Part C.
Tsatsuba Book 5 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Na Abdul'aziz Sani Madakin Gini
Posting By Abubakar Saleh AlQuyraemey
08138873799 For More Littattafan Yaƙi
.
.
Lokacin da aka iso cikin gidan sarautar sarki Hulbasu sai ya kama hannun hailur ya jashi har izuwa cikin kuryar turakarsa suka zauna aka kawo musu abinci da abinsha shi kansa hailur yayi mamakin yadda sarki hulbasu ya aminta dashi haka cikin kankanin lokaci alhalin sau daya rak suka taba ganin junansu
ma wannan haduwar ta yau itace ta biyu amma ya aminta dashi kamar haka Hailur yace a cikin ransa wata kila saboda abin karamcin da nayi masa ne a daji shi yasa ya saka mini da irin wannan tarba, bayan an kawo musu wannan abinci da abin sha na alfarma sai sarki yayiwa hailur tayi amma sai hailr ya kasa cin abincin ya kura masa idanu kawai a lokacin da tuni Sarki ya gabatar da wajan loma biyu yana shirin kai ta uku kenan sai ya lura da cewa hailur baya cin abincin kuma yayi shiru fuskarsa na nuna alamun tunani.
.
Koda ganin haka sai sarki Hulbasu yai murmushi a gareshi yace kwantar da hankalinka ya kai abokina kayi sani cewa a halin yanzu matarka da yarka jaruma siyama suna can tare da matata da kuma gimbiya shadila matar sarki shardas cikin aminci suna cin irin wannan abinci dake gabanmu koda jin haka sai hailur ya saki ajiyar zuciya tare da jinjina kai alamar gamsuwa da furucin da sarki Hulbasu yayi masa nan ya saki jikinsa ya fara cin abincin, har suka ci suka koshi dayansu bai kara cewa uffan ba sai bayan sun nutsu sannan sarki ya dubi hailur yace yakai abokina kayi sani cewa hankali shine yake gani amma ba idanu ba tabbas akwai boyayyen al amari a tare dakai wanda kake boye mini amma ina so ka sani cewa ba a boyewa abokin kuka mutuwa yakamata ka gane cewa shi masoyi na kwarai har abada masoyi ne shi kuwa masoyi zaka sameshi mai rike amana da kare masoyinsa da sallama rayuwarsa a gareshi a koda yaushe komai RINTSI DA TSANANI, na rantse maka da girman iyayena da kakannina ba zan taba cin amanarka bakona juya maka baya musamman idan kayi la akari da irin taimakon da kayi mini a cikin daji wanda har na mutu ba zan manta dashiba, ina son ka saki jikinka da zuciyarka ka sanar dani duk abin dake faruwa shin menene tsakaninka da shadila matar sarki shardas?
.
Na lura da duk abin da ya faru dazu a tsakanin kai da ita a filin GASAR JARUMTAKA, naga hawaye na zuba a cikin idanunta sa adda rawanin fuskarka ya kwaye tayi arba dakai, shin kun san juna ne dama ?
.
Ka sani cewa ko ka sanar dani wannan sirri ko ka ki tuni yanzu rayuwarka da ta iyalanka tana hannuna domin inda ban shigo daku nan ba cikin gidan sarautata tuni kun dade da zama gawa, lokacin da sarki yazo nan a jawabinsa sai hailur yaja dogon numfashi ya ajiye sannan ya dubeshi a lokacin da idanunsa suka ciko da kwallah yace yakai wannan sarki mai Adalci kayi sani cewa gimbiya shadila matatace a baya kafin sarki shardas ya mallaketa, koda jin wannan batu sai idanun sarki hulbasu suka zazzaro tsoro ya kamashi kuma jikinsa ya kama kyarma shi hailur sai yaci gaba da bayani yana mai cewa a ranar angwancina da ita ne sarki shardas da dakarunsa.suka kawo ma kabilarmu harin Mamayar bazato sukayi ta ragargazar dakarunmu kuma suka kame matayanmu da yawa a matsayin bayi ni ne kadai jarumin da na gagaresu har ma nayi gumurzu da sarki shardas amma a karshe ya jefani kasa daga saman wani tsauni mai tsananin tsawon tsiya sanadiyar da na rasa hannuna guda daya na hagu kenan kuma kafata guda daya itama ta sami wannan nakasa ta shagidewa, nidai kawai farkawa nayi na tsinci kaina a cikin wata bukka a tsakiyar daji koda na yunkura domin na mike zaune sai naji na kasa domin gaba daya jikina babu kuzari, yayin da na sake yunkurawa domin na yaye mayafin da aka lullube ni dashi akan shimfidar da nake kwance sai naji babu hannuna guda daya na dama, nan take na kwarara wani uban firgitaccen ihu cikin tsananin bakin ciki da razana.
.
Faruwar hakan keda wuya sai ga wani dattijo tare da wata kyakkyawar budurwa sun shigo izuwa cikin bukkar da shigowarsu sai suka durkusa a gabana dattijon ya dubeni a dimauce yace yaro me ya faru gareka ka tsandara wannan uban ihu haka shin wani mugun mafarki kayi ko kuwa wani mugun abune ka gani.
.
Sa adda naji wannan tambaya sai hawaye ya zube mini na dubi dattijon cikin nutsuwa nace me yasa kuka ceci rayuwata baku barni na mutu ba yanzu menene amfanin rayuwata a doron kasa tunda na rasa komai da kowa nawa kuma na rasa lafiyata ina mai rokonku daku gaggauta kasheni yanzu domin na huta da bakin cikin dake nukurkusar zuciyata yayin da na zo nana zancena sai dattijon da wannan kyakkyawar budurwa suka kamu da tsananin tausayina.
.
Dattijon ya kalleni yace samari hakika kana da nisan kwana a duniya domin a tarihin wannan tsauni wanda ka fado daga kansa fiye da shekaru dari bakwai baya ba a taba samun mahalukin daya fado daga kansa ba ya rayu sai kai muma nan da ka ganmu muna zaune a cikin wannan daji mun fitone daga cikin wata babbar kabila da ake kira BANU IKHLAS. kamar yadda sarki shardas ya karar da kabilarka haka muma ya karar da tamu kabilar ni da wannan ya tawa ce zalina kadai muka tsira da rayuwarmu alokacin.
.
Sa adda ya kawo farmaki zuwa kauyanmu nida ita
bama nan muna cikin daji muna yin farauta bayan mun dawo mun iske iyayanmu da yan uwanmu da duk danginmu sun zama gawa sai muka kama kuka mutum daya kacal muka samu da sauran numfashi a jikinsa shine ya gaya mana cewa sarki shardas ne da kansa shida dakarunsa suka zo sukayi mana wannan mummunar barna da dai muka ga cewa ba zamu iya daukar fansa a kan sarki shardas ba sai muka hada kayanmu muka sake komawa cikin daji muka ci gaba da farauta, amma bamu zauna a waje daya ba sai muka ci gaba da tafiya muna ketawa ta gefen garuruwa da kauyuka amma bama zama a inda babu cibiyar ruwa. Tabbas ruwan dake kasan wannan tsauni da ka fado ne ya kawoka nan domin daga can zuwa nan tafiya ce ta kwana saba in da hudu, sa dda mahaifin zalina yazo nan a zancensa sai na cika da tsananin mamaki kuma na sake kamuwa da bakin ciki mara misaltuwa don haka ban san sa adda na fashe da kuka ba ina mai cewa ina ma na mutu ban rayu ba sakamakon fadowa daga kan wannan tsauni tun da yanzu bani da kowa kuma bani da komai a wannan daji, koda jin wannan batu sai tausayina ya kama zalina da mahaifinta zalina ta dubeni tace yakai wannan jarumi ma aboci kwarjini da jarumtaka ka yi sani cewa yadda baka da komai da kowa a wannan duniya haka muma muka kasance ni da mahaifina amma tunda yanzu kaddara ta hadamu mun sameka ka samemu, zaifi kyau mu rungumi kaddara bisa yadda ta samemu mu ci gaba da rayuwa ko don nan gaba mu ga yadda karshen mulkin sarki shardas zai kasance koda kuwa mu bazamu iya ganin karshen nasa ba, ka sani cewa babu wani abu madawwami kuma komai nisan jifa kasa za fado, don haka duk abinda sarki shardas ke takama dashi watarana sai ya fado kasa tunda idan ba mutuwa akwai tsufa akwai lokacin da yanaji yana gani ba zai iya yin zaluncin da yake yi ba yanzu koda mu bamu ga wannan lokaci ba ina son ire irenmu sugani.
.
Lokacin da zalina tazo nan a zancenta sai jikina dana mahaifinta yayi sanyi saboda mun san cewa duk abinda ta fada gaskiya ne, tun daga wannan rana zalina da mahaifinta sukaci gaba da jinyata har na sami lafiya ya zamana cewa ina iya mikewa tsaye na dogara sanda na bisu izuwa daji don yin farauta amma fa duk sa adda na dubi hannuna na hagu naga babu shi kuma naga kafata ta dama ta shagude sai na fashe da matsanancin kuka na bakinciki domin gani nake kamar rayuwata bata da wani sauran amfani duk sa adda na fara wannan kuka sai zalina da mahaifinta sunyi da gaske sannan suke rarrashina na dawo cikin hayyacina....
TSATSUBA
Littafi Na Uku (5)
Posting By Abubakar Saleh AlQuyraemey
08138873799 For More Littattafan Yaƙi
.
.
Lokacin da aka iso cikin gidan sarautar sarki Hulbasu sai ya kama hannun hailur ya jashi har izuwa cikin kuryar turakarsa suka zauna aka kawo musu abinci da abinsha shi kansa hailur yayi mamakin yadda sarki hulbasu ya aminta dashi haka cikin kankanin lokaci alhalin sau daya rak suka taba ganin junansu
ma wannan haduwar ta yau itace ta biyu amma ya aminta dashi kamar haka Hailur yace a cikin ransa wata kila saboda abin karamcin da nayi masa ne a daji shi yasa ya saka mini da irin wannan tarba, bayan an kawo musu wannan abinci da abin sha na alfarma sai sarki yayiwa hailur tayi amma sai hailr ya kasa cin abincin ya kura masa idanu kawai a lokacin da tuni Sarki ya gabatar da wajan loma biyu yana shirin kai ta uku kenan sai ya lura da cewa hailur baya cin abincin kuma yayi shiru fuskarsa na nuna alamun tunani.
.
Koda ganin haka sai sarki Hulbasu yai murmushi a gareshi yace kwantar da hankalinka ya kai abokina kayi sani cewa a halin yanzu matarka da yarka jaruma siyama suna can tare da matata da kuma gimbiya shadila matar sarki shardas cikin aminci suna cin irin wannan abinci dake gabanmu koda jin haka sai hailur ya saki ajiyar zuciya tare da jinjina kai alamar gamsuwa da furucin da sarki Hulbasu yayi masa nan ya saki jikinsa ya fara cin abincin, har suka ci suka koshi dayansu bai kara cewa uffan ba sai bayan sun nutsu sannan sarki ya dubi hailur yace yakai abokina kayi sani cewa hankali shine yake gani amma ba idanu ba tabbas akwai boyayyen al amari a tare dakai wanda kake boye mini amma ina so ka sani cewa ba a boyewa abokin kuka mutuwa yakamata ka gane cewa shi masoyi na kwarai har abada masoyi ne shi kuwa masoyi zaka sameshi mai rike amana da kare masoyinsa da sallama rayuwarsa a gareshi a koda yaushe komai RINTSI DA TSANANI, na rantse maka da girman iyayena da kakannina ba zan taba cin amanarka bakona juya maka baya musamman idan kayi la akari da irin taimakon da kayi mini a cikin daji wanda har na mutu ba zan manta dashiba, ina son ka saki jikinka da zuciyarka ka sanar dani duk abin dake faruwa shin menene tsakaninka da shadila matar sarki shardas?
.
Na lura da duk abin da ya faru dazu a tsakanin kai da ita a filin GASAR JARUMTAKA, naga hawaye na zuba a cikin idanunta sa adda rawanin fuskarka ya kwaye tayi arba dakai, shin kun san juna ne dama ?
.
Ka sani cewa ko ka sanar dani wannan sirri ko ka ki tuni yanzu rayuwarka da ta iyalanka tana hannuna domin inda ban shigo daku nan ba cikin gidan sarautata tuni kun dade da zama gawa, lokacin da sarki yazo nan a jawabinsa sai hailur yaja dogon numfashi ya ajiye sannan ya dubeshi a lokacin da idanunsa suka ciko da kwallah yace yakai wannan sarki mai Adalci kayi sani cewa gimbiya shadila matatace a baya kafin sarki shardas ya mallaketa, koda jin wannan batu sai idanun sarki hulbasu suka zazzaro tsoro ya kamashi kuma jikinsa ya kama kyarma shi hailur sai yaci gaba da bayani yana mai cewa a ranar angwancina da ita ne sarki shardas da dakarunsa.suka kawo ma kabilarmu harin Mamayar bazato sukayi ta ragargazar dakarunmu kuma suka kame matayanmu da yawa a matsayin bayi ni ne kadai jarumin da na gagaresu har ma nayi gumurzu da sarki shardas amma a karshe ya jefani kasa daga saman wani tsauni mai tsananin tsawon tsiya sanadiyar da na rasa hannuna guda daya na hagu kenan kuma kafata guda daya itama ta sami wannan nakasa ta shagidewa, nidai kawai farkawa nayi na tsinci kaina a cikin wata bukka a tsakiyar daji koda na yunkura domin na mike zaune sai naji na kasa domin gaba daya jikina babu kuzari, yayin da na sake yunkurawa domin na yaye mayafin da aka lullube ni dashi akan shimfidar da nake kwance sai naji babu hannuna guda daya na dama, nan take na kwarara wani uban firgitaccen ihu cikin tsananin bakin ciki da razana.
.
Faruwar hakan keda wuya sai ga wani dattijo tare da wata kyakkyawar budurwa sun shigo izuwa cikin bukkar da shigowarsu sai suka durkusa a gabana dattijon ya dubeni a dimauce yace yaro me ya faru gareka ka tsandara wannan uban ihu haka shin wani mugun mafarki kayi ko kuwa wani mugun abune ka gani.
.
Sa adda naji wannan tambaya sai hawaye ya zube mini na dubi dattijon cikin nutsuwa nace me yasa kuka ceci rayuwata baku barni na mutu ba yanzu menene amfanin rayuwata a doron kasa tunda na rasa komai da kowa nawa kuma na rasa lafiyata ina mai rokonku daku gaggauta kasheni yanzu domin na huta da bakin cikin dake nukurkusar zuciyata yayin da na zo nana zancena sai dattijon da wannan kyakkyawar budurwa suka kamu da tsananin tausayina.
.
Dattijon ya kalleni yace samari hakika kana da nisan kwana a duniya domin a tarihin wannan tsauni wanda ka fado daga kansa fiye da shekaru dari bakwai baya ba a taba samun mahalukin daya fado daga kansa ba ya rayu sai kai muma nan da ka ganmu muna zaune a cikin wannan daji mun fitone daga cikin wata babbar kabila da ake kira BANU IKHLAS. kamar yadda sarki shardas ya karar da kabilarka haka muma ya karar da tamu kabilar ni da wannan ya tawa ce zalina kadai muka tsira da rayuwarmu alokacin.
.
Sa adda ya kawo farmaki zuwa kauyanmu nida ita
bama nan muna cikin daji muna yin farauta bayan mun dawo mun iske iyayanmu da yan uwanmu da duk danginmu sun zama gawa sai muka kama kuka mutum daya kacal muka samu da sauran numfashi a jikinsa shine ya gaya mana cewa sarki shardas ne da kansa shida dakarunsa suka zo sukayi mana wannan mummunar barna da dai muka ga cewa ba zamu iya daukar fansa a kan sarki shardas ba sai muka hada kayanmu muka sake komawa cikin daji muka ci gaba da farauta, amma bamu zauna a waje daya ba sai muka ci gaba da tafiya muna ketawa ta gefen garuruwa da kauyuka amma bama zama a inda babu cibiyar ruwa. Tabbas ruwan dake kasan wannan tsauni da ka fado ne ya kawoka nan domin daga can zuwa nan tafiya ce ta kwana saba in da hudu, sa dda mahaifin zalina yazo nan a zancensa sai na cika da tsananin mamaki kuma na sake kamuwa da bakin ciki mara misaltuwa don haka ban san sa adda na fashe da kuka ba ina mai cewa ina ma na mutu ban rayu ba sakamakon fadowa daga kan wannan tsauni tun da yanzu bani da kowa kuma bani da komai a wannan daji, koda jin wannan batu sai tausayina ya kama zalina da mahaifinta zalina ta dubeni tace yakai wannan jarumi ma aboci kwarjini da jarumtaka ka yi sani cewa yadda baka da komai da kowa a wannan duniya haka muma muka kasance ni da mahaifina amma tunda yanzu kaddara ta hadamu mun sameka ka samemu, zaifi kyau mu rungumi kaddara bisa yadda ta samemu mu ci gaba da rayuwa ko don nan gaba mu ga yadda karshen mulkin sarki shardas zai kasance koda kuwa mu bazamu iya ganin karshen nasa ba, ka sani cewa babu wani abu madawwami kuma komai nisan jifa kasa za fado, don haka duk abinda sarki shardas ke takama dashi watarana sai ya fado kasa tunda idan ba mutuwa akwai tsufa akwai lokacin da yanaji yana gani ba zai iya yin zaluncin da yake yi ba yanzu koda mu bamu ga wannan lokaci ba ina son ire irenmu sugani.
.
Lokacin da zalina tazo nan a zancenta sai jikina dana mahaifinta yayi sanyi saboda mun san cewa duk abinda ta fada gaskiya ne, tun daga wannan rana zalina da mahaifinta sukaci gaba da jinyata har na sami lafiya ya zamana cewa ina iya mikewa tsaye na dogara sanda na bisu izuwa daji don yin farauta amma fa duk sa adda na dubi hannuna na hagu naga babu shi kuma naga kafata ta dama ta shagude sai na fashe da matsanancin kuka na bakinciki domin gani nake kamar rayuwata bata da wani sauran amfani duk sa adda na fara wannan kuka sai zalina da mahaifinta sunyi da gaske sannan suke rarrashina na dawo cikin hayyacina....
TSATSUBA
Littafi Na Uku (5)