Gabatarwa
Tsatsuba Book 5 Complete Hausa Novel · about 11 min read
TSATSUBA
Littafi Na Uku (5)
Part A.
Na Abdul'aziz Sani Madakin Gini
Posting By Abubakar Saleh AlQuyraemey
.
Lokacin da jaruma siyama da sadauki darkus suka bingire kasa suna fitar da numfarfashi kamar ransu zai fita a dai dai wannan lokaci ne aka buga gangar tsayar da yaki sannan alkalin gasa ya rugo izuwa cikin tsakiyar fili ya fuskanci jama a yace yaku jama a kuyi sani cewa wannan gumurzu tsakanin sadauki darkus da jaruma siyama babu zakara a tsakaninsu wato sunyi MUTUWAR KASKO don haka zasu sake haduwa a zagayen karshe na wannan wasa wanda za ayi rana i ta yau don haka yanzu zamu kirawo jarumai na gaba domin aci gaba da wannan gasa, gama fadin hakan keda wuya sai aka dauke sadauki Darkus da jaruma siyama daga cikin filin aka kaisu can gefe daya maimakon a shigar dasu cikin wannan asibiti wanda aka tanada domin yiwa jaruman gasar magani, dalilin da yasa kuwa ba a shigar da su cikin wannan asibiti ba shine babu mai wani babban rauni a cikinsu akan hancinsu da bakunansu ne kadai jini ke diga lokacin da jaruma siyama ta dawo cikin haiyacinta sai ta dubi inda su sarki hulbasu ke zaune tana mai mamakin dalilin da ya hana mahaifinta zuwa inda take a lokacin da hankalinta ya gushe bayan an tsayar da wasansu, bisa mamaki sai siyama taga babu mahaifinta a inda yake zaune amma kuma sai taga shardila ta kura mata idanu ko kiftawa batayi duk da cewa kuwa ta rufe fuskarta da bakin kyalle idanunta kadai ake gani nan fa hankalin siyama ya dugunzuma ainun in ba don ma ta hango mahaifiyarta ba ta taso daga inda take zaune ta taho wajenta ba da mikewa zata yi ta bazama mahaifin nata Hailur, da isowar zalima wato mahaifiyar siyama sai ta rungumete cikin murna tana mai yi mata jinjina bisa bajintar da ta nuna a wannan wasa da tayi.
.
A dai dai wannan lokaci ne wani likita yazo garesu da nufin zai duba tafiyar siyama amma sai zalina ta tsaidashi tace babu wani likita da zai duba lafiyar yata face ni don haka mun gode bama bukatar taimakonka, koda gama fadin hakan sai zalina ta bude wani kullin tsumma dake hannunta ta dauko wani ruwan magani a cikin wata yar doguwar kwalba ta mikawa siyama siyama ta karba ta bude murfin kwalbar ta sa abakinta tasha mukurwa biyu kacal sannan ta rufe kwalbar ta mai dawa zalina.
.
Faruwar hakan keda wuya sai jinin dake yoyo a hannun siyama da bakinta ya tsaya cak kamar bai taba diga ba kuma nan take taji duk gajiyar dake jikinta ta dauke fuskarta ce kawai da idanunta a dan kumbure sakamakon naushin da darkus ya yi mata a can gefe daya kuma likita ne ke duba sadauki darkus ana sa masa magani a kan hancinsa don tsaida jinin dake yoyo koda darkus ya dawo cikin hayyacinsa ya waiga bayansa yayi arba da jaruma siyama sai ya daka mata harara yaji ya tsaneta fiye da komai a rayuwarsa, nan take zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone bisa ganin cewa yarinya karama ta gagareshi a filin gasa, nan fa ya fara tunanin cewa ta kowanne hali sai ya kaita kas a zagaye na biyu da zasu hadu wato a wasan karshe da za ayi na gasar idan rana ta zagayo kuma babu abinda zai yi ya dawo da kimarsa da mutuncinsa a birnin face ya kashe wannan karamar yarinya siyama ya zamana cewa ta mutu murus har lahira a cikin filin gasa.
.
Koda mai gabatarwa yazo tsakiyar fili yaci gaba da jawabi sannan ya kirawo sunayan jarumai na gaba wadanda zasuyi fafata a wannan gasa.
.
A dai dai wannan lokaci ne sarki hulbasu ya dubi Hailur yace yakai abokina hakika ka baiwa yar ka horon yaki na ban al ajabi domin ta bani mamaki matuka kuma akwai alamun cewa zata iya lashe wannan gasa amma ka sani cewa lashe wannan gasa ba abune mai sauki ba saboda babu irin abinda jaruman gasar nan basayi don ganin sukai gaci, suna yin tsafi tuggu da makirci iri iri don ganin sun sami nasara ta kowacce hanya don haka dole ne kasa ido akan yarka domin daga yanzu rayuwarta na cikin hadari kada ka tafi izuwa gida kai tsaye daganan ina son ku biyoni izuwa cikin gidan sarautata domin ku dauke hankalin makiya dolene ku sauya gidan zama kuma nima zan baku shawarwari da taimako.
.
Wai shin ma kasan kuwa irin ladan da yarka zata samu idan ta lashe wannan gasa ta jarumtaka ? Koda jin wannan tambaya sai hailur ya sunkui da kansa kas saboda yaga shardila ta kalleshi don kada taga kwayar idanunsa ta shaidashi sai yaki yarda ya dago kansa sa ar ma da yayi ko kadan bata jin abin da suke tattaunawa shi da sarki kasancewar suna magana ne cikin kus kus yadda babu mai iya jin abinda suke tattaunawa
.
Hailur ya risina cikin girmamawa yace yakai abokina wane irin lada za a baiwa yata idan ta lashe wannan gasa sarki hulbasu yayi murmushi sannan yace da farko dai za a bata babbar gona guda daya daga cikin manyan gonakan garin nan gami da dinare dubu dari bakwai sannan kuma zan bata mukamin shugabar dakarun dake tsaron lafiyata muddin zata iya rantsuwa bisa rike amanata da kuma siyar da rayuwarta don kare tawa idan har ta sami wannan mukami zata rinka samun albashi mafi tsoka a kan duk albashin da ake biyan dakaruna daga wannan matsayi kuma zata iya zama sarkin yakin birnin nan gaba daya bayan ta fuskanci wadansu jarrabobi da matakai.
.
Duk mutumin da ya sami wannan dama wacce yarka ta samu dole ne ya fuskanci makiya da yawa daga cikin manyan fadawana domin sun san cewa zai zone yafi su matsayi da arziki, lokacin da sarki hulbasu yazo nan a zancensa sai hankalin hailur ya dugunzuma ainun take yaji yayi nadamar sanya siyama a cikin wannan gasa saboda dalilai guda biyu dalili na farko shine yanzu ya sanya rayuwar siyama a cikin hadari domin zata tara abokan gaba wadanda za su rinka farautar rayuwarta kamar yadda mai jin kishirwa ke neman ruwan sha, abu na biyu kuma idan ta tsallake kowanne hadari da dukkan matakai da zata nisanta dashi inma bai yi sa a ba ya rasata gaba daya kamar yadda ya rasa matarsa shardila wacce ya tabbatar da cewar tana dauke da juna biyu a lokacin da suka rabu.
.
A yanzu da hailur yaga yarima hulkas sai ya fara tunanin ko dansa ne wannan yaro ko kuma dan sarki shardas ne
tabbas babu mai bashi amsar wannan tambaya face shardila da kanta kuma yana shakkar ya sadu da ita domin idan wani daga cikin dakarunta ya gansu komai ya dagule kenan domin sai sarki shardas ya samu labarin cewa yana raye to ba mashi ba matarsa zalima da yarsa siyama ma rayuwarsu ta shiga hadarin da shiba zai iya kare suba hailur ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa yace ta yaya zan iya saduwa da shardila a sirrance ba tare da kowa ya ganni ba ko yaji babu wanda zai iya taimaka mini na iya ganawa da shadila asirrance face sarki hulbasu, hailur baya son sarki hulbasu ya san cewa shine ainihin abokin gabar sarki shardas wanda tuni aka dauka cewa ya mutu tun shekaru bakwai baya, hailu na cikin wannan tunani ne yaji an ruguntsume da wani masifaffen azababben yaki a tsakiyar filin gasa koda ya daga kansa yayi arba da jaruman biyu dake fafatawa a filin gasar sai ya cika da mamaki, ba komai ne ya sashi wannan mamaki ba face ganin cewar dayansu amintaccen yaronsa ne sadauki Ruhaisu jarumin da ya aminta dashi dari bisa dari a cikin dukkanin yaransa lokacin a yake kan matsayin shugaban kabilarsu.
.
Koda hailur yayi arba da ruhaisu sai farin ciki ya lullubeshi domin indai ruhaisu na tare dashi zai iya nemo masa ire iren sauran jama arsu da sukayi saura a raye domin su sake tayar da kabilarsu kuma su taimaka
masa wajan bashi kariya dashi da iyalansa jarumin da yake karawa da ruhaisu kuwa wani narkeken katone wanda ya ninkashi girma da tsayi sau uku kuma a zahiri ma yafi shi surar sdaukantakada jarumtaka ana kiransa da suna Jamar, amma suna fara artabu sai jamar ya raina kansa domin ruhaisu yafishi zafin nama da iya yaki nan da nan ya rikitashi kuma ya kuntatashi sai gashi Jamar yana ta ja da baya kuma yana ta kokarin kare kansa baya ma iya kai hari koda ruhaisu ya tabbatar da cewar yafi jamar iya yaki da fadan hannu sai kafa sai ya shammaceshi ya daka tsalle sama ya doki habarsa da guiwarsa ta dama saboda karfin dukan sai da jamar yayi sama a lokacin da jini yai tsartuwa daga cikin bakinsa yana saman kafin ya fado kasa sai ruhaisu ya kara dukan kirjinsa da karfin gaske kawai saiji akayi jamar ya fado kasa tim kamar giwa ta fadi kuma ya baje kas a sume ko kyakkyawan motsi ba yayi.
.
Koda ganin haka sai filin gasar ya rude da shewa aka kama yiwa ruhaisu tafi da jinjina ba don komai ba sai don saboda shine jarumi na farko da ya fara lashe wasansa na farko a cikin kankanin lokaci da fara gasa tunda ko rabin sa a ba ayi ana gumurzun ba ya sami wannan nasara ana cikin wannan yanayi ne hailur ya dubi sarki hulbasu yace hakika wannan jarumi ya burgeni matuka zan so na gana dashi, koda jin haka sai
sarki hulbasu ya yi murmushi yace ai wannan mai saukine zan shirya duk yadda zaka gana dashi nan ba da dadewa ba yanzu ina so kaje ka ruko yarka da matarka ka shigo cikin tawagata domin mu shiga cikin gidan sarautata tare
.
Koda jin haka sai hailur ya dubi sarki hulbasu cikin alamun damuwa yace bana son na shiga cikin filin nan ranka ya dade ka taimaka min ka aika wani daga cikin hadimanka ya taho da siyama da zalina koda jin wannan batu sai sarki hulbasu yayi murmushi yace shikenan an gama, nan take sarki ya kira wani hadiminsa ya turashi yaje ya taho da jaruma siyama da mahaifiyarta suka shigo cikin tawagar sarki hulbasu.
.
Koda hailu ya yunkura zai mike tsaye daga kan kujerar da yake zaune sai santsi ya kwashe shi ya zame zai fadi kasa a lokacinne rawanin da hailur ya rufe fuskarsa dashi ya zame kafin ya mayar da rawanin kan fuskarsa shadila ta yi arba dashi domin ya hada idanu da ita cikin kaduwa yai sauri ya mayar da rawanin ita kuwa shadila sai ta kame a inda take tsaye saboda tsananin mamaki da kaduwa da murna bata san sa adda hawaye ya fara zubo mata ba...
.
Duk da cewa itama ta rufe idanunta da bakin kyalle sai da sarki hulbasu ya lura da halin da take ciki amma sai ya basar yayi kamar bai fahimci komai ba ita kuwa luzuraina sam bata lura da duk abinda ke faruwa ba yarima hulkas ne ya lura da irin satar kallon da mahaifiyarsa ke yiwa abul siyama kuma yaga sa adda hawaye ya zubo mata, nan take hankalinsa ya dugunzuma ainun ya rasa dalilin faruwar wannan lamari don haka sai zuciyarsa ta kama zargi da wasu wasi amma ya kasa gane abin ma da yake zargi da wasi wasin a kansa haka dai sarki da mukarrabansa suka mimmike tsaye a cikin filin gasar aka kawo musu dawakansu suka hau sannan suka fice daga cikin filin gasar dakaru na zagaye dasu gaba da baya da kuma tsakiyarsu.
.
Ashe tun sa adda aka gama fafatawa tsakanin sadauki darkus da jaruma siyama tuni sadauki darkus ya kebe da wadansu zakwakuran yaransa ya basu umarni akan cewa da zarar sun ga jaruma siyama da iyayanta sun fito daga cikin filin gasar a kashe su a sirrance ba tare da kowa ya gane abinda ya kashe sun ba baya ga wannan mugun abu da sadauki darkus ya shirya ashe shima sarkin yakin sarki hulbasu ma ya tura wadansu yaran nasa ma a sirrance sun je can hanyar bayan gari sun labe rike da da kwari da baka sun dana kawai jira suke suga giftawar jaruma siyama da iyayenta akan hanyarsu ta komawa gida su sakar musu harbi su kashesu lokacin da shi sarkin yaki wanda ake kira suna RINZALU da kuma sadauki darkus suka ga cewa siyama tare da iyayanta sun shiga cika da mamaki kuma hankalinsu ya tashi saboda sun san cewa lallai dukkan shirinsu ya watse, nan take sarkin yaki rinzalu ya nufi tawagar ta sarki da nufin ya shiga cikinsu amma sai yaga dakarun sarki na musamman masu tsaron lafiyarsa sun shiga gabansa sun hanashi shiga cikin tawagar. Al amarin da yai matukai baiwa sarkin yaki rinzalu mamaki kenan kuma ransa ya baci saboda ba a taba hanashi shiga cikin tawagar sarki ba sai yau nan take ya fara tunani a cikin zuciyarsa yace wai shin wane irin matsayi ne da jaruma siyama da iyayanta a wajan sarki hulbasu haka har da yake kare rayuwarsu wai shin ma yaushe ya san su har da suka sami matsayi a wajansa kamar haka amsoshin da rinzalu ya kasa baiwa
kansa kenan haka dai ya hakura yana ji yana gani ya juya da baya yaje ya shiga cikin sauran yan uwansa.
.
Ayi hakuri mu kwana anan sai kuma Allah Ya kaimu gobe da yardar Allah, kafin nan dai ni ɗin ne Abubakar Saleh AlQuyraemey.
--
TSATSUBA
Littafi Na Uku (5)
Littafi Na Uku (5)
Part A.
Na Abdul'aziz Sani Madakin Gini
Posting By Abubakar Saleh AlQuyraemey
.
Lokacin da jaruma siyama da sadauki darkus suka bingire kasa suna fitar da numfarfashi kamar ransu zai fita a dai dai wannan lokaci ne aka buga gangar tsayar da yaki sannan alkalin gasa ya rugo izuwa cikin tsakiyar fili ya fuskanci jama a yace yaku jama a kuyi sani cewa wannan gumurzu tsakanin sadauki darkus da jaruma siyama babu zakara a tsakaninsu wato sunyi MUTUWAR KASKO don haka zasu sake haduwa a zagayen karshe na wannan wasa wanda za ayi rana i ta yau don haka yanzu zamu kirawo jarumai na gaba domin aci gaba da wannan gasa, gama fadin hakan keda wuya sai aka dauke sadauki Darkus da jaruma siyama daga cikin filin aka kaisu can gefe daya maimakon a shigar dasu cikin wannan asibiti wanda aka tanada domin yiwa jaruman gasar magani, dalilin da yasa kuwa ba a shigar da su cikin wannan asibiti ba shine babu mai wani babban rauni a cikinsu akan hancinsu da bakunansu ne kadai jini ke diga lokacin da jaruma siyama ta dawo cikin haiyacinta sai ta dubi inda su sarki hulbasu ke zaune tana mai mamakin dalilin da ya hana mahaifinta zuwa inda take a lokacin da hankalinta ya gushe bayan an tsayar da wasansu, bisa mamaki sai siyama taga babu mahaifinta a inda yake zaune amma kuma sai taga shardila ta kura mata idanu ko kiftawa batayi duk da cewa kuwa ta rufe fuskarta da bakin kyalle idanunta kadai ake gani nan fa hankalin siyama ya dugunzuma ainun in ba don ma ta hango mahaifiyarta ba ta taso daga inda take zaune ta taho wajenta ba da mikewa zata yi ta bazama mahaifin nata Hailur, da isowar zalima wato mahaifiyar siyama sai ta rungumete cikin murna tana mai yi mata jinjina bisa bajintar da ta nuna a wannan wasa da tayi.
.
A dai dai wannan lokaci ne wani likita yazo garesu da nufin zai duba tafiyar siyama amma sai zalina ta tsaidashi tace babu wani likita da zai duba lafiyar yata face ni don haka mun gode bama bukatar taimakonka, koda gama fadin hakan sai zalina ta bude wani kullin tsumma dake hannunta ta dauko wani ruwan magani a cikin wata yar doguwar kwalba ta mikawa siyama siyama ta karba ta bude murfin kwalbar ta sa abakinta tasha mukurwa biyu kacal sannan ta rufe kwalbar ta mai dawa zalina.
.
Faruwar hakan keda wuya sai jinin dake yoyo a hannun siyama da bakinta ya tsaya cak kamar bai taba diga ba kuma nan take taji duk gajiyar dake jikinta ta dauke fuskarta ce kawai da idanunta a dan kumbure sakamakon naushin da darkus ya yi mata a can gefe daya kuma likita ne ke duba sadauki darkus ana sa masa magani a kan hancinsa don tsaida jinin dake yoyo koda darkus ya dawo cikin hayyacinsa ya waiga bayansa yayi arba da jaruma siyama sai ya daka mata harara yaji ya tsaneta fiye da komai a rayuwarsa, nan take zuciyarsa ta kama tafarfasa kamar zata kone bisa ganin cewa yarinya karama ta gagareshi a filin gasa, nan fa ya fara tunanin cewa ta kowanne hali sai ya kaita kas a zagaye na biyu da zasu hadu wato a wasan karshe da za ayi na gasar idan rana ta zagayo kuma babu abinda zai yi ya dawo da kimarsa da mutuncinsa a birnin face ya kashe wannan karamar yarinya siyama ya zamana cewa ta mutu murus har lahira a cikin filin gasa.
.
Koda mai gabatarwa yazo tsakiyar fili yaci gaba da jawabi sannan ya kirawo sunayan jarumai na gaba wadanda zasuyi fafata a wannan gasa.
.
A dai dai wannan lokaci ne sarki hulbasu ya dubi Hailur yace yakai abokina hakika ka baiwa yar ka horon yaki na ban al ajabi domin ta bani mamaki matuka kuma akwai alamun cewa zata iya lashe wannan gasa amma ka sani cewa lashe wannan gasa ba abune mai sauki ba saboda babu irin abinda jaruman gasar nan basayi don ganin sukai gaci, suna yin tsafi tuggu da makirci iri iri don ganin sun sami nasara ta kowacce hanya don haka dole ne kasa ido akan yarka domin daga yanzu rayuwarta na cikin hadari kada ka tafi izuwa gida kai tsaye daganan ina son ku biyoni izuwa cikin gidan sarautata domin ku dauke hankalin makiya dolene ku sauya gidan zama kuma nima zan baku shawarwari da taimako.
.
Wai shin ma kasan kuwa irin ladan da yarka zata samu idan ta lashe wannan gasa ta jarumtaka ? Koda jin wannan tambaya sai hailur ya sunkui da kansa kas saboda yaga shardila ta kalleshi don kada taga kwayar idanunsa ta shaidashi sai yaki yarda ya dago kansa sa ar ma da yayi ko kadan bata jin abin da suke tattaunawa shi da sarki kasancewar suna magana ne cikin kus kus yadda babu mai iya jin abinda suke tattaunawa
.
Hailur ya risina cikin girmamawa yace yakai abokina wane irin lada za a baiwa yata idan ta lashe wannan gasa sarki hulbasu yayi murmushi sannan yace da farko dai za a bata babbar gona guda daya daga cikin manyan gonakan garin nan gami da dinare dubu dari bakwai sannan kuma zan bata mukamin shugabar dakarun dake tsaron lafiyata muddin zata iya rantsuwa bisa rike amanata da kuma siyar da rayuwarta don kare tawa idan har ta sami wannan mukami zata rinka samun albashi mafi tsoka a kan duk albashin da ake biyan dakaruna daga wannan matsayi kuma zata iya zama sarkin yakin birnin nan gaba daya bayan ta fuskanci wadansu jarrabobi da matakai.
.
Duk mutumin da ya sami wannan dama wacce yarka ta samu dole ne ya fuskanci makiya da yawa daga cikin manyan fadawana domin sun san cewa zai zone yafi su matsayi da arziki, lokacin da sarki hulbasu yazo nan a zancensa sai hankalin hailur ya dugunzuma ainun take yaji yayi nadamar sanya siyama a cikin wannan gasa saboda dalilai guda biyu dalili na farko shine yanzu ya sanya rayuwar siyama a cikin hadari domin zata tara abokan gaba wadanda za su rinka farautar rayuwarta kamar yadda mai jin kishirwa ke neman ruwan sha, abu na biyu kuma idan ta tsallake kowanne hadari da dukkan matakai da zata nisanta dashi inma bai yi sa a ba ya rasata gaba daya kamar yadda ya rasa matarsa shardila wacce ya tabbatar da cewar tana dauke da juna biyu a lokacin da suka rabu.
.
A yanzu da hailur yaga yarima hulkas sai ya fara tunanin ko dansa ne wannan yaro ko kuma dan sarki shardas ne
tabbas babu mai bashi amsar wannan tambaya face shardila da kanta kuma yana shakkar ya sadu da ita domin idan wani daga cikin dakarunta ya gansu komai ya dagule kenan domin sai sarki shardas ya samu labarin cewa yana raye to ba mashi ba matarsa zalima da yarsa siyama ma rayuwarsu ta shiga hadarin da shiba zai iya kare suba hailur ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa yace ta yaya zan iya saduwa da shardila a sirrance ba tare da kowa ya ganni ba ko yaji babu wanda zai iya taimaka mini na iya ganawa da shadila asirrance face sarki hulbasu, hailur baya son sarki hulbasu ya san cewa shine ainihin abokin gabar sarki shardas wanda tuni aka dauka cewa ya mutu tun shekaru bakwai baya, hailu na cikin wannan tunani ne yaji an ruguntsume da wani masifaffen azababben yaki a tsakiyar filin gasa koda ya daga kansa yayi arba da jaruman biyu dake fafatawa a filin gasar sai ya cika da mamaki, ba komai ne ya sashi wannan mamaki ba face ganin cewar dayansu amintaccen yaronsa ne sadauki Ruhaisu jarumin da ya aminta dashi dari bisa dari a cikin dukkanin yaransa lokacin a yake kan matsayin shugaban kabilarsu.
.
Koda hailur yayi arba da ruhaisu sai farin ciki ya lullubeshi domin indai ruhaisu na tare dashi zai iya nemo masa ire iren sauran jama arsu da sukayi saura a raye domin su sake tayar da kabilarsu kuma su taimaka
masa wajan bashi kariya dashi da iyalansa jarumin da yake karawa da ruhaisu kuwa wani narkeken katone wanda ya ninkashi girma da tsayi sau uku kuma a zahiri ma yafi shi surar sdaukantakada jarumtaka ana kiransa da suna Jamar, amma suna fara artabu sai jamar ya raina kansa domin ruhaisu yafishi zafin nama da iya yaki nan da nan ya rikitashi kuma ya kuntatashi sai gashi Jamar yana ta ja da baya kuma yana ta kokarin kare kansa baya ma iya kai hari koda ruhaisu ya tabbatar da cewar yafi jamar iya yaki da fadan hannu sai kafa sai ya shammaceshi ya daka tsalle sama ya doki habarsa da guiwarsa ta dama saboda karfin dukan sai da jamar yayi sama a lokacin da jini yai tsartuwa daga cikin bakinsa yana saman kafin ya fado kasa sai ruhaisu ya kara dukan kirjinsa da karfin gaske kawai saiji akayi jamar ya fado kasa tim kamar giwa ta fadi kuma ya baje kas a sume ko kyakkyawan motsi ba yayi.
.
Koda ganin haka sai filin gasar ya rude da shewa aka kama yiwa ruhaisu tafi da jinjina ba don komai ba sai don saboda shine jarumi na farko da ya fara lashe wasansa na farko a cikin kankanin lokaci da fara gasa tunda ko rabin sa a ba ayi ana gumurzun ba ya sami wannan nasara ana cikin wannan yanayi ne hailur ya dubi sarki hulbasu yace hakika wannan jarumi ya burgeni matuka zan so na gana dashi, koda jin haka sai
sarki hulbasu ya yi murmushi yace ai wannan mai saukine zan shirya duk yadda zaka gana dashi nan ba da dadewa ba yanzu ina so kaje ka ruko yarka da matarka ka shigo cikin tawagata domin mu shiga cikin gidan sarautata tare
.
Koda jin haka sai hailur ya dubi sarki hulbasu cikin alamun damuwa yace bana son na shiga cikin filin nan ranka ya dade ka taimaka min ka aika wani daga cikin hadimanka ya taho da siyama da zalina koda jin wannan batu sai sarki hulbasu yayi murmushi yace shikenan an gama, nan take sarki ya kira wani hadiminsa ya turashi yaje ya taho da jaruma siyama da mahaifiyarta suka shigo cikin tawagar sarki hulbasu.
.
Koda hailu ya yunkura zai mike tsaye daga kan kujerar da yake zaune sai santsi ya kwashe shi ya zame zai fadi kasa a lokacinne rawanin da hailur ya rufe fuskarsa dashi ya zame kafin ya mayar da rawanin kan fuskarsa shadila ta yi arba dashi domin ya hada idanu da ita cikin kaduwa yai sauri ya mayar da rawanin ita kuwa shadila sai ta kame a inda take tsaye saboda tsananin mamaki da kaduwa da murna bata san sa adda hawaye ya fara zubo mata ba...
.
Duk da cewa itama ta rufe idanunta da bakin kyalle sai da sarki hulbasu ya lura da halin da take ciki amma sai ya basar yayi kamar bai fahimci komai ba ita kuwa luzuraina sam bata lura da duk abinda ke faruwa ba yarima hulkas ne ya lura da irin satar kallon da mahaifiyarsa ke yiwa abul siyama kuma yaga sa adda hawaye ya zubo mata, nan take hankalinsa ya dugunzuma ainun ya rasa dalilin faruwar wannan lamari don haka sai zuciyarsa ta kama zargi da wasu wasi amma ya kasa gane abin ma da yake zargi da wasi wasin a kansa haka dai sarki da mukarrabansa suka mimmike tsaye a cikin filin gasar aka kawo musu dawakansu suka hau sannan suka fice daga cikin filin gasar dakaru na zagaye dasu gaba da baya da kuma tsakiyarsu.
.
Ashe tun sa adda aka gama fafatawa tsakanin sadauki darkus da jaruma siyama tuni sadauki darkus ya kebe da wadansu zakwakuran yaransa ya basu umarni akan cewa da zarar sun ga jaruma siyama da iyayanta sun fito daga cikin filin gasar a kashe su a sirrance ba tare da kowa ya gane abinda ya kashe sun ba baya ga wannan mugun abu da sadauki darkus ya shirya ashe shima sarkin yakin sarki hulbasu ma ya tura wadansu yaran nasa ma a sirrance sun je can hanyar bayan gari sun labe rike da da kwari da baka sun dana kawai jira suke suga giftawar jaruma siyama da iyayenta akan hanyarsu ta komawa gida su sakar musu harbi su kashesu lokacin da shi sarkin yaki wanda ake kira suna RINZALU da kuma sadauki darkus suka ga cewa siyama tare da iyayanta sun shiga cika da mamaki kuma hankalinsu ya tashi saboda sun san cewa lallai dukkan shirinsu ya watse, nan take sarkin yaki rinzalu ya nufi tawagar ta sarki da nufin ya shiga cikinsu amma sai yaga dakarun sarki na musamman masu tsaron lafiyarsa sun shiga gabansa sun hanashi shiga cikin tawagar. Al amarin da yai matukai baiwa sarkin yaki rinzalu mamaki kenan kuma ransa ya baci saboda ba a taba hanashi shiga cikin tawagar sarki ba sai yau nan take ya fara tunani a cikin zuciyarsa yace wai shin wane irin matsayi ne da jaruma siyama da iyayanta a wajan sarki hulbasu haka har da yake kare rayuwarsu wai shin ma yaushe ya san su har da suka sami matsayi a wajansa kamar haka amsoshin da rinzalu ya kasa baiwa
kansa kenan haka dai ya hakura yana ji yana gani ya juya da baya yaje ya shiga cikin sauran yan uwansa.
.
Ayi hakuri mu kwana anan sai kuma Allah Ya kaimu gobe da yardar Allah, kafin nan dai ni ɗin ne Abubakar Saleh AlQuyraemey.
--
TSATSUBA
Littafi Na Uku (5)