← Book details Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 2 OF 14

PART 2

Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel · about 170 min read

_PAGE 3
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
_MY FIRST NOVEL _
"wakenan?" ya tambayi Mummy yana kallonta
"eh da ita yarinyar daka dawo dan ita mana, tunda tana maka abunda bana maka, wallahi kaji tsoron Allah, ba irin Magiyar da banyi maka ba, Amma kayi biris amma yanzu dayake tafini ai gashi kadawo"
Tsyawa yayi ya zubawa Mummy ido tagama, Yayi tsaki ya tashi ya fice yana masifa.
Haka yakoma dakinsa yana mita yana tunanin meyasa ma yaje inda take.
Jalila tanata lissafi gobe su Abba zasu dawo, dan haka ta tsananta Addu'a Allah yabata sa'a yasa Abba ya janye batun Aurawa Jawwad Naja.
Yauma Jalila taje school, sun kammala lectures, sunfi to itada Zahra, Zahra tace
"Yawwa nikam Jalila naji Wata suna hira tace wai jiya wani hadadden gaye yazo yasaki a mota ya tafi dake, amma wai dagani dan shaye2 ne dan wuyansa hada sarka, ga wani irin Aski akansa, ina fatan lafiya ba wata matsalar bace?"
Dan karamin tsaki Jalila tayi aranta tace"
dan jaraba da masifar mutane komai kayi idonsu akanka
"Eh haka akayi, seme kuma?"
"A'a ba komai dama nayi tunanin ko mutanen baban Saleema ne"
"basu bane, Yayana ne" Jalila tabata amsa a takaice, Dan zare Ido Zahra tayi
"dama kinada yaya dayake shaye2, na zata Yaya Jawwad ne kawai Yayanki"
"Akwai wani to, kuma akansa nayiwa Alhaji Kabiru baban Saleema, abunda yanzu yana daf da zuwa prison shida 'yan tawagarsa"
"Amma Jali....
" Ke zahra kin isheni wallahi, nagaji ga yunwa ina ji se faman tambayoyi kikemin, sekace wata likita, haba se Allah ya kaimu gobe"
Inda sabo Zahra tasaba da halin Jalila, tanada saukin kai Amma tanada tsari a komai nata, in bakasan halinta ba zakace batada kirki ne kawai, bata da san yawan tambaya.
Mummy ta bawa Ilham kudi tace ta kaiwa Nana ta ajiyewa Maama in ta dawo a bata, Ilham ta karba harta shiga gidansu Nana wani tunani ya fado mata a rai, dan haka tayi murmushin mugunta tashi. Tana fitowa hakan yayi dai2 da dawowar Jalila daga makaranta sukayi karo a kofar gida. Ilham ta tsare Jalila da ido tana mata kallon zaki gamu dani ne.
Jalila tace "Ilham wai kin manta maganar danayi mikine? Ki dawomin da Al'qur'anina tun muna sheda juna dake"
Ilham ta rike kugu ta kalli Jalila "idan naki fa? Me zakiyi?"
"Aimeyi baya fada se dai kigani a aikace, zakiga matakin dazan dauka, ki kawomin abina na gayamiki"
"ina jiran ganin matakin dazaki dauka din, amma kafin ki dauka ni ki saurari nawa"
"banida lokacin saurarar duk wani shirmenki, ba abunda kika isa kiyi min, nagama magana Ilham"
Jalila tasa kaii ta shige gida.
Kwana hudu kenan basu kara haduwa da Jalal ba, haka nan yaji yana kewarta sosai. Koba komai yayi missing neman maganar ta.
Sannan tunda abun nan yafaru tsakanin sa da Mummy be kuma shiga cikin gidan ba. Mikewa yayi yafito zetafi gidansu Jawwad.
Yana kokarin fitowa daga part dinsa Ya hango Ilham a jikin mota tanata boye kudi a jikinta, yana ganin haka yasan bata da gaskiya amma bebi takanta ba ya fice.
Jalila tana zuwa ta dire Jakarta ta shiga tayi wanka, ta fito tayi sallar Azahar ta kwanta bacci, se la'asar ta tashi, tayi sallar la'asar sannan taji tana jin yunwa.
Jalila tana zaune akan dadduma kafin tabar kan daddumar ta, Ahmad ya kirata suka dinga hira har kusan 40 minutes, Nana kallon ta kawai takeyi seda tabari tagama sannan tace
"Jalila wai dan Allah ina kika samo wannan Ahmad din, iya sanina ba kya son duguwar waya amma kalli yadda kika zage kina waya"
Jalila tayi murmushi sanna tace
"Nana a Bauchi na samo shi, yanada kirki sosai"
"kinga niba wannan ba magana nakeso muyi masu mahimmanci"
"inajinki amma ki hanzarta inajin yunwa"
"bawani in hanazarta, ki zauna kigama wayar se yanzu zakiji yunwa?
Jalila dan Allah ki gayamin hakikanin meke tsakanin ki da Yaya Jalal?"
Jin maganar tayi wani banbarakwai, batayi zaton jin wannan tambayar ba
"kamar yaya? Kinga wani abune da baki yadda dashi ba? Meyasa kikamin wannan tambayar"
"Jalila ruwa baya tsami banza yadda Ilham ke takura tsanarki tabbas wani abun tagani, tana claiming kuna soyayya ne, nima da nayi wani nazari zancenta yana kusada gaskiya"
"Mtseww niban san yakuke so inyi ba, da muna fada da shi, ance banida kunya inamasa rashin kunya, yanzu na dena ance ina sonsa to ya zanyi, Nana niba son Jalal nakeba, ina tausayinsa ne musamman danaji labarin waye shi, Nana a baya nikaina nasan na bata masa rai dayawa, yadda nake masa rashin mutunci da bakaken maganganu, naga ban kyauta ba sannam ba'a gyara da barna, muddin kanaso ka temaki mutum ya dena aikata laifi indai zakayi masa hayaniya baze dena ba, zaka kara tinzira shine, na fuskance shi yanada mataukar saukin kai, na gane hakanne a zuwan dasu Hanan suka danyi, Hanan gashi sa'ata ce, tafini tsiwa amma yana sakarmata fuska har yayi mata wasa, ita bata masa rashin mutunci kamar ni, shiyasa nima na sassauta yi masa wulakanci,
Amma babu soyayya tsakanin mu, ina fatan kin gane"
Mikewa tsaye Nana tayi tana shirin fita ta waigo tace
"Naji amma ban yadda ba" Nana ta fice daga dakin, tunani Jalila ta dingayi kozata gano wani dalili ne yasa ake kallon soyayya ce tsakanin ta da Jalal amma bata ganiba share wannan tunanin tayi ta mike ta fito itama domin neman abunda zataci dan ba karamin yunwa takeji ba.
Koda ta duba kitchen ba'ayi girki ba bakomai tayi tsaki ta fito daga kitchen din.
Daki takoma ta hado goldenmorn dinta ta fito farfajiyar gidan domin shan iska, tasamu kujera ta zauna tana cin Abincinta, Abba takira a waya yakara tabattar mata da gobe Insha Allah ze dawo, ji take kaman ta Jawo gobe Abba yadawo dan ta kagu ta dau mataki akan Naja.
Tanata wannan tunanin aka kira wayarta, A zatonta Ahmad ne amma se taga bakuwar lamba dagawa tayi tasaka a kunnenta tareda yin Sallama
Caraf taji matar ta Ambaci sunan ta "Jalila yakike ya gida?"
"lafiya kalau Alhamdilillah"
"Antyn Jalal ce, nasan baki gane me maganar ba"
Murmushi Jalila tayi tace
"yi hakuri Anty ban dau muryarki
bane, ya gida ya kukaje gida ranar"
"lafiya kalau nasan baki dauki muryata bane, Jawwad nakira nace ya turomin lambarki mudinga gaisawa, ya mutan gidan naku?"
"lafiya kalau Anty, yasu Mahmud?"
"Ahha Mahmud Nana zaki tambaya shi, muntafi da kwana uku yakoma U.K"
"Allah sarki, aikam kullum suna tareda Nana a waya"
"Aikam naga shi can nasa hankalin ya karkata, se fatan Allah ya tabattar da alkhairi"
"Hakane Ameen ya Allah"
"Jalila ya Amanata dana bar miki?"
Dan murmushi Jalila tayi tace
"Yana nan Anty"
"Kundena fadan dai ko?"
Murmushi Jalila takumayi tace "Anty kenan"
"Au kunya na baki? Jalila bamuda kalaman dazamuyi Amfani dasu gurin gode miki akan namijin kokarin da kikeyi keda Jawwad akan Dan uwanmu mungode Allah yasaka maki da Alkhairi"
"Haba Anty meye wani abun godiya kuma? Ni banga wani abu da nakeyi ba"
"inke baki ganiba mu mungani ai, ko iya yanzu kin taka rawa gurin canza abubuwa dayawa a tareda shi, munyi waya dashi yacemin daze bar kasar nan kika hanashi"
"hmm sa'a kawai nayi, nazata ma ze min duka, Allah yakara shirya shi, nima nagani ya rage Abubuwa sosai"
"Ameen Jalila, haba baze iya dukanki ba ai, he respect you fiye da yadda kike tunani, ki kulamin da amanata Jalila, inaji a jikina abubuwan da Jalal yake zezama tarihi sanadinki"
"Allah yasa, Munagodiya Jalila, Allah ya jikan magabatanki"
Jalila ita bataga me tayi ake mata wannan godiyar ba, Jalal din da banda fada ba abunda ke hadasu, dan haka Tace
"Anty yaushe zanzo abani turaren maiduguri ne? "
"Kibari in Aurenki yazo har kano zanzo in hadaki, kamshi sekin gaji, Allah ya nunamin Aurenki"
Dariya Jalila tayi ta kashe wayar, Antynsa tanada saukin kai, gata da abun dariya, Amma ita bataga me tayiba daza'ayita yimata wannan godiyar ba.
Washegari da safe Jalila bata tafi makaranta da wuri ba, seda tagama gyara gidan dan kusan kwana biyu Naja bata gidan, Halima dama Maama ta dade da sallamarta, Manu direba be dawo daga kai Nana ba, tunda ita Nana da wuri ta tafi school yau,
Taita gyaran gida, da kokarin dora girki saboda dawowar su Abba, be kamata abar gidan bakowa ba gashi ba'ayi girki ba.
ta fito ta leka part din Jawwad, taga inya tashi ta kaimasa Abinci, Amma ta hango Jalal yana shan sigari, Jawwad kuma baya palourn, da niyyarta ta fadawa Jalal bakar magana amma tafasa ta shiga palourn. Batayi sallama ba unexpected ya daga kai ya ga Jalila, hade rai tayi sosai taki kulashi shima be kulata ba, ta duba ta kalleshi tace "Ina Yaya Jawwad?"
"ki duba mana" yabata amsa a takaice
"Ina zan duba?" ta tambayeshi a ransa yace "lallai yarinyar nan kyaleta yayi bekuma kulata ba yanata shan sigarinsa, tambayarsa takuma yi
" wai yana ina? "
"Zoki duba rigata kona sashi a ciki"
Bude baki tayi tana kallon sa, Jalal dan rainin hankali ne, amma ta shareshi ta dakko wayarta takira Jawwad be dauka ba, tsaki ta danyi taje tayi knocking kofar bedroom din Jawwad amma ta tarar yana bacci. Mayarwa tayi ta rufe ta juyo zata fita, Amma Jalal bashida niyyar dena shan taba, gashi yana kallon boom TV ne music ne kawai yake tashi, yana shan sigarinsa yana lumshe ido, ya jingina a jikin kujera. Dan girgiza kai tayi tazo gabansa ta tsaya ta dauki remote ta mayar saudi qur'an, bude ido yayi ya kalleta sannan yace "Meye haka?"
"Abunda ka gani" ta bashi amsa
"mayarmin inda take da farko"
"Bazan mayar ba" dago Jan idonsa yayi yana kallon ta, wani tunani tayi a ranta, ta fuskanci fitsarar da rake masa baya sashi dena abunda yakeyi, dan haka tace
"Ka karyane? Da safiyar nan kake shan sigari, kamanta me likita yace maka ne? Kobaka son lafiyar kane?"
Shiru yayi ya dauke kai, ba karamin haushi takeji tana masa magana ya mata banza ba amma ta dake tace
"Am talking to you, kamanta you said you want change, and i promise to help you out, please badanni ba a kashe sigarin nan please, na zata dena mu'amalarka da wannan jakin Jejen zesa ka canza kadena shaye2, amma meyasa har yanzu baka dena ba?"
Juyowa yayi yana kallonta, tayi kalar magiya, a hankali yace
"ba lokaci daya nafara shaye2 ba, don't expect me to stop it at once, Jeje ya dade yana cutar dani, na dade ina shaye2 bazan iya dena wa lokaci daya ba"
Tausayinsa ne yakamata, dan haka tace "I understand, kadena sha dayawa, a hankali zakaga ka dena" gyada mata kai kawai yayi, ta dan kalleshi maganar zahra ta tuna, "wani handsome guy"
Ba karya Jalal yanada kyau, inama ba ya wannan shaye2, da seyafi haka kyau, Amma tana fatan Allah yasa abunda ta shirya akansa yayi tasiri ya dena shaye2.
"inaso kamin wata Alfarma"
"fade ta Allah yasa zan iya"
"zama ka iya, ba me wuya bace ba"
"inajinki"
"Dan Allah kadena saka sarkan nan, you are Muslim, bekamata ace kana yawo da itaba, da dinma nasan saboda Jeje ne kaima ka kwaikwaya please ka cireta"
Kallonta yakeyi amma bece komai ba, can kuma ba tareda ya cire sarkar ba yace
"meyasa idan aka kirani da dan shaye2 kike jin haushi bayan kema kina gayamin? Dan shaye2 mara tarbiyya wanda ya raina iyayensa, idan wani ya gayamin kinajin haushi, Amma kekina gayamin"
Gaba daya taji jikinta yayi sanyi, har bataso ta tuna irin bakaken maganganun datake masa abaya, musamman idan ta tuna labarin Rayuwarsa tabbas tayi wauta, amma tace
"Waye ya kiraka da dan shaye2 naji haushi?"
"mutane dayawa, bari in tuna miki daya, Oga KB mahaifin Faruk, ban taba tunanin yadda kika tsaneni a wannan lokacin ranki ze baci dan anci zarafina baa"
"har yanzu kanajin haushin abunda nayi maka abaya ko?
" ko kadan gaskiya kika fada ai, banida tarbiyya, ban cancanci zama
Abokin yayanki ba kaddararsa ce tareda tawa shi.......
"Enough dan Allah, wannan abune daya riga ya wuce please"
Kallonta ya kumayi sannan yasa hannu ya cire sarkar wuyansa yace "Insha Allah nayi alkawarin bazan kuma saka sarka a wuyana ba"
Murmushi tayi "Are you serious"
"dagaske nake miki"
"kai gaskiya na yadda you want change, Allah ya shirye ka da gaggawa" murmushi yayi yace
"Ameen ya Allah"
daga nan ta mike tayi waje a ranta tace
"da haka Insha Allah kafin inyi Aure seka dena shaye2 in Allah ya yarda"
Yau fasa zuwa school tayi ta zauna ta shirya Abinci saboda dawowar su Mummy, bayan tagama ta kaiwa Jawwad nasu, ta gyra ko ina a gidan se kamshi yakeyi.
Bayan tagama komai ta zauna tana tilawar Alqur'ani, wajen karfe daya Abba suka dawo gida, ta dinga murna tana musu barka da hanya, duk hassadar mutum yasan gidan nan ya sha gyara amma Abba ne kawai ya yaba, Maama nunawa tayi bataga ma me akayi ba.
Bayan sunyi salla ta kawo musu Abinci. Takoma dakin su.
se la'asar Nana ta dawo daga school nan ta dinga murna su Maama sun dawo, Jawwad seda magariba ya shigo cikin gidan yayiwa Su Abba barka da dawowa, wannan karon kamar kullum Abba yarabawa kowa tsaraba sunata murna, sun hadu a palour ana hira.
Abba yace "Jawwad ranar Asabar Insha Allah za'akai kudin Aurenka kamar yadda Maamanka ta bukata, inda wani shiri da kake ganin zakayi to kaje kayi, Jalal yagama komai next month Insha Allah zakafara zuwa gurin Aikinka"
Wani irin gumi ya dinga tsatstafowa Jawwad, yariga yagama karaya, sannan yana jin matukar kunya da nauyin ya bude baki yagayawa mahaifinsa baya son zabin da mahaifiyarsa tayi masa, Jalila ta kurawa Abba ido alamar bata gamsu da abunda yafada ba, Abba ya kalleta yace "ya dai 'yar Baba? Kokinada magana ne?"
Juyawa tayi ta kalli Maama data tsareta da ido, magana kam akwaita a bakinta amma ba' a gaban Maama ba, girgiza kai tayi alamar A'a, ta mike ta tafi dakinsu tanata safa da marwa, tana tunanin ta ina zata fara yiwa Abba bayani, tasan kotayi Maama karyata ta zatayi.
Gajiya tayi da sintirin datake taje ta bude wardrobe zata dau towel tayi wanka, ta bige wata jakar Naja ta fado kayan ciki suka zubo dayake bata zugeta ba, a sama inner wears dinta ta dora a kai, amma kwayoyi ne da kwalaban syrup a cikin jakara, binsu da ido Jalila ta dingayi yayinda tayi mutiwar tsaye.
Da sauri ta durkusa ta tattare mata su ta mayar mata da jakarta yadda ta ganta, nan tunani yakara yiwa Jalila yawa bazata taba bari a Aurawa namiji kamar Jawwad wannan tanbadadiyar ba,ko Nana bata gayawa abunda ta gani ba, tayi shiru da bakinta.
Wasa2 duk yadda Jalila taso ganin Abba personally Maama ta kankane, ta tattare a part dinsa bata matsawa ko nan da can, seda aka kai kudin Auren nan, naira dubu dari Abba yaje ya kaimusu, su Yaya mairo hada kira wayar Maama tana mita wai duk Arzikin da Allah yayi musu amma ace kudin Aure akawo dubu dari, mecec dubu dari a kudin da suke dashi, Maama taita lallabata tace tayi hakuri zasu hade a kayan lefe.
Yayinda gefe abun duniya ya damu Jawwad, begayawa Hanan halin dayake ciki ba, ko Abinci baya iyaci, duk ya rame. Jalila da kanta taje ta dinga bashi kwarin gwiwar yacigaba da Addu'a komai zeyi dai2.
shikansa Jalal abun ya dameshi, meyasa za'ayiwa namiji Auren dole, ko mace be kamata ayiwa ba balle Namiji, shima Jawwad saboda nusaranci da kunya baze iya cewa baya sonta ba, wani lokacin kawaicin Jawwad yana batawa Jalal rai.
Jalal yanata tunanin wani taimako ze iyayiwa Jawwad, dan shima baze bari ayi wannan Auren ba, tunda Jawwad baze iyaba zeje yasamu Abba da kansa yagaya masa Jawwad baya son yarinyar nan, yana wannan tunanin yaji message ya shigo wayarsa,
Koda ya karanta, tsayawa yayi yanata juya message din shidai yasan tabass wannan message bana sa bane saba lamba akayi, dan haka ya barshi a matsayin anyi missing number ne aka turo masa, dan hukumar dasuka turo message din da sun san wayeshi sun san laifin dayake aikatawa da basu turomasa abunda suka turoba.
Jalila ta yanke hukuncin yau zata samu Abba ko agaban waye, zata nuna masa illar abunda yake shirin yi
Kai tsaye part din Abba taje, ta shiga da sallama a bakinta, ya amsa sallama sannan yace "dama ina son ganinki, Baby ankaiwa yayanki kudi ze Auri 'yar uwassa, kune' yan mata kunfi sanin menene kuke so, kuma kuna tareda ita, maybe a kayan lefe akwai abunda takeso maybe ku tayi hirar daku, ba lallai tagayawa iyayen ta ba, dan haka inda wani abu da take bukata kokune tagayawa kota rubuto, saboda asan me za'a samata a kayan lefe"
"Abba wannan Auren fa bame yuwuwa bane?" mamakine ya kamashi yace "meyasa Jalila?"
"Baya sonta fa"
"Amma na kirashi na tambayeshi yace min ya yadda"
"Haba Abba zuwa yanzu yakamata kagane halin Yaya Jawwad, tunda kake ka taba nuna kana son Abu yace bayaso? Wallahi Abba Auren nan tamkar kasa hannune da kanka ka rusa doguwar tsaftataciyar katangar rayuwar Yaya Jawwad ne, Abba please kayi bincike"
"karya kikeyi bakar munafuka, ba wani bincike daza'ayi, yarinya 'yar dangice, me tarbiyya da sanin yakamata suna son junansu, Amma dan munafunci shine kike bata mata suna a gurin sirikinta, kedai Azzaluma ce, ni ina kudina ma da Mummy ta bayar akawomin? Ilham tace tabaki amma dan son zuciya baki baniba seda na buga waya aka gayamin ke aka bawa"
Daga Abba har Jalila tsayawa sukayi suna kallon Maama, Jalila takasa gane inda Maama ta dosa
*ABDUL JALAL*
_Story and writing_
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girls_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Abba ransa ya baci dajin kalaman da Maama ke fadi dan haka yace
"zainab meye haka kuma? Kibar ta ta fadi abunda yake bakinta mana, be kamata ki katse mata hanzari kidinga jifanta da wannan muna nan kalaman ba akanme? Na dade ina tunanin Jalila bata jin dadin zaman gidan nan, Allah ka dai yasan mekike mata inba na nan, nayi shiru ne dan bata taba gayamin wani abu akan irin zaman da take ba, kallonki kawai nakeyi zainab "
Se yanzu Maama ta shiga hayyacinta take tuna maganganun data fada idonta ya rufe ta manta shaf agaban Abba tayi su, cikin kokarin kare kai tace
" kayi hakuri Abban Jawwad, raina ne ya baci, iya sanina Naja batada wani aibu amma Jalila se kokarin kushe Auren take, kuma da ina cuzguna mata aida zata gaya maka tunda kasan bakinta baya shiru"
Jalila kallon Maama kawai take, Abba yayi tsaki yace "Inajinki Jalila cigaba da maganar ki"
Jalila tace
"A'a Abba base muncigaba ba, Amma Maama ni Ilham bata bani kudinki ba, tsawon zamana a gidan nan ban taba daukan cokali da sunan ha'inci ba, kina aikena gurare da dama da kudi, har banki kike turani da ATM card dinki ban taba batar miki da ko kwabo ba abaya, wallahi ni Ilham bata bani kudi ba"
Yadda Jalila take maganar kasan zuciyarta a cunkushe take da bacin rai, dan har idonta yatara Hawaye, Maama kuwa fakar idon Abba tayi ta watsawa Jalila wani kafirin Kallo.
Abba yace
"ke Zainab kikoma can kuyi maganar kudinku, ni 'yata bata sata, bata ha' inci na yadda da ita, Jalila tashi kije Allah yayi miki Albarka, karki sake ki zubar da hawayenki a banza"
Jalila jinjina masa kai kawai tayi ta mike, tana fitowa taji hawaye nabin fuskarta wani bayan wani, koda Jalila ta koma daki Nana tana bacci dan haka ta samu guri ta takure ta fashe da kuka, hada sheshsheka tana kuka tana surutai
"Ummi kingani ko? Da tun farko kin tafi dani da kome zefaru tare ze samemu amma kinmin Nisa, kin barni inata fama da wahalar Rayuwa, banida matemaki se Allah"
cikin bacci Nana taji kukan Jalila, koda ta bude idonta Jalila ce ke faman sharbar kuka, da sauri ta sakko daga kan gadon tazo gabanta tareda fadin
"Jalila lafiyarki kuwa? Gayamin me yasamiki?"
Shiru Jalila tayi se kuka data cigaba, duk yadda Nana tayi Jalila taki gayamata me yafaru, Nana ta rumgumeta tana fadin
"tunda bazaki gayamin ba bazan takuramiki ba, Amma dan Allah kidena kukan nan, Jalila banajin dadin ganin kina kuka haka dan Allah kidena in bahakaba nima zaki sani kukan"
Jinjina mata kai kawai Jalila tayi, ta zame ta kwanta akan cinyar Nana, ta juyarda kanta hawaye na cigaba da zuba.
Da Naja ta dawo gidan seda Maama tagaya mata abunda ta tarar da Jalila tana gayawa Abba, Naja ta dinga masifa taana zataga bayan Jalila, setasa ta bar gidan da kafarta, tunda ita mayyace, Maama ta gaya mata wai Jalila ta cinye mata kudi dubu tamanin Abba yace karta kuma daga maganar shi yasan Jalila bazatayi haka ba, suka kuma haduwa sukasa Jalila a gaba da gori, Maama ta hade kai da Naja suka cigaba daYiwa Jalila barin miyagun maganganu, Amma sam Nana bata san meyake wakana ba, zuwa makaranta ne kawai kesa Jalila samun raguwar pressure dake kanta, shima yanzu makarantar idan taje kuka takeyi bata jin lectures din. Jalila batayi mamakin abunda Ilham tayi mata ba dukda abun yamata ciwo, Amma a yanzu ita ba wannan ne ya dameta ba, maganar Auren nan ce yake damunta.
Wasa2 Jawwad yayi rama ta ban mamaki, yana cikin tashin hankali an saka biki a kusa watanni shida, ko Abinci baya iya ci, nutsuwarsa daya idan yana waya da Hanan, kokuma Idan Jalila tana masa nasiha da bashi kwarin gwiwa, ko Abinci baya iyaci, duk haskensa seda yayi duhu, Jalila tarasa ta ina zata fara shawo kan matsalolin nan.
Yanzuma gurin Jawwad ta tafi don ba karamin tausayi yake bata ba, taje ta kaimasa Abincin rana, ta tarar ya idar da salla ta jira Jawwad yayi Addu'oin sa ya shafa, sannan tace
"Yaya Jawwad nasan kana cikin damuwa, amma kadinga kokarin kwantar da hankalin ka, ina nan inata kokari sannan ina Addu'a Allah ze kawo mafita"
Murmushin yake
yayi wanda yafi kuka ciwo yace "ina Addu'a baby, ina fatan Allah yabani ikon cin Jarrabawa"
"Insha Allah komai ze wuce sannan nace ya batun zuwan ku kaduna kuwa? Bana son plan dina ya tafi a banza"
"Ina sane Jalila, zamuje Insha Allah, kafin lokaci ya kure"
"to shikenan, amma ka dena wannan damuwar kaji Yayana?"
"Na dena babyn Ummi"
Murmushi tayi masa
"yawwa haka nakeson ji, bari in dawo in gyara maka dakin nan, naga yayi kura"
"to shikenan Autar Ummi nagode sosai, Allah ya sanyawa Rayuwar ki Albarka, Yadda kike kokarin faranta min Allah yabaki mijin daze kula dake ya soki ya rikemin ke Amana, a lokuta da dama kina sadaukar da farincikinki dan ganin wasu sun samu nasu farincikin, Allah yabaki wanda ze kulada ke, yabaki mijin marainiya, wanda ze kula dake da maraicinki"
Taji dadin Addu'ar yayan nata, Amma takasa cewa Ameen sema Hawaye daya taho mata.
Tagama abunda take a cikin gida, taje domin gyara bangaren Jawwad, Jalal na kalmashe akan kujera yana game a system, sukaci Abinci shida Jawwad, yacigaba da game dinsa, tunda ta shigo ba wanda ya kula wani tsakanin ta da Jalal, Maama takira Jawwad a waya tace yaje cikin gida tana son ganinsa, jiki ba kwari ya tashi ya tafi, dan yasan be wuce akan maganar Naja ba.
Jalila tasan babu alamun Jalal yayi sallar Azahar, ta duba taga system din a jikin caji take yake amfani da ita, tasa hannu ta kashe main socket na dakin, system ta dauke dama babu caji, kallonta yayi
a fusace ze masifa amma yakasa, ganin irin kallom da take masa,
"Kayi sallar Azahar kuwa?"
"ban Sani ba, ko innayi ke zanyiwa?"
"Subhanallah karkayi sabo, ai ba fada bane, Salla fa, haske me girma ga tarin lada ga ma'abota yinta akan lokaci, kaga da kana bata mahimmanci sosai da yanzu Rayuwarka ta canza, da abubuwa dayawa kadaina aikata su, karfe uku ta wuce amma bakayi salla ba, wanda ya mutu baya salla kasan makomarsa wuta ce ta saqara, wadda ake sa wanda basa salla, Ai baka son shiga wuta ko dan gidan daddy? Ta tambayeshi kaman tana magana da yaro karami"
Be Amsa ba se kallon ta dayake, tasa hannu ta janye system din
"Yawwa abokin Yaya, kayi yaki da shedan, ka yaki zuciyarka ka daure, kaga in kayi sallah sekayi Addu'a, Allah na karbar addu'a bayan sallar farilla, kaje kayi salla"
Mikewa yayi ya nufi bedroom din Jawwad ba tareda yace mata kala ba yaje yayo Alwala, yana shiga tayi Ajiyar zuciya mutum kaman wani dan karamin yaro, komai se an lallabashi Allah ya shirye ka, yanzu tagama gane halinsa, ba yasan fada ne sam, indai zaka gaya masa magana da fada, to zakuiyi fada dashi. Jalila tanata goge2 ta kunna TV takai sunna tv ana karatun Al'qur'ani, tana aikinta tanayi, sosai takejin dadin karatun suratul Yusuf,
dauke wuta akayi dan haka tv ma ta dauke, ta danyi shiru, kawai taji an dora daga inda ta tsaya, waigawa tayi ta ga Jalal yana karasa mata ayar, ya iya karatun qur'ani, bata manta randa ya kaita makaranta ba ranar data fara jin yana karatu, Murmushi tayi tace
"cigaba mana"
"A'a kedai kicigaba, na manta Aya tagaba, bana tilawa, bana tuna haddata duk na manta, kwakwalwar ta toshe"
"Ahh waika manta, ba wani kamanta"
"Am serious na manta, cigaba maybe inkin cigaba in tuna"
Ba musu kuwa ta dora, tana cikinyi setaji yakama yanayi,
"Amma kace ka manta? Dama ka iya karanta Al'qur'ani haka, inama kana yawanyi da ko a hanya kaga giya zaka dauke kanka ne, waye ya koya maka karatu haka?"
"A islamiyya sannan kuma Ummi, bazan manta ba"
Maama ta cazawa Jawwad kai akan Naja, yana zuwa dakin ta shiga yi masa fada "Wallahi Jawwad ka kiyayeni tun ban bata maka rai ba, shine ka hada kai da wannan makirar yarinyar take kokarin ziga mahaifinka akan Auren nan ko? To wallahi ka kiyayeni akan Auren nan zan iya cimaka mutunci, kuma in har muna raye baka isa ka kuskurewa Auren nan ba, indai zanyiwa yayata biyayya kai waye da bazaka yimin ba? "
Sunkuyar da kai Jawwad yayi yace" kiyi hakuri Maama, niba ina kokarin kuskurewa Auren nan bane, kiyi hakuri dan Allah "
"ni rufemin baki, se anyi magana kadinga wani ayi hakuri, Naja tagayamin wulakancin dakake mata, ka fifita waccan yarinyar akanta shima ka kiyayeni Aure zakuyi da Naja, dole ka dinga janta a jiki ku fuskanci juna"
"to Maama yadda kikeso haka za'ayi insha Allah" duk abun nan Naja na gefe a zaune tana tauna chewing gum, tana hararsa, da Nana tana dakin Maama itama, amma bacin rai yasa tabar dakin.
Har Jawwad ya yunkura ze fita yabar dakin, Naja tayi karaf tace "Yaya Jawwad dan Allah zan shirya zaka kaini anguwa" shiru yayi bece komai ba, Maama tace "kobazaka kaita bane?"
"zan kaita bari inyi sallar la'asar"
Haka ya taho ransa babu dadi, yarasa me yake masa dadi, gaba daya Maama ta canza yaya mairo kullum cikin zigata take kansa har wani sarawa yake yi, ya nufi dakinsa amma yana zuwa dakinsa abunda ya tarar ya bashi mamaki, kunnuwansa suna jiye masa kira'ar Jalal, yana karanta qur'ani , wanda rabonda Jalal ya karanta Al'qur'ani baze iya tunawa ba, to mutumin dabe damu da salla ba, ina zeyi karanta alqur'ani.
Jalal yana cikin biyawa ya kakare, Jawwad yakarasa masa, tuni Jawwad ya manta da bacin ran dayake yi yace "Jalal yau kaike karatu haka? Amma naji dadi, yaushe rabo"
"kanwarka ke kokarin ta kureni, nace mata na manta tace senayi shine nake tunowa naji ashe da saura, haddar bata gama zubewa ba"
Jalila tace "niba kureka nake ba, aiba takura maka nayiba"
Jawwad yace "Baby kinga Jalal, wallahi ba karamin kwarone ba da muna yara, kwakwalwar sa tana kawo wuta, duk lesson din daza'ayi a kansa yake daukewa, gaskiya yau kinciri tuta baby, yanzu dai mu cigaba da tilawar nima ayi dani"
Murmushi Jalila tayi, Jalal yabata mamaki yau sosai, da Jalal yacigaba da karatu da al'umma zasu amfana yanada kwakwalwa sosai, Jalila tace "to kucigaba ni zanyi Alkalanci"
dariya Jalal yayi wadda take masa kyau dan be fiyeyiba yace "Jawwad kai zaka fara, nifa babu haddar ta zube, shekaru Ashirin baya da yin haddar kuma kaga bayi nake ba"
Jawwad yace "hakan ma ka yi kokari fa, amma dan cigaba zan na tuna maka, nayi missing din karatun ka" murmushi Jalal yayi, yafara kokarin dorawa, yana cikinyi ne kawai yafara tari, jikinsa yana rawa, Jawwad yace "lafiya meyafaru Jalal?"
Tari sosai Jalila ta dakko ruwa Jawwad ya karba yana kokarin bashi amma yasa hannu ya make ruwan, ya fadi kasa, nan take idonsa yafara juyewa jijiyoyin kansa dana fuskarsa suka mimmike, nan take fuskarsa tayi murtuk yakoma Jalal dinsa na ainihi dan shaye2 wannan murmushin da Annurin na fuskarsa ya dauke gaba daya, tashi yayi daga kan kujerar dayake yakoma kan doguwar kujera ya kwanta ya rufe idonsa.
Jalila tace
"Yaya Jawwad meyasameshi kuma?"
Ajiyar zuciya yayi yace "Jalila haka yakeyi wani lokacin, ko yana cikin nishadi inka fara masa nasiha gaba daya jikinsa ze hau rawa, ya canza Amma ze ware Insha Allah"
Jinjina kai tayi takarasa aikinta tana mamaki sannan ta fice.
Jawwad yayi mamakin yaushe suka shirya haka har take sashi abu yayi, Amma da ya tuna kokarin da Jalila ke tayi akan Jalal, da kuma Alkawarin data taba yi masa akan zata taya shi addu'a da kokarin ganin Jalal ya shiryu, murmushi yayi yace "lallai baby kinada sa'a mace ta farko daya ji maganar ta tun bayan lalacewarsa"
Jawwad sam ya manta da batun wata Naja, seda Maama ta kirashi a waya, haka ya tashi ransa ba dadi ya dakko key din motarsa ya fito.
Shigar data saba yice yauma tayi, jikin nan duk a matse se wani dan ficicin gyale, ya bude motar ya shiga, itama budewa tayi ta shiga gaba daya motar ta bule da kamshin turarenta dayake hawa ka, ya kunna motar yace "Ina zaki?"
"Shopping zaka kaini zan sayi kayan kwalliya"
Bekuma ce mata komaiba ya kunna motar yaja, ya kaita kofar wani store ya ajiyeta, ta kalleshi "to muje mana"
"Ba inda zani, in bazakiba inada abun yi" yafada a hasale
Tsaki tayi ta bude motar ta fita, tana fita ya kashingida ya kira Hanan, seda ta kusa katsewa ta daga cikin muryarta na shagwababbu tace "My Haidar am sorry bana kusada wayarne" murmushi yayi yace
"gaskiya ban hakura ba, seda ta kusa katsewa za'a daga wayar"
"ni gaskiya kayi hakuri ko inyi kuka"
"No don't cry, Ya kike?"
"Lafiya kalau sedai ina missing dinka"
"Insha Allah zan shigo Kaduna next week zanzo in ganki, na kusa tafiya lagos Daddy ya samo min Aiki a can"
"masha Allah can't wait to see you my dear, wallahi naji dadi Haidar, Allah ya kawomin kai lafiya, ina yayana kuma sirikina?"
"Wake nan?" ya tambayeta
"Yaya Jalal mana"
"Eh ina sa ran tare zamuzo dashi, Amma yaushe yazama sirikinki?"
"Yacemin yabani kai yazama sirikina, nikuma zan masa tukuici da Jalila dan ita zan bashi shine tukuicin dazan bashi" dariya Jawwad yayi yace
"ba ruwana kunfi kusa keda su"
Sosai ya manta da batun Naja, yaketa murmushi, Kuruciyar Hanan tana birge shi, yanzu duk wata kunya ya ajiyeta, She's so kind
Har Naja ta dawo motar wayarsa yakeyi da Hanan.
Naja ta fusata matuka a hargitse tace "wannan wane irin rashin mutunci ne? An samana rana Amma kana waya da wata wannan ai wulakanci ne kuma a gabana"
Karaf a kunnen Hanan, Jawwad kashe wayar yayi dan yasan yanzu kome zece Hanan bazata saurareshi ba yanzu, dan taanada matukar kishi, ya kalli Naja yace
"Ke zabin Maama ce" wannan kuma zabina ce, dan haka ki kylaeni"
"ni kake gayawa haka ko? Wallahi zakaga rashin mutunci, kuma ko bakaso seka Aureni, kacigaba da yimin wulakanci, nikuma zancigaba da hadaka da mahaifiyarka"
Bece mata komaiba ya kunna motar yatafi, shi gaba daya hankalinsa da tunanin sa yana kan yaze shawo kan Hanan.
Suna zuwa gida yafita ya barwa Naja motar, daya koma daki ya tarar Jalal ya tashi, yazo ya zauna kusada shi yace "Sannu ka tashi kenan?" Jalal ya jinjina masa kai
Jawwad yace "Jalal dan Allah sati me zuwa, inaso inje kaduna" murmushi Jalal yayi yace "Zakaje gurin Hanan kenan?"
"Eh amma tare zamuje da kai, zaka rakani"
"meyasa sena raka ka?"
"kaima naka zuwan yanada mahimmanci, dan Allah ka rakani"
"to naji, amma senayi shawara"
Jawwad yace "ba wata shawara da zakayi, Akwai damuwa ne?"
Jalal yace "damuwar menen?"
Nan yagayawa Jalal yadda sukayi da Naja, har Hanan taji, Jalal yace "tun farko bekamata ka boye mata halinda ake ciki ba, Amma yanzu ka kira kanwarka ka gayamata, tafara yimata bayani kafin kaje kaduna" Jawwad yace "Hakama za'ayi ka kawo shawara, kai Amma Inajin kunyar Jalila sosai"
"meye kuma Abun jin kunyar? Kirata ni zan gaya mata" ba musu ya kira Jalila a waya yace tazo farfajiya yana kiranta.
Befi 3 minutes ba sega Jalila tazo, Hannunta dauke da wani karamin teddy da kuma wayarta, bakinta kuma dauke da alawa me tsinke, Jalal kura mata ido yayi aransa yake zancen zuci in be manta ba, saura watanni shida Jalila tacika shekaru gome sha tara Amma har yanzu bata dena halin yarinta, kana kallon ffuskarta zaka san yarinyace, sedai Kwakwalwarta ba kowane babbane ze iya lissafin da kwakwalwarta takeba tasamesu akan fararen kujeru a harabar gidan, tayi mamakin ganin Jalal kaman bashine dazu ya canza gaba dayaba.
Taja kujera ta zauna tace "gani Allah yasa ba lefi nayi ba?"
Jalal yace "ke tunda kin saba lefi, duk lokacin da aka kiraki bakya kawo komai a ranki se laefi kikayi, kodayake ke ai aikata laifi a jininki yake"
Bakinta yayi jawur saboda Alawar datake sha, kallonsa tayi ta harareshi ta dan murguda baki tace "Eh tunda kullum 'yan sanda sesunzo sun tafi daniba, aidole kace laifi a jinina yake"
Yadda bakinta yayi jawur din nan tana juyashi ba karamin birge Jalal yayi ba, Jawwad yayi murmushi yace "Allah yabaku hakuri, dazu gwanin sha' awa naji dadin yadda naganku, Amma yanzu kuma zakuyi fada"
Jalila cikin shagwaba tace "toba shine yace ina laifi ba"
"to kice ba kyayi mana? Shekarun baya ina seda kikasa Abba zuwa kaduna kin tabo 'yar gidan masu bullet"
gaba daya sukayi dariya, saboda Jalal da sigar tsokana yayi maganar" gaba daya Jalila mamakin Jalal takeyi, ya iya barkwanci da tsokana, Amma inbaka zauna dashiba bazaka gane hakan ba, kuma abun mamaki lokaci daya seya birkice yakoma Jalal dinsa mashayin giya.
Jawwad yace "Baby wani taimako nakeson kiyimin"
Ta gyara zama takara rungume teddy tace "with due respect, ina jinka babban yaya"
Ya yunkura zeyi magana suka jiyo hayagagar Maama ta nufosu itada Naja,
"saboda ka cimin mutunci kake gayawa Naja wai baka sonta kanada wadda kakeso, Jawwad yaushe kakoma haka? Yaushe kafara bijirewa umarnina? Ya koyamaka ko? Zama da Jalal yasa kafara bijiremin, har kake waya da wannan shedaniyar yarinyar a gabanta, na samaka ido tsakanin ku kar mahaifinka yakawo wani abu aransa amma duk baka ganiba ko? "
Jawwad yace" Maama nifa bahaka mukayi da itaba, kuma ba ruwan Jalila bada ita nake waya ba, na gayamata ita zabinkice, nima inada zabina"
Tas Maama ta dauke shi da mari, gaba daya sukayi tsit dan ba karamin mamaki abun yabasu ba,
Shiru Jawwad yayi ya sunkuyar da kai ko tari beyiba, cigaba tayi da zazzga masa masifa Jalila tace
"haba Maama, biyayyar da Yaya Jawwad yake miki in baki gode masa ba bekamata ki zageshi ba, kuma da ze canza hali da ya dade da canzawa dan Allah karki kuma dukansa"
"rufemin baki kasurgumar munafuka kawai, bake kike zigashi ya bijirewa umarnina ba, jarababbiya wallahi zanyi maganinki, kuma baki isa ki hana Auren nan ba, jarababbiyar banza"
"Kuma makira barauniya ba, mara usuli gata barauniya abun kunya itace ke kokarin kusheni wai kar a Aureni, ai garani da dangina uwa da uba, kekuwa fa, dangin uba babu, na uwarma ba wanda yasansu, kodayake ina wani dangi daza'a nuna tunda Arnane" Naja ce take wannan maganar tana jujjuya ido da kebe baki kamar uwatta. Jalila tace
"Naja, nina godewa Allah da yadda ajiyeni, da naso rushe Aurenki lokaci daya zan bata komai wallahi, Maama Niba barauniya bace ba, Ilham bata bani kudinki ba, akira Ilham din gani gata tafada miki lokacin data bani, sannan ni bazan ziga Yaya Jawwad ya bijirewa Umarninki ba, Amma kijawa Naja kunne wallahi takuma zagina, sena ambaci uwatta na zageta, nagaji da abunda kukemin Maama menayi miki, kullum ba damar inyi motsi se anciwa uwata mutunci? "
A fusace Maama ta daga hannu zata mari Jalila, Jalal da tun dazu beyi magana ba yai sauri ya shiga tsakani ya rike Hannun Maama, ya girgiza kai yace
"A'a Maama, Jawwad ma dana san zaki mareshi bazan bari ba, gaskiya Jalila tafadi, uwa batafi uwaba, sannan in baki godewa Jawwad kiyiwa Allah godiya da samun da nagari ba, be kamata ki butulce ba, ya miki biyayya akan abunda bayaso amma baki ganiba, mahaifiyata misali ce a gareki, nikadai ta haifa amma nakasa yimata biyayya, karkiyi kuskuren da Mummy tayi a rayuwarta, kizo kina da nasani, dan Allah"
Ina yinku ABDUL JALAL group da sauran masoya wannan Novel irin sosai din nan fa
inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing, gashi nan na muku dogon page, in banga ruwan comments inna shura takalma na posting se rana ita yau
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
What's app only 07063065680.
*ABDUL JALAL*
_Story and writing_
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girls_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Jalal nagama magana yasakarwa Maama hannunta, Jawwad kam mamaki da bacin rai ya hanashi magana, Maama bata taba marinsa ba, lokacin yaji yakara tsanar Naja, juyawa Jawwad yayi ya nufi part dinsa zuciyarsa tana suya, da sauri Jalila tabi bayansa ta bar su Agurin a tsaye, Jalal ma bin bayansu yayi, ita kanta Maama jikinta yayi sanyi da marin da tayiwa Jawwad, yadda taga ya sunkuyar da kai ya tafi bece mata komaiba da kuma maganganun da Jalal yayi, Amma ta maze ta cigaba da banbami.
Jawwad na zuwa ya zauna ya dafe kansa yayi shiru yana saka abubuwa daban2 a ransa, da sauri Jalila ta karaso ta zube agabansa tana
kuka amma takasa magana se sheshsheka, dagowa Jawwad yayi ya zuba mata ido amma yakasa magana, Jalal ne yakaraso ya tarar dasu a haka, yasamu guri ya zauna a kusada Jawwad, ya kalli Jalila yace
"kidena wannan kukan haka, kikoma gida komai ze wuce Insha Allah"
Shiru tayi tacigaba da kukan a hankali cikin kuka tafara kokarin furta "Am sorry Yaya Jawwad,...."
Maganar ta sarke takasa karasawa, Jawwad yace "Jalila ke yakamata abawa hakuri, tashi kije kidena kuka, nasan abunda kikeji akan yadda akemiki a gidan nan but am really sorry komai ze wuce kinji" gyada masa kai kawai tayi, tace "Yaya Jawwad karka canza lokacin tafiyar nan, kayita tanada mahimmanci"
"zanyi Insha Allah"
yabata amsa jiki a sanyaye, ta mike zata fita ta juyo ta kalli Jalal tace "Ilham! Ilham.... Sekuma tacigaba da kuka ta fice da sauri ta tafi cikin gidan da yanzu takejinsa kamar prison.
Nana batasan me akeba, tana can tana manne da Mahmud a waya, dan haka koda ta fito palour Maama ta tarar tana sababi, ita zuwa yanzu lamarin Maama har tsoro yake bata, kullum cikin fada take, takoma halin 'yar uwatta na masifa ko gajiya batayi, Nana batabi kan maganar da Maama takeba ta wuce kitchen tadora girki.
Jalila ta shigo palour, Maama na kokarin shiga dakinta se hararta takeyi tana tsaki, sannan ta shige Naja ma wani tsaki tayi tace
"hmm nidake naga wanda ze Nasara, duk wani iyayinki da iya munafurci da kinibibi na kafirai da kuka iya sedai kiyi kigama dan nafi karfinki wallahi kar nake kallonki nafiki iya tashanci, banza 'yar Arna kawai, wadda uwarta ta yasar ta tafi gararinta"
idon Jalila yayi jawur dan kuka, cikin matukar bacin rai da masifa Jalila tace
"Naji nakuma yadda kinfini iya tashanci, tunda kin tsotsa a Nono mana, nagode Allah har mahaifina ya koma ga mahallicinsa ba'akamashi da 'yar waniba, naki uban fa? Shekararsa biyar a prison da kyar aka karboshi, tashanci gashi nan ke kinayi yayarki da
an uwanki nayi, sannan kinfini tashanci nikuma nafiki kai da iya wasa da hankali, ki kiyayi ranar dazan miki tonon silili, kuma Aure ne da yardar Allah baza' ayi shiba, saboda nagama shirina akanki, lokaci kadan ya rage kifada tarkona"
Nana data fito daga kitchen bata taba jin wannan labarin na mahaifin Su Naja ba, itakuma Naja daskarewa tayi a gurin dan mugun mamakine yakamata, dan ta girmi Jalila kuma tun kafin a haifeta abun yafaru bakowa yasani ba, Amma ita ya akayi tasani.
Jalila tuni ta shige daki, ta nufi bandaki ta dauro Alwala tazo ta hau sallaya tafara gabatar da sallar magariba.
Jalal yanata rarrashin Jawwad
"Jawwad tun asalinka me biyayyane da hakuri ba kamar niba, dan Allah kayi hakuri ka kwantar da hankalinka, kasan iyayenmu mata daukar ziga baya musu wahala, ka kwantar da hankalinka kayi hakuri"
Wata irin Ajiyar zuciya Jawwad yayi yace "Jalal Abunda yafaru naji babu dadi, amma abunda yafi batamin rai halinda wannan marainiyar Allah keciki, Jalal hakurin Jalila yakai a yaba mata, duk fitinarta tanada kawaici da hakuri, kuma tanada biyayya, duk abunda Maama take mata bata taba nuna mata bacin ranta ba, akan Jalila nasan Abba ze iya rabuwa da Maama, amma bata taba gayamasa abunda ke faruwa ba, Jalal inajin tausayin yadda rayuwar Jalila ke kasancewa daga wannan se wannan, nasan yau kwana zatayi kuka, kuma Jalal abunda Ilham tayi bata kyauta ba, be kamata tayiwa Jalila hakaba, son zuciya ba halinta bane"
"Nasani Jawwad, komai zezo da sauki zan dau mataki akan hakan, kaji ka kwantar da hankalinka"
"Shikenan Jalal, ka shirya jibi Insha Allah zamuyi tafiyar nan"
"Allah ya kaimu"
Jawwad ya amsa masa da Ameen, Jalal ya tashi ya fito, a harabar gidan yaci karo da teddyn Jalila da sweet dinta a kasa, yasa hannu ya dauka teddyn ya tafi dashi.
Bayan Jalila ta idar da salla, Nana tace "Jalila dan Allah meya faru kikewa Naja wannan maganar? Abun yabani mamaki ni bantaba jiba fa, kodai fushi ne yasaki"?
Jalila idonta Jawur ta kalli Nana tace "Nana duk bacin raina banawa mutum kazafi, kuma bana gori yauma raina ne ya kai makura a baci, sannan ba karya nayiwa mahaifin Naja ba, kuma na fada ne kozan samu sassauci akan bakanta min da ake, kullum aka tashi gori sedai ace uwata Arniya, kawai saboda...... Kasa karasawa tayi, maganar ta sarke saboda kuka
"Am really sorry sister, i feel your pain nasan ba dadi abunda yake faruwa dake amma kiyi hakuri dan Allah"
Wayar Jalila ce tafara ringing Ahmad ne Amma bazata iya dagawa ba ta kashe wayar.
Jalal na zuwa gida ya ajiye teddyn Jalila akan gadonsa ya tafi cikin gida, a palour ya tarar da Mummy amma ya shareta ya nufi dakin Ilham, tana kwance akan gado tana chatting ya fado dakin, zumbur ta mike zaune dan tasan indai taganshi a dakinta toba Arziki, ya kureta da jajayen idonsa yace "Tambayarki zanyi, idan kikamin karya sena shakeki, yaushe kika kaiwa Jalila kudi tabawa Maama?" hade rai tayi
"Na kaimata kudi, nace ta ajiyewa Maama inji Mummy"
"karya kikeyi"
"niba karyanake ba"
"zan tattakaki wallahi, karya kike"
"wayyo Allah mummy, kizo ki temakeni" ganin tana ihu ya harzuka Jalal jikinsa yafara rawa ya janyota daga kan gadon ya zuba mata mari
"Nizaki rainawa hankali? Nizakiyiwa ihu uban me nayi miki?"
Mummy kam a sukwane takaraso dakin
"lafiya meye haka metamaka?"
Banza yayiwa Mummy yace "waike wace irin dabbace ne? Ranar akan idona kike soke kudi a jikinki, naganki da idona amma saboda baki da mutunci kin dorawa yarinya kinsa se kuka take, wace irin zuciya ce dake haka?"
Se yanzu Mummy tagane inda ya dosa dan haka tace
"to mara mutunci, dama saboda waccan yarinyar kazo kake wannan zare idon kake kokarin shaketa, kaji kunya wallahi ka fifita wata banza can bare akan 'yar uwarka"
"Karki kara dangantani da wannan shedaniyar niba' yar uwata bace ba, tanemi 'yan uwanta can baniba, kuma kicigaba karki fasa, indai wannan yarinyar ce you know what she's capable of doing, ba' a tabata ta hakura, kuma wallahi kika kuma yi mata wani abu makamancin haka sekin bar gidan nan tunda ba gidan ubanki baneba"
Mamakine yakama Mummy suka bude baki suna kallonsa gaba daya,
A fusace Mummy tace "kai ka kiyayeni, akan waccan banzar yarinyar zaka ci zarafin Ilham, kuma har kake nema ka gayamin bakar magana haka? Jalal kanayiwa kanka hisabi kuwa?"
"Karki kara ce mata banza, ga banza nan agabanki" ya nuna Ilham
"tayimin abunda ko raina nabata bazan biyata ba, bashida amfani yimiki wani bayani tunda son zuciyarki kawai kikasani, amma lokaci ze bayyana komai" har ya juya ze fita daga dakin idonsa ya sauka akan Alqur'ani nan a saman rio, zuwa yayi yasa hannu ya dauka ya duba tabbas Alqur'anin ne, Amma me yakawo shi hannun Ilham? Be tsaya tambayarta ba yai waje abunsa.
Yana fita Ilham ta dora hannu aka tace "Nashiga uku mummy, wannan wace irin masiface? Wace irin kiyayya yaya Jalal yakemin haka?" Mummy tace
"kinga dan Allah darene, kidena min ihu, hankalina ya karkata wani gurin, tabbas yaron nan yana sonta, kenan seta juyamin
a, yadda yake wannan masifa kanta, har yana wannan kumfar bakin akanta ina baze yuwu ba wallahi, ba'a haifi yarinyar dazata juyamin
a ba, koya fifitata akaina ba"
(su Mummy amanta lokacin da ake juya
an wata
Ilham cikin kuka tace "Wallahi bawani sonta dayake, tana bashi kanta ne kawai, nikuma bazan iyaba shiyasa baya sona se ita dan Allah Mummy kiyi wani abu".
"ke rufemin bakini, yanzu ba wannan issue dinne agabana ba" ta juya tabar Ilham da sakakken baki.
Koda Abba ya dawo beji motsin yaran nasa ba, dan yasaba yazo yatarar da Nana da Jalila suna kallon ko wani abun a palour, dan haka yake tambayar Maama
"wai ina yaran nan ne? Banga kowa a cikinsu ba, Jawwad har ya rufe kofarsa, sukuma 'yan matan banga kowacce ba lafiya dai ko?"
Maama tace "lafiya kalau, sun kwanta da wurine kawai" dahaka suka bar zancen.
Washegari da safe yakasance Asabar, Jalila tana baccin dole, dan kwanakin naan bata iya bacci, ga matsanancin ciwon kai saboda kuka, wayartace tafara ringing Hanan ce dan haka ta daga, amma da mamakinta taji Hanan tana kuka, nan da nan hantar cikin Jalila ta kada tace "Hanan lafiya kuwa?"
Cikin kuka Hanan tace "Jalila dama Haidar Aure zeyi kuka boyemin?kuka kyaleni naketa masa wannan makauniyar soyayyar?"
"Haba Hanan, waya gaya miki haka?"
"ya zakice waya gayamin? Jiya muna waya da kunnena naji, muna waya dashi wata tana cewa wai ankusa bikinsu yake waya da wata, Jalila am so disappointed, meyasa kukayumin haka?"
"Hanan bazaki ganeba, yanzu haka cikin rikici muke dagani har Yaya Jawwad"
"Jalila duk rikicin da kuke ciki bekamata kumin haka ba, amma nagode"
Jalila na kokarin yimata bayani amma Hanan ta kashe wayar ta, dafe kai Jalila tayi ta marasa dame zataji, Hanan, Jalal, Jawwad kokuma wannan tashin hankalin.
Jawwad ya gayawa Abba zeje kaduna, Abba be hanashi ba, ya fuskanci Jawwad baya walwala, amma Abba yabarshi a stress ne na shirye shiryen biki da kuma tunanin rabuwa da gida ze tafi wani gurin aiki.
Jalal yakira yagayawa Abdallah cewar zasuzo,
Hanan kam tasha kuka, Abdallah yazo mata da labarin Jawwad zezo, amma sam batayi murna ba, Mummy se rarrashinta take, amma kuka kawai takeyi.
Daddyn Hanan yasan da zuwansu Jawwad dan haka befita
ba yana gida.
Shabiyun rana su Jalal suka iso kaduna garin gwamna, sunsami kyakyawar tarba a gurin iyayen Hanan. Har cikin gida Abdallah ya kaisu Jawwad suka gaida Mummy, Abunda ya daurewa Mummy kai be wuce yanayin abubuwan Jawwad sak Yusuf dake bauchi, boye mamakin ta tayi suka gaisa sosai, har cikin ranta ta yaba da hankalin Jawwad, har ranata takw Addu'ar Allah yasa Jawwad ya auri Hanan.
Abdallah yaje dakin Hanan yasameta a daki idon nan jawur ta sha kuka, yace mata "to uwar kishi gashi can yazo, yakamata kije ya ganki tunda danke yazo, amma fa naga shima kaman bashida lafiya ne, naga ya rame sosai"
Da sauri ta mike zaune tace "dan Allah bashida lafiya?"
"hmm magulamaciya, da kikace haushinsa kikeji, keda a rayuwarki ba kya uzuri, inkin ga dama kicigaba da kukan karkije" ya fice yabar mata dakin, bayansa tabi da harara, tayi zamanta taki tashi, seda Mummy ta biyo sahunta taita mata mita sannan ta mike, jallabiya tasaka baka se mayafinta ta tafi palourn da aka sauki su Jawwad.
Kallo daya zakayi mata kasan tasha kuka, tana zuwa tasamu guri ta zauna ta takalli Jalal tace "Yaya Jalal sannu da zuwa ya hanya?"
Murmushi Jalal yayi yace "lafiya kalau Hanan, ga Jawwad din na kawomiki"
Kallon Jawwad tayi kawai tafara kuka, Jalal yace "Ikon Allah, su mata komai nasu na kukane, hakama Jalila takeyi, mikewa yayi yafita yabasu guri.
Jawwad ya tashi daga inda yake yazo gabanta ya zauna ya dan zuba mata ido sannan yace " dama zaki iya fushi dani haka? Haba My i don't expect this from you, Hanan bakiga na rame ba, ina cikin damuwa komai yayi min zafi narasa ya zanyi" nan ya kwashe komai ya gaya mata, gaba daya tausayinsa yakamata tace
"Am sorry Haidar kishinka yasani nayi maka haka, dan Allah kayi hakuri, Amma yaya Jawwad bazan iya jure ganin ka Auri wata baniba, Jawwad zan iya hakura ka auri wata ka hadamu amma banda wannan yarinyar"
"Meyasa?"
"sister dinkace, nibazan fadi komai ba, Amma zancigaba dayi mana Addu'a"
Jawwad yaayi ta rarrashinta harta saki jikinta suka fara hira
Koda Jalal yafito Abdallah ya janye shi dakinsa suka dinga hira, bayan sunyi Sallar Azahar, suka tafi part din daddyn su Abdallah.
Daddy ya karbesu da fara'a ya kalli Jawwad yace "barka da zuwa sirikina ashe kuna tafe"
Sunkuyar da kai Jawwad yayi saboda kunya kodan karamcin nan da sukayi masa zenemi alfarmar Abbansa ya barshi ya auri Hanan.
Matsana suka zauna a kujerun dake palourn suka gaisa, ya tsaida idonsa akan Jalal ya lura da yadda bayason magana sosai, sedai in anyi abu ya danyi murmushi
Daddy yadubi Jalal yace "My son, Kaine Jalal kenan?" Jalal yayi mamaki dan yasan daddyn Hanan besanshiba, amma ya akayi yakama sunansa haka? Jalal ya gyada kai yace "eh nine"
Daddy yace "Ai ina ganinka naganeka, ammm nace bakaga tex message da'aka turamaka ba?"
Jalal ya dan dirirce yace "Wane message?"
Daddy yace "Eh akwai hukuma dasuka turomaka message na daukar aiki mana, zakaje screening"
Shiruu Jalal yayi sannan yace "Ammafa daddy nima ina shaye2, tayaya NDLEA zasu daukeni aiki?"
Tausayinsa ne yakama Jawwad yace "haba Jalal aiba a haka, ka amince mana, sun san kanayi suka daukeka ai"
Daddy yace "ABDUL JALAL don't mind kaji, ai munsan kana shaye2, karka damu you are my son dukda bansanka abaya ba amma yanzu nasamu
a, dama yaran sunmin kadan, nayi magana da daddynka ma, An riga an baka aikin, ba wani abu ai zaka iya, Jajircewarka akeso sannan kaikuma kayi kokarin denawa, zaka temakawa hukuma, ni yadda naganka din nan with good body structure aida a soja nasaka kaima"
Gaba daya sukayi murmushi tunda daddy cikin sigar zolaya ya karasa maganar banda Jalal daya shiga tunani yayi shiru,
Daddy yakuma cewa "Am sorry munmaka laifi nida diyata ko? Tasani nasa an soke maka visa, tuba muke bamuyi hakan dan bata maka ba"
Murmushi Jalal yayi ya sunkuyar da kai suka cigaba da hira, bayan Azahar suka daura haramar komawa gida, sukayi sallama dasu sannan suka nufo kano, daddyn Hanan duk ya lurada yadda Hanan take nan nan da Jawwad ya yadda ba karamin so takewa Jawwad dinba.
Bayan tafiyar su Mummyn Hanan tace "Daddy ka lurada yaron nan Jawwad kamarsa daya da Yusuf, wallahi hatta murmushinsa irin na Yusuf din Baba sagir ne"
"Na gani nima, Amma kamnin twins girl dina yafi fitowa, tun lokacin dana ganta nakeji ajikina kaman akwai alaka tsakaninmu, Amma ni yanzu abunda yake raina inason tuntubar mahaifinsu, indai Jawwad yana sonta yafito kawai, tunda naga hankalinta yafi karkata gareshi"
Kaman Mummy tayi masa bayanin yakusa Aure, amma tafasa tace "To Allah ya tabattar da alkhairi amma gaskiya ni na yaba da hankalin sa, gashi nutsatse"
Tunda suka taho hanya Jalal yayi shiru yakasa magana, Jawwad ya dubeshi yace
Jalila sosai take rashin lafiya, bata ko cin Abinci zuciyarta a cunkushe bata sha'awar komai, ga wani matsanancin ciwon kai dayake hanata bacci, ko makaranta bata iya zuwa, Nana tayi2 taje Asibiti tace mata ba wani matsala bane damuwa ce kawai take damunta,
Ta yunkura ta mike zata shiga toilet, kawai taji jira gaba daya garin yayi mata baki kirin, aikuwa ta fadi a gurin tana fidda numfashi da kyar, Naja na kan gado tana kallon Jalila tace " ahaka bakinciki da mugun abunki zasu hadu su kasheki, ki barmu a duniyar nida Jawwad muyi Aure, Allah yasa ki mutu shegiya"
Jalila tanajin Naja amma bazata iya motsa ko dan yatsanta ba Nana data dawo dauke da kofin tea ganin Jalila a kwance yasa ta jefar cup din tazo kanta da sauri tana girgizata, Jalila tasa hannu ta dafe kanta tace "Nana kaina ze fashe"
"Sannu Insha Allah ze dena ina zuwa"
Taje ta dakko youghurt a fridge tazo tana bawa Jalila danta fuskanci hada yunwa ke damun Jalila,
Naja ta kallesu tayi tsaki "Aikin banza wahalallu"
Tunda su Jawwad suka nufo kano, Jawwad yakejin faduwar gaba dan besan meze tarar ba dan shi yanzu ko zuwa gidan baya so, shikam Jalal se sakawa yake yana warwarewa, shi meye amfanin yin wani aiki, Jawwad yaji shirun yayi yawa dan haka yace "ya dai naji kayi shiru haka? Ko har yanzu baka yadda da aikinbe?"
Jalal ya danyi tsaki sannan yace "Jawwad nifa kaina yagama daurewa a ina Baban Hanan yasanni da harze bani aiki, kuma yana cewa sungama magana da daddy, yaushe akayi wannan zancen bansaniba? Tayaya zan fara hana wasu sha da fataucin miyagun kwayoyi bayan ni inayi? Ka gayamin tayaya?"
"wannan ba abun damuwa bane bafa, kaiba ruwanka da wani tone2 na meyasa aka baka aiki, kuma ai ansan kana shaye2 akabaka ko?"
Shiru Jalal yayi baya tunanin ze iya wannan aikin, tayaya za'ace me hana laifi yana aikatawa.
Haka suka cigaba da shiru kowannensu yana sakawa yana kwancewa har suka iso kano.
Jalila tunda ta danci Abinci tasha magana tasamu nannauyan bacci yayi awon gaba da ita.
Koda su Jalal suka dawo, kowa gidansu ya nufa, Jalal ya tafi gida, shima Jawwad ya tafi gidansu.
Kwana uku da zuwan su Jawwad kano, tunda suka dawo Jawwad baya shiga gidan saboda gudun fitina sam baya wuni a gidan.
Jalal yayiwa teddyn Jalila guri akan gadonsa, yana son yaganta yabata abunta sannan ya tambayeta ya akayi Alqur'ani daya bata yaje hannun Ilham? Har yayi wanka ze kwanta yaji kamar ana hura masa wuta a zuciyarsa da kansa gaba daya jikinsa ya dau zafi a sukwane ya nufi fridge dinsa ya ciki cikinsa da giya sannan yaji daidai.
Da safe Jalal yasamu daddynsa a daki yana bacci dayake saukar dare yayi, ba tunanin komai Jalal ya tasheshi, koda daddy ya tashi Jalal yafara jeramasa tambayoyi
"daddy da saninka aka samomin aiki a hukumar sha da hana fataucin miyagun kwayoyi?" daddy yace
"Dafarko dai ban saniba sedaga baya, General Abdurrashed ya kirani a waya, yacemin 'yarsa tanemi ya sama maka aiki a wannan hukumar inbazan damuba in turamasa CV dinka, shikenan na amince"
Jalal yayi saroro yana kallon Daddynsa "Wace' yar tasa?"
"kai zan tambaya ai"
Shiru Jalal yayi, kawai ya mike ya sakko daga kan gadon daddy yafice daga dakin.
Jawwad yana dakinsa, Nana tazo tace masa Abba yana kiransa, haka ya tashi gabansa na faduwa, yana fatan Allah yasa ba wani laifin yayi ba, yana zuwa, ya tarar da 'yan gidan a palour banda Naja, Abba yayi shirin fita, Abba yace masa "Jeka ka canza kaya, Bauchi zamuje yanzun nan"
Cikin mamaki Jawwad yace "Bauchi kuma Abba?"
"Eh bauchi mana, kayi sauri a yau nakeson mudawo"
Cikin Mamaki Maama tace "Abban Jawwad ni nakasa gane meke faruwa haka, tun jiya kake bacin rai, kaki saurarata yaukuma ba zato ba tsammani kace bauchi zaka tafi, mezakiyi a bauchi ne?"
Kallon ta ya danyi yace "ba dole inki saurararki ba, ki shirya munyi magana da baban Jalal, ranar Lahadi shida 'yan uwansa zasu kawo kudin Auren mahmud da Nana, sannan zanje bauchi inne mawa
ana Auren' yar mutunci, sannan karki kuskura in dawo in tarar da yarinyar nan Naja a gidan nan, tabarmin gidana a yau"
"Amma meyasa?"
"in mun dawo kyaji meyasa"
Jalila dake gefe tace "Abba Allah ya kaiku lafiya, ka gaishemin dasu, kuma akwai wani albishir dana boye banyimaka ba sekaje bauchi zaka gani"
Abba yayi murmushi yace "to shikenan Baby, kema inason kafin lokacin bikin Nana ki fidda miji ku karasa karatun a dakinku" Jalila ta sunkuyar da kai tana murmushi,
Abba kuma yasa kai yabar palourn.
Mummy tana zaune suna hira daddy a babban palour Jalal yashiga da sallama, suka amsa masa gaba daya, yaje kan Mummy ya tsaya fuskarnan babu alamar walwala ya jefa mata wata jarida a hannunsa yace "ga shi nan yanada kyau ki duba Labari na uku a cikin wannan jaridar, yanada mahimmanci agareki"
Ina yinku ABDUL JALAL group da sauran masoya wannan Novel irin sosai din nan fa
inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing, gashi nan na muku dogon page, in banga ruwan comments inna shura takalma na posting se rana ita yau
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
What's app only 07063065680.
*ABDUL JALAL*
_Story and writing_
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girls_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Tsayawa Mummy tayi tana kallonsa, yace "ki dauka kiduba mana, kika tsaya kina kallona, ganin da yayi Mummy bata da niyyar taba jaridar yasashi yasa hannu ya bude ya ajiye mata a gabanta,
Hoton Kabir ne da Jeje da wasu mutane da bindigogi agabansu, tittle din ta karanta, da hanzari jikinta na rawa ta dau jaridar tafara dubawa, an yankewa Kabir zaman gidan yari na shekaru goma sha biyar sakamakon saida makamai da fataucin miyagun kwayoyi, sannan an yanke masa shekaru Ashirin a prison saboda Yunkurin kisan kai, da kuma shekaru goma sha hudu sakamakon lalata da kanan yara mata.
Sekuma su Jeje da'aka yankewa hukuncin shekaru ashirin2 a gidan prison.
Daddy ne yasa hannu ya karbi Jaridar shima ya duba, Jalal yace
"Mummy Allah yakawo karshen mutumin da dasa hannunsa a lalacewata, shiyabada kwangilar koyamin shaye2 saboda ya huce takaicin abunda kikayi masa akaina, kalli keda laifi nida karbar hukunci"
Daddy yace
"Jalal kai waya gayamaka shiya bada kwangilar hakan?"
"ba gayamin akai ba, Jeje abokina yaronsa ne, idan nagaya muku wanda yayi sanadiyar kama Jeje da uban gidansa har nasan wannan lamarin kila karyatani zakuyi, sanin hakan bashida Amfani, Mummy yakamata ki zubar da makamanki kikoma ga Allah tun kafin kema ya dankeki, Kabir makiyinane na boye bansan dashiba sedaga baya, nasan makiyana na fili, suma ina nan nasasu a Addu'a very soon Allah ze yimin maganinsu"
Yasa hannu ya dauke Jaridar ya fice.
Daddy yaja ajiyar zuciya yace "Khadija lokuta da dama bana ganin laifin yaron nan, ba wai ina goya nasa bayane ba, amma kinmasa laifuka masu tarin yawa, ba kya duba haka se wanda yakemiki, anyway Ansamosa aikinyi na gwamnati wanda muke saka ran ze dauke masa hankali daga kan shaye2"
Kallon Daddy tayi tace "bangane ansamosa aiki ba, wani irin Aiki? Me Jalal yanema yarasa da zeyi wani aiki, ina kamfaninsa na sarrafa robobi meyasa bazaka bashi abunsa ya rike ba?"
"ba an samomasa aiki ne dan wani abuba, ansamo masa ne dan hakan zesa yayi kokarin dena shaye2, kuma bazan iya cewa wanda yasamo masa din A'a ba, kuma nima naga dacewar hakan"
"wai waye ya samo masa?" ta tambaya cikin kosawa
"General Abdurasheed ne"
Dan zare ido tayi tace "Ina yasanshi daze bashi aiki, sannan wani irin aikine haka? Dan dana baze aikin soja ba"
"Eh ya gayamin Jalila ce tace tanason yasama masa aiki a NDLEA, hakan ze temaka masa wajen dena shaye2"
Hade rai tayi sosai tace
"Baze yuwu ba, baza'a mayar minda
a bawa ba,
Akan mene? Meye hadinta dashi dazata sa a samo masa aiki, banda cin mutunci tasan yana shaye2 shine zatace yayi aiki a hukumar yaki da shaye2 salon tasaka akama shi, kokuma taji dadin juya shi yadda takeso ko? Dama yanzu na fuskanci maganarta yakeji akanta ba irin wulakancin daba yawa Ilham, to bata isaba da raina babu yarinyar dazata juyamin
a, baze yuwu in haifi
a wata ta juyamin shiba"
Mikewa daddy yayi tareda yin murmushi yace "Eyya kin makara khadija, duk abunda kayi se an maka, ki gode Allah da yarinyar ba cutar dashi take ba, dan ta damu da halin dayake cikine hartasa a sama masa aiki, nayi farinciki da hakan, kuma batun kice baza'a juya miki
a ba daga baya kenan aikin gama ya gama" be jira yaji martanin da zatayi ba ya shige bedroom ya kulle kofarsa.
Jawwad ko sallama basuyi da Jalal ba suka tafi bauchi shida Abba.
Maama kam a sukwane take tambayar Jalila "me Abba ke nufi, me kika gaya masa haka? Sannan wa zeje nemawa Aure?
"niba abunda nagaya masa, yaushe rabon da in zauna dashi balle ince masa wani abu, nibansan waze nemawa aure ba be gayamin ba"
A fusace Maama takoma dakinta tana tunanin yazata bullowa lamuran.
Jalila takoma daki suka dinga murna itada Nana, Jalila tace "Nana ban taba zaton Abba ze yadda da abunda nagaya masa ba"
Dan bata rai Nana tayi tace "Jalila nayi mamakin abunda ya fusata Abba haka, har yayi fushi yake ikrarin abar masa gida, nayi mamaki sosai be taba hakaba fa"
"to yanayi na rayuwane Nana, tunda kikaga haka akwai abunda ya bata masa raine, sannan akwai dalilin dayasa yayi haka"
Nana ta dan numfasa tace "Jalila nifa damuwata naji Abba yana batun akawo kudin Aurena, Allah yasa ba dana Yaya Jawwad za'a hadamin ba, nan da wata hudu da 'yan kaifa kenan"
Nana takarasa maganar kaman zatayi kuka
Jalila tace "to meye aciki? Keda rabin rankine fa Mahmud zaku kasance inuwa daya"
"To Jalila karatun fa? Kinsan Mahmud a kasar waje yake nasa karatun tayaya abun ze yuwu?"
"ze yuwu mana, kicigaba da naki karatun a can riba biyu, Allah sarki Rayuwa hajiya Nana za'a zama matan Aure, bari in lissafa yaushe zaki haihu"
Hade rai Nana tayi "Ke Jalila komai sekin sako wasa a cikine? Inamiki maganar serious kinamin wasa, ke yanzu akace za'ayi aurenki nan da watanni hudu kin shiryane? Ni yanzu ma meyasa Abba bece a hada dake ba"
Dariya Jalila tayi tace "gidan Ahmad yana bauchi, shi yana aiki a maiduguri, ni ina karatu a kano tayaya kike zaton inyi Aure yanzu, se nagama tukuna"
Wayar Jalila tafara ringing, ta kalli Nana tace "Excuse me, let me pick the call"
Nana ta daga mata kai, Jalila ta amsa wayar tareda yin sallama
Amsamata yayi sannan ya dora da "Babyna kwana biyu kin gujeni you are not picking my calls, ina fatan ba laifi nayi miki ba?"
Cikin siriyar muryarta na shagwaba tace
"Ohh no ni bakamin laifi ba, bana dan jin dadine kawai, amma yanzu Alhamdilillah naji sauki"
"Ya salam amma baki gayamin ba, yau zan shigo kano dama shiyasa na kiraki, in kin amince zanzo in ganki"
"Babu damuwa my one, ina fatan in ganka nima am missing you"
"Like serious, karkisa inyi Ihu attention din mutane ya dawo kaina"
Murmushi tayi tace "ba sekayi ihuba, aini yakamata inyi, kwana nawa zakayi a kano?"
"zanyi sati daya Insha Allah, zanyi wani assignment ne"
"Shikenan Allah yakawo ka lafiya"
"Ameen my queen, bazaki tambayi Antynki ba?"
Dan yamutsa fuska Jalila tayi tace "Ainasan tana lafiya tunda najika haka"
Murmushi yayi yace "Queen da alama kinada kishi sosai, anyway sena shigo, idan nazo da wuri zaki ganni yau, in ban shigo da wuri ba se Allah ya kaimu gobe"
"to shikenan Allah ya kaimu, take a good care of your self"
"Ok Baby i will Insha Allah" ta katse wayar, Nana ta zuba mata ido tana kallonta, Jalila tace "Madam lafiya kuwa?"
"Lafiya mana, nina kasa gane inda kika dosane, gane lamarinki se Allah mutum baya taba ganeki, gaba daya rayuwarki zigza ce"
Sosai Nana tabawa Jalila dariya tace "rayuwartawa ce zigza, lallai ma Nana bakida dama, Rayuwata normal ce kaman ta kowa"
"A'a ban yadda ba, Allah yasa ayi miki aure kafin ayiwa Yaya Jawwad"
"Ba Ameen ba, back to sender muguwa kawai"
"eh amma ni kikayimin fata saboda son kai"
Wayar Jalila ce takuma daukar ruri, ta kai hannu ta dauka tana dubawa taga Hanan ce dan haka ta kashe wayarta.
Tunda suka fara tafiya Abba beyiwa Jawwad wani gamshashen bayani akan wannan tafiyar ta bazata ba, yanason yayiwa Abba magana amma yakasa duk sunyi shiri Jawwad na driving,
"Dama Aliyu akwai wadda kakeso kaki ka gayamin kabari ake kokarin auramaka wannan yarinyar?"
Tambayar tazowa Jawwad a bazata, kuma idan yaji Abba ya ambaci sunansa na gaskiya kai tsaye haka, alama ce ta
he is so much serious.
Jawwad ya dan sosa keya yayi shiru
"yaka sosa kai kayi shiru? Kamin bayani mana"
Cikin kame2 Jawwad yace"Amm.. Dama Abba, ai..."
Abba yacce " Jawwad da farko sister dinka Jalila tagayamin inyi bincike akan yarinyar nan Naja, tacigaba da gayamin hakan, sannan taki gayamin komai game da Naja, sedai cewa inyi bincike, tacigaba da nunamin cewa kunyarka da kawaicinka baze bari ka nuna abunda ke ranka ba, na dauki maganarta serious nafara kokarin bincike, ina kan binciken ne, Mahaifin Hanan ya kirani yamin magana akan in dai dagaske kana son 'yarsa yabaka dama ka fito, wanda ni bansan da zancen ba, nayi kokarin in zauna da kai muyi maganar kafin ta kai ga haka Jalal yazo ya sameni har gurin aiki yamin bayani akan alakarka da' yar gidan general Abdurrasheed, sannan ya daukeni ya kaini inda aka gayamin komai akan Naja, bantaba tunanin Mamanka zata zaba maka mace irin wannan mara kamun kai a matsayin mata ba, Jawwad meyasa baka gayamin abunda ke ranka ba, kabari nakusa gangancin saka rayuwar ka a hatsari? "
"Abba nasam bazaka zabamin abunda ze cutar dani bane, banason bijirewa umarninka dana Maama, shiyasa na amince"
"Nasan da wannan Jawwad, amma dukda haka a matsayin mu na iyaye yanada kyau mudinga baku zabi, ba wai bin son zuciyarmu da tirsasamuku akan abunda bakwa ra'ayiba, yana da kyau kadinga fa
an ra'ayinka ba laifi bane naji dadin kokarin yimana biyayya dakayi, Allah yayi maka Albarka yakara ha
amin kanku, Allah ya shirya mana ABDUL JALAL dukda kasancewar halinsa amma yadamu da lamuranka sosai, yadda yazo ya sameni kaman zeyi kuka, Alhamdilillah nayi mamaki naga abubuwan sa sun fara raguwa, yafara dawowa hanya, ya rage rashin ji"
"hakane ya rage sosai makuwa, abokiyar fadansa keta kokarin sashi a hanya ai"
"Wa kenan?" Abba ya tambaya
"Jalila mana, tanata kokari akansa, kuma naga inga masa nasiha koba duka ba yana
an dauka"
Abba yace "masha Allah, at least kaga an samu improvement, itama General Abdurrashed yamin magana, yace akwai abokin
ansa dayake sonta, wai Ahmad sunansa kowaye?, yabiyo ta hannunsa a nema masa Aurenta, amma nace na bashi wuka da nama shima babanta ne, duk abunda yaga dace yayi"
Jawwad yai murmushi yace "hakane Abba, lokacin da mukaje kaduna yamin zancen nima, yace shima mutumin sojane yana da kirki sosai"
"Hakane, Allah ya tabbatar mana da alkhairi yamuku zabi da abokan zama nagari" Jawwad a zuciyarsa yace Ameen.
Hanan taita kiran wayar Jalila amma Jalila taki dagawa, saboda bataji dadin abunda Hanan tayi mata ba, sako Hanan ta turimata kamar haka
"Assalamu Alaikum, Am very sorry my twiny, nasan na miki laifi kiyi hakuri dan Allah, Yaya Jawwad yazo kano shida Jalal, yamin bayanin komai abunda ke faruwa, kiyi hakuri so dakuma kishinsane yasa namiki haka, sannan naji Yaya Abdallah yana maganar Ansamawa Jalal aiki za'a gama interview ranar laraba amma har yanzu bejeba, you have to take action"
Jalila nagama karantawa ta kira Hanan, seda Jalila ta kira sau biyu sannan Hanan ta dauka tace
"'yar rainin hankali inata kiranki kinki
agawa, amma da kikaji batun ABDUL JALAL harkin kirani"
Jalila ta hade rai kaman Hanan na ganinta tace "ke banason wulakanci, ai banji dadin abunda kikayimim ba sam wallahi"
"Nasani amma ai nace kiyi hakuri, you won't understand how far my loves go on your brother, inasonshi ina kishinsa shiyasa na shiga damuwa, inata addu'a dai amma ina cikin damuwa Queen"
Tausayin Hanan yakama Jalila tace "ki kwantar da hankalinki kinji my twiny, komai ze wuce kece zaki zama matar Yaya, ina nan ina tayaku da Addu'a"
"Masha Allah, Allah yabiya ki da mafificin Alkhairi Jalila, bazan iya biyan kaunar da kike nunamin ba"
"bakomai Sister na, nace are you serious Jalal beje interview din nan ba?"
"Wallahi dagaske nake miki, hala aikinma kekisa aka samo masa?"
"to meye naki aciki nason kisani, nice nagayawa Daddy ya samo masa, kuma be isa ya watsamin kasa a ido ba zan sameshi, seyaje interview din nan"
Dariya Hanan tayi tace "wai zaki sameshi irin Mum din nan tasa, kai lamarinku din nan yana birgeni wallahi, kowa da guntun taurin kansa dan Allah duk yadda kukayi ki gayamin dan wallahi....
Katse wayarta Jalila tayi jin Hanan zata fara mata bare2.
Ilham shiryawa tayi takanas ta tafi gidansu, domin taji abunda yakamata suyi, dan ita ta riga ta karaya da lamarin nan bata tunanin akwai nasara dan kullum Jalal kara bau
ewa yake, babu alamar ze sakko.
Tayi sa'a ummannata tana gida, suka kule a daki kaman yadda suka saba in Ilham
in tazo.
"Umma nifa najiki shiru ya'ake cikine? Na
ora mata sata amma Jalal bakiga rashin mutuncin dayayi min ba, wallahi son yarinyar nan yake, kincemin zakije Nijar gurin wani malamin amma shiru kullum abubuwan kara tabarbarewa sukeyi"
Umma tace "ke nayi maganar zuwa nijar, munyi waya da mutumin na masa bayanin komai, amma budar bakinsa wai yayi bincike akan yarinyar indai inason a yimin aiki akanta zan bashi dubu
ari biyar, nikuma ina naganta? Banida ita bani da wata kadara da zan sayar in bashi wannan uban ku
in, dan haka nakoma gurin wanda muke zuwa tun farko, shikuma yacemin baze iya aiki akanta ba sedai a kara watsa rayuwar Jalal"
"to Umma batun Auren namu fa?"
"shima za'ayi ne amma yace mu
an kara hakuri"
"umma kenan, mu kara hakuri fa kikace? By mistake idan Asirin ya karye gaba
aya kuma yaya zamuyi?"
"bazeyiba, malamin yabani wannan tabbacin ki kwantar da hankalinki burinmu seya cika, sena wulakanta shi shida uwarsa hada uban nasa, bana yafiya ga wanda yamin laifi"
"to shikenan Umma, Allah yasa, ni ba
ri in tafi, zan
an tsaya inyi siyayya".
Dogon wandone a jikin Jalila da riga, dan haka ta
akko katon hijjabinta me hannu tasaka ta fito part
in Jawwad taje tana tsammanin ganin Jalal a can amma baya nan, rabonta da shiga gidansu Jalal kuwa harta manta, direct ta nufi gidansu Jalal, amma tarasa ina zatayi tasan dai be dace ta tafi part dinsa nemansa ba, fasawa tayi ta juyo tanufo gate zata fita itakuma Ilham ta shigo.
Tsayawa sukayi suna kallon kallo itada Ilham, ha
e rai sosai Ilham tayi tareda yin tsaki tazo zata gifta gefen Jalila ta wuce, caraf Jalila tasa hannu ta riketa ta janyota gabanta suna fuskantar juna, a fusace Ilham tace "ke dalla malama meye haka? Meyasa bakida tunani ne?"
Jalila taja wasu seconds tana karewa kwayar idon Ilham kallo sannan tace
"banida tunani kam, dole ki fadi haka, kinsan ba'a tabani a zauna lafiya, dan haka sekinyi hakuri da duk abunda zaki gani har se kin biya abunda kikayimin"
Hararta Ilham tayi takuma kokarin rabawa ta wuce ta barta, amma Jalila takuma shan gabanta tace
"Ilham nasani tsawon shekaru ina bata miki rai, kinyi alwashi daban2 akan ganin bayana, baki taba nasara ba se wannan karon da kika
ora min sata, to bari kiji in gayamiki wani abu dabaki saniba, babu abunda zakiyi a rayuwa ki rama abunda nayi miki, na riga nagama dake Ilham, kuma Wallahi Jalal baze taba aurenki ba, nagaya miki dama muddin kudirina yayi karo da naki sena watsa naki, kudirinki akansa yaci karo da nawa na watsa shirinki watsawa ta har gaban abada zanso ingaya miki wani abu daya kamata ki sani amma ban saniba ko kinason ji"
Kallonta kawai Ilham take batareda tayi magana ba, Jalila ta
ora tace
"Ranar da Jalal ya kwanta a Asibiti, kukazo duba shi keda Mahaifiyarki kisani idonsa biyu yaji duk abunda kuke fa
a, dan haka ki cirewa ranki cewar burinki ze cika, Na riga naganoki Ilham tuntuni shiyasa nayi miki illa inda ba wanda ze gani, na illata shirinki bakida wata dama data miki saura, damarki
aya shine ki jajirce kicigaba da jarraba sa'arki kozaku daidaita"
Jalila takarasa maganar tana mata wani mugun kallo sannan ta juya tayi ficewarta, gaban Ilham ne ya shiga dukan hamsin2, kaddai Jalila dagaske take, amma to in hakane da yaji aida ya
auki mataki, "kai karyane bejiba, koma yaji wallahi seya Aureni, se burin mahaifiyata yacika"
Ta shige cikin gida da sauri hada tuntube.
Maama takasa zaune takasa tsaye, Naja batasan budurin da'akeba dan lokacin da Abba yayi wannan maganar bata nan tafita yawonta, harta dawo Maama tarasa ta inda zata fara mata bayani.
Jalila na fitowa taga Jalal ya dawo a mota, yana kokarin shiga gida, ganin da yayi ta tsaya ta ki tafiya ta kura masa ido yasan akwai magana a bakinta, tsayawa yayi agaban ta yayi parking, yana tsayawa ta zagaya inda yake,
age mata gira yayi alamar meke faruwa?
an kallonsa tayi tace
"daga ina?"
"kin aikenine?" ya tambayeta
"Ohh No Allah yabaka hakuri"
Yace "Ina Jawwad ne? Na duba baya nan ban san inda ya tafiba?" hade rai tayi itama tace
"ka duba shi mana, kokabani ajiyarsa ne?"
Kallonta yayi, wato ta rama kenan
Yace "A'a ban baki ajiyarsa ba"
"dama.." sekuma tayi shiru
"Dama me?"
"inada magana ne"
"fadi ina jinki"
"toka fito daga motar mana"
"In fito kuma? Gaskiya ni yunwa nakeji, zuwa zanyi in kwanta, naje neman Abinci narasa me zanci, dama in kin bawa Jawwad nake ci nima amma yanzu baya nan nasan bazan samuba"
"Hmm to kace Ilham tabaka mana"
Hade rai yayi sosai yana Kallonta, sunkuyar da kai tayi tana dariya kasa2
"Yi hakuri, ai yanzu mundena fa
a ka jirani a part din Yaya Jawwad zan kankaro maka kanzo in za kaci" tayi maganar tana dariya, tana matukar kyau idan tayi dariya, gya
a kai yayi ta juya ta tafi, yabi bayanta da kallo harta shige gida, sannan yaja motar ya shiga da ita gida.
Gida takoma taje ta
akko masa breakfast
in Jawwad da yatafi beci ba, dayake da zafinsa a cikin flask, tana zuwa ta tarar dashi a zaune a palourn Jawwad yana jiranta, ta shiga tayi sallama amma be amsaba, seda tazo kansa ta tsaya takuma yimasa sallama ya
ago ya kalleta ya amsa a hankali, ta ajiye tray din tace
"Yana daga hakkin musulmi akan musulmi in yayi sallama ka amsa masa, kadinga amsa sallama please"
Shiru yayi yaki kulata, Jalila tarasa wane irin miskilin mutum ne Jalal, koma tace
an rainin hankali kana masa magana yana jinka amma yayi maka banza dan tsabar wulakanci,
ta aje masa Abincin ta zauna a kujerar dake kallonsa. Ta danne fushinta
Ya hada Abincinsa yafara ci, can yace "Me ya kai Alqur'ani dana baki hannun Ilham?" yai tambayar kamar bashi yayi ba
auka tayi" tabashi amsa a takaice
"Ya'akayi ta
auka baki hanata ba?"
"Ina bauchi aka aikota taganshi shine ta
auka"
Bekuma cewa komai ba yacigaba ds auna loma, can Jalila tace
"Ya akai kasan yana gurin ta?"
Kallonta yayi ya danyi murmushi
"in kinaso in dawo miki dashi, yana gurina, amma bakiga abunda na ajiye a cikiba ko?"
an yatsina fuska tayi sannan tace
"Nifa tsawon lokacin da yayi a gurina banga komai a ciki ba"
"zan dawo miki dashi kikuma dubawa"
"to naji zan duba"
Ya cigaba da cin Abincin sa, can ta
an nisa tace
"An baka aiki ance kaje interview kaki why?"
agowa yayi ya kalleta, "dama nayi tunanin kece kikasa aka nemamin wannan aikin, tayaya ina shaye2 zakice asamomin aiki a hukumar dake yaki da shaye2, amfanin me zanyi ko nima so kike a kamani?"
"calm down let me explain, mezesa in so akamaka? da hakane naso akamaka da nasa an ka maka kaida abokinnaka jeje ai"
agowa yayi ya ha
e rai kaman be taba dariya ba
"Am sorry banyi hakan da wata manufa ba, sedai inkana aikin na farko ze rage maka yawan damuwa, sannan ze sa ka kara kokarin kadena shaye2 kaima, at least in kana da gurin zuwa ze kara dauke hankalin ka daga kan Shaye2"
Zuba mata ido yayi yana tunani daban2 akanta, ta damu dashi dayawa, she's so simple and calm, matsalarta kawai taurin kai da rashin kunya, Amma tanada zuciya me kyau.
Tsarguwa tafara yi da kallon dayake mata tace
"Ya dai?"
"meyasa kika damu dani haka?"
Shiru tayi dan bata san mezatace masa ba, basarwa tayi tace
"dan Allah kaje interview din nan karka watsamin kasa a ido"
"Senayi shawara" yabata amsa
"shawara kuma, dan Allah mene kuma na wani shawara dan Allah Yaya Jalal kaje please karkasa inji kunya" da shagwaba takarasa maganar
Bude baki yayi tareda yin murmushi kaman karta dena magana
"Nine Yaya kuma yau, yarinyar bakida kunya fa"
"Aida
inma dan muna fada ne amma yanzu mundena fa
a, dan Allah kaje ba dan halina ba, kaji Yayana
an gidan daddy abokin Yaya Jawwad, badan halina ba" murmushi yayi ya
an girgiza kai yace
"Aikuwa kinsan indan halinkine bazaniba, innayi tunani zan gaya miki"
"to Allah yasa inji alkhairi"
Be amsaba ya kai hannu ya dauki cup ya kai bakinsa amma jikinsa yafara rawa yakasa kaiwa
"lafiya menene kuma?"
Ajiye cup din yayi, yai shiru yana rintse ido"
Da sauri ta mike ta nufi inda yake tana fa
in "Subhanallah meyafaru?"
Dagowa yayi idonsa yayi jawur yace
"Gi.. Giy..... Giya,.... Giya zansha, ita nakeson sha"
"giya kuma? Meyasa zaka sha giya?"
Numfashi yake ja ya mike tsaye ya nufi hanyar fita, idonsa yayi jawur jikinsa se rawa yakeyi da sauri ta sha gabansa
"dan Allah Jalal karka sha giya, meyasa idan kuma kasha ka bugu daga nan ka mutu mezaka cewa Allah? Dan Allah karka sha kayi hakuri zaka ji bakason sha"
Tureta yayi ze fita, takuma tare kofa tana masa magiya, yasa hannu ya hankadata jikin kofa ta bige kafa
a ta fa
i a gurin shikuma ya fice kaman wani horrorn dayake bukatar jini.
Godiya mara iyaka ga members na kungiyar mu me tarin Albarka Perfect writers association, Allah yakara ha
a kanmu.
Abdul Jalal Novel Fans
kaunarku a ruhina take, inajin dadin comments dinku hada wakokin da'ake reramin
Masu bina private suna min comment kokuma bani karfin gwiwa, da masu biyoni suna neman littafina da masu karantawa wanda bansansu ba ina godiya Allah yasaka da alkhairi Allah yabar kauna.
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
What's app only 07063065680.
*ABDUL JALAL*
_Story and writing_
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girls_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Tsayawa Mummy tayi tana kallonsa, yace "ki dauka kiduba mana, kika tsaya kina kallona, ganin da yayi Mummy bata da niyyar taba jaridar yasashi yasa hannu ya bude ya ajiye mata a gabanta,
Hoton Kabir ne da Jeje da wasu mutane da bindigogi agabansu, tittle din ta karanta, da hanzari jikinta na rawa ta dau jaridar tafara dubawa, an yankewa Kabir zaman gidan yari na shekaru goma sha biyar sakamakon saida makamai da fataucin miyagun kwayoyi, sannan an yanke masa shekaru Ashirin a prison saboda Yunkurin kisan kai, da kuma shekaru goma sha hudu sakamakon lalata da kanan yara mata.
Sekuma su Jeje da'aka yankewa hukuncin shekaru ashirin2 a gidan prison.
Daddy ne yasa hannu ya karbi Jaridar shima ya duba, Jalal yace
"Mummy Allah yakawo karshen mutumin da dasa hannunsa a lalacewata, shiyabada kwangilar koyamin shaye2 saboda ya huce takaicin abunda kikayi masa akaina, kalli keda laifi nida karbar hukunci"
Daddy yace
"Jalal kai waya gayamaka shiya bada kwangilar hakan?"
"ba gayamin akai ba, Jeje abokina yaronsa ne, idan nagaya muku wanda yayi sanadiyar kama Jeje da uban gidansa har nasan wannan lamarin kila karyatani zakuyi, sanin hakan bashida Amfani, Mummy yakamata ki zubar da makamanki kikoma ga Allah tun kafin kema ya dankeki, Kabir makiyinane na boye bansan dashiba sedaga baya, nasan makiyana na fili, suma ina nan nasasu a Addu'a very soon Allah ze yimin maganinsu"
Yasa hannu ya dauke Jaridar ya fice.
Daddy yaja ajiyar zuciya yace "Khadija lokuta da dama bana ganin laifin yaron nan, ba wai ina goya nasa bayane ba, amma kinmasa laifuka masu tarin yawa, ba kya duba haka se wanda yakemiki, anyway Ansamosa aikinyi na gwamnati wanda muke saka ran ze dauke masa hankali daga kan shaye2"
Kallon Daddy tayi tace "bangane ansamosa aiki ba, wani irin Aiki? Me Jalal yanema yarasa da zeyi wani aiki, ina kamfaninsa na sarrafa robobi meyasa bazaka bashi abunsa ya rike ba?"
"ba an samomasa aiki ne dan wani abuba, ansamo masa ne dan hakan zesa yayi kokarin dena shaye2, kuma bazan iya cewa wanda yasamo masa din A'a ba, kuma nima naga dacewar hakan"
"wai waye ya samo masa?" ta tambaya cikin kosawa
"General Abdurasheed ne"
Dan zare ido tayi tace "Ina yasanshi daze bashi aiki, sannan wani irin aikine haka? Dan dana baze aikin soja ba"
"Eh ya gayamin Jalila ce tace tanason yasama masa aiki a NDLEA, hakan ze temaka masa wajen dena shaye2"
Hade rai tayi sosai tace
"Baze yuwu ba, baza'a mayar minda
a bawa ba,
Akan mene? Meye hadinta dashi dazata sa a samo masa aiki, banda cin mutunci tasan yana shaye2 shine zatace yayi aiki a hukumar yaki da shaye2 salon tasaka akama shi, kokuma taji dadin juya shi yadda takeso ko? Dama yanzu na fuskanci maganarta yakeji akanta ba irin wulakancin daba yawa Ilham, to bata isaba da raina babu yarinyar dazata juyamin
a, baze yuwu in haifi
a wata ta juyamin shiba"
Mikewa daddy yayi tareda yin murmushi yace "Eyya kin makara khadija, duk abunda kayi se an maka, ki gode Allah da yarinyar ba cutar dashi take ba, dan ta damu da halin dayake cikine hartasa a sama masa aiki, nayi farinciki da hakan, kuma batun kice baza'a juya miki
a ba daga baya kenan aikin gama ya gama" be jira yaji martanin da zatayi ba ya shige bedroom ya kulle kofarsa.
Jawwad ko sallama basuyi da Jalal ba suka tafi bauchi shida Abba.
Maama kam a sukwane take tambayar Jalila "me Abba ke nufi, me kika gaya masa haka? Sannan wa zeje nemawa Aure?
"niba abunda nagaya masa, yaushe rabon da in zauna dashi balle ince masa wani abu, nibansan waze nemawa aure ba be gayamin ba"
A fusace Maama takoma dakinta tana tunanin yazata bullowa lamuran.
Jalila takoma daki suka dinga murna itada Nana, Jalila tace "Nana ban taba zaton Abba ze yadda da abunda nagaya masa ba"
Dan bata rai Nana tayi tace "Jalila nayi mamakin abunda ya fusata Abba haka, har yayi fushi yake ikrarin abar masa gida, nayi mamaki sosai be taba hakaba fa"
"to yanayi na rayuwane Nana, tunda kikaga haka akwai abunda ya bata masa raine, sannan akwai dalilin dayasa yayi haka"
Nana ta dan numfasa tace "Jalila nifa damuwata naji Abba yana batun akawo kudin Aurena, Allah yasa ba dana Yaya Jawwad za'a hadamin ba, nan da wata hudu da 'yan kaifa kenan"
Nana takarasa maganar kaman zatayi kuka
Jalila tace "to meye aciki? Keda rabin rankine fa Mahmud zaku kasance inuwa daya"
"To Jalila karatun fa? Kinsan Mahmud a kasar waje yake nasa karatun tayaya abun ze yuwu?"
"ze yuwu mana, kicigaba da naki karatun a can riba biyu, Allah sarki Rayuwa hajiya Nana za'a zama matan Aure, bari in lissafa yaushe zaki haihu"
Hade rai Nana tayi "Ke Jalila komai sekin sako wasa a cikine? Inamiki maganar serious kinamin wasa, ke yanzu akace za'ayi aurenki nan da watanni hudu kin shiryane? Ni yanzu ma meyasa Abba bece a hada dake ba"
Dariya Jalila tayi tace "gidan Ahmad yana bauchi, shi yana aiki a maiduguri, ni ina karatu a kano tayaya kike zaton inyi Aure yanzu, se nagama tukuna"
Wayar Jalila tafara ringing, ta kalli Nana tace "Excuse me, let me pick the call"
Nana ta daga mata kai, Jalila ta amsa wayar tareda yin sallama
Amsamata yayi sannan ya dora da "Babyna kwana biyu kin gujeni you are not picking my calls, ina fatan ba laifi nayi miki ba?"
Cikin siriyar muryarta na shagwaba tace
"Ohh no ni bakamin laifi ba, bana dan jin dadine kawai, amma yanzu Alhamdilillah naji sauki"
"Ya salam amma baki gayamin ba, yau zan shigo kano dama shiyasa na kiraki, in kin amince zanzo in ganki"
"Babu damuwa my one, ina fatan in ganka nima am missing you"
"Like serious, karkisa inyi Ihu attention din mutane ya dawo kaina"
Murmushi tayi tace "ba sekayi ihuba, aini yakamata inyi, kwana nawa zakayi a kano?"
"zanyi sati daya Insha Allah, zanyi wani assignment ne"
"Shikenan Allah yakawo ka lafiya"
"Ameen my queen, bazaki tambayi Antynki ba?"
Dan yamutsa fuska Jalila tayi tace "Ainasan tana lafiya tunda najika haka"
Murmushi yayi yace "Queen da alama kinada kishi sosai, anyway sena shigo, idan nazo da wuri zaki ganni yau, in ban shigo da wuri ba se Allah ya kaimu gobe"
"to shikenan Allah ya kaimu, take a good care of your self"
"Ok Baby i will Insha Allah" ta katse wayar, Nana ta zuba mata ido tana kallonta, Jalila tace "Madam lafiya kuwa?"
"Lafiya mana, nina kasa gane inda kika dosane, gane lamarinki se Allah mutum baya taba ganeki, gaba daya rayuwarki zigza ce"
Sosai Nana tabawa Jalila dariya tace "rayuwartawa ce zigza, lallai ma Nana bakida dama, Rayuwata normal ce kaman ta kowa"
"A'a ban yadda ba, Allah yasa ayi miki aure kafin ayiwa Yaya Jawwad"
"Ba Ameen ba, back to sender muguwa kawai"
"eh amma ni kikayimin fata saboda son kai"
Wayar Jalila ce takuma daukar ruri, ta kai hannu ta dauka tana dubawa taga Hanan ce dan haka ta kashe wayarta.
Tunda suka fara tafiya Abba beyiwa Jawwad wani gamshashen bayani akan wannan tafiyar ta bazata ba, yanason yayiwa Abba magana amma yakasa duk sunyi shiri Jawwad na driving,
"Dama Aliyu akwai wadda kakeso kaki ka gayamin kabari ake kokarin auramaka wannan yarinyar?"
Tambayar tazowa Jawwad a bazata, kuma idan yaji Abba ya ambaci sunansa na gaskiya kai tsaye haka, alama ce ta
he is so much serious.
Jawwad ya dan sosa keya yayi shiru
"yaka sosa kai kayi shiru? Kamin bayani mana"
Cikin kame2 Jawwad yace"Amm.. Dama Abba, ai..."
Abba yacce " Jawwad da farko sister dinka Jalila tagayamin inyi bincike akan yarinyar nan Naja, tacigaba da gayamin hakan, sannan taki gayamin komai game da Naja, sedai cewa inyi bincike, tacigaba da nunamin cewa kunyarka da kawaicinka baze bari ka nuna abunda ke ranka ba, na dauki maganarta serious nafara kokarin bincike, ina kan binciken ne, Mahaifin Hanan ya kirani yamin magana akan in dai dagaske kana son 'yarsa yabaka dama ka fito, wanda ni bansan da zancen ba, nayi kokarin in zauna da kai muyi maganar kafin ta kai ga haka Jalal yazo ya sameni har gurin aiki yamin bayani akan alakarka da' yar gidan general Abdurrasheed, sannan ya daukeni ya kaini inda aka gayamin komai akan Naja, bantaba tunanin Mamanka zata zaba maka mace irin wannan mara kamun kai a matsayin mata ba, Jawwad meyasa baka gayamin abunda ke ranka ba, kabari nakusa gangancin saka rayuwar ka a hatsari? "
"Abba nasam bazaka zabamin abunda ze cutar dani bane, banason bijirewa umarninka dana Maama, shiyasa na amince"
"Nasan da wannan Jawwad, amma dukda haka a matsayin mu na iyaye yanada kyau mudinga baku zabi, ba wai bin son zuciyarmu da tirsasamuku akan abunda bakwa ra'ayiba, yana da kyau kadinga fa
an ra'ayinka ba laifi bane naji dadin kokarin yimana biyayya dakayi, Allah yayi maka Albarka yakara ha
amin kanku, Allah ya shirya mana ABDUL JALAL dukda kasancewar halinsa amma yadamu da lamuranka sosai, yadda yazo ya sameni kaman zeyi kuka, Alhamdilillah nayi mamaki naga abubuwan sa sun fara raguwa, yafara dawowa hanya, ya rage rashin ji"
"hakane ya rage sosai makuwa, abokiyar fadansa keta kokarin sashi a hanya ai"
"Wa kenan?" Abba ya tambaya
"Jalila mana, tanata kokari akansa, kuma naga inga masa nasiha koba duka ba yana
an dauka"
Abba yace "masha Allah, at least kaga an samu improvement, itama General Abdurrashed yamin magana, yace akwai abokin
ansa dayake sonta, wai Ahmad sunansa kowaye?, yabiyo ta hannunsa a nema masa Aurenta, amma nace na bashi wuka da nama shima babanta ne, duk abunda yaga dace yayi"
Jawwad yai murmushi yace "hakane Abba, lokacin da mukaje kaduna yamin zancen nima, yace shima mutumin sojane yana da kirki sosai"
"Hakane, Allah ya tabbatar mana da alkhairi yamuku zabi da abokan zama nagari" Jawwad a zuciyarsa yace Ameen.
Hanan taita kiran wayar Jalila amma Jalila taki dagawa, saboda bataji dadin abunda Hanan tayi mata ba, sako Hanan ta turimata kamar haka
"Assalamu Alaikum, Am very sorry my twiny, nasan na miki laifi kiyi hakuri dan Allah, Yaya Jawwad yazo kano shida Jalal, yamin bayanin komai abunda ke faruwa, kiyi hakuri so dakuma kishinsane yasa namiki haka, sannan naji Yaya Abdallah yana maganar Ansamawa Jalal aiki za'a gama interview ranar laraba amma har yanzu bejeba, you have to take action"
Jalila nagama karantawa ta kira Hanan, seda Jalila ta kira sau biyu sannan Hanan ta dauka tace
"'yar rainin hankali inata kiranki kinki
agawa, amma da kikaji batun ABDUL JALAL harkin kirani"
Jalila ta hade rai kaman Hanan na ganinta tace "ke banason wulakanci, ai banji dadin abunda kikayimim ba sam wallahi"
"Nasani amma ai nace kiyi hakuri, you won't understand how far my loves go on your brother, inasonshi ina kishinsa shiyasa na shiga damuwa, inata addu'a dai amma ina cikin damuwa Queen"
Tausayin Hanan yakama Jalila tace "ki kwantar da hankalinki kinji my twiny, komai ze wuce kece zaki zama matar Yaya, ina nan ina tayaku da Addu'a"
"Masha Allah, Allah yabiya ki da mafificin Alkhairi Jalila, bazan iya biyan kaunar da kike nunamin ba"
"bakomai Sister na, nace are you serious Jalal beje interview din nan ba?"
"Wallahi dagaske nake miki, hala aikinma kekisa aka samo masa?"
"to meye naki aciki nason kisani, nice nagayawa Daddy ya samo masa, kuma be isa ya watsamin kasa a ido ba zan sameshi, seyaje interview din nan"
Dariya Hanan tayi tace "wai zaki sameshi irin Mum din nan tasa, kai lamarinku din nan yana birgeni wallahi, kowa da guntun taurin kansa dan Allah duk yadda kukayi ki gayamin dan wallahi....
Katse wayarta Jalila tayi jin Hanan zata fara mata bare2.
Ilham shiryawa tayi takanas ta tafi gidansu, domin taji abunda yakamata suyi, dan ita ta riga ta karaya da lamarin nan bata tunanin akwai nasara dan kullum Jalal kara bau
ewa yake, babu alamar ze sakko.
Tayi sa'a ummannata tana gida, suka kule a daki kaman yadda suka saba in Ilham
in tazo.
"Umma nifa najiki shiru ya'ake cikine? Na
ora mata sata amma Jalal bakiga rashin mutuncin dayayi min ba, wallahi son yarinyar nan yake, kincemin zakije Nijar gurin wani malamin amma shiru kullum abubuwan kara tabarbarewa sukeyi"
Umma tace "ke nayi maganar zuwa nijar, munyi waya da mutumin na masa bayanin komai, amma budar bakinsa wai yayi bincike akan yarinyar indai inason a yimin aiki akanta zan bashi dubu
ari biyar, nikuma ina naganta? Banida ita bani da wata kadara da zan sayar in bashi wannan uban ku
in, dan haka nakoma gurin wanda muke zuwa tun farko, shikuma yacemin baze iya aiki akanta ba sedai a kara watsa rayuwar Jalal"
"to Umma batun Auren namu fa?"
"shima za'ayi ne amma yace mu
an kara hakuri"
"umma kenan, mu kara hakuri fa kikace? By mistake idan Asirin ya karye gaba
aya kuma yaya zamuyi?"
"bazeyiba, malamin yabani wannan tabbacin ki kwantar da hankalinki burinmu seya cika, sena wulakanta shi shida uwarsa hada uban nasa, bana yafiya ga wanda yamin laifi"
"to shikenan Umma, Allah yasa, ni bari in tafi, zan
an tsaya inyi siyayya".
Dogon wandone a jikin Jalila da riga, dan haka ta
akko katon hijjabinta me hannu tasaka ta fito part
in Jawwad taje tana tsammanin ganin Jalal a can amma baya nan, rabonta da shiga gidansu Jalal kuwa harta manta, direct ta nufi gidansu Jalal, amma tarasa ina zatayi tasan dai be dace ta tafi part dinsa nemansa ba, fasawa tayi ta juyo tanufo gate zata fita itakuma Ilham ta shigo.
Tsayawa sukayi suna kallon kallo itada Ilham, ha
e rai sosai Ilham tayi tareda yin tsaki tazo zata gifta gefen Jalila ta wuce, caraf Jalila tasa hannu ta riketa ta janyota gabanta suna fuskantar juna, a fusace Ilham tace "ke dalla malama meye haka? Meyasa bakida tunani ne?"
Jalila taja wasu seconds tana karewa kwayar idon Ilham kallo sannan tace
"banida tunani kam, dole ki fadi haka, kinsan ba'a tabani a zauna lafiya, dan haka sekinyi hakuri da duk abunda zaki gani har se kin biya abunda kikayimin"
Hararta Ilham tayi takuma kokarin rabawa ta wuce ta barta, amma Jalila takuma shan gabanta tace
"Ilham nasani tsawon shekaru ina bata miki rai, kinyi alwashi daban2 akan ganin bayana, baki taba nasara ba se wannan karon da kika
ora min sata, to bari kiji in gayamiki wani abu dabaki saniba, babu abunda zakiyi a rayuwa ki rama abunda nayi miki, na riga nagama dake Ilham, kuma Wallahi Jalal baze taba aurenki ba, nagaya miki dama muddin kudirina yayi karo da naki sena watsa naki, kudirinki akansa yaci karo da nawa na watsa shirinki watsawa ta har gaban abada zanso ingaya miki wani abu daya kamata ki sani amma ban saniba ko kinason ji"
Kallonta kawai Ilham take batareda tayi magana ba, Jalila ta
ora tace
"Ranar da Jalal ya kwanta a Asibiti, kukazo duba shi keda Mahaifiyarki kisani idonsa biyu yaji duk abunda kuke fa
a, dan haka ki cirewa ranki cewar burinki ze cika, Na riga naganoki Ilham tuntuni shiyasa nayi miki illa inda ba wanda ze gani, na illata shirinki bakida wata dama data miki saura, damarki
aya shine ki jajirce kicigaba da jarraba sa'arki kozaku daidaita"
Jalila takarasa maganar tana mata wani mugun kallo sannan ta juya tayi ficewarta, gaban Ilham ne ya shiga dukan hamsin2, kaddai Jalila dagaske take, amma to in hakane da yaji aida ya
auki mataki, "kai karyane bejiba, koma yaji wallahi seya Aureni, se burin mahaifiyata yacika"
Ta shige cikin gida da sauri hada tuntube.
Maama takasa zaune takasa tsaye, Naja batasan budurin da'akeba dan lokacin da Abba yayi wannan maganar bata nan tafita yawonta, harta dawo Maama tarasa ta inda zata fara mata bayani.
Jalila na fitowa taga Jalal ya dawo a mota, yana kokarin shiga gida, ganin da yayi ta tsaya ta ki tafiya ta kura masa ido yasan akwai magana a bakinta, tsayawa yayi agaban ta yayi parking, yana tsayawa ta zagaya inda yake,
age mata gira yayi alamar meke faruwa?
an kallonsa tayi tace
"daga ina?"
"kin aikenine?" ya tambayeta
"Ohh No Allah yabaka hakuri"
Yace "Ina Jawwad ne? Na duba baya nan ban san inda ya tafiba?" hade rai tayi itama tace
"ka duba shi mana, kokabani ajiyarsa ne?"
Kallonta yayi, wato ta rama kenan
Yace "A'a ban baki ajiyarsa ba"
"dama.." sekuma tayi shiru
"Dama me?"
"inada magana ne"
"fadi ina jinki"
"toka fito daga motar mana"
"In fito kuma? Gaskiya ni yunwa nakeji, zuwa zanyi in kwanta, naje neman Abinci narasa me zanci, dama in kin bawa Jawwad nake ci nima amma yanzu baya nan nasan bazan samuba"
"Hmm to kace Ilham tabaka mana"
Hade rai yayi sosai yana Kallonta, sunkuyar da kai tayi tana dariya kasa2
"Yi hakuri, ai yanzu mundena fa
a ka jirani a part din Yaya Jawwad zan kankaro maka kanzo in za kaci" tayi maganar tana dariya, tana matukar kyau idan tayi dariya, gya
a kai yayi ta juya ta tafi, yabi bayanta da kallo harta shige gida, sannan yaja motar ya shiga da ita gida.
Gida takoma taje ta
akko masa breakfast
in Jawwad da yatafi beci ba, dayake da zafinsa a cikin flask, tana zuwa ta tarar dashi a zaune a palourn Jawwad yana jiranta, ta shiga tayi sallama amma be amsaba, seda tazo kansa ta tsaya takuma yimasa sallama ya
ago ya kalleta ya amsa a hankali, ta ajiye tray din tace
"Yana daga hakkin musulmi akan musulmi in yayi sallama ka amsa masa, kadinga amsa sallama please"
Shiru yayi yaki kulata, Jalila tarasa wane irin miskilin mutum ne Jalal, koma tace
an rainin hankali kana masa magana yana jinka amma yayi maka banza dan tsabar wulakanci,
ta aje masa Abincin ta zauna a kujerar dake kallonsa. Ta danne fushinta
Ya hada Abincinsa yafara ci, can yace "Me ya kai Alqur'ani dana baki hannun Ilham?" yai tambayar kamar bashi yayi ba
auka tayi" tabashi amsa a takaice
"Ya'akayi ta
auka baki hanata ba?"
"Ina bauchi aka aikota taganshi shine ta
auka"
Bekuma cewa komai ba yacigaba ds auna loma, can Jalila tace
"Ya akai kasan yana gurin ta?"
Kallonta yayi ya danyi murmushi
"in kinaso in dawo miki dashi, yana gurina, amma bakiga abunda na ajiye a cikiba ko?"
an yatsina fuska tayi sannan tace
"Nifa tsawon lokacin da yayi a gurina banga komai a ciki ba"
"zan dawo miki dashi kikuma dubawa"
"to naji zan duba"
Ya cigaba da cin Abincin sa, can ta
an nisa tace
"An baka aiki ance kaje interview kaki why?"
agowa yayi ya kalleta, "dama nayi tunanin kece kikasa aka nemamin wannan aikin, tayaya ina shaye2 zakice asamomin aiki a hukumar dake yaki da shaye2, amfanin me zanyi ko nima so kike a kamani?"
"calm down let me explain, mezesa in so akamaka? da hakane naso akamaka da nasa an ka maka kaida abokinnaka jeje ai"
agowa yayi ya ha
e rai kaman be taba dariya ba
"Am sorry banyi hakan da wata manufa ba, sedai inkana aikin na farko ze rage maka yawan damuwa, sannan ze sa ka kara kokarin kadena shaye2 kaima, at least in kana da gurin zuwa ze kara dauke hankalin ka daga kan Shaye2"
Zuba mata ido yayi yana tunani daban2 akanta, ta damu dashi dayawa, she's so simple and calm, matsalarta kawai taurin kai da rashin kunya, Amma tanada zuciya me kyau.
Tsarguwa tafara yi da kallon dayake mata tace
"Ya dai?"
"meyasa kika damu dani haka?"
Shiru tayi dan bata san mezatace masa ba, basarwa tayi tace
"dan Allah kaje interview din nan karka watsamin kasa a ido"
"Senayi shawara" yabata amsa
"shawara kuma, dan Allah mene kuma na wani shawara dan Allah Yaya Jalal kaje please karkasa inji kunya" da shagwaba takarasa maganar
Bude baki yayi tareda yin murmushi kaman karta dena magana
"Nine Yaya kuma yau, yarinyar bakida kunya fa"
"Aida
inma dan muna fada ne amma yanzu mundena fa
a, dan Allah kaje ba dan halina ba, kaji Yayana
an gidan daddy abokin Yaya Jawwad, badan halina ba" murmushi yayi ya
an girgiza kai yace
"Aikuwa kinsan indan halinkine bazaniba, innayi tunani zan gaya miki"
"to Allah yasa inji alkhairi"
Be amsaba ya kai hannu ya dauki cup ya kai bakinsa amma jikinsa yafara rawa yakasa kaiwa
"lafiya menene kuma?"
Ajiye cup din yayi, yai shiru yana rintse ido"
Da sauri ta mike ta nufi inda yake tana fa
in "Subhanallah meyafaru?"
Dagowa yayi idonsa yayi jawur yace
"Gi.. Giy..... Giya,.... Giya zansha, ita nakeson sha"
"giya kuma? Meyasa zaka sha giya?"
Numfashi yake ja ya mike tsaye ya nufi hanyar fita, idonsa yayi jawur jikinsa se rawa yakeyi da sauri ta sha gabansa
"dan Allah Jalal karka sha giya, meyasa idan kuma kasha ka bugu daga nan ka mutu mezaka cewa Allah? Dan Allah karka sha kayi hakuri zaka ji bakason sha"
Tureta yayi ze fita, takuma tare kofa tana masa magiya, yasa hannu ya hankadata jikin kofa ta bige kafa
a ta fa
i a gurin shikuma ya fice kaman wani horrorn dayake bukatar jini.
Godiya mara iyaka ga members na kungiyar mu me tarin Albarka Perfect writers association, Allah yakara ha
a kanmu.
Abdul Jalal Novel Fans
kaunarku a ruhina take, inajin dadin comments dinku hada wakokin da'ake reramin
Masu bina private suna min comment kokuma bani karfin gwiwa, da masu biyoni suna neman littafina da masu karantawa wanda bansansu ba ina godiya Allah yasaka da alkhairi Allah yabar kauna.
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
What's app only 07063065680.
*ABDUL JALAL*

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
_*Story, &writing*_
_and edited_
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Jalila ta bugu sosai, ta rike hannunta tana rintse ido saboda azabar zafi, shikam yasa kai ya fice yabar dakin.
Ta dade a gurin a zaune, sannan ta mike ta koma cikin gida tana yamutsa fuska.
Su Jawwad kam har la'asar sannan suka isa Bauchi, Abba yakira daddyn Hanan a waya yagaya masa sun karaso, aka turo wasu sojoji sukazo suka tafi dasu har estate din, Ba Jawwad ba har Abba seda yayi mamaki irin tsaruwar da estate din yayi sekace barrack duk inda ka juya sojoji ke shawagi a ciki, akai musu Jagora zuwa gidan daya kasance nan ne center.
A dankareren dakin Daddy akayi musu iso, da murna daddyn Hanan ya tarbi su Abba, suka gaisa yai musu barka da zuwa, seda suka fara gabatar da salla sannan daddy yai umarnin akawo musu Abinci.
Wasu matasan 'yan matane dabasu wuce sa' anin su Hanan ba su uku suka kawo Abincin suka ajiye, tareda gaida Abba da Jawwad,
aya daga cikinsu wadda da gani kasan hutu da jin dadi ya ratsata tace
"daddy wannan yana matukar kama da Yaya Yusuf, ko shine sirikin naka?" Jawwad ya sunkuyar da kai saboda kunya
Daddy yace
"kaniyarki yusra, sarkin surutu, tunda kunkawo Abincin kukoma, ki gayawa Inna bakin sun iso zasu shigo anjima su gaisheta"
Murmushi Yusra tayi tace
"Yadda kace haka za'ayi daddy"
Abba yace "General wannan ma 'yar wajenka ce?, tana kama da Hanan"
"' yar wana ce, gaba dayansu yaran 'yan uwanane, Aini Hanan da Abdallah kadai Allah yabani, sekuma diyata Autar mata Jalila, Zuma kenan ga zaki ga harbi"
Gaba daya sukayi dariya, daddy yace su ci Abinci, Amma gaba daya Jawwad yakasa sakewa yaci Abincin nan saboda kunya "Sekace wani mace
, (ya kuke gani in goga Jalal ne?
yaseen cin abunsa zeyi)
addy yace "Jawwad baka cin Abincin nan fa, nifa banason fulatanci, ka saki jiki kaci Abinci"
Jawwad murmushi kawai yayi yakuma sunkuyar da kai.
Bayan sun kammala, Abba ya gyara zama sannan yace
"to Captain ni dai da farko Jawwad be gayamin yana soyayya da Hanan ba, har nayi masa zabin matar Aure nida mahaifiyarsa, Amma yanzu nagane akwai matsala a dangane da zabin da mukayi masa, kuma Kanwarsa Jalila da Dan uwansa suka sanar dani halin da'ake ciki har kaima ka kirani a waya kazomin da wannan zance na Jawwad ya fito in dagaske yake"
Daddy yace "Hakane, nima mahaifiyar Hanan dince ta sanar dani halin da'ake ciki, kuma gaskiya yarinyar tanada manema dayawa kuma ta nuna shi Jawwad din takeso, shiyasa nima nayi maka magana"
Abba yace "Hakane, Amma zangaya maka wani abu, inkaga zaka bawa Jawwad 'yarka a haka to shikenan, inkuma kaga baze yuwu ba semu hakura"
Daddy yace "ina jinka fadi muji"
Abba yace "kaga maganar gaskiya a yanzu a bangaren mahaifi Jawwad bashida kowa se Allah sekumani, sedai bangaren mahaifiyarsa, banida wa bani da kani, kani na
aya shine mahaifin Jalila kuma Allah yayi masa rasuwa tun Jalila nada shekaru biyar, kuma daga ni har mahaifinta babu wanda yasan suwaye dangin iyayenmu sakamakon suma gudun hijira sukayi daga garinsu, in kana ganin zaka iya bashi 'yarka a haka shikenan "
" Haba Alhaji Usman, Ai Jawwad ko
an tsintuwa ne babu abunda ze hana in bashi' yata indai yana sonta, yanada hankali ga nutsuwa da tarbiyya wannan ba abun damuwa bane ba, bari muje ku gaisa da Mahaifiyata semu karasa gidan Yayana, shi ze karbi kudin Auren"
Abba yace "Nagode kwarai da wannan karamcin naka general, Allah yasaka da alkhairi"
Daddy yace "tsakanina da kai babu batun godiya, bari muje".
Jalila takoma gida ta fara baccin dole saboda azabar zugin da hannunta yakeyi, se kusan la'asar ta tashi, shima hayaniyar Naja ce ta tasheta dayake ita Naja wani lokacin kaman banza haka take bata magana a hankali, ga hauma hauma kamar rainon gabuwa, wannan hargowar ce ta tashi Jalila.
Sannan da alamu har yanzu Maama bata gaya mata sakon Abba na tabar masa gida ba, dan har yanzu tana giginta da rawar kai, Jalila ta tashi tayi sallar la'asar tanemi abun zubawa a cikinta.
Shikuwa Jalal tunda yaje ya sha giyarsa yayi tatul wani nannauyan bacci ne ya kwashe shi be farkaba se magariba, ya shiga yai wanka yai sallolinsa, bayan ya idar ne ya dau wayarsa yakuma kiran Jawwad, wannan karon Jawwad ya dauka Jalal yace "wai dan Allah ina ka shiga ne haka? Tun safe ban ganka ba, na tambayi kanwarka tace bata san inda kake ba"
"Aiba bata nayi ba, kuma ba saceni akayi ba kaganni tareda Abba muna Bauchi"
"Bauchi kuma? Me ka keyi a Bauchi?"
"bazaka gane ba, sena dawo kawai akwai Labari"
Murmushi Jalal yayi, yadda yaji muryar Jawwad yasan yana cikin farinciki, Jalal yace
"To seka dawo din, amma tafiya ba sallama haka?"
"Nima ban san da tafiyar ba, babu shiri Abba yace inzo mutafi"
"to shikenan Allah yadawo daku lafiya"
"Ameen ya Allah" sukayi sallama
Bayan sunyi sallamane Yusuf ya shigo palourn daddy, Sallama yayi suka amsa gaba daya, Yusuf ya kalli Abba ya durkusa ya gaisheshi ya amsa masa cikin sakin fuska, ya juya ya kalli Jawwad ya mika masa hannu suka gaisa.
Daddy yace "Yusuf ga Abban Jalila fa"
Murmushi Yusuf yayi yace "Ai ina shigowa jikina yabani, ina kallonsa naga akwai alakar Jini, wannanne yayanta kenan sirikinmu"
Daddy yace "ya akayi kasani?" Yusuf yace
"Kai daddy yadda yarinyar nan ke fadarsa, ko kunya ba taji ranar inajinta itada Nawwara (matarsa) tanata yabonsa hada yi masa waka, kaf estate din nan ba wanda besan haidar ba ko ince Jawwad"
Gaba daya sukayi dariya, Yusuf yace
an uwa Allah yabaka wuyan
auka, dan wallahi Autar daddy fitinanniya ce, ga yarinta a cikinta" haka sukaita taba hira Yusuf yajanye Jawwad suka fice zuwa bangaren Inna.
Suka shiga da sallama, kamar kullum tana kan darduma tana lazimi, suka zauna a gefe suna taba hira harta idar, sannan ta juyo ta kallesu dan kura musu ido tayi, Jawwad yace "Sannu Inna"
"Yawwa
an nan, Yusuf wannan kuma ina ka samoshi, kar in fadi wani abu ace nayi rikici"
Yusuf yace "Inna Yayan Jalila ne"
Murmushin fuskarta ya fa
a sannan tace "Masha Allah, Nayi farincikin ganinka yarona, Kanwarka me kama da mairota da na dauka itace, ashe ba ita bace ba ina kabaromin me sunan larabawan?"
"Tana lafiya Inna, tace a gaisheki"
"Allah sarki yarinyar kirki me hankali, idan ina basu labarin kanwata se suyita lallabani wai kar in rikice musu da kuka, itakuwa kanwarka zama take muyita hira naita bata labarin wannan kanwartawa"
Yusuf yace
"zaki farako inna, dan Allah kiyi hakuri, kekowa sekin bashi labarin kanwarki, ko labarin tsofaffinki ba kyayi kamar ita, kimsan bakida cikakkiyar lafiya"
Jawwad yace
"A'a kabarta ta fada maybe hakan ze rage mata damuwa, tunda kaji haka akwai kyakyawar alaka a tsakanin su"
Yusuf yace "Ai intana wannan labarin nata daga nana zata fara kuka, kuma in tafada bata iya cin Abinci jininta ya hau sosai"
Sallamar Su daddy ce ta katse musu hirar suka amsa musu Sallamar amma banda inna da ko juyowa takasa yi.
Daddy yakaraso gabanta ya durkusa yace
"Inna ga baban Jalila, kuma sirikinki yazo ya gaisheki ne"
jinjina kai tayi ba tace komai ba, Abba ya zagayo gabanta ya durkusa gaba daya ta zuba masa ido ko kyaftawa batayi, tace
"Imamu ne? Imamu ina Mairona" cikin sanyin jiki Abba yasa hannu yakamo Hannunta ya rike a nashi a hankali ya furta "Innarmu.... Inna Hafsatu, Allah yasa kece, kece wadda Inna take bamu Labari Yayarta"
Fashewa da kuka tayi ta rungume Abba tana fadin
"Alhamdilillah nagaya musu, Amma sunki yarda suna ganin kaman rikici nane kawai, tunda naga yarinyar gurinka nasan tsatson Mairamunace, nasan zuwa yanzu ba lallai tana raye ba, amma ina son inga ahalinta"
Hawaye sharkaf a idon Abba yace
"Na dade ina bulayin neman ki Inna, Allah ya karbesu gaba daya, dasu da tilon
an uwana, ya mutu yabarmin 'yarsa Jalila se yarana biyu, ban taba tunanin Allah ze karbi Addu'a ta ba, yau naga dangin iyayenmu"
Gaba daya jikinsu yayi sanyi, kowa seda yayi hawayen tausayi, Abba yasha wuyar bulayi da yawo garuruwa ko Allah zesa yasamu wani nasa ashe suna kusa da juna, alakar yara ta ha
a amma basu saniba, Ashe shiyasa kamannin Jalila da Hanan sukayi yawa, hatta yanayin halayensu iri daya.
Abba yasa hannu yana gogewa Inna hawaye cikin zolaya yace "Kamanki daya da Innarmu, sedai duk babanmu yafi ku kyau"
Murmushi tayi tace "Ai shima
an uwana ne, kuma mairo tafishi kyau, Allah yayi musu rahama gaba
aya.
Nan hirar asali da tushe ya barke, nan da nan Labari ya kara
e estate din nan cewar ansamo dangin mairo kanwar Inna, nan da nan gidan yafara cika da dangi da 'yan uwa don ganewa idanunsu hakikatul Amri.
Daddy yace tunda hakane kadasu Abba sukoma yau, su
anyi musu ko kwana
ayane Inna taji
i kuma sannan suga' yan uwa.
Haka kuwa akayi, Abba yakira Maama yace bazasu dawo a yauba saboda wasu dalilai, ba wanda suka gayawa abunda yafaru, hatta Daddy be gayawa su Hanan ba.
Jalila takira Ahmad ya sanar da ita cewar baze shigo yauba, saboda yayi dare a hanya sedai zuwa gobe Insha Allah, seda suka sha soyayya sannan sukayi sallama gefe daya kuma hannunta se ciwo yakeyi, da wanine yai mata abunda Jalal ya mata yau da seya gane bashida wayo, shima
in dan yanzu bata son yawan fitina da shine saboda gaba
aya yanzu tausayi yake bata, da dane da seta rama. Amma to meyake damunsa haka? Lokaci
aya mutum ya rikice kaman wani me tabin hankali, yana zaune lafiyar Allah amma ya birkice lokaci daya wai seyasha giya.
Jawwad kasa boye farincikinsa yayi, seda ya kira Jalal a waya, yana
agawa Jawwad yace "My man kana inane?"
"Ina gida mana, ina zanje tunda baka nan? Wai yaushe zaku dawo? Tun dazu nake zuba ido amma baku dawo ba"
"Ai mu ba yau zamu dawo ba"
"Se yaushe?"
"Ai bazaka gane ba Jalal bansan yadda zan fasalta maka farincikin danake cikiba"
"Abba yaje nema maka Auren Hanan a Bauchi" Jalal yafada kai tsaye
Da mamaki Jawwad yace "ya akayi kasani?"
"Zuciya tace tagayamin"
"ban yadda ba dama can kasani kai shiru kaki gayamin, amma akwai saura ai"
"to gayamin inaji"
"Abba ya gano danginsu daya da
e yana nema"
Murmushi Jalal yayi yace "Alhamdilillah, na dade ina fatan hakan ya tabatta, kakarsu Abdallah ce Inna Hafsatu da Inna mairo take fada take bamu Labari ko?"
Cikin mamaki Jawwad yace "wai dan Allah ya akayi kasani?"
"Allah ne yasanar dani, dan Allah kadawo da wuri, ni bana jin dadi in baka nan"
"wai kana in dawo da wuri, kamanta in Allah ya kaimu next week zan tafi inda aka turani aiki"?
"kumafa hakane se yanzu nakejin babu da
i, amma Insha Allah hakanne mafi Alkhairi agaremu baki daya"
"Amma ni ina mamaki yadda akayi duk kasan wannan zancen ni ban saniba" dariya Jalal yayi yace
"Ba abun mamaki bane, kai dai seka dawo kawai
Seda suka gama hira da Jalal ya katse wayar, Jawwad yaji kaman ya kira Jalila amma ya fasa, dan yasan idan ya kirata farinciki seyasa yagaya mata abunda ke faruwa kuma Abba ya gargade shi akan kar kowa yasan wannan zancen a yanzu harse sun koma gida.
Maama tarasa ta inada zatayiwa Naja bayanin Abba yana bukatar ta bar masa gida, saboda tana matukar Jin tsoron Masifar Yaya Mairo, tarasa abunda yake mata dadi, yanzuma da Abba yayo waya seda ya jadadda mata baya son ya dawo ya tarar da Naja cikin Iyalinsa, tarasa ta inda zata fara harga Allah bazata iyaba sedai inya dawo shiya koreta da kansa, can wani bangaren na zuciyarta yake cemata banda ma ya raina miki hankali, ita Jalila dake zaune a gidan meyasa bece ta bar gidan ba, shekarar Jalila nawa a
gidan, se yanzu zece Naja tabar gida, indai Naja zata bar gidan nan to dole Jalila ma ta kama gabanta, Maama tayi kwafa tace
"Zaka dawo ka sameni, dai2 nake da kai"
Naja se iyayi take tana wasu irin abubuwa na ban haushi wai ita zatayi Aure, A gaban su Nana take waya da kawarta sunata shirye shiryen abunda zasuyi da biki, ba kunya Naja take cewa a mata booking na kayan mata na tashin hankali, masu tsada, se wasu irin lissafi takeyi, kala2 party da zatayi, da irin expensive clothes da zasu saka itada kawayenta.
Tagama wayarta su Jalila suna jinta, tana gamawa Nana ta tinstire da dariya,
cikeda tsarguwa Naja tace "ke Nana meye abun dariya haka?"
"A'a ni ba dake nake ba, mahmud ne yabani dariya a waya"
Itakam Jalila bata samu zarafin dariya ba tana fama da ciwon hannu, ko uffan ba tace ba.
Nana tagayawa Jalila Abba yace bazasu dawo yauba, Akwai abu me mahimmanci daya rikesu, Jalila a ranta taketa addu'ar Allah yasa abunda take tsamanni ne ya tabatta.
Washegari da safe Monday ce Jalila tace bazata makaranta ba, Dan haka Nana ita kadai ta tafi, tai kwanciyar ta tana bacci, Zahra takirata a waya tagaya mata zasuyi test karfe goma shadaya da rabi na safe, Jalila sam bata da niyyar zuwa makaranta haka ta tashi tana tsaki tayi wanka tasaka kaya, doguwar riga pitch da mayafinta se wata 'yar karamar Jakarta ta dauka, iyakacin Jakar nan ta dauki waya da kudi da
an abunda baza' a rasa ba sekace jakar roko,
Jalila Ta fito fuskar nan babu walwala,
ta tarar Maama na palour tana karyawa itada Naja, yanzun ma hirar bikin suke, Jalila ta durkusa tace
"Maama zan tafi school, yanzu aka kirani zamuyi test anjima"
Banza Maaman tayi mata taki kulata, dama batayi tsamannin Maama ta amsa ba, tayine dan hakan shime tarbiyar da Ummi ta dorata, ta mike jiki a sanyaye Zata fita Naja tace
"Aikin banza wai za'a school za'a tafi yawon gantali dai irin wanda uwale ta saba yi"
Maama tace "dan Allah kidena shiga harkar yarinyar nan shiyasa take kara rainaki"
ai kafin Maama ta gama magana Jalila ta waigo tace "ta Uwale tayi kyau, kekuma ki saurar kiga naki sakamakon, anzo an bararaje ana cin duniya babu a house, gara ki zage ki ciki kafin ki kara gaba, Akuya kawai"
Ashar Naja ta mulmulo zatayi Maama ta dakatar da ita, Jalila kuwa tayi ficewarta ranta bakikkirin babu dadi.
Maama tace
"kyaleni da ita, ki zuba ido zakiga matakin da zan dauka akanta"
Jalila na fita ta hango Mummyn Jalal
tareda Ilham da alamu wani gurin zasuje, da kaman ta basar tayi tafiyarta sekuma taga hakan be dace ba, dan rabonta da taga Mummy harta manta dan ko gidan bazuwa takeba yanzu, dan haka ta nufi inda motarsu take, Mummy tana kokarin shiga, Jalila da fara'arta ta karasa ta durkusa ta gaida Mummy, amma ga mamakin ta taga Mummyn tayi mata wani irin mugun kallo kamar bazata amsa ba sekuma ta amsa da kyar, Jalila taji ba dadin abunda Mummy tayi mata, amma ta dake ta mike tace "Mummy Adawo lafiya sekun dawo"
Mummy ta yamutsa fuska tace "Yawwa dama ina son ganinki kuwa, akwai magana me mahimmanci da nakeson mu tattauna dake, dan bazan saka ido abunda ke faruwa yacigaba ba"
Seda gaban Jalila yai mummunar faduwa, wannaan wane irin abune ita kowa ma laifi take masa, kowa ya tsanenta a fili tace "to Mummy Allah yasa ba laifi nayi miki ba? Zanzo Insha Allah, Adawo lafiya"
"Munafukar banza barauniya, me bin
an mutane, Akuya kawai"
Taji sautin maganar Ilham ta sauka a kirjinta saitin zuciyarta, dukda yadda maganar tayi tsauri tareda dukan zuciyar Jalila, amma ta danne taki juyowa ta kuma kallon inda suke, ta mike tacigaba da tafiya.
Jefa kafarta take ba tare da tasan ina take saka kafar tata ba, Hawayene yake bin idonta, Allah ya temaketa unguwar tasu se kayi minti goma babu wanda yazo ya wuce, kuma wajen karfe tara ne duk wasu sun riga sun fita, hakan yakara bata damar zirarar da hawayen ta son ranta, tana cikin tafiya ne taji ana mata horn kaman za'a kashe mata kunne, ita dai iya saninta ba a tsakiyar titi take tafiya ba gefen hanya ne, Amma an cika mata kunne da horn, banza tayi tacigaba da tafiyar ta.
motar aka sa aka sha gabanta, sannan yafito daga motar yace
"Bakya jin ina miki horn ne ? Sekace wata kurma, Kuma Se yanzu zaki tafi school karfe tara? Allah ya shirye ki, zo muje in ajeki ta nan zan wuce" ya dinga jero maganar daya bayan daya
Juyowa tayi ta kalleshi, ya saka farin yadine dukda kansa babu hula yayi kyau sosai, dan zata iya kirga sau nawa taga Jalal da dogayen kaya, kallonta yayi sosai yaganta kaman a birkice, hawayene a fuskar ta, idonta har yafara Ja, cikin tsiwa tana hararsa tace
"bazan hauba ai da can ba kai kake kaini ba, salon in hau motar ka, ka karasa karyani bazan hauba"
"hmm bazaki hauba ko? Bazaki hau motar mahaukaci ba, Dama interview din nan zani, Amma tunda bazaki hauba se inkoma kuma bazan kuma zuwa ba"
Cikin sauri tace "A'a yi hakuri zan hau, Amma dan Allah karkayi gudu dani" tafada hawaye na zubowa daga idonta
Gaba daya tausayinta ya kamashi, kome yasata kuka haka a titi, itada take da dakakkiyar zuciya? Abunda ze satana tafiya tana kuka ba karami bane ba
"bazan ba, a hankali zan tafi" ya fa
a a takaice
Ta bude motar ta shiga, shima yazaga ya bude ya shiga, ya kunna motar yai mata key, suka fara tafiya, ya kalleta yace "Kukan me kike?"
"bakomai"
"bana son karya fa"
Shiru tayi masa, ta maida kanta titi kyaleta yayi tunda yaga batasan fa
a masa, maybe is her personal issue. Suna cikin tafiya Jalal yayi parking ya kalleta yace "Zoki rakani zanci Abinci, banyi breakfast ba"
"Ni bazaniba, kaje ka dawo, nibana son ana ganinmu tare" ta fada tareda dauke kanta daga kallonsa
Ba tareda ya kalleta ba yace
"ohh yeah, be kamata adinga ganinki tareda
an iska mara tarbiyya ba, kar azata irinmu daya, bari yanzu zan
dawo"
Ta fuskanci haushi yaji, amma ta basar dan itama ranta a bace yake Befi 5 mintues ba ya dawo da leda a hannunsa, ya kunna motar suka cigaba da tafiya, yana tuki tana goge hawaye, sekace kurame, baya son ya kalleta yaga tana kukan nan, kukanta yanasa shi tuna lokacin da Umminta ka gudn abunda ze sashi kuka shida Jawwad, gani Jalila tayi ya canza hanya dan haka da sauri tace "A'a yanaga ka canza hanya?"
Be kalleta ba yace "Wani guri zaki rakani"
Zare ido tayi "saboda me makaranta fa zani, zanyi test"
"Nasan makaranta zaki, amma tunda kika shigo motata sekinje, don't mind club zamuje kawai, zan danyi caji"
tab ba ruwana, yan ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP, kunji Jalal dinku da rigima,)
Abba sunga "yan uwa sunga dangi, Abba be taba tunanin suna da wannan dangin ba, a hakanma sunada 'yan uwa a wasu garuruwan, A yau Abba yace lallai zasu koma kano saboda yanada ayyuka dayawa, se sun dawo ziyara ta musamman dan kara sanin juna, ba karamin farinciki akayi ba ganin Inna ta samu zuri'ar Kanwar ta, Ashe ba a banza ba Jalila da Hanan suke wannan kamannin.
A ranar su Abba suka dawo gida, tun Asuba suka taho, basu baro bauchi ba seda aka yanke watanni hudu, a matsayin lokacin Auren Jawwad da Hanan, sedasu Abba sukayi maganar Ahmad, Abba yace duk abunda daddy ya yanke dai2 ne, daddy yace "se Jalila ta kammala Makaranta ze bawa Ahmad, saboda yanayin karatunta dakuma aikin Ahmad
Su Abba se
karfe shadaya suka sauka a kano, Suka sauka da matukar farinciki.
Abba na shiga cikin gida yaci karo da Naja, a palour tana waya, bece mata komaiba ya wuce part dinsa,
Maama haushinsa takeji akan yace Naja tabar masa gida dan haka tana jin sun dawo taki zuwa inda yake, ya shiga part dinsa yai wanka ya canza kaya,
da kansa yaje ya sami Maama a daki Yace
"kina jin mun dawo amma kikasa fitowa kiga yamuka dawo? Shikenan ina miki Albishir Anbawa Jawwad Auren 'yar wajen Captain Abdurrasheed wato Hanan nan da wata hudu Insha Allah"
Wani mugun kallo tayiwa Abba tace "kamar yaya? Yaza' ayi akaiwa Naja kudin Aure dan munafunci kuma aje akaiwa wata, mata biyu ze Aura kenan, Jawwad din kwaya nawa yake daze auri mata biyu?"
"mace
aya ze Aura wato Hanan, maganar Naja na soketa an barmusu kudin Auren, zanje da kaina in samu iyayenta, Sannan kije ki sallami yarinyar nan tabarmin gida, tun kafin raina ya baci, bana kaunarta a cikin iyalina, kema yakamata kuje ku kara binkice akanta"
"Impossible" Maama ta fada da karfi
Masoya kaunar da nake kumu tasa nai muku dogon page gashi nan, senaji Comments dinku love you all
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
What's app only 07063065680.
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Cikide fusata Maama ke fadin "ni zakayiwa haka? Ka watsamin kasa a ido, a kai kudin Auren yarinyar mugama gayawa duniya za'ayi biki sannan kazo min da wata maganar banza, wallahi baze yuwu ba Jawwad bashida matar data wuce Naja
Abba yace
"Shikenan tunda ke zaki daura masa auren ai seki aura masa Najar in gani"
Ya juya ze fice tace
"Kuma wallahi bazata bar gidan nan ba, in dai Naja zata bar gidan nan to Jalila ma seta bar gidan nan"
Cak Abba ya tsaya ya juyo yace
"gida nawane, duk wanda yake ciki a karkashin ikona yake, idan yarinyar nan ta kai magariba a gidan nan to Wallahi zaku tafi tarene, ta tattara tabarmin gida nagaya miki, Jalila nan gidansune, nine mahaifin Jalila, Jalila bata da uwa ba uba seni, ita kuma wannan tanada iyaye dan haka ta koma gidansu, kowa ya zauna a gidansu" yana gama fadin haka ya juya ya fice.
Jawwad yana zuwa ya canza kaya, ya nufi gidansu Jalal amma yatarar baya nan, dan haka ya koma gida ya samu guri ya kwanta dan ya huta
A fusace Jalila tace
"Wallahi bazani club ba, ka tsaya in sauka in yaso kaje inda yafi club be dameni ba"
Shiru yamata ya cigaba da tukinsa, yana satar kallon yadda ta rintse ido tana masifa, ganin yaki kulata yasa a fusace tace
"Magana fa nake maka, wai meye haka?"
Fitooo yafara yi mata yana murmushi, Jalila ta kai karshe a kuluwa, ya dan kalleta yace
"meye kuma na tashin hankali bafa cewa nayi zamuje Kisha giya
ba rakiya kawai zakiyi insha mutafi"
Ta fuskanci so yake ya raina mata hankali, dan haka tayi shiru taga gudun ruwansa, ta dauke kanta zuwa ga kallon window tana share kwalla lokaci zuwa lokaci gani tayi tafiyar taki karewa dan haka takara fashewa da kuka me sauti Da sauri Jalal yace "Ke meye haka kuma? Nifa ba Jawwad bane da zakimin shagwaba"
Ido duk hawaye tace "Eh aida Yaya Jawwad ne yasan inada test bazemin haka ba, kuma Allah ya kiyaye in maka shagwaba in maka shagwaba ince nayiwa wa?" tai maganar tana harararsa da kumburarrun idanunta
Dan hade rai yayi yacigaba da tukin ba tareda yace komai ba itakuma tana hawaye.
Wata unguwa suka shiga, wadda kome za'ayiwa Jalila bata san inane ba, wani katon dogon gini ya nufa, kana ganin yanayin ginin da girmansa kasan kamfani ne, yana zuwa aka bude masa wani katon nannauyan gate ya shiga da motar, tundaga bakin gate din ma'aikatan ke durkusawa suna gaisheshi, dagani gurin kamfanine, yaje yasamu guri yayi parking, da sauri akazo aka bude masa motar ya fito,
ya zagaya yace mata
"fito"
"ni bazan fito ba, kawai ka maidani inda ka dakkoni"
"Wallahi in baki fito ba zakiyi biyu babu, kirasa test dinki kuma inki zuwa interview"
Kara hade rai tayi sosai ta bude motar ta fito tana zumbura baki, fuskarta tayi jawur, yayi gaba ta bishi abaya.
Babban abunda ya daurewa Jalila kai be wuce yadda taga duk inda Jalal ya ratsa ma'aikata manya da kanana suna girmama shiba, dan wasu har kasa suke zubewa suna gaida shi, Akayi sa'a in suka gaisheshi yana daga musu Hannu, Haka Jalal ya dinga ratsawa da ita tsakanin ginin katafaren gurin daya kayatu yadda yakamata, ko ina tsaf dashi, suna zuwa wata kofa sukaga wani mutum, ya girmi Jalal sosai ya mika masa hannu sukayi musabiha, mutumin yace "Yallabai yau akwai ruwa da kankara kaine a kamfani yau, rabonka da nan shekara nawa?"
Murmushi Jalal yayi yace "Ya aikin?"
"Lafiya kalau anata fama"
Jalal yace "Masha Allah hakan yayi kyau"
Daga nan yai gaba Jalila tacigaba da binsa, wata katafariyar kofa sukazo Jalal yasa hannu a aljihunsa ya dakko key yabude kofar ya kalli Jalila yace "Bismillah" tareda yi mata nuni da cikin gurin, jiki a sanyaye kuma a matukar tsorace ta shiga ta tsaya a bakin kofar tana rarraba ido, Office ne dankarere, sekace na hamshakin sarki ko gwamna, babu abunda babu a ciki, idonta ne ya sauka akan hotunan dake cikin Office din, akwai hoton shugaban kasa, gwamna da na sarki, sekuma hoton Daddyn Jalal, ta juya daya bangaren tangamemen hoton Jalal ne da Jawwad sanye da kaya iri daya sunyi murmushi an rubuta J&J global concept, sekuma hoton Jalal shikadai, ba karamin kyau yayi a hoton ba Ganin da Jalal yayi a tsorace take ta takure a tsaye, ya maida kofar ya rufe yasa mata key, kallonsa Jalila ta tsaya ta nayi a matukar tsorace hankali yace "muje ko?"
"ni ba inda zani, ka maidani makaranta zan tafi fa"
Baya kaunar wannan gaddamar ta Jalila dan haka be tsaya bata lokaci ba ya danko hannunta da karfi, hakan yasa ta saki wani uban ihu saboda zafi, hannun dayake mata ciwo ya rike, a tsorace ya cikata yana kallon yada tuni ta rike hannu tana Hawaye
"Meye haka? Sekace wadda nayiwa wani abu" ya fada adan gigice
"eh dole kace haka mana, jiya ba kai ka hankadeni na fadi akan hannun ba, yana min ciwo shine ka famamin" Jalila gaba dayanta shagwababbiya ce
Dan shiru yayi yana kokarin tuna abunda ya faru shi gaba daya ya dauka a mafarki abun ya faru ba gaske ba yace "Ok naji amma yanzu zauna"
Guri ta samu akan kujera daya ta zauna, yace "zan iya ganin hannun?"
"Bazaka gani ba" ta fada tareda janye hannunta
"Shikenan tunda kimce bazan ganiba, am sorry, ban san nayi miki ba, a tunanina mafarki ne, idan kinga na shiga wannnan yanayin kidena zuwa inda nake, kome zanyi karkiyi kokarin hanani, in bahakaba wataran zan iyayi miki illa"
Dan kallonsa tayi tace
"to meyasa kake hakan?"
"Nima ban saniba, haka kurum nake tsintar kaina a wannan yanayin, Jawwad ne kawai ya damu da halin da nake shiga, Mummy da ba damuwa tayi daniba, tana ganin kawai shaye2 danake ne ya janyo min hakan, dayawa idan nayi kokarin dena shaye2, kokuma raina ya baci, se in shiga wannan yanayin "
yayi maganar cike da damuwa, cikin tausayawa tace
" Ka dinga yawaita Azkar, kuma ka kulada ibada zaka dena jin abun insha Allah"
"bazan iya ba" ya fada kai tsaye
"Meyasa bazaka iyaba?"
"Har yanzu baki gama sanin waye ABDUL JALAL ba dukda yanzu kinsan abubuwa da yawa akaina fiye da iyayena, just keep praying for ABDUL JALAL, and I really appreciate your efforts on me, Thank you, Allah ya jikan Abee"
Jinjina kai tayi amma takasa magana,
Can tace "dan Allah me nayiwa Mummy? Na gaisheta dazu da kyar ta amsamim tace inje tana son ganina, Allah yasa ba laifi nayi mata ba?"
"meyasa kike tunanin laifi kikayi mata?"
Hawayene ya zubo daga idonta, shi Jalal har mamaki take bashi, kaman shan ruwa haka take kwararar da Hawaye, basa mata wuya sam tace
"Yanzu duk lokacin dana motsa ko nayi wani abu se ansamu wanda zasuce na musu laifi, kowa ya tsaneni komai nayi laifine, mutane kalilan ne suke sona A duniyar nan, daga masu kirana munafuka, se makira, barauniya, karuwa, Arniya se masu cewa uwata ta gudu ta banni, ba ataba barina inyi awa24 cikin farinciki se an samu me batamin rai"
Takarasa maganar cikin kuka muryarta na sarkewa, tasa hannunta biyu ta rufe fuskarta tana kuka me tsuma zuciya, Jalal jin kukan nata yake a kahon zuciyarsa, yaji gaba daya komai ya kwance masa, yace
" Kidena kuka mana, kin manta ke kikemin nasiha amma yanzu kike kuka, Allah baya mantawa da bawansa, Allah yasan halinda kike ciki, ni da nake gabanki a yanzu na isheki misali na isheki darasi, ba'a nasara ba tareda an sha wahala ba, kisawa ranki matakin nasarar kine kike takawa, duk wanda yayi miki gori a rayuwa ko ya cutar dake kisa a ranki kinfi shine, Allah yana son bayinsa masu hakuri, semene dan duniya batayi dake in har ubangijin da yayiki yanayi dake shikenan, kiran da Mummy tayi miki karki sake kije, bashida wani amfani na gaya miki"
Ya mike ya nufi wata katuwar drower ya bude, ya duba ya debo wasu takaddu yazo gabanta ya zube su yace "dauki wannan takaddun, ki dubamin abunda za'a iya nema a gurin, zanyi breakfast yanzu"
Yakoma kan kujera daya yazauna ya fara cin Abincin sa daya siya dazu, Jalila tasa Hannu tana duba takaddun, duk na makarantun da Jalal yayine, abun mamaki results dinsa sunnuna shi din kwarone, kuma duk an masa kyakykyawan yabo a jikin results din, daga ido tayi tana kallonsa yana cin Abincin sa hankali kwance, ba ita yake kalloba amma taji yace
"Ya dai kike kallona? Ko zakici ne?" girgiza masa kai tayi alamar A'a, tareda maida hankalinta kan Takaddun gabanta
Yace "Au Ashefa bazaki iya cin Abincin hannun dan iska ba, karkije na zuba kwaya a ciki ko?"
Shiru tayi masa yagama ciye ciyensa, ya mike yana kuma duba wasu takaddun, yaji muryar Jalila tace
"wai Inane nan?"
"Kamfanina ne?" ya bata amsa
Zare ido tayi, ya kalleta yace
"kina mamakine? Nawane mallakina, akan wannan dukiyar ne aka halakar da rayuwata, dukiya mugun abu me halakar da mutane, me haddasa gaba da kiyayya, me tafiya da Imanin ma'abota kwadayinta, Akan dukiya Mummy tayi cin amana tayi yaudara ta auri daddy,
Akan dukiya Mummy ta ajiyeni tayi tafiyarta lokacin da nake bukatar taimakon ta,
Akan dukiyar akabada kwangilar ruguza rayuwata,
Akan dukiya Mummy ta rabu da mutane dayawa, Akan dukiya da daukar fansa aka halakar da rayuwata,
Ilham da mahifiyarta suna son su dauki fansa akaina ne su gaje dukiyar dana mallaka, itakuma Mummy takasa fahimta, tunda suka kyalla ido sukaga Daddy yasayi kamfanin nan yabani, suka kasa nutsuwa, ke sheda ce, Kinsha kama Ilham na kokarin samin magani a Abinci, kuma ta dade tanayi min hakan saboda dukiya, Akan dukiya.......
Sekuma yayi shiru ya dafe teburin gabansa yayi shiru, gaba daya Jalila ta zuba masa ido, jin yadda yake sarrafa magana daki daki ta sigar rarrashi da wa'azi, ko a mafarki in wani ya gaya mata Jalal ze haka karyatawa zatayi.
Yacigaba da cewa "Ban taba kukan babu a rayuwata ba, babu innemi abu in rasa ban taba ba, bansan talauci ba, Amma nidai wannan dukiyar da taza memin bala'i, gara ace talaka futik Mummy ta aura in tsira da mutuncina, A rayuwa bazan manta da mutanen dasuka soni dan Allah ba, family dinku mutane ne masu mahimmanci a rayuwata, kinga Jawwad na yadda in rasa duk abunda na mallaka saboda shi, Yana sona badan dukiya ta ba, duk abunda zamuyi baya sako lissafin dukiya ta, bayan Umminki da Jawwad ban taba zaton zan samu wanda ze tsaya akan lamarina ya damu dani kamar ki ba, bana manta Alkhairi, kinmin abunda banida abun biyanki, dukda bakida kunya, ga taurin kai da tsaurin ido, ga rashin kunya da iyayi, bazan manta yadda kike putting rayuwarki a risk saboda dan iska mara tarbiyya me kama da 'yan daba, dan daba yana godiya" ya karashe maganar yana kashe mata ido,
Murguda masa baki tayi ta dauke kai, ya danyi murmushi yace "Ai bazaki taba canza hali ba"
Ya kwashi takaddunsa ya mayar da sauran yace mata "Tashi mu tafi" ta mike tayi gaba yazo ya bude kofar suka tafi, sosai Jalal ya dingayiwa ma'aikatan nan barin kudi kaman besan ciwonsu ba.
Suna cikin tafiya Jalila tace "Amma meyasa baka zama a kamfanin, at least you will keep yourself busy zaka manta da wasu abubuwan" dan shiru yayi sannan yace
"Ta yaya ina cikin wannan halin zanzo inyi aiki, Akwai manager kamfanin nan dan abokin daddy ne shike kulada komai, duk lokacin danazo na zauna da sunan zanyi Aiki se wannan abun yasa meni, idan na birkice senayi barna sosai kafin in bar gurin, wani lokacin har illa nake wa wasu, shiyasa wasu ke kallon ko inada tabun hankali, kokuma illar shaye2 ne, rabona da gurin nan nafi shekaru goma, yanzun ma saboda takaddun nan nazo, kuma abun mamaki naga nashiga na fita lafiya yau saboda muna tare da ke"
"To Allah ya baka lafiya, Amma yakamata kanemi magani sannan ka dinga Addu'a"
Tasa hannu ta cire farin carbin counter dake hannunta ta ajiye masa tace "ka dinga Amfani dashi, ze temaka maka" Be iya cewa komai ba se kallon ta da yakeyi, har Jalila manta data bashi sekuma taji yace
"Thank you" itama banza tayi dashi taki kulashi.
Haka suka cigaba da dan taba hira har sukazo makarantar, zata bude tafita yace "tsaya, wai ke wannan ce jakar makarantar?"
"Eh mana" ta bashi amsa
"wannan ba jaka bace sekace Jakar tara kudin bara, ina litattafan karatun?"
"Jakar tara kudin maulace bata bara ba" Ji yayi kaman ya tuntsire da dariya amma ya fasa, yasa hannu ya dau Jakar ya bude jotter ce se biro da kudinta dari biyar se waya, yasa hannu a Aljihunsa ya dakko kudi yasamata ya mika mata, ta kalleshi "Ni inada kudi cire abunka"
"Fitarmin daga Mota ko insa lock inyi gaba dake wallahi" Hannu tasa tana kokarin cire kudin ta ajiye masa yace
"Bana kyauta amayarmin, karki bari raina ya baci fita ki barmin mota, mara kunya"
Ikon Allah yanzu suka taho girma girma cikin mutunci amma se wani korarta yake kaman rokarsa tayi, ta hade rai ta bude motar sannan tace masa "Allah yabada sa'a"
"Ameen" ta rufe masa motarsa tayi gaba.
Maama fa hankalin ta ya kai makurar tashi, idan tace zata tsananta maganar nan zata iya rasa Aurenta, dan haka ta nufi part din Abba dan ganin ta inda Zata bullowa Al'amarin, Amma ta tarar yayi ficewarsa, takoma daki tanata nazari, daga baya ta yanke shawarar gayawa Naja halin da'ake ciki, takira Naja dakinta ta sanarda ita abunda ake ciki, Amma bata gaya mata batun Abba yace tabar masa gidansa ba Aikuwa take Naja tafara ruwan bala'i "Harni za'a ciwa mutunci dan tsabar wulakanci da cin fuska, Akaimin kudin Aure in fara shiri sannan ace anfasa saboda tsabar rashin ilimi, wannan ai halin banzane da Jahilci" Maama na kokarin yiwa Naja bayani amma taki saurararta tayi ficewarta, taje ta kira Yaya mairo a waya tana kuka gaya mata, ai tun daga wayar Yaya mairo tafara surfa zagi ta inda ta shiga bata nan take fita ba ta cewa Naja gata nan zuwa gidan.
Jalila test kawai tayi ta dawo gida, dan har yanzu bata jin karfin jikinta sosai tanata nazari akan Jalal, mutumin daya mallaki wannan dukiyar mezeyi da wannan Aikin? Amma akwai ayar ta
mbaya game da Al'amuran nasa, wani lokacin har mamaki yake bata in yana abun Arziki kaman bashi ba, kuma babban abun mamakin dukda yadda Jalal yake wasa da ibasa, yake shaye2 hakan besa dukiyarsa rashin habaka ba, haka taketa tunani harta koma gida,
Amma abun takaicin tana zuwa gida ta tarar da wannan rigimar da akeyi, Hakan ya tabattar mata dasu Jawwad sun dawo, muryar Yaya mairo data jiyone yasa gabanta faduwa, dan sam bata kaunar matar nan, Jalila tana ta Addu'a ta shiga palourn, ta tarar Naja tanata kuka, yayarta sa'ada tana rarrashin ta, Maama tayi zugum Yaya mairo tana sirfa mata bala'i, Jalila tayi sallama ta maze zata wuce, Gaba daya suka dawo kanta da zagi da cin mutunci da tsinuwa, ai kawai tayi kamar kujeru ne kawai a palourn ba mutane ba, ta shige daki ta canza kaya abunta, tayi tunani a ranta muddin tacigaba da zama a yanzu, zasu cigaba da zaginta ne itakuma bazata hakura ba, dan ba shiru zatayi musu ba mussaman in aka hada da cin mutuncin iyayenta, dan data san abunda zatazo ta tarar kenan da bata dawo gidan yanzu ba, ta mike tasa hijjabinta, takuma zuwa ta ratsasu a palour tayi ficewarta tana jinsu suna ita ta haddasa komai ita tayi munafunci batabi takansu ba takara gaba. Tana fita motar Abba ta shigo layin dan haka tayi murmushi aranta tace "yau gidanmu akwai drama" ta tsaya tana jiran karasowar Abba, ya karaso kofar gidan yayi parking cikin fara'a tace
"Abba saukar yaushe?"
Shima cikin fara'a yace "Ai tun karfe goma muka dawo, na dan fitane nayi wani uzuri"
"Masha Allah, sannunku da Hanya, amma tunda na dawo ko Yaya Jawwad ban ganiba"
"Ina zaki ganshi dama? Yana can farinciki ne ya hanashi fitowa Jeki aiken da'akayi miki ki dawo Akwai albishir masu yawa, babyn Ummi"
Cikin murmushi tace "to shikenan bari inyi sauri in dawo" tafada cike da zakuwa, Abba ya shiga gida, se yanzu tafara tunanin ina zata? Kawai ta yanke shawarar zuwa gurin Mummy taji laifin da tayi mata, dukda Jalal ya gargadeta akan yin hakan.
Tana shiga gidansu Jalal ta tarar da motarsa, abun ba karamin mamaki yabata ba, Anya kuwa yaje interview din? Ta tambayi kanta, taga moyar Mummy dasuka fita dazu alamar sun dawo, haka tayita wasi2 harta shiga cikin gidan, palourn ba kowa tayi sallama amma shiru tasamu guri ta zauna akan kujera, wata yarinya da take musu aiki tacewa dan Allah tayiwa Mummy magana, seda Jalila tayi kusan mintuna goma shabiyar sannan taga Mummy ta fito, da fara'a Jalila tace
"Mummy ina wuni?" Mummy tace
"rike ina wuninki, na baya da kikayi ma sun isa, Allah ya amfana" nan take Jalila ta sha jinin jikinta, Mummy tasamu guri ta zauna ta dubi Jalila a wulakance tace
"Dama na kiraki naki dan inyi miki kashedi akan
ana, sannan in soke haramtacciyar alakar da take tsakanin ku" cikin rashin fahimta Jalila tace "Mummy haramtacciyar Alaka kuma?"
"Eh haramtacciya mana, ko ta halatta ne? Tunda yake jin maganar ki fiye da tawa ai dole akwai abunda ke tsakanin ku, da kike masa Ilham ma sheda ce"
Nan Mummy ta ware ta kwalawa Ilham kira, Ilham ta fito tana ganin Jalila ta ya mutsa fuska kaman me shirin yin amai dan taga kashi, Ilham tazo ta zauna tace "Mummy gani"
Mummy ta nuna Jalila tace "gata nan nace Akwai haramtacciyar alaka tsakanin ta da Jalal amma ta karyatani"
"Mummy ai kinsan ba mutunci ne da ita ba tunda bata san darajar manya ba, tarbiyya ta mata karanci"
Mummy ta gyara zama tace "Ina bukatar duk wata alaka dake tsakanin ki Da Jalal tazo karshe a yau, kiyi nisa da dana, ba ruwanki dashi kome ze aikata, ai ba fina sonshi kikayi ba, a palourn nan agabana kinsha kiransa mara tarbiyya, lattace, kuma dan rashin kunya seki lallaba kina kokarin kara lalata min shi bayan abaya duk fitinarsa ba Ruwansa da mata, Amma kina kokarin kizama se abunda kikeso shi zeyi ni uwarsa ban isa dashi ba seke?" Jalila shiru tayi ta sunkuyar da kai ko tari kasa yi tayi
Ilham tace
" Wallahi Mummy na sha ganinsu suna rungume juna, kuma har part dinsa take zuwa dakin sa, in karya nayi ki karyatani mana munafuka, Kuma...... Setayi shiru takasa karasawa, sakamakon saka idonta da tayi a na Jalal dayake tsaye ya harde hannunsa a kirjinsa, ba Ilham ba hatta Mummy seda ta tsorata,
cikin is da Izza yace "Kuma me? Karasa mana"
Zazzaro ido Ilham tafara yi, jin muryar sa yasa Jalila daga idonta sukayi ido hudu takuma sunkuyar da kai.
Yakara so cikin palourn ya kalli Mummy sannan ya maida idonsa kan Ilham yace
"ki karasa maganar ki ina jinki, ke dan baki da kunya har kin manta ke abunda kika dinga yimin abaya ko danni bana zuwa ina fada, wato kin manta lokacin da kike kawomin kanki har part dina in dare yayi ko?" zare ido Ilham tayi tafara kokawa da numfashi, bata taba tsammanin ze iya fadar hakan ya tona mata asiri ba
Ya kakkafe Ilham da, ido yace
"koba ayi bane?" kasa magana tayi se wani gumi data dinga jinsa yana ratsa cinyoyinta, ya maida idonsa ga Mummy yace
"Kinji kunya, 'yar cikinki cefa, yarinyar data dingayi miki biyayyar dani da kika haifa ban miki ba, ita kikewa wannan bakaken maganganun, meye da
annaki da za' a dinga, binsa, niba hankali ba niba tarbiyya ba, sedai abini ko asoni dan dukiya ta amma bani da abunda mace kamar Jalila zata bini sedai irinsu Ilham dabasu san ciwon kansu ba" gaba daya suka zubo masa ido, da sauri Jalila ta mike tayi hanyar fita, jin yana kokarin janyo mata bakin jini tana fita ya rufa mata baya,
Ilham tace "Wallahi Mummy Jalal karya yakemin, ni ban taba kai masa kaina ba, Mummy dan Allah kisa baki ya Aureni, wallahi Asiri tayi masa"
"ke dalla rabu dani niba wannan ne ya dameni ba, kina gani yake gaya min magana akanta, ashe har an samu uwar data haifi wadda zata mallakemin da, ya gayamin magana akanta? Baze yuwu ba wallahi, se na dau mataki akansa da ita kanta"
Ilham ma mikewa tayi tabi bayan Su Jalal dan ganewa idonta meze faru, ayita ta kare a yau.
Har suka fito harabar gidan yana kiranta taki tsayawa, seda yasa hannu ya fizgota sannan ta tsaya
"Jalila meye haka? Ina miki magana kina jina kinki tsayawa, uban me yakawo ki bance karki zoba dama?"
Cikin kuka tace "Dan Allah malam kadena min shouting, meye Amfanin abunda kayi? Zaka sa mahaifiyarka da kanwarka su kara tsanata, Mahaifiyarka tace batason ganina tareda kai, ko a hanya karka kara nuna ka sanni, bani ba kai, kayiwa mahaifiyarka biyayya kanemi Aljannarka, dama ba wani abune tsakaninmu ba mutunci ne da girmamawa tunda bata so shikenan "
Gaba daya idon Jalal yayi Ja, a hankali yace
"kince kowa yaje yayi rayuwarsa ko? Kinfison in kara komawa cikin harkar shaye2 kenan kaman yadda nake abaya? Ke Garkuwa ce a taredani me kike tunani idan kika barni, sanadiyar kasancewar ki tare dani yasa ina kara kokarin yaki da shaye2 da nake abaya, kina tunanin inkika min haka kin min adalci? "
" Kayi Rayuwarka inyi tawa, yafi adinga min kallon mazinaciya, zancigaba dayi maka Addu'a a duk inda kake, Amma bani ba kai ko a hanya balle a cigaba da zargina"
Tofa!
Masoya kaunar da nake kumu tasa nai muku dogon page gashi nan, senaji Comments dinku love you all
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
What's app only 07063065680.
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Juyawa tayi ta fice da sauri tana goge hawaye, Ilham dataga duk abunda yafaru tayi wani tsallen farinciki, amma da tuna irin tonon sililin da Jalal yayi mata dazu se taji jikinta yayi sanyi ta juya da sauri ta koma gida.
Jalal bashida zabi da ya wuce ya bar gurin shima kamar wanda kwai ya fashewa a ciki yakoma part dinsa, zuciyarsa kaman an kunna masa wuta saboda bacin rai, side bed dinsa ya kalla yaga Alqur'anin nan da kuma teddyn Jalila a gurin, a hankali yace
"do she really mean what she said, zata barni gaba daya, bani ba ita? Jalila why? karkimin haka mana, nasan ba'a kyauta miki ba, Amma kar laifin Mummy ya shafeni"
ya zauna a gefen gadon sa ya rintse ido, ya dinga tuno moments dinsu tare, da fitar da sukayi dazu, ji yayi kansa yana juyawa zuciyarsa ta masa nauyi, ya kunna sigari yafara sha, ya sha takai kara biyar amma beji yadda yakeso ba seda ya dakko merlot red wine ya sha ya fita daga hayyacinsa sannan ya yada kwalbar a gurin shima ya zube.
Ita kuwa Jalila seda ta samu guri a cikin flowers tayi kukanta ta gode Allah sannan ta nufi palourn gidan, tunda ta shiga ita dai taji Abba yana bayani yayinda Yaya mairo keta haya gaga, sam Jalila bata gane me suke fada danji take kaman zata fadi ta wucesu ta shige daki ba tareda ta kula kowa ba, tana zuwa ta haye gado ta ja blanket ta cigaba da kuka da kuma tunani, shikenan yanzu kuma kallon mazinaciya mahaifiyar Jalal take mata? Gaskiya tsakanin ta da Ilham se Allah yasaka mata, amma ba komai zata rama ne, zatayi wa Ilham daurin da bata isa ta kwance ba"
Jawwad ya farka daga baccin dayake cike da farinciki ya tashi yayi salla, sannan ya nufi cikin gida dan ganin Maama dakuma 'yan kannensa dan yasan zuwa yanzu sun dawo daga school. Yana fitowa manu direba ya shigo harabar gidan da mota, ya jira manu yayi parking Nana ta fito daga motar kallo daya zakayi mata kasan a gajiye take, se jefa kafa take kawai tana ganin Yaya Jawwad ta yalwata murmushinta tareda fadin "Oyoyo mutan Bauchi, Ashe kun dawo?"
"Mun dawo Nana, ya school din? Naganki ke kadai ina Jalila?"
"Yaya Jawwad kasan Jalila manyan kwarine, yau bataje school ba, amma ancemin angan ta dazu ta shiga zasuyi test"
"Shikenan mukarasa ciki, yau Akwai Albishir masu dadin gaske, muje in gaida Maama tukuna" suka jero tare zuwa cikin gida.
Abba yace "Hajiya mairo ban yanke wannan hukuncin dan cin mutuncin ki kona zuriyarki ba, sedai dan hakan shine masalaha
ga yarona, idan baki saniba yaka mata kikara sa ido da bincike akan yaranki, Amma dana san haka abun yake, da tunda fari ban yadda da batun hada Auren nan ba, nasamawa Jawwad wata yarinyar itama Naja, taje Allah ya hadata da rabonta dan binciken danayi akanta gaskiya bazan iya bari Jawwad ya aureta ba"
Yaya mairo tace "dama dai can ka shirya cin mutuncina nida yarinya ta, amma inda arziki da mutuci ita daudar gora ai a ciki ake shanyeta, koma me take aikatawa silar Auren ai sekaga ta shiryu"
"Hajiya Mairo, da abunda ze yuwu ne da na hakura anyi auren nan amma baze yuwu ba, kuyi hakuri, sannan Naja ta koma gidan mahaifinta ta zauna"
Maama da tun dazu batayi magana ba tace
"Dan girman Allah kayi hakuri mun yadda ya auresu su biyu ma bakomai, amma idan akayi haka kaman amci mutuncin gidanmune"
Abba yace
"Ni ban Janye batun Auren nan dan cin mutuncin wani ba, amma da abunda ze yuwu ne dana hakura anyi, zanje in samu mahaifinta muyi maganar, dan ba dake ma yakamata muyi wannan zancen ba"
Naja kam se rusa uban kuka takeyi
"Dan Allah ku kyale masa dansu, sekace shi kadaine namiji, kokuma mijin gold ne? Banda kaddara me zatayi da wani Jawwad mutum sam be waye ba waishi Ustaz, dalla kidena kuka kiyi rayuwar ki kamar kowa, ki manta dashi"
Sa'adah ce ke wannan maganar cikin fitsara da rashin kunya, Abba ya mike yana kokarin bar musu palourn su Jawwad suka shigo jin hayaniya yasa
Jawwad yace "Abba lafiya kuwa?"
"Rufe mana baki kasurgumin munafiki daga kai har ubannaka da waccan makirar jarababbiyar, kun shiga kunfita kafasa Auren yarinyata dan ku kunya tamu a duniya to ta Allah ba taku ba, Matsiyatan banza dana wofi hadda wai tabar gidan nan dadinta tanada gidan uba ba'a titi take kwana ba"
Yaya mairoce ta wangale makogaro taketa zazzaga rashin mutunci san ranta, ta kalli Naja tace
"Jeki kwasomin kayanki mu tafi, Nina gayamiki sekin samu wanda ya fishi, Azzalumai kawai"
Maama ke kokarin kwantarwa da Yaya mairo hankali ta hanyar cewa
"Yaya dan girman Allah kiyi hakuri, zan shawo kan matsalar nan, dan Allah"
Naja tace "ba wani shawo kan matsala, ni bana son karya irin wadda kika saba yi, an kaimin kudi kin lallaba kun hada kai ze auri wata, kuma ana kokarin yimin sharri wallahi Allah ya isa ban yafe ba aikin banza kawai"
A harzuke Jawwad yace
"Wallahi kika kuma zagarmin uwa sena wanka miki mari, baza'a Aureki dinba, waze Auri mace irinki ace itace uwar yaransa, Kika kuma zagarmin iyaye sena bata miki rai"
Aikuwa Yaya mairo tayi kansa ta hanyar cewa
"Rufemin baki mara mutunci, har kanada bakin magana, iyayennaka ba kananan mutane bane, masu baki biyu, matsiyacin ubannaka dan Allah ya bashi Arziki ze wulakanta munida yarana"
A fusace Nana tace "A'a kinga Yaya mairo dakata, ubanmu fa ba sa'anki baneba, Maama ce 'yar uwakki dan haka kuje kiyi keda ita, da kike kiran ubanmu matsiyaci ya gama muku komai, dawainiyar ku ba wadda baya dauka yayi muku rana, da tsiyar tasa da kike fada ya muku rana ya maganta muku abubuwa dayawa, meye ba' ayi muku a gidan nan, wani abunma ku sata sann.........
"Ke Nana rufemin baki, Yaya mairon Sa'ar kice? Maama ta katse ta,
Jawwad juyawa yayi ya fice, dan a rayuwarsa baya son tashin hankali sam,
Nana tace "Allah sarki Jalila baiwar Allah, dukda abubuwan dakike mata Maama nasan Jalila bazata taba kallon tsabar idonki takira ki da makaryaciya ba, yau sega wanda kikeso din suna zagin ki, dama Allah ai ba Azzalumin sarki bane, musamman Naja tazo gidan nan danta kori Jalila, ga reshe ya juye da mujiya ai, bata kori Jalila ba, bata auri Jawwad ba kuma ita an koreta"
Nana tai wucewarta zuwa daki ta barsu a tsaye cirko2 suna cigaba da masifa.
Nana na shiga dakin ta tarar da Jalila ta kima bargo akanta tanata bacci duk hayaniyar nan baccinta take, Nana ta tatttaro kayan Naja ta fito mata dasu palour ta ajiye,
Tace "ga kayanki nan, daga nan bama bukatar ki a dakinmu"
Ta juya takoma daki tasa key, ta barsu da Maama a gurin.
Jawwad sam ransa ba dadi, bangare daya yana cikin farinciki, bangare daya kuma ransa a bace yake ya tafi dakin Jalal domin suyi hira, yagaya masa halinda ake ciki, Amma abun haushin yana zuwa ya tarar da gogan yayi mankas baccin sa kawai yakeyi, dan dafe kai Jawwad yai ya zauna ya tattare kayan shaye2n gefe daya, ya zauna a gefen gadon Jalal, yana kallonsa garin da dan sanyi sanyi ga fanka ga A. C Amma Jalal gaban goshinsa se zufa yake, Jawwad ya dan girgiza kai, tareda fadin
"Allah ya shirye ka dan uwa" sannan yasa hannu ya daddaki pillow da Jalal yake kai, a hankali Jalal ya bude ido ya saukesu akan Jawwad ya mayar ya lumshe idonsa, Jawwad yace
"Jalal ka tashi kai salla" dan karamin tsaki Jalal yayi yace "nika kyaleni please"
"haba Jalal bakayi salla ba, ka daure ka tashi mana"
Juyawa Jawwad baya yayi ya rungume pillow se ya tuna maganar Jalila
"Inkaana Ibada, kana Addu'a Rage wasu Abubuwan"
Sekuma ya danyi juyi ya mike da kyar yaje yai wanka da Alwala yazo ya gabatar da sallar Azahar da la'asar, fuskar nan tasa murtuk kaman be taba dariya ba.
Jawwad ya dinga masa hira yana bashi labarin abubuwan da suka faru a Bauchi, da dramar da aka gama yi a gidansu yanzu, Amma se ya lura sam hankalin Jalal baya kansa yayi zurfafa a tunani ne, lokaci zuwa lokaci ya kanyi tsaki.
Jawwad yace "Jalal wai me yake damunka ne? Ina ta magana hankalin ka baya kaina, se faman tsaki kake, menene?"
Ajiyar zuciya Jalal yayi sannnan yace "Bakomai don't mind me"
"ban yadda bakomai ba, ka gayamin please"
"Am serious bakomai, kawai yanayin ne bayamun dadi"
"to Allah ya sawwake, Amma Jalal kwana biyu ina ta murna ka dena zuwa club, shaye shayen ma kaman ka dena amma nazo na tarar kasha giya, haba Jalal why"
Dan shiru Jalal yayi dan yanajin muddin baze rabu da wannan damuwar ba akwai yuwuwar yakoma ruwa tsundum, dan maganganun Jalila sunyi matukar tasiri a zuciyarsa, a fili yace
"Am sorry Jawwad, ina bakin kokarina, kasan wani lokacin halinda nake shiga idan ban shaba, Amma Insha Allah very soon zan dena gaba daya"
"to Allah ya amince"
Daga nan Jawwad ya lallaba Jalal ya jashi suka fita zaga gari da nufin ya debe masa kewa.
Seda aka gama wannan tarzomar aka gama su Yaya mairo suka tafi sannan Allah ya nufi Jalila da tashi daga baccin da take, ta kalli Nana tace "Nana meyasa baki tasheni ba? Gaskiya na sha bacci tunda na dawo na kwanta se yanzu na tashi"
Nana tace "Mhmm ke kinta bacci bakisan drama da'akayi ba yau"
"Tame fa?" Jalila ta tambayi Nana irin bata san meyafaru ba,
Nana ta labarta mata komai, Jalila ta jinjina kai ita babban abunda ya bata mata rai be wuce yadda Nana ta gaya mata irin cin mutuncin da suka dingayi wa Abba ba, hatta zagin da sukayi wa Maama yabata mamaki, bata taba zaton zasu yiwa Maama hakaba saboda yadda take kyautata musu.
Nana ta gayawa Jalila cewar tunda Abba ya shige daki da wannan abun yafaru ko Abinci be ciba, ba karamin tausayin Abba ne yakamata ba takara tabattar da Yaya mairo daga ita har Yaranta basuda tarbiyya dan haka Jalila salla kawai tayi ta shiga kitchen ta dora Abincin dare saboda Abba ya samu yaci.
Sunkuma waya da Ahmad ya gaya mata yauma tayi hakuri abubuwa ne sukayi masa yawa shiyasa baze samu zuwa ba, Jalila ta karbi uzurinsa saboda yanayin aikin nasa.
Jalila ta shirya Abinci me rai da lafiya, bayan sallar magariba ta kaiwa Abba nasa har daki, Amma da mamakin ta ta same shi cikin fara'a, yace "'yar gidan Abba Girki akayi min haka ne?"
"Eh Abba, gashi nan kaci ka koshi sannan inzo inji Albishir din da zakayi min"
Yai murmushi yace "Ai Albishir din bana kine ke kadai ba, ki kira womin sauran' yan uwanki muci Abincin tare"
"to shikenan Abba yadda kace haka za'ayi"
Haka kuwa akayi taje ta kira Nana, ta wuce dakin Jawwad dan kiransa, Amma Jawwad yanata rubuce2 shikuma Jalal yanata babbakawa cikinsa hayaki.
Dauke kanta tayi kaman bata ganshi ba tace "Mutanen Bauchi, Yaya Jawwad ko kanemeni ko?"
Haka nan jin muryar ta yasa gaban Jalal faduwa har yake kokarin boye sigarin hannunsa
Jawwad yace "nina isa, dazu na shiga cikin gidan amma na tarar ana fitina shiyasa na tafi"
"to shikenan, Abba yace in kiraka duk tare zamuci Abinci saboda Akwai Albishir daze mana"
Jawwad yace "Allah Auta, wane Albishir zeyi mana?"
"Ahh kajika ai kai yakamata in tambaya, tunda tare kuka dawo"
"to shikenan gani nan zuwa" Jalila ta mike ta fice, Sam Jalal beji dadin wannan dauke kan da tayi masa ba, Jawwad yace "Jalal zo muje"
"A'a jeka seka dawo" Jalal ya bashi amsa, Jawwad yace
"Wallahi baka isaba, tashi muje, Abban bakonka ne? Yakamata muje tare"
Jawwad ya takurawa Jalal, badan yaso ba ya bishi, suna shiga palourn Abba Idon Jalal akan Jalila yafara sauka, tana sanye da riga da skirt na Atamfa, kaman ajikinta aka dinkasu cif dasu, tayi parking din gashin ta, ta kashe dauri ba kwalliya a fuskar ta amma tayi kyau matuka, bata kalli inda Jalal yake ba suka cigaba dayiwa Abba surutu ita da Nana, Su Jalal suka Zauna, Jalal suka gaisa da Abba, Abba yace Jalila zubawa su Jalal Abincin mana"
Ba tace komai ba ta fara zuzzuba musu Abinci, dakin yayi shiru suna Cin Abinci se surutun Nana dake tashi, gaba daya Jalila takasa sakewa taci Abinci saboda tsabar kallon da Jalal yake mata, bakowa ze gane ita yake kallo ba amma ita tasan ita yake kallo, shi kansa ba iya cin Abincin yake ba jujjuya cokali kawai yakeyi, Jalila tace "Abba ka gayamana Albishir din naka, nifa duk na kagu inji"
Abba yayi murmushi ya kalli Jawwad yace
"Jawwad gaya musu mana" sunkuyar da kai Jawwad yayi yana murmushi, Abba na yayi murmushi sannan yace "Na canza maganar Auren Naja da Jawwad, zuwa Jawwad da Hanan, nan da wata hudu Insha Allah"
Wata irin Ajiyar zuciya Jalila tayi, Nana tace "dama ni zuciya ta tabani, Masha Allah, Allah yasanya Alkhairi ya nuna mana lokacin"
Jalila tace
"Abba ni na rasa abunda zance gaba daya, mungode Allah daya sa ka gano abunda nake ta maka nuni, Abba Allah yasaka da alkhairi wannan aini akayiwa ga Yayana Kuma 'yar uwa ta, Amma shine Yaya Jawwad baka gaya mana ba, itama Hanan bata gayamin ba"
Abba yace "Itama Hanan din bata sani ba ai, daddynta be gaya mata ba, sannan babban Albishir na biyu shine; Kakar Hanan itace yayar mahaifiyar mu, Inna Asma" au"
Da Sauri Jalila ta waiwaya gurin Jalal dan in bata manta ba sunyi zancen da shi, amma kawai ta basar tace "Abba tunda naje tabani Labari nayu tunanin hakan, Amma nayi shiru ban fada ba saboda bani da tabbas, godiya ta tabatta ga Allah"
Jalal yai karfin halin cewa "Abba kaga yadda Allah ke juya lamarin sa, a baya kayi ta bulayin neman danginka, ashe suna tare da kai baka sani ba, ina tayaku farinciki Abba, Allah yakara hada kan iyalanka"
"Ameen Ya Allah ABDUL JALAL, Amma naji dadin wannan Addu'ar taka, kuma zance ka gaskiya ne, na dade ina bulayin nemansu amma ba zato ba tsammani na samesu ta silar 'yar Auta ta"
Sukayi murmushi gaaba daya. Abba ya dora da cewa " munyi magana da daddynka, Jalal ranar Asabar Insha Allah zasu kawowa Mahmud kudin Aure, suma tareda na Jawwad za' a hada, gaskiya zanso a hada da naka, yadda kuka taso tare ga aiki ya samu kamata yayi a hada da kai gaskiya"
Dan guntun murmushi Jalal yayi wanda iyakarsa lebensa yace
"Abba Jawwad dai yayi, nikam se yadda Allah yayi, babu uba nagari da ze bawa
an shaye2 auren 'yarsa, koda za' a bani saboda dukiya ta ne"
Gaba daya tausayinsa seda yakama su
Abba yace
"karka damu kaji Jalal, babu wanda ze hanaka 'ya, kai mutumin kirki ne, wanda ya zauna da kai ne ze gane hakan, Insha Allah komai ze wuce, ka cigaba da Addu'a sannan ka dinga kokarin ka dena shaye2, babu abunda ze hana abaka' ya Aure" jinjina kai Jalal yayi yace
"to shikenan nagode Abba"
Nana ta dan zumbura baki tace
"Abba wai meyasa baza'a hada dana Jalila bane?"
Abba yace "Saboda ban gaji da ganinta ba"
"Auni ka gaji da ganina kenan?" Nana tai maganar kaman zatayi kuka.
Abba yace "A'a Munyi maganar da Babanta, yace; Abari ta kammala karatu tukuna saboda yanayin Aikin Ahmad din, nan da shekara daya ne zata kammala in Allah yasa zamu gani itama zan Aurar da ita ga Ahmad"
Gaba daya kunya ta kama Jalila ta mike tace
"nikam seda safenku Abba" ta mike da sauri ta bar palourn, gaba daya Jalal ji yayi kaman Abba ya masa yayyafin wuta a kirjinsa, shima ya mike yai musu seda safe.
Haka suka watse daga palourn Abba, babu wanda yabi takan Maama balle susan halin da take ciki, ta kule a daki ta rasa abunda yake mata dadi, bata taba zaton yaran yaya mairo zasu iya zaginta ba, gashi mijinta da yaranta ma sundena shiga harkar ta suna fushi da ita.
Koda Jalal ya shiga gida, part din Daddy ya tafi, yana zuwa kaman wani karamin yaro ya tarar da daddy yana aiki akan system, Mummy na gefe suna hira, yana zuwa ba tareda ya cewa kowa komai ba ya zauna kusa da daddy ya kwanta akan cinyar sa yayi shiru kaman mara lafiya.
Daddy yace "Jalal lafiya kuwa?"
Jalal yace "daddy Anmin screening da interview, an turani Lagos zanyi wata uku acan, Jawwad ze tafi nasa gurin Aikin next week Monday "
Daddy yace "Eyya shiyasa ka damu haka? Kayi hakuri kaji yaron kirki, yasa haka shine mafi Alkhairi a gareku"
Mummy tace "nifa gaskiya bana son wannan aikin da zeyi, meya nema ya rasa da ze tafi wani yawo daban"
Mikewa Jalal yayi tareda yin tsaki yabar dakin, ya koma Part dinsa, koda ya koma ya sauya kaya ya kwanta domin yayi bacci amma abu ya ga gara, juyi kawai yakeyi idonsa ya bushe, ta shi yayi zaune ya kurawa teddy dinta da carbin da ta bashi ido, abubuwa da dama na masa yawo a kwakwalwa, Espicially lokutan da sukeyi tare, yana kallon teddy ya tuna lokacin da take rike da teddy ga sweet abakinta tana dariya, yana tuna tsiwarta, kwarin gwiwa, tausayinta, nasiha da murmushinta, ya tuno maganganun Abba dazu wai za'a Aurar da ita ga wani AHMAD!!! gaba daya yaji kansa yana juyawa, yazama dole ya nisanta kansa da duk wani abu da zazesa ya dinga tunata, Baze manta Alkhairan ta ba, tunani yakasa barinsa dan haka ya mike ya fice daga gidan gaba daya.
Jalila ma juyi ta dingayi tana tunani da tausayin Jalal, tabbas Jalal abun tausayi ne, yana bukatar me jansa a jiki musamman yanzu da Jawwad zeyi nesa dashi, tana fargabar yakoma shaye2 kamar da, Amma a yanzu bazata iyayi masa komai ba, dan gudun kuma fadawa mummunan zargin da mahaifiyarsa ke mata. A takaice se gefin Asuba bacci ya dauke ta
Jalal be dawo gida ba se Asuba, yaje club ya kwana yana shan giya, seda yayi mankas, da Asubar ma bata sake shi gaba daya ba ya dawo gida cike da maye.
Yau tun bayan da Jalila ta dawo daga school, tayi waya da Ahmad ya gaya mata yau zezo, dan haka se shiri take domin tarbarsa.
Jalal tunda giyar ta sake shi, yai wanka ya shirya kayansa daze bukata a Akwati, yaje cikin gida yai sallama da Daddy, yaita saka masa Albarka tareda fatan Nasara, tunda Ilham taji batun yasamu Aiki ta hanyar Jalila, kuma zeyi wannan tafiyar akan Aikin, hankalin ta ya tashi, wai se yayi wata uku acan, to in baya nan tayaya zata cigaba da gudanar da aikinta akansa?.
Karfe biyar yagama shirinsa, saboda Jawwad ne ze kai shi Airport, ya sa hannu ya dauki teddyn Jalila da Alqur'anin nan da kuma carbin data bashi, ya nufi gidan su Jawwad, saboda so yake ya nesanta kanshi da dukkan wani abu daya shafe ta.
Amma abunda yayi tozali dashi bayan ya shiga gidanne yasa yaji tamkar jijiyoyinsa sun dena harba jini yadda yakamata.
Autar Ummi wato Jalila ya gani tayi kwalliya cikin wani dankareren leshi, tayi kyau matuka suna hira da Ahmad, kai da gani suna cikin shaukin soyayya, Jalal yaji wani Abu ya tsarga masa tun daga kansa zuwa tafin kafarsa, kirjinsa yai masa nauyi matuka A hankali yafara jan kafarsa dayake ji tamkar ba nasa ba ya nufi inda suke.
Idonsa Akan Jalila har ya karasa inda suke, Jalila ce tafara daga kai tana kallon sa, gani tayi kamar ya danyi rama, yana zuwa Ahmad ya miko masa hannu da nufin su gaisa, kawai Jalal ya daga masa hannu, ya zubawa Jalila idanunsa da sukayi jawurr wanda yasa hantar cikinta kadawa,
Ya ajiye mata Alqur'anin, a gabanta da teddyn, ya juya ya nufi hanyar fita
Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what's App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry.
Ina godiya da kulawa.
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
What's app only 07063065680.
Watpad @Ayshercool7724
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Shiru Jalila tayi ta kalli kayan daya ajiye mata sannan tabi bayansa da kallo har ya fice daga gate, din shiru tayi ta tafi tunani, Ahmad yace
"my queen, meya farune?"
Da sauri ta dawo hayyacinta tace "bakomai fa"
"Amma waye wanan?" ya tambayeta yana me kureta da ido, ta dan sauke numfashi tace "Yaya na ne"
"Yayanki queen, ba Jawwad ne kawai Yayanki ba?"
"Abokin Yaya Jawwad ne, dan haka Yayana ne kawai"
"Amma babu wani abu a tsakanin ku kuwa?"
"Meyasa kake min wannan tambayar? Ko baka yadda dani bane?"
"Ahh haba waneni ince ban yadda da gimbiyata ba, ina so ne in tabattar da abunda ke tsakaninku, dan da idonsa yana shaye2"
Ba karamin haushi maganar Ahmad ta bata ba, kenan shima yanayi, in ba yanayi ba, ba abunda idon Jalal yayi dayake nuna yana shaye2, dan haka tace
"baya shan komai, kawai bashi da son magana ne, baya kula mutane"
Kyaleta Ahmad yayi yaga alamar bata son zancen suka cigaba da hira, Jawwad ne ya fito ze wuce su Jalila ya tsaya suka kuma gaisawa da Ahmad dayake dazu sun gaisa, Jawwad yace "to sirikina zan iya ce maka se anjima, ni zan tafi kai Jalal airport ne"
Da sauri Jalila tace "Ina zashi?"
Jawwad yayi murmushi yace "Aiki mana, an tura shi Lagos, se lokacin biki inaga ze dawo, bari inje karyai ta jirana, kin san baya son jira, se anjimanku" Sukayi sallama da Ahmad ya fita.
Ahmad ya maida idonsa kan Jalila yace "Gimbiya naso a ha
a bikin nan hada namu, na kagu in mallakeki"
Murmushi kawai tayi amma hankalinta baya kansa, tanata zancen zuci ne, dayaga haka yace "queen naga kaman Akwai abunda yake damunki, bari in tafi semunyi waya"
Ta mike ta rakashi har bakin gate sannan ta dawo ta zauna akan kujerun tana nazari
"At least yakamata ace sunyi sallama da Jalal, tayi masa nasiha, Amma bata tunanin zata iya kuma rabarsa ba saboda mahaifiyarsa.
Jawwad ya ga sam fuskar Jalal a daure take, babu alamar walwala ko fara'a, Jawwad yai masa magana yafi a kirga, amma ko daya be bashi amsa ba, dan haka ya kyleshi suka cigaba da tafiya a haka kaman kurame.
Gajiya Jalila tayi da zaman tunanin ta mike ta tafi cikin gida, Nana tana zaune a palour suna waya da Mahmud,
"Nana waike dan Allah ba kya gajiya da wannan wayar ne? Kuyita surutu tun ana fadar gaskiya se an koma fadan karya"
Nana taki kula ta seda ta gama wayarta sannnan tace
"waike Baby an gaya miki kowa irin kine me tsarin tsiya, ke yadda ba kya son yawan waya kowa ma hakane, ai a rana inji muryar Mahmud sau hamsin bazan gajiba, musamman mu da muke distance relationship, ai Ahmad din nan ma ban wani yadda kina sonsa ba"
"Inasonshi sosai, amma hakan bashi ke nufin a dinga uzzuramin da surutu ba"
"Hajiya Jalila, kyaji da shi dai"
Hanan ca ta kira Jalila a waya, ta daga tasa a kunnenta
"hello Baby, 'yar uwata rabin jikina ashe Family dinmu daya Baby? Narasa inda zan sa kaina dan farinciki, dazu Abba yake gayamin kuma wai an kawo kudin Aurena da Haidar, Baby na rasa me zanyi dan farinciki"
Murmushi Jalila tayi tace "na riga ki ji ai, kiyi Azumi ki godewa Allah"
"queen na rasa inda zan saka raina dan farinciki, daddy yace zasuzo karbar kudin Nana, narasa yadda zanyi dan murna"
"haka Al'amarin ubangiji yake Hanan, yana juya komai yadda ya so"
"Hakane Queen, amma naji haushi da baza'a hada da nakiba, ni ina Jalal ne ma?"
"yaje interview din nan ai, an turashi lagos zeyi wata uku"
"Allah sarki bawan Allah, wallahi Jalila bana kaunar Aurenki da Abokin Yaya Yusuf din nan, in duniya da gaskiya Jalal ya kamata ki Aura"
Wani dogon tsaki Jalila tayi ta kashe wayarta, dan bata son Hanan ta bata mata rai.
Jalila ta mike har zata bar palourn taga Maama tazo ta wuce kitchen, gaba daya Jalila bata jin dadin yadda kowa ya fita harkar Maama, dukda abubuwan da Maaman tayi mata, Akwai lokutan da ta kyautata mata, dan haka taga be dace ta mata hukunci da laifin da take mata ba, dan haka tabita kitchen din, Maama na kokarin kunna gas Jalila tayi maza taje ta karbi lighter tace "Maama kawo in kunna miki, me zaki dafa?"
"barmin Abina zanyi"
"A'a Maama, tunda ba abunda nake ki barshi in dora miki"
Jalila ta karbi lighter ta kunna gas, dan jimm Maama tayi tana Kallon Jalila, yadda Jalilan ke Acting kaman Maama bata taba yi mata wani abu na bacin rai ba.
Jawwad suka isa airport yayiwa Jalal Sallama amma ya amsa masa a ciki, sam baya walwala, yasan halin Jalal baya son takura, tunda be niyyar gaya masa meke damunsa ba, ya ja Akwatinsa yayi gaba yabar Jawwad.
aka Jawwad ya taho yanata tunanin me akayiwa Jalal yake wannan bacin ran haka?
Bayan Jalila ta gana yiwa Maama girki, ta koma daki, ta dauki Alqur'anin nan tana ta jujjuyawa, Kamshin turaren Jalal yakeyi, hakama dan teddyn ta, tasa hannu ta ta dinga duba Alqur'anin nan page by page, amma sam bata ga komai a ciki ba, kodai Jalal dama yana son raina mata hankali ne kawai?
Shiru tayi ta tuna yadda taga yana yinsa bayan ya gansu tareda Ahmad, Fuskar nan tasa a daure babu alamun sassauci, tayi shiru ta cigaba da zancen zuci, ;yanzu ze tafi lagos bashi da kowa a can, babu me kula dashi, Allah kadai yasan meze aikata,
"kinfi so in cigaba da shaye2 na ko? Ke Garkuwa ce a gareni" ire iren wannan maganganun nasa da Maganganun Antynsa da take gaya mata tabata amanar Jalal ne yasa take tunanin Anya hukuncin data yanke yayi dai2 kuwa?
To Amma nikuma mutuncina fa? " gaba daya ta rasa me yakamata tayi? Yanzu tana gaya Hanan, tasan Hanan zata canza mata magana tafara kawo wani abu daban, dan haka tabar Abun a ranta ta cigaba da Yiwa Jalal Addu'a.
'yan kwanakin nan sam Abba ya dena shiga harkar Maama, har gara Jawwad ma yana zuwa gaisheta, Nana kuwa seda Jalila tasata a gaba ta nuna mata be dace ba abunda take yiwa Maama, wannan abunda yafaru tsakanin ta da Abba ne da kuma' yan uwan ta, sannan ta samu Nana ma take shiga sabgar Maaman, Abba ya gayawa Maama ranar Lahadi zasuyi baki, za'a kawo kudin Auren Nana, abakin su Nana taji batun haduwa da 'yan uwan Abba a Bauchi, ba tayi mamaki sosai ba jin ance su Hanan' yan uwansu Abba ne ba, sakamakon matukar kamannin dake tsakanin Jalila da Hanan, sedai taji haushin rashin sanar da ita da Abba beba.
Tun ranar Juma'a suke shirye2 domin bakin daza'ayi, Jalila ce jagorar girke2 da shirin yadda za'a karbi baki.
Gefe guda Jawwad yana ta shirye2 Ranar litinin shima ze tafi gurin nasa Aikin, ba karamin kulawa Hanan take bashi ba, da soyayya da kuma shagwabarta, yanayin yadda take nuna yarinta
a wasu bangaren ba karamin birge shi yake ba.
Kamar yadda aka saka ranar lahadi daddyn Hanan yazo Kano aka karbi kudin Auren Nana, itama lokaci dayane dana Jawwad dakuma Abdallah Yayan Hanan, ranar har mutan bauchi seda sukazo garin kano karbar kudin, da kuma kara taya juna murnar haduwar su a matsayin 'yan uwa. Jalila taji dadi da akazo hadda Hanan da Mummynta, Maama seda ta sha jinin jikinta ta raina kanta ganin manyan mutanen da sukazo gidan, Abun Arziki ya hadu dana Arziki, dangin Su Jawwad dana Su Jalal, Ranar anci ansha, kai ka dauka bikin Aure akeyi rana ce me matukar tarihi da wannan Ahali bazasu manta ba. Jalila sam bata samu kebewa da Hanan ba, saboda Hanan na manne da Jawwad, sam bata jin kunyar kowa take nuna masa soyayya.
Mummyn Hanan se mita take tace "Ni gaskiya naso a hada abun nan hada na Jalila, in aurar da 'ya' ya uku, amma in shirya da kyau, amma bakomai anata se nafi shiri ko Jalila?"
Ita dai Jalila sedai tayi murmushi ta sunkuyar da kai.
Duk yadda Maama take jin kanta take kuma jin haushin Auren Hanan da Jawwad boyewa tayi, Saboda sam bata da makusa, 'yar dangi ce, kuma' yar uwar dan tace, tana da kyau dai2 gwargwado kuma tana da Ilimi, yanayin kyau da gayun mahaifiyar Hanan ya isa ya nuna maka 'yar ta ma hakan take. Koda ta hasko Naja seta ga abun se A hankali, kuma tun abun nan da sukayi mata ta tabattar da Ko Auren akayi Naja zata iya wulakanta ta.
Da ire iren wannan tunanin yasa ta ajiye duk wani bacin rai aka shiga hada2. Tareda tsara yadda suke ganin bikin ze kasance, Ba laifi Mummyn Hanan ta saki jiki Maama, Sunyi hira sosai kaman sun saba, sannan suka tattauna akan yadda harkar bikin yaran nasu ze kasance. Se la'asar Suka tafi, mutanen Bauchi suka tafi, Su Hanan ma a ranar suka juya kaduna saboda Su Hanan suna jarrabawa, su kuwa danginsu Mahmud, suna kawowa Mahmud kudin Aure sukaci Abinci suka juya Borno.
Wasa2 sosai tunanin Jalila ya hana Jalal sukuni, da yafara aiki in ya tuna da ita gaba daya se yaji duniyar tayi masa zafi, yarasa inda zesa kansa, meyasa Mummy tayi masa haka? Idan yaji abun ya dameshi se ya tafi club yaje ya cika cikinsabda giya, dukda wasu lokutan yana bawa aikin da yaje yi mahimmanci, Sam Jalal bashi da sakewa da mutane, dan haka be saba da kowa ba, sedai yana girmama shugabanninsa na gurin aiki, girmamasun da yake besa sunga alamar ze bari su taka shi ba, inda yake burgesu yana maida hankali akan aikinsa sosai.
Duk lokacin da yaje Club mata da suke damun sa ne ga kuma shigar tsirara da suke yasa shi dakatar da kansa ga zuwa Club, idan yaji ba yadda zeyi se yayi shaye2 se yayi abunsa a dakinsa na hotel da yake ciki.
Amma duk da haka yarasa dalilin da yasa mata ke binsa, sedai in baze fito ba.
Hannah ce zaune akan kujera tana kwalliya, Sa'ada na kwance akan gado tana danna waya, dan dakatawa da kwalliyar Hannah tayi ta dan kurawa madubi ido, sekuma can ta daki kan mirror tace "Impossible baze yuwu ba wallahi"
Sa'adah ta waigo ta Kalle ta tace "lafiya kuwa?"
"Akwai matsala Sa'ada" Hannah ta bata amsa
"matsalar me fa?"
"Sa'ada ki kalleni ki kara, kimin kallon tsaf tun daga sama har kasa, ki kalli yadda nake gara kan maza, in taka wanda naso in wanke wanda naso, amma a hakan har rububina wasu suke, in sauke Ajina in cewa Jalal idan ya Aureni zan dena bariki, Amma ya watsa min kasa a ido"
Wani dogon tsaki Sa'ada tayi tareda fadin "Nina dauka ma wani mutumin kirkin ne, A she akan wannan mashayin ne, ni ba wannaan ya dameni ba a yanzu"
Hannah tace "Mutumin kirki ne mana, ki kalleshi kallon tsaf Sa'ada Namiji ne irin wanda duk wata mace zatayi burin Aure, shaye2 ne kawai matsalar sa, da farko da nakewa su Jeje aiki, nna zata zan samo kansa ta sauki ya yadda dani, Amma duk wata dabara da kisisina ta matan bariki nayi amma yaki amincewa dani"
"to kibi wani mana, ko shine kawai namiji?"
"bazaki gane ba Sa'ada, bakiga irin kirar da Allah yayi masa bane, kuma da kike ganinsa a haka, dukiya ce dashi kaman abun banza"
"Ya akayi kika sani, nasan dai babansa yana da kudi, amma shikam ko aikinyi ba shida shi" Sa'ada tayi maganar tana yatsina fuska
"Hmm to wallahi har ki mutu in ba wani ikon Allah ba, kaf danginku daku da abunda kuka mallaka, bazaku kaishi dukiya ba, yana da kudi da mahaifinsa yasa ake juya masa, Jeje yaso ganin bayan dukiyar nan shida mai gidansa amma abun be yuwu ba suka kare a prison"
Sa'ada ta tashi zaune tace "to ke yanzu meye abunyi, ni ban taba sani ba, kin san ya taba kusa tonamin Asiri ina zuwa club agaban babarmu"
Dariya Hannah tayi tace "Abune mawuyaci ya tona miki Asiri, bar ganinsa a haka, yasan abunda yakeyi, naje har gidansu na dana masa tarko, amma ga dukkan alamu ya tsallake shi, wannan karon zan masa tarkon da zan rike shi a wuya, be isa ya kuma subuce min ba"
"Yakamata kam, Amma ni nan tunanin yadda zan huce abunda abokinsa Jawwad yayiwa Naja nake, kiri2 yafasa Auren ta, yarinyar nan duk ta shiga damuwa"
"Allah sarki, to wai ya'akayi aka fasa Auren? Waye yaje yai mata gulma a gurin baban nasa?"
"ya za'ayi in sani, Amma da nafi kyautata zaton wannan munafukar kanwar tasa ce"
"Wace kanwar tasa ya'akayi tasan abunda Naja take? Ko dai itama tana ta bawa?"
"Ke bari, wata yarinyace yadda kika san boka haka take, ni dai ban san tana wani biye biye ba, Amma kina zaune in taso seta nemo waye ubanki koda ke baki sani ba, wai ita Jalila makirace ta bala'i, idan tace bata san abu seta ga bayansa, tasa Jawwad ya fasa auren Naja se kawarta"
Jin an ambaci Jalila yasa Hannah zare ido tace
"Kan bala'i ai nasan wannan yarinyar, tabdijan ni zan gaya miki makira ce, ke wallahi keda kike bariki tafi ki iya rashin mutunci, ke zata iya yuwu wa ita tasa aka hana, bari in gayamiki yarinyar nan tafiki bala'i, dan koni tasa min ido akan Jalal, ita take rusa min komai "
Cikin mamaki Sa'ada ta kalli Hannah tace" wai kin santa ne? "
" Nikuwa na santa, kuma nasan illar ta, munyi Arranging da Jeje mun gama komai, zamu sace Jalal ranar birthday din sa, idonta na kanmu, muka bugar da shi da giya ta shammace mu tasa aka dauke shi daga gurin, ke ina jin kishin cewa ita tasa aka kama Oga KB"
Zaro ido Sa'ada tayi cike da mamaki tace "Ke haba dai? Shikuwa oga KB yana me,duk iya kuri da gadarar rashin mutuncin nasa, yarinya ce fa karama"
Hannah tace "hmm ke dai bari, mace kenan, kaidin wata yafi wata, irinsu kuma sa'a ce dasu a rayuwa, kibi a sannu kawai"
"Tabdijan amma babu kama, dan bakiga cin mutuncin da muke mata ba mu da babarmu, kin san uwarta tsohuwar arniya ce, bakiga cin mutuncin da muke mata ba"
Hannah tace "Yawwa kuma ga cin mutuncin da tayi muku nan, kuma ta gama daku ba"
"Sosai makuwa ta gama damu"
"shiyasa wannan karon shirina ita da Jalal ne, dan bana ta wannan Ilham din dan wannan ba mace bace, wannan tafi hatsari, baze tsallake wannan tarkon ba a yanzu, na duba mashayar da yake zuwa ba adadi amma ance ya dena zuwa, duk da haka zan nemoshi"
Yauma duk da tarin farinciki da Jalila ta tsinci kanta a ciki yau, amma bacci ya kauracewa idanuwanta, jikinta na bata Jalal yakoma shan giya, da kyar ta samu bacci ya dauke ta, amma mafarkin Jalal a cikin wani yanayi na shaye2, yasata farkawa, gabanta na wata irin mummunar faduwa, wayarta ta dakko ta duba karfe biyu da rabi na dare, ga shi ita ba lambar Jalal ce da ita ba, tarasa mema zatayi gallery dinta ta shiga tana dubawa, tsofaffin ajiyayyun hotunan ta take dubawa, hotunan da sukayi da Jalal tun wani zuwa da Hanan sukayi, haka taita kallon hotunan, a haka har ta kawo kan hotunan birthday dinsa, cin karo tayi da wani hoto da'akayi harda Hannah a ciki, take gaban Jalila ya fadi, dan sam ta manta da Hannah, kuma barin Hanna ba tareda daukar wani mataji ba tamkar kashe maciji ne ba'a sare kansa ba a rayuwar Jalal.
A hankali ta ajiye wayar, ta sakko daga kan gadon ta shiga toilet tayi alwala tazo ta tada salla.
Ranar litinin Jawwad shima yayi nasa shirin tsaf domin tafiya Gurin nasa aikin dake birnin tarayya, Abba yayi masa Nasiha sosai tareda sa masa Albarka, haka ma bangaren Maama, tayi masa Addu'a da sa Albarka, dukda marin da Maama tayi masa akan Naja, hakan besa ya nuna mata har yanzu yana fushi ba, Bangaren Jalila kuwa har kuka tayi, saboda zatayi kewar Yayan nata sosai
Abba yace "Jalila kina kuka dan zeyi tafiya, kuda kwanan nan zeyi Aure gaba daya zasu bar gidan, su barki seke kadai"
Kara fashewa da Kuka Jalila tayi, Nana tace "Abba ka gani ko? Wannan yar taka ta fiye shagwaba wallahi"
Jawwad yace "haba babyn Abba, sekace ba jaruma ba, zan dawo ai kidena kuka"
Sukayi ta tsokanarta ita kuwa dagaske take kukanta.
Haka sukayi sallama da Jawwad shima yakama hanyar tafiyar sa.
Jalal yana waya da daddyn sa sosai, sannan suna waya ds Jawwad, suna shirye2 yadda biki ze kasance a tsakanin su.
Abban su Jawwad yana kasuwanci ne a tsakanin Kano da lagos, dan haka in yaje suka haduwa da Jalal.
Jalila Nason sanin halin da Jalal yake ciki, amma babu wata hanya da zata san hakan, dan haka taketa kokarin boye damuwarta.
Maama Allah ya temaketa Abba ya sakko daga fushin dayake da ita, sannan tunda abun nan ya faru Su Yaya mairo ko a waya basu kara neman Maama ba, abun ya dameta sosai dan haka ta shirya da kanta taje gidan su.
Tunda tayi sallama suka amsa suka shareta suka ki kulata, ita tayiwa kanta gurin zama, ta gaida Yaya mairo amma taki kulata, seda ta bata 'yan kayan data saba kaimusu, shine Yaya mairo ta dan saki rai suka gaisa, Naja ta gani a lullube tana bacci, Maama tace "Yaya, Naja ba lafiya ne?"
Kafin Yaya mairo ta amsa Naja ta fara magana cikin maye "Ni... Ni.. Ba... Wallahi baaaaani da.... Da lafiya, Shiyasa naiwa kaina caaajiii, baaaa danki yaki Aure na baaaaaa, wallahi....
Cikin tsawa Yaya mairo tace" yimin shiru dan ubanki, ciwon mara take, shine ta sha magani fiye da ka'ida"
Gaba daya jikin Maama yayi sanyi saboda babu tantama Naja maye takeyi. Shiru tayi takasa cewa komai, Naja ta cigaba da surutai, can kuma ta kwalla uwar kar, sega jini na gudu a tsakar dakin daga karkashin Naja.
Se bayan la'asar su Jalila suka gama lectures ta gaji matuka, haka kurum tun suna lectures takejin gabanta yana faduwa, da kyar ta tsaya aka gama lectures ta fito, danma manu direba ne yaje dakko ta daga school, abunda yabata mamaki be wuce ganin motar Hannah a gabansu ba, tana tsala gudun wuce sa'a, kuma da alama layinsu zata shiga, Jalila tasa Manu direba yayi parking a farkon layinsu, ta sauka ta shiga layin da kafarta, aikuwa tana zuwa taga Hannah tayi parking din motarta ta shiga gidansu Jalal, Jalila batayi shawarar komai ba ko tunani tabi bayan Hannah zuwa cikin gidan.
Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what's App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry.
Ina godiya da kulawa.
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
What's app only 07063065680.
Watpad @Ayshercool7724
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
A hankali Jalila ta cigaba da bin bayan Hannah, ba tareda ita Hannah ta sani ba, Hannah ta bude kofar babban palourn ta shiga, Jalila ta biyo bayanta amma ta tsaya a corridor yadda ba wanda ze ganta, Hannah ba karamin mamakin kyai da tsaruwar gidansu Jalal tayi ba, an kashe masa dukiya matuka, tun daga harabar gidan zaka gane mzauna gidan na cikin ni'imar ubangiji ta dukiya da yake bada ita ga wanda yaso a lokacin da yaga dama.
Koda ta shiga palourn ba kowa, seda ta tsaya ta karewa tangamemen palourn kallo, sannan ta jinjina kai tareda yin ajiyar zuciya, ta fara sallama, Mummy dake kitchen ta amsa tareda fitowa da jug a hannunta, suka gaisa da Hannah, Mummy na mata kallon rashin sani,
Mummy tace "bari in kira miki Ilham din, dan a zatonta kawarta ce" Hannah tace "A'a ba gurinta nazo ba, Mummy dan Allah Jalal fa?"
Mamakine yakama Mummy amma ta dake tace "Ai kusan watansa guda baya gari, yana lagos"
Hannah tace "Ai dole ya lallaba ya gudu lagos mana, Ina fatan mahaifinsa yana nan"
Mummy tace "lafiya kuwa?"
"Ina fa lafiya, ina son ganin mahaifinsa tunda shi baya nan"
"me mahaifinsa ze miki ne? Ki gayamin menene?" hakan yayi daidai da fitowar Ilham da alama fita zatayi, kawai taga Hannah, take gabanta yayi mummunar faduwa, kirjinta yafara dukan goma2, ta wani hade rai, ta karaso palourn cikin kasaita kaman gidan father dinta, tazo ta tsaya tareda kama kugu tanawa Hannah kallon da wacce kika zo?.
Kallo daya Hannah tayi mata ta dauke kai, tareda yin murmushi a ranta ta kalli Mummy tace "Gara in gayawa mahaifin Sa abunda ake ciki, na gaya masa wancan karon be dau mataki ba, shi namjine ke ba lallai ki iya daukar abunda zan fada ba"
"ki Fadamin bakomai ni mahaifiyarsa ce ai"
Hannah ta gyara zama, sannan ta kalli Mummy tace "wancan karon da nazo nayiwa mahaifinsa magana, nace yayi yadda zeyi a hadu mu rufawa juna asiri amma ba'ace min komai ba, nikuma asirina yana daf da tonuwa, Ina dauke da cikin Jalal na watanni uku a yanzu"
Da sauri Jalila tasa hannu ta toshe bakinta tana zare ido, gaba daya taji kafafuwanta suna rawa.
Hannah ta cigaba da cewa "muna haduwa da Jalal a hotels, kokuma idan yake night clubs, yasaba yimin ciki yace in zubar, wannan karon likita yace
rayuwata na shirin fadawa hatsari muddin na zubar da cikin nan, ga iyayena na kokarin ganewa, soyayyar Jalal ce tasa na bashi kaina, wallahi koya aureni ko nayi kararsa ya kula dani da dansa"
Hannah ta karasa maganar cikin kukan kisisina, kasa magana Ilham tayi saboda mamaki.
Hatta Mummy kasa motsawa tayi daga inda take, se ido da take bin Hanna dashi
Hakan yayi dai2 da fitowar Daddy sakamakon jin hayaniya sama2
"lafiya me yake faruwa haka?"
Kafin su bashi amsa, ya sauke idonsa akan Hannah, be manta ta ba, ya kalleta yace "yarinya lafiya kuwa?
Cikeda karfin hali Hannah ta korawa daddy bayani kamar yadda tayi wa Mummy
"Karya kikeyi, Wallahi Jalal baya neman mata, mata basa gaban shi, yana shaye2 amma be yadda da neman mata ba, Jalal ba mazinaci bane ba" Ilham tayi maganar ilahirin jikinta yana rawa
"Masha Allah, dukkan yabo ya tabatta ga Allah, kin fadi magana kuma kin karyata kanki Ilham, tunda kinsan Jalal ba mazinaci bane, ta yaya kika san ina bashi kaina?"
Jalila ce ke maganar cike da kwarin gwiwa, gaba daya suka juyo inda Jalila take, kanta tsaye ta tako har gaban Ilham ta Kalle ta ido cikin ido tace
"Nagode Allah, kinyiwa Jalal kyakyawar sheda, yadda baya neman mata nima ba'a haifi namijin da Jalila zata bashi kanta a titi ba, Wallahi Ilham kinji kunya, tun wuri ki canza hali, tun kafin ki kaini bango in miki abunda se kin kasa shiga mutane"
Ta juya ta kalli Hannah tace
"Ni na manta da ke a doron kasa, in ban manta ba haduwar mu ta karshe yafi shekara, katsam jiya kika fadomin a rai, da irin abubuwan da kike aikatawa, haka nan naji kasa sakewa, zuciya ta tanata bani wani abu zw faru, katsam akan hanyata naga motarki na kokarin shigowa layinmu, shiyasa na biyoki dan duk inda kikaje babu Alkhairi Hannah "
Gaba daya kan Hannah ya kwance bata taba tunanin zata hadu da Jalila a wannan lokacin da take shirin hurawa Jalal wutar da babu me iya kashe masa ba.
Jalila ta kalli daddy tace
"Wallahi daddy karya take yiwa Jalal, ba wani abu dayake tsakanin ta dashi, sema ita da take kokarin cutar da shi"
With full confidence Hannah tace
"Karya kike inyiwa Jalal karya, ina dauke da cikinsa ne, kuma wallahi wannan karon bazan zubar ba, kamar yadda yasaba sani ina zubarwa"
Cikin tashin hankali daddy yace "Jalal din nawa ne yai miki ciki? Kiji tsoron Allah, bana tunanin hakan ze faru, wancan karon akan wannan maganar yayi fushi har ya nemi ya bar kasar nan, narasa waye me gaskiya a tsakaninku"
Jalila tace "Daddy ka kyale ta taje ta kai duk inda zata kai, Kai ka haifi Jalal kasan abunda ze iya da wanda baze iya ba, kasan baya shakkar kowa, idan ya aikata baze ji tsoron gaya maka ba, Daddy karya takeyi wallahi, I dan ba haka ba, taje ta shigar da karar"
Sosai Jalila take kokarin kare Jalal, abunda yabawa daddy mamaki, dan agabansa ya sha ganin irin artabun da sukeyi da Jalal, amma wani tabbaci take da shi akan Jalal haka, kuma y'a kayi tasan Hannah?
Ilham kam harar Jalila kawai takeyi ji take tamkar taje ta maketa a gurin, sekace Jalal din ubanta ne, ita so take tayi amfani da wannan damar, a tirsasawa Jalal yin Aure, amma Jalila nata karewa.
Mummy tace "Waike meye haka? Ban hanaki shiga duk wani shirgi daya shafi dana ba, banda munafunci da son jin kwakwaf hada biyo ta kizo kiji me ze faru, kina.......
"Rufe min baki khadija, Kinsan meyasa take kokarin kareshi, meye da dannaki da kike wani kumfar bakin adena shiga harkarsa"?
Daddy ya kalli Jalila yace "Jalila a ina kika san wannan yarinyar?"
Jalila ta kalli Hannah tace "daddy nasanta a gurin birthday din Jalal ne, Kuma sannan"
Sekuma tayi shiru, "Sannan kuma me?"
Daddy ya tambayeta, Jalila tace "bakomai daddy, amma makaryaciya ce"
Hannah ta fashe da kuka tace "Shikenan tunda ba 'yar kuce niba kun zabi zubewar mutuncina, wallahi mutuncina baze zube ni kadai ba, ku saurari sammaci, wallahi karar Jalal zanyi"
"Karki fasa sekin dawo, Amma idan har karya kike abunda ya faru da iyayen gidanki ze faru dake, idan har kin iya makirci za' a nuna miki ranar dukiya, ki fice kibar gidan nan da kafafuwanki kafin insa akama min ke"
Hannah ta tsorata da gadar zaren da Jalila tayiwa su Jeje suka rufta, dan haka ba kunya ta juya zata fice, daddy yace "Amma ta tafi ba'a gano bakin zaren ba"
Jalila tace "daddy ka rabu da ita, ko ta kai kara, kota bari ya dawo ayi maganar amma babu dalilin da zesa ta dinga maka karya tana bata maka rai akan danka"
Ta juya ta kalli Mummy tace "Mummy Allah ya huci zuciyarki, ban biyo Hannah dan shiga cikin lamarin iyalinki ba, sedan sanin hatsarin Hannah ga rayuwar Jalal, Amma Insha Allah kome ze faru bazan kuma shiga lamarin ba, in dai ya shafi gidan nan"
Ta juya zata fice, daddy yace "Jalila ita wannan yarinyar wacece? Sannan meye hatsarin ta ga Jalal? Menen alakarsu?"
Jalila tace "Daddy ba a bakina yakamata kaji ba, amma dai nasan babu wata alaka ta kusa dake tsakaninsu, na tafi se an jima" ta juya ta fice zuciyarta cike da bacin rai.
Maama ta dubi Yaya mairo tace "Yaya wannan jinin kuwa na lafiya ne?"
"Al'adace haka yake zuwar mata"
"haba Yaya, kalli guda gudan dayake zuba kice min Al'adace, yakama tunda nazo da mota mu kaita Asibiti"
"ba wani Asibiti da zamu kaita" yaya mairo ta bata amsa tana kokarin temakawa Naja ta mike zaune, amma tana tabata taga bata motsi, numfashinta da kyar yake fita, ga jini se cigaba da fita yake daga jikin Naja, ba shiri Yaya mairo ta mike, Maama ta temaka mata suka gyara Naja, suka sata a mota se Asibiti,
Sunkai awa biyu suna jira, Yaya mairo takira Naja a waya, tazo suka hadu a Asibiti, likita ya fito ya tambayesu alakarsu da Naja, sukayi masa bayani, yace su bishi office dinsa, haka suka bishi sukaje suka zazzauna suka zubawa likita ido, ya danyi gyaran murya sannan ya kallesu yace
"To kun san duk abunda yasamu bawa mu kaddarine daga Allah, kuma Allah yana jarrabar bayinsa ta ko ina, kuma dukkan musulmi se yayu Imani da kaddara sannan Imaninsa ze cika, Hakikanin gaskiya mara lafiyar ku tana dauke da ciki karami, kuma tayi Amfani da miyagun kwayoyi wanda hakan yayi sanadiyar zubewar cikin jikinta da kuma lalacewar mahaifarta"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji un" shine abunda suka dinga nanatawa, gaba daya Maama taji jikinta yafara rawa, Yaya mairo ta dora hannu aka tafara ihu, likita yace "Haba baiwar Allah kamar ba yanzu nagama yi miki nasiha ba, ba wannan bama, yarinyar nan ta zubar da jini da yawa, Akwai bukatar a sama ta jini, kuma a bincike da mukayi tana da cutar Hepatitis B, (ciwon Hanta), dan haka ku gaggauta nemo Jini, a duba a 'yan uwa wanda jininsu yayi dai2 se a samata"
Haka suka fiti office din nan suna salallami, jiki a sanyaye Yaya mairo tace "bari a kira yayanta a waya, Zainab kira Jawwad suzo a duba in jininsu zeyi a samata"
Da sauri Maama tace "Wane Jawwad din? Jawwad yana Abuja ya samu Aiki ai, nikam Yaya mairo ga wannan" tasa hannu a Aljihu ta dakko kudi tabata sannan tace "ga wannan ku sai magani, zan koma gida magariba tayi, se na dawo dubiya, Amma yakamata kunemo wanda yake da alhakin cikin nan, yazo ya dauki nauyin ta, se anjimanku"
Maama ta juya ta fito daga ward din, tana ta tunani tareda mamaki, da kyar Maama ta kai kanta gida, saboda tunani da Mamaki, da tuno marin da tayiwa Jawwad saboda Naja se taji gaba daya jikinta yayi sanyi.
Haka ta koma gida jiki a sanyaye, tunda ta koma take tunani, Nana ta lura da Yadda Maama jikinta yake a sanyaye dan haka taje ta sameta a daki take tambayar ta "Maama wai me yake damunki ne? Tukuna ma ina kikaje?"
Dan shiruu Maama tayi, sannan tace "Nana naso inyi ganganci da rayuwar dana"
"gangancin menene?"
Nan ta kwashe komai ta gayawa Nana, Nana tayi murmushi tace
"Allah sarki Rayuwa, Maama kinga wannan abun to izina ne a gareki, Allah yasa kar alhakin marainiyar Allah ya kamaku, kunsaka Jalila kuka ta zubda hawaye ba a dadi, ku zageta ku mata cin mutunci, ku mata gori amma se gashi su sunyi Abun kunyar da 'yar arnan ba tayi ba, Maama lokaci yayi da yakamata ki gane su waye ke kaunar ki, Yaya mairo' yar uwakki ce amma abun hannun ki takeso, ki duba irin biyayya da Jalila tayi miki tsawon lokaci, duk fitsararta da kuke fada, ke dai bata taba yimiki ba, se dai Yaya mairo, Maama a ci zarafin iyayen mutum dacin abun ya wuce yadda kike tunani, kun cutar da ita gaskiya, fatan Allah ya yafe muku, yanzu seki gane, Ummi da take ba musulma ba da farko, tayiwa 'yarta tarbiyar da wanda aka haifa a musulinci bata yiwa' yatta ba, Allah yasa hakan ya zama izina a gareku"
Maama kasa cewa komai tayi, se jujjuya maganganun Nana da takeyi, tabbas Maganganun Nana gaskiya ne,
Nana tace "Maama bari inje daki inada Assignment da zanyi"
Gyada mata kai kawai Maama tayi, Nana kuma ta fice, koda taje dakinsu Jalila tana kwance idonta a rufe, kaman me bacci, amma ba baccin take ba, tunanin abubuwa da dama ne ke zagayawa a cikin kwakwalwarta.
Daddy yakasa samun sukunibda abunda ya faru, gaba daya hankalin sa yaki daidaituwa, yarasa maganar wa zebi, ta Jalila kokuma ta Wannan yarinyar, Amma yakasa bawa kansa amsar wani tabacci Jalila take da shi akan Jalal, Mummy ta lura da yadda daddy ya dami kansa dan haka tace
"Ni dai a ganina wannan yarinyar da gaske take, ba'a shedar mutum, shiyasa nake son mu aurar da Jalal, shekarunsa ya kai ya ajiye iyali, ita kuma wannan yarinyar da tazo da wannan maganar, indai da gaske take, a lallabata abata kudi tayi hakuri"
"bana tunanin Jalal ze aikata haka, kuma tunda Jalila ta bada sheda akan Jalal, abun dubawa ne, amma yazama dole in bincika, lamarin yaron nan na ma rasa yazanyi, Allah ya shiryamana zuri'a"
Dadd yasa hannu ya dau wayarsa ya kira Jalal a waya, seda ta kusa katsewa sannan Jalal ya daga, koda ya daga ma beyi magana ba, shiru ya gudana na wani dan lokaci sannan daddy yace "Jalal kana jina?"
"Ina jinka daddy"
"ya kake ya aikin kuma?"
"lafiya kalau Alhamdilillah daddy, kana Nigeria kenan?"
"Eh ina nan, nakira ka ne, ina so muyi magana"
"ina jinka"
"Wace ce Hannah?"
Gaba daya Jalal ya manta da wata Hannah a rayuwarsa, Amma ya maze yace "Ban Santa ba"
"Jalal ban sanka da karya ba, wannan yarinyar itace kwanaki tazo min da waccan maganar, wannan karon tazo min da maganar wai tana dauke da ciki kuma nakane, Amma Jalila ta karyata ta, sannan tacemin Yarinyar tana da matukar hatsari ga rayuwarka, kamin bayani "
Ba abunda ya farantawa Jalal rai sama da jin batun Jalila ta kare shi, duk da furucin da tayi na bashi ba ita, daddy yace" Jalal ya naji kayi shiru? "
"to me zance maka daddy? Duk hukuncin daka ga dauka akaina dai2 ne, inma ka yadda gaske ne ko karya, dan Allah ni ku kyaleni hankali na ya kwanta, ina jin dadin zamana a inda nake karku daga min hankali"
"Amma Jalal meye hadinka da yarinyar nan har take bibiyar ka? Tana ikrarin zata kai kararka"
"Daddy in dai har bana nan, a bayan idona yarinyar data tsaneni zata bada shedar kirki akaina me kake so ince maka, kana so inta rantsuwa ne seka yadda dani? Kasan ba haka nake ba, Idan bata kai karata ba ni zan dau mataki akanta"
"Amma meye hatsarin yarinyar ga Rayuwar ka? Kamar yadda Jalila ta fada?"
"ka tambaye ta mana, tunda a bakinta kaji"
"Jalal yaushe zaka dawo?"
"ba yanzu ba, se nan gaba, nifa zamana anan yafi min zaman gidan nan, da za'adinga takura min"
"to shikenan tunda haka kace"
Haka sukayi sallama ya kashe wayar.
Mummy tace "wai nifa nakasa gane wannan maganar, ita Jalila wacece dinsa da za ta fadi abu ka yadda, ya akayi tasan abunda mu bamu sani ba akan danmu, haka akeyi?"
Murmushi daddy yayi ya dan kashe mata ido
yace "haba deejat to meye a ciki? Kin samu me kulamiki da son, you have to thank her, har gida tazo dan kare shi"
Kara kunna Mummy yayi, dan haka ta tashi fuuu ta bar masa dakin.
Ilham tayi safa da marwa yafi sau Ashirin a dakinta, tana son ta tabbatar da Hannah dagaske take koda wasa, yanzu abun ya kuma kwabe mata, da ta manta da batun Hannah, amma yanzu yakin ya kuma zame mata biyu, ga Jalila ga Hannah, da tana tunanin tayi maganin Jalila, tunda tayi mata makirci a gurin Mummy, "Amma Jalila nan naci ne da ita bata da zuciya, shegiya se nayi maganin ta, sena kuma kunna mata wata wutar, to amma in dagaske Jalal yayiwa Hannah ciki fa? Da sauri tace" kai karyane, da Jalila yayiwa Hannah ciki da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, karya takeyi"
Ilham ta fito daga dakinta har tana tuntube ta tafi daki Mummy, tana zuwa ta tarar Mummy ta cika tayi fam, fuskarta sam babu walwala, Ilham taje ta zauna a kusa da Mummy tace
"Mummy lafiya kuwa?"
"ke rabu dani, ni zancen wannan yarinyar mana, gaba daya daga Jalal din har ubansa naga hankalin su ya karkata kan wannan yarinyar Jalila, ga itama wannan wadda tazo din da wannan maganar cikin"
"mhmm wallahi Mummy in bakiyi wasa ba yarinyar nan se ta hana Jalal din ma shigowa gurinki, ta ne Santa shi dake, meye nata na sawa anema masa aiki a nesa? Kuma ga daddy yafara biyewa maganganun ta, wallahi Mummy da sannu zata janye miki shi gaba daya"
Mummy ta numfasa tace "ni Ilham gaba daya kaina ya kwance akan lamarin Yaron nan, narasa yadda zanyi"
"to Mummy kiyiwa daddy maganar, ayi mana Auren mana, saboda ayi maganin abun, tunda har ya fara bin mata"
A fusace Mummy tace" Ke dan Allah ki rabu dani, kina gani ba irin kokarin da banyi ba, Amma abu ya ga gara, ni ki kyaleni nace ki bani lokaci, sena fara shawo kan matsalar, ni na miki alkawarin Auren nan, ki karamin lokaci in gama da wannan matsalar mana"
Ilham ba tace komai ba ta mike ta bar dakin, tana fita tayi kwafa tace "Wallahi zaki gane kuskuren ki Mummy, zanyi maganinki, sena Auri Jalal din na mallake shi, ke da shi sedai kallo"
Amin Afuwa nayi busy sosai,
Gashi nan ba editing
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
PART
_PAGE
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Shiru Jalila tayi ta kalli kayan daya ajiye mata sannan tabi bayansa da kallo har ya fice daga gate, din shiru tayi ta tafi tunani, Ahmad yace
"my queen, meya farune?"
Da sauri ta dawo hayyacinta tace "bakomai fa"
"Amma waye wanan?" ya tambayeta yana me kureta da ido, ta dan sauke numfashi tace "Yaya na ne"
"Yayanki queen, ba Jawwad ne kawai Yayanki ba?"
"Abokin Yaya Jawwad ne, dan haka Yayana ne kawai"
"Amma babu wani abu a tsakanin ku kuwa?"
"Meyasa kake min wannan tambayar? Ko baka yadda dani bane?"
"Ahh haba waneni ince ban yadda da gimbiyata ba, ina so ne in tabattar da abunda ke tsakaninku, dan da idonsa yana shaye2"
Ba karamin haushi maganar Ahmad ta bata ba, kenan shima yanayi, in ba yanayi ba, ba abunda idon Jalal yayi dayake nuna yana shaye2, dan haka tace
"baya shan komai, kawai bashi da son magana ne, baya kula mutane"
Kyaleta Ahmad yayi yaga alamar bata son zancen suka cigaba da hira, Jawwad ne ya fito ze wuce su Jalila ya tsaya suka kuma gaisawa da Ahmad dayake dazu sun gaisa, Jawwad yace "to sirikina zan iya ce maka se anjima, ni zan tafi kai Jalal airport ne"
Da sauri Jalila tace "Ina zashi?"
Jawwad yayi murmushi yace "Aiki mana, an tura shi Lagos, se lokacin biki inaga ze dawo, bari inje karyai ta jirana, kin san baya son jira, se anjimanku" Sukayi sallama da Ahmad ya fita.
Ahmad ya maida idonsa kan Jalila yace "Gimbiya naso a ha
a bikin nan hada namu, na kagu in mallakeki"
Murmushi kawai tayi amma hankalinta baya kansa, tanata zancen zuci ne, dayaga haka yace "queen naga kaman Akwai abunda yake damunki, bari in tafi semunyi waya"
Ta mike ta rakashi har bakin gate sannan ta dawo ta
zauna akan kujerun tana nazari
"At least yakamata ace sunyi sallama da Jalal, tayi masa nasiha, Amma bata tunanin zata iya kuma rabarsa ba saboda mahaifiyarsa.
Jawwad ya ga sam fuskar Jalal a daure take, babu alamar walwala ko fara'a, Jawwad yai masa magana yafi a kirga, amma ko daya be bashi amsa ba, dan haka ya kyleshi suka cigaba da tafiya a haka kaman kurame.
Gajiya Jalila tayi da zaman tunanin ta mike ta tafi cikin gida, Nana tana zaune a palour suna waya da Mahmud,
"Nana waike dan Allah ba kya gajiya da wannan wayar ne? Kuyita surutu tun ana fadar gaskiya se an koma fadan karya"
Nana taki kula ta seda ta gama wayarta sannnan tace
"waike Baby an gaya miki kowa irin kine me tsarin tsiya, ke yadda ba kya son yawan waya kowa ma hakane, ai a rana inji muryar Mahmud sau hamsin bazan gajiba, musamman mu da muke distance relationship, ai Ahmad din nan ma ban wani yadda kina sonsa ba"
"Inasonshi sosai, amma hakan bashi ke nufin a dinga uzzuramin da surutu ba"
"Hajiya Jalila, kyaji da shi dai"
Hanan ca ta kira Jalila a waya, ta daga tasa a kunnenta
"hello Baby, 'yar uwata rabin jikina ashe Family dinmu daya Baby? Narasa inda zan sa kaina dan farinciki, dazu Abba yake gayamin kuma wai an kawo kudin Aurena da Haidar, Baby na rasa me zanyi dan farinciki"
Murmushi Jalila tayi tace "na riga ki ji ai, kiyi Azumi ki godewa Allah"
"queen na rasa inda zan saka raina dan farinciki, daddy yace zasuzo karbar kudin Nana, narasa yadda zanyi dan murna"
"haka Al'amarin ubangiji yake Hanan, yana juya komai yadda ya so"
"Hakane Queen, amma naji haushi da baza'a hada da nakiba, ni ina Jalal ne ma?"
"yaje interview din nan ai, an turashi lagos zeyi wata uku"
"Allah sarki bawan Allah, wallahi Jalila bana kaunar Aurenki da Abokin Yaya Yusuf din nan, in duniya da gaskiya Jalal ya kamata ki Aura"
Wani dogon tsaki Jalila tayi ta kashe wayarta, dan bata son Hanan ta bata mata rai.
Jalila ta mike har zata bar palourn taga Maama tazo ta wuce kitchen, gaba daya Jalila bata jin dadin yadda kowa ya fita harkar Maama, dukda abubuwan da Maaman tayi mata, Akwai lokutan da ta kyautata mata, dan haka taga be dace ta mata hukunci da laifin da take mata ba, dan haka tabita kitchen din, Maama na kokarin kunna gas Jalila tayi maza taje ta karbi lighter tace "Maama kawo in kunna miki, me zaki dafa?"
"barmin Abina zanyi"
"A'a Maama, tunda ba abunda nake ki barshi in dora miki"
Jalila ta karbi lighter ta kunna gas, dan jimm Maama tayi tana Kallon Jalila, yadda Jalilan ke Acting kaman Maama bata taba yi mata wani abu na bacin rai ba.
Jawwad suka isa airport yayiwa Jalal Sallama amma ya amsa masa a ciki, sam baya walwala, yasan halin Jalal baya son takura, tunda be niyyar gaya masa meke damunsa ba, ya ja Akwatinsa yayi gaba yabar Jawwad.
Haka Jawwad ya taho yanata tunanin me akayiwa Jalal yake wannan bacin ran haka?
Bayan Jalila ta gana yiwa Maama girki, ta koma daki, ta dauki Alqur'anin nan tana ta jujjuyawa, Kamshin turaren Jalal yakeyi, hakama dan teddyn ta, tasa hannu ta ta dinga duba Alqur'anin nan page by page, amma sam bata ga komai a ciki ba, kodai Jalal dama yana son raina mata hankali ne kawai?
Shiru tayi ta tuna yadda taga yana yinsa bayan ya gansu tareda Ahmad, Fuskar nan tasa a daure babu alamun sassauci, tayi shiru ta cigaba da zancen zuci, ;yanzu ze tafi lagos bashi da kowa a can, babu me kula dashi, Allah kadai yasan meze aikata,
"kinfi so in cigaba da shaye2 na ko? Ke Garkuwa ce a gareni" ire iren wannan maganganun nasa da Maganganun Antynsa da take gaya mata tabata amanar Jalal ne yasa take tunanin Anya hukuncin data yanke yayi dai2 kuwa?
To Amma nikuma mutuncina fa? " gaba daya ta rasa me yakamata tayi? Yanzu tana gaya Hanan, tasan Hanan zata canza mata magana tafara kawo wani abu daban, dan haka tabar Abun a ranta ta cigaba da Yiwa Jalal Addu'a.
'yan kwanakin nan sam Abba ya dena shiga harkar Maama, har gara Jawwad ma yana zuwa gaisheta, Nana kuwa seda Jalila tasata a gaba ta nuna mata be dace ba abunda take yiwa Maama, wannan abunda yafaru tsakanin ta da Abba ne da kuma' yan uwan ta, sannan ta samu Nana ma take shiga sabgar Maaman, Abba ya gayawa Maama ranar Lahadi zasuyi baki, za'a kawo kudin Auren Nana, abakin su Nana taji batun haduwa da 'yan uwan Abba a Bauchi, ba tayi mamaki sosai ba jin ance su Hanan' yan uwansu Abba ne ba, sakamakon matukar kamannin dake tsakanin Jalila da Hanan, sedai taji haushin rashin sanar da ita da Abba beba.
Tun ranar Juma'a suke shirye2 domin bakin daza'ayi, Jalila ce jagorar girke2 da shirin yadda za'a karbi baki.
Gefe guda Jawwad yana ta shirye2 Ranar litinin shima ze tafi gurin nasa Aikin, ba karamin kulawa Hanan take bashi ba, da soyayya da kuma shagwabarta, yanayin yadda take nuna yarinta
a wasu bangaren ba karamin birge shi yake ba.
Kamar yadda aka saka ranar lahadi daddyn Hanan yazo Kano aka karbi kudin Auren Nana, itama lokaci dayane dana Jawwad dakuma Abdallah Yayan Hanan, ranar har mutan bauchi seda sukazo garin kano karbar kudin, da kuma kara taya juna murnar haduwar su a matsayin 'yan uwa. Jalila taji dadi da akazo hadda Hanan da Mummynta, Maama seda ta sha jinin jikinta ta raina kanta ganin manyan mutanen da sukazo gidan, Abun Arziki ya hadu dana Arziki, dangin Su Jawwad dana Su Jalal, Ranar anci ansha, kai ka dauka bikin Aure akeyi rana ce me matukar tarihi da wannan Ahali bazasu manta ba. Jalila sam bata samu kebewa da Hanan ba, saboda Hanan na manne da Jawwad, sam bata jin kunyar kowa take nuna masa soyayya.
Mummyn Hanan se mita take tace "Ni gaskiya naso a hada abun nan hada na Jalila, in aurar da 'ya' ya uku, amma in shirya da kyau, amma bakomai anata se nafi shiri ko Jalila?"
Ita dai Jalila sedai tayi murmushi ta sunkuyar da kai.
Duk yadda Maama take jin kanta take kuma jin haushin Auren Hanan da Jawwad boyewa tayi, Saboda sam bata da makusa, 'yar dangi ce, kuma' yar uwar dan tace, tana da kyau dai2 gwargwado kuma tana da Ilimi, yanayin kyau da gayun mahaifiyar Hanan ya isa ya nuna maka 'yar ta ma hakan take. Koda ta hasko Naja seta ga abun se A hankali, kuma tun abun nan da sukayi mata ta tabattar da Ko Auren akayi Naja zata iya wulakanta ta.
Da ire iren wannan tunanin yasa ta ajiye duk wani bacin rai aka shiga hada2. Tareda tsara yadda suke ganin bikin ze kasance, Ba laifi Mummyn Hanan ta saki jiki Maama, Sunyi hira sosai kaman sun saba, sannan suka tattauna akan yadda harkar bikin yaran nasu ze kasance. Se la'asar Suka tafi, mutanen Bauchi suka tafi, Su Hanan ma a ranar suka juya kaduna saboda Su Hanan suna jarrabawa, su kuwa danginsu Mahmud, suna kawowa Mahmud kudin Aure sukaci Abinci suka juya Borno.
Wasa2 sosai tunanin Jalila ya hana Jalal sukuni, da yafara aiki in ya tuna da ita gaba daya se yaji duniyar tayi masa zafi, yarasa inda zesa kansa, meyasa Mummy tayi masa haka? Idan yaji abun ya dameshi se ya tafi club yaje ya cika cikinsabda giya, dukda wasu lokutan yana bawa aikin da yaje yi mahimmanci, Sam Jalal bashi da sakewa da mutane, dan haka be saba da kowa ba, sedai yana girmama shugabanninsa na gurin aiki, girmamasun da yake besa sunga alamar ze bari su taka shi ba, inda yake burgesu yana maida hankali akan aikinsa sosai.
Duk lokacin da yaje Club mata da suke damun sa ne ga kuma shigar tsirara da suke yasa shi dakatar da kansa ga zuwa Club, idan yaji ba yadda zeyi se yayi shaye2 se yayi abunsa a dakinsa na hotel da yake ciki.
Amma duk da haka yarasa dalilin da yasa mata ke binsa, sedai in baze fito ba.
Hannah ce zaune akan kujera tana kwalliya, Sa'ada na kwance akan gado tana danna waya, dan dakatawa da kwalliyar Hannah tayi ta dan kurawa madubi ido, sekuma can ta daki kan mirror tace "Impossible baze yuwu ba wallahi"
Sa'adah ta waigo ta Kalle ta tace "lafiya kuwa?"
"Akwai matsala Sa'ada" Hannah ta bata amsa
"matsalar me fa?"
"Sa'ada ki kalleni ki kara, kimin kallon tsaf tun daga sama har kasa, ki kalli yadda nake gara kan maza, in taka wanda naso in wanke wanda naso, amma a hakan har rububina wasu suke, in sauke Ajina in cewa Jalal idan ya Aureni zan dena bariki, Amma ya watsa min kasa a ido"
Wani dogon tsaki Sa'ada tayi tareda fadin "Nina dauka ma wani mutumin kirkin ne, A she akan wannan mashayin ne, ni ba wannaan ya dameni ba a yanzu"
Hannah tace "Mutumin kirki ne mana, ki kalleshi kallon tsaf Sa'ada Namiji ne irin wanda duk wata mace zatayi burin Aure, shaye2 ne kawai matsalar sa, da farko da nakewa su Jeje aiki, nna zata zan samo kansa ta sauki ya yadda dani, Amma duk wata dabara da kisisina ta matan bariki nayi amma yaki amincewa dani"
"to kibi wani mana, ko shine kawai namiji?"
"bazaki gane ba Sa'ada, bakiga irin kirar da Allah yayi masa bane, kuma da kike ganinsa a haka, dukiya ce dashi kaman abun banza"
"Ya akayi kika sani, nasan dai babansa yana da kudi, amma shikam ko aikinyi ba shida shi" Sa'ada tayi maganar tana yatsina fuska
"Hmm to wallahi har ki mutu in ba wani ikon Allah ba, kaf danginku daku da abunda kuka mallaka, bazaku kaishi dukiya ba, yana da kudi da mahaifinsa yasa ake juya masa, Jeje yaso ganin bayan dukiyar nan shida mai gidansa amma abun be yuwu ba suka kare a prison"
Sa'ada ta tashi zaune tace "to ke yanzu meye abunyi, ni ban taba sani ba, kin san ya taba kusa tonamin Asiri ina zuwa club agaban babarmu"
Dariya Hannah tayi tace "Abune mawuyaci ya tona miki Asiri, bar ganinsa a haka, yasan abunda yakeyi, naje har gidansu na dana masa tarko, amma ga dukkan alamu ya tsallake shi, wannan karon zan masa tarkon da zan rike shi a wuya, be isa ya kuma subuce min ba"
"Yakamata kam, Amma ni nan tunanin yadda zan huce abunda abokinsa Jawwad yayiwa Naja nake, kiri2 yafasa Auren ta, yarinyar nan duk ta shiga damuwa"
"Allah sarki, to wai ya'akayi aka fasa Auren? Waye yaje yai mata gulma a gurin baban nasa?"
"ya za'ayi in sani, Amma da nafi kyautata zaton wannan munafukar kanwar tasa ce"
"Wace kanwar tasa ya'akayi tasan abunda Naja take? Ko dai itama tana ta bawa?"
"Ke bari, wata yarinyace yadda kika san boka haka take, ni dai ban san tana wani biye biye ba, Amma kina zaune in taso seta nemo waye ubanki koda ke baki sani ba, wai ita Jalila makirace ta bala'i, idan tace bata san abu seta ga bayansa, tasa Jawwad ya fasa auren Naja se kawarta"
Jin an ambaci Jalila yasa Hannah zare ido tace
"Kan bala'i ai nasan wannan yarinyar, tabdijan ni zan gaya miki makira ce, ke wallahi keda kike bariki tafi ki iya rashin mutunci, ke zata iya yuwu wa ita tasa aka hana, bari in gayamiki yarinyar nan tafiki bala'i, dan koni tasa min ido akan Jalal, ita take rusa min komai "
Cikin mamaki Sa'ada ta kalli Hannah tace" wai kin santa ne? "
" Nikuwa na santa, kuma nasan illar ta, munyi Arranging da Jeje mun gama komai, zamu sace Jalal ranar birthday din sa, idonta na kanmu, muka bugar da shi da giya ta shammace mu tasa aka dauke shi daga gurin, ke ina jin kishin cewa ita tasa aka kama Oga KB"
Zaro ido Sa'ada tayi cike da mamaki tace "Ke haba dai? Shikuwa oga KB yana me,duk iya kuri da gadarar rashin mutuncin nasa, yarinya ce fa karama"
Hannah tace "hmm ke dai bari, mace kenan, kaidin wata yafi wata, irinsu kuma sa'a ce dasu a rayuwa, kibi a sannu kawai"
"Tabdijan amma babu kama, dan bakiga cin mutuncin da muke mata ba mu da babarmu, kin san uwarta tsohuwar arniya ce, bakiga cin mutuncin da muke mata ba"
Hannah tace "Yawwa kuma ga cin mutuncin da tayi muku nan, kuma ta gama daku ba"
"Sosai makuwa ta gama damu"
"shiyasa wannan karon shirina ita da Jalal ne, dan bana ta wannan Ilham din dan wannan ba mace bace, wannan tafi hatsari, baze tsallake wannan tarkon ba a yanzu, na duba mashayar da yake zuwa ba adadi amma ance ya dena zuwa, duk da haka zan nemoshi"
Yauma duk da tarin farinciki da Jalila ta tsinci kanta a ciki yau, amma bacci ya kauracewa idanuwanta, jikinta na bata Jalal yakoma shan giya, da kyar ta samu bacci ya dauke ta, amma mafarkin Jalal a cikin wani yanayi na shaye2, yasata farkawa, gabanta na wata irin mummunar faduwa, wayarta ta dakko ta duba karfe biyu da rabi na dare, ga shi ita ba lambar Jalal ce da ita ba, tarasa mema zatayi gallery dinta ta shiga tana dubawa, tsofaffin ajiyayyun hotunan ta take dubawa, hotunan da sukayi da Jalal tun wani zuwa da Hanan sukayi, haka taita kallon hotunan, a haka har ta kawo kan hotunan birthday dinsa, cin karo tayi da wani hoto da'akayi harda Hannah a ciki, take gaban Jalila ya fadi, dan sam ta manta da Hannah, kuma barin Hanna ba tareda daukar wani mataji ba tamkar kashe maciji ne ba'a sare kansa ba a rayuwar Jalal.
A hankali ta ajiye wayar, ta sakko daga kan gadon ta shiga toilet tayi alwala tazo ta tada salla.
Ranar litinin Jawwad shima yayi nasa shirin tsaf domin tafiya Gurin nasa aikin dake birnin tarayya, Abba yayi masa Nasiha sosai tareda sa masa Albarka, haka ma bangaren Maama, tayi masa Addu'a da sa Albarka, dukda marin da Maama tayi masa akan Naja, hakan besa ya nuna mata har yanzu yana fushi ba, Bangaren Jalila kuwa har kuka tayi, saboda zatayi kewar Yayan nata sosai
Abba yace "Jalila kina kuka dan zeyi tafiya, kuda kwanan nan zeyi Aure gaba daya zasu bar gidan, su barki seke kadai"
Kara fashewa da Kuka Jalila tayi, Nana tace "Abba ka gani ko? Wannan yar taka ta fiye shagwaba wallahi"
Jawwad yace "haba babyn Abba, sekace ba jaruma ba, zan dawo ai kidena kuka"
Sukayi ta tsokanarta ita kuwa dagaske take kukanta.
Haka sukayi sallama da Jawwad shima yakama hanyar tafiyar sa.
Jalal yana waya da daddyn sa sosai, sannan suna waya ds Jawwad, suna shirye2 yadda biki ze kasance a tsakanin su.
Abban su Jawwad yana kasuwanci ne a tsakanin Kano da lagos, dan haka in yaje suka haduwa da Jalal.
Jalila Nason sanin halin da Jalal yake ciki, amma babu wata hanya da zata san hakan, dan haka taketa kokarin boye damuwarta.
Maama Allah ya temaketa Abba ya sakko daga fushin dayake da ita, sannan tunda abun nan ya faru Su Yaya mairo ko a waya basu kara neman Maama ba, abun ya dameta sosai dan haka ta shirya da kanta taje gidan su.
Tunda tayi sallama suka amsa suka shareta suka ki kulata, ita tayiwa kanta gurin zama, ta gaida Yaya mairo amma taki kulata, seda ta bata 'yan kayan data saba kaimusu, shine Yaya mairo ta dan saki rai suka gaisa, Naja ta gani a lullube tana bacci, Maama tace "Yaya, Naja ba lafiya ne?"
Kafin Yaya mairo ta amsa Naja ta fara magana cikin maye "Ni... Ni.. Ba... Wallahi baaaaani da.... Da lafiya, Shiyasa naiwa kaina caaajiii, baaaa danki yaki Aure na baaaaaa, wallahi....
Cikin tsawa Yaya mairo tace" yimin shiru dan ubanki, ciwon mara take, shine ta sha magani fiye da ka'ida"
Gaba daya jikin Maama yayi sanyi saboda babu tantama Naja maye takeyi. Shiru tayi takasa cewa komai, Naja ta cigaba da surutai, can kuma ta kwalla uwar kar, sega jini na gudu a tsakar dakin daga karkashin Naja.
Se bayan la'asar su Jalila suka gama lectures ta gaji matuka, haka kurum tun suna lectures takejin gabanta yana faduwa, da kyar ta tsaya aka gama lectures ta fito, danma manu direba ne yaje dakko ta daga school, abunda yabata mamaki be wuce ganin motar Hannah a gabansu ba, tana tsala gudun wuce sa'a, kuma da alama layinsu zata shiga, Jalila tasa Manu direba yayi parking a farkon layinsu, ta sauka ta shiga layin da kafarta, aikuwa tana zuwa taga Hannah tayi parking din motarta ta shiga gidansu Jalal, Jalila batayi shawarar komai ba ko tunani tabi bayan Hannah zuwa cikin gidan.
Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what's App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry.
Ina godiya da kulawa.
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*
Chapter 2 · 0% Book details