki mai kyau. Don haka zata iya soma koyon tafiya. Ismail ya kalli doctor. Ismail ya kalli Doctor salis yace, za'a iya Sallamar mu? Sbd gsky duk abinda muke dashi ya qare. Doctor salis yace, karka damu malam Ismail, kayi qoqari sosai. Ba duka namiji za'a samu ya tsaya kan matarsa haka ba. Mimi ta dago, ta kalli Ismail, idanun ta da alamun tambaya. Sai yayi murmushi, ya kalli likitan, ai yaya baya kasa dawainiya da qanwarsa. "Take likitan ya kalli Mimi, sai ya tuna 6aran6aramar da yayi, don haka yace, "oh na manta hakane, yaya ne ashe. "
Yammacin ranar, Ismail babu yadda baiyi ba da Mimi ta dan soma takawa, amma taqi, sai kuka takeyi wai ba zata iya ba. A qarshe haushi ne ya cika Ismail ya fita waje ya zauna akan benci. Tunanunnuka ne kashi-kashi suka addabeshi, yana mamakin yadda yaketa neman layin Hajiya sauda, amma baya samu itama kuma ta daina kiranshi. Sannan yau sati uku kenan da ita hajiyar ta sallami Mahmud daga koyar dasu hasana. Ko yaushe in Ismael yayi ma Mahmud wannan qorafin, sai yace, karka damu ni dama ko basu sallameni ba, dole in barsu tunda kaga karatu zamu tafi. Game da rashin waiwayar 'yarsu kuwa ka qara haquri.
4⃣Gashi yana tunanin ina zai samu kudi, ko ba don ciwonta ba, ko don sbd tafiyarsa. Sannan in an sallamesu, ina zai ajeta? Domin gsky bai kyautu ba yasa ta dakin zaure.Duk bama wannan ba, gurin wa zai barta? Yana jiyo ta daga ciki tana magana cikin shagwa6a, "to kazo mana, ka kamani zan kwanta ne fa kaji! Shiru yayi mata, sai dai zuciyar sa tana tambayarsa meyasa ynxun Mimi bata kiran sunansa? Bata cewa, Ismail, bata cewa, malam. Nauyinsa take ji, ko menene? Oho! Tayi, har ta gaji tayi shiru. Saida yaji kiran sallar la'asar, sannan ya shiga dakin. Har lokacin idanunta da hawaye. Ya kalleta, sai kuma ta bashi tausayi, yace, khadija! Taqi kallonsa. Ya gane alamun tayi fushi kenan. Yace, zan yi miki alwalla ne, nima zan tafi masallaci. Ta kumburo baki, to ka kiramin nurse Ramatu. Inaso inyi fitsari ne. Yace, ba zan kira wata ba. Muje in taimaka miki. Nurse dinnan fa da kkga tana kulaki, ina bata wani abu. Kwanakin nan da bani dashi, ban bata ba, kinga tana shigowa? Mimi tace, to fa, kai namiji ne, shine zaka taimaka min? Banida lokacin 6atawa khadija, sallah zanje. Menene zaki 6oyemin wanda ban gani ba? Kuma tunda ni matsayin wanki nake, ai ba wani damuwa. Ta zaro idanu, me ka gani? Bayan yaya Amina ce takemin komai. Da zaka ce... "kafin ta kai qarshen maganar, har ya dauketa cak ya sakata a toilet din. Ya zaunar da ita a kan kujerar da yaya Amina kan zaunar da ita in zatayi mata wanka. "sai kuma me zan taimaka miki dashi? " ka fita nidai kawai! Zaki iya yin komai harda fitowa? Tace, nidai ka fita! Murmushi yayi sannan ya fice, "to karki dade, kusan mintina hudu tace, "to kazo ka fito dani! Tayi maganar, ranta a 6ace. Ya shiga, inyi miki alwalla? Ta turo baki, "ni nayi abina. "A qasa yayi mata shinfidar sallah, yace, kiyi a qasa, tunda an kwance maki. Yasa mata hijabin sannan ya fita. Bayan ya dawo ya soma hada kayan da yaya Amina ta cire mata da safe. Yace, zanje gida inyi wankinmu, ya dan taru, sai kuma inyi wanka. Ta 6ata rai, cikin shagwa6ar ta tace, ni kuma ka barni da wa? Yace, da Allah mana! Dama shine mai tsarewa. Kinga kuma kinji sauqi babu laifi ko? Ya qarasa cikin sigar lallashi. Ta matse kafada cike da shagwa6a, idanunta suka soma zubo da hawaye, nidai bazan zauna ba. Ya ce, (cikin takaici ) karki zauna, inkin gaji da zaman Asibitin kidan taka mana, ki yarda kidan taka ko a sallamemu, amma kinqi. Ya dauketa cak ya dora ta akan Gado. Sai na dawo. Bata dai ce komai ba, shi kuma yayi tafiyarsa.
[17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa

7⃣Ta aje cake din hannunta akan gado, "Nidai ka tafi dani mana." yace kwantar da hankalinki, wannan ba abin damuwa bane, ga yaya Amina, sai ku tare, inkin sauqi sosai, in nazo sai mu tafi. Tace, to ka fadawa yaya Amina dinne? Yace, ban fada mata ba, amma nasan cewa ita babu matsala. Tace, shikenan yaya jikinta fa? Yace, da sauqi, dukda banbi ta gidanta ba. "Ya ciro wayarsa, bari in kira Abban su saddam ya bata mu gaida ta. "sun gaisa da abban su saddam, sai ya tambayi mai jiki. Abbansu saddam yace, gatanan tanata rawar sanyi, ta qudundune, ta dai sha magani. Ismail yace, to ka gaisheta. Khadija ma tanayi mata sannu. Abbansu saddam yace, zataji. Ya kalli Mimi, kinji har ynxun jikin ko? Tace, Allah warki yaya! Allah ya bata lfy. Washe gari yaya bata samu zuwa ba, sbd jikin nata. Ismail yace, to yau yaya zamuyi da wanka? Ko in miki? Ta zaro idanu, tana kallonsa, a ranta tace, shi wannan nufinsa dole sai yaga tsiraici na ne? A fili tace, na haqura sai taji sauqi. In tazo zatamin, harda gashina zata wankemin, yayi datti, duk ya dameni. Yace, wai meyasa baki yarda dani ba, sai kace zanyi miki wani abu. Ki tsaya ko gashin ba sai in wanke miki ba? Naga yadda tayi miki ranar nan mana. Tace a'a karka samin ruwa a kunne. Ni saloon nakeson zuwa. Yace to yau kidan taka ne mana khadija. Kinga basu so mu tafi da wata matsala ne. Da sunga kindan taka zasu sallamemu, sai in kaiki duk inda kk so. Ranar dai da qyar ya samu ta dan taka, daya biyu yana sagale da ita, sai ko ta fada jikinsa. Wani iri yaji, tsigar jikinsa ta motsa. Yayi mamaki, bai ta6a jin haka ba aduk irin daukanta da yakeyi mata a cikin wannan jinyar. Cikin sauri ya dagota daga jikinsa, muryarsa a sarqe ya dago ta, "kin cika ragwanta, to zauna kidan huta.
8⃣Cikin sati daya, mimi tana dan fita tare da taimakon yaya Amina don taji dan sauqi ta dawo, da kuma taimakon uban gayya, Ismail. Burinsu lokacin a sallamesu, domin basuda kudi a hannunsu. Ranar litinin kuwa Doctor salis da lukman, likitan da yayi mata dori suka tabbatar ma da mimi sallama. Ismail yayi murna tamkar dan kurkuku a ranar daya fito. Duk sunyi murna sosai. Yace, ma yaya Amina ta shirya kayansu, shi kuma zaije ya dan karkade dakinsa. Yaya tace, ina zata? Gidanmu zamu wuce tunda mun riga mun sanar da Abbansu saddam. Yace da inason indan gyara mata dakin na Gidanku, tare da dan sa mata abin kwanciya kafin dai mu wuce. Tace, hakane. Tare da Mahmud suka share ko ina na dakin sannan suka dauki shatar tasi zuwa asibiti. Likitoci da Nurses sunyi masu murna da barin asibitin, nan ne ma Doctor salis ya basu tabbacin cewa, duk lokacin da wata bukatar taimako ta taso, to qofa a bude take su tunkareshi. Yaba Ismail katinsa mai dauke da lambobinsa a jiki. Ismail ma bai qwauron baki ba ya fada masa cewa, shi zai tafi karatu ne a madina, amma duk abinda ya taso ga yaya Amina nan. Doctor salis yayi masa fatan alheri, tare da samun nasara.
Zainabu tana zaune a bakin gadonta da 'yar rediyo a hannunta, tana sauraro. Ta babansu ce ta dauko lokacin da zata dawo gdn Alhajin bayan barowarta daga asibiti, sosai rediyon ke debe mata kewa, da shirye-shiryensu, musamman wanda suke karanta littafin hausa. Da ta qagara taji wani littafi da ake karantawa, sai ta samu bushira tana ce mata ina zata samu littafai? Bushira tace mata, sai dai na haya. Wannan ne mafarin karance-karancen ta. Kuma suna debe mata kewa don tana cin karo da matsalolin da suka zarta nata. Kuma tana qaruwa sosai. Don haka sai tayi haquri ta dangana, ta kuma ci gaba da kai ma Allah kukanta. Shi kuma Alhaji lawal bai canza ba, saima abinda yayi gaba. Hakanan wani abin dake damunta shine tunda ta dawo gidan batayi al'ada ba. Saidai bataji wani canji a jikinta ba. Tsoronta daya, kar dai wani cikin ne ta sake samu, domin gsky ba tada burin hada zuri'a da Alhaji lawal, sai dai masoyinta Ismail. Kullum cikin sa take, duk da wata zuciyar tana fada mata cewa, Ismail yayi mata nisa. Amma bata debe tsammani ba tunda tana Addu'a.
[17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
Chapter 2 · 0% Book details