← Book details Bahagon Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 4

Gabatarwa

Bahagon Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 113 min read

 BAHAGON RAYUWA


BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM DUK KAN GODIYA YA TABBATA GA UBANGIJIN MU SARKIN TALIKAI DA YA KAWO MU WANAN LOKACIN TARE DA BAMU LAFIYA INGANTTACIYA A RAYUWAN MU,
YABO DA GODIYA YA TABBATA GA ALLAH WANDA YAI MUNA NUNFASHI TARE DA MA ABUBUWAN RAYUWA ACIKIN HIKIMOMIN SA YA ALLAH MUNA MASU ROKONKA DAKA BAMU IKON GODE MAKA AKODA YAUSHE MU KASANCE CIKIN BAYI MASU TSORON KA MASU MAKA BAUTA TSARKAKKE A RAYUWAN MU,


WANNAN RABARI NE MAY DAN TABA ZUCIYAR MAY KARATU TA DA WASU SAKWANI A CIKIN SAI DAI BAIDA YAWA SOSAI DON BUKATAN MAKARANTA NAYI TARE DA FATAN ZAMU AMFANA DA DAN SAKON DAKE CIKIN SA ,
NAGODE TAKU HAR KULLUN ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU GA MASU SON JIN KARSHE ZASU IYA KIRANA DA WANAN NUMBER DIN KAMAR HAKA 08036959257 DOMIN YIN REGISTER, , , ,

BAHAGON, , , , , ,


⚓1⃣


Gidane ginan kasa
wanda da ganin sa kasan akwai talauci da kauyanci a cikin sa sai dai duk da kasancewar gidan karami akwai tarin jama, a a cikin sa sosai.
Gida ne wanda ya kumshi matan aure guda uku ko wace da nata zurian don dama irin wanan gida babu komai a cikin sa sai gasar haihuwa a tsakanin matan dake gidajen.
Ba wai damuwa da rayuwa akayi ba banda bakin kishi da hassada juna a tsakani, abinda ba kai tsanmani ba shine mutum yakan riska a cikin irin wanan gidajen.
Sai dai kuma tallakawa ne fitik din su don abinda zasuci ma watarana aiki ne a gare su sai dai kowa taiwa rayuwan ta dana yayan ta dabara su sami dan abinda zasu aikawa cikin su.
Ga ko wani daki a cike da yara bi da bi irin haihuwan nan na kafin ka yaye ka samu wani.
Sai dai su matan gidan hakan ba takura bane a garesu sai dai ma jin dadin rayuwa don babu wacce aka bari a baya daga cikin su wurin saka nata irin.
Duk da uwargidan da may bi mata sunfi yawan iyali a gidan amma kuma suna kyashi da hassadan ganin Rabi amaryan su itama da ba ta dade ba da shigowa cikin su tana kokarin cin masu ga haihuwa.
Gsshi dai ba wani tallafi suke samu ba daga mijin nasu wanda zasu taimakawa rayuwan su dana yayan amma kuma kullun zance ya tashi sai su manta da nasu su shiga sake mata magana a tsakar gida.
Sai idan ta gaji ne takan mayar masu da martani da cewa haihuwa aina Allah ne kuma yaya arzikine kowa kuma na dashi batai bakin ciki da nasu ba ai.
Duk hakkurin irin na Rabi, sau da yawa takan shanye ta take irin abinda akewa diyan ta a gidan tayi kamar bata gani ba.
Sai dai tana mai bawa yayan nata shidda tarbiya sosai fiye da sauran yaran dake gidan da tarbiyan su sai a hankali.
Abu daya ne talaucin su bai hana yaran gidan yin karatun boko ba har ma da na addini wanda diyan Rabin sun fi maida hankali ga kowani fanni na karatun nasu.
Gashi bata shiga tsabaga kowa haka ma yayan nata suke a gidan zata iya zama a daki ida ba wani abin bane zai fito da ita waje.
A haka dai suke zaune a gidan da dadi ba dadi watarana aci watarana kuma a hakkura asawa sarautar Allah ido a gani.
Uwar gidan da suke kira da mama tana da diya tara mata bakwai maza biyu, sai may bi mata inna tana da diya takwas maza uku mata biyar.
Sai ita Rabi dake da diya shidda maza hudu mata biyu yar ta ta fari mace ce ana kiran ta da safiya may bi mata kuma Aisha, sai mazan issah dauda, aminu da shaibu sai karamin da take goyo da suke kira da abu.
Duk inda zaka nemi yan uwan da ke son jinunan su to yaran Rabi sun kai can don suna balain kaunar junan su sosai a rayuwan su.
Allah may rufin asirin bawan sa dan karfin da Safiya ta fara kawowa ne ya ragewa Rabi wani wahala a gidan da take fuskanta na rayuwa.
Don safiya yarinya ce mai hazaka ta dauko yan kule, kulen dan abin makulasan yara tana zuwa makatan ta dashi wanda ta hakane uwar ke dan samun na sabulu daga ciki da sauran abubuwab rayuwan yau da kullun.
Wanan dan walwalan da ubangiji yai masu sai kuma hassada da kyashi yazo ya shiga cikin zukatan sauran matan gidan.

************ ************
Tun dawowan su daga makaranta ta dan tsaya shago ta sayo dan madara da suga wanda take ganin zai isheta yin dan gulusuwan da zatayi gobe na zuwa makaranta dashi ta shigo ta samu kamar kullun sauran mutanen gidan suna tsakar gida suna harkokin su na yau da kullun kamar yadda suka saba.
Bata shiga dakin su ba tabi iyayyen gidsn da wasu daga cikin yayyen ta tana masu sannu da gida.
Ba wai amsawan dadi ake mata ba amma hakan bai hana ta gaida su kamar yadda ta saba a kullun suna amsa mata cikin gajewa da halinta.
Idan kuma da zata wuce bata gaidasu ba wani matsala ne hakan don har rankwashi sai tasha a gun wata a gidan ranan.
Da sallama ta shiga dakin mahaifiyar ta tana zaune ninke kayan wankin da tayi na kanne ta tun safe ta samu tanayi a dakin.
Uwar ta amsa mata sallaman ta cikin mutunci tare da fadin kun dawo tace eh tare da kokarin sauke dan jakar makaranta dake makale a kafadan ta.
Bata zauna ba ta fara kokarin ciro dan sayayyan da tayo a hanyar dawowan ta tare da ciro sauran dan kudin da ya rage tana kokarin yiwa uwar bayanin komai.
Haba yar nan bayyani kuma namay fa cire jakar ki zauna ki huta ga dan ganye nan dana gyara maku da garin rago kici kisha ruwa ki huta kafin lokacin zuwa islamiya yayi maku.
Ta zauna ke nan da niyar ta cire safan dake a kafan ta taji ana kwala mata kira a tsakar gidan da Safiya safiya da karfi.
Cikin takaici da bacin rai uwar tace dama na sani ai ba za a bari ki zauna kici dan abincin ba ma yanzu za, a nemay ki da wani aikin kuma.
Taja guntun tsaki tana cewa yar tashi kije idan kin dawo kyaci ai, cikin takaici Safiyan ta ture kwanon data bude.
Cikin ranta tana fadin kamar ni kadaice yarinya a gidan daga dawowanabza a fara kwala min kira da bakin aike ko aiki, komai sai dai a kirani ace nice zanyi ni kadai.
Kafin ta kai ga fita ta sake jin muryan Inna tana fadin wai Safiyan bata jinane ko may wai ?
Da sauri ta amsa da naam Inna gani tafe ina daura zani ne dama tafita waje tana karasa daura zanin da takeyi din.
Cikin takaici Rabi ta jawo marfin kwanon data bude don cin abincin data aje mata ta rufe tana fadi a ranta, in dai don aji ta bakinane ake wanan halin bazaku taba jina ba a kan hakan.
Duk yaran dake gidan nan wasu ma basuje ko ina ba tun safe amma ba a aike su ba sai wacce ta biyo rana ta shigo yanzu ake kwalawa kira haka.
Ko sai yaushe zasu daina wanan halin hassadan nasu a gidan nan haka oho don dai wani abin da gaiyya ma suke masu shi.
Jin muryan Inna tayi daga waje tanawa yar nata fada aka may take kiranta ta shige daki taki fitowa tun dazun.
Tace inna ina cire uniform ne a jikina dama ba kin fitowa nayi ba sai inna din tace ai dolen ki ma ki fito ga tatsin kamu can a roba yana jiran ki tun dazun har ya fara kumbura.
Safiya takai kallon ta ga inda kammun yake a bude fam ga roba sai kudajen da suka mutu a saman shi ba ako dan sakaya shi da wani abu ba.
Ta sauke ajiyan zuciya tare da cewa Inna don in dan ci abinci kafin na fara don banci komai ba tun safe dana fita gida.
Wani irin tsawa ta daka mata tace kai amma lalai safiyan nan wuyar ki ya isa yanka yanzu ni zan saki aiki har ki tsaya kina cewa wai na bari ki dan ci abinci.
To ki zauna kada ki tatse idan ya gama yoyewa sai ki fito kina ca kin shige daki kuna gulman da kuka saba dake da munafukar uwar ki ko.
Haba inna gulma kuma dani da ummi ta ake bude baki zatai magana taji saukan mari a fuskan ta kayauuu, .
Daidai lokacin kuma mahaifin su da ya dawo daga wurin aikin jiman shi ya shigo gidan yana ganin ta dafe kumcin ta bai tsaya bin ba asi ba yace ke Safiya ungo nan yai mata dakuwa yana fadin.
Ashe rashin kunyar da ake fadi kina dashi yakai haka ban sani ba uwar taki ne zaki tsaya kinawa musawa a gaban ta.
Inna tace gara dai da kagani da idon ka yau idan an fadi ace an sakawa yarinya tsana don ba a kaunar su a gidan.
Safiya tana share hawaye ta wuce ta fara gyara inda zatai tatsin kullun don duk kwanonin da akaci abincin daren jiyane a gurin ba a wanke ba har lokacin.
Wanda tasan kuma karshen ta itace zata wannke su idan ta gama don haka ta mayar da hankalinta sosai ga abinda takeyi.
Sai dai har lokacin Inna na tsaye da baba suna kare mata zagi har da mama dake gefe tana kashewa yarta karama kwarkwata a kai.
Hakan bai ishi baba ba sai da yakai kofan Ummi dake ci gaba da gyaran dakin ta ya daga raggan labulen ta da ya dafe saboda dauda da tsufa dayayi.
Zagin Ummin yake sosai a kaina ina jin shi sai sharan hawaye nake ina aikin dake a gabana mai yawa ban dai san may ummi tace dashi ba naji yace da ita da karfi akan yar taki har kike son ki mun rashin kunya Rabi ?
Ban yi aune ba naji ya fada dakin ya fara dukan ummi sai ihu take kamar yadda ta saba idan yana dukan ta din don yau bashine karo na farko da naga yana dukan ta ba.
Aiki nake jikina sai tsuma yake saboda muryan ummi dake ratsa kunnuwa na a lokacin da ina da hali ko karfi a ranan babu abinda zai hana na kwatar mata hakkin ta a gidan nan.
Tun ina iya kuka ciki ciki har takai na bude murya na sosai ina fitar da sautin kukan nawa a fili kowa najiyoni a gidan .
Sai da ya gaji ya fito daga dakin yana haki ya kara nufa na da zagi da baki irin wanda bai dace mahaifi yana wa yar tashi ba.
Ina jin ya nufo ni na mike da gudu na bar wurin don nasan idan na tsaya zan sha na jaki ranan ba bisa laifin komai ba.
Sai da naga ya shige na fito inda na labe baci gaba da aikina da nakeyi inayi ina kallon kofan mu ko zanga fitowar ummina daga dakin ta amma naji shiru.
Sai da na karasa har wanke wanke na na samu daman shiga dakin namu inda na samu ummi kwance saman matatan katifan ta daya sude ta kifa ciki tana sharban hawaye.
A hankali nakai tsugunne daidai kan ta ina fadin ummi sannu kiyi hakkuri ummi nice naja maki hakan.
Ta sa hannun ta share hawayen da ya fito daga idanuwan ta ta dago da kyat ta dan motsa tana fadin ba komai yar nan akwai Allah yana kuma tare da mai gaskiya.
Tace jeki ki shirin makaranta kada ki rasa haddan na yau a wuce ki ga abincin nan ki dauka ki ci ya dai bushe ko.
Na koshi nace da ita abu ga mahaifiya sai ta manta da nata damuwan naji tace dani da sauri may kikaci maza dauki ki ci ki wuce don kin makara ko.
Ban ki ba ina ci ina shan maji har nagama na shirya a gurguje na bar gidan da sauri sai dai duk abinda nake ina tuna irin wanan cin zarafin da baban mukewa mahaifiyana.
Ina jin matan gidan na faman sakin magana a kan mu suna fadin ai kadan ma muka gani don sai mun raina kan mu a gidan.
Ban tsaya ta kan su ba nafice abina don inda sabo na saba jin wannan kalaman a gun su tun ina yar ficiciyata har zuwa yanzu.
Mun dawo daga islamiya banga Ummina a gidan ba gashi babu halin na tambayi wani inda ta tafi a lokacin.
Waje na fita na yayo dan kirorin da zan hura wutan da zan yi madarana dashi har lokacin ummi bata dawo ba gidan.
Na hada ina kokarin tukawa ne naji mama ta kwala min kira nasan ba komai bane abincin dakin mu take kirana na dauka gashi idan na bar madaran zai iya konewa.
Ba yadda na iya dole na sauke shi a hakana na tafi bata barni na dawo gurin aikina ba sai dana kawar wa kowa da abincin shi na koma lokacin har ya sandare ko a haka rai a bace na juye ina nifin dakin mu naji sallaman ummina ta dawo gidan.
Sai dai fuskanta yana a kumbure har lokacin sannu da zuwa nake mata a cikin zakuwa da ganin ta ta amsa min a dararare ta shiga dakin gidan ba wanda yai mata kin dawo.
Itace ta fara shiga daki nabi baya ta kofi na dauko na dibar mata ruwan sha don ban tsanmanin ta sha ko ruwa har wanan lokaci nan naji matan gidan suna dariya suna fadin.
Mutum ma da wani gata gare shi da har zaiyi yaji don baisan kunya ba ya juyo babu ko dan rakiya zikau ya dawo shi kadai.
In mutum ya isa ya nuna shi din dan gatane mana muga tsomamun iyayyen mutum sun dawo dashi.
A haka dai za a kare uwa lalace diyan ma haka na sai bakar wahalan banza kawai a duniya.
Ban tsaya karasa sauraren su ba na debi ruwana na shige na sake fitowa na hada kan nannena suje suci abincin da aka samu dafawa a ranan don ranan girkin Inna ce ranan da wuya a rasa dan abin tsakurawa idan tana girki a gidan.
Ni dai ina zaune ina zubawa yan kannena abinda zasu ci ina jiyo dariyan su da yaran su wanda nasan akan zance guda suke yin sa.
Ranan dai a haka muka kwana da ummi ba tako iya magana sai idan ya kama nice nai ta controling din kanne na har sukai barci.
Fita nayi duk da dare ya soma na karbo mata magani a gurin mai shagon uguwar mu ta hadein.
Zan shigo gida na hade da uwale yar wurin mama take cewa ke kuma daga ina haka ko har kin fara fitan dare ne bamu sani ba.
Nace a marairaice haba uwale sheri kuma zaki min daga ganina najuya naji ta shako bayana tana fadin wake sherin yar iskan banza kawai dake.
Nace to yanzu may nai maki kuma tace ko zaki zage ni ne yanzu ki koma daki irin na uwarki jiki yai tsami.
Nace saukin abin dai ai ba uwata kawai ake duka a gidan ba sai ko naji ta shake ni da karfi tana fadin da uwar wa ake duka in ba uwar ki ba kawai.
Ta fara duka na sai ga dan wurin inna ya zai shigo yaya haruna don shi ba ruwan shi da harkan kishin gidan mu duk daukan kanne yake muna gaba dayan mu bai biyo sauran yaran gidan ba.
Yace ke sake ta mana may tai maki tace dashi cikin hasala wai fa uwata take zagi don kawai nai mata magana daga ina take yanzu.
Yace ke din daga ina kike ko wani ya baki gadin ta ne a gidan ku dai wanan bakin dan ubancin naku shi zai cuce ku wata ranna a gidan nan.
Ta ture ni da karfi sai da na bugu ga rubaben bangon katangar gidan mu na dafe goshina ina kuka na shige ciki.
Ina mamaki irin wanan bakar tsanar da mutanen gidan mu sukai muna mu da mahaifiyar mu.
Wanda har hakan ya shafi wasu daga cikin dangin mahaifina suma basu kaunar mu ko kadan magana kadan in dai ya shafe mu yanzu zagi ko duka ne zai biyo baya.
A yadda na samu ummi ta zauna daga kofa nasan duk abin da muke yana a kunnen ta kasancewar gidan namu ba wani babba bane a haka muke rayuwa a matse a cikin sa.
Nabawa ummi maganin ta tare da debo ruwan da zata sha dashi na jawo dan keson tabar man roban da nake kwana a sama na kwanta daga gefen yan kanne na wanda kafin gari ya waye duk sun jika ni da bolin su.
Sai idan babana yana dakin ummi ne nakan je dakin mama na kwanta daga kofa makure babu wuri a kasa wai babu inda zan saka mata tabar ma a dakin ta.

********* ********* *********
Gidan mu ana kiran shi da gidan Jima don duk wani nau,in fata zaka samay shi a gun baba wanda yake sarafawa ya mayar dashi fata.
Mahaifin mu ya gaji wanan sanan ne a gun mahaifin shi shima mahaifina kamar yadda na fada maki a baya mata uku ke gareshi irin auren karfin hali na malam bahaushe.
Mama itace ta wanke shi suna da shekara uku da aure ya auri inna wacce dama da ita yai samartakan shi tana budurwa tai aure ta fito ya aureta.
Sai inna ta daya aura daga baya a wani kauye tazo gun yan uwan ta ya ganta ya shiga nema da yake Allah yayi dashi rabon zuria a tsakani kuma.
Don saida yan suka suka dinga suka amma ummi tace sai shi take so tun wannan lokacin da aka kawo ummi gidan matan gidan suka dauki tsana da tsangwana suka saka mata tun abin na dan dadi har takai zama ya koma zaman hakkuri kamar yadda matan hausawa da yawa suke zaman yi a gidajen su.
Idan ka dan yunkura daukan mataki sai ace kayi hakkuri don iyali sin taru suma matan abinda suke duba ke nan wani lokaci akan idan sun bar diyan su may yai makomar su kuma gidan gun matan dake gidan.
Suma kan su kishiyoyin ummi din ba barin junar su sukayi ba don zakaji fada ya gaure a tsakanin ko kan diya ko kuma kayan abinci idan wata zata karbi girki a cikin su.
Wanan halin da wuya ai kwana biyu cikakke basu samu baraka ba irin hakan wanda sai mutane sun shigo rabo daga waje.
Haka yasa gidan namu ya kara suna gun mutanen uguwar mu gashi yaran gidan ba tarbiya ko kadan komai girman mutum zasu iya ci masa mutunci don samun daurin gindi a gun uwayen su da sukayi.
Ba yabon kai ba don ina dakin ummi a gaskiya ko kwatance za a yi da dakin mu ake kwatancen masu daman gidan na mu a unguwa.
Da wanan rayuwan muke zama a unguwar mu hakana yau da dadi gobe ba dadi don dai an fimu karfi ta ko ina a gidan dole sai zama na hakkuri kawai a tsakani tunda Allah ya riga ya hada zaman mu a cikin su.
Bawai iya mu ba har wani wanda ya rabe mu haka nan suke hassada dashi da bakin ciki .
Yadda duk ake son tarbiya muna samun shi a gun uwar mu don duk da matsin kishiyoyin da take ciki batai sake dabawa diyan ta tarbiya ba wanan fannin sai dai kawai talaucin da rayuwa na kakanakayi da muke a gidan.
Allah ya taimake ni duk diyan dakin namu muna da dan kokarin mu a fannin karatun mu ba wanda baida kokari a cikin mu.
Wanan ne daman da muka samu zance na rayuwa don da wuya ai hutu wani cikin mu bai dan samu kyauta ba nabajin ta muna dan samun abin dan more rayuwa a hankali.
Ga irin dan kyaututukan da muke ciyowa a wurin musabika da kuma quzee din mukeyi a makarantar boko.
Maimakon a taya mu murna a gida sai tarin takaici ko a ce an dai bamu ne kawai don bakin iya yin mu.
A haka zamu wuni ranan cikin bacin rai a gidan saboda hattara da tsangwaman da zamu shiga gun mutanen gidan mu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:10 PM - Ummi Tandama: BAHAGON, , , , , , ,

🧕🏿2⃣🧕🏿

FREE PAGE


SEENABU MAKAWA


MAISON WANNAN NOVEL ZATA IYA KIRANA DA WANNAN LAYIN DON YIN REGISTER 300 TA BANK KO RECHARGE CARD NA 400
ZAINAB IDRIS MAKAWA ZENITH BANK 2253380105 SAINAJI KU MASOYA AI HAKKURI DA MU WRITERS YANAYI NE YA KAWO HAKAN DA FATAN ZAKU FAHINCE MU, , , , ,


Sauri nake ina shirin tafiya makaranta kasancewa yau monday don nasan akwai dogon assembly da wasu bayanai a irin wanan ranan.
Socks na jawo na fara sakawa a kafana daya yayin da na ji an fara kwala min kira a tsakar gida.
Haushi da takaici ne ya rufe ni a lokaci daya don nasan wani sabon fitina ina zata dora min duk wanan saurin da nakeyi zai tashi a zero ke nan bazan samu assemby din da nakewa kwadayin samu ba kuma wata kila aike ne ko wani aikin zanyi.
Na aje socks din ban saka ba don karba kiran inna din samun ta nayi tana kokarin dama kunun koko take cewa dani na kwaso kayan zuba kunun ko wani daki na kawo mata.
Na juya rai bace naje karbo kayan na kawo ina kokarin ajewa ne takai idon ta akan roban dakin mu sai kawai naga tai cilli dashi a gefe daya.
Ni dai ina tsaye ina kallon ikon Allah ta fara zubawa sai data gama zubawa kowa ta jawo roban ta dan yafuta ta dan zuba muna rabin abinda take awo dashi ta dangwara mun sai na dauka na nufi daki ina juyawa a hankali ina kallon kunun da rai bakwai zasu sha su rayu a gidan.
Ina kokarin rufe roban ne naji ummina tana cewa babu kunun ne ko don naga kin dawo da roban hakana ba komai a cikin sa.
A sanyaye na ce akwai ima anzuba muna ta mike ta jawo roban tana kdllon kunnun dake a cikin sa sai naga ta dauki roban zata fita.
Da sauri na tare ta nace ummi kiyi hakkuri kusha hakana may duniya don Allah bata saurare ni ba ranta ya baci tafita.
Ba wai wanan ne karo na farko da Inna ke muna haka ba a gidan koda yaushe in dai ita zata raba abinci to na dakin mu kan kankare ne kuma ko mutum biyu baya isa a dakin namu.
Ina ga yau ta gaji ne gashi kuma mun kwana babu ko kwandala a dakin balle ta dan sai garin kwaki ko kanzo tabawa yara dan abin dake gare mu munyi kitso da wanki dashi a cikin sati.
Muryan Ummi naji tana fadin haba yaya wanan koko aiko su shaibu ba zai isa ba balle sauran yaran har akai ni.
Sai naji Inna tace da ita au da kika fito kikai min tsaye a kai zikau dake tsoron ki zanji na kara maku babu ko may ?
Ummi tace kawowa nayi ki duba ki gani ga sauran roban nagani duk a cike amma ki duba abinda kika zuba muna don Allsh dai.
Tabe baki tayi tare da fadin yanzu aike akeji kunu ne shi naga daman zubawa idan kin isa ki diba ki kara maku tunda keda diyan ki kune yan gwal a gidan ku kadai akaiwa bakin cin abinci cikin mu.
Ummi tace ba sai na diba ba ai idan bazaki kara ba abarshi don ban san wa zanbawa ba wazan hanawa ba, cikin yaran.
Eyye lalai ma Rabi wuyan ki ya isa yan ka wallahi to bara kiji ke din nan dai da nake gani baki kai min can ba kunu ne ba zan kara ba sai kiyi abinda zakiyi dama naga tun da na zuba munafukar yar ki take bin kunnun da kallo tana min wani tsiwa a kai.
Nifa din nan kujera ce daidai da zaman kowa idan wani abu kike ji da safe nan daidai nake dake yanzin nan don ban daukan raini da wullakancin kowa.
Don idan mutum yai min tsiya yanzun nan na nada mai dukan tsiya inbuge shi in bugi banza naga wanda zai rama mai kuma.
Ummi dai bata tanka taba ta duka tana kokarin juye kunun a roba da sauri inna ta tare tana fadin kada ki lalata muna kunu da wanan kazamin roban naku daya dafe don tsufa.
Muryan babana naji ya fito daga dakin inna yana fadin wai may nene ya akayi ne kuma da farar safiyan nan haka ?
Wani irin harara ta watso mashi tace wanan yar kauyen matar taka ke son shiga mun hanci da kudundune da safen nan akan kunun dana dama na basu.
Niko idan ta kawo rainin da sukewa mutane kaina yanzu zata sha na jaki wanan iskancin ta tsaya iya kai tai maka shi can bani ba.
Baba yace muga kunun sai ummi ta nuna mai ya kada kai yace haba Rakiya yanzu wanan dan kunun ace rai bakwai zasu sha shi ai babu gaskiya ga wannan zance yakai ido ga sauran robobin da aka cika yake cewa wanan nasu waye haka shi ?
Tace ko zaka shigar mata ne naga daga jin muna zancen mu na mata kayi wuf kafito kana kokarin saka bakin ka ciki.
Fitowan ka ba zai hana ni yin abinda nai niyar yi ba akai don ba wani yai wahalan dama min ba.
Ita har waye da zata fito tace min wai banyi daidai ba ko iskancin nasu ne zai kawo gare ni yau kuma ?
Ummi ta wufta da kunun a roban dake gaban inna ta juye tace ga kunun ki nan ki barshi Allah da ya halice mu ba zai barmu da yunwa ba yana sama yana ganin mu.
Tace da baba kagani ko kaga irin cin kashin da tai min dai a gaban ka ko ita wacece da zanyi wahala dama kunu ta fito tai min wullakanci dashi.
Ummi ta juya bata ce da ita tak ba ta nufi dakin ta inna ke fadin samun wuri banza diyan masiyata yar kauye wanda bata da tarbiya ta uwa ta uba.
Ummi ta ce a, a yaya maganan nan iya ni dake ne baikai na iyayye ba fa don haka ki daina zaga min iyayyena da basu ji basu gani ba da safen nan.
Don ni iyayena ba mutanen banza bane ko da suke kauye ba wanda ya taba ganin su suna roko a wurin wani.
Dama mahaifin inna maroki ne ya tsufa amma har yanzu yana roko a cikin gari kowa yasan shi sai inna ta fusata da maganan ummi din.
Tai wuf ta kamo hijjabin dake wuyan ummi ta shake ta har idanuwan ta suka firfito waje tana fadin rokon sata ne ko maita da zaki min gori dashi.
Bata bata amsa ba ta sake sabon shake ta daga inda baba yake yana karasowa yana fadin sake ta mana Rakiya kasheta zakiyi ne ko may ?
Kafin ya karaso ta kaita kasa ta danne tana duka tana fadin gobe ki kara zagin ubana don yana roko roko ai ba sata bane duniya.
Jin sun kicimay yasani fitowa da sauri ga ummi a kasa inna ta haye tana duka mahaifin mu na kokarin banbareta daga saman ta.
Ihu na saka da karfi har yasa mutanen gidan gaba daya fitowa dama wanda bai tashi daga barci ba ya falka.
Ya banbareta saman ta shi da mama tana huci tana fafin gobe kice zaki kara zagina yar iska don an kyale ki har zaki kaiga zagin iyayye na.
Haka kawai don samun wuri yar kauyen banza a kauyen may kuke sha banda ruwan kasari da gwabe da safe.
Mama tace don dama sunyi hayaniya da yamman jiya a, a Rakiya baki da gsskiya ni kaina na san baki basu abinci yadda ya dace ba yau ba.
Ta juya kan mama tana fadin bani bayarwa kedin daban ne wurin basu wake kwashe abincin bakeda yara ki ba ku goma a daki daya katan banza kin tarasu ba moriya.
Daga can Nura dan mama daya taso daga barci ihu na ya tayar dasu yace kada kice zaki zagi maman mu yanzu rayuka su baci wallahi.
Su dai da kika raina don basu kawo karfi ba ki tsaya a kansu amma mu kan idan kokai wa maman mu yanzu zaki ji mu don kin dai san mun fiku karfi da yawa kuma.
Da sauri na karasa na daga ummi ina gurza kuka ina mata sannu ummi a cikin kuka itama din kukan take sharba a lokacin.
Tsawa baba ya daka min wai na raba su da ihu kada na tara mashi mutane a gida a dauka ko anyi mutuwa ne a gidan tun da safe haka.
Yaya Sani dan wurin Inna din ne mai dan dama a gidan mu yace a, a baba ai dole ne Safiya ta kuka irin wanan wullakancin haka a daki uwarta a gaban ta don basu da karfi kuma a hanata kuka ai cin zalun yayi yawa mana.
Ya juya gare ni yana fadin ke ba makaranta zaki ba maza kije ki shirya ki tafi kada ku makara bar su da Allah kowa ya zalunci wani Allah na gani ai don ba anan duniya zata tabbata ba ai.
Na dago kai nabi babana da kallo na sake kallon yaya sani din na juya nabi bayan ummi muka shiga daki.
Sai naji Inna na fadin kaikan sani anyi hasara wallahi yanzu akan kishiya da yan uba kake fafin wanan maganan haka to tunda kaji haushi sai kazo ka rama masu nasan ka isa wawa kawai wanda bai san ciwon kan shi ba.
Banji may ce da ita don rashin kunya a gidan mu ba sai na tsaya fadi ba ba abin kunya bane da yaci wa uwar shi mutunci a bainan jama, a.
Ina kokarin daukan dan tsunman jakan makaran ta ina goge hawaye ummi ke fadin kuyi hakkuri yar nan mu kuma namu rayun a haka yazo muna gidan nan Bahagon rayuwan Allah ya nufe mu da gani cikin su.
Yaya sani ne ya dago labulen dakin yana fadin ke Safiya miko min roban kunun naku naku nan ya dauke da katon roban da inna ta dama kunu a cikin sa gaba daya.
Uwar na daga wurin madafa tana fadin wai ko dan nan ka ka daya kuwa ko an hada dakaine an mallake min ban sani ba wai ?
Jikina na rawa na dauko roban dake gefe na mika mai ya raba kunun biyu ya juye muna a roban mu yana fadin maza ku sha ku tafi kada ku makara.
Da sauri na dauka na ciki na fara zubawa yan kanne na don ina gudun inna ta shigo ta hana mu sha kuma.
Har muka gama inna bata bar zagin Sani ba zagi irin wanda ba a son uwa taiwa diyan ta shi take faman zuba mashi.

********* ********* *********
Ko da muka shiga school ranan mun makara sosai nasha bulala na na wuce aji raina a bace ba don bugu ba sai dai abinda na bari a gidan mu na cin kashin da akewa mahaifiyan mu.
Don ni a iya sani na banga wani hslin rashi biyayyan da take nuna masu ba a gidan don ko aiki yai masu yawa watarana sai ta taya su idan kuma diyan su ko sune basu da lafiya zakace wani nata ne ba lafiya ta shiga sintiri gaida mashi ke nan a cikin su.
Ita ranan da duk wani yaron ta zai kwanta ciwo babu mai lekashi har ya ji sauki ya mike ba su gaida mutum.
Don Allah maijin kan bawan sa ne da wuya dan dakin mu ya kwanta ciwo a gidan mu sai can ba a rasa ba zakaji wani cikin mu ba lafiya.
Zan dai iya cewa ummin mu mace da bata da kyashi ko hassada kuma mu kan mu ta koya muna wanan akidar nata na matukar hakkuri tare da sanin ya kamata .
Ba don halin nan nata ba na irin rayuwan da kishiyoyi da miji suke mata a gidan na wullakanci amma daidai da rana daya bata mayar da martani irin wanda bai dace ba a kan su.
Ni na rasa may ke jawo wanan kiyayyan haka akan mu da uwar mu sai yanzu da wayo ya fara zo min ne na fahinci ba komai bane illa zalar kishi irin na macen bahaushe kawai.
Don ummin mu yarinya ce a cikin su kuma har yawan haihuwar da tayi bai sa kyaun ta da dirin ta ya gushe ba gare ta wanda su sauran sai dai kawai zaman rayuwa.
Zan iya cewa a gun mahaifiyan mu yan dakin mu maka kwaso dirin mu mazan mu da matan mu ba laifi uban mu ma dogo ne sai dai shi baki ne amma baya ga tsayin nashi komai na mahaifiyar mu muke debowa.
Daga hasken fata tsayin don itama tana dashi zuwa suma hanci da idanuwa manya masu fari kal dasu.
Don idan zagi ya tashi dashi matan gidan mu ke zagin mu ko yaushe sai suce damu shegu masu zubin uwar su.
Sai kaji guda ta karbe da cewa ba dole ba tunda tafi miji jaraba dama ai ance wanda yafi jaraba a wurin saduwa shi da ke biyowa a duniya.
Tun ban san kallaman ba har na fara fahintar ma anan shi idan sun fadi na turo baki ina maijin haushin kalamin su gare mu.
Ranan dai sunan naje makaran ta ne amma babu wani abinda na iya tsinanawa a karatuna na dawo gida da bacin rai na samu ummi ta dan gyagiji tana aiyukan ta a tsakar gida.
Uniform din kannena kwaso duk da tsofi ne amma bana taba barin su da dauda kullun na dawo sai na wanke muna su na sha idan sun bushe na buge nakai daki kafin mu wuce islamiya.
Do ba halin na barsu nazo na iske an masu ba daidai ba ko tukunya za a sauke dasu ake saukewa idan an tashi aiki in suna shanye a waje.
Mun gama shirin mu muka shirya zuwa islamiya mun fito ke nan yaya sani yana zaune a daban su na yan matasa yace dani ke Safiya zo nan.
Jiki na min bari na nufe shi sai naji yace dani kunci abinci nace eh yaya munci yace to ki saurareni kiji daga yau duk wanda kika ga zai daki ummin ki ki nemo sanda kema ki buga mashi ninace a mutu har liman.
Da sauri na dago kai ina mamakin kalamin shi yace eh don abin yai yawa daga magana sai duka irin haka itama Rabin na fada mata ta daina zama ana mata wanan cin fuskan tun bakuyi wayo ba har gashi kun tasa ana bu daya a gidan.
Yace baki ji may Nura ya fada bane kowa ma ai uwarshi ya sani don haka ninace ki rotsa mutum koma waye.
Yace maza ku tafi kada ku makara zance a gun yaya sani muka samu sauki dakin mu don yafi kowa zama tantiri a gidan mu.
Sai gashi kuma Allah ya dora mu a kan shi yana jin mu a gidan ko dan ladabin da muke mashi ne oho ?
Don zamu ganshi komai yawan abokan shi sai mun duka mun gaida shi idan kaya muka gani a hannun shi zamu karba a hannun shi mukai dakin su.
Shima idan yar dahuwar shi ya samo ni zai nema na dafa mai kuma ko ya bani bana karba nace ya bar shi, sai idan ya zare min ido zan karba naci ko na bawa kan ne na suci.
Tun wanan fadan da akayi gidsn mu ummin mu ta dan samu baki idan ana mata wanin abin cin fuska zata zage ta mayar da martani kamar yadda akai mata ba dadi din itama.
Abin dake ci mun rai shine irin yadda gamu da yawa a gidan mu amma kowa a ware yake ba mai hurda da wanin shi dan dama tsakanin yaran dakin mama dana Inna akwai dan shiri a tsakanin su.
Nice dai babu halin idan suna zaune ko suna wanin abin da ya shafe yara mata nace zanzo wurin yanzu zakaji sun fara hattarana.
Suna fadin ke kuma may kika zo yi nan munafuka kawai sai wata tace muguwa mai irin halin uwar ta kawai in ba gulma ba may kika zo saurare nan.
Dole zan bar wurin don zagi da hattara irin haka yasa ko suna abin su bana shiga shirgin su ina daki da ummi na ko ina wani aikin a waje sai dai abinka da yaro inayi ina sauraren su sai na manta na saka baki wata rana su kyale ni wata rana kuma nasha ba dadi garesu.
In kaji dariya na ko farin cikina muna tare da kanne na ko kuma na fita zuwa makaranta ne.
Idan baba ya shigo yaga bana cikin su yanzu zai fara fada dani wai ina tsabbare kaina a cikin yan uwana.
Sai kaji Inna tace mugun hali ya ci may idan batai hakan ba ko uwarta baka ganin komai nata a makidance takeyi shi don dai kawai duniya ta zage mu.
Ace muna gallaza mata ita da uwarta a gidan kasan mutum baida gadon ka amma yana da na maganan ka yanzu.
Sai kaji baba ya amsa da naga alama ai an koya mata halin tsiya ta iya itama.
To ba dole ba kullun suna daki ana mata hudubar tsiya a kai dabiar da ba zai amfane ka ba ko yau tana tsabbare sun hada kai da uwar ta a daki suna wance tayi min abu kaza don may bazata tashi da mugun hali ba kuwa ?
Abin yana ban mamaki don sai inga ai komai a baiyyane yake ai a gidan ni dai a iya sani wani fitina bai tasowa ace da Safiya a cikin sa.
Ko wani ya kawo kara daga waje yace ai Safiya tai mun wani abin suko ko yaushe cikin sallama mashi ake ana kawo karan su gun shi.
Sai dai abin mamaki wanan bai sa yayyena maza su kini ba a gidan namu don su basu matsa min kuma ba su yarda ai min sheri a gaban su yanzu zasu ce zasu daki yarinya idan tai masu tsiya tun dai yaya sani.
Kuma duk wanan abin idan sun dan samo kudin su gun Ummina zasu nufo dashi ta baye masu har ya kare.
Da haka har ummi ke dan samu tana basu shawaran abinda zasu yi wanda zai amfane su a rayuwan su, sai kuma iyayyen nasu suka koma cewa.
Wani sallon yaudara ne don ta raba su da yayan su ummi ta dauko sukai mata ahir da yaran su shikan yaya sani da ya samu labari tun a nan yau zaune tsakar gida yana fadin.
Oho wai ni za aiwa yau don a raba ni da mai taimaka min a dinga kwace min kudi to ban yarda ba babu wanda zai hanani bawa maman safiya a jiyan kudi na a gidan nan.
Ke mama da kike fadin haka ba nan Nura ya sayo akuya ba ku kai masa sheri aka sayar da akuyan akace mai ya bata.
Cikin tsawa mama tace dashi kai kada ka kawo min diban albarka idan kaje kayo shaye shayen kane kake son saukewa a kaina bazaka sha da dadi ba yanzu na saka yara na suyi maka tsinanen duka a gidan nan.
Wuf daya yayi ya yanko reshen darbejiyan dake baya gidan mu yana fadin yau naga shegen dan ki daya isa ya tabani a gidan nan idan ba a kwashi gawan shi ba shege nake.
Yau kuwa zan gwada maki halin mashayan da kika kira min aiko yai cikin su a kofan dakin ta da take tsaye da diyan ta a take suka watse.
Suna rige rigen shiga daki wani na ture wani daga kofan dakin wurin shiga dakin don yai masu mai ka uwa da wabi baki daya.
Ashe fadan bai kare ba sai ga Inna ta na cewa idan har yaron na yana shaye shaye ke ko diyan ki barayin kororo ne da karuwai, waye bai san abin da suke a gari ba har akuyan da kike fadin an sace dake da diyan ki kuka sace shi ai.
Nan fada ya kaure tsakanin ranan dai gidan mu babu dadi tonon asiri zalla suka dinga yiwa junan su har abin dake a boye saida kowa yaji shi gare su.
Baba na kasuwa dole aka kirashi shi yazo ya kashe wanan wutar fitinar da ya ruru a gidan don gaba daya yaya Sani ya haukace masu a gidan.
Iyakarmu kallo da saure sai washe gari da baba ya kira sulhu da safe kuma suka so su dora laifin gun ummi na mai farin jini a gare su.
A nan ma yaya Sani baiyi shiru ba yace may ye laifin ta a ciki kudi dai ne har gobe ko kaya ita zanbawa a jiya ni babu ruwa na da zancen kishin ku.
Dole inna tana ji tana gani suka saka mashi ido don ya riga da ya kangare ba mai iya lankwasa shi a halin yanzu.
Idan ya shigo gida har da gaiyya yake jan ummi na da hira a cewan shi haushin mama yake ji don itace ke kulla duk wani makirci a gidan.
Ita ko Inna bata tsayawa saurare sai ta hau ta zauna a kai daga baya kuma mama ta zamay jikin ta ta nuna bada ita akayi zancen ba ta bar Inna a ciki.
Mu dai a gun mu har gobe gaba dayan su a yan uwa muka dauke su ba mu banbanta a tsakanin mu dukkan su a yan uwa muke daukan su.
Sai dai su a gun su ba wani canji a gare mu dasu har gobe halin yana nan na yan ubanci da suke nuna muna a gidan.
Mun zama su shanun ware ko bare da suke kyankyamin mu daga cikin su suna bakin ciki su bude ido su ga dan dakin mu na wani abin ci gaban rayuwa yanzu sheri zai tashi a tsakani sai anga bayan abin an durkusa.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:10 PM - Ummi Tandama: BAHAGON, , , , , , , ,


🧕🏿3️⃣ 🧕🏿


FREE PAGE, , ,


SEENABU MAKAWA, , ,

NA ROKE KI DAN ALLAH DON SON MANZON RAHAMA IDAN DA ZUCIYA BIYU ZAKI SHIGO GROUP DIN KADA KI SHIGA DON ALLAH DON BAZAN YAFE MAKI BA WANDA KIKA TURAWA HAKKIN YANA AKAN KI YAR UWA DON ALLAH KI HAKKURI DA DAUKAN HAKKI AKAN NOVEL DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE KIN SANI BA PUBLISH NOVEL BANE DA KI KE FADI KIN BIYA NE DON ALLAH MU SAHIRCE WA JUNA AKAN HAKA YAR UWA KAN ABINDUNIYA DAFATAN ZAKI KU FAHINCE NI.


Yau alhamis bamu shiga islamiya don haka na ke son zuwa ziyara gidan yan uwan mahaifiyar mu dake a cikin gari.
Zaune nake ina kwaliya a kofan dakin mu yayin da mutane gidan mu ke ta aiyu kan su na yau da kullu a cikin su har da ummi na wacce ke wanke kofi.
Sallama aka shigo dashi gidan dashi shi ne ya dauki hankalin kowa a gidan baki daya tare da amsawa.
A, a mutanen lagos yau she agarin abinda su maman mu ke fada ke nan mu yara muka shiga sannu da zuwa.
Ta dan tsaya a tsakar gida suna gaisawa sama sama da mutanen gidan da ga nan ta kwasa tai dakin mama,
Daya bayan daya ake shiga gaida ita tana amsawa don sanin muhinmanci ta ga iyayye mu baki daya.
Gwago kulu ke nan kauna ne ga mama kuma yar uwa ga mahaifin mu don mama da mahaifin mu yan uwane dukkan su auren gida ne sukayi irin matar fari zabin iyayye din nan.
Haka yasa mama ke shimfida mulkin ta yadda taso a cikin gidan daga ita har yaran ta ko magana ake a gidan wanda ya shafi gida zakiji mama tace mu din kujera ne dole a bi mu.
Don da mijina aka samay ni ko anki ko an so dole ne a gan mu a gidan babu yadda za yi damu dan mu yandagi ne.
Watarana idan tana irin wannan habaicin Inna takan biye mata suyi tayi sai sun gaji har ta kan ce ban ga macen da zato tace zata shifida min doka ba a gida na.
Sai dai duk wannan haukan ga may wayau da hankali yasan Inna ce ke shimfida mulkin ta a gidan don baba a can hankalin shi yafi karkata.
Ni dai nakan ce tsoro ne don wani lokaci zaka ga ya juya gun wata da zaran inna taga haka yau zata birkice mashi da masifan dare daban na rana daban saiya dawo a kan ta.
Duk wani dan uwan mahaifin mu da zai za gidan wirin mama zai yadda zangon shi ba zai tafi wani daki ba sai in wani dalili ya kawo mai shi.
Wannan abin yana kona wa inna rai don ita mace ce mai son taga komai ita ne a kan gaba a gidan namu.
Saida na kanmala kwaliyana na saka hijjab dina na karasa kofan mama ina fadin sannu da zuwa gwago alokacin sun hade kai da mama suna magana a hankali kasancewan su biyu ne a dakin ki.
Cikin dan hanzari ta amsa min da yawwa na juya zan tafi sai take cewa wa nake gani kamar sai tai shiru can tace ba yar wurin Rabi bane ?
Mama tace itace tace, mana tace ikon Allah girman dan mutum baida wuya har yaushe yaushe aka haifi yarinya nan diba yanzu yadda takai da girma.
Sai naji mama tace ta biyo tsawon kafan uwar tane kisan Rabi ba baya ba wurin tsawo shine suka kwaso ai duk haka yaran suke in kin gansu.
Nidai na tafi ba abina ban tsaya jin sauran abinda zasu fada ba don dai zancen bai kare ba na bar su akai.
Dariya naji sun kwashe dashi wanda nasan wani sheri aka fada wanda yai dadi har sukayi hakan .
Mu Huda muka fita da kannena gidan gwagon mahaifiyar mu muka fara zuwa inda muka samu taro na arziki ta rasa ida zata saka mu.
Haka mu ke gani idan munje gun ta muna samun taro yadda ya kamata sabanin dagin mahaifin mu, wanda basu ma san da zaman mu ba nake gani.
A binci ta shiga girka wa don idan muje wuni muke a gidan ta, nafito na kama mata aiki yadda ya kama ta har muka kan mala yin komai.
Abinda bamu saba ba gidan mu an cika muna kwano da shinkfa da mai da yaji sai ci muke yi hannu baka hannu akushi.
Ga zobo mai sayi data sayo muna mu sha dashi mun kai kat na kwashe kayan da mukai aiki da amfani dasu da wanda mukaci abin ci akin sa.
Na gyara mata gida sai nace da ita zamu mu gaida su mama watau diyan ta ke nan dake aure a cikin uguwa.
Tace kada mu dade don mu koma gida da wuri mun tafi inda can ma muka samu taro yadda ya kama ta sun bamu alheri su man shafi da sabulu da omo da dan kudi muna ta murna mun samu kyau ta .
Gwago ma tai muna abin arziki muka dawo gida bayan sallah la, asar cike da zudin kyautan bajin ta da muka samu.
Muna tajin dadi muka nuna wa ummi alherin da tan uwanta suka kai muna ta sani tare da fadin shine abin dayasa bani son kuna zuwa gidan su don dawai niya kuke kai masu.
Kani yai caraf yace ummi cewa sukayi fa mu dinga zuwa ko yaushe kuma kikece damu kada mu koma abamu .
Gaba daya dariya muka sa mai ummi tace damu tare da dubana nida nake da wayo a cikin su yawan zuwa zai sa su gaji daku ne ku zauna matsayin da Allah aje ku Allah zai dube mu.
Jikina yai sanyi don na fahinci may ummi take nufi din a sanyaye na ce in sha Allahu ummi baza kara zuwa mu kai masu nauyi ba haka.
Dan abinda muka samu ummi ta ware min wani abu acikin sa waina kara jari dashi na sana, a na da nakeyi kada mu kashe a baki daya.
Wanan kudin shine sillar da har takai mun da samun sauki a dakin mu don a hankali na fara sarrafa kudin biyar na kamowa goma gama na zama ashirin ashirin ya koma wazo har zuwa sama.
Idan baka raina sana, a tau watarana sai ya koma maka babba don tun ina dan madara har na koma ina soya ruwa ana saye a gida.
Sai gashi har nawaje suna shigowa saye na hada da aya da sauran makulasa sai sanaa ya koma na ummi na.
Sannu sannu ina sana,ar har muka koma mangyada da sauran abin amfani kudi na shigo muna.
Sai hassada da kyashi ya shigo a cikin wa yan gidan mu nan kuma bamu da sauran shakat gare su zasu ce damu ganin muna dan sana,an dake kawo mu kudi ya muke son yi masu gani gani.
Sai suka da habaici ya tashi har zance yakai gun baba na magana kadan yanzu zai yo cikin ummi da zagi yace wai mutane suna shigo mai gida don su din ga lekan may asirin gida suna fita waje suna fadi.
Nan mama ta turza don kan taki yarda da zancen baba na wanga karon ta ko hankace mashi da fitina tana cewa ai da takoma in irin halin da ta fito gara ta hankura dashi ta tafi inda ake son cigaban ta yafi mata don ta ganne cigaban ta akewa hassada bakomai ba.
Inda watane ke wanan sana, ar aiba za hana ba amma don anga tana samu za ai mata bakin ciki ga sana,an ta, kowa na dan sana,an shi cikin gida bai yi magana ba, sai nata ne za ia wa bakin ciki.
Da haka zancen ya mutu karshe mama ta ce ya kyale ta taita sana an ta tunda kowa na saman sanaar ashi badon aina tasa ba dole ta kyale ummi ta ci gaba da sana, an ta tana na kallo ba yarda zata yi a gidan.
Wanan ke nan ya wuce saura wani kama don ummi ta kyatare wanan karon daga kaidin ta.
Wanan abin da akeyi ina yar shekara goma sha uku da haihuwa amma duk idon gidan mu na ga kaina gaba dayan su kamai yan yazu ace safiya ce.
Koban ji ban gani ba don dai kawai ai min fada suji dadi yanzo zasu jawo abinda za ai min fadi din .
Duk wani aiki aike yi mai dadi da akasin sa duk ni zan yi amma duk wanan ban tsira akan shi ba don cewa suke wai lalaci da raggaci yai min yawa.
A haka jebawan mu shiga secondary yafito inda naci makarantan kwana aiko take yan gidan mu suka nuna bakin cikin su ka zancen.
Suke cewa makaratan kwana ko lalacewa may zaki koyo banda lalacewa a makarantan kwana bokon diya mace ko lalacewa.
Kai komai sun fada akan wanan zuwa karatun nawa karshe dai baba sha zuga sai cewa yayi abar zancen karatu don shi bai ga amfanin yin karatu ga ya mace ba.
Ina ji ina gani aka watsar da zancen karatu na ganin da gaske baba keyi na sulale jiki na tafi wurin gwago na fada mata komai.
Batai sanyi ga gwiwa ba ta sami babana a kasuwa don magana bai yi a gida nan dai gwago ta shawo kan shi har ya yarda amma da sharadin .
Baba hannun shi a ciki ko kwadalan shi ciki gwago tace taji ta dauka akwai Allah zakawo mafita.
Amma yace ba zai yarda da batun zuwa makarantan kwana ba gwago tace taji zasu samo jeka ka dawo na tafi.
Wannan shine dalilin zuwa na makaranta da nayi mutane gidan mu dai sun ga ina shirin ba su san komai ba.
Ranan da zan fara zuwa hankalin kowa a gidan ya tashi don sai suke zargin mahaifin mu ne yai min ko mai.
Nan ko ina ta saka shi a gaba da cewa munafucin banza da wofi idan an tanbaye shi kudin yace bai dashi amma ya dau ki yar gwal ya saka a makaranta don ran uwar ta yai dadi.
Ba dole ba yana gudun bacin ran uwar ta kada ta hana shi kwana da ita ya rasa jin dadin shi.
Da abin ya ishi baba yai ratsuwa har ya gaji shi ba dasanin shi bane baiba ma san wanda yai samo min makaranta ba amma nasu yarda ba.
Sai cewa yayi ya biya min din suda yake wa dayan su lalurori fa saiko fada dashi da inna har takai ga yin ya ji a gidan.
Yaya sani yace safiya ki shirya da kaina zan kaiki in ga wanda ya isa ya hana ki zuwa na gane yan bakin ciki ne mutanen gidan nan.
Da yaya sani muka tafi makaranta sai da yaga komai ya kamala ya dawo gida.
Tun wanan lokacin aiki ya rage man agidan namu saboda ban da lokacin zama a gida har su ganni suce in ma su aikin.
Sannu a hankali girma ya shi gana yanzu na fara ganewa bawai son ummi ne mahaifin mu ba yayi ba kawai dai shakun matan shine yake ji.
Na gane hakane ta yadda idan ya fakaici idon matan shi yake nuna kulawan shi kan ta har nama yakan dan ja ta da wasa ko da ba, a.
Sai dai idan matan shi sun gani ya kan dan yi kamay kamay kamar bashi ne daga karshe dai ya koma fada kamar bashi ba.
Kadai muke zaman mu da dadi ba dadin a gidan watarana mu kwana da farin ciki watarana akasin sa.
Sannu tashi na kamal aji uku zan shiga babba ajin aga da secondary sai ga gwago tazo daga lagos nan mukai ta murna da zuwan ta sai awan kararon bata ita kadai tazo muna ba.
Ita da zurian ta da maigidan tazo ganin mu nan aka shiga ina aka saka da ita da diya ta da maigidan ta don dai ba karamin son ta yan uwa keyi ba, in zata zo takan sayo abubuwan anfani tajo ma iyayyen mu da shi.
Nikan ina saurin naje makaranta don haka tsayawa nayi daga kofa na gaida su dan suna dakin mama ne zaune har mijin nata da yaran ta.
Take cewa wanagani kamar yar wurin Rabi haka koyaushe za a gan ki kamar ke kadai ke kiwo a gidan gaki tsatsab dake kamar wata wayyayiya.
Murmushi kawai nayi zantafi sai naji tace wanan ai takar ita koke kiyawu agidan.
Ta juya tana magana da mama bandaiji abin da suka fada ba nai tafiyana don ina saurin in tafi makaranta.
A kofan gida muka tarar da wani matashi yana shan taba zaune saman mota kallo daya nai mashi na kawar da kaina daga gareshi.
Sauri nake na wuce don da gani tare suke da gwago mu sai naji yace ke shiga ciki ki dabo min ruwa nasha.
Na dauka badani yake ba ina kokarin wuce wa naji ya sake cewa dake nake fa na juya baya na ko zanga wace yake magana da ita.
Sai naga babu kowa a tare dani na dan tsaya kadan yace ruwa nace ki debo min a ciki.
Juyawa nayi nakoma na debo mashi ruwan nakawo mashi ya kurba sau daya yake cewa wanan wani irin ruwa ne mara dadi.
Nace shi muke sha a gidan mu don haka shi ke gare mu, oho i see waya kaleni sama da kasa yake cewa karbi ki mayar .
Haushin sa ne yakama ni lokaci guda don ya rena muna wayau da arzikin gidan a haka dai na karba na wuce shi don warin taba duk ya isheni da hamami.
Na dawo zan wuce yake cewa dani ke yana kokarin kuna wani taban a bakin shi shigo kice wa su mum sufito haka nan dan Allah.
Kamar nace bazan tafi ba sai dai na juya zantafi sai gasu sun fito daga cikin uban na gaba suna biye a bayan su.
Nikan nawuce abina ban tsaya kara sauraren su ba don dama nakara zuwa islamiya duk da nasan bawai buguna za ayi ba amma ya kamata ace na isa a cikin lokaci.
Har na isa makaranta ban dana jin warin taban da aka sha a jiki na ba gani nake duk jikina warin taba yake kamar nice nashi taba din .
Mun dawo na debi kayan mu na wanke don ban samu wanke wa da rana ba aka raba tsaraban gwago ko wani daki aka bamu.
Saida na shigo dakin mune na samu tsaraban da gagwo ta kawo muna a gefe, na samu wuri na zauna gefe ina cewa da ummi.
Wanan mutumin dasu gwago suka zo dashi dazun baida tarbiya zama fa yayi kofar gida yana shan taba a gaban ko wa.
Ummi tace dani wa kina nufin ubale aishine dan gwago kuna fari duk sain an ni shi sunyi aure amma shi, shashanci ya na shi yi wai shi dan fari yana takama da zama cikin kabilu ya saje dasu.
Nace Allah ya kyauta amma kan wallahi bai yi ba wallahi mutun sakace wani ibom can.
Muna cikin magana mukaji fada ya kaule a tsakanin mama da inna kan kayan da gwagon mu ta kawo tsaraba inna ke cewa da mama wai tarage kayan ta basu abin da taga dama.
Mama ta bata amsa da cewa yar uwarki konawa ina yar uwa nane dai ko kaya kuma abinda naga dama kenan na bayar inkina so ki karba inbaki so zaki iya mayar.
Mama tace idai kayane je ki ta ci saukin abindai muma muna da yan uwa bake kadai keda su ba balla ki kawo muna bakar magana.
Muna daki da ummi muna sauraren su har suka sude bamu leko ba sukayi suka kare ba mu leka waje ba.
Washe gari kuma da safe suka aza sabon fitina a gidan baba na dakin inna ya fito yake cewa daga yanzu indai rabo zai kawo fitina kowa ya rike abin sa a zauna lafiya.
Da haka karshen fitinan ya mutu kowa in yaga dama ya rike kayan shi ba dole araba wa saura inna tace yafi nono fari.
Mu dai namu dasu ido don sun fi kusa wanda yace zai shiga fadan su a ciki zai kwana minti goma yai kadan aga sun shirya tsakanin su.
A yau asabar bamu zuwa makaranta don haka na shirya cikin kayan da mama lami ta ba ina son zuwa gaida kawata da bata da lafiya.
Wanan ne karo na farko da na sa kayan a gidan mu don basu san ni da kayan ba nan sukayo mani ca da idanuwan su naji mama tana fadin.
A yau kwaliya akaci haka yau sai ina da wanan adon nai murmushi kawai ba tare da na bata ansa ba sai naji inna na fadin ke ma dai yaya da wani zance ki.
Yarinya kekaga tana wanan irn kwalliya haka ai kin san abinda take yi inba mashin shine ai banza ya kai zomo suwa ke ma kin san aida wallakin wai goro cikin miya.
Muka hada ido da ummi na sai taimin da alama da ido na kyaleta na kara shiryawa nake cewa zan tafi tare da yi masu sallama.
Inna tace dama diya mace inta dadani namiji ai ba tafiba hankalinta bai taba kwanciya yawon gantalin za, a ake sallaman mu.
Kai akwai ki da wani zance wallahi ina safiya da ga wani saurayi kyalle ta dai da nacin son karatu a rayuwan ta inji mama ke fada mata haka na.
Ta ja tsaki tace ai ku ke kara zugata wanda baida lokacin kan shi a gida kulun boka watafi son karatu adaiyi shaani kawai wai an cuci na kauye.
Na fito gida ina tunanen kallamin inna ba zaka taba jin kalman alheri abakin ta ba in ba yayan ta bane sai na sheri.
Ita da bakin ta take fadi wata rana yarinya ga kyau ga wanka amma babu saurayi yau kuma ta can za ta kuma ce maza naka bi.
Naje gidan su Amina na samu bata da lafiya sosai amma ta samu sauki na dan zauna da ita mukai hira nawani lakaci na mike zani gida don kar na dade Inna tace sai da ta zubar nadawo kuma.
Mun fito tare da Amina donta dan taka ta walwale jikin ta muna tafe muna hira inda muke tafiya a hankali ina bata labarin text din da kayi muna, bata nan yadda ya kaya.
Hon din motane ya damay mu daga bayan mu da kara daga ni har ita ba wanda ya juya dan gani ko wa nene mai mator kuma bai daina hon din ba.
Ganin ba zamu tsaya ba yasa shi fito wa a motar ya biyo mu, sallama yai muna duk muka juya a lokaci daya muna kallon shi.
Nikan a zato na sun san juna ne sai kawai na fara tafiya na barsu tare ban tsaya ba kada naja wa kaina magana ban yiba ance nayi ina ga na tsaya.
Sai naji yace don Allah malama ko zaki taimaka taimaka min da yar uwar ki ta saurare ni min ti biyu in ba damuwa.
Safiya dake ake magana inji Amina, na juyo nace wani a cikin mamaki yace nasan badaidai ba ne na tare ku a hanya.
Amma kuma dole yasa na tsada ku a hanya yanzu don idan kun tafi ban san ina zan kara haduwa daku ba.
Nace gaskiya bazan tsaya ba sunana ya baci ga ban za a saman hanya sai yai murmushi yace naga alama ai amma don Allah kibani dan lokaci nasan wani abu gare ki.
Allah daya ke hada mu dashi har da Amina din yasa na tsaya badon na so ba ya ce sunana sulaiman ni dan garin nan ne saidai ba anan nake ba.
Ina fatan zaki bani amsa ga tambaya a wurin ki don Allah ida bazaki damu ba zan so nasan gidan ku don na gabatar da kaina.
Gaskiya malam kayi hakkuri saboda karatu nake yi sai an jima nan nabar su tsaye awurin na wuce.
Ya dan rintse idanuwa shi tare da sauka da ajiya zuciya yana mai sauke num fashi , ya dan yi murmushi tare da duban Amina dake gefen shi tsaye yace.
Idan ba damuwa ki tai makeni da noba ta kokuma gidan su zai fi sauki a gare ni nan dai yabawa Amina tausayi tabashi addresen gida yai mata godiya ta tafi.


Ban da lafiya da fatan zakuyi hakuri da mistake din kuka gani anan kwana uku ina typing ban iya hadawa ba.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:10 PM - Ummi Tandama: BAHAGON, , , , ,


🧕🏿4️⃣ 🧕🏿


SEENABU MAKAWA


DON ALLAH NAMIJI KAYA SHIGA DON MATAN MUTANE MUKA KA TARA ANAN INKA KA SHIGA ALLAH YA SAKA MU NA
DON ALLAH YAR UWA ABIN DUNIYA KAR YA JAKI GA HALAKA IN KI BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYABA DON BAZAN YAFE MAKI HAKKI NABA, , , ,


Dare ne kowa na zaune a tsakar gida saboda zafi da duhu da akwai yaro ya shigo yana kwala sallama a kofa.
Baba na gida ya amsa yaron yace wai ana sallama a waje sai baba yace yaya Nura ya duba yagani.
Zuwa can ya dawo yace wai wani wai wurin Safiya yazo amma ya ba son ganin ka.
Inna tai caraf tace Safiya kodai Ainau, Safiya ina taga saurayin da zai mata sallama, ga wayannen ta tanan wake maganan ta.
Yace nidai abinda ya fada min kenan na fada yasamu wuri ya zauna yaci gaba dacin abincin sa.
Inna tace tashi maza Ainau jeki ki gani wake sallama dacewan Ainau yar wurin Mama taje ta ga ba wurin ta bane tadawo kafin Ainau ta dawo ta shige da yar ta mairo daki.
Sukayi ku ku ku da ita saiga Aina tadawo tana fadin Inna ba wurina bane wannan fa dangaye ne ke sallama a waje.
Saiga Mairo ta fito zata har takai kofa taji ance ke dakata wurin ki aka zo ko kuwa tace zan duba na gani ne.
Maza koma ki zauna yaya sani ne ke wannan maganan da mairo daga dakin Inna ta daka mashi tsawa tace kabari tafita ta duba mana ko ita akewa sallama.
Ya ce yaushe mairo ta koma Safiya a gidan nan ne ke bana son rainin woyo maza kidawo wurin nan tun ranki bai baci ba.
Sanin hali yasa ta juwoyo simi simi ta da dawo cikin gida ta zauna ya mike ya fita zuwa kofan gida wurin bakon da kansa.
Duk wanan kace nacen magana da suke faman yi kunnen mu nida ummi sukeyin sa, kallo daya zai kayi min kagane a rikice nake.
Ummi dai batai min magana ba don tsaban tsoro duk jikina ya dauki rawa a lokaci daya can najiyo muryan yaya sani yana kwala min kira.
A rikice na fito daga dakin na rabe gefe guda a tsugunne lokaci guda yake cewa dani, akwai wanda kukai magana dashi zai zo gida ne ?
Gaba daya hankalin yan gidan mu ya dawo gare mu suna sauraren mu a hankali na bude bakina zanyi magana .
Naji Inna tace dani ke yan zuwa har da masu mota kike tsayawa don tsaban miskilan da munafunci irin naki na gado.
Nasoma rantsuwa baki na rawa ina fadi wallahi tallahi na rantse da Allah inna bantaba magana dakowa waye ba
Ji nayi yaya sani yace Safiya na amsa da sauri da naam ya ce tashi kije inda ake maki sallama waje.
Ai gara dake daza ki jawa mai mata kika jawo muna su diyan su da kara da doki duk zuwa yake wurin su fa.
Maza tashi tafi kada yaga an tsaida shi kin dade baki fito ba ya dauka bakya nan ne.
Na mike gwaiwa da sanyi da ce tau yaya nufi kofar gidan wurin wanda aka ce din yana min sallama wanda yaja min zagi da zargi agida uwurin mutanen gidan mu.
A kofan gida nahango shi tsaye ya jingina jiki da mota hannu daya kuma ya dafa motar shi dashi ya tsura wa kofar gidan mu ido.
Yana gani na ya dan muskuta tsayin shi yagyara da kyau har na iso kusa dashi.
Fuskana kamar zanyi kuka a lokacin nazo na tsaya sai yace dani ba gaisuwa yan mata kamar baki na na ciwo nace dashi Ina wuni ?
Shima cike da yanga yace min lafiya lau yan mata,
Wai halan ba ke kadai bane Safiya a gidan naku sai naga wasu yan mata nata fitowa da sunan safiya mana.
Saida na dan bata lokaci kafin nace ni kadai ne mana kawai da sun fito ne sun dauka wiri su aka zo yaron yai matuwa yace safiya don sun ga ba wanda ke aikowa kirana sai yau.
Ya nisa tare da cewa "kai, kice ni din nazo a sa, a ke nan nine zan bude fage in bar tarihi.
To amma naso naga baba ne da kaina koda yake ai naga yayan mu ya bani go ahead naci gaba da zuwa .
Kallon sa nakeyi ta gefen ido ya yagyara tsayuwar shi da kya yace na samu goyon baya kai tsaye ke na kinga duk lokacin da nake son ganin ki ina iya zuwa.
Na turo baki ina cewa indai na amince da hakan ko nifa na fada maka karatu nake son yi ban da lokacin tsayawa soyayya.
Ba zabin ki nake son ba illa yaka ki bani hadin kai shikaratu nufi ne na Allah.
Don haka ki bar Allah yai maki zabi kar ki raja, a a bangare daya don kinfi son karatu kice gareshi zaki tsaya.
Kunya bakin ciki da takaici suka sauka min a lokaci daya na rasa amsa da zanbashi kawai sai hawaye suka dinga zubo min .
Ganim ina kuka yasa shi cewa subbahanallahi ko ban fadi daidai bane ga magana na kike kuka.
Ganin bazan yi shiru yace Allah ya naki hankuri idan kin huce na dawo mu gaisa watarana dama yan yanzu zuwa nayi wurin baba don neman izini ban samay shi ba naga yayan ki.
Ya bude motar shi ya dauko leda cike dakaya ya miko min nace yabarsu na gade yake cewa Safiya nadai gane bakiyi naam dani ba ne.
Nace ba hakana bane in son samu ne nafison saina gama karatuna tukun yace wanan baida matsala mudai samu fahintar juna tukun shi yafi.
Nan nabarshi da kayan naki karba ashe ya samu dan makwabtan mu yace ya biyo ni da kayan ciki.
A Cikin gida kuwa tun fitana mutan gidan suka kasa suka tsare suga yadda za a yi yayin da inna take ta masifa da yaya sani akan wai nata mata shiga hanci da kudundune kan ala, amarin ta inda take shiga ba nan take fita ba.
Shigowa na kenan yaron da ya biyo ni da kaya ya shigo gidan shima inda na nufa can yaron ya nufa da kaya niki niki.
Yaya Nura ne yake tambayan yaron maynene yadauko a hannu shi haka sai yaron kewa Safiya ace nadauko mawa .
Gaba daya suka sako ido suga kamay nene a cikin ledan saidai bazasu iya ganin ko may a ciki ba saboda duhun dakeyi.
Inda da hali dazasuce akawo ledan suka abinda ke cikin sa sai dai hakan bazai yuyu ba don yaya sani na gida alokacin.
Dole da ido suka koma yin magana ba halin su maganta yai cikin su da rashin kunya.
Har washe gari kayan na nan a jiye ba a taba ba ba a kuma bude ba a cewar umma in yazo na mayar mai da kayan sa kada na nadauko mata wahala tana zaune kalau.
Daga ni jar ummi tsoron taba kayan muke ja agidan bamu yarda nun taba komai ba daga ciki Ummi tai mashi dogon ajiya.
Abim duniya ya isheni a raina ga kayan mutumi a je a gidan mu ina tsoron tabawa a tsakar gidan mu sai habaici ake min cewa a samu a hanawa dangi.
Amina na samu a school nake fada mata halin da nake ciki don dai gaskiya ni sulaiman yafi karfina da soyyaya.
Dariya Amina ta soma yi min tana cewa safiya kenan ina kika taba jin haka kedai kawai kice matsayin ku ba guda ba.
Amma zancen yafi karfinki bai taso ba don dai sulaiman mijin da mata da yawa zasu so ne.
Balle mutumin daya nemi izzini ta gidan ku ai zance ya kare iyaka muyi fatan alherin ga hakan, nisawa nayi nace da ita Amina nifa in son samu ne nafi son sai na gama karatu kafin na fara zance da wani namiji .
Safiya kin kwantar da hankalin ki bafacewa akayi zaki aure shi ba dole, abune nufin Allah .
Nace haka ne amma ni sherin mutanen gidan mu nake jiwa don masheran tane na karshe sun sa yadda zasu kulla wa mutam sheri ya zama gaskiya .
Da dai zai jaye ya je gaba yane mi wata zai fi sauki don ina gudun jefa shi a cikin zargin mutamen gidan mu.
Ba tadai yarda sai bani karfin gwiwar da tayi akan na hakkura naga ya gudun shi in yasu sai nayanke hukunci akai.
Sulaiman mutumin kirki ne sosai a yadda na fahinci shi ba a garin yake zama ba zuwa yake duk karshen wata kokuma farkon wata.
Idan zaizo yakan yo muna sayayya yadda ya kamata ya zo muna dashi har kullun yazo bani sakewa dashi amma shi sai yake daukan hakan da kurciyane kawai.
Tun yana zuwa ban sauraren shi har yakai na fara sauraren shi ina dan bashi lokaci sannu sannu har kowa ya fara sanin shi a gidan mu.
Dan idan yazo zai ba da kudi da kayan rabo irin su sabulu da manshafi a rabawa mutanen gidan mu, inda ni kuma yakan kawo min kayan provition na amfanina.
Wannan abin shiya tsone idon mutanen gidan mu don walwalan da suke ganin mun samu a gidan.
Tsegumi da kazafi yaki karewa a gidan sai cewa suke wai babana yaga kudi shiyasa idon shi ya rufe bai iya magana wai har cewa sukeyi .
Sulaiman na dauka na da mota muna fita yana yawo a cikin gari maganganu dai marasa dadi suke kai da kawo akan zancen.
Sai dai ummi na hankalinta yakan tashi dajin wannan zancen sai da dare tan tayar dani daga barci ta sakani a gaba da cewa.
Yar nan kirufa min asiri ki kamaka kan ki karki tona min asiri a cikin abokan zama abin na da suke fada gamay dake Allah yasa ba gaskiya bane kodai daya ke nasan ki nasan halin ki.
Nasan abin da zaki iya da wanda bazaki iya ba amma dai dolene na kara tsawata maki akan hakan.
Don Allah ki kafa mutuncin ki ki rufa muna asiri yar nan bani kadai ba har da mahaifin ki nakan son rantse mata cewa ba gaskiya bane sai ta dakatar dani da cewa bar ni na fada maki yar nan.
Nice mai fada maki gaskiya duk duniyan nan ku nake da ku nake gani ina alfahari a duniyan.
Idan ummi tafadi haka nakan ji wani irin tausayin ta a raina wana abin yasa sulaiman ya rage zuwa gidan mu wanda
Hakan kuma suma ya shafe su don dan abin da suke samu ya daina zuwa yana basu sai kuma suka koma cewa .
Ya gama dani ya gudu suna dariya suna fadin na goga masu tsiya a ranan da sukai dariya a ranan kuma yan uwan sukaima suka zo wurin babana da kaya niki niki na nema wa sulaiman aure na.
Amsan da baba ya basu shine sai yayi shawara da matan shi don ina da yanne har hudu a gaba na ..
Yara suka shigo da kaya ciki niki niki kowa ya fito yana gani ana sake magana nidai muna daki da mahaifiya na ba wanda yaleko daga cikin mu.
Ana cikin wanan haya niyar gwago lagos ta bugowa mama waya ta layin Nura yana bawa mama ba, a jin abinda take fada sai da mama ta shiga daki.
Tace wai hayaniyar may kuke yi a gidan ku ne haka ina jin na hayaniya kamar mutane da yawa wurin.
Mama ta ba ta amsa da muna kallon kayan da aka kawowa Safiya ne shi meke ta surutu.
Gwago tace wacce safiya ba dai safoyan naku da nake son naiwa yaya magana ba a kanta.
Mama tace Safiya dai yar wirin Rabi na nan gidan nake maki magana sai gwago tace kaya kayan fa?.
Akwai matsala ne inji mama take tamabayan ta akwa matsala kan don dama ina son nemawa yaron nan auren ta ne yanzu kuma naji wani magana can.
A, a ta yaya za ayi gida bai koshiba akaiwa daji dole asan nayi dai akan haka amma dai zan fadawa malam di don ya sani a san abin yi.
Nan dai sukayi kulle kullen su da mama har suka gama mama ta kashe wayan tun da mama ta fito take anna shuwa da guda a tsakar gadan karshen ta suka shige daki da inna.
Shiru shiru basu fito ba sai wani lokaci mai tsawo suka fito suna murna suna dariya tun nan Ummi na tasha jinin jikin ta.
Washegari da safe magana ya fara fitowa a gidan mu cewa wai dan gwago na lagos za a bani da farko jin su mukeyi sai ranan da sulaiman yazo zan fita babana ya dakatar dani.
Ya tashi ya fita zuwa wurin shi bansan may ya fada mashi ba sai tashin motan sulaiman kawai naji ya tafi.
Baba yana dawowa cikin gida ya kwala min kira da sauri nafito daga dakin mu yake cewa dani .
Safiya wanan yaron dake zuwa wurin ki na dakatar dashi don zan hadaki da dan wurin gwogon ki na lagos ne.
Saboda haka daga yau bani sin jin zancen wanan yaron a gidan nan duk abin da kuka san kunci na shi ku tattara mashi a mayar mashi da abin shi.
Gaba na ne ya fadi na dago kai a razane na kalli babana zan yi magana sai hawaye ya hana ni fadin komai muryan baba ne ke cewa kin dai ji abanda na fada maki.
Nace a sanyayye naji baba ina mikewa ya kwala wa ummi kira yana cewa ina rabin take ne kizo kiji ke ma hukuncin da na yankewa yar ki.
Ummi ta fito duk jamaan gidan sukayi tsit suna sauraren shi yace yar daga yau ban son na kara ganin wani yazo gun ta.
Kuma ku hada nashi i nashi tun wuri ku mayar shi da kayan sa kinji magana na ya karasa kamar mai fada.
Daga kofan inna inda take zaune tace, hum,in a, she akwaita kuwa a gidan nan, yo wasu kaya kayan kayan da ake shigewa dasu daki muku,muku a cinye ina za a samay su ai yau ga ranan ta.
Ummi ta kada kai kawai ta wuce zuwa dakin ta koda ta shiga ta samu na kifa kai a gwiwa na ina kuka.
Cikin kuka nace ummi kin ji abinda baba yace,
Naji amma yaya zamuyi kin san halinsa baban naku sarai balle maganan da aka shirya yin shi akan mu.
Dom haka kar ma kisaka wa ranki damuwa akan abinda ki kasan bamai hanawa sai Allah
Tace dani ba kuka zakiyi ba don kuka bashine mafita ga wanan zancen ba samun mafita shine abin yi.
Da yake cewa dan gwagon ki zai hada ku dashi shidin ma ya san ki ne ko kuwa dai wani irin hadi zaiyi.
Nace ummi Allah yasa dai ba wanan mai shan taban bana yake nufi ba zai hada ni dashi aure.
Yanzu dai ki bari kisamu gwago da safe ki sanar da ita halin da ake ciki don mu san mafita.
Nace ummi kina ganin baba zai yarda da maganan gwago har ya yarda yajanye maganan shi .
Tace sai mun jeraba mun gani tukun don a gaskiya in dai yaran laraba ne ban ga mai tarbiyan da zace zaki aura a cikin su ba.
Yaran da idon su ya bude da duniya basu kallon kowa da daraja a idon su kowa a hankade suke ganin shi.
Kuka na saka wa ummi a cikin daki tu tana saurare na har tagaji ta kwanta ta bar ni nasan itama dai ta kwanta ne ba wai barci ta samu yi ba.
Da safe ban shiga makaranta ba gidan gwagon ummi naje na saka ta gaba ina ta kuka da kallamai masu tsuma zuciya.
Gwago tai rarashin duniya ta ga ina batan shiga cikin wani hal dole ta aikwa diyan ta suzo tana neman su.
Sin zo sun samay ni take mayar masu da abin da ke faruwa kowan su yace gaskiya takuran yai yawa har da auren ma baza a bari inyi wanda nake so ba.
Sun yake magana cewa zasu je su sami babana akan zancen don su dauki matakin da ya dace.
Sai dai baba bai saurara masu ba ko kadan inda yake shiga ba nan yake fita ba yana cewa wa ya haifa mashi yar da zai fada mai yadda zai yi da ita.
Karshe dai aka tashi baran baran dasu da shi kowa na kunfan baki ran su ya baci suka tafi.
Bayan tafiyan su ya kira mahifiyana ya sauke mata kwadon balai har t
yake ikirarin cewa kan zancen nan sai ummi na tabar mashi gidan shi.
Ga zaton shi ummi zatai shi amma ga mamakin shi sai yaji tace da yafi nono fari wallahi indai kagani haka shi yafi maka to ka matsa.
Ta shige dakin ta tana bakar magana wanda sai yaune take mayar mashi da ansa a tsakar gida.
Su ko inna dadi suka ji yadda baba yake muzanta ummi dani a tsakar gida suna jin dadi sai cewa sukay mai abu ja mara abu ja.
Samun wurin mahaifi ya ya yanke sha wara kan diyar shi amma don karfin hali za a zo a ce ga yadda zai yi.
Bani ci bani sha nabi na ramay dana fito tsakar gida yanzu zakiji su inna na cewa yarinya an cuce ki an hadaki da tsoho wai a cewan su Ahmed ya tsufa baiyi aure ba za a daukeni yarinya karama a bashi.
Su dinga fadin wai ai karyan kilibibi ya kara min don ban ga wurin yi ba a gidan gwago don bazan kawo mata haka ba gida.
Daga ummi har ni bamu jin dadin mutanen gidan mu habaici da yaben magana bamu da shakat a gidan ko kadan.
Har takai rainin wayon yana son taba mutuncin ummi hakan yasa ranan nai magana wa mutan gidan .
Dan wurin inna ya dauki roban ummi yai wanki dashi maimakon ya mayar ida ya dauka sai ya barshi a tsakan gida ummi tai magana ya taso kamar zai duke ta uwar na gani bata tsawata mashi ba.
Bansan lokacin da nasa baki ba ga maganan fadan ya koma nawa duk da nasan ba iyawa zanyi ba.
Uwar tace ina na fito takama mu tai muna tas ni da ummi da sauran yaran dakin mu.
Baba ya dawo inna ta kwashi karya da gaskiya ta fada mashi inda yake shi banan yake fita ba a gidan.
Ga inna irin matan nan ne dabasu so a taba su diyan su amma suna iya yiwa dan wani ka mita magana daya sai anyi kwana barkatai ana maimaita shi.
Fitina ya ishi ummi tace kai yaya ina dai anyi wanan zancen ya wuce aiko ta hayayyako wa ummi da masifa da jidali .
Wanan abin ya kara jefa ummi cikin damuwa da kuci da takurawan ta kasance cikin tashin hankali haka yasa na kara shiga damuwa da halin da mahifiya na ke ciki.
Damuwa yayi min yawa ga auren da akeson min na dole a kaina ga halin da ummin mu take ciki da mutanen gidan.
Ranan itace da girkin gida girkin da ba komai ake kawo masu nahadi cikkake ba sai mutum yayi dabaran da kan sa.
Da taimakona ummi ta samu ta kammal aikin ta na dauka nakaiwa kowa nashi dakin su na koma dakin mu na zauna sai dai na kasa aiwata komi akaina na rasa manene abinyi don kawo sassuci na alamarin namu a gidan.
Haka na kwana da wanan damuwar a raina ban samu barcin kirki ba tara dani dama tun da wanan zancen ya fara bani barcin kirki a tare dani.


Kuyi hakkuri please kadan kuka samu


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:10 PM - Ummi Tandama: BAHAGON , , , , ,


🧕🏿5️⃣🧕🏿

DON ALLAH YAR UWA IDAN BAKI IYA HAKKURI DA YANAYI, NA ROKEKI KI AMSHI KUDIN KI TUN RAYUKAN MU BAI BACI BA DA JUNA , KOMAI NA RAYUWA ALLAH KE BADA IKON YIN SA DON HAKA MUYI HAKKURI DA JUNA, , , , ,
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA.
IDAN KIN FITAR MIN DA NOVEL ALLAH ZAI KARBAN MIN BASHI NA A WURIN KI


Da asuba na fito tsakar gida ina shara don kasancewan ummi ca mai girki ranan.
Ummi na gani ta fito daga dakin ta cikin zumbulelen hijjabin ta na sallah idanuwanta na zubar da hawaye.
Kai tsaye ta nufi hanyar kofar gida tsatsiyar dake hannuna na aje na nifi wurin ta da sauri tare da riko hijjabin ta nace.
Ummin mu ina zaki ?
Tajuyo hawaye na zuba a idon ta cikin raunaniyar murya tace dani.
Gidan mu zan tafi .
Take nawa idanuwan suka ciko da kwalla don nasan wannan tafiyan da zatayi bana lafiya bane cikin rudani nace mata.
Ummi may yasa zaki tafi kibarmu cikin gidan nan ?
Batayi magana ba sai hawayen daya karu a idon ta ta juya taci gaba da tafiya atake na fashe da kuka mai tsuma rai.
Na bita muka fita waje ina cewa ummi hakkuri zakiyi dan tafiya kibar mu a haka cikin wannan gida ba shine mafitaba.
Tace dani gidan mu zan tafi na gaji da wannan zaman na kunci da bakin ciki.
Na sake cewa da ita kiyi hakkuri ummi watarana sai labari, sai ta dan kalle ni tace dani .
Haba yarinya da ace za a daina ai da an daina shekara nawa ana bu daya shikenan mutum tsakanin ka da mutane babu zaman lafiya .
Duk gida an tsane ka har ku yashafe ku sai yaushe wanan halin zai kawu.
Ina shirin bata amsa baba ya fito don zuwa sallah yana ganin mu har yaso cewa su waye a nan ?
Ko ya gane mune sai yaja tsuki ya ce ai ki kyale ta tafi tunda har yanzo ita bata san tai hakkiri ba sai ya wuce.
Nace da ita ummi ki daure don darajan mu ki koma tace yaya basu hana na kwatar wa kaina yanci ba.
Dakyat ta yarda muka koma ciki munyi arziki mutanen gidan basu fito ba har ta koma ta shiga dakin ta.
Shi kan shi baba da yaga bata tafi ba da alama yaji dadin hakan don yasan abune mawuyaci ta tafi gidan su su kyale ta ta dawo din.
Hakana muka wuni agidan cikin bacin rai sai dai ina yi ina kara kwantar wa ummi din da rai.
Da dadare baba ya dawo baiga dan dakin mu a waje ba ya shigo dakin namu ganin ya shigo yasa mu fita dakin na shimfida mu tabarma a waje muka zauna.
Ummi na zaune a bakin gadon ta ya samu wuri ya zauna a kusa da ita yace Rabi niban san ina hakkirin ki yaje ba yan zu.
Har yarinya karama zatafiki tunane, ina iya hakkuri na gurin naga na kyautata maku amma hakan ya gaza samuwa.
Kiyi hakkuri don Allah ki yafe min ba laifina bane nakan rasa may ke yawan kawo maku wanna matsalan.
Ummi dai bata tanka shiba ta kawar da kan ta gefe daya don bata son ko kallon shi balle ganin shi.
Ganin haka yasa shi mikewa yabar mata dakin yana cewa a bani abinci na ci ya fice.
Ya nufi hanyan fita ta bishi da hararan tsana don kwata kwata ta gaji da shi zaman auren dai sukeyi ita bata ga wani amfanin hakan ba.
Ta mike tana jin wani tukukin bakin ciki a ranta ta rasa yaya zatayi ta magance matsalar dake damun ta a ranta batare da wani yaji ba.
Matsawan tana son kawa karshen auren nan sai dai idan nata auren zai tabo ne hakan kuma tonon asiri ne gurin yayanta

********* *********
*********
A gurin mutanen gidan mu muke jin wai su gwago zasu zo ai maganan auren mu da dan ta .
Zan iya cewa kowa a gidan mu bai san wanan mijin da ake cewa anyi min ba a cikin yara don haka aka matsu da su zo din .
Ba wani yi gyara ba balle kwalliya don taron bakin da zasu zo, ranan weeken ne don haka kowa yana gida bamu fita ba.
Muna zaune a cikin dakin hira muke da ummi na ina dariya mukaji ana masu sannu da zuwa da bakin lagas.
Gwago ce ta fara shigowa gidan ita daya mutanen gidan mu sai raba ido suke suga mikin nawa.
Suka kwasa sukayi dakin mama a ca aka shiga zuwa gaida ita dakin na mama
Ummi ce ta fara zuwa cikin mu taron ta gidan yawa da gulma nan aka saka ido akan ta.
Ta gaida gwago bata tsaya ba ta dawo dakin ta ta umurceni da naje na gaida ita din , na saka wani tsohun hijjabi a jiki na fita.
Daga kofa na tsaya nake cewa gwago sannu da zuwa ta juyo da sauri tana cewa karaso mana ciki Safiya.
A hankali na taka na shiga dakin na tsugun na kasa take cewa dani a a baki san yau zamu zo bane banga kiyi kwalliyan taron mijin naki ba.
Na dukar da kai na kasa take cewa dani tare muke suna nan kofar gida kin san shi ba mai son shiga mutane bane.
Haka yake tun yana karami da gudun mutane amma yi saa ya yarda ya biyo mu ne.
Sai mama tace ai shi hali shi tun na kurciya yana nan mashi ke nan baya son hayaniyan nan dai kamar yadda na san shi ashe ?
Ina suke ban dago ba take cewa dani maza ki shirya ki samay su a kofar gida.
Na tashi simi simi na fita daga dakin na koma dakin mu na zauna ban fadawa ummi abin da tace dani ba.
Sun dade da mama daki sun kashe murya sai zuwa can mama ke cewa safiyan tana can waje ne har yanzu.
Yar wurin mama ta amshe da cewa bata fita ba tana nan gida sai mama din ta taso tazo har dakin mu da kan ta tana min fada.
Hijjab din ummi na salla na zura a jikina na fita idanuwan yan gidan mu caaa a kaina
Na samay su su biyu a waje na karasa wurin su da sallama a bakina ko wanin su ya kunna taba yana zuka.
Jin sallama na da sukayi dayan yai saurin kashe taban hannun shi shiko dayan ko a jikin shi bai masan na zo ba.
Sun saka kida na tashi kamar gidan dj mutum ya shiga da kyat na bude bakina saboda warin taban da yacika wurin ina jin kamar zan yi amai.
Na kara gaidasu cikin murya a sanyayye sai gudan ya amsa min dayan wanda nake ganin shine dan gwagon mu yana dai zaune.
Sai can gudan yace dani a, a ko ke ce Safiyan a hakalin na bashi amsa da eh da sauri ya dago kai ya kalle ni, na sake cewa kunzo lafiya.
Mai maganan ya bani ansa da lafiya kalau mun samay ku lafiya ya karatu nace Alhamdullahi sai nai shiru.
Jefi jefi can yace barin dan taka wurin mai shagon can na sayo abu nasan yayi haka ne don ya dan bamu wuri.
Tafiyan shi ke da wuya shiru ya biyo baya har na wani lokaci sai naji yace barka da fitowa.
Nace barka mu da wuni.
Yace ya kike lafiya na bashi amsa.
Na jingina jikina da motar su don na gaji da tsayuwa yace da fatan anyi maki bayani a gida.
Sai na girgiza kaina nace ba wanda yai min baya ni an dai ce nazo na gaishe ku.
Ya ce Ok in kin koma za suyi maki yace ina dai fatan kin san abu ga makaranta don naga kamar har yanzu da saura.
Ko da yake wannan matsalar gwagon ki ne nace dashi namu dai.
Yadda na fadi maganan sai ya fahinci ko ban gane dukkan abin da yake fadi ba.
Yace ina baki fahinci magana ba cewa nayi iyayyen mu sun yi cewa zasu hada a tsakanin mu sai dai ni a tsarin rayina nafison macen da ta mallaki hankalin ta .
Macen data waye tasan duniya ya nunani yace dube ki ina ganin duk baki fi shekar sha hudu ba in ma kin kai.
Na yi wani gajeren murmushi nace to yaya na iya da zabin a kaina babu komai sai dai nima in son samu na samu yaro sauriyi mai shekaru kalilan wanda zai rike ni tsakani da Allah.
Amma tunda iyayye suka sani babu komai Allah ya tabbatar da alheri a tsakani.
Yaji haushin amsan da na bashi yace ba laifi nima hakan zan daure nai maneji dake kafin kan ki ya waye.
Nace abin na da sauki tunda kaima da wayewar iyayye kake kuri tunda sun sani nasan da sannu zai waye din kaga ba maganar na waye ko ban waye ba dole ne nayi biyyaya ga magabata na.
Tun da sune masu iko dani banice ke da ikon kaina ba zanyi biyyaya a gare su.
Ya sake jin haushin magana na amma a fili yacewa yayi ashe ra, ayin mu yazo daya kenan kan biyyaya ga magaba tan mu sai ki shirya zaman ukuba a tare dani.
Nace insha Allahu in yin hakan shine farin cikin mahaifi na a shirye nake da na rugumi duk wani ukuba da zan sama a gidan ka.
Sai ki shirya ke nan yarinya don ba zan yi renon banza a rayuwa na nace dashi Allah ya shige muna gaba.
Nace idan ka gama zan koma ciki hanya a bude take maki zaki iya tafiya sai dai kina da daman fadawa iyayyen naki irin ra,ayin .
Na dan yi jim na wani lokaci sannan nace dashi idan son samu ne kaine babba kai ya kamata ka tun kare su da zancen.
Saboda kai zasu fi daukan zancen ka da muhinmanci ya ce yin hakan ba zai yuyu a gare ni ba amma ba matsala.
Ya fara dube dube a cikin motan nidai duk warin taba ya ishe ne a wurin gani nake kamar a kamfanin taba na shiga.
Sai naji yace dani ga wannan kya kara kisai littafi da biro, sai na girgiza kaina ba tare da nakarba ba nace ka barsu na gode ina da wadatar littafi da biron.
Ya langabar da kai tare da karya harshe acikin turanci yace you will regret later sai kuma a harshen hausa yace ai ba cewa nayi kina da matsalar su ba,
Nace to na gode ban karba ba na fara tafiya yace to shike nan, na soma takawa a hankali shi kuma ya bini da kallon tsana.
Bayan na ahiga gida dakin mu na nufa yayin da masu gulma an zuba ido a ga abin da zan shigo dashi.
Tun shigana gida san bani da natsuwa ziciya ta kwata kwata bata natsu da wanan hadin ba ko banza bai a cikin tsarin mazan da nake so.
Wayewan shi yayi yawa bai laifi yana da tsarin maza amma dai tsarin dan maciji don farine dogo ga iya gaye komai nasa karfafa ne amma ziciyan sa da jikin shi babu tarbiya a ciki.
Sai dai ban da zabi akan haka don bani da ikon bijirewa maganan mahaifina don haka naci alwashin tursasa zuciya na da hakkuri koda kuwa yin hakan zai rasa farin cikina.
Sai da gwago ta gama abin da takeyi ta fita zuwa waje zuwa can ta dawo ciki da wasu ledaji a hannun ta.
Ta nacewa ga wannan na sarakkuwa nane kayan mun gani muna sone muka zo dashi zan dawo idan yaya ya dawo gida mu gana kafin mu tafi.
Har suka tafi ban sake ganin shi ba nadai ji labari cewa sun tafi an tsaida bukin mu da zaran na gama karatuna wanda yazo saura wata uku mu kanmala.
Ba waya ke gare ni ba balle ya dinga kirana haka yasa ban ji daga gare shi shima baiji a wurina.
Na dan kwatar da hankalina don na fuskaci jerabawan dake tafe min na final exam da zamuyi duk da ban sa rai ga cewa zan samu ci gaban karatun nawa.
Kulliyomin ba wani kwaciyan hankali a tare dani gashi duk biyayya da nake keyi ba gani akeyi ba don saida yakai an hada gwago fada da baba na da ummi wanda nasan bakowa yai wanan hadin ba sai mutanen gidan mu.
Har yakai ummi na ta kasa hakkuri tai tafiyan ta gidan su sai suka koma fadin cewa don tagacewa buki na ya taso ne ba ta aje komai ba yasa ta tafi gidan su wai.
Wanan tafiyan na ummi shi ya rage muna walwala sosai dani da kan ne na a gidan ko yaushe ina daki ina barzan kuka.
Yan kane na sukan damay ni da tambayan yaushe ummi zata dawo idan nace ta tafi gidan su kila ba zata dawo ba sai su fashe da kuka.
Na rasa mai ke mun dadi gashi nima dake dan kula dasu ana ahirin yi min aure a lokacin duk da ba wani alaman shirin aure da akeyi a gidan namu .
Don ban gani a kasa ba kamar yadda idan za ai buki ake ta faman shirye shiryen buki agidan namu.
Ban san may mama tagani ba ta sako dama sherin na wurin inna don ita ce tace wai ummi na na fadin sai da gwago tasan cewa dan ta bai da tarbiya zata ce a hada shi da diyar ta.
Ta fadi maganan wurin yan uwan su mama da suka kawo kaya gidan mu su kuma suka kwasa suka je suka fadawa gwago maganan .
Nan gwago ta shiga fada tana zagin ummi wai damay diyan ummi sukafi diyan ta don ma za a rufa mata asiri a auri yar ta.
Ta aikowa baba magana akan cewa ya ja wa ummi kune ga baganan da take sake mata shi kuma baba bai tsaya binke ba yai cikin ummi da masifa har yana cewa tana bakin ciki da hurdan da yake yi da yan uwan shi.
Shine akan wawiyar yar ta take son hada shi da yan uwan shi ta bata isa ba wallahi idan bata iya ganin auren haya a bude yake mata ta tafi gidan su.
Ita kuma ummi ta kasa hakkuri ta mayar mashi da ansa cewa ba tai bakin ciki da su ba sai yan zu inma tayi bakin cikin ai dole ne don ba aiwa yar ta adalci ba ai ga yannan ta agidan abadasu mana.
Rikici yai rikici don itama ummi ba raga masu ba wannan karon ta rufi idon tamayar masu da mai zafi.
A karshe sika kwasa da baba har yakai tabar gidan cikin dare duk magiyan da nake mata bata tsaya ba.
Mama ta sulce jiki ta samu wani wan baba ta fada mashi halin da ake ciki ta kuma ce a gaskiya ita bata taba jin ummi tai wannan maganan ba.
Baba musa ya samu babana sai cewa baba yayi dashi ta tafi mana idan hakan yafi mata alheri.
Baba musa yace dashi matsala gidan ka baka bincike baka kuma son a fada maka gaskiya kun samu boyar Allah kuna cuta mata ita da diya ta cikin gida.
An tabbatar min da cewa bata fadi wanan maganan ba yau kake da Rabi a gidan nan ya kamata kasan abida zata iya aikatawa da wanda bata iyawa.
Nan dai suka rabu da shi babu dadi ranan da yamma da baba ya dawo gida yana ta fada da baba musa.
Mama tace dashi ai bai fadi karya ba gaskiya ya fada wa ya taba ji a gidan nan lokacin da Raba ta fadi hakan.
Sai inna ta caraf tace kina nufin ke nan karya ne sheri akai mata ai idan bata fada anji ba alama ya nuna hakan.
Yace kin ga idan ke zaki je ki dawo da ita ban hanaki ba ai bani na kore ta ba sherin ta ne yakore ta balle ku matsa min.
Yaya sani na gida zaune yana cin abinci yace baba a gaskiya maganan gaskiya kuna cin amanan boyar Allah nan ga mama ta fadi gaskiya tace bata ce ba ai shike nan .
Ke inna in kina rage sheri ki rage don ke ma diya mata ke gare ki gasu nan har guda biyar maki.
Tace to ubana baki zakai muna ko may yace ni gaskiya nake fada maki tace bako haka ba.
Ya mike yabar abincin da yake ci yace to tabar maku gidan sai kuyi yadda zakuyi da diyan nata.
Ya shura takalman shi ya bar gidan.
Sai fada ya koma tsakanin inna da mama tonon asiri ya tashi baba yana zaune yana jin komai.
Dole gidan ya koma babu armashi kowa na cikin damuwaidan ka cire inna da diyan ta suke an shuwa a gidan kawai.

********* ********* *********
Kwana uku shiru babu wani motsi a gidan kwakwara mama ta kara samun baba a kan zan cen.
Ta nuna mashi damuwar ta tana cewa malam ka dubi Allah kaje kadawo da matar ka ta dubi yaran ta yara sun koma kamar marayu a gidan.
Yace ina son zuwa sai dai ban san da wani ido zan kalli Rabi da shi ba don don iyayyen ta sun mani mutunci amma ni na kasa rike masu ya.
Gobe zan sami malam lawal ya rakani muje ko zata dawo in kuma ahi zai tafi wala ba a sa.
Mama cikin nuna damuwa sosai ta ce dashi da haka yafi don ace anyi buki yar ta bata gida gara dai ayi hakkuri.
Washe gari ana gama sallah asuba baba ya samu malam lawal da maganan yai mashi bayanin komai bai boye mashi ba.
Malam lawal yace a gaskiya baka kyauta ba da baka bincike a gidan ka ai yaron ka gaskiya ya fada a tare ake hade kai dakai ana cuta wa Rabi.
Sannan fa ka sani yanzu ba aiwa yaro dole samu da wayawan kai da aka samu ita yar uwar naka ta nuna dan ta tasani.
Gashi an fara samun haka tun ba a yi auren ba idan anyi akazo aka samu matsala wa aka cuta yar ka da uwarta.
Daga karshe dai baba ya nuna su tafi su kadai don shi yana jin nauyi da kunya zuwa ya tun kari iyayyen ta.
Sun isa garin da sanyin safiya sai dai basu samu mahaifin nata ba a gida amma yayan ta da kannen ta suna gida.
Bayan sun gaisa malam lawal yace dama mun biyo sawun Rabi ne don Allah ayi hakkuri ta koma tsakanin harshe da hakori ma ana samun matsala bare mutum da mutum balle zaman aure da ya gaji hakan.
Yayan nata yace haka ne amma naso ace shi malam Audu yazo da kan shi don ko mu a kauye mun daina wa yaran mu auren dole.
Bayan haka duk hakkurin da Rabi ke yi ita da yar ta baya gani sai da ya kora muna ita gida dom ya nuna muna ya gaji dasu.
To idan shi ya gaji dasu da ai har diyan nata ya koro muna mu bamu gazawa da su.
Malam lawal ya jijiga kai yace ai dai yi hakkuri a madadi na abokin sa ina bada hakkuri koma may nene ya hada su tsakanin miji da mata ne.
Hakan ba zai sake faruwa ba tunda idan mukayi laakari ai hakan bai taba faruwa tsakanin su ba tun suna zamanin kurciya yanzu da aka tara iyali.
Yayan ummi yace eh saboda hakkurin irin nata ba shine zaa ce bai taba faruwa ba amma ia duk halin da take ciki muna da labari.
Yanzu ko da anin ya isheta ai da kan ta ta ne may mu dama ranan muke jira don duk abin da yasa kaga Rabi ta bar diyan ta to abin yaya kamari.
Malam lawal bai gaji da bada hakkuri ba har mahaifin ummi din ya dawo gida ya samay su.
Nan su malam lawal aka shiga gaisuwa dashi nan dai malam lawal ya gabatar da bukatan su na bikon ummi din.
Tsohon yai shiru can yace a gaskiya Rabi bata taba yaji ba nasan halin Rabi da hakkuri abu daya zaisa na yarda na mayar da ita dakin ta shine.
Bukin yar ta da yataso amma idan ba haka ba Rabi bata komawa gida nan ya isa haka na.
Ya dubi dan shi daya yace shi ga ka kira min Rabi, kanin ummi ya shiga kiran ta ta shirya tafito don amsa kiran mahaifin nata.
Sai fitowanta ne ta ga su malam lawal ta durkusa a gaban mahaifin nata cikin ladabi tsoho ya dube ta yace.
Rabi ga abokin mijin ki sun zo bikon auren ki don haka maza ki shirya ki bisu.
Take idanuwan ummi ya ciko da hawaye zata yi magana tsohon ya daga mata hannun tare da cewa.
Haba Rabi ban sanki da mussu ba, ita rayuwa hakkuri akeyi da komai ki yi hakkuri ki koma daki mijinki ko domin yayan ki .
Tabude baki zatai magana tace baba amma, , , , ,
Ya koma katseta cikin tsawa yace kin san ni sarai bani son mussu aiko ?
Tashi ki je ki shiryo ku tafi.
Badon ummi ta soba haka ta shiga ta shirya tana shiri tana kuka ta fito da lulubin ta suka nufi tasha da su baba lawal.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:10 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON , , , , ,


🧕🏿6️⃣🧕🏿


INDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , ,


Lokacin da suka dawa bata zo gida ba wurin gwago ta nufa malam lawal ya je ya dauko baba yazo dashi gidan gwago.
Gwago da malam lawal suka su gaba da nasiha akan a zauna lafiya arike hakkin iyalin abawa kowa hakkin ta yadda ya dace.
Baba yace insha Allahu komai ya wuce zaa gyara da yarddan Allah zai kulla da hakkin iyalin shi
Da daddare su gwago suka rakota gida ta dawo dakin ta tare da kara mata nasiha a zauna lafiya ta kyale kowa da halin sa.
Lokacin da suka shigo gidan mutanen gidan suna waje zaune mu kuma muna daga cikin dakin mu sai naji murya kamar na yar uwar mama na sallama.
Hakan yasa ni mikewa in leka aikuwa nahango tafe da ummi na buga tsale ina cewa lah ga ummi mu ta dawo.
Mukayo kanta da murna suka shiga dakin komai yana nan tsab yadda ta barshi dakin ba laifi suka samu wuri suka zauna.
Zauna na durkusa ina gaida su kaunan ummi ke cewa dani wanan wata irin amaryane ba kwalliya ko kadan.
Na turo baki gaba take cewa ai ko bakya son mijin a dan yi maki gyaran irin na amare ko ?
Wannan wani gyara zata samu babu kwaciyan hankali ahaka suke ahirin kai ta gashiko ance mijin nata dan duniya ne inji kaunan ummi gudan.
Aiko ba komai a dan gyara ta in ba haka suke so su kwashe ta sukai ba akara samun abin fada masu nan gaba.
Take cewa dani washe gari ki same ni gidana da safe da dan abin da zan maki koda yake ma an makara duk da haka dai hakan za a yi.
Sun dan zauna nan nake basu labarin irin yadda mama tai ta matsa mashi akan ya dawo da ummi dakin ta da kuma yadda tai ta dan taimaka muna da ummi bata gidan.
Nan da zasu fita suke gaida mama din suna fadin ga Rabi nan ta dawo Allah kauda tautsayi tsakani.
Mama tace ba komai zama tare ke kawo wani abin amma in an ciza aka hura sai ya wuce.
Har suna shirin fita daga gidan sai inna tace muda ba a gayar wa sai ace mu mutu.
Baku duk mutuwa ai amma dai baku so ganin hakan ba anso ace bata dawo ba sai gashi ta dawo din bakin cikin haka zai kashe mutum.
Inna tace bakin ciki ya kashe wa matar da baa bi bayan ta ba ta wanke kafa ta dawo don kwakwa irin naku.
Tace wa ke nan zaune gida kamar kayan wanki tun yaushe mijin naki ke bin sawo har kauye.
Abun da yaba inna haushi ke nan tace ke kinyi kadan ki shigo kice zaki zage ni har dakina.
Mama lami tayi zaton dukan ta inna zatayi kafin inna ta karasa daga hannu taji an kwashe ta da mari tajuyo a cikin mamaki taji an sake sauke mata wani marin .
Aiko danbe ya kicimay masu take gida ya rude sai ga inna a kasa mama tabita ta haye da duka da yakusa.
Ganin inna bata diban komai a jikin mama lami yasa hausi yar inna dauko faskaren icce ta nufi mama dashi sauran ma suka dauko tadai samu mama dashi sau daya zata kara buga mata ne mama ta kauce iccen hau kan jikin inna.
Sai ga jini tarrrr yana zuba daga goshin inna din yaran suka kara fasa kururuwa mutane suka fara shigowa har da su yaya sani da abokan shi.
Yaya sani har ya dauko icce zai shiga dukan su dashi sai yaji mama na fadin yanzo kin ga abin da kika jawa kan ki in da suka shigo basu tan ka ki ba kin kyale sune sun tafi da baa kai ga haka ba.
Amma kin bisu da zagi da gori yanzu gashi har kin jawo yar ki tai maki rotse akai.
Sai jikin shi yayyai sanyi ya yarda iccen da ya dauka kasa yana cewa ashe inna ke kika ja wa kan ki gashi yanzu an barki da jinyan jiki.
Baba ya shigo gidan ya samu gidan a har gitse da kyat ya samu mama ta mayar mai da abin da ya faru yake cewa shi ba ruwan shi ta dauki mataki da kan ta in zata iya don shi bai sata ba.
Nan inna tashiga balle ballen bagana ida take shiga banan take fita ba wai baba an je an hada shi da boka da malam kan shi ya zare.
Baba ya shigo dakin mu don ya gaida ummi zamu fita yace mu zauna yake cewa ummi kin dawo lafiya ya mutanen gida.
Ta amsa shi da kyat da suna lafiya.
Yace don Allah Rabi kiyi hakkuri da halin inna kin saba da halin ta kiyi hakkuri a zauna lafiya.
Bata tankashi ba ta kawar da kai daga duban sa ma sam bata son ganin shi.
Shima yace da mu da ita sai da safen ku.
Allah yakai mu ta bashi amsa dashi.
Yana fita na sauke ajiyan zuciya nace ummi kiyi hakkiri tun da ya gane laifin sa abin ya wuce.
Ya gane ko yana shirin ganewa ai da sauran sa duk wanda yace ya karkata wuri daya a gidan sa ai kullun yana tare da tashin hankali.
Don dai yanzu in suyi min ba kyale su zanyi ba sai dai duk adauke mu masu fitinan don kyaluwa bai yi.
Abin da na lura dashi da baba da mama ke aiwatar da shirin bukin su sai ko gwagon ummi da suke dan jefawa ciki wani lakaci.
Mun kara jerabawan mu na karshe kowa na farin ciki da hakan a ban gare na bakin ciki ne tar ga zuciya na .
Sai dai ba wanda zan fadawa naji sanyi sallama muke da junan mu na samu Amina bakin get tana jira na mu tafi.
A kasa muke tafiya don bamu son mu rabu Amina ke cewa mun yi barka da saka uniform yanzu muna da freedom din kan mu ba mai takurawa rayuwan mu.
Take naji wani iri a raina tace ni dai nursing school nake son zuwa idanuwana suka ciko da hawayen bakin ciki lokaci guda don a da tare muke wanan burin kowa ya fadi abin da rayuwan shi ke so.
Nin nayi shiru tana ta magana take cewa dani bakiji bane Safiya, cikin raunaniyar murya nake ce mata ina jin ki ni nasan wana daman ya wuce ni ke nan a rayuwa na.
Tace saboda may zakice hakan wanda zaki aura din ba dan birni bane zai iya barin ki kici gaba da karatun ki bayan kuyi aure.
Na hade wasu yawun bakin ciki nace da ita kayya Amina wanan auren da za ai min takar bauta zan tafi yi wanda yafi wanda nake yi a gidan mu.
Da sauri tace saboda may kika ce haka nan nake koro mata da yadda mukayi ranan da suka zo da mahaifiyar shi.
Na kara dace Amina ke kin taba ganin anyi aure mijin bai ma san da zaman matar da za a aura mashi ba.
Na kara sa cikin kuka da fadin zan yi biyayya ga mahaifina shi dake gurin yaganni cikin irin wannan rayuwa.
Zan zauna na rugumi kaddaran da ubangiji ya aiko min dashi amma ni nasan babu komai cikin yin hakan da suke son yi sai hada zumunci fada.
Tace matsalan Safiya shi baba yaki gane gaskiyan magana wa yan nan matan na zugashi in gaskiya ne ai suna da diya mata suba dasu ma ai sun fi kusa da gwago din.
Nace da ita ai fakewa sukayi da cewa wai ni nayi karatun boko suko saura basu yi ba don haka ni ce na dace dashi.
Tun ban da wayyo nake jin irin wayyewar su da kuma irin tarbiyan su ba daya ba da namu amma mama cewa tayi wai zaman birni ne kawai.
Har muka kai gidan su Amina maganan muke muna tafiya ganin yadda na bata fuska da kuka yasa ta cewa dani na shiga gidan su na wanke fuskana.
Mahaifiyar ta na tsakar gida taga shigowan mu take cewa damu yaudai kunyi barka sai kuma a fada wani.
Ganin yanayi na yasa ta katse maganan nata ta biyomu cikin dakin ta da muka shiga.
Ta samay ni zaune Amina a gefe na ina kuka wiwi tace may zan gani wai haka yau duk kukan karasa makaranta ne haka ?
Amina ne ta iya bata amsa da cewa mama matsalar auren ta ne take wa kuka.
Sai mahaifiyar ta tace yanzu yaushe raban naji an tursasawa yarinya auren dole can.
Irin wanan ma mijin ai ba zaiga darajan su ba bare kuma ke.
Cikin kuka nake sanar mata da yadda mukayi dashi din duk abin da ya fada min da suka zo.
Taja gwaron numfashi tace shi baban naki ne bamai saukin kai ba, bai san yanzu an bar irin wanan auren hadin ba ne.
Ai lokaci ya shude na irin haka sai dai kiyi hakkuri Allah yana sane dake yi addua idan akwai alheri ya tabbatar muna.
Nace Mama wallahi shima mutumin bai ko san suna yi ba don kwatakwata yace ni ba tsarin shi bane yadda na lura shima umurnin mahaifiyar shi yake bi don nagane so yake ni na fitar da rashin amincewa ga iyayyen mu a fili san nan gashi miti biyu yai yawa bai kuna taba ya zukaba.
Kaini ban ma taba ganin mai sha irisa ba wata kilama ba iya taba yake shaba.
Don ranan da na fara ganin sa tare fa suke da iyayyen shi amma babu kunya yanata zukar tabanshi in na tunashi a raina duk hankalina sai ya tashi.
Nayi hakkuri na jure wai don na farantawa baba rai amma na gaza sakewa a raina.
Ba wani soyayya tsakani na dashi saima munanan halayyanshi da yake nunawa a fili.
Nakara fadi cikin wani irin kuka saboda Allah mama ta ya ya zan samu natsuwa har nai farin ciki ga auren da na san bubu komai cikin sa sai tarin kaskanci.
Mama ta girgiza kai cikin damuwa tace kidaiyi hakkuri don bamu da wata zabbi sai abin da Allah yayi.
Ta dan tsagai ta tana mai matukar tausaya mani tace gaki yarinua mai hankali ace za a hada ki aure da mara tarbiya mara mutunci.
Da sun bar sulaiman ya ci gaba da neman ki aiko su da sun dara amma a kai bakin ciki da kasancewan ku tare.
Yanzu ina mutunci ga irin hakan da ake shirin yi nace mama don ma baki shiga gidan mu kin gani bane ummina fa bata dade da dawowa gidan ba duk akan maganan.
Maman Amina tai salati ta sanar da ubangij tace badai ta dawo gidan ba ko ?
A hankali na share hawayen dake fuskana nace tadawo amma dai har yanzu cikin fitina suke din inna ba barin halinta zatayi ba.
Tace kin ga Safiya ki tsayar da hankalin ki debi kwanaki uku zuwa bakwai duk abin da ya sauwaka daga biyu zuwa uku dare.
Kirinka nafila ko wani raka,a ko wani raka,a ki karanta kulhuwallahu kafa goma sha biyu a bayan fatiha.
Idan ki idar ki zauna ki yi yabo gun mahallicin mu sai ki hada da istigfar duk abin da ya sauwaka kar ya gaza kafa dari, sai ki kara karata kulhuwallahu kafa goma sha biyu ko wani da bisimillah shi safiya muddin kika rike wanan zaki ga abin mamaki idan har ba a fasa auren ba to mukkadarine daga Allah Allah ba zai barki ki tabe haka na ba.
Cike da gansuwa da maganan ta nace nagode mama insha Allahu zandage dayi yau din nan zan fara basai gobe ba.
Amina ta tashi ta debo min ruwa a buta na wanke fuska na dashi bayan na wanke maman ta tayi tayi in ci abinci naki sai da zuciyana ya samu natsuwa.

********* ********* *********
Bike ya rage saura sati biyu duk nabi na ramay kulliyomin bani da kwaciya hankali tare dani yan gida mu sai shirin buki suke yi.
Ranan ina zaune sai ga yaya Nura da wayan shi har dakin mu wai ana magana dani a waya na karaba ina mamakin waye zai kirani da wayan shi.
Na karba da sallama na amma sai naji muryan wanda naki jini a wayan yana cewa ke yar kauye watau kina nan ga bakan ki ko.
Nagane shime a layin duk da gabana ya fadi amma a fili sai nace muna dai a bakan mu ko don kaina mayen da ka dafe min kana son shiga cikin rayuwana.
Yace ke manya na san bakomi kikewa ba sai son ace kina lagos kina aure ko ?
Nace wanan ba shine matsalan ba don ba nice farko shiga lagos daga kauye ba kafin ni wasu sun rigani.
Yace a harzuke suwa kenan kike nufi oho mahaifana kike son ki zaga ko may ?
A yadda ka dauki maganan nawa hakan nan amsa yake don bani ce farkon shiga birni ba.
Avikin tsawa yace ke dakata kiji kiyiwa bakin ki waigi ki san wanda kike magana dashi, ke har wata mace ce da zan tsaya ina bata lokacina a gare ki.
Yan mata wani iri ne ban gani ba ke har kinada abu yiwa maza feleke ne yaja tsuki yace a fusace.
To ki sani ba irin Ahmed akewa irin feleken nan ba don ni baki cikin tsarina kin sani bakuma zaki taba samu ba.
Daga kawai ana son rufa iyayyen ki asiri a taimake su da har ina macen take nan.
Nace a rifa wa iyayyena asiri taimake so ko a rufawa naka kai da ka tsufe masu awaje kar akai ga abin kunya duk barinki ya kare babu maija.
Ya kut nasan ran shi yakai kololowar baci ne da magana yace zan gwada maki yanzu nake a cikin bariki kuwa.
Kinga ni dama kiran ki nayi gwagon ki ta damay ni in akwai event din zakuyi na sani.
Nace akan wanu aure zayi event badai wanan auren kaddaran ba naka zan tsaya bata lokacina akan sa.
What ever you take it duk daya gare ni sai dai in ke baki so nasan wa yan nan mastiyatan yan uwan ki na su.
Nace dadin abin dai ba a taba canza ma tuwo suna sai dai a kira shi da tuwon abu kaza.
Au aikin banza bade za a iya saka mai suna ba ya kashe wayan shi yana jan tsuki.
Wasu zafafan hawaye ne suka zubo a idona nace wannan wani irin tarbiya ya samu ko kadan muddin ba zai ragawa iyayye na bazan raga mashi ba.
Duk da kalaman da yake fada min suna da zafi kalamai ne na cin zarafin iyayye don haka na kara tsanar shi a raina.
Haka ummi ta shigo ta samay ni a cikin damuwa yanayina kadai ummi ta duba tasan raina a matukar bace yake cikin sallon hikima irin manya ta tuhumi abin dake faruwa.
Tace dani kina nan kina bata ranki ga abin da kika san ba zai hannu ba sai nace da ita ummi wannan mutumin ne baida mutunci .
Ko yaushe sai so ya zageni da iyayye na har da aibatani bai dauke shi a bakin komai ba don shi bai san darajan iyayyen shi ba.
Ummi ta jijiga kai sannan tace, abinda nake so dake yi hakkuri yi kuma tawassali da Allah in sha Allahu aniyar sa tabi shi baji a gare ki sai dai a gurin sa.
Abin da nake so dake shine kibi umurnin mahaifin ki koma maynene tsakanin shi da yar uwan shi ne bai shafe ki ba ke dai ki zage ki neme aljannan ki a gurin mijin ki zai fita masu ai in dai halin sa ne.
Kibar biye mashi ranku na baci ko banza ba saan yiki bane shi don ya girmay ki balle kuma ga aure zai shiga tsakanin ku.
Wanan magana na ummi su suka sanyaya min zuciyana take naji komai ya kawu min a rai na samu karfin gwiwan rake mashi abinda na kulla yi duk da manufar sa akaina na kuntata min.

Kamar yadda su gwago sukace basu son akaini da tarkace duk da haka an yi min kokarin wasu abubuwa wanda sam mutanen gidan mu basu zaci hakan ba.
Don ko yan uwan ummi sun hada kudi cas suka kawo mata tare da sauran tarkace na amfani gida.
Yayan da abokan arziki na cikin gari suma suka kawo nasu gudun mawan take kaya ya hadu ayadda baa zata ba.
Inna da ke cewa suga yaidda za ai buki uwa bata aje komai ba ta manta abin daga Allah yake don Allah shikewa bawan sa budi yadda yawo.
Yan uwan ummi sun yake shawara a tafi da kudin asai mun abin daya kamata a can idan an tafi kayan lafen dasu gwago suka kawo sai da inna tasa aka bude shi ita da diyan ta duk suka wawashe abin da suke so ciki.
Ina zaune a dakin mu don cikin gidan baimin dadin fita ina ummi sai shige da fice sukeyi na hada hada buki ni dai abin mamaki yake bani a raina.
Muryan yaya Sani naji a tsakar gidan namu yana kwala min kira na fito da sauri ina amsa kiran nashi.
Ya na kallona ganan sa ya fadi ya tsorata ainun da irin rama da ya gani tare da ni.
Ya ke Safiya lafiya irin wanan zabgewa da kikayi haka, keda ya kamata murna zakiyi aure ki huta da halin gidan nan .
Take idanuwa na suka ya kawo kwalla na dan sake mashi murmushin yake nace gani yaya.
Sai naga jikin shi yai sanyi da leda a hannun shi nasan abu yake son in dafa mashi a lokacin.
Sai ya juya dashi yana fadin barshi dai har ya taka yace dani Safiya zo nan sai nabi bayan shi muka fita.
Jikin bango na rabe a lokacin ne kuma kwalla ke zubo min a idanuwana babu kakautawa.
Na sa gefen hijjabi na ina shrewa sai naji ya sauke ajiyan zuciya dan kalle ni tausayina ya kara kama shi.
Ganin dagani sai shi a wurin kuma shi kadai ne mutum a gidan mu bayan ummi na dazan fadawa damuwa na.
Nace yaya Sani ina cikin wani hali wanda ba mai iya fitar da ni sai Allah dakuma baba.
Yace na sani Safiya karatu kike so amma baba yanuna karfin haihuwa a kan ki zai maki auren hadi na katse shi da cewa auren dole dai yaya.
Don wanda zaa bani ba ao na yakeyi baba kuma darajan iyayyen mu yake gani ba.
Ya zaro idanun shi waje alaman mamaki fa abin da na fadi din yace wa ne shi don uban shi.
Na girgiza kaina nace ko kadan baida mutunci yaya gashi kuma mashayin ne sosaiyace dani kuma baba ya san da haka din nace ban sani ba yaya.
Ki kwantar da hankalin ki zan yi bincike akai inna gane gaskiya kika fada min zan yi duk abin da zanyi in ga an fasa auren nan .
Maganan yaya sani shi kwantar min da zuciya har na dan ji sanyi a raina sai ya miko min leda da imdomei a ciki yace jeki ki dafa kici kafin in dawo.
Naji dadi a raina na ahiga nayi yadda yace na dafa indomei na shiga dakin mu muka ci da kan ne na.
Yaya sani kuma tafiya ya bincika inda yajiyo halin Ahmed babu dadi ko kadan a wurin yan uwa dake zuwa.
Yaya sani yace wanan abin duk sherin su inna ne ba komai ba nai mamaki ga su hausi yannen ta ne amma ce wai za ai mata aure ita.
Nan ya dawo gida ya ta yar da haukan shi ya kira yan uwan baba mu suka hadu ya fada masu halin da ake ciki.
Suka taru da dare akan baban mu suna fadin wanan baiyuyuwa ba ai muna auren dole ba bamuyiwa diyan mu.
Baba yai wuf yace babu mai hana wanan auren sai Allah yadda lanto ta nemi arziki a gidana haka nima zan mata shi da cewan wai gwago.
Sabada haka yadda nayi niyya haka zan yi saidai idan na kaita ta fito matsalar ta ne wannan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:10 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,


🧕🏿 8️⃣ 🧕🏿


YAR UWA IDAN AKWAI MASU NEMAN ACCOUNT NOBA DONA TA WURIN KI GA NOBA NA NAN SHINE 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO NOBAN WAYANA DON ALLAH KU TAIMAKA MIN.
AKWAI MASU KARBAN KUDI SUCE ZASU TURO MIN AMMA BASU BANI SAI SU RIKE A HANNUN SU IDAN NA TURA SU TURA WA MAI SHI NOVEL DON ALLAH KUJI TSORON ALLAH YAN UWA.
MASU CEWA BAN MAGANA YAUSHE ZAN TSAYA HIRA YAUSHE ZANYI TYPING SAI DAI INDAN ZAMU CIRE KWANA BIYU BA TYPING NE SAI HIRA SAI KUZABA MIN.
NAGODE NAGODE DA KASANCEWA KU TARE DANI KAUNA NE YA JAWO HAKAN SAI KUYI HAKKURI DANI YAN UWA


Ina zaune bayan na gama gyan gida tare da dan dafa abin da zanci tunda shi ba damuwa yayi da abincin dare ba sai dare sosai yake dawa kuma a buge.
Kofa naji a na murdawa sai na tashi na bude ban yi tsan manin shi bane a lokacin.
Shine tsaye bakin kofan ya kara daure rain shi naja baya tare da mashi sannu da zuwa tun da yau ya shigo cikin dan hankalin shi gidan.
Bai ko kalleni ba ya shige ciki da hanzarin shi nikan na koma na zauna inda nake da farko .
Sai zuwa can ya fito yana saye da gajeren wando da yar faran singlet ajikin shi ya samu kujera ya haye yana kokarin kuna taba.
A kawo ma abincine nagama nace dashi sai yai wani dagowa ya kalle ni a hankade yaci gaba da abin da yakeyi.
Na ja gafe daya na kama kaina na natsu ga kallon tv da nakeyi saboda yin hakan shine alheri a gare ni tunda naga yana jin tsiya yau din.
Haka muka zauna zugun zugun sai busar taban shi yake yi wanda warin ya cika falon ya hana ni sukuni gaba daya a wurin.
Nake zan shige ciki naji yana cewa ke kawo min abinci in ci zan fita , koda na kawo mai abincin ko cibi uku baiyi ba dan dama yaci dan doyan da na hada wurin girkin dashi.
Ya tsamay hannuwan shi ya ture plate din gefe daya kasa daurewa nayi nace cikin damuwa abincin bai maka bane in dafa ma wani.
Kamar dama jira yake tsutsayi yaja ni nai mai magana sai ko ya mike da sababi kamar wanda naiwa bakar magana yana cewa.
Ke kada ki kuskura ki nemi takura min da tambayan banza da wofi ke zaki sani cin abincin dole ne kokuwa da zaki damay ni da nacin tsiya.
Jikina yai sanyi na tsaya kawai ina kallon shi a cikin mamaki karo na biyu na sake tambayan shi cikin girmamawa may kuma nai maka daga tambaya kawai .
A fusace ya jefamin wani irin harara tare da cewa ke wai baki da hankaline ki barni mana kon zauna kina damuwa na kawai da bakin nacin ki.
Na dago idona cike da damuwa ina kallon shi daga abin arziki kawai sai hattara irin haka sai dai a fili fadi nayi Allah baka hakkuri na ga bakaci abincin bane.
Sai ya zubo min wani irin kallo na fushi yace a hasale ke don Allah ki wuce dakin ki, ki bani wuri kaganin ki ma kara tada min da hankali yake yi.
Zanyi magana yace waike wata irin yarinya ne mara hankali sai ya dakatar dani da hannun shi na dama cikin wani irin murya mai cike da tsawa yace nace ki wuce ki bani wuri in ba haka ba zan yi maganin ki yanzu nan.
Na juya zuwa ciki hawaye na zuba min na fada saman gado na ina bakin ciki da dana sanin wanan zaman kaddaran da na samu kaina a cikin sa zama da mashayi mara tarbiya.
Zuwa can naji ya fita yabar gidan na sauke a jiyan zuciya a hankali na mike na fito do in yi sallah.
Bai shigo gidan ba sai wajajen karfe goma lokacin har na kwanta sai dai ban yi barci ba ko da alama yau baya a cikin maye do banji yana haukan nashi ba.
Ban fito ba shi ma bai nemay ni ba don haka sai da gari ya waye na fito a falo naga ledan daya shigo na kayan break fast da su sabulu da omo da maclean da sauran su.
Ban taba nadai kaqar na fara gyaran gidan ina tsaka da gyaran falon gidan ya fito da jallabiya a jikin shi.
Tsaida abin da nakeyi nay na gaida shi da ina kwana yaya ?
Sai ya jefe ni da kallon nan da na tsana bai ce uffan ba ya dauke kan shi gefe guda.
Dukawa nayi naci gaba da aiki na sai da na gama naje na duba abinci na samu ya dahu na zuzuba a cikin plate nadawo na sama shi falon nace.
Ga abin karyawa nan na gama a saman table bani bukata ya bani amsa dashi a fusace .
Da mamaki nake kallon shi idona ya ciko da hawaye nadake nace don Allah yaya idan laifi nai maka laifine ka fada min abin da nayi sai in gyara don gaba.
Wai ke wata irin yarinyace idan gidan kike son na bar maki zan iya bar maki kin isheni nida gidana kin hana ni shakat wallahi.
Wanan ai takurawa rayuwa ne an daukoki kin zo kin zauna wa mutum a gida kin hanani shakat dani da gidana .
Da mamaki nake kallon shi nace nima bayin kaina bane zama a gidan ka umurnin iyayyene nake bi hakana.
Ya fadi a fusace da cewa very good dama zaman umurnin naki iyayyen kike bi , ni sai kiyi kokarin hadani da nawa yan uwan da iyayye ko ?.
Da sauri na kalle shi ina cewa ai iyayyen ka da yan uwanka duk nawa ne hannu ya daga min yana cewa ba yan uwanki bane kan, don da basu zo gidan nan kin yi masu wullakanci ba sun koma rai bace.
Na soma kallon shi baki bude ina fadi cikin mama ki da cewa ni har yaushe wani dan uwa na zai shigo na wullakan tashi ina nima su nake gani a matsayin nawa yan uwan a nan garin.
Kai ya girgiza min yana cewa ba gaskiya bane hakan don da basu gidan nan kin masu taron wullakanci ba.
Kin raina masu wayau ko bari su zauna bakiyi ba kike cewa wai bana gida kina kokarin rufe kofa su fita kullun suka shigo abinda kike masu ke nan.
Da sauri nake kallon shi cikin mamaki baki bude nace har yaushe suka shigo gidan nan in ba jiya ba kuma nan suke zaune suna tanbayan ka nace baka nan ruwan ma da na kawo masu basu sha ba nan suka tafi suka barni dashi basu ko sha ba.
Yace kenan dai sun zo din ko tabbacin cewa sun shigo kenan gidan kin masu wullakancin ko ?
Gabana yai mugun faduwa sosai ni?
Dama sherin da sukai min kenan to wallahi wallahi ban masu wullakanci ba a gidan nan yan uwana ne fa su dan may zanyi masu haka.
Wani harara ya watso min yace da yan uwanki ne aida baki wullakan ta su ba harkina fadin magana a kaina , nace ba haka bane ya daga min hannu yana fadin ya isa haka maganan ya isheni ji ki sani kuma ba zan dauki raini ga yan uwa na ba a gidan nan.
Ya juya ya shige dakin shi can ya fito ya dauki key din motar shi ya fice a hasale yabarni tsaye in da nike.
Kwana uku cur muka dauka bai damuwa da harkana a gidan haka muke zaune dashi ba dadi ta ko ina saukin abin yana barmin abinci inci wanda raina yake so.
Sai dai na fahinci akwai matsala a tsakanina da yan uwan shi ke nan amma na rasa gane ta ina wanan matsala ya ke tsakani da su.
Haka muke zama har na tsawon kwanaki ranan ko may ya gani oho sai naga ya fito yana bude kulan abincin da nayi da safe don yanzu yakai nabar gaidashi don ko na gaida shi baya karbawa tun ranan da na gaishe shi yace dani
Ke wata irin yariya ce wai mara zuciya gaisuwan na dole ne ko an baki ajiyana ne wai tun wanan ranan ban kara gigin gaida shi ba a gidan kowa harkan gaban shi yake yi.
Bayan ya gama ina saurare fita shi sai naji shiru alaman bai fita ba ke nan agidan.
Wuraren shadayan rana na fito a zotona yana dakin shi ne ashe yana falo kwance ban sani ba.
Gashi ba daman in koma yace dani munafuka sai na daure na wuce shi zuwa kitchen.
Dole hakana nake aiki duk na daburce na gama abin da nakeyi a kitchen nafito na nufi hanyan daki sai naji yace dani zo nan.
Gabana ya yanke ya fadi a sanyaye na iso gabanshi nace gani sai dai ban yarda na kalle shi ba shima din ta gefen ido yake kallona.
Yace dani ke baki iya gaisuwa bane ko may ?
Na nisa tare da cewa gaisuwan nawa ne naga baka so shiyasa tun da ba ajiyan ka aka bani ba.
Sai naga yayi tsam ya mike yayi amfani da hanayen shi biyu ya rike min hannu da karfin tsiya saida na sake kara.
Sai da yaga na jirkita don kan shi yadan sasauta rikon dayai min din yana kallon fuskana dake fitar da hawayen wahala.
Jinayi gaba daya jikina ya hau rawa don kusantan juna da mukayi a lokacin.
Hakanan gabana banda bugawa ba abin da yakeyi ba bata lokaci ya shiga kokarin manna bakin shi a nawa, nayi kokarin kwacewa shi kuma yai amfani da karfin shi ya hanani kwacewa .
Abin da ya kama daga bakina zuwa wuyana babu inda bai mana bakin shi ba da kiss ban yarda mun kalli juna ba sai ruwa hawaye dake zuba min nace cikin karfin hali don Allah yaya kayi hakkuri ka kyale ni.
Kamar hadiyeni zaiyi yace ina bakin naki mai fadar bakar magana ya shiga zan kyale ki amma ki sani duk kika kara min rashin kuya a gidan nan nasan maganin ki.
Don kawai ya kyale ni warin taba ya isheni tankar zan yi amai nake ji na amsa mashi da uhm mhm.
Ya sake ni da karfi har ina gauruwa da kushin da sauri na shige daki na na barshi wurin tsaye.
Jikina na rawa na fada daki ban daki na nufa naje kamar zanyi mai ina ta jakarjn amai bai fito ba na wanke bakina nafito duk jikina ya mutu..
Ban fito ba sai da naji yabar gidan na fito ina kallon wurin da yasha taba duk ga guntun taba a yashe a kasa.
Tsaki nayi na dauko perker na kwashe tare da gyara falon ina jan tsuki hawayen ta kaici na zuba min ko nace zan ja Allah ya isa gawa zan ja shi.
Ga mahaifina daya sani dole ko ga gwagona ta jawo min haka gashi har yau ban saka ta a idona ba.
Ban may su sadiya suka ce ainihin nai masu ba a gidan wanda har ya hasala ta da diyan ta gaba ki daya sun dauke kafan su da zuwa wurina.

********* ********* *********
Tun wanan rana na koma jin tsoron shi zan tashi da wuri inyi aiyunakana na shige ban fitowa sai ya fita zan fito falo in zauna.
Kaina ya isheni da kaikayi don haka naji ina son yin kitso na rasa yadda zanyi dashi gashi yana damu na.
Don haka ranan zai fita da safe na samay shi yana cin abinci na dan tsuguna nace da shi don Allah ina son in fita zuwa gyaran kai don kaina na bukatan gyara.
Baiyi magana saima nuna yayi kamar baijini ba na kara maimaita abinda na fada da farko ya dago ya kalle ni a lalace yace umurnina kike jira komay ?
Nace bakyau mace ta fita bada imurnin mijin ta ba yagama ya mike yana ce min kin san garin ne da zaki fita idan kin shirya na saukrle ki wani wuri a nan cikin unguwa.
Da sauri nace na shirya na shiga daki na sauko hijjabi na saka da man kitso nafito ya bini da kallon kamar zai yi magana sai kuma yaja tsuki kawai ya fita.
Na bishi baya ya juyo cikin tsawa yana fadim ni zan rufe maki gida ko may sai na juya da sauri na tafi rufe gidan kafin in zo har ya tayar da mota ko ina shiga ya fisgi motar da kar fin tsiya dan can kasan lalayin mu ya kaini ina sauka ya mika man kudin kitson na karba yaja motar shi ya tafi.
Ni na kai kaina wuein mai kitson nai komai nan na hadu da wata mata bahausa muna dan hira da ita harna sake jikina sai nake cewa idan zatai kitso wani karon tazo zan mata.
Ita kuma ta fara tallanta min kitson wurin matan hausan dake kusa sukai aman, na da zancen kitson nawa.,
Na dawo gida cikin walwala da dan sakin jiki koba komai yau na hadu da hausawa yan uwa na mun taba hira duk da dai ba a jaha daya muka fito dasu ba amma naji dadin hakan ayau.
Sai dare ya dawo banfito ba balle in gan shi sai da safe ko da na tashi na samu har da abinci yaci sosai.
Na hada breakfast na aje mashi komai da zai bukata na wuce daki abina zaune nake na kunna kira, a ina bi a hankali.
Ya shigo dakin sai ganin shi nayi a kofan dakin daga shi sai gajeren wando babu ko riga ajikin hannun shi rike da taba yana busawa.
Shi kan shiyagane dan firgita danayi a wannan lokacin da gani shi sai kawai ya sai ya kyalkyale da dariya.
Ya lura da taban da nake kallo sai naga ya kalla ya dan girgiza kan shi saiya kashe taban gaba daya a dakin.
Kusa dani yazo ya zauna yana bare tomtom ya jefa a baki yana tsotso a hankali.
Kusa dani yazo ya zauna ya shiga neman hannu na sai nai tsam na mike tsaye na koma can kusa da window na tsaya na bashi baya sai tuna nake koma na barmai dakin ne sam ban san ya baro gado ba yazo inda nake.
Sai ji nayi ya zagaye man kuguna da hannayen shi biyu yana fadin yau zan cire wanan jin kai da kike min a gidan nan.
Take na zazzaro idanuwa na don tsoron abinda naji ya fada sai yace may kike nufi dama yana kokarin rungumoni na shiga kokarin kwatar kaina yace dama kiwon ki nake yi da nufin ki kina cinye min abinci ga bazane.
Ko kina nufin baki san abida aka kawo ki yi nan bane sai girki da shara ki kwanta kawai ko nufi kike baki san matsayina a wurin ki bane yanzu.
Rokon shi na shiga yi ina fadin kayi wa Allah ya Ahmed ka kyale ni don Allah, na samu na kwace kaina gare shi zan gudu naji ya kara fisgoni tare da zaro min ido wanda tuni sun juye sun koma wani launi.
Yace don't be stupid baki da hankaline kike jayayya dani koke mahaukaciyane kina nufin haka zan zauna dake ina kallon ki.
A sanyayye na sunne kaina idanuwa sai kwalla ke fita nace don Allah kayi hakkuri har na shirya sai ya watso min wani kallo na bai amin ce ba.
Ya kara juyani a hankali muna fuskanta juna kaina yana kallon kasa na ji ya kara dagoni tuni naji ya hada bakina da nashi irin na jiya.
Ya rinka aikawa da wasu iron dabaru na salo salon na saukan hankali masu kama da siddabaru da gusar da hankalin matum.
Tsaye nake kikau kamar dutse na rasa sanin dadin da yake ji har yake lumshe idanuwan shi har takai yana fitar da wani sautin nunfashi.
Jikina har lokacin rawa yake yi zuciya sai bugawa yake yi uku uku sai da ya gaji da jagula na dan kan shi ya janye daga gare ni yana kallona ido cikin ido ina share hawaye yace bakauyiya kawai ashe ma kodan kiss din nan baki iya ba.
Bakina yana rawa nace kaina kasa dan kuya nace ban iya iskaci ba don ni ba yar iska bace yace ok ashe bakin naki bai mutu ba ke nan .
Zan ko gwada maki kin hadu da dan iska yau don sau kinyi regreting din fadar baka ga abinda zai maishe ki mace.
Dago ido nayi na kalle shi tare da shiga firgicin kallaman da naji ya fito bakin shi sai dai babu komai a idon nashi sai tsaban fitina irin wanda katattare da lafiyyen tazurun gaye da ya dade baiji mace a tare dashi ba.
Kai tsaye ya shiga rabani da kayan jikina tare da yi min gargadin kar in kuskura in motsa sai faman rokon shi nake yi har da hawaye da majina .
Amma bai saya fasa abinda yake yi ba saida ya barni daga ni sai under wear kadai ya tsaya yana kallon na daga sama har kasa har yatsun kafana.
Ya tabbatar da duk abinda yake so da kwaydayi gun mace ya samu a jikina ashe kallon da yake min na yariya don ina cikin hijjab na ko yaushe.
Azahiri ba hakan abinyake ba don na zarta tunanen sa fiyye da yadda yake tsamani .
Take kirjin shi ya shiga bugawa da karfin gaske yayarda mahaifiyar shi tai mashi zabin daya dace dashi yau.
Lallai zai more a gun wanan yarinyan duk wani lafiyayyen nami ya gani dole ne ya kyasa can yace cikin tsawa me , , kukan may kikeyi haka ?
Naji muryan shi ya juye kamar batashi ba don maganan ya juye kamar wanda ya damu da ni .
Da kyat na daure na bude bakina mace don Allah yaya kayi hakkuri kada ka taba ni.
Ya nisa yace in nai hakkuri may zaki bani da zakice nayi hakkuri kafin in yi magana sai ji nayi ya ratsa hannayen shi a saman kirjina yana barazanan soma murza su hakan ya sani firgici.
Na soma wash innallilahi kayi hakkuri don Allah yaya idaniwan shi a lumshe yake fadin tsaya kin san bana wasa dake ko?
Na gaya maki ki daina jayayya dani ko, in ba hakaba wallahi yau sai na sumar da ke gidan nan fuska a murtuke yake magana.
Hawaye masu zafi suka yi min kwale a fuskana na nasan yau nawa ya samay ni mai kwatana a wurin shi sai Allah.
Ban fasa zubar da hawayen da nakeyi ba naji ya kamo ni ya manna a jikin shi yana wani nishi yana fadin ki saki jikin ki karki tsorata dani zan yi ne kawai na bar ki.
Duk wandan nab sabatun da yakeyi yana yin sune hade da lasan kumcina da fatanjikina da jin maganan shi kasan ba a cikin hayacin shi yake ba.
Ranan kan ban san ida nake ba azaba yasa na kasa motsawa sai kuka da nakeyi wiwi harda karkadawa shiko ya kasa saurara min ya kasa yi min komai a hankali haka kuma yaki saurara min tsawon lokaci tun ina kuka da hawaye har suka kafe suka daina fitowa.
Ganun da yayi na zama kamar somamiya don tsaban wahala sannan ya saurara min ya matse ni cikin gamsuwa yana fidda sambatu kamar mara hankali yana fadin thank you mum, i love you pretty, I love you so much hold me now hald me, please.
Da kyat na samu ya mike ya barmin dakin ya barni kwance cikin galabai ta da wahala babu mai tai maka min.
Sai da na dan samu natsuwa na rarafa zuwa ban dakin dake dakin na wa na dade zaune ina kuka ina kiran suna mahaifiya ta har na gaji na daina hawaye suka kafe min da kyat na samu nai wanka na fito ko mai ban shafa ba nakai kwance.
Barcin wahala ne ya dauke ni har ya shirya ya fice gidan ban sani ba sai wurin karfe uku na rana na falka koshi yun wa ne ya tayar dani.
Da kyat na taka naje falon cikin sanda don ban sani ba ko yana falo lakacin don tsoron shi nakeji tsoron mu hadu dashi yanzu nake ji a raina.
Nayi arziki baya nan har na gama abinda zanci na shige daki dakyat nai sallah na koma na kwanta zazzabi ya rufe ni.
Ban falka ba sai dare natashi don inyi sallah har yanzzu jikin nawa ba karfi sosai kwana biyu haka nai ta fama a gidan ni kadai shi kuma bamu kara haduwa da shi ba.
Sanu a hankali na soma samun natsuwa a gidan sai ranan gashi ya dawo a cikin mayen shi duk da na rufe kofa haka yazo yana dukan kofan dole na bude mashi.
Baai tsaya jiran komai ba haka ya afkamin nan na shiga dukan shi da yakusa amma bai hana ahi cin ma bukatan shi ba.
Ya fita ya barni ina kuka ni daya a daki babu wanda zai lalashe ni kan haka na gaji nai shiru ina jan Allah ya isa.
Bamu hadu dashi ba sai wani safiya na fito ashe bai fita ba mukai kicibis dashi a falo da sauri cikin kaduwa naja baya yace ke may nene haka wai halan ni dodone da zaki kama guda na.
Bari kiji in ke manya ne baki cina don kawaii na taimaka maki zaki hauni da cizo da yakusa banza dake ma.
Jikina na rawa amma na dake nace dashi ko gobe kazo min a cikin maye haka zan yi ma tunda ni ina tsoron Allah .
Yace waye bai tsoron Allah nace kai mana sai ko ya biyoni a guje na kwasa nai daki nai sa a kafin ya iso na sakey.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:11 PM - Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,


🧕🏿🧕🏿7️⃣


YAR UWA KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA DON BAA YAFE BA ONLINE NOVEL NE NA KUDI,


Yaya Sani bai da karfin da zaitare baba ya hana ai bukin nan gida ya cika da yan buki yan uwan ummi suzo sun mata kara na rufin asiri yadda ya kamata don kowa bai tsanmaci hakan ba.
An daura aure bayan sallah azahar duk masu cewa basu san angon ba sun san shi ranan.
Kowa sai albarkacin bakin sa yake fadi walima akai mun na sauka shine zance event din da akayi kawai.
Nan gidan mu na kwana acewan su washe gari run da safe zamu kama hanya zuwa ida suke.
Hakan akayi washe gari muka kama hanya bisa rakiyan mama da mama lami su kadai zaa tafi da su sai so da suka zo wurin daurin aure daga can.
Sai dare muka shiga garin don haka bazan iya cewa ga yadda garin yake ba don da dare muka shiga.
Gidan gwagona muka fara tsayawa nai mamakon ganin gidan da suke zaune ciki ana cewa suna lagas sai mitum ya dauka a cikin wani daulan duniya suke da zama ashe abin ba haka yake ba.
Dan gidane tsohon gina suke zaune ciki mai dakuna hudu gidan duk ya gage saboda tsufa.
Ashe sana, a take sosai irin na arewa irin su kamu, hura kunu mai zafi da kosai da kayan amfamin na arewa da sauran tarkace da matan hausawa za su bukata.
Kazab tan gidan kawai ya ishi mutum ya raina masu mama lami tace cikin rada lagas din kega in kaji ance mutum na kudu sai ka dauka wani dadin duniya yake can ciki.
Washe gari aka kaimu gidan da zamu zauna shi wanan gidan ba laifi don gida ne dan matsakaici dashi da daki biyu da falo ya dan sha kayan zamani an zuba ya kara haska wurin .
Muka kebe ni da mama lami tana bani shawara da cewa kin safiya ga komai a gidan mun sama don haka yan may zakiyi da su.
Nace mama ki koma dasu kawai ba abin da zan yi da sunan ni.
Tace a, a ba haka za a yi ba zan raba biyu in baki rabi ki boye in kin san gari sai ki samu dan sana a kinayi kin dai ga sarakuwa taki ita ma ba zaune take ba nema take yi.
Don yanzu bida na kai yafi komai dadi ina kin iya kitso da sannu sai ki fara dan yi sai kuma dan abin da kika ga yana karbuwa anan din.
Mama lami bata boye ma su mama yadda mukayi ba sai mama ta bada shawaran cewa ai dabaran ba ma gwogo na wani abu ace in samu sanaa na rike.
Chapter 1 · 0% Book details