← Book details Zinare Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 3

Gabatarwa

Zinare Part 1 Complete Hausa Novel · about 255 min read

M] +234 702 541 3080: 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ZINARE*


NAFISA ALIYU SASAAL
Arewabooks@sasaal


*BISMILLAH*

✍️ 7:30pm 5-7-2025

*Labarin ZINARE ƙirƙirarren labari ne, gagaruwan ciki da wasu ƙasashen ciki duk ƙirƙirane, idan wani sashe na labarin ya yi kamaceceniya da rayuwar wata/ni to akasine*

*CHAPTER 1*

*"BA A RANAR DA MUKA SHUKA IRI ZA MU GIRBI AMFANINSA BA, DOLE SAI MUN JIRA, MUN YI HAƘURI, TARE DA YIN AIKI TUƘURU."*

01

Yankin Tudu, Daular Sarki Hammam, sassanin wasannin ƙarshen mako.

Yara Matasa Maza da Mata ma su shekaru 15 zuwa ƙasa ne suka cika filin wasan.
Ɓangaren Maza daban na Mata ma daban.

A ɓangaren Maza, a tsakanin ƙungiyoyin biyu da suke gwabza wasan ƙwallon ƙafa kowa na ƙoƙarin nuna ƙwarewarsa, da zafin namansa. Wannan yasa ihu da tafi yake ta tashi daga kowani ɓangare, bakunan wasun su kamar zai yage saboda dariya da ihu.

Kujerarsa ba ta kusa da ta kowa, fuskarsa daban take data kowa, ba bu murmushi balle dariya. Ba ya tafawa kamar ragowar kamar ma dai bai san me ake yi a wajen ba, ko wanda aka tilastawa zuwa sansanin wasannin dole. Tsayayyen dogon hancinsa ya shafo ya na lumshe fararen idanuwansa, Kamar ance ya waiyawaya bangaren da Matan suke wasannin su. A daidai lokacin wata matashiya mai irin Shekarunsa ta kwaso ƙafar ƙaramar yarinyar da bata wuci shekaru 6 ba, mugun dariya ya kwashe da shi yana ƙara waiwayowa kansu dakyau, zaman ƴan borin da yarinya tayi ne yasa ya ƙara kwashewa da dariya.

Ya na son mugunta a rayuwarsa sai dai baya iya yiwa wani amma yana so yaga anyi a gabanshi, saboda daɗin da yake ji, musamman idan wanda aka kai ƙasan ba shi da gaskiya.

A hankali yarinyar ta miƙe fuskarta duk hawaye da majina, nan ma dariya ya ƙara kwashewa da shi, ya na jin daɗi a ranshi. Mai ya kaita cikin manyan da ba sa'anninta ba yin wasa, banda ga ƙananu Yara Ƴan uwanta suna na su wasannin? Miƙewarta tana karkaɗe ƙasar jikinta haɗe da zare idanuwanta da hawaye ya ɓata ne ya ƙara sashi sakin dariya kafin ya ɗauke kanshi yana sauke ajiyar zuciya nishaɗin da ya samu.
A take asalin fuskarsa da ba fara'a sam ta dawo yadda ta ke.

A can nesa da shi Sufyan yaron da bai wuce shekaru 11 ba ne ya zubamai ido, ya daɗe ya na kallon duk wa su motsinsa har hankalinsa ya bar wajen wasannin da ake yi gaba ɗaya. Maiyasa ba ya dariya sai ya ga mugunta? Maiyasa ba ya magana sai da ƙwaƙwarar dalili? Ya na son ya matsa kusa da shi ya yi masa magana kamar yadda Mahaifinsa yake umartarsa duk ranar da zai fito ire-iren waɗannan guraren da shi kaɗai yake iya sumun damar ganinsa kai tsaye, amma tsoro ya ke ji duk da ratar shekaru hudu ne kacal a tsakaninsu.

NAILA da aka kwashewa ƙafafu jikinta ta ƙarasa karkaɗewa har cikin ranta takejin takaicin abinda akayi mata, banda zafin da take ji a bayanta. Kalle-kallen wanda zata kaiwa ƙara ta fara yi har idanuwanta suka faɗa gurin dayake zaune shi kaɗai. Da gudunta na yaranta ta nufesa rabin fuskarta duk ƙasar da hannunta ya kwasa.

Gabansa ta zagayo ta tsaya batare jin tsoro ko shakka ba.
Da ƙaramin muryarta na yara ta fara koromasa bayani ta na sauke ajiyar zuciya.

Ba ya wasa da yara, balle ya ce ya taɓa wasa da ita a wani wajen ne yasa ta zo har gabansa ta tsaya. Tsaf yake sauraronta, a bayanin na ta da yanda take kame-kamen dole sai ya bi mata haƙƙinta yasan itace bata da gaskiya amma take so a rama mata, rabin fuskarta ya kalla tare da tuno yadda aka kwashe mata ƙafafuwa tayi zaman ƴan bori, sai ya kwashe da dariyar mugunta

Ya kai wasu daƙiƙu ya na yi kafin ya gimtse fuskarsa yana ɗauke kallonsa daga kan fuskarta. Tsayawa Naila tayi ko zai ce mata ta zo su je ya rama mata amma sai taji shiru. Ƙasar fuskarta ta ƙarasa karkaɗewa da kyau. Sai a lokacin ta gane wajen wanda ta zo. SULAIM ne ɗan gidan ABDUH DHAHAB ɗin daya zama ƙashin bayan Yankin su kuma Abokin Mahaifinta. Indai shine Dama bazai kulata ba, dan da tasan ma shine da bazata zo ba.

Barin wajen ta yi tana tunano abinda zatayimai tunda yaƙi kulata dama kuma tasan kurma ne baya magana.

A haka wasannin ya ƙare kowa ya fara haɗa kayan wasanninsa don tafiya Gida.

NAILA; Sanyin iskar da yake busa ta ne yake ƙaramata ƙaimin tunanin abinda zata haɗamai lokacin da take kallon takun sawayensa shi kaɗai, saɓanin ragowar da suka jero da Abokannan su.

★washe gari ƙarfe bakwai na safiya a harabar gidan Abduh Dhahab ya yi mata, sanye cikin Uniform ma su tsafta, kafaɗarta rataye da jakar buhu shima a wanke ƙal.

Baki Malik Mai share harabar gidan ya saki, lokacin da ya yi ido biyu da Naila, tambayarta dalilin zuwanta ya yi yana ajjiye tsintsiyar hannunsa.

Dariya ta fara ƙyalkyalewa da shi sannan ta ce;

"ina kwana Malik, dama Sulaim ne yace na biyo ya kaini Makaranta a kekensa"

kai ya girgiza mamaki da wayon ƙaramar yarinyar na kamasa uwa uba ƙarfin halinta. Kafin yayi magana Sulaim ya fito da Kekensa shirye cikin Uniform ɗin daya bambanta da nata color.

Sulaim kallo ɗaya ya yi wa Naila ya ganeta, duk ɓacin ran daya fito da shi sai ya nemi gushewa;
"Anata tunanin zata iya ƙuntatamasa kenan?" Ya tambayi kansa.

Kai kawai ya jinjina ya na karkata Kekensa mai kyau da tsada ta gefen da take tsaye. Dasauri ta É—ane tana sakin dariyar nishaÉ—i haÉ—e da É—agawa Malik da ya saki baki hannu.

Gudun dayasa Naila sakin kuka da majina Sulaim ya ke yi da ita a kan keken. Duk inda suka gifta sai an kalleta ma su dariya na yi. Kafin su isa Makaranta mazaunanta har ƙaiƙayi su ke mata. Bai ce mata komai ba bayan ta sauka ya bar wajen.

Naila takai minti goma a tsaye tana kuka kafin ta shiga aji.

Bayan kwana biyu
Sulaim ya É—auka Naila zata gajiya amma sai ya ga kullum sai tazo. Tun hankalin mutanen Yankin ba ya kansu har kowa ya fara Ankara haka ma Mahaifinsa sai dai bai ce komai ba.

Tun ƙarfin halin Naila baya birge Sulaim har ya fara birgesa, ya dawo kullum da kansa yake tsayawa a ƙofar Gidansu ya ɗauketa.

A ɗan kwanakin da suke zuwa Makaranta tare Naila ta fahimci Sulaim ba kurma ba ne Selective mutism ne. Tun yana yaro har ya kai shekaru huɗu bai iya maganar arziƙi ba, kuma a haka sai ya wuni baiyi magana ba musanman a cikin mutane. Ya na jin nauyin yin magana a wasu lokutan da ma wasu guraren. Da farko yawon kaishi Asibitocin wa su Yankunan Matar da Mahaifinsa ya aura bayan tafiyar Mahaifiyarsa ta yi-ta yi saboda son da takemai. amma duk inda taje amsa ɗaya ne ba sauyi.

SULAIM;
Rayuwar neman kuɗi da kafawa zuciya ra'ayin riƙau na tsayuwa kan matsaya ɗaya tare da aikin ƙarfi tuƙurun Mahaifinsa ya horar da shi a kai, wannan dalilin ne ya yaƙara duƙufar da maganarsa, saboda shima Abduh mahaifinsa ba gwanin surutu ba ne kuma tare suke wuni su na aiki, idan ya dawo daga Makaranta.

Sannan Abduh Dhahab ya keɓancesa daga Abota da kowa musamman da ya ga sunfara tsokanarsa da kurma. Tun Sulaim yana jin ƙiwiya da nauyin yin aikin ƙarfin ƙera Tukwanen da sukeyi har ya haƙura ya saba.

Sulaim ya fi jin daɗin saurarar maganganun mutane a kan ya yi. Daga Makaranta ba ya zuwa ko ina sai wajen sana'ar Mahaifinsa, sai kuma filin wasannin ƙarshen Mako.

Sauraran hirarrakin mutane ba tare da ya tofa ba, ya taimaka ƙwarai wajen mayar da shi Yaro na daban a cikin dubban Yara ƴan uwansa saboda basirarsa.

Matsowar ƙarshen watan cin Kasuwar babban Yankin ne yasa ko ina ya ɗauki harama don kusan dukka mutanen Yankin kowa da abinda yake siyarwa don samun kuɗin shiga daga baƙin da suke shigowa.

Haka yake a Gidan su Sulaim da suke ginshiƙin Kasuwar gaba ɗayanta. Ba ji ba gani suke ƙera Tukwanen dake ɗaukar idon duk wanda ya kallesu tare da kwaɗaituwar son mallakar su.

A gidan su Naila ma haka zancen yake. Mahaifiyarta kayan wasan Yara take ƙerawa na laka, irin su kwano, murhu, cokali, da randar ruwa ƙananu gwanin ban sha'awa, dukka na wasan Yara. Kuma da yawan gaske takeyinsu amma baya kwantai duk sai an siyeshi.

Zuwan Naila Makaranta tare da Sulaim ya ƙara farfaɗo da zumunci a tsakanin Mahaifiyarta da Matar Mahaifinsa, tun da dama can akwai alaƙar jini amma Abduh Dhahab ya datsesa saboda hana Iyalinsa shiga wajen kowa da ya yi.

A tsakanin kwana huɗun da ya rage aci Kasuwar Zinare, Ɓakin fuska a manya motocin da ya zama abin kallo ga Mutanen Yankin su ka bayyana a Daular Sarki Hammam.

A fadar Sarki Hammam baƙin fararen fatar su ka shaida abinda ya kawosu, wato siyan Tukwanen Abduh.

Har gidan Abduh Sarki Hammam ya sa akayi musu rakiya.

Bayan sun kai, ƙememe Abduh yaƙi fitowa balle su gana, haka suka haƙura suka ƙara dawowa Fadar Sarki Hammam ya taimaka ya yiwa Abduh magana, ya siyar mu su da Tukwane.

Sarki Hammam da kansa ya tura a kirawo masa Abduh.

A ɓangaren Ɗayyib Ɗan uwa ga Abduh Dhahab kuma Aboki, Mahaifi ga Sufyan.
Bai samu nutsuwa ba, har sai da aka bincikamasa dalilin zuwan Baƙin da kuma wajen wanda su ka zo, ta hanyar Aminansa da baƙin suka shigo Fada akan idanunsu.

A ranar bayan Sallar Magriba labarin FaÉ—uwar ÆŠayyib ya riski Abduh Dhahab. A dai-dai lokacin da kiran Sarki Hammam ya riskesa.

Ɗan jim Abduh ya yi, yana sauraran ɗaya daga cikin Aminan Ɗayyib da yasa su ka bincikamai zuwan ɓaki da kuma dalilin zuwansu da wajen wanda suka zo, bayannan kuma ya yanke jiki ya faɗi. Wanda ko shakka ba ya yi akwai abinda Ɗayyib ɗin ya shirya.

A tsarin Abduh baiyi niyyar Aminta da ɓakin da suka zo ba, don ko ganinsa bai bari sunyi ba ne saboda ba zai siyar musu ba.

Tayaya zai kwashe dukka Tukwanen ZINAREN da mutane suke baro Yankunan su da jahohinsu don siya, ya siyarwa da mutane ƙalilan bayan yasan bazai iya ƙera wa su Tukwanen ba kafin zuwan ranar? Bayason Darajar Yankinsa da Kasuwar da ya sha gwagwarmaya kafin kafuwarsa ya yi faɗuwar Tasa, amma yana ganin lokaci ya yi, da ya kamata ya sallama komai. Godiya ya yiwa wanda ya kawo masa labari, sannan ya ɗauki hanyar zuwa ganin Sarki Hammam.

"Mai zai sa ÆŠayyib ya yanki jiki ya faÉ—i mai hakan yake nufi" Abduh ya tambayi kansa, lokacin da ya kutsa Fadar Sarki Hammam.

Bayan Sarki Hammam ya gama koro masa jawabi bai ja da nisa ba ya ce ya amince, don haka Sarki Hammam ya ce yaje Sashen Baƙi suka ƙara tattaunawa da su.

Kafin Abduh ya shiga wajensu sai da ya fara shiga Sashen Ɗayyib, yanayin yadda ya gano makirci ƙarara a ciwon nasa ne yasa kai tsaye bayan ya shiga wajen baƙin Fararen Fatar ya ce mu su;"Gobe su kawo kuɗi ku kwashi Tukwane"

Jikinsa a sanyaye, ya yi musu sallama ya nufo gida.
Bayan ya dawo gida, pillow da abin lulluɓarsa ya ɗauko ya dawo ɗakin Sulaim, rauni da tsoro na shigarsa akaron farko tun fara gwagwarmayasa...🏻

09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥


SASAAL
Arewabooks@sasaal


02


SULAIM;
★washe gari da Safe. A shirye yake tsaf cikin Uniform fuskarsa a turɓune, da zafin nama ya ke yunƙurin fito da kekensa, kalaman Mahaifinsa na ƙara sukar zuciyarsa, kullum ya tambayesa kuɗin kashewa sai ya ce masa;

"Ba a ranar da mu ka shuka iri, za mu girbi amfaninsa ba, dole sai mun jira kuma mu yi haƙuri, tare da yin aiki tuƙuru. Ka je Makaranta yau ma ba ni da kuɗin da baka"

Waɗannan kalamai su Mahaifinsa yake yawan nanata mai, duk lokacin daya miƙamasa hannu da sunan ya ba shi kuɗin da zai siyi abu a Makaranta ko yin wa su uzururrukan da ba su zama tilas ba. Duk da ga kuɗin ya na ganin su muraran amma sisi ba zai ba shi ba.

Kamar kullum da haushin hanasa kuɗin da ya yi ya yaƙarasa fito da kekensa ya bar Gidan, ƙofar gidansu Naila da ke kusa da na su gidan ya ja ya tsaya. Yana kaɗa kararrawar, ta fito a guje, Ta na hawa ya fige keken ko gaisuwar da take masa bai amsa ba.

Yanayin yadda ya ke tsala gudu a kan keken kwatankwacin ranar da ya fara ɗaukarta ne ya sa ta ƙanƙamesa da siraran hanayenta da ko kusa ba su ratsa rabin cikinsa ba.

A haka suka isa dogon ginin da ke kewaye da ajujuwan karatu. A hankali ya kwanto da keken duk da ba wani ƙato ba ne ta sauko. Idanuwanta ma su kalar tausayi ta ɗago ta kallesa, sannan ta ɗagamai ɗan ƙaramin hannunta. Kamar yanda ya saba bai ɗaga mata na sa hannun ba kuma bai ce mata komai ba, sai kanshi daya ɗan karkata gefe yana lumshe fararen idanuwansa haɗe da jinjina mata kai.

Murmushi da ya bayyana ƙananun haƙoranta ta saki, kafin ta nufi ajinsu da ɗan gudu tana ƙara waiwayarsa.
Shima murmushin da shi kaÉ—ai yasan yadda ya ke yin kayansa da salo mai birgewa ya saki ya na juya kan kekensa ya bar wajen.

GIDAN ABDUH DHAHAB
Tarin Tukwane sababbun ƙerawa ma su kala mai kyan gani a ido da ƙwari a hannu ne jere a ƙaton filin da yake ƙerasu, Lokaci ɗaya ido bazai iya ƙirga su ba saboda yawansu, Ƙira mabanbanta akayiwa tukwanen. Gefe guda Abduh Dhahab da siffarsa ta fi kama da na tsoho, ko mai rangwamen hankali, a tsaye, duk da fuskarsa ta ɗan ƙuruciya kan gani kasan ba wai tsufar shekaru ba ne, tsufar bautar da ya ke yi ne, da kuma rashin tsaftace jiki.

Fararen Fatar da suka zo Daular Sarki Hammam ne a gefensa, su na cinikin Tukwanen da ya jera da harshen nasararsa da ke fita fes kamar ba shi ba.

A haka Sulaim ya dawo da kekensa ya same su. Hannu ya É—aga musu haÉ—e rusunar da kansa alamar gaisuwa kafin ya wuce aihinin cikin gidan su.

Yana ƙoƙarin sa ke fitowa cinikin su ya faɗa a kan idanuwansa su ka ajjiyewa Mahaifinsa kuɗi ma su yawan gaske a cikin jaka.

Mamakine ya kama Sulaim, maiyasa Mahaifinshi zai siyar da Tukwanen da saura kwana uku a ci kasuwar su? mai zai cewa mutanen da za su taso da ga maƙotan Yankunan su da mutanen Birni ma su zuwa sara? Dole yasan wata sabuwar wahalar zai ɗora mu su, su sake ƙera wa su Tukwanen, amma ta yaya hakan zai yiwu?

Ranshi a ɓace ya ƙara komawa cikin Gidan. Matar Mahaifinsa ya samu a ɗaki. Da hannu ya tambayeta ta san dalilin da ya sa Babansa ya siyar da Tukwanen da za su fita kasuwa da shi jibi ba? Alamar ba ta sani ba ta yi masa. Agogon ɗakinta ya kalla ya na fita da sauri ya bar Gidan gaba ɗaya.

ABDUH Dhahab
Bayan Fararen Fatar sun sa an É—ebe musu Tukwane,
Ƙwalla ne ya tararwa idanunsa da su ka zama jajayen ƙarfi da yaji, saboda bauta da neman kuɗi da ya ke yi tsayin shekaru ba tare ya mora ko ya bari Iyalansa sun mora ba, shi dai kawai burinsa cigaban Yankinsa.
Ɗakinsa ya wuce da tarin kuɗin. Yanayin yadda ya samu fuskar Ɗayyib jiya da ya shiga dubasa na ƙara dawomasa.

A baya Zuciyarsa babu ɗigon rauni ko tsoro sai burin kafuwar Yankinsa, amma a wannan karon zuciyarsa tsoro ne fal a cikinta, a ransa ya yanke ya zama dole ya bar Yankin a wannan karon ya haƙura saboda ba shi da zaɓi ko don ginuwar rayuwar Sulaim da shi kaɗai Allah Ya mallakamai, bayan ya adana kuɗin ficewa ya yi ba tare da ya sanar da Iyalinsa inda zai je ba.

SULAIM;
Bayan ya baro gida Makarantarsu Naila ya wuce, kasancewar su sun rigasu tashi saboda jarabawar da suka fara.

A bakin makaranta ya sa mu Naila da jakarta na buhu saƙale a kafaɗarta. Bai ce mata komai ba ya kwanto da keken ta hau. Har suka ƙaraso ƙofar Gidansu da ya ke maƙota da na su Gidan bai ce mata komai ba. Ya na sauketa dasauri ta sa ɗan ƙaramin hannunta tana lalubar jakarta, kwandala biyu ta fito da shi ta na miƙamai.

"ga shi ka siya wani abun"
Ta faɗa da ƙaramin muryarta na Yara, ta na jiran amsarsa. Saboda sarai tasan ya na magana.

Ɗan mitsitsin hannunta ya kalla da kuɗin sannan ya girgiza kai alamar a'a ya na karkata kan kekenshi alamar tafiya zai yi. Ƙin matsawa ta yi daga gurin ta na kallonshi. Har ya fara tafiya ya kasa jurewa ya juyo.

Hannunshi ya miƙa mata alamar ta kawo kuɗin. Da sauri ta miƙamai ta na dariyar da ya bayyana jerarrun ƙananun haƙoranta. Shima murmushin bazata ne ya tahowa laɓɓanshi wannan dalilin ya sa yabar wajen da zafin namansa.

Har ya rage saura kwana biyu aci kasuwa, Sulaim bai ji mahaifinsa ya yi misa zancen ƙara ƙera wa su tukwane ba, kuma bai ga alamun ya na da niyyar yin wasu ba, wannan dalilin yasa yafara zargin abubuwa dayawa har ya kasa runtsawa, musamman daya ga Mahaifinsa ya tattara duk uban dukiyar da ya ɗauki shekaru yana tarawa a cikin ƙaton buhu ɗaya.

★Washe gari jikinsa sam ba bu ƙwari ya yi shirin Makaranta ya hau kekensa ya nufi ƙofar Gidan su Naila. Tana tsaye ta shirya tsaf cikin wankakkun uniform ɗinta, karkata keken ya yi ta hau.

Bayan sun isa Makaranta ya na sauketa ya juya batare da ya kalleta ba. Sai taji sam ba daɗi a ranta, kafin ta haɗu da ƙawayenta ta manta da komai.

NAILA;
A na tashinsu ta taho da gudu, nan ma Sulaim bai amsa mata gaisuwar da ya saba amsawa da gyaɗa kai ba, duk sai ta ƙarajin ba daɗi, jikinta ya yi sanyi.

Ya na sauketa ta fara lalubar jakarta, soyayyiyar Aya ta fito dashi mai yawa da ta siya kwandala biyu ta miƙamai. Bai karɓaba sai kallonta da ya tsaya yi.

"ga shi Yaya"

ta faɗa da tsoron yanayin fuskarsa. Murmushin yaƙe ya yi ya ce;
"Naila" da muryarsa mai tsada a wajen mutane da daɗin sauraro ga wanda ya samu ji. kanta da ɗago dasauri ta na washe ƙananun haƙoranta kafin ta ce "na'am"
"Idan kina so na karɓa to ki faɗi sunana na ji" ya faɗa yana kallon fuskarta.

dariyar yaranta ta ƙyalkyale da shi, daɗi kamar ya sumar da ita, sai da ta tsagaita sannan ta ce. "Sulaim" ta ƙasara faɗa tana murmushi haɗe da rufe fuskarta. Shima murmushin fuskarsa ce ta faɗaɗa ya na kallon yadda take dariya kamar an bata aljanna. Hannunsa ya miƙamata, da sauri ta miƙamai Ayar ta na shigewa cikin Gidansu ranta fari fes saboda ya yi mata magana baki da baki, ba da kai ko hannu ba. Sannan ta matsu ta shiga gida ta basu labari.

Bayan ya zura Ayar da ta bashi a aljihun gaban rigarsa kasa tafiya ya yi sai da ya ɗan jima a zaune a kan kekensa kafin ya bar ƙofar Gidan...

ABDUH DHAHAB;
bai dawo gida ba, sai dare, Iyalin Mairam ba ta tambayarsa inda ya je, saboda tunda da ya daina kwana a É—akinta take fushi.

SULAIM;
A daren ranar ma kasa runtsawa ya yi, saboda tunani da hasashen da bai san dalilin su ba. Ya na jin ƙewar Naila ba tare da yasan dalili ba ga fargaban dalilin da ya sa Mahaifinsa ya sayar da Tukwanen da zai fitar da su kasuwa washe gari ba tare da ya ƙera wa su ba.


Ƙarfe 2:00am ya ji alamar motsi, gefen Mahaifinsa da ya dawo kwana a ɗakinsa ya kalla ya ga alamar barcinsa ya yi nisa, miƙewa ya yi tsaye.

Wani ƙaramin ƙarfe mai tsini da kaifi ya ɗauka ya soke a gefen ƙugunsa, kafin ya fara takowa tsakar gidan a hankali.

Ya na ƙarasa fitowa tsakar gidan akayi masa yankar da ya sa shi buɗe dukka girman muryarsa a gefen kafaɗarsa na dama. Dole ya zube ƙasa zuciyarsa da gangar jikinsa na karɓar raɗaɗin azaba lokaci ɗaya.

"Au ashe iskanci ne dama ka iya magana?"

Wanda ya yankesan ya faÉ—a ya na sakin dariyar mugunta. Tsaf Sulaim ya É—auki muryarsa duk da ba ya cikin nutsuwarsa.

"Zan Barka a raye matsawar ka faÉ—amin ina Mahaukacin Ubanka ya ke" wanda ya yankesan ya faÉ—a yana É—agoshi.

Shiru Sulaim ya yi ya na kallon fuskarsa dake sakeye cikin baƙin ƙyalle.

Ƙaramar wukar hannunsa yasa ya ƙara yankar gefen kunci Sulaim da ƙarfi haɗe da ƙara maimaita: " ina Mahaukacin Ubanka Abduh Dhahab ya ke, a ina ya zuba tarin dukiyar Tukwanen Zinaren da ya siyarwa Turawan da su ka zo kwana uku da suka wuce? Su na ina!" A wannan karon Sulaim bai saki ƙara ba, sai zaburar dayayi ya soke shi da ƙarfen da ya soke a gefen ƙugunsa a dai-dai saman kafaɗarsa tunda ya na da tsahon ƙafa.

"yaushe Mahaifina ya gama girbar amfanin Irin da ya sha wahala da azabar shekarun shukawa, da har zakazo karɓan na ka kason!?" Sulaim ya tambayesa da sansanyar muryarsa da azaba ta sa ya ƙara yaushi.

Sulaim Bai gama sauke hannunsa da haɗiye yawun kalamansa ba ya ƙara yankarmai gefen kafaɗarsa na hagu haɗe da fesar da hucin haushin kalaman da Sulaim ɗin ya jefesa da shi. Shima Sulaim bai zube ƙasa gaba ɗaya ba sai ya da ya zaro ƙarfen da ya sokamai a kafaɗa ya ƙara kafamai a tsakiyar cinyarsa da dukka ƙarfin daya rage mai. Kusan lokaci ɗaya su ka zube ƙasa. Kowannen su ya na sauke numfarfashin azaba ga jinin da ya ke bin jikin kowanne su.

Kasa jurewa Matar Mahaifin Sulaim da ke laɓe ta yi ta fito ɗaga ɗakinta don tsaf ta haddace muryar wanda ya shigo musu gida.

Da kuka ta fito ta na ba shi haƙuri. Wanda ya yanki ya na ganin fitowarta ya miƙe da sauri kamar ba shi ba, saboda hasashen mallakar dukiyar Tukwanen Zinaren da Abduh Dhahab ya ɗauki tsahon shekaru ya na bautar tarawa ba tare da ya bari ko shi kansa ya mora ba.


Itama tambaya ya titsiyeta da shi ya na rintse idon azabar da ya ke ji, "a ina Abduh Dhahab ya ajjiye kuɗin Tukwanen Zinaren da ya siyarwa Turawan da suka zo? kuma a ina ya ke ɓoye dukka dukiyarsa ki faɗamin na ƙyaleki a raye?" Shiru ta yi ba ta ce masa komai ba, sai kallon bayansa da ya ga ta na yi. Bai kawo komai ba a ransa ya ɗauka halin da Sulaim yake ciki ta ke kallo.

Ganin bazata faɗa ba yasa ya kai mata hauri ta bugi bango da ɗaya ƙafarsa mai lafiya. Ya na juyowa inda ya bar Sulaim yaga ba bu shi a wajen. Kenan Abduh Dhahab yana gidan? maiyasa bai fara bincika ɗakunan Gidan ba tukunna?

"Abduh!!!!" ya faɗa da ɗan ƙarfi yana zare dukka girman idanuwansa da su ka yi jajir

Pito ya yi, abokannan rakiyarsa da suka maƙale suna jiran umarninsa suka shigo Gidan. Biyu zama su ka yi ɗauremasa ciwukan da Sulaim ya ji mai, bayan sun zare ƙarfen cinyarsa, ragowar kuma suka hau bincika gidan.

Sun samu ÆŠakin Abduh Dhahab da duk amintakarsa da Mutum ba ya bari ya shiga, sun bincika amma babu ko sisi a ciki.
Hanyar da jinin Sulaim ya ɗiɗisa su ka dinga bi su na haskawa, har suka samu ta inda Abduh Dhahab da Sulaim suka bi suka bar gidan, ta ƙofar da ba su san da shi ba.

Zabura ya yi ya na haska ƙofar bayan da Abduh Dhahab ya bi har zuwa inda jinin ya tsaya. Dariya yaƙen azabar da ke nuƙurƙusarsa ya saki ya na kutsa kai cikin gidan bayan sun ɓalla ƙofar Moƙocinsa kuma Amininsa da suke kyautata zaton nan Abduh ya shiga.
Da matar gidan su ka ci karo tana salla a tsakar gida. Bai amsa tambayoyin da ta ke jero mu su na dalilin shigo mata gida kai tsaye ba ya ce:
"Sarah! Ina Mijinki ya ɓoye Abduh Dhahab da Ɗan shi? Asibiti ya kai shi, ko su na cikin Gidannan? kifaɗamin gaskiya ko na wulaƙantaki" ya ƙarasa faɗa ya na ƙare mata kallo ta hasken farin watan daya haske gidan.

Da sunan Ubangijin da take ambata ta yi jarumtar furta "Mallam ba ya gari, ya tafi Fansar Litattafai, Asibitin kuma sati É—aya kenan ba a yi aiki a cikinsa ba"

dariya su ka bushe da shi don ko a ranar sun ga mijinta. Ƙasan Gidan ya haska ya na kai dubansa dai-dai wajen da Jinin da ya ɗiɗisa har zuwa inda ya tsaya.

Dai-dai inda Mallam ya ke ajjiye kekunan hawarsa har guda biyu jinin ya tsaya. Dariyar ƙeta ya sa kafin ya ce. "ashe Mallam mai Asibiti da zai fita da dukka kekunansa ya fita Fansar Litattafai kenan? Ki faɗa min wanene ya tuƙa ɗaya keken?" Kai ta girgiza haɗe da yin duk addu'ar dayazo bakinta.

"Wallahi kinji na rantse idan baki faɗamin gaskiya ba zan ƙona gidanan da ke da ƴaƴanki gaba ɗaya." kuka tasa ta na roƙonsa da magiya kala-kala.

Ganin ta na ɓata mu su lokaci ya sa ya ce a ƙona Gidan tunda taurin kai ne da ita. Ta na jin haka ta ce Abduh Dhahab ya zo da Ɗan shi amma sun tafi Asibiti. Dasauri ya ce: "ya zo da kuɗi?"

"Bansaniba amma dai yazo da buhu mai girma da abu a cik.." bai bari taƙarasa ba, su ka bar Gidan.

Ko da sukaje Asibitin Mallam, ba bu Abduh Dhahab da Sulaim kuma ba bu ko sisi sai Mallam da su ka samu yana ƙoƙarin dawowa Gida.

"A wani ɗakin ya ɓoye Abduh Dhahab da Ɗanshi da kuma dukiyar da ya ƙullo a buhu?" Suka tambayi Mallam.

Shiru Mallam ya yi kamar kurma. Sunfi minti 15 su na ta tambayarsa kafin ya basu amsar Abduh Dhahab yana cikin Asibitin da dukiyarshi.

"A wani sashe na Asibitin? kuma a wani ɗaki?" Su ka ƙara tambayarsa Tunda Asibitin ba laifi ya na da girma. Shiru ya yi yaƙi ba su amsa kuma ba bu inda ba su duba ba babu Abduh Dhahab kuma sun kasa gano shaidar ɗakin da zasu sameshi ga dai keken Mallam daya tuƙo a gefe jini duk ya ɓatashi. Kuma Mallam ya kafe Abduh Dhahab na cikin Asibitin da ɗanshi da dukiyarshi. Ganin kamar raina mu su hankali haɗe da son tona mu su asiri ya ke yi. Sai suka turashi cikin Asibitin su ka kulle.

A can gidan Mallam
Suna fita Matarsa ta tattara Æ´aÆ´anta su ka nausa hanyar Yankinsu a cikin daren kamar yanda Mallam ya umarceta kafin ya zo ya samesu.

Bayan sun tura Mallam cikin Asibitin sun kulle, wuta suka saka, sannan suka ƙara dawowa gidan Abduh Dhahab suka yiwa Matarsa kashedi mai zafin da ya kai ga guntule mata ƴan yatsu biyu, tare da yashe duk wasu dukiya da suka samu a ɗakinta na tarin kuɗin la'adar da Abduh yake biyanta idan ta tayasu aiki.

★washe gari labarin gobarar Asibitin Mallam ya karaɗe Yankin, Da farko ba'a fahimci gawar su waye a ciki ba, sai da Surikin Mallam ya biyo jin ba'asi bayan isar Matar Mallam Yankinsu anan ya tarar da mummunar labari, ya kuma tabbatarwa da Mutanen Yankin su Mallam ne suka ƙone, da iyakacin hujjar da ƴarsa ta bashi.


Duk da a kwai waɗanda suka ɗan ji abinda ya faru a cikin daren, amma sukayi shiru su ka ƙi magana, kowa ya ja bakinsa ya tsuke, tunda matar Abduh Dhahab bata farfaɗo ba, tun cikin daren zuwa wayewar gari balle ta faɗi sunan waɗanna su ka aikata a ɗauki mataki a kansu, kamar yanda Sarki Hammam ya bayar da shela.

Gawar Mutum huɗun da aka zaro sun ƙone ƙurumus bakyan gani don babu fuskar wanda aka gane balle a banbance. Ɗayyib ya na kwance lulluɓe cikin abin rufa sai kuka da ihu ya ke yi jikinsa ya na rawa, haɗe da sabbatun su fito masa da Abokinsa Abduh Dhahab, wallahi bai yarda Abduh Dhahab ya mutu ba, wanene ya kashemasa Abduh Dhahab Aminin ƙwarai?


0


09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥


SASAAL


03

A fadar Sarkin Hammam aka sallaci gawarwakin da Sarki Hammam da kansa ya jagoranta. Kafatanin Mazan Yankin ne sukayiwa gawarwakin rakiya izuwa makwancin su. Kafin dawowar su Dangin Mahaifin Mairam (matar Abduh Dhahab) sun zo sun É—auketa saboda gudun abinda zai biyo baya, haka Malik maiyiwa Abduh Dhahab hidimar shara duk safiya shima ana dawowa da ga kai su Abduh makwanci aka nemesu aka rasa shi da Iyayensa.


A wannan ranar kasuwar da Abduh Dhahab ya sha gwagwarmaya shekaru kafin kafuwarsa na siyar da Tukwane ma su Taken Tukwanen ZINARE don cigaban Yankinsa ya yi faɗuwar tasa da ba'a taɓa tunani ba.

Domin duk wanda ya zo ya ji mutuwar Abduh Dhahab ba ya iya tsayawa ya ke juyawa inda ya fito. Dubban mutanen Yankin sun tafka asarar abincin siyarwa da su ka dafa da sauraran kayan amfanin da suka sarrafa don siyarwa baƙin da suke shigowa.

Anya mutuwar Abduh Dhahab bazai kawowa yankin su Talauci mai ƙarfi da koma baya ba kuwa? tunda ta nan suke samun kuɗin shiga ta hanyar abubuwan da suke sarrafawa su siyarwa Baƙin da su ke shigowa, ga kuɗin hayar masauƙin da suke samu da ga wajen baƙin da suke zuwa daga nesa. Dukka wannan ya rushe kenan? Tambayar da Mutanen Yankin suke ta yiwa kansu kenan..


NAILA
Ta fi minti Talatin a tsaye a harabar Gidan su Sulaim ta na jiran fitowarsa, bayan tasha kukan daya ɓata Kyakkyawar Fuskarta da hawaye da majina. Don ita bata yarda Sulaim ya mutu ba.
Daƙyar Babanta ya janyeta shima na shi ran na suya.

Da Surukin Mallam zai koma Yankinsu Sarki Hammam ya umarcesa ida anyi Ukun su Mallam ya kawo masa Sarah ya na son yi mata tambayoyi, tunda Matar Abduh bata hayyacinta. Da "to" Surukin Mallam ya amsa amma har cikin zuciyarsa bayajin Sarah ɗiyarsa zata ƙara taka Yankin..

Da yammacin ranar aka binne su Abduh Dhahab, sai gaba ɗaya mutanen Yankin suka koma zancen asarar da suka tafka, ba tare da sun ƙarabi takan abinda ya yi makasudin ajalin Abduh Dhahab da Ɗansa har ma da Mallam ba. Wannan lamari ya yi matuƙar sosa ran Dajjito Junaid.

Junaid ɗaya daga cikin Dattawan Yankin ne, kuma na hannun daman Sarki Hammam, ba shi alaƙar Jini ko na dangantaka da su Abduh Dhahab.

★washe gari Dattijo Junaid tattaki ya yi har Yankin su Sarah Matar Mallam. Ya sameta a mawuyacin hali mai ban tausayi, iyayenta sun karramashi tare da bashi abin sha don jiƙa maƙoshi. Tambayar duniya Sarah taƙi faɗar waɗanda suka zo gidanta neman Mallam, ƙarshe da Dajjito Junaid ya matsa mata kuka ta fashe da shi raɗaɗin kisan gillar da akayiwa Mijinta na cigaba da sukarta. Ta yaya zata faɗa bayan tasan za su bibiyeta.

Har Rana ta yi Dattijo Junaid bai bar Gidan su Sarah ba. A kan idonshi Iyayen Sarah da ita kanta da Æ´aÆ´anta suka fito da kayayyakin su don yi balaguro tunda sun san dole a bibiyi Æ´arsu gudun kar ta faÉ—i gaskiyar abinda ta sani.

Hawaye Dajjito Junaid ya share ya na bin bayan su. Cikin taushin harshe da amon dake bayyana irin raɗaɗin dayake ji a ƙasar zuciyarsa ya ce;

"Sarah tunda bazaki bani ƙarin haske akan abinda ya faru ba, ki taimaka ki faɗamin inda Mallam yake samun taimakon inganta babban Asibitin mu, da kuma Makarantun ƴaƴamu na roƙeƙi" ya ƙarasa faɗa yana haɗa fararen hannayensa waje ɗaya alamar roƙo. Tsayawa Sarah ta yi zuciyarta na karyewa tsananin tausayin Abduh Dhahab da Sulaim na bijiromata. Sai da ta tattaro dukka jarumtar daya bata damar shanye kukan dake neman cin ƙarfin maganganun da takeson faɗa sannan ta ce;

"Abduh Dhahab shi ne wanda ya gina makarantu da Asibitin daya bawa Mallam amana bayan ya roƙi Mallam ya yi mishi alfarmar kar ya bari kowa ya sani har sai idan shi ya buƙaci hakan da kanshi. Ya ƙare rayuwarsa da Ɗansa wajen bauta muku da son ganin cigaban Yankinku, amma duk da haka sai da kukayi sanadiyar ajalinshi. Tir! da wannan Yanki na ku" ta ƙarasa faɗa tana fashewa da kuka haɗe da barin Dajjito Junaid tsaye da sakekken baki.

Dattijo Junaid Tafiya yakeyi da iya ƙarfinsa amma sai yake ganin kamar baya sauri, burinsa ya isa Yankinsa ya ba su labarin da zai dawo da su hayyacinsu su binkico shaiɗanin dayayi sanadiyar rushewar Yankin su.

Da Yammaci Dattijo Junaid ya iso Yankinsu da labarin alkhairin Abduh Dhahab,
Ba bu wanda ya yarda da shi, sai ma cewa da suke yi;

"Abduh Dhahab ɗin da yake mayen kuɗi ne, zai yarda ya bautawa Yankinsu da dukiya mai yawa irin wannan? Kawai ƙage da rashin son zaman lafiya Dajjito Junaid yake son kawowa Yankin su" ire-iren maganganun da sukai tayi kenan har da masu kwashewa Dattijo Junaid albarka.

★Duk da haka Dajjito Junaid bai gajiya ba washe gari ya ƙara ɗaukar harama ya na shela layi-layi.

"Ya ku mutanen Yankin Tudu! Ina jiyemuku ranar nadamar da zakuyi nan gaba da kuma talauci mai raɗaɗi da azabar da zai iya riskarku matsawar kukayi butulci baku tsaya tsayin daka wajen ganin an binciko waɗanda suka kashe Abduh Dhahab da Iyalinsa ba, lallai sakayya mai raɗaɗi yana nan zuwa garemu, matsawar kuka yofintar da zance na. Haƙiƙa nan gaba kowa a cikinmu zai ɗanɗana kuɗarsa, Wannan wahalar nake jiyemana mutanen Yankina"

Leƙosa sukeyi wa sun su na dariya tare da yin Allah wadai da kalamansa, su na cewa;

"ai mu Abduh Dhahab ya cuta, tunda dama sihiri ya yi wa Kasuwar Zinaren da idan ya mutu Kasuwar da ya gina shima zai mutu baza mu moraba, tsabar mugunta da ya shiryamana har Tukwanensa ya kwashe kaf ya siyarwa da Turawa mu kuma ya barmu da tafka asara" har ya gama Shelarsa ya wuce Fadar Sarki Hammam babu wanda ya ƙullasa.

Da Dajjito Junaid ya yi magana a fada Sarki Hammam, ansamu waɗanda hankalin su ya karkata kan anya labarin da Dattijo Junaid ya zo dashi ba gaskiya ba ne ba kuwa? Haka a ɓangaren Sarki Hammam ɗari bisa ɗari ya yarda da zancen Dajjito Junaid har ya bada tabbacin ƙara zurfafa binciken waɗanda suka aikata wannan mummunan aikin. Dama ya daɗe yana kokwanton waɗanda Mallam ya ce suke ɗaukar nauyin dukka ayyukan tun farkon buɗe Makarantun da Asibiti, da yanda ake biyan ma'aikatan jinya da malaman Makaranta albashi akan lokaci, da yanayin kulawar da ma'aikatan suke samu duk ba iri ɗaya bane da wanda suka samu gwamnati take ɗaukar nauyi.

Ragamar binciken komai Sarki Hammam ya miƙa a hannun Dattijo Junaid.

A wannan ranar da tsananin farin ciki Dajjito Junaid ya nufi Gida.
bai runtsa ba har sai da ya fara kamo bakin zaren abinda yake zargi.

A Yammacin wata Laraba ya shirya kaiwa Sarkin Hammam ziyara, don gabatar da shaidun da zai ƙara buɗe idon mutanen Yankin har su bashi goyon baya wanda ya yi dai-dai da cikar su Abduh Dhahab sati biyu a kaburburan su. Kafin ya buɗe gidanshi anrigasa buɗewa.

★washe gari, har rana ta fito Ba bu wanda yaji ɗuriyar Dajjito Junaid da Matarsa dama kuma Allah bai ba su haihuwa. Wannan dalilin ya sa aka ɓalla Gidan tunda ana da tabbacin su na ciki. Cikin jinin daya bushe aka samu Dattijo Junaid da wuƙa soke a gefen cikinsa, bakinsa ma jini duk a bushe ko da suka duba bakin anyanke mai harshe. Tsohuwar Matarshi kuwa tana Ɗaki a kulle tsoro da tashin hankali ya daɗe da sumar da ita. Mamaki da tsoron ne ya dirarwa mutanen Yankin Tudu, amma dayake yawancin su ma su ƙaranci tunani da kuma hangen nesa ne, sai suka fara surutun;

"ai shi ya jawowa kanshi, tunda ya ce shi bazai kama bakinsa ba"

Ba bu wani cikakken damuwa ko alhinin abinda ya faru da Dattijo Junaid a zuƙatan mafi akasarin mutanen Yankin, wannan ya sa suka cigaba da harkokin gabansu, tare da alƙawartawa kansu jan bakunansu su yi shiru tunda ba su shiryawa mutuwa ba, don babu wanda yaji ko da ihun naiman taimakon su Dattijo Junaid da Matarsa balle su sa ran idan sunyi ihu za su iya samun taimako.

Cikin hikimar Ubangiji numfashin Dattijo Junaid ya dawo cikin tsananin azabar rayuwa ko mutuwa tunda Allah bai ƙaddara ajalinsa a hannun waɗanda suka zo kashesa ba, Itama iyalinshi ta farfaɗo banda kuka babu abinda take yi. Keɓantaccen wajen da babu mai shiga sai Sarki Hammam da mai Maganin da zai dinga duba lafiyarsa Sarki Hamman ya tanada a cikin Marasautar tare da kashe maganar bincike akan kisan su Abduh Dhahab.

Ba bu wanda ya gamsu da maganar Sarki Hammam saboda sun san dole yayi bincike ta ƙarƙashin ƙasa. Don haka waɗanda suke da alhakin kisan suka shiga tararrabi tare da fara tunanin ƙirƙiro abinda zai kawar da hankalin mutanen Yankin da shi kanshi Sarki Hammam.

NAILA;
tun tana sa ran wata rana Sulaim zai dawo har ta gaji da cire rai, sai dai Gidan su ya koma dandali taruwa Yara abokannan wasanta tana ba su tahirin rayuwarta da Sulaim, har da tatsuniyoyi ta ƙirƙira na labarinta da Sulaim. Ba ta fita wasa kullum tana Gida kamar ba Naila mai son wasa da neman tsokana ba.

A cikin watanni biyu da mutuwarsu Abduh Dhahab wani gagarumin Talauci yafara kunnowa Yankin kai. Rana ɗaya suka wayi gari babu Malaman Makaruntun su, Asibitin Mallam da Sarki Hammam yasa aka gyara dukka ma'aikatan jinyar sun gudu. A cikin yini biyu Mutane biyar suka rasa ransu saboda rashin ma'aikatan jinya. Ba bu wani Ɗan Yankin Tudu da hankalinsa bai tashi ba, ciki har da Ɗayyib da bai jima da samun sauƙi ba.

A rana ta uku Mahaifin Naila da ya tashi da tsananin ciwon ciki shima ya rasa ransa zuwa yammaci duk da maganin gargajiyan da akayita É—irkamai don sun je Asibitin Gwamnati ba ma'aikata. Asibitin Mallam dama tuni aka rufeshi tunda dukka ma'aikatan sun gudu.

Rasuwar Mahmoud Maihaifin Naila wani babban gibi ne mai girman gasken da su Naila ba su da abin maye gurbinsa har abada.

A cikin watannin da suka biyo baya wani irin Talauci ya yi wa Yankin mamaya mai ƙarfin gaske, ga shi babu wadataccen ilimi ba bu Ma'aikatan lafiya masu sanin makamar aiki. Zuwa Lokacin Dattijo Junaid ya samu lafiya amma babu damar yin magana.

Suna cikin wannan yanayin Abdullah ya bayyana a matsayin ƙwararren Likitan da Gmannati ta turo.

Sarki Hammam ya yi Farin cikin bayyanar Abdallah a matsayin Likitan da gwamnati na musamman, Saboda sabon abune a garesu, domin shi da al'ummar Yankinsa rayuwa suke yi tamkar ba ƴan ƙasa ba, babu gwamnati da hukuma sam a lamuransu, sai ɗan abinda ba'a rasa ba, shiyasa kowa yake yin abinda ya ga dama

Bayan kwana biyu
Cikin iko Allah marasa lafiya suka fara samun kulawa ta musamman. Mutanen Yankin sun saki jiki da Abdullah tare da wani irin so da sukeyimai saboda sauƙin kansa da iya mu'amalarsa. Wannan dalilin yasa ya buɗe aji koyawa Matasan da suka kai shekaru 18 mata da Maza dabarun kula da mara lafiya da karɓar haihuwa cikin Hikima.

Da kayan aikin dayazo yake koyawa mu su. Kafin rufuwar wata biyu wasun su har sun ƙware.

A hankali labarin alkhairin Abdullah ya fita ko ina na Yankin sai ya zamana har a maƙotan Yankin su ana zuwa ɗaukar Matasa wala Namiji ko Mace don duba majinyaci ko karɓar haihuwa. Cikin lokaci ƙanƙani talauci Yankin ya fara raguwa walwalarsu ta fara dawowa.

A cikin watanni shida Abdullah ya yaye Ɗalibansa haɗe da ƙara ɗiban wa su. Sarki Hammam da Dattijo Junaid baƙaramin alfahari sukeyi da Abdullah ba, girmamashin da suke yi ma na daban ne.

A na cikin haka aka tsinci ƙaramar Yarinya anyi mata fyaɗe mara kyan gani a bayan Ofishin Abdullah.

Duka na rashin imani da manta halacci Mutanen Yankin sukayiwa Abdullah. kafin sanarwar ya isa ga fadar Sarki Hamman har sun sumar da shi.

"Wani irin ƙwaƙwalwa ne a cikin kan Mutanen Yankin Tudu, kuma wacce irin zuciya gare su mai tsanin butulci da manta alkhairi? Ta ya ya Abdullah zai iya yiwa Yarinya ƙarama fyaɗe na rashin imani irin wannan? shin ina hankalin su yake? Maiyasa ake amfani da toshewar basirar su wajen sa su su dakushe cigaban Yankin su da kansu batare da sun sani ba?" Dattajo Junaid ya tambayi kanshi zuciyarsa na Suya.

Daƙyar Fadawan Sarki Hammam suka fatattaki Mutanen Yankin da bulalai.
Babu wani ƙwararren Likita a ƙasa da zai iya kula da Abdullah, sai masu maganin gargajiya aka nemo.

★washe gari duk da haka Mutanen Yankin basu haƙura ba gangami sukayi har Asibitin suna faɗin abi mu su haƙƙinsu, a cikin su har da waɗanda Abdullah ya koyar kuma suke samun alheri. A cewar su "dama sun san dole akwai wanda ya turoshi don cin mutuncin Yankin su" Daƙyar fadawan Sarki Hammam suka ƙara fatattakarsu da bulalai.

★washe gari da sassafe aka tashi da labarin guduwar Abdullah daga Asibiti bayan ya farfaɗo, fadawan Sarki Hammam ne suka bada labarin wani ne yazo da sunan dubanshi shikuma Abdullah ya yi mishi rakiya a daddafe zuwa motar daya zo dashi gabannin Asubahi daganan kuma basu ƙarajin ɗuriyarsa ba.

Labarin sam bai yiwa Wa su marasa goyon bayan lamarin daÉ—i ba musamman Sarki Hammam da mutanensa. Dattijo Junaid kuwa har da kukansa.

Labarin abinda mutanen Yankin sukayiwa Abdullah da labarin guduwarsa har wajen Yankin wannan sai ya sa musu baƙin jini tare da kafa tsoron su da ƙyaƙyamin kulla alaƙa da su a zuƙantan maƙotan Yankunan su.


A wannan yanayin Mahaifan Maman Naila suka zo ɗaukarta tunda ta gama Takaba tuntuni. ko da aka buƙaci su tafi da Naila tunda Yarinyarce, ƙin amincewa sukayi bayan baƙaƙen maganganun da suka gasawa Mahaifiyar Mahmud kakar Naila tare da yin Allah wadai su tafi Yankinsu da jinin mutanen Yankin Tudu.

Dole Naila ta koma wajen Kakarta ta wajen Uba da zama bayan kukan da ta sha har da zazzaɓi.

Cikin watannin da suka biyo baya, Mutanen Yankin suka ƙara komawa Talaucin da yafi na baya muni da raɗaɗi. Ga ƙyama da suke fuskanta daga dukka ƙabilun dake kewaye da su, ko Aure ɗan Yankin Tudu yaje nema ba'a ba shi.


Rana ɗaya dukka matasan Yankin suka yi zuciya suka koma Gona har da Ƴaƴa mata saboda raɗaɗin Talauci da rashin abin yi. Don ko aure Mazan Yankin suka fita nema a mokatan Yankin su ba'a ba su, balle su yarda Ɗan su ya auro mu su Ƴar Yankin Tudu. Wannan dalilin yasa suka fara auren Junansu cikin tsananin Taulauci.

Bayan amfanin Gona ya yi, suka fara fita dashi kasuwanni Yanki-Yanki. Abin mamaki duk Yankin da suka kai ba'a siya sai su ce "Allah Ya raba su da cin kayan amfanin gonar mutanen Yankin Tudu" kamar waɗanda sukayi bar ruwa da guba haka Kayansu ya koma a idon Mutane. Ko wani bare daga wani ɓangaren da bai sansu ba ya yi niyyar siya sai aja kunnensa da kar ya kuskura idan ba haka ba kuwa, tamkar ya kirawa kansa mutuwa ne.

Mutanen Yankin Tudu suna ji suna gani suka ƙara komawa Talaucin dayafi na da raɗaɗi da azaba

Suna cikin wannan yanayin Salman ya shigo Yankin a matsayin mai koyar da sana'o'in da gwamnati ta turo...✍🏻


09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥


SASAAL


04

Bayyanar Salman a Fadar Sarki Hammam a matsayin mai koyar da Sana'o'i ya yi matuƙar faranta ran Mutanen Yankin kamar dai lokacin Abdallah, saboda ya zo akan gaɓar da suke tsananin buƙatar ire-irensa.

Ɗayyib ne ya kawo shawarar mai zai hana a kai Salman Gidan marigayi Abduh Dhahab da tun bayan Mutuwarsa yake a garƙame a matsayin Masauki?. Ba bu jaa kowa ya yi na'am da shawarar Ɗayyib tunda Salman ya ce shi ma Maƙeri ne.

Bayi Sarki Hammam ya bawa mukulli suka gyara gidan.
ÆŠayyib da kansa yayiwa Salman rakiya har gidan Abduh.

Bayan sati É—aya.
Da tsananin Farin ciki da wani ƙauna mara iyaka Ɗayyib ya nufi Salman bayan ya gama kallon irin Tukwanen da Salman ƙera. Rungumesa ya yi ya sumbaci gefe da gefen kunchinsa, sannan ya ce;
"A ina ka koyi ƙera irin Tukwanen da Aminina Abduh Dhahab yake ƙerawa? Tun bayan mutuwar Abduh muka shiga wani yanayin na ƙangin rayuwa, saboda mutuwar Kasuwar Tukwanen Zinaren da yasha wahala kafin kafuwarsa, ba bu wanda ya yi hikimar koya a cikin mu lokacin da ya ke raye, daga shi sai Ɗansa Sulaim ne kawai suka iya ƙerawa. Sai ga shi bayan munfidda rai da ƙarasamun rayuwa mai daɗi Allah Ya Kawo mana kai. Alhamdulillah!" Ɗayyib yaƙara faɗa ƙwalla kwance a ƙasan fararen manyan Idanuwansa.

Salman bai ce masa komai ba sai murmushinsa daya faɗaɗa yana komawa wajen Tukwanen daya ƙera. Har Ɗayyib ya gama santin Tukwanen ya bar gidan Salman bai ce komai

Da Ɗayyib ya kaiwa Sarki Hammam labarin Tukwanen da Salman ya ƙera, Umarni Sarki Hammam ya bawa Fadawansa su bi layi-layi suyi shelar Bayyanar Salman a matsayin mai koyar da Tukwanen Zinare sak irinna Marigayi Abduh Dhahab.

A yammacin ranar suka cika umarninsa,
Nan da nan farin ciki ya mamaye zuƙatan Mutanen Yankin, maimakon su godewa Allah su ƙara sanin amfanin Marigayi Abduh Dhahab a Yankinsu sai suka hau Sukarsa da ce wa;
"Allah Ya sa shima wannan ba irin Abduh Dhahab ba ne mai mugun zuciyar da zai yi sihirin da Kasuwar Tukwanen Zinaren zai ƙara rushewa idan bayanan" da ire-iren kalaman sukai ta sukar Marigayi Abduh Dhahab kenan.
Ba su tsagaitaba har sai da labari ya jewa Sarki Hammam. Da kakkausar Murya ya yi gargaɗin duk wanda yaƙara sukar Abduh Dhahab abisa son zuciyarsa to zai fuskanci hukunci mai tsanani.

Ba bu kunya mutanen Yankin suka cika gidan Abduh Dhahab, Yara da Manya, Maza da Mata Don koyan ƙera Tukwane.

ÆŠAYYIB
Da wani irin takaici yake kallon É—ansa Sufyan, ba don kalamansa suna yimasa daÉ—i ba ya cigaba da saurararsa.

"Baaba tayaya zan koyi ƙera Tukwane da wannan kyan nawa? Baabah ba ƙera Tukwane ne ya dace da Matashi kyakkyawa irina ba. Ni burina shine naje Babban Birni nayi Karatu mai zurfin da zan kawowa Yankina cigaba, amma ba koyan ƙera Tukwane ba gaskiya" Yaƙarasa faɗa yana yin ƙasa da kansa da suma baƙi mai laushi ke kwance luf a kai.

Tabbas! Ɗanshi Sufyan kyakkyawane amma idan aka haɗa kyansa da na Sulaim daya ƙare rayuwarsa wajen bautar ƙera Tukwane to tabbas Sufyan ɗin ba komai bane.
Da taushin Muryar da yake burin Sufyan É—in ya fuskancesa har yagane abinda yake yimasa kwaÉ—ayi ya ce;
"Sufyan Idan har Sulaim da Allah Ya yiwa baiwar kyau ninkin baninkin naka zai ƙare rayuwarsa wajen ƙera Tukwane bisa umarnin Mahaifinsa, to banga dalilin da zai hanaka bin nawa umarnin ba. Sana'a baya hana karatu sai dai ma ya taimaka wajen ragewa Iyayenka ɗawainiya kuma kai kanka sai ka fi jindaɗin kayiwa kanka abu batare da ka jira an ɓata maka lokaci ba. Kaje kayi shawara da Mahaifiyarka amma kasani idan har ka saɓawa umarnina to babu ko sisina a harkar neman Iliminka." Ɗayyib ya na gama faɗa ya miƙe ya bar wajen.

Sufyan ba a iya Cikin zuciyarsa yake jin raÉ—aÉ—i kalaman Mahaifinsa ba har a kan fuskarsa.
Yaushe labarin kyan Sulaim zai gushe a zuƙantan mutanen Yankin. Ya na son ace yana da kyau duk da yayi imanin shi ɗin kyakkyawane, don matan Yankinsu da na maƙotan Yankinsu har so suke yi yayi musu magana. Amma duk wannan yabon kyan nasa da sukeyi da zarar hirar Sulaim ya ratso sai su hau ƙodashi da faɗin da Sulaim ya girma a raye to da babu wani Matashin da zai kamosa a kyau kaf faɗin Yanki, a wasu lokutan ma sai su ce har da maƙotan Yankunansu, duk ranar da irin haka ta ratso a gabansa ko labari yazo kunnensa yini yakeyi yana kallon ƙaton madubin Gidansu.

Hindu Mahaifiyarsa mai taya ɓera ɓari kullum ƙara zugasa take yi da cewa; "ba wai su na zuzuta kyan Sulaim ba ne don dagaske ya na kyan ba, sai don Tukwanen Zinaren da Mahaifinsa ya ƙirƙirowa Yankin, idan shima yaje Babban Birni Ya yi karatu mai zurfin da kaf faɗin Yankin ba bu mai kwatankwacinsa to ba shakka shima zai zama abin kambabawa, kar ya kuskura ya yarda da batun Sana'ar da Mahaifinsa ya jima yana burin ya yi, idan ba haka ba Sulaim shi zai cigaba da zama Saurayi mafi kyau a Yankin duk da baya raye, idan ma ya lura sun mayar da labarin kyan Sulaim kamar wani Tarihin da suke kambawawa. musamman ga waɗanda ba su sanshi ba" har alƙawarin auren gata tayimai da wacce zata bauta mai kamar Sarki idan har ya cikamata burinta na zuwa Babban Birni karatu.

WaÉ—anan huÉ—ubobin da su Sufyan yake kwana kuma yake tashi.

A ɓangaren Mutanen Yankin ma su koyan ƙera Tukwane a wajen Salman sosai suka nuna jajircewarsu da farko, amma da tafiya tai tafiya sai suka fara nuna gajiyawarsu har sai da Salman ya zaburar da su da kalaman asalin wanda ya ƙirƙiri Tukwanen;

"Ba a lokacin da muka shuka iri, zamu girbi amfaninsa ba dole sai munjira kuma munyi haƙuri tare da yin aiki tuƙuru" waɗannan kalamai na Salman baƙaramin tsoratar da Mutanen Yankin ya yi ba, musamman ga waɗanda sukayiwa Abduh Dhahab farin sani. Tsoron kar su wayi gari wata rana su ga babu Salman don sun fi alaƙanta shi da aljali saboda kalamansa masu kamaceceniya da Abduh Dhahab, sai suka ƙara zage damtse.

Labarin kamaceceniyar kalaman Salman da Abduh Dhahab dayake yawo a gari har kunnen Naila da Kakarta. Naila data kasa samun sukuni a sace ta tafi Gidan ba tare da sanin Kakarta ba.

Sai da ta yi zuwa har biyu amma ta kasa shiga sai dai ta laɓe tana Kallonsa.

A ranar zuwanta na uku Salman ya kamata. Har cikin gidan ya riƙo hannunta ya shigo da ita.

"Maiyasa kullum kike zuwa ki maƙale kina kallona, mai kike nema?"
Salman ya tambayeta yana kallon cikin idonta.

Murya na rawa Naila ta ce "inaso nasan labarinka, inaji a jikina kamar Kanada alaƙa da su Sulaim, shin dagaske Sulaim yaƙone bazai ƙara dawowa ba?"

Kamar wanda ya ke son haddace halittun fuskarta haka Salman yake kallonta kafin ya ce;
" Ki je nan da Sati biyu ki dawo zan baki labari" ya ƙarasa faɗa ya na turata waje haɗe da kullo ƙofar Gidan.

Daga wannan rana Naila ta fara lissafin kwanakin da Salman ya É—ebarmata ba tare da sanin Kakarta ba.

A ɓangaren Mahaifiyar Naila tun bayan komawarta Yankinsu, zumuncin da dama can akwai shi tsakaninta da Mairam Matar Abduh Dhahab ya ƙara ƙarfi kullum ita take kula da Mairam a gidan take wuni sai dare take dawowa gida. Mairam tana samun sauƙi amma kullum a cikin kuka take ba magana.

Ranar da ta buɗi baki ta tambayi Ruwa, gidan ruɗewa sukayi da farin ciki ba iya su kaɗai ba har mutanen Yankin da labari ya je wa. Murnar fara maganar Mairam kaɗan-kaɗan yasa Mahaifiyar Naila yanke shawarar kwana a gidan, acewarta " yau kwana zamu yi muna hira" ta ƙarasa faɗa tana dariya.

Babu zato babu tsammani
A daren ranar aka kawo mummunar harin da ya faÉ—a kan Mahaifiyar Naila.

★washe gari da Sassafe Jama'ar Yankin suka kewaye gidan.

kuka mai raɗaɗi da ciwon gaske Kakannin Naila suka ƙanƙanme juna su na yi, lokacin da sukayi ido biyu da gawar ƴarsu. Ga shi Mairam da Mahaifanta sun gudu, tun Asuba..

Bayan an kimtsa gawar Mahaifiyar Naila kafin a kaita, Mahaifinta shi da Mutanen Yankinsa sukai gangami har Fadar Sarki Hammam, don suna kyautata zaton fara maganar Mairam ne yasa suka zo kasheta don karta faÉ—i abinda ta sani tsautsayi ya faÉ—a kan ta su Æ´ar.

Bayan sun samu shiga Daular Sarki Hammam maganganun ma su nauyi a harshe da raɗaɗi a zuciya Kakan Naila da mutanen Yankinsa suka fara zazzagewa Sarki Hammam da Muƙarrabansa. Zafin kalamansu dayake nuna cin fuska ƙarara ga Sarki Hammam yasa Fadawansa nufarsu da manyan bulalai.

Sarki Hammam dakatar da su ya yi, sannan ya yi wa Kakan Naila alƙawarin yin adalci matsawar ya bincika ya gano dagaske da hannun Mutanen Yankinsa akan kisan gillar da akayiwa Ƴarsu to zai hukuntasu dai-dai da abinda suka aikata.

Da wannan yarjejeniyar Kakan Naila da mutanensa suka bar Yankin, ko kallon Naila dake kuka kamar ranta zai fita basu yi ba.

Su na tafiya Naila da Kakarta suka shirya suka nufi Yankin.

Abun takaici bayan isarsu ko wajen zama ba'a basu ba, a cikin bainar jama'a, Kakanninta suka ce sun yafe ta, babu su babu ita, kuma karsu ƙara ganin ƙafarta a Yankinsu.

Naila tana kuka suka dawo Yankin Tudu.


A yammacin ranar sai da Sarkin Yankinsu Kakannin Naila na wajen Uwa, yaje har Yankin Tudu duk dai akan kisan gillar Mahaifiyar Naila, alƙawarin da Sarki Hammam ya yiwa Kakan Naila shi yaƙara yiwa Sarkin su.

Bayan Sarkin su ya dawo ya tattauna da Kakan Naila. A take Kakan Naila ya yafewa Iyayen Mairam tunda tafiyar tasu shine nutsuwar su da na Mutanen Yankin gaba É—aya.

Naila bayan sun koma Gida kafin dare ya yi zazzaɓi mai zafin gaske ya rufe ta har bata gani da kyau.

A haka tasha jinyar da tayi sati Uku a kwance. Bayan ta wartsake ta tuna alƙawarinta da Salman sai dai babu damar zuwa saboda shirye-shirye bikin sake buɗe Kasuwar Tukwanen ZINARE, da za'ayi washe gari.

A ɓangaren Salman tuni ya manta da batunsa da Naila ya cigaba da abinda ya kawosa.

A daren washe garin da za'a buÉ—e Kasuwar Tukwanen Zinare, Sarki Hammam ya gayyacesa cin abinci..

Salman ya samu Tarba mai kyau daga Sarki Hammam, bayan sun kammala cin abinci, Sarki Hammam ya buƙaci tattaunawar sirri da shi game da shugabancin kasuwar Tukwanen Zinare.

Sarki Hammam da kansa ya faÉ—i sunan wanda yakeso ya zama Shugaban Kasuwar da kuma Mataimakinsa. Salman bai musa ba, shi dama aikinsa koyar da Tukwane kuma ya yi ya gama.

Sai dare sosai ya dawo Gida.

★washe gari kowa na Yankin bakinsa a washe, saboda dawowar Kasuwar Tukwanen Zinare babban nasara ne gare su baki ɗaya.
Bayan anci ansha Salman ya fara jawabi;

Bayan ya yi godiya ga Allah ya É—ora da jawabin godiya da kuma muhimmancin sana'ar da suka koya.
Can murnar kowa ya tsaya lokacin da Salman yake ƙoƙarin sanar da Shugaban Kasuwar Tukwanen ZINARE. Kowa burinsa ace shine ko wani nasa ne.

A bisa tattaunawar da Salman ya yi da Sarki Hammam bayan sun gama cin liyafar daya gayyacesa a daren jiya, ya sanar da ÆŠAYYIB a matsayin shugaba DATTIJO JUNAID kuma mataimakinsa.

Hayaniya ne ya ɓarke wasu suna ganin Dittijo Junaid da baya iya magana bai cancanci ya zama Mataimakin Ɗayyib ba, wa su kuma daga Ɗayyib har Dattijo Junaid ɗin duk basa so. A haka taro ya watse wasun su rai a ƙuntace da alwashi kala-kala.

Salman tare da Dattijo Junaid da Ɗayyib, gidan Abduh Dhahab dayake a matsayin Masauƙin suka wuce don yin bankwana saboda washe gari zai koma ƙasar su.

Sun shafe awanni suna tattaunawa kafin dukkan su su miƙe suna ƙarayin musabaha. Dai-dai lokacin da suke yunƙurin fitowa sukaji ana kwaɗa sallama haɗe da ɗan bubbuga Gidan.

Tare suka fito Salman ya buɗe ƙofa, kafin ya ankara aka fara sararsa ta ko ina...

Kamar dai Shekarun baya lokacin su Abduh babu wanda ya leƙo, duk da anajin kururuwarsu✍🏻

09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥 ZINARE 🔥


SASAAL


05

★washe gari da dukuku Maƙotan da suka ji kururuwarsu suka kai koken sun ji ihu a gidan Marigayi Abduh Dhahab jiya da daddare.

Sarki Hammam a kiɗime ya miƙe shi da Muƙarrabansa suka nufi gidan Abduh.

Kafin gari ya ƙarasa haske labari ya karaɗe ko ina.

Kafatanin Mutanen Yankin Tudu ne suka yiwa Gidan Marigayi Abduh Dhahab zobe, kowannen su zuciyarsa cike da tsoro da wani fargaba mai girma gaske. Yunƙurin faɗar gaskiya a Yankinsu ko kawo wani cigaba ya zama babban musibar da Mutum zai iya rasa ransa a kai.

A cikin Gidan Marigayi Abduh Dhahab Gawar Salman ne a yashe, ya yi kacha-kacha cikin jini, sai Dattijo Junaid da shima idonsa ɗaya yake a tsiyaye bayan raunuka marasa kyan ganin dayake jikinsa. Haka Ɗayyib shima wuƙa ne soke a gefen cikinsa sai raunukan da ba'a rasa ba.

Sarki Hammam kansa ya ɗaga sama, sai da ya tabbatar ya shanye ƙwallar da ya yiwa ganinsa yana sannan ya ɗurkusa a gaban Gawar Salman.
Baƙin cikin da yake ji bai tsaya a iya cikin zuciyarsa ba har saman fuskarsa, yana son Salman sama da son da ya yi wa Abduh, saboda ya taimaki Mutanensa a lokacin da suke da tsananin bukata, amma wannan baisa sun rangwantamai ba har sai da suka kaishi ƙasa kamar yanda su ka kai Abduh. Fari ƙal ɗin hannunsa da ya ɗan fara yamushewar tsufa yasa ya shafi fuskar Salman, kafin ya miƙe don a samu damar fitar da su daga Gidan.

Fito da Salman a luluɓe har kaa, saɓanin ragowar yasa zuciyar kowa ƙara karyewa. Banda koke-koken muryoyi daban-daban ba bu abin yake tashi a ƙofar Gidan.
To ko dai Tukwanen Zinaren ne ba'a so a Yankinsu tunda shine sana'ar da yafi kowawa Yankinsu kuɗin shiga? Wanene yake musu wannan Ta'addacin a Yanki? Daga Abduh Dhahab har Salman dukkan su maƙera ne, ma su kamaceceniya a ɗabi'u har ma da wasu maganganunsu. kenan anfiso su cigaba da rayuwa cikin azaba da ƙangin Talauci? Tambayar da Mutanen Yankin Tudu suke ta yiwa junansu kenan.

Kamar shekarun baya da suka shuɗe, Daular Sarki Hammam aka wuce da Gawar Salman anan aka Sallacesa, bayan an miƙa su Dattijo Junaid da Ɗayyib Asibitin da babu likitocin azo a gani.

Fargaba mai gusar da nutsuwa ne ya dabaibaye zuciya Sarki Hammam, dalilin haka yasa Jininsa ya hau dole aka buƙaci Likita daga Babbar Birnin Abyad don kula da shi da su Ɗayyib.

Kafatanin Mazan Yankin Yaransu da Manyansu ne suka tafi kai Salman makwancinsa cikin su har da Manya masu faÉ—a aji a fadar Sarki Hammam.

Daf da zasu shiga Maƙabarta aka sani harbin bindigar da yasa mutane dayawa darewa . Ma su ɗauke da Gawar Salman ma ajjiyesa su ka yi sai dai su ba su gudu ba, su na dai tsaitsaye. Ƙarar Harbin da'asaki sau biyu a jere ne yasa suma suka tarwatse aka bar Iya Gawar Salman.

Mota mai tudu baƙi mai tsananin sheƙin dake bayyana girman dukiyar da'a zuba kafin mallakarsane ya yi parking a gefen Gawar Salman.

Maza majiya ƙarfine suka fara fitowa ɗaya bayan ɗaya har su uku a jere kafin fitowar na huɗunsu.
Fitowar na huɗunsu ne yasa Bashar kawun Ɗayyib kuma mai faɗa aji a Masauratar Yankin Tudu da ke laɓe a ɓoyarsa shi kaɗai kuma ya sawa zuciyarsa dole sai ya ga duk abinda zai faru zare dukka girman fararen manyan idanuwansa na Usul ɗin Mutanen Yankin Tudu. Fitsari mai ɗumin gaske na biyo jikinsa, a take ya ji idanunsa na ƙyaƙyayin azaba. Amma duk da haka taurin zuciya, da kafawa duk abinda yasa a gaba ƙahon zuƙa sai yaga bayansa yasa ya ƙi kulle idanuwansa kamar yadda ragowar su ka yi a maɓoyarsu.

Ba bu rahama a fuskar na huÉ—unsu da yafi su girma da tsaho, hannu ya sa ya É—auke Salman a makara, yanayin yanda ya É—agashi na bayyana rauninsa. dasauri ragowar ukun suka buÉ—emasa bayan mota ya shimfiÉ—esa.

Harbi suka ƙara saki amma duk da haka fararen idanuwan Bashar da suka koma jajaye na tsaye ƙyam a kansu. Yunƙurin shigar su Mota yasa ya ɗan lumshe idanuwansa na seconni ko zai samu sassaucin zugin azabar da idon yake mai.
Ɓude idanuwan da Bashar zai yi ya tsinci Mutum biyu a gabansa, dama ba bu wani tazara a tsakaninsu. Ya kasa ihu saboda duniyar fargabar daya tsinci kansa a ciki. Kamar Kayan wanki haka suka ɗebesa har Gaban mutumin da Kallonsa daga nesa kaɗai ya sa shi sakin fitsari. Ƙasa Bashar ya yi da kanshi jikin da dama can lallaɓawa yake yi saboda yawan shekaru ya fara karkarwa. Ɗago shi ya yi suna kallon tsakiyar idanuwan juna, idon Bashar kamar an tsiyaya jini tsabar jan da sukayi. Ƙasa Bashar yaƙarayi da kanshi saboda gudawan daya tahowa mai, ba ya kuma burin ya ƙara kallon ko da fuskarshi ne balle cikin idanuwansa saboda tsoro. Bashar bai gama saƙe-saƙen da yake yi ba yaji ya ƙara ɗago Kanshi. Da ƙarfi ragowar suka buɗemai baki. Gurnanin azabar gaske Bashar ya saki lokacin da na huɗunsu ya ciremai harshe kwatankwacin yadda aka yanke na Dattijo Junaid. Watsar da shi su kayi suka faɗa Mota kamar iska haka suka bar wajen da Yankin Tudu gaba ɗaya.

Gurnanin azabar da Bashar yake yi babu wanda bai jiyosa ba a maɓoyarsa ba, amma tsoro ya hana kowa fitowa duk da Matsayin da Bashar ya ke da shi a Daular Masarautarsu.

A ɓangaren Sarki Hammam duk bai san wainar da'ake toyawa ba saboda barcin daya ɗaukeshi, suma waɗanda suka rage a Masarautar laƙwas su kayi kamar basusan abinda yake faruwa ba, tunda wanda zai tilasta mu su fita kai agajin bai san ma anayi ba.

Sai da kowa ya yi hour biyu da ɗoriya a maɓoyarsa sannan duk su ka firfito, zuwa lokacin tuni Bashar ya yi suman azaba. Ko takan inda harshen da suka yanke yake basu bi ba suka saɓashi a guje sai Asibiti. Daga Asibiti kowa ya silale ya yi Gida haɗe da kulle ko ina.

Har aka kwana aka wuni Yankin Tudu tsit kamar babu kowa.

A ɓangaren Naila tayi kukan mutuwar Salman, har sai da ya saukar mata da ciwon kai mai nauyin gaske, gashi babu damar fita kaita Asibiti saboda tsoro. Haka Kakarta tayi ta yimata jiƙe-jiƙe har zuwa washe garin da ta ji ɗan dama-dama.

Da wani kallo ta kalli Kakarta murya na rawa ta ce;
"Maiyasa ake kashe kowa haka, shin su Abduh da aka kashe basu da dangine? su waye danginsa maiyasa ba su É—auki mataki ba? da sun É—auki mataki da yanzu ba akashe Salman ba, Kaka su waye dangin Abduh Dhahab? maiyasa suka wofintar da al'amuransa a haka?"

Kaka murmushi ta yi tana shafa kan Naila ta ce;
"Ki bari ki ƙarasa warwarewa In Sha Allahu zan baki labari"


SARKI HAMMAM
★washe gari da Sarki Hammam ya farfaɗo ya samu labarin abin ya faru. A gaggauce ya yace a shirya mishi zuwa ganin Bashar.

Lokacin da ya isa Asibiti da ake yiwa su Ɗayyib, Dattijo Junaid da Bashar maganin gargajiya kafin ya shiga Ɗakin da Bashar yake saƙon Dattijo Junaid ya riskeshi na;

" idan ya shigo yane raye, a faɗamasa yazo gareshi yana da saƙo."

Sarki Hammam ya na jin saƙon Dattijo Junaid ya fasa shiga Ɗakin Bashar ya wuce na Dattijo Junaid bayan ya dakatar da kowa daga bin bayansa.

Kallon yadda Dattijo Junaid ya koma kaÉ—ai wani abin fargaba ne. Bayan ya yi mai ya ya jiki ya naimi waje ya zauna.
Alama da salon maganar kuramen da Dattijo Junaid ya saba yakeyiwa Sarki Hammam bayani, cikin ikon Allah, Ubangiji ya bawa Dattijo Junaid ikon yin bayani kamar da bakinsa yake magana tsabar yanda Sarki Hammam ya ke fahimtarsa.

Bayan ya gama bayani Hannunsa Sarki Hammam ya kamo. Junaid Amininsa ne tun suna Yara amma banbancin Gidan da suka fito ne ya nisanta Amintakarsu dole, Bayan ya zama Sarki Junaid ya dawo ƙarƙashinshi Bashar ya maye gurbinsa na Amini.

Sarki Hammam Ya na cikin wannan tunanin Allah Ya amshi ran Dattijo Junaid. Kuka ya zauna yi kamar ƙaramin Yaro. Ya yarda Bawa baya mutuwa har sai idan lokacin da Ubangiji ya ɗebarmasa sun cika, banda haka tayaya Dattijo Junaid zai yi ƙarfin zuciyar rayuwa bayan yana kallon ajalinsa a kusa dashi ko da yaushe kuma ya ja bakinsa ya yi shiru?.

Mutuwar Dattijo Junaid da hasken da Sarki Hammam ya samu dangane da badaƙalar dake addabar Yankinsa a ɓoye bai tsaya a iya hawan jininsa ba har jinya ya kwanta, don dole aka fitar dashi Babban Birni Abyad.

Mutuwar Dattijo Junaid da abinda ya samu Bashar ya kasa hankalin mutanen Yankin kashi-kashi. Wa su sun yarda waɗanda suka zo a Baƙin Mota sune suke yiwa Yankinsu aika-aika, wa su kuma suna ganin sam ba haka bane idan hakane aiba Bashar zasuyiwa haka ba kawai dai Ƴan uwan Salman ne suka zo ɗaukar fansa, to amma ta ya ya akayi suka san mutuwarsa? tunda babu komai na Salman da ba'a bincika ba amma an kasa gano daga inda yake.

Daga wannan lokacin baƙin jininsu sai ya ragu a zuƙatan Maƙotan Yankinsu saboda da yawa sunfi yarda masu Baƙin Mota ne suke yiwa Yankin ta'asa tuntuni, ba wai Mutanen cikin Yankinba

Bayan wani lokaci, Sarki Hammam ya dawo daga Babban Birni Abyad, Bashar shima ya samu sauƙi.

A Fadar Sarki Hammam aka gayyato ƙwararrun ma su zane don su zana wanda Bashar ya haukace yana ta kwatance har da kaisu gidan Abduh Dhahab, duk wannan kwatancen na shi ba bu wanda ya ɗauki hasken komai Sai Sarki Hammam dashi ƙadai yasan wanda Bashar yake nufi daga bayanin da Marigayi Dattijo Junaid ya yi masa. Shara da tsaho yake ta kwatantawa, banda wannan ya kasa siffanta komai. Sai da ƙyar ya fara zayyano siffar wanda sam babu ko mai kamanninsa a Yankin. Dole yana ji yana gani masu zane sukayi tafiyarsu.

Kwanaki bayannan Sarki Hammam yasa atara mishi mutanen Yankin don zaɓar sabon Shugaban Kasuwar Tukwanen ZINARE da Mataimakinsa tun da har lokacin Ɗayyib bai samu sauƙi ba..


41 3080: 🔥ZINARE🔥


SASAAL
Arewabooks@sasaal


06

Kamar ko da yaushe Layi-layi aka bi ana shelar Sarki Hammam ya na buƙatar ganin Mazan Yankin a Masarautarsa..

Kafin ka ce me, kafatanin Magidanta Yankin sun cika harabar Masarautar.

Bayan an ansanar da su saƙon Sarki Hammam, na shin akwai Mai son zama Shugaban Kasuwar Tukwanen Zinare a cikinsu? Ba bu wanda ya ɗaga hannu, ɗaya bayan ɗaya suka dinga sulalewa kafin Minti Talatin filin ya dawo fayau babu kowa, dalili; kowa tsoro yake ji, kar ya karɓi Shugabancin shima a biyosa har gida akashe shi.

SARKI HAMMAM;
Da labarin guduwar Mutanen Yankin ya riskesa ajiyar zuciya ya sauke. Shikenan! Maƙiya Yankin sunyi nasara akan Mutanensa, dama tsoro da gudun mutuwa akeson dasa musu, su dawwama yin rayuwa cikin Talauci, da ƙin faɗar gaskiya ko da za'a kashe na su a gabansu saboda su tsira da rayukansu, duk da mutuwar dai da aka dasa musu tsoronta suke gudunta zai riskesu idan kwanansu ya ƙare.

Kansa ya dafe, ya na jin raɗaɗi a cikin zuciyarsa kenan Mutanen Yankinsa sun gwammace ko shekara nawa Ɗayyib zai yi a kwance zasu jirashi ya jagorance su, idan ya ga zai iya idan kuma ba zai iya ba su haƙura da kasuwar gaba ɗaya. "Kaico" Sarki Hammam ya faɗa a sarari.

★Kasa jurewa ya yi, washe gari ya ƙarasawa ayi shelan;
"shin da wanda ya ke so ya zama Mataimakin ÆŠayyib idan ya warke?" Nan ma babu wanda ya amsa tsit sukayi a cikin Gidajensu kamar ruwa ya cinyesu.

Da aka ƙara sanar masa babu wanda ya daki ƙirji ya fito, Gaba ɗaya sai ya rasa abinda yakemasa daɗi, ba shi da wanda ya yarda da shi a kusa da shi balle ya tattauna damuwarsa da shi, saboda masu aikata ɓarnar a kusa da shi suke ta yanda ba shi da yadda zaiyi ya yakicesu, kuma ko da ya faɗi ma su aikata ɓarnar kai tsaye babu wanda zai yarda da shi.

Ya zama dole ya canza salon dabarar mulkinsa shima, don tsirar da Mutanen Yankinsa.

Bayan wani lokaci...

A ɓangaren Ɗayyib ba laifi yanata samun sauƙi saboda ƙwararrun likitocin da suke shigowa dubashi akai-akai, don da farko a Yankin Tudu ya yi ta jinya, sai dai rashin likitoci ya sa aka fitar da shi wani gari da yake kusa da Babban Birnin Abyad.

A cikin watanni ya warke tsaf kamar bai taɓa jinyaba. Da tsananin farin ciki shi da Iyalinsa suka ɗauki hanyar Yankin Tudu.

A ranar da ya dawo Gida bayan ya huta Sashen Bashar da yake a matsayin ƙanin Mahaifinsa Jalal uwa ɗaya uba ɗaya ya nufa.

BASHAR
Lokacin ya yi ido biyu da ÆŠayyib da sauri ya rungumesa ya na yi mai kwataccen ya ya jiki?

Amsawa ÆŠayyib ya yi haÉ—e da jajantamai abinda ya sameshi.

Bayan sun ƙara gaisawa, Ɗayyib ya tambayi Bashar garin ya ya haka tafaru? Da kwatancen Gidan Abduh Dhahab ya fara.

Ɗayyib mutum ne mai kaifin Basira da saurin Fahimta, wannan dalilin ya sa kai tsaye ya fahimci dole wanda ya gutsewar Bashar harshe yana da alaƙa da Gidan Abduh Dhahab.
"Sulaim ka gani, ko Abduh ko Mairam?" ÆŠayyib ya tambayeshi a nutse. Shiru Bashar ya yi takaicin ÆŠayyib na kamasa tayaya zai iya faÉ—amai bayan ya ambaci sunayen su dukka a lokaci É—aya? Ganin ya yi shiru kamar mai tunanin yasa ÆŠayyib umartar a nemo mai zane....

Bayan mai Zane ya iso..

Fuskar Abduh ya fara zanawa da kwatancen da ÆŠayyib ya ke yi mai, Bashar ya ce ba shi bane an zana Sulaim da Mairam suma ya ce dukka ba su bane.

Bashar miƙewa ya yi yana kwatanta tsaho da shara, har ya gama kwatanta iyakacin abinda zai kwatanta babu wanda ya fahimcesa.

Dole Ɗayyib ba shi da zaɓi tunda sam yakasa fahimtar wanda Bashar yake nufi don haka ya sallami mai zane.
Mai zane yana tafiya shima ya bar Sashen zuwa na Jalal Mahaifinsa ransa babu daÉ—i.

Da Daddare
Bayan Ɗayyib ya koma Gida, har dare ya nutsa, ya kasa runtsawa har wajen ƙarfe ukun dare. Babu irin tunanin da baiyi ba game da wanda Bashar yake nufi amma yakasa gano wanene wannan. Ba don yana jin barci ba ya kwanta haɗe da rintse idanuwansa.

★washe gari da Asuba da tsananin ciwon kan rashin samun isasshen barci ya ɗora alolar Sallar Asubahi, har lokacin da tunanin wanda Bashar yake nufi maƙale a cikin zuciyarsa. Dama baya zuwa Masallaci, a tsakiyar ɗakinsa ya shimfaɗa abun Sallah ya tayar.

Ɗayyib yana cikin sallah raka'ar ƙarshe ƙwaƙwalwarsa ta harba. Shaidan ya samu damar wasa da hankalinsa haɗe da tuna masa abinda ya kasa tunawa
"shara? tsaho? Anya ba MALIK Bashar yake nufi ba?

WANENE MALIK;
MALIK hadimin Gidan Abduh Dhahab ne, kullum shi yake sharar harabar Gidan duk Safiya kuma ÆŠa ne ga Amininsu ÆŠayyib da Abduh Dhahab. Tun yana Yaro Mahaifinsa ya bawa Abduh Dhahab shi yake masa Hidimar share-share.

Bayan kai gawar su Abduh Dhahab makwanci aka naimi Malik da Iyayensa aka rasa sun gudu, babu wanda yakawo tunanin komai a ransa, sai tunanin sun gudune don tsiratar da rayuwarsu, tun da Malik yasan wasu sirrikan na Abduh Dhahab sama da su ÆŠayyib da suke Abokanansa.

Malik ya na da tsaho na gaban kwatacce don dalilin tsahonsa yasa Abduh Dhahab yake tsananin sonsa saboda irin siffar Sulaim Ɗansa dana Mahaifiyarsa Nanaah yake da shi, ba irin Siffar Mutanen Yankin Tudu ba, Taƙaitaccen labarin Malik kenan...


Ɗayyib cikin rashin nutsuwar zuci da na gangar jiki ya sallame. Daƙyar ya taushi kansa har ya bari gari ya yi haske. Wani ƙulli ya ɗauka ya zura a aljihunsa, sannan ya bar gidan.
Wajen masu zane ya fara biyawa ya taho da har mutum uku, suka nufi Gidan Bashar..

Bayan sun haÉ—u a Sashen Bashar da kansa ya kwatanta mu su Malik suka zanashi kamar zai yi magana.

Bashar yana ganinsa ya miƙe jikinsa yana rawa haɗe da gyaɗa kai alamar shine.
ÆŠayyib bai ce komai ba har sai da ya tabbatar ya sallami ma su Zane sun tafi, saura isu-isu Æ´an Gida sannan ya matso kusa da Bashar yana kallon tsakiyar idanuwansa ya ce;

" Idan Malik da kowa yasan matsayinsa a Gidan Abduh Dhahab zai kamaka kai kaɗai akaf faɗin Yankinan ya yankemaka harshe to ba shakka kanada masaniya akan Kisan Abduh. Menene gaskiya?" Ɗayyib ya tambayi Bashar idanuwansu sarƙafe a cikin na juna.

Wani irin yaushi idanuwan Bashar sukayi haka tattaurar zuciyarsa. Bai ce komai ba sai ƙasa da ya yi da kansa domin tambayar Ɗayyib alamu ne na shima ƙarshensa yazo.

Jin shiru bai ɗago ba har na tsahon daƙiƙu yasa Ɗayyib dafashi, sharaf ya zube ƙasa daga zaunen dayake kamar Gini. Ɗayyib ne ya kinkimesa da sauri ya yi gaba, Kafin su je wajen mai magani rai ya yi halinsa.

Da labarin mutuwar Bashar da abinda ake zargi, ya riski Sarki Hammam bai ce komai ba banda hutun da yake ɓukata don haka ya Yanke shawarar da zarar anyi bakwai zai bar Yankin na wasu watanni kafin nashi shima lokacin ya yi.

Mutuwar Bashar ya sanya nutsuwa a zuƙatan mutanen Yankin don gani suke yi dama Bashar da Allah Ya tonawa Asirine kaɗai matsalar Yankinsu kuma gashi ya mutu, ba su yi tunanin ina magoya bayan Bashar ɗin suke ba, domin bai isa ya yi wannan ɓarnar shi kaɗai ba.

Tuni kowa ya saki jiki suka fara ƙera Tukwane ba ji ba gani don tunkarar Kasuwar Tukwanen Zinare da ƙafar dama, har lokacin Ɗayyib ba shi da Mataimaki, shi kaɗaine Shugaba.

NAILA;
Tun tana tambayar Kakarta game da su wanene ahalin su Abduh Dhahab har ta gaji ta haƙura.

Da kowa ya fara haɗa kayan sana'ar da zai shiga Kasuwar Tukwanen Zinare da shi, kayan wasan Yaran da mahaifiyarta take yi itama dama can ta iya, tafara ƙerawa Kakarta tana tayata. Gwanin sha'awa ta ƙera su Tukwane, randar ruwa, murhu harda talabijin duk na lakar ƙasa.

Mutanen Yankin da ƙafar Dama suka shiga kasuwar Tukwanen Zinare, domin babu wanda bai siyar da kayan sana'arsa ba.


*********************************************
Kwanaki sun miƙa, Shekaru sun shuɗe abubuwa sun sauya, yawanci daga sauƙi zuwa tsanani.

SUFYAN ÆŠA A WAJEN ÆŠAYYIB;
ya zama ƙosasshen Saurayi, kyakkyawan da yake taƙama da kyansa da kuma zamowar Mahaifinsa Shugaban Kasuwar Tukwanen ZINARE. ya yi niyyar ajiye burinsa na zuwa Babban Birni ya yi ilimi mai zurfi amma ranar da faɗa ya haɗasu da Kabeer Abokinsa ɗan Gidan ƙanin marigayi Dattijo Junaid ya ce masa;

"Taƙamar mai kakeyi? Babanka Shugaban Kasuwar Tukwanen Zinare ne? Hmm! Kasuwar Zinaren da Abduh Dhahab ne yasha wahalar kafasa, bayan ransa kuke cin arziƙi shi kakeyiwa taƙama? idan ban da ajali waye ma yasan Babanka balle kai? Ko lokacin da Sulaim yake raye, shi da ma Mahaifinsa ne ya ƙirƙiri Kasuwar Tukwanen Zinaren daga filin da ya gada a wajen Mahaifansa, kuma fika kyau da nasaba bai yi mana abinda kake yimana.
Kabari duk ranar da ku ka ƙirƙiri wani cigaba na ƙashin kanku a wannan Yanki ba na cin arziƙin wa su ba sai kazo ka ɗaga mana kai. Banza mai macacciyar zuciyar da bai san komai ba sai son ace masa ya na da kyau ɗan daudu kawai!"

waÉ—annan kalamai na Kabeer sun sosa ranshi tare da sashi kukan da zuciyarsa ce kawai bai haÉ—iya ba. tsanar Kabeer kuwa babu inda bai ratsaba a jikinsa.

A ranar ya fuskanci zamowar Mahaifinsa Shugaban Kasuwar Tukwanen Zinare kaɗai bai wadatar ba bai kuma zama wani abin kambabawa ko abin ayaba a wajen Mutanen Yankin ba, sai ma ƙara dawo musu da soyayyar Abduh Dhahab da Iyalinsa da ya yi a cikin zuƙatansu, shi kuma ba wannan ne burinsa ba. Burinsa kowa ya manta da Abduh Dhahab ne ya ƙirƙiri Kasuwar Tukwanen Zinare, su riƙi Mahaifinsa tamkar shi ya ƙirƙiri Kasuwar tun usul, su kuma girmamashi a matsayinsa na Ɗa Namiji ɗaya tilo a wajen Shugaban Kasuwarsu.

Ko da ya bawa Mahaifiyarsa labari, maimakon ta tausheshi sai ta ƙara zugeshi tare da ƙara tadamai tsimin burinta na tafiya Babban Birnin ya yi ilimi boko mai zurfi.

HINDU MAHAIFIYAR SUFYAN
Tabbacin amincewar Sufyan da ta samu ne, ya sa ta shiryawa tafiya Yankinsu wajen Malaman dubanta, don su duba mata Matar data dace Sufyan aura don tafiya da ita Babban Birni ta dinga yi masa Bauta kamar yadda ta tsara a baya.

NAILA
Itama ta zama kyakkyawar Budurwa kuma makitsiyar da mutanen Yankinta suke alfahari da ita.

Ba ta daina sana'ar ƙera kayan wasannin Yara na laka ba, sai dai ta daina fita da su Kasuwar Tukwanen Zinare saboda harajin da ake tsawwalawa ma su ƙananun sana'o'i irinta. A ɓangaren kitso tana samun ciniki don ba Makitsiyar da ta iya kowani kalar kitso kamarta. Har Daular Sarki Hammam take zuwa yiwa Iyalinsa kitso su biyata da kuɗi mai tsoka.

Duk tsayin wannan shekarun fuskar Sulaim na manne a cikin zuciyarta don har kuɗi ta biya ƙwararren mai zanen Yankin ya zanata ita da Sulaim a waje ɗaya, ta kai Gidan hoto aka wanke mata ƙaraminshi, da shi take yawo duk inda zata je.

**********************************************
Tsawwalawar Haraji ya kawo koma baya ga masu ƙananun Sana'o'i a Yankin Tudu harma da ma su manyan jari. Ga ɓullowar Gidan rawar daya zamewa Yankin musiba, a cikin Kasuwar.

Gidan rawa an ƙirƙirar shine ne a cikin Kasuwar Tukwanen Zinare, har da Masauƙin da aka kewaya da katakwaye da langa-langa kamar Ɗaki ga waɗanda dare ya yiwa, kuma kowa ya kasa tunkarar Ɗayyib da yake shugaban kasuwar su ji wanene ya kawo gidan rawa, su kuma shaida ba sa so, saboda dalilin haka Matasan Yankin sai su sha wahala su ƙera Tukwane da zarar sun siyar sai su wuce Gidan rawa da Kuɗin, haka ɓaki ma su shigowa, wa su ma suna shigowa ne kawai don suyi sharholiyarsu su koma ba don su sayi komai ba.

Wannan lamari yana ciwa Mutanen Yankin tuwo a ƙwarya amma tsoron rashin sanin wanda ya kafa Gidan rawan, tunda ga shi Shugaban Kasuwar Ɗayyib bai hana ba kuma bai kai ƙara wajen Sarki Hammam ba, wannan yasa suke Kwana da ɓakin ciki suna tashi da shi. Ƙewar Marigayi Abduh Dhahab da suka mayar abin zagi a baya na damun zuƙatansu, da maganganun Marigayi Dattijo Junaid.

Ƙara ta'azzarar komai ga shi kowa yakasa magana yasa Kabeer Abokin faɗan Sufyan yanƙurawa, don bazaiyiwu saboda tsoron mutuwa su kashe kan su da Kansu ba.

Faɗan da ya tada hazo ne ya ɓarke a tsakanin Kabeer da mai gadin gidan rawar. Dayake Kabeer matashine mai garin jiki da zafin nama sak Siffar mutanen Yankin Tudu kuma baya shaye-shaye ya sa yasamu damar yiwa Matashin da ba su ma san asalin ɗan ina bane saboda duhun fatarsa dukkan tsiya.


Ba bu wanda baiji daɗin abinda Kabeer ya aikata ba, don wasun su sun cire tsoro sun fito sunata maganganun sam bai dace ace an gurɓata Kasuwar Tukwane da Gidan rawa ba...

Kabeer ko a jikinsa zuciyarsa sakayau ko ba komai, yasamu ya amayar da abinda yake sukar zuciyarsa da na Mutanen Yankinsa. saɓanin Mahaifinsa da zuciyar ke cike da tsoron abinda zai biyo baya.

Tun Mahaifin Kabeer yana jin tsoron martanin da zai biyo bayan abinda É—ansa ya aikata har ya saki ransa ya cigaba da harkokinsa..

Bayan wata ɗaya, watan cin Kasuwar Tukwanen Zinare yaƙara zagayowa. A gaggauce Kabeer da Mahaifinsa suke kimtsa Tukwanen su don fita Kasuwa. Su na zuwa suka tarar da Rumfar su.....✍🏻

09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥


SASAAL
Arewabooks@sasaal


07

Su na zuwa su ka tarar da rumfarsu a rushe, yanayin shafewar wajen ma kamar ba'ataɓa kafa Rumfa ba. Kafin Mahaifin Kabeer ya dawo daga ɗimuwar da ya shiga, tuni Kabeer ya nufi kewayayyen rumfar da ke matsayin ofishin Ɗayyib.

Abin mamaki kamar wanda ake jira tun kafin ya kaiga inda ya nufa, matasa masu irin Shekarunsa suka rufe shi da duka ta ko ina.

Ihun naiman taimakon Kabeer ne ya fito da Ɗayyib haka Mahaifinsa daya ƙaraso a guje ya na haki.

Dakatawa su kayi da dukansa saboda ihun da Mahaifinsa ya kurma, kowannensu na numfarfashi saɓanin Kabeer daya goge jinin bakinsa ya yinƙura ya miƙe yana kallon inda Ɗayyib yake tsaye. Da zafin da yake ji a cikin zuciyarsa da gangar jikinsa ya fara magana;

" da a haka Abduh Dhahab da muka mayar abin aibatawa ya gina Kasuwar Tukwanen Zinare da bai kai ko ina ba zai mutu, ban nufo ofishinka don naci zarafinka a matsayinka na Shugaba garemu ba, sai don na kawo maka ƙorafin rushewa Mahaifina Rumfa da akayi. Menene laifina? Idan faɗan da nayi waccen watan ne, ina neman yafiyarka ka dawowa da Mahaifina Rumfarsa. Ni na haƙura da zuwa Kasuwar gaba ɗaya, don matsawar ina zuwa dole wata rana zan kasa jurewa nayi yunƙurin dakushe duk wani abinda zai kawowa Yankina koma baya ko akan waye kuw.." bai ƙarasa ba saukar naushin da yasa shi zubewa ƙasa warwas ya dakatar da shi daga Matasan da suka yi masa duka.

Da gudu Mahaifinss ya nufoshi yana kuka haÉ—e da kiran sunansa. ÆŠayyib ma tsawa ya dakawa Matasan da su ka bar wajen.

Rige-rigen É—aukar Kabeer kowa yake yi don kaishi Asibitin Mahaifinsa ya hana yace a barshi ya kaishi Gida yana da maganin da zai bashi.

Bayan su Kabeer sun je Gida, aka Turo kiran Mahaifinsa daga Fadar Sarki Hammam, bai wani jima ba ya dawo..

Mutanen Yankin;
Abinda ya faru da Kabeer yaƙara zama zanannen layin da kowa zai ji tsoron ƙetarawa, har ya yi azarɓaɓin faɗar gaskiyar a kan duk wani abu ba dai-dai ba da ake aikatawa. Jiki a sanyaye kowa yaci Kasuwarsa ta wannan rana.

KABEER;
Cikin tsananin Azaba Kabeer ya farka gabannin sallar magriba bayan É—ure-É—uren maganin gargajiyan da suka yini suna yimai. Daga Mahaifinsa har Mahaifiyarsa hannunshi suka kamo suna rige-rigen yimai sannu da jiki.

Cikin taushin harshe Mahaifinsa ya fara magana;
" Kabeer lamarin Yankin nan sai addu'a faɗar gaskiya duk ƙanƙatarsa ya zama abin tsoro, amma naje Fadar Sarki Hammam na samesa da Shugaba Ɗayyib ya yi alƙawarin kawo ƙarshen gidan rawar da abokin kasuwancinsa ya ƙirƙiro kuma ya bani haƙuri, Kabeer ko da wata ɓaraka za ta kuma kunno kai, ba na so na ƙara jin bakinka idan ba so kakeyi su kashemin kai a banza ba na roƙeka!." ya ƙarasa faɗa da kuka mai sosa zuciya.
Kai Kabeer ya É—agamai alamar ya ji.

Fara kiraye-kirayen Sallar Magriba ne yasa Mahaifinsa yin alola ya bar Gidan. Itama Mahaifiyarsa miƙewa tayi don yin alola kafin ta taimakamai shima ya yi. Ta na yunƙurin zuba ruwa a buta taji ana bubbuga Gidan a hankali. Fasa zuban ruwan tayi ta ɗauki mayafi ta lulluɓe jikinta.

Ta buɗe ƙofar, wanda ya ke bugawa bai jira izininta ba ya yi gaba ya barta da buɗaɗɗen baki, zuciyarta na bugawa da ƙarfi ta nufo cikin Gidan ƙafarta na harɗewa.

Mayafin fuskarsa ya yaye.

A take fuskarshi da yake abin tsoro a wajen duk wani Mutumin Yankin Tudu a tun shekarun baya da'a yankewa Bashar harshe ya bayyana.
Da sauri ta dafe bakinta hawaye na ɓulɓulowa wani kan wani. Kai MALIK ya girgiza mata sannan ya ce;

" mai kike yiwa kuka?" Bata kaiga ba shi amsa ba Mahaifin Kabeer ya shigo don yakasa zaman Masallacin daya saba bayan sun idar saboda fargaba.
Shima ruɗu da tashin hankali ya shiga sai dai shi ya yi ƙarfin halin zube gwiwoyinsa dukka biyu a gaban Malik ya na roƙonshi;

" ka tausayamin, haƙiƙa ni bani da wata masaniya a kan yanke harshen ɗan uwana Junaid, haka Iyalina. Ka yi haƙuri ka barmin ɗana ya rayu da mu saboda shi ya rage a kusa da mu, na roƙeƙa" Kai Malik ya ɗaga sama yana kallon ƙofar Ɗakin da Kabeer yake tsaye yana Kallonsa ya ce;

" na zo ku bani Kabeer na tafi dashi, wata rana nayi alƙawarin dawo muku da shi a yanayin da zakuyi alfahari da shi, ba lallai naushin Sihirin da su ka yimai ya barshi ya rayu ba, kuma ko da ya rayu wata rana dole zasu rabaku da shi" yana ƙarasa faɗa ya matsa inda Kabeer yake a tsaye.

A kafaɗa ya saɓashi duk girmanshi, batare jiran amincewar su ba. fuskarshi ya ƙara lullɓewa ya nufi hanyar barin Gidan. Da ya juya baya, Kabeer hannayenshi duka biyu ya ɗaga a hankali ya na yiwa Iyayenshi sallama, tausayinsu na mamaye ilahirin zuciyarshi. Suma kuka suka saki bayan fitarsu suna ƙanƙame juna.

Ba su yi tunanin zasu iya runtsawa ba bayan Malik ya tafi da Kabeer. Domin Malik tamkar mala'ikan É—aukar rai haka yake a wajen Mutanen Yankin Tudu.

Haka kawai suke jin nutsuwa a ransu tare da gasgata alƙawarin da Malik ya yi musu na zai dawo mu su da Kabeer wata rana a yanayin da zasuyi alfahari da shi.

★washe gari Mahaifin Kabeer ya fitar da labarin ɓacewar Ɗanshi, don ko mai zai faru bai isa ya ce Malik ne ya zo ya tafi da Kabeer ba, indai ba so yakeyi shima yabi Ɗan uwanshi Junaid ba.
Babu wanda bai ƙara shiga taitayinsa ba.

Ta ɓangaren Mutanen Yankin da basu da masaniya a kan komai, tsoron faɗar gaskiya da alwashin ɗauke ido akan komai suka ƙara sawa ransu.

Ta ɓangaren waɗanda suke da hannu tsumu-tsumu da waɗanda suka san abinda yake faruwa amma basu da damar faɗa suma sun shiga ruɗun wanene ya ɗauke Kabeer?....

Bayan kwanaki..
Kamar komai bai faru ba haka kowa ya cije ya cigaba da harkokin gabanshi, saboda ma su ƙarfin haline ma suke iya shiga yiwa Mahaifan Kabeer jaje, ragowar kuwa tsoron shiga Gidan ma sukeyi saboda gani sukeyi da zarar sun shiga jaje za'a biyo su Gida suma a sace su, ko a yanke musu harshe.
*****************************
A ɓangaren Hindu Mahaifiyar Sufyan taje Yankinsu, ta gana da Malaman tsibbunta har mutum Uku kuma amsar duk ɗaya ne;

"Naila Makitsiya a Yankin Tudu itace tsanin hawar matakin nasarar Sufyan. Duk tsananin duk abinda zai faru karta kuskura ta bari Aurenta ya suɓucewa Sufyan, saboda sana'ar kitsonta shine mafarin nasararsa, daganan kuma zai haifar da gagarumin abinda zai sa Sunanta da na Mijinta Ɗayyib har da na shi kanshi Sufyan ɗin ya zama abin faɗe ga kowa ba a iya Yankin Tudu kaɗai ba har ma da duniya baki ɗaya. Canji mai girma gaske zai zowa Yankinku a wannan lokacin, amma fa dukka hakan bazai tabbata ba har sai Sufyan ya auri Naila ya samu matsuguni Babban Birnin Abyad."

Kamar haÉ—in baki dukka amsa É—aya ta samu daga bakin kowannen su sai dai sigar maganar da ya ke bambanta amma dukka ma'ana É—aya yake bayarwa.

Mallakar matsuguni a Babban Birnin Abyad ko da na haya ne abune mai matuƙar tsadar da duk kuɗin da Ɗayyib yake taƙamar yana samu a Kasuwar Tukwanen Zinare bazai wadatar ba balle ta lallaɓashi ya amince.

Da farko bata taɓa kawowa Sufyan yin Karatu a Babban Birnin Abyad ba, sai hasashen garuruwan da suke kusa da shi, don ko a Yankinsu Sarki Hammam ne kawai yake iya zuwa can ya yi kwanaki amma ba ire-iren su masu iya arziƙin Yankin Tudu ba. Ta ina zata samu kuɗi masu yawan da zasu isa Sufyan ya tafi Makaranta har ya kama mu su matsuguni a Babban Birnin Abyad?...

Mahaifiyarta da kusan dukka ɗabi'unta ta gada ta tunkara da batun. Cikin ƙwarin gwiwa ta bata shawarar mai zai hana su tara dukka kadarorinsu waje ɗaya su kasa shi kashi uku su siyar da kashi biyu....

Da farko Hindu ƙin amincewa tayi da shawarar Mahaifiyarta ta har na tsahon Kwana uku. Tuno da Sufyan zai samu gagarumin ɗaukakar da sunansu zai zama abin faɗe ba a iya Yankin Tudu kaɗai ba har da duniya baki ɗaya ya sa ta amince.

Hindu bata dawo Yankin Tudu ba sai da kuɗi masu yawan gasken da ta zubo a Akwatin ƙarfe garƙame da mukulli.

A daren ranar ta tari Sufyan da zancen. Manyan idanuwansa farare ƙal ya zaro, tsabar ruɗewa hannuwansa har rawa sukeyi wajen kamo nata hannun.

"Ummi ki ka ce me? rayuwa a Babban Birnin Abyad? Kina nufin na kai matsayin da zan tafi can nayi Karatu Ummi ki ƙara faɗa dan Allah ko nine banji da kyau ba" Sufyan ya faɗa a ruɗe.

Dariya ruÉ—ewarsa ya bata, don haka da ta É—an dara, kafin ta zayyanomishi duk abinda ya faru da shawarar da Kakarshi ta bata har ta samu ta dawo da kuÉ—i ma su yawan gasken da zasu isheshi ya naimi Makaranta, su kama Gida har na tsahon shekaru biyu.

Lokacin da ta sa ɗan mukulli ta buɗe Akwatin kuɗin zabura Sufyan ya yi har sai da ya miƙe tsaye yana nuna kuɗin, duk girman kanshi da jinkanshi kasa jurewa ya yi yasa kuka yana ƙanƙameta, haɗe da faɗin;

"Ummi ba Naila ba kowa kike so na aura na amince, na gode Ummi Allah Ya sa na cikamiki burinki kamar yanda kika cikamin Burina" Bayanshi take shafawa ranta fari ƙal.

Bayan Ɗayyib ya dawo ya huta ta sanar dashi duk abinda ya faru bata ɓoyemai ba. Da farko ya ɗanyi jim da bata laifin da ba taje wajen Malaman tsibbu ba, da bata tono abinda yafi ƙarfinsu da zai kaita ga siyar da kadarorinsu na manyan kuɗaɗe irin wannan ba.

Ƙara marairaice murya tayi har sai da tasan yanda tayi ta yaudareshi ya yi alƙawarin nemo kuɗi ma su yawan gaske domin Sufyan ya ƙara a kai, su biya kuɗin hayar shekaru uku maimakon biyu, kafinnan sun san komai zai bayyana kanshi. Hindu zata iya cewa bata taɓa kwanan farin ciki irin na wannan ranar ba.

Shima Sufyan a ɓangarenshi yakice batun Naila ta taɓa abota da Sulaim ya yi ya amincewa rungumar Aurenta hannu bibbiyu kafin ɗaukakarshi ta bayyana.


Kwana biyu bayannan Hindu ta bayyana a Gidansu Naila da sunan ta zo kitso. Ba iya Naila da Kakartane kaɗai ne sukayi mamaki ba, har da maƙotansu da waɗanda suka ga gilmawarta.

A iya sanin da sukayiwa Iyalan Gidan MUSAA DHAHAB Magadan Sarautar Yankin Tudu kuma masu faÉ—a aji a Yankin Mutanene ma su girman kai, da kai Kansu inda Allah Bai kai su ba, kama daga kan asalin Æ´an Gidan har zuwa kan baren da'aka auro, idan ka cire Marigayi Abduh Dhahab da É—ansa su kaÉ—ai ne suka banbanta.


Zuwan Hindu Iyali ga Ɗayyib Uwa ga Sufyan da yake ƙafafa da jin yafi kowa, saboda Shugabancin Kasuwar Tukwanen Zinaren dayake hannun Mahaifinsa waɗanda ganta ta shiga gidansu Naila suka san dole da manufa ba wai don zuwa wajen Naila kitso kaɗai ba.

CIKIN GIDANSU NAILA;
Rasa wajen da zata bata ta zauna Kakar Naila ta yi, duk da akwai ƴar tsama a tsakaninsu tun shekarun baya, amma saboda Sashensu na Masarautar Yankin Tudu ya fi nasu gidan kyau nesa ba kusa ba da ababen more rayuwa, duk da suma nasu Gidan ba laifi da kyansa dan yafi na dubban mutane a Yankin, yasa ta ke ƙoƙarin yi mata ƙara tunda batasan abinda ya kawota ba.

Cikin sanyi hali da na murya da kuma sanin girman na gaba Naila ta buɗe matsakaicinta bakinta mai ɗauke da siraran laɓɓa ta ce;

"Barka da Rana Ranki ya dade, da kin turo har gida zanzo nayi miki ba sai kinzo ba" murmushi mai kyau Hindu tayi tana dafa kafaɗarta saboda sanyi da daɗin muryarta da ya yi matuƙar birgeta ta ce;

" Karki damu ɗiyata gaba idan zan ƙarayi sai kizo Gida kiyimin" Kai Naila da gyaɗa itama da kyakkyawar murmushi a saman fuskarta.

Hindu da dabara take kallon duk wa su motsin Naila har aka fara yimata kitson da tace guda goma take so.

Kuɗi mai yawa kwatankwacin wanda Iyalan Sarki Hammam suke bawa Naila idan taje Gidan yi musu ƙananan kitso ta bata. Daƙyar ta karɓi kuɗin don sai da Kakarta ta saka baki.

Yanayin Naila da dabi'unta sun matuƙar burge Hindu, don da ba dan burin auren Mace ƴar Babban Birnin da takeyiwa Sufyan kwaɗayi ba, da ta amince Naila ta zama Surukarta ta din-din.

09132403788
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥


SASAAL
https://www.arewabooks.com/dashboard/info


08

ÆŠAYYIB.
Da ranar cin Kasuwa ya ƙara zagayowa, Harajin da zai kai iya adadin kuɗin gidan hayar da ya yi alƙawarin biyawa Sufyan na Shekara ɗaya a Babban Birnin Abyad ya tsawwalawa Ƴan Kasuwar Tukwanen Zinare. Wasun su har da kuka su na magiya amma ba bu wanda aka saurarawa. Sai bayan an tattara kuɗin ya zo yake basu haƙurin In sha Allahu Kasuwa mai zuwa hakan bazai faru ba. Dubban mutane ne suka koma Gida ransu a ƙuntace.

Ko da ÆŠayyib ya tattara kuÉ—aÉ—en basu kai adadin abinda yake nema ba har sai da ya haÉ—a da wanda ya jima ya na tarawa.

Tun kafin zancen neman Auren Naila yaje ga kunnen Danginta da ita kanta da Mutanen gari Dangin Ɗayyib suka nuna sam basu amince ba. Ta ya ya Naila ƴar Gidan Mahmoud da yake Madinki talakan fitik zata shigo zuri'arsu? Hakan zubar da ƙima da mutuncin Masarautarsu ne don haka sam su basu yarda ba.
Da labari yajewa Jalal murmushi ya yi a zuciyarsa tare da bada Umarnin a nemawa Sufyan Auren Naila ba tare da jinkirtawa ba.

A ɓangaren Mutanen gari, ba su yi mamaki ba saboda sunyi zargin haka tun zuwan Hindu Gidan. A ɓangaren ƴan uwan Mahmoud da suke Uba ɗaya jiki na rawa suka amince ba tare da sanin Kakar Naila ko amincewar ita kanta Nailan ba.

KAKAR NAILA;
Da labari ya riske Kakar Naila tsabar zabura sai da miƙe bakinta yana rawa take ambaton Sunan Allah don tasan ruwa baya tsami banza kuma tun a zamanin Budurcin Babbar Ƴarta Yayar Mahaifin Naila tasan wacece Hindu da makircinta. Itace silar rushewar auren Ɗan uwanta da Yayar Mahaifin Naila saboda kawai ba su da kuɗi. Baƙin cikin rushewar auren ne ya yi sanadiyyar mutuwar Ƴarta.

To idan zata hana Yayanta auren Yayar Mahaifin Naila saboda talaucisu tun a waccen zamanin wani dalili ne zai sa yanzu ta amince ÆŠanta ya auri Naila tunda su dai sunanan a Talakawansu ba bu abinda ya sauya?

Naila da take gyara dogon gashin kanta mai cika da tsaho a gefe ba tace komai ba, sai ƙwallar da yayiwa ganinta yana. Ba ta da abin cewa, tunda burinta macaccen burine a zahiri, amma a baɗini rayayye ne a cikin zuciyarta tunda da shi zata mutu.

Tasan ko da Sulaim ya na raye ba lallai ya so Mace irinta ba. Sai dai Mutuwarsa ya sa tanajin ƙwarin gwiwar da wataƙila ya na raye da zai iya auranta suyi rayuwar farin cikin da take hasashe.

Tasan dole wata rana, irin wannan ranar zata zo domin bazata dawwama a haka ba tayi aure ba, shiyasa tayi alƙawarin sawa kanta jarumtar amsar duk Namijin daya zo mata a matsayin Mijin aure, tunda son Sulaim a cikin zuciyarta ba Ɗan adam ba ne irinta balle ta yaƙeshi.

Kusa da ita Kakarta ta zo ta zauna tana kamo dukka hannayenta daga tazar gashin da takeyi.

Cikin tausayin jarabawar da yake samun Nailan akai-akai ta ce;

" karki kiyi kukan zuci ke kaÉ—ai Naila ki fito da shi sarari muyi tare"

Naila tanajin haka ta saki Kukan daya maƙalemata tuntuni. Sun kai minti Talatin a haka kafin Kakarta ta jata Ɗaki. Manne da juna suka zauna kan Naila kwance a samar Kafaɗarta.

A hankali Kaka ta ce;
"Ba na jin tsanar Sufyan a raina duk da labarin ɗabi'unsa marasa kyau da nake ji a bakin mabanbanta Mutune, sai dai ina tsoron wani irin ƙulli Hindu ta ƙulla da har zaisa ta amince ki auri Ɗanta. Hindu Ƴar masu rufin asirce a Yankinsu, dalilin haka ta ƙulla makircin da ya haramtawa Habeebah yayar Mahaifinki auren Yayaanta saboda talaucinmu, domin sana'ar Ɗinki muka gada daga Iyaye da kakanni, dalilin wannan baƙin cikin Habeebah ta rasa ranta. Babban burin Hindu a waccen lokacin shine ta auri Ɗan babban Gida, Allah Kuma ya cika mata burinta. Babban Ɗa ga Ƙanin Sarki Yankin Tudu na wacce lokacin Ɗayyib ya nuna yana sonta, har sukayi aure. Abinda yake bani mamaki da tsoro shine idan har Hindu zata guji Ɗan uwanta ya auri Habeebah saboda Talaucin mu tun a waccen zamanin, wani dalili ne zaisa yanzu ta bari Ɗan da ta haifa a cikinta jinin Sarautar Yankin Tudu a wannan zamanin da burika suka yi yawa ya aure ki duk da ƙin amincewar da mutanen Masarautar suka nu na kamar yadda na samu labari?"

Naila ba tace komai ba sai ƙara ƙanƙameta da tayi da dukka hannayenta, a haka barci ya fara ɗaukarta.

Sai da aka kira Sallar la'asar sannan suka miƙe, kowannen su zuciyarsa ba daɗi.

Har dare ya raba Kakar Naila ta kasa runtsawa, sai kai da take girgizawa lokaci zuwa lokaci saboda zuciyarta dake hasaso mata ai gara Halayyar Hindu da Halayyar mutanen cikin Masarautar Yankin Tudu.
Hannuwanta ta sarƙe waje ɗaya, Allah Ya ɗauki ran Mahmoud da Mahaifiyar Naila a tsakankanin Shekaru kaɗan kuma Allah ya jarabceta da mugayen Ƴan uwan uwa da na Uba gaba ɗaya idan aka cireta ita kaɗai ba bu wanda ya ke son Naila ko ya raɓeta sai domin buƙatar kanshi. Idan har ta zuba Ido Naila ta auri Sufyan to tabbas taci amanar Naila ba kuma zata yafewa Kanta ba, dole ta samo mafita ko da kuwa zai kaita ga gaban Sarki Hammam ne, don Masarautar Yankin Tudu tamkar Masarautar Uƙubane ga baren cikinta har ma da Ƴaƴan cikinta.

Naila shafa gefenta ta yi taji ba bu Kaka. A hankali ta miƙe, a tsakar gidansu ta hangota ta na zarya. Da sanyin tafiyarta ta ƙarasa bayanta. Cikin taushin harshe ta fara magana;

"Lokacin da na wayi gari ba bu Sulaim ya ƙone, na ji raɗaɗi a raina, da na zo na rasa Mahaifi sai na ƙarajin raɗaɗi amma ba irin wanda naji lokacin da na rasa Sulaim ba. Da rasa Mahaifiya sai na ƙarajin raɗaɗin da sam ba shi da haɗi da irin waɗanda na ji a baya. Abin nufi zafin rasa abu a zuƙatan mu na da alaƙa ne da yanda matsayin abun yake a wajen mu, saboda haka nasan abinda kike ji Kaaka, amma karki bari hukuncin Ubangiji ya hanaki barci wajen tunani har ki kasa neman mafita a wajen Shi. Zuciyata mai kaushi ce akan abinda ba na so Kaaka. Auren Sufyan ba ya nufin komai gareni balle har ya hanani barci, abu ɗaya na sani, idan abu mara daɗi ya sameni kuma na jure na yi haƙuri to tabbas Ubangiji Zai musanyamini da mafi alkhairinsa."
Naila ta ƙarasa faɗa da siririn kuka tana ƙanƙame Kakarta.
Itama Kakaa da rawar murya ta ce;
"Hakane Naila, amma ki sani zanyi iya yina don samar miki mafita domin nasan Hindu dole ta na da wata manufa, Naila ba na son rasaki, ke kaÉ—ai nake gani na ji daÉ—i"
dukkansu kuka suka sa, su na ƙara ƙanƙame juna a haka Naila ta jata suka koma ɗaki.

Sun É—auki tsahon mintina a haka kafin Naila ta ce;
" Maiyasa ki ke tsoron Masarautar Yankin Tudu, ko saboda kashe-kashen da akayi shekarun baya ne?"

Kai Kaaka ta girgiza tana lumshe idanuwanta labarin asalin Masarautar kamar yadda Marigayi Mijinta babansu Mahmoud ya bata labari na dawo mata, fuskantar Naila ta yi ta ce, "kinsha tambayata wanene Abduh Dhahab su wanene ƴan uwansa ban taɓa baki labari ba, amma yau zan baki ko don ki fuskanci gaba"

```MASARAUTAR YANKIN TUDU```

Sarki Musa shine Sarki na farko da ya kawo sauyi mai girma a Yankin Tudu lokacin Mulkinsa. Daga wannan lokacin mutanen Yankin suka samu ƴanci da sauƙin abubuwa da dama, da shigowar gwamnatin sama-sama cikin lamuransu. Sarki Musaa yana da ƴaƴa da yawa Maza da Mata daga Uwaye daban-daban amma wanda ya yi zarra a cikin su kuma ya fi ƙarfin arziƙi shine ABDULYASAR MUSA DHAHAB, Abdulyasar su biyu Mahaifiyarsu ta haifa, kafin Allah Ya ɗauki ranta. Matsi daga Kishiyoyi da asirce-asirce kala-kala da har ya yi sanadiyar mutuwar ƴar uwarsa, shi kuma yake fuskanta azaba daga ɓangaren kishiyoyin Mahaifiyar su bayan ranta ya sa Mahaifinsa Musaa ɗaukeshi daga cikin Ƴan uwansa zuwa Babban Birnin Abyad wajen Abokanan Kasuwancinsa don yin ilimin zamani dana Addini.

Anan Babban Birnin Abyad Abdulyasar Dhahab ya yazama Babban ÆŠan kasuwa.

Kasuwanci Zinare yakeyi da taimakon Bature Francis Ɗan Aminin Mahaifinsa da ya ɗorasa a hanya har yazama hamshaƙin mai Arziƙi.
Dalilin wannan Kasuwanci na Zinare da ya ɗauka da matuƙar muhimmanci sama da Abokanan Kasuwancinsa ya sa suka sauya mai Suna daga Abdulyasar Musaa zuwa Abdulyasar Dhahab.

Bayyanar Abdulyasar Dhahab a Yankin Tudu a matsayin hamshaƙin ɗan Kasuwa babban abin alfahari ne a wajen Mahaifinsa Sarki Musa. Bayan dawowar Abdulyasar, babu wanda yasan dalili Gaba mai ƙarfi ya sarƙe a Masarautar tsakanin ƴan uwa biyun da suke aminai wato Sarki Musa Jamil Kakan-Kakan Ɗayyib Mahaifin Sufyan.

Abdulyasar bai jima da dawowa ba Allah Ya amshi ran Mahaifinsa Sarki Musa. A waccen lokacin anso naɗa Abdulyasar a matsayin magajin Mahaifinsa ko dan ƙarfin arziƙinsa amma ya nuna bayaso da suka takura ya tattara ya gudu na ɗan lokaci. Dole aka naɗa Yaya ga Sarki Musaa Mahaifin Sarki Hammam.
Ƙarfin arziƙin Abdulyasar Dhahab da taimakon shi ga Talakawa Yankin sai ya shafe sunan kowa a Masarautar su kamar shine Sarkin Yankin. Lamarin ya na sosa ransu matuƙa, wannan dalilin yasa suka fara kaiwa dukiyarsa hari ta kowacce siga tare da alƙawarin kaishi ƙasa ko ta halin ƙaƙa.

Su na cikin wannan yanayin matar Abdulyasar Dhahab ya aura bayan dawowarsa ta haifa ɗa Namiji Ubaidullah. Da taimakon Iyalinshi bayan ta haihu saboda kwaɗayin abin duniyar da sukayi alƙawarin za su ba ta na kaso maiyawa, ta taimaka musu suka kai Abdulyasar ƙasa, duk da haka Abdulyasar Dhahab bai bar rayuwar Ɗanshi Ubaidu ya lalace kamar yanda suka so ba, ya miƙa amanarshi hannunshi abokannan kasuwancinshi suka tafi da shi can wata nahiyar, shi kuma ya cigaba da gwagwarmaya da azzaluman Masarautar su.

Ubaidu bai tashi dawowa Yankin Tudu ba sai da kowa ya fara mantawa da shi, da kyakkyawar Matarsa da Ɗansa mai kama da shi Abdullah(Abduh Dhahab) ya dawo, lokacin Abduh har zama ƙaton saurayi, har da ƴar Yayar Matarshi Aysha da Mahaifiyarta ta mutu suka dawo Yankin Tudu. Ga dukiya mai tarin yawa da Ubaidu Dhahab ya dawo da shi.

Dawowar Ubaidu Dhahab da dukiya da kuma zankaɗeɗiyar Matar da babu ma su irin siffarta a Yankin Tudu ya yi matuƙar sosa ran maƙiya Masarautar. Maimakon su yaba sai suka hau kushewa da aibata Ubaidu Dhahab ya auro bare mai kyan da zata kashe shi ta kwashe dukiyar da ya tara. Duk Abdulyasar na sane da su sai dai bai ce komai ba, sai jikansa Abdullah da yaja a jiki.
Sanin matsawar Abdulyasar ya na raye ba zai barsu su kai Ubaidu ƙasa kamar yadda su ka kaishi ba, ya sa suka fara shayar da shi guba a sirrince ta hanyar amintacciyar hadimarshi. Cikin ruwan sanyi suka kashe Abdulyasar ba tare da kowa ya ankara ba, sai daga baya Mutanen gari suka ji ƙishin-ƙishin.

Mutuwar Abdulyasar ba iya Ubaidu da Iyalansa kawai ya taɓa ba har da mutanen gari, saboda alkhairinsa.

Bayan wani lokaci suka dawo kan Ubaidu. Duk da sun kashe Abdulyasar sun kasa kai Ubaidu ƙasa ta cikin ruwan sanyi kamar Mahaifinsa, sun tusawa ɗanshi Abdullah ƴaƴansu ya aura yaƙi yarda, saboda alƙawarin auren da ke tsakanin Abdullah da ƴar Yayar Mahaifiyarsa Aysha da suka taho tare da ita. Babu yadda su ka iya, haka suka haƙura Abdullah ya auri Aysha. Daga wannan lokacin ne suka ƙara duƙufa wajen ganin bayan Ubaidu ko ta halin ƙaƙa, da suka ga sun kasa, sai suka bishi har Gida suka yi mai kisan gillar da ya tashi hankalin mutanen Yankin.

A lokacin Iyalinshi Mahaifiyar Abduh Dhahab Nanaah tayi ƙururuwar abi mata haƙƙinta amma babu wanda ya saurareta sai ɗanta Abduh Dhahab da ya tayata fafutuka, sai dai shima a lokacin ba shi ƙarfin yin komai.

Baƙin cikin hakan yasa ta tattara kayanta ta bar Yankin Tudu aka nemeta aka rasa. Shima Abduh tattara komai nashi ya yi ya bar masaurata zuwa Gidan ɗaya daga cikin gidan da Mahaifinsa ya gada a wajen Abdulyasar Dhahab tsakiyar Talakawa.

Daga wannan lokaci Abduh Dhahab ya barrata kansa da masaraurar Yankin Tudu, ya dawo kamar kowanni ɗan gari. Ba bu tsinke daga dukiyar Ubaidu da ba su ga bayanshi ba. Duk da wannan abubuwan da suka faru Ɗayyib da yake nunamai tsananin ƙauna ya na tare da shi. A sabuwar Unguwar da Abduh ya dawo ya yi sababbun Amanai, Mallam, Mahaifin Malik da kuma Mahaifinki Mahmoud, duk da sun girmewa juna a shekaru hakan bai hana amintarsu saboda hali da ya zo ɗaya.

Abduh ya na da buri mai zurfi, da kuma kishin Yankinsa, ya na son ya kawowa Yankinsa cigaba, kamar yadda Kakanshi da Mahaifinshi sukayi yunƙuri Allah bai ƙaddara ba. Wannan dalilin yasa ya fara tunanin mai zai ƙirƙiro sabo da zai kawowa Yankinsa cigaban da kowa zai amfana???


Abduh ya share sama da wata ya na tunanin abinda zai ƙirƙiro amma ya kasa samun mafita. A wani dare Ubangiji ya sanya masa tunanin ƙirƙirar Tukwane. To amma ai akwai mutane ma su ƙera Tukwane da yawa, ƙirƙirarsu kaɗai ba zai zama wani sabon abu da zai ja hankalin mutane ba, dole sai ya haɗa da wani sabon abinda mutane ba su san da shi ba. Har ya gama saƙe-saƙensa a wannan rana bai samu mafita ba.

★washe gari har Iyalinsa Aysha da ke ɗauke da tsohon ciki ya tuntuɓa itama ba bu wani basirar da ya zo mata.

A haka Abduh ya ƙara shafe wata ya na tunanin abinda zai sa Tukwanensa su zama ma su jan ra'ayi da kwaɗayin mallakar su a wajen Mutane. Ya na cikin wannan tunanin sana'ar Kakanninsa na Zinare ya faɗo mai. Mai zai hana ya yi wa nashi Tukwanen laƙabi da Tukwanen Zinare, ya tambayi kansa, hakan zai zama sabon abu a wajen mutane, kuma abin rububi domin ko da mutum ba shi da niyyar siya zai so ya ga yaya Tukwanen Zinaren su ke, daganan wataƙila yaji sun yi mai ya siya.

Da ya yi shawara da iyalinsa ɗari bisa ɗari ta amince, amma daga baya da ta fuskanci ɗan abinda ya rage mu su suke samu su ci, su sha Abduh yakeson kwashewa ya kafa sana'ar Tukwane sai ta nuna sam bata yarda ba, dama can lallaɓawa takeyi ta gaji da talaucin da suke ciki shine yanzu zai ƙara kwashe abinda ya rage ya yi jarin Tukwane da shi. Da lallaɓawa da kuma nuna mata gagarumin nasarar da zasu samu, cike da yaƙini Aysha ta amincewa Abduh.

Da zallar basirar ƙere-ƙeren da ya koya a wajen a Abokansa na bakin Kasuwar Iyakar Yankin Tudu, Abduh ya ƙera Tukwanen da ya yiwa laƙabi da Tukwanen ZINARE zuciyarsa cike da ƙwarin gwiwa da kuma yaƙinin ko bai siyar ba a take wata rana zai siyar.

Lokacin da mutanen Yankin suka ga Tukwanen da Abduh ya ƙera dariya suka bushe da shi haɗe da faɗin " Abduh ya zo da abinda ba shi da wani amfani zai zallar yaudara, shikenan dan Kakansa da mahaifinsa sunyi kasuwancin ZINARE sunyi arziƙi, sai ya ce shima sai ya yi, to ai zasu ga waɗanda za su siyi waɗannan ruɓaɓɓun Tukwanen na sa, wai Tukwanen ZINARE tunda ya ɗauka kowa Mahaukaci ne irinsa."

Tsaf surutansu yake dawowa kunnen Abduh, ya na kuma sukarsa, sai dai ba shi zaisa ya ja da baya ba, sana'ar Tukwanen Zinare ba gudu ba ja da baya.

A ranar ta farko da Abduh Dhahab ya fita da Tukwanen Zinare Kasuwar maƙotan Yankinsu ba bu wanda ya siya, da ya tarkatosu ya dawo Gida sai mutanen Yankin suka dinga yi masa dariya. Matarshi Aysha da baƙin ciki ta kwana, dalilin haka ta tashi da naƙuda washe gari.

A hannun mai maganin gargajiya Aysha ta haifi Sulaim. Kallon fuskar jaririn kaɗai ƙarfin gwiwa yake ƙarawa Abduh Dhahab haka Aysha domin bai bar komai na Kakarshi Mahaifiyar Abduh Nanaah da basusan inda take ba, kamar ita ta haifeshi.
Da yawa idan suka shigo Barka da hassadar kyan jaririn suke barin Gidan.

Tsahon lokaci
Abduh Dhahab ya cigaba da gwagwarmayar fita da Tukwanensa Kasuwanni ba tare da gajiyawa ko ƙosawaba. A haka ya shafe shekaru biyu ya na wannan bautar babu wani cinikin arziƙi. Matarshi Aysha ta sha yunƙurin guduwa saboda talauci ya na lallaɓata ta haƙura.

A cikon shekaru na biyar ɗin da ya yi yana bautar bin Kasuwanni Allah Ya amshi roƙonsa aka siye Tukwanensa tsaf, har da neman ƙari. Addireshin Yankin Tudu yake ta basu tare da yi musu alƙawarin ƙera wasu Tukwanen ma su yawa ga waɗanda suka nuna su na son sari domin siyarwa. Lokaci da rana Abduh Dhahab ya tsayar mu su, tare da alƙawarin ba za su bar Yankin Tudu ba tare da iya adadin Tukwanen Zinaren da suke buƙata ba.

Da tsananin farin ciki ya nufo Gida, sai dai ya na zuwa ya tarar Aysha ta gudu, sai Sulaim da ya tarar da takarda a hannu. Abduh ya yi kuka shi da Ɗanshi kafin su haƙura su fuskanci rayuwarsu da sam babu walwala a ciki.

Ba ji ba gani Abduh ya ke ƙera Tukwane.

Ranar da ya rage saura kwana biyu ranar da ya yi alƙawarin kafa Kasuwar Tukwanen Zinare ya cika bai runtsa ba kwana ya yi kaiwa Allah kukansa....

Wane fata kuke yiwa Abduh Dhahab da masu irin zuciyarsa???

SASAAL


09

★Washe gari Abduh ya tuntuɓi Abokanansa su Ɗayyib, Mahmoud( Mahaifin Naila), Mallam da Mahaifin Malik su fito da Kayan sana'ar su idan da rabo sai su sayar batare da sunyi wahalar bin Kasuwanni da suka saba ba. Ga mamakin Abduh babu wanda ya yi yunƙurin tankamai, kamar ma ba su san abinda ya ke faɗa ba. Kunya suke ji su fitar da Kayansu azo ba'a siya ba ayi mu su dariya. Mahmoud Madinki ne, kayan yara da na manya dinkakku yake bi Kasuwanni yana siyarwa, Mallam kuma Qur'ani da littafan addinin musulunci yake fansarwa, Mahaifin Malik kuma maganin gargajiya yake siyarwa. Ɗayyib ne kawai baya sana'ar hannu taƙamaimai sai abinda ba'a rasa ba. Da Abduh ya fuskanci inda suka dosa sai ya nuna kamar bai damu ba, amma har cikin zuciyarsa baiji daɗi ba.
Da yaƙini Abduh ya share ƙaton filin Ubaidu Mahaifinsa da kaɗai ya rage filinsa basu wawashe ba, ya jere Tukwanen da ya ƙera.

A gefe ya shimfiɗa buhu shi da Sulaim suka zauna bakinshi bai gajiya ba da ambaton Sunan Allah. Har lokaci ya fara tafiya babu wanda ya zo daga waɗanda sukayi alƙawarin zuwa.

Mutanen Yankin sai suka fara leƙoshi su na dariya, bai nuna ya gansu ba, balle su gane abinda suke yi mai yana sukar zuciyarsa. Yunwa da ƙishi ne yasa Abduh Dhahab yunƙurin miƙewa tunda yasan ko yunwa zai kashe Sulaim ba zai yi magana ba. Har ya miƙe hayaniyar mutane daga nesa ya dakatar da shi. Fuskokin mutane ƙalilan ya gane a cikinsu amma ragowar duk yawon kasuwannin da ya gamayi bai taɓa ganin su ba. Waɗanda sukayi alƙawarin zuwa siyan Tukwanensa ne, bakin Abduh kamar zai yage wajen tarbar su, kafin shuɗewar hour ɗaya sun yi ciniki sun siye Tukwanensa gaba ɗaya. Mutum ɗaya a cikin su ne ya tambayi ina zai samu fansar Qur'anin akan sari?. Abduh Dhahab manta abinda su Mallam suka yimasa ya yi, ya nufi hanyar Gidajensu da sauri kamar zai tashi sama, batare da tunanin za'a iya sace masa Ɗansa ko dukka kuɗin cinikin da ya yi ya zuba a ƙarƙashin buhu ba, shi dai burinsa ya kira Abokansa ayi musu ciniki.

Jiki na rawa, Mahmoud da Mallam da Mahaifin Malik suka nufo Kasuwar Tukwanen Zinare da Kayansu. Da rububi akan siye kayan har sai da suka ƙara komawa Gida suka ɗebo wasu. Mahaifin Malik ne kawai maganin gargajiyarsa ta ɗan yi ragowa.

Bayan Kasuwa ta tashi kowa ya adana kuɗinsa bakin kowannen su a washe, sai suka ɗaga Abduh Dhahab sama suna dariya jindaɗi da waƙeshi da waƙe kala-kalan da ke nuna jarumtarsa da dagiyarsa.

Daga wannan rana Abduh Dhahab ya kafa Kasuwar Tukwanen ZINAREN da kafatanin mutanen Yankin su ke amfana da shi.

Bayan komai ya dai-daita Abduh Dhahab ya fita wani Yankin ya auro Mairam. A dalilin Mairam Mahmoud ya ga Mahaifiyar Naila ya aura saboda yawan zuwa Gidan da takeyi, kafin daga baya Abduh Dhahab ya haramtawa Mairam shiga ko ina, don dalilin shigarta Gidan Mahmoud ne aka fara samun masu zugata, ta dinga yi masa Satar kuÉ—i tun da baya bata sai tayasa aiki..

Halaccin Abduh Dhahab yasa Mahaifin Malik ba shi Malik ya dinga yi masa hidima, tunda lokacin Sulaim ba shi da ƙarfin da zai taimakawa Abduh da wasu hidindimun.

A sirrince ba tare da sanin kowa ba Abduh Dhahab ya ƙirƙiri Makarantun boko da na Islama da Asibitoci a Yankin da taimakon abokanan kasuwancinsa na Babban Birnin Abyad, amma babu wanda ya sani nima Mahmoud ne ya sanar da ni ko Ɗayyib bai sani ba. Ya damƙa amanar komai a hannun Mallam ne saboda shi kaɗai ne mai ƴan uwa masu ƙarfin arziƙi a Babban Birnin Abyad da Sarki Hammam da mutanen gari zasu gamsu taimakon daga garesu yake, amma a baɗini Mallam ko ƙofar Gidajen Ƴan uwan nasa bashi da matsayin zuwa.

Abduh Dhahab ya yi hakane don kawar da idon mutanen Masarautarsu akan lamuransa duk da sun san yana samun kuɗi amma ba su isa su ƙiyasta iya adadin abinda yake samu ba.

Abin mamakin duk da wannan girman halaccin na Abduh Dhahab ga mutanen Yankinsa bai sa sun ɗagamai ƙafa ba, a wasu lokutan sai su ce

"ai Mahaukaci ne, banda Mahaukaci wanene zai zaɓi sadaukar da iya Gadon da Mahaifinsa ya barmai domin ya yi suna ya burge mutanen gari?" Babu wasu kalmomin su na ɓatanci da baya dawomai amma bai taɓa damuwa ba domin yasan a sannu zasu gane ranarsa.

Mutanen Yankin Tudu a ɓangaren halayya mutane ne ma su son kansu, butulci da rashin damuwa da damuwar Ɗan uwansu.

A ɓangaren siffa kuma Usul ɗinsu suna da kyan fuska da haske fata, manyan idanuwa buɗaɗɗu, yalwataccen kashin kaa da kaurin jiki, mafi akasarinsu ba su da tsaho daga gajeru masu faɗi da jiki sai masu matsakaicin tsaho da kaurin jiki, idan kaga mutum da siffa saɓanin wannan to Mahaifiyarsa ko Mahaifinsa ba asalin ɗan Yankin Tudu bane. Kamar dai ke Naila baki da irin siffarsu sai irin gashin kansu haka Sufyan ɗan wajen Ɗayyib shima ba laifin yana da tsaho da ginannan jiki amma duk da haka ya sirko da irin ƙibarsu da idanuwansu, dukka saɓanin Sulaim ku ke domin Sulaim ba shi da siffa ɗaya na mutane Yankin tudu kalar fatarsa idanuwansa, tsayuwar ginannen jikinsa tun yana yaro dukka ba irin nasu bane, shi yasa suke ganin a kaf faɗin Yankin babu Matashin da daya girma a raye zai shafe Tarihin duk wani Matashi ɗan ƙwalisa a Yankin Tudu. Sai shima Malik irin hasken fatarsu da idanuwansu ya ɗauko amma sam siffarsa tsayuwarsa kamar sun aroshi daga Mahaifiyar Abduh Nanaah da Sulaim yake kama da ita. Wannan dalilin yasa Abduh ya ke son Malik har ranar da waɗanda ba'asan su waye ba, sukayi nasarar kaishi ƙasa.

Wannan shine asalin labarin Abduh Dhahab da Masarautar Yankin Tudu, sai kuma abubuwan da suke waÉ—anda ba ni da sani akai
```DOWAWAR LABARI```

Idanuwan Naila da suka ɗanyi jaa ta lumshe tana ƙara ƙanƙame hannun Kaka, itama Kaka ƙara ƙanƙame hannun Naila tayi cikin kuka ta cigaba da magana;
"Su na kashe junansu abisa son zuciyarsu, ba tare da wani haƙƙi ba. Ba su taɓa nuna ƙin bare ya shigo cikinsu kai tsaye ba sai a kanki Naila, saboda talaucinmu. Shiyasa nakejin tsoro da fargabar kar kema su kashemin ke a banza, domin bani da ƙarfin gwiwa da dukiyar da zan jaa da su."

Da ƙarfin gwiwa Naila ta girgiza mata kai tana rungumeta cikin taushin lafazi ta ce;

"bazan mutu ba har sai lokacina ya yi, idan kuma lokacina ya yi ko ba na cikin Masarautar Yankin Tudu Allah zai ɗauki raina Kaka, batun cewa a'a ko ki kai kanki gaban Sarki Hammam abisa ƙin amincewarki duk mu haƙura mu gayawa Allah, In Sha Allahu zai sauƙaƙa mana." Da haka sukayi barci hannunsu ƙanƙame da na juna.

★washe gari Kakar Naila ta tattauna da Ƴan uwan Mahaifin Naila kan su bawa Iyayen Sufyan haƙuri Naila ta kammala Makarantar sakandare tunda saura wata bakwai. Da yake babu Allah a lamuransu sai suka taso mata bakinsu a haɗe, acewarsu su kansu basu da tacewa duk abinda Shugaba Ɗayyib ya yanke dole shi zasu haƙura su bi.

Zuciyar Kakar Naila na tafasa ta nufi Gidan su Sufyan kai tsaye.
Bayan sun gaisa Kaka ta koro bayanin abinda ke tafe da ita..
Wani irin kallo Hindu take yimata da soyayyun idanuwanta da suke ƙananu a tsaitsaye farare ƙal. Murmushi ta yi kafin ta ce;
"Haba Ummu Habeebah(Kaka) ai da baki zo da kanki ba, Ni dai ina neman afuwarki akan abinda ya faru shekarun baya, sannan na fuskanceki amma bazan iya yanke hukunciba tunda Maigida Jalal( Mahaifin Ɗayyib) shi ya tura mutane da kanshi nemarwa Sufyan auren Naila. Ki bari Mahaifin Sufyan ya dawo In Shaa Allahu zan isar da saƙonki" godiya Kaka tayi mata tana yunƙurin miƙewa. Da sauri Hindu ta dakatar da ita ta hanyar faɗin;
"Bari na kawo miki abun motsa baki mana" kai Kaka ta girgiza haɗe da cewa; "bakomai Hindu, fuskantata da kikayi yafi komai yimin daɗi, Allah Ya ƙara arziƙi" duk da haka Hindu bata bar Kaka tabar Gidan batare da abinda tayi niyyar bata ba. Dama kuma tuntuni ta tanadeshi ne domin tasan har gaban abadan Mahaifiyar Habeebah bazata taɓa ƙaunarta ba.

Bayan ÆŠayyib ya dawo
Ko zancen Hindu bata yi masa ba, sai shirye-shiryen tafiya Babban Birnin Abyad da suke yi domin duba Gidan da Sufyan zai zauna da Naila saboda a gaggauce takeson ayi komai duniya tasan tasan da zaman É—anta.

A ɓangaren Kakar Naila bayan ta koma Gida ajjiye Tufar da Hindu ta bata tayi a gefe, ta na bawa Naila labarin abinda ya faru. Murmushi mai tsayawa a iya saman laɓɓa Naila ta saki zuciyarta a raunane.
Da nishaÉ—i Kaka ta ce "kinji daÉ—i ko ba ki ji ba Naila?"

Naila sai da haÉ—iye abinda take ji sannan ta ce "na ji daÉ—i Kaka Allah Ya biyaki da Alkhairin Sa" Kaka É—auke kanta tayi tana amsawa da "Amin".

Da yammaci aka turo ana sallama da Naila, ba ta tsaya ɓatawa kanta lokaci ta zura doguwar rigar da aka yiwa ado da saki baƙi da malulluɓinsa. A tsaye ta hango Sufyan, ya yi ado cikin ƙananun kayan da suka dace da siffarsa, fuskarsa ta maza masu raina mutane na tsaye ƙyam akan ƙofar Gidan su. Mutanen Yankin kowa ya wuce sai ya waiwayo ya ƙara kallonsa shi kuma yana ƙara hura siririn hancinsa.

Tsaf yake ƙarewa Naila kallo haɗe da wassafa yadda zamansu zai kasance, tana da komai da yakeso dangane da Ƴa mace abu ɗayane kawai ya yi mata cikas a wajenshi shine rashin zamantowarta ƴar hamshaƙai ko wayayyiyar Babban Birni. Ya na son ƴar masu kuɗin ba irin Naila ƴar Madinka jikar Madinka ba.

Ƙarasowarta ne ya dawo dashi hayyacinsa, da girmamawa ta gaishe shi, ya amsa yana tattare girarsa, har ya fara hura hanci sai ya tuna da hudubar Mahaifiyarsa; na ya sakarwa Naila fuska har ya samu ayi auren. A take ya saki ranshi yana janta da hira cikin aji da kamewa. Daga "eh, a'a, uhm" sune amsoshin Naila. Sufyan kamar ya shaƙeta yana ji a ransa maiyasa bazata ɗago ta kalleshi ba kamar zata lashe shi, ko dai itama har yanzu fuskar Matacce Sulaim bai bar zuciyarta ba? Tuna wannan kaɗai sai da zuciyarsa tayi bugawar daya ɗan dafe ƙirjinsa, jin kansa da ƙarin tsanar Sulaim na dirarmasa lokaci ɗaya.

Tarin sumar kanshi ya shafo cikin isa da ɗacin dayake ji a cikin zuciyarsa ya ce " ki shiga Gida, ba ni da wani shagali da zanyi kamar yadda bani da lokacin ƙara dawowa gareki, ina fatan zakiyimin kyakkyawar fahimta" ya yi tunanin zata ji babu daɗi tayi magiya da nuna zumuɗin son dawowar kyakkyawan Matashi irinsa wajenta amma sai ya ga ta ɗaga kai alamar da gamsu. Kafin ta kai ga barin wajen tuni ya tashi lafiyayyen mashin ɗinsa ya baɗeta da ƙura. Kai Naila ta girgiza mamakin abinda ya tunzurashi na kama zuciyarta.

Kaka bayan fitar Naila ta janyo Tufar da Hindu ta bata kamar ana fizgarta ta É—auko ta wanke ta soma ci, har Naila ta shigo tana gutsirar Tufar suna hira a hankali. Tana gama ci barci ya É—auketa. Da mamaki Naila take kallon yadda ta kwanta a jirkice kafin ta gyara mata kwanciya ranta cike da mamaki.

★washe gari Ɗayyib da Hindu suka ɗauki hanyar Babban Birnin Abyad, sai da sukayi kwanaki a hanya.


Maimakon Babban Birnin Abyad ɗin su yi niyyar kama gida sai a Birnin Abyad suka kama, saboda zaman Babban Birnin Abyad da kuɗin Makarantarsu yafi ƙarfinsu amma sun yanke shawarar ba zasu gayawa Sufyan ba idan ya zo ga ne wa idanunsa.

Su da suka tafi da sunan kama hayar shekaru uku daƙyar suka samu mai sauƙi shima ba da asalin tsakiyar Birnin Abyad yake ba suka kama na shekara biyu. Sai guntun kuɗin da suka adana don biyan kuɗin Makaranta Sufyan idan sun samu sun haɗa da wani. Saboda Hindu shawarar siyar da ragowar kadararsu ta yanke idan ta koma.

Har suka iso Gida labarin kyan ƙasar Abyad bai bar bakinsu ba, shima Sufyan tuni ya fara tada kafaɗa zuciyarsa da kanshi tsabar yanda yakejin girmansu gani yakeyi kamar gangar jikinsa ba zai iya ɗaukar su ba. Domin shi a yanzu yafi ƙarfin duk wani Matashi a Masarsutar su bama Yankinsu kaɗai ba tunda ko Ƴaƴan Sarki Hammam mace ɗayace ta taɓa Aure a can shima bawai cikin Babban Birnin Abyad ɗin ba ne daf da shine.


A ƁANGARENSU NAILA;
Har gari ya yi haske Kaka bata motsa ba wannan dalilin yasa Naila ta birkitota da ƙarfi, idanuwanta ta gani a kakkafe. Cikin yanayinta na nutsuwa ta fara ambaton Allah kafin ta nufi Gidan Yayyan Mahaifinta.

Kwanan su biyu ana yiwa Kaka maganin gargajiya taji sauƙi amma magana kam sai a hankali, sai ta wuni batace komai ba ko baifi tayi sau ɗaya ba, tanason bawa Naila labari da yunƙurin daƙile Hindu. Saboda kai tsaye ta fuskanci Hindu ce ta bata Tufa mai ɗauke da sirihin da zai duƙufar da ita ayi komai batare da ta iya yin yunƙurin komai ba, amma ba bu hali.

Sai dai tayi ta hira da zuciyarta. Naila tayi kuka musamman da zancen zaman Aurenta a Babban Birnin Abyad ya cika lungu da saƙon Yankin. Har shishigi Ƴammatan Yankin suka fara yimata da fadanci kullum suna Gidan.

Daga wannan lokacin Naila ta fuskanci dole ta auri Sufyan, musamman idan tanaso ta tsira da lafiyar Kakarta domin itama ta gane Tufar da Hindu Mahaifiyar Sufyan ta bawa Kaka ya mayar da ita haka.

Kakarta tana cikin wannan yanayin Masarautar Yankin Tudu suka fara gudanar da shagalin gagarumin bikin da ya tashi kan mutanen Yankin, har ma da maƙotan Yankunansu.

Da ido da hannu Naila take magana da Kaka kuma ta fahimceta, duk shagulgulan da suka yi, ɗaya aka gayyaci Naila da ƙawayenta ƴan shishigi sai ƴar Yayan Mahaifinta Laila.

Sufyan ya yi kyau kamar ka sace ce shi ka gudu murnar tafiya Babban Birnin Abyad na ƙara haukata kanshi yanajin inama da Kabeer yana nan ya nuna masa shi ba'asan yinsa bane, kuma ba da iyakacin Shugabancin Kasuwar Tukwanen Zinare suka dogara ba.

Wani irin kyau Babban Birni Abyad yake da shi har Sufyan da bai taɓa zuwa ba yakewa zumuɗi???...✍🏻
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥


NAFISA ALIYU SASAAL


*CHAPTER 2*

*TAFIYAR NAILA DA SUFYAN BABBAN BIRNIN ABYAD*


Pg 10

NAILA;
A dai-dai lokacin da mutanen Yankin su ke ji inama da su ne zasu tafi Babban Birnin Abyad Naila na maƙale da Kakarta ranta ba daɗi.

Gabannin sallar magrib Malamin da ya ke yiwa Kaka rubutu ya aiko da shi.

Kaka da ke cikin matsanancin damuwa saboda abubuwa ma su muhimmancin da takeson sanarwa Naila amma babu hali laƙwas tayi idonta ƙyam a kan dogayen yatsun Naila da ke juyemata rubutu a kofi.
Kanta Naila ta kamo bata saketa ba har sai da ta gama sha. Yunƙurawa tayi ta miƙe, sai dai ko taku ɗaya ba ta yi ba ta ji Muryar Kaka na ambaton sunanta
"Naila"
Da sauri ta juyo cikin mamaki kafin ta rungumeta da ƙarfi haɗe da kai mata sumba a gefe da gefe ƙuncinta. Da tsananin farin ciki ta ce;
" na ji daɗi sosai Kaka fargaba da komai ya gushe da ga gareni tunda ga shi kin faɗi sunana sosai Allah Ya cigaba da karemin ke Kaka" Kaka da tsananin farin ciki ta amsa da "Amin" sai dai bayan amsawarta ƙwallane ya cika idanuwanta da su ƙyam a kan Naila.
Ta yunƙura zatayi magana Naila ta dakatar da ita, ta hanyar girgiza mata kai. Amma duk da haka bayan wasu daƙiƙu sai da ta numfasa cikin karyewar zuciya ta fara magana;
"Kafiyata da nuna ikona ba za su yi tasiri a garemu ba, tunda tun kafin muje ko ina Hindu ta fito mana da manufarta ƙarara. Amma Allah Ba ya barci Naila, da ƙarfin mulkinSa zuwanki ƙasar Abyad babban nasara ne a gareki, makircinsu shine matakin nasararki In Shaa Allahu."
maganganun Kaka sun ƙarawa Naila ƙwarin gwiwa a kan wanda take da shi, har tanajin zata jurewa duk wasu ƙalubale da zasu biyo bayan zaman auren su da Sufyan.

A haka suka raba wannan dare su na hira saboda washe gari Naila za ta bar Gidan, mafi rinjayen hirar ta su a kan Tufar da Hindu ta ciyar da Kaka ne da kuma shawarwari da dabarun zaman Gidan Miji.

★washe gari da sassafe Dangin Mahaifin Naila su ka zo ɗaukarta, saboda sunfi son a zo ɗaukarta a inda su ka tsara. Kaka bata tanka ba sai rungume Naila da ta yi bayan ta sumbaci goshinta. Cikin ƙarfin halin danne kukan da ta ke yi ta ce; "Ki kula Naila, inanan ina jiran dawowarki wata rana da dumbin nasarar da zaki zamemin abin alfahari da Mutanen Yankinki gaba ɗaya, ki mayar da hankali kan sana'arki saboda sana'ar kitso baiwane mai girma a ƙasar Abyad. Daga ƙarshe ki tuna da shawarwarina, haƙuri, juriya da biyayya sune matakan nasararki" daga haka Kaka ta saki hannun Naila da ke kuka kamar zata shiɗe.


Barin Gidan Kaka zuwa Gidan ƙannen Mahaifinta ya tabbatarmata da ta bar Gidan Kaka kenan sai kuma wata rana idan da rai da lafiya. Bayan sun kai can zagaye ta su ka yi kowannen su na faɗar albarkacin bakinsa da sunan nasiha.

Ba bu nisihar Kawunnanta ɗaya da ya shigeta saboda kallon maƙiya ta ke yi mu su, kamar yadda su ka nunamata ƙiyayya a zahiri.

Ba ya tabbatar da ita cikakkiyar Marainiya ba ce, sai da dangin Mahaifinta su ka miƙata Masarautar Yankin Tudu. Sufyan ya na zaune a tsakankanin Iyayensa, wannan ya tunamata da nata Iyayen dalilin haka sai kukanta ya ƙaru, takaicin yadda ƴan uwan Mahaifinta su ka dinga ƙasƙantar da kansu duk don samun wajen zama a wajen Ɗayyib kamar ya kasheta.

A ranar ta zagaya Masarautar Yankin Tudu ta kuma tabbatar da kyansa da mutane su ke zuzutawa, har gaban Sarki Hammam sai da ta kai gaisuwa. Bayannan aka miƙata ɓangaren da zata kwana.

Bata shafe hour biyu da kwanciya ba Matasan mata ma su kusan shekaruna su ka shigo, da alama turosu akayi don tayata kwana. Ba su san ba barci ta ke yi ba su ka fara hira.

Cikin jimami É—aya ta ce;
"Ai ni na jiyo abinda yafi ƙarfina, ni dama na yi zargin Uwar gida Hindu bazata taɓa yarda wannan makirin ɗan nata ya auri ƴar ƙaramin Gidan da su ke talakawan fitik ba sai da wata manufa"

Cikin rashin yarda ɗayar ta ce "Ni kam sam na kasa yarda da zancenki Ƙawata, ta ya ya zata sadaukar da dukiyarsu da ake zuzutawa a kan abinda ba ta da tabbaci a kai, anya kuwa kin jiyota da dakyau?"

"Wallahi tsaf na jiyota, ke harda sharaɗi ta ce ta kafamai, karya kuskura ya kusanci Matar kar a haifo mu su ƙasƙantaccen jika, ya bari su ga kalar ɗaukakar da zai samu."

Naila tana jin su suka kwashe da dariya haɗe da tafawa, kafin ɗayar ta ƙara cewa;

"To wallahi ki adana wannan dogon bakin naki idan ba haka ba shi zai kai ki ya baro kin ji na gayamiki."

Da sauri ta damƙi bakin na ta kafin ta saki su ƙara kwashewa da dariya.

Daga kwancen da Naila take jikinta ya fara rawa, gumi da zazzaɓi su ka lulluɓeta lokaci ɗaya. Kuka mara sauti mai fitowa tun daga ƙasar zuciya na zuwar mata, ƙwarin gwiwarta na bin iska. Ta ɗauki lokaci tana kuka mara sauti kafin wahalallen barci ya fara ɗaukarta, har barci ya ƙarasa ɗauketa ba su daina tattaunawa ɓoyayyun sirrinkan da su ka shafi Masarautar ba.

★washe gari da ta farka da su tayi tozali su na barcinsu hankali kwance, daga yanayin suturun jikinsu ta gane ba Bayi bane Ƴaƴan Gida ne.

Shagali na musamman aka ƙara shiryawa kafin tafiyarsu Ƙasat Abyad.

Faɗa sosai Jalal kakan Sufyan da Mahaifinsa Ɗayyib su ka yimata. A ɓangaren Mahaifiyar Sufyan Hindu faɗar hannunka mai sanda tayimata mai surke da baƙaƙen maganganun da ke nuna ba Mata ta aurawa Sufyan ba Baiwa ta auramai. A gabanta ta ƙara jaddadawa Sufyan Umarninta, wanda bata raba ɗayan biyu akan hirar da taji ƴammatan jiya su na yi ne. Ba bu wani mai faɗa aji a Masarautar Yankin Tudu da baiyimata nasiha ba, wa su na su nasihar ta lallami suka yi mata wa su kuma gori da nuna iyaka ne kai tsaye.

Daga haka Drivern da zai kaisu iyakar Yankin Tudun da zasu hau Motar ƙasar Abyad ya ƙaraso. Sufyan da ke sanye cikin tsadadden farin yadi mai taushi, malalacin murmushin da ke nuna jin kanshi ya saki haɗe da ɗagawa Mutanen Yankin da su ka yi kirco-kirco su na washe baki hannu.
Idanuwansa a kan Mahaifiyarsa suka tsaya daga ƙarshe, alamar jinjina ya yi mata kafin ya shigo Mota ya na gyara zamansa a gefen da Naila ta ke.

Da sannu da sannu motarsu ta fara motsawa har lokacin mutanen Yankin na ɗaga musu hannu, kukan da Naila take ɓoyewa ya bayyana saboda tuna Mahaifana da Kakata da na san tana can tana kuka.

Naila ta bar Yankin Tudu da tarin rauni da tabo a cikin zuciyarta, ko yaya zamanta a ƙasar Abyad zai kasance??

Kuyi manage
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: .🔥ZINARE🔥


SASAAL


11

Duk kukan da Naila ta ke yi, Sufyan ya na jinta amma bai ce kanzil ba. Sai da ya fuskanci ba kukan ganin ido ba ne na gaske ne, sannan cikin isa da izzar fitarshi zakka a kaf faɗin ahalinsa saboda samun nasarar tafiya ƙasar Abyad yin karatu ya ce;
"Kukan na menene? Kinsan ina zakije kuwa? Dan Allah karki ɓatamin farin cikina, ke da ma baki da Iyaye, ko ni da na ke da Iyaye a raye bandamu sai ke. Kar ki bari tun kafin tafiyarmu ta yi nisa ki fara saɓawa umarni na kinji na gayamiki" da ga haka ya ɗora farin yatsun hannunsa da bai san wahalar komai ba a saman dogayen yatsun Naila.

Maganganunq sun soketa irin sukar da Marainiya ƴar uwa ta ce kawai za ta san zafin su, saboda ƙara jaddada matan da ya yi da gaske bata da Iyaye don haka bata da abin yiwa kuka.

Bata ƙara ko da tari ba sai idanuwanta da ta lumshe tana jin yadda Drivern Motar su ya ke kwarara gudu.

A tashar da zasu hau Motar da zai yi tafiyar kwanaki kafin isarsu ƙasar Abyad Drivern da ya ɗaukosu ya sauke su. Hannun Sufyan maƙale da nata, ya je ya siyamusu tikiti, suka shiga ƙaton Mota mai ɗaukar fasinja da yawa zuwa ƙasar Abyad.

Ba su jima a ciki ba bayan sunci abinci, aka fara sanarwa tashin motar da komai na cikinsa ya ke kamar na jirgin Sama.

A gefen Sufyan ta ke zauna, kamar zai sumbaceta haka ya sunkuyo da sunan ɗauramata belt. Bayan ya ɗauramata ya ƙara kamo hannunta ya sarƙewa da na shi.

Murmushi mai ciwo ta saki a cikin zuciyarta, tana ganin ba lallai Sufyan ya cika alƙawarin da ya ɗaukarwa Mahaifiyarsa ba.

Tafiyar su bana yini da kwana ba ne tafiyar kwanaki ne, saboda da su Sufyan hamshaƙan ma su arziƙine da jirgin sama za su biya masu ba mota ba. Duk inda zasu tsaya ba bu magana a tsakaninta da Sufyan sai kayan guzurin da Mahaifiyarsa ta zubamai a ƙaramin Akwati mu ke ci akai-akai.

```BIRNIN ABYAD```

Lokacin da Motarsu ta iso Birnin Abyad, yanayin sanyin ƙasar, hasken Mutanen ciki, gina-ginensu, da wasu irin motoci ma su kyan gani a ido da kwaɗayin son shigarsu ne su ka haske mudu idanuwa.
Idanuwan Naila da ta ke jinsu kamar madara saboda haske a Yankinsu sai ta ke jin su a Birnin Abyad kamar sun koma jajaye saboda kyawun mutanen Birnin da take gani da gine-ginen su. Sai ta ke hasaso Yankinsu kamar wani kusurgumin daji mai duhu da ya ke da ƙaracin kayan more rayuwa. Fatarsu da na ke ganinsa mai haske da kyau a Yankinsu a take ya dusashe a idanuwanta ya koma sak na ƴan karkara, ƴan karkarar ma su ƙarancin komai na cigaban rayuwa.

A maganganunsu ta fuskanci ba sa kai ƙarshen zance sai sun haɗa da harshen nasarar da Malaminsu yake ta kwaɗaitar da su, su koya.

Wa sun su kuma nasarar kawai su ke yi babu sirki.

Tunano yadda Mutanen Yankin Tudu su ka dinga ɗago musi hannu lokacin tahowarsu sai tausayin su ya ƙara tsargamata musamman Kakarta da Mahaifanta.

Mahaifinta ya ƙare rayuwarsa a dinki ƙarshe rashin gatan Asibiti ya yi sanadiyar ajalinsa, haka Mahaifiyarta. Kakarta ce dai ba ta cire rai tare da Yaƙini haɗe da fatan wata rana ta zo taga duniyar Birnin Abyad ba.

A ɓangaren Sufyan shima ji ya yi duk ya muzanta, wannan jiji da kan da sumarsa da ya tara duk domin ya zo ya Yaƙi Ƴammatan Birnin Abyad sai ya bi ruwa, ya na jin inama da yana da hula a kusa ya lulluɓe gashin saboda Kunya. Farin fatar da ya ke yiwa Mutanen Yankin Tudu yanga da shi sai ya ga ashe da sauransa, Kananun kayan da idan ya sa a Yankinsu maza da mata su ke bi su na kallo har da tuntuɓe sai ya tashi kamar na ƴan Karkara.

Lambar wayar wanda zai kai su gidan da Iyayen Sufyan su ka kama musu ya zaro a ƴar ƙaramar jakar da ya ɗauko ya na yanga da shi a Yankin Tudu saɓanin isowar su Birnin Abyad da ya ɓoyeshi a hammata.

Cikin ƙarfin hali ya tambaya aka nunamai wajen kira. Shi kanshi sakayayyen wajen kiran da aka sakaye da gilashi abin a yaba ne.

Naila Nutsuwar ya ne ya ta taimaka wajen sakaya gidadancinta, saɓanin Sufyan da dama can ba wani cikakken nutsuwa ce da shi ba, dan dole ya ƙaƙabawa kanshi nutsuwar dole kamar ba Sufyan Ɗan gidan Ɗayyib shugaban kasuwar Tukwanen Zinare ba😂.

Ba su wani jima ba, Uban gidan ÆŠayyib mazaunin Birnin Abyad ya zo É—aukarsu.

Sai da suka tashi hawa Motar inda zamu je Makka ta fahimci ABYAD sunan ƙasar ne Birnin Abyad kuma shine inda aka sauke su kuma anan Mahaifan Sufyan su ka kama Gida, BABBAN BIRNIN ABYAD kuma shine asalin Babban Birnin da kaf faɗin ƙasar ba bu kamar shi.

To idan har Babban Birnin Abyad da take ji a bakin Mutanen Yankin Tudu ya fi inda suke ciki kyau da tsari to ya ya kyansa da mutanen cikina za su kasance??? Naila ta tamabayi kanta, lokacin da suka isa inda zasu shiga Mota.

Bayan sun shiga motar da za ta kai su Gidan da aka kama musu, idanuwanta su ka faɗa kan Motocin da akace su ne masu shiga Babban Birnin Abyad, ko da batayi karatu mai zurfi ba, bata kuma saba riƙe kuɗi ma su nauyi ba tasan ba motocin shigar mutane ne irinsu ba.

Tafiyar Motocin take kallo tana jin kamar ta fito ta bi su. Sai ta ke jin kamar tana ƙewar abinda ita kanta batasan menene a inda za su je ba, tana kallon tafiyar motocin wani yanayi na tsarga zuciyarta, haka ta yi taji har Motocin suka ɓacewa ganinta.

Kasa jurewa ta yi ta tambayi wanda ya zo É—aukarsu; " hour nawa ne tsakanin Birnin Abyad da Babban Birnin Abyad"
Amsar "hour biyar" ya ba ta tare da shaidamata mutum zai iya zuwa a ranar ya dawo a ranar. Sufyan da ya ke tunanin ta yi tambayar ne domin ta nuna Iyayensa ƙarya suke yi, da su ka ce sun kama mai Gida a Babban Birnin Abyad harara ya watsomata ya na cije baki.

Unguwar su da Gidan da aka kama musu abun a yaba ne, duk da ba ta jin komai akan Sufyan na soyayya ko makamancin haka sai da ta ji ya ɗan birgeta, saboda gida ne da bata taɓa mafarkin zata kwana a cikin irinsa ba har ƙarshen rayuwata.

SUFYAN;
Da Sufyan ya yi tozali da living room da two Bedrooms ɗin da su ka sha kayan ado dai-dai misali a matsayin hidimar da Mahaifansa su ka yi mai sai ya ji kwaɗayin son karya alƙawarin Mahaifiyarsa akan Naila na bin iska daga gangar jikinsa.

Da farko kafin tahowar su ya yi zargin ashe dukiyar da ake zuzutawa Kakansa na wajen Uwa ya mutu ya bari duk ƙaryane, banda ƙarya ne tayaya za'ace da dukka wannan dukiyar da wanda Mahaifinsa ya samo akayi hidimar kamamai Gida ba ma Siyamai ba da biya masa Makaranta a Birnin Abyad? Sai da ya gani da idonsa sannan ya tabbatar da dagaske ba ƙananun dukiya ba ne za su zaunar da mutum a unguwar da aka kama mu su Gida ba.( a nasa ganin kenan, domin a wajen masu zuzurutun dukiya, gadon da ake taƙamar Hindu tana da shi, bai wuce kuɗin kashewar mai arziƙi a yini biyu ba).


Idan har Mahaifiyarsa za ta yi irin wannan sadaukarwa saboda É—aukakarsa ba tare da damuwar komai ba, to ba bu abinda zai hana shima ya sadaukar mata da na sa farin cikin.

Amma duk da haka dole ya rage zafi, domin ba zai iya kwana É—aki É—aya da Naila ya tashi da ita ba tare da ya rage zafi ba.

Gidan ba su su ƙadai ba ne, mutum huɗu ne a Gidan amma kowa rayuwarsa yake yi, ba tare da damuwa da rayuwar Ɗan uwansa ba.

NAILA;

wanka ta yi ta ƙimtsa jikina. Sai a lokacin taga kamar ta ɗanyi kyan gani, saboda dattin Motar da ta wanke daga jikina. Ɗakin da Sufyan ya bata a matsayin nata take ƙarewa kallo, nutsuwa na saukarmata.

Cikin baƙaƙen Abayoyin da ta taho da su masu adon saƙi ta shirya ta tayar da Sallah ta inda ta ga an shimfiɗa abun Sallah alamun nan ne gabas.

Bayan awannin;
Uban gidan Ɗayyib ya hidimta musi ƙwarai da jikinsa da lokacinsa har ma da kuɗin aljihunsa. Abinci mai daɗin da basu taɓa ci ba ya siyomusu Da Suturar sawa kala biyu da ya siyo Sufyan don fara zuwa Makaranta sai wayar hannu da layi a ciki shima mai kyau dai-dai misali.

A kunyace Sufyan ya sa hannu ya karɓa ya na ƙara tabbatar da ashe ba shi kaɗai bane ya raina kayan jikinsa ba dagaske kyan ne ba su da shi.

Da yake saukar Safiya suka yi bayan sunci abinci, Uban gidan ÆŠayyib ya yi mu su Sallama da sunan washe gari zai dawo.

Barci ya kwashe kowannensu a É—akin da ya ke.

Ba su farka ba sai azahar shima babu wanda ya fito a cikin su tunda kowanne da abinci da zai ci a na dakin. Sai wajen ƙarfe 9 da ƴan mintina na dare Sufyan ya shigo ɗakin Nsila.

Gaisheshi ta yi ta ƙara gyara lulluɓin kanta.

Wayo da kuma shekarun da Sufyan ya fita yasa ya fara goge maganganun ƴan matan da ta ji a Masarsutar Yankin Tudu. Da farko kusa da ta ya matso ya zauna saboda ya lura kamar ta na da sani ko hasashe a kan abinda ya ke ranshi. Cikin taushin lafazin da lumshe idanuwansa da su ke tsaye ƙyam a kan fuskarta ya ce;

"Na san surutai da yawa za su yi ta zuwa kunnenki Naila, amma iyakacin wannan Gidan da kuɗin motar da Iyayena suka kashe mana ya kamata ace kin watsar da surutun auren manufa akayimana da ke, Mahaifiyata Mace ce mafaɗaciya kuma tana tsananin so na wannan dalilin yasa ta kuɗiri niyyar auramin matar da zata bauta min kamar Sarki da Baiwarsa, amma kisani Naila har cikin raina ban zaɓe ki domin kisha wahala a Gidana ba, sai domin muyi zaman aure ki bani goyon baya ɗari bisa ɗari akan karatu na. Mun zo nan ga shi kuma kuɗin Mahaifana ya ƙare a wannan hidimar da suka yimana, kuma a halin yanzu ina buƙatar suturun sawa kuɗin hidindimun makaranta da kuma abinda zamu ci Naila."

Naila da batasan sanda ta É—ago kanta ba, idanu ta zubamai domin sam bata fahimci ina ya dosa ba.

Fahimtar hakan ya sa ya cigaba da magana cikin ƙaramin sauti.
"Naila da Baiwarki zaki taimakamin Ni kuma na yi alƙawarin mayar da ke mace ƴar gata a cikin ƴan uwanki Mata."

Still Naila bata fahimci ina ya dosa ba don haka ta ƙara gyara zama.
Da kame-kame ya ce "ina so ki bi dukka Gidajen Unguwarnan ki sanar da su kina kitso, a kwai ma su ra'ayin kitso a cikin su, da wannan kaɗai zaki taimakamin Naila na roƙeki"

Dan jim Naila ta yi maganganun Kaka na dawo mata "ki mayar da hankali kan sana'arki saboda sana'ar kitso baiwane mai girma a ƙasar Abyad."

Cikin yarda da rauni irina Æ´a mace Naila ta É—aga kai alamar ta gamsu ko dan Kaka tayi alfahari da ita.

Da sauri Sufyan ya rungumeta kafin ya yi dabarar ragewa kanshi zafi, Bayan wani É—an lokaci ya tattara ya bar É—akin.

NAILA;
Da murmushin raɗaɗin da marata yakemin na mirgina na kwanta, abinda Sufyan bai sani ba zuciyata Macacciyace ba bu rai balle a yaudareta, da sha'awa yana da yare da ko ya taɓani baza ta ji komai ba sai dai bani da ikon hakan.
"Idan ƙarya yakemin domin ya zalunci ne Allah Shi ne gatana," daga wannan hirar zucin Barci mai nauyi ya ɗauketa...✍🏻
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/I1wZrvGJP2s3QIyUuJ4ig7?mode=r_c


🔥ZINARE🔥


SASAAL


12

★washe gari bayan nta yi sallar Asubahi bata koma barci ba, har sai da gari ya yi haske.
Barcinta bai yi nisa ba, Sufyan ya tasheta. Da kayan da aka siyomai jiya ya yi ado, ya yi kyau dai-dai misali domin baza ta ce sosai ba, a matsayinsa na Mazaunin Birnin Abyad. Bayan ta gaishesa ya ji bataƙara da komai ba sai ya haɗe rai ya na ƙara shafa wuyar Rigarshi.

Sam bata fahimci ina ya dosa ba, sai da ya yi tsaki haÉ—e da faÉ—in;
" Anya kuwa Naila ki na da lafiyar ido, na san babu Macen da za ta ce banyimata ba, amma ke kullum sai ki dinga nuna kamar Ni ɗin ba wani mai kyau ba ne, ko Hassada ki ke yimin?" ya tambaya da iya gaskiyarsa haɗe da murza zoben silver da ya ke matuƙar ji da shi.

Dariya ƙeta musamman a kan mugunta ba halinta ba ne, amma da ta ƙaremai kallo na tuna irin siffar Mutanen da suka gani a lokacin da suka iso Birnin Abyad sai da ta dara har jerarrun haƙwarana su ka bayyana. Tunda ta ke bata taɓa ganin Namiji mai son ace mai ya na da kyau ba irin Sufyan domin ko Mace albarka, "shi kuma kalar jarabawarsa kenan." Ta faɗa a cikin ranta amma a zahiri miƙewa ta yi kafaɗunsu na gogar na juna ta ce;

"Kai kyakkyawane ko ba ka yi kwalliya ba, balle yanzu da kayi ado da kayan da aka siya a Birnin Abyad, Godiya ta tabbata ga Ubangijin halittun da ya halicci Namiji kyakkyawa irinka Mijina."

Dariya da bata taɓa gani ya yi irinsa ba ya saki, ya na kamo fuskarta, sumba ya saukemata a goshi tsabar daɗin da yake ji har wani lumshe ido yake yi yana binata da kallo kamar zai lasheta.
Sallama ya yi mata, Har ya fita ya ƙara dawowa ya na jaddadamata alƙawarin da ta yi mai.

Bayanshi ta bi da kallo maganar Kaka na faɗomata; " ko wani Namiji da kalar halinsa, halin Mijin wata ba zai taɓa zama irin naki halin Mijin ba, dole a samu banbanci duk ƙanƙantarsa, don haka ki karanci halayyar Mijinki saboda samun sauƙin zama da shi." Ta gazgata zancen Kaka a kan Sufyan saboda duk daɗin soyayya ko kwalliyar da Mace za tayi domin ta ja ra'ayinsa ba ya ɗaɗashi da ƙasa a kan ta zauna ta na zuzuta kyansa da yaba kwalliyarsa sama da kyan da ya yi.

Kamar yadda nta alƙawartawa Sufyan da maƙotansu da su ke cikin gida ɗaya ta fara, ba ta jin turancin arziƙi amma kuma hakan bazai daƙusar da ƙudirinta ba. Ko da kwatacce ne da haɗe-haɗen iya wanda ta iya zata yi mu su bayani har su fahimta.

Biyun dukka Mata ne kuma tayi sa'a dukkansu gashinsu na kitsawa ne amma ɗaya kai tsaye ta shaidamata bata da ra'ayin yin kitso saboda zafi ya ke mata. Cikin ƙanƙan da kai kamar ta saba da ita ta kwantantamata ta zo ta gwada yimata hannuna ba shi da zafi. Ga mamakinta cikin raha ta ce to ta je around 2:00pm na dawo.

Abinda Ruwaida Maƙociyarta ta ce mata na ta je ta dawo ya ƙaramata ƙarfin gwiwar tunkarar ko ina domin tallata sana'arta. Mutum na ƙarshe a gidansu Namijine ɗan asalin ƙasar Abyad fatarsa fara fat.

Ta na shiga Sashensa Da sauri ta fito duk kiran da ya ke ƙwalamata bata juyo ba, tama jiyoshi ya na dariya da alamun mamakin Gidadancita ya ke yi.

Duk Gidan da zata shiga Daƙyar ake barinta, wasu su yimata tarba mai kyau wasu kuma su wulaƙantata. Gida na ƙarshe kuma mafi kyau a layin shi ta tunkara sai dai kai tsaye dakarun da su ke gadin Gidan su ka hanata Shiga.

A gajiye na dawo Gida, saboda ba laifi ta yawatu, ba kuma komai yasa ta dage ba, sai don sauya tunanin Sufyan daga wanda Mahaifiyarsa ta É—orashi a kai.

Kamar yadda Ruwaida ta ce ta dawo ƙarfe biyu haka ta koma akan lokaci.

Yanayin ɗiban kitson da yadda ya kwanta a saman farin tafin kan Ruwaida ya yi matuƙar ƙayatar da ita ga shi sam ba zafi, godiya tayimata da tsananin farin ciki a saman fuskarta.

Da Ruwaida ta tashi sallamarta, da iya adadin kuɗin a ke biyan makitsa a Birnin Abyad ta biyata, nutsuwarta ce kawai ta riƙe Naila.

A lissafin kuɗin da tayi zuwa na ƙasarsu, ko Iyalan Sarki Hammam da ake matuƙar ji da su, suke biyanta da kuɗi ma su ƙauri ba su taɓa bata kwatankwacinsa ba.

Ƙwalla ƙwance a ƙasan idanuwanta ta ke yiwa Ruwaida godiya.

Dariya Ruwaida ta saki cikin mamakin yadda Naila ta damu ta tambayeta daga ina take?

Saboda ta ƙara tausayamata ta naimomata customers, Naila ta fara ba ta labarin ita da Mijin tane su ka zo, ya zo Karatu ne kuma kuɗin iyayensu sun ƙare shine suke neman kuɗin cin abinci da sauran buƙatun rayuwa. Dafata Ruwaida tayi cikin tausayawa ta yimata alƙawarin zata naimo mata mutanen da zata dinga yi musu kitso ta na samun kuɗi amma na tambayi Mijina shin zai barta zuwa Gida-gida yin kitso?

Naila ba ta zaɓi yanke hukunci ba tare da ta tambayi Sufyan ba, don haka ta ce ta bari na yi shawara da shi idan ya dawo.

Daga haka dukayi sallama kuɗinta ma ƙanƙame a hannunta.

SUFYAN;

Lokacin da su ka isa Jami'ar Birnin Abyad da Ubangidan Ɗayyib ya yi cuku-cukun samo masa ya yi mamaki tare da ƙaƙabawa zuciyarsa cika alƙawarin Mahaifiyarsa babu gudu babu ja da baya.

Bayan sun gama yin komai. A ranar ƙarfe 12:00pm Sufyan ya fara ɗaukar lectures saboda tuni su ka fara ba bu shi.

Bayan sun gama lecture Harabar Makarantar ya fito ya naimi wajen zama, tunanin kuɗi da yadda zai yi kalar rayuwar da zai samu Mace wayayyiya ƴar Birnin Abyad ɗin da zai yaƙi mutanen Yankin Tudu da ita na ya zauna yi. Ya na cikin wannan yanayin wata matashiya mai kyan gaske ta raɓa gefenshi ta zauna. Sanye take cikin ƙaƙanun kayan Saint Laurent riga da wandon da suka amshi farin fatarta sai lulluɓin da ya lulluɓe iyakacin wuyarta bai sauko kafaɗunta ba.
"Barka dai kyakkyawan Matashi, sunana Sumaya, kai fa?" Ta faɗa da harshen nasara mai ɗauke da cikin wani irin sanyi murya tana miƙamai hannu.

"Kyakkyawan Matashin" da ta faɗa ya fi bugar da kan Sufyan a kan kyan fuskarta. A ƙiyastin da ya yi a cikin daƙiƙu zata yi sa'ar shekaru da shi, babu wani abu mai kyau a saman fuskarta da gangar jikinta da Naila da take cikin talauci bata da shi currently. sai wayewar da ta fi Naila da kuma hasken fatarta mai tsananin haske sosai.

Cikin salo da yadda ta birgesa har cikin ransa da jin nan take ya samu Abokiyar rayuwa ta zahiri matsawar ba ta fi ƙarfinsa ba ya ce;

" Barka dai ya ke kyakkyawa Sunana Sufyan na ji daɗin haɗuwa da ke" ya ƙarasa faɗa yana damƙar hannunta.
Daga haka kamar wasa hira mai cike da aji da zuzutawa kyansa irin yadda ya ke buri da ga Naila batayi ya ɓarke a tsakaninsu, har da musayar lambar waya.

Kan Sufyan bai ƙara ɗaukar zafi da kwaɗayin mallakar dukiya ba sai da yaga Sumaya har ɗan ƙaramin mashin mai kyau take da shi, ba irin na shi na Yankin Tudu ba.

Da aka tashesu Da sakin fuska ta yi masa tayin hawa, ba tare da ɓata lokaci ba ya ɗane.

A hirarrakin su kafin su isa Gida Sufyan ya fuskanci Sumaya ba wata Æ´ar ma su kuÉ—i ba ce a Birnin Abyad, naiman kuÉ—i ne ya kawo Mahaifanta har su ka haifeta a nan ta kuma yi dacen samun scholarship a Makarantarsu.

Ran Sufyan fari fes Sumaya ta saukeshi a layin Gidan su, kamar kar su rabu haka su ka yi sallama, Sufyan ya nufi hanyar Gate ɗinsu da ƙayataccen murmushi a saman fuskarsa.

NAILA;
Wanka ta yi taƙara shirya kanta cikin abayar ta dai mai adon saƙi, sai dai ba baƙi ba ne kamar ragowar. Ta na ƙoƙarin shiga kitchen don duba abinda zata iya dafawa daga Abinci da Ubangidan Ɗayyib ya kawo mu su, ta ji ana knocking. ƙofar ta nufa da saurinta, tana buɗewa taga ashe Ruwaida ce, kanta ba bu kallabi da alama bata da mu dashi ba duk da kasantuwarta cikakkiyar Musulma. Mazubin abinci mai kyau ta gani a hannunta. Cikin gwari-gwarin Turanci da zata fahimta Ruwaida ta shaidamata Abinci ta kawomata sannan gobe idan Mijinta ya amince ta shirya zata kaita wani Gida a ƙarshen layinsu da zan ta yi kitso. Godiya mai tarin yawa Naila ta yi mata sannan su ka yi sallama.

Bayan Naila ta koma ciki
Kasa taɓa abincin ta yi, ta zauna zamam jiran dawowar Sufyan su ci tare.

Sufyan;
Da murmushi a saman fuskarsa ya ƙwankwasa Naila ta buɗe mai ya shigo, yana ganinta ya kalli Abayar jikinta sai ya sauya fuska. Har cikin ranta bata kawo komai ba, sai ɗaukar da ta yi masa a matsayin bauɗaɗɗen mutum mai saurin fushi.

Fuska ba walwala ya amsa gaisuwata haɗe da sumbatar ƙuncinta kamar yadda al'adar Yankinsu ya ke.

Ruwan wanka ta nufi hanyar ɗakinsa domin haɗa mai ya dakatar da ita, ya miƙe ya shige har da mirzo mukulli, ita dai Na'ilah ba ta damu, ta dawo ta zauna

Bayan ya fito ta gabatar masa da Abincin da Ruwaida ta kawo musu, ba bu tambayar ina ta samo? Ta ci ko ba ta ci ba? Ya zauna ya take cikinsa sai kaÉ—an da ya ragemata. Jiki a sanyaye ta É—auka ta ci ranta babu daÉ—i.

Sufyan fahimtar sauyi a fuskar Naila yasa ya fara ƙorafin ai bai san bata ci ba, kuma maiyasa ma ba tasa hannu sunci tare ba? Batace mai komai ba, amma na ɗan ji sanyi a raina yadda ya nuna kulawarsa.

Bayan ta gama ci ta kai kwanukan madafi, ta fito da kuɗin da Ruwaida ta bata, da kuma naiman izininsa akan Gidan da ta ce zata kaita, ga mamakinta Sufyan ƙanƙameta ya yi yana dariyar nishaɗi, ba tare da wani jinkiri ba ya fara kasafta kuɗin.

"Naila kuɗinnan kawai abinda ya kamata shine na ƙara riga ko kala ɗayane ragowar kuma na samu na cin abinci a Makaranta Kinga yau ma da yunwa na wuni. Allah Ya yi miki albarka Naila" ya ƙarasa faɗa yana shafa duk inda hannunsa ya kai.

Tambayar izinin fitarta gobe da ta tambayesa murya na rawa ya ce ya amince ya na ƙara samata albarka.

Cikin dabara da girman zaluncin rashin tunanin halin da zan faɗa idan tasa buƙatar ta biya ya fara ragewa kanshi zafi, har sai da yaji ya gamsu dai-dai misali sannan ya tattara ya yi daƙinsa ya bar Naila a wajen.

SUFYAN;

Bayan ya shiga ɗakinsa wanka ya ƙarayi fuskar Sumaya da ya ke maƙalemai a cikin zuciyarsa na wasa da nutsuwarsa, sai ya ke ganin anya batafi Naila kyau ba? Dariya ya saki ya na lalubo wayarsa. Ba shi da kati kamar yadda ya sanar da Sumaya don haka ya zauna zaman jiran kiranta.

Kiranta ya na shigowa ya yi maza ya É—aga.

Sun jima su na hira kafin su yi sallama ran kowannen su fari fes.

Sumaya da Sufyan soyayyar da zai kai su ga aure sukewa junansu, duk da yinin su É—aya da haÉ—uwa.

Sumaya tana ganin ta samu Talaka irinta tunda Sufyan ya gayamata Karatu ya zo yi da Yarinyar da Mahaifansa su ka dage sai sun aura mai kar ya zo Birnin Abyad ya na neman Mata, idan ya so duk ranar da ya gama Karatu ya saketa idan kuma ya ji yana sonta to su cigaba da zamansu, shi kuma baya sonta ba kuma zai iya rayuwa da ita bayan ya gama Karatu ba. ÆŠari bisa ÆŠari Sumaya ta yarda da zancen Sufyan.

Shima Sufyan gani ya ke yi Sumaya itace Macen nunawa. Mace Æ´ar Birnin Abyad mai kyan sifa da tarin ilimi kuma ba Æ´ar talakawar fitik irin Naila ba.

Tabbas! Mahaifinsa Ɗayyib zai yi alfahari da shi Kuma Tarihi zai maimaita kansa domin kamar yadda Marigayi Ubaidullahi Dhahab ya dawo Yankin Tudu da tarin dukiya da kuma zankaɗeɗiyar Matar Aure haka shima zai koma Yankin Tudu da tarin Dukiya da kuma Sumaya a matsayin Matarsa..✍🏻
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/I1wZrvGJP2s3QIyUuJ4ig7?mode=r_c


🔥ZINARE🔥


SASAAL


13

Har Dare ya yi Sufyan bai ƙara fitowa ba, dama ba wani damuwa ya yi da nemi Masallaci ba, kuma ya riga ya cika cikinsa..

NAILA;
Ba ta damu da rashin fitowar Sufyan ba tayi kwanciyarta bayan ta shiga Madafi da samawa cikinta wani abun..

★washe gari bayan Sallar Asubahi ba ta koma barci ba kamar jiya.
Bayan ta gama azkar ta tashi na ƙimtsa ko ina. Abinci mara nauyi ta dafa musu, ta jere a kan teburin cin abinci. Da ta tabbatar komai ya kammala sai ta koma ɗakinta domin yin wanka.

Sufyan ranshi fari fes ya tashi, saboda mafarkin ya zama hamshaƙin mai Dukiya sanadiyyar Sumaya. Bai koma barci ba, sai dai ba zama Karatun Alkur'ani ko azkar ya yi ba, wanka ya shiga.

Har Naila ta kammala girki gaban madubin washroom ya na kallon kansa, fatarsa kuwa tsabar dirza da soso a tunaninsa hakan zai sa ya ƙara haske, har zafi ya ke mai. Duk motsin Naila ya na jinta har ta kammala ta wuce daƙi.

Da sauri ya fito ya cinye kusan dukka abincin, yanajin alamun fitowarta ya tattara ya fita da sauri.

NAILA;
Lokacin da ta fito ta ga son zuciyar da Sufyan ya aikata bata yi mamaki ba, saboda tana san ran zai iyayin sama da haka matsawar hudubar Mahaifiyarsa bai bar zuciyarsa ba.

Ragowar ta ƙarasa cinyewa, bayan abincin ya ɗan sauka ta nemi waje ta kwanta tana jiran zuwan Ruwaida.

Misalin ƙarfe ɗaya da rabi na rana Ruwaida ta ƙwanƙwasa ƙofar sashensu. Da hanzari Naila ta lulluɓe sumar kanta har zuwa ƙasan kafaɗuna da yalwataccen malulluɓi. Da fara'a sosai na tarbe Ruwaida. Kamar dai jiya ba bu lulluɓi a ƙanta sai ƙaramin scarf ɗin data nannaɗe gashinta da shi. Ba ta karɓi tayin shigowarta Sashen su ba ta ce ta taho su tafi.

Su na tafe su ɗan hira har su ka kusa kai wa ƙofar Gidan da ya yi matuƙar birge Naila, amma jiya da ta je zata shiga tallata kitsonta aka hanata shiga. Nunawa Ruwaida gidan tayi haɗe da yimata bayanin abinda ya faru. Da farko dariyar da ya sa ta ɗan ranƙwafawa Ruwaida ta yi kafin ta ƙara kallon Naila ta kuma sakin murmushi, da sauƙin turancin da ta san zan fahimta ta ce "Karki ƙara zuwa saboda ba wajen zuwanki ba ne"

"Saboda me?" Naila ta tambaye Ruwaida da mamaki kwance a saman fuskarta.

Babu wasa a saman fuskar Ruwaida ta ce;
"Gidan Simbi ne, Matar Uzair. Ahalin Shahararren É—an kasuwa a Babban Birnin Abyad, ta zo gudanar da wani bincike ne a Asibitin jami'ar mu. Rayuwata ba bu sakewa sam, yawan zuwanki da sunan makitsiya zai iya janyomiki matsala don haka ki kula."

Naila jigum ta yi mutum ɗaya ta taɓa ji da irin sunan a Yankinsu, kuma itace ƴar autarsu Malik uwa ɗaya uba ɗaya. Don haka faɗar sunanta sai ya dawomata da tunanin abinda su ka faru shekarun baya. Simbi sun bar Yankin Tudu ta na yarinya ƙarama ta girmemata da Shekara ɗaya.

Naila a ranta ta ce;
"Nasan ma ba ita ba ce domin babu yadda za'ayi ko Malik da ya ke Babban yayansu ya mallaki irin wannan Gidan a Birnin Abyad balle ita."
Bata ƙara cewa Ruwaida komai ba har suka zo giftawa ta dai-dai saitin Gidan.

Naila ba ta da ciwon ido balle ta ce shi ya haddasamata ƙarancin gani, fitowar Mota mai ɓakin gilashin da akayi ƙasa da shi kaɗan saboda ɗagawa dakarun da su ke gadin gidan hannu ne yasa Naila tayi baya kafin ta saki ƙarar da ya ja hankalin har na cikin motar ya ɗago kai saitin da suke kafin ya zuge gilashinsa gaba ɗaya ya fice daga layin.

"SALMAN!" Naila ta faɗa a sarari, sai kuma ta tuna Salman to ai ya mutu, tun shekarun baya, to idan ba Salman ba ne wanda ta gani yanzu a Mota to wanene wannan? ko ƙaninshi ne? Ta tamabayi kanta.

Da hanzari Ruwaida ta tarota ta na faÉ—in "Naila! Menene ya sameki, kinsan shi ne? Ko bakyajin daÉ—i ne mu koma gida?"

Razanarta Naila ta shanye ta miƙe tsaye ba tare da bin bayan Motar da kallo ba ta ce;
"Na shiga razani ne sai na ke ganin kamar na sanshi"

Ajiyar zuciya Ruwaida ta sauke kafin ta ce "ohh Allah! Naila kin bani tsoro to ai mutane ma su kamaceceniya su na da yawa a duniyar nan ki kwantar da hankalinki kinji?" Kaina Naila ya É—aga mata alamun na gamsu.

Gidan da suka je dukka su Æ´ammatane su biyar kuma abokanan karatun Ruwaida. da alama Makarantarsu a kusa da nan yake.


Jarumtar Naila da son ta tara kuɗi domin cikawa Kaka burinta yasa ta yi juriya kitsa mu su gashin kansu dukka irin na Ruwaida ta yi mu su. Waje ɗaya suka haɗamata kuɗin da ya sanyaya rainta ta ji zazzaɓin da ya ke shirin rufeta ya sauka. Ba su wani jimaba bayan ta gama yi mu su suka bar Gidan. Yanayin shiru-shirun da ta koma lokaci ɗaya ya sanya Ruwaida itama cikin damuwa.

Dalilin haka ya sa bayan sun kai ta ja Naila ɓangaren kafin Sufyan ya dawo.

A kan kurajerun living room É—inta ma su taushi Naila ta lafe tana kallon shige da ficen Ruwaida daga parlo zuwa Madafi.

Cikin yanayinta na barkwanci Ruwaida ta ce Naila ta taso taa tayata girki.

Naila ta na shiga idanuwanta suka sauka a kan Tukunyar girkin Ruwaida, sunan jiki ne yasa ta ƙarasa kusa da Tukunyar da sauri, "DHAHAB" ne rubuce a jikin Tukunyar kuma tare da sunan a ka ƙera Tukunyar ba sticker aka manna ba. A take zuciyarta ta yi bugawar da ya sa na jingina da bango ƙwaƙwalwarta na tariyo mata shekarun baya.

Ruwaida da raha ta ce " kema Tukunyar ya birgeki ko?, ai Kamfanin ahalin su Simbi ne, Yayana a can ya ke aiki shi ya yi min kyautarsa ranar murnar zagayowar haihuwa ta, kinsan kuwa nawa ake siyar da Tukunyar nan, Tukunya ne mai matuƙar tsada, Ni kaɗai ce mai shi a cikin ƙawaye na, Tukunya ne da Sarakuna da ma su dukiya su ke girki da shi, shi kanshi Yayana da yake aiki a can da albashi shi muke rayuwa da ahalina a wadace, kinga kuwa ai ba ƙananun kuɗi ba n.." zubewar Naila ƙasa kamar gini ne ya dawo da hankalin Ruwaida da ke surutun Tukunyar Dhahab kanta. Hankali a tashe ta ja Naila da ƙyar zuwa living room.

Sashen Dr. Yasar moƙocinsu da Naila ta gudarwa Ruwaida ta nufa.

Da taimakon Yasar Naila ta dawo hayyacinta ko da su ka tambayeta abinda ya sameta ta faɗi bata ɓoye mu su abinda ya rikita ta ba.

Bayan ta gama ba su taƙaitaccen labarin Yakinsu Ajiyar zuciya dukkan su, su ka sauke.

Har cikin ranta Ruwaida ta yarda da gaske kamanceceniyar Mutumin da Naila ta gani sak Salman da Tukunya mai irin sunan Abduh Dhahab ne kawai su ka rikitata a matsayinsu na mutanen Yankinta ba tare da wani alaƙa ba a tsakaninsu ba, saɓanin Yasar da ya kasa yarda Naila ba ta da haɗin komai da abinda ya rikitarta sai alaƙar Yanki kawai.

Sai gabannin la'asar Ruwaida ta taimakamin na koma sashena.

SUFYAN; Bayan sun fito daga lecture, Sumaya ya sa rakasa ya zaɓo kalar rigar da take so. Sauƙin kayan sawar Ƙasar Abyad da abincin cin su ne yasa itama ya siya mata irin rigarsa su ka yi anko, ragowar kuɗin kuma abinci ya siya mu su mai lafiya suka ci suka ƙoshi, ɗan canjin da ya rage ya loda kati saboda kiran Mahaifinsa Ɗayyib.

A ɓangaren su Ɗayyib da Hindu lokacin da Sufyan ya kirasu ya basu labari sun sa masa albarka tare da nu na tsananin jin daɗin yadda Naila ta fara samun kuɗin da zai yi karatunsa hankali kwance, saboda Ɗayyib ya shaidamai bayan tafiyarsu da kwana ɗaya akaci Kasuwa bai san dalili ba sam babu cikini.

Bayanin Mahaifinsa sam bai É—aga mai hankalin ba, tunda ya samu Naila ta fara sana'ar da su ke samun kuÉ—in shiga. Bai ba su labarin haÉ—uwar sa da Sumaya ba saboda ya san bazasu ba shi goyan baya ba, za su ce yayi wuri ya É—akata shi kuma abinda ba ya son ji kenan.

A wannan yini da Sufyan da Sumaya su ka ƙarayi a Makaranta, shaƙuwa mai ƙarfin gaske ya ƙara shiga tsakaninsu. Kowannen su ya na jin ya yi dace da Abokin rayuwa dai-dai burinsa.

Kamar jiya ita ta koshi har bakin Layi.

NAILA; Bayan ta dawo kasa aikata komai ta yi, barcin ma da ya ɗauketa a zabure na miƙe saboda mummunar mafarkin da ta yi, wai ga Salman ya biyota zai ciremata harshe. A take wani irin tsoro da kaɗaici ya soma tsargata.

A haka Sufyan ya shigo ya same ta. Bai tantace muryata da kuka ya dusasar ba, balle kayan jikinta da batayi wanka balle ta sauya su, kuÉ—in da'aka biyata a wajen kitso ya tambaya bayan ya zauna.
Dama su na gefeta, don haka ta ɗauko ta miƙamai.
Da ƙarfi ya ce "Allah! Naila sannu da aiki, Naila idan na gama Karatu na samu aiki sai kinfi kowa jindaɗi, kuɗin da kika ba ni yau ma riga ɗaya kawai na siya da shi, haka na wuni da yunwa. Yanzu kinsan mai za'ayi zan ɗauki kuɗinnan na ƙarasa siyan kayan sawa kinga mun gama da wannan, ɗan abin ya rage kuma na riƙe kuɗin makaranta ko ya ya kika gani, ko da yake bari na tashi na je yanzu saboda gobe lecture 7:00am zan shiga." Ya ƙarasa faɗa ya na miƙewa.

Kafin Naila ta ahaÉ—iye hawayenta tuni Sufyan ya fice, ko tambayar dalilin da ya sa ban tayi girki ba baiyi ba.

Sufyan ya zaɓi zuwa ya siyo ba tare da jiran gari ya waye ba ne saboda Sumaya karta sa ran zai kuma siyamata wa su kayan.

Ko tsinke baiyi hikimar siyawa Naila ba tunda itama kayanta duk Abaya ne ma su arahar gaske ga adon da aka yi mai na saƙi sak na ƴan karkara. Chocolate kawai ya iya siya da Naila shima kuma sai da ya haɗa da na Sumaya.

Daɗin samun komai da sauƙi yasa yake ta murmushi shi kaɗai har ya dawo Gida.

Lokacin da Sufyan ya dawo Naila ta ga bai siyomata ko tsinke ba kasa shiru ta yi ta ce;

"Ba ka kyauta ba, tayaya zaka siyo kaya iya kai kaɗai bandani? " Da farko da zafinsa ya ɗago amma kome ya tuna sai ya fasa ya fara lallashita haɗe da tambayar abinda ya ke damunta. Da salon dabaru Sufyan ya kalamacata har ya yi nasarar tserewa daƙinsa bayan ya bata abinda ya siyomata.

Naila ta so ta ba shi labarin abinda ta gani amma gudun kar ya kira ya fesawa Mahaifiyarshi ya sa taja bakinta ta yi shiru.

Daga wannan ranar Sufyan ya ƙara zage damtse wajen yin ado da kaya kala-kala, da zarar ta samu kuɗi zai siyeta da daɗin baki ya karɓe, har Mahaifinsa ya sa ya tura Yaro a kaiwa Kaka waya suka gaisa Naila.
Ranar da Naila ta gaisa da Kaka bata runtsaba, saboda tanaso ta bata labarin abinda ta gani da wanda Sufyan yakemata amma babu hali domin zama Sufyan ya yi gadinta da sunan kallon talabijin.

A haka rayuwar ta miƙawa Naila da Sufyan, da kuɗin sana'ar kitsonta ya ke komai na Makaranta har ya yi wa Budurwarsa Sumaya hidima, duk Naila bata sani ba, da kuɗinta dai ya ƙara ƙawata living room ɗin su har da ɗakin kwanansa.
A ɓangarena Suturar sawa kuwa Naila bata da na arziƙi, idan tayi ƙorafi sai ya ce mezatayi da sutura ita da ba fita na ke yi ba, kitso kawai yake zuwa, shi dama kuma ba ya son idan zataje yiwa Mutane kitso ta yi kwalliya kar wani ya ƙwacemasa ita, shi ya fi son ya ganta ta yi ado da kayan da ta taho da shi saboda hakan na tunamai da Yankinsu.

A kwana a tashi Ruwaida ta fuskanci Sufyan cutar Naila yake yi domin kuwa duk ta rame tayi duhu saboda ƙewa da damuwa. Shawarar Naila ta fara ɓoye kuɗinta Ruwaida taba ta, idan sun taru za ta rakata ta siyi suturun sawa, idan Sufyan ya tambayeta ina ta samo ta ce ita ta siyamata da kuɗinta.

Bayan kwana biyu
Sufyan ya jera kwanaki uku ya na tambayar Naila kuɗi sai ta ce babu, da ya ga dai dagaske ta ke babu kuma aljihunsa ya yi ƙasa sai titsiyeta da tambayoyi, ƙarshe tana Madafi tana girki ya shiga ɗakinta ya bincike har sai da ya samu kuɗin da take ɓoyewa. Ta na tsaye ya shigo Madafi da kuɗin a hannunshi kafin ta yi magana ya kwasheta da mari cikin zafin rai yake masifar yasan Ruwaida ce take zugata, wallahi ta ci darajar itace take naimomata customers da sai ya ci mutuncinta ya wulaƙantata.

Sufyan ya yi tunanin ganin sauyi ko wani gagarumin ɓaci rai a saman fuskar Naila, amma sai ya ga akasin haka kamar baiyimata komai ba, cikin neman magana ya ce
"gaba zakiyi da ni saboda nayi miki faɗa ko,? to wai Naila saboda wa nakeyin wannan karatunnan? Saboda ke nake da ƴaƴan da zamu haifa, Naila saboda tsoron kar mu zo mu tara ƴaƴa babu kuɗin kula da su yasa kikaga na daure har yau ban kusanceki ba, duk wannan bai sa ki tausayamin ba haba Naila sai a fara zugaki ki na ɓoyemin samunki."

Murmushin mai ciwo Naila ta yi ta kalli fuskarshi ta ce;

"matacce ai ba shi da ran yin rigima da rayayye, idan kuma kasan yau ai ba kasan gobe ba, dalilin baiwar kitson da Allah Ya bani yasa ku ka kawoni Birnin Abyad, ga shi kana mora har ka na da ƙarfin halin yin iko da shi. Ba ni da ƙarfin yi ma iyaka amma lokaci zai yi maka a yanayin da baka taɓa tsammani ba"....✍🏻
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: https://chat.whatsapp.com/I1wZrvGJP2s3QIyUuJ4ig7?mode=r_c

🔥ZINARE🔥

( ```The Gripping family saga with high Caliber)

```
SASAAL


14

Sufyan sak ya yi a tsaye har Naila ta gama magana ya kasa ce mata komai, har na ɓacewa ganinsa.
Bayan tafiyarta kafaÉ—arsa ya É—aga
A ganinsa mai zai jiyewa takaici? kuɗi ne dai dole ya karɓesu saboda da su ya dogara.

NAILA
★washe gari kamar ko yaushe bata koma barci ba, sai da ta gama Breakfast.

Ko da koma barci ta farka misalin tara na safe, ta fito Parlo a yadda ta jera abincin haka na samesa Sufyan bai ci ba. Tasan ya yi hakane saboda kuɗaɗents da ya karɓe, a karon farko hawayen takaicinsa su ka zubomata, bata tsawaita zubda hawayenta ba, bata kuma hana cikina abinci ba. Bayan ta ci na ƙoshi na fito harabar Gidan shan iska.

Yasar ta hango ya na yunƙurin fitowa, da farko ta yi niyyar guduwa saboda ba ta son haɗuwarsu, amma da na tuna taimakon da ya yi msta ranar da accident ɗin sashen Ruwaida ya faru sai ta jirkirta.

Yasar manazarcin halayyar ÆŠan adam ne, kuma likita a babban Asibitin Birnin Abyad. Gaishesa kawai ta yi ta matsar da kanta gefe.

Matsowarsa kusa da ita ya sa ta juyo tana zare ido.

Yadda ta zare ido na ne ya sa shu saki dariya ya na shafa tarin sumar kanshi da ya tattara wajen É—aya ya É—aure kamar Mace.

Ba bu zato ta ji ya ce;

"Maimakon zama haka mai zai hana Mijinki ya naima miki gurbin karatu a jami'ar su, idan ma ba shi da hali ki naimi izininsa ni zan biya miki Fisabilillah."

kalamansa sun wanke dattin da ya jima danƙare a cikin ƙwaƙwalwar Naila na tsahon lokaci, maganarsa abun dubawa ne a gareta, kuma shawara ne mai kyau amma tuna Sufyan ya sa ta ce;

"mijina ba zai yarjemin ba" ta faÉ—a da murya da ya bayyana rauninta.

Yasar ya kai wa su daƙiƙu ya na kallonta kafin ya murmusa da cewa;

"idan Mijinki ya na da sauƙin kishin da zai barki zuwa Gidajen da maza da mata su ke rayuwa, kamar Campus ɗin su Ruwaida kiyiwa Ɗalibai kitso, to babu dalilin da zai sa ya hanaki naiman ilimi. Menene amfanin neman da ba zamu gina gobenmu da shi ba?"

Kamar talabijin haka Naila ta zubawa fuskar Yasar mai tsananin haske da kyau ido, ba haskensa da kyansa ta ke kallo ba, gaskiyar da ya faÉ—a take gani a saman fuskarsa.

YASAR Duk da ya san Naila ta gamsu ɗari bisa ɗari kuma ta yarda da maganarsa amma tana kwakwanton naiman mafita sai ya ƙara ce mata;

"ga hanya mafi sauƙin warwarewa kanki komai, ki fara naiman izininsa a kan na ce zan biyaki kuɗi mai yawa ki kitsamin kaina, ki ji mai zai ce, idan ya ce a'a sai ki san dabarabar da za kiyi ki tambayesa izinin naimar miki jami'a, idan kuma ya ce eh, kin samu hanyar da zaki tafi Jami'a cikin sauƙi, ki nutsu ki warware komai dalla-dalla za ki fahimce ni da kyau".

Cikin nauyin baki Naila ta yi mai godia. Har ya ɓacewa ganinta bata daina kallon hanyar da yabi ba.

Yinin ranar a tunani ta ƙaresa domin ta kasa yarda Sufyan ba ya kishinta, shi da ya ce kishin ta ne ya ke hanashi siyamata kaya kar wa su, su ga kyanta, duk da tasan ba ya sonta sosai kamar kuɗin da na ke samu, amma ta yarda da zancensa.
Kusantowar lokacin dawowar Sufyan ya sa ta miƙe ta ƙarayin wanka, kayan dai da ta taho da su daga Yankinmu ta saka, duk sun ƙode sun jeme.

SUFYAN; Sufyan kayan ciye-ciye da ice cream kala-kala ya siya mu su shi da Sumaya, har sun dawo sunyi lecture ya tuna rashin siyawa Naila kaya zai ƙara tunzura ta, har ta ɓullo da wata dabarar tara kuɗin a inda ba zai gani ba balle ya ƙwata, musamman wajen Ruwaida, kuma siya mata kayan zai kawar da tunanin ba ya sonta ba ya son farin cikinta a ranta. Bai naimi rakiyar Sumaya ba ya tafi, kusan rabin kuɗin da ya ɗaukemata ya siyamata kaya da su ba dan ransa ya so ba.

Da ya dawo Makaranta da Kayan Ƙiri-ƙiri Sumaya ta nuna ƙishinta, ranar ko ƴar hirar da su ke yi a kan hanya ba su yi ba, bakinta a gaba take tuƙi, takaici da kishi na nuƙurƙusarta. Ko da ta sauke Sufyan kafin ya yi mata sallama ta figi mashin ɗin ta.
Jiki a sanyaye Sufyan ya shigo gida.

Da Sufyan ya shigo bai bawa Naila kayan da ya siyo ba, É—akinsa ya wuce da kayan ransa fal kokwanton ko dai gobe ya kaiwa Sumaya, saboda bai ji daÉ—in yadda su ka rabu ba.

Jikinsa ba kuzari ya tsakuri abincin da ta girka, itama Naila tata fuskar sam ba fara'a. Bayan ta tabbatar ya huta ta sako masa hirar neman izininsa zata yiwa Yasar moƙocinsu kitso tare da bayyana masa irin kuɗin da ya ce zai ba ta. Ga mamakinta Sufyan ko alamar banbanci tsakanin jinsi Namiji da na Mace bai nuna ba yace ai neman kuɗi ne babu Matsala. Zuciyarta da jinina na gudana da sauri-da sauri ta tambayesa izinin komawa Makaranta, kai tsaye ya ce mata;

"ba ni da kuɗi, ko kuɗin da kike ba ni kike yiwa baƙin ciki Naila?" Muryarta ta na rawar kukan da ya tahomata tana ƙoƙarin dannewa ta ce;

"ance ba sai ka biya ba za'a samomin Scholarship" kamar an tsikaresa haka ya miƙe ya na masifa kamar zai taune harshensa. Sai da ta bari ya gama kumfar bakinsa, sannan ta miƙe haɗe da cewa;

"zuwa Makaranta da sunan naiman ilimi sai zama aji ɗaya da Maza, amma kowa da Mazauninsa, ba bu kuma tilas ɗin mu'amalantar juna, iskanci ne. Amma zuwa Gidan da Maza su ke rayuwa da sunan sana'a haɗe da kama kansu na kitsa saboda za su bani kuɗi mai yawa shi ba Iskanci ba ne Sana'a ce ko? Idan ka rayu a matsayin miji a gareni sannan ka zaɓi zaluntata da duƙushemin rayuwa wacce riba za ka samu Sufyan?"

Ƙasa ya yi da kansa, ganin ba shi da mafita sai ya fara lallashinta haɗe da garzayawa ɗakinsa a hanzarce ya kwaso kayan da ya siyo mata yake kokwanton ba ta. Kamar zai yi kuka haka yake magiyar gwadata ya ke yi kamar yadda akasarin Maza suke yaudarar Mata da sunan gwaji.

A cewarsa idan banda gwadata ya ke yi ta ya ya zai yarda ta yiwa Yasar kitso sai ka ce ba Musulmi ba, shi kansa Yasar ɗin ai ba mutumin ƙwarai ba ne, idan ban da haka ta yaya zai ce Matar aure ta yi mai kitso. Da ire-iren waɗannan kalaman ya so yaudarata.

Ba bu daɗin bakinsa ɗaya da ya samu gurbi a cikin zuciyar Naila, amma ta ji daɗin kayan da ya siyomata. Kamar komai ya wuce haka ta nunamai, domin ya ƙara shashantar da ita sai ya fara ragewa kanshi zafi kamar yadda ya saba.

Bayan ta koma daƙina kuka da ya sanyamsta ciwon kai ta yi, ba ta da wanda zats buɗewa zuciyarta ta zazzage masa dukka damuwarta sai dai tasha kukanta ita ɗaya a ɗaki.

★washe gari da Sufyan zai fita Makaranta Cikin dabara ya ke ja mata kunnen rage mu'amalantar Ruwaida idan ba haka ba zata kaita ta baro.
Abinda bai sani ba
Kalaman Ruwaida ga Naila ma su taushi ne haka zuciyarta da niyyarta dukkan ma su kyau ne a kan Naila, idan ma cuta ce Ruwaida ta rasa wacce zata cuta sai irin Naila.

Naila Ba ta ce mai kanzil ba har ya bar Gidan.

Da ga ranar ta ƙauracewa zaman harabar Gidan saboda Yasar, idan ka ganta a waje to Ruwaida ce ta haɗata da customer, ko kitso idan aka biyota Gida a living room ta ke zama su yi.

A hankali a hankali Naila ta fara rama mai busar da Mutum tambayar duniya idan Ruwaida ta yi mata sai na ce mata"ba komai".


Sufyan ya haramtamata gaisawa da Kaka kullum sai ya ce ya kira ÆŠayyib Mahaifinsa ba ya samu.

A kwana a tashi cikin hikimar Ubangiji suka shekara É—aya da rabi a Birnin Abyad.

A ɓangaren Sufyan ya canza ya ƙara haske ya yi kyau sak mazaunin Birnin Abyad, saɓanin Naila ta da ta bushe ta rame idan ta yi dariya sai haƙora su cikamata fuska.

Ta ƙara samun customers wa su ta je Gida tayi musu wa su kuma su biyota Gida, duk tarin kuɗin da take samu Sufyan ne yake kwashewa domin akwai ranar da ta ɓoye kuɗi a wajen Ruwaida, har ya titsiyeta da tambaya.

Bata ɓoye masa su na wajen Ruwaida ba, a ranar sai da ya yi mata dukkan da ya hanata motsi. Bayan ya fita Makaranta ya kira Mahaifinsa ya yi mai bayani. A take shima ya sanar da Uban Gidansa, washe gari jami'an tsaro mata suka zo har Gidan su ka jawa Ruwaida kunne haɗe da karɓe kuɗin da na ke tarawa, bayannan su ka yi mata tsakani da ni.

Ruwaida ta na tsoron abinda zai taɓa karatunta. Ba tare da ta nemi ƙara ganin Naila ko tambaya ta sane abinda aka yi mata ko ba na sane ba, ta tattara Kayanta ta tashi bar Gidan, sai ma su kwashe kayanta kawai Naila ta gani.

Tun da ga lokacin sai Naila ta ƙara zama kamar sha-sha-sha. Ga shi Yasar tun da ya ya bata shawara na yi watsi da shi har take gudun haɗuwa da shi ya tattara lamarinta ya watsar ko haɗuwa sukayi ta gaishesa daƙyar ya ke amsawa. Yasar bai ƙara tsanar Naila ba sai da ya ji labarin abin da ya faru tsakanin Sufyan da Ruwaida. Daga wannan ranar ko gaishesa Naila ta yi baya amsawa.

Abubuwan da su ka faru da Naila sun sa ta yi losing hope, sai ta ke ganin sakarwa Sufyan komai ya yi iyakacin zaluncin da Allah Ya ƙaddara a cikin rayuwata shi kawai ya fiyemata sauƙi.

Da ga wannan dukan farkon da Sufyan ya yimata ya mayar da ita kamar jaka, akan abu ƙalilan sai ya zaneta, ɗai-ɗaikun ranaku ne baya kai hannunsa jikinta, ga dabaru da ya ɓullo da shi, haka zai sakamata videon tsaraicin wa su ya ce ta nutsu na kalla irinsa zata yimai. Da farko gardamar bazan yi ba ta yi mai, ai kuwa ya kamata ya yi mata dukan tsiya, abisa tilas ɗin rashin zaɓi ta fara bin umarnin Sufyan.

A haka su ka ƙara shafe shekara ɗaya cikin uƙuba da tsanani, ba ta gaisawa da Kaka, ba ta da abokin hira, domin wacce ta tare a ɓangaren Ruwaida sai da Yasar ya ja mata kunnen kar ta kuskura ta kula Naila idan ba haka ba zan ƙulla mata sharrin da Allah ne Kaɗai zai wanke ta.

Da kuɗin guminta Sufyan ya ke rayuwa, da kuɗin guminta ya ke tari a Bankin da Ubangidan mahaifinsa ya yi mai jagora ya buɗe, da kuma kuɗin guminta ya ke yiwa budurwasa Sumaya siyayya. Ita kuma ko cikakken Suturar sawa ba ta da shi, idan ta yi dariya tsananin munin ta sai ya bayyana saboda rashin namar fuska har wani yamushewa fatatar ta yi. Sufyan ma ya kance ba ta da abinda zai mora a jikinta duk ta rame sai ƙasusuwan da zasu jimai ciwo, da wannan yake fakewa sai dai ya tuɓe ya yi ta umartata tana yimai abinda zai gamsar da shi.

A ɓangaren Sumaya da Sufyan soyayyar su kullum ƙara armashi ya ke yi saboda basa ɓoyewa junansu komai sai na ɓangaren da ya shafi sirrin su, Sumaya ko sunan Naila bata son ji a bakin Sufyan wannan dalilin ya sa baya yi mata hirar ta.

A yammacin wata asabar Naila ta shirya zuwa Gidan ƙawayen Ruwaida da ta taɓa kaita, domin ba ta muzantata a wajen kowa ba, dukka ƙawayenta waɗanda su ke kiranta ta yi musu kitso ba su daina ba, Ruwaida ce dai kawai ta ƙauracewa haɗuwa da ita.

Ta na fitowa na haɗu da Yasar, da ta gaishesa daƙyar ya amsa yana gyara zamansa a han ɗan tudun da ya ke zaune.

Naila bata yi nisa da Gidan su ba, ta hango lafiyayyen mota mai farin gilashin da mutum zai iya ganin na ciki, fuskar Salman ta gani kamar dai yadda ta gani a farkon zuwanta Birnin Abyad. Da gudu ta tunkari mota da ya ke tafiya a hankali ta na kuka haɗe da magana da iyakacin ƙarfin muryarta;

"Salman na san kai ne ka tsaya ka cikamin alƙawarina na roƙeka, ina shan wahala ka taimakeni ba ni da kowa a Birnin Abyad ka ji ƙaina ka faɗamin ina SULAIM yake? da gaske ya ƙone ya mutu?"

kamar yadda Naila ta yi tsammani bai tsaya ba tana ji tana gani su ka haɗa ido cikin ido da mutumin da ta ke ganin sak Salman sannan yaƙarawa Motarsa gudu ya barta a wajen. Ƙasa ta zube ina kuka.

Yasar da ya ga komai kuma ya kasa jurewa nufo inda Naila ta ke ya yi, ya kamo hannunta ya kawota har harabar gidansu. Cikin taushin murya ya ce;

"Naila menene ya ke damunki, ka faÉ—amin gaskiya daga ina ki ke(ma'ana Yankinta) "

kasa magana ta yi saboda shesheƙa.

Naila ta ɗauki mintina a haka, kafin ta daki ƙirjinta saitin zuciyarta inda ke ji kamar zai fashe, sannan na fara magana sheshekar kuka na tare ta;

" ina shan wahala🥹, ina so na koma Yankina, ina ji kamar zan mutu..."✍🏻
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: https://chat.whatsapp.com/I1wZrvGJP2s3QIyUuJ4ig7?mode=r_c

🔥ZINARE🔥


SASAAL


15

Tana na gama furta ciwo da raɗaɗin da ta ke ji a cikin zuciyata, sai ta ƙasa magana saboda kukan da ya ci ƙarfina.
Kamar talabijin haka Yasar ya zubamata fararen idanuwansa.

Ta kai wa su daƙiƙu tana kuka, kafin ta cigaba da magana;

"Sufyan ya na ganamin azaba, ya na dukana, ba ya barina na mori kuɗin da na ke samu. Ruwaida ita ce take taimakamin kuma ya yi mata sharri saboda ina tara kuɗi a wajenta ta bar gidan nan. Ni marainiya ce, ba ni gata kuma ba ni da ƙarfin yin komai ka taimakamin na koma Yankina"

Kai ya sunkuyar ƙasa saboda tausayi ya jima a haka kafin ya ɗago ya ce;
"Ina ne Yankin ku Naila? Kuma maiyasa Æ´an uwanki tunda sun san ba su da halin da za su iya taimaka miki a ko wani lokaci su ka ba wa Sufyan ya taho da ke har Birnin Abyad? Wannan gangancine mai girman gaske"

Ba bu ƙarya a maganarsa amma ƙaddara ta riga fata. Cikin sanyin yanayin da ya ɗan fara shigar Naila ta ba shi labarin Yankin da ta fito. Amma ba ta ba shi labarin dalilin da yasa ta ke bibiyar mutumin da ta ke zargin Salman ba ne.

Yasar ya gamsu da bayaninta, amma sai ya ƙara jefomata tambayar "maiyasa ki ke kiran Mutumin da ya wuce ɗazun har ki ke cewa ya taimaka miki? Wanene kuma Sulaim ɗin da kike tambayarsa ɗan uwanki ne? Ki faɗamin gaskiya idan da hali zan iya taimakawa."
Ƙur Naila ta yiwa Yasar da ido, tarihin abinda ya faru na kusantowa ganina kamar a lokacin su ke faruwa.

Waje ta samu ta zauna Yasar ya biyo bayanta.
A baya labarin Yankinta da mahaifanta sun mutu kawai ta faɗamai da rashin adalcin danginta na ɓangaren Uwa da na ɓangaren Uba, amma tunda ya nuna zai taimaketa ta koma Yankinta to dole ya san asalin inane Yankin Tudu da kuma surƙullen da ya ke cikinsa.

Kamar Yasar ya na ganin komai haka ta ke ba shi labari tun da ga lokacin da ta yi wayo har zuwa mutuwar Salman da abubuwan da suka faru bayan nan har aurenta da Sufyan da kuma manufar Mahaifansa a kanta.

Mamaki ne zalla a saman fuskar Yasar, banda yana da ilimin nazatar Ɗan adam da kai tsaye zai ƙaryata Naila, wani irin Yanki ne wannan? Wa su irin mutanene ma su ƙaracin basira ne a Yankin?

Kusantowar lokacin dawowar Sufyan ya sa Yasar gajarta tunaninsa. Cikin alhini ya ce;

"Tabbas! Naila akwai DHAHAB CITY a Babban Birnin Abyad, Unguwar da wani mashahurin mai arziƙi ya gina, Shekaru goma sha biyar baya. Ahalina ne ma su tsauri da tsantseni domin dai-dai ma su gadin alƙaryar Dhahab ababen tsoro ne, sai dai shi ba sunanshi Abduh ba sunansa Muhammad Dhahab kuma a zahirin da mu mutanen gari mu ka sani Ɗan asalin ƙasar Abyad ne, amma wa su na cewa ba shi da asali babu wanda yasan gaskiya. Duk wani mai hidima da ma'aikatan Company's ɗin su, su na da record ɗin komai na sa, rayuwar su ba bu sakewa sam duniyar su tamkar daban ya ke da namu, ba bu wanda yasan sirrinsu sai makusantan su, Tun shekarun baya na naimi aikin tsaron sashen Mahaifiyar Muhammad Dhahab a yanar Gizo kamar yadda na ga an wallafa saboda ma su irin ilimina ake nema, amma saboda sun kasa samun cikakken bayani asalin ni ɗan inane da kuma inda Mahaifana su ke zaune, sai su ka fasa ɗaukata duk da cancanta ta, na yi kuka a waccen lokacin saboda albashin aikin ninkin wanda na ke samu a yanzu ne sau huɗu. Gane rashin samun cikakken asalina ya sa suka hanani aikin sai na tattaro Mahaifana na tara kuɗi na siya mu su Gida a Birnin Abyad, saɓanin daa da su ke zaune a bayan gari. Sai dai duk da na yi haka samun aikin sai ya gagareni haka na gaji na haƙura.

Bayyanar Simbi ahalin Gidan Muhammad Dhahab a Asibitin mu sai ya dawomin da burina na baya, wannan dalilin yasa na fara bibiyarta ta taimakamin saboda zan ƙara samun sakewa wajen taimakawa mahaifana har na samu na yi aure, amma sai Simbi ta wulaƙantani dalilin da ya sa nayi zuciya kenan na haƙura da aikin.

Amma Naila dole yanzu zan ƙara zage damtse har Simbi ta saurareni, saboda shigata Dhahab zai bayyanarmin alaƙar tarihin Yankin Tudu da rayuwar su, fatana ki tayani da addu'a."

Baki, hanci, da ido dukka Naila ta saki tana kallon Yasar, cikin kokwanto ta ce "menene sunan wanda aka ce shine Mijin Simbi mutumin da ya ke yimin kama da Salman?"
ÆŠan dariya Yasar ya yi kafin ya ce;
"A binciken da na yi Simbi sam ba ta da Miji, kuma wanda ki ke gani sunansa Uzair, ba shi cikakken lafiya sosai saboda ya taɓa ciwon da ya yi shekara shida a kwance kafin ya warke, bansan wani ciwo ba ne, amma na samu bayanin ne da ga Yayan Ruwaida amintaccen ma'aikaci a kamfanin su, shima a sirrince ya faɗamin don haka ki kiyaye" kafin ya ƙarasa tuni Naila ta ɗora hannuwanta dukka biyu a kan bakinta alamun ba bu wanda zai ji.

Dariya Yasar ya yi kafin ya ɗora da nasihar ta kwantar da hankalinta da ƙarfin mulkin Allah sai sunyi nasarar shiga Dhahab ko a masu goge-goge ne.

Naila sai ta ji dukka ƙuncinta ya yaye sai ta ke ganin kamar komai ya zo ƙarshe, da wannan farin cikin sukayi sallama ta koma ciki ta yi wanka ta ci abinci. Gidan kitson da bata je ba kenan ta kwanta barci.


Daga wannan ranar Naila bata ƙara ji daga Yasar ba gaba ɗaya ma sai ta daina ganinsa. Da farko ta ɗan damu sai da ya ba da gajeran saƙonsa na suturar sawa ma su kyau da kayan ciye-ciye ya risketa ta kwantar da hankalinta.

Babban akwatinta ta sauko da shi, na ɗura kayan a cikin gudun kar Sufyan ya gani saboda ya kusa dawowa. Ta na kici-kicin mayar da akwatin hotonta da na Sulaim da ta sa aka wanke mata ƙaraminsa ya faɗo, da sauri ta ɗauke saboda har ga Allah batasan ya na cikin aljihun bayan Akwatinta da ta taho da shi ba, kuma tasha zuba kuɗi a ciki na kwashe amma hoton bai taɓa bayyana kansa ba. Da wani irin farin ciki ta ke kallon hoton. Batasan ta ɗauki lokaci a haka ba sai da taji Muryar Sufyan a bayanta, dama kuma da ɗayan key ɗin Parlon ya dawo tafiya Makaranta.

Firgitarwar da bayyanar Sufyan a lokacin da bata yi tsammani ba ne, yasa ta saki ƙara haɗe sakin ƙaramin hoton ƙasa, kallon hoton Sufyan ya fara yi sannan ya yunƙuro dasauri zai ɗauka ransa na suya, kafin ya cimma hoton tuni ta yi hanzarin ɗaukewa tana zare ido.

Fes Sufyan ya ga waɗanda suke jikin hoton, ciwon da ya jima da shafesa a tarihin rayuwarsa ya yunƙuromai. Cikin ɗacin zuciya ya fara dukanta ya na ƙwallo da ita, ya na cewa;
"ba ni hoton nan wato amanata ki ke ci ko? Shi yasa kullum bakya ganin kyawuna, kina maƙale da wannan hoton shaiɗanin da ya addabi mutane duk da ba ya raye, wallahi idan baki bani ba sai na kusa kashe ki" maganganun sa ba su ƙarawa Naila komai ba sai ƙaimin ƙara dunƙulewa da ta yi da hoton waje ɗaya, idan ya kasheta ma ai ta huta da uƙubarsa.
Har ya gama dukanta bata warware daga ɗunƙulewar da ta yi ba, cikin azabar kishi ya sa mukulli ya kullota yana huci...
Kuma ya yi rantsuwar ba zai buɗeta ba har sai ta bubbuga da kanta ta yarda bashi hoton ya ƙona sannan ta ba shi haƙuri.

Haka Naila ta kwana ta wuni kulle, inda Allah Ya taimaketa akwai kayan ciye-ciyen da Yasar ya aikomata da su, idan ta É—anci sai ta kora da ruwan banÉ—aki ta É—oro alwala ta kaiwa Ubangiji kukanta.

A haka ta shafe kwana uku tana manejin abinda Yasar ya bata tana korawa da ruwa kuma cikin hukuncin Ubangiji sai ta ji na ƙoshi.

A ranta take faÉ—in;
Banda shirmen Sufyan idan har shi da ya ke a iya haka yana ganin yafi ƙarfina to ina ga SULAIM da ya fishi komai ace ya na raye mai zai yi da ita? Sulaim tamkar Aboki ya ke a gareta har ya bar duniya, ba bu soyayya balle alƙawarin aure a tsakaninsu. Dalilin da yasa soyayyarsa ta samun matsuguni a cikin zuciyarta shine barinsa duniya, ta hanyar da dole a tausayamai, a kuma kasa mantawa da shi. Amma ko a raye ko a Mace bazata taɓa sawa ranta lallai Sulaim sai ya so ta ko ya aureta ba, matsawar ba ƙasƙancin da Sufyan yake nunamata dama take so ta fuskanta ba.

SUFYAN; A kwana na biyu da kulle Naila a ɗaki kafatanin kuɗin da ya ɗan rage a Bankinsa saboda ya turawa Gida kuɗi a rabawa Danginsa har da Dangin Naila da Kakarta da sukai ta samai albarka tare da farin cikin Naila tana cikin daula, su ka ƙare, ga shi ya saba siyawa Sumaya kaza, da su ice cream da sauransu har Gida ya ke siyamata ta kaiwa Iyayenta.

Tun washe garin da ya kulle Naila yake sa ran yunwa zai ci ƙaniyarta ta buga ƙofar ta ba shi haƙuri haɗe da ba shi hoton, amma ya ji shiru.

Kwana uku da kulleta daƙyar ya kalato canjin aljihunsa ya tafi Makaranta. Ranar ba su ci abincin arziƙi ba don haka ya keɓe ya kira wayar da ya tura kuɗi aka siyawa Mahaifiyarsa .

Hindu masifa takeyi bayan gama saurarar Sufyan kamar zata cijeshi ta waya..

"yanzu kai saboda ba ka san ciwon kanka ba shine zaka kulleta ka janyowa kanka asarar kuɗi ma su yawa, a kwana ukun nan banda kulletan da kayi da nawa zata samo maka? Amma wallahi Sufyan sam ba bu basira a cikin ƙwaƙwalwarka, har yanzu ba zaka daina kishi da Sulaim da yake matacce ka gina rayuwarka ba, Yankin Tudu kowa ya na samaka albarka, kai kana can kana shirme? To idan bata so Sulaim ba a matsayinsa na mutumin da su ke tafiya Makaranta tare su dawo tare su yi raha tare kuma ya ƙone lokaci ɗaya ba wa kake so ta so eh? dabba mara tunani!"

Saukar kalamanta sai da ya sauya kalar fararen idanuwansa, ya na jin kamar ana barbaɗa masa yaji, zagin da Ɗayyib Mahaifinsa ya ɗoramai da shi bayan ya karɓi watan ne yaƙarasa birkitasa, cikin rawar murya ya ke ba su haƙuri amma still Ɗayyib faɗi ya ke

" to yanzu haka Kasuwar Tukwanen Zinare ya mutu miɗis, sabuwar yunwa ta kunnowa Yankin mu kai, saboda an samu hamshaƙin mai arziƙin da ya saci fasaharmu ya mayar da su Tukwane na alfarma a kaf faɗin duniya ba bu inda ba'a siya, mu kuma an watsar da namu saboda ya zama tsohon yayi. Shine kai mun samu ka tsira zaka dawo damu baya, Allah Ya wadaran wannan son kyau na ka Sufyan! kai kullum ba ka da zance sai zancen Mutumin da tuni ya ruɓe a ƙarƙashin ƙasa, idan ka dama ka gyara to, idan kuma baka dama ba kai sani. Kasan da abinda zaka biya kuɗin hayar ku idan ya ƙare"

Sufyan kanshi ne ya ɗauki zafi a take ya fasa kuka yana ba su haƙuri. Shi gaba ɗaya ya manta da kusantowar biyan kuɗin hayar su.

Tahowar Sumaya inda ya ke ne yasa ya yi mu su sallama haɗe da yi mu su alƙawarin komai ya wuce, In Shaa Allahu zai gyara.


NAILA
Kayan ciye-ciyen da Yasar ya aikomata da shi ba laifin ya na da yawa, amma ba irin sosai ɗinnan ba, rashin sanin ranar da Sufyan zai buɗeta yasa take cancanensa kar ya ƙare ta rasa abin ci, saboda ko zai mutu bazata ba shi Hotonta da Sulaim ya ƙona ba.

Da yammaci ta na zaune a inda ta yi sallar la'asar ta ji ya buɗe kofar, fuskarsa ba yabo ba fallasa. Bai ce mata komai ba, ya bar ƙofar a buɗe ya juya ya fice.

★washe gari saboda rashin kuɗi ko Makaranta bai je ba. Ya na ɗaki ma su zuwa tambayar kitso su ka zo har mutum uku, ɗam jim Naila ta yi kamar ta ce mu su ba ta da lafiya, amma yadda su ka nuna su na son kitson ya sa ta amince. Sufyan dake laɓe yana kallonsu ajiyar zuciya ya sauke bayan ta amince ya koma ya kwanta yana murmushi.

Bayan ta gama su na fita ya yi zumbur ya fito ya ƙwace kuɗin fuskarsa ƙunshe da dariya.

YASAR; duk wata hanya da zai bi ya samu ganin Simbi abin ya ci tura, abinda ma ya lura da shi kamar ba iya son haÉ—uwa da shi ne ba ta yi ba, gaba É—aya gudun mutane ta ke yi. Ranar da ya ji labarin saura kwana É—aya ta gama abinda ya kawota ta koma Dhahab a bakin ofishinta ya wuni.

Ta na fitowa ma su gadin lafiyarta su ka rufa mata baya, kai tsaye tasa a hana Yasar bin bayanta. Sai dai kafin su kaiga riƙeshi ya taka da gudu zuwa inda motarta ya ke dai-dai inda ta ke tsaye yadda za ta jiyosa cikin yanayin maganar da matsawar tasan Naila zata fahimcesa a hankali da kuma sauri ya ce;

"Yankin Tudu, Daular Sarki Hammam Naila ƴar Gidan Mahmoud madinki, Aminin Abduh Dhahab....✍🏻
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: https://chat.whatsapp.com/I1wZrvGJP2s3QIyUuJ4ig7?mode=r_c
🔥ZINARE🔥


SASAAL


16

"Yankin Tudu Daular Sarki Hammam, Naila ƴar gidan Mahmoud madinki, Aminin Abduh Dhahab." Yasar ya ƙarasa faɗa zuciyarsa na bugawa da sauri.

Dukan mai laifi kai tsaye ba tare da gudanar da ƙwaƙwaran bincike ba laifi ne mai girman gaske a ƙasar Abyad. Wannan dalilin yasa ko da jami'ai masu tsaron lafiyar Simbi suka cimma Yasar ba su taɓasa ba sun dai yi mai katanga tsakaninsa da ita.
SIMBI; Designer jakar hannunta mai tsananin nauyin kuɗin da ya dace da arziƙinsu ta ƙanƙame da fararen hannunta ma su sanyi kyau ga mai Kallonsu, kafin ta juyo da kyakkyawar fuskarta. Idanuwanta da suke farare ƙal ta zubawa fuskar Yasar, batason dogon magana da shi, saboda doguwar magana a tsakanin su tamkar karya alƙwarin Alhalinta ne, don haka ta ce;
"A ina kasan dukka wannan?."

Jira take yi ya saki layi ta sa akamashi saboda gudun shigarta matsala amma da yake Yasar wayayyene akan aikinsa da kuma fahimtar inda ta dosa kai tsaye ya ce;

"Layinmu gidan na uku hannun hangu makitsiya mai ƙaracin shekaru."

Jami'an tsaronta shirme suka É—auki kalaman Yasar saboda ba su fuskanci ina kalamansa su ka dosa ba tunda ba su ji abinda ya faÉ—a lokacin da ya risketa ba. Umarnin barin wajen suka ba shi, bayan Simba ta shiga Mota.
Yasar bai musa ba ya juya ya bar wajen, maimakon ya koma Gidansa sai ya wuce na Iyayensa saboda yasan dole abi bayansa, domin ko shakka ba ya yi labarin tare Simbi da ya yi da tsayawarta ya isa Babban Birnin Abyad.

SIMBI; bata manta fuskar Yasar ba, saboda tun ranar da ta gansa ta ji ya birgeta a ƙofar Gidan da ya faɗa, kuma a wannan ƙofar Gidan ya naimi taimakon aiki da gareta gaba da gaba na ƙarshe lokacin ta fito workout, gudun matsala da sanin abun da take saƙawa zuciyarta akansa ba zai taɓa tabbataba yasa tasa a wulaƙantashi saboda ya yi zuciya kar ya ƙara bibiyarta.

Bata manta Naila ba, ba kuma zata mantata ba har abada, saboda ƙawarta ce kuma maƙiyiyar Ƴar uwarta Barirah.

WAIWAYEN SHEKARUN BAYA
Lokacin wasannin ƙarshe mako a Daular Sarki Hammam akwai wata matashiya mai kusan Shekarun Sulaim da ta kwashewa Naila ƙafafu saboda ta matso kusa da inda su ke wasa, har Naila ta kawo ƙararta wajen Sulaim. Ƙanwar Malik ce Uba ɗaya Sunanta Barirah.

Mahaifinsu Malik, ya auri Mata biyu matarsa ta farko ita ce Mahaifiyarsu Malik, tun da suka haifi Malik ba su ƙara samun wani ba har Malik ya kai shekaru biyar, son ƴaƴa ya sa shi ƙara aure, ya auri Mahaifiyar Barirah. Bayan wani lokaci ta haifin Barirah sa'ar Sulaim daganan itama ba ta ƙara ba, sai Mahifiyar Malik da ta ƙara haihuwar Simbi, baƙin kishi da rashin son zaman lafiyar Mahaifiyar Barirah ya sa Mahaifin Malik sauwwaƙemata ya kuma karɓi ƴarsa Barirah.

Barirah muguwar gaske ce musamman idan taga ta fika ƙarfi, ba ta baro komai na halin Mahaifiyarta ba. Da farko bata tsani Naila ba tana dai cin zalinta matsawar suka haɗu, amma daga lokacin da Sulaim da take son ya kulata ya riƙe Naila a matsayin ƙawa ta tsaneta ko aikota akayi Gidansu sai ta ranƙwasheta.

Wannan tsanar bai sauya zani ba duk tsayin shekarun da su Barirah suka kwashe a cikin daula.

DAWOWAR LABARI

A cikin Mota Simbi take hira da zuciyarta
Tabbas! bata manta fuskar Naila ba, amma mai ya kawo Naila Birnin Abyad? Allah Ya sa ba wani Yaƙinne yake shirin tunkaro su ba.


Bayan kwana ɗaya kafin Komawar Simbi Babban Birnin Abyad, ta yi yunƙurin bincike don tabbatar da ainihin abinda yasa Yasar ya iya yin kasadar tararta kai tsaye saboda matsalar Naila kawai da kuma abinda ya kawo Nailan Birnin Abyad, kafin komai ya lalace. Ta hanyar kiran Bushra da take sa'arta, wacce suka zama tamkar zuri'a ɗaya a Dhahab, kuma take kyautata zaton zata iya yimata bincike akan Naila, saboda ba ta so take wajen Naila da kanta ta ganeta. babu ja Bushra ta amince dama kuma tana Birnin Abyad itama bata koma ba.

NAILA ; kamar kullum da sassafe ta yi ayyukanta bata wahalar da kanta wajen girkawa Sufyan Breakfast ba saboda ba ci zaiyi ba, idan ta yi a wajen yake barmata kayanta.

Wanka ta yi ta ɗauko Abayar da ta zamemata tamkar ta gado ta saka, saboda tana jin tsoron saka wanda Yasar ya aikomata da su gudun duka da ga Sufyan, domin wanda Sufyan ɗin ya siyomata masu sauƙin kuɗine marasa quality duk sun zaizaye wa su guraren ma duk sun yage.

Bayan ta gama saka kaya turare ta fesa saboda customers kamar yadda Rufaida ta É—orata a kai tuntuni saboda a wasu lokutan jikin mutum ya kan É—anyi tsami wanda hakan ya ke takurawa ma su zuwa kitso musamman idan suka É—ora kansu a tsakanin ciyoyi.

Sana'ar da ya zamemata jiki ko da yaushe ta zauna yi( tunani) wa ni lokacin ta saki kuka wa ni lokacin kuma ta yi dariya. Ta na cikin tunani ta ji ana ƙwanƙwasa ƙofa. Da hanzari ta miƙe ta nufi ƙofar, ta buɗe.

Bata taɓa ganin fuskarta ba, don haka tayi mata tarba na musamman tana washe haƙoran da suke ƙara bayyana ramata. Ƴar gayu ce kuma da alama daga Gidan arziƙi ta fito.

A lokutan baya Naila ba ta da yawan surutu ba ta da yawan dariya irinna rashin kamun kai, amma tunani da ƙunci rayuwa suka sa ta zama mai tsananin surutun da ita kanta batasan tanayi ba, ga dariya da take yawan yi na rashin dalili wanda ya zarta a kirashi fara'a.

Ba mai yawa wacce yazo kitson ta ce ta na so ba, don haka ta yi mata irin yadda take buƙata.

Da ta tashi tafiya kuɗi mai yawan da daa abayane ta bawa Naila su ihun murna zatasa saboda tana da yaƙinin zata tara ta gina Gobena da su, amma yanzu Sufyan ya na dawowa zai ƙwace.

Rashin fara'ar Naila da yadda ta yi ƙasa da kaine yasa wacce ta zo kitson ta magantu;

"Baiwar Allah ko kuɗin ne ba su yi miki ba, na ga kamar ranki a ɓace" ta ƙasara faɗa tana karantar yanayin Naila.

A hankali Naila ta ɗago idanuwanta da ƙwalla yasa ta ke ganinta dishi-dishi ta ce;

"Na gode! na gode!! Allah Ya biyaki, amma dan Allah daga ina kike na baki kuɗin ki taramin?" Naila ta ƙarasa faɗa kamar wacce batasan me take yi ba.


Idanu ta zaro ta ce; "ta yaya ba ki Sanni ba zaki bani ijjiyar kuɗi bakya tsoron na gudu da su? saboda me ke bazaki ɓoye a ɗakinki ba ko ɓarayi su na damunku na sanar da jami'ai?"

Kai Naila ta girgiza hawayen da bata iya yiwa idanuwanta shamaki da su ya tahomata.


Idanuwa wacce ta zo kitso ta ƙara zarowa wannan karan da mamakin bayyane a saman fuskarta, cikin tashin hankali ta ce;

"Menene matsalar Baiwar Allah?"
Cikin kuka Naila ta ce;
"Inaso na koma Yankina amma bana iya tara kuɗi Mijina kwashewa ya ke yi domin gina gobensa, ya na dukana kullum, ki taimakamin kinji Don Allah nasan kinfi ƙarfin su bazaki Gudu da shi ba"

kamo Naila ta yi zuwa jikinta tana shafa bayana ta ce;

" Ya ya sunanki kuma ina ne Yankin ku? Ko zan iya taimakawa"
Da sauri Naila ta ce ; " sunana Naila, yankin mu shine Yankin Tudu"

Naila tana jin lokacin da zuciyar wacce ta zo kitso wajenta ya ya buga da sauri, saboda kanta dake jingine har lokacin a saman KafaÉ—arta.

Da sanyi murya wacce ta zo kitso wajenta ta ce;
" Maiyasa ba zaki bawa Mijinki kuÉ—inki ya gina gobensa ba, gina gobensa ai tamkar gina na ki ne"
Kuka Naila tasa tana roƙonta ganin kamar ba ta fuskanceta ba.

Gwauron numfashi ta sauke, tana kallon Naila ta ce;
"Zan karɓa amma sai kin sanar da ni dalilin dayasa baƙyason mijinki ya mori kuɗinki alhali kuna tare bai sake ki ba"

Kamar wacce take jira haka Naila ta soma sako mata zance da wanda ta tambaya da wanda bata tambaya ba.
Da Naila ta gama labari
Ba ta ce mata komai sai bayanta da ta ɗan bubbuga tayi mata sallama ba tare da karɓi kuɗinba.

Ba kowa Ba ce tazo wajen Naila kitso ba fa ce Bushra wacce Simbi ta Turo, kuma ta naÉ—i dukka hirarsu da Naila.

SIMBI; Recording É—in da Bushra tasa mata, da yake Bushra gwanar tausayi ce ta kuma sauraro tana kuka.

Daga wannan ranar kullum sai Simbi ta tura Bushra Gidan Naila da sunan tayata hira a haka suka samu dukka bayanan da suke so, amma har lokacin Simbi ba ta tuna fuskar Sufyan ba tunda sun bar Yankin Tudu ya na yaro.

Har lokacin komawar Simbi Dhahab ya yi, ba su samu damar bincikar Sufyan ba, don haka ta bar ragowar aikin a hannun Bushra ta tattauna da Yasar a sirrince domin ya taimaka musu wajen bibiyar Sufyan.


NAILA
Dalili yawan tambayoyin Bushra da yadda ta saki jiki da ita duk da kasancewarta ƴar masu hali yasa Naila ta fara zargin ko Sufyan ne ya turota, da ta fara zargin haka sai ta daina bata kuɗinta ya ɓoyemata ta nuna mata ta sauko ta fison Mijinta ya gina gobensa domin su tashi tare su tsira tare.

Babu kalar tambayar da Bushra batayiwa Naila ba akan wasu sirrika na Sufyan da ta gano amma Naila taƙi faɗa saboda tsoro.

YASAR; kamar yadda ya yi zargi bayan barin wajen Simbi za'a bibiyi bayansa haka kuwa a kayi, A sirrince É—aya daga cikin masu tsaron tafiyar Simbi ya bi bayansa ya bincika babu makitsiya a gidan, daga haka ya É—ora mizanin maganganunsa akan shirme kamar yadda sukayi zargi tun farko.

Da sunan Ganin likita Bushra ta samu keɓewa da Yasar daya koma gaban Mahaifansa da zama saboda tsaro.

Alƙawarin naimarmasa aiki ta yi matsawar ya gayamata Ɗan gidan wanene Sufyan a Yankin Tudu.

Ko batayi alƙawarin cikamai burinsa na samun aiki a Dhahab ba ya yi alƙawarin taimakon Naila ta koma Yankin su ta kowacce fuska.

Bai ɓoyewa Bushra komai ba, ya kuma roƙeta ta riƙe amana, kuma a shirye yake domin ba da gudunmawa idan hakan ta taso.

BUSHRA
A wannan rana kwanan tunani Bushra ta yi. Matsawar Simbi tasan Sufyan jinin masarautar Yankin Tudu ne, to ba shakka ba za ta taimaki Naila ba, dama kuma can ba wai tana son taimakon Naila ta wata fuskar bane daban sai na mayar da ita Yankinsu. Amma ga Bushra ba irin wannan taimakon takeson yi wa Naila ba, wanda zatayi farin ciki na har abada takeson yi mata.

Ko da sukayi waya da Simbi kai tsaye ta sanar mata bata gama bincike ba.

A cikin kwana biyu Bushra ta binciko Sufyan ciki da wajensa har da soyayyarsa da Sumaya da abinda yakeyi da kuÉ—in Naila saboda ta samu tabbacin baya sana'ar komai.

Ta na son Naila taje Dhahab amma ta yaya?
Ta na kuma son Sufyan ya ɗanɗani azaba ƙiri-ƙiri irin ɗanɗanar da zai gusar da nutsuwar zuciyarsa yana ji yana gani, amma dole sai ya riski Dhahab to amma ta yaya riskarsa Dhahab zai yiwu?

Tsakiyar Dare ta naimi layin Mahaifanta, sunyi magana ya fi na hour huɗu, kafin ta suyi sallama, ba tare da jinkiri ba, ta dannawa Yasar kira. Suka tattauna yadda zasu ɓullowa Sufyan.

★washe gari Bushra da ke lulluɓe cikin shigar larabawa ita da Yasar suka kaiwa Sufyan ziyara Makaranta. Sufyan tsaf ya gane Yasar, wannan dalilin yasa ya tsamke fuskarsa ya na bawa Sumaya umarnin ta jirasa yana zuwa.

Da suka keɓe bayan sun Gaisa sama-sama
Suka ce masa takardunsa daga kan na primary har na secondary suke so da kuma shaidar takardun jami'ar da ya ke zuwa zasu samar masa aiki a Dhabah amma sai takardun Makarantarsa sun kasance na Birnin Abyad, za kuma a samar mishi sabon jami'a a can idan ya kama aiki.

Kwaɗayin da burin duniya su suka taru suka lulluɓewa Sufyan ido ya kasa tantace cuta da so da kuma tantance ina ne Dhabah maiyasa suka zaɓi naima mai aiki. Jikinsa na rawa ya tashi gefe ya kira Mahaifinsa.

ÆŠayyib ihun murna yasa ba tare da tsayawa saurarar sunan Ma'aikatarba ya kira amininsa.

Ɗayyib ya na kiran Amininsa ya sanar da shi buƙatarsu
Kai tsaye amininsa ya sanar da shi bashi da hanyar da zai samarwa Sufyan takardun bogin primary da sakandaren ƙasar Abyad.

Ko da Ɗayyib ya kira ya sanar da Sufyan a take jikinsa da ke rawar murna ya yi sanyi laƙwas.

Jiki a sanyaye ya dawo wajensu Yasar ya yi musu bayani. Bushra da ke tantance son banza irin na Sufyan kai tsaye ta ce zata samar mai amma sai ya yi mata alƙawarin barin matarsa ta naimi jami'a ya kuma daina karɓe mata kuɗin sana'arta.

Son banza bai sa Sufyan ya tambayar kanshi ina Bushra ta samu labari ba, ya ce ya amince amma a iya bakinsa ya tsaya, domin har cikin ransa ya yi alƙawarin jami'a sai dai Naila ta ga anayi....

A cikin kwana biyu Bushra da ƙarfin ikon Mahaifinta a ƙasar Abyad suka samarwa Sufyan takardun bogi.

Tare da Takardun Yasar Bushra ta shigar ta hanyar yanar Gizo tare da addu'ar dacewa,.domin batason Malik yasan aikinta kai tsaye duk da akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu.

Duk wannan wainar da ake toyawa Naila batasan ana yiba, sai shige da ficen Sufyan da take gani a ruÉ—e.

BUSHRA
★washe gari abinda ya shigar da Bushara Toilet ya fi sau uku shine Ɗaukar Sufyan aiki tare da wani irin albashin da ya tsoratata. Ba ita kaɗaiba dai-dai da Mahaifinta ya shiga zullumi da ta sanar mai, ya kuma gano akwai babban Yaƙi domin ko rantsuwa ya yi bazai yi kaffara Malik da ya ɗaukesa aiki ya gano wanene SUFYAN.....✍🏻
[7/23, 9:38 PM] +234 702 541 3080: 🔥ZINARE🔥


SASAAL


17

Har yamma ta yi liƙis nutsuwar Bushra bai dawo jikinta gaba ɗaya ba. Idan wayarta ta yi vibrating har firgita takeyi.
Dole zancen Mahaifinta ya zama gaskiya banda haka Sufyan bai cancanci ya samu aiki lokaci É—aya haka ba, dama dai Yasar ne da takaddunsa suke nunawa gogewarsa.
Har dare Mahaifinta bai kirata ya samu kira daga saman Dhahab ba wanna dalilin yasa ta É—an samu nutsuwa a ranta, amma duk da haka sai da ta kira Simbi.
Yanayin muryar Simbi da shawarar da take bata na ta dawo ta ƙyale Naila domin ita ta fasa taimakonta ne yasa Bushra ta ɗan jo sanyi a ranta, saboda da an samu matsala zata ji a bakin Simbi, sai a lokacin ta samu sukunin kiran Yasar tayimai bayani.

Shawarar su haÉ—u washe gari a Gidansu Naila suka yanke.

NAILA; tunda ta ɗauke yardata a kan Bushra ta miƙawa Allah komai tare da alƙawarin ba zata ƙara naiman taimako a wajen kowa ba.

A tsakanin kwana da wuni Sufyan sam bai tambayeta kuÉ—i ba, kuma a kan idonsa ta kitsa kan mutum biyu.

Bata yi mamaki ba, domin ga dukkan alamu akwai gagarumin al'amarin da ya tisosa a gaba.

A daren cikon kwana na huÉ—un da ya yi da daina tambayarta kuÉ—i, kuma itama bata ba shi ba, ya kirata É—akinsa.

Cikin muzurai yake sanar da ita samun aikinsa dalilin tonon Asirin da ta yi masa a wajen Bushra É—aya gano daga baya, to ga kuÉ—inta ya barmata amma ta jira hukuncin da zai biyo baya.

Har ya gama kumfar bakinsa da maganganun izgilancinsa Naila batace masa komai ba.

Daga ƙarshe ya jamata kunnen karta kuskura Bushra da Yasar su naima mata jami'a ta yarda ta je. Idan kuma ta saɓawa umarninsa wallahi sai ya hukuntata da hukuncin da har ta mutu bazan manta da shi ba.
Babu abinda ya motsa daga jikinta balle ya gane na fahimcesa ko bata fahimcesa ba, takaicin hakan yasa ya haureta da ƙafa ya na faɗin;
"Fice min daga ɗaki, sha-sha-sha kawai ai gashi garin ki tonamin asiri kin janyomin daukaka, kuma wallah na rantse bazaki ci ko sisi daga arziƙina ba"
Sam surutansa ba su dameta ba, tunda zai barta ta dinga tara kuÉ—inta. Kuma ko su Bushra sun tambayeta tanason zuwa jami'a da babban murya zata amsa "eh". Kanzil ba tace ba har ya gama masifarsa ta bar ÆŠakin.

SUFYAN; ranshi fari fes yake ji, sunan ma'aikatar da za'a samarmai aiki na kai kawo a cikin zuciyarsa, anya babu wani sirri a cikin wanda ya kara DHAHAB(ZINARE) a cikin sunansa, Abdulyasar Dhahab Ubaidullahi Dhahab, Abduh Dhahab, duk ba su bar duniya ba sai da suka zama ababen koyi, ga shi ya kuma samun wani mai arziƙin a Babban Birnin Abyad shima Dhahab. Tabbas! A kwai wani ɓoyayyen abu a cikin wannan sunan tunda shi kanshi asalin DHAHAB(zinare) ba abun yadawa bane abune da ake kokawa a kansa. Kakanninsa da suka ƙi kwantar da kai subi Abdulyasar Dhahab tun farko ai gashi za su mutu babu wanda ya sansu sai ƙananun muƙamin Sarautar da suke taƙama da ita. Anya bazai koma Sufyan Dhahab ba kuwa? Dariya ya bawa kanshi yana shafa sumar kanshi, tare da ayyanawa ransa irin girman kuɗin da zai dinga kashewa sumarsa, duk da dai bai san iyakacin albashin da za'a biyasa ba. Yanzu matsalarsa ita ce Naila, hanyar da zai rabu da ita ya korata Yankin Tudu kawai yake nema ba tare da su Bushra da Yasar sun ga baƙinsa ko butulcewarsa ba, tunda ko yana so ko baya so Naila ce sanadi. Da Sumaya yake son su tare a Babban Birnin Abyad idan komai ya yi masa yadda yake so.

Tuna irin abubuwan da zai yi idan ya fara aiki yasa ya tashi yana taka rawa.

NAILA; bayan ta koma ɗaki kuɗinta ta ƙara adanawa tana lissafa irin kayan da zata siyawa Kaaka duk ranar da Allah ya ƙaddara tafiyarta, godiya tayiwa Allah sannan na godewa Bushra tare da alƙawarin naiman yafiyarta duk ranar da Allah Ya haɗata da ita abisa munana mata zato da tayi.

Ranta babu damuwar komai sai godiyar sauyin da ta fara samu nayi alwalar kwanciya barci, cikin abinda bai gaza minti biyu ba, bayan tayi addu'o'i barci mai nauyi ya É—auketa.

★washe gari iyakacin abincin cikinta ta girka.

Sufyan fita ya yi ya jubgowa kanshi siyayyar lafiyayyen Breakfast daga kuÉ—inta da yake tarawa a Banki.

Daga dawo
Ko kallonsa batayi ba ta tattara na bar living room ɗin. Hakan da tayi ba ƙaramin haushi ya bashi ba, don haka ya hau zage-zage da gorin ai ta kusa daina ganinsa sai ta dafa gidan ta cinye ni kaɗai idan ta samu kuɗin biyan haya, domin wallahi shi bazai biya ko sisi ba, ko ta tattara ta koma Yankin Tudu tunda bata da kunya ta fara rainashi bazatw roƙeshi ya sammata abinda ya siyoba ta sawa kanta girman kai alhali ita ba ƴar kowa ba ce face ƴar Madinkin da ya ke talakan fitik ta sanadiyyar rashin kuɗin zuwa Babban Asibiti ciwon ciki ya kasheshi.

Kamar babu mutum a gidan haka Naila tayimai shiru, amma a É—aki kuka takeyi zuciyarta na suya.

Bai daÉ—e da gama Breakfast ba su Yasar suka iso Gidan.

Jiki na rawa ya shigo da su Living room yana baza kunnuwar jin dalilin zuwansu har Gida. Ba su fara bayani ba sai dai suka bashi umarnin kiran Naila.

Da ya shigo kiran Na'ilah sai da ya
Na mata kunnen karta kuskura ta saɓawa abinda zai ce ya yi mata, sannan ya kamo hannunta muka fito tare.
Naila tana hangosu ta ƙwace hannunta ta nufi Bushra.
ƙam ta rungume Bushra tana nanata kalmar ta yafemata ta zargeta da cin amanarta ashe tanadin da ban taɓa tunani ba tayimata.

Sufyan harara yake watsowa Naila ta ƙasan ido saboda ya matsu ya ji dalilin da ya kawo su. Sai da Naila ta nutsu tukunna sannan Bushra ta fara yi mai bayanin samun aikinsa da kuma irin albashin da za'a dinga biyansa duk wata.

Duk yadda Sufyan ya so yaja aji ko ya kame kansa kasawa ya yi ya miƙe zurbur yana zaro idanunsa, kafin ya fashe da kuka yana yi musu godiya. Kai suka girgiza a tare suna haɗa bakin faɗin;
"Naila zaka yiwa godiya dalilin gwagwarmayarta kakai matsayin da kake kai a yau, don haka karka manta alkhairinta domin shine tsanin nasararka" da gigin farin ciki ya fara nanata "Naila na gode! na gode!! na gode!!!" A tunanin Naila Sufyan ya sauya kenan don haka ta taso ta ƙanƙamesa tana yiwa su Bushra godiya, suma murmushine kwance a saman fuskokinsu.

Bushra bata nanata naimarwa Naila jami'a ba tunda sun riga sun yi maganar da Sufyan tun farko kuma ya nuna ya amincewarsa. Bayan wani lokaci Yasar yayimusu sallama Bushra kuma ta zauna Naila ta kitsa mata kanta. Shima Sufyan barin Gidan ya yi da sunan zuwa Makaranta, zuciyar Bushra na suya tabi bayansa da kallo saboda ko shakka batayi wajen Sumaya zaije. Kenan Sufyan ba zai taɓa sauyawa ba.

Naila da bata fahimci komai ba bakinta a washe take yiwa Bushra kitso tana janta da hira.

A hankali a hankali hirarsuu ta faÉ—o kan Sulaim da yadda suka haÉ—u da sanadiyyar mutuwar Mahaifiyarta da ko Yasar Naila ba ta faÉ—awa ba, ta dai ce masa Mahaifiyarta ta mutu.

Bushra tari ne ya sarƙeta ta hau yi babu kakkautawa, sannu Naila ta fara yimata kafin ta wuce kitchen ta ɗauko mata ruwa.

Bayan tarin ya tsagaita sai ta yiwa Naila murmushi ta ce;
"idan har kin aminta dani inaso ki É—aukomin hoton Sulaim na gani."

Da hanzari Naila ta miƙe tana dariya na nufi Ɗakina.
Bayan ta ɗauko ta miƙawa Bushra,
Bushra ta ɗebi mintina tana kallon hoton, sannan ta miƙamin tana janyo gilashinta mai ɗan duhun da Naila take iya ganin idanuwanta amma ba sosai ba ta manna.

Naila ba ta kawo komai ba a ranta ta hau yaba gilashin da ƙoda irin kyan da ya yi mata. Bushra ba ta ta cewa Naila komai ba sai ɗan danne-dannen da ta yi a waya.

kamar daga sama Naila ta ji Bushra ta ce;

"Idan yau ace Mairam Matar Mahaifin Sulaim kuma Æ´ar Uwar mahaifiyarki da Mahaifiyarki ta rasa ranta wajen hidimtamata amma tabi umarnin iyayenta ta gudu ta barki duk da tasan zakisha wahala, kika ganta cikin daular da take da damar nemanki ta taimaka miki amma batayi ba yaya zaki ji?"

Kanta Naila ta ɗago dakyau hawayen tuna irin mutuwar azabar da Mahaifiyarta tayi na zubowa ƙuncinta, cikin dakiya da kyakkyawar fata ga kowa ta ce; "wataƙila tana da dalili, ina kyautatamata zato a duk inda take, idan da rai da rabo wata rana Allah zai ƙaddara saduwarmu, amma gareni na yafe mata duniya da Lahira." Ta ƙarasa faɗa tana fashewa da kuka.

Rungumeta Bushra ta yi cikin ƙosawa ta ce;

"Yaushe zaki daina barin hawayenki suna zuba Naila? dole duk wani matakin nasara na tare da ƙalubale, Karki bari yawan kukanki yazama lagonki a wajen maƙiyanki"

Kai Naila take girgizawa. A haka Bushra tayi ta lallashinta har ta yi shiru. Kafin ta bar Gidan sai da ta bata kuɗi masu yawa tace ta ɓoye zata ƙara dawowa kafin ta wuce Babban Birnin Abyad.

SUFYAN; Kuɗin Naima da yake tarawa kaf ya kwashe sukayi ƙwarya-ƙwaryar walima shida iyayen Sumaya da ƙawayenta, tare da alƙawarin da zarar yaje Babban Birnin Abyad ya samu yadda yake so shirye-shiryen auren su da Sumaya zai kankama.

Sai dare sosai ya dawo Gida.

★washe gari ma da sassafe ya bar gida. Duk Naila ba ta damu ba, ta bar shige da ficen nasa a matsayin shirye-shiryen tafiya Babban Birnin Abyad.

Ranar da jirginsu zai tashi a bakin Bushra da zo gidan Naila ta ji labari, sai dai bata nunamata batasaniba.

Bushra ta yiwa Naila kyautar kuɗi masu yawan gaske ta kuma yimata alƙawarin zata zana jarabawar share fagen shiga jami'a da taimakon Yasar. Da ta tashi tafiya waya mai kyau da tsada ta bata ta ce ta ɓoye kar ta bari Sufyan ya gani.

Naila bata fahimci tsanarta ya yi nisa a zuciyar Sufyan kuma har abadan bazai taɓa ƙaunarta ba, sai da taga dare ya yi babu Sufyan ko da ta kira Yasar da wayar da Bushra ta bata da lambobin su a ciki, a nan takejin labarin ashe Sufyan tun da yamma jirginsu ya tashi. Ta yi kuka mai raɗaɗi da ciwon da bansan iyakarsa ba bayan sunyi sallama da Yasar, kafin ta haƙura ta kulle kanta a ɗaki.

Tafiyar Bushra da Sufyan ne yasa Yasar dawowa ɓangarensa tare da ƙaramar ƙanwarsu da zamu zasu jarabawa tare sai dai Naila ta girmeta amma ta fi Naila girman jiki.

Naila ta ji daɗin dawowar Yasar da ƙanwarsa, da kai tsaye ɓangarenta ya turota don tayata kwana.

A take Naila ta saki ranta domin fuskantar sabuwar rayuwata.

SUFYAN; kafin tafiyar Babban Birnin Abyad tunda sassafe Naila tana barci ya ɗauki iya ƴan kayan da zai ɗauka ya bar gidan, a Makarantar suka wuni da Sumaya tana kukan zatayi ƙewarsa. Gudun lalacewar komai yasa bai barta ta rakasa airport ba kamar yadda ta buƙata.
Tare da Bushra suka hau jirgi..

Bayan sun isa filin jirgin Babban Birnin Abyad mota daban-daban suka hau da Bushra baima ƙara ganinta ba, kamar ba tare suka taho ba. Ma'aikacin Company ya kira kamar yadda Yasar da ya kira ya yi mai bayani haɗe da turomai Number.

Kamfanin Dhahab bai ƙarasa c
Tsakiyar Babban Birnin Abyad ba kuma anan inda Company ya ke anan staff quarters É—insu yake.


Apartment ɗin da yasa Sufyan zubewa ƙasa yana yiwa Allah godiya aka kaishi. Ranar kwana ya yi bawa Sumaya labari haka su Ɗayyib da ya kira. Sam ya manta da Naila.

Kan Sufyan bai ƙara kwancewa ba sai da aka kaishi Office ɗin da ake ce nashi ne.

Duk da Sufyan yana da son banza da kwaɗayin son tara abin duniya sai da ya tsorata ba kaɗan ba. Tayaya ya samu matsayin da ko da dukka karatunsa ya kammala ba zai samu ba? anya Bushra da Yasar da Naila ba haɗa baki sukayi domin a siyar dashi ba tunda yana cinyemata kuɗin kitso? Hannunsa na karkarwa ya lalubo wayarsa😂.


🔥


SASAAL


18

Duk number wanda ya kira ba ya samu hatta number Bushra da bai ƙara gani ba a kashe yake. A take nadamar rashin siyawa Naila waya ya lulluɓesa, da yanzu ita zai kira yayiwa barazana tunda yasan matsoraciyace.

Fatar hannunsa, takalmin ƙafarsa da kayan jikinsa ya kalla, ya ƙara kallon ofishin bai san sanda ya fashe da kuka ba. Sam Chemistry bai haɗu ba dole akwai manufa. Cikin kuka yake ƙara zagaye ofishin har da Bedroom da washroom.

Lokacin da ya gama ƙarewa komai na ofishin kallo sai ya ƙara sakin kuka, hannunsa na tsuma ya ƙara lalubo wayarsa a karo na biyu ya dannawa mahaifinsa kira, saboda daa baiyi niyyar kiransu ba kar ya ɗaga musu hankali.

Duk son duniyar Sufyan a bayan Hindu Mahaifiyarsa yake haka itama duk son duniyarta a bayan Ɗayyib suke, domin shi bashi da tsoro akan duk wani abu daya kafawa ƙahon zuƙa.

Sufyan cikin kuka yake bawa Ɗayyib labari. Maimakon ya ji tashin hankali a muryarsa sai ya ji ya saki ƙaramin dariya.
Da ƙwarin gwiwa ya ce;
"Naila bata da muguwar zuciyar sayar da kurwarka Sufyan"
Kai Sufyan ya girgiza idanuwansa ƙyam akan kujerar alfarmar da yake a matsayin mazauninsa.

"Baaba bazaka fahimta ba, ba su kirani interview ba balle na tantance ƙwarewa ta ce yasa suka bani wannan ofishin, babu wani abu daga neman aiki sai shiga ofishi, tun daga ranar da na sauka ko Bushra banƙara gani ba, Baaba ni dai kawai haƙura zanyi da aikin nan"

Da zafin muryar da zai nutsar da Sufyan kar yaja musu asara ÆŠayyib ya ce;

"Ka kwantar da hankali ka, duk na sa Ubangidana ya bincikamin komai, kana tunanin rayuwar kara zube kakeyi a Birnin Abyad? Har soyayyarku da Sumaya na sani, da bushashar da kakeyi da KuÉ—in sana'ar Naila, dama abinda muka turaka kayi kenan?
To ka buɗe kunnuwanka dakyau ka saurareni. Ka mayar da hankali kan aikinka domin fansar dukiyar da Mahaifiyarka da ni kaina muka sadaukar akanka ba ka zauna yin shirme ba. Inaso ka tara kuɗi Ubangidana yaƙara bincikamin komai a kan ma'aikatarku domin sanin muhimman abubuwa akan mai kuɗi sai da kuɗi.
Yaya ma sunan ma'aikatar taku ka ce?"

Kafin Sufyan ya ɓude bakinsa da ya yimai nauyi saboda kalaman Mahaifinsa da suka sanyaya mai jiki, an buɗe ƙofar ba tare da naiman izini ba. A gigice ya katse kiran.

Rashin nutsuwar da yake ciki da kuma rashin sanin matsayin da aka bashi yasa bai tuhumi wanda ya shigo maiyasa bai naimi izini ba.

Ɗayyib bai haƙura ba ya cigaba da kira Sufyan a ɗan gajarce ya ɗaga ya ce ya bari idan yaje Gida zasuyi waya.

Cikin ƙwarewa bayan sun Gaisa da wanda ya shigo yake koyawa Sufyan yadda zai gudanar da aikinsa.

Fara'ar fuskar Baturen da yadda yake nunamai yadda zai gudanar da aikinsa ne yasa Sufyan ya É—an saki jiki.

Ko da Baturen ya fita sai da ya ƙara ƙarewa komai kallo yanajin alfahari da girman kansa na ƙaruwa a hankali. Murmushi ne ya kufcemai bayan ya sauke ajiyar zuciya wawtar dayaso tafkawa na dawomai.

Bayan Sufyan ya isa Gida ko cikakken hutun minti biyu bai yi ba, aka aiko mai da lafiyayyun kayan fita Office. Cikin isa yake gwada kowanne kanshi na ƙara girma.

Da yake Sufyan sha-sha-sha ne ko da ya nutsu maimakon ya kira Mahaifinsa sai ya kira Sumayya suka yi ta waya har barci ya É—aukesa.

★sai washe gari da safe ya tuna da kiran Mahaifinsa, a gurguje ya kirasa suka gaisa sama-sama.

Irin motar da aka zo É—aukarsa zuwa office ne yasa ya ji daÉ—i kamar ya kashe shi, cikin isa ya gyara kwalar rigarsa haÉ—e da motsa kafaÉ—unsa kafin ya shige.

Daga wannan rana aikin Sufyan da ya mayar da kai ya miƙa, cikin kwanaki ya ƙara gogewa ya fara ɗaukar hanyar zama Sufyan Dhahab ɗin da yake fata.

A computer yake ganin irin Tukwanen da Company Dhahab suke ƙerawa amma bai taɓa ganinsu ido da ido ba, domin ma'aikar da ake ƙera Tukwanen daban yake da na sarrafa shinkafa da yake aiki. Sai dai labarin Tukunyar da ya ke datsa jefi-jefi a wajen Abokanan aikinsa.

Hankalin Sufyan ya ƙara tsayuwa waje ɗaya bayan samun tabbacin Turawane manyan Company, ƴan asalin ƙasar Abyad tsirrai ne a ciki.

Cikin ɗumbin narasa, kwanciyar hankali, ƙaruwar soyayyarsa da Sumaya, manta Naila gaba ɗayanta, rayuwar Sufyan ya miƙa.

BUSHRA; tun ranar da ta sauka a Babban Birnin Abyad bata samu nutsuwa ba sai da ta tattara ta bar ƙasar gaba ɗaya. Saboda har lokacin bata cire ran samun kira daga Malik ba. Lokacin da taje Dhahab ma a tsaitsaye suka gaisa da Simbi Uzair ya dawo da ita Gida. Daga wannan rana ta ƙauracewa ƙasar Abyad gaba ɗaya, sai saƙon kuɗi da take aikawa Yasar ya bawa Naila.

NAILA; Duk da ta saki jikinta a wasu lokutan tanajin ranta babu daÉ—i, tanaason magana da Kaaka amma bata da hanyar samunta.

Tana cikin wannan yanayin ta zana jarabawar share fagen shiga jami'a ita da ƙanwar Yasar. Har lokacin babu kira daga Sufyan, kuma bai zoba, ko Yasar ya daina kira a waya.


Kwanaki biyu da gama zana jarabawar su aka kira Yasar Interview a Dhahab Babban Birnin Abyad.

Rai babu daɗi Yasar ya fara shirin tafiya Babban Birnin Abyad. Bazata taɓa manta alkhairin da ya yimata ba, da abubuwa dayawa da bazan taɓa iya mantawa da su ba, ya yi mata alƙawarin zaman ƙanwarsa a tare da ita.
Sai dai da yaje yiwa Iyayensa sallama ƙememe suka nuna ba su amince ƴar su ta zauna a inda babu mafaɗi ba, da yake Naila ta rakasa domin dawowa tare da ƙanwarsa a gabanta suka dinga sakin maganganu marasa daɗi da nuna ita ɗin ba wata abar aji tausayi ba ce. Bata yi kuka ba, ba kuma taga laifinsu ba amma ta ɗan ji haushinsu tunda ko ba komai ai sai su yi tunanin suma tasu ɗiyar zata iya tsintar rayuwarta a cikin kwatankwacin irin wanda ta riski na ta a ciki.

Har suka dawo Gida haƙuri Yasar yake bata, ta na ta nunamai babu komai.

A washe garin ranar da ya rage saura kwana ɗaya Yasar ya tafi Babban Birnin Abyad ya kai Naila ya buɗemata asusun ajiyar kuɗi a Babban bankin Birnin Abyad, tare da siyayyan kayan abinci da kayan maƙulashe kala-kala.

★washe gari da sassafe Yasar ya fito zai tafi. Ta yi kuka irin kukan da ban san iyakarsa ba, sai take ji kamar ita kaɗaice a duniyarta, sai ta ke jin kamar ta bishi taga inane wannan Dhabah ɗin, su waye a ciki, tanaji a jikinta kamar ta san su, kamar tana da alaƙa da su. Cikin kuka ta ce idan ya je ya gaishemata da mutanen cikin Dhahab. Duk yadda Yasar yaso ya jure kasawa ya yi yasa kuka da haka suka rabu da Naila ba tare da sanin ranar da zasu ƙara ganin juna ba.

Naila bata taɓajin kaɗaicin da ta ji ba a kaf rayuwata irin ranar da Yasar ya bar Birnin Abyad. Ko ina yayimata shiru wa su lokutan sai ta ji kamar motsi a bayanta wa su lokutan kuma sai ta ji kamar ana kiran sunana. A wannan dare ta gane girman rahamar zama da mutum a waje ɗaya.

A haka wahalallen barci ya É—auketa cike da mafarkai ma su ban tsoro.

A haka ta shafe kwana uku cikin kaÉ—aici duk da tana waya da Yasar jefi-jefi a rana.

Tun tana jin tsoro har ta haƙura ta sanyawa zuciyata dakiya.

Da sannu zuciyarta ta ƙeƙashe ta daina jin tsoron komai. Zata tashi da safe ta yi Breakfast ta ci na ƙoshi idan rana tayi ta tafi Gidan Customers ɗinta wa su kuma su biyota Gida. Idan Dare ya yi ta ɗauki kuɗi a cikin kuɗin sana'arta ta je nasha Ice cream a wajen da Yasar ya nunamata.

A haka rayuwata ta miƙa, jarabawarau ta fito tayi kyau. Da taimakon Abokin Yasar ta samu gurbi a jami'a mai zaman kanta na Birnin Abyad duk Bushra ce ta biya ta hanyar Yasar, shi kuma ya turawa amininsa.

KuÉ—in siyayyar kayan abinci da abubuwan amfani Yasar ya turomata. Da ta rasa kalar godiyar da zanyi musu shi da Bushra kuka na sanya.

Duk da Bushra ta ƙauracewa waya da ita, ta ƙauracewa zuwa inda take domin ta jima da dawowa Babban Birnin Abyad amma saboda tana tsoron kar ta cigaba da zuwa wajen Naila asamu matsala, sai ta daina kiranta, ta daina zuwa wajenta ko ta shigo Birnin Abyad gudun kar ta ƙara saka Naila a cikin matsala.

Da taimakon Abokin Yasar Naila ta kammala komai na fara attending lectures

A ranar da ta fara zuwa Makaranta da yamma bayan sallar la'asar ta fita siyayyar abinda zatayi amfani dashi tunda a Hostel zata zauna saboda tazarar Makarantar da Gidansu.

Doguwar Riga mai taushi da faÉ—i taa sa ta naÉ—a mayafin da ya yiwa fuskarta da ya rage rama kyan gaske. Waya da card É—in da zatayi siyayya dashi kawai ta É—auka.

Wajen siyayya mafi girma a Birnin Abyad ta nufa saboda a can zata samu duk abinda take so.

Tun shigowarta ta hango Sufyan hannunsa sarƙafe da na Macen da bata sani ba (Sumaya).

Ya yi kyau irin kyan da yake buri, ya ƙara haske da ƙiba kamar ba Sufyan ba. Macen ce ta fara hangota kamar ta Santa, sai ta ƙara ƙanƙame hannun Sufyan cikin kishin da ya bayyana a saman fuskarta. Naila ba ta nuna ta gansu ba, ta fara ɗaukar abinda ya kawota.


Duk yadda Matashiyar da ke tare da Sufyan ta so janye hankalin daga ɓangaren da Naila take sai da ya waiwayo.

Da farko bai gane Naila ba sai daga baya. Hannun Sumaya ya saki da sauri ransa na suya, hassadar yadda ta canza har ta samun ƴanci da kuɗin yin siyayya a wajen da ya kawo Budurwarsa na cin zuciyarsa. Naila tana sane da tahowarsa kafin ya ƙaraso ta yi wuf ta nufi wajen biya. A kwai mutane a wajen don haka ya juya ya na ɗaukar komai a hanzarce don suyi su gama, bai damu da yadda Budurwartasa take ƙunci ba.

Lokacin da ya iso da jibgin kayan siyayyarsu lokacin Naila ta nufi ƙofar fita.

Yaso jirkintawa su gama biya amma ganin kamar hakan zai ɗauki lokaci har Naila ta ɓacemasa kawai sai ya miƙawa Sumaya card ya bi bayanta da sauri ba tare da tsayawa kallon ƙuntatacciyar fuskar Sumaya ba.

Ya na fitowa Naila tana shiga Taxi kafin ya shiga Mota tuni mai Taxi ya bar wajen.

Lafiyayyen motar da Company Dhahab suka siyamasa ya shige a hanzarce. Da speed ya bi bayansu kar su tsere mai, ganin sun É—auki wani hanyar daban ba na gidan daya sani ba sai ya ji hassada na naiman kassarashi zuciyarsa na tiriri.

Naila suna isa gare É—in Makarantarsu da É—an hanzari ta sauko daga Taxi dama tun a ciki taa sallamesa.

Gate É—in Makarantar nufa hankalinta a kwance duk da ta hango motar da na ke kyautata zaton na Sufyan ne.

ID ta nuna ta Securities su ka barta ta wuce.

Tana shiga ta ƙara shiga Motar da zai kai ta har bakin Hostel ɗinsu. Sai a lokacin ta saki ɗan dariyar da ya ƙaramata kyau tana hasaso irin ƙuncin da Sufyan zaiji domin tasan ko shi yafi kowa kuɗi baza'a barshi ya shigo ba, tunda bashi da Numbern wayar kowa kuma bai san kowa ba a Makarantar.

Sufyan sai ta nutsuwarsa ya yi bayan ya yi parking domin kai tsaye suka hanashi shiga kamar yadda ya so.

Ba irin bayanin da bai yi ba, babu kuma irin rantsuwar da baiyi ba shi Mijin Naila ne amma suka nuna su sam basu santa ba duk kwatancen da ya yi musu.

"shin yamasan a gaban wani University yake tsaye kuwa? Securities suka tambayeshi.

Sai a lokacin ya ɗaga kai yana kallon sunan da yake jiki saman Dogon Ginin ɓaro-ɓaro a take ya ji hassada na naiman kasheshi jirin baƙin ciki na naiman kai shi ƙasa. Sum-sum ya dawo wajen Motarsa yana jin muzanta a karon farko tun bayan tafiyarsa Babban Birnin Abyad.

Da ya shiga Mota kasa jurewa ya yi, ya fara dukan kujerun motar ya na surutai "Ni Naila zata yiwa taurin kai, har ta yarda su kawota jami'a irin wannan, wallahi! Wallahi!!! Wallahi!!! Sai nayi sanadiyyar barinta Birnin Abyad wayyo zuciyata zata fashe" ya ƙasara faɗa ya na dukan saitin zuciyarsa....✍🏻
[7/24, 9:20 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥


SASAAL


19

Sufyan ba wannan ne zuwansa Birnin Abyad na farko ba. Tun lokacin da aikinsa ya miƙa komai ya yi mai yadda yake so ya fara kawowa Sumaya ziyara.

Sumaya macece tasan kuma abinda Sufyan yake yiwa Iyalinsa ba daidai ba ne, a addini har ma da al'ada amma son kai da tsanin son zuciyar kutsa kai cikin abinda batasan mafarinsa ba yasa take ganin kamar Sufyan ma son Iyalinsa ya ke yi banda haka ya saketa mana kawai ita ya gabatar da ita a wajen Iyayensa suyi aurensu. Har layin tasha zuwa taga yaya Naila take..

Son zuciyar Sumaya kaÉ—an ne akan na Mahaifanta, domin su cewa su kayi bazasu ba shi Sumaya ba har sai ya saki Naila.

SUMAYA
Da Sufyan ya dammaƙa mata Card zuciyarta ce kawai bata haɗiya ba, kishi ya toshe komai nata gani take yi duk kuɗin da Sufyan yake ikirarin ba shi da shi Naila yake kashewa ba Iyayensa yake turawa ba kamar yadda ya faɗa. Saboda tun fara aikin Sufyan ranar ne kawai tasan ya yi mata siyayya ma su nauyin kuɗi, duk zuwa idan ya yi ƴan kuɗine yake rabawa Mahaifanta. Amma ga Matarsa nan tayi kyau tasa sutura na alfarma, saboda kishin ma kar wani ya ganta har rufa mata baya ya yi yana muzurai sai ka ce wani sakarai. To kenan yaudararta ya ke yi da ya ce ba ya zuwa wajen Naila?

Da kuka shaɓe-shaɓe ta tari Taxi ta nufi Gida.

SUFYAN; bayan ya gama bige-bige da ayyana irin ramuwar gayyar da zai yi akan abinda Naila ta yi mai sai ya É—auki hanyar Gidan su Sumaya.

Kukan da take yi da irin maganganun da take saki Iyayenta na ƙara tunzura ta ne su ka ƙara harzuƙa Sufyan, cikin tsananin fushi ya buge kofin tangaran ɗin da su ka zuba masa lemo a ciki, a take ya fashe. Sumaya tana yunƙurin zaginsa ya zuba mata marin da ya taɓa zuciyar Iyayenta, Babanta ma na yunƙurin kwasamai mari ya riƙemai hannu, kafin ya jefar da hannun da iya ƙarfinsa. Cikin isa da takaici ya ce;

"ki je mun rabu! kuma karki ƙara nemana tunda har yau baki fuskanci Naila itace mukullin ƙofar nasarata ba" yana gama faɗa ya bar madaidacin living room ɗin da aka ƙawata da kuɗin Naila kafin ya samu aiki.

Da sakakken baki ya bar su, saukar kalmarsa na "sun rabu" na cakar zuƙatansu sama da raɗaɗi marin da ya saukewa Sumaya da hannun Mahaifinta da ya jefar, saboda Sufyan da shi suke taƙama domin sanadiyyar haɗuwarsa da Sumaya rayuwarsu ta sauya ba kaɗan ba. Sumaya kuka take yi har da birgima, danasanin abinda ta aikata na mamaye zuciyarta. Sufyan baya ɓoyemata tasan da kuɗin kitson Naila suke ci suke sha a makarantar kuma sanadiyyar Naila ya samu aikin da ya ke yi, amma ita ta rasa dalilin da ya sa ta tsani Naila.

Daga wannan rana Sufyan ya ƙauracewa kiran Sumaya. Ga hotuna da ya ke saki masu kyan gaske a shafukansa, duk domin Sumaya tasan ko a jikinsa. Ya yi narasa kuwa domin Sumaya ƙara gigicewa tayi. Ba dare ba rana kullum sai ta turamai saƙo.

Rasa yadda zata shawo kanshi yasa ta turamai saƙon tayasa fakon Naila, har ya samu damar mayar da ita Yankin Tudu kamar yadda yake yawan faɗe tun kafin ya tafi Babban Birnin Abyad.
cikin jimami ta zauna zaman jiran amsar da zai bata.

NAILA; cikin nasara da wadatacciyar nutsuwa ta fara gudanar da karatunta.

A ɓangaren sana'arta kuɗi ta ke samu ba kaɗan ba, saboda ƴaƴan manyan mutane da suke Campus ɗin su waɗanda kansu ya ke kitsuwa a wajenta suke yin kitso.

Cikin watanni ta ƙara zama wayayyiyar mace sai sanyin kyau da ɗabi'a. Ba ta shiga sabgar da bai shafeta ba tana kuma tsayawa a iya matsayina.
Tana zuwa Gida jefi-jefi musamman ranar sati. Batun Sufyan kuwa tuni ta share shi a ranta, ta mayar da hankali kan abinda ya kaita Makaranta. Yasar kullum shi yake ba ta ƙarfin gwiwar yin karatu idan sunyi waya, domin shine matakin zamanta a Birnin Abyad na din-din har ta kawo Kaaka su ƙarasa rayuwarsu. Wannan ƙwarin gwiwar da Yasar yake bata ba ƙaramin dadinsa ta ke ji ba.

A hankali komai ya yi ta sauyawa watanni na shuɗewa, shauƙin son zuwa Yankin Tudu domin ganin Kaaka na ƙara mamaye ran Naila, a haka suka fara shirye-shiryen zana jarabawar da zamu yi hutu mai ɗan tsahon da zata iya zuwa Yankin Tudu ta taho da Kaaka. Kamar yadda Yasar ya shawarceta tunda tana samun kuɗi.

SUFYAN; bai daina son Sumaya ba amma yanason ta gane shi ɗin Namijin da za'a lallaɓa ba wanda za'ayiwa hargagi ko rashin kunya ba. Ko da yaga saƙonta fuska ya yi, domin yasan ba ta da wani abun tsinanawa, kawai don ya kulata ne.

Magiya da nacinta ba dare ba rana ne ya dawo da soyayyarsu har ya fara yunƙurin tarar Mahaifansa da batun ta, tare da shawarar da ya yanke na sawwaƙewa Naila kafin ya aiwatar da ƙudirinsa a kanta.

Cikar Sufyan shekara ɗaya a ma'aikatar Dhahab yasa sukayi mai kyautar da ya hanasa runtsawa. Waya kuwa kwana sukayi suna yi da Ɗayyib, cikin isa Sufyan yake bada umarnin abinda za'ayi da kuɗin. Ba bu lissafin yinƙurin yin wani abu na cigaban Yankinsu a kason kuɗin da duk wani kuɗi da yake turawa sai Gidan Sarautar su da aka ƙara ƙawatawa, musamman ɓangaren Mahaifansa Ɗayyib da ɓangaren Kakansa Jalal.

Ba bu wani tsarin tallafi da suka tsiro da shi a matsayinsa na Ɗan Yankin da ya samu cigaba a Babban Birnin Abyad sai dai mutanen gari su gani a jikin Iyayensa, ƴan Masarautar su da Gidajensu, duk da mummunar talaucin da suke fama da shi. Har lafiyayyen titi aka shimfiɗa daga farkon shigowa Yankin Tudu har ƙofar Masarautar su.

A ɓangaren Ɗayyib da Sufyan ya fara samun kuɗi Gidan Game ya buɗe ƙato matasa su samu kuɗi suyi ta bugawa Yara kuma su sato kuɗin Mahaifansu. Abun takaicin sai Matasa da Iyayensu sun sha wahala sun ƙera Tukwane sun samu an siya daƙyar sai Ƴaƴan su kwashe kuɗin su gudu gidan Game ɗin Ɗayyib.

Cikin ƙanƙani lokaci shima ya fara zama hamshaƙi.

Dukka wannan facakar sai dai Æ´an uwan Naila da Kaakarta su ji labari, kamar dai gama garin mutane ba surukan Sufyan ba.

Ɓullowar batun auren Sumaya da Sufyan, ya tayar da ƙura a tsakanin Hindu da Ɗayyib don sai da sukayi faɗan da ya kaita ga tafiya Gidansu. Ta kafe bata yarda da auren ba matsawar ita ta haifi Sufyan domin malaman tsibbunta sun sanar da ita sakin Naila zai rusa komai, haƙurin mutanen da suka zubawa Sufyan ɗin ido ya na zaluntarta har suka ɗaukesa aiki zai ƙare daganan suyi masa ɗaurin talalar da zai mutu a ɗaure.

Sam ÆŠayyib bai yarda da batun Hindu ba, acewarsa É—aukakar Sufyan daga Allah ne, babu wata Naila don haka dole su bar Sufyan ya rayu da abinda yake so.

Ankai ruwa a tsakanin su har sai da Jalal Mahaifin ÆŠayyib ya shiga faÉ—an da suke yi a sirrince don bakowa ba ne yasan Hindu bata gidan ba.

Sai da Mahaifiyar Hindu ta saka baki, sannan ta yarda da auren amma da sharaÉ—in ko zai saki Naila sai lokacin da ta yarjemai. A kan haka suka bar zancen.

Da tsananin rawar kai Sufyan yake rabon katin aurensa ga Manyan ma'aikatarsu. A cewarsa ma bai taɓa Aure ba.

Labarin auren Sumaya da Sufyan sai da yaje har kunnen Bushra, ba tare da ɓata lokacin ba ta naimi Yasar ya toshe duk wata hanya da Naila za ta iya jin labari, saboda kar hakan ya kawomata tsaiko a jarabawar da take zanawa. Kuma da zarar ta gama ya shirya mata tafiya Yankin Tudu.

A rabon Invitation card da Sufyan yake yi ne, Baturen da yake sama da shi ya bashi shawarar ya shirya katin gayyata na musamman ga GM wataƙila ya samu alheri mai yawan gaske.

Da yake Sufyan ɗan son banza ne a daren ya biya kuɗi mai yawa aka shiryamai katin gayyata na musamman. Washe gari kafin ya shiga office ya miƙawa ogansa ya bawa GM ba tare da nutsuwa ya yi tunanin maiyasa tunda ya ke aiki a Dhahab bai taɓa ganin GM ba, ko da gilmawarsa ne.

Gaba ɗaya sai Sufyan ya matsu ranar Aurensa ya zo, irin shagalin da ya tanadi maƙudan kuɗi za'ayi a Yankin Tudu na sanyashi jin alfaharin da bai taɓa jiba.

Ɗayyib da su Sarki Hammam da ya yi kwantan ɓauna kamar yana tare su ne su suka zo Birnin Abyad Gidansu Sumaya naimawa Sufyan aure. A take Iyayen Sumaya da suka matsu da komai suka ce sun bashi sati mai zuwa a ɗaura aure su tafi da Ita Yankin Tudu su je can suyi Biki, a maimakon wata ɗaya da suka tsara da Sufyan tun kafin zuwan Iyayensa ya yi rawar kan buga katin gayyata.
Iyayen Sumaya sun ce su basu da wani shagali da zasu yi bayan É—aurin Aure.

Abin takaici daga Ɗayyib har da muƙarabansa da suka zo Birnin Abyad tare ba bu wanda ya tambayi ina ƴarsu Naila Ƴar Yankin su take? a wani yanayi take ciki?. Kowannen su fuska ya yi yana dirzar duniyar da ya samu.

Da rawar jiki Sufyan yake ƙara bawa manyansa haƙurin matso da lokaci kusa an samu akasi. Wa su sun nuna zasu je wasu kuma tambayarsa suka yi babu wani shagali da za'ayi ranakun da zasu biyo bayan ɗaurin auren da zasu iya zuwa? Da sanyin jiki ya sanar da su na Yankin Tudu tunda yasan ba lallai su je ba.

Ga ɗumbin mamakinsa washe gari ya samu saƙo GM ya ce ya amsa gayyata amma ba zai samu zuwa ɗaurin aure ba, sai dai na Yankin Tudu da za'ayi In Shaa Allahu. Sufyan ihu yasa ya na tsalle, har ya fara hango irin ƙafafa da zafin kan da zai yi, inama da Naila tana wajen ya nunamata ko babu ita shi ya zama kafin Allah a Dhahab sai dai ta mutu da baƙin ciki.

Cikin walwala da son Daular da ya ke iya canza tunanin ɗan Adam lokaci ƙanƙani su Ɗayyin suka cika sati guda a Birnin Abyad.

Ranar ÆŠaurin aure
Irin fareren Turawan da suka zo ɗaurin auren Sufyan da Sumaya a Birnin Abyad ne yasa bakin Ɗayyib yaƙi rufuwa. Bayan komai ya lafa sun keɓe Ɗayyib ya murmusa cikin alfahari ya ce;
"Sufyan ina alfahari da kai akanka na fara samun cikar burina na tsayin shekaru, kaga Ubangidana ko, sam bai halarci ɗaurin aure nan ba kuma nasan yana gari, dama ina sane da shi, tun daga kan takardun da na ce ya samar maka ya ƙauracewa waya dani, to dama haka rayuwa take, yau ina jina na daban ya ya ma kace sunan wannan Ma'aikata taku mai albarka." Ya ƙarasa faɗa yana kafa lemo mai tsada a baki.

Sufyan da ke murmushin isa É—an dariya ya yi kafin ya ce "DHAHAB"
Azababben tari ne ya sarƙe Ɗayyib lemon da ya kurɓa ya soma biyomai ta hanci da baki...

NAILA; A dai-dai lokacin da Tari ya sarƙe Ɗayyib Naila ta kammala haɗa kayan tafiya Yankin Tudu....✍🏻

Wanene General manager company sarrafa shinkafar Dhahab da Sufyan yake aiki a ƙarƙashin shi?😄

Maiyasa ya zaɓi zuwa wata ƙasar shagalin ta ya murnar ma'aikacin da ya ke ƙasan-ƙasansa duk da girman matsayinsa.

Yaya zaman Naila a Yankin Tudu zai kasance shin zata dawo ko bazata dawo ba? Kaaka tana raye ko bata raye?

Wani 🔥🔥 ne zai kama a Yankin Tudu?

Next page In Shaa Allah
[7/25, 8:47 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥


NAFISA ALIYU SASAAL


*CHAPTER 3*
*YANKIN TUDU🔥*


Page 20


NAILA; da ƙananun kayan Calvin Klein ta yi sauƙaƙaƙiyar adon da ya dace da siffarta ya kuma haska kyanta.
Fuskata ƙunshe da murmushi take kallon mutanen Birnin Abyad, farkon zuwansu Birnin ita da Sufyan na dawomata. Rashin banbancin da ke tsakanin fatarsu ta ɓangaren murjewa a yanzu yasa ta ɗan faɗaɗa murmushinta. Ashe komai zai sauya, ashe itama zata zama ƴar gayu kyakkyawar Macen da zatayi alfahari da kanta wata rana.

Dogon mota mai kyau ta hau, idonta tsaye ƙyam a kan hanyar Babban Birnin Abyad.
A wannan karon tana alaƙanta kallon hanyar da Yasar da Bushra da suke can tare da Sufyan, murmushi ta yi data tuna abinda su Bushra suka ɓoyemata, duk da Bushra tasa Yasar ya ɓoyemata koma sai da taga komai a shafin Sufyan kamar yadda take bibiya lokaci zuwa lokaci.

Babban sauyin da ta samu a komawarta Yankin Tudu shine jirgin da ta bi a maimakon Mota da taimakon mutumin Bushra bayan isarta Airport. Cikin É—an tsoron da ya mamaye ranta saboda hawarta jirgi a karon farkon kenan jirgin su ya É—aga zuwa Iyakar Yankin Tudu da Babbar tashar da filin saukarsa ya ke.

SUFYAN; Da hanzari ya nemo ruwa ya miƙawa Ɗayyib, haɗe da nanata kalmar "sannu" da yake tayi ba ƙaƙƙautawa.

Ɗayyib ya ɗauki tsahon mintuna ya na tari, fararen idanuwansa da suka ƙara haske saboda daular da ya samu na kwana biyu ya juyewa zuwa jajaye marasa kyan gani.
Da salon murya da Sufyan bai san Mahaifin nasa da shi ba ya ce;
"Kasan menene DHAHAB" cikin rashin fahimtar ina ya dosa Sufyan ya ce; "Zinare mana Baaba"
"Sufyan ina nufin kasan mafarin ƙirƙirar Dhahab, tunda kake a duniyarka ka taɓajin mai inkiyar banda Ahalin Marigayi Sarki Musa" cikin rashin fahimtar abu da wuri Sufyan ya ce;
"Waccen Dhabah ɗin ai zuri'arsu ta mutu Baaba, waɗannan turawa ne ba ma ƴan asalin ƙasar Abyad ba ne, kusan dukka manyan da suke samana Turawa ne."
ÆŠayyib cikin rashin gamsuwa ya ce;

" Wanene mamallakin ma'aikatar ba ina nufin GM É—in da zai zo shagalin bikinka ba, tunda ance suna da reshe da yawa, asalin mamallakin Dhahab É—in nake nufi gaba É—ayanta, kasan sunansa da inda yake da zaune"

Sufyan ido ya zaro cikin mamaki ya ce; " Babaa ba ni da issue da duka waɗannan abubuwan da ka lissafo burina kawai na samu kuɗi, Ni ma na zama Dhahab ɗin kaina, tunda na lura sunan ya na da wani ɓoyayyen sirri, shine kawai."
Kamar talabijin haka Ɗayyib ya zubawa bakin Sufyan ido, zuciyarsa kuwa Allah Ne kaɗai yasan faɗinta da sirrikan data ƙunsa.

Da kaushin murya ya ce;
"Daga ranar irin ta yau kafara saka lissafin abinda na tambayeka a cikin ƙwanyarka, domin ba ra'ayi ba ne ko ganin dama ba, tilas ne musan su wanene masu Dhahab, aikinka zai fara daga yau Sufyan!"
Ɗayyib yana gama faɗa ya miƙe jiri na ɗibansa sama-sama.

Kafaɗa Sufyan ya ɗaga alamun ko a jikinsa, shi ba shi da wannan ra'ayin da dai maganar kuɗi ne da kyau to da sai iya inda ƙarfinsa ya ƙare, amma ace duk Kuɗin da ya tara sai ya je yana binciken abubuwan da basu shafesa ba, why not ya ba shi shawarar ƙirƙirar wani hanyar da zai ƙara tara dukiya shima ya zama Dhahab ɗin da'akewa kokawa shekara da shekaru har ake salwantar da rayuka duk domin a kawar da su.


SUMAYA
Tasha gyara kyanta da farin fatarta sun ƙara fasowa. Sufyan daya ganta kamar ya siɗeta bini-bini ya kirata a waya su share mintina suna hira.

Kayan alfarmar da zai fitar da Sumaya ta zama ta musamman sama da yadda Ubaidullah ya kawo Kakar Sulaim Nanaah Yankin Tudu aka tanadarwa Sumaya da taimakon ÆŠayyib da kansa aka fitar da adon kayan da ya dace da Masarautarsu.

Bayan komai ya kammala tsirran ƴan uwan Sumaya da kansu yake rawar Ƴar uwarsu tayi dacen gidan kuɗi da Sarauta suka fara shirye-shiryen tafiya Yankin Tudu.

Ranar Alhamis da ya rage saura kwana biyu shagin Yankin Tudu suka É—ugunzuma dukkansu, abin birgiyar daga Company su Sufyan aka turo da motoci na alfarmar da zai kaisu Airport.

Sarki Hammam da ya jima da yin kwantan ɓauna domin tsiratar da rayuwarsa da samun bayanai murmushi yake saki cikin ransa ya na mamakin ɗabi'unsu.

WAIWAYE
Shekarun baya...

Labarin da Dattijo Junaid ya bawa Sarki Hammam, labari ne akan ɓarnar da su Ɗayyib suka kwashe shekaru su na yi a ɓoye.

Bayan rasuwar Dattijo Junaid Sarki Hammam ya shiga É—imuwa da zullumi. Saboda yasan shi ma wata rana matsawar zai yi tsayuwar tsayin daka akan gaskiya to tabbas zai bi sawun su Dattijo Junaid ba da jimawa ba..

Rasuwar Bashar ya ƙara jefa zuciyarsa cikin ɗimuwa, musamman da ya ji ƙishin-ƙishin ɗin ba fa mutuwar Allah da Annabi Bashar ya yi ba, ana zargin Ɗayyib ne ya shaƙamai guba.

A hutun da Sarki Hammam ya tafi Babban Birnin Abyad bayan rasuwar Bashar ya haɗu da Malik, ya kuma gano Dhahab ɗin da su Ɗayyib suke kokawar sai sun ɓaddashi ya na nan daram a Babban Birnin Abyad, amma kamar yadda Malik bai sanar masa wanene yaƙara kafa Dhahab daga cikin zuri'ar Marigayi Sarki Musa ba, shima bai zurfafa dole sai ya sani ba.

Sun yi taƙaitacciyar tattaunawa da Malik.
A cikin tattaunawarsu Malik ya bashi shawarar ya shiga jikinsu Ɗayyib domin sanin motsinsu, ya zubawa zaluncinsu ido har zuwa lokacin da Ubangiji zai ƙaddara ƙarshensu. Idan kuma suka yi zaluncin da ya ratso da haƙƙin wani to ya sanar masa, shi kuma zai yiwa kowaye a cikinsu hukunci dai-dai da abinda ya aikata..

Bayan dawowar Sarki Hammam daga Babban Birnin Abyad sai ya zama É—aya daga cikin Informer Malik a cikin Masarautar Yankin Tudu, da ma Yankin baki É—aya ba tare da kowa ya ankara ba...


*YANKIN TUDU*

NAILA; lokacin da jirgin su ya sauka a iyakar mafarin shiga Yankunan su, murmushi ta saki, zuciyarta na azalzalata tanajin ƙarfin gwiwar da bata taɓa jiba.

Cikin kasuwar chanjin wajen da yake kusa da Airport ta shiga aka canza mata kuɗin ƙasar Abyad zuwa na ƙasarsu, bat rage ko sisi ba. Kuɗine masu yawan gaske don haka ta zuba su a cikin jakar da ta tanada domin su. Masauƙin baƙi ta nufa na canza Suturar jikint zuwa Abayar da suka fi amfani da shi a Yankin Tudu duk da wanda bata da ɗan bambanci.

Drivern da ya ɗaukosu ita da Sufyan shekarun baya shi ya ƙara ɗaukarta. Da shi da Motar tasa duk sun tsufa sun jeme.

Gudu yake yi amma sai take ganin kamar baya sauri saboda yadda ta matsu ta riski Kaka ta ga ko ita yaya ta koma?

Hirar yadda Yankinsu ya koma Driver yake yimata muryarsa a raunane da yadda Sufyan ya ke kashe KuÉ—i a iya Masarautarsu da mutanen cikinta.

Naila bata tsawaita magana da shi ba, saboda yadda zuciyarta take suya.

Lokacin da suka shigo Yankin Tudu batasan sanda dariyar da ya bayyana jerarrun haƙwaranta ya kufcemata ba.

Suna isa ƙofar gidan Kaka da zumuɗi ta buɗe murfin motar, kuma tayi sa'ar babu mutane. Duk suna cikin Gidajen su sai tsirran da ba'a rasa ba. Da taimakon shi ta sauko da kayan tsarabar da ta jibgo. Kuɗi ma su nauyi ta ɗauko ta bashi da sunan kuɗin da ya ɗaukota. Ƙasa ya zube yana kuka cikin shesheƙa ya ce;
"Allah Ya aramin ranar da zan saka miki da abinda kikayimin Allah Ya haska gabanki Ya haska bayanki, Na gode! Na gode!!!" Kai ta girgiza mai haÉ—e da kutsawa Gidan Kaaka.

Murnarta ce ta koma ciki sanda tayi ido biyu da yadda Kaaka ta rame ta lalace fatarta ta yamushe kamar babu ruwa a jikinta.
Da farko Kaka bata gane Naila ba, sai daga baya, da gudu ta taso garin ta iso inda Naila ta ƙame a tsaye ta zube ƙasa saboda tuntuɓen da ta yi. Da sauri Naila ta ƙarasa suka ƙanƙame juna, tana kuka itama Kaka tana kuka.

A haka Drivern ya gama shigo mata da kayanta. Kaka kallon Naila tayi ta shafa fatarta sai ta fashe da kuka, ta yi haka ya kai sau uku, kafin ta miƙe tayi hanyar waje.

Naila bayanta tabi da kallo tana share hawayebta.
Jakar kuÉ—in da ta zo da shi ta adana tana sakin murmushi.

Layi-layi Kaaka ta bi tana kuka tana cewa;
"Ya ku ƴan uwana mutanen Yankin Tudu ku fito ga jikata Naila ta dawo daga Ƙasar Abyad, ku fito ku ganta Mutanen Yankin Tudu"

Kafin ka ce me, dangin Mahaifin Naila, da mutanen gari daga kowani ɓangare sun cika Gidan. Kowannensu idan ya yi dariya sai dai kaga haƙoransa ya cika masa fuska saboda rama. Maza da mata haka suka cika Gidan Kaka.
Da Naila ya kalli fuskokinsu da yadda suke dariyar da yake nuna irin farin cikin da suke ji sai ta fashe da Kuka.
Suma da yawansu sai suka saka kuka suna zayyanomata labarin irin talaucin da suke ciki.

Tsabar da ta taho da shi a take ya ƙare wa su ma basu samu ba. Bayan kowa ya watse Mahaifiyar Kabeer da ta kasa tafiya ta matso kusa da Kaka, da ƙaramin murya take roƙon ita bata samu ba su taimaka mata, da Naila ta kalleta ta tuna da ɗanta Kabeer ɗaya fita Zakka a ƴaƴansu saboda zafin naima sai ta fashe da kuka, da sauri ta miƙe shiga Ɗakin Kaaka na ɗauko kuɗi ta bata.

A wannan dare kwanan labari Naila sukayi da Kaka cikin kuka mai taɓa zuciya.
Da ƙarfin gwiwar Kaaka dana Yasar Naila ta yanke shawarar ƙin zuwa Gidan su Sufyan idan ya ji haushi ya bata takardarta ta.

★washe gari labarin dawowar Naila da shirye-shiryen shagalin bikin Sufyan da ƙin zuwan Naila gaishe da Mutanen Masarautar Yankin Tudu ya bazu ko ina, har kunnen Hindu mahaifiyar Sufyan da Kakansa Jalal.

Ƙura ba taƙara tashi ba, sai da Naila ta ɗebi dubban mutane Yankin suka shiga Kasuwar Maƙotan Yankinsu abisa shawarar Kaaka suka siyo ɗayyan abinci a farashi mai rahusa. Aka fara rabawa Talakawan Yankin.

A wannan rana sai da hankalin duk wani mai faÉ—a aji a Masarautar Yankin Tudu ya tashi, domin É—abi'ar da Naila ta tsiro da shi É—abi'un Zuri'ar Marigayi Sarki Musa ne. Labari bai tsaya a iya Yakin Tudu ba har kunnen Sarki Hammam, Sufyan da ÆŠayyib da suke can Birnin Abyad suna shirye-shiryen tahowa.

Sufyan kishine ya kamashi, shi kuma Ɗayyib da yake komai nasa a lissafe yake tafiya, a take ya alaƙanta kalan taimakon da Naila ta da mamallakin Companyn Dhahab da ɗansa yake aiki, kenan dole akwai ɓoyayyen dalilin da yasa aka ɗauki Sufyan aiki kai tsaye, saboda ko maƙaho a Yankin Tudu yasan irin taimakon da akace Naila ta yi yasan irin na jinin Marigayi Sarki Musa ne. Domin su ne suke taimako da gumin su, su kuma kawowa mutanen Yankin su cigaba da ƙwaƙwalwar su.

Lokacin da labari ya riskesu su na Airport, don haka suka matsu su iso ayi shagalin biki agama su kawo ƙarshen komai.

A can Yankin Tudu wajensu Naila
Ba bu tsangwama babu nuna waccen nawa ne, wannan ba nawa bane, Naila ta bada umarnin su kasafta abincin a tsakaninsu.

kuka da addu'o'in Tsofaffi, Maza da mata, Matasa, da Yara ne yake ta tashi tare da kabbarorin su ta ko ina.

Maimakon sanya idon da bindiddigin auren Sufyan sai Mutanen Yankin suka mayar da hankali wajen yiwa Naila addu'o'i da fatan nasara mai É—orewa.

A wannan rana Naila ta wuni cikin jindaɗi da soyayya daga ɓangaren Mahaifi harma da ɓangaren Mahaifiyarta da suka samu labari.

Kaf kuÉ—in da Naila ta É—auki shekaru tana bautar yin kitso da wanda Bushra da Yasar suke bata ta tattara ta bayar aka siyi kayan Abinci, sai abinda ba'a rasa ba daya ragemata ta bari a jikinta, tana addu'ar Allah Ya kawo ninkinsu.

Barci mai cike da nutsuwa suka yi ita da Kakaa.

Ranar da su Ɗayyib suka sauka wanda ya yi dai-dai da ranar cin kasuwar Zinare Naila da Mutanen Yankin sukayi shawara sukayi shawarar rushe Gidan Game ɗin Ɗayyib, da suma ƙiris suke jira har da matasan da suka ƙara ganin mutuncinta saboda abincin da rabawa Iyayensu, tsanar Ɗayyib ya yi kane kane a zuciyarsu.

Bayan gama cin Kasuwa kowa ya addana abinda ya samu suka taru suka rushe ƙaton wajen da Ɗayyib ya kewaye da langlanga.

Sannan Mazansu da Matansu sukayi tattaki har ƙofar Gidan Sarki Hammam da saukarsu kenan sukayi ƙorafin basason Gidan Game da Gidan Rawa lalata masu Yanki yake yi!.

Kayan Game ɗin cikin wajen da suka rusa babu wanda ya taɓa ko ɗaya, Matasa majiya ƙarfi ne suka Tattaro suka zuɓe a ƙofar Masarautar Sarki Hammam.

Da yake bikin Sufyan suke burin suyi hankali kwance sai Sarki Hammam ya fito ya basu haƙuri.

Ɗayyib mutuwa ne kawai baiyi ba. Jalal Mahaifinsa da muƙarabansa a ranar suka shirya taro a kan Naila saboda sun samu labarin ita ta kitsa komai, tare da bawa Sufyan umarnin sakinta da gaggawa, da shawarar kama Naila da Kakarta suka fara yankewa sai dai hakan zai tunzura mutanen Yankin da dama can a gajiye suke ayi tashin hankalin da ba sa so, shine suka yanke shawarar Sufyan ya saki Naila.

Hukuncin su Jalal gagarumin rigima ya tayar domin Hindu a take ta nuna Sumaya ba ta yimata ba idan kuma Sufyan ya sakeni sai ta tsinemai.

Sumaya dake lulluɓe cikin mayafi bata fuskanci duk abinda yake faruwa ba, ita da ƴan uwanta sai zare ido sukeyi.

Jalal ne ya daki ƙasa kai tsaye ya ce ƙaryar Hindu ya na so kafin rufuwar mintuna Talatin takarkar Sakin Naila ya isa ga ahalinta.

GIDAN KAKA
Sarki Tsafin Yankin Tudu da su Jalal suka butulcewa saboda ɗaukakar da Sufyan ya samu ne yasa Maza majiya ƙarfi masu ƙarfin tsafi a Jikinsu su yi gadin kaf faɗin kewayen Gidan Kaka saboda Naila.

A ɓangaren Matasan Yankin suma ƙofar Gidan Kaka suka mayar majalisar su har da abin shiffiɗar kwanciyar su saboda tsaron kar a biyoni cikin dare, Ni ma kuma ban gajiyaba wajen ambaton Ubangijin halittu.

NAILA; bayan ta huta suka ƙarayin waya da Yasar ya kuma ƙaramata ƙarfin gwiwar kar ta gajiya nasara na nan tafe In sha Allahu kafin dawowarta.

Da bayin Gidan Sarki Hammam Mata ta ɓangaren Jalal suka isar da saƙon Jalal na sakin Naila a gidan Kaka da rufa ido ɗaya a cikinsu da dama don abinda aka turota da ragowar kenan ta ɗauke wayar Naila.

Su Naila ba su ankara ba sai bayan tafiyarsu.

A daren Ɗayyib ya yi duk wani bincike shida Sufyan da ƙwararren masanin na'ura mai ƙwaƙwalwa a Masarautar amma basu ga alama ɗaya daya haɗa Naila da Ma'aikatar su Sufyan ba. Cikin ɗacin hali Sufyan ya farfasa wayar ya cire layin ya karya.

★washe gari layi-layi fadawan Sarki Hammam suka bi suna gayyatar mutanen Yankin filin wasannin ƙarshen mako don gudanar da shagalin bikin Sufyan.

★
Ranar da ya kama shagalin bikin Sufyan da Sumaya. Sufyan ya yi ado na kece raini duk da ba haka yaso ba Naila ta ɓatamai komai.

Sarakuna daga Yanki-Yanki Æ´an kasuwa da Æ´an siyasa, su aka warewa waje na alfarma har da wajen da GM É—in Sufyan da sukayi waya suna kan hanya zai zauna.

A cikin Dattawan da suka je gudun abinda zai biyo baya har da Mahaifin Kabeer da ya tsufa ya yanƙwane saboda wahala.

Lokacin da taro ya yi taro motocin ÆŠayyin da Sufyan ya sabunta suka tafi taro GM É—in Companyn sarrafa shinkafa ta Dhabah.

Isowarsa Motar da Gm yake ciki da saukarsa daga Mota duk akan idanuwan Mahaifin Kabeer.

Dark blue suit mai nauyin kuɗin gasken daya kwantawa farin fatarsa da kakkaurar jikinsa ya sanya. Gashin kansa dake amsar gyara na kwance luf. Lokacin da ya fara takawa, Mahaifin Kabeer da yunwa tasa ya ranƙwafa ya yanko wajen da aka hanasu ƙetarawa saboda su talakawa ne da gudu. Cikin ihun da ya haɗe da kuka ya ke faɗin;
"Ashe Malik zai cikamin alƙawarin da ya ɗaukarmin! sai dai ya shammceni, da na san irin wannan alfaharin yake nufi da na tattara masa dukka Ƴayana ya tafi da su.
kabeer ÆŠana ashe da gaske zaka dawo garemu bayan mun cire rai, lallai Allah Abun godiya ne."

Cak Kabeer ya tsaya haɗe da buɗe dukka hannayensa da ke fitar da wani irin ƙamshi. Cikin soyayyar Uba da Ɗa kabeer ya rungume Mahaifinsa.

Babu wanda bai miƙe ba, babu kuma wanda bai razana ba daga waɗanda suka san Kabeer har waɗan da basu sanshi ba.

Da wani irin fushi Ɗayyib yake taka ƙasa kamar zai hudasa, gaban Sufyan da shi ma yake tsaye kamar mutum mutumi ya tsaya ya na kai hannunsa saitin ƙugun wandonsa.

Da zafin zuciyar azabar dake neman halakasa tashi É—aya ya ce;
" Lallai ban haifo É—a ba sai soko kaicona! Nasan Malik ya É—auke Kabeer ya inganta masa rayuwarsa da turomana shi a irin wannan lokacin domin ya nuna mana iyakar mu, kuma ya yi nasara.
Amma idan har Malik zai mallaki dukiyar da zai sauya rayuwar Kabeer, Kabeer kuma ya sauya taka kai kuma ka sauya namu to tabbas su na da Ubangida, Uban gidan da ya kamata ace kasani tuntuni, amma sai gashi ko Kabeer ɗin ma baka sani ba Balle kuma Ubangidan su, daga yanzu har zuwa ajalinka ba zan taɓa yafe maka ba Sufyan har sai ka gano min wanene DHAHAB 🔥?????
Ɗayyib ya ƙarasa faɗa yana yankar ƙuncin Sufyan da wuƙar da ya zaro a ƙugunsa, a take jinin kumatun Sufyan ya yi tsartuwar da ya fallatsa har saman fuskar Ɗayyib....✍🏻

Barka da Jumu'a.
[7/27, 9:52 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥


NAFISA ALIYU SASAAL


Page 21


Sufyan kansa ya sunkuyar ƙasa, raɗaɗin yankar da Mahaifinsa ya yi mai a kunci da yankar da Kabeer ya yi masa a zuci na naiman zautar da shi. Shi da kansa kunyar kansa yake ji, baƙin ciki mai girma na da ɗa mamaye zuciyarsa.

Ɗayyib da ya juya ya kalli irin gyaran da Masautar Yankin ya samu da dukiyar da kai tsaye za'a kirasa da na Malik da irin manyan mutanen da ya ɓata dukiya ya gayyata saboda Kabeer kawai, sai ya ƙara juyowa. Da wani irin fushin mai girma yake yankar Sufyan ta ko ina yana maimaita
"Ko Marigayi Sarki Musa zai dawo duniya a raye ba zan yimasa irin wannan hidimar ba na rantse da Sarki Allah! Sufyan ka cuceni! Ka cuceni!!"

Daƙyar aka ƙwace Sufyan da ya yi kacha-kacha da jini a hannun Ɗayyib da ya zama kamar Mahaukaci.

Mutanen Jalal ne suka ja ÆŠayyib cikin Gida, shi kuma Sufyan aka wuce da shi Asibiti yana ihun azaba kafin ya sume.

Sarki Hammam a take ya bayarda umarnin a rufe iyakar Yankin Tudu, kuma a turo masa Kabeer cikin Iyayensa da gaggawa.

Da ƙananun gulmammaki taron shagalin bikin Sufyan ya watse maimakon yabo da ya ci burin yasamu a wajen Mutane.

Kamar yadda Sarki Hammam ya bada umarni haka akayi sai dai babu Kabeer babu Iyayensa. Da gaggawa Sarki Hammam ya ƙara bayarda umarnin abi duk Yankin da yayyen Kabeer mata suke aure a kamo su. Sai dai suma duk basanan acewar Surukansu sun bar Gida da sunan zuwa shagalin bikin Ɗan shugaban kasuwar zinaren Yankinsu tare da rakiyar Mazajen su da Ƴaƴan su.
Babu inda ba su bincika ba amma babu Kabeer babu ahalinsa. Dagaske dai Kabeer ya gudu da dukka ahalinsa.

Ɗayyib da labarin ɓacewar Kabeer da ahalinsa ya riskesa Ihu ya kurma haɗe da ɗaura ɗamarar binciko Kabeer da ahalinsa a duk inda suke. Fadawan Sarki Hammam majiya ƙarfi Jalal ya bawa umarnin tare Ɗayyib daga barin Masarautar, ya na fizgewa suna tarosa, daƙyar suka danneshi aka nemo likita ya yi mai allurar barci.

WAIWAYE
Da Malik ya ɗauko Kabeer daga gidansu a sirrince ya fitar da shi iyakar Yankin Tudu sukabi Jirgin samansu zuwa ƙasar Abyad.
Daga wannan rana Malik baiyi ƙasa a gwiwa ba sai da Kabeer ya zama abinda zai sosai zuciyar Ɗayyib da shi. Ya na shirin ɗauko Iyayen Kabeer, bikin Sufyan ya Kunno Kai, don haka suka turasa bayan sun shirya yadda zai taho da Iyayensa da zarar taro ya hargitse.

A zahirin gaskiya Kabeer shugaban Sufyan ne a wajen aiki amma ba shi ne GM ba, Uzair da Naila ta taɓa ganin mai tsananin kama da Salman ne GM.

DAWOWAR LABARI
Lokacin da ÆŠayyib ya fara yiwa Sufyan magana, Kabeer ya sulale da Mahaifansa har da Æ´an uwansa suka bar Yankin, dama kuma tuni motocin É—aukar su Kabeer yana Yankin amma saboda taron mutane yasa babu wanda ya ankara.

NAILA;

ɗaukemata waya da Bayin Gidan Sarki Hammam sukayi ya zama iyaka tsakaninta da Yasar, saboda tanan kawai yake iya sanin halin da take ciki. Lamarin ya sosa zuciyarta tare da ɗaga mata hankali sama da Sakin da Sufyan ya yi mata, domin ko bai saketa ba, dama tayi alƙawarin bazata ƙara iya rayuwar auren rashin ƴanci da shi ba.
Damuwar da ta shiga akan hanyar da zan ƙara samun Yasar ba ƙaramin tashin hankalin Kaka ya yi ba, cikin ƙarfin halin ɓoye ta ta damuwar take jaddamata ko da karo-karon ne zasu haɗamata kuɗin Mota ta koma Makaranta ita da ƴan uwan Mahaifinta dana Mahaifiyarta har ma da mutanen Yankin.

Wannan ƙarfin gwiwa da Kaka ta bawa Naila sai ya gusar da duk wani damuwa da fargaba da ke danƙare a cikin zuciyarta na fara walwala kamar kowa.

A haka suka kwashe kwanaki uku cikin gidajensu, ba tare da dogon zirga-zirga ba, abisa umarnin Sarki Hammam.

SUFYAN; yasha azaba irin azabar da bai san akwai irinsa ba, kullum cikin kuka yake tunda ya farfaÉ—o daga duniyar azabar da Mahaifinsa ya kaisa.
Sumaya ta na gefe itama tasha kuka idanuwanta duk sun koɗe, wahalar da bata taɓa tunanin zatasha ba har su gama rayuwar Aurensu da Sufyan shi take sha, idan zai yi fitsari da Toilet duk ita take taimaka mai gashi da raki kuma ita dama can ba saba aikin wahala ta yi ba.
Ga shi
Bayin ma da aka bari Maza ne masu gadinsu balle su taimaka mata.

Ƴan uwanta suma gaba ɗaya sun matsu su koma Birnin Abyad, danasanin rako Sumaya Yankin Tudu na damun zuciyarsu.

A ɓangaren Hindu bayan barinta Yankin Tudu zuwa Yankinsu, kai tsaye wajen Malaman dubanta ta wuce.

Tabbacin suka bata na; nasarar Sufyan da isarsa tsakiyar Babban Birnin Abyad da kuma samun É—aukakarsa mai girman gaske ya na tare da Naila, babu abinda ya sauya.

Amma ita da Sufyan sun karya dokar da aka shimfiɗa musu tun farko. Na farko zaman Sufyan a Birnin Abyad saɓanin Babban Birnin Abyad da aka sharɗan ta musu, na biyu gaggawar Sufyan na yin Soyayya da Sumaya har da aurenta. Na uku sakin Naila da ya yi, shi ya ƙara wargaza komai.
Da rawar murya kuka Hindu take roƙon asama mata wata mafitar tun da wannan ya lalace.

Sihirin da za'a shayar da Naila ya bata na tsahon kwanaki uku ba tare da rarrabewar kwanaki ba. Zata dawwama a ciwon da babu magani, bayan tasha wahala Sufyan zai je da sunan taimakonta.

Idan har Iyayenta sun amincewa Sufyan ya samu damar ɗaukarta zuwa Masarautar su to ta dawo za'a bata maganin da zai karyar sihirin da sukayimata ta samu sauƙi, daga nan sabon shirin tunkurarsu Babban Birnin Abyad zai kankama da zafin da dole nasara ta tabbata. (Anya wannan nasarar zata tabbata🤔)

Da wannan ƙwarin gwiwar Hindu ta fara shirye-shiryen dawowa Yankin Tudu, bayan tayi kwanakin da ta ɗibarwa kanta.


ÆŠAYYIB
Har sati ɗaya ya shuɗe idanuwan Ɗayyib ba su washe ba, baya iya magana saboda baƙin cikin da suka yi mai karo. Ko Asibiti yakasa zuwa duba Sufyan, itama Hindu tattare lamarinta ya yi ya watsar, burinsa ya samo ina Kabeer da Malik su ke, su bashi labarin wanene Uban gidansu.
Babban Malamin duba da suka musanya bayan faɗarsu da Sarkin Tsafin Yankin Tudu Jalal ya gayyato tun daga wata ƙasar domin fayyace musu abinda Ubangiji ne Masani akai.

"Ina su Malik da Kabeer suke? A wacce duniya suke rayuwa? Shin dagaske Kabeer shine Uban gidan Sufyan. Wanene ko wacece asalin Uban gidansu? WaÉ—annan tambayoyin shi su ÆŠayyib suke neman haske a kansu ido rufe.

Bayan sun gama korowa Malamin duba bayani.

A duban da ya yi
Abu ukun da suka tambaya bayyanannu ne amma na ukun saninsa sai Allah.

Na farko inda Malik da Kabeer suke da duniyar da suke rayuwa, na biyu kuma shin dagaske Kabeer shine Uban gidan Sufyan,

Na ukun da ya kasa gonowa shine sanin asalin Uban gidan su.

Amma ya kuÉ—urce a ransa bazai gayamusu ba sai abinda zai faranta ransu su biyasa kuÉ—i mai tsoka, don haka ya gyara zama ya yace;

"Kabeer da Malik suna wani gari ne Daf da shiga Babban Birnin Abyad, kuma suna rayuwa ne kusa da Company da Sufyan yake aiki ba a cikin asalin ƙwaryar Babban Birnin Abyad ba.

Kabeer kuma ba shine Uban gidan Sufyan ba, a yadda dubana ya nunamin Kabeer ba shi baya aiki ma da Ma'akatar su Sufyan kawai rufa ido ya yi muku. Asalin Ubangidan Malik kuma Macece wacce ta taɓa zama a nan Yankin Tudu amma nakasa gano asalin wacece"

Da sauri Ɗayyib ya miƙe yana dariya, cikin yaƙini ya ce idan ba Nanaah Faɗima ba ( kakar Sulaim matar Ubaidu) to Aysha ce( matar Abduh Dhahab Mahaifiyar Sulaim). Da sauri malamin duba ya gyaɗa kai alamar gaskiya ne.

Kuɗi masu nauyin dake bayyana jindaɗinsu suka sauke mai. Da murmushin samun nasarar duƙunƙune sun da ya yi, ya saɓa jakarsa ta zallar fata ya yi musu sallama. A zahirin gaskiya Kabeer da Malik tabbas a kusa da Company Dhahab suke rayuwa, amma da gaske Kabeer shine Uban gidan Sufyan yasan idan ya faɗi gaskiya a matsayinsa na babban malamin duban da suka ɗauko tun daga wata nahiyar ba zai samu kuɗi mai tsoka ba, batun Macece ko Namiji ne asalin Uban gidan su Malik ba shi da sanin komai akai, shima ya faɗa ne don ya faranta musu shima su faranta mai. Da mugun murmushi malamin duba ya hau motar da zai sadashi da iyakar Yankin Tudu da tumulin kuɗinsa a jaka.

Da gaggawa Ɗayyib da bai taɓa zuwa duba Sufyan ba ya ɗauki hanyar Asibiti, ɗauke da wayar Sufyan da ya jima a kashe.

Bai damu da halin da Sufyan yake ciki ba, ko yaya yanayin jikinsa yake ya naimi waje ya zauna.
Cikin sanyi murya Sufyan ya gaisheshi. Da sakin fuska ya amsa yana yi mai yaya jiki, ko kallon inda Sumaya take baiyi ba, balle ya yi mata godiyar hidimar da takeyi da É—ansu, sai ta basu guri zasuyi magana da ya faÉ—a a kausashe.
Jiki a sanyaye Sumaya ta bar Ɗakin nadamar auren Sufyan na mamaye ruhinta, tausayin Naila da ta fita shaƙar takaici da rashin samun rayuwar Ƴanci na tsarga mata, "ashe haka Naila take ji? Wallah na cuci kaina kaicona!" Ta faɗa ƙasa-ƙasa cikin kuka.

Bayan fitar Sumaya Ɗayyib ya mayar da kansa kan Sufyan. Wayar Sufyan ɗin ya miƙamai.
Babu wasa a fuskar ÆŠayyib kamar ba Mahaifinsa daya sani a baya ba.

Jiki a sanyaye Sufyan ya kunna ya ajjiye yana jiran umarnin da zai biyo baya.

"A baya ina lallashinka domin ka yi min biyayya akan abinda kai ne zaka samu cigaba ba ni ba, amma ka bijiremin, to a wannan karon ba cigabanka bane kai kaɗai cigabanmu baki ɗaya, mun gayyato malami daga wani Birni, ya kuma shaida mana Kabeer ba shine Uban gidan ka ba, rufa ido ya yi mana, ba wai don ban yarda da shi ba, sai don na ƙara tabbatarwa nakeson ka kira wanda ya miƙa katin gayyatar bikinka wajen GM ɗinku ka ji dagaske ne ko a'a"

Sufyan yaso ya musa, amma tuna irin yankar da ya sha yasa ya fara lalubo number jikinsa yana rawa.

Bugun farko aka ɗaga da Muryar jimamin da ya nuna andaɗe ana naiman mutum ba'a samesa ba. Bayan sun gaisa da hanzari Baturen yake tambayar lafiya, bai dawo aiki ba ko fushi yake yi GM bai samu halartar taron shagalin bikinsa ba, ya yi haƙuri uzuri ne ya tareshi, ga ayyuka ta ko ina a office amma ba bu shi, don Allah ya dawo.

Daga Sufyan har Ɗayyib ajiyar zuciya suka sauke mai ƙarfi kafin Ɗayyib ya tashi ya rungume Sufyan cikin kukan farin ciki ya ce;

"ɗana Sufyan ina mai neman afuwarka, sai dai banason wannan damar ya zama abin sakankacewa garemu, inaso ya zama fitilar haska mana asalin wacece ta ƙara dawo da Dhahab a tsakanin Nanaah Faɗima da Aysha" Sufyan da yake son tambayar su wanene Faɗima da Aysha shiru ya yi tuna Mahaifinsa zai iya tuhumar mai yasa bai sansu ba.

A haka ÆŠayyib ya share hours ya bar Sumaya zaune a waje ba tare da damuwar komai ba. A wannan yanayin Hindu ta iso Asibitin kallon inda Sumaya take batayi ba balle ta amsa gaisuwarta.

A wannan karon ma É—ari bisa É—ari ÆŠayyib ya amince da batun da Hindu ta zo dashi, tare da bawa Sufyan umarnin sakin Sumaya da zarar sun koma Birnin Abyad ya ajjiye maganar Soyayya ya fuskanci gobensa. Sai dai dole sai sunyi taro na musamman a kan yadda za'a shayar da Naila sihirin da Hindu ta zo da shi.

Shi dai Sufyan kai kawai yake É—aga musu saboda tsoron yin magana ma yake yi.

Tun a baya kowa yasan mutanen Yankin Tudu da son kansu da tsananin butulci, sai dai talauci da tsananin rayuwa ya sa suka sauya zuwa mutanen ƙwarai, amma duk da haka ba'a rasa nono a ruga kuma baza'a taɓa taruwa a zama ɗaya.


NAILA
Sartaj ya na ɗaya daga cikin matasan da suke yawan shigowa Gidan Kaka, kuma yana daga cikin waɗanda suka dinga bata kariya, yawan shigowarsa ya haifar da shaƙuwa a tsakaninsu har yakan ci abinci Gidansu.

Da ƙwaɗayin asalin jinin Yankin Tudu da butulcinsu da bai gama barin jinin Sartaj ba su Ɗayyib su ka samu dama sukayi amfani da shi. Sai dai shure-shure baya hana mutuwa....✍🏻

Na gode da Addu'o'inku Allah Ya bar mu tare Ya kuma bar zumunci.
[7/28, 9:46 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥


NAFISA ALIYU SASAAL


Page 22

Kuɗi masu nauyi a hannu da rashin albarka wajen sauke buƙatu Jalal da kansa ya biya Sartaj, bayan ya siyar da yardar da amince dake tsakaninsa da su Naila.

Da tattacen kayan marmari Sartaj ya fara amfani. Ya na zaune suna hira da Naila har ta shanye. A kwana na biyu da yankakkun kayan marmari ma su kyan gani a ido ya yi amfani. A kwana na ukun da ya kasance na ƙarshe da abincin Gidan Kaka ya yi amfani.

SUFYAN; Sufyan bai ƙarasa warkewa ba suka tattara suka koma Birnin Abyad da sunan idan sun isa ya miƙawa Sumaya takardar ta kafin ya wuce Babban Birnin Abyad bakin aikinsa.

NAILA;
Labarin tafiyar Sufyan bai zama abin damuwa a gareta ba, domin abinda kake so shi kakeyiwa kishi.

A hankali ta fara ramewa ƙasusuwan jikinta suka fara bayyana kansu kamar ba ta cin abinci, kasalar rashin son yin Sallah a kan lokaci da ƙinyi azkhar na neman zamemata jiki.
A cikin kwana biyar tayi wani irin ramar da ya tsoratar da kowa.
Kaka bata wahalar da kanta wajen kai Nsila Asibiti ba, tunda tasan su wanene Iyayen Sufyan. Malamin da ya taimaka mata a waccen lokacin da Hindu ta ciyar da ita Tufa mai É—auke da sihiri ta nufa.

Bai buƙaci a kawo Naila ba da kansa ya zo. Ya na ganinta ya tabbatarwa da Kaka abinda take zargi, sai dai sihirin da aka yiwa Naila ba irin nata bane, samun maganinsa abune mai matuƙar wahala domin a wajen wani Malami da ke gabashin Yankin Tudu za'a iya samu maganin karya Sihirin.

Cikin kuka Kaka take faɗin; "wanene ya zaɓi Duniya akan lahira?, wanene ya zaɓi shayar da marainiyar Allah sihiri irin wannan, Allah bamu da kowa sai Kai!"

Babu wanda bai tausayawa su Naila ba.

Cikin fusata matasan Yankin suka nufi da suka samu labari suka nufi Gidan Sarkin tsafin Yankin Tudu ya duba musu wanene ya shayar da Naila Sihiri?..

A take kuwa yana dubawa ya gano Sartaj ne.
Gangamin Matasan Yankin Tudu ne sukayiwa Gidansu Sartaj zobe, Sartaj ba shi da Uba sai Uwa itama ta fara tsufa.
Cikin alhini da fargaba take sanar da su yanzunan Sartaj ya ce mata zaije Fadar Sarki Hammam gurin Mai girma Jalal wai yana naimansa.

Bayaninta ya ƙara fusatar da Matasan tare da ƙara tabbatar da maganar Sarkin Tsafi, don haka suka koma Gidajensu kowa ya ɗebo makamai sai fadar Sarki Hammam.

A fito musu da Sartaj su yankemai hukunci dai-dai da abinda da ya aikata. Suke ta nanatawa bayan isarsu Harabar gidan Sarki Hammam.

Ihun su da maganganunsu ma su khaushi ne yasa Sarki Hammam umartar fadawansa su lallashesu su kuma sanar da su Sarkin Tsafin Yankin Tudu ba gaskiya ya faɗa ba, so yakeyi ya hanasu zaman lafiya tunda ya ci amanar Masarautarsu ta koresa shiyasa su ma yake so ya tunzura su. Kuma lallai ya na bada umarnin kar wanda ya taɓa lafiyar Sartaj idan ba haka ba zai fuskanci hukunci mai tsanani.

Duk da an sanar da Matasan Yankin Tudu wannan jawabi na Sarki Hammam basu motsa ba, har sai da Sarki Hammam ya fito da kanshi ya taushesu da kalamai ma su taushi tare da tabbatar musu da ƙarya Sarkin Tsafin Yankin Tudu yake yi, Sartaj da ya ke na hannun damar Naila tayaya zai ciyar da ita sihiri?

Ba don sun gamsu ba sai don bin umarnin Sarki Hammam wajibi ne a garesu suka tattara suka dawo Gida.

Da labarin abinda ya faru ya isa wajen Kaka ba tace komai ba sai kuka da takeyi tsoron mutane da rashin yarda da su na ƙara kamata.

Bayan zuwa Matasa wajen Sarki Tsafi, da kansa yazo duba Naila har ya faÉ—i wasu maganganun da Kaka tayi watsi da su nan take.

★washe gari Matasan Yankin suka yanke shawarar fita naimo Malamin da zai yiwa Naila magani a Yankin gabashin da ake ce yake ko kuma ya basu maganin su kawomata.

Kaka da tana dama da ta hanasu domin ko sun karɓo bazata iya yiwa Naila amfani da shi ba, saboda bata yarda da kowa ba.

Matasan Yankin mu su Goma sha uku, sun kwashe kwanaki huɗu a gabashin Yankin Tudu amma ba su samu Malamin ba, sai maganin da suka ƙarbo daga takwarorinsa.

Da hannu bibbiyu Kaka ta karɓi maganin su, tare da tarin godiya mai yawa. Sai dai tana karɓa ta zubashi a shara.

Sartaj ya fito yana rayuwarsa kamar kowa amma bayayin nisa da Gida a wayonsa kar wani ya yi mai wani mugun abu. Hanyar Gidan Kaka tuni ya zama haramiya a garesa.

Cikin watanni biyu Naila ta ƙanƙance ta tsotse ta dawo kamar ba ita ba idan Kaka ta kalleta sai ta fashe da Kuka tana cewa;
"Ba sai mun nemo mai warware mana sihiri ba, mai warware mana yana tare da mu, kuma In Shaa Allahu da ƙarfin mulkinsa sai kinga har jikokinki Naila"

idan Kaka ta faɗi haka Naila fuskarta da ta dawo ƴar ƙarama ta yamushe take kawarwa gefe tayi kukan da batasam iyakarsa ba.

Kaka bata gajiyawa wajen kaiwa Allah kukansu, dare da rana, Safiya da yammaci. Jinkirin samun sauƙin Naila bai sa Kaka ta karaya ba.

Taimako da ake basu ne ya farayin ƙasa, abincin ci ya fara gagararsu, yunwar da ya yi sauƙi a Yankin Tudu ya dawo sabo fil, amma duk da haka da zarar sun ci kasuwar Tukwanen Zinare Matasan Yankin zasu haɗowa Kaka kuɗi, haka ƴan uwan Mahaifin Naila, a wasu lokutan har da Kakanninta na wajen uwa.

Shawarar dawo da sana'ar Mahaifiyar Naila na ƙera kayan wasan Yara na lakar ƙasa Kaka ta yanke. Drivern da yake fita iyakar Yankin Tudu ta roƙi alfarma ya dinga kaita bakin tasha tana siyarwa idan tayi ciniki ta biyashi, tunda kullum sai yaje.

Kai tsaye ya nuna mata kyauta zai dinga kaita ya dawo da ita amma tana ganin barin Naila a gida ba zai zama matsala ba, mai zai hana ta dinga lulluɓeta suna tafiya tare? Da sauri Kaka ta amince domin itama fargabarta kenan yadda zata bar Naila ita kaɗai a Gida.

Ba ta naimi shawarar kowa ba, kwana biyu bayannan suka fara bin Driver zuwa Iyakar Yankin Tudu.

A gefe Naila take rakuɓewa, Kaka kuma matafiya take bi tana tallata musu su zo su siya kayan lakar da ta ƙera Fisabilillah. Cikin hukuncin Ubangiji, sai tausayin Kaka da tausayin yadda Naila ta koma ya sa mutane suka yi ta siya har da masu ba su kyautar kuɗi.

kullum ba sa dawowa Gida da rogawa sai ya ƙare. kuma Driver bai taɓa karɓar ko sisinsu ba.
Duk wannan wahalar da Kaka take sha haka take ƙara raba dare a zaune tana kaiwa Allah kuka, domin bata iya tsayuwa saboda shekaru da wahalar da take sha.

Ƴan uwan Mahaifin Naila sun kawo ƙorafin ta dinga barin Naila a Gida, amma ta nuna sam bata yarda ba, tunda suma ba zama sukeyi ba kowa nema yake fita, matansu kuma ba lallai su kula da ita ba.

A lokacin da suka cika sati shida da fara fita Iyakar Yankin Tudu, jirginsu Sufyan ya sauka. Ya dawo Yankin Tudu, Motocin Mahaifinsa ne suka je tarbarsa amma da yake gulmar halin da su Naila suke ciki ya je mai tun kafin ya iso, sai ya gwada zuwa inda suke zama, don kawai yayimusu izgilanci kafin ya wuce.

Lokacin da ya iso ɗan rumfar da suke zama Kaka tana can tallatawa matafiya kayansu Naila kuma tana rakuɓe da ruwan shan da Kaka ta bata a gefenta. Dariyarsa kawai Naila ta ji a kanta.
Kafin ya fara magana Cikin izgilanci;

"Naila korarriyar Ɗalibar da talauci ya hana iyayenta naima mata magani ta warke ta koma Makaranta, ba kina ganin zaluntarki mukayi ba, lokacin da muka yi miki gata muka kaiki Birnin Abyad muka baki makwanci. Amma saboda butulci don kawai ina karɓar kuɗin kitson da kike yi kika zaɓi tozartani, yanzu gashi Ni da ke waye yake ji a jikinsa, kalleki dan Allah."
Naila bata É—ago ba sai yawun da take ta tofawa ruwan hannuna kamar zautacciya.

Farar fuskarsa da ya ke matuƙar ji dashi ya shafa dai-dai satin Yankar da Ɗayyib ya yi masa da bai gama bajewa ba ya ƙara ce wa;
"Banso haukarki tasa bakya gane maganganuna ba, amma wannan yawun da kike tofarwa da adanawa kikayi wataƙila kya rage wannan yamutsewar da kikay..." Saukar ruwan har cikin bakinsa yasa ya kurma ihu haɗe da tsalle kamar ƙaramin Yaro kafin ka ce kwabo tuni Matafiya sun cika wajen, suna kallon Sufyan da yake ihun "Saliva! Saliva!!" Haɗe da waftar ruwan hannun mutane yana wanke fuskarsa da bakinsa.

Gudun abun kunya ba tare da bin ba'asi ba Fadawan Sarki Hammam suka jashi Mota. Abinda Sufyan bai sani ba maganar Naila ta koma kamar ta Æ´an yara ba kowane yake Fuskantar ta ba, ko azabar ciwon ya tashi sai dai ta yi ta kuka bata iya bayani yadda za'a fuskanceta. Shiyasa Kaka bata wahalar da kanta wajen tambayar abinda ya faru ba ta koma wajen tallata kayanta, suma mutanen da suka taru kowa ya kama gabansa.

A hanyar su ta dawowa Naila tke yiwa Kaka kwatancen abinda ya faru. Dariyar da rabonta da yin irinsa har ta manta Kaka ta ƙyalƙyale da shi, har suka isa gida lokaci zuwa lokaci sai ta saki dariya.

A wannan dare Naila tasha azaba irin azabar da batasan yadda zata misaltashi ba, da taimakon addu'o'in da Kaka take tofamata barcin ya ɗauketa. Kafin wayewar gari ta ƙara fita hayyacinta, babu wanda hankalinsa bai tashi ba.

SUFYAN; har ya suka isa gida bai sanar da Fadawa abinda ya faru ba suma kuma ba su tambayesa ba sai sannu da suke ta jeromai.

Ya yi wanka ya fi sau biyar haka bakinsa ya wanke yafi a ƙirga. Da daddare bayan Sallar isha suka ɗauki hanyar Yankinsu Hindu Mahaifiyarsa shi da da ita.

A daren Malaman Hindu Suka turo jinnun da zasu matsawa Naila da zarar Sufyan ya zo da buƙatar komawarta tare da albishir ɗin samo Malamin gabashin da suke nema Su Kaka za su amince a mayar da aurensu.

Sufyan aka bawa maganin da Naila zata sha sihirin ya karye ya zura a aljihun bayan wandonsa.

Gaba ɗaya sai ya matsu gari ya yi haske domin a daren suka ƙara dawowa Yankin Tudu.

Da Safe ko wanka bai yi ba balle ya karyawa ya nufo Gidan Kaka da sunan duba jikin Naila kamar yadda suka tsara a daren bayan dawowarsu kafin zuwan su ÆŠayyib. Babu wanda ya rakosa, fuskarsa a tsamke alamun dai ba'a son ransa zai zo ba.
Sallama ya yi Kaka da batasan shi ba ne ta basa izinin shigowa.

A tsakar gida ya samu Kaka ƙannen Mahaifin Naila su na ɗaki tare da ita kowa ya na tofamata duk addu'ar da ta zo bakinsa.

Kaka tana ganinsa ta dakata daga hura wutar da takeyi. Cikin ladabi kamar gaske ya tsugunna yana gaisheta. Kafin ya ɗago Kaka ta rarumo ƙaton iccen da ya ke ci da wuta ta nufesa. Sufyan ya na hangota ya yunƙura ya miƙe a guje, garin wannan yunƙurawa Maganin bayan aljihunsa da aka basa tun daren jiya baiyi wanka ba kuma bai cire kayan ba, dama kuma aljihun bawani zurfi ne da shi ba ya faɗo ƙasa ba tare da ya ankara ba.

Ƙur Kaka take kallon magananin, kafin ta yi Bismillah ta na yunƙurin kai hannunta.

Muryar mutum taji a bayanta.....✍🏻
[7/29, 10:01 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥


NAFISA ALIYU SASAAL


Page 23


Da hanzari Kaka ta ɗauke ƙullin maganin ta wurgashi kwanon gefenta.

Yayyan Mahaifin Naila ne suke yunƙurin fitowa. Sallama su kayi mata, tare da alƙawarin kawo wani malamin ya ƙara duba jikin Naila. Su na fita Kaka ta sauke ajiyar zuciya, ba ta koma ɗakin ba tasa mayafi ta lalluɓe jikinta sai gidan Mallam.

Mallam
Juya maganin yake yi a hannunsa fuskarsa da yalwataccen murmushi ya ce "Tabbas! Allah ba Ya barci, sun biyota har gida sun shayar da ita sihiri, Allah kuma Ya ƙaddara su zasu ƙara biyota gida da makarin sihirin." Kaka da ke ta zare ido alamun bata fahimta ba domin ta ɗauka wani bala'in Sufyan ya ƙara kawo musu. Dalla-dalla Mallam ya yi mata bayani.
Ko
Cikin kuka Kaka takai goshinta ƙasa tana yiwa Allah godiya.

Sai dai wani hanzari ba gudu ba, shayar da Naila maganin a Yankin Tudu zai dawo da hannun agogo baya, domin da zarar sun ga ta warke zasu ɓullo ta wata hanyar, mai zai hana tunda Naila tana da matsugunin haya a Birnin Abyad da kuɗinsa bai ƙareba tunda Bushra kuɗin shekaru uku ta biya kamar yadda Naila ta faɗa, Kaka ta bi can suyi jinyar tare.

Kaka wani irin kallo take yiwa Mallam fuskarta ɗauke da murmushi, kafin ta fashe da kuka domin ta rasa abun faɗa, bata taɓa kawo irin wannan shawarar a cikin zuciyarta ba balle ta samu mafitarsa a zahiri sai gashi Mallam ya haska mata hanya. Ta na godiya tana kuka.

Bayan tasha kuka sai ta ƙara naiman shawararsa akan yadda zasu tara kuɗin motar zuwa Birnin Abyad.

Kaka da murnar da ta danne a cikin zuciyarta ta dawo Gida, cikin jakar da take adana muhimman abubuwa ta anada maganin makarin sihirin jikin Naila.

Kaka har Yankinsu Mahaifiyar Naila ta yi tattaki ta kai mu su koken ance akwai malami a Birnin Abyad da zaiyiwa Naila magani ta warke kuma ita bata da halin da zasu iya tafiya tare, su taimaka mata da abinda suke da shi.

Kakan Naila mutum ne mai jama'a, don haka kafin tafiyar Kaka ya shiga layi-layi yana roƙon a taimaka mai za'a kai jikarsa ƴar gidan marigayiya Birnin Abyad neman magani kuma basu da hali a taimaka. Kafin rufuwar hour uku sai ga kuɗi masu yawa sun taru. Kakannin Naila ba su cire ko sisi ba suka bawa Kaka kuɗin tare da alƙawarin kowawa Naila ziyara kafin su wuce.

Kaka ɓoye kuɗin ta yi ta tunkarin yayyan Mahaifin Naila bayan ta dawo, suma ɗari bisa ɗari suka bayarda da goyon bayansu, saboda samun lafiyar Naila ta koma bakin karatunta shine burinsu domin daga gareta suke sa ran samun canji. Suma layi-layi suka bi suna shela.

A ranar dai ba'a samu waÉ—anda suka bayar da kuÉ—i ba, amma washe gari bayan sun ci Kasuwar Tukwanen Zinare suka dinga kawo kuÉ—i, kafin kace me kuÉ—in zuwa Birnin Abyad har da na cin abinci da extra sun haÉ—u.

Su ma Yayyen Mahaifin Naila tasu gudummawar suka kawo, tare da tattaunawa sirri da Kaka, akan idan Naila ta warke kar su dawo, su yi zamansu a can ta dinga kula da Naila, tunda ta iya riƙe Sufyan har da taimakon Mahaifansa da sana'ar kitsonta to suma zasu samu ingantacciyar rayuwa a chan, za su ƙara taro wasu kuɗin da zasu dinga cin abinci kafin jikin Naila ya ƙarasa warwarewa.

Kaka tana kuka tana godiya suma kukan suke yi suna nuna mata cigaban Naila shine burinsu.

Bayan komai ya lafa Kaka ta koma gidan Mallam domin yimasa godiya akan shawarar da ya ba ta. Wa su addu'o'in yaƙara bata, domin yasan duk daran daɗewa su Jalal za su samu labari warkewar Naila, duk da ba lallai Sufyan ya ba su labarin yardar da maganin da ya yi ba.

SUFYAN; bayan ya fito daga gidan Kaka daidaita tafiyarsa ya yi kamar komai bai faru ba. Bayan ya kai gida ɓangarensa ya wuce ya yi wanka ya yi Breakfast dukka ransa ba daɗi da abinda Kaka tayi mai lokaci zuwa lokaci sai ya saki tsaki, a haka ya koma barci Bayan ya yi wayar sirri da Sumaya.

WAIWAYE
Sufyan lokacin da ya bar Yankin Tudu da Sumaya abisa umarnin Mahaifansa na idan sunje Birnin Abyad ya saketa, su na isa Birnin Abyad maimakon ya cika umarninu kai tsaye masauki ya wuce da Sumaya Æ´an uwanta kuma suka wuce Gida.

Bayan sun nutsu sunci abinci sunyi wanka da Maganganu ma su daÉ—i yake ta lallashinta tare da nunamata duk wasu abubuwa da suke faruwa akwai dalili ba wai laifin Mahaifansa ba ne har da ce mata;

"Mahaifina mutumin ƙwarai ne mai sauƙin kai, amma rashin fahimta da butulcin mutanen Yankina yasa suke ganinsa kamar azzalumin da ya hana Yankinsu cigaba. Mahaifiyata Macece mafaɗaciya amma da zarar kun saba ta sauko daga fushin sakin Naila da na yi zata fara sonki, fushinta na wani lokaci ne, kuma Ni bazan taɓa son Naila ba, saboda mutumin da na fi tsana a rayuwarta take so har yanzu, da hotonsa take yawo, kuma akansa ta zaɓi bijiremin. Saboda haka nake roƙonki Sumaya ki kwantar da hankalinki ki bani haɗin kai"

A kaf maganganunsa ba bu wanda Sumaya ta fahimta tunda ya ambaci ba ya son Naila ne saboda tana yawo da hoton maƙiyinsa. Cikin kasa danne kishin Naila da ya yunƙuromata ta ce;
"Kenan da ba don tanason wanda ka tsana ba, ka na sonta kenan? Dama can itace bata sonka kakeyimin ƙarya? Sufyan banajin aurenmu zai kai labari saboda kowa naka ba ya sona, hatta Mahaifinka ƙiri-ƙiri na hango tsanata a cikin idanunsa. Tun kafin komai na mu yayi nisa kawai ka sauwaƙemin."

Sufyan murmushi ya saki yana kallonta, tayaya zai sha dukka wannan Yankar daga mahaifinsa kuma ya ɓata shekaru yana kashe mata kuɗinsa da na Naila ta ce haka kawai zata suɓucemai shi ba zai moreta ba? Su kansu Mahaifansa da zai bayyana musu bautar da ya yi mata da basu ba shi umarnin sakinta ba. Sai da ya numfasa sannan ya fara yaudararta da yaudararrun kalamansa da rabi da kwantansa duk ƙaryane, saboda yasan har abada Iyayensa ba za su taɓa sonta ba, amma shi kam bazai yi gangancin sakinta da wuri ba, sai ya samu wacce ta kwanmai ko Naila ta dawo hannunsa kamar yadda suka tsara.

Da dare ya yi,
Sumaya da yake gwanace wajen son duniya tana ganin Sufyan ya fita ya dawo da lodin Siyayya ta fara sakin ranta, sannan ya kuma cewa ta biyosa Babban Birnin Abyad idan taji batason zama da shi yayimata alƙawarin sakinta, babu ja ta amince.

★washe gari suka je har Gidan Iyayenta ta yi musu bankwana.

Muguntar Sufyan yasa ya biya tsohon Gidan su ko zai samu mukullin sashen Naila kafin su tafi, ga mamakinsa hanasa shiga Gidan akayi gaba ɗaya, haka ya dawo suka ɗauki hanyar Babban Birnin Abyad ransa a ƙuntace.

Kyan matsugunin Sufyan na Babban Birnin Abyad ba ƙaramin tafiya da imanin Sumaya ya yi ba, a take ta manta irin ƙiyayya da wahalar da ta sha a Yankin Tudu. Tana jin ko Iyayen Sufyan ba su isa su rabasu ba.

Bayan kwana biyu da zuwansu Babban Birnin Abyad.
A zahirin gaskiya yanayin yadda yake yiwa Naila gadara da abinda yaga dama wajen sauke buƙatarsa sam ba iri ɗaya bane da na Sumaya, ƙiri-ƙiri take nuna ita batason wannan ita bazata iya wannan ba.

Wannan dalilin yasa ya ƙara karɓar shawarar Iyayensa hannu bibbiyu, Naila tamkar baiwa take sai yadda ya ga dama zai yi da ita, ta ƙiyi kuma jikinta ya gayamata tunda bata da gatan kowa dalilin dawowarsa Yankin Tudu kenan.

DAWOWAR LABARI
★washe gari Ɗayyib ya tura wakilansa kan komen Naila ta hanyar Yayyan Mahaifinta da suka yaudara da kuɗi a baya.

Da ƙarfin gwiwarsu dukkansu suka haɗa bakin ba su yarda Naila ta komawa auren Sufyan ba har sai ta samu sauƙi, kuma ko ta samu sauƙi sai sun ji ta bakinta idan ta amince. Idan kuma har da gaske Sufyan magani zai nema mata kamar yadda suka faɗa to yafara naima mata kafin ta koma Gidansa.

Martanin Yayyan Mahaifin Naila akan komenta gidan Sufyan mummunar labari ne a wajen ÆŠayyib, Jalal, Hindu da Sufyan kanshi.
A wannan dare dukkasu sukayi tafiyar Sirri zuwa Yankinsu Hindu, suka bawa Malamin duban Hindu kuɗi maiyawa ya ƙara tura mugayen aljanun da zasu addabi Naila ta ji kamar zata mutu har sai ahalinta sun sallama sun amince da komenta.

SARTAJ WANDA YA CIYAR DA NAILA GUBA
Fitar su ÆŠayyib da rashin dawowarsu da wuri ne, yasa Sartaj gajiya da zaman jiransu kan gulmar da ya kawo musu; na ga Naila can an shirya kaita Birnin Abyad gobe da sassafe neman magani.

Da ya ga dai bazai samu ganin su ba, haƙura ya yi ya nufo gida..

Ya na É—anyi nesa da Masarautar Sarki Hammam, MALIK da ya sauko daga mota ya bayyana a gabansa gaba É—ayansa....
Bayyanar fuskar Malik ga duk wani É—an Yankin Tudu, babban abun fargaba ne. Saboda ba ya zuwa ya tafi bai bar shaida ba.

Sartaj mummunar gani ya yiwa Malik saboda bai sakaya fuskarsa da hutu ya yi kamu mai kyau ba, a zallarsa ya fitomai.

Fararen idanuwansa masu tsananin haske da girma Malik ya zubawa ƙafafuwan Sartaj da suketa rawa kamar an jona mu su shocking.

Da zafin takunsa ya ke tunkaro Sartaj da gumi ke tsiyayowa tun daga cikin gashin kaa, har cikin suÉ—aÉ—É—en takalminsa.

Da sauri Sartaj ya yunƙura zai gudu, fitsari da bayan gida na zuwarmai lokaci ɗaya.

Munfashi Malik ya sauke kafin ya taka sawun da ya basa damar cafkar Sartaj.
Guri É—aya ya tsayar da fuskar Sartaj yana kallonsa shima ya na kallonsa. A hankali Malik ya É—age girarsa É—aya ya ce;

"kasanni?"

"Ni dai ina neman afuwa, wallahi na daina" Sartaj ya faɗa daƙyar muryarsa na karkarwa.

"Na ce kasanni?" Malik ya ƙara tambayarsa kamar bai ji abinda ya ce ba.

"Na sanka! Au wallahi bansan ka ba" Sartaj ya faÉ—a a ruÉ—e.

"Tabbas ba ka sanni ba, domin da ka sanni da bakayi abinda ka yi ba" Malik yaƙarasa faɗa yana kai hannunsa bayan wandonsa.

"Au na tuna, na sanka wallahi! kuskure ne daga yau na daina, na daina kai gulmar kowa kuma ba zan ƙara cutar da kowa ba, Dan Allah ka yafemin wallahi sharrin shaiɗan ne."

Yana ƙoƙarin ƙarayin magana Malik ya kwantar da shi ƙasa ya na cewa;

"Bayyanata a Yankin Tudu na mutane ne ma su kafiya irinka, ba na zuwarwa laifi ɗaya sai sun taru. Idan na barka gobe sharrin shaiɗan zai sa ka ƙara kai musu wani rahoton, ba tare ka tuna da kashedina ba amma idan na bar maka shaida Fa??"

Azabar ficewar ƙafar Sartaj ɗaya ne yasa ya shi sakin ihun da ya karaɗe Yankin.

Kafin fitowar Fadawan Sarki Hammam babu Malik ya shige Mota ya bar wajen, sai Sartaj da ke kwance cikin jini da ƙafarsa ɗaya da aka yanke rungume a hannunsa, kamar yadda Malik ya maƙalamai a tsakanin Hannuwansa.
Ihu su ma suka kurma.

Tuni mutane suka fara firfito daga Gidajensu.

Duk da Sartaj ya ba wa Mutanen Yankin Tudu tausayi hakan bai hanasu murmusa a ɓoye ba, acewar su sakayyar abinda ya yiwa Naila ne.


NAILA; A wannan dare tasha azaba irin wanda bantaɓa ji ba, Kaka tana kanta, da ƙarfin gwiwa tare yaƙinin samun sauƙi daga wajen Ubangiji take tofamata addu'o'i wasu ta tofa a ruwa ta shafa mata. Bayan wani lokaci barci ya ɗauke Naila.

Hannunta Kaka ta É—aga sama tana ce wa;

"Ya Ubangiji! da wanda ya ke zuwa ya biya kuɗi a sanyawa Naila ciwo, da wanda yake turo ciwon, da shi kanshi jinnun da yake assasa ciwon duk Kaine Ubangijinsu Ya Allah! Ya Allah kayimin maganinsu da gaggawa Don ƙarfin Mulkinka, Ka sauƙaƙamin tafiya da ita Ya Allah."

Itama Kaka a kusa da Naila barci ya É—auketa

★ washe gari da asuba Driver ya iso ƙofar Gidansu Naila, kafatanin mutanen Yankin da suka san da tafiyar duk sun hallara a ƙofar Gidansu, duk suna kuka da addu'o'i kala-kala ɗauke a bakunansu.

Ɗaya bayan ɗaya suka dinga rungume Naila, suna sumbatar ƙuncinta, Naila ta zaune a Mota tayi laƙwas Hannuna a cikin na Kaka, Yayyan Mahaifin Naila suna kuka suma suka rungumeta, Naila dai bata iya kuka sai kai da take ɗaga musu.

Suna yunƙurin tafiya Kakannin Naila na wajen uwa suka iso da mutanensu, kalaman su ga Naila na ƙarfin gwiwa ne, tare da tarin yaƙini a kanta.

Da haka Motar Naila ta fara tafiya kaka tana kuka Naila itama sai a lokacin hawaye ya zubomata tana É—agamusu kai, Mutanen Yankin Tudu suna kuka su na kuka suka rabu.

Misalin ƙarfe Takwas na safiya suka isa Iyakar Yankin Tudu da wajen hawa motar Ƙasar Abyad.

Driver shi ya taimaka musu har motar su ta tashi, shima da yaga Motarsu ta fara tafiya hawayensa ya sharce yana ɗago mu su hannu...🥹[7/30, 8:44 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥


N. A. S


Page 24

SARTAJ
★washe gari yana farfaɗowa daga dogon sumar azabar da ya yi da ihun kiran Malik yafara yana roƙo da magiya.

A surutan Sartaj da aka sanarwa su ÆŠayyib da su kayi dawowar cikin dare suka fuskanci Malik yana bibiyarsu, irin bibiyar da basu san ta hanyar da zasu toshesa ba. Kuma sun kasa gano wane yake kai masa rahoto.

Mutanen Yankin da suka ji ai aikin Malik ne ya yankewa Sartaj ƙafa, tsoron gulmar kowa da cin amanar junansu ne ya ƙara shigarsu. Tunda ga shi an yankewa Sartaj ƙafar da yake zaryar kaiwa su Ɗayyib gulma dashi.

"Amma mai yasa Malik bai taimaki Naila ba, ko bai san halin da take ciki ba ne??????" Tambayoyin da suke ta yiwa junansu kenan.

Duk nacin da akayi Sartaj ya buɗe baki ya faɗi ina yaga Malik har ya yanke mai ƙafa, ƙin yin magana ya yi.

Washe gari da su ÆŠayyib suka zo dubasa ihu ya kurma yana rufe fuskarsa, alamun bayason ganinsu. Har suka bar É—akin bai buÉ—e fuskarsa ba.

Har Sartaj ya warke ba ya iya yin gulmar kowa, balle ya ambaci sunan Malik, gani yake yi kamar idan ya ambaci sunansa zai bayyana a gabansa.

Ranar da su ÆŠayyib suka yanke shawarar neman mafita akan Sartaj a Fadar Sarki Hammam gudun tonuwar asirinsu washe gari aka nemesa aka rasa shi da tsohuwar Mahaifiyarsa.

Ɓatan Sartaj da mahaifiyarsa ya yi matuƙar tayar da hankali Mutanen Daular Sarki Hammam, sama da yadda labarin tafiyar Naila da Kakarta Birnin Abyad ya tashi hankalin su, domin sun san ko su Naila sunje dole su dawo, saboda maganin matsalarta ya na wajensu. Saɓanin talakawan Yankin da suke ganin Sartaj ya gudune saboda abun kunyar da ya aikata.

A karon farko aka fara saka jami'ai a duk wani hanyar da zai kai mutum cikin Yankin Tudu domin kawo ƙarshen Malik, shima Sufyan cikin gaggawa ya shirya komawa, saboda ɓacewar maganin da yasan dole idan ya cigaba da zama za'a tambayesa ya na ina? da kuma gudun kar ɓarna Malik ta ratsa da shi, domin zuwa lokacin ya fuskanci a kwai wasu manyan sirrikan da bai san da su ba...

NAILA
Allah Ya amshi addu'ar Kaka. A tafiyar kwanakin da suka yi, ciwon Naila ya na yawan tashi, amma da zarar ya tashi Kaka za ta rungumeta ta yi ta tofamata addu'o'i har sai jikinta ya yi yaushi barci mai nauyi ya É—auketa

BIRNIN ABYAD

Da taimakon Allah suka isa Birnin Abyad. Kaka ta zuba ƙauyanci wasu lokutan garin Kallon Mutane har tuntuɓe takeyi.

Da ɗan ƙarfin da Naila take ji, take yi mata raɗar motar da zasu hau a kunne. Da hannu kaka take kwatanta mu su komai tunda batajin turanci, kuma batajin asalin yaren ƙasar. Kamar ko da yaushe idanun Naila maƙale a hanyar Babban Birnin Abyad, ƙewar Bushra da Yasar na bijiromin, suka wuce hanyar.

Gidansu Naila ba ƙaramin burge Kaka ya yi ba.
Ba ta hutu ba bayan sunyi salla ta fara gyara ko ina na sashen.
Da taimakon Kaka bayan ta gama gyare-gyarenta Naila tayi wanka. A ranar Kaka ta farayimata amfani da maganin su Sufyan kamar yadda Mallam ya koya mata. Bayan wannan ta haÉ—a har addu'o'in da ya bata.

Da guzurin kayan abincin da suka taho da shi daga Yankin Tudu suka fara amfani, kafin Naila ji sauƙi su canza ƙudi su siyo wasu.

A cikin kwana uku sauƙi ya fara samuwa, Naila tana iyayin komai da kanta, har tayi Sallah a tsaye a kan ƙafafuwanta.

Kwana biyu bayan nan Naila ta shirya ita da Kaka suka tafi Gidan Iyayen Yasar domin jin halin da yake ciki.

Yasar ya na kwance babu lafiya tsohon watanni biyar kamar yadda Mahaifiyarsa ta faÉ—a musu bayan sun gama gaisawa, ta ce Accident ya yi a kan hanyarsa ta dawowa daga Babban Birnin Abyad. Ya na barci lokacin da su Naila suka isa, bai farka ba har sai da suka fara haramar tafiya.

Da mamaki yake kallonsu kamar bai ganesu ba, har sai da Naila ta gaisheshi ta faɗamai sunana sannan ya fahimci ita ce. Da zafin naman ɗan ƙarfin da yake ji ya gyara zamansa ya na faɗin

"Naila! Maiyasameki kika koma haka? Ciwo kakayi? Maiyasa baki dawo Makaranta ba? Na so zuwa har Yankin Tudu cigiyarki Saboda na kira wayarki bana samu wannan tsautayin ya afkamin ki gafarceni."

Kai Naila ta sunkuyar ƙasa tana Kuka.
Kaka ce ta basu labarin jinyar da Naila ta yi. Dukkansu sun tausayawa Naila har Iyayen Yasar da a baya suke gudunta. Sun É—an jima a Gidan kafin su dawo Gida.

★washe gari sai ga siyayyar kayan abinci da kayan motsa baki kala-kala har da kayan sawar Kaka, da wayar amsa kira duk daga Gidansu Yasar. Su Naila sunyi farin ciki matuƙa tare da godiya mai tarin yawa.

A hankali a hankali jikin Naila ya fara murjewa saboda canjin cima, muhallahi da kuma lafiyar da take ƙara samu. Itama Kaka tsaf ta yi kyau, su na waya da mutanen Yankin Tudu lokaci zuwa lokaci da number da suka rubuto mata a jikin takarda.

Bayan Naila ta samu sauƙi, Yasar da kansa ya jagoranceta har Makarantasu duk da baya iya tafiya sosai saboda karayar ƙafarsa da bai gama warkewa ba.

Naila bata samu matsalaba albarcin Yasar da kuma shaidun da suka gani da ido, saboda har lokacin akwai banbanci da yadda nake a baya kafin ta bar Birnin Abyad.

Da farin ciki Naila ta dawo Gida, itama Kaka daÉ—i ne ya kamata, tayi ta yiwa Yasar godiya tana samai albarka.

A cikin watanni biyun da Makarantarsu Naila suka ƙaramata a matsayin hutu, jikinta ya yi kyau kamar bata taɓa jinya ba. Da kanta ta kai Kaka sukayi siyayya kafin su wuce Gidansu Yasar.

Irin motocin da muka gani a harabar gidanne yasa Naila ta cewa Kaka su juya, domin jikinta ya na bata wakilai ne daga wajen aikinsa na Babban Birnin Abyad. Sam Kaka ta nuna bata san zanceba ba, a cewar ta; "mu ina ruwanmu da su? mu da ba wajensu muka zo ba."

A living room ɗin farko idanuwan Naila suka sauka a kan mutumin da ta ke gani tamkar Malik, duk da ya sanya tabaran rage hasken ranar da ya sakaye idanuwansa, ga kuma tarin ƙasumbar da ya bari a fuskarsa. Sai mace ɗaya da take zaune a kujera daban itama Naila ta kasa gane ina ta santa ina ta taɓa ganinta kuma da wa take yi mata kama.

Kamar yadda Naila take Kallonsu bayan ta gaishesu haka Macen da ba wani shekaru bane da ita ta ƙuramata ido.
Kaka tunda ta gaishesu ta nufi cikin Gidan wajen ƙannen Yasar da suke wasa da dariya.

Namijin ne ya fara miƙewa gaba ɗayansa yana miƙawa Yasar hannu. Miƙewarsa ya sa ya fito sak a Malik ɗin da Naila take zargi, kallon da ta yi masa shekarun baya a gidan Abduh Dhahab yana shara da safiya ya ƙara dawowa idanunta. Zumbur ta miƙe tana kallonsa kamar zata cinyesa, kafin ta ambaci sunansa mahaifiyar Yasar da take ganin girmansu a matsayin su na Manyan Iyayen Gidan ɗanta ta ja hannun Naila ta zaunar da ni a gefenta, a tunaninta ciwon jinnun da Kaka tace ta yi ne ya ƙara dawowa. Da harshen ƙasar Abyad take ba su haƙurin Naila ba ta da lafiya ne.

Macen ce ta amsa mata amma Namijin fita ya yi. Itama Macen miƙewa tayi Zinaren da ta yi ado da shi na walwali a kunnenta da wuyarta.

Har mota Mahaifiyar Yasar da Yasar suka yi musu rakiya, har lokacin Naila tama zaune kamar an dasata.

Bayan sun dawo Yasar yake tambayar Naila n
Ta san su ne? Naila yasan ko tayi masa bayani ba lallai ya yarda da ita ba don haka ta ce mai "a'a." Har suka bar gidan bata saki jikinta ba, duk Yasar yana ankare da ni.

Rashin walwala da yadda Makka take haÉ—e rai bayan sun koma Gida yasa Kaka ta ce ta zo ta rakata su siyo abu, Yasar ya bata kuÉ—i.

Waccen wajen Siyayyar da ta taɓa haɗuwa da Sufyan ta ce suje. Ƙananun kayan CK da Yasar yake yawan siyomata ta sanya sai malulluɓi mai girman da ta nannaɗe har rabin fuskata da shi gudun haɗuwa da Sufyan, ko Sumaya.

Bayan isarsu
Su na cikin siyayya idanuwanta suka faÉ—a kansa da jami'ai biyu a bayansa, wannan dai mutumin da na gani a Gidan su Yasar da rana ne.

Ya na fita ta rufamai baya da hanzari ba tare da ta saurari Kaka da ke tambayar "Naila ina zaki je?"

Yana ƙoƙarin zura gangar jikinsa a Mota Naila ta ƙaraso ɗan nesa da Motar da Gudu, cikin ɗan ɗaga murya ta ce "Malik, dan Allah idan kaine ka tsaya na roƙeƙa"...✍🏻

Duk mai son Ɗaukar Malik haya a Yankinsu tayimin DM saboda irin su Sartaj😂😂 I came in peace ☹️
[7/31, 10:04 PM] nafisaaliyusasaal: 🔥ZINARE🔥


NAFISA ALIYU SASAAL


Page 25


A kaikace yake kallonta, irin kallon da batasan yadda zata fassarashi ba.

A kan idanunta Driver ya tashi mota, duk da haka Mutumin yana kallonta kamar wanda bai Santa ba amma yake tunanin a ina ya taɓa ganinta

Tana ji tana gani mutumin da take kyautata zaton Malik ne ya yi tafiyarsa.

Tafiyarsa ba tare da ya buɗe baki ya cemata komai ba ya yi matuƙar sosa zuciyarta, har ya sata ta fara tunanin to maiyasa take bibiyar duk wani wanda abu ya taɓa haɗasa da Sulaim? mai take so su sanar da ita? Kenan batsyi imani da ƙaddara ba. Ko so take yi su cemata Sulaim yana raye? To idan ma Sulaim ɗin ma ya na raye cewa ya yi damacan ya na sonta ko zai iya aurenta? Maiyasa bazata rungumi maraicinta ta rufawa kanta asiri ba kamar yadda Allah Ya rufamata. Abinda da ya yi Sufyan shi ya yi Sulaim saboda daga tsatso ɗaya suka fito sai dai banbancin ra'ayi da ɗabi'a.

Jikina a sanyaya ta koma wajen Kaka, har suka dawo Gida bata saki ranta ba. Tun Kaka tana lallashinta da tambayar abinda ya ke damunta har ta gaji ta shareta.

Naila Sanyawa zuciyarta lallai sai ta manta Sulaim da duk wani abu daya dangacesa ne, ta fuskanci abinda zai kawowa Yankinta cigaba ne ya sanyamin zazzaɓi mai zafin gaske.

★Da Asubahi ta yi ko miƙewa da kyau bata iya yi saboda ciwon kai.
Kaka hankalinta ne ya tashi, cikin kuka takeyimata faɗar idan zaman Birnin Abyad ɗin ne banaso to na tattara su koma Yankin Tudu, su ƙarasa kasheta tunda ba zan kwantar da hankalina ba.

Da sassafe ta kira Yasar tana mitar ƙuncin da da Naila ta kwana da shi, yanzu gashi ta tashi da zazzaɓi.
Naila tana jin Yasar ya na tausarta Kaka tana ƙara haƙiƙancewa ya zo ya tambayeta idan zaman Birnin Abyad ɗin ne bataso sai su tattara su koma Yankin Tudu.

Ba su yi hour biyu da yin waya da Yasar ba, sabon Drivern da'aka Ma'aikatarsa ta ajjiye masa ya kawo shi gidansu.

Kaka ta na ganinsa ta miƙe zubur tana cewa;

"Ni bani da zaɓi, tunda bata tausayin kanta, tafison na mutu ina ƙunsar baƙin ciki, kuma daga yau Ni dai ba bu ruwana da ita" murmushi Yasar ya yi yana gaisheta, daƙyar ta haƙura da mitarta ta amsa gaisuwarsa kafin ta bar ɗakin.

Kafin Naila ta gaishe da Yasar ya katseta da ambaton sunanta
"Naila"

A hankali na ce "na'am"

"Menene alaƙarki da su Malik Dhahab? domin tun jiya ina sane da sauyin yanayinki, baki taɓa ɓoyemin komai ba amma jiya kin ɓoyemin Naila, menene gaskiya? " Yasar ya ƙarasa faɗa yana kallonta.

Haɗin sunan Malik da Dhahab shine abinda ya ƙara tsananta ciwon kan Naila lokaci ɗaya, kenan dai da gaske Malik ɗin Yankin Tudu mai gutsirewa mutane harshe ta gani, to ko dai da harshen mutanen dayake gutsirewa ya yi kuɗi har ya koma Malik Dhahab? Tunda a sanin da ra yi musu a shekarun baya talakawa ne fitik.

"Naila kinyi shiru, ko dai da gaske Yankin Tudu kikeson ku koma kamar yadda Kaka ta faÉ—a?" Yasar da ya gaji da dakon jiran amsarta ya tambaya.

Kanta ta girgiza sannan ta fara magana muryata a sanyaye;

"Nasan Malik a Yankinmu shekarun masu yawa baya, ina bibiyarsa ne domin na tambayesa ina Sulaim da gaske wuta ta ƙoneshi ya mutu, sai dai ƙiri-ƙiri Malik ya nuna bai Sanni ba bai ma taɓa gani na ba, wannan ne ya yi min ciwo har ma tashi da zazzaɓi."

Da mamaki Yasar ya ce;

"Anya kuwa Naila kinsan wanene Malik? Su Malik fa asalin ƴan ƙasar Abyad ne, domin da harshen da mafi rinjaye kuma mafi wahala na ƙasar Abyad dukka ahalin Gidan su ke amfani, yare ne mai wuyar koya a wajen bare, ko dai kama yake yi miki da waccen Malik ɗin?"

Tasan dama ba lallai ya yarda da ita ba, don haka kai tsaye ta karɓi yardar Malik kama yake yimata da waccen Malik ɗin.

Nasiha Yasar ya yimata tare da tunamata yaƙinin da mutanen Yankinta suke da shi a kanta, don haka na mayar da kai tayi karatu bakin iyawarta.

Kamar zata iya cire komai a ranta ta amsawa Yasar da "to" haÉ—e da yimasa godiya.

Ya na É—an jima a Gidan kafin a mayar da shi gida.
Bayan tafiyarsa dalla-dalla Naila ta zauna ta warwarewa Kaka komai. Kaka tsohuwace mai saurin fahimta da sauƙin hali bata da birkicewar wa su tsofaffin.

Cikin hikima ta nusantar da Naila, ko da ace Sulaim yana raye ba Mijin aurenta ba ne, ta tsaya a iya matsayinta ta kuma tsaya tsayin daka wajen manta baya ta fuskanci gaba, kar ta manta haɗakar kuɗin Mutanen Yankin Kakanta, da na Mutanen Yankin Tudu ne ya kawosu Birnin Abyad ba domin komai ba sai don ta yi karatu, saboda daga gareta suke sakaran samun canji, kar ta bari tunanin wanda da zai samu damar ƙara dawowa duniya bata kai matsayin da zai sota ba ya lalatamata tunaninsa har ta kasa zama abinda mutanen Yankinta suke yi min fata.

Sufyan da bai gaji arziƙiba, bai kuma gaji sarauta ba ya gujeta balle Sulaim da ya gaji Sarauta gaba da baya tare da tarin arziƙine zai so ta, Karta kuma wahalar da kanta wajen tunanin Sulaim yana raye ko baya raye, ta ƙaddarawa ranta ya mutu, ba kuma zai ƙara dawowa ba har abada!

Maganganun Kaka gaskiya ne, amma É—aukarsu ga Naila a lokaci É—aya abune mai kamar wuya, amma tasawa ranta zatayi iyakar iyawata don ganin ta fidda mutanen Yankinta kunya.

Kwanaki bayannan, ta fara bin gidajen Customominta, ta kuwa yi sa'a hannu bibbiyu suka karɓeta har ta samu kitsa kan wasu, A ranar da kuɗi masu nauyi ta dawo gida.

Daga wannan rana Naila ta ƙara himma akan sana'arta, har zuwa lokacin da ranar komawarta Makaranta ya yi.

Yasar ne yayimata siyayyar komai. Shi da Kaka da ƙannensa ne sukayi mata rakiya har Makaranta.

Kasantuwar Naila a Jami'ar ƴaƴan masu wadatar Birnin Abyad bai sa ta kai kanta matsayi da su ba, kitsonta takeyi ido rufe, kuɗi kuwa kamar anayimata yayyafin su, domin wasunsu biyan fariya da isa sukeyimata ita kuma na karɓa hannu bibbiyu tana godiya.

Watanta É—aya a Makaranta ta dawo tayi weekend tare da Kaka, sannan da bata ajjiyar kuÉ—in kitson da ta samu ta dinga tara musu.

SUFYAN.
Babu abinda ya sauya tsakaninsa da Sumaya, yawan ƙorafi, batason wannan, ita wannan take so da dai sauransu. Rashin mafita yasa Sufyan yake lallaɓawa, kuɗi kuma idan ya samu na su Ɗayyib ne. Sumaya sai dai ta samu ɗan abinda ba'a rasa ba.

Wata rana taro ya kai Sufyan Companyn Dhahab da suke ƙera Tukwane. Lafiya qalau suka gama taro ya fito, a hanyarsa ta fitowa ya ga mutumin da ya zo Yankinsu a matsayin Kabeer saboda shi dai ya kasa yarda da gaske Kabeer ne. Basarwa ya yi, ya nufi Motarsa. Har ya shiga Mota ya tuna ya manta tabaransa a teburin da ya zauna. Da ɗan zafin nama ya juya saboda aikin dayake jiransa a office.

Baya ya dawo yana matse idanuwansa da suka farayimai yaji. Masu tsananin kamanceceniya da Malik, Salman, Kabeer ya gani a waje ɗaya. Ƙara buɗe idanuwansa ya yi gaba ɗaya yana zaresu. Babu wanda ya kallesa a cikinsu har su ka gama gaisawa suka tafi sai wanda yake tsananin kama da Malik ne ya rage a tsaye yana duba wayarsa.

Sufyan bai motsa ba sai gumin dayake tsiyayomai, yana cikin wannan halin Maigidanshi Baturen da suka zo tare ya fito daga ɗakin taron, da sauri ya ƙaraso kusa da shi yaja hannunsa har gaban wanda yake kallo.

A gabatarwa da Baturen yake yi Sufyan ya ji ya ambaci Malik Dhahab shugaban Companyn Tukunyar Dhahab na ƙasar Abyad. Malik baya kallon fuskar mutum sai cikin idanuwansa, kamar yadda ya koya daga iyayen Gidansa, don haka kai tsaye cikin idanun Sufyan da suka fara canza kala yake kallo

Tafin hannun Malik mai girma da faɗi ya miƙawa Sufyan, shima Sufyan ƙasa ya yi da kansa kafin ya ɗago hannunsa da ya jiƙe da gumi tare da yimai nauyi ya miƙawa Malik bayan ya laso laɓbansa don ya tabbatar da harshesa ya na bakinsa bai fita ba.

Haɗuwar tafukan hannuwansu waje ɗaya yasa Sufyan ya ɗan ɗago kansa a hankali don satar kallon fuskar Malik, charaf idanuwansa suka faɗa cikin nashi, kafin ya sunkuyar da kansa ƙasa Malik ya ce; "Sufyan Ɗayyib Jalal right?"
Ambaton sunansa da salon da yasan dole sai wanda ya sanshi a Yankin Tudu ne zai iya faɗa da kuma Muryar da ya tabbatar masa da dagaske Malik ne a gabansa yasa idanuwansa juyewa numfashinshi ya ɗauke nan take ya zube ƙasa.

NAILA.

A makaranta ta haɗu da ƙawa ƴar masu arziƙin da take biyanta kuɗin kitso mai nauyi, da style kala-kala take zuwa a wayarta ta yi mata sak irin wanda ta kawo. wannan dalilin yasa suke ɗasawa da ita har sukan yi hirar da ya shafi Kaka da Yankinsu da ita.

Amira mai zuwa kitso wajen Naila da suka fi ɗasawa sun riga su Naila gama Exams. Ana saura kwana ɗaya zata tafi Gida ta zo da wani style ta ce Naila mata. Bayan mun gama take shaidawa Naila Babban Birnin Abyad zataje tsare-tsaren Bikin ƴar uwarta, wataƙila idan kitson ya yiwa ƙawayenta su zaɓeta ta zo tayi mu su, domin dalilin da yasa tace tayi mata irinsa kenan. Ko Kakarta ba zata amince ba?

Naila Tuna muradinta na son zuwa Babban Birnin Abyad yasa ta ji kamar ta amsata mata kai tsaye sai dai da ta tuna faÉ—an da Kaka tayimata akan Sulaim, sai tace bata ba, amma ta bari idan taje gida zata tambayeta idan ta amince zata sanar mata....
A akan haka suka rabu.


Shin Kaka zata amince kuwa??😄

🔥ZINARE🔥


SASAAL


Page 26


Har su Naila gama Exams bata daina tunanin tattaunawarsu na zuwa Babban Birnin Abyad da Amirka ba. Amma ta sawa ranta amincewar Kaka shi ne nata.

Ranar da ta koma gida
Da murna Kaka ta tarbeta bayan girki-girke ma su daÉ—i da ta shiryamata, sai da ta huta ta ci abinci, takasa sakowa Kaka zancen zuwanta Babban Birnin Abyad yin kitso saboda tsoron yadda Kaka zata fassara zancen take yi.

★har washe gari ta kasa yi mata zancen tafiyar, Sai Kaka da kanta ce ta kalleta cikin dariyar da ya haɗe da mamaki ta ce;
"Me kikeson faÉ—a kika kasa Naila? Tun jiya ina ankare da ke, karki ji nauyi ki faÉ—amin zan fahimceki kinji"
Murmushi ta yi tana murza goshinta, cikin kame-kame ta ke bata labari yadda sukayi da Smira.
Kaka kallon Naila takeyi maganganu Sarki tsafin Yankin Tudu lokacin da ya zo duba Naila na amsa kuwa a cikin kunnenta "Naila zata warke amma akwai jarabawar da ya fi wannan raɗaɗi a gaba, domin zata isa Babban Birnin Abyad, da ƙarfin ikon Allah! Amma daga lokacin ƙullin shekarun da aka kasa warwaresa zai fara warwarewa da kansa, arziƙin da Sufyan ya yi gajen haƙurin ya riskesa zai bayyana, wannan yana ɗaya daga cikin abinda Mahaifiyarsa take kwaɗaitar masa ya gaza fahimtarta, da ya yi haƙuri da zai zama wankakke abisa laifin da Kakannin-kakanninsa suka jima su na aikatawa aban ƙasa, ko da Naila ta warke ta koma Birnin Abyad, Birnin Abyad ba mazaunin Naila ba ne. Ba lallai ki yarda da maganganuna ba, amma daga ranar da sanadi ya kai Naila Babban Birnin Abyad, zaki gasgata batuna" furucin Sarkin Tsafin Yankin Tudu kenan lokacin da ya zo duba Naila, amma Kaka tayi watsi da zancensa acewarta; Boka Ɗan uwan shaɗai ne, don haka babu gaskiya a maganarsa..

Tuna wannan yasa Kaka a zafafe ta ce;
"Wallahi ban amince ba Naila, kinsan abinda kike faɗa kuwa? Babban Birnin Abyad har abada ba wajen zuwanki ba ne, karma ki ƙara tambayata don bazan lamince ba na gayamiki" Kaka taƙarasa faɗa cikin masifa! Tsabar masifa har rufe idanuwanta take yi kafin ta fashe da kuka.

Birkicewar Kaka lokaci ɗaya da yadda take magana har da su fashewa da kuka ba ƙaramin tsoro abin ya bawa Naila ba, cikin haushin yadda ta hantare ta har da su kuka ta ce;

"Kaka kukan me kike yi, ni fa kawai shawararki na nema, bance dole sai na je ba, sannan ke kika ce na gayamiki kar na ji nauyin komai zaki fahimce ni, amma gashi akan kawai na faÉ—a miki gaskiya shine kike masifa har da su kuka, dama can dai haushina kike ji, daga dawowata zaki sanyani cikin damuwa, na fara ciwo kuma kiyimin sharrin Yankin Tudu nake son komawa, gaba É—aya kin canza Kaka." Tsit ta yi tana kamo hannun Naila. ÆŠan fizgewa Naila ta yi tana cewa;
" ki ƙyale ni Kaka, tunda kin fara jin haushina a ɓoye bansani ba, ni ma daga yau babu ruwana da ke"

Hawayenta ta share still ba ta saki hannun Naila ba, da sanyi jiki ta ce;
" to zauna na faÉ—a miki gaskiya ina fatan kema za ki fahimceni, ki janye batun zuwanki Babban Birnin Abyad"

Son labari irin Naila yasa ta zauna da sauri jikin su na gogar na juna.

Abinda Sarkin tsafin Yankin Tudu ya faÉ—a ta maimatamata sannan ta É—ora da;
" Naila bawai na gazgata maganganun sa bane ɗari bisa ɗari, amma a yanzu a jikina nake jin ko dukka maganganunsa ba su zama Gaskiya ba, to baza'a rasa gaskiya ko da yaya bane ciki, duba da yadda su Hindu suke fafutukar dole sai kin koma cikin rayuwar ɗansu, Naila inajin tsoron matsalar da zai ƙara kunnowa rayuwarmu kai a yanzu, ki gafarceni"

Da mamaki Naila ta kalli Kaka tana tattare girarta waje É—aya ta ce;
"Saboda iya wannan dalilin zaki haramtamin samun kuɗin da zai sauya rayuwar Yankina? Kinsan nawa za'a biyani Kaka?. Rayuwarmu bazai taɓa cigaba da tafiya a haka ba, dole sai da gwagwarmaya tare da ƙalubale Kaka, baƙin ciki da farin ciki basa dawwama a rayuwar Bawa, idan warware ƙullin ne zai zama cigaban Yankinmu mai zai hana mu tunkari warwaresa ko da hakan zaisa mu rasa rayukanmu, tun da dai dole zamu mutu wata rana. Kaka kiyi tunani tunda na ki tunanin yafi nawa zurfi, ba kuma zanyi yin kaina ba dole zan jira umarnin ki, amma Kaka ki tuna gina kanmu da Yankinmu wajibunne, saboda Yasar shine ƙarfin gwiwar zamanmu a Birnin Abyad, to idan ya mutu fa? ko ya gaji damu fa? Jira zamu yi tayi sai dai wani yayimana gwagwarmaya mu muji daɗi mu ba za muyi da Kanmu ba? Saboda muna tsoron mutuwa?
Kaka kiyi tunani a nutse, kuma karki ji shakkar sanar da ni duk abinda kika yanke, In Shaa Allah zan yi miki biyayya kin ji."
ta ƙarasa faɗa tana rungume kaka bayan na sumbaci goshinta.

Tun a lokacin bugun zuciyoyinsu ya sauya daga tsoro zuwa ƙarfin gwiwa.


SUFYAN
Da ya farka ya ganshi a gadon Asibiti baiyi mamaki ba.
Sumaya tana ganin ya farka ta ajjiye wayar hannunta tana matsowa kusa da shi, sannu take ta nanatamai tana kamo hannunsa. Laƙwas Sufyan ya yi. A hankali ya buɗe bakinsa ya zaro harshensa.

"Sumaya kina ganin harshena, yana cikin bakina?" Ya yi tambayar yana karkaÉ—a harshensa.

Da mamaki Sumaya ta ce; "gashinan kana karkaɗawa, maiyasa zaka yimin irin wannan tambayar Baby, relax har yanzu zafin ciwon bai gama sakinka ba, bari na kira Likita" ta ƙarasa faɗa tana sakin hannunsa haɗe miƙewa ta bar ɗakin.
Ajiyar zuciya Sufyan ya sauke, sai dai kafin ya yi relax ɗin da Sumaya ta ce, asalin fuskar Malik da babu Tabarau babu komai sai ƙasumbar da shima an ragesa sosai saɓanin jiya da ya cikemai rabin fuska ya bayyana a ɗakin, mai kamannin Salman sak na biye da shi a baya.

Jikin Sufyan ne ya saki, tabon tsoron Malik da ya kwana da shi washe gari ya ɓace na dawowa sabo fil, idanuwansa ya kulle gam kamar mai barci.

Ido Malik ya lumshe kafin ya saki murmushin da sam bai masa kyau ba saboda bai saba ba, da iya ganin fuskarsa kaɗai zai iya kawar da Sufyan a doron ƙasa ta hanyar bugawar zuciyarsa. Amma Yaron tausayi yake bashi bai san komai ba sai abinda suka ɗorasa akai, ya jima da karantar Sufyan shi ba faɗan kawar da wani ne a gabansa ba, shi dai burinsa ya zama kyakkyawa ya tara kuɗi shima ya zama Dhahab ɗin kansa kamar yadda suke sauraran duk wa su hirarrakinsa ta offishinsa har ma da Gidan da yake kwana.

Da buɗaɗɗen muryarsa mai nauyin dake amsa amo da ya dace da kalar siffarsa Malik ya ce "sannu da Jiki Sufyan Ɗayyib Jalal, Allah Ya ƙara afuwa, ga colleague ɗina Uzair ku gaisa" ya ƙarasa faɗa yana nuna Uzair.

Sufyan daya kasa gaishesu da sunan ya na barci, kuka ya fasa idanuwansa a kulle, kansa a can gefe. Hannuwansa biyu ya haɗa waje ɗaya ya ɗagashi can sama dai-dai saitin su alamar roƙo. Tsabar kukan da yakeyi kafaɗunsa da ko ina nasa rawa yakeyi.
Malik miƙewa yayi zai fita saɓanin Uzair da ya tsaya kallon Sufyan da mamaki. Da taushin Muryar da sam baya kama da na Salman yake tambayarsa da yaren ƙasar Abyad

"maiyasa kake kuka?"

Damacan Sufyan ba wani sanin Murya Salman ya yi ba balle ya tantance.
Sufyan bai amsa ba still yaƙi kallon gefen da Malik ya bar Uzair a tsaye.

Sufyan na jin Muryar likita ya ɗan saki ajjiyar zuciya sai dai ƙara jin Muryar Malik a bayansa ya sa ya sume kansa ya karyo kamar zai faɗo daga kan gadon.

Hannun Malik Uzair ya ja suka fito waje.

Da fuskar tausayi Uzair yake tambayar Malik wanene Sufyan? Maiyasa yake jin tsoron da ya ke sashi sumewa idan ya gansu?

"Yankin Tudu, Babban ÆŠa namijin ÆŠayyib Jalal" Malik ya faÉ—a yana kallon Diamond Bracelet É—in hannunsa.
Wayar Uzair ne ya faÉ—i kasa a take gilashin baya da na gaba yayi kwatsa-kwatsa.

Dariyar muguntar da ba kasafai Malik ya fiye yi ba yasa ya na kama hannun Uzair da ya sanƙame a tsaye. Wayarsa ya sunkuya ya ɗaukarmai suka bar wajen.

Sufyan sai da ya yi kwana biyu yana fama da zazzafan zazzaɓi jininsa har hawa ya yi, baya iya ɗaga kiran kowa, da zarar ya ji motsin ƙofa gabansa yake faɗuwa, hankalinsa baya dawowa jikinsa har sai yaga wanda zai shigo.

Likita ne ya zaunar da shi yayi mai faÉ—an yana so ne ya kashe kanshi? Ko wani abun ake yi mai a Asibitin da yake sashi yawan fargaba?

Hannu likita Sufyan ya kamo yana kuka yana bashi labarin su Malik ne suke basa tsoro. A wannan ranar daƙyar Sufyan ya nutsu ya kwantar da hankalinsa tunda likita ya yi masa alƙawarin su Malik ba zasu ƙara dawowa ba.

Da yammaci ya dannawa Mahaifiyarsa kira, bayan Sumaya ta tafi Gida ta É—an huta.
Kamar tayi shekaru tana jinya haka Sufyan ya tsinkayi Muryar Mahaifiyarsa. Saitin zuciyarsa da bugunsa yake fita da ƙarfi ya dafe ya ce;
"Menene yake damunki Ummeena? Kwanana biyar bani da lafiya babu wanda ya nemeni a cikinku, ashe idan ba buƙatar kuɗi ba, ba ni da wani amfani a gareku"
Murmushi tayi kafin ta ce;
"Sufyan É—ana na fika shiga halin jinya, domin ciwona ba irin naka bane" gyara zama Sufyan ya yi yana yi mata sannu cikin tausayawa. Kamar daga sama ya ji tace;
"Ina ka jefar da makarin sirihin jikin Naila Sufyan?" Kame-kame ya farayi, sauƙin dole na zuwarmasa lokaci ɗaya.
Murmushi taƙarayi ta ce;
"Sufyan! Malik zai iya riskarka a koda yaushe, amma kafin na baka labari, inaso duk halin da kake ciki karka ɗara kwana biyu baka isa Birnin Abyad wajen Naila ba, duk iya yadda za kayi karka bar Naila ta isa Babban Birnin Abyad ba tare da ta amincewa komen aurenku ba, ko kwanciya ne kayi a ƙasa ka roƙi yafiyarsu, domin Naila itace Makamin tsirarka daga su Malik albarkacin matsayin da take da shi a Dhabah. Karkayi watsi da umarnina kamar yadda kayi watsi da shi ka cigaba da zama da Sumaya, idan ka isa Birnin Abyad duk abinda ka riska ka yi gaggawar kirana domin na baka wasiyyata ta ƙarshe." Tana gama faɗa ta datse kiranta.

Shi dai Sufyan bai san abinda ya samesa bayan katse wayar Mahaifiyarsa ba, sai da ya wayi gari yaga Sumaya tsaye a kansa tana kuka..

Daƙyar Sufyan ya daure ya ƙara kwana ɗaya a Asibiti. A gaggauce ya sanar da Sumaya ta shirya kayanta, a kwai aikin da zaiyi a Birnin Abyad.

NAILA
Suna zaune da Kaka kiran Amira Customarta ya shigo wayarta. Domin Kaka taji komai a sarari ta saka Muryar Amira bayan ta É—aga.

Bayan sun Gaisa cikin zumuɗi take sanar da Naila kitsonta ya yi matuƙar jan ra'ayinsu kuma sunyi alƙawarin biyanta kuɗi masu nauyin gaske. Amma zatayi kwana biyu acan tana yi musu, sannan tayi mata bayanin tace musu tana da Kaka, sun ce zasu turo tikiti da komai mu taho tare.

Kallon Kaka Naila tayi tana jiran umarninta.

A hankali ta ɗaga kai alamar ta amince!!!!.....😄

Shin Sufyan zai riski Naila.???
🔥ZINARE🔥


NAFISA ALIYU SASAAL


Page 27


Bayan sun yi sallama Naila ta katse wayar, rungume kaka ta yi, ta sumbaci ƙuncinta tana dariya. Kai Kaka ta girgiza jikinta a sanyaye.
Kamar Naila bata lura da sanyi da jikin Kaka ya yi ba ta É—auko waya ina kiran layin Yasar.

Da tsananin farin ciki Naila ta basa labari.

"Alhamdulillah!" ya furta da daukakkiyar sauti kafin yafara tsokanarta da "Finally yokel sister ta zata leƙa Babban Birnin Abyad, har na hango idanuwanki wallahi" Kaka da ke sauraronsu dariya tasa haɗe da sakin ajjiyar zuciya.
Da tsokana Naila suka ƙare waya da Yasar.

Da yammaci Kaka Mallam ta kira, ta yi tsammanin zai soki zuwansu Babban Birnin Abyad amma sai taji ya furta "Alhamdulillah" ƙwarin gwiwa da addu'o'in tsari kala-kala ya ƙara bata domin acewarsa; abinda zaiyi sanadin zuwan Naila Babban Birnin Abyad ya daɗe ya na jira kuma gashi Allah ya kawo.


Kafatanin kuÉ—in da Naila take tarawa A banki ta turawa account É—in mutanen Yankin Tudu.
Kafin dare ya yi kiraye-kirayen su sai shigowa yake yi, abun dariyar duk da wayan mutum biyu ake wayan, talauci ya hana da yawansu mallakar wayoyin hannu.

Kaka bakinta kamar zai yage, banda "Ameen Ya Allah! Ameen thumma Ameen!" Babu abinda take maimatawa. Ba su daina kira suna Godiya da addu'o'i ba har sai da chajin wayar ya ƙare.

A jiyar zuciya Kaka ta sauke, lokaci zuwa lokaci sai ta saki murmushin farin ciki. Kusa da ita Naila ta matso taa zauna ta ce ;

"ya ya zakiji idan akace mutanen Yankin mu, sun samu farin cikin da ya fi wannan?"

"Zan ji daÉ—i Naila sama da wanda na ji a yanzu" Kaka ta faÉ—a da murmushi kwance a saman fuskarta.

"To ki saki ranki mu shiga Babban Birnin Abyad, In Shaa Allah ba zamu dawo ba sai da nasarar da zai kawowa Yankinmu gagarumin sauyi." Murmushi suka sakarwa juna.

Da yake Yasar ya zo hutun ƙarshen Mako Gida, ziyarar bazata shi da ƴan gidansu suka kai Gidansu Naila don tayata murna.

Kaka baki ta saki da ta ji abinda ya kawosu kafin da kwashe da dariya ta na cewa "wai ni kuyimin bayani wani irin arziƙi Naila zata samo a wannan Babban Birnin Abyad ɗin da kowa yake farin ciki, kar fa muje a siyar da mu" Dariya Yasar da Iyayensa suka kwashe da shi, ƙannensa da suka saba wasa da dariya su na tsokanarta.

Cikin raha Yasar yake bawa Kaka labarin da zarar ta shiga Babban Birnin Abyad zatasan ko wanda ya yi wanke-wanken rana É—aya dole ya fito da kuÉ—i mai tsoka.

Ana raha da wasa mukayi Dinner da su Yasar.
Sai dare sosai suka tafi Gida.

★washe gari su Naila suka fara kimtsa kayan da zasuyi tafiya da shi, amma har lokacin abinda yake bawa Naila mamaki shine tayaya za'ace zuwansu na kwana biyu ne zai warware ƙullin shekaru aru-arun da ko Kakanta ba haifa ba lokacin, ko dai ta Kaka kashesu za'ayi.

★washe gari daya kamar ranar tafiyarsu, tsaf Naila ta shirya cikin baƙin Abaya haka Kaka irin Abaya ɗaya suka sanya na Company ɗaya.
Har Gida ƙanin Yasar ya zo ya ɗaukesu saboda tare zasu wuce da Yasar don haka sai sun fara biyawa Gidansu tukunna

A dai-dai lokacin da Motarsu Naila ta gifta ta hangi Sufyan A cikin Motar da take kyautata zaton Taxi ne. Mamakin abinda ya kawoshi ta yi cikin daƙiƙu kafin na tattara lamarinsa na watsar tana danna wayarta.

SUFYAN.
Ƙwallane ya tararwa manyan idanuwansa da suka ƙara zama farare ƙal lokacin da mai gadi ya tabbatar masa da su Naila sun fita yanzunan ita da Kakarta. Yasan kuma ba Makaranta ta je ba, domin can ya fara biyawa akace sunyi hutu, a hankali ya nemi waje ya zauna ya zaro wayarsa. Bugu ɗaya Hindu ta ɗauka.

Ko sallamarsa Hindu bata amsa ba ta ce;

"Ka riski Naila?"

Jiki a sanyaye ya ce; " a'a"

Kuka ta saki na tsayin mintuna shida kafin ta É—ora da;
"Son zuciya shine mafarin halakata, bayan tafiyarka muka gano ka yardar da maganin makarin asirin jikin Naila a gidansu kamar yadda Malamin Yankinmu ya sanar mana, maimakon Jalal da Mahaifinka su ga laifinka, sai suka juye laifin akaina, acewarsu duk nina tsiro musu da wannan musibar, sun tisani a gaba da asiri kala-kala kullum cikin ciwo nake, na je wajen Mahaifiyata ÆŠayyib ya zugeta ta koroni.
Sufyan mafita ɗaya ya ragemaka, ka koma bakin aikinta ka riƙi aikinka da gaskiya da amana, amma a kowani yanayi ka ji tsoron Allah kuma kaji tsoron Malik, domin baya ganinka ba kuma ya tare dakai amma ka sani yana saurararka a duk inda kake a Babban Birnin Abyad kamar yadda malamin duba ya sanarmin, a yanzu amfaninka a wajen Ɗayyib shine ka bincikomai su wanene DHAHAB? banda wannan baka da wani amfani a gareshi, su kuma su Malik suna tare da kai ne domin ganin iya gudun ruwan Jalal, kamar taku ɗaya haka kake da mutuwarka Sufyan a tsakanin Ɗayyib da su Malik, amma abinda na faɗawa Ɗayyib ya hukuntani shine wanɗanda suka ƙirƙiri sabon Dhahab ba abokanan yaƙar su ba ne, saboda suna da damar shafe Yankin Tudu da mutanen cikinta, domin ko kai kanka da kake cikin Daularsu har yanzu mai asalin Dhahab ɗin bai san dakai ba, wataƙila da ya sani da tuni ka jima da ruɓe a cikin ƙarƙashin ƙasa. Ina gayamaka dukka wannan ne domin kayi takatsantsan kamar yadda malamin duba ya sanar da ni, ina nadama Sufyan, ka yafemin. Ba lallai mu sake magana makamanciyar wannan da kai ba, ba kuma lallai ka dawo ka riskeni a raye ba, amma Allah Ne shaida bani da masaniyar komai a kan kisan su Abduh da ahalinsa." Ɗif wayar Hindu ya katse kamar dai waccen ranar.

Wayar Sufyan ya bi da kallo yana zare idanuwansa da suka koma jajaye cikin ƙarajin da ya tashi dukka jijiyoyin wuyarsa da goshinsa ya na furta "Ummee! Ummee!! Ummee!!!" A lokaci ɗaya yana ƙara kiran layinta da baya shiga kwata-kwata. Hankali a tashe Mai gadin gidansu Naila ya kiran layin agajin ƙasar. Kafin su iso Sufyan ya zube ƙasa idanuwansa a juye.

NAILA.

Wannan hanyar da take bi da kallo tsayin shekaru yau gashi zata tunkareshi da ƙarfin ikon Allah.

In Shaa Allah anan Free pages É—in ZINARE ya tsaya. Ga waÉ—anda suka bibiya ba su da halin biya na gode da comments da addu'o'in ku, ga waÉ—anda suke da wadatar biya suma ina godiya mai tarin yawa Allah Ya bar zumunci.

KuÉ—in motar zuwa Babban Birnin Abyad Naira 500 ne kacal, ta wannan account É—in
Nafisat Aliyu Muhammad First Bank 3207955182 tare da tura shaidar biya ta 09132403788,08138665117. Ga masu bibiya kuma ta Arewabooks sai su ɗora. In Shaa Allah zamu cigaba da Posting ranar Monday, 4, August, 2025 da misalin ƙarfe 8:00pm

Na gode🙏🏻
🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥


ZINARE.

2

BY

NAFISAT ALIYU SASAAL
Chapter 1 · 0% Book details