← Book details Uwa Uwa Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 9

Gabatarwa

Uwa Uwa Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 239 min read

Root Entry
WordDocument
0Table
Data
Normal
Default Paragraph Font
Table Normal
No List
UWA UWA CE!
LITTAFI NA
AYA.
BATOOL MAMMAN.
SHIMFI
KIRIKASAMMA, JIGAWA
1983
Nishi take mai kama da gurnani saboda tsananin ciwon da take ji. Ko da wasa bata taba tsammanin ciwon nakudar da mata ke yawan fada ya kai haka ba. Mace ta kasa gane a wace duniyar take. Idan ba ta kama bakinta ba sai dai ka ji tana sumbatun da basu da kan gado. Addu'a kuwa bata san nawa ta kama ta saki kafin ta kai karshe ba. Yau Kulhuwallahu, Falaki da Nasin da ko cikin bacci basu bace mata ta kasa kai karshen ko daya. Sai ta karanta ayoyi biyu a nan ta kama wata. Halilala ma da kyar take cijewa ta kai karshe. Iska take furzarwa akai-akai ta baki ta hanci. Ashe shi yasa Malamin makarantar darensu ya ce duk wadda ta rasa rayuwarta wurin haihuwa tayi shahada. Ladanta daya da wanda ya rasu a wurin yaki. Mahaifiyarta ce ta fado mata a rai a wannan yanayin.
"Allah Ya jikanki Inna. Inna idan na yi miki laifi ki yafeni. Innata bani da kamarki duk fadin duniya." Ciwo na tasowa ta ce "Inna ki ceceni."
"Allah dai Ya ceceki Mari kada ki yi sabo mana."
Ba da niyya ba ta kalli idanun surukarta Inna Mairo cikin radadin ciwo ta ce "kin san irin ciwon da nake ji ne Inna Mairo? Nan..." ta nuna mararta "...ne yake rabewa gida biyu. Yanzu kema a haka ki ka haifo Inuwa?"
Dan murmushi Inna Mairo tayi saboda sanin cewa Mari ba a hayyacinta take ba. Ita da ta sha wannan wahalar sau goma sha uku sai dai ta bada labari.
Wani irin ciwo ne ya damki mara da bayan Mari ta kai hannu ta cafko hannun Inna Mairo. Gani take kamar ba za ta tashi ba saboda azabar ciwo.
Harira unguwae zoman ta sake danna gefe da gefen cikin sannan ta kuma lekawa. Kai ya taho amma da alama hanyar tayi masa kadan. Sabuwar rezarta ta dauko ta ce da Inna Mairo ta matso kusa da tochilan ta haska mata da kyau. Acibalbal din da aka kunna bata da hasken da zai wadaceta tayi abin da ya kamata.
Mari ciwo bai barta taga abin da ake shirin yi mata ba. Harira ta saka tochilan din a cikin dankwalinta ita kuma Inna Mairo ta rike hannuwan Mari. Rezar ta dan kara a jikin wutar acibalbal din ta dauke ta danna kowane gefe a jikin zaninta. Ji ka ke kit-kit ta kara Mari ta hagu da dama. Wannan izaya bata da kalmar kwatance. A kan ce mata basu ganewa idan an karasu saboda ciwon nakuda amma Mari kam taji komai.
Budar bakinta za ta yi ihu wani nannauyan nishi ya taso mata. Da dan sauran kuzarin da ya rage mata ta cije baki tayi nishin. Hamdala Harira tayi tare da karfafa mata gwiwa akan ta kara wani domin ga kan jariri nan ya kara turowa gaba. Ta daddage tayi kuwa sai ji tayi an canyara kuka irin na sabbin haihuwa bakin duniya. A take ta nemi wannan azababben ciwo ta rasa sai son ganin abinda ta haifa.
"Sannu Mari. Sannu da kokari. Allah Ya raya shi Ya baki lafiyar shayarwa." Inna Mairo ta furta tana share mata gumi.
Kunya taji ta lullubeta da ta tuna cewa ba don dan ya fito ba sakon tsinuwa da Allah Ya isa ta shirya bata domin ta isar ga Inusa maigidanta.
Harira ta nade jinjirin a zani ta mikowa Inna Mairo. Da saurinta ta mika hannu za ta amshe shi hannun ya yi 'yar kara. Fuskar Mari wadda ta dago kai tana son satar kallon dan nata ta kalla tayi murmushi ganin Marin ta kawar da kai gefe.
"Da dai korafin karya min hannu zan miki amma na fasa. Dauke shi ku ji dumin juna kafin na dawo."
Da hannu Mari ta rufe fuskarta mai dauke da murmushin da ya gagara buya. A hankali ta bawa Inna Mairo hakurin rikon da tayi mata wanda da alama ya janyo mata rauni. Wani murmushin ta sake yi mata sannan ta tashi domin dora ruwan wanka tana murza hannun da take jin ya yi mata nauyi. Tana tausayin matar dan nata saboda ta tashi marainiya mara gata a wurin danginta. Shi yasa bata yarda an tafi da ita wankan jego ba lokacin da matar kawunta ta matsa akan hakan.
Harira ma fita tayi aka bar Mari da jaririnta. Sai da ta tabbatar babu sawunsu a kusa ta matso dashi kirjinta ta rungume. Hannunta yana dan rawa ta bude fuskarsa da kyau. Hawaye taji ya ciko idanunta saboda kaunarsa da ta shigeta farat daya. Bata jin za ta iya hada shi da kowa sai dai idan a gaba ta sake haihuwa. Tunanin kadai sai da yasa tsigar jikinta tashi da ta tuna halin da take ciki mintuna kadan da suka wuce. Addu'a tayi masa ta neman tsari da kariya tare da albarkar rayuwa. Kafin a fara shigowa dakin har ta gama kissima rayuwarsa har aure. Burinta ya zama da nagari abin kwatance. Ya yi ilimi mai zurfi irin wanda taga ana yi a birni lokacin da take aikatau kafin tayi aure. Idan so samu ne ma ya zama babban likita ko lauya.
"Dinkin nan zan zo in cigaba in tara kudin siya maka duk abin da za a nema a makaranta na karatun."
Ta fada masa kamar yana fahimta. Guda ta jiyo ta tabbata yanzu duka matan gidan sun sami labarin haihuwarta. Yanzu dakin zai cika duk da asuba ce da matan 'yan uwan mijinta da sauran kannensu da basu yi aure ba. Ajiye jaririn tayi da sauri kar a ganshi a hannunta a kirata mara kunya. Can kasa kamar mai yi masa rada tayi magana tana murmushin tsananin farinciki da jindadi.
"Bi'izinillahi sai kayi arabi da boko. Kayi sauka sannan kayi digirin digirgir irin na dan Hajiyar da na yiwa aiki."
Rana na soma fitowa ruwan wanka ya yi zafi. Matar kanin Malam wato kawu ga mijinta Inuwa ce ta zaga bayan gida da ita inda za'ayi mata wanka. Jaririn kuma saboda hannun Inna Mairo da alama ya sami gocewa ko targade sai matar wan Inusa ce tayi masa wanka. Tana murnar rabuwa da ciwon haihuwa ashe akwai wani a gaba. Ruwan wankan da zafi sosai ake yarba mata darbejiyar da take ciki. Tun tana daurewa har ta hada da ihu. Ciki da baya sun sha matsa da dannawa. Bayan an gama wankan ta miko mata wani kwabi da kyallen kunguzu. Kallon kwabin da yafi kama da lalle tayi ta tamutsa fuska.
"Me zan yi dashi Gwaggo?"
Idan bata yi da gaske ba take taken Mari ba za ta saka ba saboda haka ta amshe ta ce yaba mata da kanta. Lalle ne aka kwaba da kauri da wani garin magani aka cusa mata. Mari sai gumi kawai take yi na wahala da ciwo. Bayan an gama sakawa kuma aka toshe wurin da kyallen kunzugu sannan aka bata zani ta daura.
Tare suka fito tana taku da kyar zuwa daki. A haka aka ce ta shayar da jaririn bayan ko zaman kirki ta kasa. Haka aka cigaba da yi mata kwabin lallen nan na tsahon kwana shida sai ta nemi tsagar wurin karin ta rasa. Ciwo ya hade tsaf ya warke (don Allah kada wacce ta gwada).
Ranar suna jariri yaci sunan kakansa Auwalu aka yi masa lakabi da Abbati.
DALA, KANO
1985
Kukan ya ishe shi. Idan ya bari suka kara minti biyar a dakin yana da tabbacin zai sami tabin hankali. Bai so Innayo ta karbi girki daga yin arba'in ba. Jiya ma haka suka kwana jaririyarta Hasiya tana ta canyara kuka. A fusace yasa kafa ya haureta tana baccin da ana gani za'a gane cewa a gajiye take likis. Da yake muryar Hasiyan ba karfi gareta ba shi yasa bata ji kukan da ta shafe mintuna tana yi ba.
"Dalla can malama tashi ki dauki 'yarki."
Bugun ya shigeta sai dai kukan da ta ji ya dauke zafin dukan. Hannu ta kai da sauri ta lalubi 'yarta cikin hasken farin watan da ya ratso ta tagar dakin. Rarrashinta tayi nata idanun suna yi mata yajin bacci ta soma shayar da ita. Jin yarinyar tana ta ajiyar zuciya yasa ta jin babu dadi a ranta. Maganin mura ta sha ya saka mata nannauyan bacci ga kuma gajiyar aikin da tayi.
"Baiwar Allah kin dade kina kukan nan da alama ban ji ba. Ayi hakuri" ta kare maganar tana shafa mata kai.
"Mtsew" Alh Rabi'u ya buga tsaki.
A cikin duhun dakin ya tashi ya lalubo wandon kayan da ya dawo dasu daga kasuwa ya saka hannu a aljihu. Sautin sulalla na karo da juna Innayo taji ta kalli bangaren da yake tsaye.
"Alhaji idan wani abu kake nema bari ta gama na kunna maka fitilar kwan. A duhun nan ba ganin..."
Kasa karasawa tayi ganin ya nufota. Duk da ba ganin fuskarsa take yi ba amma ta fahimci ransa a bace yake. Hannunta ya kama ya zube mata sulallan da bata san ko nawa bane.
Da kakkausar murya ya yi mata magana cikin fushi.
"Gashi nan na saya sai ki tashi ki koma dakinki."
Sam bata fahimce shi ba.
"Me ka saya?"
Daurewa ya yi saboda dare ya raba ya bata amsa ba tare da ya kara daga sautin muryarsa ba.
"Kwananki na saya Innayo! Ki dauki 'yarki ku koma dakinki. Zan dinga biyanki daga yau har ki kara wata arba'in din."
Hankali a tashi ta fara tambayarsa laifin da tayi masa. Lokacin kuma Hasiya ta zabi ta sake bare baki tana kuka. Kan Innayo har wani sarawa yake saboda rashin isasshen bacci da gajiya. Wuni take a gaban murhu ga fama da yara. Biyar nata har jaririyarta ga kuma hudu na matarsa ta farko da ya saka shekara biyu da suka wuce.
A yanzu su biyu ne a wurin maigidan nasu Alh Rabi'u kuma ita ce matsayin uwargida. Amaryar tasa Asabe ma ta dan kwana biyu tunda haihuwarta biyu yanzu. Iyakarsu da shi ya aunawa maigirki hatsi ga icce jingim a gidan. Sauran abin da za'a hada da hatsin a tayar da abinci kuwa sai dai mace ta nema. Asabe ko wata bata cika ba ta fitittike ta nemi ya raba musu girki. Kowacce tayi nata. Wadda miji ke hannunta ranar tayi da shi. Ita da ta zo cin arziki gani tayi sadakinta ma idan bata yi wasa ba a cefanen ciyar da 'ya'yan koshiyoyi zai kare. Haka kuwa akayi. Ya amince ya raba ya bar masu 'ya'ya da wahala. Bayan rabuwarsa da uwargidan taki daukar ko guda cikin 'ya'yanta. Har yau basu san me ya hadasu ba amma ko tantama laifin ba zai wuce nasa ba. Mahaifiyarsa ya kaiwa yaran da fari yayansa ya ce bai isa ba. Ga tsufa da tayi ga sanin halinsa na son banza. Jibge mata su zai yi sai an ganshi. A dole ya dawo dasu gidan ya rabawa matansa. Asabe tayi tsalle ta dire a gaban yaran ta ce ba za ta dauki ko daya ba. Tausayi suka bawa Innayo ana rabonsu a tsakar gida kamar ba mutane ba ta karba ta hada da nata. Zancen irin wahalar da take sha wurin ciyar dasu ma bai taso ba.
"Nufinka bani da girki har sai mun kara wasu kwanaki arba'in din?" Ta tambaye shi da mamaki.
"Ashe kin fahimta ki ke wani neman ba'asi." Shimfidar Hasiya ya tattaro mata "tashi ki tafi bacci ne a idona. Kuma ki kwantar da hankalinki ba wai Asabe zan baiwa kwanakin naki ba. Kukan nan ne kawai ba zan jura ba."
Maganganunsa sun bata mata rai amma ta daure taki bashi amsar da za ta sa taji sauki a zuciyarta. Tashi tayi jiki ba kwari ta fice ya kada kai a wurin ya kwanta.
Kamar kullum washe-gari karfe bakwai a bakin murhu tayi mata da goyon Hasiya. Da safe 'yar tsala take sayarwa da kuli-kuli. Da rana kuma dambu. Daidai lokacin tasowar yara daga islamiyya kuma tayi danmalele. Don ciniki kam sai dai tayi hamdala. Kudin ne dai duk yawansu basa isarta. Yara tara ne a gabanta da ita kanta cikon ta goma. Ga kudin laraba ga sayen abinda ba a rasa ba na boko.
Ta sallami yaron karshe da bokiti cike da 'yar tsala da zai kai kasuwa taga fitowar Asabe daga dakin Alh Rabi'u da danta a hannu. Suna hada ido ta gatsina fuska gami da murguda mata baki ta shige dakinta. Bata bi ta kanta ba ta sauke tandar ta dora ruwan wanka. Yaran gidan duka sun tafi makaranta sai wadda ta yaye tana bacci a daki.
Alh Rabi'u ta gani ya fito cikin shirin tafiya kasuwa. Dauke kai tayi kamar ba za ta yi masa magana ba saboda haushin abin da ya yi mata, sai kuma dai ta daure ta ce,
"Sannu Alhaji."
Da yake ba shi da gaskiya sai ya hau sababin borin kunya.
"Na dai biyaki kin kuma cake kudin bare ki ce an ci amanarki."
Zama tayi akan tabarma ta kwanto goyonta kafin tayi magana cikin rashin jindadi.
"Wani abin kaji na ce?"
Hannuwan babbar rigarsa ya nade fuskar nan tasa a hade. Bai so haduwarsu ba shi yasa ya zauna a daki niyarsa sai ta bar tsakar gidan ya fito. Daina jin motsinta da suka yi ne tasa shi cewa Asabe ta duba musu. Ita kuma don ta tura mata haushi ta fito sai ya zata ta gama suyarta ta shige daki ne.
Muryarsa a sama tunda ya san yaran masu wayo suna makaranta yake mata magana.
"Banda fitina ma irin taki Innayo daga yin arba'in ringidi-ringidi kin kwaso jiki kin dawo turakar maigida..."
Maganganunsa a take suka fara tunzura ziciyarta domin ta fahimci ci mata mutumci yake son yi. Kalamansa na gaba basu bata damar yin wani tunanin kirki ba sama da zubar da hawaye.
"...karfe takwas da rabi don bala'i duk kin saka yara bacci kin taho dakina ke mai girki. To magana ta gaskiya ni ba zan dinga kwana da wannan yarinyar tana yi min kuka ba." Ganin tana ta zubar da hawaye yasa shi cewa "Idan arba'in din ne baki son maimaitawa sai ki dinga barinta a dakinki ko ruwa A'i ta dinga bata. A shekarunta yanzu yaci a ce za ta iya kulawa da jinjinya."
Ido sharbe da hawayen bakincikin wannan terere da ya yi mata kuma a kunnuwan Asabe ta ce "yanzu Alhaji kayi min adalci kenan? Ka dakeni kuma ka hanani kuka. Ita Asaben ba goyo gareta ba?"
"Ban san kina kishi da namijin da ta haifa min ba sai yanzu. Yaro dan wata biyar da an kwantar dashi baka sake jin kukansa sai gari ya waye. Wai ma da ki ke zancen adalci ke shi kika yi min da kika haifi mata har biyar?"
Zancen kenan kullum! Ita da babarsu A'i sun haifa masa 'ya'ya mata. Asabe ma ta farkon ta mace ce cikon ta goman matan. Na shadaya ne ya fito namijin da ake muradi.
Idan ta biye masa ita zai cigaba da konawa zuciya a banza. Tashi tayi ta shige daki ko amsa bata bashi ba. 'Ya'ya mata Allah Yaso bata kuma ta gode. Sake kudurin ganin ta inganta rayuwarsu tayi. Idan ta kama ta kara wata sana'ar za ta kara. Burinta a rayuwa su ginu su zama mutanen da sai dai a rabesu a sha inuwarsu. Ta yarda ita kadai ta gama shan wahalar rayuwar duniya indai 'ya'yanta za su jidadi a gaba.
BARNAWA, KADUNA
2000
Zazzage akwatin da ta ajiye akan gadon tayi ta sake bin kayan ciki daya bayan daya tana jerawa a nutse. Tafiya ko da unguwa ce mara nisa tana da wani abu guda, sai mutum ya bincika kayansa sau goma kafin ya bar gida amma yana zuwa inda zai je sai ya tuna wani abu mai mahimmanci da ya manta. Hayaniyar yaranta ta ji daga falo da alama fada suke yi. Ba sai an fada ba kusan kodayaushe suka yi fada mai laifin daya ne.
"Lilu zo nan"
Ta daga murya tana kiran danta na uku. Bai zo din ba kamar yadda tayi tsammani sai ma ambaton "sai na rama" da yake yi cikin kuka. Sanin halinsa na rashin kunya yasa ta tashi da kyar saboda nauyin ciki ta bisu falon. Babban mai suna Suhaib akwai saurin fushi. Farha mai binsa sarkin tsokana. Sai Khalil da kowa yake kira Lilu mara kunya, ga taurin kai da saurin kuka.
"Allah nagode Maka" ta ce tana kallon yadda suka hargitsa falon kamar gidan mahaukata. Abubuwa kalilan ne a muhallinsu na asali. Yaran na ganinta suka shiga taitayinsu don sun san hali. Tana sonsu tana tattalinsu amma bata yarda da sakarci ba. Cikin hikima ta iya bi dasu duka da halayensu. Idan kayi abin fada ko duka kuma baka tsira. Khadija mace ce mai zafin nama da sanin ya kamata. Idan suka yi kiriniyar ta gama fadan sai ta koma gefe tana yi musu addu'ar shiriya. Fatanta kowannensu yana girma halinsa mara kyau yana raguwa har ya barshi gabadaya. Yanzu ma sulhu tayi musu ta kuma ja kunnen Farha akan tsokanar kaninta saboda raini da ya gama shiga tsakaninsu. Falon ta sake kallo sannan ta cira kafa ta taka kitchen ta leka ta dawo.
"Ina Nasima?"
"Ban ganta ba." Yaran suka hada baki wurin fada.
A falo ta bar 'yar budurwar mai aikin nata tare da yaran ta tafi sake hada kayan tafiya asibiti. So take ta tabbatar komai yana ciki kada ayi irin na haihuwar Lilu. Sai da aka gama shirya yaro babu shawul babu zanin nade shi saboda tana tsakar nakuda ta hada kayan.
"Ku taso ku kwashe tarkacen kayan wasanku kafin na kira Nasima ta zo ta share falon."
"Wash Mami hannuna..." fadin Lilu yana yarfe hannu.
Hade rai tayi tun kafin tayi magana ya mike tsaye "tashi makyuyaci. Idan aikin baki ne naka yafi na kowa tashi. Amma da an ce za a more ka sai ka dinga langabewa."
Fita tayi tana cije lebe jin kafarta tana rikewa ta zaga bayan gidan tana kwalawa Nasima kira.
Nasima tayi matukar razana da jin muryar uwardakin nata a kurkusa da inda take kwance. Hannuwan mutumin da suke bin jikinta ta doke da sauri tana mikewa tsaye. A razane shi ma ya dauki jakar da ya dawo da ita daga office yana gyara zaman necktie dinsa. Gaba ya yi yana yiwa Nasima inkiya da ta dakata kada ta biyo bayansa. Bata bari ya tafi ba ta bishi da sauri ta ware hannuwanta a gabansa. Mamakin karfin halinta ya yi a wannan yanayin da matarsa take gab da kamasu ya yi saurin zaro kudin da ya san su take nufi ya dora mata.
"Yaya Tahir?" Khadija ta kira shi da mamakin rashin sanin dawowarsa.
Da saurinsa ya tareta ya kama fadan borin kunya. "Me ya fito dake kina jan kafa ke da likita ya ce kina bukatar absolute bed rest? Meye amfanin Nasima a gidan da ba zaki huta ba?"
Murmushi tayi tana yabon irin kulawar da yake bata a ranta.
"Nasima nazo kira."
Hararar Nasiman ya yi "idan kin gaji da aikin ne sai a nemi wata."
Hakuri ta bawa Khadija kai a kasa cikin sassanyar muryarta ta makiran yara. Duka duka da kadan ta haura shekara sha shida, amma fitinarta a boye tafi ta wata 'yar arba'in din. Tamkar hawainiya haka ta kware wurin boye halayenta. Sumumu kasau, macijin sari ka noke shi ne tashenta a wurin saurayinta na farko wani Alhaji a kasan layin.
Sai da suka shiga daki yake cewa Khadija wai yau yaji wa'azin da ake cewa kayi kyauta da dama hagu ba sai ta sani ba.
"Shi ne fa ina shigowa na hango wannan kazamar 'yar aikin taki tayi baya. Da yake kanta kamar dusa aka zuba maimakon kwakwalwa inata kiranta na bata sadaka bata ji ba. Ni kuma na riga nayi niyar yi da fatan Allah Ya saukeki lafiya. Shi yasa na bita bayan."
Kwalla taji ta sauko mata ta farinciki. Tana alfahari da mijinta domin ta san sai an tona ake samun irinsa. A da kam ta wahala akan 'yan matansa amma da dabara ya nuna mata ya bari. Baya son ta wahala kuma baya son damuwarta. Tana cewa wash zai bar duk abinda yake yi yazo gareta. Ga saurin bata hakuri idan ya bata mata rai. Kulawa sosai yake bata duk da mai aikin da ta dauko 'yar makotansu tun tana laulayi. Da zarar ya dawo gida bayan yara sun tafi Islamiyya yake turata daki tayi bacci. Wai nan so yake ta huta da kyau kafin su dawo. A wannan lokacin yake samun kebewa da Nasima ba tare da saninta ba. Nuna mata yake ya tsani yarinyar domin kada ya bar kofar zargi a tsakaninsu.
"Nagode Yayana amma don Allah ka rage hantarar Nasima. Kaga amana take a hannunmu."
Ruwa ya tashi watsawa jikinsa ya nuna mata kamar baya son zancen. Yana bandaki shi kadai yake tsakin zuwanta bayan gidan dazu. Bin mata sana'arsa ce tun yana matashi. Khadija 'yar kanwar babansa ce aka hadasu wai ana ganin idan ya yi aure zai rage. Babu wanda ya bata zabi kawai aka ce ta auri dan uwanta don ya shiryu. Ya kuwa nuna musu shiriyar tasa kamar gaske saboda yana son Khadijan. Da yake kwararren dan duniya ne babu wanda ya san ya cigaba da harkokinsa a waje.
Dawowarsu unguwar nan abin nasa ya kara baci tunda ya ga Nasima komai ya kwance masa. A zahiri yake nuna mata kyama amma a badini tafi kowa. Ita ce kawai a gabansa kuma bashi da burin da ya wuce ganin lokutan da suke samun kebewa a gidan ko a wuraren da ya saba kai 'yan matansa.
Khadija bata san wainar da ake toyawa ba. Da zuciya daya take zaune da kowa. Gidansu Nasima a can kasan layinsu yake kuma sun fi kowa karamin karfi. Abinci a rana bai fi su ci sau daya ba idan an sami faraga. Shi ne fa ta nemi Nasima ta dinga tayata aiki suna biyanta karshen wata.
A ranar da daddare ta sake yi masa maganar dauko kanwarta ko tasa su tayata zama ko da zuwa tayi arba'in ne idan ta haihu.
"Na fada miki ba zuwansu ne bana so ba amma a gani na me zai hana ki dauko waccan yarinyar?" Ya ce da sigar laluma.
Dan jim tayi tana tunani kafin ta fada masa dalilinta na neman ta gida.
"Na fara tunanin sallamarta ne kawai." Gabansa ne ya fadi zai yi magana ta dora da cewa "ka san ko Lilu da yake dana muna fada akan rashin kunya balle Nasima. 'Yan kwanakin nan sai tayi zamanta a baya taki aikin. Idan na kirata a murya sai ka ji lafiya amma a fuska sai in ga kamar tana hararata."
Dariya ya kwashe da ita duk kuwa da fargabarsa ta cikas da korar Nasiman zai kawo masa.
"Shi yasa nifa bana sonta. Ke kuwa da anyi magana sai ki ce marainiya ce. To kema dai naga alama kin gaji da aikin ladan kenan."
"Ba gajiya nayi ba." Ta amsa masa ganin kamar yana ganin asarar kudi yake da biyanta bayan aikin nata babu yawa.
"Zan yiwa mamanta magana ta fara kwana. Idan ta cigaba da halinta sai mu rabu."
Zuciyarsa kamar an zuba ruwan sanyi don farinciki. Nasima tana gara shi a 'yar haduwarsu ta bayan gida. Minti biyar idan tayi sai ya biyata. Idan ta fara kwanan zai fi samun lokaci tare da ita.
Bayan ya tafi aiki washegari Khadija ta je gidansu Nasima da misalin shabiyun rana. Lokacin yara suna makaranta ta barota ita kadai tana wanke-wanke. Tarba ta girmamawa ta samu daga wurin mahaifiyar Nasima. Bayan sun gaisa ta fada mata abinda ya kawota.
Ladidi ta dan bata rai "haba Mamin Suhaib? Yanzu don kina son Nasima ta dinga kwana
har sai kin fito a wannan yanayin da kike? Ai cewa za ki yi kawai ta fada min magana ta zauna."
Dan murmushi Khadija tayi tare da girgiza kai. Don tana taimaka musu ba shi ne dalilin da zai sa su juyata son rai ba.
"A'a gara dai na zo da kaina. Ban fada mata ba ma na ce sai naji amsarki."
"Allah Sarki Mamin Suhaib. Yasin shi yasa nake kara ganin girmanki. Kina da mutumci kuma kin san mutumci. Allah na tuba banda ma kin dage ai da ko kwandalarku ba zan karba a matsayin albashinta ba. Ciyarwar da kuke mata damu kanmu ta wadace mu."
A zatonta sai washegari ko nan da kwana biyu Nasima za ta taho sai gata ta dawo da kaya niki-niki kafin magariba. Lokacin ko cikakkun mintuna talatin bata yi ba da tafiya. Da mamaki Khadija take kallonta tana turo katuwar jaka da wata karama sai ghana must-go.
"Ashe da shirinki."
Tabe baki tayi Nasima tayi ta ce "uhm".
Khadija ta daure zuciyarta daga take taken fitsarar da take gani a wurin Nasima. Shirin nata cikin kankanin lokaci ya bata mamaki ganin bata san da zuwan ba sai da ta gama aiki za ta tafi ta fada mata. Ita kuwa tuni sun gama shirinsu da Tahir.
Mamakin Khadija ninkuwa ya yi da taga Nasima ta nufi dakin baki da kofarsa take a cikin falon da kayanta. Idan tayi tunanin ko mamanta ce ta hada mata kaya kafin ta koma gida to da ya akayi ta san dakin da za ta zauna bayan ko su Suhaib basu sani ba. Kama bakinta dai tayi tana kallon ikon Allah.
Nasima kuwa tana shiga dakin ta buga wani uban tsaki. Ta lura Khadijan sai wani fiffika take yi ita mai miji. Mijin da yake a tafin hannunta matarsa har wani daga kai za ta yi mata? Sake yin tsaki tayi da ta kula tsohuwar katifarsu Lilu ce aka ajiye mata a dakin da wankakken bedsheet da pillow.
"Kut! Ai wallahi gado za ka zo ka saka min a dakin nan ko na kama gabana. Lallai ma Khadijan nan kin rainani."
Shu'umin murmushi tayi da ta tuna tuggun da ta shirya mata. Lokaci ya yi da Tahir zai bata nata 'yancin ko ta kwata ta karfi. Ba zai yiwu bane ya cigaba da raina mata wayo. A gaban matarsa ya fada mata magana a bayan idonta kuma ya dinga lallabata. Da Tahir ya dawo Nasima tana daki ta ji hayaniyar yaran.
Da saurinta ta mike ta gyara kwalliyarta ta fesa turare ta fito.
Shirt dinsa ce a jikinta ta hada da zani da dankwali iri daya.
"Daddy oyoyo" ta ce da karamar murya kai a kasa.
Kallonta ya yi sama da kasa wani abu na fizgarsa gareta. Ba don idon yara ba da sai ya biya ladan wannan ado. Gwalo tayi masa karaf a idon Khadija wadda ta fito daga kitchen da tray a hannu. Nasima sai ta wayance ta kuma yin gwalon.
"Nima na rama Lilu." A zuwan wasa suke yi dashi.
Tahir sai ya karbe da cewa "anya Khadija ba rainon mutum hudu ki ke ba? Ita da ta zo taimaka miki ta buge da wasan yara."
Bai bawa Khadija damar yin magana ba ya bukaci ta tara masa ruwan wanka. Daki ta nufa zuciyarta cike da wasi-wasin abin da ba ta son zargi. Abincin ma daki ta kai masa a ranar. Sai da suka kwanta ta sako zancen shirt din.
"Ni fa kamar shirt dinnan taka da nayita nema wancan wankin na gani a jikin Nasima dazu."
'Jaraba sai da ta gane' ya ce a zuciyarsa.
"Oh ashe bamu yi maganar ba. Rannan na tsinceta a bayan mota tayi datti. Ina jin daga kayan wankin ta fado. Na dauko zan yar shi ne da ta gani ta ce tana so."
"Ka dai san ina bata kaya. Idan kari take bukata ai da sai kayi min magana. Rigarka ai ba abin sawarta bace."
Da bacin rai take magana ya soma bata hakuri. Zuciyarta sam babu dadi har wani zazzabi taji yana neman kamata. Abubuwan da take ta son turewa game da Nasima sun sami wuri sun manne mata a rai.
Bayan kamar minti arba'in tana fama da guntun ciwon marar dake tsungulinta taji kamar hannun Tahir a saman fuskarta. Da alama karkada hannun yake ya gani ko tayi bacci. Da gangan tayi motsi ai kuwa ya dauke hannu ya kwanta da sauri. Juya mata baya ya yi ta bude ido ta tabbatar baccin karya yake yi. A hankali tayi kwafa ta sake rufe ido. Ba afi minti goma ba ya sake kada hannun. Wannan karon luf tayi takaici na nukurkusarta. Akwai abin da yake boye mata. Fatanta Allah Yasa ba Nasima bace. Tana jinsa ya tashi ya shiga bandaki. A cikin kunnuwanta taji ana bude dakinsu shi ma ya bude bandakin. Sannu a hankali ta bude ido kadan don kada a san ta farka ta hango Nasima a bakin kofar. Abin ya daina bata mamaki ma tunda har take da karfin gwiwar zuwa dakin. Da yatsa Nasima take yafito Tahir da ya fito daga bandaki, shi kuma yana nuna mata Khadija wadda duhun dakin yasa basu gane ta bude ido ba. Barazanar shigowa Nasima tayi masa ya yi murmushi yana yi mata inkiya ta karaso mana. Ba kunya ta sako kafa a kofar dakin ya yi saurin karasawa ya dagata a kafadarsa suka yi gaba. Kememe Nasima taki yarda a koma dakinta wai ita a gadonsa za ta kwanta. Sanin rigimarta yasa ya ce da Khadija su kwana a nata dakin.
Rufe kofar da ya yi a hankali ya yi daidai da matsanancin bugun zuciyar Khadija. Hawaye take yi ba tare da ta sani ba ta tashi da kyar ta bude kofar ta fita. Dakin Nasima ta nufa bata same su ba sai ta nufi na Tahir. Daga bakin kofa take jin dariyar Nasiman tana rokonsa ya daina yi mata cakulkuli. Shi kuma yana cewa ta rage murya.
Sai da ta tsaya ta hadiyi wani yawu mai daci sannan ta murda kofar da karfinta. Ganin da tayi musu yasa komai na jikinta tsayawa cak. Murdawar cikinta ce ta dawo da ita duniyar mutane ta rike cikin tana salati.
AYA MAFARIN IRGA.
Duk hukuncin da uwa za ta yanke akan 'ya'yanta tana yi ne da tunanin hakan shi ne maslaha a rayuwarsu ko da kuwa a gaba shi zai zamto mafarin kukansu.
Kwakwalwarta babu abin da take hasko mata sai yanayin da ta ganshi tare da Nasima lokacin da ta farfado. Idanunta a rufe amma hawaye yana sintiri daga kwarmin idanun zuwa kunne ya sauka akan pillow. Daga kamshin da take ji na dakin kadai ta fahimci a gadon asibiti take. Sakayau take jin jikinta babu wani nauyi sai na zuciyarta da ta koma tamkar dashen dutse. Cikinta ta shafo a hankali taji babu tokarewar nan ta dan da ya kusa zuwa duniya. A firgice ta tashi wani irin radadi na ban mamaki ya soki mararta.
"Bar garaje Khadija jikinki da danyen ciwo." Cewar Yakumbo mahaifiyar Tahir.
Da yake bata san da ciwon ba tashin bai wahalar da ita ba kamar komawa ta kwanta. Ita ba a kwance ba ita kuma ba a zaune ba haka ta saka hannuwanta ta dafe gefen gadon don kada ta fada da karfi. Yakumbo ce ta taimaka mata ta koma ta kwanta tana rarraba idanu. Tambayoyi ne akan harshenta ta kasa amayar dasu saboda sabon al'amarin da take ji a jikinta.
Yakumbo ta sake cewa "Bari na fadawa nos kin farfado" har ta kusa kofa ta dawo ta dafa mata kai "sannu kin ji. Allah Ya baki lafiya."
Khadija ta kula da hawayen da Yakumbon ta dauke daga gefen idonta kafin ya sauko. Jikinta sai ya kara yin sanyi da tunanin ko me yake faruwa ba alkhairi bane.
Yakumbo bata jima da fita ba Mamanta ta shigo tare da kannenta da su Farha. Kowa sannu yake yi mata tana amsawa da ka. Sallamar Tahir taji ta dawo mata da duk wasu lokuta da sai a yanzu take fahimtar raina mata wayo suka yi shi da Nasima. Runtse idanu tayi tana jin Mamanta tana tambayarta ko cikin ke mata ciwo ta girgiza kai. Shi kan shi Tahir din ganin idonta biyu sai da yaji kamar ya koma saboda firgici. Saukinsa daya yaransa da suke wurin Mama jikinsu a sanyaye da yanayin Maminsu. Yana da tabbacin ba za ta yi wani abu a gaban 'ya'yanta ba.
"Ku bashi wuri mana ya zauna kun yi
are-
are akan gadon." Mama ta furta tana nunawa kannen Khadija hanyar fita daga dakin.
Mutum biyu ne dama suka zauna a gefe sai suka tashi amma basu fita ba. Tahir ya kalli Khadija ba shiri yau shi ne da sauke kai kasa. Tsoronta ne ya mamaye masa zuciya saboda irin kallon da take yi masa babu komai a cikinsa sai tsana da disappointment.
Mama kuma ta kara masa zafi da cewa "Ina mai-aikin taku yau? Kodayake ya kamata yau ta huta."
Dawowar Yakumbo da likita ce ta taimaka masa bai bayar da amsar da za ta zama zallar karya ba. Kukan jinjiri ne ya biyo bayan shigarsu dakin a hannun Matron. Da dan murmushinta ta nufi gadon bayan gaisawa da jama'ar dakin.
"Ina nan ni dai. Doctor ki gama dubata ta bawa bebina abincinta mun gaji da shan madara."
Kallon kunshin shawul din Khadija take yi a lokacin da likitar ke yi mata tambayoyi game da jikinta. Babu abin da take fahimta sai gyada kai da take yi idanunta fal hawaye akan dan da bata ganin fuskarsa.
Likitar sai ta kalli Yakumbo da alamar tambaya "Maman Khadija ya naga kamar bata san me ya faru da ita ba?"
"Farfadowarta kenan na taho kiran Nos sai na hadu dake."
Da ido Maman ta kalli kannenta suka fice tare da su Suhaib. Tahir kamar ya nutse ya kasa kallonta. Likitan ce ta karbi bebin ta dora mata a cinya.
"Khadija kin san cewa tun farkon cikin nan akwai matsala har kina yawan zubar da jini ko?"
Bata amsa ba sai bin fuskar yarinyar da har kunne an bula mata take da kallo.
"Yau kwana kenan..." da sauri ta daga kai ta kalli likitan jin cewa kwananta biyu bata hayyacinta "maigidanki da mai-aiki sun kawoki cikin dare kina ta zubar da jini a sume. Ta ce zamewa ki ka yi a toilet wurin faduwa cikin ya bugu da sink. Kafin ki farfado faya ta fashe ga jinin bai tsaya ba."
"Hummm" ta ce da guntun murmushi idanunta akan Tahir. Yakumbo tana kallonsu ta kuma ha yadda yaki daga kai ya kalli matarsa.
"Ba cs din bane kadai Khadija harda mahaifar muka cire."
Sautin da taji ya ziyarci kunnuwanta ga dukkan alamu shi ake kira saukar aradu a yanayin tashin hankali. Zabura tayi za ta tashi a karo na biyu tana fama dinkin kasan mararta.
"Kwanta don Allah kada ki yiwa kanki rauni. Kaddara bata wuce kowa. Gashi an ciro miki jaririyarki lafiya kalau."
'Yar ta rungume ta fashe da matsanancin kuka.
"Ki yi hakuri Khadija. Mun yi iya yinmu amma jinin yaki tsayawa. Taimakon Allah ne kawai muka sami baby din tunda sun ce basu san tun yaushe ki ka fada kan cikin ba." Likitar ta karasa yi mata bayani.
Kukanta bai tsaya ba kowa na dakin ya tausaya mata. Yakumbo kuwa haka kawai tun farkon labarin dama bata wani yarda ba. Yanayin Khadijan a yanzu sai ya karfafa mata zarginta. Don ta tabbatar sai cewa tayi da Tahir ya rarrasheta mana. Mugun kallon da Khadija ta watsa masa wanda ya dakatar dashi ya bata amsarta.
"Mijin naki ki ke yiwa wannan kallon don rashin hankali kamar shi ya dora miki lalurar." Mama ta ce da ita cikin fada.
"Allah sarki" inji Matron "kar ki ga laifinsa da kyar ya yarda yasa hannu. Yarinyar da suka zo tare ce ma ta dinga tausarsa akan ya amince a cire saboda kada a rasa ki."
Numfashinta neman daukewa ya yi a wannan lokaci. Wato duka karairayin zuwanta asibitin sai da Nasima ta ingiza shi ya yarda aka cire mata mahaifa. Bata san me za ta yi musu ta huce ba. Ya ci amanarta ya kuma cutar da ita.
Gani tayi su Mama na fita daga
dakin tayi murmushin takaici. Ta san irin abin nan ne ace a basu wuri ita da mijinta. Ana rufo kofar ya taho gareta da sauri.
"Nasima don Allah kiyi hakuri ki rufa min asiri. Na san ban kyauta ba amma don Allah in ci darajar 'ya'yanmu."
Tahir ya cika babban munafuki har tana mamakin yadda akayi ta kasa daukan haske ko sau daya. Saboda nisan da ya yi shi yasa bai ji kunyar kiranta da sunan mai-aikinta ba.
"Khadija. Suna na Khadija." Ta ce dashi muryarta a dake.
Bakinsa ya doke da sauri ya sauka kan gwiwoyinsa.
"Ki yafeni Khadija."
Ba shi take kallo ba. 'Yarta ta karshe a duniya take kalla tana nadamar biyayyarta a baya. Da bata amince ta aure shi ba da basu hada jini da mazinaci ba.
"Na yafe maka tun kafin ka roka duk da baka yi nadama ba."
"Nayi. Wallahi nayi nadama sosai."
"Baka yi ba. Na rantse da Allah da kayi nadama da baka taho da ita kawoni asibiti ba. Da bata zauna jinyata har ana cigiyar rashin zuwanta a yau ba."
Busassun labbansa ya lasa a hankali. Ya san ba za ta taba yarda ba amma shi ya san cewa ya yi nadama. Yana dai yiwa Nasima irin son da ba zai iya hakura da ita ba. Idan kurar nan ta lafa aurenta zai yi ya kama mata gida daban. Zai cigaba da zama da Khadija saboda wani sashe na zuciyarsa yana ganin girmanta. 'Ya'yan da ta haifa masa kuma duk munin halinsa yana sonsu kuma ya san suna da hakki a kansa. Muryarta ce ta katse masa tunani.
"Kafin a sallameni ka rubuta min takardar saki. Ba zan tona maka asiri ba saboda bana son duniya ta nunawa 'ya'yana yatsa akan halinka. Kai dai ka tanadi abin da za ka fadawa iyayenmu tunda karya a jininka take. Sharadi na daya ne." Kallonta ya yi "kada ka yarda ka dora min laifi a matsayin dalilin rabuwarmu. Ina fata ka fahimceni."
"Ba zan iya sakinki ba. Khadija ina sonki."
"Ka daina yiwa kanka karya akan abin da baya zuciyarka."
Zancen gabadaya baya so ayi shi a asibiti amma ya san ba shi da hurumin cewa tayi shiru. Yana son cigaba da zama da ita amma ba ya jin zai zama adalci gareta ya tursasata ta cigaba da zama tare dashi bayan yanzu ya fara son Nasima. Tunda dai za ta rufa masa asiri ya san komai zai zo da sauki. Juyawa ya yi zai fita ta kira sunansa.
"Tahir! Za ka yi nadama a nan gaba sai dai ina tsoron kada ta zo a lokacin da komai ya lalace. Ina gudun kada hakkin 'ya'yan da ka batawa rayuwa ya rataya a wuyan 'ya'yana."
Da yake maganar ta tsorata shi bai san lokacin da ya ce "wallahi ba ni na bata Nasima ba a haka na sameta."
Kallon da tayi masa ne ya sa shi jin nauyin furucinsa. Sunkuyar da kai kawai ya yi yana jiran ya ji me za ta ce sai yaji shiru. Juya masa baya tayi tana zubar da zazzafar kwalla. Ta so Tahir a lokacin da bata da zabin da ya wuce bin umarnin iyaye. Ta sadaukar da farincikinta na son waninsa saboda tsira daga azabar Allah. A yau ta rasa mahaifi da kuma igiyar auren da take jira ya datse duk a dalilinsa. Ita mai iya tsaya masa ce ya kara aure idan yana so. Shi yasa take mamakin dalilinsa na yin zina. Zinar ma ta fuskar wulakanci gareta. Kalaman mahaifiyarta take tunawa a wani lokaci da ya wuce tana yiwa kaninta fada zai tafi jami'a a wani garin.
"Zina masifa ce. Idan ka yi da 'yar wani kai ma sai ta zagayo jikinka inda za ka ji ciwo mai radadi. Ko ni, ko 'yan uwanka, ko iyalinka ko 'ya'yan cikinka"
Addu'a ta soma yi musu tana fatan Allah Ya karesu daga wannan mummunar dabi'a. Za ta sadaukar da rayuwarta wurin kula da tarbiyarsu da fatan rufowar asirin mahaifinsu. Aure kuwa ta yi ta gama. Abin da ya yi saura ba rayuwarta za ta yi amfani dasho ne wurin ganin yaranta sun sami ingantacciyar rayuwa.
Bayan kwana biyu suka sake kebewa da Tahir a dakin. Tuni tayi masa akan takardar sakin ya ce da ya saketa gara ta tona masa asiri. Amsarsa ta tayar mata da hankali ta kuma sanyata tunanin dalilinsa na sauyawa bayan da ya amince.
Yanayinta ya kalla a ransa yana yabon kaifin basirar Nasima. Yana fada mata zai saki Khadija ya aureta ta fitittike ta ce sam bata yarda ba. Nuna masa tayi duniya za ta zagesu idan suka yi haka. A ranta kuwa gudun kada ya bata rikon 'ya'ya take yi. Tafi son ayi auren a gaban Khadijan ta ganta suna masu matsayi daya a gidan. Ita ta bashi shawarar wadancan kalamai domin a cewarta Khadija za ta zauna don 'ya'ya. Tunda aka kai yanzu maganar ganinsu bata tashi ba to ya sani cewa indai akan 'ya'yanta ne za ta rufa masa asiri.
Ga zahiri ya gani. Sai ga Khadija tana kuka tana rokonsa saki kamar ba ita ya yiwa laifi ba. Da aka murda kofar dakin da sauri ta share hawayenta harda karyar ciwo ke cinta. Da wannan barazanar ya samu ya rufe bakinta har aka yi sallama. Da wani ya san abinda uban 'ya'yanta ya aikata ko da kuwa mahaifuyarta ce gara ta cigaba da zama dashi ko babu soyayya. Ba za ta so labarin gamon da tayi ya taso a lokacin da wani alkhairi ya doso rayuwar 'ya'yanta ya wargaza ba.
KHADIJA: A jerin ire-iren iyaye mata ta fado a jinsin masu shanye komai domin 'ya'yansu. Ta yarda ta fanshi zubar hawayensu ta hanyar sadaukar da farincikinta. Karesu zata yi muddin rai kada kazantar mahaifinsu ta wargaza rayuwarsu a gaba.
*****
KIRIKASAMMA
1995
Ta san ya ji ta sarai amma bata sare ba ta cigaba da binsa da roko da laluma saboda muddin ya sa kafa ya fita yau to magana ta kare. Kiran sunansa tayi da dan karfi ganin ya kusa kofar fita. Indai bukatarta za ta biya tayi alkawarin jure duk wani jan rai da wulakanci daga Inuwa.
"Malam inata magana baka ce komai ba har za ka fita."
A fusace ya juyu kamar zai mangareta ya soma fada.
"Ke dai Mari da mayya ce ki ka kama mutum Yasin sai buzunsa. Haba! Ni na taba ganin bakin naci irin wannan? To duk jarabarki sai ya tafi yadda ake tura 'ya'yan kowa."
Hargaginsa ya fito da sauran matan gidan daga bangarorinsu. Zaman kauye babu abin yi har jiran barkewar rikici suke don a bawa ido abinci. Gidan nasu kuwa an sami karuwar jama'a, kama daga matan da ake kara aurowa zuwa hayayyafar da ake yi kusan duk shekara.
"Rigimar me ku ke yi da rana tsaka Inuwa?" Mal. Sa'idu babban wa ga mazam gidan ya tambayesu amma aka rasa mai bashi amsa.
Mari sadda kai tayi kasa zuciyarta tana bata cewa hakuri kawai za ta yi wannan karon a tari gaba. Mal Sa'adu da sauran 'yan uwan Inuwa babu mai goyon bayanta. Maganar nan kuma ko Inna Mairo ba bayanta za ta bi ba.
"Kya yi shiru kuma yanzu? Ai sai ki bude baki ki fada musu abinda ki ke rokona" cewar Inuwa yana duban yayansa "wai makaranta ce bata so a tura Abbati."
"La haila ha illallahu..."
Mata sai tafa hannuwa kamar sun ji gagarumin sabo. Shi kuwa Mal Sa'adu cewa ya yi maganar ba ta tsaye bace su biyo shi sashensa.
Durkuso Mari tayi a gefen tabarmar da Inuwa ya zauna. Bata ma yi niyyar zama ba domin rashin kunya za ace tayi. Mal Sa'adu ne ya yi magana cikin jimami.
"Yanzu ke Mari karatun Muhammadiyyar ne ba kya so? To ko dai kin canja addini ne bamu da masaniya?"
Kai da hannuwa ta karkada a tare "a'a Malam. Cewa nayi a barshi ya cigaba da karatun a nan ba sai an kai shi Kano ba almajiranci ba."
Matan gidan dama ba kaunarta suke sosai ba saboda fifikon da Inna Mairo ke nunawa a kanta. Gashi tayi karatu har matakin aji uku a firamare kafin Inuwa ya aurota. Su kuwa babu arabi ba boko. Anyi musu baiko tun tana shekara goma. Sai ta tafi aikatau Dutse inda ta sami wayewar kai. Gidan da tayi aikin suka saka ta a makaranta. Sun so a barta ta karasa amma gidan su Inuwa suka ce idan bata dawo anyi auren ba a dawo musu da kudinsu. Haka nan tana ji tana gani aka rabota da ilimin da ta fara jindadinsa. Wannan ne yasa ta dage aka kai 'ya'yanta firamaren garin sannan suna zuwa makarantar allo da ta dare. Da sana'ar dinkimta da take dan samun kudi take yi musu hidimar makaranta. Su biyar ne yanzu. Abbati babba da mai binsa Sani sai 'yan mata uku. Al'adar gidan ta tura yara maza almajiranci kwatakwata bata burgeta. Ta ga yadda almajirai ke watangaririya idan sun tafi karatu, bata marmarin 'ya'yanta suyi irin wannan rayuwa.
"Lallai Mari. Ke ko 'yar kunyar nan ta dan fari ma ba kya ji har kike kallon idon Malam kina cewa a bar miki da a gabanki?" Uwargidan Mal Sa'adu ta furta da sigar nuna tayi ba daidai ba.
"Ko ma dai mene ne wannan sabon abin da ki ka zo dashi ba al'adar gidanmu bace. Zuri'ar gidan nan suna zuwa almajiranci tun talan-tale. Naki dan da bai fi na kowa ba shi ma zai je. Sai dai kuma idan zaki sake masa uba." Mal Sa'adu ya kare da tsorata ta.
Idan aka ce ta sake masa uba tamkar ana tuhumarta da laifin haifar dan da ba na sunna bane. Muryarta a karye ta bashi hakuri "Allah Yasa hakan shi ne mafi alheri."
"Karatun allo hairan ne! Abbati zai je kamar sauran 'yan uwansa ya rubuce sittin kuma ya haddace shi."
'Nima haka nake fata' Mari ta ce a ranta tana mikewa tsaye. Jiki ba kwari ta shiga dakinta tana jin kamar an zare mata laka. Wannan karon an mata fin karfi amma ba za ta yarda badi a kai Sani ba.
Kafin ranar tafiya ta shanya kanzo gari guda ta gyara masa. Man gyada ma ta soye shi da albasa ta kuma daka masa yaji. Tayi kuli-kuli, carbin malam, hallaka kwabo da duk wani abu da take tunanin zai ci daidai karfinta. Nasiha kuwa har ya soma gajiya da ji.
"Ka yiwa malaminka biyayya Abbati."
"Banda kwadayi ko dauke dauke."
"Idan an turaku bara ka ce na hana. Ga kayan abinci nan ina ta hada maka hatsi. Zan fadawa Babanka ya bawa malamin. Idan ya so in sun dora sanwa a dinga dibar maka."
"Abbati kada ka je bara fa. Daga cikin gidan wani zubin sai an zageka an zagi uwar da ta kawoka duniya kafin a baka kwantai."
"To Baaba" yake cewa ga duk nasihar da fadan nata. Har yanzu bai san ma'anar karatu da ake cewa za'a kaishi tare da sa'ansa dan yayan Inuwa ba. Yayyansa da suka tafi garuruwa daban daban yake sha'awa. Idan zasu zo suna dan kullo tsarabar birni su kawo. Kuma shi da Baaba ke son ya zama likita yanzu ne zai yi karatu na 'yan birni ya fara allura.
Mari tayi kuka sosai ranar da zasu tafi. Bai taba nisa da ita ba musamman saboda tsoron fadansa. Indai rigima ake yi da wuya ka ga Abbati a ciki. A gidan manya da yara idan ka cire mahaifansa da 'yan uwan babansa ana tsokanarsa da Abbati solobiyo. Rashin kuzarinsa yana daga cikin manyan dalilanta na son ya zauna a gida. Kazalika shi ne ya kara rura wutar kiyayyarta da zuwansa almajiranci. Banda iyayen sun riga sun farlantawa kansu kai yaransu maza akwai makarantu yanzu a garin nasu na ilimin islama.
Har soro ta fito tana kuka da zasu shiga a-kori-kurar da ta zo daukarsu. Hawaye take wani na bin wani tana ta nanata masa abubuwan da ta fada masa.
"Mu kuwa kamar tsinar namu 'ya'yan muke bamu san zafin nakuda ba." Cewar guda cikin faccalolinta.
Wata ta amshe da cewa "mu da aka jima ana daukar namu ba."
"Wai kuma a haka fa don dan fari ne. Wannan da Sani ne zai tafi sai tayi mana karamin hauka."
A gigice ta kalli amaryarta da ko haihuwar fari bata yi ba tana neman ballo mata ruwa. Ranta a bace ta ce,
"Bakin ki ya sari danyen kashi. Sani ba zai je bara ba da yardar Allah. Wannan ma don anfi karfina ne."
"Ai kuwa zan nuna miki babu dan da za ki fi karfinmu a kansa. Kai Inuwa.." Mal Sa'adu dake bayan matan ba tare da saninsu ba ya yafito kaninsa "tsayar da direban nan ka hado kayan Sani."
Ba Mari ba shi ma sai da ya razana. Sani shekararsa tara ga karamin jiki kamar dan bakwai.
Mal Sa'adu ya juya a fusace ya kira ragowar kannensa. Duk wanda dansa sai badi zai tafi ya ce a hada masa kaya yau. Sauran matan basu ji dadi bane saboda basu shirya ba. Mari kuwa da ta gama magana da kanwar Inuwa dake aure a Kazaure sai da ta kusa haukan da ake kira mata. Sun gama shiri za ta dawo ta ce a bata Sani saboda bata da namiji sai ta tura mata kudi a kaishi bodin.
A buhu Inuwa ya cusa kayansa tana kuka tana tumami amma Mal Sa'adu ko gezau. Inna Mairo ma tayi masa magana ya ce babu matar da za a auro tafi karfinsu. Idan bai yi haka ba sauran ma zasu raina mazajensu ne.
Kukan Mari a kofar gida har makota ana ji. Ana saka Sani a mota ta sauko dashi tana magiyar a barshi ta yarda a tafi da Abbatin. Ita a nufinta ko shi kadai ya yi bokon ya zama wani abu a gaba zai taimakawa yayansa. Shi kuwa Abbati da zuciyar kuruciya sai ta ayyana masa mahaifiyarsu bata kaunarsa tafi son kaninsa. Kukan shi ma ya saka ta mika hannu za ta sauko dashi Inuwa ya daka mata tsawa.
"Ki mayar dasu ko su sauko ku kama hanyar gidanku tare." Ransa ne ya baci da jama'ar da ta tara musu ana ta gulmarta wai bata da rikon addini.
Mutanenmu da matukar tsoron kalmar saki. Ba arziki ta saki yaran tana zaman 'yan bori a kasa. Tana ji tana gani motar nan tayi gaba aka tafi da 'ya'yanta. Abbati za'a sauke shi a Kano shi kuma Sani da sauran yaran a Zaria saboda can ne suke da manyan yayye.
MARI: Ga Mari ba mutuwar auren kadai take tsoro ba harda inda za ta kai yaran. Iyaye basa raye ga talaucin kauye. Idan aurenta ya mutu kannensu ma masomin tagayyarar rayuwarsu kenan. A wannan lokacin maslahar da ta hango bata wuce ta sadaukar da mafarkin cigaban manyan 'ya'yanta akan rayuwar kannensu ba.
*****
KANO
1995
"Masu gida. Magadan Alhaji. Ku zo ku dauka na gama rabawa" Asabe ta kira 'ya'yanta tana rangwada murya.
Gajeren tsaki gami da murmushi Innayo tayi ta cigaba da barar albasar gabanta. Ina abin gado a tattare da Alh Rabi'u har da mutum zai yi tinkaho? Tabbas arzikinsa ya karu a shekarun nan haka kuma tsiya ta rashin son wadata iyalinsa ta kankama. Innayo bata sake haihuwa ba tun Hasiya. Asabe kuwa ta jera maza uku bayan wanda suka yi goyo tare lokacin Hasiya. Salon kishin Asabe ya dade da dena bata mata rai. Ita bata yarda bane sai ta cusa mata haushi ta kowane hali. Innayo kuma bata da wannan lokacin. Har yanzu da ta aurar da duka 'ya'yan uwargidan Alh Rabi'u bata hakura da dena neman kudi ba. Yadda ta gina su haka take ta fafutukar gina nata. Dukkansu sai da suka gama sakandire da guminta aka yi bikinsu.
Abu daya ke yi mata ciwo a rai wanda yasa ta dada jajircewa akan 'ya'yanta. Tun lokacin bikin A'i babbar 'yar Alh Rabi'u mahaifiyarsu ta sake bayyana a rayuwarsu. Mijinta Kansila ne a lokacin suna ta damashere da dukiyar talakawa. Innayo bata son auren ta kuma fadawa A'i, amma sai ta tsallake ta sanar da mahaifiyarta Laraba. Ita kuma ta tsaya mata sun ga mai arziki. Alh Rabi'u dama tuni ya mika wuya ya yi mubaya'a ga wannan hadi. Tana ji tana gani akayi auren. A'i da kannenta suka koma jikin mahaifiyarsu. Ita dai bata fasa yi musu komai da ta saba ba amma tsakaninsu babu wannan mu'amalar ta uwa da 'ya'yanta. Komai nasu na shawara da Laraba suke yi. A ranta ta kan ce uwa uwace! Shekara na zagayowa Kansila ya biyawa A'i, Alh Rabi'u da Laraba hajji. A gabanta kannen A'i suka shigo da tsaraba mai tarin yawa ita kuwa da 'ya'yanta aka bisu da dan madina da bagaruwa. Alh Rabi'u kuwa 'yan mazansa ya gwangwaje ya bata robar zam-zam irin 'yan kulalan nan adadin 'ya'yanta.
"A sha a sami tubarrakin Annabi Isma'ila." Ya ce lokacin da ya ajiye mata a gefen katifa.
Idan ta ce wannan abu bai yi mata ciwo ba tayi karya. Ita ma za ta so nata 'ya'yan su zame mata inuwar hutawa a gaba. Auren irin su Kansila da ta san dukiyar yawanci zuwa take ta tafi da an gama gwamnatinka ne bata so. Sai ya zamana bata da dare bata da rana. Sana'ar abinci ta iya kuma ita ta kara fadadawa.
Muryar Zara ta ji wadda Hasiya take bi tana magana bakin tsiwar nan a gaba ta zumburo shi.
"Ni dai gaskiya ki canja sana'a Innayo wallahi gulmarmu ake yi a makaranta. Ko? Ko Hasiya?" Ta waiga bayanta inda Hasiya ta tsaya jikin kofa.
"Ni dai ban sani ba." Hasiya ta ce tana ja da baya gudun fadan Innayo.
Haushi ya turnuke Zara ganin Hasiya za ta bata mata shiri ta harareta.
"Banza kawai. Ke kin fi so a dinga jin tsamin geron 'yar tsala a jikinki duk safiya a makaranta"
Ita da gaske take son mahaifiyar tasu ta sami wata sana'ar ba ta abinci ba.
Sai da Innayo ta gama barar albasar ta daga kai "yau ke ce da yin danmalelen dare. Ga albasar nan ki yanka kanana Hasiya za ta karbo tumatir ki hada."
"Innayo" Zara ta kira ta kamar tayi kuka.
"Mai abinci ta fi almajira kuma ta fi mai shiga makota tana bani bani. Idan kin raina min sana'a ni ki ka raina." Ta bata amsa ko kadan muryarta bata daga ba.
Daga gefensu Asabe ta tsoma baki tana dariyar shakiyanci "sunan wani wai shi girkau. An tasa yara a gaba ana ta kone musu sinadarin kyau da wutar icce ai dole su yi bore. Shiga makota bani bani kuwa dabara ce sai mai wayo. In mutum ya isa ya gwada mana."
Innayo bata kula ta ba sai 'ya'yanta da ta bi da kallo daidai suka fahimci ma'anar kallon. Daki suka shige Zara tana botsarewa ita a dole bata son aikin.
"Tara ki nake yi Zara. Idan ki ka kaini bango kin san sauran" cewar Innayo daga bakin kofa.
Zara bata kara cewa komai ba. Innayo na fita kamun bikin 'yar kanwarta da yamma ta turawa Hasiya aikin da jan kunnen kada ta sake ta ce ita tayi.
Bayan Hasiya ta gama ta fita waje kiran almajirin da yake kai musu bakin hanyar wata makarantar dare tayi. A kofar gidansu yake zama da an yi magariba. Tana jiran karasowarsa daga daya tsallaken layinsu a-kori-kurar da ta dauko su Abbati ta zo ta wucesu zuwa makarantar dake cikin unguwar.
"Kai ina Munzali?" Suka ji muryar Asabe daga bayansu. Rabonta da shi tun kafin ta sauke abincin rana. Shi ne babban danta namiji.
"Ban gan shi ba" yaron ya bata amsa.
"An ce min tare ku ke zuwa filin kwallo."
"Bai je ba yau. Su Shazali ya bi yawo."
Da ta bi ba'asi sai ta gane su Shazalin wasu matasa ne almajirai kamar yaron Innayo din. Hankalinta ne ya soma tashi saboda an kusa Isha'i.
"Cire wandonka na ce" Shazali ya ce da fada saboda bata masa lokaci da Munzali ke neman yi.
Idanu a waje cike da tsoro Munzali ya sake kama wandonsa ya kankame.
"Na ce maka bana jin komai. Ni gida zani Asabe za ta dakeni idan ban koma ba."
"Kai ma ka tsaya sai wani lallaba shi kake yi. Dalla bani wuri na nuna maka yadda ake yiwa sababbin shiga." Cewar wani dan kwaya abokin Shazalin.
Matsawa ya yi ya turo masa Munzalin da ya fara turjiya gabansa. Shi ya rike hannuwan abokinsa kuma ya dauke Munzali da mari kafin ya zare wandon ya yi wurgi dashi.
Dariyarsu ce ta fara karade kangon kafin ihun azaba da Munzali ya saka yana kiran Asabe ta cece shi.
BIYU IDANUN DABA.
Duk duniya babu mai rufa maka asiri sama da mahaifiyarka. Komai lalacewar da sai ta kure sai kuma ta jure za ta iya fadawa duniya. Da mai kyakkyawar zuciya da ma mai akasinta duka suna yi ne domin kada rayuwar dansu ta lalace a wani mataki. Amfani ko kuskuren yin hakan ga dan da akayi dominsa kuwa gaba ce kadai za ta nuna.
Tsohuwar naira biyar da ta gama shan wahala tsakanin kwandastoci da direbobin tasi ta yayyage Shazali ya dauko daga aljihunsa.
"Ungo ka tafi gida." Ya sakawa Munzali a aljihun gaban rigarsa.
Yaron da kyar yake tsayuwa saboda bakar azabar da ya sha a hannunsu. Da ya tashi tsaye ma kafafunsa duka rawa suke yi.
Warce kudin abokin nasa da suka tafka ta'asar tare ya yi yana magana irin ta takadiran 'yan kwaya.
"Kai da talo-talo ne wani sa'in. Banda hauka ya za ka ce ya tafi gida bamu yanka masa wainin (warning) ba" kwalar Munzali ya ci ya fizgo shi gabansa ta karfin tsiya sai da ya yi kara "idan ka sake ka fadawa wani abin da muka yi maka sai na yanka uwarka. Ka san dai na santa ko? Ko ba Asabe Gantali ba ce gyatumar taka?" Ya karashe da yi masa tsawa.
"Ita ce" Munzali ya amsa da sauri jikinsa na bari. Ga ciwo ga tsoro.
Sai da suka tabbarar ya gama tsorata sannan suka kama gabansu. Tsoro bai bari ya zauna a wurin da sunan ciwo ba. Ga duhu ga kukan kwari da kananan dabbobin da suka mamaye kangon. Da jan kafa ya fito yana cije baki tare da runtse idanu. Idan hawaye ya taho sai ya sharesu da sauri saboda ya rike kashedin da aka yi masa. Tafiyar minti shabiyar zuwa gidansu sai da ya rubanya ta.
Asabe sai kai gwauro da mari take yi wurin neman Munzali. Ta shiga duka makota gidajen da yake da abokai bata same shi ba. Nemansa take yi saboda nutsuwar kanta ba wai don Alh Rabi'u zai yi mata fada ba. Tarbiyar yaran a wuyan uwar da ta kawosu duniya ya rataya a nasa tunanin. Ummakati yayarsa ta gama karantawa wasu gidajen da za ta je ta fita ita ma ta sake daukar mayafi.
Tana isa soro Munzali na shigowa. Basu da wutar nepa amma akwai hasken farin wata saboda wurin babu rufi. Kunnensa ta jawo iya karfinta sai da ta durkusar dashi a gabanta sannan ta hau shi da fada tana jibgarsa. Bata taba yarda hukunya 'ya'yanta a gaban Innayo. Kullum nunawa take nata 'ya'yan basa laifi.
Munzali bai yi kuka ba ko ya roketa tayi hakuri kamar yadda ya saba idan ya yi mata laifi. Zazzabi yake ji ga ciwo babu wani sauran kuzari ko da na kuka ne a tare dashi.
"Shegen yawon tsiya kamar wanda makiya suka sako a gaba. Ban hanaka yin dare a waje ba? So ka ke babanku ya sani ya daina baka kudin makaranta?"
Naira biyar din da Shazali ya bashi ce ta fado ta kyalla ido ta gani ta dauka ta karkade. A kirjinta ta soke kudin sannan ta cigaba da yi masa fada kunnensa a tsakanin yatsunta tana ja.
"Ki yi hakuri Asabe."
Ya iya cewa da kyar yana jan jiki. Bayansa ta bi tana cewa gara ma ya saki jikinsa domin bata yi masa dukan da zai saka shi irin wannan tafiya ba. Ko kadan tunaninta bai bata ta binciki inda ya sami kudin ba. Ita bata ma son tayi zancensu bare ta ji cewa ba wadanda za ta iya ci bane. Inda ya je ma ba laifi bane indai zai dawo kafin duhun dare.
Innayo ya wuce bai gaisheta ba kamar kullum. An koyar dasu kiyayyar kishiya da 'ya'yanta tun kafin su gama wayo. Yana shiga bandaki ya fashe da wani sabon kukan. Bai taba jin ciwo makamancin abin da yake ji yanzu ba. Ga cikinsa ya kulle amma yana tsoron yi ya tadowa kansa sabon ciwo. Kukansa ya sha ya dauki wandonsa da ya baci da jini ya jefa cikin shaddar (masan kasa) ya fito. Rigarsa ta wuce gwiwarsa ma saboda haka babu mai gani.
"Munzali ina wandonka?"
Muryar Alh Rabi'u ta karade tsakar gidan.
Kafin ya bada amsa Asabe tayi saurin amshewa ta ce wai don ya ga babu wuta ne ba mai ganinsa shi yasa ya fito.
"Zai gyara Alhaji. Da kaina zan yi masa fada." Ta ja hannunsa "Bashi hakuri ka wuce muje ka ci abinci."
Da dassashiyar murya ya ce da Alh Rabi'u ba zai kara ba. Shi kuma jin muryarsa a haka ya tambaye shi me ya same shi. Nan ma Asabe bata bari ya yi magana ba saboda kada wani ma ya ji cewa tayi masa fada ya yi kuka.
"Mura ce. Murar zafi ce Alhaji. Ka san ta da bakin naci."
Gyaran murya ya yi abinsa ya wuce ba tare da ya sake kulasu ba. Da yaje daki ya tarar da abincinsa wanda Innayo ta kai ta ajiye kafin ya shiga dakin. Da kafa ya ture farantin da ta jera langar tuwo da miya a kai ya zauna yana sassauta daurin tazugen wandonsa. Daga gidan wata sananniyar mai danwake yake ya ciko ciki. A kasuwarsu magidanta kalilan ne basa sayen danwakenta. Ga tsire da ya saya ya hada dashi da lemon kwalba. Wata uwar gyatsa ma ya yi ya kwanta zai yi bacci.
"Mungode fa da ka saukemu Malam har kwana biyu. Ba don kai ba da sai dai nayi kwanan tasha." Cewar Inuwa yana mikawa Mal Alto hannu.
"Babu komai. Ni ke da godiya da ku ka kawo danku wannan makaranta mai tarin albarka."
Tsamurarren malamin ya bashi amsa idanunsa akan buhu da kullin ledojin dake gaban Inuwa.
Kamar Inuwan ya gane ma'anar kallon kuwa ya fada masa cewa kayan abinci ne ya kawo masa. Ya turo mafi girman buhun wanda shi ma ledoji ne a kukkule a ciki da murmushinsa.
"Wannan kuma kayan abincin Abbati ne. Akwai kanzo da hatsi harda shinkafa. Da yake yana da 'yar matsalar shiririta shiyasa uwar ta ce don Allah kada a barshi ya je bara. Ko rana da dare ne kadai idan anyi girki daga cikin gidan a zuba masa. Wallahi ba ma shi da ci sosai." Wani irin kallo yaga Mal Alto yana binsa dashi ya yi maza ya kara da cewa "kuna iya saka shi wanki, shara ko aike. Fatanmu ya samu ilimi mai amfani kamar 'yan uwansa ba sai ya hada da barar ba."
"Ba damuwa. Bara ce dai kadai baka so ko? Iyalina zasu dinga girki dashi. Kar ka damu."
Haka nan zuciyar Inuwa bata aminta da kalaman Mal Alto ba amma bashi da zabin da ya wuce barin dansa a nan. Idan ya mayar dashi gida Mal Sa'adu ba zai masa ta dadi ba. Har ransa shi ma ba ya ra'ayin yaransa suyi barar amma bashi da zabin cewa a'a. Zuciyarsa ta kwankwashe shi akan ya tafi da dansa sau ba adadi amma ya ki ji. Nan gaba kadan yana sa ran a kira Abbatinsa da Gwani. Haka nan ya fice ya barshi kamar yadda ya baro Sani a Zaria ya kama hanyar tasha zai koma gida.
Abbati kuwa ya yi kuka sosai. Bayan kimanin rabin awa da fitar Inuwa lokacin Mal Alto ya tabbatar duk inda yake yana hanyar Kirikasamma. Dorinarsa wani babban dalibinsa ya dauka ya zubawa Abbati a baya shi kuma bai ce komai ba. Dalibin da yake yin abin daya san malamin nasu ya yi na'am dashi ya ce,
"Tashi shagwababbe. Ni ban san akwai sangartattu a kauye ba sai yau. Wai kada a bari kayi bara. To uban me ya kawoka birni idan ba shinkafa da miya ba? Babban naka ya raina Malam ma."
A firgice Abbati ya tashi yana kuka hannuwansa na susar inda bulalar ta same shi.
"Ku je a bashi roba ya bi 'yan uwansa bara idan an fito daga karatu shabiyun rana. Sannan ka fada masa duka tsare-tsaren tafiya barar don kada a sami matsala." Cewar Mal Alto kai a kasa yana jan wani katon carbi kamar ba shi yake maganar ba.
Ba kowa ya san halin Mal Alto ba saboda iya kankantar da murya da nuna shi na kwarai ne. Ya goge sosai wurin ci da addini. Mutane suyi ta kawo masa yaransu yana bautar dasu. Idan an tashi komawa gida kuwa sai an yi dogon gargadi akan iya rike baki kada a fadi me yake faruwa a makarantar. Da yake yana taba tsibbu a boye har rubutun kafe yaran yake yi. Duk wanda yaje ganin gida sai ya dawo. Wadanda wahala ta zamewa jiki har suka rika suka fara yawo irinsu Shazali kuma suyi ta dauko masa magana. Akwai 'yan daba, 'yan kwaya, masu haura katanga da duk wani nau'in gagararren mutum a gidan. Karatu ne suke yi babu ikilasi ko kankani. Idan mutum yayi magana cikin 'yan unguwa ace yana kalubalantar karatun addini.
Ana fitowa shabiyun rana aka bashi wata kodaddiyar roba. Kayansa kaf dinsu har na jikinsa an dauka an kai cikin gidan Malam. Akwai wadanda girmansu ya zo daya a cikin 'ya'yansa. Jakar kayansa ta koma babu komai sai wasu tsummukaran kaya da aka fito dasu daga cikin gidan.
"Kafin karfe uku ka tabbatar ka dawo."
Abbati ji yake kamar mafarki yake yi. Babu abin da ya fahimta a karatun har suka fito saboda fargaba. Ya dauki kwano ya bi bayan wasu yara da ya zauna kusa dasu da ana karatu. Wani lungu suka shiga ya daga kafa da saurinsa ya cimmusu.
Babban cikinsu ya saka dariyar muguntap suka cigaba da tafiya har karshen lungun ashe bayan gidaje ne. Tarfa shi suka yi babban ya tattale masa keya.
"Ba kaine aka ce ba za ka yi bara ba? Ya muka ganka da kwano?"
Sauran suka sa dariya.
Hannuwansa duka biyun a keyarsa yana kare dukan da suke yi masa na cin zali ya ce "Don Allah ku bari na biku."
"Ai baka isa ba. Ka nemi hanyar da za ka dinga bi saboda gidajen nan wurin namu ne. Idan muka kara yawa abincin ba isarmu zai yi ba."
Wasu na duka da kafa wasu da hannu a haka suka kore shi daga lungun jikinsa duk ya yi futu-futu da kasa. Gefen hanya ya samu da ya gaji da yawon ya zauna gashi ko wakar barar bai iya ba. A nan bacci ya yi awon gaba dashi kudaje suna ta kai kawo a jikinsa.
Munzali ne ya fito daga gidansu da jan kafa ya hango Abbati yana bacci a karkashin bishiyar kofar gidansu. Yau kwana biyu kenan da gamonsa dasu Shazali. Rashin kula na Asabe yasa ta yarda da ya ce mata a wurin bal ya turgude kafa shi yasa baya tafiya da kyau.
Da kafa ya shuri Abbati ya tashi a tsorace yana rarraba idanu. Kansa ne ya juye ya manta a ina yake sai da ya ga robar bararsa.
Munzali ya kankance ido ya ce "kai dan makarantar Mal Alto ne?"
"Eh."
"Shi ne kayi kwanciyarka kana bacci gashi har anyi la'asar sun kusa fitowa. Tabdi. Wallahi duka ake yiwa marasa komawa da wuri."
Ba a makarantar yake ba amma layin bayansu take. Yawancin abokan buga kwallonsa daliban can ne. Duk wanda ya makara wurin komawa ba karamin duka yake sha ba. Kwal-kwal idanun Abbati suka yi da hawaye sai ya bashi tausayi da ya ce masa ba zai gane hanya ba.
"Muje na raka ka amma ba zan shiga layin ba." Ya ce don yana gudun sake haduwa dasu Shazali.
Har farkon layin ya kai Abbati ya juya zai tafi ya hada ido da Shazali. Fitsari ne ya subuce masa tsabar fargaba ya fara ja da baya. Jan hannun Munzali da Shazali ya yi daidai da waigowar Abbati. Yana kallo har suka bacewa ganinsa. Bai san meye tsakaninsu ba kuma ba ihu Munzali yake yi ba shi yasa bai yi tunanin komai ba.
Kangon suka koma babu mutane ko hayaniya a wurin. Hannu Shazali yasa ya toshe masa baki sannan ya kuma maimaita masa rashin imanin nan.
Sai da ya gama ya lura da hawayen dake fuskar Munzali shabe-shabe da majina.
"Allah Ya isa. Mugu. Azzalumi. Dan wuta."
Cikin bacin rai Shazali ya riko habarsa ya matse "Ni kake zagi Munzali? Don ma ka samu ina sonka. Idan ka ce zaka yi min rashi kunya tattaka ka zanyi in taka banza a wurin nan."
Da kafa ya shura masa daurin bakar ledar da ya riko tun kafin su zo wurin. Munzali ya bude yaga langa ce cike da shinkafa da miya harda nama yanka biyu. Ga salad an yanka da tumatir da albasa. Duk wannan bakar wahalar da ya sha sai ya nemeta ya rasa a lokacin. Ga zobo kullin naira bibbiyu guda biyu da sauran kankararsu. Hannu baka hannu kwarya yake danna shinkafar nan. Ba shi ya daga kai ba sai da ya sude kwanon tas. Rabonsa da shinkafa da miya tun sallah karama da A'i ta aiko gidansu. Wata hudu kenan. Wanda ake ci a dakin Innayo kuma Asabe ta ce ta tsine idan suka karba. Wai guba za ta saka musu saboda bata da maza. Tafi ganewa girka musu wulakantaccen abincin da Alh Rabi'u ke kawowa.
Shazali na kallonsa ya saki murmushi "nima kudi na samu a wurin Alhajin da yake min irin abin da nayi maka. Idan kana zuwa wurina kullum har kaza zan saya maka da tsire."
"Akwai ciwo don Allah kada ka sake."
"Kai dalla can baka san idan ana yi kullum zaka daina jin zafin ba? Da kan ka za ka nemeni wataran." Ya yi masa wata irin dariya.
Da wayo ya dinga hillatarsa har ya amince gobe zai zo kangon ya same shi. Da zai fita ya sake bashi naira biyar tare da gargadi.
"Muddin ka sanar da wani da kai da duka 'yan gidanku zan kai gidan yankan kai!"
Sai bayan kwana goma suka sake haduwa da Abbati da jikinsa duk tabo da sabbin ciwuka. Daga bara Abbatin yake bai samo komai ba zai koma makaranta. Ranar ta kama alhamis ba sa karatu.
"Don Allah muje gidanku ko kanzo ne ka kankaro min." Ya roki Munzali.
"Nima babata bata da abinci. Ka dawo anjima idan kun fito barar dare zan baka abinci Yasin harda nama."
Cikin Abbati har wata kara yake saboda yunwa ya amince a guje. Kayan abincin da yazo dasu Mal Alto ke ci. Gashi bashi da aboki ko daya cikin 'yan uwansa almajirai kamar ma sun tsane shi.
Hasashen Shazali ya zamo gaskiya. Kwana biyu Munzali yana riga shi zuwa kangon. Ya saba yanzu ko babu kudi so yake ayi. 'Yan biyar biyar da yake batarwa a sayen kayan kwadayi har yau Asabe bata tambayi inda yake samo 'yan canji ba. Ranar da ta tsinci naira goma a aljihunsa ma boyewa tayi da sauri tana murna.
"Masu 'ya'ya mata ne da fargaba idan an gansu da kudi. Da namiji kuwa indai ba barawo bane babu inda zai samu sai wurin abokan arziki." Ta murmusa ita kadai "Munzali ba dai jama'a ba. Duk inda ya gifta sai an kira shi."
Kamar yadda ya alkawartawa sabon abokinsa da ko sunan juna basu sani ba da kansa yau ma yaje kangon. Shazali da wannan abokin nasa yazo. Bayan sun gama aka mika masa langar abinci da naira goma. Dadi kamar ya kashe shi. Ya duka yana juye abincin a leda Shazali ya tambaye shi me yasa ba zai ci a nan kamar kullum ba.
"Aboki nayi wani sabon zuwa a makarantarku. Abin tausayi idan ya yi bara ba ya samun abinci."
Dan tsorata Shazali ya yi "ina fata baka fada masa me muke yi ba ko?"
"A'a." Yana kallon kofa ya ce "In tafi? Na ce ya jirani."
Sallamarsa suka yi ya tafi da murna. Bai shiga gida ba saboda ya san sai Asabe ta ci ko bata bawa 'yan uwansa ba. Bai jima ba kuwa ya hango Abbati yana layi kamar zai fadi saboda yunwa. Karancin shekarunsa basu hana shi tausaya masa ba. Zuciyarsa tana da saurin rauni wanda da ace ya sami kyakkyawar tarbiya da kulawa da anyi mutumin kirki abin alfahari. Shekarunsa goma amma ya san ya gane mabukaci kuma ya yi abin da zai sama masa mafita daga yunwar da yake ji.
Cikin soron gidan makotansu da ba kasafai ake bi ba ya ja shi suka shiga ya bude langar. Abbati yawu ya tsinke jikinsa yana rawa ya tsoma hannu a ciki. Tare suka ci amma Munzali bai fi loma uku ya yi ba. Abbati ya barwa abincin.
"Nagode. Nagode don Allah ka ce da mamanka nagode kaji."
"Ba Asabe ce ta bani ba. Wani abu nake yiwa wasu sai su bani abinci idan an gama."
Mamakin ashe akwai aikin dake kawo abinci irin wannan Abbati ya yi "zan yi. Don Allah kaje dani gobe."
Cike da kuruciya Munzali ya ce "kai wallahi sun ce idan na fada zasu kaini gidan 'yan yankan kai."
Jiki a
sabule Abbati ya koma ya zauna murnarsa ta koma ciki. Wani tunani Munzali ya yi ya ce masa "kasan me? Ni suna bani kudi ko abinci. Idan naje aka yi dani kai ma sai nazo nayi maka sai na sammaka kudin ko abinci. Ka yarda?"
Wata dariya Abbati ya saka ya washe bakin da ya bayyana gibin turamensa biyu.
"Na yarda."
Munzali ya mike tsaye yana cewa "amma fa idan ka fada zasu yankamu har babarka da babanka."
"Ba zan fada ba." Abbati ya nanata yadda zai amince masa.
"To tashi ka cire wandonka."
A cikin soron da babu wadatar haske Abbati ya zaro idanu "cire kuma? Iskanci ne fa. Wai ma ya sunanka?"
"Munzali."
"Ni kuma Abbati. In fada maka Baaba ta ce duk wanda yake cewa a cire wando wuta zai je ba zai ga Annabi Muhammadu (SAW) ba."
Dariya ce ta kama Munzali ya ce "kai nima haka na zata. Ashe wai idan aka yi da mace da namiji ne mutum zai shiga wuta. Irin wannan kuwa dadi ake ji kuma a baka abinci."
"Baaba bata fada min namiji yana cewa namiji ya cire wandi ba. Kila da gaskiyarka shi ba na 'yan wuta bane."
A wannan daren Abbati mai shekaru goma sha biyu amma babu wayo da idon uwa ya fara koyon wannan mummunar dabi'a saboda yunwa da rashin gata a wurin Munzali.
Munzali da ya koya masa bai san muni da zunubin dake cikin wannan alfasha ba saboda rashin saka ido na uwa da uba.
Daga wannan ranar abotarsu tayi karfi. Munzali zai jure ko mutum nawa Shazali yazo dasu ayi a bashi abin da za'a bashi saboda Abbati ya ci abinci. Ana fitowa barar dare Abbati zai zo suyi shima ya biya shi. Abincin tare suke ci sannan ya raba musu kudin daidai. Zuciyarsa bata taba raya masa ya cuci Abbati kada ya bashi kudin da ya samo ba.
Abin taysayi. Abin kuka. An kulla abotar kuruciya da aka so ginawa bisa alkhairi amma mummunar alfasha ta zamo jigonsa.
Kaico! Allah kadai Ya san Abbati da Munzali nawa ne a tare damu cikin wannan masifa bamu sani ba. Wasu suna mu'amala da 'ya'yanmu wasu da kannenmu.
*****
"Ke kuwa Khadija kamar me haihuwar fari me ya fito dake yawon arba'in? Ko har kin gama warkewa?"
Yakumbo ke wannan fadan tana karbar jaririya Sauda daga hannun Khadijan. Su Lilu kowa da murnarsa ya je jikinta suna tambayar ta ire iren cimar da take ajiyewa a dakin domin jikoki.
Sai da ta sallamesu suka fita daga dakin sannan ta zauna suka sake gaisawa da Khadija.
"Jiki ya yi kyau. Allah Ya kara miki lafiya. Naji dadi sosai da yadda ki ka karbi kaddararki. In sha Allahu wadannan yara zasu zame miki sanyin idaniya. Allah Ya muku albarka."
"Amin"
Khadija ta amsa tana kokawa da hawayen dake son zubowa. Ita kadai ta san irin bacin rai da bakincikin da take kunsa a wurin Tahir a kwanakin nan. Nasima bata kara zuwa gidan ba tunda ta koma. Sai dai ya fito mata da salon wulakanci irin na namijin da ya fahimci karin aure a matsayin lokacin cin zarafin ta gida. Bata yi sati da komawa ba ta canja shawara ta ce ya saketa.
"Kin san abin da zai faru idan muka rabu. Kowa zai san me nake yi kuma kan 'ya'yanki zai koma."
"Na sani Tahir amma duk da haka ina so ka sakeni kafin zuciyata ta buga. Kayi min adalci albarkacin zaman da muka yi a baya da yaran nan."
"Zan miki. Ke ki je ma na sake ki saki daya. Amma ki sani nayi miki rantsuwa ko Yakumbo bata isa ta sakani baki yaran nan ba. Zan daukesu mu koma Lagos tare da Nasima."
Cak ta tsaya tana kallonsa idanunta cike da hawaye.
"Yaya dama haka kake ko duka son Nasiman ne ya mayar da kai haka?"
"Ki dauki duk wanda yayi miki bani da damuwa. Na ce ki zauna mu rufawa juna asiri sai dawo da hannun agogo baya ki ke yi. To ga sakin nan kin samu ki tafi da Sauda idan kin yayeta zan zo na karbi abata."
Da kyar ta lallaba ta zauna a bakin gado bayan ya fita. Ta kasa gaskata abubuwan da suke faruwa yanzu musamman sakin da ya furta mata. Halayensa ba bakinta bane a da amma ko a wancan lokacin da yake tashen akuyancinsa yana shakkar ta sani. Yanzu kuwa akan kankanuwar yarinya ya yanke igiyar auren shekara tara.
Abin da basu sani ba daga shi har ita shi ne Nasima da Ladidi mahaifiyarta suna kauye ana yi musu aiki akan Tahir. Duk yadda za'ayi ya aureta ko babu izinin iyayensa suke so. Sannan ya fifita ta akan kowa. Shi ya bayar da wannan kofa daga ranar da ya fara nemanta. Ladidi ta san komai game da halayyar 'yarta amma tunda ta zame mata jari shi kenan.
Fuskarta ta wanke ta fito falo ta sami kanwarta ta gama girki ta zubawa yaran. Dakinta inda Gwaggo kanwar mahaifiyarta mai kulawa da ita tayi masauki ta shiga. Kuka ta saka mata ta sanar da ita sakin da ya yi mata. Hankali a tashe ta zari mayafi ta tafi gidansu ta sanar da Mama. Tare suka dawo ta kora musu jawabin abin da ya faru.
"Khadija na san Tahir bai kyauta ba amma shi ne rufin asirinki. Idan kin fito waye zai auri mace mara mahaifa?"
Kai ta girgiza tana karyata cewa mahaifiyarta ce take fadin wannan magana bayan ta fada mata matsalarta.
"Dena yi min wannan kallon na fiki sanin halin maza. Kwansu da kwarkwata ban dauke miki uban da ya kawoki duniya ba duk jirginsu daya."
Kiris ya rage ta saki Sauda saboda firgici "Baba ma yana neman mata?"
Mama tayi murmushin takaici "ban fada miki don ki daina ganin girmansa ba amma babu irin cin kashin da ban gani ba lokacin da yake manajan banki. Ni da yake kawosu har cikin gida ya ce abokan aikinsa ne in yi musu girki."
"Me?"
Zantukan sun kadata sun yi matukar bata mamaki.
"Rayuwarku da tsoron kada ku tagayyara yasa na zauna. Kema kuma ina shawartarki da ki rungumi kaddararki kiyi zaman 'ya'ya."
"Yanzu Mama saboda 'ya'ya sai mata su dinga zama da fasikai?"
"Idan kin fita kin san gidan wa zaki fada? In kuma baki yi aure ba ina zaki kai wadannan yaran ke ba sana'a ba kuma babu aiki. Babanku ya yi ritaya kannenki ma da kyar ake biya musu kudin makaranta. Ga zumunci da zai lalace kuma karshenta a bar miki 'ya'ya a hannun kishiya ta gallaza musu. Shawara daya zan baki. Idan ya dawo ki roke shi ya mayar dake kafin kowa ma yaji. Dama can an san halinsa ai aka aura miki. Lokacin ba yadda banyi ba aka ce zan raba zumunci."
Khadija na kuka Mama ta cigaba da tausarta akan tayi hakuri. Al'adarmu ta fifita farincikin namiji akan mace. Ko mun sani ko bamu sani ba mun nunawa maza zamu nemo dalilin zama dasu duk lalacewarsu saboda gudun zawarci. Babu uwar dake son 'yarta ta fito daga gidan aure amma addini ma ya halarta fitar domin a zauna lafiya.
Tahir bai yi mamakin ganinta ba da ya dawo da yamma. Dauke kai ya yi ya shige dakinsa. Zuciyarta na kuna ta tashi ta bishi dakin.
"Na amince zan zauna."
"Ya dai fiye miki. Ki turo min kofar idan kin fita." Ya ce daga kwance.
Bata san daga gidan Yakumbo yake ba ya kai mata zancen auren Nasima ta fattako shi.
"Tunanin me kike yi ne Khadija? Inata magana kin yi shiru."
Dago kai tayi ta kalli Yakumbo tayi murmushin dole.
"Babu komai."
Ba yarda tayi ba tunda ta san Tahir yana neman aure. A wannan yanayin ba Khadija ba duk wanda yaji zai kira shi butulu ne. Ace daga cirewa matarsa mahaifa yana kiran sake aure. Nasiha ta dinga yi mata akan karbar kaddararta ta cire mahaifar amma bata sako zancen auren nasa ba. A gidan suka yi azahar sannan suka tafi gidansu Khadija a bayan layin da kafa.
Da yamma Tahir ya zo daukarsu ya fara biyawa ya gaishe da Yakumbo. Bai samu sakin fuska ba tunda ya ce mata zai yi aure.
" 'Yar waye yarinyar da kake nema ne wai?"
Sosa keya ya yi "ba fa bakuwa bace Yakumbo. Mai aikinmu ce Nasima..."
Kaf...Yakumbo ta kwade masa baki cikin fushi "mai aikinku fa kace. Kenan ma Khadija ta sani. Wannan wane irin cin fuska ne haka?" Alamun zai mata tijara ta gani sai ta zabi lallaba shi akan dai ta yarda da wannan danyen aiki "Idan auren kake so ka bari Saudatu ta shekara sai ka nemi wata"
"Nasima kadai nake so!"
"To ba za ka aureta ba duk abinka."
Tahir dagewa ya yi babu jin nauyi ya nunawa mahaifiyarsa fa bata isa ba.
"Akan mace nake fada kana fada Tahir?"
"Meye aibunta? Ba gara na auri wadda Khadijan ta sani ba."
Tsananin bacin rai yasa ta samun wuri ta zauna tana rike kai. Wani tunani ne ya darsu a zuciyarta ta kalle shi a razane.
"Wannan bakin naci da kake kafa min akan yarinyar nan anya wani abu bai shiga tsakaninku ba?"
Kai ya sunkuyar yana wasa da mukulli bai musanta zarginta ba. Hawaye tuni ya balle mata ta nuna shi hannu na rawa "Khadija ta san ita kake neman aure ko?"
Da ka ya amsa mata.
"Ko dai ta kamaku ne?"
Nan ma da ka ya amsa. Yakumbo taji kamar ya soka mata kaya a kahon zuciya. Tashi tayi tana kaiwa duk inda ta samu a jikinsa duka.
"Bana so in yi maka baki Tahir, tun kuruciyarka kake gasa min zuciya. Allah Ya sani ban zubar da mutuncina a waje ba amma akanka meye banyi ba. Saboda ka shiryu na tursasa kanina ya baka 'ya. Mahaifiyarta har yaji tayi amma na dage ko ayi ko in saka shi ya saketa. Tahir duk kai na yiwa wannan" kuka ne yaci karfin Yakumbo ta kifa kai a cinyarta.
Jikin Tahir ya dan yi sanyi amma a ganinsa akan me zata hana shi auren da addini bai shata masa layi a kai ba.
"Idan nayi auren nan ba zan sake bin wasu ba."
"Iya abin da za ka iya cewa kenan? Akwai hakkina, da na matarka da na zuri'arka mai zuwa a gaba ma da na gabanka ba a wuyanka. Tahir. Tahir. Tahir kaji tsoron Allah idan kayi auren nan."
Da murnarsa ya tashi zai fita ta dakatar dashi "ban amince don kafi karfina ba. Nayi ne kawai saboda kada ka cigaba da cusgunawa Khadija. Ina jin kunyar iyayenta. Ina nadamar kafewa su baka ita. Kada ka bari Allah Ya sakawa fushina a kanka ko da ban kai kararka gareShi ba." Zuciyarta kamar ta ballo kirjinta take ji.
Kalaman mahaifiyarsa sun dan tsaya masa a rai amma biyan bukatarsa ya zarce kwabar da zuciya take yi masa. Ko babu komai akwai zalunci mai girma tursasawa Khadija zaman kishi da Nasima bayan ta gansu ra'ayil aini. Bai san dalilin Nasima na son ya cigaba da zama da Khadija ba amma ba ya son bata mata rai.
Asiri ke cin Tahir amma idan bera da sata to daddawa ma da wari. Da bai bawa Nasima kofar ganin tana da matsayin da zai ci amanar matarsa akanta ba da ba za ta taba tunanin mallakarsa ta wannan siga ba.
Yakumbo kmar kowacce uwa ita ma ta haifi Tahir tana mai tattalinsa. Tayi fadi tashi dashi har ya zama mutum. Idan yana ciwo tayi kuka ko ta shiga damuwa. Murmushinsa daya tamkar mukullin aljanna yake a gareta. Soyayyarta gareshi bata bari ta sangarta shi ba. Yau fari gobe tsumma haka ta rayu da duka 'ya'yanta. Bata sani ba kuma ba da son ranta ba an wayi gari daya daga cikinsu ya zama mazinaci kuma mara jin magana.
Duk da ko 'yar da ya tashi da wannan dabi'a har duniya ta tsane shi ya taba rayuwa a tsumma ana sambarka. Anyi wani zamani da ake mika shi daga wannan hannu zuwa wancan ana cewa 'Allah Ya raya.' Uwa tana ta murna bata san kaddarar da aka rubutowa rayuwarsa. Idan da adalci ba kowane lalataccen da bane za'a zargi mahaifiyarsa. Indai Uwa ce, to burinta yafi kowa shiryuwa ko da bata bada gudunmawar da ta dace wurin yiwuwar hakan ba. Sai mun hadu bayan sallah in sha Allah. Allah Yasa mu amfana da wadannan kwanaki masu daraja da albarka.
UKU DUWATSUN MURHU.
Kwanaki sun zo sun wuce kamar kiftawar ido ya rage saura kwana shida Nasima ta tare. Abin kamar a mafarki haka ya zo wa Khadija. Rayuwarta, iyalinta, mafarkinta da komai nata lokaci guda ya sauya. Mata da yawa a irin wannan lokacin da mazajensu zasu kara aure suna shiga wani hali. Kalmar kishiyar kadai basa so amma idan akwai ilimi, tawakkali da hangen nesa sai mace ta karbi kaddararta har ma ta mori alkhairin da yake ciki. Wadda za'a aurowa mai-aikinta kamar Nasima nata bakincikin yana karuwa ne da tunanin cin fuska da miji ya yi mata. Shi ma da anyi auren an kwana biyu zuciya tana iya samun salama radadin ya gushe tare da shudewar lokaci. To amma idan amaryar ta kasance matar da ta gida ta kama kuru-kuru ce tare da maigidan fa?! Ta ina za ta fara kuma wane bangon za ta dafa domin jin sassauci? Tambayar da ta addabi zuciyar Khadija kenan a yau da Tahir ya fada mata za'a zo jeren Nasima.
"Dakina yafi girma saboda haka shi Nasima ta zaba. Ki kwashe kayanki daga naki dakin kafin azahar don za'a jera min nawa kayan a ciki."
Magana ce yake yi mata da sigar nuna isa don kada ma tayi tunanin kawo nata korafin. Wato dakinsa Nasima ta zaba. Kodayake babu mamaki tunda ta gama sanin dakunan gidan. Bayanin karshe da ya yi mata na rainin hankali murmushi tayi masa ta amsa shi da 'to'.
"Kinga ke za ki tashi da dakuna biyu harda falo." Da hannu ya nuna mata bangaren dakunan yaransu wanda hanyar zuwansa take a gefen hagu na karamin falon gidan.
Tsarin ginin na mai karamin iyali ne dama. Idan ka shigo babban falon ne a farko. A cikinsa akwai kofar karamin falon da Khadija kan shiga da bankinta idan Tahir yana da baki a lokacin. Shi sai ya zauna a babban. Dan korido ne a cikin falon da kofa uku. Dakuna biyu sun saka bandaki a tsakiya. Daki daya gadajen yaran ne irin siraran nan. Daya mai hawa biyu, Suhaib a sama Lilu a kasa. Mai hawa dayan kuma na Farha. Daya dakin kuwa karami ne sosai. Nan Tahir ya tsara idan sun kara datawa Farha za ta koma da kansa a da. Idan an koma falon akwai wani korido din mai zuwa dakin Tahir da na Khadija. Ga bandakin baki a falon da kofar kitchen duka a cikinsa. Manyan dakuna ne daidai iyayen gida da bandakunansu. Yanzu ya ce ta kwashe kaya. Bata ma san ta ina za ta fara ba balle yadda za ta yi dasu.
A wurin ya barta baki bude. Watanta uku da haihuwa taji sauki sosai. Ra'ayoyin dangi sun kasu biyu game da auren nan. Dadaddun masu bakincikin hadin Tahir da Khadija kamar su zuba ruwa a kasa su sha. Kowa taso ya auri 'yarta saboda matashi ne da ya soma kama naira daga gama jami'a. Mafi yawansu kuwa sun aibata Yakumbo sun ga laifinta wurin bashi goyon baya. Abin da tayi domin tsare auren Khadija ba sani suka yi ba. Zahirin suke gani wato ta fifita dan da aka cuci Khadija aka aura mata.
Unguwar Barnawa ma cikin kankanin lokaci ta dauki zancen wani magidanci da zai auri mai'aikin gidansa. Wanda suka san su kuwa sunayensu suke kamawa. Sun sha zagi da muggan fata a bakin mutane a dalilin auren cin amana da ake tunanin sun yi. Makota sun shaida Khadija ta kyautatawa gidansu Nasima sosai.
Lokacin da suka tare ta leka duka gidajen layin ta gaisa da kowa. A sannan ta fuskanci bakin talaucin da ya yiwa gidansu Nasima kawanya. Saboda tsabar babu ko tabarmar da za ta zauna basu da ita sai dankwalin kan Nasiman Ladidi babarta ta ciro ta shimfida mata. A take tausayinsu ya shigeta. Kullum da rana tana yin girki ya zarce bukatarsu. Idan ta gama sai ta tura Suhaib ya kira kanwar Nasima ta zuba musu. Tahir ya kan ce kada tasa rai da kwashe ladan saboda yana da nasa kason na mai siyowa. Sai su yi dariya su mayar da zancen wasa. Anyi haka na kamar wata biyu sannan Nasima da Ladidi suka zo godiya da neman aiki.
"Idan ya dawo zan sanar dashi sai na fada muku yadda muka yi." Ita ce amsar da ta basu a mutumce. Ba bukatar mai-aikin take yi ba saboda ita ba aiki take ba. Lilu ma shekararsa hudu lokacin. Tsakaninsa da yayyensa dai duka kwanika tayi. Daga kansa ne ta sami dogon hutu.
Godiya suka yi mata Ladidi harda hawayenta tana godiya. Cewa ma tayi ko babu albashi indai zasu dauke mata baki daya cikin wadanda take ciyarwa ta gode.
"Ni kuwa Nasima ba kya tsoron matan layin nan su tona miki asiri akan irin abin da ya faru a gidan Alhaji?" Cewar Ladidi bayan sun fito.
Juya idanu tayi tafiyarta tana canjawa gabadaya zuwa irin ta masu turo kirji gaba.
"Kafin su farga na gama dashi."
Da sauran rashin yarda babarta ta ce "uhm uhm fa. Kin tuna uban dukan da Hajiya tayi miki da rashin abincin da muke fuskanta saboda babu mai baki kudi yanzu?"
Yatsina fuska tayi irin na tantiran da basu ganin kimar iyayensu "wancan ma akasi aka samu kuma dai shi Alhaji matsoraci ne. Amma baban Suhaib dinnan...hmmm"
Ladidi ta kece da dariyar jindadi "labarta min. Ko dai har kun fara haduwa ne? Naga kina abu kai tsaye kamar anyi an gama."
Murmushi Nasima tayi. Bata son saurin sakawa Ladidi rai amma tabbas ita ta san irin kallon da Tahir yake yi mata duk ranar da suka ci karo a layin.
Bayan kwana hudu ta fara aiki. Ladidi jiki na rawa take karanta mata littafin rashin albarka.
"Ki bita da ladabi da biyayya. 'Ya'yanta ki jasu a jiki kamar naki. A bayan idonta kuma kada ki dagawa mijinta kafa. Na san indai surar mace na gigita namiji wannan mutumi ba zai gagara ba. Ki janyo hankalinsa sannan ki gara shi ta yadda zai rasa sukuni. Wannan karon gidan nake so ki shiga na gaji da barnar kudi wurin zubar miki da ciki."
Dalilinsu daya na biyewa wannan kazamar rayuwa. Uba ya mutu ya barsu da bashi babu gadon komai sai gidan da shima ya gada a wurin nasa iyayen. Danginsa sun yi kokarin taimakawa Ladidi wurin raba 'ya'yan su rike taki amincewa. Ita so tayi su dinga bata kudi bayan suma din babu mai katabus. Girman zumunci ne ma yasa su wannan yunkurin. Ta zauna babu abin da ke shigo mata sai kawai ta nunawa 'ya'yanta cewa dangin babansu basa kaunarsu ne. Ita kuma nata dangin suna kauye ba zuwa za tayi ta zauna ba. 'Ya'yan ne jarinta tunda suna da kyaun fuska da daukar hankali duk talaucinsu. Babbar bata biyewa Ladidi ba. Tafi duka kannenta kyau da kyaun hali. Aurenta tayi a Kaura Namoda tana dan aikowa Ladidi abin da ya samu. Nasima ce ta dasa dan ba a fitina sai mai bi mata ita ma ta fara yawo yanzu.
Fuska biyu ta kwararrun munafukai Nasima take nunawa a gidan. Khadija bata ganin wata kofar zargi sai gabanin dawowarta gidan tayata zama da ta fara yi mata rashin kunya. Tahir kuwa sai da yaji duk duniya babu macen da zuciyarsa ke kauna sama da ita. Da kananun shekaru ta kware a barikanci. Sai ya zo wucewa sai ta dinga bude jiki da dabara.
"Wayyo kadangare"
Ta dinga ihu watarana da Khadija ta fita cikin sauri da Farha ta kusan hadiyar kwankwalatin kwalbar fanta. Asibiti ta tafi kaita ta bar Nasima dasu Lilu a gida. Da yake makira ce tana jin dirin motar Tahir ta turasu daki. Yana bude kofar ta saki zanin tana tsalle-tsalle.
"Kadangare ne a zanina" ta ce da kukan kissa tana makale masa a jiki.
Tahir an sami abin da ake so ya matso yana cewa ta tsaya ya duba mata. Ya tabbatar Khadija bata gida tunda ta iya yi masa haka. Bai yi kasa a gwiwa ba ya biye mata tunda dama jira yake. Ranar ya fara kaita dakin Khadija yaci mutumcin aurensa a cikin gidansa. Sai da suka fito suna murmushi yake tambayarta inda Khadija take.
Kwabe fuska tayi ta soma kikkifta idanu. Muryarta ta karyar kamar mai shirin kuka.
"Tun yanzu ka fara nuna min iya matsayina."
Jikinsa ya janyota "Me nayi?"
"Yanzu yanzu fa kake tambayata matarka. Wato na gama nawa amfanin."
Ganin tana hawaye gabadaya sai hankalinsa ya tashi. Rarrashinta ya dinga yi da kalamai masu dadi sannan ya dauki kudi ya damka mata. A fakaice tayi murmushin mugunta sannan ta maida masa kudin aljihunsa.
"Ni ba kudinka nake so ba."
Wani irin dadi ya mamaye zuciyarsa jin ba shi kadai yake hauka ba. Aljihunsa tas ya zazzage ya bata duka kudaden dake ciki. Suna wannan yanayin Suhaib ya fado falon daga dakinsu yana kiranta.
"Inata nemanki Anti. Lilu ne na kasa cire masa belt ya yi kashi a wando."
Da azamarta ta mike tana murmushi "Liluna kenan. Yau dai yana min shagwaba son rai." Sai da ta juyawa Tahir baya ta cigaba da magana "Ta wata kakarmu ta ce duk yaron da ya wuce shekara guda yana kashi a wando uwarsa tayi asara."
Juyawa tayi suka hada ido da Tahir ta dora da cewa "ka san mutanenmu na kauye ba dai iya zagi ba da raina kokarin mutum ba. Shi Lilu ma da yake karami babu wani a gabansa."
Tafiya tayi ta barshi yana juya zancen a zuciyarsa. Yafi sau biyar zai iya tunawa da Lilu ke yi a wando. Amma duka lokutan dukan gaske Khadija ta yi masa. Yayyensa babu wanda ya yi haka. Sai zuciyarsa ke bashi ko ta fara gazawa a tarbiya ne.
Yana zaune Khadija ta shigo da Farha a bayanta. Da dankwalin kanta ta goyota saboda ta sha wahala. An ciro kwankwalatin da ya karce mata makwogaro sannan anyi mata allurai. Da sauri ya tashi yana tambayarta ina taje.
Wani irin kallo tayi masa na mamaki sai yaji kamar ta fahimci halin da yake ciki.
"Nasima bata fada maka abin da ya faru ba?" Ta ce tana shigewa daki ta kwantar da da ita akan gado. Ganinsa tayi a yamutse ba yadda ta barshi ba ta dawo falo tana labarta masa abin da ya faru. Tashi ya yi zai koma duba Farhan yana jin babu dadi da tsautsayin da ya sameta ya bashi kofar cin amanar mahaifiyarta. Zai daga labule Nasima ta fito tare dasu Suhaib. Khadija ta tashi ta kama kunnuwansu ta murde kowannensu ya saki kara.
"Ban hanaku tsalle akan gado ba? Kuna ganin tsautsayin da ya sami Farha baku tsoron ku fado."
Sai da gaban Tahir ya fadi ya kasa karasawa ciki. Yana jin Lilu ya fara rantsuwar basu bane ya juyo ya musu abin da bai taba ba. Marinsu ya yi duk su biyun saboda tsoron kada ta yarda dasu ta fara zargin wani abu.
"Ba zan yarda da rashin kunya ba. Maminku tana magana kuna karyata ta. Idan ba ku ba waye zai hau gadon ya yi mata tsalle? Na sake ji ko gani sai na zaneku. Ku wuce ku bani wuri."
Da kuka suka bar falon. Khadija tayi mamakin daukar zafinsa haka. Ta dade tana rokonsa ya dinga taimaka mata akan kwabar yaran idan sun yi laifi ya ki har ta hakura. Da ta biye masa da yanzu sun gama sangarcewa. Yau da laifin ba mai girma bane a idonta sai gashi ya yi musu marin da ko ita aka yiwa sai ta rike kumatu. Ba dai ta ce komai ba ta bar wurin. Da Nasima za ta tafi ta tambayeta me yasa bata fada masa inda taje ba.
"Naji kin ce Farha amma ban ji sauran maganar ba Anti. Wani abin ne ya faru?" Ta tambayeta tana rarraba idanu.
"Baki sani ba fa ki ka ce?"
"Anti ko dai nayi laifine? Kiyi hakuri."
Khadija bata ce komai ba. Sai yanzu ta tuna Nasima tana wurin abin ya faru amma bata juyo ba.
"Allah Ya kyauta" kawai ta iya cewa saboda rashin sanin matakin dauka ta bar zancen.
A haduwar Nasima da Tahir ta gaba ce tayi masa kukan da ya karyar masa da zuciya.
"Na san za ka yi mamakin ganin ni ba budurwa bace. Ba zan maka karya ba da kaina na sayar da mutumcina. Talauci da yunwa sunyi mana yawa. Babu mai son taimakonmu. Da mutane suka gane cewa zan iya komai domin ciyar da mahaifiyata da kanne shi ne maza suka fara nemana. Na san cewa kaima kana cikinsu amma ba yadda zanyi saboda albashina ba zai ishemu ba."
Daga ranar ya bude mata bakin aljihu sai yadda tayi. So yake ya nuna mata yafi sauran mazan. Kudi kam bata da matsalarsu. Tahir kuma ita take juya akalarsa. Khadija sun maida ta hoto suna badakalarsu a gidan bata sani ba. Kiyayyar da yake nunawa Nasima ta zame mata katangar hana hango komai a tsakaninsu. To gashi yanzu anyi aure!
"Mari kin ji labarin ana neman masu casa a gidan Sarkin Noma?"
Audugar da Mari take kadawa ta ajiye ta kalli kawarta Tasalla da murmushin da yafi kama da dariya.
"Ki bari don Annabi."
"Yasin da gaske nake. Wannan karon ina tsammanin mata sai sun cika tsakar gidan saboda alherin da ya yi bara."
Tsam Mari ta tashi ta shiga daki ta dauko mayafi. Tasalla tana ta tsokanarta wai ladan aikinta wannan karon harda amaryarta zasu ci.
"Ko Malam in fada miki sai dai kallo. Yaran nan zan rabewa in je in dubosu." Kwalla ce ta taho mata ta goge da habar mayafinta "Har mafarkin Sani nake Tasalla. Ya yi kankanta sosai da bara. Ga Abbati kin dai san halinsa. Duk inda ya shiga raina shi ake yi. Ba zan taba yafewa Mal Sa'adu ba."
Da sauri Tasalla ta dora hannu a bakinta "bari fada kar a ji. Wan mijinki ne fa."
"Wan miji ai ba uban miji bane. Don baki ji yadda nake nadamar haihuwar mazan ba. Da mata ne wa ya isa ya tura su almajiranci?"
"Kul Mari. Ba'a yiwa Allah tawaye akan haihuwa." Cewar Tasalla.
"Astangafirullah" Mari ta ce da sauri tare da yin tofi a gefe na neman barranta daga zunubin kalamanta.
Sun yi sa'ar samun gurbi cikin mata goman da ake nema suyi aikin casar shinkafa da masara a gidan Sarkin Noma. Mari kason mutum biyu take karba ta wuni tana aiki. Banda wannan ta cigaba da dinkinta duk da kuwa ba wani mai tsada bane ga bashi a wurin mutanen kauye. Haka take musu dinkin ta shafawa idanunta toka sai an biyata kudinta. Tuni tayi suna kuwa. Ana cewa bata da lamuni wurin kudi amma ta iya dinki. Duk abin da ta samu sayayya take yiwa Abbati da Sani. Yaran dake gabanta ba komai take basu ba saboda ganin suna gaban mahaifinsu.
Bayan sati uku ta nemi izinin Inuwa za ta je Zaria da Kano ganin 'ya'yanta. Shi kuma ya sanar da Mal Sa'adu. Nan da nan zance ya zagaye gidan aka yi ta aibata ta. Sauran matan babu wadda ta taba zuwa ganin nata. Idan lokacin komawarsu gida ya yi ana basu hutu su tafi su taimakawa iyayensu musamman da damina.
"Wai ke Mari kanki aka fara haihuwa ko naki kadai aka kai almajiranci? Wannan rashin ta ido har ina?" Mai bin Mal Sa'adu ya ce da ita yana muzurai.
Inna Mairo ce ta kawo mata dauki wannan karon.
"Bana son bakin hali. Kun dauke yaran yanzu meye aibunta don ta ce zata ganinsu? Na rantse da za'a jarabceku da laulayin kwana daya kafin ma ayi batun nakuda bana jin da mai yarda dansa ya matsa ko nan da zaure. Ba ita ba ma duk mai so a barta taje ta ga nata."
Ashe sauran ma suna so baki da zuciyar yi Mari ta fisu. Faccalolinta da suke da yara a wasu garuruwan kowacce sai ta fara shiri. Ba lokaci daya zasu je ba saboda kada a bar gidan babu mata. Kaya niki-niki haka Mari ta hadawa su Abbati. Don karfin hali harda shinkafa, kwan zabi da garin kunu. Da ta tashi kuma ta yiwa iyalan malamansu tasu tsarabar.
Zabinta hudu ta tafi dasu suka fara wucewa Zaria ita da dan rakiyarta dan wajen kanwarsu Inuwa. Duhun dare ya kawo kai suka isa unguwar da makarantar take. A cikin layin sun yi arba da almajirai sun fi goma. Yawancinsu duk daga bara suka dawo da abincinsu. Can gabansu suke hango kura tana tashi ga ihun yara da alama dambe ake yi.
Yayin da dan rakiyarta ya yi tsaki ita ido ta zuba tana tausayin yaran da karancin gata ya sa rayuwarsu walagigi irin haka.
Yaro daya ne a kasa guda uku na tumurmusarsa. Baka jin komai sai kukansa gami da tsinuwa da zagin da yake aika musu. Sauri Mari ta kara da niyar ta isa ta rabasu sai ga wani gardi (babba cikin almajiran) da dorina. Yana zuwa ya shiga sambada musu kan mai uwa da wabi. Ji kake taf-taf ga ihun yaran suna sosa inda bulalar ta sauka. Na kwancen da ya kasa tashi ya fi tafka. Ya kuma daga hannu zai zuba masa Mari ta gane ko waye. Babu wanda zai ce ga lokacin da ta motsa kafa sai ganinta suka yi ta duka ta rufe Sani. Bulalar a gadon bayanta ta sauka ta gantsare kwalla mai zafi tana taruwa a idonta.
"Baaba?" Sani ya ce da mamakin da ya gauraya da murna.
Da ka ta amsa shi saboda radadin dukan nan. Ya kuwa kankameta yana kukan dadi. Almajiran da suke wurin suka ruga ana rige rigen fadawa Malam abin da ya faru.
Ita dai Mari daga Sani tayi tana karkade masa jiki. Farinwata ya haska mata shi da kyau taga yadda ya rame kamar ba shi ba. Ya sake kankancewa sai kai shirim kamar ya kumbura. Lebensa sama da kasa a kumbure sannan karshen lebban ta kowane bari ga alamun ciwo. Wurin duk ya tsattsage. Su kauyawa ne amma ba kazamai ba. Zuciyarta tana kunci ta dauke shi yana ta warin rashin wanka. Nan kuma taji abu ya karci hannunta. Ta shafa kafarsa da kyau taji wani mummunan faso da ya mamaye 'yar kafar. Bata ma san ina za ta nufa ba a lokacin sai ga malamin makarantar tasu ya taho yana baza babbar riga.
"Baiwar Allah daga ina? Ance kin yi rabon fada tsakanin dalibai na." Kula ya yi da Sani da ta dauka ya rungume wuyanta da 'yan hannayensa ya daka masa tsawa "to tambadadde daga ganin mata ka makale mata. Ai sai ka sauko tunda ba uwar da ta sallamoka daga kauye bace." Ya mayar da hankalinsa ga Mari yana dan murmushi "haka muke fama fa. Iyaye mata kamar basu san zafin haihuwa ba. Yara da kananun shekaru a kawo a jibge mana. Ba kuma wani kudin azo a gani suke biya ba. Shi wannan ma dai mai idon mayun sam bai kwanta min ba. Kar ki raina kuruciyarsa hatsabibin gaske ne."
Ta so ace wadannan kalaman a kunnen Mal Sa'adu ake fadarsu ya ji da kyau ba ita ba. 'Ya'yan da suke haifa cikin gumi da jini ke irin wannan rayuwar kuma laifinsu ake gani. Zuciyarta ke bugawa da karfi tana son bashi amsa amma tana hango laifin nasu da ya fada.
"Don Allah zamu sami masauki zuwa wayewar gari." Mari ta katse surutun da yake ta yi da wannan tambaya.
Kallonta ya yi sama da kasa tare da dan rakiyarta ya girgiza kai. Haka kawai a wannan zamani da ake fama da 'yan yankan kai bai ga dalilin saukar bakuwar da bai sani ba.
"Sai dai nasa a raka ki gidan Mai Unguwa."
"Nagode, ina kayan Sani suke mu dauka?"
"Baiwar Allah wai daga ina kike ne?" Ganin karfin halinta ya yi na son satar dan mutane a gabansa.
"Mahaifiyar Sani ce daga Kirikasamma. In Allah Ya so ka bar ganin mai idanun mayu kamar yadda ka kira shi daga yau."
Kunya mai tsanani ce ta rufe Malamin. Gidansa ya tafi dasu yasa iyalinsa suyi musu abinci. Da aka kawo ko hannu bata saka ba sai da ta kula Sani yana ta kallo ta janyo kwanon. A baki ta bashi ya ci ya koshi. Ta fita wanke hannu kafin ta dawo bacci ya dauke shi. Shafa shi ta dinga yi tana hawaye. Wai wannan ne Saninta. Yaro mai kiba da kuzari duk ya lalace.
Kayan Sani duka sunyi datti ga wari. Wando da riga ta samu tun asuba ta roki sabulu ta wanke masa. Da yake ana zafi sosai kafin su tashi tafiya sun bushe. Da kanta tayi masa wanka ta dirje masa jiki. Suna shan koko taji ana cewa yaran da suka yi masa duka jiya biyu cikinsu sun kwana suna zawo. Ana tsammanin abincin da suke fadan a kai lalatacce ne.
"Sani ka ci abincin?" Ta tambaye shi hankali a tashe.
"Loma daya nayi suka kwace."
'Kemis zan fara zuwa na saya masa ja da yalo kafin muje tasha' ta ayyana a zuci. Da zasu tafi bata fasa ba ta ajiye musu tsarabar da ta kawo. Neman magani ta dinga yi ido rufe amma bata sami kemis ba sai a tashar ta sayi maganin zawo a wurin wani mai tallan magunguna. Irinsu kemis guda ne a kansu suna sayar da kusan kowane irin magani na bukatar yau da gobe. Ita ba ilimin abin ba haka zalika mai maganin ma sayarwa kawai yake yi. Haka ya hado mata magunguna kala biyar wai duka na zawo da ciwon ciki. Filagil kadai ta gane sai magnesium na ruwa da ake girgizawa kafin a sha. Sauran kuwa kafinol ne hade da boscopon da panadol extra. Burinta kada wani abu ya sami danta saboda haka kai tsaye ta bashi na ruwan.
Hakura tayi da zuwa ganin Abbati zata koma gida har sai Sani ya dan murmure. A hanya ya soma ciwon ciki yana ta amai. Daga baya sai zawo duk ya fita hayyacinsa. Shi yake ciwon amma Mari ke kuka. Sauran fasinjoji kuma suka dinga hantararsu saboda wari ya ishesu. Babu wanda ya san lalurar da ta kawosu wannan matsayi aka dinga cin mutumcin 'yan kauye a gaban idonsu.
Kafin su isa Kirikasamma Sani ya fara sankamewa idanunsa a waje gwanin ban tausayi. Mari tayi kuka har muryarta ta dashe wurin yi masa sannu.
"Baaba cikina zai tsinke ki kara min magani."
Sam ta manta da magungunan da ta saya ai kuwa ta roki ruwa a wurin wata da ta kulla a farar leda. Ta ballo bibbiyu kowanne kamar yadda mai maganin ya ce mata ta bashi.
Cikin zakuwa take tambayarsa "Ka fara jin sauki?"
"Eh" ya amsa idanunsa suna kakkafewa.
A zaton Mari bacci ne. Rungume shi tayi tana dan jijjiga shi har rai yayi halinsa bata sani ba. Ashe rabon su gana ne ya kaita Zaria. Da zasu fita daga motar wata ta ce mata jikinsa kamar ya saki.
Da murmushi ta ce "bacci ya samu."
Goya shi tayi ta dauko wasu kayayyakin. Sauran kuma dan rakiyarta ya dauka suka dauki hanyar gida a kafa. Lokaci lokaci take gyara goyon ta yi masa sannu. Rashin amsawarsa a wurinta saboda bacci ne.
Sun kusa isa gida ta hango Inuwa a majalisarsu ta karkashin bishiyar darbejiya. Mamakin dawowarta a yau yayi tunda kwana uku ta ce za ta yi. Silifas dinsa ya zura ya taso da sauri da ya fahimci goyo tayi.
"Ba dai Sani kika dauko ba Mari? Me kike so na cewa Malam?"
"Maganar ba ta hanya bace ka bari muje gida. Bashi da lafiya ba zan iya barin shi a can ba."
Dan murmushi ya yi sanin cewa ita ma akwai taurin kai. Yana son yin yadda take so amma ba zai iya sabawa yayansa ba.
"To kwanto min shi na dauke shi naga kema a gajiye kike."
Ba musu ta kwance goyon Inuwa ya tare zai saba shi a kafada yaji yanayin jikin wani iri. Mutum biyu cikin abokansa suka taso jin ba'asi ganin ana kwance goyo.
"Sani ne jikin ba dadi ta taho dashi gida." Inuwa ya fada musu.
"To kawo shi mana ka tayata da sauran kayan."
Mijin Tasalla ne Lukumanu ya karbe shi sai ya dago shi da sauri jin ya tafi baki daya. Hannunsa na rawa ya ce,
"Sani. Sani bude ido..."
Mari sai ta tsaya tana son cewa bacci yake taga duk sun rufa a kansa ana jijjiga shi. Inuwa da karfi yake kiransa jikinsa yana tsuma.
"Sai dai hakuri Inuwa amma Sani ya amsa kira."
Kalaman Lukumanu kenan da suka shiga kunnuwan Mari. Duniyar tsayawa tayi cak bata iya tuna komai sai ranar da ta haife shi. Ranar da taji ciwon nakudar da ya zarce na Abbati. Lokutan da ta dinga sake-saken burikanta akan kyakkyawar rayuwar da take masa fata kamar yadda ta y
iwa Abbati. Fuskar Saninta wanda yake ta kuka ba zai je almajiranci ba take gani. Yaron da jiya jiyan nan ta ganshi ana turmususa a cikin kasa akan lomar abinci.
A kwana na biyu da rasuwar ta dan dawo hayyacinta. Kuka take yi ta rungume ledar magungunan da ta bashi. Muryarsa ke yi mata amsa amo tana jin lokacin da yake rokonta ta kara masa magani. A yayin da wasu zafafan hawaye ke kwarara a idanun Mari sai ta bawa Inuwa tausayi. Shi ma din zuciyarsa ta dinga raya masa lallai su dawo da Abbati gida.
Wani abin ban tausayi ga wannan mata bai wuce har ita ma ta koma ga Allah SWT ba za ta taba sanin ainihin sanadin ajalin danta ba. Komai a rayuwa yana da sila. Hakkin ran Sani yana rataye a wuyan jama'a da dama. Babban cikinsu Mal Sa'adu mai ingiza kai yara almajiranci. Ga Inuwa da ya kasa jajircewa wurin kare amanar da Allah Ya bashi ta 'ya'ya daga dan uwansa. A gefe guda ga Malamin tsangayarsu da bai rike amanar da aka bashi ba ta yaran mutane. Matar da yayi bara a gidanta ta bashi lalataccen abinci saboda rashin sanin girman hakkin bil adama. Yaran da karancin tarbiya da kulawa ya janyo suka yi masa duka akan abincin da ya samo. Mai sayar da maganin da bashi da iliminsu ga mutane saboda neman kudi. Gwamnatin da ta yarje masa yawo a tituna da kwararo yana sayarwa bayan bashi da lasisin bada magani. Kaico! Hatta Mari da ta bawa Sani magungunan nan bisa rashin sani da tsantsar soyayya irin ta uwa da
a bata tsira ba. A takaice dai the society killed Sani!
Kalmar hutu kanta tana da dadin fada a baki balle kuma idan jiki zai same shi a aikace. A wurin Innayo kuwa daga mai arziki sai wanda bai san ciwon kansa ba kamar Asabe ke hutawa. 'Yan mata biyar a gabanta babu mai basu sai abin da Allah Ya hore mata daga kasuwancinta. Biki ko suna da wuya yake hanata dora tukunya. Abin da ya kama dole taje to lallai wata cikin 'yan matan za ta zauna a gida. Yau kuwa dole ta saka ta zaman gida tana hutun dole.
Ranar ta kama litinin. Ta tashi da ciwon kirjin da ya kan damketa lokaci zuwa lokaci. Yaran nata kuma duka suna makaranta. Zara da bata kaunar karatu sai gayu ta so zaman jinya amma Innayo ta kora ta. Hudu suna zango na uku a makaranta. Jarabawa ake yi ta canjin aji ba za ta so a sanadiyarta wata ta maimaita ba. Babbar kuwa shekararta ta farko kenan a School of Nursing. Ayyukan da basu zama dole ba Innayo ta dauke mata a gidan saboda kawai ta sami isasshen lokacin karatu.
Tsakar gidan nasu tsit sai ita kadai a daki. Alh Rabi'u yana kasuwa. Asabe kuma makota ta shiga saboda an kusa sauke sanwar rana. A can za ta ciko cikinta su kuma yaran ta dafa musu gurjiya kowa ya ci ya sha ruwa babu ruwanta.
Zumbur Innayo ta tashi da ta tuna ta sa a jika mata gero tun dare amma ciwo ya hana ta wanke a kai nika. Idan ta barshi zai lalace gashi har kwano uku. Tashi tayi da kyar tana dafa bango ko ruwan ne ta samu ta canja. Bandaki ta fara zagawa domin rage mara taji taku da 'yan maganganu anayi. Gida na jama'a bata wani damu ba ta kammala ta fito. Babu kowa har yanzu a tsakar gidan ta zauna tana wankin geronta.
Kwana biyu da suka wuce Munzali ya yi wata magana da dan kanwar Asabe da yazo musu hutu. Shi satin da ya gabata suka gama tasu jarabawar. Yaron mai suna Halliru ya girme shi da kusan shekara biyu.
"Idan ka yarda muka yi aradu yau abincinka da nama" ya ce saboda ya fahimci amfani da kayan kwadayi yana taimakawa wurin samun biyan bukata.
Halliru ya kai masa duka a kafada yana dariya"ashe kai gara ne ban sani ba" karkada hannu ya yi tare da jijjiga kai yana yi masa kallon rainin wayo "to bari kaji in fada maka da mata ake yi ba maza ba. Na taba gani a lungun gidan Mai kalanzir din unguwarmu."
Dan jim Munzali ya yi yana nazari daidai kwakwalwarsa kafin ya ce "kai ka taba yi da macen ne?"
A kunne Halliru ya rada masa cewa suna yi da kanwarsa idan babu kowa a gida. Ya kara da yi masa bayanin yadda suke jindadi. Shi ma 'yar makota ce da ta girme shi ta koya masa shi kuma ya koyawa kanwar. Da 'yan shekarunsu ya kwadaitawa Munzali son gwadawa.
Shi ne fa ya bawa 'yar makotansu inda Asabe ta shiga kwadayi kafi-kaza ya taho da ita gida lokacin da Innayo ta zaga.
Tare suka je gidan da Asabe ta kore shi da mugun kallo "shegen yaro kwalamamme. Ka biyoni salon taga munyi mata yawa taki zuba min abincin. Banda abinka idan ta bani ba zan rago muku ba?"
Cike da tsiwa ya ce "za dai ki rago musu. Yaushe rabona da cin abincin makiyalla."
Baki ta sake maganar ta shigeta ta daga hannu za ta kai masa mari "kut! Nice ma nake makiyalla?"
Juyawa ya yi zai tafi idonsa caraf akan 'yar gidan da bata fi shekara shida ba. Da sauri ya dago ledar kafi-kazan yana kiranta. Kafin ta iso sai da Asabe ta karba ta barbada a tafin hannunta ta lashe.
"Munzali kenan. Kai dai ba dai mutane masu insani ba. Kwanakin nan har wani kumatu ka dire." Ta kai hannu ta yi masa dukan wasa "ni ko saura ne ka dinga rago min a leda mana. Sai bakin hali irin na ubansa."
Shigewa tayi shi kuma Munzali ya sami damar hillatar yarinyar suka tafi gida. Ya zata gidan ba kowa. Dakin Asabe ya shiga da ita inda babu kowa ya ce ta zo ya koya mata wani abu.
Da kananun shekarunsa shaidanci ya shige shi har ya sami amincewarta ta cire kaya yadda ya umarceta. Karatun Halliru ya soma aiwatarwa akan yarinyar da bata san me ake yi ba.
"Kar ki fadawa kowa kinji. Zan dinga baki tsamiyar biri da kafi-kaza."
"Harda tsamiya gaye?" Ta tambaye shi da murmushi.
"Duk abin da kike so zan dinga baki indai baki fada ba."
A can gidansu kuwa Asabe tana ta sharbar faten tsakin da babarta ta bata.
Innayo tana wankin gero taji kamar ana magana kasa-kasa. Gajiya tayi da sharewa ta tashi ta nufi dakin. Duk a zatonta abokan Munzali ne. Satin da ya wuce Asabe ta tafi yawonta aka zo aka dauke mata kudin dashi. Tayi ta rantsuwa wai cikin 'ya'yan Innayo ne. Shi ne ta tashi ta leka don kada a sake sakata biyan kudin da ta san karya ake musu.
Tana daga labule tayi mummunan gamo. Da sauri ta afka dakin ta cakumi wuyan Munzali ta kifa masa wani gigitaccen mari. Tana dukansa amma jikinta ke rawa kuma ita ke fitar da hawaye. Idanunsa kyamas abin sa ya ja wandonsa ya mayar. Yarinyar kuwa ko a jikinta. Kafi-kaza ne tayi dumu-dumu dashi tana ta lasa.
Ta baya Innayo taji an riko mata wuya tana juyowa Asabe ta dauketa da mari ita ma.
"Kashe min dan zaki yi?" Ta kwance dankwali taci dammara "muguwa, makira. Ba tun yau na san magadan Alhaji sun tsole miki ido ba. Wato niyarki ki karshi a daka babu kowa ki fice."
Yau daya Innayo ba ta kishi take ba. Tausayin Asabe ma take ji saboda wannan halayya idan Munzali ya tashi da ita ba karamar masifa bace.
"Ai dai kya tambayeni me ya yi kafin ki fara sababi. Ganinsa fa nayi akan wannan yarinyar daga shi har ita ba wando...."
Wani irin bugu Asabe ta yiwa kasa da hannu ta tafa hannuwan tana hargagi "ahayyeeeee....anyi walkiya na ganki Innayo. Yau dai rigar munafunci ta sauka an miki tsirara a idona. Wato kiyayyar taki da 'ya'yana har ta kai kiyi musu irin wannan sharri mai muni."
"Asabe. Asabe ki ajiye maganar kishi ki duba tarbiyar 'ya'yanki. Meye ribata idan nayi masa sharri."
Juyo dashi Asabe tayi duk da fargabar dake zuciyarta amma sam ba za ta yarda Innayo tayi mata dariya ba.
"Kai Munzali wai da gaske ne?"
Sai da ya kumburo baki ya ce "Biyoni tayi fa shi ne ta ce in kaita bayi tayi fitsari. Kawai ina cire mata wandon ta hau dukana."
Ajiyar zuciya Asabe ta sauke ta kalli Innayo "to kin dai ji. Haka kawai za ki kulla masa sharri. Yo Allah na tuba yaron nan nawa ma yake? Me ya sani? Ko an fada miki kowa ma irin wadancan shirgin ne da ki ka tara a daka suna yawon ta zubar?"
Lokacin ya yi! Tana kai karshen maganar Innayo ta rama marin dazu. Ba lafiya gareta ba amma tuni ta manta da ciwon. Zagi ba irin wanda Asabe bata yi mata ba ta ja gefe tana kallonta. Damben da take so ta biye mata suyi ne ba za tayi ba. Munzali salin alin ya ja hannun yarinyar ya kai ta kofar gidansu ya kara gaba.
Dare ya raba Asabe ta kasa baccin kirki. Tashi tayi ta koma rumfarta ta taba Munzali.
"Ka tabbata dazu Innayo karya tayi maka?"
Sai da ya murza ido saboda bacci sannan ya ce "Halliru ne ya ce wai da mata yafi dadi."
A baya ta daka masa duka a razane "bude ido don ubanka. Kayi da gaske?"
Lokacin ya wartsake ya girgiza kai "ni ban yi mata komai ba."
Jinjina kai tayi ta ce ya kwanta. Ta san karya yake. Har kasan zuciyarta ta yarda da Innayo da subutar bakinsa ta dazu. Sai dai kuma ko ana muzuru ana shaho ba za ta taba yarda ace laifinsa bane. Wannan magana anyi an gamata daga yau
AFAFUN TEBUR.
Kwana goma cif da tarewar Nasima a gidan Tahir. Amarci suke irin wanda iyayen gida ke tsoron ayi musu kishiya su ga irinsa. Kullum sabon nau'in fitsara da rashin kunya Nasima ke kirkira wanda zai batawa Khadija rai. Abin da bata sani ba kuwa shi ne fitar Tahir da aurensa kacokan daga zuciyar Khadijan. Zaman 'ya'ya take yi kamar yadda matan aure da yawa suke yi. Bata da dogon buri ko hangen komai sama da inganta musu rayuwa. Ba don su ba komai wuya da tuni ta koma gidan mahaifinta.
Sati guda ta sani addini ya bawa amarya budurwa tayi tare da ango kafin a raba kwana tsakaninta da ta gidan. A sati dayan sai take yi musu girki na kyautatawa ba don ta burgesu ba sai don ta sami ladan rama sharri da alkhairi. Anyi satin an wuce shiru Tahir bai yi mata maganar su raba kwana ba. Girki kuma bata ga alamun Nasima za ta shiga kitchen ba sai ta cigaba da yi saboda yaranta.
Tana cikin wanke salad Nasima ta shigo kitchen din dauke da kwalin sabon food flask. Tukunyar shinkafar da Khadija ta bari ta karasa turara ta nufa kai tsaye. Khadija bata nuna ta san da wanzuwarta a wurin ba sai da taji ta bude tukunyar. Don karfin hali ma harda cokalinta a hannu ta danna shi kasa domin ta tabbatar ruwan ya tsotse.
"Lafiya?"
Baki ta murguda mata gami da fari da idanu "lafiya kamar ya?"
Ran ta ya soma baci sai dai tayi alkawarin Nasima tayi kadan tayi fada da ita.
"Abincina naga kina shirin budewa."
"Abincinki ko abincin mijinmu? Naga dai shi ya saya don kin girka hakan ba ya nufin ba zamu ci ba."
'Kar ki biye mata' Zuciyarta ta kwabeta a lokacin da taji kamar ta mareta. Suturar jikinta da tun tarewarta irinsu take sakawa ta kalla ta kawar da kai. Gajeren wando ne da bai kai rabin cinyarta ba sai damammiyar vest. Anayi ne don ta tofa ace ta ce shi yasa take bawa iska ajiyarta.
"Ki jira na dibarwa yara tukunna."
Wani irin kallon raini Nasima tayi mata ta soma cewa "ke kin i..." sai taji an bude kofa kuma ta tabbatar Tahir ne. Langabe kai tayi ta kwantar da murya tana bubbuga kafa duk jikinta na rawa "ni dai don Allah Anti Khadija ki karba haka nan. Wayon hutawa kawai kike yi min kin barni inata fama ni kadai."
Kitchen din Tahir ya shigo Nasima ta kwabe fuska tana yi masa shagwaba "Diya (Dear) wai kaji ta kara mana satin amarci ba yanzu za'a fara rabawa ba."
Ko ita ta sarawa kissar Nasima. Jinjina kai tayi harda 'yar dariya.
"Sai fa ba Diya ba"
"Me ki ka ce?" Tahir ya tambayeta ta da murmushin jindadi a zatonsa sun fara hada kai ne.
"Ban ce komai ba" sai ta mayar da dubanta ga Nasima "na baku wata guda don Allah kada ki ce baki karba ba. Da so samu ne ma zan fi son karba idan ki ka fara tofe-tofe da tashin zuciya."
Ta karasa maganar ne tana dibar abinci. Da ta gama ta zo fita ta dakata a gaban Tahir.
"Af...Diya" ta furta kalmar yadda Nasima ke fada da tsantsar rashin wayewa "na ce kada ka manta yaba kyauta tukwuci. Zan zo amsar nawa idan mun gama cin abinci. Da yake ma mu ba mayunwata bane idan za ka saurareni yanzu na san zasu iya jira."
Lebensa ya cije. Magana Khadija ta yaba musu daga shi har Nasima. Haushi ya kama shi ya nemi yunwar ya rasa. Data kawo musu daki ko kallo kwanukan basu ishe shi ba. Tunanin maganganun Khadija ne ya addabe shi.
"Waye ya bata izinin karin kwanakin ma?"
Ya yi kwafa shi kadai. Kila fushi tayi don ya kara kwana uku akan bakwai din. Nasima ya kalla wadda har yau bata dena yiwa abinci cin yunwa ba ya tashi.
A daki ya sameta ta goya Sauda. Tana ganinsa ta dauko form din JAMB ta mika masa. Ta riga ta cike komai, izininsa kawai take nema.
Kallon rashin gamsuwa ya fara yi mata ta hade hannuwanta biyu a kirji. Fuskarta babu alamun za ta yarda da kalmar a'a.
"Da can me yasa baki taba cewa zaki koma makaranta ba da na hana sai yanzu. Don nayi aure kina tunanin bani da sauran hurumin sawa da hanawa a gidana?"
"Kana dashi matsawar ina amsa sunan matarka. Amma ina so kayi min adalci guda daya. Kar ka manta har na koma ga Mahaliccina hotonku kai da matarka ba zai taba..."
Baya so ta kai karshen maganar saboda kar ta ga alamun kunya a tare dashi. Karanta form din ya shiga yi da karfi har sai da tayi dan murmushi.
"Bari nayi sauri naje banki kafin su rufe na ciro miki kudin registration. Allah Ya bada sa'a."
Anyi an gama komai cikin nasara. Khadija ta sami gurbin karanta Business Administration a ABU Zaria. Shirinta take yi hankali kwance ta manta da duka wata damuwar gidansa.
Nasima tana ta fama da laulayi. A gabanta take wasu abubuwan kamar su tara yawu da yunkurin amai. Idan tana yi da tsantsar tausayi zaka ga Khadija tana yi mata sannu. Ko daga murya bata taba yi mata. Haushin da take son bata karshe ita take ji.
Gida Tahir ya kama mata a Zaria mai daki biyu da falo. Ana saura kwana uku ta tafi ya shiga dakinta yaga akwatunan da ya tabbatar ba nata bane ita kadai.
"Kada ki ce min da su Suhaib za ki tafi."
Murmushi ya gani a fuskarta da ta dago kai. Ya fara tsanar murmushin saboda yadda bakar magana cikin nutsuwa take biyo bayansa.
"Haba Diya. Kada ka ce min kayi zaton zan barsu a wajen amarya. Yanzu don Allah idan kai ne ita zaka so na bar maka 'ya'yana? Idan kaine ni za ka bar mata 'ya'yanka?"
Shiru ya yi ta fita daga dakin ya bi bayanta da sauri. Tsohon dakinsa wanda ya zama na Nasima ta shiga. Rabonta da dakin tun tana kwashe 'yan tarkacenta. Zuciyarta wani irin kunci tayi mata. Bakinta har yana daci saboda tunawa da yanayin da ta taba ganinsu amma ta daure.
Sallama tayi Nasima ta zo ta bude kofar tana yatsina. Ganin Tahir a bayanta sai ta saki fuska.
"Anti nemana kike? Ai da kin turo su Lilu sun kirani."
Sai da Khadija ta kallesu su biyun sannan ta ce "dama Diya ne ya ce na bar miki yara nace gara dai mu koma Zariyan tare. Kina fama da laulayi ba iya wahalarsu zaki yi ba. Duk da haka dai na ce bari naji ta bakinki."
Langabewa Nasima tayi don bata ga dalilin da zai sa ta karbi yaran ba. Daga haka ma tana fatan maganinsu ya ci tayi gaba kenan har abada.
"Zan so zama dasu Anti. Bari dai na sauke nauyin nan da kaina zan zo na dawo dasu."
"To kai kaji Diya. Za ta so zama dasu amma sai ta haife nata. Bari na barku zan karasa hada kayan."
Tafiyarta tayi ta barsu Nasima na rungumo shi yana kwacewa. Fada ya soma yi mata ba ji ba gani.
"Yanzu ke ko kunyar idona baki ji ba ki ke nuna ba za ki iya zama da 'ya'yana ba?"
Turo masa baki tayi da tsiwarta ita ma.
"Haka ka ji na ce? Kuma nima dai haihuwar nan zanyi. Idan ma takama ake yi da 'ya'ya nima zan haifa maka wasu."
Ransa yake ji a jagule. Dama gashi ta fara sire masa. Abin da yake doki ya riga ya samu har ya fara tunanin komawa titi abin sa. Ga Khadija duk ta canja. Da yatsa ya nunata kamar zai tsokane mata ido.
"Bar ganina haka wadannan yaran basu da na biyu. Ina son abuna kuma idan kina neman zaman lafiya a gidan nan dole ki so su."
Bai kara saurararta ba ya tafi dakinsa ya banko kofa cikin bacin rai. Zama ya yi yana tunanin me yasa yake ganin kamar Khadija ta daina sonsa? Ba haka yake so ta dinga yi masa ba. Kishin da ya tsammaci gani wanda zai tabbatar masa da sauran matsayinsa a zuciyarta duk babu. Baya mantawa kafin wata dayan nan da ta kara musu ya cika gabadaya Nasima sai da ta gundure shi. Don ma yana jin sonta a zuciyarsa ne da bai san me zai faru ba. Yana ta tuhumar kansa me yasa ya yi saurin aurenta. Da ya sani kuruciyarta kawai ya mora ya bata abin da zai bata a waje. Yarinyar sam bata da aji.
"Wai Diya...sai kace wani dabba. Mtseww"
Tunawa ya yi Khadija ma tana fada idan ta so cusa masa haushi ya yi dan murmushi. Tunda dai bata tafi ba zai cigaba da lallaba abarsa. Da tsohuwar zuma ake magani. Mata nawa ya nema bayan aurensu amma duk inda ya gama yawonsa wurinta yake dawowa.
Da yake ita keda girki ranar da ya koma dakinta ta cigaba da yi masa komai yadda ta saba. Kallonsa tayi yana ta biyewa yaransa suna wasa tayi kwafa. Ba za ta taba bari ya gane kudurinta ba. Da kudinsa za tayi karatu. Burinta ta sami jari ko aiki a gaba wanda za ta iya rike kanta da 'ya'yanta. Komai dadewar lokaci, komai tsufa, za ta bar gidan Tahir.
Nasima kuwa ta dade a tsaye inda Tahir ya barta. Tsoro ya gama mamaye zuciyarta domin ta kula ba tun yau Tahir yake hantararta ba.
"Na rantse kayi karya Tahir. Ni da kai yanzu muka fara zaman aure."
A ranar ta tambaye shi zuwa gida ya amince. Washegari yana fita ta tafi wurin Laraba. 'Yan kudaden da yake bata ta fiddo duka aka bawa wani malamin tsibbu. Ya hado mata magunguna da bayanin cewa da basu zo ba a ranar zai saketa. Wai bokan Khadija ne yake musu farraku.
"Laraba kin ji ko? Na fada miki yanzu kamar bana burge shi ga yawan fada." Ta ce cike da gamsuwar karyar bokan.
Kulle-kullen da ya basu ta dauka ta tafi dasu gida tayi amfani dasu yadda ya ce.
To gidan dai rayuwa ake yau fari gobe tsumma. Khadija tana Zaria da yaranta sai dai Tahir ya ziyarce su. Ko suna hutu sai ta fake da karatun yaran. Sai lokutan hutu gama-gari take zuwa gidan. Karatunta take yi hankali kwance sannan tana sayar da zobo da ginger. Tun tana kullasu a leda har ta koma yin na roba. Kasuwa ta karbu har freezer ta kara saya da ribar cinikin.
"Ina cewa matarka bata da hankali ashe kaine babban mara hankalin. Inuwa! Inuwa ka bani kunya." Mal. Sa'adu ya furta rai a bace.
Sunkuyar da kai Inuwa ya yi kunya ta mamaye shi. Yayan nasa bai tashi yi masa tijara ba sai da yaga sauran matan kannensa sun zo wucewa. Ai kuwa tsayuwa suka yi a fakaice aka gama jin fadan.
"Amma saboda Allah Yaya kana ganin irin mutuwar da Sani ya yi. Idan bamu yi wani abu ba shi ma Abbatin haka zamu rasa shi"
Murya har dakuna mafiya kusa ake jin fadan Mal. Sa'adu yana cewa "Wanda ya rasu a wurin neman ilimi yana cikin jerin shahidai idan baka sani ba. Kuma tunda mutuwar ta kuruciya ce idan an je lashirar ba kai da Marin za'a fara cewa ya ceto ba. Kila ni da na assasa tafiyar ma sai ya gama daku zai ambaceni."
Inuwa dagewa ya yi shi ma"Ni dai gaskiya zan dauko shi na saka shi a ta allo da boko a nan."
"Ahap...tushen magana ya hito da za ka zauna kana yi min kwana-kwana. Daga makarantar 'yan aljanna za ka kaishi ta 'yan wuta. Wai ma shin 'ya'yanka aka fara kaiwa ne? Gidan nan kowa yana kaiwa. Don naka ya rasu sai ka kasa karbar kaddara?"
Fadan Mal. Sa'adu yaki karewa. Inuwa tun yana mayarwa har ya kasa katabus. Sauran 'yan uwansa ne suka hade masa kai aka fara yi masa nuni da cewa Mari tafi karfinsa kuma ita take juya shi. Bahaushen mutum da jiji da kai da gudun raini sai yaji tsoron kada su raina shi. Har kasan zuciyarsa ba ya so amma kuma rashin son ayi masa kallon mijin-tace ya danne komai. Sun kunno shi sosai sannan ya shiga ciki ya hau Mari da fada.
"Abbati ba zai dawo gida ba kuma ban yarda ki je Kano ganinsa ba. Tunda dai zasu zo hutun Takutaha nima ba zuwa zanyi ba."
Wani abu ta hadiye da ya tokare mata wuya da kyar sannan ta daga kai ta kalle shi. An kusa wata biyu da rasuwar Sani amma har yau ta kasa komawa daidai. Da ciwo mai raunana zuciya da ruhi a tare da ita. Dashi take kwana dashi take tashi. Duniyar sam ta daina yi mata dadi. Gani take ta gaza a matsayinta na uwa. Kwanakin farkon rasuwar saboda ta sa abin a rai har mafarkinsa take yi yana tuhumarta da wulakanta amanar Allah.
Shekararsa bakwai kacal a duniya. Sa'anninsa da suke cikin gata wasu ko kyakkyawan tsarki basu iya ba. Wasu su dawo daga makaranta suna bore suna ihun sun girma uwa ta kamasu tayi musu wanka da kanta. Wasu a basu abinci a baki. Wasu uwa ta shagwabasu da soyayya ba don su lalace a tarbiyya ba. Almajiri kuwa sai yadda Allah Ya yi. Ga kuruciya, ga rashin gata kuma a haka cuta za ta kama shi. Babu magani babu kuzarin yin bara sannan ba lallai a sami mai damuwa da halin da yake ciki ba balle a taimaka masa. Idan da tsananin ciwo zai saka shi amai a makwancinsu babu abin mamaki wurin samun masu yi masa tsawa da hantara kuma ace ya goge wurin. Idan ya yi zawo a jikinsa sauran dalibai su toshe hanci su guje shi.
(Ke da yake da yake yiwa shara, wanke-wanke ko zuwa aike idan ya yi fashi ki hau shi da fada. Cikin dan albashin da kike bashi ki cire na kwanakin da bai zo ba. Ya wuni a rana yana wanki ki bashi ragowar abincin jiya kila ko dumamawa baki yi ba. Hakika tallafawa almajirai kafin gwamnati da masu ruwa da tsaki su dakatar da wannan al'adar jihadi ne. Idan wani mahaifiyarsa tana da rai kuma ta yarda yazo wani tasa uwar irin su Mari ce ko maraya ne. Idan wasu duniya ta lalatasu kamar Abbati wani kuma is innocent kamar Sani.)
"Allah Ya kaimu Takutahan" ta iya cewa kadai.
Watannin sun wuce a yayin da bawa yake ta fadi tashin neman na kai. Wannan mummunar alfasha ta gama shiga jikin Abbati da Munzali. Ranaku daidai ne basa haduwa. Shazali da abokansa suka koma amfani dasu biyun. Saboda haka yanzu abincin Abbatin ma ko bai hadu da Munzali ba zai samu a wurinsu. Ya murmure fiye da yadda ya zo daga kauye. Ya kuma zama fitsararre mara kunya da kawaici. Babu mai saka shi ko ya hana shi a makarantar saboda Shazali ya tsaya masa.
Malaminsu ya dade da sallama su Shazali. Sun zame masa karfen kafa. Babu karatu kuma sun ki komawa gidajensu.
Ana gobe hutun Abbati ne tare da Munzali dasu Shazali a kangon suna cin abinci. Tsire ne da biredi sai kwalbar lemo a hannun kowannensu.
Shazali ya kusa sati yana juyayin gabatar musu da wata bukata amma yana gudun kada cikin surutu su fadawa wani. Amininsa ne ya ankarar dashi cewa
a zasu fada fa da tuni wancan abu ya dade da yaduwa. Sai da ya kula duka suna jindadin abincin ya kawo zancen.
"Da ace kullum ni nake baku kudin abinci ko na baku ba gara ku dinga bina inda nake samowa ba ku ma ku dinga shanawa da kyau."
"Al'Qur'an ko ma ina ne ni dai zan bika." Cewar Abbati da zumudi.
"Kai fa Munzali?"
"Abbati ma zai yaje bare ni."
"A wurin irin abin nan da muke yi zasu dinga yi daku sai a baku kudi. Idan ku ka fadawa wani a take zaku mutu."
Wannan ba abin damuwa bane tunda sun riga sun saba. Abbati bai ji dadi ba saboda dole sai bayan ya dawo daga gida za'a kai shi.
Ranar da zasu tafi 'yan uwansa na wasu makarantun a Kano ne suka hadu da 'ya'yan makota duk 'yan gari daya suka tafi tare. Yana shiga mota ya shafe shafin su Munzali. Hankalinsa ya yi gida Baaba Marinsa yake son gani da kannensa. A nasa haukan yake son ganin Sani ya fada masa abin da yake yi yana samun kudi da abinci.
Zancen zuci yake wanda don dadin da abin ya yi masa har dan tsalle ya yi akan kujerar mota. 'Shi ma idan ya yi mu tara kudi mu kai Baaba Makka da Madina'. Bai san abin da yake ya munana ba. Ya dai san kila Mari tayi masa fada. Munzali ya ce manya ne kadai suke yi.
Mari tana yayyafawa itacen da ta gama yiwa Abbati miyar zabi taji muryarsa.
"Baaba. Baaba na dawo. Baaba Sani ma ya zo?"
Murnar da ta tashi da ita sai ta nemi komawa ciwon rashin Sani. Murmushi tayi saurin yi domin kada ya zata bata murnar ganinsa har ya iso gareta. Da murnarsa ya taho zai rungumeta sai taji kunya. Tsakar gidan da mutane duk an zuba musu idanu. Yana isowa sai zai riketa sai ta dafa kansa.
"Kun dawo lafiya?"
Bai biye mata ba ya rungumeta yana dariya.
"Lafiya kalau Baaba. Ina Sani? Ya zo gida?"
Kwalla ta sake tarar mata a karo na biyu ta kawar da kai gefe "Sani kadai ka sani ba ka cigiyar sauran?"
Uwargidan Mal. Sa'adu tana jinsu ta murmusa da gayya ta ce "Wai wane Sanin ake zance ne? Ko marigayi?"
Mari ta dubeta cikin bacin rai ganin Abbati ya juya da sauri.
"Haba Yaya Deluwa kya dai bari ko abin ci ne yaci mana."
"Au, wai dama bai ji labarin mutuwar kanin nasa ba?" Deluwa ta furta kamar bata ji me Mari ta ce ba.
Abbati sai ya matsa kusa da ita hankalinsa a tashe.
"Iya Deluwa wane Sanin ne ya rasu?"
Sauran matan gidan duk sai suka fito aka dinga cewa "Allah Sarki" da karyewar murya mai cike da alhini. Yanayin tashin muryarsu kadai sai yasa mutum yaji babu dadi.
"Sani ai ya kusa arba'in biyu a kabari. Yaro yunwa da rashin gata suka yi ajalinsa." Inji wata faccalar ta ta.
Deluwa ta cafe da saurin kwabarta "ko kiyaye bakinki dai. Ah to. Malam ya ce mutuwar jahadi ya yi tunda a bakin neman ilimi ne."
Wani irin kuka Abbati ya saka yana zubewa a wurin. Mari da ta sami damar motsawa ba ita ta tsaya ba sai a tsakar dakinta. Ita ma nata kukan take yi har Abbati ya shigo ta share idonta da sauri.
"Zauna in zubo maka abinci. 'Yan uwanka ma babu wanda yaci suna jiran dawowarka."
"Baaba da gaske saboda yunwa Sani ya rasu?"
Tambayar ta daki zuciyarta. Ta laluba ta rasa amsar da ta dace ta bashi.
"Bana son yawan tambaya. Almajiranci ne anyi an gama. Ka dawo kenan ba za ka koma Kano ba."
Nan fa Abbati ya yi wuf ya mike yana mai tuno Munzali da abin da suke yi sannan da irin abincin da suke ci wanda bai taba samu a kauyen.
"Ni dai zan koma."
Bata kawo komai ba a ranta illa gargadin da tayi tsammanin anyi masa akan kada ya zata ya gama karatun kenan. Kannensa mata ta kira suka hadu su hudu ta zuba musu abinci a babban farantin da ya kasance murfin fanteka. Shinkafa ta dafa musu wadda ta kwana hudu tana tsinta. Sai miyar dage-dagenta da tasha naman zabi taji gishiri da kafi zabo (vedan).
Farincikin ragowar yaran a bayyane yake. Cikinsu babu wanda bai hadiyi yawu ba tun kafin ta ajiye musu abincin. Naman ta saka musu yanka dai-dai shi kuma Abbati guda uku.
Abin dariya da ban tausayi ya hade duka lokaci guda. Ci suke kamar mayunwata yau an sami shinkafa. Abbati kuwa loma daya ya yi da kyar ya kasa ci. Ko kadan girkin da mahaifiyarsa ta sha wahalar hada kayan yinsa da wahalar girkawa bai burgeshi ba. Salam haka yake jin dandadon girkin. Miyar ma a idonsa bata yi kyau irin na wadda ya saba ci ba. Ga kannensa suna ta wawa shi kuwa shinkafa ma har ta soma gundurarsa.
Mari ta lura baya ci sosai duk sai ta damu. Me yiwuwa ko zancen rasuwar Sani ke damunsa. Sai da suka gama tayi masa magana. Naman ma tana kallo ya bar musu suka cinye.
"Abbati ka cire damuwa daga ranka ka dinga saka Sani a addu'a kaji. Yanzu me ka ke marmarin ci? Naga kamar ka kasa cin shinkafar."
"Da kin sani tuwo ki ka yi min Baaba."
Yana gama magana ta tashi. Iccen da ta zubawa ruwa ta tura gefe ta duba bata da isasshe. Yaran nata sun fice wasa dole ta saka mayafi ta fita. Da kanta ta karbo itace a wurin kanin Inuwa a waje tazo ta hura ta dora ruwan tuwo da miya.
Kan kace meye wannan ta gama tuwon dawa da miyar busasshiyar kubewa. Dakunan faccalolinta dake kusa da ita sai leken tsakar gidan suke ana hadiyar yawu. Inuwa kansa da ya shigo bai iya daurewa ba ya bukaci ta zuba masa.
"Malam ga fa naka abincin. Tuwon na Abbati ne."
Zai sake magana ta bude tasar yaga shinkafa da miyar nan. Tuni ya manta da batun tuwo ya tsoma hannu ko wankewa bai yi ba. Loma manya manya ya dinga shirgawa kafin ta farga sai kwano babu kwayar shinkafa ko daya. Ya daga kwanon sha ya kurbi ruwa sannan ya yi mata godiya. Akuyarta ta sayar ta auno shinkafa, kayan miya, zabi da kayan abincin da ya san bai ajiye ba kuma bashi da kudinsu.
Tana lura da yadda 'ya'yan gidan ke mata kai kawo a bangarenta saboda girkin da tayi. Da can ma tare suke cin abinci da nata yaran. Amma tun tafiyar su Abbati karatu aka dinga gulmarta ana cewa bata san darajar addini ba. Da kansu iyayen suka raba musu kwano. Gwaggo Mairo kadai ta kaiwa abincin ta sharesu.
Da Abbati ya dawo daga gaishe da 'yan uwa da ganin abokansa ta ajiye masa tuwon fuskarta dauke da murmushi. Wani guntun kakide da aka bata a gidan Sarkin Noma da take ta janjani yau duka ta zuba masa. A zatonta yadda Sani ya zauna cikin wahala da rashin abinci shi ma hakan ne.
"Ashe kakiden nan rabonka ne nake ta boyonsa sai ranakun daidai muke ci. Na san ka fimu bukata."
Kallon tuwon nan ya yi yaji gabadaya zuciyarsa tana tashi. Miyar a idonsa tsululu tayi sai mai a sama. Ya kile fiye da zato da tsammani. Abincin sayarwa ma ba na kowacce 'yar talla suke ci ba.
"Ci mana Abbati. Ko a baki ka ke jira na baka" ta ce tana 'yar dariya.
Kwanon ya ja gabansa ya saka hannu. Kadan kadan yake gutsira sai Mari ta tashi ta bashi wuri. Karshenta dadewar da suka yi basu hadu ba ce take saka shi kunyarta.
Tana tashi ya bi bayanta ya tabbatar ta bar harabar bangarensu sai ya dauko kwanon ya nufi garken awakinta. Dama tuwon ya yi da hannunsa tana kallo. Lokacin Inuwa ya aiko ta a bashi buta zai yi alwala a waje. Mamaki ne ya kamata yadda Abbati ya hade rai ya jagwalgwala tuwon ya juyewa awakin.
Ita bata ci ba. Bata bawa mahaifinsa da kannensa ba amma ya wulakanta shi haka. A jikin kyaure ta labe tana kallonsa har awakin suka cinye sannan ya ajiye kwanon a wurin wanke-wanke. Kwalla ta mayar da ta cika idanun ta taho kamar shigowarta kenan.
"Ba dai har ka gama ci daga fita ta ba?"
"Na cinye shi tas Baaba."
Da yake da akwai kuruciya a tare dashi bai yi lissafin tazarar lokacin da ta fita bai isa ace ya cinye ba.
Kada kai kawai tayi bata nuna masa ta ganshi ba amma daga ranar ta sanyawa duk motsinsa ido. Abinci kullum ci yake kamar magani. Da ya dan sami wanda zai ji kuzari sai ya tashi. Hankalinta fa ya tashi ta tafi wurin Mai maganin shawara ta karbo masa. Mutumin ba kudi yake karba ba sai dan abin sadaka. Haka tazo gida ta dinga tafasa masa yana sha tana yi masa sirace. Babu wani chanji a tare dashi amma haka ta daure kullum ba fashi sai anyi. Ana haka Jummai kanwarsu Inuwa dake aure a Karkarna wani kauyen Jigawan ne shi ma tazo ganin gida. Ta taho da 'yan yaranta guda uku su ga kakarsu Inna Mairo. Babban namiji da bai fi sa'an Sani ba sai kannensa mata biyu.
Ranar da ta kara wargaza farincikin Mari ta kama alhamis. Ita da Jummai ke gurfane gaban Mal. Sa'adu suna magiyar kar a mayar da Abbati Kano.
"Yaya tunda Mari bata so kuma ga abin da ya faru da Sani don Allah a hakura mana" cewar Jummai kamar za tayi kuka. Ita da Mari sun kasance aminai tun kuruciya.
Mari da take suruka ba zai iya zaginta ba amma Jummai sai da ta zubar da hawaye saboda kaifin maganganunsa gareta.
Suna can suna roka masa ingantacciyar rayuwa ashe shi kuma jarabar tsiyar da ya koyo ta kwana biyu tana addabarsa. Ya rasa da wa zai yi a gidan ba tare da an tona masa asiri ba.
Shigowarsa gida kenan daga wajen wasan gare-gare da suke yi da abokansa ya hango Hanne. Ita ce 'yar Jummai ta biyu. Ita kadai ce take kwaba kasa tana wasanta. Munzali ya bashi labarin ranar da ya yi da 'yar makotansu.
"Ba don munafukar Innayo dinnan ba da kullum sai na daukota munyi. Amma kawai ta shigo mana daki don gulma."
Bai manta yadda suka zauna suka zagi Innayo ba bayan Munzali ya ce masa matar uba ba uwa ba. Wannan karatun Asabe ne ya yi amfani dashi wurin sake batawa Abbati tarbiya. Bai taba raina amaryar babansa ba sai yanzu da yake jin da za ta shiga hurumin Mari zai rama mata.
"Hanne zo ki karbi adua" ya kirata yana fito da aduar da suka tsinto a hanyar gida.
"Bana sha."
"To zo muyi wasan doki. Sai na goyaki mu shiga dakin baya."
Dakin bayan kamar rumbu yake. Kayan abinci ne idan mazan gidan sun girbe amfanin gonarsu kowa nan yake ajiyewa.
Da sauri ta taso ta dane bayansa. Yana ta gudu da ita da wayo da wayo ya tafi dakin bayan.
('Ya 'yar uwa, ban ce ki dora zargi akan 'ya'yanki ba. Amma yana kyau idan suna wasa a kebantaccen wuri lokaci zuwa lokaci ki dinga lekensu a boye. Zamani ne muke ciki mara dadi. Kina iya kokarinki wani ko wata azzalumi makiyin Allah zai koya musu mummunar dabi'ar nan tun da kuruciya..kada ki raba kan 'ya'yanki saboda mugun zargi amma kuma kar ki yarda ki shantake kina musu kallon basu san komai ba Tunda uba zai iya yiwa 'yar cikinsa ciki ta haihu to ki kaddara KOMAI IS POSSIBLE. Allah Ya karemu daga sharrin yai da gobe.)
Daga wasan doki Abbati ya danne Hanne. Bata san me yake yi ba illa kashedin da yake ta nanata mata. Idan ta fada sai ya yanke mata baki.
Suna wannan yanayin hankalinsa ya yi gaba sai ga matar guda cikin kawunansa ta kawo kai. Sai da gabanta ya fadi da ganin halin da yaran suke ciki. Amma saboda bakin hali da kishin faccaloli bata yi musu magana ba. Shi kuma bai ganta ba. Lallabawa tayi ta koma ta kira kawayenta cikin matan gidan. Su hudu suka dawo suna kallonsu suna sallallami.
"Ai sai ku kirata tazo tagani. Tana can gaban Malam ana rokon kar ya koma ita da kawarta. Ashe 'ya'yan iska suka ajiye mana a gidan."
'Yar aiken Jummai ta kira
"Zo ki ga Hanne."
Yadda tayi maganar Mari ta fahimci babu lafiya. A w
urinta da na kowa ne kuma ko wane yanayi Hanne ke ciki ba sai mahaifiyarta ce kadai ya kamata ta gani ba. Idan abun taimakawa ne ta taimaka mata.
Kusan duka matan gidan ta gani a tagar dakin bayan. Jikinta sai ta hau rawa ko buhu ne ya fadowa Hannen. Da gudu ta tafi dakin kai tsaye Jummai na biye da ita. (Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Ya Allah kar Ka taba nuna mana 'ya'yanmu a cikin wannan yanayi. Ya Allah Ka tsare al'urarsu daga alfasha ta fin karfi ko ta ra'ayi. Amin).
Abbati ta gani dare-dare akan Hanne yana mu'amala da ita cikin kwarewa. Kunnuwan Mari suka toshe bata ma ji ihun da Jummai ta saka ba. Idanunta suka makance. Jininta ya hau duk da ba asibiti taje ba domin duniyar cak ta tsaya mata. Bata san da yadda aka yi ta isa garesu ba sai sautin maruka kawai da suke tashi.
Finciko Abbati tayi waje tana kai masa duka kamar an aikota. Magana take yi amma baka gane jumla ko daya saboda harshen ma ya harde. Hawaye kuwa ya sa ko ganin inda take kai dukan bata yi. Amma duk da haka soyayuar danta tana nan cikin zuciyarta domin ita din uwa ce mahaifiya gareshi!
BIYAR NA YATSUN HANNU.
Tun ana jin ihu da magiyarsa har muryar ta dauke sai nishi kawai yake fitarwa . Sai da ya kusa daina numfashi Mari ta barshi. Ita ma din gefe ta samu ta tsuguna tana nata kukan. A hankali ta daga kai ta saci kallonsa da ta daina jin nishin nasa. Duk tsiya duk lalacewa Abbati jininta ne, danta ne wanda take yiwa soyayyar da bata da kalmar kwatance.
"Dan iskan yaro. Wallahi bari Malam ya zo komawa zai yi inda ya fito don bai isa ya zo ya lalata mana 'ya'ya ba"
Muryar Deluwa ce ba wata ba. Tana fara magana sauran ma suka dinga tofa nasu ana ta kwashewa Abbati albarka. Jummai ta bar wurin tare da Hanne ta tafi dakin Inna Mairo. Abin da ya faru din ya girgiza Innar ta taso da kyar saboda ciwon kafa na girma ta taho bayan. Abbati ta gani a yashe kamar gawa ga matan gidan ana ta zage-zage. A can gefe kuwa Mari ce ta zuba masa ido. Lafiyarsa take son tabbatarwa amma tana tsoron nuna tausayinta gareshi a ce bata damu ba. Ajiyar zuciya ta sauke da taga Inna Mairo ta iso wurin.
Abbati ta duka ta tayar yana numfarfashi ta gallawa Mari harara. Fada ta soma yi mata cikin bacin rai.
"Kisan kai ki ka yi niyar yi ko me? Zo ki kama min shi a kaishi daki." Da sauri kuwa Mari ta taso.
"Inna da kanki?" Cewar daya daga cikinsu tana matsowa gabansu za ta daga shi.
"Ban son munafurcin banza da hofi. Kafin nazo da tana dukan nasa akwai wadda ta hana ne?"
Deluwa ta tabe baki "yo Inna me zai sa mu hana uwa yiwa danta hukunci?"
Ko ta kanta Inna Mairo bata bi ba ta nuna Abbati "Mari dauki danki muje dakina."
Soyayyar uwa akwai ban mamaki! Mari so take danta ya shiryu. Tana son fahimtar dashi munin laifinsa amma hukuncin tana yi ne ba don tana so ba. Uwaye su kan yiwa 'ya'yansu hukunci mai tsauri wani zubin har ya zarta laifinsu domin kada a ga gazawarsu. Sau tari suna daukar wannan matakin ne domin a zuciyarsu suna hangowa 'ya'yan ceto daga wadanda suke wurin. Abin da Inna Mairo ta hango kenan wanda su Deluwa basu gani ba. Ta san cewa babu horon da uwa za ta yiwa danta ba tare da ya yi mata ciwo fiye da dan a zuci ba. Sannan su ma 'ya'yan zukatansu sun fi nadama da jin kunya idan hukunci ya tafi tare da tausayawa ko da ba daga mai horar dasu ba.
Kunyar ganin Jummai a dakin Mari taji sai kawai ta sake shi don kada taga kamar bata damu da laifinsa ga Hanne ba.
"Jummai don Allah kiyi hakuri" ta ce muryarta na rawa.
"Ba komai fa Mari kar ki damu." Ta mayar mata amma ko ido ta kasa hadawa da ita. Ba laifin Mari bane ta sani amma 'yarta kuma fa? Ba don an gansu da wuri ba kila barnar da zai yi sai tafi haka.
Muryar Mal. Sa'adu suka ji a kofar dakin yana doka sallama.
"Ina yake tsinannen yaron nan?"
Inna Mairo ta zaga wurin girki da kanta za ta dora ruwan zafin gasa masa jiki. Bata ji zuwan Mal. Sa'adu ba. Shi kuwa don kada su bata masa lokaci sai ya sa kai cikin dakin ya janyo Abbati waje.
"Shegantakar da kake yi kenan Abbati? To Yasin ba dai a gidan nan ba. Daga yau idan kaga mace ma sai ka sauya hanya matsiyaci."
Kausasan kalmominsa sun yiwa Mari zafi. Bata ki a hukunta shi ba amma da wannan sigar ba. Kara kuntata kawai zuciyarta take yi da takaicin silar lalacewarsa. Kofar dakin ta fito tana gani ya jefawa manyan 'ya'yansa Abbati ko kula da rashin karfin jikinsa bai yi ba. Dukan da Mari tayi masa kadai ya jigata shi. Yaran kuwa kamar jira suke suka dinga tafkarsa da tsumagiyar darbejiya. Abbati sai gurnani yake a wahale don kukan ma yaki fita.
Zuciyar Mari ta dinga harbawa da tsoron kar shi ma yabi Sani. Da tafin hannunta ta toshe baki saboda kada sautin kukan da ya taho mata ya fito. Tana ji tana gani ake yiwa danta dukan-kawo-wuka. Tabbas ya yi laifi amma duk wurin aka rasa mai taimakonsa saboda ba nasu bane. Da abin ya yi yawa saboda dukansa suke babu digon tausayi tana gudun kar ayi masa lahani cikin kuka ta ce,
"Malam na hukunta shi. Yanzu na gama dukansa."
A harzuke ya mayar da dubansa gareta "ni kike fadawa haka? Ni za ki cewa kin hukunta shi?"
"Nufinta a dena dukar mata da. Ai idan baku yi da gaske ba ma ina tsammanin yana daf da komawa dan mace duk da ubansa yana raye." Cewar Deluwa don ta kara zuga shi.
Kafa daya daga cikin 'ya'yan nasa ya daga zai saukewa Abbati a ciki sai ga Inna Mairo ta dawo. Da karfinta ta ce "kwarankwatsa dubu idan kafarka ta same shi sai na tsinewa ubanka gashi nan" ta nuna Mal. Sa'adu "kuma duk ku bar min wuri taron marasa mutumci. Indai mugunta da bakin hali abin yi ne don Allah kar ku fasa." Ta juya ga amaryar Mari "ke kuma da hankali ya isheki da suna dukansa ke ya kamata ki agaje shi ki dauke shi."
Sum-sum matan suka fice aka bar Mari hannunta har kaikayi yake tana son juya Abbati taga yanayin da yake ciki amma ido ya hana. Mal. Sa'adu yana yiwa Jummai tambaya game da halin da Hanne ke ciki sai ga Inuwa a guje da fatanya a hannu.
A kan dansa ya sauke ido ya tafi da zafin nama zai taba shi Inna Mairo ta hana. Ta san zance ya kai gareshi ne yazo dukansa.
"Don Allah Inna ki barni na zane masa jiki gobe ma ya kara..."
Tsakin da Mal. Sa'adu ya buga ya janyo hankalinsa.
"Da raina da lafiyata kake tunanin ba zan hukunta shi ba har sai ka zo? Kodayake kaima gara kayi masa naka domin ya san girman laifinsa."
Ran Inna Mairo ya kai kololuwar baci da yadda Mal. Sa'adu yake nuna rashin mahimmancinta a wurin tana matsayin mahaifiyarsu.
"Ku kashe shi ku huta tunda ban isa ba."
Kamar ya yi kuka Inuwa ya ce "amma Inna har nawa Abbatin yake da za'a ce har ya san mace?"
Juyo masa da Abbati tayi ya ga yadda fuskarsa ke fitar da jini kuma ta fara kumbura sai jikinsa ya yi sanyi.
Zama suka yu jigum sai tashin sababin Mal. Sa'adu har Inna Mairo ta gasa masa jiki. A dakinta ya kwanta zazzabi ya rufe shi. Mari ko dakin bata shiga ba ta zauna a waje har lokacin bata bar hawaye ba. Ana la'asar duka mazan gidan suka hallara a bangaren Inna Mairo. Ita ta soma magana a matsayinta na babba a gidan.
"Kun ga illar wannan almajirancin da karfi da yaji ku ka kakabawa 'ya'yanku yinsa ko?"
"Gidan nan kowa ya san kin fi son matar Inuwa saboda ta dan zauna a birni. Banda haka Inna ba sai kin kushe lamarin addini ba don ki goyi bayanta."
Mal. Sa'adu ne ya yi wannan maganar da gatsali. Kannensa kansu sun yi mamaki duk da ba tun yau yake kokarin nuna ya fita matsayi a gidan ba tunda shi ne namiji.
Da yake mace ce mai saurin fahimta kuma kamar Mari ta jima abubuwa da dama na rayuwar bahaushe musamman na karkara yana damunta, sai kawai ta girgiza kai.
"Malam ni fa ba matar ubanka bace, haihuwarka nayi saboda haka ba zan yarda ka fada min bakar magana a fakaice ba."
Maganar ta dan dake shi sai dai nuna hakan zai iya sakawa kannensa su fara bijirewa umarninsa.
"Gaskiya ce kawai na fada miki. Tunda dai mune maza ki bari muyi magana mu shawarta yadda zamu bullowa lamarin nan."
Shiru tayi na wani dan lokaci sannan ta tashi jiki a sanyaye. Ta san haka suka tashi suna gani iyayensu mata basu da mahimmancin da ya wuce yi ko bari a idon mazajensu. Shi yasa idan sun girma suke raina uwayensu su kuma taka matansu. Sa'adu ya dade da rainata tun mahaifinsu yana da rai. Idan tayi magana ya ce jarumin namiji kenan. Kirjinta ke suya da bakincikin rayuwar da tana da yakinin idan an kokarta za'a iya wadda ta fita dadi. Za ta bari suyi shawararsu ko don kada sauran masu jin maganar tata cikin kannensa su ga suna sa'in'sa suma su bi sahu.
Bayan tafiyarta Inuwa ya yi tsalle ya dire cewa Abbati ya gama karatu a Kano. 'Yan uwansa kuma suka dage suma sai ya koma domin ba zai zauna ya lalata musu nasu yaran ba.
Tabe baki Mal. Sa'adu ya yi har suka gama gardamarsu sannan ya kwalawa Mari kira. Tana fitowa ya ce ta je ta taho da Abbati. Yaron ko tsayuwa akan kafafunsa ya kasa amma haka ta kawo shi ta zaunar.
A zuciyarsa yake jin haushin kowa musamman Mari da ta bari aka sake yi masa duka. Idan ita tayi bai ga dalilin da zai sa ta bari ayi masa dukan da ya kusa ajalinsa ba. Duk yadda zai yi ya bar Kirikasamma zai yi don yanzu ya fahimci bashi da masoyi sama da Munzali. Shi ne farkon wanda bai hada jini dashi ba amma ya damu da damuwarsa. Kamar daga sama kuwa yaji Mal. Sa'adu yana tambayarsa a ina ya koyi wannan dabi'a.
Bai yi wata-wata ba ya ce "Nan."
Inuwa ya zabura ya ce "Nan? Nan garin kake nufi?"
Kai ya gyada da kyar. Muryar Mari ya ji tana kuka a kusa dashi.
"Karya yake Malam. Da a garin nan ne da na dade da sani. Ka yiwa Allah da ManzonSa ka bar shi a gabana."
Basu san bata bar wurin ba sai yanzu. Mal. Sa'adu ya ce da Inuwa ya koreta daga wurin ko kuma shi ya tsame hannu daga abin da ya shafesu. Da rawar jiki Inuwa ya ce ta tafi.
Gani tayi shirunta babu abin da zai haifar sai karin cuta ga danta. Tana mikewa ta hau masifa tana zubar da hawaye.
"Babu inda zani. Haba! Da me kuke so naji ne? Wallahi Allah a Kano aka lalata yaron nan. Idan ya koma Allah kadai Ya san abin da zai zama kuma. Don Allah Malam ka barshi a gida mu saka masa ido."
Galala suka tsaya kallonta kafin Mal. Sa'adu ya yi gyaran murya bayan ya tashi tsaye fuskarsa a hade.
"Inuwa zabi yana gareka. Ko mutumcin gidan nan da addininka ko matarka amma Billahillazi yau dinnan sai ka zabi guda."
Ya girgiza matuka ya kalleta tana tsuma da mugun bacin rai. Ta gaji ta kai makura akan mulkin Hitilan da Mal. Sa'adu yake gwada musu a gidan.
"Mari ki bashi hakuri."
"Ba zan bayar ba! Idan da wanda ya cancanci a bashi hakuri to a bayana yake." Sai kuma muryarta ta karye " Haba Maigida? In rasa Sani wannan kuma ya dawo a haka sannan ka ce in bashi hakuri? To hakurin me?"
"Inuwa matarka bata da kunya."
"Ba dole danta ya yi iskanci ba tana da irin wannan halin."
"Dole ka rabata da 'ya'yanka."
Shawarwarin sauran 'yan uwansa kenan da basu son abin da zai batawa Mal. Sa'adu rai har ya yi fushi dasu. Shi kadai ke sakawa da hanawa a gidan.
Kallonsa suka dinga yi ana jiran jin me zai ce.
"Ki je gida na sake ki saki daya."
Kirjinta ne ya hau dukan uku-uku amma a haka ta kama Abbati za ta tafi bangarensu daukar gyale.
"Sakar min da."
Kallo mai tsayawa a rai ta yiwa Abbati. Kallon da zai yi ta tayar masa da tsigar jiki saboda tarin ma'anoninsa har a shekaru masu zuwa. Za ta iya dafa Izu sittin cewa karya yake yi a Kano ya koyo abinsa. Tun yanzu saboda wasu dalilai ya zabi komawa can akan zama da ita. Duk wani fadi tashinta yau ya katse shi a dalilin haduwa da Munzali.
Murmushin biyan bukata Mal. Sa'adu ya yi. Yau dai ga karshen rashin kunyar Mari. Ba a taba surukar da take turjiya akan umarninsa ba sai ita. Idan ta zauna sauran ma zasu koyi bijire masa. Yanzu kuwa ko ta wane hali ba zai taba bari Inuwa ya dawo da ita ba.
Kafin Magariba ta fita zuwa gidan wani kawunta a garin Maigatari. Inna Mairo har kuka tayi ta umarci Inuwa ya mayar da ita amma yaki saboda maganar Mal. Sa'adu tafi ta kowa.
Bayan sati biyu su Abbati suka koma Kano. Inuwa ya sani ba sai an fada masa ba cewa rabuwa da Mari kuskure ne sai dai kuma ya yarda cewa hana almajiranci sabawa addini ne. Wanda baya son addini kuwa ba abokin rayuwa bane. Shi da 'yan uwansa suka dunguma Karkarna gidan Jummai. Mal. Sa'adu ya sake baiwa mijinta hakuri akan abin da ya faru.
"Kuma matsawar ina raye yana kawo girma za'a daura musu aure. Kai Inuwa ka rubuta ka ajiye. Abbati ba shi da mata sai Hanne."
"Wai Ladidi tace ki dafa mata shinkafa da miya, sannan ki tura a sanar da ita da wuri don bata so ya huce."
Kalaman Jiddo kenan ga Nasima tana fada mata sakon mahaifiyarta. Sakuwarta ce sai dai ba ciki daya suka fito ba. Jiddo 'ya ce ga yayar Ladidi daga garinsu Soba. Dan kudin da ake ganin ta fara kamawa tun bayan auren Nasima da Tahir shi ne aka turota cin arziki. A haka duk wani aikin wahala ita take yi musu a gidan.
Kallon wulakancin da ta saba ta yiwa Jiddo, tana jin kamar ta sa hannu ta mare ta saboda takaicin da take kwasa na Ladidi a 'yan kwanakin nan. Ta tsiro da wata sabuwar dabi'a ta cewa anan gidan za ta dinga cin abincin rana. Da ace da hali ma ba dan Tahir ya kan dawo da wuri ba to na dare da na safe ma nan za ta so ta dinga ci. Ita dai ta zauna a saka mata kaset a bidiyo tana kallo tana kwasar gara, ta ce a miko mata wannan a miko mata wancan. Cikin bacin rai Nasiman tace mata
"ki gayamata cewa nima fita zanyi idan na dafa zan aiko mata dashi gida."
Nan Jiddo ta juya ta fice. Ba jimawa ta dawo, tace ladidi tace a bar mata makulli idan ta gama zata tafi da makullin gida idan yaso Nasima in ta dawo sai ta biya can gidan ta karba. Takaici ya sake kama Nasima, tayi kwafa ta tashi ta shiga kitchen ta dauko wata tukunya ta mikawa kanwar tata.
"Gashi nan ki kai mata, ki ce jiya nayi amma na manta ban sa a firij ba shine tayi tsami. Ta saka kanwa in ta gyara miyar, ta dafa shinkafar da zataci."
Tana gama fadar haka ta dangwarar mata da miyar ta koma ciki abinta. Shiru shiru da Jiddo taga bata fito ba ta zari tukunyar miyan ta kama hanyar gida.
Ba dai haka taso ba amma haka nan ta karbi tukunyar rai a bace. Taci burin zuwa gidan Nasiman, gashi akwai wuta taje tai kallo tana cin abincinta a karkashin fanka. Da ta kai tukunya kitchen ta bude taga nama zuqu zuqu hankalinta gaba daya ya tashi, nan da nan ta jiqa kanwa ta gyare miya ta dafa shinkafa ta zauna ta ci. Saboda bakin hali ma bata rage wa kowa cikin yaran nata ba. Ta cinye abincin ta tas, naman ma bata bar musu ba.
Sai dare tukunna cikinta ya soma ciwo, yanata kulululun kuka, kafin asuba tayi gudawa ya kai sau goma. Garin Allah na wayewa, ta sake tura Jiddo a fadawa Nasima bata da lafiya azo a kaita asibiti.
Zazzafan bugun da ake yiwa gate din ne ya tashi Tahir a firgice daga bacci ya fita kofar gida. A nan ya tarar da kanwar Nasima suna magana da Mallam Ado maigadi. Bayan ta gaishe shi ta sanar da shi abun da yake faruwa. Ko a jikinsa don bai ma yarda ba. Ya dai ce Allah Ya bata lafiya tare da juyawa ya koma cikin gida. A zatonsa irin shirin da suka saba masa ne don tatsar kudi a jikinshi. Tuni ya riga ya dawo daga rakiyar su, auren ma ya fice masa rai don dai ba yadda zaiyi ya rabu da ita ne.
Da kunnuwan sa ya ji wani lokacin da Ladidi take cewa Nasiman akawo mata Mardiya yaye don su samu hanyar cin kudin gurinsa. Shi kuwa daga jin haka kafin su farga washegari ya dauke ta ya kaita wurin Yakumbo. Gashi har yanzu kusan satin ta biyu gurin bai ma karbo ta ba. Lokacin haihuwarta sun tatse shi son rai. Shi da ya saba mu'amala da mata a waje ya san duk wadannan karairayin na cin kudi. Sai dai kawai ya kyalesu suka zata wankarsa suke. Daga lokacin ne ya dinkewa Nasima da ta dawo.
"To sai ki tashi bakin naki ne. Daya daga cikin kannenki ni ba rike sunayensu nake ba."
Bai ko damu da fada mata me ya faru ba kamar bai ji sakon ba haka ya ja bargo ya koma baccin sa.
Da haushin kalamansa na rashin rike sunayen kannenta gami da tashinta daga bacci ta fita. Fitar tata ke da wuya sai gata ta dawo ta dan tattaba shi don ya tashi,
"Wai Ladidi ce ba lafiya"
"Tun a wajen na ce Allah ya bata lfy." Ya sake juyawa ya cigaba da baccinsa.
Ta danyi kwafa a ranta ta fita da niyyar shirin tafiya. Bayan tayi wanka ta shirya ne ta shigo ta same shi yadda ta barshi yana baccinsa hankali kwance. Bata ji dadin yadda ya nuna halin ko in kula ba amma dama itama ba daraja bane da uwar a idonta.
"Amma dai Diya yanzu fa nace maka Ladidi ba lafiya baka ce komai ba."
"To me kikeso na ce miki?" Ya ce da alamun kosawa.
"Kudin zuwa asibiti zaka bani mana."
"Bani dasu, dan Allah ki barni na samu bacci me dadi kar ki dame ni." Ya juya mata baya yana tunanin ko idan ya tashi ya je Zaria wurin Khadija.
Fuuuu ta fice tare da bugo masa kofa ta tafi gidan su. Halin da ta iske Ladidi ya wuce yadda tayi tsammani. Haka suka kwasa sukayi a asibiti ba yadda take. Allah dai ya taimaka akwai yan kudade hannun Nasiman dasu ta biya aka basu gado tare da saka mata ruwa.
Suna zaune asibiti har la'asar. Ladidi jiki ya dan lafa ta samu ta lallaba ta tashi zaune.
"Wash, Nasima me zamu samu ne na dan saka a ciki? Me kuka dafo ne a dan tarfa min naci."
Shekrke ta kalli uwar tare da sakin wata yar dariya.
"Amma dai wallahi Ladidi a gaishe ki. Ace kin kwana kina cikin wannan yanayi amma daga dan samun salama sai ki hau neman abinci."
Marairaice fuska tayi "To yar nan ya za ayi? Kinga ko fa magungunan nan da ake narka ma ba za suyi aiki ba in babu abinci. Ni a bar zancen nan dan Allah ku zuba min na ci. Allah ma yasa dai ba mai da yaji ba ne. Nafi son harkar miya kun san akwai gina jiki."
Rai a bace Nasima ta yarfe hannuwa "To ni dai babu wani abinci anan. Tun safe da muka kawo ki ko tashi ban daga nan ba balle wani zancen abinci."
Tuni fuskan Ladidi ya rikide tai kicin kicin ta hade rai.
"Yanzu kina nufin haka zan wuni na kwana ban ci abinci ba fisabilillahi. In zawon da na kwan inayi be kar ni ba ai sai yunwa tayi sanadi na."
Nasima ta juya ta kalli Jiddo a wulakance.
"To kinji dai sai ki tashi kije ki dafo ki kawo ko."
Ba musu Jiddo ta ta mike har zata fita ta juyo ta nema kudin mota, Nasima ta ciro a wulakance ta dangwara mata a hannu tana cewa "saura in kinje ki dade".
Jiddo bata ce komi ba ta fice abunta tana fatan Allah dai ya kai damo ga harawa Ya bata ikon cikar burinta dan tsaf sai ta rama duk wannan wulakanci da ake mata.
Tana sauka daga bus a bakin layinsu maimakon ta wuce gida sai ta tsaya kofar gidan Nasima. Ta gaishe da Malam Ado tace masa Nasima ce ta aikota. Bsi hanata shiga ba tunda ya san kanwar matar gida ce.
Ganin motar Tahir a farfajiyar gidan ba karami dadi yayi mata ba har da sakin dan murmushinta.
Yadda duk aka kai aka kawo aka yi auren Nasima da Tahir din ai babu abun da basu sani ba. In dai kura na maganin zawo to shakka babu yau zan wa kaina magani ta fada a ranta tare da cusa kai cikin gidan
A falo ta iske Tahir ta gaishe shi a ladabce tare da fada masa Nasima ce ta aiko ta yin girkin asibiti. Bai ce mata komai ba sai tunanin irin wannan karfin hali nasu, dan me ba za suyi a nasu gidan ba sai a nashi. Hanyar kitchen ya nuna mata ya kau da kai ya cigaba da abun da yakeyi.
Kafin ta wuce sai ta cire mayafi ta aje kan kujera, ta wani hau yarfe gumi daga su wuya da kirjinta. Jujjuya jiki ta dinga yi na daukar hankali. Tahir kamar baisan tana gun ba, ita ko bata fasa ba har sai da ta tabbatar ya waigo ya kallo inda take nan ta juya masa baya ta wuce kitchen din.
Bata jima da shiga ba ta saki wata kara har sai da Tahir ya dan firgita ya taho da azama zuwa kitchen din dan ganin me ya faru. Tsalle ya sameta tana yi tana direwa ita nan a dole hannun ta ya kone.
Sai ya tuna da lokacin da Nasima ta fara rungumar sa a cikin gidan da irin wannan sigar. Sabanin Nasima, ita Jiddo bata nufo shi ba. Yayi dan murmushi a ransa tare da yi mata sannu ya juya zai fice kawai ta saka kuka. Hakan ya sashi dawowa.
"Naga hannun" ya umarceta.
Kamar jira take ta mika masa. Yasa hannu ya riko hannun nata ba kunya ba tsoron Allah. Daman yaya lafiyar kura balle yaga abin da rai ya biya. Ya hau hura mata yana kallon cikin idonta, ita kuma tana wani sussune kai.
"Ko muje daki na shafa miki magani ne."
Ta sunkuyar da kanta tana matse ido wasu hawayen na zuba "A'a ka barshi ma ba zafi."
"To kukan na meye?" Ya tambaya hannunsa a bayanta yana shafawa. Suna hada ido ya kanne mata nasa yana murmushin 'yan duniya.
"Babu komai" ta ce baki na rawa.
Dakinsa ya ja ta tana binsa kamar bata sani ba tana kuka. Rarrashinta ya yi ya sake tambayar dalilin kukan.
"Hannuna zugi yake yi min da wuya na iya girkin. Idan na koma haka kuma Nasima da Laraba ba kyaleni zasu yi ba."
"Kar ki damu. Muje na saya musu sai ki kai."
"To ai za ta yi min fada idan taji kai ka saya." Ta ce a shageabe.
"Zan yi mata bayani."
Godiya ta dinga yi masa har suka bar gidan. Da dai bai yi niyyar zuwa asibitin ba amma tunda yana son samun kan Jiddo sai ya bi a sannu. Da suka isa asibitin shi ya dauko ledojin abincin tana biye dashi a baya. Ta bude masa kofar kafin ya shigo Nasima ta soma zaginta.
"Uban me ya tsayar dake daga zuwa girki bayan babu nisa."
Hawaye ta sake tarawa a idon tana rawar murya ta bata hakuri. Tahir kuma yaji ransa ya baci. Ita da Ladidi suna ganinsa suka fara murna.
Duk da Nasima taga abinci ya kawo amma sai da ta tambayi Jiddo ina wanda ta dafa.
"Konewa nayi Nasima. Shi ne Abban Mardiya ya ce na barshi zai siyo."
Mantawa tayi da yadda take ladabin kura a gabansa ta hau zazzaga mata bala'i.
"Wani salon karuwancin ne wannan ko me? Gidana na tura ki? Me ki ka je yi?"
Ai sai Jiddo ta fashe da kuka
"Naji kin ce naje gida nayi girki. Na zata gidanki ki ke nufi."
Sake bude baki tayi Tahir ya mike a fusace sai tayi shiru tana taune lebe saboda bacin rai. Ta fi Jiddo iya bariki. Idan ta ce za ta shiga huruminta sai ta kwashi kashinta a hannu.
Daga ranar ta ja mata kunne akan kada ta sake zuwa gidanta ko da wasa. Ladidi ta sake matsa mata. Ba don tana morarta da aiki ba da ta korata inda ta fito. Jiddo ta amsa da to. Aka kwashi kwanaki Tahir baya ganinta. Sai rannan bayan ta gama fakonsa ya hangota a gefen gidansa tana share hawaye. Da sauri ya taka burki ya fita wurinta.
"Ke lafiya?" Bai rike sunanta ba.
Fashewa tayi kuka ta rike ciki tana matsawa.
"Don Allah ka taimakeni. Cikina, cikina."
"Muje ciki wurin Nasima. Ko kuma shiga mota bari na kira ta mu kai ki asibiti."
Hannunsa ta kamo da sauri tana zubewa a kasa "ni dai la taimaka min ka mayar dani garinmu." Kallon rashin fahimta ya yi mata ta ce masa tun ranar da ya kaita asibiti da abinci Nasima ta hanata shiga gidanta. A can gidansu kuma Ladidi ta matsanta mata. Abinci ma sai da kyar ake bata. Yanzu haka ma ciwon na yunwa ne.
Da yake idanunsa sun rufe sai yaga kamar da gaske ta fada. Ransa ya mugun baci ya shiga da ita gidan. Nasima bata nan bai san inda taje ba. Khadija kuma ta zo hutu da yara saboda bikin kanwarta bai san suna ciki ba. Akan idon Suhaib ya shigar da ita dakinsa. Ya koma ya hada mata abincin da Nasima ta ajiye masa ya kai mata. Ta ci ta koshi sannan ya ce ta taso zai kaita hotel ta kwana gobe sai ya kaita gidansu.
Khadija ta gama yiwa Sauda wanka kenan Suhaib ya fada mata Abbansu ya dawo.
"Amma Mami naga ya shiga dakinsa da bakuwa maimakon ta zauna a falo ta jira ki fito."
Gabanta taji ya fadi. Ba abin mamaki bane daga halayyar Tahir amma tayi zaton ya yi hankalin da zai daina kawo tarkacensa gidan aurensa. Yadda fuskarta ta sauya a idon Suhaib ya gane akwai matsala. Da ta ce ya zauna ya kular mata da Sauda tana zuwa sai yabi bayanta ba tare da ta sani ba.
Batun zuwa hotel kadai taji a kofar dakin ta kwankwasa. Ya zata Nasima ce saboda haka kai tsaye ya bude. Ganin Khadija a tsaye sai yaji kunya ta lullube shi.
"Ko don lafiyarka idan ma baka tsoron Allah Ya kamata ka yiwa kanka fada."
Da sauri ya ce "ba fa abin da kike zato bane. Taimakonta kawai nayi."
"Hmmm, taimako a uwar daka? Ina jiye maka ranar nadama domin wallahi hakkin duka matan da ka ke lalata dasu ba zai barka ba."
Haushi yaji tunda bai yi din ba kuma take gaya masa magana. Kafin ya ce wani abu Nasima da ta dawo ta shigo wurin. Bata san me yake faruwa ba ta taho da gadara da tsiwarta.
"Duk jarabar mutum dai yau girkina ne tunda ban san zaki zo ba. Sai ki koma sai gobe."
"Ke miji ya dama Nasima. Idan kin shiga kya yi maganar girki da ta ciki ba ni ba."
Ai kamar ta watsawa Tahir wuta ya ji takaicin abin da ta ce. Hannu yasa ya janyota za ta bar wurin ya kwasheta da mari.
"Wato ban dameki ba? To idan kin isa ki saki kanki."
Hannuwa yaji daidai kugunsa aka dage aka hankada shi sai da ya daki kofar dakin ya fadi. Yana tashi yaga Suhaib yana huci kamar maciji.
"Ni ka ture Suhaib?" Ya ce da tsantsar mamaki.
"Me yasa ka mari Mami?" Yaron ya bashi amsa kai tsaye. Bakinsa Khadija ta doke da sauri tana cewa ya bawa babansa hakuri.
"Khadija halayyar da ki ke koya musu kenan?"
Za ta yi magana suka ji sautin ihun Jiddo ya fada dakin yayin da Khadija taja hannun Suhaib. Amma kunnuwansa sun jiyo masa kalmar 'karuwa' da Nasima ke kiran Jiddo.
Lokacin da Khadija ta ce suyi magana da ta ciki ta fada dakin da sauri. Jiddo dama tana jin muryarta ta kwanta akan gado ta kwaye zani har cinya. Bata ma gane ko wace ce ba saboda azabar kishi sai da ta finciko wuyanta.
"Jiddo?" Ta ce da rawar baki "ni za ki yiwa haka? Mijin nawa zaki nema saboda ke 'karuwa ce'."
"Nasima kiyi hakuri babu abin da muka yi." Ta ce tana kukan munafurci. Idanunta sun rufe ta shiga dukanta ba ji ba gani.
Da kyar Tahir ya kwaceta ya kuma tsinkawa Nasiman mari.
"Ki je gida sai na nemeki. Zan zo na karbi Mardiya don ba za ta zauna a gidanku na marasa tarbiyya ba."
Hauka ne kadai Nasima bata yi ba. Tana ta kokarin sake kamo Jiddo ya shiga tsakani. Da kuka ta bar gidan da alwashin sai taga bayan Jiddo. Ita kuma tana ganin fitarta ta soma kukan rayuwarta ta kare domin ba ita ba hatta mahaifiyarta sai Ladidi ta ciwa mutumci.
"Zan baki matsayin da basu isa su tabaki ba."
Ya kuwa aikata abin da ya ce! Sati hudu a tsakani sai ga Jiddo ta dawo gidan a matsayin amarya. Dakinsa ya zama nata.
Nasima da Ladidi suka haukace wurin bin bokaye da malaman tsibbu. Zumuncinsu da 'yan uwa da yawa ya lalace. Da kyar da sudin goshi bayan wata biyar ya yarda ta dawo gidansa. Kazamin kishi suke bugawa ita da Jiddo kamar zasu ga hanjin juna.
Tun daga kan Mardiya bata sake haihuwa ba. Jiddo ta zubar da ciki yafi a kirga a kauye har ya taba mahaifarta. Ita ko haihuwar bata yi ba. Khadija ba ta shiga sabgarsu daga su har mijin da suke rigima a kansa. Tana gama karatu kamfanin da tayi bautar kasa suka riketa. Albashinta ta shiga tarawa har ya isa sayen fili. A hankali ta soma gina kayanta saboda ta matsu ta raba 'ya'yanta da kazamin gida irin na mahaifinsu. Duk da haka tana kokari sosai wurin shanye abubuwa da rufawa Tahir asiri don kada su san halinsa. Kusan babban burinta a rayuwa bai wuce nesanta su daga sanin halinsa da kwatanta aikatawa ba.
Sai dai tunda kudi suka sake zama a hannunsa rashin mutumcinsa ga duka matan ma ya karu. Ita da yake ragawa darajar 'ya'ya ma ya daina. Nasima da Jiddo dama basu da wanban darajar. Gida ne tambadadde wanda mai shi ya lalata da hannunsa. Abu daya suka tsira dashi wato makauniyar soyayyarsa ga 'ya'yansa. Su biyar dinnan bashi da na biyunsu. Don ma Suhaib ba ya sakin jiki dashi ko kadan.
Tun ranar da ya mari Khadija ya dauki karan tsana ya dorawa mahaifinsa. Da sannu yana kara wayo ya gane halinsa ciki da bai. Sai yake jin inama wani ne can Abbansa ba wannan manemin matan ba. Khadijan da yake yi dominta kuma kullum fada take masa akan ya bi mahaifinsa don neman rabauta ranar lahira. Sai yake ganin kamar cin kashin da ake mata baya damunta. Yana shekara goma sha biyar ya fara zukar tabar wiwi a boye saboda yawan damuwa da halin da iyayensa ke ciki. Lilu kuma ya zama mugun fitinanne mai yawan dauko magana. Duk kaffa-kaffa da Khadija take yi da rayuwar 'ya'yanta saboda mahaifinsu ba zai hana kaddara ta cimmusu ba wata rana.
***
SHIDA RANAKUN AIKI.
Kwance tashi ba wuya a wurin Allah, yaran Innayo duk sun girma amma har kawo yau sana'o'in da takeyi babu wanda ta daina.
Girma ya soma kama ta, ga wahalhalun ayyukan da takeyi domin ta rufawa kanta da ahalinta asiri. Sannu a hankali lafiyar idanunta ya soma tabuwa sakamakon yawan zama gaba murhun da takeyi. Amma haka nan take daurewa don samar wa yaranta ingattacciyar rayuwa. A kullum burinta
Yaranta manyan uku duk sunyi aure Uwani, Maimuna da Salima, saura Zara da Hasiya a gabanta. A yadda rayuwa take gara musu tsugunne bata karewa Innayo ba.
Uwani ta gama School of Nursing abinta har ma ta kama aiki a Abdullahi Wase Specialist Hospital Kano wanda ake yiwa lakabi da asibitin Nasarawa. Tana samun kudi sosai sai dai anyi rashin sa'a. Halinta yana neman zarta na mahaifinta. Mugun mako da kyashi gareta. Mijinta yana da rufin asiri daidai gwargwado. Lab Technician ne a asibitin nasu. Bai taba dora mata nauyin da ba nata ba na kula da gida ko 'ya'yansu guda uku. Tana da wadatar da za iya taimakawa mahaifiyarta musamman ta harkar lafiyarta amma kullum cikin kiran babu take. Don ma kada Innayo ta dinga tambayarta kudi sai wata ya raba ta kan leko gidan. Tana zama bata da zance sai na bukatunta wadanda kudin hannunta ba sa su isa ta biya ba.
Ita kuma Maimuna lokacin da Allah ya kawo mijin rimi-rimi ya amince za ta cigaba da karatun da take a Legal. Sai dai anayin aure ko wata biyu ba a rufa ba zance ya juye. Innayo tace indai don kudin ne zata cigaba da daukan nauyin 'yarta. Yace yaji ya amince dama kudin ne baya so ya biya. To kuma sai mahaifiyar sa ta ce bata yarda ba ko dai tayi zaman aure ko ta fita taje tayi karatun ta.
Nan kuwa yace to sai dai ra ajiye karatun. Maimuna shaukin soyayya na dawainiya da ita a lokacin tuni ta amince da bukatarsa. Innayo taji ciwon wannan abun amma ba yadda zatayi haka ta hakura. Haihuwa biyu duk ta tsufa ta lalace. Babu cima mai kyau ga tashin hankalin uwar miji da talauci. A hankali nauyinta ya sake komawa wuyan Innayo kuma bata yi mata komai da kyashi domin 'yarta ce.
Salima kuwa watarana suna zaune kwatsam Alh Rabiu yazo wai yayi mata miji kuma aure nan da nan zaayi ba bata lokaci. Nan fa innayo da Alh Rabiu suka hau suka duro ta dage tana so yar ta tayi karatu ko don gudun abin da ya sami Maimuna amma yaki yarda sam. Karshe dai haka wannan ma ta hakura akai auren. Ashe basu sani ba auren biyan bashi yayi mata ga mijin mashayi ne na bugawa a jarida. Yau duka gobe tsangwama haka dai itama Salima rayuwar ta kare babu wani cigaba.
Banda lalurar ido tsabar damuwa da halin da 'ya'yanta suke ciki sai hawan jini ya sarketa. Innayo bata fasa komai ba. Tashi karfe hudu na asuba har jikinta ya saba. Kwata-kwata bata san hutu ba. Zara da Hasiya da suka rage take take fatan ko za a samu wani abu na cigaba a rayuwarsu.
To matsalar Zara karya ce sama da kasa take dawainiya da ita. A dole ita sai tayi rayuwar da za'a ce ita 'yar wani ce, ita dai kar a rainata. Hasiya kuwa ba sawa ba fitarwa. Yadda bata son rigima haka take kin halayyar Uwani da Zara. Maimuna da Salima kuwa tausayi suke bata.
Zara ta gama sakandire da wata shida aka kawo kudin aurenta. Lokacin Hasiya tana aji shida ita kuma ita ma ta kusa gamawa. Saurayin nata da ne ga guda cikin mashahuran 'yan kasuwar da Kano take ji dasu a Singa. Alh. Rabi'u kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha. Yadda yake jindadi da mijin A'i haka yake fata daga mijin Zara. Asabe kuwa hadiyar zuciya ne kawai bata yi ba. Hankalinta in ya yi dubu ya tashi wurin nemarwa Ummakati miji na wuce sa'a. An sanya biki wata biyu masu zuwa.
Innayo ce zaune a daki da Uwani da Hasiya ga kayan amfanin gida irin su kuka da daddawa da ta siyo tana rabawa gida uku. Uwani dake kashingide akan gadonta ta dago kai.
"Ki dan kara min kukar Innayo kin san Usman bai ki kullum na kada masa ba."
Murmushi Innayo tayi ta debi cokali bibbiyu a sauran kaso biyun ta kara a daya. A zahiri ita ba da Uwani take rabon ba. Ta san tana da kudin saye. Nata ne da Maimuna da Salima. Ba yadda ta iya ta hakura da natan. 'Yan kudaden hannunta duk sun kare wurin siyayyar auren Zara. Wadannan din ma cikin nata ne ta dibar musu.
Dan gyaran murya tayi tana juyayin samun biyan bukata a wurin Uwanin.
"Uhmmn. Dama abin da yasa nace ki zo saboda maganar Zara ne."
Tashi tayi zaune tana hade fuska
"Wallahi indai harkar kudi ce sai dai kiyi hakuri. Na fada miki adashi nake yi kuma sai nan da wata hudu zan dauka."
"Yanzu ba za ki iya rokon arziki a baki daukar watan nan ba? Kinga bikin ya matso ko bamu sayi kujeru ba."
Tashi Uwani tayi. Da ta san dalilin kiran ma da ta kirkiri dalilin kin zuwa.
"Ki nema a wurin Baba ko a rokesu a daga bikin. Ni wallahi yanzu dubu ashirin ma ba zance za a samu a jikina ba. Gobe nake shirin ranto talatin a asibiti. Sai na rab
a muku ke da Baba kuyi hidimar bikin."
Muryar Innayo kamar za ta yi kuka ta ce "iya gudunwamarki kenan a bikin kanwarki? Uwani idan baki tausaya min ba waye kuma zai min? Sauran 'yan uwanki duka abin a tausayawa ne a gidajen mazajensu amma ban taba cewa ki kawo wani abu na basu ba. Na zata kina da hankalin duba yanayin da suke ciki ki ..."
Yanzu taji magana. Ta rasa dalilin da yasa Innayo ta kawo ido ta saka akan albashinta. Lokacin da take hana idanunta bacci tana kwana karatu me Maimunan da Saliman suke yi? Basu tsaya sun gina rayuwarsu ba kowace tayi aure. Sai kuma ake tunanin ita za ta dauki dawainiyarsu saboda bata san zafin nema ba. Muryarta a sama ta soma magana.
"To ni dai ba zan dauki nauyin kowacce katuwa ba wallahi. Dubu talatin kuma ita kadai zan iya fitarwa saboda nima bani dashi. In don nace ki kara min kuka ne to ki bar abarki. Haba! Ba damar nazo gidan nan kin dinga tasowa da bukatun kudi..."
Tasss...taji saukar gigitaccen mari. Da kyar ta bude idonta da ya kanne saboda zafin shigar marin tana neman wanda ya yi mata wannan aikin. Hasiya da Innayo ne a gabanta. Kalaman autar tasu ne ya nuna mata hannun waye ya sauka a kuncinta.
"Idan su Yaya A'i sun wulakanta rikon da Innayo tayi musu basa dubanta yanzu ke kina da wata uwar ne bayan ita?" Cewar Hasiya lokaci guda tana fashewa da kuka. Muryarta ta dinga yin sama-sama saboda taki yin shiru.
"Kullum ki ka zo gidannan kin dinga kiran babu kenan saboda kada ki taimakawa uwar da ta biya miki kudin makaranta. To Allah Ya hadaki da babun nan da kike kira don girman..."
"Hasiya kama gabanki. Fita kada ranki ya baci. A gidan wa ki ka koyi rashin kunya haka?" Innayo ta furta da kwalla a idonta.
Kwallar ta sake tunzara zuciyar Hasiya. Rainin wayon yayarta ta ya kaita makura. Idan bata amayar da ranta ba tana jin zuciyarta sai ta buga.
"Innayo ki barni don Allah. Dubi dakinki don Allah." Ta nuna kowacce kusurwa da hannunta "Dakin da Yaya Uwani ta mayar kemis a gidanta fanka biyu ce da ta bango da ta tsaye. Ke kuwa fankar tsayen ma da kyar take juyawa. Nima tashi nayi na ganta a gidan nan."
Bakincikin marin da Hasiya tayi mata yasa ta kasa cewa komai. Duk abin da ta fada gaske ne to amma gaskiya tana tsoron talauci. Idan tana bada kudin sai su koma matsayin da ta tashi a ciki. Innayo ce ta kama hannun Hasiya ta fita da ita daga dakin. Tana juyowa taga Uwani ta saba jakarta tana gyara mayafi.
"Uwani."
Ta kira ta a sanyaye. Banda kudin bikin Zara da take nema harda na zuwa asibiti. Kwanakin nan sam bata jindadin jikinta daurewa kawai take yi. Dan abin da take dashi idan ta taba a zuwa asibiti dame za ta aurar da Zara? Danginta suna kauye a haka ta fi da yawa rufin asiri. Shi kuwa Alh. Rabi'u bakin hali ya raba shi da nasa sai jefi-jefi.
"Innayo sai naci mutumcin Hasiya. Dani take zancen. Kar ma ki bani hakuri don wallahi ba zan hakura ba."
"Zan yi mata fada. Yanzu dai ki taimaka min da ko dubu biyu ne in je asibiti gobe. Bani da kudi a hannu duk nayi sayayya dasu."
'Innayo ba dai naci ba' Uwani ta fada a zuciyarta. A ganinta duk abubuwan da take yi sun isa su sa tayi fushi ta daina tambayarta komai. Ba dole su A'i suka gujeta ba. Kila su ma roko ta damesu dashi. Dubu daya da dari biyar ta bata tasa kai ta fita.
"Nima ba kudin gareni ba."
Hasiya tayi kukan bakinciki a ranar. Bata ga me Innayo tayi da ya cancanci wannan wulakancin daga 'yar cikinta ba.
Washegari ta rakata asibiti. Hawan jininta ne ya tashi tana daf da samun stroke idan bata huta ba. Sannan likita ya bada shawarar ta rage damuwa daga ranta. Da ta fadawa su Maimuna babu abin da suka iya zuwa dashi dubiya sai sannu da fatar baki. Innayo din ce ma ta ce ta basu kullin kayan da ta ajiye musu. Zara kuwa bata zama ana ta shirin biki da kawayenta 'yan karya.
Da daddare ne ma da ta dawo daga rabon kati ta saka Innayo a gaba da kuka.
"Wancan gadon na soro ne gadon da ki ka saya? Dangin Unais raina ni zasu yi. Kuma har yau ban ga kujerun ba. Idan auren ba zai yiwu ba kawai zan ce masa na fasa."
Tana jin motsin Hasiya tayi shiru. Tunda Uwani ta dawo ta fadawa Alh. Rabi'u marin da tayi mata itama take shakkarta. Shi kuwa har uwar daka ya kirata ya zazzageta tunda Uwani ta bashi dubu shabiyar tayi mutumci a idonsa.
Da maganganun Zara Innayo ta kwana a ranta. Gari na wayewa taje gidan A'i. Tangamemen gida ne na zamani. A wani karamin falo aka ajiyeta har A'in ta sakko bayan kusan minti arba'in.
"Innayo kece a gidan namu? Nima ina son zuwa kawo gudunmawata ta bikin Zara." Juyawa tayi ta koma sama. Bata dade ba ta dawo da leda mai baka da yalo ta bata.
Godiya tayi tun kafin ta bude sannan ta fadi abin da ya kawota.
"Don Allah rance nake so A'i. Kujeru zan sayawa kanwar taki da sauran kayayyakin da basu samu ba."
Kallon tausayi ta bita dashi kamar gaske "banda abinki Innayo kiyi mata komai daidai karfinki mana. Kodayake naji ance dan masu kudi ne. Zara da rawar kai maimakon ta kawo tsaranta shi ne ta dauko wanda yafi karfinta."
Daurewa tayi bata ce komai ba tunda nema take. Wai A'i ce take yi mata haka? Lallai duniya baka shaidar da ko da naka ne bare na wani.
Ta sami bashin tayi ta murna ta karba ta tafi gandun albasa inda kafintoci ke kware basirarsu. Ta sayi kujeru aka biyota dasu hae gida.
Zara na gani ta tabe baki alamun basu yi mata ba. Innayo sai ta shige daki kawai ta fashe da kuka.
"Allah kar kasa 'ya'yana su maye gurbin mahaifinsu wurin wulakantani. Idan nayi kuskuren tarbiyarsu Allah Ka shirya min su. Ya Allah na yafe musu. Da wanda suka yi da wanda zasu yi a gaba."
(Haka rayuwa ta kan zo wa bayin Allah. Sai mu wahala akan wani abu da tunanin samun jindadi a tare dashi nan gaba. Idan lokacin girbar dadin ya zo lokuta da dama sai mutum ya kare da shan mamaki. Babu abin da Innayo bata yiwa 'ya'yanta ba na kyautatawa amma har yanzu bata ga wani abin buga kirji game da cigaban da ta jima tana yi musu fata. Duk da su din jininta ne to amma kar mu manta jinin Alh. Rabi'u ne. Basu tashi sun ga mahaifiyarsu tana da kima ba. Wannan zai iya rage mata daraja a idanunsu. A wahale suka ganta kuma dabi'ar dan Adam ce gudun wahala da talauci. Sai mai hankali, hangen nesa, tuna baya da tsoron Allah ne yake jajircewa wurin sakawa iyaye musamman uwa da alkhairi.)
Anyi bikin Zara ba yadda take so ba amma dai ta bar gidan kamar yadda ta jima tana buri. Sai jifa jifa take zuwa gidan nasu saboda tana kunyar a ce Innayo mahaifiyarta ce. Ga talauci ga rashin wayewa. Mijinta ko a jikinsa. Bata nuna masa tana ganin girman mahaifiyarta ba shi ma bai ga dalilin girmamata ba.
Abu na karshe da ya karasa kashewa Innayo jiki ta fitar da rai daga samun saukin rayuwa shi ne auren Hasiya. Wata uku bayan bikin Zara aka aiko musu da mummunan labari. A'i tayi hatsari ta rasu. Shi kuma babban danta da suke tare ya sami rauni a kansa.
Wannan labari ya gigita Innayo ya kusa zarar da Laraba mahaifiyar A'in. An sha koke-koke an hakura. Ranar da aka yi sadakar uku Innayo ta sayar da filin da shi kadai ya rage mata kadara ta biya bashin da A'i take binta na kudin kujerun Zara. Mijinta Hon. Habu ya ce ya yafe, idan ma adadinsu ya shiga gadon 'ya'yansu zai biya a madadinta. Kafin ta isa gida Laraba har ta je ta ce ta bata kudin. Ba musu ta dauko ta bata.
Kafin ayi bakwai ashe Alh. Rabi'u yana can yana kulle-kullen yadda zai cigaba da ci daga jikin Hon. Habu.
"Ga kanwarta Hasiya ba sai ta maye gurbinta ba. 'Ya'yanka suna bukatar uwa da za ta kula dasu tsakani da Allah."
Da mahaifiyarsa ya yi shawara ta ce ya amince. Dama ta kula a 'ya'yan Innayo din Hasiya ta fita daban.
Basu san hawa ba basu san sauka ba sai sadaki aka miko musu ranar da A'i tayi arba'in. Da uwa da 'ya aka rasa mai rarrashin juna. Asabe ta dinga habaici da zage-zage wai wa ya san me suka kulla har haka ta faru? Sai da Allah Ya kawowa Ummakati miji mai rufin asiri bayan shekara guda sannan ta daina zaginsu.
Hasiya ta tare da bakincikin auren dole da katse mata karatu. Mahaifiyarsu bata da mataimaki a gidan ga yawan rashin lafiya. Kaddara ta mayar da ita uwar 'ya'ya hudu da kananun shekaru.
Bata taba zaton zama zai hadata inuwa guda da 'ya'yan da suka raina mahaifiyarta ba. Sai gashi Abbas, Ummi, Murja da 'yar karamarsu Hajara (Ayaah) sun koma karkashin iko da kulawarta. A wannan lokacin ne kuma Innayo ta tashi tsaye wurin son ganin ta kashe wannan aure. A idanunta Hasiya ta maye gurbinta ne tamkar tarihi yana neman maimaita kansa.
Asabe kuma ta canja sheka daga yawon makota ta zamar da mijin Ummakati injin tatsa. Munzali ya kawo karfi ya yi kudi amma iyakarta dashi ta ce danta ne a baki ko ya bata idan ya yi niyya.
2018
A yayin da uwa ta haifi danta bata san gobensa ba ko anjima ba amma tana gina kyakkyawan buri aka rayuwarsa. Idan so samu ne ya fi kowa nutsuwa, kyaun hali, kudi da kyaun halitta. Ita dai ace nata ya yi zarra akan duk wani abu da zuciya take muradin samu. Burika ba kasafai suke cika ba. Da dadi ko ba dadi koda da nakudar haihuwa ce kadai dole a jinjinawa gudunmawar uwa akan danta.
Tabbataccen abu ne cewa kaddara ita ce kashin bayan rayuwar kowanne dan Adam. Akwai mai dadi da mara dadi wanda sau tari tafiyar rayuwa daga ranar haihuwa ke kai mutum ga tasa. Waye yake tare da mutum a wadannan lokutan sama da UWA? Kokarinta wurin bada kyakkyawar tarbiya kadai ba shi zai kare mutum daga afkawa ga kaddarar cizon yatsa ba. Addu'a da taimakon Allah su ne jigo.
Wata za ta kokarta amma akasin mafarkinta ne zai faru.
Wata za ta shantake amma duk da haka kyakkyawan alkalami ya rinjayi mummuna akan zuri'arta.
Wata tayi mai kyau taga mai kyau.
Wata tayi mara kyau taga mara kyau.
A karshe dai ba a canjawa tuwo suna.
Mari uwa ce
Innayo uwa ce
Khadija uwa ce
Asabe da Nasima ma dukkanninsu uwaye ne.
Shekarar ta kama dubu biyu da sha takwas. An sha gwagwarmaya an yi fama. Iyaye, gari (society), abokai da ma ainihin halayyar da aka haifi mutum da ita sun kai manya da kananan taurarinmu ga matsayin da suke a yau.
BAKWAI RANAKUN MAKO.
LAGOS
2018
Mukullai da cheque bibbiyu mutumin ya ajiye akan hadadden teburin gilas din dake gabansa yana kallonsu. Dukkaninsu kyawawa ne ga cikar halitta da kwarewa a gayu. Haduwarsu ta hudu kenan amma bai taba ganinsu da sutura daban daban ba. Hatta safa wannan iri daya suke sakawa.
"Ga tukwicinku nan. Kun shigo da kafar dama domin na kwana biyu ban ji sun yabawa wani kamarku ba. Kudin kuma ku chanja wardrobe saboda akwai baki wata mai zuwa."
Abbati da Munzali suka yi murmushi kowannensu ya dauki check da mukullin da yafi kusa dashi suka fita tare kamar 'yan biyu. Wandon jikinsu baki ne 3-quarter. Suka dora yellow din (hooded vest) riga mai karamin hannu hade da hula. Kafarsu bakaken original nike slippers ne irin na shakatawa. Agogo da askin kansu komai iri daya. Kyawawan matasa ne da suke ji da duk wani abu da cikakken matashi zai yi tinkaho dashi a wannan zamani. Abbati yana da shekara talatin da biyar yayin da Munzali yake da talatin da hudu.
Suna zuwa farfajiyar gidan shakatawar suka ga an bude motocin da suka wuce a lullube lokacin shigarsu. Lexus ne RX 2015 biege iri daya guda biyu. Wani irin ihun murna suka saka tare da rungume juna suna tsalle.
"Mutumin, yau akwai shagali fa" cewar Munzali yana yiwa Abbati kallon bani da na biyunka.
"Ai dole. Ba don maganar nadin sarautar nan ba da munje Dubai." Abbati ya mayar masa yana kallon cheque din. Miliyan goma goma ne a jiki.
"Kai dai kawai ka ce za ka je ganin uwargida Hanne."
Wawan duka Abbati ya kai masa da muguwar harara.
"Uwar Hanne zan gani ba Hanne ba."
Munzali ya kwashe da dariyar jindadi. Baya hada kowa da Abbatinsa. Yana kuma kishinsa kamar yadda kowane masoyi ke kishin abin da yake so. Iya tsahon rayuwarsa wani mahaluki bai taba nuna masa soyayya kamar Abbati ba. Shi dai ya san cewa yana da uwa da uba. Suna raye har yau amma cikinsu babu wanda zai ce ya san shi sani na hakika. Haihuwarsa suka yi suka bar wa duniya tarbiyarsa.
Yadda Abbati yake ga Munzali shi ma haka ya dauke shi. Bambancinsu bai wuce Baaba Mari da matsayinta bai tawaya a zuciyar danta ba. Munzali tamkar tsani yake ko kuma madogara a gareshi. A lokacin da iyaye suka watso shi hannun duniya babu wanda ya kama shi ya rungume sai Munzali. Shi ne gatansa wanda bai taba bari ya yi kewar iyayensa ba tunda suka hadu. Ya ciyar dashi kuma ya hana rayuwarsa tagayyara kamar ta sauran almajirai. Indai halacci yana sa dan Adam ya riki wani ya so shi kamar kansa to hakika bai ga ta inda Munzalinsa ya cancanci juya baya ba.
Sau tari iyaye maza suna son kasancewa cikin rayuwar 'ya'yansu amma sai neman abincin da zasu ci ya dauke uba ya nesantasu dashi. Irin wannan uba za ka same shi mai yawan dokin lokutan zuwa gida domin ya saurari kuruciya, shirme da zallar soyayyarsu gareshi. Akwai kuma kishiyoyinsu irin su Alh. Rabi'u. Shi a gida daya suke kwana amma rabonsa da bada kudin sayawa dan cikinsa panadol ma ya manta. Bai san komai ba sai cikinsa da biyan bukatarsa.
Idan aka sami uba irinsa ko wanda dole ta raba shi da gida da wahala ace uwa bata nan. Ita ke kokarin maye gurbin uban kuma ta taka tata rawar. Asabe bata cikin wannan sahun! Burinta daya ne. Me za ta samu a jikin 'ya'yan da tayi wata tara tana dakonsu a cikinta. Indai za ta ci ta koshi ta saka mai kyau to komai nafila ne.
Munzali kamar sauran 'ya'yanmu yana bukatar kulawar majibintansa. Ayi tattalinsa a shagwaba shi. Ayi masa fada idan ya kuskure. A taka masa burki idan yana neman tsallake layin da dabi'ar dan Adam da addini suka shata masa. Bai sami wadannan ba sai a wurin Abbati. Tun kafin su gama gane rayuwa Abbati yake son sa da zuciya daya. Ba zai tuna lokaci na karshe da Asabe ta san bashi da lafiya ba musamman idan ciwonsa na namoniya ya tashi. Amma tun kafin ya daina kwana a gida Abbati ke jinyarsa. Wani lokaci da ya tashi sai da ya kwana biyu bata leka dakinsu ba inda yake kwana da kaninsa. A rana ta uku ne ma da lalitarta ta kone kurmus babu 'yan canji yaji muryarta tana yiwa Innayo bala'i.
"An sako min da a gaba saboda hassada da bakinciki. 'Yar fitar nan da yake yana roro min abin arziki a wurin mutanensa kina neman saka masa hannu."
Dariyar da Innayo tayi kafin ta bata amsa sai da ta bata haushi.
"Asabe kenan. Yau kuma rigimar dani kike ji? Da nice ke gyale zan dauka na bazama nemansa ba zaman karyar son 'ya'ya amma ban san halin da suke ciki ba."
Gyalen kuwa ta janyo akan kyauren dakinta tana mai cigaba da kumfar baka da borin kunya ta kare da cewa,
"Dama fitar zanyi." Kugu ta kama tana karkada hannu daya kamar 'yan mata a wurin ga
a "Kuma ki gaggauta fadawa bokanki ya yi karya don bashi da rabo akan ahalina ehe."
Har ta kusa rijiyar dake daf da kofar gidan taja tunga ta tsaya. Tuno wani abin karin haushin tayi ta kuwa kalli Innayo ta kwashe da dariya.
"Su 'ya'yan so din wai uwar me suka tsinanawa wahalalliya? Ai in fada miki dadin haihuwa bai wuce ki haifa ki mora ba. Amma ka haifa kuma a more kuruciya da lafiyarka a gujeka wai....uhumm bari nayi gaba."
Daskarewa Innayo tayi tana jiyo sautin Asabe tana rangada ahayye nanaye da salon wulakanci. Zafafan hawaye ta goge ta duka ta cigaba da tatar gero.
"Wata rana zan huta. Balle ma indai sun huta basu yi irin rayuwata ba ni bani da sauran damuwa." Ta fadi da dan karfi tana baiwa kanta kwarin gwiwar cigaba da aikin gabanta.
Munzali yana dakinsu ya gama jin zantukansu. Bai jidadin kalaman Asabe ga Innayo ba. A ransa yake jin inama ita ta haife shi. Ya tabbata da zai ga gata mara misaltuwa kamar su Hasiya.
Sai da yaji tsakar gidan shiru ya lallaba ya fita. Murmushi ya karade ramammiyar fuskarsa ta kwana biyu da ya yi tozali da Abbati ya rakube a dakalin gidan. Shi ma yana ganinsa ya taso da saurinsa.
"Ya jikin? Ga abinci na samo maka. Akwai sauran kudi in siyo maka lemon kwalba? Ko kunun zaki? Kafi son lamurje ko?"
Dariya ce ta subucewa Munzali ganin Abbati duk ya rude. Kwana biyu da yake ciwon sai Asabe ta fita yake fitowa. A wurinsa yake wuni yana jinyarsa. Don kokari har kemis yaje ya siyo magungunan mura don a zatonsa mura ce da zazzabi ke damun Munzalin.
Wannan kadan daga irin abubuwan da suka kara masa kaunar Abbati kenan. Kulawa yake so kuma babu ta inda Abbatin ya gaza nuna masa ita. Abbati has always been there. Babu mai yi masa fada ko gyara masa wani abu sai shi. Tasgaron da ya mamayi wannan kyakkyawar alaka ba komai bane illa alfashar luwadi. Saboda sakar masa ragamar rayuwar da iyayensa suka yi da kananun shekara daga Asabe har baban nasa babu wanda yake gani da mutumci har ya girma. Sai dai ya kawo kudi su karba babu bincike ko damuwa. Tunda ya ce kasuwanci yake magana ta kare.
Yunwa, bala'i ce wadda mutum zai iya komai domin kawar da ita idan ba ya kai zuciya nesa ba. Munzali ne ya mikowa Abbati hannun taimako a lokacin da take neman kassara shi. Halinsa na tsoro da rashin son rigima sauran daliban suke dogara dashi suna cutar dashi. Shi ma Munzali da baya makarantar ya tsaya masa. Sai da ta kai hatta manyansu suna shakkar taba shi saboda fadan Munzali. Duk kulawa da soyayyar Mari gare shi bai hana shi jin zafin barinsa da suka yi zuwa bara ba ita da mahaifin shi. A lokacin da ta so ya zauna a gida bayan rasuwar Sani ya riga ya saba da abin da suke yi. Amma ba shi ne makasudin kin zamansa ba. Bai ga yadda zai iya rayuwa babu Munzali a cikinta ba.
Shekaru suna gaba yana dan yin karatun addini sama-sama. Bai jima ba ya gane muni da girman abin da suke yi. Lokacin da ya kai shekara ashirin abin ya dame shi matuka. Shazali yana kaisu wurin manyan mutane ana amfani dasu a basu kudi sosai. Tuni Shazalin ya bar makarantar ya zama kawalin almajirai mai gidan kansa.
Wannan sana'a tasu ta dami zuciyar Abbati. Ya yi nufin ya fadawa Munzali su daina su nemi sana'a ko ta wankin mota ce. Kullum abin yana ransa amma ya rasa yadda zai fito masa da maganar. Tsoronsa kada yaji haushi ya nemi rabuwa dashi.
Wata rana yana zaune jiran isowar Munzali su je su sami Shazali tunani ya dame shi. Bai ji zuwan Munzalin ba sai da ya taba masa kafada.
"Allah Yasa ban barka jira ba. Matar nan (Asabe) ce wai na ranta mata dubu biyu."
"Ka bata ko?" Abbati ya tambaye shi yana tashi tsaye.
"Kudin da muka samo a gidan nan ne fa na shekaranjiya ta gani ta saka min ido. Ni kuma na riga nayi amfani dasu."
Idanu Abbati ya zaro. Dubu biyar biyar aka basu shi ko dari biyar bai cinye ba. Zai tambaye shi me ya yi da kudin ya miko masa leda. Atamfa ce guda daya da lesuka biyu.
Kallon tuhuma Abbati ya yi masa
"Na meye wannan?"
"Kayan sallar da ka ce zaka sayawa Baaba dasu Atine (kannen Abbatin)"
Zuciyarsa yaji tayi nauyi ya kasa magana. Abu daya ya sani. Munzali yana matukar kaunarsa. Ko kyamar almajirai bai taba yi masa ba.
"Kai da ka ce baka da kudi duk ka kashe naka?"
Murmushi Munzali ya yi. Shi ba maraya ba amma yana da wanda yafi uwa da uba a zuciyarsa saboda sakacinsu.
"Ka fini bukata kai da zaka je gida gobe. Na hannunka sai kayi kudin mota da wanda zaka bawa Baaba ta rike. Kafin ka dawo kullum zan dinga fita in tara mana."
Abbati yaje gida da tsaraba. Baaba Mari tana gidan kawunta a Maigatari. Ta kasa gaba ta kasa baya sai tunani. Duk sanda yazo hutu yaje ganinta sai ta tuna masa kada ya kusanci zina. Kar ya manta abin da ya faru shekarun baya. Idan 'yan matan sun zo su ma maganar kenan. A wahale suke rayuwa ana gasa su a gaban mahaifinsu. Da Abbati ya fara girma ne idan yazo ake daga musu kafa tunda da 'yan canjinsa a hannu.
Ya je gaishe ta wannan karon ma ya bata kayan ta tsatstsare shi da ido.
"Sana'ar me kake yi ne?"
"Jiran shago nake hadawa da karatun" Ya amsa mata kai tsaye "Wannan ma ubangidana ne ya baki." Ya mayar da hannunsa da ya riko kudin da yake niyar bata ya dunkule.
"A kula dai. Banda daukar kayan mutane. Banda ha'inci ko cuta."
"To Baaba."
Kwanansa biyar a garin ya koma Kirikasamma. Da isarsa gida da Gwaggonsu Deluwa ya fara cin karo a zaure. Guda ta saki tana ganinsa ta fara habaicin da ta saba wanda ya saka shi dakata karfi da yaji.
"Ango manya, na Hanne ka sha kamhi. Da Malan har iya cewa a bika Maigatarin ai...hummm, su Mari idan aka ga d'a sai ayi bulunbukwi a manta da an tsani almajiranci. Ledar da ka tafi da ita can ka barota kenan?"
Sauran surutan nata ba shigarsa suke ba. Kalmar 'na Hanne ka sha kamhi' ke kai wa da komowa a kwanyarsa. Me hakan yake nufi? Bai furta tambayar ba ya shige ciki da sauri. Kafin ya kai bangarensu tuni gudar Deluwa ta sanar da Mal. Sa'adu dawowarsa. Yana ajiye jaka dan aike na fada masa sakon kira. Gabansa ne ya fadi. Bai manta ba! Ta ina zai taba manta dalilin mutuwar auren Baaba Mari?
"Wa ka fadawa za ka je Maigatari?" Cewar Mal. Sa'adu fuska a daure bayan Abbati ya amsa kiran nasa.
A dakile ya bashi amsa da cewa "Babu kowa." A ganinsa baya neman izinin kowa musamman na wan mahaifinsa kafin yaje wurin mahaifiyarsa.
"To ba zan dauki raini ba. Sai kazo ko kwana biyu baka iyawa a gidan ubanka amma ka iya tafiya dangin dangiro ka kai musu dan abin da ka tara. Ita kuma ko kunya babu ta karbe bayan ta gama aibatamu da karatun da aka tura ka."
"Baaba ce Dangin dangiro din? Baaba Marin da ta haifeni?"
Yadda ya fadi maganar da bacin rai muraran a idanunsa sai yasa Mal. Sa'adu yin lakwas. Tabarmar kunya ya nade da hauka ya sako bakunan kannensa cikin maganar yana cewa su taya shi gani Mari ta zugo danta ya raina shi. Da kyar aka bashi hakuri sai da Baba Inuwa ya zazzagi Abbati a gabansa.
Baki Mal. Sa'adu ya turo gaba shi a dole ransa ya baci ya ce "sai ka shirya gobe ka je kaga amaryarka. Da baka dawo ba munje an daura aurenka da Hanne jiya. Ai baka manta alkawarin da muka yiwa shi uban nata ba hekarun baya."
Dif Abbati yaji kamar an sara masa guduma a ka. Aure?! Shi kuwa me zai yi da mace yanzu? Macen ma wadda rabon da ya sanyata a ido tun tana shekara hudu. Tunaninsa ya tsaya a inda ya auno shekarunta na yanzu. Shadaya shi ne har an aurar da ita kamar zai gudu.
Lokacin da mallam Saidu yace masa sai bayan shekara biyu zata tare bai damu ba. Sai kuma wani tunani ya darsu a zuciyarsa wanda yasa shi sakin guntun murmushi. Ko ba komai ya sami hanyar da zai fadawa Munzali aibun abin da suke aikatawa tunda dalilin bari ya samu. Abu ne da babu ko sabanin fahimtar malamai game da haramcinsa saboda haka bari ya zama wajibi.
Washe gari suka shirya tare da dan Mal. Sa'adu don zuwa ganin Hanne. Haka ta fito tana ta sussune kai wai ita nan amarya a gaban angonta, bakin nan ya sha jan baki ga fuska da dige digen jagira. Yarinya karama amma wai ta san shi mijinta ne, abin ma dariya ya bashi.
Bayan ya koma da yan kwanaki kadan ya shirya dawo Kano da farinciki zai ga Munzali dan yi masa fada da fatan kubutar dashi shi ma amma nan ya tarar da mummunan labari. An kama Munzali yana police station.
Sanadin rufe shin ba komai bane kamar yadda ya ji daga bakin wani dan makarantarsu da ya san abotarsu illa sumamen 'yan kwaya da aka kawo unguwar. Hankalin Abbati in ya yi dubu ya tashi. Munzali ko taba baya sha. Shan kayan maye bai kasance cikin dabi'unsu ba.
Jin kwanansa hudu a can ya da
a jefa shi cikin tararrabin halin da yake ciki yanzu. Bai yi kasa a gwiwa ba ya nufi gidansu. Ya dai san ba a maraba dashi domin Asabe ta gargade shi da rabar danta tunda ta gane almajiri ne. So yake yaje ya tabbatar ba a sake shi ba sai ya nemi station din da yake.
Ya dade yana sallama kafin yaji wata murya ta amsa a fusace. Da azamarsa ya shiga soron gidan ya tsaya turus sakamakon maganganun dake tashi a tsakar gidan.
Muryar da ta amsa sallamar shi ya gane ta Alh. Rabi'u ce saboda hango shi da yake yi a tsaye yana sababi.
" Dan iskan yaro kai, ni zai zubarwa da mutunci a unguwar nan? Ashe wai a wani kango aka same shi da talatainin dare. Kuma jama'a sun yi ittifaki akan yawan ganinsa a wurin kamar kangon ubansa."
'Shazali yake jira' Abbati ya ce a zuci. Babu abin da ke kaisu kangon nan yanzu sai jiran zuwan Shazali ya kaisu wurin mutanensa.
"To ni dai ka kawo kudin sai naje nayi belinsa" Asabe ta ce a sakalce. Ta riga ta gama bincike dakin Munzali tas babu kudi. Da ace ta samu dama rabonta za ta dauka sai ta fito dashi. Ta rasa uwar me yake boyo a dakin da ya kori kaninsa ma daga ciki.
"Nawa ne kudin?" Cewar Alh. Rabi'u a fusace kamar an ce ya bada ransa.
"Dubu ishirin da biyar ne. Ka bada ishirin sai na cike sauran."
Sake bata rai ya yi cike da fushi sai kuma ya fashe da wata irin dariya. Kudi irin wannan indai ba kodarsa take so ya sayar ba a ina zai samu.
"Kisan kai ya yi da zan biya talatin da biyar? To babu! Ya zauna su koya masa tarbiyar da ki ka kasa koya masa. Aikin banza. Baki da aiki sai yawon makota kina kwadayi. Ke dai kin shiga uku. Ko kishin yadda Innayo take tsaye kan nata 'ya'yan ba kya yi."
Habawa! Ran Asabe ya fi nasa baci saboda hadata da Innayo da ya yi akan kudi. Hannuwa ta tafa ta rike kugu tana sauke nata ruwan bala'in.
"Aikin 'bur in ji tusa. Kai dai anyi lusarin namiji. Ka haifi 'ya'yan ka bar mata da wahalar rayuwarsu. Kuma 'ya'yan Innayo din akwai wata ta dukan kirji a kai ne? Ba gara nawa ba akalla ko banza yana bani kudi."
Kanta ya yi kamar zai kai mata duka "ni kike fadawa wannan maganar?"
"An fada din lusari ko karya nayi?"
"To Yasin ba zan bada ko kwabo ba."
Hannu daya ta saka ta rufe bakinta tana masa ihu
"Wohhhhh, anji kunya. Lusari. Dama me zaka iya fitarwa bayan kayi gadon bakin hali."
Shi dai bai tanka ba tunda ya sabule ba zai bayar da kudin ba. Dakinsa ya shige ita kuma ta yi rantsuwar sai dai a barshi a kulle don bata da kadarar sayarwa akan dan da dama ba wani tausayinta yake ba. Mayafi ta dauko ta sanar da sauran yaranta wadanda a kunnuwansu aka gama bala'in zata je gidan Ummakati. A lokacin auren duka duka bai yi shekara ba. Hasiya ce ma take neman shekara ta biyu a nata gidan.
Innayo kuwa tun safe da take ganin take taken rigimar kudin belin ta fita. Uwani da Zara ko ba a hada da sauran kannen A'i ba zasu iya hada kudin belin dan uwansu. To amma ta san fakewa zasu yi da rashin halin Asabe su ki taimakawa. Wannan kenan.
Yau idanun Abbati sun gane masa abin da yasa Munzali baya kaunar iyayensa. Gabadaya son kai ya musu katutu babu mai cikakkiyar damuwa dashi. Kudin belin ne ma ya dame shi. Dubu ashirin da biyar da yawa. Bai je station din ba ya tafi gidan Shazali. Cikin sa'a ya same shi. Ko gaisawa basu yi ba ya ce,
"Rance nake nema don Allah na dubu ashirin da biyar."
Shazali ya kanne ido "babu sai dai akwai manya da suka shigo gari. Kayi sa a domin kuwa harda mataimakin wani gwamna cikinsu. Idan zaka iya aikin na tabbata nan da gobe ka tara dari ma ko sama da haka."
Bashi da zabin da ya wuce karbar wannan tayin. Munzali ne fa. A wuni da daren ranar sai da ya ziyarci mutum biyar. Kudi kuwa don ma sun san ba wayayye bane amma duk da haka dubu dari biyar ya saka a gabansa yana kallo. Jikinsa har bari ya dinga yi saboda kudaden sun bashi tsoro. Haka ya hau titi zuciyarsa na fat-fat da fargaba. Gani yake kowa ya kalle shi zai gano adadin kudaden.
Shazali ne ya fada masa wane station ne yaje da kudin belinsa a hannu. Sergent din da yake wurin ya fadawa sunan wanda yazo fitarwa.
"Kawo dubu goma saboda da daddare aka gan shi. Da da rana ne sai mu karbi biyar."
A haka shi Sergent din mugunta ya yi masa. Shi kuma muryar Asabe ce ta dawo masa. Kenan karya tayi da masifar da ta hau danta. Da gaske Munzali bashi da kowa sai shi. Wani irin tausayinsa ya sake mamayarsa.
Kwalla ya dinga zubarwa da aka turo keyar Munzalin. Ya yi dukun dukun ga dingishi yana yi.
"Dama na san zaka zo Abbati. Na san wallahi ba za ka barni a nan ba. Nagode..."
Rungume shi Abbati ya yi suka fashe da kuka. Sergent ya tabe baki yana tunanin shakuwa ce ta 'yan uwa.
Abbati~Munzali ya yi masa gata tun bai san me ake kira gatan ba. Ba zai taba iya barinsa ba bayan ya san shi kadai ne tsaye a rayuwarsa.
Munzali~Abbati ne kadai ya taba bashi daraja ta dan Adam. Shi kadai yake kaunarsa da zuciya daya ba don wani abu ba. Iyayensa basu damu da kowa ba sai kansu.
Fita suka yi Abbati ya tallafi nauyinsa. Asibiti suka fara zuwa ya biya kudin gado don ya ce a kwantar dashi ya huta. Wani karamin private ne da suka gani a hanya. A nan aka gyara targaden aka saka masa ruwa. Abinci mai rai da lafiya suka ci sannan bacci ya dauke Munzalin. Sai da safe Abbati ya nuna masa kudin da ya samo.
"Me ya kamata muyi dasu?" Abbati ya tambayi Munzali.
Munzali ba amsa. Bakincikin iyayensa ke damunsa. A gefe guda yana taya amininsa farincikin samun abin da zai iya raba shi da talauci. Ya jima yana tunani sai jin muryar Abbati ya yi.
"To ga naka nan. Kowa ya dauki dari biyu. Wannan kuma.." ya nuna chanjin darin da ya taba yana musu hidima ciki "sai mu dinga cin abinci da sauran bukatu."
"Kudinka ne Abbati. Ka dai bani na abincin ka san cikina babu juriya" ya kare da dariya.
Sun yi ta kai ruwa rana akan Munzali da yaki daukar kudin. Shi yana ganin Abbati ya fishi bukata tunda yana da iyaye a kauye.
Da dai ya tabbatar Munzali bazai dauki kudin ba duk abun da ya ce, kawai sai ya dauki jakar ya fice. Kai tsaye gidan Shazali ya nufa, ya ci sa a kuwa ya same shi. Nan ya shaida masa yazo neman alfarma gunsa dan Allah ya sama masa gidan haya wadda yake mara tsada sosai. Daki biyu da bandaki ko da daya ne. Shi bai ma yi tunanin kitchen ba ko wani yadda za a ci abinci shi dai gidan yake so a sama musu ko da ma daki daya ne kuma yana so ya zama nea da gidan unguwar da aka sansu.
Wani murmushin gefen baki Shazali ya saki
" dan gari, ashe ka gane abun da nake ta so ku fahimta tuntuni" nan ya amshe kudin ya kuma shaida masa in Allah ya yarda nan da sati daya gida ya samu.
Bai ma yi tunanin zai cutar shi ba ko raba daya biyu haka ya dunkule duka kudin Naira dubu dari hudu cus ya mika masa yayi gaba bayan yayi masa godia sosai.
Da ya koma asibiti Munzali yayi ta tambayarsa ina kudin, me yayi dasu? Ya ce masa ba komai.
Fita ya yi ya koma wurin likitan ya nemi alfarmar lallai a bar Munzali ya kara ko sati daya ne a asibitin dan yana so ya samu hutu sosai.
Shima likita dai yaga kudi, abinka da private hospital iya kudinka iya shagalinka. Muddin zasu biya to fa shi babu damuwa. Qka bar Munzali ana ta sa mishi ruwa lokaci zuwa lokaci, yana samun kulawa mai kyau jikin sa yana kara kwari.
Bayan sati daya kuwa ya koma gidan Shazali, da kansa ya dauke shi a babur dinsa ya kai shi rijiyar zaki wurin gidan da ya sama musu din dan ya gani, a lokacin babu gidaje sosai a wurin. Gida ne ba laifi dan har da dan gate dinsa.
Gidan dubu dari aka kama haya, ya biya dillalai da sauransu de komai ya kama dubu dari dari da arbain sai canjin sa dubu dari biyu da sittin ya mika masa duka.
Ya ce "ga canjin ka ni bazan dauki komai a ciki ba. Ku rike wataran zai muku amfani. Aiki kuma duk randa kuke son ku cigaba da samun kudi to kun san inda zaku sameni."
Ya damka masa mukulli da takardun da akayi cike cike (tenancy agreement) yace gobe kazo ka sameni zamuje kaima ka sa hannu a gaban maigidan a karkare komai da komai.
Farinciki a gurin Abbati a wannan lokacin ma bazai misaltu ba. Ya koma asibitin, ya sanar da Munzali halin da aka ciki. Shi kanshi mamaki ya ishe shi. Yanzu gida ma Abbati ya kama musu kawai don saboda yana jiye masa komawa gaban iyayen shi tunda da idon sa ya gani cewa ba kaunarsa sukeyi ba.
A cikin sati guda suka tarkata suka koma can. Shi dai Munzali ya koma gida Asabe, har ta fara murna tana fadin ashe har an fito da kai, tana neman ta fara mai zancen ko za a samu kudi a wurinsa ko wani abu, yace mata ya samu aiki ne, an basu gida a Rijiyar Zaki da shi da abokin aikin sa, kasuwanci sukeyi zasu dinga tafiya Abuja da Lagos.
Farinciki ya isheta tana ta murna hadi da yadawa Innayo habaici ita uwar mai shi. Danta ya samu aiki zai dinga shiga cikin manyan mutane.
Munzali bai wani jima ba ya tattara yan komatsan sa ya fice ko tunanin ta tasa kaninsa ya bi ya gano inda ya koma bata yi ba. Sannan bata damu da mahaifinsa ya san halin da ake ciki ba.
Shi ko Abbati daman ba abin da ya cewa Malamin makarantar su, kawai shafawa akayi aka neme shi aka rasa. Ya san yanda zaiyi da iyayensa duk ranar da ya koma gida.
A kwana a tashi ba wuya a wajen Allah. Shekaru hudu da soma rayuwarsu su kadai haramtaccen arzikinsu ya bunkasa. Da fari Abbati ya so su bar mu'amala da Shazali amma abu yaci tura. Sun riga sun saba da wannan masifa sannan rashin kudi a hannunsu ba abu bane da zasu jure. Musamman ma shi Abbati da su Mal Sa'adu suka taso a gaba da bani-bani. Lokacin Inna Mairo ta rasu. Deluwa ta zige Jummai mahaifiyar Hanne cewa kudi ne dashi amma Mari kadai yake bawa. Jummai da kullum abin da ya yiwa 'yarta a shekarun baya yake dasa mata jin haushinsa sai ta hau dokin shaidan. Ba dama yaje ganin gida sai sun tatike shi. Bayan Hanne ta tare ya fahimci ashe kukan dadi yake da farko. Da yake
a cikin gidansu aka basu daki Deluwa ce ta zama uwardakinta. Hanne har laluben aljihu tana yi masa. Sannan basu da sirri komai sai ta fada mata. Saboda haka duk abin da yazo dashi gidan kowa sai ya sani. Bai isa kuma ya ce babu ba sai zagi ya koma kan mahaifiyarsa. Ita ake dorawa laifin hana shi yi musu alkhairi da karbe komai nasa.
Wannan abu yana ci masa tuwo a kwarya. Dalilinsa kenan na cigaba da wannan mummunar alfasha. A ganinsa da kudin da suke mutuntawa zai samawa Baaba Mari lafiya daga sharrinsu. Yau da wata sana'ar ya koya a wurin Munzali sabanin wannan da kila wani karatun za a biya ba wannan ba.
A bangaren Baaba Mari kuwa da ta fuskanci irin kudaden da Abbati yake facaka dasu musamman lokacin auren kannensa sai da tsoro ya darsu a zuciyarta. Rufo kai tayi bayan an gama bikin tazo har gidan neman Baba Inuwa. Ranar ta sha habaici a wurinsu musamman matarsa da suka dan yi zaman kishi. Toshe kunnuwa tayi a gidan wata makociyarsu da tayi masauki ta jira ya dawo.
"Ni kuwa Malam ka taba zuwa ganin ubangidan yaron nan a Kano? Wace irin riba suke samu har yake iya daukar nauyin abubuwan da suka fi karfinsa?" Ta furta cikin girmama lamarin.
Jinjina kai ya yi yana tunani, lokaci guda shi ma yaji zuciyarsa ta dora masa alhakin rashin binciken dan nasa. Bai kai ga bata amsa ba suka ga Mal. Sa'adu ya nufosu a kofar gidan fakam-fakam yana baza babbar riga.
"Salamma alekun. Kai Inuwa tashi ka wuce gida." Ya ce fuska a murtuke sannan ya kalli Baaba Mari "kin dai ji kunya. Ni tunda nake ban taba ganin rashin kunya irin wannan ba. Ki taso kafa da kafa tun daga Maigatari ki biyo bazawari. Don kin haifa masa yara shi kenan kuma bashi da sauran rayuwa?"
Baba Inuwa har yanzu shi da 'yan uwansa basu da katabus sai abin da yayansu ya ce ya tashi da sauri.
"Ba abin da ka ke zato bane. Magana tazo akan irin kudaden da Abbati yake juyawa da bamu san... "
Hannu ya daga kamar yana magana da dan karamin yaro "kai arrr. Kinibibin matan ne ban sani ba ko me? Ta taho dai bikonka tana so ayi kome tunda ta rasa manemi shi ne za ta fake da sakawa yaro ido." Ido cikin ido ya kalli Baaba Mari tayi saurin dukar da kai "ko kin ki ko kin so Abbati jininmu ne kuma mun fiki iko dashi. Dan abin da yake kashe mana ki ke bakinciki shi ne zaki soma tada zaune tsaye da tsugudidinku na mata. To ahir dinki. Idan baki da kalamin san barka a gare shi ki kama bakinki akan aibata shi."
Ranta in ya yi dubu ya baci. Ta gaji da wannan fin karfi mara fasali akan 'ya'yanta. Auren ma da akayi duka matan a nan cikin gidan ake rabawa'ya'yan 'yan uwa.
"Allah Ya san zuciyata. Yaran nan amana ce Ta bamu nake kokarin saukewa kun hana. Idan har Abbati yana mugun abu ina masa fatan shiriya. Ina addu'a Allah Ya bude idanunku ku gane gaskiya komai tsawaitar lokaci."
"Rashin kunya za ki min?" Cewar Mal Sa'adu cike da mamakinta.
Baba Inuwa don kada ya bata mishi rai shi ma ya hauta da fada "rashin kunya za ki yi masa Mari?"
Bata ce komai ba ta koma cikin gidan da ta fito. Su Baba Inuwa ma suka koma nasu gidan yana jin yayansa yana mayar da zance akanta. Karya da gaskiya haka ya hada ya kara mata bakin jini.
Daga ranar Abbati ya ci alwashin yin kudi sosai domin ya saya mata mutumci a idon duniya. Ya kuma yi sa a. Tunda ragamar gidan ta dawo wuyansa ya koma mai sawa da hanawa. Hatta Mal Sa'adu komai sai ya ce a jira Abbati ya zo.
Da karfin ikonsa yasa aka mayar da auren Baaba Mari da Baba Inuwa. Ita dai bata so ba amma ta dawo ne saboda saka ido akansa.
Zancen da ake yanzu nadin sarautar Sarkin Samari za ayi masa a garin Kirikasamma. Haihuwar Hanne uku duka yaran kafin suna suke komawa. Duk da baya sonta yana son haihuwa. Kudi ne sun tara sun tada kai. An kai iyaye Hajji an rushe gida an sabunta shi. Karafaren gida mai bangare biyu suka saya a Sharada cikin Kano suka tayar da ginin zamani guda biyu iri daya sak.
Kamar Abbati shi ma Munzali da kudi ya sayawa kansa soyayyar iyayensa. Asabe jiki kullum yana rawa akan bukatunsa. Shekara biyar baya ya auri 'yar kanwarta mai suna Zakiyya. Dangi duk sun dawo jikinsa sai yadda ya ce. Daga haihuwar farko suka rabu saboda tana da wayo. Ta matsu kwarai ta gano ainihin sana'arsa. Ganin ta fara zarginsa ya saketa daga zuwa gida wanka. Yarinyar kuwa ya saka mata Mariya saboda soyayyarsa ga Abbati. Komai na sunanta Abbati ne ya yi. Ya bata yarinyar da shagwaba da gata. Qibdiyya suke kiranta. Bata rasa komai ba. Idan suka yi tafiya har gasar yi mata siyayya suke yi. Duk wanda tafi son kayansa ya dinga tsokanar dayan kenan. Tuni suka daina neman juna. Sun mayar da alfashar sana'arsu kadai suna cewq kawunansu idan sun tara da yawa zasu tuba.
Qibdiyya ce farincikin Munzali da Abbati.
Qibdiyya sanyin zuciya da idanuwansu.
Qibdiyya ta kara kusancinsu.
Qibdiyya ce JARABAWARSU!
A cikin kunnuwan Innayo aka yi kiran sallar asuba na farko da na biyu amma har aka idar bata iya mikewa daga gado ba. Ilahirin jikinta ke ciwo kamar ana soka mata allurai. Wannan yana da nasaba da ciwon hakorin da take fama dashi tun shekaranjiya. Mukamukinta na dama, bangaren hakorin mai ciwo ya kumbura suntum. Uwa uba kwanakin nan saboda zafin da ake fama dashi kusan kullum da ciwon kai take kwana ta wuni. Taje asibitin sha-ka-tafi na unguwar satin da ya wuce an ce jininta ya kuma hawa. Ba dole ya hau ba?!
Ita kadai take kwana ta wuni kamar mayya. Rayuwarta a matsayin matar aure suna kawai ta amsa amma babu alamunta idan ka cire rabon 'ya'ya. Asaben ma bata gaban Alh. Rabi'u. Shi dai ya ci banza da hofi a titi ya zauna gulma a majalisa. Idan ya dawo maigirki ta mika masa abinci idan ya ga dama ya tsakura. Dan na cefanen ma ya daina basu, a cewarsa 'ya'yansu sun kawo karfi.
Lamarin Uwani har yanzu da take matsayin Metiron (matron) a asibitin Nasarawa bai chanja zani ba. Sai an kai ruwa rana ihsani ke giftawa tsakaninta da Innayo. 'Ya'yanta kuwa basu saba da kakarsu ba. Da wahala ta saka su a ido. Idan ta leka gidan saboda dadewar da Uwanin take bata zo ba sai ace suna makaranta.
Maimuna da Salima ba cas ba as! Saboda tabarbarewar rayuwarsu da ta 'ya'yansu Innayo ta kasa daina sana'a. Ranakun da jikinta ya motsa ne kadai bata 'yar tsala. Cinikin a jikinsu yake karewa. Nasu 'ya'yan suna yawan zuwa domin a wurinta sun fi samun abin ci. Idan sun zo ba komai take karuwa dashi ba sai dadin wahala. Amma haka take jurewa da wasa da dariya su tayata aikin abincin ta basu su ci su kaiwa uwayensu.
Zara? Hmmm, babu abin da ya canja a tattare da ita sai kudi da mijinta ya sake yi. A yanzu haka har gidan mai gareshi. Ga shaguna da motocin haya. Yana sakar mata sosai amma kunyar a dinga rabata da Innayo yasa sai ta dade bata waiwayeta ba. Ya kara aure kuma matar 'yar masu kumbar susa ce. Idan ana taro 'yan uwan surukan gidan suyi ta shiga da fita cikin kayan alfarma ana kece raini. Ita da bata da na nunawa sai ta zabi kawai ta rayu babu su da dai su matso jikinta taji kunya.
Su duka hudun nan Innayo tana zubar da hawaye akan rayuwarsu ta yanzu sabanin mafarkinta. Sai dai duk kukanta a kansu bai kai wanda take yiwa Hasiya ba.
Tarihin da take gudu ne yake maimaita kansa akan 'yarta mai jin kanta. Hon. Habu ya shiga gagarin 'yan siyasar da aka daina damawa dasu kafin shekara da aurensa da Hasiya. Kan kace kwabo ya sayar da duk wata kadararsa sun dawo rungumar hannu. Ga Abbas a kwance har yau jiki yaki lafiya. Hasiya sai ta koyi kunshi take yi a unguwa. Sannu a hankali tayi suna mutane suke zuwa sosai. A rana sai ta sami dubu biyu ko uku. Idan satin biki ne kuwa har takwas tana hadawa. Lallen nata dari biyu dari uku take karba. Da wannan kudin suke cin abinci har ta bawa Honorable na sokewa a aljihu. A nasa bangaren shi ma yana fafutuka sai dai babu canji. 'Ya'yansa sun dauki Hasiya uwa banda Ayaah. Ita ce karama amma tafi kowa daukar zugar kakarsu Laraba da sauran kannen mahaifiyarta. An nuna mata Hasiya bata kaunarsu da zuciya daya, nema take ta rabasu da mahaifinsu.
Wannan bauta da Hasiya take yi a ganin Innayo babu abin da zai biyo bayanta sai kwatankwacin wanda ya sameta. Yau an wayi gari wadanda ta karar da karfinta akansu duka sun gujeta. Shi yass ta ari halin da ba nata ba tana kuntatawa Honorable da 'ya'yansa kawai don ya gaji ya sako mata 'yarta.
Gwiwoyinta sun dade da sarewa akan ganin hasken rayuwa. Ta jima da karbar kaddararta amma bata yarda Hasiyanta ta zama Innayo ta biyu ba. Za ta yi iya yinta taga wannan aure mai tsahon rai ya turgude kowa ya huta.
('Yar uwa ko kin san cewa yanayin gidan miji yana taimakawa wurin shaping din wace irin uwa mace za ta zama? Mata da yawa na aure da kyakkyawar zuciya amma abin da suke tararwa a gidan aure sai ya sauya musu zukata. Kuna tunanin da Alh. Rabi'u ya cika namiji Asabe ta isa ta zama ballagar uwa? Ba don bakin halinsa ba me zai sa Innayo mai kyakkyawar zuciya ta dage zai auren Hasiya ya mutu duk da su Ayaah 'ya'yanta ne?)
Ummi da Murja sun gama sakandire da gumin Anti Hasiya. Magungunan Abbas ita take saya. Kudin makarantar Ayaah yana wuyanta har yanzu. Honorable yana bakin kokarinsa amma samunta a kunshin nan yafi nasa nesa ba kusa ba. Jarabawa ta Allah dai har yanzu ita ko batan wata bata yi ba.
Jarabawar Innayo da Anti Hasiya ta shallake dukkan danginsu ta fada akan Hajaratu Ayar Allah.
****
Sautin muryar shugaban tsangayar kimiya da fasaha a jami'ar Ahmadu Bello Zaria (ABU) ce ta karade dakin taron inda yake cewa
"And lastly, the award for best research goes to none other than the reknowned Pharmacologist in person of Dr. Khadija Khalid." Yana dariya ya kara da cewa "Please keep clapping until she comes to the stage."
Zuciyarta sai da ta doka dan tsallen murna gami da faduwar gaban dake tattare da sanin cewa yanzu idanu zasu yi mata caa. Cike da farincikin ganin wannan rana da ta kammala PhD dinta har gashi ana yi musu convocation ta mike tsaye. Mazaunin maigidanta Alh.Tahir a teburin manyan baki ta kalla da tunanin ganin zai dan karfafa mata gwiwa koda da gyada kai ne kafin ta hau. Bata yi mamakin ganin ba ita yake kallo ba. Za ta iya rantsewa ma bai ji lokacin da aka kira sunanta ba. Cikin dandazon mutanen da suka zo domin iyalansu ta nemo babban danta da ido. Dan halak din ita yake kallo yana dago mata hannuwansa bibbiyu fuskarsa dauke da madaukakin murmushi. Wannan kadai ya isheta. Ta tashi cikin takun girma ta hau stage din.
Sanye take da doguwar riga da zani na swiss voile navy blue mai adon yellow din fulawa. Ta daura dankwali irin na Maryam Babangida sannan ta yane kanta mayafin kashka mai kauri yellow. Komai na jikinta ido zai nuna maka na kudi ne. Fuskarta babu kwalliya mai hayaniya. Sauda autarta taso fente mata fuska taki yarda. Suna waje saboda mutum biyu aka yarda a shiga dasu dakin karbar takardar shaidar gama karatun.
Suhaib na ganin ta hau ya mayar da idanunsa ga mahaifinsa. A take duk wata fara'arsa ta dauke. Alh. Tahir ne yake yiwa wata inyamura dake zaune a bangaren ragowar baki magana. Kujerar da yake a teburin manyan baki tayi kusa da bangaren inda su Suhaib din suke kuma ita ma yarinyar nan take. Kayan jikinta sun dameta ga uban attachment a ka.
Vice Chancellor (VC) din University of Nigeria (Nsukka) ne zai bata award din. Sai da ya gama kwarzanta kwazonta sannan ya damka mata. Ta karba da murmushi ta juya koda wasa bata yi gangancin sake kai idanunta inda Alh. Tahir yake ba. Yau ranar farinciki ce wadda ta kara kusanta ta da cikar burinta.
Bayan an gama kowa ya watse ita kadai ta fita daga hall din. Ta zata Suhaib na bayanta sai da tayi masa magana taji bai amsa ba.
A ciki Alh. Tahir bai san Suhaib din na kusa dashi ba. Complimentary card dinsa ya mikawa inyamurar bayan ya rubuta nambar da tabbas za ta same shi idan ta kira.
"Kar ki manta ki kirani." Ya kanne mata ido "sai kin fini farincikin amsa wannan gayyata."
"My Alaji..dole zan kira" ta ce da gurguwar hausarta tana mika hannu.
Basu ankara ba daga ita har Alh. Tahir din sai ganin hannu suka yi a tsakiyarsu. Ya warce katin ya dukunkune shi a hannunsa sannan ya sakarwa yarinyar murmushi.
"Kin fadi jarabawar da Babana ya yi miki. Da baki karba ba kyautar kudi zai yi baki."
Yarinya ta zaro idanu waje na rashin fahimta. Alh. Tahir kuwa sai uban murmushin dole yake kamar sauna yaga wawan zama.
Da turanci yadda za ta fahimta da kyau Suhaib ya ce "Abba ya ce 'yan matan yanzu duk basu da tarbiyya indai sun ga kudi basa jin komai wurin bin dattijai marasa tsoron Allah."
Hankali a tashe jin ta kusa yiwa kanta sawarwara ta shiga jijjiga kai "nooo, ahhh. Abeg na the name I wan see. Alaji shebi I say I no go follow you."
Suhaib ya kalleta ya kalli mahaifinsa ya yi gajeren tsaki ya sa kai ya fita. Duk tsiya da jaraba dai ya tabbata dole Abban nasu ya hakura da ita.
A waje kuwa zuciya cike da farinciki Mami Khadija ta fito daga hall din, tana ta waige waigen neman 'ya'yanta cikin daruruwan jama'ar da suka cika harabar wurin, kowa yazo convocation din 'yan uwan sa.
Tana tsaye tana kallon su dai dai ta ji an taba kafadarta. Ta waiga nan ta ga Suhaib tsaye yana sakar mata murmushin nan da ya saba yi mata mai cike da tausayin ta hadi da nuna sanin halin da take ciki. Har kullum Suhaib ya kasance mai shiga damuwa akan yanayin da ta tsinci kanta a hannun maihaifinsu.
Murmushi ta maida masa tana kara jin tausayin dan ta a cikin zuciyarta. Iya tsahon rayuwarsa tana ganin bai taba damuwa da wani abu ba sama da ita da kuma halin da take ciki, komai nasa ita ce. Bangaren mu'amalarsa da mahaifinsa kuwa, a lokuta da dama tana ganin kamar laifinta ne da ya raina shi. Sai dai kuma babu yadda zatayi, duk iya kokarinta na ganin ta dauke damuwa daga fuskarta yayinda take tare da Suhaib, tabbas sai ya gane halin da take ciki. Wannan yasa ya raina Mahaifinsa fiye da tsammani baya ganin girman sa ko na miskala zarratin, tayi fadan, tayi nasihar, ta ja shi a jiki duk dan taga ya aje wannan matsalar ta Tahir a gefe yayi masa kallon uba dan ta san sharrin da ke tattare da kin yin biyayya da kyautatawa ga mahaifa amma abu ya ci tura. Addu'a kawai take yawaita yi masa.
Babban kalubalenta a kan rayuwarsa bai wuce shaye shayen da ya sa a gaba ba domin neman saukin bacin rai. Gashi har yanzu babu alamun dainawa a tare dashi. Sa'arsu daya Ya gama makaranta har yayi bautar kasa. A lokacin Alh. Tahir yaso kwarai ya tura shi yaje yayi Masters a kasar waje amma fir taki yadda saboda ta san cewa a kan idon ta ma ya aka kare da shaye shayen balle idan yayi nesa da ita. Shima kansa baya son tafiyar, saboda gani yake babu wanda ya damu da yanayin mahaifiyar tasu sama dashi. Wannan ita ce rayuwarta da Suhaib. Tana matukar son shi, kusan ma duk cikin 'yayanta tafi nuna masa so da kulawa, saboda yadda tasan yana sadaukar da duk wani abu na rayuwarsa dan ganin murmushi shimfide akan fuskarta.
Bayan ta gama kallonsa tana wannan tunanin, ta maida dubanta ga Farha dake tahowa gare ta. 'Allah sarki Farha', ta ce a cikin zuciyarta. Yarinya kyakkyawa ga kyawun sura. Duk wani cikar zati na 'ya mace da za ayi sha'awa ace ana so kama daga kyan hali, dabi'a, yawan fara'a, ladabi da biyayya, iya girki babu ta inda Farha ta gaza. Amma har yanzu ko da wasa babu wanda ya taba sallama kofar gidan su da sunan manemin aure.
Wannan abu yana matukar damunta yana ci mata tuwo a kwarya. Ita ma Farhan yanzu take bautar kasa amma babu mashinshini kwata kwata a rayuwar ta. A duk sanda ta dubeta tana jin wani irin kunci da bacin rai a zuciyarta. Mai yiyuwa ma abin da mahaifinsu yake wa 'yayan mutane ne yake dawowa kan yaranta. Haka take yawan ayyanawa a cikin zuciyarta.
A bangaren Farha abin itama yana damunta fiye da yadda za'ayi tunani. Sai dai kuma tana nata kokarin ganin cewa iyayenta basu rage ta da komai ba ta dinga nuna hakan bai dame ta ba. Lokuta da dama takan tsinci kanta cikin kuncin rai har takai ga kwana tana kuka da tunane tunane kala kala.
Son auren bai dameta ba kamar yawan tunanin ta ina ta gaza, mene bata dashi da ya janyo mata bakin jini. Ko irin saurayi yazo taji bata so ta kora ma babu. Irin samarin unguwa ma haka ko yan class daya da zasu nuna suna sonka ko da ba da aure ba irin dai school soyayyar nan duk babu. Kawayenta su zauna ana ta hirar saurayi, haka za tayi zugum tana jinsu ba za ta iya cewa uffan ba akai. Daga karshe ma har gani suke ko ta sawa kanta boko ne ganin mahaifiyarta lecturer ce ko itama bokon ta sa a gaba. Zolayarta suka koma yi ana kiranta Farha Boko addini. Sai ta biye musu kawai aka tafi a hakan, kamar da gaske abin bai dameta bane ba ko baya gabanta. Nan kuwa tafi kowa son taji wani ya zo da kokon barar neman soyayyarta. Itama ace yau dai ta taba yin saurayi.
Bayan ita, sai da Mami tayi dogon juyi tukunna da idanuwanta sannan ta hango Lilu can tsaye da abokai. Wani murmushin takaici ta yi a ranta, wato abun da ta kwana tana yi masa fada akai har suka kwanta bacci ta bayan kunnuwansa ya wuce.
Ta rasa gane irin kin ji da masifar kiriniya irinta Lilu. Kunnuwansa kamar an cusa masa duwatsu an toshesu, baya ji kwata kwata. Fitinanne ne na bugawa a jarida. Shima duk sanda ya yi abubuwansa, Tahir take hangowa, takan ga karshen ta abubuwan da yayi ne Allah ya jarabce shi da 'ya'ya haka.
Khalil bashi da tsawo, har takanyi mamakin yanayinsa jikinsa kamar mutumin ruga. Karamin jiki gareshi babu kiba sai fadin rai da jin shi ma ya isa. Ya fi sauran 'yan uwansa kyau har mutane kan ce masa mai baby face.
Da wannan fuskar kamar ta salihan bayi yake yaudarar mutane, idan yayi abu mutane kanyi mamaki har suga kamar ma karya ne ace wai shi ya aikata hakan. Iya saninta game da halayyarsa ta san baya shaye shaye. Amma akwai hulda da abokan banza, har club yana zuwa. Ga kuma azabar son mata har mamakin sa ma ta ke, shekaru ba wani abun azo a gani ba amma idonsa idon mace sai yayi yadda yayi ya tsarata. Ko da bai fara aikata me gabadayan ba to fa ya dau hanya gadan gadan wurin gadon halin ubansa. A gida ma duk wani abu na fitina, ko abun da za ace bari ko wani abu mara dadi a to sunan sa ake ambata.
Yanzu haka da take hangoshi tsaye yake tare da wasu abokansa yana ta zuba zance daga inda take tana iya jiyo muryarsa ana shewa ana dariya. Ga gashin kan san nan yayi wani irin askin gefe da gefe anyi lowcut, tsakiya ya tara gashi kamar kan zakara. Ita dai ta san ba buzu ta haifa ba amma idan ka ganshi banbace shi da buzu tabbas zai baka wahala. Gashin gaban ne ya wani nannade ya kwanta luf luf yana sheki. Wannan ne dalilin fadan su a daren jiya. Tayi tayi ya fadacmata me yake shafawa haka, har tana ce masa idan ma relaxer ya fara sawa to Allah ya tsinewa mai kamanceceniya da mata. Sannan ta ce idan zai zo taron convocation din to ya tabbatar ya aske kansa askin mutunci.
To gashi dai yazo babu askin da alama kuwa har ya fita nuna farinciki ma yadda yake ta shewa da abokai.
Bayan shi kuma sai autar ta Sauda. Ita yanzu suke shirin gama secondary tare da Mardiyan Nasima, don tare aka saka su makaranta.
Sanda aka saka Sauda, duk da Mardiya bata kai shekarun shiga ba haka Nasima ta nace sai an sakata tsabar masifar kishi dake azalzalarta. Matsalar Sauda shi ne raina duka matan Abbansu. Bata ragawa kowa indai zai shiga gonar Maminta. Amma Allah Ya hada jininta da Mardiya. Nasima tayi kokarin ranasu har ta gaji. Sannan sabanin yayarta Farha da ta rasa manema, ita kuma har sun mata yawa. Shi yasa Allah Allah take ma ta gama makaranta ayi mata aure kafin masifar Tahir ya rabe ta. Tunda manema ne da ita ta ko ina babu babba babu yaro kowa Sauda. Ita da ta haifo su ma bata ga da me saudat din ta dara Yar uwarta ba to amma abu na ubangiji baka da ta cewa se Hamdala.
A gefensu kuwa Mardiya ce a tsaye tana murmushin yake. So take ta karaso wurin Mami amma tana jin nauyi. Sauda ta figo hannun kanwarta suka taho tare ta rungume su daya bayan daya.
Mardiya ita ce babban misali na rayayye ya fita a cikin matacce. Iyayenta basu da halin yabo ko daya amma ita dabi'unta ababen burgewa ne. Tana son 'yan uwanta da mahaifi sannan a gefe tana yakin boye mummunan halin mamanta Nasima.
Su biyar Abba Tahir ya mallaka. Ya dauki son duniya ya dorawa 'ya'yansa. Hatta Suhaib da shi kadai ya san boyayyen halinsa yana son abin sa. Duk wani so da gata da barin kudi ba ta inda ya ragesu. Tunda ya yi kudi arziki ya habbaka.
Bayan gama daukar hotuna iyalin suka hadu a motoci biyu. Ta Alh. Tahir ce ta fara fita saboda takura da ya yi da kallon da Suhaib yake watsa masa. Dayar kuwa Lilu ne ya ja su zuwa gida...
Kaddarar shekarun da Alh. Tahir ya diba yana tafka ashararancinsa da 'ya'yan mutane a yau ne za ta rabi dukkan 'ya'yansa. Domin a wannan rana ne Munzali da Abbati suka shigo garin Kaduna akan hanyarsu ta zuwa Kano.
TAKWAS GOMA BA BIYU.
Tun kafin ta iso bangaren da 'yan kunshin suke zama wanda yake hanyar kofar fita Anti Hasiya ta san takun waye. Sautin kwas-kwas da takalminta mai mugun tsini yake yi har tsakar kan mutane ake ji. Dunduniyar duka takalman ta cire wurin tsinin sai qusa ke kartar fasassun tiles din da aka saka a wurin . Budurwa ce da take cikin ganiyar shekarun 'yan matancinta. Tana da kyaun kirar jiki da na fuska. Kayan jikinta sun matseta don siket din sai da ta dinga tsalle tana jan shi sama kafin ya shiga. Rigarta kuwa ko anyi rantsuwa babu kaffara kana gani ka san da kyar take sauke numfashi. Ga rabin kirji duk a waje haka ma bayanta. Kanta babu dankwali sai wani yalolon mayafi sa ta yane kan dashi. Ana ganin zara-zaran kalbar da tayi da zaren lilo a cewarta shi ba haram bane.
"A haka zaki fita?" Cewar Anti Hasiya ganin tana niyar fita kai tsaye.
Maimakon amsa Ayaah gatsina fuska tayi ta nufi kofar gidan gadan gadan za ta fita. Anti Hasiya tayi murmushin takaicin wannan hali nata. Wani salon fitsara da rani bata tunawa dasu sai taga tsakar gidansu cike da 'yan kunshi. A lokacin take yunkurin taka matar da take matsayin uwa a gareta don kawai ta zubar mata da mutumci. Bukatarta ta dade da biya domin dadaddun kwastamominta kusan kowa ya san tana da 'yar da take neman fin karfinta ba don a tsaye take ba.
Murja dake gefe tana tata sana'ar ta kitso ta saki kan matar gabanta ta taso a harzuke.
"Ba dake Anti take ba?"
Ayaah tayi mata kallon raini tana jujjuya idanu "ai fa tunda ki ka fara kama matsabbai bakinki ya bude. To haka zan fita uwata ko zaki hana ne?"
Wata mata ta kada baki ta ce "ke kuwa 'yan mata idan baki ga girman yayarki ba bai kamata kiyi haka a gaban mahaifiyarki ba."
Dukan kunnuwanta tayi a tare tana murguda baki hagu da dama tare da farfari da ido kamar sabon kamun aljanu.
"Mahaifiya? Tabdi. To ni mahaifiyata tana kasa Hajiya. Wannan matar..."
"HAJARA!"
Ba Ayaah ba kusan duka matan wurin harda Anti Hasiya kuwa sai da tsawar Honorable ta kada musu ciki.
"Baki da bakin amsawa ne?" Ya sake cewa a harzuke yana tsaye a kofar da ta raba ainihin tsakar gidan da barandar da ake zaman kunshin.
"Gani Baba" ta ce da sauri lokaci guda kwalla na zubo mata.
"Share wadannan munafukan hawayen kizo ki wuce mara kunyar banza."
"Baba gidan Anti Hasina (kanwar A'i kuma yaya ga Hasiya) zani."
"Kin wuce ko kuwa?"
Bata jira ya kuma magana ba ta bi ta gefensa ta shige ciki tana kuka. Dan dukar da kai ya yi ya bawa matan hakuri.
"Ai shekarun nan sai an kai zuciya nesa. Allah Ya shirya mana zuri'a." Matar dazu ta furta da dan murmushinta.
Ciki ya koma zuciyarsa tana tukukin bacin rai. Tsakaninsa da Hasiya yafi kowa sanin cewa ba soyayya bace. Ya sakawa zuciyarsa Allah ne Ya kawota cikin rayuwarsu domin ta zame masa bangon jingina. Idan ya tuna yadda har A'i ta rasu bai taba taka kafarsa gidansu ya gaishe da Innayo ba kunya kan rufe shi. Shi yasa baya ganin laifinta da taki goyon bayan auren nasu har yanzu. A yayinda mutane da yawa marasa tawakkali zasu alakanta aurensa da Hasiya a matsayin silar karayar arzikinsa shi alkhairi ya hango. Ya sani sarai cewa ko uwar 'ya'yansa da wuya ta zauna tsahon shekarun nan tana dawainiya dashi. Ba yadda zaiyi ya raba 'ya'yansa da kakarsu Laraba da kannen mahaifiyarsu amma yana bakincikin alakarsu. Yaji dadi da sauran basa daukar zuga amma Ayaah zugar ce ta tadda hali. Da fada yana fitowa mutum kila ba za ta ganu ba yanzu. A kanta ya fara dukan 'ya'yansa amma kullum dada kangarewa take yi. Shekararta goma sha shida da watanni, yanzu take ajin karshe a sakandire.
Bayan sun shige ciki sai da Anti Hasiya ta dauki mintuna kafin ta ita cigaba da zanawa matar gabanta lalle. Lokuta marasa adadi ta kan ji kamar ta yiwa Ayaah dukan tsiya amma sai ta daure. Maraicinta take dubawa da kuma sanin cewa duk ranar da ta kai mata hannu akwai yiwuwar ta karairayata. Bata iya fushi ba sam. Sai ta dade tana tara mutum kafin ta dauki mataki. Abu na biyu kuwa bai wuce fargabar da take fama da ita akan kalaman Innayo ba. Tana yawan fada mata cewa yadda su A'i suka watsa mata kasa a ido ta tabbatar da wuya idan ba haka su Ummi zasu yi ba. Gashi ita bata haihu ba ma balle tasa rai da samun mai jinkanta a gaba.
'Ba duka aka taru aka zama daya ba. Dan da zai ji kan mutum ba lallai ya fito daga cikinsa ba.' Haka take yawan fadawa zuciyarta.
Daga karfe uku ta rufe karbar 'yan kunshin ranar. Sai bayan la'asar ta gama ta shiga ciki tayi wanka. Ummi tayi abinci ta ci sannan taje ta duba Abbas. Yana yawonsa ko ina sai dai kwakwalwar ce ta dan tabu. Maganarsa ta hankali bata tsayi yake komawa shirme. Kwanakin nan yana yawan tashi da ciwon kai irin wanda yake yi tun bayan hatsarinsu. Ganin har lokacin yana kwance ta koma dakin Honorable.
Kudin da take tarawa ta dauko. Dubu hamsin ne da 'yan kai suka rage bayan sun sayi kayan abinci sannan ta biyawa Ayaah kudin NECO da WAEC. Dubu shabiyar ta cire zata kaiwa Innayo washe-gari. Wata shabiyar din ta bawa Honorable a kai Abbas asibiti. Ashirin din kuma zata rike goma sai goman kai ta siyo kayan lalle. Dama haka take yi duk karshen wata ta raba musu ribarta.
"Hasiya ki bar kudinki. Na yiwa wani abokina dan majalisa magana zai bamu tallafi akai Abbas asibiti a duba shi sosai."
Kin karbar kudin da ya miko tayi, "ka fara kaishi ko magani su bashi na saukin ciwo kafin tallafin yazo."
Da kyar ta samu ya karba a daidai lokacin da suke jin ihun Abbas din cikin azabar ciwo. Da gudu-gudu Honorable ya fita ya samo mai adaidaita sahu suka kaishi asibiti. Sai karfe tara na dare aka sallamosu.
Kafin su dawo saurayin Ayaah ya kawo mata ziyara. Tunda babu idon babba a gidan tayi shiga irin wadda take so ta fita ba tare da sauraron gargadin Ummi da Murja ba.
"Wowwww baby so ki ke ki kasheni ne da wannan kwalliyar? Kin san ina matukar son kwalliya. Ganinki haka ya cire min duk wani bacin rai da na taho dashi." Ya ce tana isowa jikin motarsa.
Kanta taji yayi gingirin ya kara girma saboda tsabar dadin da taji da yabawarsa. Hankalinta kwance ta gillo masa karya da suka soma hira saboda yadda da soyayyarsa da tayi.
"Babanmu ya ce ka fito."
Sarai ya fahimceta sai ya bagarar ya gyara tsayuwarsa.
"In shigo dai ko Baby?"
Kallonsa tayi da rashin fahimta ta ce "ka shiga ina?"
"Oh, ba kina nufin na shiga ciki mu gaisa bane?"
Da saurinta ta gyara masa "nufina ya ce ka turo ayi magana saboda asa rana."
Rabeel sai ya mike tsaye da kyau yadda za ta ga tsayinsa ya daure fuska yana jera mata tambayoyi "amma ba dai ce masa kika yi mun tsayar da maganar aure ba ko? Yaushe muka hadu? Ke da kike karatu me zaki yi da aure?"
Tsoron kar shi ma ya kufce kamar sauran yasa ta kwantar da murya tana bashi hakuri
"Dama ba wai auren za a daura yanzu ba. Kawai dai don ya san da kai ne kafin na gama makaranta."
Kofar motarsa ya kama zai shige yana sababin da ya kwana biyu yana neman damar yi. Ya gaji da gafara sa bai ga kaho ba. Ta kware wurin kwadaita masa jikinta da irin shigarta amma taki bari ya dara daga rike mata hannu. Ya zata a waye take yazo kwasar ganima ashe kidahuma ce. Ga damar sulalewa ya gudu ya samu ba bata lokaci kuwa ya cafketa.
"Yadda bana son a katsewa kannena mata karatu kema ba zan katse miki ba. Na zata Baba zai yarda kiyi zurfin ilimin da zamu yi alfahari dashi ni dake da 'ya'yanmu amma na fahimci ba haka ba. Tunda da wuri yake son aurar dake gaskiya ki nemi wani."
Hankalin Ayaah in yayi dubu to duka ya mike tsaye. Bata da burin da ya wuce tayi aure ta bar gidansu. Gwaggo Laraba dama ta fada mata Anti Hasiya ce ta hana Murja da Ummi aure sannan sun kasa shiga jami'a. Daga mai dinki Ummi sai Murja dake kitso. Ga babansu ta hana arziki ya zauna masa domin ta juya shi. Shi yasa ita ta dage da karatu sosai don ta sha alwashin shiga jami'a. Abin kaddara duk kokarinta bata ci kwalifayin (qualifying) ba shi yasa Anti Hasiyan ta biya mata kudin NECO da WAEC. Ta fara murna wannan saurayin sun yi wata biyu shi ma yana shirin subucewa.
Murmushi ta kirkiro na dole ta ce "Lahhh, wasa fa nake maka. Baba so yake na zama likita ma."
Ai kuwa ya hade girar sama da kasa
"Ayaah ni kam ba zan iya hada inuwa da makaryaci ba. Kamar baki san haramcin karya ba ki kalleni ki yiwa mahaifinki karya da sunan wasa?"
Hawaye ta soma tana bashi hakuri ya shige motarsa yaja. A ransa yana cewa ta fiye bakin naci. Tun satin farko da yazo ya fahimci ita aure kawai take so.
"A nemi wani wahalallen ba ni ba" ya ce yana dukan sitiyari.
Kamar kiftawa da bude ido Ayaah ta neme shi ta rasa. Kuka sosai ta fashe dashi tana mai gasgakata Gwaggo Laraba. Lallai bokan Anti Hasiya ya iya aiki. Yanzu yanzu ta fito yana dariya amma ko rabin awa basu yi ba ya tafi.
Rabeel bai zame ko ina ba sai gidansu abokinsa Danliti wanda ya bashi aron mota. Waya yayi masa ya fito karbar makulli.
"Amma Rabilu yau kayi sauri ko baka sameta ba?"
Dariya ya yi sannan ya kwashe yadda suka yi da Ayaah ya fada masa.
"Kuma sai ka barta?" Cewar Danliti da mugun mamaki.
"To zama kake so nayi a sani auren da ban shirya ba?"
"Kai dai gaula ne. Irinsu ai da sa musu rai da aure ake moresu. Yarinya danya shakaf kamar wannan ka tsallake ka barwa wani?"
Maganar ta shigi Rabeel ya cije yatsa yana maganar 'yan tasha yadda ya saba "ban yi tunani ba Yasin. To yanzu meye shawara?"
Danliti ya lashe lebensa na kasa "sa'arka ta kare saura tawa. Can zani na gwangwaje son rai..."
"Wannan yarinyar kamar kifi ba bari zata yi ka mori komai ba."
Danliti ya shige motar da ya gyara zai mayar gareji kafin ubangidansa ya fahimci bata kwana a can ba "muje ka rakani na mayar da motar nan na baka satar ansa domin gaba."
Jirgin Abuja su Munzali suka shiga. A can suka dauko motarsu wadda suka ajiye a gidan shakatawar daya daga cikin mutanen da suka ziyarta a Lagos. Babu bata lokaci suka kamo hanyar Kano saboda shirin bikin nadin sarautar Abbati sati mai zuwa.
"Wai kuwa ya maganar mai yiwa Qibdiyya alkyabba ne? Ka tabo shi mana muji idan ya gama mu tsaya a Zariyan" Abbati ya tambayi Munzali suna daf da shiga Kaduna.
Da sauri Munzali ya dauki waya ya kira mutumin da ya bawa aikin dinkunansu shi da Abbati da 'yarsu. Telan kwarrare a dinkuna irin na kayan sarauta. Kwatanta musu wata plaza ya yi mai suna Diamond plaza.
"Kwananmu hudu da kama shago a nan mun baro Zariya. Ban fada maka bane Alh. Munzali saboda idan na gama da kaina zan kawo muku Kanon."
"Ka gama na Qibdiyya? Babanta ya dameni wallahi." Munzali ya ce yana dariyar hararar da Abbati ke jefa masa.
"An hada komai saura takalman."
"Zamu biyo"
Sau biyar Mardiyya tana kin daukar wayar Mamanta Nasima saboda tsoron me zata ce mata. A na shidan sai ta tura mata text wanda yasa da kanta ta kira a tsorace.
(Idan baki dauka ba zamu hadu ne a gida. Shashasha mara mutumci.)
Ringing din farko Mama Nasima ta dauki wayar ta fara surfa mata zagi.
"Saboda baki daukeni a bakin komai ba ki ka shirya ki ka bisu ko? Tun ranar da babanki ya fada ban ce babu inda zaki ba?"
Mardiyya sai ta wayance kamar bata ji me ta ce ba "Mama muna hanya"
Rai a bace ta ce "Au, baki ma ji me na ce ba kenan. To ki ce su saukeki a shago yanzun nan."
Mardiyya ta kashe wayar ta taba Sauda dake gefenta.
"Mama tana nemana a shago."
Sauda ta dan zura kanta gaban motar ta ce "Ya Lilu don Allah mu biya shagon Mama a ajiye Mardiyya."
Bai so ba sai dai kuma Mardiyya tafi karfin haka a wurinsa. Tana kaunar 'yan uwanta suma suna sonta ciki kiwa harda Suhaib.
"A ina yake?"
"Diamond plaza" Farha ta bashi amsa.
U-turn ya yi ya koma titin da suka baro domin sun bar hanyar plazar a can baya. Farha ce ta kira Mami Khadija ta sanar da ita inda zasu fara zuwa ta ce babu matsala. Ta ma jidadi domin abin da take son yiwa Alh. Tahir zai fi a bayan idon 'ya'yansa.
Suna shiga harabar plaza din Lilu ya hango wata jar mercedes benz ya daki sitiyari yana dariya.
"O.M.G! Wayyo Ya Suhaib mintsine ni na farka."
Suhaib ya girgiza kai yana dan murmushi "kana da matsala Lilu. Yanzu zaka yi sauri mu ajiyeta ne ko mota zaka tsaya kallo?"
Kallon rashin yarda da maganar da ta fito daga bakinsa Lilu ya yi masa.
"Mercedes benz E cla
ss, E dinma 350. Ya Suhaib dream car dina ce fa kake yi mata kallon raini."
Su Farha dake baya suka bushe da dariya don Lilu kamar zai yi kuka.
"Tunda dai iyakarka da ita bai wuce dream din ba ai shi kenan." Ya zura hannu ta taga ya dagawa motar da ta sha tint glass hannu "ke dream car Lilu na gaisheki."
"Ya Suhaib ka sace min gwiwa. Burina na mallakin motar nan kasa kafa ka dagargaza da wannan abin da kayi."
'Yan matan suka cigaba da dariya yayinda Lilu yake ta mita kamar ya ari baki. Kusa da motar yaje ya yi parking yana cewa sai ya shafata ko za ayi kararsa.
"Muje na raka ka Lilun Mami." Farha ta ce hannunta a jikin hannun kofa.
Mardiyya ta janyo hannun Sauda bayan ta fito daga motar.
"Zo ki rakani muma mu taba."
Kamar ba su Suhaib yake kira ba duka kannen nasa suka fice suna dariyar yadda jikin Lilu ke rawa yana zaro wayarsa. Jingina ya yi a jikin motar ya gyara kwalar rigarsa. Farha ya mikawa wayar ta karba tana murmushi.
"Allah Sarki 'yan matan KASU zasu shiga uku da hotunan karya."
Yana zura hannayensa a aljihu idanun Abbati dake zaune a mazaunin direba yana ta dariyar hirarrakinsu suka sauka akan Farha.
"Ya Ladif" ya sami kansa da furtawa a hankali yana shafar sumar kansa da take shan gyara.
'So ne? Wannan ce soyayya?'
Karon farko a rayuwarsa mace ta burge shi. Mace ta dauki hankalinsa. Ganin Farha ya yi tamkar tauraruwar da wata ba ya cika sai da kasantuwarta kusa dashi.
It was love at first sight...
TARA DAGA KE SAI GOMA.
I just published "10" of my story "UWA UWACE...". https://my.w.tt/ZvVtc6Nojab
UWA UWACE...10
Batul Mamman
Allah don isar da tafi kowacce isa
Allah don mulkin da bashi da wa'adi
Allah don rahamar da bata yankewa
Allah don girman zatinKa
Allah don kadaitar mulkinKa
Allah don buwayarKa
Ka karawa Annabi SAW daraja
Ya Rabbi mamallakin sammai da kassai Ka kare mana zuri'a daga dukkan sharri.
Ya Allah Ka karesu daga sharrin masharranta da sharrin kawunansu domin hakika kowane dan Adam akwai dabi'ar da aka halicce shi da ita mai kyau ko akasinta. Ya Allah kar Ka buga misalin Allah wadai damu ko 'ya'yanmu.
Ya Allah Ka azurta iyayenmu da mafi girman daraja da daukaka daga cikin AljannarKa. Allah Ka yafe musu, Ka jikansu, Ka kara musu lafiya, Ka kyautata halayensu, Ka inganta mu'amalarmu dasu da kuma sauran mutane. Amin
RABBIR HAMHUMA KAMA RABBAYANI SAGHIRA
Babu sautin da kunnuwan Abbati suke ji sama da bugun zuciyarsa. Sassanyan murmushi ya kufce masa a lokacin da ya dora hannun damansa akan kirji saitin zuciyarsa.
"Ya Farha kawo kema na dauke ki" muryar Lilu ta katse tunaninsa.
"Farha" ya gwada kiran sunan akan harshensa.
Daga wajen murmushi tayi wanda ya kara narkar da zuciyarsa ta ce
"Haka kawai ina tsaya masu motar su fito a tsareni in sha kunya."
Mardiyya da Sauda ya dauka har lokacin Munzali bai fito daga wajen tela ba. Farha ta gaji da surutunsa na rokon ta dauka ta jingina da motar bangaren direba.
"Irin abin nan zanyi kamar nice mai motar na zo shopping."
Hannun ta kama kamar za ta bude, Lilu ya saita ta zai dauka Abbati kuma ya cire lock. Tana dan daga handle din kofar ta bude. Daga ciki ya turota ai sai ta gigice su duka hudun suka kwasa a guje suka nufi shagon Mama Nasima. Suhaib na ganin haka ya fito daga mota da sauri. Wurin Abbati dake tsaye yana dariya ya karasa ya mika masa hannu.
"Don Allah kayi hakuri"
Abbati ya saki fuska sosai "ni zan baka hakuri saboda na tsorata maka kanne. Muje na tayaka kiransu" ya nuna hanyar matattakalar da suka hau.
"Kar ka damu na san inda suka je" Suhaib ya bashi amsa yana hawa benen. A ransa yake ayyana mutumin yana da saukin kai duk kuwa da cewa kana ganinsa tun daga sutura har fatar jiki ka san akwai kudi.
Shagon Nasima da take sayar da kayan kitchen suka shiga. Allah Yaso babu kwastoma ko daya a ciki sai 'yar budurwar dake tayata aiki. Mardiyya ce ta fara shiga ta hau ta da fadan da ta fara a waya.
"Tsinannen yawo da rashin kishin uwarki yasa ki ka bijerewa maganata ko? Wace uwar za a baki a wurin da yasa ki fita da sassafe kafin na tashi?"
Tuni idanun Mardiyya suka kada suka yi ja tana shirin yin kuka. Farha, Lilu da Sauda sai suka yi turus. Mama Nasiman kanta ta dan ji kunyar ganinsu amma sai ta fuske.
Fuska ba wani annuri ta ce "yau kune a nan? Ince dai lafiya."
"Lafiyar kenan. Kanwarmu wadda babu mai iko da ita sama da Alh. Tahir mahaifinta muka kawo" Lilu ya bata amsa shi ma fuska a hade.
"Rashin kunya zaka yi min? Khadija ma..."
"Wallahi kar ki soma. Da fa bamu san asalin balbela bane." Farha da bata da hayaniya ta ce a tsiwace. Ita da 'yan uwanta basa gani su kyale in dai abu ya shafi mahaifiyarsu.
Mardiyya kuka ta saka. Ita ma ta san labarin auren cin amanar da mahaifiyarta tayi da babansu. Ba dai su san da maganar suna neman juna ba amma sun san mai'aikin gidan ce. Haka zalika sun san Anti Jiddo 'yar uwarta ce. Sauda ma kukan take tayata. Ana haka Suhaib ya shigo. Mama Nasima ta nuna masa kannensa cikin bacin rai.
"Ka fita dasu kafin na kira Alhaji. Ba zan yarda ku zo har nan ku min rashin kunya ba."
Da ido kawai ya kallesu suka fice daya bayan daya.
"Kiyi hakuri"
Ya ce da ita bayan sauran sun fita. Maminsu ta gargade shi sosai akan yiwa matan babansa rashin kunya. Mota suka nufa ya karbe mukullin daga hannun Lilu. Bai ce dasu komai ba yaja suka tafi. Suna fita Abbati da Munzali suna shiga shagon Mama Nasima.
Yawun bakinta taji ya kafe ta nemi na hadiya ta rasa saboda ganin matasan masu kudi a gabanta. Komai da komai na suturar jikinsu da ido ke gani iri daya ne. A cikin 'yan dakiku ta gama lissafin tsadar kayansu ta gane sun tsallake raini nesa ba kusa ba. Harara ta gallawa Mardiyya wadda take jin zafin zuwanta a mace gashi bata sake haihuwa bayanta ba. Jikinta na rawa saboda rashin sanin daraja da kimar kai ta matsa gabansu.
"Alhaji me ku ke so? Ke Debora miko musu katalog (catalogue) dinnan su duba kaya."
Kamar wani zai rigata da sassarfa ta ce su biyota office dinta. Wani dan daki ne da aka sakaye daga gefe da kofar gilas. A nan take zama idan ta shigo shagon. Waige waige Abbati ya dinga yi yane neman su Farha. Munzali yana 'yar dariya ya tura shi gaba zuwa ofishin Mama Nasima tana fesa airfreshner.
"Tunda ka kawomu ko kofi ne sai ka saya." Ya rada masa a kunne.
Da suka shiga sun sameta tana goge kujerun zaman baki da dankwalin kanta. Murmushi take ta dokawa ta nuna musu su zauna.
"Mardiyya. Ke Mardiyya kawo musu abin sha. Alhaji me zaku sha? Idan babu sai Debora ta sauka ta siyo."
Sai da Mardiyya ta goge hawayenta ta taho zuciyarta tana zafi. Haka ta tashi ta fahimci mahaifiyarta tana bare-bare da zubar da mutumci gaban masu kudi. Idan ta sansano kudi a jikin mutum to babu ya shi a wurinta. Yaro sa'an Mardiyya ma sai ta duka masa. Neman kudi take kamar tayi sata. Tunda bata da magajin da zai tatso mata da yawa a jikin Alh. Tahir sai ta fake da kasuwanci tana kwasar kudi son rai. Duk da haka tana son kasuwancin domin yana hadata da manyan mutane.
Shigowar Mardiyya keda wuya idanun Abbati suka sauka a kanta. Murmushi ya yi sosai.
" 'Yan mata ashe nan ku ka gudu. Dama ku muka biyo. Ina 'yan uwan maki?"
A darare ta kalli Mama Nasima sai taga ta kyafta mata ido da sauri. Da dariya ta ce dasu "Ba dai Mardiyya ku ka biyo ba? Ikon Allah. Ai 'yata ce ta cikina. Waye surukin nawa a cikinku?"
Mardiyya ji tayi ina ma kasa za ta tsage a lokacin ta shige ciki. Daga ganin mutane ta kasa zaune ta kasa tsaye.
Ita kuwa Mama Nasima ko amsa bata jira sun bayar ba ta dora da cewa "zo ki zauna bari na kawo lemon da kaina."
Da taga Mardiyyan ta kasa daga kafa ma saboda takaici ta soma fada "meye haka ne zaki barsu jira kamar sa'anninki?" Ta dube su da dan murmushi "kuyi hakuri fa. Yaran yanzu da ka ce kana son su sai su dinga ganin kamar kun zama sa'anni."
Tana fita Mardiyya tayi saurin zagayawa yadda zata fuskancesu da kyau.
"Don Allah kuyi hakuri da maganar Mama. Sannan kayi hakuri da muka tsaya a jikin motarka."
Murmushi Abbati ya yi yana jin tausayinta. Yanayin abin da mahaifiyarta tayi ba kowa ya kawo masa rai ba sai Munzali. Haka Asabe take gigicewa idan suka je gidan. Yanzu kamar ta goya shi bayan da almajiri take kiransa. Munzalin ya kalla yaga ya yi shiru. Ya tabbata shi ma ta bashi tausayi ne.
"Ga mai motar nan ni dan rakiya ne."
Caraf a kunnen Mama Nasima. Da saurinta ta karaso ta zuzzuba musu maltina mai sanyi a kofunan tangaran da yanzu ta bude daga kwali cikin kayan shagon. Da zata basu har wani dan durkuso tayi wanda ya tsayawa Mardiyya a zuci don takaici.
"Ma sha Allahu. Ai nima mota ta tana nan a waje. Zaku ganta wata koriya koriya nan. 3.8 miliyan maigidanmu ya saya mana ni da kishiyoyina. Mu uku ne nice ta biyu." Ta dan yi shiru na abin da bai kai sakan biyar ba sannan ta cigaba da magana tana tura musu tray din da ta dora kofunan "ku sha mana ai an zama daya. Ya sunanku ne?" Ta kare da tambaya tana doka murmushinta mai ban haushi.
Munzali zai yi magana Abbati ya take masa kafa ya nuna kansa
"Ni suna na Abbati shi kuma Munzali."
Kacokan ta mayar da hankali gare shi "Allah Sarki Alhaji Munzali. Ya su Mummy? Ya fama da jama'a?"
Kasa jurewa Mardiyya tayi ta fice. Wannan zub da kimar ya yi yawa. Abbati da Munzali kuwa da kyar suka danne dariyarsu. Munzali ne ma ya yi karfin halin cewa zasu tafi.
"Kun dai karbi nambar wayarta ko?"
"Yanzu zamu karba" Munzali ya bada amsa yana yin gaba.
Tana ganin Abbati ma zai fita ta dakatar dashi "Alh. Abbati ai da ka jira shi a nan. Sai da irin haka zasu fuskanci juna."
"Haka ne" ya ce yana tsayuwar dole.
Suna fita Munzali ya karbi nambarta. Hakuri ne dai take ta bayarwa ya ce kada ta damu. Nambar ma ya karba ne saboda kiran gaggawa da Abbatin yayi masa. Bai sani ba ko zai bukaci hakan.
A ciki tambayoyi ta tsare Abbati dasu ya dinga bata amsoshin da ya ga dama. Ba jimawa Munzali ya kira shi ya ce mata zasu tafi. Haka ta taso Mardiyya a gaba har bakin mota suka rakosu.
"Ka gaishe da Mummy da Daddy don Allah. Ka turowa Mardiyya nambarsu sai na kira mu gaisa a fara sabawa da juna."
Munzali da Abbati na ganin sun bar wurin suka hada ido suka kwashe da dariya.
"Mutumina ka gaishe da Mummy da Daddy" cewar Abbati yana kyakyatawa.
"Ya kaga Asabe tana amsa sunan Mummy" shi kuma Munzali ya ce yana tasa dariyar.
Sai da maganar ta fito ya yi saurin kallon Abbati ya doki bakinsa da kansa "sorry Abban Qibdiyya Allah subul da baka ne."
Abbati ya girgiza kai "ni dai na fada maka UWA UWACE. Tunda ta kawoka duniya tayi maka komai."
Duk da Munzali yaso daurewa amma sai da muryarsa ta dan yi rawa ya ce "Komai fa ka ce Abbati. Asaben ce tayi min komai?" Wani zazzafan hawaye ne ya sauko masa gashi shi yake tukin lokacin ya share ido da karfi "na rantse maka idan yau za a bani zabi kai zan zaba akan uwar da ta haifeni. Bata damu da komai nawa ba sai aljihu." Yana maganar yana hawaye sosai. Haka Allah Ya yi shi mai matukar son kulawa. Kuma duk yadda ya kai da basarwa ba karamin kwadayin ranar da Asabe za ta nuna masa mahimmancinsa yafi karfin kudi yake ba.
Hawayensa ya tayarwa da Abbati hankali ba shiri ya sake karbar tukin. Shiru suka yi a motar har suka wuce Zariya sannan Abbati ya katse shirun motar.
"Munzali"
"Na'am" ya amsa yana ciccijewa irin na wanda ransa ya baci yana jiran rarrashi.
"Dadina da kai ka ki girma. Ko kunya babu kake faman kuka kamar karamin yaro."
"Allah abin ne da haushi." Kawai ya sake fashewa da kuka.
Abbati yana tuki ya daga hannu ya make shi a kafada "ka min shiru don ubanka. Haka kawai za ka dinga min kuka kamar na dauko rikakken rago."
A take Munzali ya soma dariya ya karkace baki ya ce "
aaaaa,
aaaaa,
aaaaa"
Abbatin ma dariyar ya kama yi. Sai da suka yi mai isarsu sannan ya yi gyaran murya wanda yasa Munzali mayar da hankali gareshi.
"Misali a kawo maka mace da namiji duka kyawawa ace ka zabi daya wanne za ka zaba?"
"Me yasa ka tambaya?"
"Maganar sai mun zauna ka bari muje gida"
"Nifa ka san bana son jan rai kawai ka fada."
Bakinsa ya ji ya dan yi nauyi amma yana ganin dole ya yi magana.
"Munzali yaushe zamu daina wannan sana'ar?" idanunsa akan titi ya cigaba da magana tunda ya samu hankalin Munzalin na gareshi "ina tsoron kada mu dore a haka har asirinmu ya tono mu gogawa Qibdiyya abin da ba zai kankaru ba."
A hankali Munzali ya ce "ka sami macen da ka ke so ne? Ko yarinyar dazu ce da kaimu shagonsu?"
"Ko daya" ya sami kansa da cewa saboda yadda zuciyarsa ta raya masa cewa bashi da tsaftar jiki da ruhin da suka isa bashi dama ya furtawa Farha kalmar so.
"Idan kana so mu daina ka sani ba zan tsallake maganarka ba. Nima fa na san haramun ne amma hanyar da na sani kenan ta samun kudi."
"Munzali bamu da maraba da karuwai fa. Biyawa mutane bukata muke yi su biyamu. Bana so mu tabbata akan wannan abu" ya ce yana dan tsare shi da ido.
Jikin Munzali ya dan yi sanyi. Yana son bari shi ma amma yana tsoron kada haka ya zama dalilin rabuwarsa da Abbati.
"Idan mun daina me zamu yi?"
Abbati ya ce "yanzu zamu ga amfanin adult education (yaki da jahilcin) din da muka yi. Kudaden da muke samu muyi amfani dasu mu bunkasa shagunanmu na kasuwa. Ko mu bude irin super store dinnan ko mall."
"Kai kana sha'awar mata ne?" Munzali ya kasa hakuri sai da ya tambaye shi.
"Na zata bana yi Munzali amma daga baya na gane nafi son mace akan namiji. Nifa sana'a na dauki abin da muke yi sai kuma sabo. Amma ina ji a jikina zamu iya dainawa idan mun sa kanmu. Mu dai yi tunani a kai mu nemi mafita."
Kai tsaye Munzali ya amsa masa sai dai yana ji a jikinsa zasu wahala. Sun girma cikin wannan dabi'a har ta kai da kyar yake iya zuwa ga matarsa. Cikin Qibdiyya ma rabo ne kawai ya sani. Shi kuwa Abbati rashin so da mugun halin Hanne na dauke dauke yasa duk zuwansa gareta baya wuce rabo. Sai gashi 'ya'yan ma basa zama. Dadin dadawa sun saba da rike manyan kudi. Suna cikin matasan dake tashen kudi da 'connection' na sannin manya a yanzu
(Ina so 'yan uwa su sani cewa mutane masu neman jinsinsu kala biyu ne. Akwai homosexuals masu neman jinsinsu kadai. Basa taba sha'awar wani daban. Akwai kuma bisexuals. Sune masu sha'awar jinsinsu walau mace ko namiji da kuma wanda ba nasu ba. Suna iya mu'amala da kowanne su jidadi. Abbati da Munzali sun kasance cikin wannan jerin. Sabo yasa basu damuwa da mata, ba wai don matan sun daina daukar hankalinsu ba.)
Kayanta ta rage ta saka wata doguwar rigar yadi mai laushi sannan ta fito falonta inda aminiyarta a wurin aiki take zaune. Da fara'a ta sake tashi a karo na biyu ta rungumeta.
"Congratulations Dr. Khadija."
"Godiya nake Assistant Prof. Zuwaira" ita ma ta kirata da nata mukamin suka dara.
Suna zama Dr. Zuwaira kamar yadda kowa ya santa a wurin aiki ta mike " 'yar uwa guduwa zan yi fa tunda naga tare da maigidan ku ka dawo. Dama makara nayi ban samu na zo miki a makaranta ba na ce bari na biyo gida."
Dan bata rai Mami Khadija tayi "ba za ki zauna walimar da 'ya'yanki suka shirya min ba? Saboda ita mutane da yawa basu je Zariyan ba. Ana la'asar za a fara."
"Zan dawo Doctor. Babban abin da ya kawoni akan maganar gidan nan ne. Na san kin ce a yau dinnan za ki yi masa idan ya kawo zancen komawarku sabon gida." Da tausayi ta kalli kawarta da ta dauka tamkar kanwarta "Khadija fight for your marriage don Allah kada hakurinki na shekaru ya tashi a banza. Ki duba ki gani ido rufe nake neman aure da shekaruna da komai saboda shi ne babban martabarmu."
Murmushin takaici Mami Khadija tayi idanunta na cikowa da kwalla. Ba don suna shigowa gidan motar Dr. Zuwaira ta shigo ba da tuni kila ta karbi takardarta a hannun Alh. Tahir.
"Magana fa nake kin tafi duniyar tunani"
A gajiye da lamarin aurenta ta soma magana.
"Kin san komai Anti Zuwaira. Abin da na kasa fadawa 'yan uwana ban boye miki ba. Don Allah kada ki shiga sahun masu bawa mata shawarar zama da mazinaci."
Kwalla ce a idanuwanta. Kuka take son yi ko zata sami sassauci. Ta wahala matuka kafin ganin cikar burinta. Aiki ba dare ba rana har ta tara isassun kudi tayi gini a nan cikin Kaduna. Gidan da Alh. Tahir ya kama mata haya a Zariya tun lokacin karatunta har ta soma aiki ya dade da saya. Da sunanta ya saya ya bata takardun gidan. Wanda ta gina yanzu zai wadace su ita da 'ya'yanta har suyi aure. Daki hudu ne. Mazan kowa daya sai matan a guda ita ma a daya. Takaicinta daya ta gama ginin daidai lokacin da shi ma Alh. Tahir ya gama tsantsara gida na kece raini. Kafin yasa ranar tarewa take so ta karbi takardarta ta bar shi da matansa na aure da 'yan matansa na titi.
"Khadija" Anti Zuwaira ta kirata a hankali da sigar laluma "idan kun rabu kin san da wa zaki hadu a gaba? Yawancin maza haka suke sai dai na wani yafi na wani. Ga 'ya'ya har hudu tsakaninku. Me zaki ce musu shi ne silar rabuwarku? Abin da hakuri bai bamu ba Khadija rashinsa ba zai bamu ba. Na isheki misali. Tun da sauran kuruciya na fito amma miji yaki samuwa. Ke banda tsoron Allah da sai na fada wani hali. A yadda nake ji yanzu ina dana sanin kai kararsa har aka rabamu."
Khadija ta dakatar da ita da cewa "dukan Anti Zuwaira? Yanzu har kina nadamar fita daga gidan wanda ya miki dukan da ki ka kusa rasa rayuwarki?" Da dan karfi ta ce "ba dole maza suke cigaba da cusgunawa mata ba. Suna yi muna turewa kawai saboda kar a kiramu zawarawa ko a rabamu da 'ya'ya."
"Khadija wace uwa ce mai hankali zata so barin 'ya'yanta a gidan da ita ta kasa zama?"
"Haka ne. Nima zamansu nayi domin dasu ya yi min barazana a lokacin."
Anti Zuwaira ta ce "yawanci duk hakurin da muke yi kenan. Fight to save your marriage and your husband."
Kuka mai ciwo Mami Khadija ta fashe dashi tana jin zuciyarta tana tukukin bacin rai "wane auren? Wane mijin? Anti da idanuna ba labari ba na kama shi da Nasima. Har yau ..." ta fada tana dukan kirjinta dake suya "ban manta da hoton da na gani ba. Zama gida daya dasu muna kallon juna tsayin shekarun nan ya isheni bala'i. Ko matarsa ce na fada musu daki ya ya zanji ballatana mai'aikina yarinyar da ta bada shawara aka cire min mahaifa! Bai kuma tsaya nan ba na kuma same su suna rigima akan kanwarta da ya kai daki. Gasu nan duk ya ajiye a gidan amma har yanzu bai daina yawon bin mata ba. Mutumin da ya ce ya ji ya gani akan sabon Allah din ne zan wahalar da kaina wurin kwatowa? To na kwato shi daga hannun wa? Shi ne fa wanda ya kamata a dinga neman tsari da haduwa dashi. Na riga nayi masa alfarma a idon 'ya'yansa. Banda Suhaib babu wanda ya san halinsa a cikinsu. Rashin abin rike kai da 'ya'ya ke sa mata daurewa suyi ta zama to Alhamdulillah naci moriyar wannan zama. Wai Anti har kin manta silar haduwa da dalilin amincinmu? Kin san komai Anti Zuwaira ki daina bani shawarar cutar kaina. Kaddara ta riga ta hada jinina da nashi mun haihu amma wallahi ina tsoro. Ina matukar tsoron hakkin 'ya'yan mutane kada ya bibiyi 'ya'yana da Mardiyya. "
Jinjina mata Anti Zuwaira tayi domin ta san cewa Khadija jarumar mace ce. Wata biyar da fara aikinta a jami'ar ABU suka hadu a masallaci. Allah sai Ya hada jininsu daga gaisawa suka kulla zumunci. Lokacin graduation din Sauda da Mardiyya daga JS3 Alh. Tahir ya shirya musu gagarumar walima a gida. Anti Zuwaira ta sami zuwa da 'yan matan 'ya'yanta su uku. A ranar Alh Tahir ya kyalla ido yaga babbar mai suna Siyama. Bai san 'yar waye ba shi dai ya ganta a wurin taro. Sai da ya san yadda ya yi ya nemi nambar wayarta. Yarinya ita ma bata san waye ba ya soma kiranta a waya da fuskar soyayya. Tafiya na gaba ya fito da maitarsa fili ya dinga tura mata kazaman sakwanni. Da yake Allah Ya kareta kuma akwai tarbiyya da kanta ta nunawa mahaifiyarta. Ita kuma ta kwafi nambar tunda bata tare da mijinta washegari a wurin aiki ta nunawa Mami Khadija. Hankalinta duk ya tashi tana tsoron kar a bata mata 'ya.
"Ta wace hanya ya kamata mu bullo masa? Idan wani abu ya sameta ta ina zan fara? Ka kwashi shekaru kana tarbiyya da tattali wani mara tsoron Allah Ya wargaza maka."
Tausayi ta bawa Mami Khadija domin ta shaida jajircewar Anti Zuwaira wurin tarbiyar 'ya'yanta.
"Bani nambar na kira shi."
"Keeee, raba kanki. Wai baki ga messages din da nayi miki forwarding ba? Mutumin nan da gani kwararren dan iska ne. Da aurenki kada matsalata ta janyo miki jangwam."
"Tsorata shi zan yi in ce mun yi bincike a kansa zamu turo masa 'yan sanda idan ya sake kiranta."
Kamar da wasa ta saka nambar a wayarta. Suna bai fito ba tunda Alh. Tahir bai taba kiran matansa da layin ba.
Ringing biyu ya dauka a zatonsa cikin 'yan matan da yake bawa nambar ce.
Kashe murya ya yi yana wani jan haruffa irin na kwararrun 'yan bariki "Hello baby girl."
Bata gane shi ba a lokacin ta ce "babar Siyama ce yarinyar da ka ke ta yiwa barin kudi. Idan baka rabu...."
Maimakon ya ja bakinsa ya katse kiran saboda mamaki da kaduwa sai cewa ya yi "Khadija?" Da ainihin muryarsa.
"Abban Suhaib?" Ita ma ta ce nata mamakin ya ninninka nashi. Anti Zuwaira sai ta matso kusa da ita. Jikinta ya yi mugun sanyi kamar anyi mata wanka da ruwan kankara haka. Kukan ma da take jin zai kawo mata salama kasawa tayi.
"Abban Suhaib abin naka har ya kai kan 'ya'yan kawayena?"
"Tsaya kiji Khadija" ya ce a gigice.
"Kaji tsoron Allah kada watarana abokan shashancinka su turawa naka 'ya'yan irin kazantar da ka turawa 'yarta. Ka kiyayi ranar da zaka ji inama baka zo duniya da lafiya ba bare ka dinga lalata 'ya'yan mutane." Kif ta ajiye wayar.
Anti Zuwaira ta matso kusa da ita a tsorace "mijinki ne? Babansu Farha ne?"
"Shi ne" ta ce a hankali sai ta yunkura kamar za ta tashi ta fadi yaraf a kasa. Anti Zuwaira taga tashin hankali muraran a ranar. Ta zata Mami Khadija ta cika ra dinga girgizata. Ganin abin yafi karfinta ta fita ta kira abokan aikinsu. Basu jima ba aka kawo ambulance daga asibitin koyarwa na Shika. Ma'aikatan su ma da fari sun zata ta rasu sai daga baya ta numfasa da karfi.
Shabe-shabe da hawaye Anti Zuwaira ta rungumeta tana kuka. A asibiti likita ya ce jininta ya hau sosai saura kadan ta sami stroke (mutuwar barin jiki).
"Kar ki bari ciwo ya kassaraki Khadija. Idan kina da damuwa ki fada min, ko bani da maganinta da shawara zan tayaki jimami. Barin kashi a ciki baya maganin yunwa. Ki dinga fadar damuwarki don Allah."
Cikin kuka Mami Khadija ta ce "damuwar ina auren mijin da bai dauki zina a bakin komai ba saboda rashin tsoron Allah?"
Ita kuka Anti Zuwaira kuka. A ranar suka kulla aminta. A yau kuma Mami Khadija ta gama shirin ba za ta kara kwana a gidan Alh. Tahir ba da aure ko babu.
Hasiya ce mai zuwa duk satin ta duba lafiyar Innayo. Bata tafiya sai tayi mata miyar sati da girkin da zata ci ranar sannan ta gyara mata daki ta wanke bandaki. Ba don Innayo din bata son ganin su Ummi ba da su ne zasu dinga yi mata aikin. Salima da Maimuna kuma kamar hadin baki kananun 'ya'yansu ne mata. Manyan duk maza ne. Na Uwani da Zara kuma sai sallah sallah suke zuwa. Munzali ya yi gyara a gidan yanzu kowace mace tana da bandaki a cikin dakinta. Asabe bakincikin kamar ta mutu da ya ce zai hada da bangaren Innayo. Gori kuwa har ta gaji da damuwa ta saba.
Kwana na uku kenan ciwon hakori ko bacci baya barin Innayo. Tunda Hasiya bata zo ba ta san cewa dole matsala ce ta taso mata. 'Tana can tana bautar 'ya'yan miji' ta ce a zuciyarta. Wayar da Hasiyan ta saya mata ta dauka ta kira Maimuna da sanyin safiya.
"Shallo, shallo Memuna kina jina?" Ta ce da kyar hannunta dafe da mukamukinta bangaren dake ciwo.
A dan tsorace saboda ganin wayar ta sammako Maimuna "Innayo ina kwana?"
"Lafiya kalau. Ina mazajen nawa marasa cefane?" Ita ma ta amsa murya a sake.
Da dai Maimuna ta tabbatar ba matsala bace sai ta saki rai suka gaisa sosai. Da tayi tunanin ko wani abu mara dadi ne ya faru a gidan. Suna gama gaisawar dama shiri take ta ce
"Innayo Doguwa zamu tafi yanzu. An yo waya Iya (surukarta) ta zame a bayangida"
(Nima ciwon hakori nake Memuna) Innayo ta furta a zuciyarta. A zahiri kuwa addu'a da fatan sauka lafiya tayi mata. Suna gamawa ta kira Salima. Mai rakata asibiti take nema cikinsu.
Mijinta ne ya bata wayar tana gaban murhu sai fama da hayaki take za ta dumama tuwo.
"Ungo Innayo ce ke kira. Ki dauka ki tambayeta dubu goman da na ce miki. Banza karbi mana."
Tsuke baki Salima tayi domin idan tayi magana kuka ne zai taho. Sosai Hasiya ke taimakon 'yan uwanta da mahaifiyarsu sai dai samun nata ita ma ba wani mai yawa bane. Ita Salima ta san yanzu Innayo da Hssiyan ta dogara. Mijinta kuwa kamar an kwashe masa albarka. Aure har yau bata taba jindadinsa ba saboda mahaifinta bai saya mata mutumci ba. Ta kuma kasa fadawa Innayo saboda kada ta cigaba da tayar mata da hankali.
Murya can kasa ta amsa wayar bayan ya zungure mata keya "Innayo..."
"Ya naji muryarki a shake Salima?" Ta amsa a firgice.
"Da ciwon kai na kwana. Yanzu ma nasha magani amma bai sauka ba."
Mijin nata yana jin mai take cewa ya damki dankwalinta wanda ya hada da gashinta ya matse iya karfinsa. Haushi kamar ya rufeta da duka saboda taki nema masa kudin zuwa caca.
"Sannu Salima. Zan fita idan na dawo zan biyo gidan naki."
Uwani da Zara ne suka rage bata kira ba. Gabanta har dan faduwa ya yi da tayi tunaninsu. Ita ta haifesu amma kalaman da suke yi mata ke sa bata yawan kiransu. Duk da haka a gefe suna nan cikin zuciyarta. 'Yan uwan Innayo mata kaf suna kauyensu a karkashin karamar hukumar Garunmalam. Akwai kadan cikin 'ya'yansu dake aure ko kananan sana'o'i a Kano. A ganinta nemansu su rakata asibiti tamkar kwayewa kanta baya ne.
Wurin Alh. Rabi'u taje neman kudin ganin likita ya ce babu. Kudin da Hasiya ta bata satin da ya wuce tayi barka dasu. Don kokari sai ta bayar da duka ta ce wai gudunmawar 'ya'yanta ce.
Ba za ta iya zama da ciwo ba. Ruwan alwala ma da ya shiga bakinta da asuba ta kusa sakin fitsari saboda azaba. Shiryawa tayi ta tafi asibitin Sir Sunusi inda Uwani ta kai matsayin Metron (matron) a bangaren karbar haihuwa. Fatanta dai Allah Yasa tana nan tayi mata jagora bangaren hakori a duba mata.
Nisan tafiyar zuwa asibitin wanda yake kan titin Hadeja daga unguwar Dala sai mazauni ko wanda ya san Kano zai gane. Adaidaita sahu ta shiga ya cajeta kudi mai tsoka kuwa saboda nisa da goslow. Yana sauketa a bakin gate ta tambayi bangaren haihuwa guda cikin masu gadin ya nuna mata. Tana tafe tana jin yadda duk taku daya sai kunnenta ya amsa na bangaren hakorin.
Wasu nurses ta gani su hudu a bakin kofar wurin ta duka ta gaishesu saboda ganin girman masu farin kaya da mutanenmu ke yi.
" 'Ya'yan nan don Allah Uwani nake tambaya. Wata 'yar jika-jika. Ta ce min a bangaren nan take aiki."
Zaro idanu suka yi suka hada baki wurin cewa "Matron Uwani bala'i"
Daya ta ce "Iya in dai mai haihuwa ki ka kawo gara kawai ki bi tsarin asibiti kar ki daka Metron dinnan."
Innayo taji jikinta ya yi sanyi da kalaman da ake fada game da 'yarta. Ta tambayesu "akwai matsala ne ta bangarenta?"
"Ai ba kya ji mutuwar sarki a bakinmu ba. Zamu fada mata idan mun ganta" suka yi gaba abinsu.
Zaman minti ashirin a karkashin zafin rana da azabar ciwo Innayo tayi kafin Allah Ya kawo Uwani daga dakin hutunsu.
Taku daidai take yi cikin kasaita ta yatsina fuska ta ce "Wace ce aka ce tana nemana?"
Innayo ta daga kai da kyar. Bata san da yadda za ta kwatanta ciwon da take ji ba. Hasiyanta bata san da ciwon hakorin ba. Ita kuma taki fada mata saboda ta san irin nauyin dake wuyanta.
Uwani na ganinta ta karaso da sassarfa. Idanunta basu gane mata canjawar fuskar mahaifiyarta saboda kumburi ba. Ita dai kada wani ya gansu tare duk masu tsoronta cikin abokan aikinta su rainata.
"Innayo lafiya? Me yasa ki ka zo nan maimakon ki kirani a waya."
"Wurin hakori zaki kaini Uwani. Kwana biyu ko runtsawa bana iyawa."
Murya a sama sama Uwani ta ce "ni dai da kin kirani. Nan fa wurin aikina ne. Muna ta kokarin dakilar da neman alfarma da abokan aikinmu kan yiwa 'yan uwansu yanzu ni kuma zaki sani."
"Nima ba alfarma nazo nema ba. Wurin za ki rakani sai ki kara min kudi saboda sayen magani da ganin likita. Mai adaidaita baki ga yadda ya cajeni ba ya cinye kusan rabin kudin komawa gida gashi na so biyawa duba Salima"
Dariyar takaici Uwani tayi "Innayo kenan. Ki ce kudi ki ka zo karba. To ni wallahi haka na fito sikau don ko na man mota ma sai na ranta. Wata ya yi nisa."
"Uwani" Innayo ta kalleta ido cikin ido wanda hakan ya dan razanata "idan nayi miki baki wallahil azimu sai ya biki. Na bi uwata har ta koma ga Allah. Don Ya jarabceni da haihuwarki ba zan butulce maSa ba. Ke dai ki kiyayi hudowar rana da faduwarta. Shiga ki kawo min kudin ganin likita shashashar banza."
Tunda ta taso kusan yau ta taba jin Innayo tayi mata fada na gaske. Ranta a jagule ta koma ciki ta dauko dubu hudu ta kawo mata.
Ita kuwa Innayo sai taji tsoron kar fushinta ya zama silar mummunan abu ya sami Uwanin. Fatan shiriya ta dinga yi mata a zuci da cewa ta yafe mata. Tana bata kudin ta ce
"Allah Ya yi muku albarka Ya shirya min ku."
Juyawa tayi ta tafi Uwanin ta biyota ta ce "koma bakin aikinki gida zan koma."
Da yake bata da tunani sai ta koma tana fadawa kanta ai dai tayi nata kokarin. Innayo kuwa karkashin wata bishiya ta samu ta zauna ta kira Hasiya.
A duke take kan Abbas yana amai amma ganin wayar ta Innayo ce ta amsa da sauri.
"Hasiya"
Sai kuka.
Anti Hasiya bata san dalilin kukan mahaifiyarta ba amma tana jin kukan ita ma ta fara.
"Innayo gani nan zuwa. Daina kukan. Me ya faru?"
"Ki zo inda yayarku take aiki."
"Gani nan" ta ce tana mikewa tsaye a gigice.
(Uwa ta kira ki ta ce yi min kaza sai ki ji a ranki ta takuraki. Bata san uzurinki ba. Ko ta manta aure ki ke kina karkashin ikon wani? Allah Sarki...ita ma baki san uzurinta ba. Kila a wannan lokacin ke dai ce za ki iya kawo mata agaji. Kila kuma kulawarki take mararin samu. Kila kunya take so ki fitar da ita. Kila ajizancin da aka san dan Adam dashi ne ta gwada a kanki. Kila...Kila...ita dai uwa uwace ko da ta buzuzu ce.)
GOMA
AYA GOMA.
"Abu, Abu...Ke Abu!"
Da dan karamin gudu Abu mai'aikin Zara ta shigo dakinta ta sami wuri ta dan durkusa. Kafin ma ta soma yi mata fadan da ta saba ta ce,
"Ayi hakuri muna gyaran bangaren Hajiyan Fatakwal ne ban ji kiran da wuri ba."
Maganar kuwa ta sake fusata Zara wadda ke zaune akan gado ta dora kafafu akan filo saboda taruwar jinin da suke yi "amma ai kin san yau ba girkina bane saboda haka ba aikin bangarena bane gyara mata wurin zama."
Gyada kai Abu tayi bata ko mamakin halayyar uwardakinta yanzu.
"Ayi hakuri dai. Na kamawa Gaji ne saboda baki da ...."
Da hannu Zara ta dakatar da ita "ni ba surutu na tambayeki ba. Ga leda nan a kasa ki miko min."
Da azama ta dauko ledar ta mika mata sannan ta fita daga dakin. Tana zuwa bangarensu na masu aiki suka tuntsire da dariya. Duk sun san bakar kyuya da son jiki irin na Haj. Zara. Ko kadan bata son motsa jikinta a dole ita matar Alhaji. Komai sai mai'aiki tayi mata. Ba komai bane dalilinta na yin haka illa son nesanta kanta da tunawa da asalinta. Ba za ta ce ga wani lokacin kirki da Innayo ke zama da suna gida. Kullum ita ce karshen bacci kuma farkon tashi kuma har yau bata huta ba. Ita kuwa za ta mori arzikin mijinta son rai. Ba don shi din ma ba mai son bada kudi bane da ta fi haka fantamawa. Tsarin Alh. Unais shi ne wadata iyali da duk kayan jindadin rayuwa amma kafin su ji kudi hannunsu sai a dade. Da yake amaryarta ta fito daga gidan arziki ko kadan bata damu ba. Ita kuma girman kai da gudun asali sun hanata nemawa mahaifiyarta agaji. Aurensu da wata biyu mahaifinsa ya fitar da zakka. Da kansa ya tambayeta idan babu laifi a bawa Innayo duk da ya kula ba wani damuwa tayi da ita ba.
"Allah Ya sauwake. Sai kace almajira? Ko so ka ke 'yan uwanka su cigaba da raina ni?" Ta zauna a kusa dashi "don Allah kar ka taba karbar komai ka kai gidanmu. Idan zance ya zagayo ni ce darajata za ta zube a idanunsu."
Haka take zaune duk abin da take so indai bai saya ba bata yarda ta tambaya. A haukanta duk ranar da ta tambaya zai zama kamar ta amince ita din 'yar talakawa ce. Wata rana zai iya goranta mata ko kishiya ko wani a danginsa.
Ledar zazzage a gefenta ta karewa kayan ciki kallo. Turaruka ne da suka amsa sunayensu har guda goma.
"Ga turaruka ki zabi biyar ko kuma ki zuba duka a akwatin zuwa asibitin. Bana so ko da wasa a dauki dana ace anji wani abu ba kamshi ba"
Ta tuna kalaman Alh. Unais lokacin da ya ajiye ledar da zai fita kasuwa. Daya bayan daya tabi ta fesa domin tantance kamshinsu. Ta gama ta shafa cikinta tana murmushin jindadi. Sai yanzu a haihuwa ta shida da ake jira ko yau ko gobe likita ya tabbatar musu da cewa da namiji ne. 'Yan matanta biyar na kishiyarta uku. Alh. Unais ya kwallafa rai akan samun namiji. Tun cikin yana wata hudu da aka fada musu mene ne yake bata kulawa ta musamman. Babu abin da ta nema ta rasa. America ma yaso kaita haihuwa amma Hajiyar Fatakwal mahaifiyarsa ta h
ana. A cewarta lokaci ne na nunawa dangi ya sami magaji. Idan sun bar kasar dokin dan zai iya raguwa a zukatan dangi.
Abubuwan alkhairin da Zara ta samu a tsukin lokacin ita kanta bata san adadinsu ba. Ga dan Adam da son idan yana cikin farinciki ko samuwa ya sami mai taya shi murna. 'Yan uwanta da ta wofintar take kewa sosai. Su take son burgewa su tayata murna amma da kunya ta fara binsu yanzu. Uwani ce dama suke mu'amala to ita kuma rokon tsiya gareta. Ga aiki ga albashi amma kullum kiran babu da tambayarta abubuwa take.
Ba don taso ba ta tashi ta bude wasu akwatuna da suke shakare da sutura sababbi marasa dinki. Ciki harda na barka da take samu na haihuwa da kuma na wurin mijin da abokansa. Tunda hannunta a kame yake irin na Alh. Rabi'u ba kasafai take kyauta ba. Idan barka ta tashi kuma mijinta yana saya ya bata ta kai. Wasu lesuka ta dauko masu tsada amma wadanda aka ci yayinsu kimanin shekaru shida da suka wuce lokacin haihuwarta ta hudu. Komai na akwatin ma na barkar yarinyar ne wadda bayan haihuwarta tayi rashin lafiya. Shi yasa bata diddinka kayan sosai ba. Guda hudu ta zabo za ta bawa Innayo, Hasiya, Salima da Maimuna su dinka su saka ranar sunan danta. Tana zuba su a leda ta tuno bala'in Hasiya ta karo atampa daya za ta karawa Innayo da ita. A kalla babu mai rainasu wannan karon ba kamar sunan 'ya'yanta na baya ba. Haihuwa ta biyar da kanta ta ce musu babu taro don kawai kada a maimaita irin na da. Basu zo ba kuwa aka ci suna aka watse. Kowa ya yi cigiyar danginta sai ta ce Innayo ba lafiya.
Wayarta ta janyo ta kira Uwani bayan ta kwanta saboda bata jurar aiki. Lokacin kusan rabin awa kenan da rabuwar Innayo da Uwanin a cikin asibitinsu. Ranta duk a jagule saboda rashin nutsuwar da ta saukar mata sakamakon rashin kyautatawa mahaifiyarta. Ganin wayar Zara sai ta saki ranta ta dauka da murmushi.
"Haj. Zara ikon Allah. Matar Alh. Unais uwar Maryama."
Zara ta murmusa "duk ni kadai Yaya Uwani?"
"Kin isa ne kanwata."
Uwani ta saba yi mata bambadanci saboda kwadayin samun wani abu a jikinta bata san irin zaman da take ba.
"To ni dai ya ku ke?"
"Lafiya kalau. Muna nan zamu fara shirye shiryen tafiya Saudiyya. Allah Ya yi Hajjin bana mun amsa kira."
Dan yamutsa fuska Zara tayi saboda bata son yawan surutu kuma ta san shi Uwanin zata yi mata.
"Na tayaki murna. Allah Yasa ayi maqabuliya."
Uwani ta murmusa amma da dukkan gaskiyarta ta ce "Amin. Zan zo karbar 'yan riyalan da ku ke dawowa dasu dai."
"Hala kin manta na fada miki watan nan zan haihu?"
Jin kamar ranta ya baci Uwani ta kwantar da murya tana tambayarta lafiyarta. Basu dade ba fushin ya gushe Zara ta labarta mata tanadin da maigidan yake yiwa haihuwarta.
"A Afficent za ayi suna. Ya biya kudi ko da sunan ya kama rana daya da masu biki zai biyasu kuma ya kama musu wani wurin. Ni abin da yasa na kira ki dama kaya ne za ki zo ki karbarwa su Innayo"
Fadin maganar ya yi daidai da shigowar Hajiyan Fatakwal falon Zara. Isowarta garin kenan ta taho bangarenta ta duba ta taji tana waya. Zama tayi a kujerar da tafi kusa da kofar dakin tana dan danna kafafunta da zummar jira ta kammala.
"Bana so wannan karon su zo a tsummokara ayi ta kallonsu."
Uwani tayi 'yar dariyar kalmar tsummokara sannan ta fada mata zuwan Innayo din asibitinsu.
"Wai ciwon hakori take kuma na ce muje a duba taki."
"Kar ma ki damu indai ciwon hakori ne da kanta za ta nemeki. Ba ma dole su yi ciwo ba. Ni kaina wallahi ina kyamar kalar hakoran nan nata." Zara ta fada tana bata rai.
"Kin san da ciwon sai da ta karbi dubu hudu a hannuna. 'Yan gulmar abokan aikina suka dinga tambayar wace na bawa kudi ni kuwa na ce matar makocinmu."
Haushi ya kama Zara. Ko me yasa Innayo ta auri mutum irin mahaifinsu bata sani ba. Hatta sauran 'yan uwanta tana bakincikin yadda suka auri talakawa. Ba dole su lalace ba. Ace maza ba za su fita su nema yadda masu kudi suke yi ba. Kalaman Uwani basu dameta ba bare su bata mata rai.
"Ni dai ki zo ki karbar musu su dinka da wuri don wallahi INA JIN KUNYAR NUNA INNAYO A MATSAYIN MAHAIFIYATA. Duk ta tsufa fiye da shekarunta. Rannan da muka je da su Maryam fa tana kiransu kin zuwa suka yi. Da muka fito Mas'uda harda amai kuma duk akan fatar jikinta da kalar hakora. Daki sai wani bashi bashi ni kaina da kyar na dinga hadiyar yawu."
Hajiyan Fatakwal mamaki kamar ya kasheta a zaune. Tuni ta manta da matsar kafa ta kasa kunne da kyau tana ji. Kalaman karshen ne suka tunzurata ta tashi ba shiri ta bankada labulen dakin ta shiga. Ba shiri Zara ta katse wayar ta tashi tarbarta harda su runguma.
"A'a kar ki kuskura ki tabani" cewar Hajiyan Fatakwal tana ja da baya "ina naga mutumcin da zai sa ki kaunaceni da zuciya daya tunda ki ke kunyar nuna uwar da ta haifeki."
Baki daya jikin Zara sai ya hau rawa. Hajiyan Fatakwal kuwa ta dinga surfa mata ruwan bala'i.
"Da wannan mummunar zuciyar a kirjinki ki ke haifa min jikoki? Wannan ba don nima a tsaye nake ba kila da Unais ne zai ce shi ma yana kunyar nuna ni."
"Hajiya don Allah ki yi hakuri" Zara ta furta a hankali tana kuka. Kukan tsoron kada surukarta ta tsaneta ko tayi mata iyaka da daular gidan.
"Wa? Ni? Ai ba ni zaki bawa hakuri ba."
Ficewa tayi tana mamakin wannan abu. Ka haifi da a cikinka ya dinga cewa yana kunyar kasancewarka uwa gareshi. Tabbas ta sani wasu iyaye matan suna abin da zai sa 'ya'yansu gudunsu musamman hali mara kyau. Amma wannan fa zancen kalar hakori da yamushewar fata take yi. Bangaren da take zama idan ta zo gidan ta tafi tana ta juya zancen a zuci.
Anti Hasiya ta tarar da Innayo ba yadda take saboda ciwo. A daidaita sahun da ta shigo ko tsayuwa bai gama ba ta diro saboda sauri.
"Hajiya kudinki dari biyar."
Sai a lokacin ta ankare da yadda ta fito daga ita sai waya babu jaka. Salati ta soma yi shi kuwa zai fara tijara Innayo ta taso da kyar ta mika masa dubu daya cikin kudin da Uwani ta bata. Chanji ya mika musu ya tafi yana surutan samari marasa kunya.
Ido cike da kwallar kumburin fuskar Innayo Anti Hasiya ta ce "Da kudi a hannunki ne? Na manto jakata garin sauri."
Abin da take dashi ta nuna mata sai Anti Hasiyan ta ce bari ta kira Uwani tazo.
"Kyaleta Hasiya. Bana ma son ganin likitan a wannan asibitin."
Anti Hasiya bata matsa mata ba ta ce "to bari na ranci kudi a wurinta sai mu wuce asibitin Nasarawa."
Suna haka sai ga wayar Honorable ya kira ya fada mata ta manta jaka. Da ta gaya masa halin da Innayo take ciki ya ce zai turo Ayaah ta kawo mata tunda asibiti dole sai da kudi.
"Ka ce ta wuce Nasarawa sai mu hadu a can"
Sai da ta gama wayar ta tambayi Innayo me Uwani tayi mata ganin har lokacin tana kwalla. Da kyar ta iya fada mata tana zubar da hawaye. Zuciya na zafi ta juya ta tambayi wani hanyar wurin karbar haihuwa ya nuna mata. Innayo na kiranta taki tsayawa. Salama tayi a wurin ko amsawa ba ayi ba ta banka kai ciki.
"Uwani Rabi'u nake nema" ta ce da wata 'yar matashiyar Nos a hasale. Teburin nurses din take duka da hannunta irin na wanda hakuri ya yiwa karanci
"Metron Uwani tana break sai anjima za ta fito."
Anti Hasiya kawai sai ta daga murya "Uwani Rabi'u. Uwani..."
Shiru tayi bayan katse wayarsu da Zara tayi tana son gaskata ita ake yiwa wannan kiran na rashin girmamawa ko kuwa.
"Uwani..."
'Kamar Hasiya'
Da sauri ta fito ai kuwa ta hango Hasiyan ta hade girar sama da ta kasa. Take takenta ta san indai ta kyaleta sai ta zubar mata da mutumci a wurin. Ga abokan aikinta sun firfito jin gulma.
"Muje waje Hasiya" ta kama hannunta za ta ja ta taji ta coge.
"Ba inda zani. Kudi za ki bani na kai Innayo asibiti."
Daure fuska tayi saboda ta san cewa ta bawa Innayo kudi ita ma Hasiyan sarkin nuna tafi kowa jinkai ba sai ta kawo ba.
"Wata ya yi nisa ba..."
Da yatsa Anti Hasiya ta nunata "wallahi ki ka kira min babu sai na tara miki mutane a wurin nan."
Kirjinta ta nuna tana kokarin danne fushinta kada su yi fada a wurin "Hasiya ni fa yayarki ce."
"Indai ke yayata ce to lallai Munzali (sakonta ne a haihuwa) da su Fati (wadanda suka hada uwa da marigayiya A'i ma yayyena ne)" ta kare maganarta da jan tsaki mai sauti.
Kasa kasa da murya Uwani tayi, dan kada a ji. Ta kula gaba daya yawancin abokan aikin kamar su matso inda suke dan tsabar son jin gulma.
"Ni kike gayawa magana Hasiya?"
Hasiya ta ce "dake nake Uwani. Kinga ki dauko kudi ki bani na kai Innayo asibiti idan kuma ba za ki bayar ba sai na ranta a wurin abokan aikin ki."
Uwani na jin haka ta sha jinin jikinta dan ta san ba ko shakka wannan ba karamin aikin Hasiya bane aikata abun da ta fada. Da sauri ta dauko jakarta, ta zaro dubu biyar ta mika mata. Hasiya ta karba ta jujjuya su cike da takaicin hali irin na yayarta.
"Indai dubu biyar ce nima ina da abin da ya fita, don na yi fitowar gaggawa ba na manto jakata a gida. Ki bani dubu goma, da zarar na koma gida zan aiko miki kudin ki in sha Allahu."
Haka Uwani ba yadda ta iya ta zaro wasu biyar din ta bawa Hasiya, tana so ta jaddada mata ita bashi ta bayar ba kyauta bane, amma kuma tana tsoron ta tabo Hasiya kada tayi mata tsiya a gurin nan. Haka nan ta hakura ta hadiye zancen a ranta ta juya da niyyar barin wurin. Batayi taku uku ba Hasiya ta kasa hakuri da wannan halin ko in kulan nata. Sautin muryarta a karye ta ce mata
"Yanzu Uwani ba za ki zo ki ko kallon halin da take ciki kiyi ba?"
Kafin ta bata amsa ta fice abinta ta nufi inda ta baro Innayo. Wasu a cikin abokan aikin Uwanin har sun riga su yin gaba, suna kallon inda Hasiya ta nufa suka ga ta riko Innayo nan suka fara kuskus. Daya daga cikin su wacce Innayo ta fara tambayar Uwani lokacin da ta zo asibitin ta ce,
"A'a wannan ba matar nan bace ta dazu da ta zo neman Metron Uwani?"
Hasiya ta juyo ta kalle ta, ta ce "mata kuma? Ita matron din taku bata gaya muku alakar su ba kenan."
Uwani ta cika tayi fam, ranta ya gama kai kololuwa wurin baci. Shike nan an kwaye mata baya a idon makiya.
Ita ko Nos da zakuwa ta tce "a'a bata fada mana ba."
Hasiya ta dubi Innayo taga kiris ya rage ta fashe da kuka. Girgiza mata kai take yi don tayi shiru gami da yafito ta da hannu tazo su tafi.
"Ba ma tafi ba Innayo ga abokan aikin 'yarki suna son saninki" ta matsa jikin Innayo din ta dafa kafadarta "ga MAHAIFIYARMU. Uwani yayata ce uwa daya uba daya."
"Ban gane ba fa. Ke da wa kenan?"
Daya daga cikinsu tai mata tambayar cike da mamaki.
Hasiya ta ce "ni da matron din ta ku mana." Ta cuna Uwani da baki. Ta juya tai tafiyar ta.
Nan ko wuri ya kaure da salallami, suna tafa hannuwa,mata an samu abun da ake so.
Hasiya na tafiya daya ta yiwa Uwani kallon mara hankali duk da kasa take da ita.
" Matron kika ce mana matar makocinku ce."
Innalillahi wa inna ilaihir raji'un ta iya cewa a zuci saboda kallon mujiyar da wanda ya isa da wanda bai isa ba ke jifanta dashi.
Su kuwa juyawa suka yi kan ka ce meye wannan kusan kowa ya samu labarin abin da ta yiwa mahaifiyarta. Wadanda suka ga Innayo cikinsu sun fahimci bata son asan cewa mahaifiyarta ce duba da yadda take. k
Kana ganinta kaga mutum dake fama da talauci daga yanayin jiki har sutura.
Hasiya kuwa kai tsaye asibitin Nasarawa ta dauke ta suka wuce. A take aka cire mata turame biyun dake azabtar da ita. Anyi mata allurai an kuma bata magunguna. Har suka kammala suka koma gidan can Dala babu Ayaah babu dalilinta ballantana ta kawo mata jakarta da ta manta a gida.
Kunun gyada mai dadi Hasiya ta dama mata ta sha da kyar.
"Ki barni haka ya isa" Innayo ta ture cokalin da ta kawo bakinta.
Tayi kicin kicin da fuska kuwa.
"Allah sai kin kara." Sai kuma ta soma mita "Haka kawai kina fama da ciwo ki kasa fada min?"
"Da ki ka zo din me ki ka yi banda kunyata 'yar uwarki? Na dauka kin fi kowa jin maganata amma ina...kina kallo ina cewa kizo mu tafi ki ka ki sai da ki ka amayar da cikinki. Mece ce ribarki?"
Hasiya ta saki murmushi "ai kuwa ni ce da riba. Yau an yi jana'izar girman kan Matron Uwani a Sir Sunusi." Sai kuma ta yi dariya ganin Innayo tana murmushi "banda abinki ma dai Innayo meye na damuwa. Ni da nake son ki bani hadin kai mu fara bincike."
Sai da ta kashingida akan gadon da autar tata ta karkarde ta gyara sannan ta ce "na me?"
"Neman 'yarki ta fari. Ina tsammanin wannan Uwanin dai musanyen asibiti ce."
"Kaniyarki"
Fadin Innayo tana son yin dariya ciwo ya hana. A cikin zuciyarta ta dinga rokawa Hasiya albarka tare da fatan ganin zuri'arta. A gefe daya kuwa kukan zuci take yi. Bata san da me ta ragi Uwani da Zara ba da suke gudunta saboda arziki. Ashe wahalar duk da tayi daga ciki har aurar dasu aikin banza ne? Ita Uwani ke kunyar nunawa duniya. Akwai Allah!
Irin kwalliyar da Ayaah ta sha ta zuwa asibiti kai jaka sai ka rantse gidan biki zata je. Bikin ma na masu kumbar susa ko 'yan karya. Idan ka ganta ba za ka ce tana tare da damuwar rabuwa da masoyinta Rabeel ba. Ga haushin Babansu ya rasa wanda zai aika kai kodaddiyar jakar Anti Hasiya sai ita.
"Idan nayi aure naga mai iko dani sama da mijina" ta fadawa kanta ta.
Tun fitowarta wani saurayi da ake kira Dangwarzo da suke harka dasu Rabilu ya kira Danliti a waya. Dama a sanadiyarsa Rabilun ya hadu da Ayaah duk da bata taba sani ba.
"Malama Ayaah sai ina" ya ce bayan ya iso kusa da ita.
Yatsina fuska tayi tana fatan kada Allah Ya kawo wanda ya santa ya gansu tare. Ta tsani Dangwarzo tsana mai girma.
"Sai inda ka aikeni."
"Maida wukar ba fada ya kawoni ba. Saukata kenan daga adaidaita na hango ki." Ya nuno mata wani cikin abokansu zaune a cikin dan sahu yana tazar kai "idan sauri kike ki shiga wancan abokina ne direban ba sai kin biya ba."
Kamar ta ce a'a sai kuma ta tuna ya ce ba sai ta biya ba. Tana faman rangwada da zuba kamshi taje ta shige ta fada masa inda zai kaita. Tafiyar minti biyar suka yi ya kira waya yana maganar da bata fahimta ba. Ita dai taji ya ce 'asibitin nasarawa' sai kuma 'idan ciniki ya fada nima zan zo d'ani '.
Danliti ya yi matukar murnar samun biyan bukata wato samun damar ganawa da Ayaah. Motar da tafi kowacce kyau a garejinsu ya dauka ya canja kaya zuwa jampa da wando da ya aro a wurin wanki. Ogansa bai san ya fita da mota ba sab
da girman garejin.
Sun kusa zuwa junction din Dan agundi direban ya dinga taka burki da gangan kamar adaidaita sahun yana da matsala. Ayaah son bati maimakon ta fita ta tari wani sai tayi zamanta. Direban ya fita yana ta 'yan kwale kwalensa nan kuwa Danliti yake jira. Haushi ya fara kama Ayaah saboda wayar Honorable yana tambayar ko ta sami su Hasiya. Mata duk tabi ta asirce musu uba ya tada hankalin kamar tashi babar ce babu lafiya.
Gajiya tayi ta fito bayan kamar minti ashirin daidai da dosowar wata mota da ta dauke mata ido da hankali. Danliti ya rage motar ya tsaya a gefensu ya sauke gilas. Kansa babu hula amma ya taje sumar da ya dan tara ta kwanta. Ta bi fuskarsa da kallo taji gabanta ya doka. Wannan yafi Rabeel kyau. A nutse ta gangara jikinsa da ido ta karewa yadin da ya saka kallo.
"Malam don Allah kwanar Wanzamai nake nema a sabuwar kofa." Danliti ya yi kamar bai ganta ba ya tambayi direban.
Da baki ya yi masa kwatancen karya saboda babu wata kwanar Wanzamai ya ce bai gane ba.
"Ni kuma mashin din nawa ya sami matsala ga fasinja ma ban san yadda zan yi da ita ba."
Sai a lokacin Danliti ya kalli Ayaah. Da gaske ta hadu yadda yake son ganin mace. Kawar da kai ya yi ya ce tazo ya rage mata hanya idan hanyarsu daya.
"Malam ita fa wannan asibitin nasarawa za ta je."
"Sai na sami lada ko 'yan mata?"
Sai a lokacin ya kalli idonta kuma ya yi mata murmushi. Ayaah ta nemi hankalinta ta rasa. Gabadaya zuciyarta ta tafi wurin Danliti har tana hango 'yan dagwai dagwai dinsu suna wasan tsere a idanunta.
Ta manta da Anti Hasiya bare jakarta da ta bari a adaidaita sahun. Jiki na rawa ta shiga gaban motar ta zauna.
Su hudu ne a falon kowa da abin da ya saka a gaba. Mami Khadija ta dinga bin su daidai da kallo tana rayawa a ranta daga yau sai yau anyi an gama. Tunda Mamanta ta amince da kudurinta ba za ta taba yarda shawarar zaman hakuri tayi tasiri a kanta ba.
Alh. Tahir ne ya tara matansa a gabansa amma tunda suka shigo yake danna waya yana doka murmushi. Mami Khadija za ta iya rantsuwa da wata budurwar yake chatting.
Nasima da waya ta shigo a kunne har yanzu bata gama ba. Zancen shiga da fitar kaya ne sai kudaden da suka shafi kasuwancinta.
Jiddo ma selfie take ta kashewa tana dariya idan ta tura. Ko wa take turawa Allah Masani.
Mami Khadija ta girgiza kai. Wannan ba gidan aure bane. Za dai ta zauna har ya gama ya yi musu maganar da yasa ya tarasu.
Chapter 1 · 0% Book details