Part C.
Tsatsuba Book 5 Complete Hausa Novel · about 21 min read
Na Abdul'aziz Sani Madakin Gini
Posting By Abubakar Saleh AlQuyraemey
08138873799 For More Littattafan Yaƙi
.
Duk sa adda na fara wannan kuka sai zalina da mahaifinta sunyi da gaske sannan suke rarrashina na dawo cikin hayyacina wani abin mamaki wanda ya daure min kai shine duk da cewar na rasa hannu daya da kafa daya ko kadan ban rasa karfin damtse na ba da kuma iya yakina don haka duk sa adda muka shiga daji farauta duk muguwar dabbar da ta zo gabanmu take nake gamawa da ita, komai yawan gungun yan fashi kuwa idan mukayi gamo dasu ni kadai nake tarwatsa su, amma zalina da mahaifinta suna taimaka mini saboda sun kware ainun a iya harba kibiya. A lokaci guda kowannansu na iya harba kibiyoyi bakwai sai dai kaga maza na zubewa kasa yayinda tsinin kibiyoyinsu suke ratsa kirazansu, A kwana a tashi sai na sami wata bakwai tare da su zalina ya zamana cewa na shaku dasu ainun musamman zalina wacce komai tare muke yi shimfidar barci kawai muke rabawa. A hakane na fuskanci cewa soyayya ta shiga tsakaninmu amma dana tuna cewa ni fa yanzu masaki ne bani da hannu daya da kafa daya sai na ga cewa idan na nemi soyayyar zalina na cutar da ita. kuma idan na tuna cewa na rasa masoyiyata shadila sai naga cewa ai na gama soyayya a duniya don ba zan taba samun wacce zan sota ta soni ba
kamarta bisa wannan daliline na rinka danne soyayyar zalina a cikin zuciyata kuma duk sa adda naga zata nuna mini soyayyar tata saina bagarar.
.
Ni abinda yake bani mamaki ma shine me zata yi da masaki muna cikin wannan hali ne mahaifin zalina ya kamu da cuta mai tsanani wacce takai shi ga kwanciya, abu dai kamar wasa kullum sai ciwo ya rinka gaba ya zamana cewa ba a samun sauki. Al amarin da ya dugunzuma hankalinmu kenan muka rasa sukuni da kwanciyar hankali ita kuwa zalina kullum bata da aikinyi sai kuka da bakin ciki da kyar nake iya rarrashinta, ba komai ne yake sata
wannan yawan kuka ba sai ganin cewa babu alamar samun lafiya ga mahaifinta kuma ga dukkan alamu ciwon nasa bana tashi bane, wata rana na tashi da sassafe ina shirin tafiya daji domin naje nayi farauta naman da zamu ci da rana a lokacin zalina na can wajan kogon da muke kwana ta dora tukunya akan wuta tana dafa mana abincin kalaci sai mahaifin zalina ya kira sunana a lokacin da nake daf da fita daga cikin kogon. Cikin tsananin mamaki na juyo na dubeshi saboda rabonsa da ya budi baki yayi magana tun daga ranar da ya kwanta wannan cuta, cikin matukar sanyin jiki na karasa daf dashi na tsugunna a gabansa inamai kura mas aidanuna ya shi kuma sai ya kamo hannuna ya dora akan kirjinsa ya dafe hannun nawa da dukkan hannayansa biyu sannan ya budi baki da kyar yace yakai hailur kayi sani cewa wannan ciwo nawa bana
tashi bane mutuwa zanyi kuma a koyaushe wa adina zai iya cika ina neman Alfarma guda daya jal a wajanka alfarmar kuwa itace ina son ka auri zalina, koda jin wannan batu sai zuciyata ta buga da karfi na dubeshi cikin mamaki nace yakai abul zalina ai idan kace na auri zalina bakayi mata adalci ba domin kana sone ta auri nakasashshe koda jin haka sai tsohon yayi murmushin karfin hali ya dubeni cikin nutsuwa yace yakai hailur kayi sani cewa a zahiri kake nakasashshe amma a zuciyarka kafi ta lafiya sannan kuma har yanzu sadaukantakarka da jarumtakarka suna nan basu ragu ba dai dai da matsayin kwayar zarra ina son ka sani cewa yata ta kamu da tsananin sanka a cikin wannan hali da kake ciki na nakasa kaga kenan ashe soyayyarta itace soyayyar gaskiya ka auri yata zalina ko don saboda ka samu zuri ar da zasu ga bayan babban makiyinmu sarki shardas ka sani cewa kowacce mace tana son ta auri namijin da zai iya kare mutuncin ta da rayuwarta koda kuwa shine yafi kowa nakasa a doron kasa lallai ku cika mini burina na ganin bayan sarki shardas wannan itace kadai wasiyyata a gareku, ashe duk wannan bayani da mahaifinta yake yimini zalina dake can kofar kogo tana sauraro don haka sai ta kasa cigaba da aikin da takeyi ta koma gefe daya ta zauna tana ta faman kuka, koda na fito daga cikin kogon dutsen rataye da takobina da nufin na shiga daji don gabatar da farautar sai naga zalina tana ta kukanta..
.
Al amarin da yasa na gane cewa lallai duk taji abinda muka tattauna kenan dani da mahaifinta cikin sanyin jiki na karasa gareta na zauna daf da ita kanta na sunkuye sai na tallabo habarta da lafiyayyen hannun nawa kuma na share mata hawaye muka kurawa junanmu idanu sannan na dubeta nace shin kin amince na zama abokin rayuwarki.
.
Koda jin wannan tambaya sai zalina ta murtuke fuska daga can kuma sai ta rungumeni ta kama kyalkyala dariyar farinciki muna rungume da juna mukaji motsi a bayanmu a firgice muka juya da sauri sai mukaga she mahaifin zalina ne ya fito daga cikin kogon dutsen yana dogara sanda da kyar yana numfashi sama sama.
.
A guje na janye jikina daga cikin na zalina na karasa gareshi na rukoshi na zo dashi wajan zalina itama ta kamashi muka zauna gaba daya sannan ta dubeshi cikin alamun tsananin damuwa tace haba ya kai Abbana yaya kai da kake cikin wannan hali zaka taso kayi tafiya sa adda abul zalina yaji wannan tambaya daga bakin yarsa zalina sai ya dubeta yayi murmushin karfin hali yace yake yata ai dole ne na taso ko don naga abin farinciki na karshe wanda idanuna zasu gani wanda shine amincewar junanku akan aure lallai ina so naga wannan aure naku da idanuna kafin rai yayi halinsa, nan take tsohon ya yiwa hailur bayanin yadda zasu daura auren bisa al adar su kabilar wato kowannansu ya yanki dan yatsansa ya diga jininsa
a cikin ruwa bayan jinin biyu ya gauraye sai kowannan su ya sha ruwan nan take kuwa muka aiwatar da hakan, muka rinka shan ruwan muna kallon juna cikin murmushi har sai da ruwan ya kare kaf.
.
A dai dai wannan lokacine farinciki ya lullube abul zalina ya dubi hailur yace yakai babban gwaro kayi sani cewa yanzu ka zama na zalina kuma zalina itama ta zama taka babu abinda zai rabaka face kaddara ko mutuwa, wannan dama shine manufar shan jinin juna da kukayi, bisa al adar kabilarmu a ranar da miji ya mallaki matarsa babu abinda zasu fara face zuwa daji farauta tare, don haka yanzu saiku tafi sannan da ku ka samo shi zaku kawo a gasa muci muyi walima da farin cikin aurenku, koda
jin wannan batu sai na dubi abul zalina cikin alamun damuwa nace haba yakai abul zalina yaya za ayi mu tafi daji mu barka kai kadai a nan alhalin kana cikin wannan halina rashin lafiya,
.
Koda jin haka sai abul zalina ya dubeni cikin murmushi yace kada ka damu dani lallai zakuje ku dawo kuma ku sameni cikin koshin lafiya da sauki fiye da ko yaushe wannan shine abinda na gani a mafarkina na daren jiya bisa wannan dalili ne ma a yau din nan na sami saukin da har na iya mikewa tsaye na taka kafafuna na fito daga cikin wannan kogo haka dai abul zalina yaci gaba da rarrashinmu har ya samu ya shawo kanmu muka amince da barinsa a wajen amma kafin mu tafi sai da ya rungumemu yana ta dariyar farinciki bayan ya janye jikinsa daga cikin namune mun juya zamu tafi izuwa cikin daji sai zalina ta waigo ta dubeshi take ta hango kwalla a cikin idanunsa.
.
Al amarin da ya dugunzuma hankalinta kenan ta dubeni tace yakai mijina nifa zuciyata bugawa take da karfi ji nake kamar idan muka dawo ba zamu riskeshi a raye ba ni kaina naga alamun hakan a tare da mahaifin nata kuma duk kalaman da yake yi na bankwana ne amma don kada hankalin zalina ya tashi sai naki sanar da ita haka dai muka nausa cikin daji muna waigen Abul siyama shi kuma ya bimu da kallo yana yi mana murmushi har muka kule muka daina hangoshi.
.
A sannan ne kuma muka falfala da azababbn gudu izuwa cikin daji mukayi ta tsala gudu ba sassauci muna neman dabbar dajin da zamu samu babu abinda zai baka mamaki face yadda nake iya gudu ina dogara sanda alhalin kafata guda daya bata da kyau kuma har tserewa zalina nake yi a gudun ni ina rike da takobi ne kuma karshen sandar da nake
dogarawa mashi neita kuwa zalina a hannunta kwari ne kuma ta rataya kwanson kibiyoyin kwarin a bayanta don haka ita bata rike wani makami sai kwari da baka.koda muka nausa cikin daji sai muka rabu ni kuma nayi gaba ita kuma tayi yamma sannan kuma muka baiwa junanmu tsawon rabin sa a akan mu hadu a bakin wani dutse dake can tsakiyar dajin kowannanmu na rataye da kaho a bayansa wanda duk sa adda ya shiga wani hadari wanda ba zai iya kubutar da kansa ba sai ya busashi komai nisan inda yake dan uwansa zai iya jiyowa har yakai mas dauki shidai wannan kaho na sihirine kuma gado ne a kabilar tasu zalina kuma mutum ba zai iya mallakarshi ba face ya kasance dan kabilarsu ko kuma ya auri jinin Kabilar.
.
Bayan mun rabu a cikin daji nida matata zalina sai muka wanzu muna masu neman abin farauta baji ba gani, lokacin da naga na shafe dan dogon lokaci ina neman abin farautar ban samu ba sai hankalina ya dugunzuma ainun saboda ina ganin cewa ai abin kunyane ace a ranar daurin aurena na kasa farauto abincin da zamu ci nida amaryata...
.
Zan dakata nan sai kuma Allah Ya kainu gobe insha Allahu afin nan daga mai ɗebe maku kewa AlQuyraemey nake cewa ku huta lafiya.
Ehm Al amin Ahmed Misau, Guyson ko A square
Ina cikin wannan haline naga wata barewa ta
nufo inda nake cikin azababben gudu gashi dai
barewar ta hangoni a gabanta rike da makami
amma ko shakkar tunkaro ni batayi ba
dada durfafo ni takeyi al amarin da yasa na fahimci
cewar lallai masifar da ta korota ta nufoni don tsira
da rayuwarta ta wuce tawa hadari, ai kuwa ban ankara ba
sai naga ashe wani murjejen zaki ne ya tasota a gaba
tun daga nesa dana hango zakin ya falfalo da azababben gudu
har tashi sama yake saboda karfin gudun nasa
kuma harshensa na zazzagowa waje daga cikin bakins ana gane
cewa lallai
wannan zaki a cikin muguwar yunwa yake
koda naga cewa barewar nan so take ta wuce ta gabana
domin ta tsira da rayuwarta sai na yunkura cikin zafin nama na
daka tsalle sama a lokacin da itama barewar ta daka tsalle da nufin ta shallakeni
muna haduwa a saman na soketa da mashina ta
zama gawa na duro kasa bisa kafafuna barewar
na sakale a jikin mashin nawa, ai kuwa sai wannan zaki
yayi tirjiya a lokacin da tazarar dake tsakaninmu
bata wuce taku goma ba
nan fa muka fara kallon kallo tsakaninmu da murjejen zakin
nazarin da zakin yake yi shine ni zai farwa sannan
ya dauke barewar ko kuwa barewar zai karba
ni kuwa nazarin da nakeyi shine ta yaya zan iya
.Ya kasance shi ba karamin tashin hankali bane
duk da na san cewa na sha yin gumurzu da manyan
dabbobin daji ina samun nasara a kansu sai da
zuciyata ta karaya akan wannan zaki domin ban
taba yin gamo da tsohon zakimai girma da kwarjinin wannan ba
nikam tuni na gama aiyanawa a raina cewa
duk rintsi ba zan iya sallama barewar ba ga wannan
zaki koda hakan na nufin zan rasa rayuwata
kawai sai na cake mashin nawa a cikin kasa
wanda ke dauke da barewar sannan na buda hannuna
mai rike da takobi ina mai
gyara tsayuwata kuma na koma gefe daya na tsaya ina
mai baw azakin zabi tsakanin barewar da ni kaina
ya zabi wanda zai fara afkawa
take zakin yayi wani irin
gurnani mai ban tsoro wanda yasa hantar cikinsa ta kada amma da na tuna cewa
amaryata
zalina na can fa tana farauta a cikin wannan daji
wata kilama yanzu ita ta dade da samo nata abin
farautar taje inda mukayi zamu hadu ta zauna
tana jirana sai naji zuciyata ta kekeashe ga barin dukkan tsoro.....
Kamar hadin baki sai nida zakin muka falfalo
da gudun tsiya izuwa kan juna muka dako tsalle
sama a tare kafin nayi wani yunkuri na saran zakin
ko sukarsa da takobina tuni shi ya sa kirjinsa ya
bangajeni
ai kuwa sainaji kamar aksusuwan kirjina sun
kakkarye nayi can baya da karfi bayana ya gwaru
da jikin wata bishiya na fado kasa a matukar galabaice
ina aman jini ta hanci da baki, koda zakin yaga
halin da na shiga sa adda shima ya duro kasa sai
ya wangame baki ya kwalla wani uban ruri anda
ya fi wanda yayi a baya mai nuna kuranta kansa
da dai yaga na kasa tashi ina ta numfashi sai
ya wuce ta gabana ya daka tsalle da nufin ya suro
wannan barewa dake sakale a jikin mashina
ni kaina ban san yadda akayi ba na sami gagarumin
karfi da kuzari kawai gani nayi na mike tsaye zumbur
na daka tsalle daga inda nake na rungumo zakin
kafin bakinsa ya cafi barewar mun fado kasa tim !
Nan fa muka kama kokawa a kasa muna ta birgima
idan zakin ya danneni yana kokarin kafa min
hakoransa sai na juye dashi nima ina kokarin
turmushe shi da karfin tsiya domin na hallakashi
sai da muka shafe kusan sa a daya muna ta bakin
artabu ya zamana cewa zakin ya karkarce jikina
da kaifin faratan hannayansa yai mini raunika
masu yawa jini na zuba a jikina amma kuma ya kasa
kafa min hakoransa a jikina
lokacin da jiri ya fara dibana na tabbatar da cewar ina daf
da halaka sai zuciyata ta kufulo cikin tsananin
zafin nama na suri zakin na dokashi akan wani
katon dutse nan take kan zakin ya dagwargwaje ya
zama gawa
A sannan ne na yanke jiki na fadi kasa cikin mugun yanayi
da kyar na iya bude jakar guzurina na fiddo magani
na shafa akan raunikan jikin nawa da hannu daya
wadansu raunikan ma dake gadon baya na in da
hannuna ba zai kai ba ban sami damar sa musu
maganin ba
a sannan ne na dauko battar ruwana na bude nash
Sai da na dan huta naji karfin jikina sannan na mike
tsaye na dauki gawar zakin na saba a kafadata
amatsayin abincinmu na rana itama barewara
sai na barta a jikin mashin nawa naci gaba da tafiya
na nufi inda zamu hadu da matata zalina
hakika SADAUKANTAKA tana da rana tabbas in ba don
na kasance sadauki ba da babu yadda za ayi na iya daukar
wannan katon zaki har na sabashi a kafadata da
hannu daya kuma naci gaba da tafiya alhalin ina
rike da barewa bisa mashina, haka dai naci gaba da
tafiya har na iso inda zan hadu da zalina matata
tun daga nesa kuwa na hango zalina zaune akan
wannan dutse tana hange hange da waige waige
ko zata gano ni, har ma ta zaku tana mikewa tsaye
akan dutsen
ai kuwa tana hangoni dauke da zakin da kuma barewa
sai ta cika da tsananin mamaki, cikin tsananin
murna ta duro kasa daga kan wannan dutse ta farfalo
da gudu izuwa gareni ta rungumeni koda taji
raunika a jikina sai ta janye jikinta daga cikin nawa
da sauri ta dubi sauran raunikan na jikina, take
hawaye ya kwararo daga cikin idanuwanta ta
dubeni cikin alamun tausayi tace yakai mijina me yasa
ka sai da rayuwarka don kawai ka cika wannan ka ida
ta al adarmu
Sa adda naji wannan tambaya sai na bushe da dariya
nace
yake matata kiyi sani cewa ko a tamu al adar namiji
baya samun matar aure a cikin sauki har sai ya
sha bakar gwagwarmaya ta hanyar gasa a neman
auren,
kuma gasa ce mai hadarin gaske wacce mutum ma
zai iya rasa rayuwarsa gaba daya, nan dai muka juya
da baya muka nufi hanyar gida, muna cikin
tafiya ne na dubi zalina na bushe da dariya, Al amarin
da yai matukar bata mamakikenan
ta dubeni tace yakai mijina kai kuwa menene dalilin
yin wannan dariya taka, kawai sai nayi ajiyar numfashi
nace gani nayi nidake mun shafe sama da sa a biyu
a cikin nan muna farauta amma ke ko fiffiken dan
tsako baki samo ba, dajin wannan batu sai itama ta
kyalkyale da dariya tace ni kaina na yi matukar mamakin
yadda ko tsuntsu guda ban iya harbowa ba daga sama
alhalin ga su nan birjik suna ta kaiwa da komowa
a sararin samaniya sai dana yi asarar kibiyoyina
sama da guda talatin, kai bama tsuntsaye ba hatta
kananan dabbobin daji sai dana kasa tsere da wajan
guda bakwai amma da zarar sun shiga cikin duhuwa
saina nemesu sama ko kasa na rasa su
koda jin haka sai nayi dariya nace ai kin san cewa komai
sa a ne da rabo
haka dai muka ci gaba da hira har ya rage saura tafiya
kadan mu iso gida
kwatsam muna cikin tafiya sai zalina tayi tuntube ta fadi a lokacin da zuciyarta
ta fara bugawa da karfi, cikin sauri na ajiye mashina
mai cake da barewa na tasheta zaune na dubeta
cikin kaduwa ina mai dudduba jikinta nace lafiya
kuwa menene ya sameki, zalina tayi ajiyar zuciya
ta dubeni cikin alanun firgici kawai sai naga hawaye
ya zubo mata take ta fashe da kuka tana mai cewa
naji a jikina cewa mahaifina yayi kaura, koda jin haka sai
nima hankalina ya tashi na dubeta cikin kwarin guiwa
nace ke haba ! Tashi mu karasa gida mahaifinki na
nan raye
kawai dai zuciyarki ce take raya miki hakan
nan dai na tasheta muka mike tsaye har zuwa wannan
lokacin ina dauke da wannan katon zakin a kafadata
ga kuma barewa a jikin mashina
haka dai muka
cigaba da tafiya harmuka
Iso gida
tun daga nisa muka hango Abul zalina kishingide
a jikin dutsen kogon da muke kwana ya dora
kafarsa daya akan daya yana barci, kuma ga sanda
a hannunsa in ba don dora kafarsa da yayi ba daya bisa
daya da kuma sandar da ya rike a hannunsa da dole ne
ace ya mutu
Al amarin zalina kuwa lokacin da ta hango mahaifinta
a cikin wannan hali tun daga nesa sai jikinta yayi sanyi
Al amin Ahmed Misau Nake Guyson Ko A square
zuciyarta ta karaya kawai sai ta yarda bakan dake
hannunta ta falfala da gudu izuwa gareshi tana
isa gabansa sai ta kura masa idanu koda taga
idanunsa a kafe suke ko kiftawa basa yi kuma babu
inda yake motsi daga cikin gabobin jikinsa sai ta
fada kansa ta rungumeshi tana mai tsandara uban
ihu sannan kuma ta fashe da kuka
koda ganin abin da
ya faru sai nima na rugo da gudu ina dogara sandata
ina isowa na warbar da wannan zaki na kafadata
kuma nayi jifa da sandata da mashin da barewar
ke tsire akai
kawai sai na tsugunna kasa bisa guiwoyina na fara
kuka aka rasa
wanda zai rarrashi wani tsakanina da zalin
nikaina Al amin Na tausaya musu gaskiya
da wannan gagarumin rashin mahaifin ta da sukayi
sai da muka shafe kusan sa a guda muna kuka sannan na
mike tsaye naje na kama kafadar zalina na
tasheta tsaye na shiga rarrashinat, sai da ta dawo cikin
hayyacinta sannan muka fara shirye shiryen
binne gawar mahaifin nata, tun daga wannan rana
muka bar wannan daji ba tare da fatan komawa cikinsa
ba
ko don ziyara ga kabarin mahaifin nata wanda ke cikin
wannan kogon dutse
haka dai mukaci gaba da tafiya a cikin daji mu
kwana nan mu tashi can ba tare da sanin inda muka
dosa ba muna neman inda yake da ni ima mu zauna
muci gaba da rayuwarmu, sai da muka shafe watanni
shida cur muna tafiya sannan muka iso wani daji dake
cikin nan kasarka ta Askandariyya, A nan ne muka zauna
muka ci gaba da rayuwa nida matata zalina inda
muka gina wata yar bukka a gefen wani tsauni
inda muke kwana har ma muka kafa wani garken dabbobin
gida muna kiwo bamu da wata sana a face farauta
kuma mu kan kai fatun dabbobi cikin birnika mu siyar
mu siyo abin da muke bukata da silallan da muka
sayar da fatan dabbobin dajin sannan mu dawo
dajin da muke da zama ba tare da mun taba sha awar
yin rayuwa ba a cikin gari har muka samu rabon
haihuwar Yata SIYAMA
tun siyama tana da shekara biyar a duniya na fara bata
horon yaki har ta cika shekara tara kuma duk irin horon da za a baiwa
babban mutum shi nake bata
hakika siyama tasha bakar wahala sosai a wajen
horon yaki kamar zata rasa ranta kuma sau tari sai
uwarta tayi ta
kuka idan taga tana shan wahalar taji kamar ta
hanani bata horon amma idan ta tuno da irin
kisan gillar da sarki shardas yayiwa kabilarsu da
zuri arsu da tawa sai ta hakura, haka dai siyama taci
gaba da koyon yaki har ya zamana cewa nima
ta fini jarumtaka juriya da naci, a bangaren iya farauta kuwa
ni kaina sai da na cika da mamaki bisa ganin irin
abubuwan al ajabin da take yi a daji da kuma irin
kwarewar da ta samu ta iya harbin kibiya fiye
da mahaifiyarta
bamuyi shawarar sanya siyama a cikin gasar jarumtaka
ba don komai sai saboda mu jarraba karfin
damtsenta da kuma iyakar jarumtakarta kuma
burinmu shine taci gaba da baiwa kanta horo gami da
tanadin daukar fansa akan sarki shardas, ina mai tabbatar
maka da cewa
yanzu haka ko sunan sarki shardas siyama taji
an ambata sai zuciyarta ta kama tafarfasa kamar zata
kone saboda irin kiyayyar da muka cusa mata
kuma a kullum bata da burin da yafi na mu kyaleta
ta tafi zuwa birnin shardas ita kadai ta shiga har
cikin fadarsa ta kashe shi amma na gaya mata cewa
ba zata taba samun nasara ba a kansa a yanzu face
idan ta mallaki wata Hula da ake kira HULAR LAMSARA
koda Hailur yazo nan a labarinsa sai idanun sarki
hulbasu
suka zazzari ya kamu da tsananin tsoro gami da
mamaki saboda rabonsa da yaji an ambashi sunan
wannan hula ta LAMSARA tun yana yaro karami sai kuma
yanzu da yaji a bakin hailur, tabbas ya sami labarin
hular lamsara a wajan kakansa wato wanda ya haifi ubansa amma bai kara jin
labarinta ba kawo i yanzu
sai da sarki Hulbasu ya baza fatake jarumai da
mayaka izuwa sassan duniya domin su nemo
masa wannan hula ta lamsara amma ba a samu wanda ya jiyo labarin inda
hular take bama
sarki hulbasu yayi gyaran murya sannan ya dubi
hailur a natse yace hakika jikina ya bani cewa lallai
akwai wani babban sirri a tsakanin shardila matar sarki shardas
kuma ina mai tabbatar maka da cewa idan sarki shardas ya gano cewa kana nan
a raye kuma anan cikin yankin kasata tobama kai ba
ko iyalinka hatta nida kaina bz an zauna lafiya ba
don zai iya zuwa ya yakeni ya kawai da mulkina
koda jin haka sai hailur ya dubi sarki Hulbasu yace
yakai wannan sarki mai Karamci me yasa ka taimakeni
Alhalin ka san cewa yin hakan hadarine ga rayuwarka
da mulkinka
koda jin haka sai sarki hulbasu yayi gyaran murya
gami da ajiyar zuciya sannan yace A rayuwata
babu abinda na tsana sama da zalunci kuma mahaifina
kafin ya gushe ya bar mini wasiyya akan cewa
idan har ina son nayi nisan kwana akan karagar mulina to
dole ne
Na guji aikata zalunci ga talakawa na dama duk
wadanda suke karkashina ko kasa dani kuma na
kwatanta adalci a tsakaninsu gwargwadon iyawata
ina so ka sani cewa har yanzu sarki shardas bai san
komai ba dangane da wanzuwarka ko baiyanarka a cikin aksata kuma
dolene kaci gaba da boye kanka har izuwa lokacin da
zaka iya fuskantarsa, duk da cewa yanzu kaga matarka
shadila da kuma danka yarima Hulkasa
amma dole ne ka hakura da mallakarsu har sai nan
da zuwa lokacin da ya dace, idan ba haka ba kuwa zaka
rasa su ne gaba daya kuma kai kanka ma zaka rasa kanka
ba zan hanaka ka gana da shadila ba amma kada ku
kuskura ku bari wannan yaro hulkas ya san cewa
kaine mahaifinsa kuma kada ku bari ya san duk abinda
ya faru a baya
hakan ba zai haifar muku da komai ba face rugujewar dukkanin burikanmu
gaba daya da kuma salwantar rayukanmu
yayinda sarki Hulbasu yazo nan a zancensa sai hankalin
hailur ya dugunzuma ainun fiye da ko yaushe har hawaye ya zubo masa kuma
zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone saboda
fishi
ya dubi sarki hulbasu yace yanzu kana nufin kace dani
inaji ina gani zan hakura da matata wadda aka
rabani da ita a daren angwancinmu da ita na farko kuma na hakura da
dana wanda tun yana ciki bai san cewa nine ubansa ba
gashi har ya cika shekara bakwai a duniya, ka sani cewa har kwnaan gobe zuciyata bata
bayar da soyayyarta ta gaskiya ba ga kowa face shadila
ina son shadila fiye da yadda nake son kaina
Al amin ahmed Misau Nake Shin tayaya kake tunanin
zan
yarda ta sake kubuce min a karo na biyu al halin ban taba
zaton cewa zamu sake hadu wa ba a cikin wannan
duniya
koda hailur ya zo nana a zancensa sai hawaye ya zubowa
sarki Hulbasu al amarin da yai matukar girgiza
hailur kenan kuma yai matukar bashi mamaki
ya dubeshi yace yakai abokina inda dalikin zubar
wannan hawaye naka mai tsada koda jin wannan
tambaya sai sarki hulbasu yaja dogon numfashi
sannan ya sa hannu ya goge hawayansa ya dubi
hailur cikin alamun karayar zuciya yace yakai abokina
kayi mini tambayar da ta fama min tsohon ciwon dake cikin
zuciyata ne kuma shine asalinsanadin da yaja
mummunar kiyayya tsakanina da sarki shardas inaso
ka sani cewa duk irin kiyayyar dakake yiwa sarki
shardas bata kai koda rabin wacce nake yi masa ba
domin duk ladabin da nake yi masa a yanzu na
dole ne saboda yafi karfina kuma bana son abinda zai
taba kasata da jama'ata, ka sani cewa bakincikin
sarki shardas ne ya kashe mahaifina kuma sarki
shardas ne sanadin dana rasa dana na fari YARIMA
HUZEIN
Cikin alamun tsananin mamaki da kaduwa hailur ya
dubi sarki hulbasu yace tayaya mahaifinka da danka
huzein suka gushe
koda jin wannan tambaya sai hawaye ya sake zubowa
sarki hulbasu ya dubi hailur cikin nutsuwa yace
yakai abokina ka saurari labarin da zan baka yanzu
dukkanin amsar tambayar da kayi min yanzu tana
cikinsa......
.
JARUMA SIYAMA DA MAHAIFINTA HAILUR SUNA CIKA
BURINSU NA DAUKAR FANSA AKAN SARKI SHARDAS ?.
.
MAI ZAI FARU IDAN SARKI HULBASU YA GAMA BAIWA HAILUR
LABARIN MUTUWAR DANSA DA MAHAIFINSA ?
.
A WANNE HALI SHADILA TAKE CIKI BAYAN TAYI ARBA DA TSOHON MIJINTA HAILUR ?
.
YAUSHE YARIMA HULKAS ZAI SAN CEWA HAILUR SHINE
MAHAIFINSA NA GASKIYA
.
Marubucin littafin Wato Abdul aziz sani M/ Gini yace
mu hadu a Littafin Tsatsuba na (6) Don jin
cigaban wannan kayataccen kasaitaccen labari
mai dumbin darasi fadakarwa da nishadantarwa
Mai debe muku kewa a kullum da ko yaushe.
Suleiman Zidane Kd 09064179602:
Posting By Abubakar Saleh AlQuyraemey
08138873799 For More Littattafan Yaƙi
.
Duk sa adda na fara wannan kuka sai zalina da mahaifinta sunyi da gaske sannan suke rarrashina na dawo cikin hayyacina wani abin mamaki wanda ya daure min kai shine duk da cewar na rasa hannu daya da kafa daya ko kadan ban rasa karfin damtse na ba da kuma iya yakina don haka duk sa adda muka shiga daji farauta duk muguwar dabbar da ta zo gabanmu take nake gamawa da ita, komai yawan gungun yan fashi kuwa idan mukayi gamo dasu ni kadai nake tarwatsa su, amma zalina da mahaifinta suna taimaka mini saboda sun kware ainun a iya harba kibiya. A lokaci guda kowannansu na iya harba kibiyoyi bakwai sai dai kaga maza na zubewa kasa yayinda tsinin kibiyoyinsu suke ratsa kirazansu, A kwana a tashi sai na sami wata bakwai tare da su zalina ya zamana cewa na shaku dasu ainun musamman zalina wacce komai tare muke yi shimfidar barci kawai muke rabawa. A hakane na fuskanci cewa soyayya ta shiga tsakaninmu amma dana tuna cewa ni fa yanzu masaki ne bani da hannu daya da kafa daya sai na ga cewa idan na nemi soyayyar zalina na cutar da ita. kuma idan na tuna cewa na rasa masoyiyata shadila sai naga cewa ai na gama soyayya a duniya don ba zan taba samun wacce zan sota ta soni ba
kamarta bisa wannan daliline na rinka danne soyayyar zalina a cikin zuciyata kuma duk sa adda naga zata nuna mini soyayyar tata saina bagarar.
.
Ni abinda yake bani mamaki ma shine me zata yi da masaki muna cikin wannan hali ne mahaifin zalina ya kamu da cuta mai tsanani wacce takai shi ga kwanciya, abu dai kamar wasa kullum sai ciwo ya rinka gaba ya zamana cewa ba a samun sauki. Al amarin da ya dugunzuma hankalinmu kenan muka rasa sukuni da kwanciyar hankali ita kuwa zalina kullum bata da aikinyi sai kuka da bakin ciki da kyar nake iya rarrashinta, ba komai ne yake sata
wannan yawan kuka ba sai ganin cewa babu alamar samun lafiya ga mahaifinta kuma ga dukkan alamu ciwon nasa bana tashi bane, wata rana na tashi da sassafe ina shirin tafiya daji domin naje nayi farauta naman da zamu ci da rana a lokacin zalina na can wajan kogon da muke kwana ta dora tukunya akan wuta tana dafa mana abincin kalaci sai mahaifin zalina ya kira sunana a lokacin da nake daf da fita daga cikin kogon. Cikin tsananin mamaki na juyo na dubeshi saboda rabonsa da ya budi baki yayi magana tun daga ranar da ya kwanta wannan cuta, cikin matukar sanyin jiki na karasa daf dashi na tsugunna a gabansa inamai kura mas aidanuna ya shi kuma sai ya kamo hannuna ya dora akan kirjinsa ya dafe hannun nawa da dukkan hannayansa biyu sannan ya budi baki da kyar yace yakai hailur kayi sani cewa wannan ciwo nawa bana
tashi bane mutuwa zanyi kuma a koyaushe wa adina zai iya cika ina neman Alfarma guda daya jal a wajanka alfarmar kuwa itace ina son ka auri zalina, koda jin wannan batu sai zuciyata ta buga da karfi na dubeshi cikin mamaki nace yakai abul zalina ai idan kace na auri zalina bakayi mata adalci ba domin kana sone ta auri nakasashshe koda jin haka sai tsohon yayi murmushin karfin hali ya dubeni cikin nutsuwa yace yakai hailur kayi sani cewa a zahiri kake nakasashshe amma a zuciyarka kafi ta lafiya sannan kuma har yanzu sadaukantakarka da jarumtakarka suna nan basu ragu ba dai dai da matsayin kwayar zarra ina son ka sani cewa yata ta kamu da tsananin sanka a cikin wannan hali da kake ciki na nakasa kaga kenan ashe soyayyarta itace soyayyar gaskiya ka auri yata zalina ko don saboda ka samu zuri ar da zasu ga bayan babban makiyinmu sarki shardas ka sani cewa kowacce mace tana son ta auri namijin da zai iya kare mutuncin ta da rayuwarta koda kuwa shine yafi kowa nakasa a doron kasa lallai ku cika mini burina na ganin bayan sarki shardas wannan itace kadai wasiyyata a gareku, ashe duk wannan bayani da mahaifinta yake yimini zalina dake can kofar kogo tana sauraro don haka sai ta kasa cigaba da aikin da takeyi ta koma gefe daya ta zauna tana ta faman kuka, koda na fito daga cikin kogon dutsen rataye da takobina da nufin na shiga daji don gabatar da farautar sai naga zalina tana ta kukanta..
.
Al amarin da yasa na gane cewa lallai duk taji abinda muka tattauna kenan dani da mahaifinta cikin sanyin jiki na karasa gareta na zauna daf da ita kanta na sunkuye sai na tallabo habarta da lafiyayyen hannun nawa kuma na share mata hawaye muka kurawa junanmu idanu sannan na dubeta nace shin kin amince na zama abokin rayuwarki.
.
Koda jin wannan tambaya sai zalina ta murtuke fuska daga can kuma sai ta rungumeni ta kama kyalkyala dariyar farinciki muna rungume da juna mukaji motsi a bayanmu a firgice muka juya da sauri sai mukaga she mahaifin zalina ne ya fito daga cikin kogon dutsen yana dogara sanda da kyar yana numfashi sama sama.
.
A guje na janye jikina daga cikin na zalina na karasa gareshi na rukoshi na zo dashi wajan zalina itama ta kamashi muka zauna gaba daya sannan ta dubeshi cikin alamun tsananin damuwa tace haba ya kai Abbana yaya kai da kake cikin wannan hali zaka taso kayi tafiya sa adda abul zalina yaji wannan tambaya daga bakin yarsa zalina sai ya dubeta yayi murmushin karfin hali yace yake yata ai dole ne na taso ko don naga abin farinciki na karshe wanda idanuna zasu gani wanda shine amincewar junanku akan aure lallai ina so naga wannan aure naku da idanuna kafin rai yayi halinsa, nan take tsohon ya yiwa hailur bayanin yadda zasu daura auren bisa al adar su kabilar wato kowannansu ya yanki dan yatsansa ya diga jininsa
a cikin ruwa bayan jinin biyu ya gauraye sai kowannan su ya sha ruwan nan take kuwa muka aiwatar da hakan, muka rinka shan ruwan muna kallon juna cikin murmushi har sai da ruwan ya kare kaf.
.
A dai dai wannan lokacine farinciki ya lullube abul zalina ya dubi hailur yace yakai babban gwaro kayi sani cewa yanzu ka zama na zalina kuma zalina itama ta zama taka babu abinda zai rabaka face kaddara ko mutuwa, wannan dama shine manufar shan jinin juna da kukayi, bisa al adar kabilarmu a ranar da miji ya mallaki matarsa babu abinda zasu fara face zuwa daji farauta tare, don haka yanzu saiku tafi sannan da ku ka samo shi zaku kawo a gasa muci muyi walima da farin cikin aurenku, koda
jin wannan batu sai na dubi abul zalina cikin alamun damuwa nace haba yakai abul zalina yaya za ayi mu tafi daji mu barka kai kadai a nan alhalin kana cikin wannan halina rashin lafiya,
.
Koda jin haka sai abul zalina ya dubeni cikin murmushi yace kada ka damu dani lallai zakuje ku dawo kuma ku sameni cikin koshin lafiya da sauki fiye da ko yaushe wannan shine abinda na gani a mafarkina na daren jiya bisa wannan dalili ne ma a yau din nan na sami saukin da har na iya mikewa tsaye na taka kafafuna na fito daga cikin wannan kogo haka dai abul zalina yaci gaba da rarrashinmu har ya samu ya shawo kanmu muka amince da barinsa a wajen amma kafin mu tafi sai da ya rungumemu yana ta dariyar farinciki bayan ya janye jikinsa daga cikin namune mun juya zamu tafi izuwa cikin daji sai zalina ta waigo ta dubeshi take ta hango kwalla a cikin idanunsa.
.
Al amarin da ya dugunzuma hankalinta kenan ta dubeni tace yakai mijina nifa zuciyata bugawa take da karfi ji nake kamar idan muka dawo ba zamu riskeshi a raye ba ni kaina naga alamun hakan a tare da mahaifin nata kuma duk kalaman da yake yi na bankwana ne amma don kada hankalin zalina ya tashi sai naki sanar da ita haka dai muka nausa cikin daji muna waigen Abul siyama shi kuma ya bimu da kallo yana yi mana murmushi har muka kule muka daina hangoshi.
.
A sannan ne kuma muka falfala da azababbn gudu izuwa cikin daji mukayi ta tsala gudu ba sassauci muna neman dabbar dajin da zamu samu babu abinda zai baka mamaki face yadda nake iya gudu ina dogara sanda alhalin kafata guda daya bata da kyau kuma har tserewa zalina nake yi a gudun ni ina rike da takobi ne kuma karshen sandar da nake
dogarawa mashi neita kuwa zalina a hannunta kwari ne kuma ta rataya kwanson kibiyoyin kwarin a bayanta don haka ita bata rike wani makami sai kwari da baka.koda muka nausa cikin daji sai muka rabu ni kuma nayi gaba ita kuma tayi yamma sannan kuma muka baiwa junanmu tsawon rabin sa a akan mu hadu a bakin wani dutse dake can tsakiyar dajin kowannanmu na rataye da kaho a bayansa wanda duk sa adda ya shiga wani hadari wanda ba zai iya kubutar da kansa ba sai ya busashi komai nisan inda yake dan uwansa zai iya jiyowa har yakai mas dauki shidai wannan kaho na sihirine kuma gado ne a kabilar tasu zalina kuma mutum ba zai iya mallakarshi ba face ya kasance dan kabilarsu ko kuma ya auri jinin Kabilar.
.
Bayan mun rabu a cikin daji nida matata zalina sai muka wanzu muna masu neman abin farauta baji ba gani, lokacin da naga na shafe dan dogon lokaci ina neman abin farautar ban samu ba sai hankalina ya dugunzuma ainun saboda ina ganin cewa ai abin kunyane ace a ranar daurin aurena na kasa farauto abincin da zamu ci nida amaryata...
.
Zan dakata nan sai kuma Allah Ya kainu gobe insha Allahu afin nan daga mai ɗebe maku kewa AlQuyraemey nake cewa ku huta lafiya.
Ehm Al amin Ahmed Misau, Guyson ko A square
Ina cikin wannan haline naga wata barewa ta
nufo inda nake cikin azababben gudu gashi dai
barewar ta hangoni a gabanta rike da makami
amma ko shakkar tunkaro ni batayi ba
dada durfafo ni takeyi al amarin da yasa na fahimci
cewar lallai masifar da ta korota ta nufoni don tsira
da rayuwarta ta wuce tawa hadari, ai kuwa ban ankara ba
sai naga ashe wani murjejen zaki ne ya tasota a gaba
tun daga nesa dana hango zakin ya falfalo da azababben gudu
har tashi sama yake saboda karfin gudun nasa
kuma harshensa na zazzagowa waje daga cikin bakins ana gane
cewa lallai
wannan zaki a cikin muguwar yunwa yake
koda naga cewa barewar nan so take ta wuce ta gabana
domin ta tsira da rayuwarta sai na yunkura cikin zafin nama na
daka tsalle sama a lokacin da itama barewar ta daka tsalle da nufin ta shallakeni
muna haduwa a saman na soketa da mashina ta
zama gawa na duro kasa bisa kafafuna barewar
na sakale a jikin mashin nawa, ai kuwa sai wannan zaki
yayi tirjiya a lokacin da tazarar dake tsakaninmu
bata wuce taku goma ba
nan fa muka fara kallon kallo tsakaninmu da murjejen zakin
nazarin da zakin yake yi shine ni zai farwa sannan
ya dauke barewar ko kuwa barewar zai karba
ni kuwa nazarin da nakeyi shine ta yaya zan iya
.Ya kasance shi ba karamin tashin hankali bane
duk da na san cewa na sha yin gumurzu da manyan
dabbobin daji ina samun nasara a kansu sai da
zuciyata ta karaya akan wannan zaki domin ban
taba yin gamo da tsohon zakimai girma da kwarjinin wannan ba
nikam tuni na gama aiyanawa a raina cewa
duk rintsi ba zan iya sallama barewar ba ga wannan
zaki koda hakan na nufin zan rasa rayuwata
kawai sai na cake mashin nawa a cikin kasa
wanda ke dauke da barewar sannan na buda hannuna
mai rike da takobi ina mai
gyara tsayuwata kuma na koma gefe daya na tsaya ina
mai baw azakin zabi tsakanin barewar da ni kaina
ya zabi wanda zai fara afkawa
take zakin yayi wani irin
gurnani mai ban tsoro wanda yasa hantar cikinsa ta kada amma da na tuna cewa
amaryata
zalina na can fa tana farauta a cikin wannan daji
wata kilama yanzu ita ta dade da samo nata abin
farautar taje inda mukayi zamu hadu ta zauna
tana jirana sai naji zuciyata ta kekeashe ga barin dukkan tsoro.....
Kamar hadin baki sai nida zakin muka falfalo
da gudun tsiya izuwa kan juna muka dako tsalle
sama a tare kafin nayi wani yunkuri na saran zakin
ko sukarsa da takobina tuni shi ya sa kirjinsa ya
bangajeni
ai kuwa sainaji kamar aksusuwan kirjina sun
kakkarye nayi can baya da karfi bayana ya gwaru
da jikin wata bishiya na fado kasa a matukar galabaice
ina aman jini ta hanci da baki, koda zakin yaga
halin da na shiga sa adda shima ya duro kasa sai
ya wangame baki ya kwalla wani uban ruri anda
ya fi wanda yayi a baya mai nuna kuranta kansa
da dai yaga na kasa tashi ina ta numfashi sai
ya wuce ta gabana ya daka tsalle da nufin ya suro
wannan barewa dake sakale a jikin mashina
ni kaina ban san yadda akayi ba na sami gagarumin
karfi da kuzari kawai gani nayi na mike tsaye zumbur
na daka tsalle daga inda nake na rungumo zakin
kafin bakinsa ya cafi barewar mun fado kasa tim !
Nan fa muka kama kokawa a kasa muna ta birgima
idan zakin ya danneni yana kokarin kafa min
hakoransa sai na juye dashi nima ina kokarin
turmushe shi da karfin tsiya domin na hallakashi
sai da muka shafe kusan sa a daya muna ta bakin
artabu ya zamana cewa zakin ya karkarce jikina
da kaifin faratan hannayansa yai mini raunika
masu yawa jini na zuba a jikina amma kuma ya kasa
kafa min hakoransa a jikina
lokacin da jiri ya fara dibana na tabbatar da cewar ina daf
da halaka sai zuciyata ta kufulo cikin tsananin
zafin nama na suri zakin na dokashi akan wani
katon dutse nan take kan zakin ya dagwargwaje ya
zama gawa
A sannan ne na yanke jiki na fadi kasa cikin mugun yanayi
da kyar na iya bude jakar guzurina na fiddo magani
na shafa akan raunikan jikin nawa da hannu daya
wadansu raunikan ma dake gadon baya na in da
hannuna ba zai kai ba ban sami damar sa musu
maganin ba
a sannan ne na dauko battar ruwana na bude nash
Sai da na dan huta naji karfin jikina sannan na mike
tsaye na dauki gawar zakin na saba a kafadata
amatsayin abincinmu na rana itama barewara
sai na barta a jikin mashin nawa naci gaba da tafiya
na nufi inda zamu hadu da matata zalina
hakika SADAUKANTAKA tana da rana tabbas in ba don
na kasance sadauki ba da babu yadda za ayi na iya daukar
wannan katon zaki har na sabashi a kafadata da
hannu daya kuma naci gaba da tafiya alhalin ina
rike da barewa bisa mashina, haka dai naci gaba da
tafiya har na iso inda zan hadu da zalina matata
tun daga nesa kuwa na hango zalina zaune akan
wannan dutse tana hange hange da waige waige
ko zata gano ni, har ma ta zaku tana mikewa tsaye
akan dutsen
ai kuwa tana hangoni dauke da zakin da kuma barewa
sai ta cika da tsananin mamaki, cikin tsananin
murna ta duro kasa daga kan wannan dutse ta farfalo
da gudu izuwa gareni ta rungumeni koda taji
raunika a jikina sai ta janye jikinta daga cikin nawa
da sauri ta dubi sauran raunikan na jikina, take
hawaye ya kwararo daga cikin idanuwanta ta
dubeni cikin alamun tausayi tace yakai mijina me yasa
ka sai da rayuwarka don kawai ka cika wannan ka ida
ta al adarmu
Sa adda naji wannan tambaya sai na bushe da dariya
nace
yake matata kiyi sani cewa ko a tamu al adar namiji
baya samun matar aure a cikin sauki har sai ya
sha bakar gwagwarmaya ta hanyar gasa a neman
auren,
kuma gasa ce mai hadarin gaske wacce mutum ma
zai iya rasa rayuwarsa gaba daya, nan dai muka juya
da baya muka nufi hanyar gida, muna cikin
tafiya ne na dubi zalina na bushe da dariya, Al amarin
da yai matukar bata mamakikenan
ta dubeni tace yakai mijina kai kuwa menene dalilin
yin wannan dariya taka, kawai sai nayi ajiyar numfashi
nace gani nayi nidake mun shafe sama da sa a biyu
a cikin nan muna farauta amma ke ko fiffiken dan
tsako baki samo ba, dajin wannan batu sai itama ta
kyalkyale da dariya tace ni kaina na yi matukar mamakin
yadda ko tsuntsu guda ban iya harbowa ba daga sama
alhalin ga su nan birjik suna ta kaiwa da komowa
a sararin samaniya sai dana yi asarar kibiyoyina
sama da guda talatin, kai bama tsuntsaye ba hatta
kananan dabbobin daji sai dana kasa tsere da wajan
guda bakwai amma da zarar sun shiga cikin duhuwa
saina nemesu sama ko kasa na rasa su
koda jin haka sai nayi dariya nace ai kin san cewa komai
sa a ne da rabo
haka dai muka ci gaba da hira har ya rage saura tafiya
kadan mu iso gida
kwatsam muna cikin tafiya sai zalina tayi tuntube ta fadi a lokacin da zuciyarta
ta fara bugawa da karfi, cikin sauri na ajiye mashina
mai cake da barewa na tasheta zaune na dubeta
cikin kaduwa ina mai dudduba jikinta nace lafiya
kuwa menene ya sameki, zalina tayi ajiyar zuciya
ta dubeni cikin alanun firgici kawai sai naga hawaye
ya zubo mata take ta fashe da kuka tana mai cewa
naji a jikina cewa mahaifina yayi kaura, koda jin haka sai
nima hankalina ya tashi na dubeta cikin kwarin guiwa
nace ke haba ! Tashi mu karasa gida mahaifinki na
nan raye
kawai dai zuciyarki ce take raya miki hakan
nan dai na tasheta muka mike tsaye har zuwa wannan
lokacin ina dauke da wannan katon zakin a kafadata
ga kuma barewa a jikin mashina
haka dai muka
cigaba da tafiya harmuka
Iso gida
tun daga nisa muka hango Abul zalina kishingide
a jikin dutsen kogon da muke kwana ya dora
kafarsa daya akan daya yana barci, kuma ga sanda
a hannunsa in ba don dora kafarsa da yayi ba daya bisa
daya da kuma sandar da ya rike a hannunsa da dole ne
ace ya mutu
Al amarin zalina kuwa lokacin da ta hango mahaifinta
a cikin wannan hali tun daga nesa sai jikinta yayi sanyi
Al amin Ahmed Misau Nake Guyson Ko A square
zuciyarta ta karaya kawai sai ta yarda bakan dake
hannunta ta falfala da gudu izuwa gareshi tana
isa gabansa sai ta kura masa idanu koda taga
idanunsa a kafe suke ko kiftawa basa yi kuma babu
inda yake motsi daga cikin gabobin jikinsa sai ta
fada kansa ta rungumeshi tana mai tsandara uban
ihu sannan kuma ta fashe da kuka
koda ganin abin da
ya faru sai nima na rugo da gudu ina dogara sandata
ina isowa na warbar da wannan zaki na kafadata
kuma nayi jifa da sandata da mashin da barewar
ke tsire akai
kawai sai na tsugunna kasa bisa guiwoyina na fara
kuka aka rasa
wanda zai rarrashi wani tsakanina da zalin
nikaina Al amin Na tausaya musu gaskiya
da wannan gagarumin rashin mahaifin ta da sukayi
sai da muka shafe kusan sa a guda muna kuka sannan na
mike tsaye naje na kama kafadar zalina na
tasheta tsaye na shiga rarrashinat, sai da ta dawo cikin
hayyacinta sannan muka fara shirye shiryen
binne gawar mahaifin nata, tun daga wannan rana
muka bar wannan daji ba tare da fatan komawa cikinsa
ba
ko don ziyara ga kabarin mahaifin nata wanda ke cikin
wannan kogon dutse
haka dai mukaci gaba da tafiya a cikin daji mu
kwana nan mu tashi can ba tare da sanin inda muka
dosa ba muna neman inda yake da ni ima mu zauna
muci gaba da rayuwarmu, sai da muka shafe watanni
shida cur muna tafiya sannan muka iso wani daji dake
cikin nan kasarka ta Askandariyya, A nan ne muka zauna
muka ci gaba da rayuwa nida matata zalina inda
muka gina wata yar bukka a gefen wani tsauni
inda muke kwana har ma muka kafa wani garken dabbobin
gida muna kiwo bamu da wata sana a face farauta
kuma mu kan kai fatun dabbobi cikin birnika mu siyar
mu siyo abin da muke bukata da silallan da muka
sayar da fatan dabbobin dajin sannan mu dawo
dajin da muke da zama ba tare da mun taba sha awar
yin rayuwa ba a cikin gari har muka samu rabon
haihuwar Yata SIYAMA
tun siyama tana da shekara biyar a duniya na fara bata
horon yaki har ta cika shekara tara kuma duk irin horon da za a baiwa
babban mutum shi nake bata
hakika siyama tasha bakar wahala sosai a wajen
horon yaki kamar zata rasa ranta kuma sau tari sai
uwarta tayi ta
kuka idan taga tana shan wahalar taji kamar ta
hanani bata horon amma idan ta tuno da irin
kisan gillar da sarki shardas yayiwa kabilarsu da
zuri arsu da tawa sai ta hakura, haka dai siyama taci
gaba da koyon yaki har ya zamana cewa nima
ta fini jarumtaka juriya da naci, a bangaren iya farauta kuwa
ni kaina sai da na cika da mamaki bisa ganin irin
abubuwan al ajabin da take yi a daji da kuma irin
kwarewar da ta samu ta iya harbin kibiya fiye
da mahaifiyarta
bamuyi shawarar sanya siyama a cikin gasar jarumtaka
ba don komai sai saboda mu jarraba karfin
damtsenta da kuma iyakar jarumtakarta kuma
burinmu shine taci gaba da baiwa kanta horo gami da
tanadin daukar fansa akan sarki shardas, ina mai tabbatar
maka da cewa
yanzu haka ko sunan sarki shardas siyama taji
an ambata sai zuciyarta ta kama tafarfasa kamar zata
kone saboda irin kiyayyar da muka cusa mata
kuma a kullum bata da burin da yafi na mu kyaleta
ta tafi zuwa birnin shardas ita kadai ta shiga har
cikin fadarsa ta kashe shi amma na gaya mata cewa
ba zata taba samun nasara ba a kansa a yanzu face
idan ta mallaki wata Hula da ake kira HULAR LAMSARA
koda Hailur yazo nan a labarinsa sai idanun sarki
hulbasu
suka zazzari ya kamu da tsananin tsoro gami da
mamaki saboda rabonsa da yaji an ambashi sunan
wannan hula ta LAMSARA tun yana yaro karami sai kuma
yanzu da yaji a bakin hailur, tabbas ya sami labarin
hular lamsara a wajan kakansa wato wanda ya haifi ubansa amma bai kara jin
labarinta ba kawo i yanzu
sai da sarki Hulbasu ya baza fatake jarumai da
mayaka izuwa sassan duniya domin su nemo
masa wannan hula ta lamsara amma ba a samu wanda ya jiyo labarin inda
hular take bama
sarki hulbasu yayi gyaran murya sannan ya dubi
hailur a natse yace hakika jikina ya bani cewa lallai
akwai wani babban sirri a tsakanin shardila matar sarki shardas
kuma ina mai tabbatar maka da cewa idan sarki shardas ya gano cewa kana nan
a raye kuma anan cikin yankin kasata tobama kai ba
ko iyalinka hatta nida kaina bz an zauna lafiya ba
don zai iya zuwa ya yakeni ya kawai da mulkina
koda jin haka sai hailur ya dubi sarki Hulbasu yace
yakai wannan sarki mai Karamci me yasa ka taimakeni
Alhalin ka san cewa yin hakan hadarine ga rayuwarka
da mulkinka
koda jin haka sai sarki hulbasu yayi gyaran murya
gami da ajiyar zuciya sannan yace A rayuwata
babu abinda na tsana sama da zalunci kuma mahaifina
kafin ya gushe ya bar mini wasiyya akan cewa
idan har ina son nayi nisan kwana akan karagar mulina to
dole ne
Na guji aikata zalunci ga talakawa na dama duk
wadanda suke karkashina ko kasa dani kuma na
kwatanta adalci a tsakaninsu gwargwadon iyawata
ina so ka sani cewa har yanzu sarki shardas bai san
komai ba dangane da wanzuwarka ko baiyanarka a cikin aksata kuma
dolene kaci gaba da boye kanka har izuwa lokacin da
zaka iya fuskantarsa, duk da cewa yanzu kaga matarka
shadila da kuma danka yarima Hulkasa
amma dole ne ka hakura da mallakarsu har sai nan
da zuwa lokacin da ya dace, idan ba haka ba kuwa zaka
rasa su ne gaba daya kuma kai kanka ma zaka rasa kanka
ba zan hanaka ka gana da shadila ba amma kada ku
kuskura ku bari wannan yaro hulkas ya san cewa
kaine mahaifinsa kuma kada ku bari ya san duk abinda
ya faru a baya
hakan ba zai haifar muku da komai ba face rugujewar dukkanin burikanmu
gaba daya da kuma salwantar rayukanmu
yayinda sarki Hulbasu yazo nan a zancensa sai hankalin
hailur ya dugunzuma ainun fiye da ko yaushe har hawaye ya zubo masa kuma
zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone saboda
fishi
ya dubi sarki hulbasu yace yanzu kana nufin kace dani
inaji ina gani zan hakura da matata wadda aka
rabani da ita a daren angwancinmu da ita na farko kuma na hakura da
dana wanda tun yana ciki bai san cewa nine ubansa ba
gashi har ya cika shekara bakwai a duniya, ka sani cewa har kwnaan gobe zuciyata bata
bayar da soyayyarta ta gaskiya ba ga kowa face shadila
ina son shadila fiye da yadda nake son kaina
Al amin ahmed Misau Nake Shin tayaya kake tunanin
zan
yarda ta sake kubuce min a karo na biyu al halin ban taba
zaton cewa zamu sake hadu wa ba a cikin wannan
duniya
koda hailur ya zo nana a zancensa sai hawaye ya zubowa
sarki Hulbasu al amarin da yai matukar girgiza
hailur kenan kuma yai matukar bashi mamaki
ya dubeshi yace yakai abokina inda dalikin zubar
wannan hawaye naka mai tsada koda jin wannan
tambaya sai sarki hulbasu yaja dogon numfashi
sannan ya sa hannu ya goge hawayansa ya dubi
hailur cikin alamun karayar zuciya yace yakai abokina
kayi mini tambayar da ta fama min tsohon ciwon dake cikin
zuciyata ne kuma shine asalinsanadin da yaja
mummunar kiyayya tsakanina da sarki shardas inaso
ka sani cewa duk irin kiyayyar dakake yiwa sarki
shardas bata kai koda rabin wacce nake yi masa ba
domin duk ladabin da nake yi masa a yanzu na
dole ne saboda yafi karfina kuma bana son abinda zai
taba kasata da jama'ata, ka sani cewa bakincikin
sarki shardas ne ya kashe mahaifina kuma sarki
shardas ne sanadin dana rasa dana na fari YARIMA
HUZEIN
Cikin alamun tsananin mamaki da kaduwa hailur ya
dubi sarki hulbasu yace tayaya mahaifinka da danka
huzein suka gushe
koda jin wannan tambaya sai hawaye ya sake zubowa
sarki hulbasu ya dubi hailur cikin nutsuwa yace
yakai abokina ka saurari labarin da zan baka yanzu
dukkanin amsar tambayar da kayi min yanzu tana
cikinsa......
.
JARUMA SIYAMA DA MAHAIFINTA HAILUR SUNA CIKA
BURINSU NA DAUKAR FANSA AKAN SARKI SHARDAS ?.
.
MAI ZAI FARU IDAN SARKI HULBASU YA GAMA BAIWA HAILUR
LABARIN MUTUWAR DANSA DA MAHAIFINSA ?
.
A WANNE HALI SHADILA TAKE CIKI BAYAN TAYI ARBA DA TSOHON MIJINTA HAILUR ?
.
YAUSHE YARIMA HULKAS ZAI SAN CEWA HAILUR SHINE
MAHAIFINSA NA GASKIYA
.
Marubucin littafin Wato Abdul aziz sani M/ Gini yace
mu hadu a Littafin Tsatsuba na (6) Don jin
cigaban wannan kayataccen kasaitaccen labari
mai dumbin darasi fadakarwa da nishadantarwa
Mai debe muku kewa a kullum da ko yaushe.
Suleiman Zidane Kd 09064179602: