← Book details Sanin Gaibu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 3

Gabatarwa

Sanin Gaibu Part 1 Complete Hausa Novel · about 283 min read

[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Page:01
Sadaukarwa ga Sa'adatu Ambassador, Maman Rumaisah, Shafin gabaki daya ta ce , Na gode da karamcin ki tare da gudummawar da kika bawa labarin nan Allah ya saka da alkhairi 😍🌹


_Shimfida_

"Ummina ki min addu'a!" Ya fada cikin matsanancin azaba, hawaye na zuba mata ta ce mishi. "Abu Turab naga gawar Abubakar ban yi kuka ba, na ga gawar Umar ban yi kuka ba, Abu turab me yasa nake kuka akan ka? Me yasa nake kuka???" Mother tears.......!


Emir of ilorin palace.
𝗔𝘀𝗮𝗹𝗶𝗻𝘀𝘂

Wadanda suka fara zama a Ilorin su ne Baruba wadanda suka zauna a can tsawon shekaru kuma suka dauki yankin nasu ne; sun tafi ba tare da sanin dalili ba. Sai kuma Ojo Isekuse, wani basaraken Yarabawa, wanda ya zauna kusa da dutsen kaifi inda mafarauta suka taru suna wasa da kayayyakinsu. An yi wa Ilorin suna ne bayan da dutsen kaifi da har yanzu yake wanzuwa. Ana zargin Ojo Isekuse ya fita ne bayan ya yi lalata da ‘yarsa, kuma wani dangi mai suna Asaju ya sauka a kusa da dutsen da ake yankan. Bayan Asaju ne mutane da dama suka zauna a kauyuka masu zaman kansu daban-daban da ke kewayen yankin da ake kira Ilorin a yau.

A farkon karni na 19, Ilorin yana arewa maso gabashin daular Oyo, yana da yawan Yarabawa, Hausawa da Fulani. Ya zama hedikwatar wani Janar na Oyo, Afonja, wanda ya kasance sarkin yakin da kujerar Ilorin ce kuma wanda daga baya ya gudu don guje wa yakin kunar bakin wake da aka tura shi ya kashe shi bisa ga umarnin Alaafin na Oyo. Shi kuma wani malamin addinin Islama mai suna Shehu Alimi, wanda ya gudu daga Oyo saboda muzgunawa kungiyar asiri ta Ogboni.

Shehu Alimi da Afonja sun kulla kawance domin yakar sojojin Oyo da ke gaba sannan suka fatattaki sojojin Oyo a yakin farko. Alaafin ya yanke shawarar tura wata babbar rundunar da ta tabbata za ta kashe Afonja tawaye tare da kawar da malamin, Shehu Alimi, wanda ya ba da tallafin soji ta hanyar gayyatar Jama’a. Dakarun Jama’a da na Afonja sun kai wani harin ba-ta-kashi a Oyo-Ile, hedkwatar tsohuwar Daular Oyo, inda suka kona ta.

Ilorin ya zama babbar siyasa da soja bayan faduwar tsohuwar Oyo. Ba tare da sunan shugaba ba, Afonja da Alimi sun ba da jagoranci ga mutanen da ke zaune a yankin. Afonja da Salih Janta, wanda kuma ake kira Shehu Alimi, sun samu kyakkyawar alaka har zuwa lokacin da Alimi ya rasu a lokacin tsufa.

Bayan rasuwar Shehu Alimi, an yi takun-saka da sarautar Ilorin, gari ne mai tasowa. Alfas sun so kafa Halifancin Musulunci bisa ilimi, yayin da Afonja ke shirin sake kafa cikakken mulkinsa, amma Abdulsalam ya fito da taimakon mayakansa. Suna da kwakkwaran iko da Jama'a wanda shi ne mafi yawan sojoji a Ilorin. An kashe Afonja ne a lokacin mulkin Abdulsalam, a lokacin da wata hatsaniya ta barke tsakanin sojojin Yarbawa da Jama’a, wanda ya haifar da matsi na Afonja. An dakatar da addinin Yarbawa da Egungun a Ilorin saboda wannan lamarin. Ilorin ta zama masarautar Khalifancin Sakkwato.[1]

Na wani lokaci, Ilorin ta kasance babbar cibiyar cinikin bayi. A da, an fi tura bayi zuwa arewa ta hamadar sahara, amma yanzu ana tura su kudu ta kasashen Yarabawa zuwa bakin teku don samar da bukatu daga Amurka, Indiyawan Yamma, da Brazil. An kwashe bayi daga kasashen Ibo zuwa gabas da kuma garuruwan Yarabawa da aka ci da yaki, da kuma daga yankunan da ke gaba zuwa arewa, ana cinikin tufafi da sauran kayayyaki.

Ilorin ya ci gaba da fadada kudu har sai da aka duba shi a cikin 1830s ta ikon girma na Ibadan, jihar Oyo. Sojojin dawakan Ilorin ba su da wani tasiri a cikin dajin da ke kudu, kuma a cikin shekarun 1850 Ibadan ta sami damar samun bindigogi daga ’yan kasuwar Turawa a bakin teku.[1] Kamfanin Royal Niger ne ya mamaye babban birnin kasar a shekarar 1897, sannan kuma aka shigar da filayensa cikin yankin Arewacin Najeriya da Ingila ta yi wa mulkin mallaka a shekarar 1900, duk da cewa masarautar ta ci gaba da gudanar.
𝗗'𝗮𝗸𝘂𝗻𝗮 𝘂𝗸𝘂 𝗱𝗮 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝗴𝗮𝗷𝗶 𝘀𝗮𝗿𝗮𝘂𝘁𝗮𝗿.


Saboda irin tarihin da ya ke da shi na musamman na Ilorin, na farko a matsayin Yarbawa daga cikin Daular Oyo, sannan a matsayinta na fulani mai mulkin Halifancin Sakkwato, tana da al’adar yin sarauta wadda ta kasance gauraya da al’adun gargajiya da aka samo daga bangarorin biyu. Duk lokacin da sarautar Masarautar (wadda ke hannun Fulani zuriyar Shehu Alimi) ta kasance babu kowa, wakilin kowace kwata a masarautar wato; Balogun Gambari (Hausa), Balogun Ajikobi (Yarabawa), Balogun Fulani (Fulani) da Balogun Alanamu (Yoruba) - tare da shugaban gidan sarautar Afonja, Mogaji Aare, da kuma babban hakiminsa mai suna Baba. Isale na Ilorin - a taru domin zabar sabon sarki tare da nada sabon sarki, bisa amincewar gwamnan jihar Kwara. Sannan an ba wa Balogun mafi dadewa sarautar Balogun hudu sarautar Balogun Agba, wanda hakan ya sa ya zama na biyu a kan Sarkin Ilorin. Dukkan Balogun na da gundumomi da suke gudanarwa a madadin sarki.

Akwai kuma sarakunan gargajiya da kowanne ake kiransa Daudu (ko Hakimin Lardi). Suna aiki ne a matsayin hakimai masu wakiltar sarki a garuruwan dake fadin masarautar Ilorin kamar su Afon, Bode Saadu, Ipaye da Malete, da dai sauransu.

Lakabi masu daraja a cikin.
𝗦𝗮𝗿𝗮𝗸𝘂𝗻𝗮𝗻 𝗠𝗮𝘀𝗮𝗿𝗮𝘂𝘁𝗮𝗿

Masu mulki
Gyara
Sarakunan Masarautar Ilorin:[3]

Fara Ƙarshen Mulki
1824 1842 Abdusalami dan Salih Alimi
1842 1860 Shita dan Salih Alimi
1860 1868 Zubayro dan Abdusalami
1868 1891 Shita Aliyu dan Shittu
1891 1896 Moma dan Zubayru
1896 14 Janairu 1914 Sulaymanu dan Aliyu
1915 Nuwamba 1919 Shuaybu Bawa dan Zubayru
17 Fabrairu 1920 Yuni 1959 Abdulkadir dan Shuaybu Bawa
30 Yuni 1959 1992 Zulkarnayni Gambari dan Muhammadu Laofe Dan Bawa "Aiyelabowo V"
1992 Agusta 1995[4] Mallam Aliyu dan Abdulkadir
1995 Zuwa Yau Ibrahim Sulu- Gambari
𝗠𝗮𝘀𝘂 𝗠𝗮𝗸𝗮𝗺𝗶𝗻 𝗺𝗮𝘀𝗮𝗿𝗮𝘂𝘁𝗮𝗿
Masarautar dai ta shaidi irin karramawa ga fitattun ‘ya’yan Masarautar da Sarki na yanzu ya yi. Wadannan sunaye ne da aka ba su;[5]

Waziri of Ilorin Emirate
Turaki of Ilorin Emirate
Zanan of Ilorin Emirate
Dan Iyan of Ilorin Emirate
Grand Mufti na Masarautar Ilorin
Madawaki of Ilorin
Malami Ubandoma of Ilorin Emirate
Tafida of Ilorin Emirate
Shettima of Ilorin Emirate
Mutawali of Ilorin Emirate.

August -12- 2009
*10:30pm*
_Hawaye ne ya zubo mata, sakamakon hango shi da tayi yana wucewa duk da kasancewar dare ne amma hasken da ya haska harabar gidan ya hasko mata shi, yana tafiya cikin ruwa dauke da lema, da alamu ita yake nima. Tirjewa tayi mutumin da ya shake wuyarta ya kuma matseta, tare da jin wani bakon al'amari yana ratsa jikinta, cikin tsannanin azaba da masifar da bata tab'a haduwa da shi ba. Wani irin ajiyar zuciya take saukewa, tana jin kamar ta mutu ta huta. Haka ya gama keta alfarmarta sannan ya tashi a kanta, duk da bata ga fuskar shi ba, sai dai kamshin turaren shi ya tabbatar mata da waye a tare da ita. A hankali ta yunkura zata mike suka sake mai da ita, haka su hudu nan suka keta alfarmarta. Kafin daga bisani suka shake ta, sai da suka ga bata motsi sannan suka kyale ta_
******************************************
Sokoto State... Binji LG
Maikulki
Rabewa gefe tayi, ta dauki kokonta ta koma can jikin bango ta tsuguna tana sha hawaye na zuba mata. D'ago fararren idanunta tayi tana kallon Mahaifin su da ya shigo. Yana kallon tsakar gidan, "wallahi duk lokacin da na kalli Sa'adatu sai naji kunya ta kama ni, musamman idan ta fita cikin mutane ana nuna mu. Duk sai naji na muzanta. Shi yasa bana kaunar tana fita da shegen idanunta a wurin." Ya fada yana tsaki. "Larai zuba min abin karyawan nan, kuma ki tabbatar sun shirya su tafi makarantar idan Allah ya jarabce ka da haihuwar bakar ƙaddara babu yadda ka iya, yanzu don Allah taya zata fahimci karatu." Tab'e baki yayi yana kallon matar da ta fito daga madafin. Duban inda yarinyar take tayi na dan lokaci kafin ta ce mishi. "Bawa baya tab'a kaucewa ƙaddaran sa, Malam itama ba sayawa kanta tayi ba, duk da haka ba zai saka mu tsane ta." Ta fada tana wuce shi. Tsaki yayi yana faɗin."haka kawai an tashi an haifa min nakasashiya a cikin Yarana." "Sai ka gayawa Ubangijin da ya baka ita ka ji" ta bashi amsa, daukar ƙara yayi nufi Yarinyar.
Ganin shi dauke da kara yasa ta sake kofin kunun hannunta, ta mike zare mata idanu yayi cikin masifa ya kira Yan uwanta. "Harirah, Rabi" fitowa suka yi sanye da Uniform, fari da hijab din su iya cinya. "Na'am Baffa" "ku bata kayanta itama ta biku tunda abin na munafunci ne ta tafi tunda na san ba gane kome zata tab'a yi ba." "Wai Malam meye Sa'a ta maka ne? Makarantar nan dai wallahi ko kana so ko baka so dole ta je" "Assalamu alaikum, iyyi lafiya?" "Yaya wa'alaikumunsalam sallama, Alhamdulillahi gara da kika dawo wallahi na rasa yadda zan yi da Malam akan Sa'a " kallon shi matar tayi,.kana ganin fuskarta kasan ranta yayi azababben ba'ci." Gyada kai tayi sannan ta nufi wurin Yarinyar me suna Sa'adatu" "Tashi ki shirya yanzu na saka hansiya ta dinka miki kayan ki." Murmushi tayi tana share hawayen ta." "Innah laminde zamu makara fa" "kuje zan kawo ta" "ba da yawuna ba zaki fita na dai gaya miki" Malam ya fada yana kad'a babban rigar shi. Juyawa tayi ta ce mishi, idan kaga ban fita ba, tow bana numfashi shi ne fita ya zama wajibi ne" ta riko hannun Sa'a ta kaita banɗaki ta wanke mata jiki, zasu fita ta riko hannunta. Ta kanne mata ido daya, tare da mata alamar ta mata wanka kawai don Allah. Murmushi tayi tana faɗin."Sa'ade zaki makara dai" hakan ta kuma dibo ruwa ta mata wanka tass. Sannan ta fito da ita shirya ta tayi, ta dauko mayafinta tana faɗin. "Larai bari na kai Sa'a makarantar." "Tow Yaya sai kin dawo" bata ga malam a cikin gidan ba, alamar yana kofar gida, koda ta fita ta same shi tare da mazan makotar su.
Haka ta wuce su, bata mishi magana ba. "Aminu idan Sa'ade ta kara girma ka aurar da ita mana tunda kaga ita Uwarta bata san harkan arziki ba." Kallon mutumin yayi kafin ya ce. "Ilya babu me auren Sa'adatu, duk da ni kaina nasan duk cikin Yarana babu me kyanta kuma ba za a kuma samu ba, sai dai ina jin takaicin haihuwar ta da aka yi a gidana babban kuskure na, shine gaya mata Yarinyar zata tafi kurmi niman kudi gashi abin haushi daya yadda Uwar lamaran ta kwadaita min arzikin da suke samu. " Shiru suka yi kafin Malam Musa ya ce mishi. "Kuma kaga kuma Laminde bata kyauta ba, ai bai dace ta kai ka gidan me gari ba domin dai nasan idan kuka samu arzikin nan tare zaku ci shi,ba kai daya ba waye ya sani ko har da Hajji zaku tafi." Kwafa. Malam Aminu yayi yana faɗin"Yo shima me garin ai bakin munafiki ne, ina cewa kin min magana yayi sai ganin dogarai kawai bisa kaina, wai daga gidan Hakimin Binji" kwafa ya kuma yana kallon hanyar da suka bi, yana tuna irin cin zarafin da aka mishi, anan yaji wani yana cewa za a kara musu malaman makaranta. "Tass mai gari ya ci zarafina, da goyan bayan hakimi, duk amanar da yake tsakanin mu na tsawon shekaru wai don Laminde ta kai ƙarata akan nakasassshiyar yarta ya zauna ya tsefe ni kamar ya samu kitso har da cewa bani da imani. Waye zai yarda a haifa mishi nakasashe kuma abin takaici nifa ban hanata kome ba, Bara kawai zata tayi mu samu kayan alatu amma uwar ta hana mu na dai san da ace ta tafi meye ba zamu samu ba? ?" "kai Malam Aminu ka ji tsoron Allah bayan haihuwar ta tasamu ciwon ba haifarta kuka yi da shi ba." "Eh meye maraban dambe da fada? Gaya min meye bambancin? An haife ta da shi ko ta samu ai duk daya ne, babu abin da ya min ciwo kamar kashe kudina da nayi na bin hawa, sannan itama Laminde aka saka ni na biya mata, Allah ya isa min" ya fada kamar zai yi kuka.
.... Inna Laminde har kofar aji ta raka Sa'ade. Sannan ta leka ajin, "Malam ayi hakuri ta makara " "Ba kome innah " "mun gode sosai" sannan ta nuna mata cikin ajin, rike yar jakar buhun simintin ta tayi me littafi kwaya uku. Zama tayi Innar ta leke ta, tare da d'aga mata hannu. Bata fuska tayi kamar zata yi kuka. Domin rashin yarda irin na Sa'ade. Murmushi Inna tayi ta bar makarantar.
A hankali taji hawaye ya zubo mata, tausayin rayuwar Sa'a take, tayi kankanta da fuskarta al'amari me girma haka. Sai dai kamar yadda Uwani matar me gari ta gaya mata dole ita zata tsayawa Sa'a..
Asalin su yan garin Maikulki ne, ko nace mazauna garin. Fulani ne da suka fito daga yankin sahara, domin yanayin su ya fi kamancecceniya da bororoji. Sai dai su fararren ne, ba bakaken fulani ba. Duk da suna yawo ne da dabobbi kafin su zauna a garin Maikulki na karamar hukumar Binji, Garin...
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Dedicated to Handicapped ❣️😓

```Ina mata yan kamshi matan yan yayi TOH ga turaren mu nan.
Ga turaren orientica kuzo kusiya arha kwasha kwasha 1700```
Page:02
Gari ne mai cike da albarka, lokacin da suka zo garin tana amarya kusan shekaru arba'in kenan. Tana da yara shida da Malam Aminu, uku maza maza uku mata. Haka abokiyar zaman ta, Larai tana da yara biyar. Ƴaran Inna Laminde sune manya akwai Zakari ya'u, suna kiran shi Ya'u sai Yusuf suna kiran shi Dabo,sai Ibrahim suna kiran shi Iro, sai Alaweeyah suna kiran Addah Weeyah sai Shamsiyah tana kiran Maman Sailuba, sai Auta wacce haihuwar yazo mata a bazata domin a tunanin su tun kan Shamsiyah don sai da ta girma sosai domin takai shekaru goma aka haifi Auta Sa'ade. Ya'u yana zaune a Sokoto shi da iyalin shi, domin da taimakon Allah da samun jajjurtaciyar Uwa Ya'u ya samu ilimin boko, na Addini kan dama suna yi. Na bokon ne Malam Aminu yaki cire kwandalar shi su amfana da shi. Fadin irin wahalar da Inna Laminde ta sha akan Yaran ta sai Allah, domin har surfe sai da tayi ita burinta Yaranta su samu ilimin. Alhamdulillahi Ubangiji ya dafa mata domin bayan Ya'u ya samu diploma akan aikin jarida, wata gidan Radio a sokoto ta dauke shi aiki, dama Yusuf yana na shi karatun domin shi jami'an danfodiyo ya samu, inda yake bangaren kimiyya kere-kere. Iro kuwa kasuwanci ya faɗa, domin yaki bokon tunda ya gama secondary ya ajiye boko, sai Allah ya saka mishi albarka shi kan yana garin Binji a can yake kasuwancin shi. Wani ikon Allah yaran duk sun san wahalar da Uwar su ta sha, haka yasa basu da wacce suka sani sai ita. Ɗakinta kuwa da ita kanta da suturan da take sakawa wallahi zaka dauka wata hamshakiya ce, nan kuwa ba kowa bace. Duk karshen wata suna hanyar me kulki dukkan su kuwa. Haka yana mugun yiwa Malam Aminu ciwo duk da ya hana su, moran shi amma Yaran basu mishi kugunta ba. A kome sukawa Mahaifiyar su zasu mishi, shima albarkacinta yake ci. Ba karamin al'amari ba ne domin lokacin da suka ce su boko zasu yi ba zasu yi kiwo ba, cewa yayi sai dai tana fita mishi da kiwo. Haka ta amince dake tana da wata kawa matar mai gari ita ta bata Shawaran ta saka Yaranta a makarantar boko, babu amfanin barin su suna yawo a daji da sunan kiwo. Ita kuwa ta amince. Shine fa aka fara samun matsala da Malam Aminu. Har aka haifi Sa'ade yarinyar ta taso cikin kulawa da soyayyar yan uwanta. Musamman Addah Weeyah da ta kusan aure. Domin itama tayi karatu har zuwa aji uku na secondary su, kafin Uban ya daka tsalle ya ce bai iya ji ba, duk da kiri-kiri yake fifita yaran Larai akan Yaran Inna Laminde. Yaran Larai sun, Yakubu, sai Jamilu, Ikilima tana aure, sai Harirah da Rabi. Ikilima tana aure a Binji gidan Sarkin Fulani. Domin Larai Mahaifiyar ta yar gidan ce, Malam Aminu kyakyawan gaske ne, idan ka gan shi ba zaka tab'a yarda shi ya tara Yara har goma sha daya haka ba. Haka itama Innna Laminde tana da kyau na asalin Fulanin Somalia. Laluran Sa'ade ya faru ne sakamakon cutar bakon dauro da aka yi, wanda kowa yasan yadda ciwon yake,. Shi ya tab'a mata wuyarta da kunnen ta daya. Bata ji da kunne daya sannan bata magana. Domin tana da shekaru biyar ciwon ya same ta, da farko har an fasa kukan ta mutu, sai da aka zo mata wanka sai a ka ga tana da sauran numfashi. Haka ta sha jinya kafin Allah ya bata lafiya. Sai dai fa bata hmm-bata humm- haka laluran ya same ta. Yayunta har asibitin Udut suka kawo ta, amma ba baki ba ido a lokacin karfi imani ne kawai yasa Inna Laminde bata mata fatan ta mutu kowa ya huta ba. Gashi a lokacin bata isa ta fita wasa ba, idan yara suka mata magana suka ga bata amsa ba, sai su watse su barta. Idan tana jin wuyan haka zata zauna tayi ta kallon uwar hawaye na zuba mata, sai taga kwano zata dauka tana budewa. Akwai lokacin da Inna Laminde ta tafi zaman bikin Ikilima da ta haihu, Yarinyar nan ta sha wahala domin ba kowa ke gane abin da take so ba, dama idan Innarta tana nan kwanciya take a jikinta ta hakan take fahimtar bata da lafiya. Sai kuma idan tana jin yunwa zata yi ta buɗe kwanika tana kuka. Tow tunda uwar ta tafi dake tana da kulafuci, don ta Uwar ce tare zasu tafi malam ya hana wai zata ja mishi magana a ce gidan shi a kwai kurma. Haka ta tafi tabarta cikin jinya domin bata da lafiya sosai, ita kuwa Inna Larai bata sani ba, sai da ta kwana bata ga tazo taci abinci ba, shi ne da safe ta leka dakin nan ta ganta a gadon bunun Innarta, yadda ta d'aga labulen dakin ta bude idanunta da suka yi jajjur, tana kallon ta kafin hawaye ya zubo mata. "Ni Maimunari yarinyar nan Allah yasa ba wani abu ke damunki ba" ta shiga ta tab'a kanta, jin yadda ya dauki zafi yasa ta fitowa ya cewa Malam da yake zaune a tsakar gida. "Malam taimaka ka bani cafeno yarinyar nan bata da lafiya, jikinta yayi zafi sosai." "Ke Larai bana son munafunci, ta mutu mana ko an gaya miki ina mara ba ita ne gara ta mutu kowa ya huta." Shiga ɗakinta tayi ta bankade zanin gadonta ta dauki kudi, ta fita yana mata magana amma ta bawa banza ajiyar shi yaji haushi kuwa, haka ya shiga dakin da tsumagiya ya shiga zane Sa'ade. Ga ciwo ga duka, Allah ya gani ya tseneta kamar ya kashe ta, yana cikin dukarta Inna Larai ta shigo gidan. Dakin ta nufa da ta ga takalmin shi. Ganin yadda yake dukar ta yasa fasa ihu, don ta suma. Fada sosai suka yi da Malam ta maida Sa'ade ɗakinta domin Rabi da Harirah sun bi Inna Laminde sunan Ikilima. Fadar irin kiyayyar da Malam yake nunawa Sa'ade sai ya baka mamaki. Haka ta taso da mugun tsoron shi, tana ganin yadda yake dariya da farincikin da yan uwanta amma ban da ita.
Lokacin da ta cika shekaru tara Ya'u da Yusuf sun tsayar da shawarar su tafi da ita wurin su, amma bawan Allah nan fir yaki kuma ya hana a sakata a makarantar. Haka suka hakura itama bata son nisa da Innarta. Ana haka wata mata da take zuwa sayan madara a gidan ta jima bata zo ba. Dama bata da aiki sai daukar yara tana kaisu birni aikatu, masu laluran kuma tana kai su irin su Abuja da Lagos bara. Haka yasa ta wannan zuwan da zata koma an bata sakon madara zata saya shi ne ta ga Sa'ade, shi ne ta tuna akwai wani me kudi a can Lagos da ya ce ta nima mishi kurma mace ko namiji zai dauki nauyin a mishi jinya. Ganin Sa'ade yasa abin da take hangowa zata samu ya kara rikita mata lissafi, tasan Malam Aminta da mugun son abin duniya, don haka tana gama amsar madaran ta dauki kuɗi me yawa ta bashi kudin madaran sannan ta bawa Sa'ade kudi me yawa tana faɗin. "Malam Aminu ga arzikn a cikin gidan ka, amma ka kasa amfana da shi, gaskiya ya kamata ka san darajar haka." Ta fada tana kallon Sa'ade. "Kina nufi wannan abin Arziki ne? Hhhhh" ya fashe da dariya, yana nuna Sa'ade da take zare idanu. Domin tasan duk lokacin da Baffan su ya nuna ta yana magana tow ba abin dadi yake fada akan ta ba. Mikewa tayi daga bawa dan ragon ta madara a fidinbotul,ta koma dakin Innar su. Da take kallon kofar dakin. Kallon juna suka yi ta koma bayan Inna Laminde ta kifa kanta tana sauke ajiyar zuciya, hawaye ne masu zafi suka zubo mata, tana matukar tausayin yarinyar da bata ji ba bata gani ba. Malam Aminu suka fita da Tabawa, anan ta tsara shi da kudin da zai samu, akan Sa'ade, ta mishi alkawarin wani sati zata zo in sha Allah. Bai fadawa Inna Laminde ba, kawai yayi gaban kan shi. Sati na zagayowa kuwa sai gata da uban kudi dama tun ana gobe zata zo, ya ke cewa Inna Laminde ta shirya Sa'ade gobe tabawa zata zo ta tafi da ita. Aikuwa tace bata san zancen ba, duk abin da za ayi sai ayi. Yarinya shekara tara ya hana a saka a makaranta sannan ya ce za a kaita wani wuri. Haka suka kwana suna rigima, washi gari sai ga Tabawa ta zo, ganin da gaske rabata zasu yi da Yarta. Don haka bata yi kasa a gwiwa ba, ta dauki yarinyar suka nufi gidan Mai gari, tun safe ake babu ɗaya shi kuwa ya kafe sai an tafi da Sa'ade, Mai gari ganin al'amarin yafi karfin shi yasa su a gaba har zuwa gidan Hakimi. Anan aka yi ta ta kare, har yake barazanar sake ta, dake suna shiga garin Binji ta samu wani Yaro a gidan Hakimi ta tura shi ya kira mata Ibrahim, can sai gashi a gaban shi aka yi Shari'ar inda Hakimi yasa a bincika mishi Makarantar Maikulki ko akwai malamai, nan me gari ya gaya mishi babu wasu malamai ba sai an kai da bincike ba, a duba kodan rayuwar Sa'ade. "Zan yi magana da shugaban karamar hukumar Binji zai yi magana Baturen ilimi in sha Allah za a kawo ma'aikata da yarda Allah, ita kuma Sa'adatu Mai gari idanun ka ya tsaya akan ta, sannan duk abin da yake tafiya zan na tuntubar ka." "In sha Allah zan saka Idanu " "kai kuma wallahi naji labarin wani abu ya kuma faruwa sai na tura sakon zuwa shugaban ƙaramar ƙungiyar kare hakkin dan Adam sun daure ka. Kuma itama Tabawa a gaya mata ta bar kasar Binji kafin na same ta." Da wannan aka kashe zancen, Allah da ikon shi ya hadata da matan me gari, tayi ta bata shawara. Yadda zata kula da Sa'ade. Koda suka dawo gidan ma tashin hankali da masifa, dama shi Ibrahim tun a can ya bawa Babar su hakuri domin yasan halin Baban su, ba zai iya rigima ba. Haka ya tasata a gaba da bakar magana kamar zai doke ta. Laminde ke nan, a yayinda takwarorinta suke kurmi da kudu niman abin Arziki shi ne zaki tozarta ni ta hanyar kai kara na, gidan Anamimin can wato ki jindadin ayi min dariya tow na gode tunda a iya gidan hakimin Binji kika tsaya na zata zaki wuce har lahira ne da ni. Karewar Gidan hakimi, tow wallahi na rantse da Allah babu hannuna a kan Yarki ku nima mata wani Uban ba ni ba." Haka gefe guda Abokan shi zuga shi suke akan Laminde tafi ƙarfin shi ashe kuri yake da karyan yafi karfin gidan shi. Ita kan Inna Larai babu ruwanta domin har ita bai kyale ba, shi yasa bat shiga cikin hayaniyar su.
--- a dawo labari.
Federal Ministry of education
Sokoto State
Kamar yadda Hakimi ya tura sakon shi, haka Shugaban karamar hukumar Binji ya tura zuwa ga Commissioner ilimi. Dr Sharif Hamidu. Kasancewar yau satin shi biyu da dawowa daga Umra. Ya kuma yi daidai da kwanakin da ya ɗauka na Hutu. "Yallabai akwai takardun da aka turo da kuma na aiki, daya daga karamar hukumar Binji. Kwantomar Binji da kan shi ya kawo yana bukatar a baka sakon" kallon sakataren shi yayi kafin ya ce. "Ok na ga ni" mika mishi takardan yayi, ya duba kafin ya zuba mishi idanu. "Suna bukatar malaman makaranta ne." "Tow ko za a tura wurin me girma Gwamna ne" girgiza kai yayi sannan ya ce. "A tura musu yan bautar kasan da za su yi service makarantun mu, sannan zan tuntubi me girma Gwamna da maganar." "In sha Allah za ayi haka." "Allah ya sa" ya furta,
Fita sakataren yayi shi kuma ya fara aikin shi da ya bari. Yana nazarin maganar da shugaban karamar hukumar ya turo mishi. Akwai yara masu yawan gaske da suke buƙatar kulawar Malami da gwamnati, a halin da ake ciki har an fara diban yaran nan zuwa birane domin niman kudi wasu Bara, da sauran su. Babban abin damuwar yarinyar da ake son a fita da ita bata ji bata magana kuma a haka za a fita da ita birni ba a san inda za a tsaya da ita ba. Cire glass din shi yayi yana mamakin wannan al'amarin. Me ya dace su? Dole a tura musu malaman, wayar shi ya janyo ya gwada kiran me girma Gwamna...
ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*

Page:03
Kiran wayar yayi bai shiga, iskar bakin shi ya furza, sannan ya cigaba da aikin gaban shi. Yana kara nazarin yadda zai ɓullo al'amarin. Domin yana son lallai a tura malamai da yan bautar ƙasa kananun hukomammin da ƙauyukan da suke cikin su. Haka ya zauna yayi dogon rubutu zuwa mai girma gwamna,
^^°°••
Kan wuri unguwar Sarki.

Fadar Sarkin Musulmi.
Alhaji Shehu Abubakar Shehu, shi ne mai martaba sarkin Musulmai, sarki na goma sha shida, Allah ya albarkace shi da nisan kwana tare da iyali masu yawan gaske, daga cikin yaran shi akwai manyan mutane kuma jami'in gwamnati da sauran su. Kananun yaran shi sune waɗanda suka gama secondary, yan mata biyu. Yayun su maza sun gama jami'a suna bautar ƙasa.
... Bangaren shi kan sa mai Martaba, babban sashi ne me cikin gashin kan sa. Zaune yake a falon shi hannun shi rike da tangaraho, yana amsa magana da ita. "Kuma kun bincika kome? Yana da kyau kafin ka zartas da hukuncin ka fara bincike, ban ga kome a tattare da shi ba, sai gaskiyar shi da nagartar shi. Karka manta mugu ko mutumin banza baya zuwa inda nake, kai ko laifi yayi ba zai tab'a zuwa inda nake ba, balle har ya samu damar zama a cikin gidan nan ka sake tunani kar ka lalata alaƙar ka da d'an ka domin wani abin da baka da sanin faruwan shi." Sun jima suna magana kafin ya katse wayar da addu'a. Kallon Hajiya Umma yayi uwargidan sa, mace me nutsuwa da kamala. Ga hakuri da juriya hadi da kawaici me yawan gaske. Kowacce mace da tazo gidan bayan ta ce, babu macen da ta sha wahala da Mai Martaba Shehu Abubakar Shehu irin ta, domin auren su na hadi ne, tasha azaba da zilla. Shi yasa har kwanan gobe shi da kansa yake jin kunyar kallonta, domin akwai wani abin da ya mata har yau tabon yana kan fuskar ta. "Ummul Hafsah." Ya kira sunan ta a hankali, yana kallonta. Yadda ta tattaro nutsuwar ta akan shi, yana daga cikin abin da yake kara kashe shi a kaunar ta, yadda duk yadda ya kirata tow zaka samu tattara kome ta ajiye ta mai da shi sama da abin. Riko hannunta yayi cikin na shi, a kalla auren su zai kai shekaru hamsin da wani abu. Yadda take kallon shi ya saka mishi wani irin nutsuwa. "Ina jin ka mai Martaba" ajiyar zuciya ya sauke yana gyada mata kai. "Ummul Hafsah! Misali Muhammad Rabi'u aka zarge shi da laifi me zaki yi akan shi?" "Ban fahimci abin da kake nufi ba?" "Ina nufin Muhammad Rabi'u a zarge shi da kisan kai me zaki iya yi dan wanke shi?" Rike hannun shi tayi tana kallon shi. "Zan hana idanu na barci na gayawa Allah matsalata, sannan na nemi taimakon shi ya fitar da gaskiya." "A matsayin ki na uwa me zaki yi bayan haka?" Ya kuma wurga mata tambayar da yasa ta kura mishi Idanu. "Ba zan gushe ba sai na tabbatar da cikakken gaskiya ta hanyar binciko me laifin , sai dai idan an fi karfina na zuba idanu na cigaba da gayawa Allah halin da muke ciki " matse hannunta yayi a hankali sannan ya cigaba da cewa. " Halin da Yaron nan yake ciki kenan Allah ya kubutar shi" "wani Yaro kenan? Ba dai dan Badi'atul Noor ba?" Ta tambaye shi jikinta yana rawa. Murmushin karfin hali yayi ya riko hannunta. "Ita Ummul Hafsah" janyota yayi jikin shi. "Kar ki karaya, kar ki bari Yaran su san halin da ake ciki domin zai iya shafar kwanciyar hankalin su da shi kan sa Yaron don Allah ki manta abu me muhimmanci yazo yi isa aka d'aga mishi hankali ba zai yi ba, sannan tun daren jiya Badi'atul Noor ta kira ni, ta gaya min halin da take ciki da matsalar da take kai. Sai yau Abdulrahman ya kira ni shima ya gaya min bana son a kai ga Yaron ya sani. " Cikin sheshekar kuka ta ce "tow in sha Allah " amma tsakani da Allah ta kad'u domin sanin da tayiwa Badi'atul Noor akan Yaranta bata wasa a kan tarbiyyar su, musamman wannan da ake zancen akan shi.
Kasancewar safiya ce kuma lokaci ne na zafi sosai. Ila kowa yasan yadda ake zafi a Sokoto. Sanye yake da sport wear. Sai facing cap, ƙafan shi sanye da takalmin kamfanin Fila. Gefen shi Yarima Sadeeq Autan Ummul Hafsah, a hankali suka fito shi Yarima Sadeeq yana kan keke shi kuma yana tafiya da kafar shi wato yana jogging. Haka suka tafi garin babu wani cunkoson mutane. Haka suka yi ta tafiya, "A.A baka kira gida ba ne?" Murmushi yayi yana cigaba da tafiyar shi har suka isa inda zasu motsa jikin. Wayar shi ya ciro ya gwada kiran Number gida har ya karaci ringing babu wanda ya dauka. Kamar ba zai magana ba, ya d'ago kai ya Kalli Sadeeq cikin sanyin murya sanan ya ce mishi. "Na kira basu dauka ba." "Amma kuma lafiya dai?" Shiru yayi yana kallon wasu matasa biyu yadda daya yake rike da hannun dan uwansa suna tafiya a hankali. Janye idanun shi yayi daga kan su, ya mai da hankali shi kan Yarima Sadeeq. "Wani abu ka ce?" Murmushi yayi yana faɗin "hankalin ka yana wani wurin ina zaka fahimce ni, mu karasa abin yake gaban mu " Haka suka gama yar tsalle tsallen su sannan suka wuce gida, wanka suka tare da shiryawa cikin shigar kayan bautar ƙasa, suka nufi sashin Hajiya Ummul Hafsah. Anan suka karya tana jan su da hira. Shigowan wasu yan mata biyu, suka nufi Ummul Hafsah suka gaida ta, sannan suka Juyawa kan su Sadeeq da A.A suka gaida shi. "Wadannan Kannen na ne, ita wancan sunan Nimrah sai wannan Amirah Yaran Amryan Mai Martaba ne" Sadeeq ya fada mishi haka, gyada kai yayi sannan ya mai da idanun shi kan Ummul Hafsah ya ce mata. "Ko kin yi magana da Ummina? Ina ta kiran su tun ranar da nazo ban same su ba, idan ya shiga basu dauka don Allah ki kira min ita mana" yayi maganar kamar zai rusa ihu, tabbas ya sakankance dayawa duk da yana da Yayu manyan kuma maza waɗanda basu zaman kasar baki daya, amma shi har yau kamar Baby ne a wurin Ummin shi, kasancewar shi Auta da Ummin shi take masifar kaunar shi. Wani irin kauna ce me zafi tsakanin shi da Mahaifayar su. Yadda ya tsare ta da idanu yasa babu shiri ta janyo wayar ta, Blackberry cobbler, ta kira layin ta. Sai da ya gama ringing sannan ta yanke. Sake gwadawa tayi ai kuwa ta dauka. "Sultanah Badi'atul Noor!" Da sauri ya sauka akan kujeran cin abincin ya koma gabanta kamar zai shige jikinta. "Baba karami yake son magana dake" "Ki bashi" mika mishi wayar tayi. "Ummina me yasa Ummul Mansurah bata daukar wayata? Ummina har sako na tura mata bata dauka ba, please Ummina ki taimaka min ta min reply" "hmm bata nan ne kuma na amshe wayar." "But why?" Yayi maganar a shagwab'e yadda zaka fahimci shi din Babyn Ummin shi ne, zaka iya rantsewa da Allah a gabanta yake, domin yadda yake narkewa like zai shiga cikin wayar ita kuwa a can wani irin tausayi yake bata. "Ummina rabona da ita yau kwana biyu fa" "ban ji me kace ba?" Ta tambaye shi a hankali, "Ummina ina ranar da ta turo min sako na tawo part din Grandma nazo na dauke ta? Tow rabona da ita ke nan" "na tuna shi kenan " ta ce mishi, "Ummina don Allah ki ce ta turo min da sako ina jiran ta" abin ya bawa Sadeeq da Ummul Hafsah mamaki, ashe dama haka yake da magana, baki daya ya koma kamar me cutar hakori. Haka suka fita. Sadeeq ya kalle shi, sannan ya fashe da dariya. "Dama haka kake Prince? Na zata duk wannan kamewar da rashin walwala duk cikin jinin sarauta ne" bai tsammaci zai amsa ko yayi wani babu ba sai gashi ta fashe da dariya shima, cikin walwala da farin ciki ya ce. "Ummina da Dad, Ya Abubakar, Ya Umar, Aunty Zakiyyah, Aunty Rumaisah, sai Gran princess Ummu Mansurah, sune farin cikina, bani da wasu bayan su, mulki ko isa, kasaita ko d'agawa basu cikin abin da yake gabana. Ni free Man ne, ina son Freedom, ko rashin maganar da kuke gani bana yi rashin sabo ne. But tunda nasan Ummina da Ummanku, yan uwa ne sosai naji zan iya spending rayuwata a sokoto ka fahimta?" Ya fada yana zuba hannun shi a cikin aljuhun wandonsa yana me d'aga kafad'ar shi. Yayi wani kitty face. Irin fuskar mage nan.
•••°°
Maikulki.
"Malam Aminu, shin baka ji labarin tallafin da gwamnatin tarayya take bawa nakasasu ba? Jiya ina jin labaran BBC Hausa, naji an kawo tallafin nan Sokoto, a madadin makarantar da zaka kaita me zai hana ka shirya ta ku tafi birni a baka taimako kai ne baka sani ba, amma Arziki ne a cikin gidanka fa. " Shiru yayi yana kallon Malam Musa, kafin ya ce "eh tow zan yi haka, amma yanzu kaga yau juma'a tana zuwa Binji wurin yayanta, idan na ce zan yi wani abu Laminde da wancan Annaminin zasu yi magana zan bari sai ranar sati Laraba sai na nime sa'a," "yawwa kaga kasami hanyar kutsawa da ita niman taimakon za a mata aikin kunne da baki kafin ace me ka tara kudi sai ka tashi gini ka auro bazawaran nan, tunda ba zaka iya sayar da shanuwarka ba" "kai Malam Kalla Ubangiji ya biya."
"Kar ka damu zaman tare yafi karfin haka, dole na tsayawa abokina irin ka, ga arzikn har akwai macen da zata maka bakin ciki da shi? Bata isa ba wallahi sai mun mori kayan mu ka kwantar da hankalin ka, an yi an gama yarinya takace kuma dole ka mori nakasar ta haka kawai za a ce baka isa ba. Inji Uban waye?" "Bari naje gidan ma wannan yarinya ba karamin takaici nake ji ba, amma yanzu da nasan zanci moriyar ta zan rage takaicina akan nakasarta. Haka ya baro gindin maina yana ayyana yadda zai tafi Sokoto da Sa'ade.
.....
Yau ma sai da aka mata wanka domin shegen tsaftar da Allah ya daura mata, shafa mata man gyatuma radau Inna Laminde tayi hannu da kafa, sai ta fito shar amma abin ka da wanda ba a iya mishi sake daukar man tayi, ta shiga shafawa a jikin ta zaka rantse da fadawa cikin mai, musamman yadda tayi naso. D'aga labulen dakin Malam Aminu yayi ta sake roban tayi a rikice, tana zare idanu waje. "Yar banza me kama da mayu." Ya fada yana shiga dakin, dukar da kai tayi kasa tana kallon yadda hawayenta yake d'iga. Wani irin lafiyayyen rankwashi ya sakar mata wanda yasa ta zaman dirshan. Tana sosa kanta, sake zuba mata rankwashin yayi fitsari ya kwace mata, "shegiya ba yau naso ki mutu ba, da na kyale ki shi ne ba zaki taya ni ni man arziki ba, ba banza Allah ya barki baki magana baki ji da kunn..." "Allahu Akbar! Ashe haka kake malam? Kashe min Y'a zaka yi? Me Bimbi ta maka? Meye ta tsare maka?" Juyawa yayi cikin borin kunya ya kalle ta yana inda-inda. "Yarinyar nan sai da nace miki matsiyaciya kika haifa amma fir kika ki ganewa, so nayi tuntuni ta mutu amma kika ki gata nan tana min kafar angulu, ita bata rayu cikin Mutane masu hikima da lafiya ba, gashi ta rayu cikin nakasasu taya zan ji farin cikin ganinta shegiya munafuka wallahi na gaji da ganin ta, Anya kuwa jini na ce ita?" Zaro idanu Inna Laminde tayi tana dafe kirjin ta. "Innalilahi wa'inna laihil raju'un Ubangiji ka hana kunne na jin mugun ji da mugun gani Malam karka sheganta min Y'a mana, ba ita tayi kanta ba malam" ta fada kuka yana kwace mata. "Tow wallahi idan har kina son na amince da ganinta a matsayin jini na ki cire hannunki akanta" "wacce irin rayuwa ce haka Malam? Gaskiya ba zan iya ba" "tow wallahi tayi ta ganin ukubar rayuwa kenan. Domin ba zata tab'a ganin farincikin a cikin gidan nan ba" ya saka kai ya fice a dakin yana mita. Zama tayi a bakin gadon tana kuka, daga ita har Sa'ade babu me bawa wani hakuri. Tashi tayi tana goge hawayenta, ta dauki kayan Makarantar ta, ta saka sannan ta saka hijab ɗinta, da jakar buhun simintin ta fito tana tafiya a hankali kamar wacce kwai ya fashe mata. Har ta fito gida kanta a sunkuye yake, bata yarda ta kalli sama ba, domin a tunanin ta Baffan su yana kallon ta, kuma zai iya make ta, Allah ya zuba mata masifar tsoron shi, domin wallahi gara mutuwa bata gan shi ba, amma Baffan su tana mishi kallon mutuwa ne baki ɗaya. Shi yasa matukar yana gida baka tab'a ganin ta a cikin yara ko a kofar gidan, domin hantar da yake mata ga duka kamar ba shi ya haife ta ba. Haka ta isa makarantar dake su harirah da Rabi sun tafi. Tana isa ta wuce ajin su.
Abin da yake damunta, bata fahimtar kome gashi nan a rubuce a bango amma bata san me ake nufi ba, haka yasa baki daya bata da wani walwla da kuzari. Ko da aka yi break tana zaune a saman window din ajin tana kallon Yara. Sai sha'awa suke bata. Amma da zata tafi cikin su yanzu zasu watse haka yasa take kallon su daga nesa. Har aka koma Aji ta koma wurin zaman ta. Wasu yan mata ne suka zo inda take suka shiga mata dariya. Kanta kawai ta kawar idanunta yana cika da kwalla. Domin idan akwai abin da ta tsana ta ga Yara suna mata shakiyanci. Haka yasa bata cika son shiga cikin su ba. Sai da malamin social studies ya shigo yaran suka koma wurin zaman su.
Ire-iren matsalolin da take fuskanta kenan ko a gida ko a makarantar su. Haka yasa ta fara kokarin kin zuwa makarantar idan aka tashi kuka take sakawa Inna Laminde ita ba zata ba. Zuba mata idanu tayi yau da ya kasance Juma'a. Duk da wankar da Inna Laminde tayi mata da wuri, wai kada ta makara, bai hana ta komawa saman gado me rumfar Innar tayi kwanciyar ta. TOP-NOTCH...
ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Page:04
Lekowa Inna Laminde tayi ta hangota d'are-d'are a gado, zaro idanu tayi cike da mamaki ta yafito ta da hannu. D'aga kafada tayi ita ba zata zo ba. "Kayya ni Laminde naga takaina. Tawo nan" ta kuma kiranta da hannu, juya baya tayi kamar ba da ita ake ba. "Sa'ade taso muje" tasan ba ji take ba da wannan kunnen, amma haka take sambatu da ta gaji da kanta, ta shiga cikin dakin ta dauko ta. Kuka ta saka tana niman kwanciya a kasa. Haushi da takaici ya cika Inna Laminde bata san lokacin da ta falla mata mari ba. Da sauri ta mike tana me kare fuskar jikinta yana rawa. Nuna mata hanya tayi babu shiri ta nufi hanyar tana kuka da ihu. Wanka ta mata har lokacin ihu take, "yau kuma sheganta kurma take ji?" Shiru Inna Laminde tayi bata kula shi ba. "Da Bara kika kaita sai kun samu tausayawar al'umma su bata sadaka." Banza tayi da shi ta cigaba da shirya yarta domin idan ta daka na Malam Aminu tabbas zata iya rasa turmin daka ta ta. Haka ta wuce dakin ta da Sa'ade ta shirya ta. Tsaf ta fito gwanin ban sha'awa hawaye ne ya zubo a Idanunta, mika mata kunu tayi ta sha. Amma tunda ta kawar da kai kamar taga kashi. Karshe fita tayi da jakar makarantar ta. Tana kuka har ta isa makarantar, tsayawa tayi a bayan ajin su zaune tana wasa da ƙara. Har aka fito tara tana wurin sai lokacin Halima da Nana yan ajin su suka zo wurin domin fitsari suka ganta zaune. Tana ganin su ta mike tana zare idanu, nufarta suka yi dama tana jin haushin an korota makaranta. Halima tana zuwa ta shure ta, bata kulata ba itama Nana ta maketa, tana mikewa ta kama kan Nana da hijab din ta shake ta, baki daya ta musu barin mahaukaciya, ta daki wannan ta daki wannan, sosai take jibgar su har sai da aka taru akan su, kafin aka wuce da su office din headmaster, duk suka durkusa. Ita dake bata da bakin magana shiru tayi, su da aka tambaye su, suka mata sharri, haka yasa aka zane ta domin sun fada bata zo makarantar ba, hakan ta fito daga office din tana kuka me mugun ciwo, kana jin kukan har cikin kanka. Aji ta wuce ta zauna tana shashekar kukan. Har aka tashi bata fasa kukan ba, koda ta dawo tun daga nesa ta hango Baffan dan dole ta share Idanunta tare da hàdiye kukanta, domin tasan ba karamin abu bane ya rufe ta da duka. Dake juma'a ce babu makaranta sai ranar monday. Suna zaune da abokan shi ana hira tazo ta wuce abin ta. Tana shiga cikin gidan ta samu an gama dafaduka, dakin su ta wuce ta cire kayanta, ta fito ta dibi ruwa ta wuce ban daki tayi wanka. Sannan ta koma daki ta saka kayan juma'ar da Innarta ta cire mata wata English me abc. Wanda Yayansu Ya'u ya musu sallah bara, sai farin hijab ɗinta yayi mata kyau, fitowa tayi dauke da abin sallah tana kallon Innar su. "masallaci zaki?" Dake ta juyo kunnen da take ji, gyada mata kai tayi. "Zauna kici abinci" motsa bakinta tayi tana girgiza kai. "Kin koshi ne?" Gyada kai tayi, dama tasan halin ta matukar tayi kuka bata iya cin abincin sai dai tayi ta fushi. Duk ranar juma'a yayan sun Iro yana turo me mashin ya kai su Binji suyi sallah da kwana biyu a can, kayanta kala biyu ta dauka suka fito domin yaron da iro ya turo ya iso. Ita kan burinta ba zata zauna a garin Binji ba, domin sokoto zata ta kai karan Innar su ta mare ta. Dama Inna Laminde tasha jinin jikinta tunda ta dake ta, yau zata tafi har Sokoto kai kara, tunda juma'a ce. Haka suka tafi Inna Laminde tana d'aga musu hannu. Dariya tayi tana faɗin, "Allah ya shirya min ke adawo lafiya daga kai kara da yaji." Lokacin da suka isa su Rabi da Harirah suka wuce gidan Yayarsu da sune ciki ɗaya. Ita kuma ta zuwa Ibrahim rigima, babu yadda ya iya dole ya bar shagon a hannun Yaran shi, suka tafi anan take son gaya mishi abin da Inna ta mata, sai misali take mishi bai gane ba.
^°°•
Kallon Yarima Sadeeq yayi yana shirya mishi kayan sa, murmushi yayi ya tashi daga kwanciyar da yake yana daukar wayar hannu ya zuba idanu hoton wata kyakyawar budurwa ce akai tana da kyau me sanyi, gata kamar baturiya, danna kiran wayar yayi ya kanga a kunnen shi, har lokacin wayar a kashe take. Kiran Ummin shi yayi yana sallama. "Ubana kana lafiya?" "Ummina baki da lafiya ne?" "A'a kewarka nake" "Ummina" ya kirata a shagwab'e kamar zai tashi sama, murmushi tayi mishi sannan ta ce mishi. "Auta baka san ka girma ba ne?" "Ummina!" "Na'am Ubana" "har yau ni babynki ne" ya fada yana narkewa kamar yabi kasa ya kwanta , sake baki Sadeeq yayi yana kallon ikon Allah, abin shi mamaki ya ba shi. Dama haka Aliyu yake, "Ga Ummu Aymana" "Bata Ummina" wayyo Allah, anan Sadeeq ya gane me ake nufi da d'an Auta domin shi Auta ne amma babu irin wannan shakuwar da yayin shi mata da maza. "Didihhhh" ya kirata kamar ana tsikarar shi. "Na'am Autar Ummi" sake narkewa yayi yanar zai shiga wayar ya ce. "Didih, kin ji wai sun tura ni wani gari can me ma sunan garin Sadeeq?" "Maikulki" Sadeeq ya bashi amsa. "Kin ji wai Maikulki" "Allah sarki auyoo my Baby brother" yatsu ya dunkule ya saka a baki, "you pity for me?" "Mugun tausayi ma kuwa, kanina me nauyin chequer billion goma za a tura wani ƙauye" ta fada muryata yana rawa. Murmushi yayi, "ya isa haka ba sai kin yi kuka ba, ina kewar ku ne, don Allah ina Babyn baby?" "Hmm bata nan idan" "me yasa kuke boye min ita, me yasa idan na tambayi Ummina sai tace bata nan please meke faruwa ne? Na kira Dad yaki picking kirana." Ya fada kamar zai yi kuka. Amsar wayar Ummin su tayi tana faɗin. "ka kwantar da hankalin ka in sha Allah zata dawo" "but Ummina " "kana son nayi fushi ne?" Girgiza kai yayi kamar yana gabanta. "A'a " "Allah ya maka albarka " daga haka ta kashe wayar. Jikin shi ne yayi mugun sanyi, wannan shi ne karo na biyu da duk lokacin da ya bukaci magana da Ummu Mansurah ake hana shi magana da ita.
"Sannu nace sannu Aliyu" murmushi "yawwa Yarima Sadeeq " sai kuma suka fashe da dariya.
^°°•
International hospital Abuja Nigeria.
Cardiac department.
Zaune yake a gaban Babban likitan zuciya, yana wasa da wayar shi. "Mr Abdulhakim! Ka cigaba da shan maganin babu abin da ya samu aikin da aka yi a zuciyar sai ma nasarar da ake kara samu. Amma dole ka kiyayye damu sannan kana yawan motsa jiki domin bawa zuciyar damar aikin da ya da ce." Ya fada yana ajiye takardan da yake dubawa. Murmushi yayi yana shafa kasumbar shi. Sai da ya lumshe idanun shi , sannan ya bude idanun shi akan likitan ya ce. "Dr kana nufin an yi nasara kenan?" "In sha Allah anyi nasara yadda binciken ya nuna min " "Alhamdulillahi, duk da bana cire tsammanin daga rahamar Allah, amma nasan na kai matakin da dole na jira ikon Allah, na gode sosai." Rubuta mishi magani yayi , tare da mika mishi. Sake musabaha yayi sannan ya amshi takardan ya nufi inda motar shi ya ke, escort din shi ne suka taso suna bin bayan shi har inda motar su yake, suka bude mishi ya shiga yana sauke ajiyar zuciya. Duba wayar shi yayi wanda ya bari a cikin motar. "Seven miss call" ya furta a hankali, duba kiran yayi. Mother kurawa fuskar wayar yayi idanu, kafin ya dauke yana shin wani irin yanayi kafin ya kira layin."Abdul ina ka shiga ina kiran ka baka dauka ba?" "Kiyi hakuri na shiga meeting ne" ya furta a hankali, kamar ba zai magana ba. "Toh yayi maka kyau, kaga sakona a wurin sakataren ka?" Lumshe idanun shi yayi, yana jin wani irin nauyi a zuciyarsa. "Baka ji me nace ba ne?" Ta fada a fusace, domin tana da mugun zafi. "Ina jin ki Mami!" Ya furta a sanyayye. "Na ce kaga sakona a wurin Mubarak?" "Eh na gani, sai dai zan zo sokoton don Allah ki bani damar haka" yadda yayi maganar a hankali yasata saukowa domin tasan bai da wadataccen lafiya. Ita kanta ba don ranta take mishi haka ba, sai dai Abdul ya girman da yake bukatar iyali a tare da shi kodan lalluran shi. Dole ya ajiye mace a tare da shi."Allah ya baka lafiya, and likitan ka ya turo min sakamakon binciken lafiyar ka don haka ka dawo da wuri, domin a tsayar da magana ɗaya." " Toh Mami sai na zo" sai da ta kashe wayar ta, ya wurgi da na shi wayar. Baki daya an mai da shi kamar dan Babyn wasan Yara, bai da cikakken ikon kan shi sai yadda Mahaifiyar shi tayi da shi. Hatta matar da ake son ya aura muradun mahaifiyar sa ce ba muradun shi ba. Mahaifin shi ya xama kamar hoto sai yadda aka yi da shi, koda yake ai ba wani abu bane tunda haka ya taso ya gani. Duk da mahaifin su babban ma'aikancin gwamnati ne da ya rike manyan mukaman gwamnati har yayi retired aka kuma dawo da shi aiki. Cikekken sunan shi Abdul Hakim Sharif Hamidu, shi ne cikakken sunan shi a sanin shi dai tun farko auren iyayen su kamar babu soyayya da shakuwa. Sai dai biyayya ga iyaye domin yadda Mami take over acting yasa suka fahimci haka. Shi kuma irin wannan auren a gaban uban kowa mace tana iya nuna maka bata sonka. Domin a yadda ya samu labari mahaifin su yaron gida Alhaji Abdul Hakim bakasanmatsi ne me kamfanin gidan siminti na sokoto baki ɗaya. Tun kafin y aurawa Sharif Daulah ya nima mishi aikin gwamnati a babban mataki, yadda ba zata rena Sharif ba. Sai dai kash duk da wannan bai hana ta mugun rena shi ba. Domin Hajiya Daulah irin mata masu mugun izza ne da jin kai. Shi kuma irin mutane ne masu hakuri da sanyin hali. Wannan halin na shi da mahaifin Daulah ya gani ne yasa shi ba shi auren yar shi domin ko bayan ran shi zai yi wuya ya wulakantata. Sannan ya kuma fahimci Sharif bai da son zuciya domin yana da kokarin niman na kan shi, haka yasa shi nema mishi aikin gwamnati kafin Auren su. Duk da haka Sharif ba tsira a hannunta ba. Za a iya kiran auren su da suna rabo. Domin rabon Yara ne ya tara su zama inuwa ɗaya. Abdul Hakim shi ne babba suna kiran shi Abdul, sai Sadikkah take bin shi sai Afiyyah sai Taufiq, idan ka cire Abdul shi ne ya dauko halin mahaifin su. Sauran duk rashin Mutuncin Hajiya Daulah suka ɗauka. Lokacin da aka yi auren su ta tashi hankalin kowa har da shi mijin, ana ta samu cikin Abdul wanda tayi ta shan maganin zubda ciki. Amma Allah ya nuna mata ikon shi ta hanyar kare cikin har ta haife shi, sai dai kuma an haife shi da ciwon zuciya, sakamakon magungunan da tayi ta durawa da cikin shi. Har kasar waje Alhaji bakasanmatsi ya kai shi ya bude mishi file, duk bayan wata uku suna kai shi. Karshe da yaga zirga-zirgan yana yawa sai ya nima musu gida a can domin a lokacin babu me kudi irin shi, haka ya nimawa surukin shi damar ya karo ilimi itama kuma tayi karatun ta. Yaso tayi karanci bangaren jinya domin D'anta, amma fir taki sai kasuwanci ta karanta. A can ta haifi Sadikkah, rasuwar mahaifinta yasa suka dawo sokoto. Inda ta kafe zata tsaya akan kamfanin mahaifinta. Kasancewar ita ce yar shi daya tal.....
ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Page:05
Ganin ita ɗaya ne yasa take mugun jin kanta, ta kafawa kanta giggiwa da wani irin izza, bata san kome ba sai niman kudi. Domin bayan dawowarsu amsar kamfanonin ta tayi ta cigaba da kula da su, koda wasa Dr Sharif bai saka kan shi cikin duniyar ta ba, gudun kar a samu matsalar reni. Hajiya Dawlah ta rena talaka, ba a bakin kome yake a wurinta, shi yasa Yaranta suka taso da bakin kiyayyar talaka, idan ka cire Abdul babu ruwan shi, a duniyar Hajiya Dawlah kudi yafi kome daraja, shi ya sa bata harka da kananun mutane, sannan duk tsiyar mutum be tab'a zuwa inda take. Akwai gayen da ya nime auren Yarta Sadikkah, duk da suna son juna be hana da Hajiya Dawlah tasan bai da kumba susa ta mishi fata-fata ba. Idan kana Niman me kin jinin talaka toh wallahi tana sawun gaba. Duk da tarin dukiyar da Allah ya bar mata, akwai abu daya da tayi akan Abdul shi ne tura shi jami'an A.B.U zaria anan yayi degree din shi na farko, duk da a lokacin masu kudin da suke tura Yaran su, kasashen waje, ita bata tura shi ba koda mahaifin yayi magana cewa tayi. "Su makarantun can koyarwar suke da practice anan kuwa koyarwar su theory ne. Duk dalibin da ya samu tarkada daga makarantun nan guda, A.B.U, A.T.B.U, B.U.K, Udut. babu inda zai shiga ba a nime rike shi ba, domin jami'o'in sun san me suke kuma suna da good stander." Ba yadda ya iya da ita, haka ya hakura ya zuba mata idanu, domin yanzu yana fara magana zata ce kome sai shi yake da iko yayi. Kowanni Uba yana da burin ya tsaya akan Yaran shi amma Dawlah taki barin shi ya tsaya a kan yaran shi, sam bai san soyayyar mace ba, har sai da Allah ya haɗa shi da wata yar katsina me suna Fareedah, sun je wani aiki ya hadu da ita, kuma cikin ikon Allah sai aka yi dace itama daga babban gida ta fito. Auren shi da Fareedah shi ya janyo rigima wanda har Hajiya Dawlah ta bar mishi gidan ta koma gidan mahaifin shi, shi kuma ya zuba mata ido, don babu mahaifin ta ba zai iya wulakantata ba, shi yasa ya bar ta da halin ta, ana cewa kowacce mace da Arzikin ta a lokacin faduwar shi da Fareedah, ya samu manyan mukamai masu ban mamaki, domin sai da ya rike daraktan a majalisar dinkin duniya, uniter Nation. Allah sai ya nunawa Dawlah duk abin da take ji da shi yana ji dashi, dukiya ilimi, suna da daukaka. Amma a kullum cewa take da bazatarta yake rawa. Allah ya albarkaci Fareedah da yara uku, biyu maza mace daya. Fareedah tana da kirki hakuri da kawaici uwa Uba, biyayya da sanin kan namiji. Sai Allah ya haɗa jinin su da Abdul wanda shine yake rike da kamfanin simintin Mahaifiyar shi, ta tsani taji Abdul yana magana da Fareedah, tayi ta fada kenan Abdul baya kaunarta yafi kaunar mahaifin shi da matar shi. Daga ita har Yaran ta sauran babu ruwan su da Dr Sharif sai Abdul shima Abdul don babu yadda ta iya da shi ne. Domin yana gama degree din shi Mahaifin shi ya tura shi Canada ya tafi yayi masters din shi. Duk da bai da lafiya, amma yana da kokari.
Wannan shi ne kaɗan daga Abdul Hakim Sharif Hamidu.
•°°°
Fadar Sarkin Kwara.
5:30pm.
Mace ce dattijuwa, tana sanye da atamfar super neuver. Tasha ruwa da jin jiki saboda yadda tayi haske, wai ma don zanin babba ce yasa bata yagalgyale ba, yadda suke tafiya zaka rantse da Allah gidan zasu bari. "Iya kina ganin fadar gaskiya zai kubutar da ni? Iya ina matukar jin tsoro" juyawa tayi tana kallon shi, jikanta ne wanda iyayen shi suka rasu suka bar mata shi. Yazo da alamari me girma, taya zata yi shiru. "Kabiru taya zamu yi shiru bayan masu laifi suna raye baka gan su ba ne." Rintsa idanun shi yayi. "Iyah mu hakura don Allah, mu bar masarautar nan" "ko daya haka ba zai faru ba" ta cigaba da tafiyar ta, kamar zata kifa. Tana isa sashin Sultanah Badi'atul Noor, wacce ake mata lakabi da Sultanah karama. Suka jan tunga suka tsaya, "Gajiyah me ya kawo ki bangaren Sultanah karama?" Sarkin kofa ya tambaye ta, kasancewar an bashi umarnin tsaya a kofar sashin Sultanah tun faruwar al'amarin kisan Ummul Mansurah da ake zargin D'anta da yi, Sultan Abdulrahman Dan Aliyu Sulu Gambari ya hana kowa shiga wurinta, kuma kar a bari ta fita sai da dalili. "Sarkin kofa, alfarma nazo nima ina son ganin Sultanah" kallonta yayi Gajiyah mutuniyar kirki ce, ba zai iya hana ta shiga ba, don haka ya ce mata. "Kin san dokar hana shiga da fita da aka kafa, don Allah kar ki jima a cikin sashin domin Sultan zai iya zuwa kowani lokaci " gyada mishi kai tayi cikin farin ciki" In sha Allah ba zan wuce yadda kake tunani ba." Bude mata kofar sashin aka yi, ita da jikanta suka shiga cikin sashin. Zubewa bayi suke suna gaishe ta. Domin ita din jakadiya ce ta Sultanah Babba. "Gajiyah kece yau a bangaren Sultanah karama?" "Eh wallahi nice Zuwairah ina uwar dakin take?" "Tana lazumi ne" shiru suka yi kafin tace. "Don Allah ki nima min iso alamarin ujula ce" shiru tayi kafin ta ce mata. "Shi kenan bari na mata magana" wucewa tayi cikin babban falon, can ta wuce hanyar upstairs din, hango Iyatuh tayi dauke da kayan wanki. Murmushi tayi mata ta ce mata. "Sannu da kokari Yar nan?" "Yawwa Mama Zuwairah." Ta wuce dakin Sultanah Badi'atul Noor, ta bude a hankali, Aljannan duniya kenan. Duk inda ake niman kayan alatu na rayuwa ya samu a falon, katon hoto ne ita da Yaranta biyar. Maza uku mata biyu. Fuskartar ce juya ta jimami, wucewa tayi har bakin kofar ta buga. Gyaran murya aka yi, bude kofar tayi bakinta dauke da sallama. "Assalamu alaikum " ajiye Alqur'anin hannunta tayi tare da zare glass din idanunta ya zubawa Zuwairah ido" zubewa tayi a kasa tana mata kirara. "Barka da warhaka, uwar dakina baya giya marayu, me uban ma kin goye shi, Uwargidan Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari, takawarki lafiya Giwa me tafiyar kasaita, Barkan ki da hutawa uwar zakuna uku, Babar Didih da Addah, Mamar Hamma Bubah, Uwar Sanda Babuga. Makiyan ki fadawar ki. Allah ya dawo miki da farincikin ki" zuba mata ido tayi, kafin ta ce mata. "Zuwairah da na jinki" gyara zama tayi sannan ta ce mata. "Ranki shi dade Gajiyah tana son ganin ki" "ki je idan aikota aka yi ta sako ne ta baki" "ranki shi dade, bana tunanin sako ne kamar ita da kanta tazo domin ta ce min ujula ce." "Tow ki mata iso" ta cigaba da karatunta, "na barki lafiya " ta juya ta fita, ajiyar zuciya ta sauke tana me jin kwalla na cika mata idanu. Duk Yaranta basu tare da ita, Zakiyyah da Rumaisah kawai take jin sauki daga gare su, Autan ma sun taso shi a gaba. Lumshe idanunta tayi tana tasbihi ga Ubangiji wanda ya cancanci girmamawa da bautawa. Tana zaune a wurin Gajiyah da jikanta suka shigo dakin, zama suka yi ta zuba musu idanu. "Barka da hutawa, akawala baki musaya, hankaka meda dan wani nata, alfadari kike me ado da zinari, maliya me ruwan alkhairi, Uwar Zakiyyah da Rumaisah, Hajiyar Abubakar da Umar, Innar Aliyu Abu turab, mun zo da babban al'amari ne me girgizarwa." Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta mai da dubarta ga kofar dakin ta. Juyawa Gajiyah tayi zuwa ga kofar dakin. Inuwar mutum ne a wurin. Mikewa tayi ta nunawa Gajiyah barandar da yake dakin ta waje, anyi wurin domin shan iska ne. Tashi suka yi tare da nufar wurin. Sai da ta rufe kofar dakin ta, bayan ta leka bata ga kowa ba. Sannan ta nufi wurin su ta rufe kofar wurin shan iskar. "Ina jinki " taryan-taryan ta labarta mata, abin da Jikanta Kabiru ya gaya mata. Mikewa tayi tana kallon waje, ba zaka iya tantance abin da yake ranta ba. Domin wani irin fuska take da shi, na ba zaka iya gane fushinta da farar ba, duk da ta kasance mace mara yawan fara'a. Amma tana da faran-faran da mutane, yanayin ta ne kawai ba me yawan fara ba, amma idan ta zauna a cikin Yaranta har da dariya take yi, tana da wuyar sha'ani ce. "Gaskiya ka fada Kabiru?" "Na rantse da Allah gaskiyar kenan" "shi kena, amma Gajiyah me yasa kika zab'e fadar gaskiya bayan kowa yasan ke kina tare da Sultanah Babba ce" hawaye ne ya zubowa dattijuwan, ta saka hannu ta goge tana fadin. "Koda ni ban rayu ba, ina fatan shi din ya samu kyakkyawar rayuwa, Sultanah ban zabi haka domin nima mishi alfarma ba, asalima ina son nayi amfani da haka ne niman kusanci da Ubangiji na, nayi wanka da zunubi, a yanzu kuwa ni da banza daya ne, don Allah ki taya ni kare rayuwar shi, wallahi bani da wani abu da zan iya kare shi" "zaki iya tafiya, shi kuma ya zauna a bangaren auta. Domin tunda kika kawo shi ba zan yi sake da shi ba. Shi ne shaidana" "Na gode sosai Sultanah " har zasu tashi ta ce mishi. "zauna kai" komawa yayi ya zauna yana kallon kasa. "Zaki iya tafiya " zama yayi, ta zuba mishi idanu. Kan shi a kasa, kafin ta ce mishi. "Kana son zama a nan?" "Eh...eh... Sultanah " ya fada muryan shi yana rawa. Murmushi tayi tana kallon shi. *Idan na sake ya bi kakar shi* "Sultanah abubuwa daya sun faru a cikin masarautar nan don Allah ki hako wasu domin kyautatawa ce haka" kallon Gajiyah tayi sannan ta ce mata. "Ba zan iya hako abin da zai mai da kasa ya binne ni ba, wanke Yarona kawai nake son yi ba tada abun da ya wuce ba." "Idan kuma kina da alaka da hakan fa?" Gajiyah ta wurga mata tambayar. "An san da wuyar biri bai hana a daure shi a kugu ba, akan me zan saka kai na cikin abin da ya wuce babbar matsalata wanda ya kashe Yarinyar da babu ruwanta, sannan aka jinjinawa Abu Turab" "Sultanah" "don Allah ki je" sultanah ta fada. Har ta isa bakin kofar sai ta tsaya tana kallon Jikanta da Sultanah. "Wata rana zaki so ki san me ya faru, idan wannan lokacin yayi, ki ziyarci garin ka'injin don Allah " "Allah ya nuna mana," "Ga amanar shi nan" "Allah ya taya ni riko" ta fada. Tafiya Gajiyah tayi, bai zama dole ta rayu ba, amma ya zama dole ta gayawa Sultanah gaskiya, tana fita daga cikin sashin ta kalli Sarkin kofa ta ce mishi. "A gafarce ni mai kofa." "Ba kome, amma kin san zuwan kinan akwai hatsari ko?" Goya hannunta tayi a baya, "me yafi ciwo a ce kayi bauta a maida kai saniyar ware? Ka tab'a gane cewa kalilan ne a masarautar nan suka san amfanin mu? Ko kasan." "Gajiyah abu shida ke aiki a Masarautar nan, Kudi, mulki, hassada da makirci, mugunta da kwadayi, don Allah ki cire hannunki a wannan al'amarin" "Bakwai ne Sarkin kofa, fansa kowani bangare burin shi fansa" "don Allah ina baki shawaran ki cire hannunki a cikin wannan lamari, domin kin manta da Cin amana, wnada ka yarda da shi zai iya cin Amanar ka akan kuɗi da zai kare, akan dan abin da bai da tabbas, don Allah ki janye hannunki" tafiya tayi bata ce kome ba. *Haka ne duk abin da muka lissafo shi ne yake faruwa, idan har akwai abin da zai faru tow ba makawa yakin gaba da Sultanah ce, ita ce abin harin kowa ita da Yaranta maza uku, an fadi a kan Abu turab, shi ma ai don yana tare da ita ne, ta iya kare shi tun daga yarintar shi.* Wannan shi ne zancen zucin da take tabbas yaran sultanah sune ake hari kasancewar sune manyan...
ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Page:06
Bayan fitar Kabiru daukar wayarta tayi ta shiga niman layin mahaifinta. Bugu biyu yayi ya dauka, "Baffa!" "Na'am Noor!" "Yanzu aka zo min da wani al'amarin da ya shafi mutuwar Mansurah" "Alhamdulillahi, ki saurare ni maza kar ki yi kasa a gwiwa waɗanda suka aikata haka sun san me suke yi ba jahilai ba ne, don haka kowacce kankantar hujja boye ta zasu yi." Mikewa tayi ta fita tare da budar kasa, bata yi wasa da wannan damar ba, kai tsaye ɗakinta ta nufa domin nan dakin hutawar ne, alkyabar ta dauka ta nufi heeram, bangaren Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari. Duk inda ta gifta zubewa bayi suke tare da mika mata gaisuwa, yadda zaka fahimci tana da mugun matsayi a cikin Masarautar. Bangaren Sultan yafi kusan kowani bangare girma da tsaro, domin bayan fadawa akwai sojoji da civil defense, akwai mopol, bata yarda ta bi kofar baya da yake cikin gidan ba, so take tayi amfani da damar ta, wanda ita kadai tabarwa kanta sanin shi, yadda ta sauya ba zaka tab'a cewa akwai abin da yake damunta ba. Yadda ta sake tana amsa gaisuwar, "A hanyar isa farfajiyar heeram suka yi kicibis da Hajiya Turai, ita ce matar Sultan ta uku. " Kallon juna suka yi kowacce da abun da ranta yake kitsima mata, musamman ita Hajiya Turai da take tare da bayi da kuyanginta suna take mata baya. Duk da kallon farincikin da takewa Sultanah Badi'atul Noor, sai dai har yau tana mamakin girman halinta. Zubewa bayin Hajiya Turai suka yi suna "Barka da warhaka Giwar mata, Barka da maraici magajiyar Sulu gambari." Cikin wani irin yanayi na nuna ita din ce suke gaisarwa ta juyar da kanta izuwa gare su ta ce. "Allah ya albarkaci rayuwar ku, Turai da fatan kina lafiya" "ke baki da damuwa ne? Kin san bana kaunarki amma kika matsa min dole sai kin shiga damuwa ta, ko kunya baki ji ba, kin dibo jiki zaki tafi wurin Sultan da yace baya kaunar ganinki a bangaren shi." Wani irin blush tayi tana kara daidaita nutsuwar ta. Matsawa tayi sosai suna fuskantar juna ta ce. "Ko shi Abdulrahman bai da ikon korata idan na shiga idan kin Musa muje ki gani" ta fasa ƙasa ƙasa yadda bayin da suke bayan Hajiya Turai ba zasu ji abin da yake fada ba. Sannan ta gyara alkyabar ta, tayi gaba abinta tana murmushin karfin hali. Gidan sarauta sai ka iya takun ka, sai ka iya adana fushin ka, sai ka iya makirci sai ka iya kissa da kisisina. Bude mata kofar suka yi Hajiya Turai ta bi bayanta da idanu, an dadde ana ruwa kasa yana shanyewa, tun kawo ta gidan kusan shekaru goma sha biyar har yau bata taɓa ganin macen da ta iya wanka da ado ban mamaki kamar Sultanah ba, kuma har kwanan gobe babu wacce take irin wankar ta, karya ne babu abin da zuciyarta ya gaya mata kenan, shi yasa ta tsane ta mugun tsaya, tsabar iyayi irin na Badi'atul Noor bata yawo da bayinta ko daya. Wai a haka ma don Sultanah Babba tana tsaye kenan amma baki daya Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari bai da nutsuwa matukar abin da ya shafi Sultanah karama ce, kwafa tayi ta nufi hanyar cikin gidan ta kofar baya, leshen jikinta ruwan makuba ne, amma matar nan dan tsiya ta haɗa mishi golden alkyabar wanda ya dace da ingancin shigar jikinta, ga wani fitinannen kanshi me sanyin dadi da yake tashi a jikinta, "Mtseeeeeew tsohuwar banza ta tsufa amma kullum zuciyarta na yara ne" kwafa ta kuma yi, bayinta suka kalli juna, suna kunshe dariyar su.
Da sallama ta shiga babban falon shi, yana zaune a kasa, Sultanah Babba tana saman kujeran, Hajiya Bariyyah tana zaune a kasa, tayi kasa da kan ta. Gefe guda Hajiya Mariyah tana gefen shi, Amaryan shi. Sai Hajiya Suhailah, gabanta ne ya fadi Hajiya Suhailah Matar wan Sultan ne Sultan Abdulsamad Dan Aliyu sulu gambari, gefe guda Alhaji Marwan ne mahaifin Ummul Mansurah. Ji take kamar zuciyarta zata fashe,.asalima kamar ta juya amma kuma ma hakan zai iya janyo cece ku ce, wani malalacin murmushi Sultanah Babba tayi tana cewa. "Uwar dan gata,." "Hmmm, Sultanate masu abu da abin su kura da kallabin kitse, Allah ya kawo mu zamanin da ake yaki da gaskiya" "Aikuwa an zunguro inda ba za a iya ba." Wani munafikin murmushi Sultanah karama tayi, tana me jiman wuri ta zauna a saman kujeran, kamar yadda Sultanate ta zauna wato Sultanah Babba ita suke kira Sultanate. Kallon Badi'atul Noor Alhaji Marwan yayi. Yana mata alamu da ƙasa, domin shi kan Sultan ya kasa kome sai bin su yake da idanu, musamman yadda suke yab'a mata magana kuma murmushi take har tana washe baki, ba zaka tab'a cewa maganar su yana mata zafi ba, kallon Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari tayi cikin murmushi ta ce mishi." Allah ya huci zuciyar jan gwarzo ina bukatar ganawa da kai." A duk lokacin da ta ambace shi da jan gwarzo wallahi ji yake kamar ta dauke shi ta cilla shi wata nahiyar da babu kowa sai shi, kan shi sai yaji yayi rantalel, karkace kai tayi cikin iya kirsa ta fara wurga mishi kirari. "Wannan shine Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari,
Jan wuya
Zakin talakawa
Dodon azzalumai
Lange Lange me kamar bazai je ba
Nan gani nan bari dumamen mayya
Kududdufin barkono iyakacin mace gwiwa
Kaga Abba na Abubakar da Umar, Uban Rumaisah da Zakiyyah, Baban Aliyu Abu turab me takama da Hasbuballahu.
Rankwatakwale ba shiga jirgin ba inda kan zai zauna
Barka da Rana Mijina" jin shi yayi duk wani fushi da b'acin ran da suke tsakanin su ya kare, wato Ubangiji ya baka macen da zata kashe ka da takaici ta kuma rayaka da annashuwa arzikn ne. Kallon Mahaifiyar shi yayi da sauran jama'ar falon, ya mike yana faɗin "bari na gana da ita." Babu wanda ya ce mishi cikanka domin matukar Badi'atul Noor tana wuri wallahi babu wanda ya isa da shi. Yana gaba ta juya cikin murmushi ta ce musu. "Ba fada damu bane kwana mita." Daga haka ta wuce falon shi na musamman. Tana shiga ta same shi zaune yana wani haɗe rai, zubewa tayi a gaban shi, ta zuba hannunta akan gwiwar ta. "tun ranar da abin ya faru har yau baka ce min kome ba, ko da minti goma baka bani domin na gaya maka yadda muka yi da Baba karami ba " ta fada tana me isa gaban shi, "akan me zan baki damar magana? Bayan nasan duk abin da zaki fada wanke danki zaki yi? Idan maganar Babana ne ya kawo ki muje can na yanke hukunci." "Sultan ina son na gaya maka ɗazun na samu wasu bayanai ne na mutanen da suka yi kisan." Kallonta yayi sosai kafin ya ce mata. "Domin kare Kanki da danki shi ne zaki daurawa wasu sharri?" "Don Allah ka yarda da ni wallah......" Ƙarar tamburar masarautar suka ji sai da gabanta ya fadi, zubur ta mike jikinta yana rawa kamar zata tashi sama ta fita daga cikin falon yana biye da ita, sarkin gida ne ya shigo da mugun gudu ya zube a gabanta. "Sultanah an kashe Kabirun Gajiyah" luuuuu ta tafi zata zube cikin zafin nama Sultan ya riko kafad'ar ta, ta koma jikin shi, damuwa ta mata yawa tashin hankali yana niman kassara ta, janye daga jikin shi, ta nufi kofar da sassarfa ta nufi bangaren ta. Koda ta isa ga gawar Kabiru kwance cikin jini, window dakin Abu turab an balle shi, da alamu watsawa window ruwan battery aka yi, zubewa tayi a gaban gawar Yaron tayi, abin da kakar take gudu kenan. Juyawa tayi cikin matsanancin fushi da b'acin rai ta ce. "A tsare duk wani da me rai da yake numfashi a cikin gidan nan" "Babu wanda zaa tsare, da Abu turab ya kashe Mansurah cewa kika yi sharri ne bazai kashe ba, yanzu da kika saka a kashe dan mutane shi ne zaki fara borin kunya." A fusace ta juya tana kallon Sultanate da take maganar cikin fushi.Murmushi tayi sannan ta ce. "Ba laifi bane idan nayi hukunci a nan amma kuskure ne shiga cikin abin da yake mallakata. Sarkin dogarai! Maza a tsare kowa na ce" tunda aka fara al'amarin sai yau aka ga b'acin rai. "Wallahi babu wanda za a tsare" wani irin juyawa tayi tana kallon Sultanate, ja da baya tayi ita kanta a wannan gabbar kasa rike fushinta tayi, Sultanate zata yi magana Sultan ya ce mata. "Bangaren ta ne ko bata saka a tsare kowa ba, ni zan saka." "Au biye mata kayi abdurrahman kayi? Shi kenan Allah ya bada sa'a" ta futa daga cikin gidan, gawar Kabiru aka dauka aja fita da shi, ikon Allah ne kawai yake tafiyar da ita, amma tabbas yadda numfashin ta yake sama da kasa, zata iya faduwa domin baki daya karfin ta da kuzarinta ya kare, shigowa ɗakinta tayi, ta rufe dakin tare da shiga ban daki ta kunna ruwa, yana zuba a kanta. Bata son karaya amma tabbas abin da Baffa ya fada kenan? Da Gajiyah take cewa ta hako abin da ya wuce tow kuwa mutuwa zata yi.
Bin bayan mahaifiyar shi yayi, tunda ta shiga falonta ta zauna tana huci. "Har ni abdurrahman zan nunawa ban isa ba? Yaushe aka haifi Badi'atul Noor da zata saka doka ya goya mata baya? Ni da na haife shi bai saurare ni b sai ita, wato bani da daraja." Shigowa yayi ya zube akan gwiwar shi, tare da dan durkusawa. "Badi'atul Noor ta fini daraja kenan? Ta fini kenan tow ka je kai da ita na bar mata kai, Hakkin Mansurah kuma zan kai ku kotu a nima mata hakkinta" fada take yi inda take shiga ba nan take fita ba, fada take kamar zata rufe shi da duka, tana gamawa ta wuce ɗakinta har lokacin yana durkushe. Bai tashi ba. Duk ya rasa inda zai saka rayuwar shi..
**
Sokoto.
Yau lahadi, iro da kan shi ya zo har garin sokoto ya dauke ta, suna tafiya tana mita kome ta gani sai ya saya mata har suka Binji,shagon tela ya kaita ya amsa mata dinkin sabon uniform ɗinta. Kallon shi tayi ta daura kanta a kafad'ar shi tana jin ina ma da zata iya mishi bayani a ya maida ita Sokoto domin tunda ta je zero tension, babu tsana babu tsangwama. Har suka iso gida da magariba, da murnanta ta shiga cikin gidan tana jin kamar ta shekara bata ga innarta. "Assalamu alaikum, sannun ku da gida." "Yawwa iro ya can wurin ku?" Inna Larai ta amsa masa. "Alhamdulillahi ya muka same ku?" "Masha Allah, Bimbi an dawo kenan." Dake kunne me jin ta juya gyada mata kai tayi, ta shiga ware ledar ta mikawa Rabi da Harirah kayan su, sannan ta wuce dakin su. Inna Laminde tana sallah, ta koma gefe ta zauna. Ganin zaman ba zai kare ta ba, ta nufi waje tayi alola domin shima Iro masallaci ya tafi. Koda suka dawo tana kwance a saman cinyar Inna Laminde, bakinta dauke yake da magana da labarai amma ta rasa yadda zata bata su. Sai murmushi take, ita kuwa Innar ta dage sai mata hira take, dan ajiyar da tayi dauko wannan ajiye wancan har ya cika mata gaba da abinci. "Inna yanzu ita haka zata rayu babu me gane abin da take so?" "Allah almusawiru yana sane da ita, babu abin da zan iya sai abin da hali ya bamu" "Gaskiya akwai matsala wallahi ita zata iya ji da kunne daya amma ba zata iya mayarwa ba." "Ibrahim don ka rena ni, har ka dawo da wancan abar ba zaka gaya min ba" inji malam yana shigowa dakin, duk da taji shi, kara rufe idanu tayi tana rike zanin Innar ta. Shure kafar ta yayi ta mike zubur jikinta yana kerma......
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Fatan Alkhairi Autar Manya ❣️😻😍
Page:07
"Don Allah Malam meye haka kake kamar yaro karami? Taya zaka shure ta kamar ka samu jaki?" Inna Laminde ta fada a fusace. "Yo ai tafi kama da hakan ne" kura mishi idanun suka yi, babu wanda ya iya magana domin iskancin Malam kara girmama yake, har ya gama shirmen shi ya futa bata ce mishi kala ba, "Inna kiyi hakuri wata rana sai labari in sha Allah Bimbi zata zama wani abu." "Hmmm Amin Ya Allah, tsoro na daya ne kar na mutu Bimbi ta shiga wani hali." "Ayya Inna babu wanda yasan gawar fari" "hmm" ta ce, suka cigaba da hiran su. Dake akwai dakin su na samari nan ya wuce ya kwanta.
Washi gari da asuba, bayan sun yi sallah asuba. Daukar allonta tayi ta nufi hanyar waje da hijabinta. A tsakar da ta hadu da Innar su, dake aiki ya sha manta jan rigar ta tai, tana kallon ta. "Zaki makaranta ne?" Lumshe idanunta tai, sannan ta mata murmushi. Shafa kanta Inna Laminde tayi tana faɗin. "A dawo lafiya " murmushi tayi da ya fito da jerarrun haƙoranta. Ta nufi hanyar waje. A bakin kofar fita taga baffansu. Hàdiye yawu ko ta ya zata yi karatu ita da ba magana take ba. Asara yawun barci. Dauke kai yayi ya cigaba da jin labaran karfe shida da rabi na BBC Hausa. Yana wurin har Bakwai saura, suka dawo ita da yan uwanta. Kallon Rabi da Harirah yayi cikin farin ciki, "Allah ya muku albarka rabi da harirah." "Amin Baffa" wuce su tayi abinta, tana shiga wanka suka wuce, sai fushi take ita ba kome ya sata fushi ba iya iyaka yau Monday, kuma zata makarantar boko, sai ta fara jin ba dad'i.
A can birnin Shehu kuwa, tun ranar Friday Prince Aliyu ya ga inda aka yi Poster din shi, amma yaki tafiya domin so yake lallai ya wuce Illorin, sai da Ummin shi ta mishi fada ya hakura, tun safe aka shirya dogaran da zasu raka shi, wurin karfe goma suka nufi bangaren Mai Martaba Shehu Abubakar Shehu, ya mishi nasiha da fada, sannan ya mika mishi wani takarda wanda shi kan sa Prince yake da yakinin kudi ne, godiya yayi sannan ya nufin inda ake jiran shi, koda ya isa bude mishi motar aka yi ya shiga, daga nan suka nufi Binji local government, gidan Hakimin Binji suka fara sauka anan aka kai su local government SC suka yi abin da zasu, sannan suka wuce Maikulki, a gidan Mai gari aka sauke shi a ɓangaren wani dan mI gari da yake aiki a lagos, dake ɓangaren ya fi ko ina a gidan kyau da tsari, ko dar Mai gari bai ji ba, yasa aka gyara mishi daya daga cikin dakunan, flat ne mai mugun kyau da haduwa. Duk da an saka mishi kome a gidan sai dai babu wutar lantarki, tunanin shi ya tsaya ne lokacin da ya zaro laptop din shi, da wayar shi. Fitowa yayi yana murmushi domin yara sun cika bangaren wai sun ga baturen cikin tv. A hankali ya fito. "Yallabai me kake bukata?" "A'a Baba Abu turab zaka kira ni, nima d'anka ne." "Wane mutum Yallabai dai, kana bukatar wani abu ne?" "Eh tow Baba" ya fada yana sosa kai, "me kenan?" "Hmm dama tambaya zan yi ana samun wuta ne?" "Eh amma ba sosai ba, kuma sai da nayi tunanin zaka bukaci wuta ko dan irin kayan aikin ku na zamani." "Eh Baba" "gashi babu." "Ba damuwa, bari na fita zamu koma Binji mu nemi injin" "tow madalla, dake kaga Habibu zuwa yake da na shi ya kuma koma da ita, da ya barta ai da na saka mai sai ka kunna don Allah kayi hakuri da yanayin garin mu" "ba kome fa" ya fada yana murmushi. Yara suna bin shi. "Kai ku b'ace anan" Mai gari ya faɗa. "Kyale su Baba." Ya fada yana murmushi. Durkusawa yayi yana kallon Yaran. Sai su kalle shi sai su koma da baya, "eh Bature na" sai su tab'a hannun shi su koma da baya, dariya suka ba shi ya mike yana faɗin. "Abokaina bari na je na dawo " "laaa kunji Yaren yake " ita kanta Hausar shi cewa suke yare na, yana fita fadawan da suka rako shi har biyu suna nan. "Kun san me? Zaku bar min motar ne kamar yadda mai martaba ya ce, zamu Binji sai ku wuce sokoto" ya fada yana wucewa gaban motar ya zauna a daya wuri me zaman banza, yana nazarin abubuwan da yake bukata. Lokacin da suka isa har tasha ya kai su, sannan suka fita ya musu alkhairi domin ya koyi haka daga iyayen shi, sai sa yaga tashin su, sannan ya koma kasuwa yayi sayayya, kafin ya juyo garin yaran nan kuwa kwalin biscuit da chocolate ya saya musu. Sai yar karamar gas wacce zai yi amfani da shi incase. Lokacin da ya iso ya shake motar da kayayyakin amfani da generator. A gajiye ya dawo lokacin ana sallah azhar, shi da wani dan me gari Nazifi suka sauke kayan shi bai samu jam'i ba. Haka suka nufi cikin gidan da kayan. Yana ajiye kayan yayi alola sannan ya nufi masallaci, sai da yayi Sallah suka kuma gaisawa da mutane, sannan ya shigo cikin gidan. Aka kawo mishi abinci bai saba ci shi daya ba, ko a Sokoto da mutane yake ci, domin ko a gida a tare da Ummin su da Ummul aiyman suke ci. Fitowa yayi yaga Yaran nan, daukar butar da aka kai mishi yayi ya kira su, suka wanke hannun su, sannan ya shiga dakin ya kawo musu praying mat. suka zagaye shi a tare suka ci abincin, kusan sune suka ci har da wawar su, murmushi yayi yana kallon su. Mikewa yayi suka biyo shi dakin shi, bude kwalin biscuit da chocolate yayi ya dauki wani laida ya zuba musu. "Kuje a raba muku kun ji" a guje suka fita suna ihu. Suna fita Mai gari yana shigowa, shima fita yayi zai tattara kayan abinciin. "Ba dai basu abinci kayi ba Yallabai?" "A'a Baba " ya fada yana murmushi. "Ga zahiri nan kamar an zubawa kaji abincin, nace ko zan kira maka wani Yaro ya taya ka haɗa wutar ne?" "Eh Baba " haka ya fita ya sa aka kira mishi lawi, suka hada wutar. Sai da ya kunna inji din domin da mai ya sayo abin shi, sai yaga iya bangaren shi ne da wuta. "Dan uwa,ko zaka iya hadawa da wutan gidan baki ɗaya " " ba matsala Yallabai " domin yana zuwa mai gari ua gaya mishi tow yarima ne daga Masarautar Sakkwato. A take ya shiga girmama shi. Komawa yayi daki ya kwanta, ya bar lawi da aiki. Sai da ya gama daidai ana kiran la'asar, suka fito tare. Mika mishi kudin aikin yayi ya ce."a'a yallabai mai gari ya bani" "karba nace" ya fada yana sassauta faraa shi. "Allah yasaka da Alkhairi" share shi yayi. Alola suka yi aika suka shiga Masallacin. Bayan sIlun isar da sallah, ya jima a masallacin kafin ya fito yana kallon garin yadda ya burge shi. Nufo shi mai gari yayi yana faɗin."ko zaka zaga garin nan na kira maka Nazifi" "Eh ba zan ki ba" kiran Nazifi yayi suka shiga zaga garin, har sai garin ya fara duhu suka dawo, a can hanyar rugar su Sa'ade suka samu wata saniya ta kasa, an yanka ana niman masu saya, abin ka da jini yana yawo a jikin shi, a take yasa domin yana da kauna tare da amana da tsakanin su da nama, shi yasa yana gani ya saya, abin ya faru akan idanun Malam,domin da aka yanke kudin saniyar bai zata A.A zai saya ba, sai yaji ya ce tow a biyo shi da saniyar zai biya. Sai da aka yi sallah magriba ya biya kudin, sannan mai gari ya saka aka nimo Yaran shi suka shiga gyaran saniyar. "Yallabai ya zamu yi da saniyar?" Mai gari ya tambaye shi, " a kai cikin gidan sai su fada abin da za a basu, ina son a soya min shi yadda zai kwana biyu sauran kuma a rabawa kowa da kowa." "Sannu bako me cida dan gida" tuwon shinkafa miyar kuka da yaji kayan kamshi, ga shi zabuwa aka burge a miyar. Sai tashin kamshi. Lokacin da yaga tuwon sai da ya kira Ummin shi, bata dauka ba. Kiran Rumaisah yayi. "Addah wai me yasa Ummina bata daukar kirana?" "Abu Turab Sultanah tana wani uzuri ne a wannan gabbar ka mata uzuri don Allah " "tow princess fa?" "Ka tambayi Ummina" ta gaya mishi tana kashe wayar ta. Domin karfin hali tayi ta mishi magana domin Ummin su, ta gargade su da kar wani ya gaya mishi. Halin da ake ciki, fita ya yi bayan aka ayi sallah isha ya dawo gida. Kunna inji yayi ya kwanta abin shi. iskar fanka yayi awon gaba da shi domin ya gaji sosai. Bai san lokacin da injin din ta mutu ba, domin tunda na Nazifi ya shigo ya samu yana barci wurin karfe biyu na dare sai ya kashe injin ɗin. Suma a lokacin suka gama gyaran saniyar, sai a sallah asuba suka hadu. "Kuyi hakuri na bar ku da aiki, sannun ku da kokari." "Ba kome wallahi, Ni na kashe maka injin jiya da karfe biyu na dare." "Hmm ka kyauta domin ma gaji ne jiya nima " sosai suka sake da juna kamar sun shekara da sanin juna. "Nazif gashi ka basu su sayi abin bukata da shi. " "Ai baba ya bada kudin su mangyada da sauran su " "wato ba zai huta ba ko? Tow don Allah ka basu, su kara in case" dake Abu turab yana da mugun cika idanu da kwarjini bai musanta mishi ba ya amsa. Shi kuma ya wuce bangaren shi da yaga an kawo mishi babban flask da karami. Shiga ban daki yayi ya dauki bokiti ya wanke tass, sannan ya juya ruwan, ya shiga dakin ya sauya kaya ya fito ya wuce ban dakin. Yayi wanka sannan ya fito ya shirya, anan ya kira Ummin shi, babu wani kulawar da ya saba samu sai baki daya yayi laushi. "Ummina nayi laifi ne kuke hukunta ni da abin da ban sani ba?" Ya fada idanun shi yana cika da kwalla. "Baba karami, kayi hakuri kayi abin da ya kawo ka. Wata tara kake da shi please ka tabbatar kayi abin da ya dace karka manta da alkhairi da sadaka" "in sha Allah" ya fada yana gyada kai domin yayi kewar ta sosai. "Ummina Ummul Mansurah" "kayi hakuri gaskiya bata nan na tura England wurin su yayan ka." "Shi ne ba ku gaya min da wuri ba." "Tow uban masu gida na gaya maka yanzu ko?" "Shi kenan zan tafi makarantar da aka turo ni." "Allah ya maka albarka, ya tsare ka da sharrin maraici da dare, ya hada ka abokan alkhairi na gari, kar ka manta da yin alkhairi tare da sadaka domin maganin masifa ce, yawan ta Alkhairi yana cika mizani, sadaka maganin masifa ce, yawan nafilla yana kara kusancinsa da Allah, don Allah kar ka cutar da wani domin ba iya kai zai tsaya ba. " Nasiha masu ratsa zuciya da jiki haka ta gama mishi fada, sannan suka yi sallama, shima ya fito. Cikin gidan ta shiga ya nufi bangaren da aka nuna mishi na uwar mai gari, ya gaida ita tare sa bata hakurin yazo ba shi shigo gaida su ba, sai aiki ya kawo. Cikin fara'a ta amsa mishi, "ba kome ai mun ga aiki kake yi shi yasa baka shigo ba, da fatan wurin bai takura maka ba." "A'a ba kome " "sannu da kokari mun ga tsaraban yara" "babu kome Umma" sauran dakunan yabi suka gaisa sannan ya mikawa Uwargidan mai gari key dinki shi. Kana ya musu sallama. Ya nufi waje ya samu an goge mishi motar shi, kafin ya kalli Mai gari. Ya ce mishi."Baba ai da kafa zan tafi naga makarantar babu nisa." "Tow shi kenan Allah ya dawo da kai lafiya." "Amin Ya Allah" ya nufi makaranta.
"Yau naji labarin malamai daga Binji sun iso Allah ya baku damar ɗaukar nauyin yaran, akwai yarinyar da nake so don Allah ka saka idanu akan ta Yallabai" "ina jinka" ya tattara nutsuwar shi ya daura akan shi. "Yarinyar kurma ce bata magana kuma, akanta aka kawo ku," "babu wata gamayyar kungiyar Handicapped ne a nan?" Girgiza kai yayi yana faɗin"ko wancan satin na samu labarin uban zai fita da ita niman taimakon kan sa, kwana ɗaya nayi da kai na fahimci kome akan ka, ka taimaka mata shekaran ta goma baki ɗaya" shiru yayi yana kallon Mai gari kafin ya ce. "Allah ya bamu ikon taimaka mata domin kai ne sanadin haka" kallon Aliyu yake domin bai tab'a ji ko ganin matashi irin shi me saukin kai ba. Dan manyan mutane wanda kana ganin shi kasan kudi da mulki ya zauna a jikinsh. Sallama yayi Nishi.
------------
"Malam Aminu kana nufin Bature ne aka kawo garin nan?" "Ina gaya maka jiya a kan idanu na ya sayi saniyar da ta kasa a mutunce , da alamu me arziki ne." Inji Malam Aminu, gyara zama malam Musa yayi ya ce. " Kai haba? Kasan dai gobe zaka kai Yarka wurin niman taimakon nan ko?"
ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Page:8
"Gaskiya kan gara na kara shi akan haka, daga Makarantar zan dauke ta" murmushi Malam Musa ya mishi tare da cewa, "kar ka manta idan aka samu me yawa kar a manta da mu domin mu ma, mu dangwali arzikn yar mu" dariya ya saka yana faɗin "haba ai kaf duniya bani da masoyi irin ka, duk abin da na samu na ka ne." Ya fada suna tafawa. Da ace Malam Aminu yasa yadda Malam Musa ya tsani ganin shi da ba zai tab'a ɗaukar shawaran shi ba, amma baki daya bai da aiki sai daukar shawarar shi, bayan idan suka yi magana shi yake gayawa sauran abokan su, su kuma su gayawa Mai gari, haka yasa Mai gari ya saka a aka kira mishi Malam Musa ya ci mutuncin shi, domin ya zama mugun aboki me son ganin bayan abokin shi da munanan shawara.
.... Tunda ya bar gidan ya nufi makarantar, yara ke bin shi musamman yan mata masu tashen balaga. Abin ya basu mamaki yadda suka gan shi Bature dan gayu, kuma yana tafiya kamar mace a yangance, asalima shi mutum ne da bai da kazar kazar, haka yana nasaba da inda ya fito ne, duk da a dabi'ar shi babu maida hankali akan mulki, amma mulki da kasaita tana bibiye da rayuwar shi, hakan yana faruwa ne idan yana cikin damuwa, ko bacin rai tow hatta maganar shi na iya sauyawa. Aliyu Abu turab, dayawan mutanen da suka san tashin sa, suna mishi lakabi markabu iyalan gwamna, gadanga kusar yaƙi, bauna saniyar sake. Shigar shi makarantar ya hadu da malamai da suka zo daga Binji, wanda kana ganin su, kasan suma aiki suka zo yi, sallama ya musu ya wuce Office din Headmaster. Office din a rufe yake shi kan sa bai zo ba. Jingina yayi da bangon office din yana me sunkuyar da kan shi. "Burr-burrrrrrr" kara wata ya gulalliyar mashin kiran Yamaha ya shigo cikin makarantar, sau daya ya d'aga kai ya kalli headmaster sannan ya cigaba da tsayuwar shi, kafin headmaster ya shigo hayaniyar yara ya cika wurin. "Bata magana bata magana ohooo" dauke kai tayi kamar bata ga suna tsokanarta ba, sai a lokacin ya d'ago ya zuba mata ido, ita kanta yadda take tafiya zaka fahimci a takure take, sannan koda bai ga fuskar ta ba, ranta a b'ace yake. "Ita ce kenan?" Ya tambayi kan sa, wucewa aji tayi tana ta gaban shi. Kallon uniform ɗinta yayi yaga yadda yake daukar idanu, ba mamaki Mahaifiyar tana kula da ita. Nana ce ta bita da gudu ta kai mata duka, faduwa tayi ta mike tana kallon Nana ta ma rasa me zata ce mata, kawai ta juya tayi tafiyar ta. Shekaru goma baya haka ya ya faru da Ummu Mansurah. Murmushi yayi yana kallon su.
***
Kalambaina estate
Anan gidan Dr Sharif yake, tare da Amaryan shi Aunty Fareedah wacce suke kira da Aunty Mom.
Tun ranar juma'a ya shigo Sokoto, amma yaki zuwa gidan Mahaifiyarsa. "Yaya Abdul!" "Na'am my angel me kike so?" "Home work aka bamu ban fada da wuri ba kuma yau zamu yi submit din shi" shafa kan ta yayi yana faɗin. "Na'imatullah me yasa baki gaya min tun jiya ba, na gani." Murmushi tayi, ta zuge jakar Yayanta me suna Hamidu yana zuwa ya make kanta. "Bata da hali aikin ta kenan ba zata fada tana da home work ba sai za a tafi school." Murmushi Abdul yayi ya ce mishi. "Kowa da kalar rayuwar sa" gyada mishi kai yayi, ko babu kome Aunty Fareedah da Yaranta suna saka shi farin ciki, madadin gidan su da ba barikin soja bane amma bin doka da oda sai a slow, gashi babu dan raha da farin ciki irin na gidan Aunty Fareedah. "Sannun ku babban Yaya da kanen shi" yar fara a yayi yana faɗin. "Aunty Mom kin ga yau Hamid bai rungume Ni ba" "oya wuce kayi rungume shi" "ayi hakuri na manta ne" yazo ya rungume shi ta baya. Abin da ya rasa kenan a cikin gidan su, yana buƙatar kulawa kodan irin laluran shi, fitowar commissioner of education, yasa suka juya yana saka links din hannun rigar shi. "Mr Hakim ka manta yau zaka koma bakin aiki? Ko so kake Hajiyar ku ta cinye ni danye?" Kallon mahaifin su yayi ya ce. "a'a idan na karya zan wuce." "Yaya kai zaka kai mu school?" "Kuna so ne na kai ku?" "Eh muna so, zan nunawa Jalilah nima Yayana yana sona" make keyarta Hamid yayi yana fadin "ke dai" kafin ya karasa ta ce mishi " baki da hali, sam baki da wani abu sabo, ko basu bane?" Ta mike da kofin tea ɗinta, ta nufi kitchen. Iyayen suka zauna. "bani Jakarta" mika mishi jakar Hamid yayi, ya saka mata. "Mamarka tace kaki maganar aure duk yarinyar da ta nima maka sai kace baka so" a hankali ya fara shan tea da Auntu Mom ta hada mishi. Yana sauraron mahaifin su, haka ma Hamid da ya nutsu yana sauraron mahaifin su. Wannan yana daga cikin abin da ya kara sakawa Alhaji Sharif Hamidu, kaunar matar shi Hajiya Fareedah, domin tarbiyyar Yaranta daban yaƙe, da ace a gidan Hajiya Dawlah ce, da yanzu yaran sun fara mishi shakiyanci da rashin hankali, ita kuwa Fareedah ko fada yake ba zaka tab"a jin tayi magana ba, asalima sai tayi shiru daga baya sun had'e a oda room, ka ga yadda yake susucewa yana bada hakuri. Tasan kan mijinta, wannan yanayin har Yaran ko fada yake musu, zasu yi shiru daga baya zaka ga sun bishi daki har suna kuka yayi hakuri, karshe kuma shi zai koma rarrashin su. Shi yasa gidan yake zaune cikin farin ciki. Haka Abdul shima dabi'ar gidan Aunty Fareedah ya kama shi, koda Hajiya Dawlah ke fada ba zai taba magana ba, tana gamawa zai ce mata kiyi hakuri. "Yana da kyau kayi aure, ka samu me kula da kai." "In Sha Allah zan yi yadda kace ayi hakuri" daga haka suka ci gaba da karyawan su, yana gamawa ya mike. "Hamid kace Widad ta fito mu tafi" "ok Sir" ya fita, "Abba ka daina mishi fada a gaban mu, mu kanen shi ne. Ba dadi" kallon Aunty Fareedah Dr Sharif yayi ya ce mata. "I did something else?" "Gaskiya ya gaya maka, kuna bukatar kebe wa ai" "Allah ya huci zuciyar Ubana ba zan kuma yiwa ɗan dan uwanka fada ba a gaban ku, don Allah kaso shi yadda yake son ku. Ya shirya ya bata da kowa saboda ku." "In sha Allah Abba, ke kucilili muje " ya kwalawa Widad kira, ta fito dauke da water bottle, ta nufi hanyar waje. Domin ya dauki jakarta, gaba ya shiga shi ya shiga baya. Suka nufi makarantar. Kiran Mother ya gani gaban shi ya fadi, ya taka birki da sauri. kallon shi suka yi. "Yaya lafiya?" "Lafiya lau yan uwana. " Haka ya cigaba da tafiya be dauki kiran ba, har suka isa makarantar, daga nan ya juyar da kan motar zuwa g.r.a gidan mahaifiyar shi. Tun a bakin kofar bayan ya ajiye motar yake jin tashin muryan ta.duk sai ya diririce. "Na zata zama zaka yi har abada a can, Nace na zata shiga cikin Fareedah zaka yi ta kuma haifarka, ni baka damu da ni ba, sai ita yadda ta tsafe Ubanka shi ne zata tsafe min kai na rantse da Allah baku isa ba, nace baku isa ba" yadda take bala'i kamar zata doke shi bai saka ya ce mata cikanka ki ba. Haka ta gama yana kallon Kannen shi, kowannen su harkan gaban shi yake, a gefen shi Taufiq ya dauki wayar shi da kayan makarantar shi ya fita sannu wannan bai ce mishi ba, tana mita Afiyyah ta fito itama ko kashi yafi shi daraja, haka ta fita sai cewa tayiwa Uwar "Hajiya na tafi" "tow" kallon ta yayi bayan sun fita ya ce mata"kiyi hakuri" bayan ya hàdiye wani yawu me daci, taya za a ce kanen ka babu shakuwa da soyayya a tsakanin ku. "Ka karya ka wuce aiki" "tow" har ya mike ta kalle shi."kana shan magani kuwa?" "Eh ina sha" "tow ya batun aure?" A duburce ya juya yana kallon ta. "Nace ya batun aure?" "Hajiya dama-dama- dama" "Abdulhakim na baka kamfani na ka rike bawai don ban san ciwon shi ba ne, iyalin zaka ajiye kamar kowa sai a wuce wurin" zama yayi yana saka hannun shi a tsakanin cinyar shi ya ce mata." Hajiya yan matan yanzu suna da buri, Hajiya rayuwata babu buri dayawa, babban burina na samu macen da zata so ni, bayan nan mu gina rayuwar mu cikin farin ciki da jin dadin, bana son tashin hankali idan kika matsa na auri yan matan zan aura amma babban matsalar farin cikin da nake son samu bai zama dole ba, ki kara min lokaci, kafin ayi min aikin karshe ina sha Allah zan gabatar da matar da nake so " shiru tayi tana kallon shi, so take tayi magana amma kuma wani bangare na zuciyar ta yana gargadin ta, da tausassa mishi. "Alright zan duba al'amarin aikin da zaa maka zai dauki 4 to 5yrs Inci gaba da ganinka babu d'a babu mata? Akwai adalci a nan?" Kamar ya fashe da kuka ya ce. "Hajiya likita bai miki bayanin yanayin ba ne?" "Idan ya min bayani sai na dauka? Ko ce maka aka yi can believe da abin da suka ce? Look ina son naganka cikin iyali da wadata wanda haka ba zai samu ba, sai kayi aure " "tow hajiya " zanyi yadda kika ce.
***
Kwara
Dukkan familyn sun hadu, a cikin su har da Sultanah karama da Sultanate, babu abin da suke bukata kamar Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari ya zartas da hukuncin shi akan Aliyu.
"Binciken da aka yi, ni na yanke hukuncin a duk inda aka ga Aliyu a kashe shi, shi ne adalcin da zan iya samarwa " ya fada a matukar sanyayye. "Gara a kai shi kotu domin zan daukaka kara." Ta fada cikin kwarin gwiwa. "Badi'atul Noor!" Baffanta ya daka mata tsawa. "Kayi hakuri Baffa batu ne na D'a nasan idan da Marigayi ko mahaifina suna raye za a samar mana da adalci tare da zakulo gaskiya. A daren ranar tana bangaren Sultanate sannan ta turowa Baba karami sako, yazo ya dauke ta. Sannan bayan nan mutuwar ta, ta turo min sako Ummina ki taimakawa Abu turab kar ya ci kome da za a kawo mishi an shirya ciyar da shi guba, ga sakon nana cikin wayata. Sannan kafin mutuwar ta, inda aka kashe ta daban inda aka ajiye gawarta daban, hujja ta karshe kashe Kabirun Gajiyah da shi idanun shi ya gane mishi kisan da aka yi, sannan itama Gajiyah aka illata lafiyarta yadda ba ta san waye akanta ba." "Badi'atul Noor hujjar kare danki ne duk wannan surutun?" Kallon Hajiya Suhailah yayi kafin ta ce mata. "Bani da buri ko yau Abdulrahman ya fadi Yarana sai naso su zauna a cikin gidan nan, balle kuma kun ga wani a cikin su bayan Baba karami? Ku sani ina shiru ne kawai don bana son magana, Uwa madubin goben D'anta Na amince da duk hukuncin da zaka yi, a cikin hukuncin har da sauke ni a matsayina, tare da sauwake min matukar zaka janye kalaman ka akan shi na bar kome na cikin gidan nan na yafe kome, amma daga ranar da gaskiya tayi halin ta, tabbas a lokacin zan zartas da nawa hukuncin....
ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Page:9
"Meye nufinki Badi'atul Noor? Don na kyale ki ba wai yana nufin kin fiyi abin..." Kura mishi idanu tayi, tana murmushin karfin hali. Bata son ta nuna gazawarta a matsayinta Na uwa bata son ta nuna kasawarta a matsayin ta na Mace me daraja a wurin kishiyoyinta, don haka ta mike tare da tattara alkyabar ka, "Sultanate kece kika haifi Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari." Takawa tayi har gaban ta tana faɗin. "Ki gaya mishi na bar miki ɗan ki, domin nawa rayuwar d'an, idan wani abu ya faru da Aliyu Abu turab. Masarautar nan tayi mana kadan na rantse da Allah" daga haka ta juya ta fita bata kuma bin ta kansu ba, domin kuwa ta gama dasu. Baki dayan su mamakin ta suke ji domin ita ɗaya ce kawai take abin da ta gadama, dukkan su suna karkashin inuwar Sultanate. "Yanzu Sultanate kenan ita Badi'atul Noor babu wanda ya isa da ita?" "Hmmm! Me zance tunda ta shigo rayuwar sa, shi kenan ai sai ta fita ta bar masarautar." Ta fada tana kallon Sultan. "A'a babu inda zata, ta zauna masarautar kawai zan duba maganar ta." Zaro idanu tayi tana faɗin. "Kamar ya? Ta bar Masarautar nan kawai" "mata ta ce, taya zan kore ta tabbas nima zan yi murabus." A tsorace Sultanate ta ce. " Akan dan wannan maganar ce zaka yi murabus?" "Na gaji ne Sultanate na gaji fitinar yau da ban na gobe daban ya ake so nayi? Don Allah ku bar ta ta huta domin hutunta shi ne hutuna " ya fada haka a sanyayye. " Shi kenan " ta mike ta bar falon cikin fushi.
.........
Masarautar Kwara.
A karni na sha uku, Masarautar ƙabilar yarbawa suka amshe ta, a hannun wasu kabilu, inda suka cigaba da da addinin gargajiya. A karni na sha hudu Mujaddadi Shehu Usmanu danfodiyo ya tura da wakilin shi Malam Abdul Aalim, inda yayi kira da azo a karbu musulunci. Duk da lokacin bai shiga cikin masarautar kwara ba, yana babban cibiyar masarautar da yake ibadan ne na da, a hankali tafiya da almajiranci ya kawo masarautar Kwara. Inda ya samu Sarkin da yake kai Afonja . Sam malam Abdul Aalim bai da burin raba Afonja da mulkin shi kasancewar ba mulki ya kawo shi ba, da'awa ce ta kawo shi, amma Afonja yaki sauraron shi, asalima sai ya shirya wata runduna na musamman suka yaƙi Shehun malamin,har ya bar yankin baki daya, shi da tsararun mutanen da suka amshi musulunci. Sai ya rubuta wasika izuwa Mujaddadi Shehu Usmanu danfodiyo. Sati uku a tsakanin sai ga sakon a yaki Afonja wanda tsabar kunya domin an ci kwara a lokacin da yaki, inda kabilu uku suka ci yaƙi.
Saboda irin tarihin da ya ke da shi na musamman na Ilorin, na farko a matsayin Yarbawa daga cikin Daular Oyo, sannan a matsayinta na fulani mai mulkin Halifancin Sakkwato, tana da al’adar yin sarauta wadda ta kasance gauraya da al’adun gargajiya da aka samo daga bangarorin biyu. Duk lokacin da sarautar Masarautar (wadda ke hannun Fulani zuriyar Shehu Alimi) ta kasance babu kowa, wakilin kowace kwata a masarautar wato; Balogun Gambari (Hausa), Balogun Ajikobi (Yarabawa), Balogun Fulani (Fulani) da Balogun Alanamu (Yoruba) - tare da shugaban gidan sarautar Afonja, Mogaji Aare, da kuma babban hakiminsa mai suna Baba. Isale na Ilorin - a taru domin zabar sabon sarki tare da nada sabon sarki, bisa amincewar gwamnan jihar Kwara. Sannan an ba wa Balogun mafi dadewa sarautar Balogun hudu sarautar Balogun Agba, wanda hakan ya sa ya zama na biyu a kan Sarkin Ilorin. Dukkan Balogun na da gundumomi da suke gudanarwa a madadin sarki.
Akwai kuma sarakunan gargajiya da kowanne ake kiransa Daudu (ko Hakimin Lardi). Suna aiki ne a matsayin hakimai masu wakiltar sarki a garuruwan dake fadin masarautar Ilorin kamar su Afon, Bode Saadu, Ipaye da Malete, da dai sauransu.
Izuwa yau kabilu biyu suka taka rawan gani sosai a masarautar, Fulani da Hausawa. Masu mulki
Gyara
Sarakunan Masarautar Ilorin:[3]

Fara Ƙarshen Mulki
1824 1842 Abdusalami dan Salih Alimi
1842 1860 Shita dan Salih Alimi
Fulani suka rike wannan matsayin tun bayan rasuwar Malam Aalim,
1860 1868 Zubayro dan Abdusalami
1868 1891 Shita Aliyu dan Shittu
1891 1896 Moma dan Zubayru
1896 14 Janairu 1914 Sulaymanu dan Aliyu
1915 Nuwamba 1919 Shuaybu Bawa dan Zubayru
17 Fabrairu 1920 Yuni 1959 Abdulkadir dan Shuaybu Bawa
Hausawa sune suke rike matsayin har zuwa lokacin da mulkin ya koma hannun yarbawa.

30 Yuni 1959 1992 Zulkarnayni Gambari dan Muhammadu Laofe Dan Bawa "Aiyelabowo V"
1992 Agusta 1995[4] Mallam Aliyu dan Abdulkadir
1995 Zuwa Yau Abdurrhman Dan Aliyu Sulu- Gambari. Wanda ya kasance bayarabe ne.
Domin a samu daidaituwar mulki na zaman lafiya, yasan ya an samu auratayya a tsakanin su baki daya, bahaushe zai auri bayarabiya da bafulatana da Bahaushiya. Kafin ya kara da wata kabila idan ta mishi. Haka zalika. Sultanate ita Bahaushiya ce, mijin da ta aura kuma bayarabe ne, wacce sunanta Mansurah. Yaranta biyu ne kacal a duniya, ita ce mata ta biyu a wurin Sultan Aliyu Dan Abdullahi sulu gambari, uwargidan ta bafulatana ce, tana da Yara maza biyu mata biyu, sunan Aisha boddi ake kiranta, sai me bin Sultanate Tawakaltullah, wacce take da yara mata uku. Abdulsamad Dan Aliyu sulu gambari, sai Jamaluddin dan Aliyu sulu gambari. Sai Amrah dan Aliyu, sai Nana Asma'u dan Aliyu. Dakin Sultanate, akwai Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari, akwai Warisah dan Aliyu. Dakin Tawakaltullah tana, Rufaidah dan Aliyu, Atikah dan Aliyu, da Batula dan Aliyu. Mata uku Dan Aliyu yayi a rayuwar shi, sannan bayan rasuwar shi aka bawa Abdulsamad mulki, wanda an bashi mulkin da sati daya ya rasu sakamakon sarar maciji. Yana auren Suhailah, yaransu uku Abdulrashid Abdulsamad Dan Aliyu, yana nan tantirin mara mutunci ne, kusan sa'an Muhammad dan Dawlat khatoon , sai kanin shi Abdulkarim. Shi kan yana Saudiya tun kafin rasuwar mahaifin su, sai kanwar su Sarah wacce kawa ce ga Ummu Mansurah. Warisah dan Aliyu, kawar Badi'atul Noor ce tun Yaranta. kuma suka taso a tare. Sai dai ita Allah bai bata haihuwa ba, inda ta auri Yayan Badi'atul Noor, ita kanta Badi'atul Noor su din jinin Shehun malamin nan Abdul Aalim sahili ne, mahaifinta jinin gidan ce yayinda mahaifiyar ta, ta kasance shuwa arab. Daga yankin borno. Su uku ne a cikin dakin su. Alhaji Khamal dan Umaru yana London Nigeria ambassador a can, sai Dawlat khatoon wacce take bin sa, sai Badi'atul Noor, da take bin Dawlat khatoon. Ita aka bawa Sultan Abdulrahman Dan Aliyu, zabin iyaye ne, ita kuma Badi'atul Noor tana da wanda take so wato Alhaji Marwan Muhammad Dan shitta. Soyayya suke me tab'a zuciya da ruhi, kowa a cikin masarautar da kewayenta yasan soyayyar Marwan da Badi'atul Noor, dan sune ake musu ikirarin Layla da majnoun, domin soyayyar tayi karfi da tasa idan daya na ciwo daya ma zai kwanta, ganin haka iyaye suka shiga al'amarin su. A lokacin Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari yana can ƙasar kalaba da matar shi, Dawlat khatoon da dansu Mahmud. Ga kuma wani cikin da take dauke da shi. Aka kira shi Yayan shi Abdulsamad Allah ya mishi rasuwa. Domin tsakanin Abdulsamad da mahaifin su sati biyu ne, yana zuwa gaisuwa ba tare da wani haufi ba, aka bashi gadon mulkin dan uwansa wanda Hajiya Suhailah da ta fito daga cikin ƙabilar Hausawa take fatan a bawa D'anta a lokacin, yaron kuma yana karami don haka aka bawa kanin mahaifin shi. Sati daya da bawa Abdurrhman Dan Aliyu sulu gambari mulki Allah yayiwa dan shi Muhammad rasuwa, inda aka tsinto gawar shi a cikin rijiyar masarautar. Mutuwar yaron ya tab'a kowa domin akwai shiga rai. Wata biyu da mutuwar shi, Dawlat khatoon ya fara nakuda, tun safe ake abu daya, domin ana da tabbacin cikin jikinta tagwaye zata haifa, sai da aka kwana aka wuni, kafin ta mahaifi yaran gawarwarki, awa biyu bayan nan sai gawarta aka samu. Tace ga garin ku, Sultan ya kadu ainun. Kwanaki arba'in da rasuwarta babu wani jan lokacin Mahaifin su Alhaji Abubakar Imam Aalim ya aurawa Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari Badi'atul Noor, ita kuma Warisah aka bawa Marwan. Kawayen biyu sun shiga kidima da tashin hankali. Musamman Badi'atul Noor da tayi ta suma tana farfaɗowa. Mahaifinta ko nace gidan su, tun bayan da mulki ya fita daga cikin gidan su, suka rike malunta sune suke jagorancin babban masalacin idi, sannan shi din babban alkaline daga kotun shara'ar musulunci. Haka aka kai Badi'atul Noor gidan mijinta. Tun daga nan yar matan nan ta shiga gujegujen bata zaman gidan, idan ta fita ta gudu sai tayi kwana uku ba asan inda take ba, ko a jikin Sultan asalima radadin mutuwar matarshi ya fiye mishi kome, haka suka share wata biyar, a lokacin da mahaifin yazo ne, yake tambayar ta cikin kunya da k'ame kame ya ce mishi ai yau kwananta biyu bata gida ta gudu. Kallon shi yayi kafin ya ce mishi. "In sha Allah bata kuma fita" daga haka ya fita. Kwana ɗaya a tsakanin sai gata ta dawo da kafarta. Amma kiyayyar da take mishi bata boye ba a gaban kowa nuna mishi take bata son shi. Da wannan yanayin har alaka me karfi na auratayya ya shiga tsakanin su. Duk yadda taso ta gudu ta gaza don dole ta hakura, shi kuwa Sultan tunda ya same ta, ya samawa kan shi nutsuwa da tsiwa da rashin mutunci tayi amma bai hana bawan Allah nan gyara mata zama da bulalan shi ba, kiyayyar tai nisa da ta fara cewa sai ta kashe shi abin da ya fara hada su da Sultanate kenan, domin da farko ganin babu jituwa a tsakanin su yasa baki daya ta zuba ta agefe. Ta shiga nima mishi yaran manyan mutane. A cikin rigimar Badi'atul Noor ta fara laulayi, tayi kuka tayi Allah ya isa tsakaninta da shi yafi kwando dubu. A haka har cikin ya isa haihuwa. Ta haifi Abubakar, watan Abubakar goma ta fara laulayi, babu yadda bata yi ba amma fir cikin ya zauna sai dai ta wahala don kanta. Tana haihuwarsa shi watan shi biyar ta samu cikin Rumaisah. Daga nan ta ajiye kayan yakinta. Haka tayi renon Rumaisah har aka haife ta. Rumaisah tana da shekara daya ta haifi Zakiyyah, daga nan tace ta gama haihuwa. Kuma wani abin burgewa yadda take kula da Yaran da shi kansa mijin ba karamin al'amari ba ne, ita kanta wani lokaci har dariyar kanta take yadda tayi ta kiyayya gashi ta haifa mishi yara har hudu, Zakiyyah na da shekara shida ta haifi Ummul Aymana, anan ma taci alwashin tayi auta, Shakaran Aymana uku sai ga cikin auta. Tasha wuya sosai domin shi aiki aka mata sannan aka rufe bakin mahaifan. Aka ajiye haihuwar itama ta guda. Yaranta shida uku mata uku maza, a lokacin Sultan ya kara mata biyu, Hajiya Badariyyah, sai Hajiya Mariyah, sai Hajiya Turai wacce take mugun kishin Sultanah karama. Akwai kiyayya me yawan gaske a tsakanin su. Domin basu ki su kashe Sultan ba. Warisah matar Marwan Muhammad Dan shitta, Kanwar Sultan. Yaranta uku mata. Hamdiya da Aneesah sai Ummul Mansurah, wacce ta ci sunan Sultanate. Bayan haihuwar Mansurah ne tayi hatsari, ta rasu. Dama ta roki Alhaji Marwan don Allah ko bayan ranta ne a bawa Badi'atul Noor rikon Mansurah. Bayan rasuwar ta kuwa ya bata Mansurah haka suka taso kai ɗaya da Aliyu domin tana da jikin girma. Tun lokacin hatsarin mahaifiyar su ta samu matsalar bata magana, haka yasa Abu turab shima baya magana, wanda da yana magana tar. Juyin duniyar nan Aliyu yaki magana dole aka saka su a special school na handicapped.
Tun daga lokacin aka fara kaiwa Abubakar da Umar hari, a lokacin Alkali Abubakar ya bawa Sultan Abdulrahman Dan Aliyu shawaran a d'aga yaran daga cikin gidan a tura su London wurin Khamal. Haka suka tafi aka bar mata Abu turab. Sai dai me bayan tafiyar su, aka juyo kan Abu turab. Haka kawai yaron ya zama wani irin marajin magana, don ma Allah ya taimaka ita din ba kanwar lasa bace, bata wasa da ibada da sakaci da Addu'a, suna yi Allah ya a warware mata......
ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza.
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!!
_Sai Allah_
ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023
*Mai_Dambu*
Page:10
Last free pages
Tunda aka dauke su Abubakar wanda sune suke kiran shi da Maina, tare da Umar wanda suke kiran shi da Saraki. Aka juya kan Abu turab, domin soyayyar da Sultanah da Sultan suke mishi ya dakushe na kowa, haka yayin sh mata, basu da wani burin da ya wuce suga farin cikin dan uwansu kuma autan su. Idan ka ga yana walwala yana tare da Rumaisah da Zakiyyah, Ummu Aymana kuwa dambe kawai basu yi domin ya masifar rena ta, irin na sako da sako, duk da ta bashi shekara goma. Ga Mansurah a gefen shi shakuwar su tun daga yarinta ne har girman su. Kuma abin da zai baka mamaki yadda ya iya magana da ita, haka ma Umminsu ta iya magana da ita. A hankali lokacin yayi ta tafiya, a gefe daya idan kika cire sakalci da shagwab'a tow kar ki kara kar ki rage Aliyu sulu gambari karshe ne, har tsiya Ummu Aymana take cewa. "kai dai ka ji kunya, kai shagwab'a matarka ya zata yi?" D'agawa Ummu Mansurah gira yake ya tambaye ta, "zaki iya da shagwab'a na?" Kunya yake saka ta jin kamar ta nutse. Haka yake babu ruwan shi da boye boye, ya taso cikin kyakkyawar tarbiyya ga kawaici da kamun kai uwa Uba zurfin nazari da zurfin ciki, haka yasa baki daya ya daura tunanin shi wurin karanta tsarin shari'a, yana gama secondary school, ya samu A.b.u zaria, a cikin hausawa yayi degree din shi na farko a fannin law. A lokacin Mansurah tana nata karatun ta a bangaren jarida, saboda ana ɗaukar masu disability, domin fassara abin da masu magana suke. Lokacin da ya gama jami'a suka tafi Umara da Ummin shi da Zakiyyah wacce take aiki da First bank na Illorin ɗin. Domin ita ta biya musu a cikin wata azumi suka tafi. Tunda suka isa idan suka yi ibada suka dawo gida daura kan shi yake akan cinyar Ummin shi kafaffun shi yana saman jikin Zakiyyah, idan Mansurah tana zuwa ta gansu. Ture kansa take ya fadi. Sai ta koma ta hau cinyar Ummin ta ce mishi da hannu. "Kai ko kunya baka ji, kazo ka wani haye cinya kamar baby, tow sauka" ta koma ta kwanta. Ita kanta Ummin su tana girmama soyayyar da suke yiwa juna. Bayan sun dawo aka yi musu baiko, domin an tura su service NYC inda aka turo mishi ya samu Sokoto. Kuma dama Kakar Badi'atul Noor uwar Babanta Yar gidan Sarautar Sokoto ce, da ita da Matar sarki musulmai y'ayan mata ne, shi Sokoto a wurin shi gida ne. Ana gobe zai bar illori a ranar an kwana an wuni ana zuba ruwa me yawan gaske. Don haka basu hadu da ita ba. Ita kuwa tana can wurin Sultanate akan lallai ta rabu da Aliyu Abu turab ta auri Abdulrashid, dama ba shiri suke da yaran gidan marigayi Abdulsamad ba, har Gara Abdulkarim suna shiri da shi ma ba cancan ba, Sarah kuwa kiri kiri suke fada domin tayi mata alkawarin sai ta auri Aliyu ko zata mutu. Don haka taki da ta gaji da magiyar da suke mata, ta turawa Aliyu sako. *Prince zo ka ɗauke ni na gaji don Allah* yana falon Ummi ya kwanta akan cinyar Rumaisah yana zuba shagwab'a domin tazo tunda mijinta baya gari. "Addah don Allah zaki kawo min visiting?" "Amma dai baka da kunya kato kawai saukar min a kafa." "Haba princess please Ummina saka baki" make bakin shi tayi tana faɗin " gidan ku, Ummin mu" tura baki yayi yana faɗin. "Oho dai sai kin kawo min ziyara sokoton...." Rike kirjin shi yayi ya tashi zaune yana haki, Ummu Aymana da ta shigo ta dauko goran ruwa ta mika mishi. Karba yayi ya sha rabin goran, sannan ya ajiye. "Auta ya dai?" Kallon wayar shi yayi yana haske. *Please ki kwana a can gobe sai ki fito da wuri* yasan idan ta gani zata mishi reply. "Baba karami meke damunka?" "Ba kome Ummi." Ya fada tare da nufar falon kasa ya dauki umbrella ya nufi bangaren su, bata nan kallon Zuwairah yayi ya ce mata." Baby bata dawo ba ne?" "Eh ranka shi dade" gaban shi yana faduwa ya fita domin ya dace ace ya je din amma bai je ba, tunda ya fita tsigar jikin shi yake tashi har ya nufi bangaren Sultanate. Ya same ta zaune tana shafa man zafi a gwiwar ta. Wayar ta ce tayi kara. "Waye?" "Tow ku gama kawai" sannan ta cillar da wayar. Tunda yayi sallama ta amsa bata kuma magana ba, asalima ko kallon inda yake bata kuma ba. Tsaki yayi zai juya ta ce mishi. "Kai dan iska waye kakewa tsaki" ganin kira yayi a wayar shi. Dubawa yayi yaga number Baby. Koda ya bi kiran wayar a kashe. "Ba ni da lokacin ki" ya fada can kasa. "Mara kunya wallahi ka min rashin kunya sai na saka Abdulrahman ya sake uwarka." Kallon wukar yanka tufa a gabanta, don haka ya dawo da sauri ya dauka. "Kai dan Ubanka me zaka yi da shi?" "Zan yanke harshen tsohuwa mara jin magana ne" sun tab'a haka da Abdulrashid ya mishi gatsali akan Idanunta abin ya faru, dauran yajin barkono yayi ya guntsa a bakin shi ya watsa mishi a fuskar shi, sannan ya ja zanin da aka daura kayan abinciin ya watsar da kayan abincin ya daure kan Abdulrashid yana me zuba mishi gargadi. "Kar ka kuma shiga harkata domin bani da kyau idan ka sake na kuma ganin kanwarka tawa Baby Iskancin sai na murde wuyar ka, zan nuna maka iskancin karya kake" tun daga ranar Sultanate ta shiga hankalin ta, domin tana mishi wulakanci da cin mutuncin bai tab'a kulata ba. "Kika ce me?" Ya tambaye kai tsaye. "Shin me ma nace na manta" jefa wukar yayi ya caki apple yana kallon ta. "Uwata matsayin ta daban haka ke matsayin ki daban, kar ki sake na kuma jin wata maganar b'atanci akan zinariyata" daga haka ya fita yana jin wani irin abu na yawo a jikin shi tabbas akwai wani fararren al'amari da yake ji zai faru ko ya faru. Haka ya wuce bangaren su. Sultanate kuwa sai da ta tsuge da kashi domin dan banza ya bata tsoro, babu abin da yake razana yan gidan baki daya kamar yadda Abu turab yake nuna musu kiyayya, duk wanda ya tab'a mishi uwa sai yaci uban sa. Haka yasa dayawan mutanen suke kallon Aliyu shi ne karfin Sultanah karama, domin idan babu shi a gefenta bata da wani karsashi. Abin da basu gane ba. Itace karfin shi domin idan babu ita a gefe bai cika shiga harkan kowa ba, sannan aduniyar shi ya tsani ka tab'a mishi ita shi yasa basu ga maciji da sauran matan. Domin ko lokacin da aka bashi guba ya ci idanun shi ya kuma budewa da rashin mutunci, amma a gaban Sultan ko Sultanah Badi'atul Noor ko yan uwan shi, mugun sangartacce ne. Goya shi ne kawai ba ayi. Amma baki daya al'amarin shi na sakaltattun yara ne.
Kwanciya yayi da tunanin tura mata sako amma babu reply. Washi gari da sassafe ya wuce inda zasu tafi, bayan ya gama jiranta. Har ya bari garin babu labarin ta, wurin karfe goma na safe aka tsinci gawarta a bayan part din shi, bayan an keta mata alfarma anci zarafinta. Hankalin al'ummar masarautar ya tashi faruwar wannan al'amarin, yayinda wasu suka ce Aliyu Abu turab ne, wasu suka ce bashi ba, Sultanate kuwa ta kad'u da mutuwar yarinyar domin kaunar Warisah ya shafi Mansurah uwa Uba jikar ta takwaran ta, jikar da take so. Domin duk Yayunta sunyi auren Y'ay'an Badi'atul Noor ne, ita kuma da kanta taso haka domin kara dankon zumunci, ganin su take kamar aminiyarta dalilin da yasa take dauke kai akan Sultanate kenan. Hamdiyah tana auren Umar saraki, Aneesah tana auren Abubakar Maina, kuma dukkan su Allah ya albarkace su da zuri'a, Maina yaran shi biyu duk maza, sai Saraki shima mace da namiji, sun kwantar da hankalin su a can inda suke. Kuma suna zaune lafiya da soyayyar juna, wani abin burgewa duk shekara sau daya suke zuwa,.bata fasa musu addu'a da sadaka ba, domin tasan wayon ba shi ya ƙare su ba, Allah ne ya kare mata su.
***
Yau sati biyu kenan da fara koyarwa, idan ya saka idanun shi akan Bimbi. Sosai yake lura da al'amarin ta, abu na farko da ya fara shine saya mata materials na karatun su, a cikin wannan yanayin sau uku Malam Aminu yana zuwa daukar ta, amma ya hana shi tafiya da ita. Yau Laraba ita kanta so take ta gudu makarantar domin ta lura da yadda Baffan su yake ta lekowa dakinsu yana kallonta. Tsoro ya saka ta shirya ko karyawan bata yi ba, haka bai wani dame shi ba, domin yayi alƙawarin daukar ta. Koda Inna Laminde ta fito ta samu ta tafi, shi kuma yana wurin dabobbin sa. "Laminde wai ba zaki gama abin karyawan nan ba ki sallame yara ba ne?" "To malam ai ta tafi ita kan Harirah zo ki dauka muku." Sake laggen hannun shi yayi ya sake sake tsaki, ya fita da sauri yana jin haushin ta. Koda ya isa ya samu ta shiga Makarantar, cafke hannunta yayi yana janta. "Wai kai Malam Aminu meye matsalar ka be? Ka bar yarinyar nan ta huta mana" "tunda ba yarku bace da sauki ai" wani malami da yake koyarwa a makarantar ya mishi magana, zai kuma magana Aliyu ya rike hannun shi yana cewa "kyale shi" haka ya ja hannunta ya tafi da ita. Murmushi Aliyu yayi domin ya samu labarin halin shi tsaf. Shi yasa shi kuma ya fito da na shi tsari. Daga makarantar gida ya wuce da ita ya tsaya a wurin hiran su, ya basu ajiyar ta. Sannan ya tafi gidan shi, yaje ya shirya tsaf. Sannan yazo ya tafi da ita. Mutumin dai be tsaya a ko ina ba, sai a Sokoto. Inda yayi ta binciken Office din NGO. Sai dai kash koda ya isa yan sanda suka yi ram da shi akan ya sato yar mutane zai yi safara da ita, ya ci duka sosai domin ana samu cases haka musamman da Dr Sharif Hamidu ya saka cewa duk wanda ba a yarda da shi ba, aka gan shi da Yara a kama shi, sun yi haka ne domin dakile miyagun ayyukan da ake yi. Sai da yayi kwana uku kafin aka nemi Yaran shi domin ya fadi sunan Zakaria, sub canza mishi kammani kan, sannan aka so shiga da case din kotu domin sun tabbatar da cewa sayar da ita yazo yi. Wannan abin ya saka shi jin haushin Bimbi domin gani yake she is a bad luck a rayuwar shi. Bayan an sallame shi, matar da ta kai Sa'ade gidanta ta kawo ta, yarinya a cikin kwana uku ta haɗa kumatai. A can Maikulki kuwa hankalin kowa ya tashi domin gani suke an sace su baki daya, Mai gari sai magana yake, dalilin maganar Aliyu ya tawo har sokoton, domin yana sane da kome.
Kan wuri ya fara sauka ya huta, sannan ya kira Zakaria. Suka yi magana ya ce mishi. "Ka taimaka a maida ita gida, kayiwa Mama bayani, sauran kuma zan san yadda zan yi da shi, but ita din ta bar garin ya daina ganinta." "Mun gode sosai haka da kayi ma ka kyauta." "A'a kuyi hakuri da abin da aka mishi" "no need ya cancanci haka" kwana biyar a Sokoto ya koma gida, inda yayi karyan hatsari yayi, ya kuma umarci Zakaria da fadar haka. Bayan ya koma dakin shi Zakaria ya shiga dakin Innar su da Sa'ade. "Innar mu mun same ku lafiya?" "Lafiya lau wai da gaske hatsari yayi" "a'a" ya zauna ya gaya mata gaskiya, sannan ya kara bata labarin yadda Aliyu yazo har Office din su da maganar Sa'ade, sannan ya mika mata takardan makarantar ta.
Kukan farin ciki Inna Laminde ta saka, domin abin ya mata dad'i, tayi ta saka mishi albarka. A gefen Aliyu kuwa so yake ayi ta ta kare. Ranar juma'a bayan an taso masallaci, ya tsare Malam Aminu cikin mutuntawa ya ce mishi. "Baban Sa'ade ashe kayi hatsari?" Ya fada yana haɗe rai. Kallon fuskar shi yayi baki daya sai ya kasa boyewa Aliyu gaskiya." Kai dai manta kawai yarinyar can ya ja min dukar tsayi lokacin da kuka ce na hakura da na hakura da duk haka bai taso ba." "Wacece kenan?" Aliyu ya tambaye shi. "Sa'ade ina ga farar kafa na haifa, yarinya ta sani asara da jin kunya da zan samu me sayar da ita zan sayar da ita tunda zargina ake" mamaki ya cika Aliyu, ya ce mishi" sai ka sayar da ita?" "Kwarai kuwa" "ka nimo shaida" "yawwa ga Malam Musa kalla can" "kima gaya masa zaka yi zaka sayar da ita?" "A'a karsana ta zance mishi" haka kuwa aka yi suna zuwa gaban Malam Musa ya ce mishi."na sayar da karsanata wa baturen binni" "nawa ka mata kudi?'" "kai nawa ka saya?" "Ka fada sai na nemi ragi idan xan iya" Malam Aminu ikon Allah.
"Kai dan Bature, nawa zaka saye ta ban damu da ko nawa zaka bani ba, fata na kar na kuma ganin kafarta a gidana...."
"Na saye ta dubu dari uku."
"Ciniki ya fada" inji malam Musa.
"Kar ka sake ta kuma dawowa nan idan kaso ka tafi da ita duniyar da ba zata iya dawowa ba, na sayar maka da ita.." "Malam Aminu ya kake abu kamar kana sayar da dan Mutum?" Malam Musa kalla ya tambaye shi, a firgice ya kalle shi, "a'a kasan saniyar da sabo zai yi yiwa ta saba da shi." "Aiho na zata wani abu ne dai." Nan ya ciro mishi tan dari biyar biyar guda shida ya mike. "Zan zo na dauka da safe gobe " "shi kenan "
***
Kasancewar har yau ana bincike yasa bata wani samun isasshen barci sosai, yau tun magariba ta kwanta. Duk da taso ganawa da Sultan amma fir yaki bata damar ganin shi. Takaici yasa ta dawowa gida ta kwanta. Wurin karfe biyu na dare wayarta ya fara ringing lokacin tana wani irin mafarki, wai ga shi an danne Yaranta za a musu yankan rago, ita kuma an daure ta. Kokari take ta kunce daurin da aka mata amma ta kasa, kiran wayar ya farkar dabita bakinta dauke da salati. daukar wayar tayi ta ga Sarkin Kofa. Karawa tayi a kunnenta. "Hello Hello Hello!!! Sultanah Badi'atul Noor, ki kare yaranki idan ta kama ki tara su a gaban ki ne duk daya, ke dai ki kasance garkuwa a gare su, domin Yakin naki ne babu me taya ki sai Allah, da maku... Ahaaaaaa" ya fasa ihu da karfi ya fadi kasa. tana ji"hello sarkin kofa" "idan kin samu hali ki kare Yaranki, kar ki yarda da kowa domin kowani mutum za a iya sayan shi ya ga bayan ki. Do....." Karan karfe da buguwar abu taji...

ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan.

+234 8130269641
+234 813 731 1900
+234 906 346 7258
+227 84 50 64 76
Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar
Top-notch season 2 2023
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan.

+234 8130269641
+234 813 731 1900
+234 906 346 7258
+227 84 50 64 76
Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar
Top-notch season 2 2023.
*Page Sir Ahmadu Bello*

A firgice ta cire wayar a kunnenta, idan hankalin ta yayi dubu to ya tashi a wannan daren da sauri ta dauko hijabinta na sallah, ta fita da gudu, gudu ba na wasa ba don m Allah ya taimaka bata da nauyin jiki, jin motsinta yasa sauran masu kula da harkokin ɓangaren ta suka fito suma suka rufa mata bayan ta. Har bangaren Sultan suka nufa, suka yi ta buga kofar bangaren dakyar ya fito ya bada izinin a bude mata. Yasanta ya kuma san halinta tun kuruciya kaifi daya ce, bata karya bata munafinci bata kuma gulma, gaskiya ce zata fadeta sai dai ka mutu. Amma yau ya ganta a gabansa a cikin yanayin firgici. "Lafiya" rike hannun shi tayi tare da sau jikinta ta zube akan gwiwar ta, tana me fashewa da kuka, ganin yadda take kuka yasa shi, zama yana fuskartatta. "Badi'atul Noor!" Ya kira sunan ta, in low voice tare da riko hannunta, "meke faruwa?" Dakyar ta iya hàdiye kukan ta, ta bude baki zata yi magana aka fara buga tambura. Kura mata idanu yayi. "Abin da zaki fada min yana da alaka da buga tamburan da ake ?" Hawaye ne ya zubo mata da mugun gudu. "Yarana Abdurrhman!" Kallonta yayi sosai domin shi dai bai tab'a jin ta kira sunan shi kai tsaye haka ba, sai yau. "Mene ne ya faru?" "An kashe Sarkin kofa, kafin su kashe shi ya kira ni ya ce na kula da Yarana." Ta fada muryanta yana rawa. Tab'e baki yayi yana faɗin."kuma sai ki tawo min kina kuka?" Da sauri ta kalle shi cike da mamaki, "Abd....!" "Kin ga in dai saboda Aliyu kike wannan abin tow ki daina, ki jira sakamakon abin da zai biyo baya kawai zaki iya tafiya" ya juya zai koma sama. "Zan tsaya musu, zan tsaya musu nace, amma ka sani ba zan tab'a yafe maka ba, domin na zo ina jin zafi a madadin ka zama kankaran da zai saya ni jin sanyi sai ka zama ruwan zafi mafi zafi a rayuwata." Ta fashe da kuka. "Me yasa ne? Me yasa baka damu da abin da zai je ya zk ne? Ka sake min ragamar kula da rayuwar Yarana baki daya, meye na maka? Ehe gaya min meye na maka? Ko don yanzu babu abin da zaka mora a jikina yasa nake wulakanta Ni? Nace ko dan babu abin da zai dauke maka gajiyar ka ke cin zarafina?" "Badi'atul Noor" "meye Abdulrahman? Nace meye?" Ta tambaye shi tana kallon shi, baki daya jikin shi yayi sanyi shi ba haka yake nufi da ita ba wallahi. "Kije gobe zamu yi magana" "idan ka so kar ka nime ni, in sha Allah ba zan kuma maka magana akan halin da Yarana suke ciki ba." Haka ta juya zata fita yana kallonta, har ta isa bakin kofar ta juya tana kallon shi. "ka rubuta ka ajiye na gama kuka na, daga ranar da wani abu ya faru, sai na kashe ka." Yadda tayi maganan da wani irin confidence yasa shi shan jinin jikin shi tabbas ran yan mata ya b'aci, yana tsaye Sarkin fada ya shigo tare da zubewa a kasa, yana faɗin. "Allah ya baka nasara, me Fulani da Hausawa, an samu gawar Bilyaminu a wajen masarautar nan" "a kira masu bincike su duba shi." Ya juya ya haura sama, bai shiga dakin da Badariyyah take ba, sai Safa da Marwa yake alamar yana cikin damuwa ainun, ya hango kiyayyar shi sabo fil a cikin Idanunta, ya hango kin shi amma bai hango mutuwarsa a hannun ta yake ba, domin ya san ta kai matakin da ba zata iya rayuwa babu yaranta ba. Har garin Allah ya waye babu wanda ya rintsa daga cikin gidan baki daya domin ko yan ba ruwana tsoro ta hana su barci. Ita kanta Hajiya Suhailah tattara Abdulrashid tayi ta kintsa shi a falon, dama Abdulkarim tun bayan mutuwar Mansurah ya bar garin yanzu ga shi an kashe Kabiru ga Gajiye bata da lafiya ko magana bata yi. Yanzu kuma ga Sarkin Kofa anya babu wanda yake son ganin bayan shi.? Wannan shi ne tambayar da yayiwa kansa.
Bayan an gama bincike aka yiwa Sarkin kofa jana'izar shi. Kafin hantsi Zakiyyah da Rumaisah tare da Ummu Aymana sun zo gidan, ganin yadda Mahaifiyar su, take cikin damuwa yasa Rumaisah ta dauke wayar ta, ta kashe domin har lokacin kiran layin Abuturab take ko zai dauka. Amma wayar a kashe, dake Aymana nurse ce babba Allah ta mata da sunan na zazzaɓi ne. Take barci yayi gaba da ita domin naaa barci ne, tunda suka iso suka nufi bangaren mahaifin su, dake yana shiri sosai da Yaran shi mata, har waɗancan ƙananan yaran. Bayan sun mishi gaisuwa suka zauna suna dan tab'a hira, gyara murya yayi yana faɗin. "Ku kula da mahaifiyar ku, domin tana cikin damuwa
" Da wannan suka fito daga wurin shi, suna zauna suka lura da bata taba barci ba, sai dai lokaci zuwa lokaci tana zubda hawaye, allurar barci suka mata, duk da abokan zamanta basu san halin da take ciki ba, amma kuma suna farin ciki da halin da take ciki idan ka cire Hajiya Turai da tafito tana faɗin. "Duk zurfin cikin mutum da iya takun shi karya ta kare mishi,." Domin har harabar Sultanah karama ta isa tana habaici. Barcin awa uku tayi ta farka daidai lokacin da Maina ya kirata. Zata dauki wayar Rumaisah ta dauka tana kallon fuskar ta. "Hammayo" "Na'am ya sebo? Ashe abin da ya faru kenan bayan barin Bamanga gida?" "Eh wallahi, al'amarin yayi tsauriwa Ummin mu, ina ga." Mikewa tayi tana barin dakin yan uwan suka bita da idanu, lumshe idanunta Badi'atul Noor tayi, domin bata da karfi a jikinta "Ummin mu ko zaki watsa ruwa ne?" "Abu Turab ya kira?" "A'a Hammayo ne ya kira" gyada kai tayi tana kallon kofar. Da taimakon Zakiyyah ta shiga ban dakin Ummu Aymana ta shiga kintsa dakin kafin ta fito. A ban dakin kallon Zakiyyah tayi tana faɗin. "Cika min ruwan." "Tow" ta fada tana cika mata ruwan, sai da ta ajiye mata kome zata fita ta ce mata. "Ki kira min Abu Turab" "tow zan kira shi" A falon sama na farko ta shiga ta zauna tana waya da Maina. "Hammayo ina ga ka shirya mata zuwa wurin ku, kai da Saraki haka ne kawai zai saka ta samu nutsuwa a ranta don Allah" "shi kenan, ku shirya nan da wata sati sai ta zo, amma why not mu haɗu a Umra zai fi nan, domin a can ibada zai rage mata damuwa, nan kuma Zulimi zai kara mata zama a nan din" "kuma haka ne, in sha Allah zan kira ka idan kome ya amma kuma yaushe ta dawo ko sati Uku ba ayi ba, sai dai tazo wurin ku kawai" "kuma gaskiya ne ba damuwa tazo zan gayawa Saraki, sannan anya babu wani abu da yake faruwa?" "A'a domin dai Dad bai gaya mana kome ba, amma ita na fuskanci akwai damuwa a ranta." "Tow Allah ya kyauta" "Amin Ya Allah" ya kashe wayar sai ga kiran Abu turab, "Auta" "Adda ina Jasrah?" "Lafiyan su lau." "Ina Ummina?" Murmushn karfin hali tayi tana faɗin."tana wanka an jima ka kira" "addaaaaaaaah! Ku haɗa ni da Ummu Mansurah please" "ka jira Ummi" ta kashe wayar, ta wuce zata fita haduwa tayi da Zuwairah tana wucewa zata kai kayan abinci dakin Ummin. "Kawo na kai." "Ayya Uwar ɗakina bari naga Ummin mu mana" "tow shi kenan" haka Rumaisah ta shiga gaba Zuwairah tana bin bayanta har zuwa dakin, ajiye tiren tayi tana gaishe su. "lafiya lau." "Ina Ummin?" "Yanzu zata fito" "tow Allah ya fito da ita lafiya" tana zaune a wurin sai ga Ummin ta fito,kallon Zuwairah tayi sannan ta ce mata. "Zuwairah" "Na'am Ummin mu, Sultanah! Ya jikinki? " "Da sauki" ta wuce closet dinta, ta zaɓi kayanta ta zauna tana shafa mai maganar Sarkin kofa ya dawo mata a rai. *Kada ki yarda da kowa! Kare Yaranki" zura doguwar riga Sweden cotton fabric lacce ta saka, dan kwalin yana hannunta ta fito. Ta zubawa Yaranta idanu, "kun tab'a wani abu daga ne a cikin abincin nan?" "A'a bamu tab'a kome ba" juyawa tayi ta koma sai da ta shirya sannan ta fito daga cikin dakin fuskarta tsam zaka iya rantsewa bata da wani damuwa a rayuwar ta. "Ummin mu kin fito? Ya jikin naki?" "Alhamdulillahi da sauki sosai." Zama tayi a gaban Abincin, ta kalli azurfan hannunta yayi duhu. "Zakiyyah cire min sarkan wuyar ki" cirewa tayi ta mika mata har da kwad'on, ta jefa cikin flask na tea ɗin. Sai d ya jima ta juye tea ɗin a cikin cups din wurin. Sai da tabi abincin baki daya ta jefa sarkan, ganin kalar shi bai sauya ba yasa ta kalle su. "zan baku shawara a matsayina na mahaifiyar ku, kuma kawar ku." Kallon su tayi ganin yadda suka tsare ta da idanu bata san lokacin da ta sake murmushin dole ba, tana faɗin. "Sannun ku matsorata sai kace nace ga dodo. Abin da zan gaya muku shi ne, ku nisanta kanku daga tara masu taya ku zama. Ku kula sosai, ku saka idanu domin akwai wani al'amari da naso." "Akan me zaki tara min yara kina razana min su da shirmen ki na banza?" Ya tambaye ta yana shigowa cikin dakin. Tura baki tayi tana faɗin"akan me ba zan gaya musu gaskiya ba, ko an ce maka kowa hakuri yake da shiri irinka? Ko ance maka kowa irinka ne" a hankali Rumaisah da take babba a cikin su ta mike. "Zauna wato kece kika d'agawa Maina hankali ko?" "A'a Dad halin da Ummin mu take ciki yasa nayi tunanin ta koma wurin shi " juyawa yayi yana kallon Badi'atul Noor. "Ke" d'ago fararren idanunta tayi ta zuba mishi fess, wani abu ta ji ya tsaya mata a wuyarta. "Babu inda zaki tafi, fisabilillahi me yasa kike kin min haka? Kin fini son Ƴaran ne?" Wani dauke kai tayi tana kurban shayi, "Allah ya huci zuciyar ka" ta fada a hankali, tana sassauta fushinta. Juya harshe yayi shi da Rumaisah suka shiga yin fulatanci, tana jin su, amma bata da niyyar shiga maganar. "Batun zuwan ta Ingila na soke" d'ago kai tayi tana kallon Rumaisah. "When aka yi shirin tafiya Ingila bani da labari?" Tambaye su. "Ummi wai mun ga stresst yayi miki yawa yasa muka yi decided ki tafi can ki huta." Kasa kasa ta kalle shi tayi kwafa,jan yaran sa yayi da hira domin yasan halinta tsaf ta wanke shi ba abu me wuya ba ne, shi kansa yasan kaf cikin matan shi zai yi wuya a samu biyunta domin ba ruwanta ko waye kai, kana mata ba daidai ba, zata magana sannan san jiya bata rai, amma ba haka yana nufin ba zai iya tunkarar ta domin rarrashi ba ne. Ko yanzu da ya zo ne domin ya bata baki amma yadda yaga fuskar ta yasa shi shanye duk abin da yazo da shi.
***
Sokoto
"Ikon Allah Sophia ce ta girma haka? When haduwar bata kai haka ba." Inji Hajiya Dawlah, dariya Uwar yarinyar tayi Hajiya Nazirah mata ga tsohon IG na yan sanda, ta ce. "Gata nan ai jikin girma ne da ita, aji ta biyu a Abti tana karanta environmental." "Masha Allah, Kice muna da duba gari kenan " "Ai fa gata nan, ya jikin Abdul da fatan an yi nasarar aikin shi da aka mishi." Jim tayi kafin ta ajiye kofin hannunta ta ce." eh tow Alhamdulillahi tunda sun bashi hutu kamar yadda naso yayi aure sun ce sai sun mishi aikin karshe tun ku, amma har ga Allah ina son yayi aure." "Gaskiya ayi hakuri tukun ya samu lafiya ai kome dan lafiya ne. Ya batun shegiyar kishiyar ki?" "Tsinanniya dai tunda ta raba ni da mijina da Abdul din ba, sun zaɓe ta ta musu asiri" ta fadi maganar a raunane. "Allah ya saka miki" sun jima suna daukar alhakin Aunty Faridah. "Assalamu alaikum, sannun ku da gida Hajiya " ya fada yana wucewa dakin shi. "Abdul baka ga bakinsa ba ce, Hajiya Nazirah ce makociyar mu na London " a fisge ya ce mata "ai sannu da zuwa ya wuce" abin ya b'atawa Hajiya Daulah rai kamarta danta yaga kawar ta na arzikn ya mata kallon hadarin kaji. Jinjina kai tayi ta ce "ina zuwa Hajiya Nazirah " ta bi bayan sá, yana zaune yana bude wardrobe din shi, dama can mantuwa yayi ganin yadda ta banko kofar yasa shi d'ago kai da sauri. "Me kake nufi? Ta maka kama da yar tasha ce?" "Hajiya don Allah kiyi hakuri" ya fada domin ya dakatar da jarabarta. "Abdul Hakim" kamar zai fasa ihu ya kalle ta. "Don Allah kiyi hakuri zan dauki files ne na manta." "Wuce muje ka bata hakuri" "Toh Hajiya" ya bar binciken ya nufi waje, haka suka fito ya cewa Hajiya Nazirah. "Kiyi hakuri." "Laaa ba dai fada kika mishi ba, ai da alamu sauri yake." "Koma mene ne ba zan dauki renin hankali ba." Ta gama cika bakinta ya bar su a wurin. "Banga Afiyyah" "suna da test ai bata gida" juyawa yayi abin sa bai kuma bin ta kan su ba."Don Allah ki turo min Sophia mana, ina son su hadu da su Afiyyah" "tow ba kome zata zo dake a can abuja take wurin kanwata" "don Allah ki turo min ita su saba da Yaran nan" " in sha Allah zan turo ta" motsin Abdul yasa su juyawa suja gan shi ya waya a hankali, kafin ya musu sallama ya bar gidan. "Gaskiya Abdulhakim ya girma yana bukatar iyali amma a ce magidanci irin sa babu mace ai bai dace ba, gaskiya ki tashi a tsaye domin haka bai dace ba" cikin yanayin jimami Hajiya Daulah ta ce mata" ya zanyi tow? Kowa ya juya min baya akan sai dai a bi Shawaran likita" "likita Allah ne? Babu abin da zasu iya idan zaki nima mishi mace wacce zata kula da shi amma abar shi babu mace akwai damuwa." Ai kamar an sosa mata inda yake mata kaikayi ta ce."ya zanyi? Baki daya sun ki amincewa na nima mishi aure, sannan shima har yau yaki maganar auren sai na kawo maganar zai fara kauce kauce. Wallahi na rasa yadda zan yi anya ba hannu aka saka mishi ba?" Kallon juna suka yi baki a bude kafin suka ce. "Tabbas biri yayi kama da mutum.".....
African Queen products
Sabulun matsi
Garin matsi
Humra
Turaren wuta
Maganin Infection
Ga number wayata...08130269641
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan.

+234 8130269641
+234 813 731 1900
+234 906 346 7258
+227 84 50 64 76
Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar
Top-notch season 2 2023.
*Page Sir Ahmadu Bello*

A firgice ta cire wayar a kunnenta, idan hankalin ta yayi dubu to ya tashi a wannan daren da sauri ta dauko hijabinta na sallah, ta fita da gudu, gudu ba na wasa ba don m Allah ya taimaka bata da nauyin jiki, jin motsinta yasa sauran masu kula da harkokin ɓangaren ta suka fito suma suka rufa mata bayan ta. Har bangaren Sultan suka nufa, suka yi ta buga kofar bangaren dakyar ya fito ya bada izinin a bude mata. Yasanta ya kuma san halinta tun kuruciya kaifi daya ce, bata karya bata munafinci bata kuma gulma, gaskiya ce zata fadeta sai dai ka mutu. Amma yau ya ganta a gabansa a cikin yanayin firgici. "Lafiya" rike hannun shi tayi tare da sau jikinta ta zube akan gwiwar ta, tana me fashewa da kuka, ganin yadda take kuka yasa shi, zama yana fuskartatta. "Badi'atul Noor!" Ya kira sunan ta, in low voice tare da riko hannunta, "meke faruwa?" Dakyar ta iya hàdiye kukan ta, ta bude baki zata yi magana aka fara buga tambura. Kura mata idanu yayi. "Abin da zaki fada min yana da alaka da buga tamburan da ake ?" Hawaye ne ya zubo mata da mugun gudu. "Yarana Abdurrhman!" Kallonta yayi sosai domin shi dai bai tab'a jin ta kira sunan shi kai tsaye haka ba, sai yau. "Mene ne ya faru?" "An kashe Sarkin kofa, kafin su kashe shi ya kira ni ya ce na kula da Yarana." Ta fada muryanta yana rawa. Tab'e baki yayi yana faɗin."kuma sai ki tawo min kina kuka?" Da sauri ta kalle shi cike da mamaki, "Abd....!" "Kin ga in dai saboda Aliyu kike wannan abin tow ki daina, ki jira sakamakon abin da zai biyo baya kawai zaki iya tafiya" ya juya zai koma sama. "Zan tsaya musu, zan tsaya musu nace, amma ka sani ba zan tab'a yafe maka ba, domin na zo ina jin zafi a madadin ka zama kankaran da zai saya ni jin sanyi sai ka zama ruwan zafi mafi zafi a rayuwata." Ta fashe da kuka. "Me yasa ne? Me yasa baka damu da abin da zai je ya zk ne? Ka sake min ragamar kula da rayuwar Yarana baki daya, meye na maka? Ehe gaya min meye na maka? Ko don yanzu babu abin da zaka mora a jikina yasa nake wulakanta Ni? Nace ko dan babu abin da zai dauke maka gajiyar ka ke cin zarafina?" "Badi'atul Noor" "meye Abdulrahman? Nace meye?" Ta tambaye shi tana kallon shi, baki daya jikin shi yayi sanyi shi ba haka yake nufi da ita ba wallahi. "Kije gobe zamu yi magana" "idan ka so kar ka nime ni, in sha Allah ba zan kuma maka magana akan halin da Yarana suke ciki ba." Haka ta juya zata fita yana kallonta, har ta isa bakin kofar ta juya tana kallon shi. "ka rubuta ka ajiye na gama kuka na, daga ranar da wani abu ya faru, sai na kashe ka." Yadda tayi maganan da wani irin confidence yasa shi shan jinin jikin shi tabbas ran yan mata ya b'aci, yana tsaye Sarkin fada ya shigo tare da zubewa a kasa, yana faɗin. "Allah ya baka nasara, me Fulani da Hausawa, an samu gawar Bilyaminu a wajen masarautar nan" "a kira masu bincike su duba shi." Ya juya ya haura sama, bai shiga dakin da Badariyyah take ba, sai Safa da Marwa yake alamar yana cikin damuwa ainun, ya hango kiyayyar shi sabo fil a cikin Idanunta, ya hango kin shi amma bai hango mutuwarsa a hannun ta yake ba, domin ya san ta kai matakin da ba zata iya rayuwa babu yaranta ba. Har garin Allah ya waye babu wanda ya rintsa daga cikin gidan baki daya domin ko yan ba ruwana tsoro ta hana su barci. Ita kanta Hajiya Suhailah tattara Abdulrashid tayi ta kintsa shi a falon, dama Abdulkarim tun bayan mutuwar Mansurah ya bar garin yanzu ga shi an kashe Kabiru ga Gajiye bata da lafiya ko magana bata yi. Yanzu kuma ga Sarkin Kofa anya babu wanda yake son ganin bayan shi.? Wannan shi ne tambayar da yayiwa kansa.
Bayan an gama bincike aka yiwa Sarkin kofa jana'izar shi. Kafin hantsi Zakiyyah da Rumaisah tare da Ummu Aymana sun zo gidan, ganin yadda Mahaifiyar su, take cikin damuwa yasa Rumaisah ta dauke wayar ta, ta kashe domin har lokacin kiran layin Abuturab take ko zai dauka. Amma wayar a kashe, dake Aymana nurse ce babba Allah ta mata da sunan na zazzaɓi ne. Take barci yayi gaba da ita domin naaa barci ne, tunda suka iso suka nufi bangaren mahaifin su, dake yana shiri sosai da Yaran shi mata, har waɗancan ƙananan yaran. Bayan sun mishi gaisuwa suka zauna suna dan tab'a hira, gyara murya yayi yana faɗin. "Ku kula da mahaifiyar ku, domin tana cikin damuwa
" Da wannan suka fito daga wurin shi, suna zauna suka lura da bata taba barci ba, sai dai lokaci zuwa lokaci tana zubda hawaye, allurar barci suka mata, duk da abokan zamanta basu san halin da take ciki ba, amma kuma suna farin ciki da halin da take ciki idan ka cire Hajiya Turai da tafito tana faɗin. "Duk zurfin cikin mutum da iya takun shi karya ta kare mishi,." Domin har harabar Sultanah karama ta isa tana habaici. Barcin awa uku tayi ta farka daidai lokacin da Maina ya kirata. Zata dauki wayar Rumaisah ta dauka tana kallon fuskar ta. "Hammayo" "Na'am ya sebo? Ashe abin da ya faru kenan bayan barin Bamanga gida?" "Eh wallahi, al'amarin yayi tsauriwa Ummin mu, ina ga." Mikewa tayi tana barin dakin yan uwan suka bita da idanu, lumshe idanunta Badi'atul Noor tayi, domin bata da karfi a jikinta "Ummin mu ko zaki watsa ruwa ne?" "Abu Turab ya kira?" "A'a Hammayo ne ya kira" gyada kai tayi tana kallon kofar. Da taimakon Zakiyyah ta shiga ban dakin Ummu Aymana ta shiga kintsa dakin kafin ta fito. A ban dakin kallon Zakiyyah tayi tana faɗin. "Cika min ruwan." "Tow" ta fada tana cika mata ruwan, sai da ta ajiye mata kome zata fita ta ce mata. "Ki kira min Abu Turab" "tow zan kira shi" A falon sama na farko ta shiga ta zauna tana waya da Maina. "Hammayo ina ga ka shirya mata zuwa wurin ku, kai da Saraki haka ne kawai zai saka ta samu nutsuwa a ranta don Allah" "shi kenan, ku shirya nan da wata sati sai ta zo, amma why not mu haɗu a Umra zai fi nan, domin a can ibada zai rage mata damuwa, nan kuma Zulimi zai kara mata zama a nan din" "kuma haka ne, in sha Allah zan kira ka idan kome ya amma kuma yaushe ta dawo ko sati Uku ba ayi ba, sai dai tazo wurin ku kawai" "kuma gaskiya ne ba damuwa tazo zan gayawa Saraki, sannan anya babu wani abu da yake faruwa?" "A'a domin dai Dad bai gaya mana kome ba, amma ita na fuskanci akwai damuwa a ranta." "Tow Allah ya kyauta" "Amin Ya Allah" ya kashe wayar sai ga kiran Abu turab, "Auta" "Adda ina Jasrah?" "Lafiyan su lau." "Ina Ummina?" Murmushn karfin hali tayi tana faɗin."tana wanka an jima ka kira" "addaaaaaaaah! Ku haɗa ni da Ummu Mansurah please" "ka jira Ummi" ta kashe wayar, ta wuce zata fita haduwa tayi da Zuwairah tana wucewa zata kai kayan abinci dakin Ummin. "Kawo na kai." "Ayya Uwar ɗakina bari naga Ummin mu mana" "tow shi kenan" haka Rumaisah ta shiga gaba Zuwairah tana bin bayanta har zuwa dakin, ajiye tiren tayi tana gaishe su. "lafiya lau." "Ina Ummin?" "Yanzu zata fito" "tow Allah ya fito da ita lafiya" tana zaune a wurin sai ga Ummin ta fito,kallon Zuwairah tayi sannan ta ce mata. "Zuwairah" "Na'am Ummin mu, Sultanah! Ya jikinki? " "Da sauki" ta wuce closet dinta, ta zaɓi kayanta ta zauna tana shafa mai maganar Sarkin kofa ya dawo mata a rai. *Kada ki yarda da kowa! Kare Yaranki" zura doguwar riga Sweden cotton fabric lacce ta saka, dan kwalin yana hannunta ta fito. Ta zubawa Yaranta idanu, "kun tab'a wani abu daga ne a cikin abincin nan?" "A'a bamu tab'a kome ba" juyawa tayi ta koma sai da ta shirya sannan ta fito daga cikin dakin fuskarta tsam zaka iya rantsewa bata da wani damuwa a rayuwar ta. "Ummin mu kin fito? Ya jikin naki?" "Alhamdulillahi da sauki sosai." Zama tayi a gaban Abincin, ta kalli azurfan hannunta yayi duhu. "Zakiyyah cire min sarkan wuyar ki" cirewa tayi ta mika mata har da kwad'on, ta jefa cikin flask na tea ɗin. Sai d ya jima ta juye tea ɗin a cikin cups din wurin. Sai da tabi abincin baki daya ta jefa sarkan, ganin kalar shi bai sauya ba yasa ta kalle su. "zan baku shawara a matsayina na mahaifiyar ku, kuma kawar ku." Kallon su tayi ganin yadda suka tsare ta da idanu bata san lokacin da ta sake murmushin dole ba, tana faɗin. "Sannun ku matsorata sai kace nace ga dodo. Abin da zan gaya muku shi ne, ku nisanta kanku daga tara masu taya ku zama. Ku kula sosai, ku saka idanu domin akwai wani al'amari da naso." "Akan me zaki tara min yara kina razana min su da shirmen ki na banza?" Ya tambaye ta yana shigowa cikin dakin. Tura baki tayi tana faɗin"akan me ba zan gaya musu gaskiya ba, ko an ce maka kowa hakuri yake da shiri irinka? Ko ance maka kowa irinka ne" a hankali Rumaisah da take babba a cikin su ta mike. "Zauna wato kece kika d'agawa Maina hankali ko?" "A'a Dad halin da Ummin mu take ciki yasa nayi tunanin ta koma wurin shi " juyawa yayi yana kallon Badi'atul Noor. "Ke" d'ago fararren idanunta tayi ta zuba mishi fess, wani abu ta ji ya tsaya mata a wuyarta. "Babu inda zaki tafi, fisabilillahi me yasa kike kin min haka? Kin fini son Ƴaran ne?" Wani dauke kai tayi tana kurban shayi, "Allah ya huci zuciyar ka" ta fada a hankali, tana sassauta fushinta. Juya harshe yayi shi da Rumaisah suka shiga yin fulatanci, tana jin su, amma bata da niyyar shiga maganar. "Batun zuwan ta Ingila na soke" d'ago kai tayi tana kallon Rumaisah. "When aka yi shirin tafiya Ingila bani da labari?" Tambaye su. "Ummi wai mun ga stresst yayi miki yawa yasa muka yi decided ki tafi can ki huta." Kasa kasa ta kalle shi tayi kwafa,jan yaran sa yayi da hira domin yasan halinta tsaf ta wanke shi ba abu me wuya ba ne, shi kansa yasan kaf cikin matan shi zai yi wuya a samu biyunta domin ba ruwanta ko waye kai, kana mata ba daidai ba, zata magana sannan san jiya bata rai, amma ba haka yana nufin ba zai iya tunkarar ta domin rarrashi ba ne. Ko yanzu da ya zo ne domin ya bata baki amma yadda yaga fuskar ta yasa shi shanye duk abin da yazo da shi.
***
Sokoto
"Ikon Allah Sophia ce ta girma haka? When haduwar bata kai haka ba." Inji Hajiya Dawlah, dariya Uwar yarinyar tayi Hajiya Nazirah mata ga tsohon IG na yan sanda, ta ce. "Gata nan ai jikin girma ne da ita, aji ta biyu a Abti tana karanta environmental." "Masha Allah, Kice muna da duba gari kenan " "Ai fa gata nan, ya jikin Abdul da fatan an yi nasarar aikin shi da aka mishi." Jim tayi kafin ta ajiye kofin hannunta ta ce." eh tow Alhamdulillahi tunda sun bashi hutu kamar yadda naso yayi aure sun ce sai sun mishi aikin karshe tun ku, amma har ga Allah ina son yayi aure." "Gaskiya ayi hakuri tukun ya samu lafiya ai kome dan lafiya ne. Ya batun shegiyar kishiyar ki?" "Tsinanniya dai tunda ta raba ni da mijina da Abdul din ba, sun zaɓe ta ta musu asiri" ta fadi maganar a raunane. "Allah ya saka miki" sun jima suna daukar alhakin Aunty Faridah. "Assalamu alaikum, sannun ku da gida Hajiya " ya fada yana wucewa dakin shi. "Abdul baka ga bakinsa ba ce, Hajiya Nazirah ce makociyar mu na London " a fisge ya ce mata "ai sannu da zuwa ya wuce" abin ya b'atawa Hajiya Daulah rai kamarta danta yaga kawar ta na arzikn ya mata kallon hadarin kaji. Jinjina kai tayi ta ce "ina zuwa Hajiya Nazirah " ta bi bayan sá, yana zaune yana bude wardrobe din shi, dama can mantuwa yayi ganin yadda ta banko kofar yasa shi d'ago kai da sauri. "Me kake nufi? Ta maka kama da yar tasha ce?" "Hajiya don Allah kiyi hakuri" ya fada domin ya dakatar da jarabarta. "Abdul Hakim" kamar zai fasa ihu ya kalle ta. "Don Allah kiyi hakuri zan dauki files ne na manta." "Wuce muje ka bata hakuri" "Toh Hajiya" ya bar binciken ya nufi waje, haka suka fito ya cewa Hajiya Nazirah. "Kiyi hakuri." "Laaa ba dai fada kika mishi ba, ai da alamu sauri yake." "Koma mene ne ba zan dauki renin hankali ba." Ta gama cika bakinta ya bar su a wurin. "Banga Afiyyah" "suna da test ai bata gida" juyawa yayi abin sa bai kuma bin ta kan su ba."Don Allah ki turo min Sophia mana, ina son su hadu da su Afiyyah" "tow ba kome zata zo dake a can abuja take wurin kanwata" "don Allah ki turo min ita su saba da Yaran nan" " in sha Allah zan turo ta" motsin Abdul yasa su juyawa suja gan shi ya waya a hankali, kafin ya musu sallama ya bar gidan. "Gaskiya Abdulhakim ya girma yana bukatar iyali amma a ce magidanci irin sa babu mace ai bai dace ba, gaskiya ki tashi a tsaye domin haka bai dace ba" cikin yanayin jimami Hajiya Daulah ta ce mata" ya zanyi tow? Kowa ya juya min baya akan sai dai a bi Shawaran likita" "likita Allah ne? Babu abin da zasu iya idan zaki nima mishi mace wacce zata kula da shi amma abar shi babu mace akwai damuwa." Ai kamar an sosa mata inda yake mata kaikayi ta ce."ya zanyi? Baki daya sun ki amincewa na nima mishi aure, sannan shima har yau yaki maganar auren sai na kawo maganar zai fara kauce kauce. Wallahi na rasa yadda zan yi anya ba hannu aka saka mishi ba?" Kallon juna suka yi baki a bude kafin suka ce. "Tabbas biri yayi kama da mutum.".....
African Queen products
Sabulun matsi
Garin matsi
Humra
Turaren wuta
Maganin Infection
Ga number wayata...08130269641
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan.

+234 8130269641
+234 813 731 1900
+234 906 346 7258
+227 84 50 64 76
Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar
Top-notch season 2 2023.

"Sir Abubakar tafawa balewa*

Ya zamu yi? Matukar kika bar shi a haka ba makawa an gama da shi kamar mahaifin sa." Inji Hajiya Nazirah, "Ya zanyi?" Hajiya Daulah ta tambaye ta, "tashi zaki yi tsaye idan ba haka ba, zasu kai ki su baro ki" dag haka ta dauki jakarta tana me mata sallama hade da gargadi me shiga jiki kan shi, domin itama tana son ta samu damar shiga cikin arzikn Hajiya Daulah tun ba yau ba take son shiga itama a dama da ita, shi yasa tana zuwa ta nuna mata hoton Yarta Sophia, domin tarkonta ya kama kurciya, kuma ta samu damar haka sai dai kuma yadda ta tunzura Hajiya Daulah ta kuma nuna mata ai tana tare da ita shine dalilin da yasa Hajiya Daulah ba zata kawo cutar ta zata yi ba. Kuma a tunanin ita sai ta san raunin Hajiya Daulah kuma gashi ta samu.
***
Maikulki
Duk amintar Malam Aminu da Malam Musa kalla, dakyar da sudin goshi ya bashi dari biyar, itama sai da ya gama jin kamar rayuwar shi yake zarewa zai bashi ya kalli Malam Musa kalla ya washe baki ya mika mishi dari biyar din. "Ai Malam Kalla nasan ai na fita hakkin ka, domin kai ne kayi mana shaida" "tun jiya Juma'a aka baka kudin nan sai yau ka gadaman bani sannan ka dauki dari biyar ka bani anya malam Aminu ka san hakkin abota kuwa? Jeka da shi ma yafe" ya mike yana karkade jikin shi. Tsuru tsuru kafin yayi wuf ya tare Malam Musa kalla. "Shi kenan naji zan kara maka jaka daya a kai kaga jaka uku da rabi kenan" ya fada yana washe baki kamar sauna. "Kasan Allah bani hanya" malam Musa kalla ya fada da ƙarfi, "shi kenan xan kara maka jaka daya da rabi ya tashi jaka biyar kenan." Wani kallon banza Malam Musa kalla ya watsa mishi yana faɗin. "Kaf garin nan waye yake baka shawara na gari? Waye yake maka abin da nake maka maza hada kudinka ka bar nan" "shi kenan ka yi hakuri zan baka jaka ashirin " ya fada yana kallon Malam Musa kalla. A ran ya ce wannan da yasan Bimbi na sayar sai ya kusan kwace kuɗin. "Shi kenan zan amsa amma daga yau babu ni babu kai." Daga haka ya fisge kuɗin, "wai duk akan la'adar ne zai raba tsakanin mu? Indai akan sa ne zan baka jaka hamsin dubu goma sha biyar kenan" wani yalwataccen Murmushi Malam Kalla ya sake yana faɗin. "Ko kai fa, meye amfanin abotar na mu matukar ba zamu ribanci juna ba, madalla ya maganar Bimbi ne?" Gaban sa ne ya fadi ya kalli Malam Musa kalla ya ce mishi." Ya'u zai tafi da ita can birni domin na gaji da ganinta" "abu yayi kyau amma ya maganar niman taimakon da ita" wani irin zabura Malam Aminu yayi yana zare idanu. "A'a bar wannan zancen." "Ai kuwa shi ya dace muyi baka san idan tana birnin shi ne." "Sai an jima idan na fito sallah la'asar zan kawo maka sakon ka." Daga haka ya bar wurin kamar zai tashi sama, rigar shi kuwa iska tana kad'ata kamar an hura mata iska a cikin ta. Koda yazo ya samu ana mata kitso, domin yana fita Shamsiyah tana zuwa gidan. Dake ta iya kitso, ta kama kan tana kitsewa gwanin ban sha'awa. Inna laminde ta zauna tana saka mata lalle, kallon su yayi yaji kamar an cirr mishi duk wani abin da yake kanshi. Su gama wahalar su tana tafiya ta tafi kenan. A gidan Mai gari, kwankwasa kofar dakin shi aka yi. "Yes" "Yallabai Baba yana son ganin ka" "tow" dama zaune yake daga shi sai single da dogon wando. Daukar wani jan shirt din sa da yake gefen shi ya saka, sannan ya rufe laptop din, ya fito yana saka takalmin shi. "Haka rana yayi?" Ya tambayi Nazifi, "eh gashi nan da alamu za ayi zafi sosai " "Allah ya kawo mana sauƙin zafin" "Amin Ya Allah." Nazifi ya fada, zauren suka nufa inda me gari yake zaune yana shan iska. "Barka da Hutawa Baba " "Barka dai Yallabai." Zama yayi yana kallon yadda aka cika gaban Baba me gari da abin tab'awa. "Kayi hakuri Ni nace a kira ka, ka abin tab'awa nan bana son kana zama a dakin nan" murmushi yayi ya zauna yana kallon kayan abincin. "Gashi na koshi Baba " "a'a sai a kai maka d'akin ka" girgiza kai yayi yana faɗin."a'a xan ci ma" ya fada yana dauke kan shi."ya kuka yi da yarinyar nan ne?" Gyara zama yayi sannan ya ce mishi. "Dama ai na gaya maka tun fara aikina, makarantar bashi ya dace da ita ba, akwai makaranta nasu na musamman handicapped iya sune suke rayuwa a wurin, sannan gefe guda domin a kara musu kwarin gwiwa akwai tsirarun dalibai da suke magana da ji, domin su fahimci ba iya su ne kawai ke karatu a wurin ba." "Madalla Allah ya bika." Murmushi yayi yana kallon hannun shi. "Amin Ya Allah." Ya furta, "a sokoton kenan?" "Eh anan cikin sokoton, A.A. RAJI SPECIAL SCHOOL SOKOTO." Mai gari ya jinjina kansa. "Idan za a kaita zan je nima na ga inda take " "babu damuwa Baba, amma ina rokon arzikn don Allah kar ku bari Malam Aminu ya sani tana karatu ne, nafi son ta zame mishi bazata." Ya fada yana kallon Baba mai gari, daga yanayin maganar ya fahimci abin da yake nufi don haka ya jinjina kai yana faɗin. "In sha Allah, zamu yi kokarin haka." Sun jima suna tattaunawa akan haka. Kafin aka kira sallah azhar suka tafi masallaci. A masallacin ma Malam Aminu wasan boya suke da Abu turab, domin baki daya sai yaji tsoron kar Abu turab ya kunyata shi a cikin jama'a. Shima Abu turab ya fahimci haka, sai yaki yarda su hadu da Malam Aminu din tunda yana gudun shi ne. Shi kansa Malam girmama abin yake amma bai wani damu ainun ba, domin gani yake kamar ai ya rabu da karfa ne domin idan ba haka na, zai ta damun shi. A can kuwa Inna Laminde har da lalle aka yiwa Auta. Kome nata gwanin ban sha'awa. An daka mata yaji da soyayyar jar miya aka zuba a gwangwani, ga yajin karago da yajin daddawa, dai jar yaji. Sai garin kwaki da gyada da dakakken kanzo. Da maggi leda guda. Inna Laminde da sakalta autar ta, har da yanka mata zabi guda biyu da wani matashin agwagwa, aka hada mata a kan jar miyarta, manja a karamin gora da mangyada. sai gishiri da sabulun wanki man shafawa, man kitso da man kad'anya. Kayan dai gasu nan. aka saka a cikin Ghana most go, daidai kunnen da take ji Inna Laminde ta tsaya tare da rike mata shi. Tunda ta ga haka ta fahimci fada ne, rau-rau tai da idanunta tana kallon kasa.. "ina gaya miki babu ruwan ki da kowa karatu ya kai ki ba shiga hurumin da ba naki ba, sannan haramun ne sata da wani aikin Asha idan baki da abu za a baki lambar Yayanku ki saka a kira shi kin ji" gyada kai tayi hawaye na zuba mata, ta tsani fada a rayuwarta, shi yasa take kiyayye abin da za a mata fada, musamman ita da Baffan su ya tsane ta. Haka suka yi suna faman shirya kayanta. Har da busashen ramma, da yamma ta mata wanka domin Ibrahim zaizo da wuri tafiya da ita Sokoto har da Inna. Bayan isha Malam da yake rike da radion kamfanin Kachbo, ya kalli Laminde ya ce. "Kowa yaci zomo, ya ci gudu ban ga amfanin hana kai sararawa ba wallahi" juyawa tayi duk da babu wadataccen haske sai na fitilar kwai ta juya ta zabga mishi harara. "Malam kenan, ai kowa yaga balbela da farinta ya ganta, kana tunanin zan iya baza hakarkarina a shimfida ban kula da amanar da Allah ya bani ba ne? Ko ka yarda ko kar ka yarda ba a sauyawa tuwo suna." "Wa ni? Tow wallahi na kusan yarda mangoro na huta da kuda, hmm baki san dawar garin ba ne." Ya fada yana kara karar radion. Bata kula shi ba, ta ci gaba da aikinta, da ta gama ta wuce dakin ta. Wa shi gari tana sallah asuba ta tashi da kimtsa ɗakinta, suka karya wurin karfe goma sai ga Ibrahim da mota.a gurguje suka fitar da kayan suka wuce, domin rana ta fara yi. Koda suka fito sai da suka tsaya a gidan mai gari, suka wuce. Wurin karfe biyu zuka isa Sokoto. Gidan Zakaria suka nufa, matar shi yar me kirki ta karɓe su, ta fara hidima da su. Dake Sa'ade tana zuwa Inna ce dai bata cika zuwa ba. Abinci suka sannan suka huta. Matar Zakaria me suna Ummi ta shigo suka gaisa. Inna laminde ta ce mata. "Ummi ga dawainiya nan na kawo miki, kin san halin Baban naku. Don Allah ga Autana shi yasa nazo da kaina na roki Alfarmar ta zauna dake, ba don tana kanwar shi ba, a'a ki dauketa a matsayin kanwar ki, kafin Allah ya kawo miki naki. Idan Allah yaso zan na zuwa duba ku. Idan na samu lokaci" "Allah sarki Inna in sha Allah babu abin da zai faru. Na gode sosai domin tuntuni nake son a bani Sa'ade kika yau gata Allah ya kawo min ita, Alhamdulillahi." Auren su kusan shakara bakwai amma har yau Allah bai azurta su da haihuwa ba. Haka suka wuni a gidan itama Ummi ta kara mata da su kayan zaki a biscuit da chocolate, washi gari ya kama Monday. Bayan sun karya Inna ta ce mishi. "Ina son raka ta, amma ina jin kar ta min kuka ne" "Kai innah Sa'ade shekaran ta tara saura watani ta cika goma, idan an kaita aji biyar zasu bata, domin ta kara kwarewa a karatun su, muje ba zata yi kome ba, amma zan fara zuwa aiki idan mai gari ya iso zan zo na dauke ku" "tow Allah ya muku albarka baki dayan ku, a dawo lafiya" ta fada. "Amin Ya Allah" ya ce. yana fita da sauri. Sa'ade tana wurin Ummi suna wanke wanke, kallon su Inna tayi daga dakin da suka sauka, a ranta ta ce. 'Alhamdulillahi ko mutuwa nayi Sa'adatu ba zata yi maraici ba.' kwanciya tayi barci ya ɗan yi gaba da ita. Abuturab da Mai gari wurin karfe daya suka iso Sokoto, in da suna tsaya a kofar makarantar. A.A. RAJI SPECIAL SCHOOL SOKOTO, yana parking ya kira Zakaria. "Assalamu alaikum, mun iso ga mu a bakin makarantar." "In sha Allah mu ma, gamu nan zuwa." Zakaria ya fada. Sun kai minti Talatin a wurin kafin Zakaria da su Sa'ade da Yusuf da Inna, tare da Ummi suka iso makarantar. Buɗe musu kofar shiga makarantar aka yi musamman motar Abuturab da yake da plat Number na gidan Sarkin Musulmai. Gashi lokacin an tashi kenan daga makarantar dalibai ta ko ina, sai bin motar ake da kallo. Har suka isa bakin office din Shugaban makarantar, daga yadda Abuturab yake tafiya zaka fahimci yana da masaniya da wurin. "Prince kun iso ne?" Yarima Sadeeq ya iso da dan sassarfa yana mika mishi hannu, buge hannun yayi yana hararan sa. "baka ga baki bane" mikawa Baba mai gari hannu yayi suka gaida. "Mai garin Maikulki na karamar hukumar Binji." "Ni kuma Abubakar Shehu Abubakar. " "Yallabai Barka " Mai gari ya fada cikin girmamawa. "Zakaria Aminu Fulani " "Yarima Sadeeq." Shima Sadeeq ya fada, "amma kamar kana program a Radio station ko?" "Eh" "Yusuf Aminu Fulani, ga Innar mu, wancar kuma matar Brother ce, Mrs Zakaria Fulani, ga Sa'adatu Aminu Fulani." "Great family nice to meet you." Sannan ya juya ga Abuturab da ya koma gefe yana waya, ba zaka.iya tantance abin da yake fada ba. Amma yadda Sa'ade ta sake baki tana kallon shi zai baka dariya. Domin abin da yake ko ita da take auta ba tayi.
African Queen products
Sabulun matsi
Garin matsi
Humra
Turaren wuta
Maganin Infection
Ga number wayata...08130269641
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan.

+234 8130269641
+234 813 731 1900
+234 906 346 7258
+227 84 50 64 76
Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar
Top-notch season 2 2023.
Kamar a ce ya d'ago kan sa suka yi ido hudu da ita, da sauri ta sunkuyar da kanta, duk da ba wani lokaci suka dauka ba, sai dai ta fahimci shi babu ruwan shi, kuma be damu da rashin maganar ta ba, asalima shi ne mutum na farko da ya gwada mata zata iya karban duk abin da ya zo mata, d'age mata gira yayi ta kuma sunkuyar da kanta. Kashe wayar yayi ya ce. "Muje ko" "tow" principal da mataimakin sa ne suka fito daga office din su, suka tare su. Cikin girmamawa tare da mutuntawa. "Sannun ku da zuwa" "yawwa" suka bashi amsa ban da Abuturab da yayi shiru yana sauraron su. Shi da mai gari suka zauna, Inna Laminde da su Zakaria da Sadeeq suna tsaye. "Barkan ku da zuwa" principal ya kuma fada yana kallon Sa'ade. "Ita ce dalibar mu?" "Eh Malam ga Sa'adatu nan mun kawo maka ita. " Inji me gari, "toh madalla, kallon Abuturab yayi sannan ya ce mishi. "Yallabai me kake bukata a yi ?" "Special class ina son ta samu ilimi me kyau" "in sha Allah " sannan suka shiga tattaunawa daga akan matsalarta. "Vice kira min Malam Ayuba." "Shi kenan " da sauri ya fita domin an riga da an tashi, masinjan su ya gani ya gaya mishi ya kira mishi Malam Ayuba, can kuwa sai gasu tare. Office din principal suka nufa, suna shiga principal ya d'ago hannu zai mishi magana Abuturab ya rigashi, inda ya mika tafin hannun shi, ya saka dayan alamar "ina wuni?" Cikin farin ciki Malam Ayuba ya amsa mishi yana faɗin. "Lafiya lau." Nan hira ya barke tsakanin su, murmushi principal yayi yana faɗin."Shi kenan sai ka mishi bayani shine for master jss 1, ajin shi zata zauna" sake kallon shi yayi ya janyo Sa'ade ya nuna mishi ita. "Yar uwata ce kuma naji ance kai ne malamin su?" "Eh yallabai ni ne malamin su." Ya fada, "tow gata nan na kawo maka ita, don Allah ka kula da ita mun gama kome tun wancan lokacin" "shi kenan ba kome zan yi yadda kace ai nima yar uwata ce tunda laluran mu daya bamu kyamar dangi." "Na gode sosai da kulawar da ka bani." "Nima na gode, zamu iya zama abokai?" Murmushi Abuturab yayi ya mika mishi hannu, daga nan ya ja su, zuwa staff office aka kawo register na yan Form one, aka saka sunanta. Shi da kansa ya nimo wasu senior kurame, ya damka musu Sa'ade a hannunsu, anan fa Sa'ade tace bata san zancen ba, domin dai ba zata bisu ba Inna Laminde zata bi. Dakyar aka lallabata domin basu so ta saka a ranta cewa ba a sonta, mota Abuturab ya bude ya dauko wani karamin kwali ya mikawa daya senior din ya durkusa yana kallon Sa'ade ya saka hannu a wuyar shi alamar na rantse. "Zan kawo miki innar ki da su Yayaun ki." Ƙaramin yatsanta ta mika mishi alamar
" Alkawari zaka kulla" "na kulla " ya mika mata yatsar shi, suka kulla alkawarin zai dawo. Daga haka suka bar makarantar, lokacin da aka kai Ummu Mansurah special school haka suka yi, domin a lokacin gani suke kamar ba a kawo musu visiting ba. Tana waiwaye tana kallon su har suka b'ace. "Malam Abuturab mun gode Allah ya saka da alkhairi mun gode sosai. Allah ya raba ka da sharrin abokan halitta." "Amin Ya Allah " kallon shi Inna Laminde tayi ta ce mishi. "Ubangiji ya tsare ka daga duk abin ki, Ubangiji ya sakawa da iyayen ka da alkhairi, Allah ya daura ka saman makiyan ka, mun gode mun gode da ka mai da Sa'ade mutum, domin har na fara hango iyakarta daga makarantar Maikulki shi kenan " murmushi yayi sannan ya ce. "Muje a mai daka gida Baba Mai gari zan leka cikin gida ne" "mun gode sosai." "Maman Sa'ade mu tafi tare mana " "Tow ranka ya dade, nima ina son bin ku kuwa" inji Yusuf domin ya kwana biyu bai shiga Maikulki ba. Haka suka nufi inda motar da zai kai su gida yake ajiye anan suka kara godiya sosai, sannan motar kiran hilux ya ja su. ____Sa'ade bata tab'a tsammanin akwai irin wannan yanayin da rayuwar ba, sai da aka shigo mata da katifarta da zanin gado, seniors din nan suka shimfida mata, ta zauna tana cire takalmi, sai kallon kwana da kwana take, lumshe large eyes dinta tayi, kallon wasu yara biyu yan mata a gefen gadonta. Daya a cikin su tana cikin kwadon garin kwaki, mika mata tayi ta girgiza kai. Kallon Seniors din na saman gadon Sa'aden tayi, ta tab'a tana tambayar ta, "ya sunanta?" Kallon Id din Sa'aden tayi ta mika musu. Mikawa na saman tayi tana mata alama da hannu. "Dama muna niman wata kawa saura ta hudu ko?" Gyada kai tayi, suna zaune senior suka shirya mata kayanta, da zasu tafi dayan ta riko hannunta ta haɗa da na yan matan tace musu. "ga kawa na kawo muku, ban da fada ban da rigima idan kun samu matsala da wasu ku zo ku gaya mana. " Ta musu alama. Gyada kai suka yi, duk da bata cika gane maganar su ba, tunda ba wai ta taso da masu ba ne, me mata kenan Malam Bature. A kwai wani dabi'a da kurame ke da shi, kaf duniya babu wanda ya kai su, kaunar nasu. Sannan suna matukar girmama me yanayin su, wato me laluran su. Haka yasa dakin baki daya da suka fahimci Sa'ade itama Kurma ce, zo kaji yadda aka sakata a gaba da nuna kauna da kulawa. Basu daina Yaren su,sai da metro din su Baba Kande ta shigo, suna ido biyu da ita kowa ya kama gaban shi. Kallon su tayi tare da musu dakuwa, da sauri suka haye gado, domin an jima zasu sallah da amsar abinci. Dole su kwanta su huta. Kafin lokacin yayi
"Well-done my Man ka kyauta." "Ina son zuwa kwara amma dole sai an samu hutu tunda sun kusan fara jarabawa nan da sati tara" ya fada in low voice, kasancewar garin akwai hadari ga wani iska me dadi da sanyin, kana ga kamshin damina, kallon Sadeeq yayi yana faɗin. " Weather yau yayi dad'i " "Ba laifi muje" haka suka shiga motar Abuturab din, suka shiga tafiya yana jin wani irin dad'i da nutsuwa a ran sa. Koda suka isa kan wuri sun samu tarba me kyau, sannan ya ci abinci ya wuce dakin su ya kwanta, kiran sallah azhar yasa shi mikewa yayi alola ya nufi masallaci basu dawo ba sai la'asar, yana dawowa ya fara aikin shi. Har magriba koda suka tafi masallaci basu dawo ba sai isha abincin kawai ya ci, ya kwanta bai kuma bin ta kan Yarima Sadeeq ba, sai barci. Wuraren asuba ya farka sakamakon wani irin mafarki wai yayi da Mansurah cikin jini. Da wani irin mutuwar jiki ya tashi dakyar ya shiga ban daki, yayi wanka da alola ya dauko wani jallabiya fari ya saka, sannan ya fesa turare, ya nufi masallacin yana me saka counter a hannun shi, ana idar da sallah ya dawo cikin gidan ya shirya ya nufi wurin motsa jiki. Duk da ya gaji amma ya rasa me yasa ake boye mishi inda Ummu Mansurah take, haka ya dawo gida, idanun shi ya sauka akan matasan kwanaki duk da dayan zai iya girme mishi, da alamu wa da kani ne. Tab'e baki yayi ya wuce abin shi, akan lokaci ya wuce cikin gidan ya shirya ko karyawan bai yi ba, ya nufi inda motar shi yake ya koma inda yake bautar kasar shi..
Kwana ɗaya babu Sa'ade, Inna Laminde sai da taji wani irin kewar Yarta, kwana tayi tana jin wani irin d'aci lokacin da Mai gari take bata labarin ai sayar da Laminde Malam Aminu yayi tayi kuka ainun domin bata kawo kiyayyar ta kai har haka ba. Ta zata kawai yana kinta ne domin bata ji bata magana, ashe kin jininta yake tunda tazo a kaddran. Bata tab'a sanin cewa zai iya sayar da yar shi kamar Saniya ba, asalima Saniya tafi ta daraja sai yau da take jin labarin abin da ya aikata ashe dabba tafi dan mutum daraja? Hawaye ta share domin an kai limit din da zata iya zama da malam Aminu ba, halin shi ya gundire ta, zata bar mishi rayuwar shi yaci kansa da wadanda yake so. Haka ta kwana cikin bakin ciki da b'acin rai. Washi gari kuwa. Ta tashi abin ta tana kallon sa yadda yake ta kiciniya da saniyar sa. "Malam baka ji kunya sayar da dan mutum madadin saniya ba?" A firgice ya juya yana kallon ta, a ina taji wannan mummunan labarin? Waye ya tona mishi asirin shi a gaban iyalin shi. "Allah yana ganinka! Kuma yana ji yana gani sai ya muku hisabi da Yarka, duk cikin yaran nan ita ce daya ta tashi bata san soyayyar Uba ba, domin ƙaddara ta same ta, malam ka gaya min yaushe zaka mutu? Ka san ranar mutuwar ka ne? Yarinya na babu ruwan ta ka sayar min da ita meye laifinta? Nace meye laifinta. Allah sarki yarinya karama da bata ji ba bata gani ba. Ta fuskanci jarabawar rayuwa ka je mun barka da sallah." Ta fada cikin matsanancin kuka. Domin ya kaita bango, "na gaji da halin ka na gaji da fitinarka zan tafi na bar maka gidan ka sai kaci kanka da kanka." Ta koma daki tana kuka domin iskancin Malam ya shure tuninta.
*^^^ A hankali take shirya tana kallon yan matan nan. Ganin yadda suke shiri. Kallon abinciin da suka amso jiya suka yi na ta bata ci ba. Domin munin tuwon yasa bata iya ci ba, domin wannan ba irin girkin Innar su ba ce ko Inna Larai girkinta duniya ce. Tuwon datsa ne, sannan miyar kana ci kana jin dunkulen kuka. Bude kwalin gaban lock ɗinta suka yi, tana kallon su bata ce kome ba. A hankali suka ciro golden more da madaran gwangwani, Sugar kwali, suka mike tare da dibo ruwa suka hada mata. Sannan suka mai da kwalin suka rufe, wacce ta haɗa mata ta lock din ta shiga cusa kayan cikin kwalin tass suka fitar da wanda basu da wasu anfani a cikin lock din. Suka shirya tsaf. Sannan suna rufe mata kayan tare da bata key. Murmushi suka yi, daya babban ta mika mata ID dinta. Rahilah Adam Gwarzo, ta nuna kanta tare da juya hannunta. Ma'ana sunanta. Ita kuma daya ta nuna mata Husnah Jafar Kurmi, sai itama Sa'adatu Aminu Fulani, haka suka jira ta ta gama sha ta ma koshi, kallon su tayi domin ta iya magana da idanu tare da gira, har Gara giran Abuturab ne ya koya mata, a yar zaman su. Idanu kuwa dama daga ita sai Innarta suke maganar da idanu. Kamar da wasa sai ta ga sun amsa mata suma. Mika musu kofin tayi, tare da mata alamar a "kusha" girgiza kai suka yi Rahilah Adam Gwarzo ta nuna mata. "Yanzu na sha kwaki da madara sai dai ko Husnah Jafar Kurmi" girgiza kai tayi tana mata alamar. "Na koshi muje nasan yau koko ne ki dauki suga gyada." Haka ta dauka suka dauki kofin suka rufe mata tare da sakawa a locker suka bar hostle. Dinning suka nufa, sai da suka wanke kwanon su sannan suka shiga sai da suka bi layi, sannan aka zuba musu kunu da kosai ne. Suka samu wuri suka zauna suna sha. Duk da a takure suke sai take jin dadin haduwar ta da Rahila da Husnah. Can gefe makafi ne suna amsar nasu, ta bangaren kurame babu hayaniya sun gama karban abincin su, amma bangaren makafi Wayyo Allah. Hayaniya har turereniya. Karshe sai da masu saka abincin suka tsawata musu. Haka suka kammala cikin abincin suke bar hall din, suka nufi dakin su, tare da ɗaukar jakunnan su. A hanya gudu suke har suka isa Aji, suka isa bakin kofar suka fashe da dariya, daga nesa Sadeeq yake hangonta. "Yarinyar ta sake ta samu wasu yara biyu kuma ina ga yanayin su daya." Ya fada s wayar da yake da Abuturab. "Haka zai taimaka mata wurin karatu, matukar ka samu wanda halin ku yazo daya zaka yi karatu sosai."
African Queen products
Sabulun matsi
Garin matsi
Humra
Turaren wuta
Maganin Infection
Ga number wayata...08130269641
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: "Ya batun sayanta da kayi?" Sadeeq ya tambaye shi, shiru yayi domin ya manta batun ma wallahi, kawai ya fadawa Sadeeq din ne domin ya taya shi jajjantawa. "Shhhhhh, ka manta da batun abin da ya faru na sayanta da nayi, sauran zan duba al'amarin, sannan don Allah ya zama sirri a tsakanin mu " dariya Sadeeq yayi sannan ya ce mishi. "Ko kana kiwontawa kanka ne?" "Meye? Me kace?":"A'a bance kome ba, zan taya ka saka idanu akan ta, kuma zan hana wani saurayi ya ce yana sonta nasan nan da shekara biyar ta zama Yan mata" "Mtseeeeeew baka san ina da yarinyar da aka mana baiko ba ne? Don haka ka bar wahalar da kanka" "Baiko ba aure bane za a iya maku baiko idan Allah bai nufa akwai auren ba sai ta mutu ka fahimta " "Allah ya shirya ka" haka suka yi ta wayar su har Sadeeq ya kashe wayar. A can class kuwa gaban class Rahilah ta jata suka zauna a sit din gaba suka zauna suna dariya. Minti goma da shigowar su ajin Malam Ayuba ya shigo suka mike tare da Gaishe shi, sannan suka koma mazaunin su, fitar da kundin ajiyar sunayen su yayi, ya fara kiran sunan su.
***
Abdulhakim.
A yan kwanakin da Mahaifiyar sa, attajira Hajiya Daulah wani irin rikici take ji domin ta kara mishi masu kula da lafiyar shi, wato escort. Duk inda zai shiga suna biye da shi kamar bindi. Wani abin damuwar shi ne yadda ta saka shi a gaba da maganar aure, tun yana kaucewa har ya koma zata saka shi a gaban Kannen shi tayi ta fada da masifa. Idan ka gan shi yana da matukar sanyi da hakuri, duk fadar da take bai ce mata cika kanki ba har ta gama. "Duk abin da nake maka ina yi ne domin ina kaunar ka babu uwar da zata so danta ya kai kusan shekaru arba'in babu mace." "Hajiya amma ai kin san matsalar sa. Zai ajiye mace ne babu biyan bukata? A ajiye ma zancen ya ajiye mace zuciyar shi bata bukatar wahala. Idan har lokacin auren yayi zai yi ba, shi aure lokaci ne don Allah ki daina damun sa da zancen aure domin zai yi babu wanda ya isa ketare kaddaran sa." Dr Sharif ya fada yana shigowa falon wani irin ajiyar zuciya Abdul ya sauke a sirrance yana kara damke hannun shi da juna, domin ya tsira tunda mahaifin su ya zo akan lokaci, a fusace ta juya tana kallon shi. "Kace nayi hakuri na zuba mishi idanu? Wani irin ciwo ne haka da za a ce mutum ba zai yi aure ba " "zuciyar shi ba zata iya daukar nauyin bukatar shi na D'a namiji ba, idan kuma kina ganin auren shi ne mafita sai ki yi mishi ai tunda baki da lissafi." Ya fada yana zama a daya daga cikin kujerun falon. "Kamar ya bani da lissafi? Bayan duk abin da nake a lissafe yake " "Taufiq bani ruwa na sha, domin ita bata san yadda ake tarban miji ba" ya faɗa yana kallon ta. "Alhaji kar kace zaka biyo ni gida na kaci min mutunci." Cire hular kansa yayi ya amshi ruwan da Taufiq yake bashi. "Ko daya sai dai akan Abdul ne zamu iya samun matsala sosai. Wajibi ne ya miki biyayya na wacce ta haife shi, kare rayuwar shi kamar dole ne a kaina, domin ba zai yiwu ki kashe min shi ba." Zama tayi tana faɗin."Amma ai ba wani abu ba ne tunda auren nan kare mutuncin sa zai yi ba kuma." "Kin ga tsakaninki da Allah kin tab'a jin ko ganin yana kula yan mata?" Girgiza kai tayi, shi kuma yayi murmushi. "Ba da lafiya, idan har ya ce zai kula mace taya zai kula da ita bayan shi kansa bukatar kulawar mace yake nima? Ba wai ina bayan sa bane a'a kawai ina so ki gane idan macen da yake bukata ne zai zauna da ita, musamman idan shi yace yana sonta. Su yaran da kike hangowa idanun su a bude take idan kika haɗa su da Abdul wallahi kece zaki dawo kina zaman jinya, zuciyar shi ba zata dauka ba, ki kira likita ya miki bayanin condition din sa." Gyada kai tayi tana faɗin."Hmm! Wato yadda aka tsara ka haka zaka zo ka saka min magana a bakina Yarona daya tal da yake kula alamarina shi zaka ce na" "Hajiya ba haka bane amma gaki ga shi duk abin da kika yi me kyau ne " ya mike tare da wucewa upstairs. Tashi tayi ta bishi itama don haka ba karamin kai ruwa rana suka y ba, domin gani take kamar karya ne taya za ace kar yayi aure fada me sunan fada suka yi wai don ma shi yaki kula ta. Domin irin mutanen nan ne da basu son abin kunya a cikin iyalin su. Da taga yaƙi kulata kawai ta shiga fashe fashe kamar mahaukaciya, tana ihu da magana marasa dadi da kyau, wucewa daki Abdul yayi ya zauna tare da rike kansa. Maganar likita yana dawo mishi mishi tiryan-tiryan. "Idan nace zaka yi aure a madadin a samu zaman lafiya sai a samu matsala domin babu macen da zata zauna da kai babu sauke hakkin aure. Ita kanta zuciyar da zata yi wannan aikin babu lafiya da karfin da zata yi,kaso cassa'in na jin dadin rayuwa aure yana tare da sarrafawar zuciya ce, idan har baka samu macen da ta fahimce ka ba, zaka sha wahala sosai. Domin karfen da aka saka maia ba zata yi aiki yadda ya dace ba. Ka gane abu daya bugun zuciyar ka zata iya wuce iyaka matukar ka nace sai kayi tarayya da ya mace. Shi yasa muke kokarin ganin ka iya sarrafa na'uran cikin zuciyar koda kuwa sha'awa ce ta mafarki ta sarrafa ta. Amma abin ya ci tura" girgiza kai yayi yana faɗin. "Dr bana iya kallon mace ne, anya zan iya samun damar aure kuwa? Dr!". Murmushi likitan yayi yana faɗin. "Zaka iya aure har ka haihu, sai dai ba abu me sauki ba ne yin auren da haihuwar kafin ka samu macen da zata iya rayuwa da kai shi ne matsalar, amma ba wai ba zaka samu ba ne, zaka samu fa ka cigaba da shan magani xaka samu macen da zata zauna da kai." Bude fuskar shi da ya rufe da tafin hannun sa yayi yana jin wani irin damuwa da kunci a ran sa.
***
Maikulki.
Duk da cewa ya tsani ganinta amma yau kwana biyu kenan bai sakata a cikin idanun shi ba, ko ba kome itama Yarsa ce. Duk da yadda yake azabtar da ita bai tab'a kawowa zai ji a cikin kwana biyu rak yana bukatar ganin Yar da ya ke da yakinin bata da wani amfani a cikin gidan sa facce zama cikin gida domin kar ta janyo mishi na kasu a jikimar sam, zuba tagumi yayi yana kallon yar tinkiyarta. Ko ba kome yayi kewar mace ta. Tashi yayi zubur ya shure kofin silver da aka saka mishi koko me suna mai gida jaki. Ya nufi wane fuuuu. Kallon shi Inna Larai tayi tana faɗin."Allah ya kyauta. "Kai dai Malam baka da hali" ta fada tana dauke kofin kunun. Tafiya yake kamar zai tashi sama, duk inda ya wuce sai an bishi da idanu, kofar gidan Mai gari ya nufa, daidai Abuturab ya fito daga cikin gidan kenan. "Malam Bature sallama" ya fada yana ja da baya, domin yadda suka yi ido biyu da Abuturab ya ɗan bashi tsoro. Kuma dake yasan yayi rashin gaskiya take Abuturab ya cika mishi Idanu "Baba kai ne?" "Eh Ni ne" Malam Aminu ya fada yana ja da baya kaɗan. "Toh ja da bayan na meye? Baba sake kayi magana mana" "Dama nazo ne akan na tambaye ka ina kasa suka kai Bimbi?" Juya kai yayi sannan ya kalle shi na wani lokaci kafin ya ce mishi." Kana bukatar ta ne yanzu?" Abuturab yayi magana cikin nutsuwa da kamewa kamar ba sangartaccen nan ba. Hàdiye yawu yayi makwat yana kallon shi. "Dama.... Dama..." Ya kama in-ina, "matso na gaya maka yadda nayi da ita " matsowa Malam Aminu yayi yana zare idanu. "Ka sake wani ya san sirrin mu yanke maka kai zan yi, domin ba zan iya jure zaman gidan yari ba, tunda kai ne ka sayar min da ita ba saka ka nayi dole ba, don haka ka sha min lafiya." "Wa'iyazubillahi." malam Aminu ya fada a tsorace, "kasan hukuncin wanda ya sayar da mutum kuwa? Tow wallahi karka bata min sana'a kai ma ka kula domin zan saka a sace min kai don haka ka saka zare da allura ka dinke bakin ka" rufe bakin sa yayi jikin sa yana rawa. "Anya zan yarda da kai kuwa?" "Na rantse da Allah ba zan maka kome ba" "anya maganar ta kai zuci kuwa?" " Gasken gaske babu abin da zan maka" shiru Abuturab yayi kamar me nazari kafin ya ce. "Tow zan yarda da kai amma bisa sharadi kullum zan zo gidanka da maraici domin kar ina zaune ka kawo min jami'an tsaro ban sani ba." Tsuru-tsuru malam yayi kamar zai fasa ihu ya ce. "Ina cewa ba gayawa iyalina zaka yi ba abin da ya faru? Sannan a ina Uwar Sa'a taji labarin na sayar da ita?" Wani kintaccen kallo Abuturab ya mishi tare da cewa. "ka tab'a gani na a gidanka?" "A'a billahi lazi ban tab'a ganin ko inuwar ka ba " "toh tunda baka tab'a gani na ba, shi ne zaka min sharri Baba bani kudina na fasa sayan ta, tunda ban maka abin Arziki ba. Bani zan saka su dawo maka da kurman Yarka, kasan kuwa har mijin aure zata rasa idan al'umma suka ji labarin sayar ita kayi, ita kanta tsanar ka zata yi don Allah bani kudina na fasa sayar maka, domin idan yan sanda suka zo kama ka, kar su kama ni ai ban san haka kake ba." Wani irin rawa jikin Malam Aminu ya dauka kamar zai sake fitsari a wando, domin har ga Allah bai kaunar ya kara komawa wurin yan sanda ba, ya san mugun dukan da suka mishi. "Don Allah ka rufa min asiri." "Ai Baba baka san wani ba, hukuncin mutumin da ya sayar da mutum yanke mishi hukuncin kisa ake, don haka maza ka dawo min da kudina domin ba yarda zan yi ba" "Ayya d'an nan kayi hakuri na tuba k yafe min" shiru yayi yana kallon Malam Aminu kafin ya kalli agogon hannun shi, ya ce. "zan tafi makaranta domin ja janyo min na makara. Dole na shiga mota kenan, muna ma magana ne ko? Tow wallahi naji labarin wani abu ya faru tabbas sannan kasan ana tuhumar ka da laifin safara kwanaki ko? . Zan sayar da kai ina ganin kai kan kafarka zasu saya domin." Bai rufe baki ba ya hango malam Aminu can ya arta a guje, sai lokacin ya sake murmushi domin ya fahimci tunda malam Aminu yaci duka Allah ya daura mishi tsoron yan sanda, balle kuma al'amarin ya kuma lalacewa da zancen sayar da yar shi. Nufar makaranta yayi, sai murmushi yake lokaci zuwa lokaci har aka tashi. Al'amarin Malam Aminu kuwa, tsoro da fargaba suka mishi diran mikiya, take wani mugun zazzaɓin tsoro ya kama shi, kafin kace kwabo cikin ya murde sai gudawa, dakyar ya ke kai kan sa ban daki domin ya gama firgita sosai. Wurin karfe daya sai ga Abuturab, ya kuwa buga sallama. Zuru-zuru malam Aminu yayi jikin shi yana kerma ya juya yana kallon kofar dakin zauren shigowa gidan sa. "Barka da Baba? Babu kowa ne a cikin gidan?" Ya fada yana murmusa mishi. "Kululu" ya rintsa idanun shi." Kafin ya mike dakyar ya nufi kofar ban dakin yana shashekar kuka. Domin har ga Allah abin ya burge shi yana son Malam Aminu ya girbi abin da yayi ne. Kuma da alamu kwalliya zata biya kudin sabulu......
ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza
Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan.

+234 8130269641
+234 813 731 1900
+234 906 346 7258
+227 84 50 64 76
Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar
Top-notch season 2 2023.
African Queen products
Sabulun matsi
Garin matsi
Humra
Turaren wuta
Maganin Infection
Ga number wayata...08130269641
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: "Wa'alaikumunsalam Barka da zuwa, lale lale." Inna Laminde ta shimfida mishi taburma a tsakar gidan tana faɗin. "Ashe zaka shigo?" "Eh Inna ga ni, ya mutanen gidan mai gari¿" "Suna lafiya." Wucewa tayi ta kawo mishi ruwa daga randan kasa, yayi sanyi sosai ya ce. "Sannu Inna har da wahala" "ba wahala ba ne yiwa kai ne" ya fada idanun shi yana kan kofar ban daki. Ko ba kome ya samu wani weakpoint ko ya ce jackpot na Malam Aminu, a ban dakin kuwa ji yayi ina ma da tare da uwar hanjin shi ran shi zai fita ya huta da kallon da Yaron an yake mishi, asalima kin fitowa yayi, ya zauna abin shi yana jin hiran tare da jiran tsammanin yaushe Abuturab zai tafi ya fito. "Malam lafiya kuwa? Har yanzu bai fito ba." A ran Abuturab ya ce. 'Ina zai fito tunda yasan abin da ya shirya' a kan fuskar shi kuwa murmushi yayi yana faɗin." Ba mamaki uzurinsa bai kare ba ne"
Sai da Malam ya shafe minti arba'in a cikin ban dakin kafin ya fito yana rike cikin sa. "Sannu malam" "yawwa Larai" ya fada cikin wata irin murya kamar me shirin fashewa da kuka domin dai ya rasa yadda zai da abu turab. Haka suka gaisa sama sama. Idan ya kalli fuskar Abuturab wani irin kwarjinin tsiya yake masa don dole ya kwanta kamar mara lafiyar gaske. Haka Abuturab ya karaci hiran shi yayiwa su Inna sallama. Bayan ya musu alkhairi dakyar ta amsa, domin ba zata iya wannan abin kunyar ba.
***
Kwara
Zaune suke surukanta musamman Hajiya Mariya da take kamar zata shige cikin Sultanate. "Sultanate maganar Fadwa akan Yaron nan nake son ki tuntubi Sultan akan su, manemanta sun matsa lamba" shiru tayi na wani lokaci kafin ta ce mata."amma kin san dai ba zaki daurawa dana dawainiyar auren kanwarki ba?" Ta fada in serious tone. D'ago idanun Hajiya Mariya tayi kafin ta kalli yadda kishiyoyinta biyu suke murmushi suna rufe bakin su. "Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana. "In sha Allah zan dauke kome?" D'ago kai Sultanate tayi tana kallon Hajiya Mariya. "Na ga baki aikin fari balle baki a ina kike samun ki? Ko kin fara dauke-dauke kika fara a turakar Abdurrhman?" Maganar ta daki Hajiya Mariya. Shanyewa tayi cikin basarwa ta ce . "Subhanalillahi sai kace ban gaji arzikn ba Sultanate? Ai kome lalacewar gawar giwa tafin kiyashi ya jata." Kur Sultanate ta mata domin bata ka kawo data mata irin wannan reply din ba, ta zata shiru zata yi tunda Gulma ce ke kawo su kullum, sai yau taji saba'nin haka. Ita Sultanate duk abin da za a ce danta yayi yayi ko da kuwa hakkin da ya dace ya sauke ne sai ranta ya b'aci balle kuma abin da ya shafi iyalin shi ne kuwa. Shi yasa ta tsani Badi'atul Noor domin babu dalilin da zai saka ta tambaye ta abin da take bukata sai dai shi tsakanin d'a da uwa ya gaya mata gaskiya abun da yayi, haka yasa take mugun tsanar Badiatul Noor da yaran ta, domin ta ce kome ya samu a jikin Badiatul Noor yake kare baya tuna bayan shi. Jim tayi tana kallon Hajiya Mariyah da ta gama cika ta batse."tow Allah ya kyau lokacin, amma ke kuwa guda nawa Fadwah take da har zaku fara zancen aure " gyara zaman Hajiya Mariyah tayi tana faɗin. "Gaskiya kan bata wani girma ba, amma Sultanate shin me yasa kike jin babu dad'i ga mutuwar Mansurah? Naga tsarar Fadwah ne don haka ina ga it is best time a aurar da ita tunda gana da wanda take, ban shirya ganin hawayena yana zuba ba, Allah ya basu zaman lafiya. Na gode." Ta fada tana barin falon. A karon farko da taji masifar tsanar Sultanate domin ta lura a duniya son kan Sultanate yayi yawa. "Mariyah bamu gama magana ba, zaki tafi? Waye ya baki wannan kwarin gwiwa haka ne?" Shanye bacin ranta tayi tana kallon Sultanate sannan ta ce mata. "afwa ina da abu me muhimmanci ne shi yasa, Allah ya huci zuciyar ki" daga haka ta fita..
Abin ya bawa Sultanate mamaki, wato idan ta lura Badi'atul Noor ita ta fara mata tawaye yau gashi mariah me mata biyayya kamar kare da uban gidansa yau ta bar mata zauren ta akan dan abin da bai taka ƙara ya karya ba.. "wato Sultanate itama zata fara miki hawan kawara kenan kamar Sultanah karama?" Wani irin bacin rai Sultanate ta ji ya tsaya mata a rai ta juya tana murmushin yake ta ce musu. "A'a tana da nata uzurin dai. "Allah ya kyauta amma meye na hada Ummu Mansurah da wancan figaggiyar yarinyar? Yarinyar da tsabar girman kai ba, baka isa ta gaishe ka ba." Ba wani abu Hajiya Mariya tayi ba, amma yadda ake ririta zancen sai ka rantse da Allah ta zagi Sultanate ne. A can bangaren Sultanah Badi'atul Noor. Shiri sosai take zata tura Abuturab can wurin Yayunsa su zauna can shi yasa zata hada shi da Zuwairah da kuma Jalilah, su tafi can su zauna tare domin kaf duniya bata da amintattun bayin da ta aminta dasu kamar mutane biyun nan. "Ummin mu ko zaki duba wannan kayan." Dubawa tayi kafin ta ce mata. "Eh yayi kyau, ki saka a cikin su. Zuwairah akwai sakon Maiduguri da aka kawo min mun yi waya da Mamar takwara tace tana son turaren wuta a kai mata, ki duba story akwai kayan a wurin ki gayawa Jalilah ta haɗa a cikin kayan dake wurin ta a saka a cikin kaya, kafin ya gama bautar kasar sa mun gama shirin mu" "shi kenan an gama Ummin mu" murmushi tayi tana kallon ta. 'ki kare Yaranki, kowama za a iya sayan shi da kudi domin cika musu burin su' d'ago kai tayi tana kallon Zuwairah da ta kusan barin falon ta ce mata. "Zuwairah!" Juyawa tayi tana faɗin. "Na'am" "Kina son kudi?" Juyawa tayi sosai musamman da taji zancen kuɗi. "Sosai ranki shi dade" "idan na baki miliyan goma me zaki yi da shi?" Dariya tayi sosai sannan ta ce mata. "Allah ya baki lafiya da nisan kwana, Yarana zan yiwa hidima." "Kenan zaki iya sayar da yardanki akan kuɗi?" "Subhanalillahi, Ummin mu ai amana ɗaya ce kudi kuma daban " gyara zama Sultanah Badi'atul Noor tayi tana faɗin. "Gashi ni an gaya min cewa kowa a cikin gidan nan ya fi son kudi sama da Amana taya zan yarda da ku?" Zubewa tayi akan gwiwar ta. "Sultanah wallahi babu wanda ya isa ya siye ni na miki butulci ki yarda da ni " ita kanta Sultanah bata san me ya kawo wannan zancen ba, sai dai bata jin zata iya shiru ne a kashe ta. "Tashi ki tafi " "mun gode " "Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana." Ta fada tana barin falon. A fada kuwa. Shigowar wani mutum karfaffe ga kuma tsawo alkyabar shi sak irin na Sultan Abdulrahman Dan Aliyu ne, niman wuri yayi ya zauna, yana watsawa mutanen fadar kallon banza. "Mtseeeeeew " ya ja tsakin da Sarkin bulala sai da ya zabura. "Hattara dai waziri zaka sha ukuba" "mtseeeeeew nayi." A zabure Sarkin Bulala ya mike, Sultan ya d'aga mishi hannu. "Kar ka d'aga mishi da ya ga kad'an me ban haushi." Kallon waziri sauran mutanen fadar suka yi cikin takaici suka ce. " Kai dai baka da hali wallahi" "Eh sai me? Ku kuma babu amfanin zama da ku a rayuwa da ni ke zaune a wancan kujeran dai na fille muku kai." Murmushi Sultan yayi yana faɗin. "Kyawun dan arziki ya gaji ubansa." Mikewa Waziri yayi yana faɗin. "Da ban gaji Ubana ba wani tsiyar ce? Kai Abdulrahman wallahi ban ki naga mutuwar ka ba." "Hattara dai" "kai yi min shiru Ja'irin banza, shi Abdulrahmanu wani kwarjini ne da shi, waye bai san mulkin kama karyan da ake ayi a masarautar nan ba? Kalla gara kayi murabus yafi maka zaman da kake akanka da matar ka baka maku adalci ba wani shegen zaka yiwa adalci. Gara mutuwar ka sau dubu akan rayuwar ka, matse ka bani hanya" "dogarai ku rufe kofar " juyawa waziri yayi yana kallon Dan masani, murmushi yayi sannan ya ce mishi. "Yahya Adekunle stop pretending ka fitar da kiyayyar ka zai fi maka rayuwa a cikin inuwa bayan kasan a kowacce rana konewa kake kai ku bani hanya" ya daka musu tsawa. "Waye ya gaya maka kowa mahaukaci ne irin ka?" "Ka tambayi Abdulrahman ya gaya maka yadda na tsalleke bala'i balle Hauka" yana gama fadar haka yayi tafiyar shi. "Sam Waziri Dawood bai da mutunci." Har ya kai bakin kofar ya juya tare da kallon Dan Masani. "Tabbas bani da mutunci, sai dai ni kaifi daya ne idan bana son ka, iya gaskiyar kenan bana sonka. Ban ga hadisi ba babu hujjar wanka da tab'o ba. Abdulrahmanu ka gayawa mutanen ka, su ajiye kiyayyar su akan ka, Ni damuwata kujeran da ake zaune akan shi. Allah sarki hala kafin na zo ya tsufa " ya dawo cikin fadar tare da shafa kujeran da Sultan Abdulrahman yake zaune akai. "Wai na tambaye ka?" "Yaushe zaka mutu? Na gaji da ganin ka zaune akan kujeran nan kafin nazo ya tsufa" "yaushe kake son na mutu?" Sultan ya tambaye shi a sanyayye, d'aga kafad'ar shi yayi cikin ko in kula da yanayin Sultan ya ce. "Duk lokacin da ya maka" sannan ya ɗan sunkuya kad'an ya d'aga murya. "Ku shaida duk ranar da Abdulrahman ya mutu ni Dawud zan zama sabon Sultan" ya fada yana d'age gira daya. "kana sakaci da Addu'a Ubangiji yana tare da masu addu'a shi yasa nake maka abin da naso kafin ka mutu. Ka kula da Rayuwar yaran manyan nan maza uku " daga haka ya kuma d'aga murya domin maganar da yayi, a can ƙasa ƙasa yadda daga shi sai Sultan suka san me suke fada. "kar ka damu ni ba zan kashe ka ba, amma ina gaya maka na Barka ne domin abotar mu na shekaru arba'in ya cigaba da tafiya. Amma ka sake ka cigaba da tafiya haka babu wani sauyi juyin mulki zan maka " daga haka ya juya abin da ya bar fadar. Shiru fadar ya dauka kowa da abin da yake tattaunawa a ran shi. "Sultan yanzu shi wannan mutumin babu wani abun da za a mishi ne?" Inji dan masani. "Babu abin da zai masa, bayan abotar su na Yarinta har girma, Dawud yana abin da ya gadama." Murmushi Sultan yayi sannan ya ce musu. "Ku mishi uziri " "ai shi kenan uzuri kam ana mishi kullum sai dai rashin mutunci har yau bai daina ba, kuma baya jin zai dai na idan ya cigaba da wannan yanayin tabbas zamu dauki mataki akan shi. Tunda farko muka so koran shi ka hana mu" mikewa yayi fadawa suka mike tare da saka masa babban rigar su, suka rufe shi har ya bar fadar. A can cikin gida kuwa, Waziri Dawood wucewa wurin Sultanate yayi Dama sau uku yake shigowa duk karshen wata. Yana zuwa wurin Sarki ya mishi rashin mutunci, sannan yazo wurin Sultanate ya gaya mata bakar magana, da rashin arzikin, kafin ya wuce wurin Sultanah karama suyi hira sosai, wannan karon Sultanah Badi'atul Noor ce ta tura mishi sakon yazo don Allah tana son ganin sa. Kaf duniya Sultan bai da abokin da ya wuce Waziri Dawood abu daya ya raba amintar su. "Assalamu alaikum, Allah yasa gidan da Mala'ikun rahama, domin idan datti ya cika ya tumbtsa babu abin da ba za ayi aikatawa ba." Gabanta ne ya fadi, kaf cikin masarautar babu wanda yake mata abin da ya gadama kamar Dawud, "Wa'alaikumunsalam, lale maraba da zuwan mara kunya" "ina zan yi kunya tunda muna da irin ku a cikin masarautar nan, me zai hana ki daina bawa Badi'atul Noor ciwon kai ki fadawa duniya abin da kike aikatawa nasan zaki shiga kundin masu bajinta ta duniya" "Dawuda kenan an gaya maka kowacce magana ce ake fitar da ita? Ko an gaya maka dabi'ar ka shi zai saka na yi yadda nake so?" "Ko daya bana fatar haka, sai dai ni akwai wata..
08130269641
[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: 16
Sai dai akwai wata yar tantama da nake akan ki, kuma nasan wacece ke zaki iya aikata kome wallahi, na tausayawa Abokina da bai san irin uwar da yake tare da ita ba wallahi." Mikewa tayi ko ciwon kafarta bata tuna ba, ta ce mishi. "Zoka fita min a gida " "Bafa inda zani" tsaki tayi cikin fada da sababi ta ce. "Ban da rashin kunya da rashin girmama na gaba, taya kana dan kanwata kana gaya min abin da kaso" "don ina dan kanwarki sai akace min kar na gaya miki gaskiya, kin ga ku gaya musu ta yadda aka yi Mansurah ta mutu, domin wallahi na san kome. Kamar yadda Mutuwar Dawlat khatoon da danta, da mutuwar Abdulsamad da lalacewar Abdulrashid. Ko na fita na gayawa mutanen gari ne nace musu an raba Yaran Badi'atul Noor ne da sarautar nan gudun kar su gaji mahaifin su " wani irin zufa yake karyo mata bakinta yana rawa ta nuna shi da yatsa tana faɗin "Zargina kake?" Hada hannun shi yayi yana me kallon ta ya ce. 'ki kwantar da hankalin ki, na san wadanda suka yi kisan kuma kema kin sani me yasa kike zunguro inda yake damun mutane? Sannan meye laifin Yaran Badi'atul Noor?" "Halin ta ya shafi Yaranta." Ta fada tana juya kanta. " Shi yasa aka yi yunkurin kashe Aliyu?" Wani irin zabura tayi kamar zata fado kasa. "Me kake cewa ne? Wancan dan banza zasu kashe kuma? Me ya tsare musu naga dai ana binciken akan mutuwar da ake zargin shi yayi?" Mikewa yayi tare da saka hannu a cikin aljuhun babban rigar sa y ce mata. "Nasan ranki ya ɓaci ba? Bai kai na yadda kuka jefa Badi'atul Noor ba, wanda nasan matukar kuka cigaba da wannan tafiyar wata rana zata fito fili ta kalubalance ku, a lokacin shi kansa Abdulrahman bai da cikakken karfin kare ki da wannan nake baki shawara ki ajiye yakin ki a gefe shi kuma Abdulrashid ki daina lalata Mishi rayuwa bayan wanda aka san anyi na baya, babu adalci a rayuwar gidan nan. " daga haka ya juya ya bar falon, kasa zaune tayi ta kasa tsaye, asali yau Dawuda ya bata mamaki tabbas Dawuda yasan sirrin ta, da abin da ya dangance ta. Wayarta ta dauka.
***

After two weeks.

A gajiye take tafiya, kamar bazata iya tafiya ba, ga jakar makarantar da ya mata nauyi. Da sauri Rahilah ta amshi jakar tana mata alama sannu da hannu. Hawaye ne ya zubo mata. Har suka isa hostle kuka take, karshe ma bata ci abinci ba, da azhar yayi suka tafi masalaci acan ta cigaba da kwanciya. Abin da ya faru kuwa wata prefect ce ta shigo ajin, dake bata gani sai da madubi, shima ido daya ne yake gani dayan kan baya gani baki daya, tana shigowa ta isa gaban desk dinsu. Shi ne ta fitar da ita suka fita. Ko a ina ta samu labarin ta oho, ta wuce da ita hostle dinnsu, ta kwashe mata kayan abinci, sannan ta saka makafi yan uwanta suka zane ta. Tun da ta gane haka shi kenan, kullum sai ta saka an kawo mata Sa'ade ta zane ta. Tsoro yasa duk suka kasa kai karar ta, karshe yau da abin ya ishe ta ne ta gayawa head girl na bangaren su kurame. Kamar ta watsawa wuta fetur. Ita head girl din ta samu wancan Prefect din da magana, shi kenan fa yau da ya zama asabar bayan su fito da extral class, suka rufe ta da duka, kamar sun jaka. Suna cikin haka ne wani daga cikin dalibai maza ya shigo makarantar ta katanga. shima kurma ne, ya leko sabida yadda yaji Rahilah tana ihu da wasu irin surutu na kurame. Ya leko idanun shi ya tsaya akan yan matan, tausayin Sa'ade da suke zanewa tasa shi saukowa bayan ya karyi bulala, ya nufi cikin makarantar mata da shi, basu san da zuwan shi ba, sai jin saukar bulala suke. Ta ko ina, abin da ya firgita su kenan, suka juya da gudu. Ya d'aga sa'ade ya karkad'e mata kayan ta, sannan ya kira Husnah Jafar Kurmi wacce tsoro ya saka ta boya. Tambayar yayi da hannu. Hannunta ta kai goshinta. Sannan ta hancinta ta kuma hada hannun, "Bata mata kome ba, tun ranar laraba take dukarta kullum idan aka tashi break" "Da gaske?" Ya tambaye su, ya saka hannun shi tare da rike wuyar shi. Hannu Rahilah ta kai kumatunta tana faɗin. "Na rantse" lumshe idanun shi yayi ya bude akan sa'ade dake kuka har lokacin. "Ya isa ya mata alama da hannu. Haka suka nufi dakin su, suna jinjina abin. Wannan shi ne abin da ya faru a ranar, sai bayan la'asar suka dawo hostle. Sun samu jikinta da sauki ga kayan abinciin ta sun kashe tass. Zama suka yi, suka jika musu garin kwaki jika. Rahilah ta kawo Sugar, Ita kuma Sa'ade da ta ji dadin jikinta ta kawo gyada da kuli kuli ta mika musu, ta koma ta kwanta. Suka yi tasha amma fir taki sha, haka suka zauna har lokacin magarib yayi suka tafi masalaci basu dawo ba, sai isha shina wucewa wurin amsar abinci suka yi. Ina ko loma daya Sa'ade bata ci ba, sai amai, dole aka wuce da ita clinic, aka saka mata ruwa domin tayi weak, sannan aka kira coper Sadeeq aka gaya mishi, a daren ya kira Abuturab, wanda ya ke can ya saka Malam Aminu a gaba da Tsokanar sai ya biya shi kudinsa. Ya dauka, sun yi magana sosai sannan ya ce gobe dai shigo. Ita kuma a cikin clinic din ta kwana, Yarima Sadeeq ya koma. Rahilah da Husnah a wurinta suka kwana. Kowannen su kamar zai shige jikinta ya saka ciwon a kansa domin baki daya tausayinta ya narke musu a zuciya. Anan suka kwana da sassafe sai ga Abuturab. Abin dariya kamar mayu sun manne a gado daya, sun saka ta a tsakiyar su, suna barci. Rigar jikinta ne ya kware har saman sili-silin cinyarta ya ga shatin bulala, muryan Sadeeq yaji, da sauri ya janyo rigar ta rufe mata cinyarsa. Ya juya Yana kallon shi. "Man ya dai?" "Akwai masu cin zarafin ta a cikin makarantar nan?" "What'?" "Abin da na gani ne bari su tashi." Zuba musu idanu suka yi har suka tashi domin kansu, sai lokacin Rahilah ta tuna basu yi sallah ba, suka fita da gudu suna masu jin kunya sosai. Kallon Sa'ade yayi ya zauna a kujeran dake gaban gadon ya kalli karin ruwan ya kare. "meke damun ki?" Tashi tayi zaune tare da riko hannun shi. Ta mishi alama da hannu. "Don Allah ka kai ni wurin Innata, na yafe karatun zan je nayi kiwon yar tinkiyata" ta gaya masa. Dafa goshinta yayi sannan ya mike, kallon Sadeeq yayi sannan ya ce. "Ka gayawa shugaban makarantar na tafi da ita jinya." "Ok ba damuwa " fita yayi can sai gashi tare da mataimakin shugaban makarantar, sannan aka aka tura kiran su Rahilah suka kawo mata kayanta kala biyu. Kafin suka bar makarantar tana kuka su Rahilah suna kuka saboda shakuwa. Bai tsaya da ita ba sai wani babban private hospital a cikin garin Sokoto, suka shiga bata kulawa na musamman. Sai lokacin ya kira Zakaria, sun zo asibitin domin anan suka wuni shi da Yusuf, bai gayawa Aunty Ummi ba, sai da aka sallame su ta gansu da Sa'ade. A hankali ta zube a saman kujeran falon baki, ta kwanta kafin wani lokaci barci yayi gaba da ita. "Ni zan tafi sai gobe zan zo na ganta." "Tow Allah ya kai mu, mun gode sosai." Haka ya tafi yana jin babu dad'i. Washi gari monday karfe bakwai a makarantar ya mishi. Inda ya sa aka kira Rahilah da Husnah ya tambaye su me ya faru. Basu boye mishi ba suka gaya mishi abin da ya faru. Ya tsaya suka yi magana da shugaban makarantar, sannan aka kira yan matan. Suka zo tsoro yasa suka amsa abin da suka aikata. "Kun san me? Ai nasan kuna jina, wallahi billahi azim na kuma kama wata da laifin tab'a Sa'adatu Aminu Fulani, sai na karya yarinya. Shegu marasa kunya masu bakin ciki har cikin zukatar su. Waye bai sai halin ku ba. Look wannan ya zama deal dina da su, next time na kuma haduwa da su, kun gama karatun nan wallahi, ku ko zuciya baku da shi sai tsabar hassada da Kyashi na kuma zuwa ko a kirani kun taba daya daga cikin yara ukun nan sai na d'aye fatar ku na fasa muku kun cinye fitinanun mutane." Fada yake inda ya shiga ba tanan yake fita ba, abin ya bawa Sadeeq mamaki domin a sanin shi mutum ne da bai cika fada ba, kuma gashi nan ya zo yana bala'i kamar zai make su. Sake baki yayi yana kallon shi, yadda ya rufe idanun shi yana bala'i, sai bashi hakuri principal yake domin bai tab'a ganin masifaffen mutum irin shi ba, har ya gama masifar shi hakuri suke basa. Daga nan ya mike. "Ka shiga tsakanin su idan ba haka ba, kowacce sai na hanata sakat. Haka yayi ta gyada kai.
** Da yamma wurin la'asar yazo dauke da kayan ciye-ciye. Zama yayi yana kallon yadda take karanta wani tarihi me suka na Hausa, ya kurawa fuskar idanu, wani lokaci idan tana yin abu kamar Mansurah, murmushi yayi yana kallon kalabar kanta, gashin har kafad'arta gashi gashin baki me sirkin ja, irin na asalin fulani. Amsa yayi yana kallon ta. Tura baki tayi tana kallon littafin. Ganin yadda yake kallonta ta mike tsaye tana niman tafiya ya mata alamar ta zauna, zama tayi tana kallon window waje. "Jibi zaki koma makaranta" zaro idanu tayi tana me girgizar kanta ba zata ba. Hannun shi ya saka a wuya" na rantse sai kin tafi don haka gobe zan zo muje kasuwa kawayen ki , sun gaya min an kwashe Miki abincin ki." "Ni ba zan koma ba na gaya maka, kawai a mai dani gida " ta fada tana fashewa da kuka. Kura mata idanu yayi. "Baki son kiyi karatu ne ki zama wacce za anan nunata a tvn " hawaye ne ya zubo mata. Ta gyada kai tana nuna tana so, ya gyara zama sannan ta ce mata. "Share hawayen ki"
08130269641
[24/05, 6:00 pm] usmanlauratu71: Da dan sassarfa ta isa hostle din su, bata yarda ta shiga cikin hostle din ba, amma tana iya hangota, yadda ta tsuguna a gaban locket ɗin su, dake an gansu tare babu wanda ya kawo wani ta'addin tazo yi, tana kokarin bude locker din kenan Rahilah ta isa kwanar su. A firgice ta mike tana zare idanu. Nade hannu a kirji Rahilah tayi tana mata wani irin mugun kallo daga sama har kasa. Hàdiye yawun tsoro tayi tana faɗa mata ita bata dauki kome ba, rab'a gefenta Rahilah tayi ta kuma rufe locker din, sannan ta juya tana watsa mata kallon banza ta nuna mata hanya. "kar nan kuma ganin ki a cikin mu, ki tsaya iya kanki." Hàdiye yawu tayi ta wuce simi-simi kamar wacce aka watsawa ruwan zafi. Sannan Rahilah ta tafi ya same su.
***
Hajiya Daulah.
Tsura mishi idanu tai, ta rasa abin da zata gaya mishi ko zata mishi ta ji dadin rayuwarta asalima irin mugun b'acin rai take ji. "Abdulhakim meye nufinka? Nace ban isa da kai ba ne?" D'ago kai yayi idanun shi jajjur. "Kiyi hakuri bani da lafiya ne shi yasa ban je ba" tabbas matukar takardun shi suka fito zai gudu ya bar Hajiya ba zai iya da rigimar ta ba, ta hana shi sakat. "Ka sani ina kallon ka ne, duk lokacin da ka cika ni zan bata mata ka rai" ta fada tana bubbaga hannunta a kasa. "Allah ya huci zuciyar ki" ya fada yana barin falon, ita kanta bata son tana mishi fada anyhow, dauke kai tayi tana son ta bincika ta ina ta gaza a kulawar da take mishi? Amma baki daya baya damuwa da ita kamar yadda yake damuwa da mahaifin sa. Tana zaune a wurin Afiyyah ta shigo a gajiye, zama tayi tana kallon Hajiya. "Hajiya naga motar Yaya. Yana sama ne?" "Eh yana can" da gudu ta haura sama tana zaune. "Assalamu alaikum, Ya Abdul Barka da dai. Dama dama" kallonta yayi cikin kulawa sosai. "Kina son wani abu ne?" Ya tambaye ta a sanyayye. "Hmm uhmm, dama akan Sophia ce ta ce na" "get lost" da sauri ta juya, "mtsew" ya kawar da kan sa. Da gudu ta isa falon. "Hajiya" kura mata idanu tayi domin bata son magana. "Sophia ce ta ce min" "wuce ki bani wuri bana son magana don Allah" daga haka ta wuce mai da hankalinta tv, wurin karfe shiga Taufiq ya dawo. A kofar shigowa suka hadu. "Ya Abdul ya kake?" "Lafiya muje sallah" "tab na gaji idan na farka cikin dare zan yi sallah amma yanzu wallahi na gaji, idan bayi yau ba zan yi gobe in sha Allah" ya fada yana shiga da goyon jaka a bayan sa. "Allah ya kyauta" ya fada yana dauke ajiyar zuciya, ya nufi hanyar masjid da yake jikin gidan su, bai da so gidan ba, sai da aka bayan isha. Tunda ya shigo ya hango su a wurin cikin abinci masu aiki sai kaiwa da komowa suke. Bai ce musu cikanku ba ya wuce abin sa. "Abdul" Hajiya Daulah ta kira shi. "Na'am" ya amsa yana juyowa baki daya. "Zoka zauna ka ci abinci" ta fada a tausashe, domin bata son yayi ta yawo babu abin arzikn a cikin sa. "Na koshi" ya fada can kasar makoshinsa. "Zo nan Babana " ta fada a raunane, domin baki daya yadda yake bata son abin da zai iya lalata mata shirinta na son yayi aure ba. Takowa yayi har inda ta nuna mishi ya zauna yana kallon abinciin. "Ci" ta ce masa. Babu musu ya fara ci. "Hajiya kin mai da Yaya Abdul kamar wani yaro" inji Taufiq yana dariyar shakiyanci, murmushi tayi tana kallon Abdul din da yake cin abincin kamar bai da hakora a bakin sa. "Nayi magana da hajiya Nazirah akan Sophia ko zaka fara zuwa ne?" "Kwat" ya hàdiye abinciin bakin sa, yana kallon ta. "Baka fahimci me nace ba ne?" "Na fahimta " bata bar shi ya sake wani magana ba, domin ta lura da magana a bakin sa ta mike tana cewa"Allah ya taimaka ya daidaita kanku" "Amin" ya fada muryan shi yana rawa. Dauke kai tai tana haurawa sama, tana halkance da shi, yadda yake kallonta. Amma bata jin zata iya kyale shi. Tana barin wurin ya mike shima ya nufi waje, yana shan iska baki daya kome ya tsaya mishi cak, bai da wani kuzarin da zai fadi abin da yake damun sa, tare da fadar likita yace saboda ciwon shi ba zai iya zama da mace ba, tunda shi ciwon haihuwar shi aka yi da ita ba daga sama ya same ta ba, domin da daga sama ne tabbas da yanzu yana da mata da yara kamar kowa, kuma abin da yake kara dagula lissafin sa, shi ne har yau bai da wacce zai nuna a matsayin yana so asalima har yanzu bai da cikakken lokacin da zai kalli mace domin kansa. Sai dai ya musu kallon tsoro ya wuce. Shigowar motar Dr Sharif wato mahaifin su. Mikewa yayi ya nufi wurin sa, ya jira sai da yayi parking sannan ya kashe motar ya fito, amsar jakar hannun mahaifin su yayi yana faɗin. "Barka da zuwa." "Yawwa Abdul Hakim ya na same ku?" "Alhamdulillahi" ya fada suna jerawa, "Ya Aunty Faridah?" "Tana lafiya sun ce na gaishe ka" ya fada yana kallon sa. "Kana da damuwa ne ?" "Na'am" sai kuma yayi yar murmushi, sannan ya sosa kansa. "Ba kome" ya fada yana tafiya ciki da sassarfa. "Abdul Hakim meke damunka?" "A'a babu kome" ajiyar zuciya Dr Sharif ya sauke tare da bin bayan sa. Dakin Abban su ya kai mishi kayansa, sannan ya wuce dakin su, a duk lokacin da Mahaifin su yake gidan yana jin wani irin kwarin gwiwa da ita yake kwana, sai da Dr Sharif ya huta sannan ya wuce dinning table ya ci abinciin sa. Sannan ya wuce dakin Hajiya Daulah. Hankalinta yana kan wasu takardu ya shiga ya ja kujeran mirror ɗinta. Ya zauna yana kallon ta, "Ranki shi dade zaki bani aron lokacin ki?" "Emmm!" Ta fada hankalinta yana kan takardun, "ina son ki ajiye kayan gabanki muyi magana akan rayuwar Abdul Hakim" sai lokacin ta ajiye takardun ya zuba masa idanu. "Ina jinka" tattaro nutsuwar sa yayi ya kalle ta sannan ya ce mata. "Abdul Hakim ba zai iya zama da mace ba, duk yadda kike son yayi aure na fiki kaunar haka, domin har auren yar Sultan an bashi, ba na gaya miki haka ne domin ki d'aga min hankali ba, na gaya miki ne domin ki san matsalar d'anki, ba zai iya zama da macen da kike ra'ayi ba, likitan shi ya tabbatar da matukar shi yaga mace yana so tow zai iya zama da ita kuma idan tana son shi zata zauna da shi, ba auren dole ba." "Kana nufin zan matsa mishi yayi aure ne? Ko kana son cewa na takura mishi da zancen aure?'" "hmm" yayi murmushi me sauti yana kallon ta, kafin ya ce mata." Ko daya ina son ki tuna da cewa shi din amana ne Allah ya bamu tsakanin mu da shi akwai hisabi kar ki yi abin da zai tsaya a gaban Ubangiji ya nima mishi hakkin sa, don Allah kar ki tsannanta mishi, mu kyautata mishi gani nake kamar duk halin da yake ciki mune sanadin haka, don Allah ki yi haquri." Kamar ta rufe Dr Sharif da duka, amma haka ta rufe idanunta ta, na tsawon minti goma sha biyar, kafin ta bude fuskar ta yayi jajjur Idanunta sun kankance domin takai matukar bacin rai, jan drower gadon tayi ta zuba takardun ta cigaba da kallon Dr Sharif, a hankali tayi murmushin karfin hali, ta ce mishi. "Zaka iya tafiya kaina yana ciwo" gyada mata kai yayi domin har ga Allah baya son tashin hankali su ya shafi Yaran su, shi yasa yake mata biyayya kamar ita ke auren shi ba shi ke auren ta ba. Haka ya fito jikin shi a mace ya wuce dakin sa, itama kuma kashe wutar dakin tayi tare da ƙwanciyar ta, amma ba barci tayi ba, sai dai tana saka abubuwa masu yawan gaske akan danta da mijinta, tana son Abdul yayi aure tana son ganin jinin sa a duniya. Ba haka kawai take takurawa ba, Yes tana son ganin sa cikin farin ciki da walwala.
***
Few weeks ago.
Saturday visiting.
Tun safe suke shiri sosai, kai ka rantse da Allah sun shekara basu ga iyayen su ba, idan ka cire Rahilah da take kwance. Sa'ade anyi wanka Umma metro ɗin su, ta musu guga, sai sheki check dinsu yake, ita da Husnah, Kubrah tana rabe a gefe, duk da basu san me yasa take kin zama a cikin su ba, amma haka suke janta cikin su, inda tayi kokarin hana kanta daukar kome nasu, sai na sauran yan room ɗin, idan ana sururun anyi sata, kallo daya Rahilah ke mata ta shiga kame-kame. Dukar pillow da Rahilah take kai Sa'ade tayi, ta bude idanunta da suka yi jajjur. "tashi mu tafi kin ji" ta mata magana, saka hannu tayi a wuyarta ta ce mata. "Bani da lafiya ne" kallon kuru tayi mata, tana son hango iyakar gaskiyar Rahilah, "shi kenan" ta fada suka fita suna mata fatan Allah ya ba ta lafiya, har sun yi tafiya me nisa, sa'ade ta kalle su musu alamar su tafi tana zuwa. Ta juya abin ta, kallon ta suka yi. Kafin kamar hadin baki suma suka biyo ta, ana ta fita a room ɗin ba kowa, sai Rahilah da take zaune tsakiyar gadon tana ta rusa kuka, wani irin maraici da kewar Iyayenta take ji, bata da d'an uwa ita ɗaya suka haifa suka rasu baki daya, yan uwan Baban ta, ba zuwa suke ba, sai dai Aunty ta aiko mata garin kwaki da sugar. Yadda ta cusa kanta a tsakanin cinyarta tana kuka sai yq taba zuciyar duk wanda ya iso in da take, zagaye ta sukayi suna kallonta. Kafin Sa'ade ta dafata, a tsorace ta d'ago kai. Ganin Sa'ade ne, fadawa jikinta tayi tana kuka. Itama kuka take, abu daya ya tsara da kukan su. Shigowar Umma ta saka salati tasan ba wani ji suke can can ba, sai da ta matsa kusa da su, ta musu dakuwa tare da musu al'amar su tafi ana niman Husnah Jafar Kurmi, amsawa Husnah tayi, ta mikawa Rahilah kayanta, suna tsaye har ta shirya, a hanyar tafiya suka gamu da wasu senior sun zo niman Kubrah, Iyayenta sun zo, sai da suka fara zuwa wurin iyayen Husnah, suka gaishe su sannan suka wuce wurin iyayen Kubrah, kallon Kubrah suka yi domin basu ga a lamar Maman ta ba, sai dai da alamar matar da mijinta da dan su daya, matar tana kama sosai da Kubrah, itama bafulatana ce, komawa bayan Sa'ade Kubrah tai jikinta yana rawa, juyawa suka yi suna kallon ta. Hawaye na zuba daga idanunta. Dake dukkan su yara ne babu me hankalin da zai iya cewa wani abu ne, Yarima Sadeeq da Abuturab suna hango su, daga can wurin class. "Me ka fahimta?" "Kai dalla kawai dai bata yi appreciate da zuwan su bane" "har yau baka son kome akan masu matsalar nakasa ba, kaga lokacin da suka tawo, da gudu yarinyar ta isa wurin matar, ganin mijin yasa ya fara ja baya. " "Case closed don Allah kayi naka matsalar" Abuturab ya fada, domin baya son magana, idanun shi na kan Sa'ade da take bubuga bayan Kubrah. Takowa mijin matar yayi, ya cire hannun Sa'ade ya fara kokarin janye ta jikin sa, da karfi ta fashe da kuka. Ya juya ga Yayarta yana kallon ta irin kallon shu'umancin nan ya fara magana. "Salmah ba zaki mata magana ba." Jikinta yana kerma ta mata alamar ta daina ihu. "Ki gaya mata bana son ganin yaran nan a tare da ita ko na dauki mugun mataki " ya fada yana shiga gaban motar, sai kallon su ake, haka ta shigar da Kubrah motar, da aka saka mishi tintak. Sauke glass din motar yayi yana bin su da mugun kallo, a mugun tsorace suka juya, kamar zasu kifa. Musamman Sa'ade da ta hango tsanar su a fuskar shi. Hango Yusuf tayi yana nimansu, da gudu ta isa wurin shi dake ya basu baya, ta ja rigar shi. Juyawa yayi ta fada jikin shi tana murna.
18
Hakkin Mallakar
Mai_Dambu
08130269641
[26/05, 5:07 pm] usmanlauratu71: Rike ta tayi yana dariyar farin ciki, juya baya Abuturab yayi, yana shafa kansa. Da mamaki Yarima Sadeeq ya ce mishi. "Ya ka juya baya?" "Uwar me gabana zai maka" ya tambaye shi, a hankali. "Allah ya huc zuciyar ka. Ai ba don Yusuf dan uwanta ba ne da zasu dace idan ta girma" take kafar Sadeeq yayi da karfin gaske. Sai da yayi ƙara. "Watch your tongue" "daga fadar gaskiya" "Mtseeeeeew" Abuturab ya ja tsaki, "Malam meye najin haushina?" Share Sadeeq yayi yana kallon Sa'ade da yan uwanta da Mamanta. "Baka san Arzikin da yake cikin sanya mutane farin ciki ba ne? Da ka sani ba zaka dame ni da wani batu na daban ba." Ya fada mishi yana saka madubin sa na no respect. Wurin su ya nufa, yana isa wurin "Assalamu alaikum " ya musu sallama yana kallon ta, ta cikin madubin yadda take kara narkewa a jikin Innarta. "Gadanga kusar yaƙi, ka zo ne?" Inna Laminde ta fada tana murmushi. Zare madubin yayi yana shafa kansa. " "Eh Inna, an zo wurin auta kenan?" Dake a Husnah ta na wurin Iyayenta, Rahilah tana tare da Sa'ade, amma hankalin ta yana kan motar su Kubrah da ta bar harabar, kallon Sa'ade tayi tare da gaya mata mata magana. "Motar su Kubrah bata nan fa!" Leka wurin tayi itama. Da sauri ta mike a jikin Innarta, suka bar wurin. Abin ka da Yaranta suka tafi wurin Husnah da take hira da kannenta, ganin yadda take cikin farin ciki yasa suka barta suka tafi. Abuturab yana kallon su. Sako ya turawa Sadeeq. *Ga yaran nan ka bibiye, zasu ta wurin kawarsu* a can motar kuwa, tunda ya bar cikin mutane, ya saka yayar Kubrah ta fito waje, ya koma bayan. "Wato ke me taurin kai? Bana ce babu ruwan ki da kowa ba? Har zaki fara nunawa mutane ina miki wani abu" girgiza kai tayi tana kare fuskar ta, haka ya murde hannunta yayi ta kifa mata mari, kafin ya kai hannun shi cikin rigar ta kuka take tana, kare fuskarta. Itama Salmah da take gaban motar kuka take, domin tausayin yar karamar kanwarta. Sai da ya ga ta daina kuka tana ajiyar zuciya sannan ya ce. "fita ki bani wuri, zan mata fada." Fita tayi da danta. Hawaye na zuba mata, hannun sa ya kai bayan Kubrah, yana shafa ta a hankali yana faɗin. "Idan kika min abin da nace, zan daina hana Salmah abinci, amma idan kika ki yi min yadda nace, wallahi sai dai ta fara sata kamar ke." Gyada mishi kai tayi, d'aga rigar shi yayi, jikinta ya shiga kerma, ganin yadda ta boye fuskartar tana shashekar kuka yasa shi damko gashin kanta, ya kai tsakiyar cinyar shi. Ya danne kanta tare da tura mata kukanbanba dinsa, buga kofar motar aka yi da karfi dai da ya razana. Cikin takaici ya hango Rahilah tana buga kofar, Ita kuma Sa'ade tana wurin Salmah a fusace ya maida wandonsa, ya bude motar a hankali tare da tokarar motar, sai da Rahilah ta fadi can, ya fito idanun shi jajjur. Da gudu Sa'ade ta d'ago Rahilah, tana leka motar, a hankali ta sunkuya kamar me niman wani abu, kawai yarinyar nan ta dibi kasa ta watsa mishi a idanu, da gudu suka bude inda Kubrah take, suka juya da gudu suna barin wurin, karo suka yi da Abuturab. Musamman ita da ya koma zata fadi. Mijin Yayar Kubrah da yake ta ihun sun watsa mishi kasa a idanu, dakyar ya share idanu Salmah ta mika mishi ruwa, ya wanke idanun shi, yana fara gani ya kifa mataS pp mari, sannan ya bi bayan su. Bai gansu ba sai da yayi ta niman su, kafin ya hango su Abuturab yana tsaye da Inna suna magana ta mika mishi wani farin gora cike da madara, dafaffiya. A hankali idanunta ya hango mata mijin Yayan Kubrah dauke da wani katako, tsabar ta rikice bata san lokacin da ta ture shi ba, katakon ya sauka a gefen kafad'ar Abuturab. Sake rikicewa wurin yayi da ihu, da sauri Sadeeq ya kai mishi dauki, duk da ba wani abu ba ne. " Sake ni naci uban sa." Principal da yan sanda suka iso wurin. Zare idanu yayi yana kallon Kubrah da gefen fuskartar yayi jajjur, sai fuskar Salmah da ta yi ja shima. "Officer kuyi arrested din shi," inji Principal,
"Meye nayi? Me na muku?" "Kai yi mana shiru muje zaka ji abin da kayi" "Aliyu da fatan babu matsala ko?" Principal ya tambayi Abuturab. "Ba kome" "Allah ya tsare na gaba, mun gode da taimakon da ka mana, ita yarinyar zamu kira social warfare su shiga al'amarin da kungiyar su na Handicapped su tsaya mata, mun gode sosai" "ba kome ni dai fatana, yaran su karatu " gyada kai yayi yana faɗin."in sha Allah " bayan tafiyar Principal ne su Yusuf suke tambayar shi ne ya faru. Sadeeq ya basu labarin abin da yake faruwa. "Yallabai da Fatah babu abin da zai samu Sa'ade?" "In sha Allah babu, sai ma fatan Alkhairi da zamu mata, domin tayi kokarin." Ya fada yana kallon ta. Yadda suke cure wuri guda. "Don Allah kar ki ji tsoron kome, ki fadi gaskiya a wurin Hukuma zasu karbar muku hakkin su." Sadeeq ya fadawa Salmah da take ta kuka. Domin tsoro ne da ita kamar farar kura. Haka ta fito da kayan da tazowa Kubrah da shi suka yi ta shigar da su, har na Sa'ade da Husnah, sannan suka fito suka yiwa iyayen su Sallama, sai da Inna ta raka Salmah gidan ta tare da su Abuturab, ana suka samu mahaifin su Kubrah yana ta fada. Lokacin da Abuturab ya isa wurin shi kallon shi yayi kafin ya ce mishi. "Dattijo kaga wannan saurayin? Dan Sarkin Musulmi ne, idan yaso zai iya kai karar ka wurin Mahaifin sa kana kare mai laifi bayan mutumin nan, zalunci yake, Salmah ka aura mishi ko kubrah da zai lalata mata goben ta?" Cikin sassauta murya tsawon ya ce.Yaro baka san halin su ba ne, ita fa Kubrah sace-sace take mana shi ya sa ya dauke ta " "Eh tabbas tana sace-sace, amma waye ya sanadin? Kai da matan ka. Domin da mahaifiyar Kubrah tana raye ba zata barta da yunwa ba, ba kuma zata wulakanta rayuwarta ba. Saboda marainiya ce babu uwa kai da zaka zame musu uwa Uba ka kyamace su, ita kanta wannan tana tsoron fadar gaskiya domin kar aurenta ya lalace, Alhaji duk wanda ka gani da abin da Allah ya nufa akan su, don Allah ka rike kyautar da ya baka, yana sane da su. Bance sai shiga al'amarin aurenta ba, amma kasan hukuncin auren akan mutumin da yake niman Ya ya nime kanwa. Rayuwar Yaranka mata, nasan kana da wasu yaran amma kome lalacewar su, wata rana sunanka sai ya fito don Allah ka kula da su, idan da dama ta hakura da auren tayi karatu miji na gari zai zo" wani irin abu yaji ya tsaya a kan sa, hawaye ya shiga zubo mishi. "Na gode zan kula sosai. Shi kuma Fa'iz yaje na bar shi da Allah zai saka mana " "Amin Ya Allah, Alhaji kayi hakuri amma yaron nan ba zai tab'a barin wani ya cutar da ita ba, ka rungume su itama ta rungume danta domin wata rana ayi alfahari da su. Zamu tafi" inji Inna. "Alhaji don Allah ka toshe kunnenka Yaranka rahama ne a gare ka, kar ka ki su." Sun bar gidan zuciyar su sawai, domin mahaifin su Kubrah kamar wanda ya farka daga mafarki, haka ya nunawa Salmah dakin ta, dama su biyu ne mata, tun rasuwar mahaifiyar su kome ya lalace matar sa muguwa ce, kaninta yake auren Salmah Fa'iz, baban su Kubrah yana da rufin asiri sosai domin dan kasuwa ne da yake da manyan shaguna Central market sokoto, Fa'iz yake rike da wasu shopping complex ɗin sa. Domin matar sa ita ta sa ya bawa kaninta auren Salmah domin su kwace dukiyar sai Allah bai nufa ba, domin mutum ne da yake da lissafi, kuma abu daya da suka kasa yi akan sa shine yana da yawan ibada, sun gaza nasara a kasan sai suka raba shi da Yaransa musamman Kubrah, da ita kan an san uban yana matukar tausayinta, shine aka jona mata sata, kamar bera abin haushi ko ta dauka bata iya cin ko tayi amfani da shi sai ta ajiye yadda za a kamata, wannan yanayin matar uban ta saka shi a gaba sai da Fa'iz yazo ya amshe ta, kamar da gaske shima ya daura nashi zalunci, gashi dukiyar ubansu yake lalatawa amma basu da ikon cin abinci sai ya basu, kai ga wani mugunta da yake na son lalata Yarinyar, dakyar ya kawo ta Makarantar inda ya mata kashedin kar tayi kawa ta zauna a hka. Sai gashi tayi kawayen masu tausayi. Domin kuwa daga baya Rahilah ta saka idanu akan ta, babban abin da yake bata mamaki idan yayi Sata bata ci, zata bar shi a wurin. Haka yasa sau goma ta dauko Rahilah zata ma maidawa masu shi. Kayan su, sai dai a gama masifar anyi sata daga baya a samu, domin tasha ganin tana kuka idan tayi abin, zaman su gashi nan dai kusan tausayin junan su, suke.. ** bayan barin su Abuturab daga unguwar su Kubrah. Suka isa kan wuri, sai da ya huta ya bawa Ummu Hafsah madaran, ya kira Ummin sa, tashi yayi ya fita daga cikin gidan ya nufi can harabar gidan ya zauna. "Ummina wai meke faruwa ne? Kin sani a duhu baki ɗaya?" Ajiyar zuciya ta sauke me nauyi kafin ta ce mishi. "Allah yayiwa Mansurah rasuwa" wani irin dauke wuta yayi, a hankali yaji kamar wani irin iska me karfi tana fisgar shi, duhu me karfin gaske ya lullube idanun shi. Daga can nesa yaji ana kiran shi amma ina tafiyar tayi nisa, a wurin ya zube ba tare da yasan waye a kan sa ba. Masu hidimar harabar ne suka hango shi a kasa, babu bata lokaci aka sanarwar Sadeeq suka nufi asibiti da shi. Sai da aka ɗauki tsawon lokaci kafin aka samu kansa, sannan aka mai da shi wani daki ya huta, har dare Aliyu be farka ba, washi gari Ba'aditul Noor da Rumaisah tare da Ummu Aymana, suka iso hankalin su a tashe. Har zuwa lokacin bai farka ba, Ita kan Ummi Addu'oin tare da sallar nafilla, shi tayi tayi tana gayawa Allah kukanta. Wasa wasa Aliyu ya kwashe kwana biyu bai san waye ma akan sa ba, sai a kwana na uku da yamma domin suna fadar cewa zasu mai da shi Kwara, Allah da ikon shi bayan salla la'asar, ya bude idanun shi. Lokacin Ummi tana lazumi computer din da aka saka mishi suka fara kara, shafa Addu'oin ta, tayi tare da mikewa tana me hamdalla, ta nufi waje ta cikaro da nurse din da suke duba bashi. "Alhamdulillahi ya farka" ta fada fuskarta dauke da murmushi. "Masha Allah, Autan Hajiya ya farka." Nurse din ta fada, suka nufi dakin, ta fara duba shi kafin ta kuma fita can sai Gasu tare tambayoyi ya fara mishi, yana bin shi da idanun, ya sake kallon Ummi ya ce. "Hajiya bai farka baki daya ba, amma idan ya farka zai gane komi." Shiru tayi kafin ta ce . "Ubangiji ya tashi kafad'ar shi." "Amin Hajiya ina jin dadin yadda kike nuna kwarin gwiwa akan shi." Murmushi tayi tana kallon Abuturab ..... Top-notch 08130269641
[27/05, 7:03 pm] usmanlauratu71: Duk da haka karfin hali ne, kawai da halin da yake ciki, domin har ga Allah tana cikin damuwa da tsoron kar wani abu ya same shi, zuciyarta yayi nauyi gani take kamar wani abu zai same sa. Amma shi never give up akan sa ta wani fannin. Wayarta ce tayi tsiwa, sai da ta kalli fuskar wayar tare da kura mishi idanu, kamar tana son hango wanda ya kirata, yankewa kiran yayi ta wani ya kuma shigowa, Kirjinta yana wani irin bugawa ta dauka, tana faɗin. "Assalamu alaikum" shiru daga can gefen aka yi. "Badi'atul Noor kina wasa da ni ko? Kina wasa da abin da muke yi? Hmmm kina tsammanin." Kashe wayar tayi tana faɗin"Innalillahi wa'inna ilahi rajuun." Ta lumshe idanunta, na wani lokaci kafin ta bude akan abuturab, ya gama zaman shi kawai ya tafi can wurin Yayunsa ya zauna kamar yadda ta shirya. Haka tayi ta sakar zuci har wani lokaci. Washi gari karfe tara na safe ya farka, bakin shi dauke da Ummu Mansurah, rike hannun Rumaisah tayi tana shafa kansa. "Kayi hakuri Allah da ya bamu ita ya amshi abin sa, kar ka." Kokarin tashi yayi ta ce mishi. "Auta kwanta ka huta " "Hatsari tayi ko ciwo tayi ta mutu?" Girgiza mishi kai tayi, "xan gaya maka amma sai ka nutsu" shigowar likitan ya sa ta motsa gefe, aka cigaba da duba shi, tsawon minti Talatin kafin likitan ya ce "a bashi wani abu, sannan kar a cika damun sa ya huta sosai" "in sha Allah babu me damun sa." Haka suka fita sai ga Ummi da yan gidan su Sadeeq. "Alhamdulillahi ya jikin sa." Sadeeq ya tambaya yana niman wuri ya zauna a kusa da shi. "Ummina ciwo Mansurah tayi?" "Amma auta baka ji likita ya ce ka huta ba." Lumshe idanusa yayi, "Maina rike shi ya shiga ban daki yayi wanka" haka Sadeeq ya taimaka masa, yayi wanka da alola, karfin hali yake amma bai ki yayi ta rusa kuka ba, haka suka fito ya gabatar da salollin da suke kansa. Tunda ya idar da sallah yake sauke ajiyar zuciya, idanun shi sun yi jajjajur. Jijjiyar goshinsa sun firfito rad'a-rad'a. Jikin shi sai rawa yake, dafa hannun sa Ummi tayi "Allah da ya bamu shi ya amshe ta, na meye tashin hankalin? Nasan kana sonta amma ba yana nufin zaka haukace akan ta bane. Tafi bukatar Addu'oin mu sama da tashin hankali ko kukan mu. Allah yasa dalilin haka. Don Allah kar ka kuma jifa kanka cikin wani hali" kura mata idanu yayi, kafin ya gyada kai yana jin kamar zuciyar shi zata fita. Wani irin tausayi kan sa yayi, sai a lokacin kome ya fara dawo Mishi tsawon wata uku da yayi. "Me ya same ta ta rasu, rashin lafiya tayi ko wani abu ne ya same ta? A'a ciwon cikin ne?" Hawaye ne ya zubo daga idanun Ummin ta ce. "ko daya, tsintar gawarta aka yi a bayan dakinka" mikewa yayi tsabar kidima , rike shi Sadeeq yayi. Ya durkusa a gaban Ummi har lokacin Sadeeq yana rike da shi, ya kifa kansa a kirjin shi. bata ga amfanin boye mishi ba, domin ko bata gaya mishi ba, ya gama zaman Nigeria balle kuma idan ta gaya masa ma dole ya bar ƙasar. "Zancen da nake gaya maka har an saka duk wanda ya ganka ya kashe ka, amma an janye kayi hakuri gobe zaka bar kasar domin nasa an gama maka kome sai tafiya." D'ago kai yayi idanun shi sunyi wani irin kankancewa. "Kina tsammanin dan ya saka a kashe ni zan tafi ne? Sai na nime duk wanda yake da hannu a mutuwar Mansurah ba zan barta jinin ta ya salwanta ba" ya fada yana mikewa. "Ba zaka tab'a zuwa ba, mu wuce na kaika lagos ka bar kasar nan a idanuna " ta fada tana niman fita, da sauri ya rike hannunta, yana haki. "Don Allah ki bar ni nayi facing shi please " yadda ta ga iyakancin kokarin sa na hana hawaye zuba daga idanunsu, ta fahimci he was mad, babu amfanin hana shi ya je din tunda yasan ba bar sa za ayi ya shiga cikin gidan ba. Don haka ta fita, zuwa tayi ta nima mishi sallama, and tayi alkawarin kare jinin shi da rayuwar sa. Haka kuwa suka basu sallama, daga nan ko Binji bai kuma tunawa ba, domin airport suka wuce. Sadeeq yana rike da shi ya ce mishi. "Me yasa ba zaka yiwa Sa'ade good bye ba" wani irin jiri ne ya nime zubda shi, yayi maza ya rike Sadeeq yana numfashi. "Ka ce mata zan zo" "when?" Girgiza kai yayi yana faɗin "Ban sani ba, ban san Yaushe ba, amma zan dawo ka gaya mata tayi karatu sosai, a duk inda nake ina kallonta." Daga haka yayi shiru, har lokacin tafiyar su yayi. Suka wuce cike da kewar juna, shi da Sadeeq. After few hours suka sauka a garin kwara, daga nan aka wuce da su har gida, sai dai abin takaici tun basu kai ga isa kofar get din ba, aka hana shi shiga masarautar. Haka su Ummi suka shiga masarautar babu shi, yana tsaye a bakin kofar gidan anan yayi Sallah azhar da la'asar, magariba a wurin bai matsa ba. Abinci ma daga gidan Ummul Aymana aka kawo mishi, wasa wasa har dare yana wurin a zaune, babu tsoro a ran sa ko fuskar shi. Sai bayan isha, Ummin su ta fito kana ganinta kasan tayi kuka har ta godewa Allah, ta zo inda yake ta ce mishi. "Mahaifin ku ba zai saurare ka ba, ka tashi maza na raka ka, gidan Ummu Aymana ka kwaka gobe ka wuce England" a hankali ya mike, Zuwairah da Jalilah suka kwashe kayan abinciin, suka nufi wurin mota da su. Har gidan Aymana suka kai sa, dakyar Ummi ta bar gidan, ko da bata gaya masa ba yasan sun sha rigima kafin ta fito. Koda ta koma ta sami Sultan Abdulrahman yana jiranta da bala'i, duk abin da yake bata magana, amma wannan karon tayi abin da ya bashi mamaki domin tsaf ta tsaya ta wanke shi, sannan ta bar shi ta gaji da abin da yake mata na rashin uziri, daren ranar bata yi barci ba, abin mamaki yadda zaka fahimci akwai muguwar sarkakiya a cikin masarautar, a daren ranar aka kai hari gidan Ummu Aymana, Allah yasa mijinta soja ne, kuma gidan akwai securitys da manya manyan police dog, sai dai anyi musayan wuta, tare da raunata wani soja, faruwan al'amarin ya tashi kan Sultan shi kansa tsoron al'amarin yasa babu shiri a wayewar gari ranar ya saka aka tura Abuturab England wurin yan uwansa, tare da rakiyar Zuwairah da Jalilah, aka bar Ummi da Mama hajja da Umma suwaiba da Hidaya, duk su din bayi ne a cikin masarautar, Ummi bata samu nutsuwa ba, sai da ta ga Abuturab ya shiga cikin jirgi sannan ta sauke ajiyar zuciya, ta san ya tsira daga sharrin masu kulle-kulle.
**
A hankali rayuwar makaranta ya zama jikin yan mata uku, inda gefe guda Sadeeq bai baya mata sakon Abuturab ba, sai ma saka idanu da yayi a kan su. Yaran hudu Masha Allah, amma ta gefe guda Kubrah ta fi su shaidanci. Case dinta kuwa human rights sun dauki responsible ɗinta, inda suka maka Fa'iz a kotu, shi da Yayar sa, aka nimawa Salmah da Kubrah hakkinsu. Batun sata kuwa dukkan su sun san Kubrah na sata, sau dai suna kiyayye abin da zata dauka, rashin ji a cikin ta, kamar wacce ake kara mata shi. Sun fito shan iska kasacewar ana hutun public holiday, Sa'ade tana saman windown dakinsu, Husnah ta gefen tana wanke socks dinta. Sai tsaki take tana kwafa. Rahilah tana yanka tuwon madara da aka yi na jiya, domin dukkan su babu wanda ya ci, shi ne ta zubda miyar kubewa da aka yi, ta wanke ta ajiye musu, bayan ta gama, ta mike tare da daukar kofi ta wuce can kitchen, ta samo musu ruwan zafi, tana zuwa ta juye tuwon a cikin ruwan, ta rufe. Fitowa tayi ta dauki socks dinta da na Sa'ade, ta jika tana wankewa. Sai ga wata prefect, tana zuwa ta yi kwallo da bokitin Rahilah. Tsuru-tsuru suka yi, suna kallon ta, watsa hannu tayi cikin masifa tare da zagin su. Kallon juna suka yi, tayi ta bala'i tana zagin su, ku su dibo mata ruwa ko ta ci kutumar Ubansu. Zarar bokitin Kubrah tayi, bata ce kome ba, ta wuce dibo mata ruwan haka Rahilah da sa'ade. Suna isa burtsatsan, Kubrah ta wuce abinta baya ta ajiye bokitin, dajin cikin makarantar ta shiga, bishiyar da karara yake ta nufa, ta kuwa tsinko shi da dankwalinta, ta dawo, babu kowa a buhol ɗin, akan idanun su Sa'ade ta fasa kararan ta zuba a wurin, ta saka dukkan a cikin bokatayen, sannan ta daura musu dukkan su, nufi hostle tsakanin Rahilah da Sa'ade ba asan waye yafi wani tsoro ba, suna zuwa suka sauke juna, nuna musu toilet tayi suka kai ruwan, sannan suka koma dakin su, suka kwashe abinciin su, suka gudu. Domin sun san tabbas akwai Bidiri. Aikuwa Prefect din tana shiga ban daki, ta kwabe ita da Kawarta suka dauki ruwa suka fara cude jikin junan su. Sai da suka gama wanka tass, kaikayi ya ce salamu alaikum, tun a ban daki suke sosawa juna jiki, har suka fito, dake ana zafi, Bala'in tafi haka domin sai da suka yi ta watsi da towel dinsu, tashin hankali. Abinka da kurame ji kake ana "beebeee beeeebeee, baaaaa baaaa, aushhhhh" abinda suke fada kenan sai burgima suke kamar kan su zai fita, suna cikin haka Umma tazo. Nan ma sai da aka tafi har kitchen aka dibo manja da toka aka shafa musu. Dakyar kaikayin.ya tafi, ai kuwa suka sha alwashin zane su sa'ade, abin ka da yarinta. Da magariba suka dawo. Suna shigowa hostle din ana rufe kofar. Sai da suka zane yaran nan hankalin su ya kwanta. Dakyar suka shiga dakin su, Sa'ade nata kuka. Husnah ta ce musu. "Ya isa kuyi shiru, daga yau ba zaa kuma dukan mu ba, sai mun rama muma" kallon Kubrah tayi ta ce mata. "Ki shiga dakin Umma ki dauko mana jan bakinta, Ina da farin hoda" aikuwa ko rufe baki bata yi ba, Kubrah ta wuce dakin umma da take can wurin abinci a kitchen, ta dauko janbakin suka ajiye, sai da suka tafi masallaci, suka dawo dake ana zafi, haka suka dawo suka karbo abincin su, suka ci sannan suka bi sawun masu ƙwanciyar zafi, ana ta hira har aka yi shiru. Suka tashi baki dayan su, suka nufi dakin su, zanuwar gadon su, suka dauka kowaccen su, ta bude jikinta da hoda, bakin su suka bata da jan baki har fuskar su, sannan suja cire dankwalinsu gashin sa'ade da Husnah a kunce, Kubrah da bata da yawan gashin kitso ne akanta, sai Rahilah da aka mata kalaba, suka nufi hanyar dakin yan matan nan, yaran ko tsoron su yi gamo ba su yi ba, suka nufi window bayan dakin su. Suka shiga dakin. Iya kansu yana waje, dan tsiya suna zuwa daidai gadon Yarinyar me suna Zainaru, suka tsaya akanta, tare da tattabata. Bude idanu tayi taga mutane da fararren shiga, wani irin zufa ke zubo mata, jikin tana yana rawa. Ke Kubrah ta kama kukan Akuya. "Imeeeeeeeeeee!" Wani tsalle da Zainaru tayi sai gata a can gadon, a kuwa makafin da suke dakin sun yi kukan akuyar, Rahilah ta kama kukan kare "huuuuhuuu huhu" baki daya dakin ya hautsine da ihu, ganin sun firgita sai faduwa sune suna niman hanyar tsira, su ma suka wuce window da gudu suka koma dakin su, domin baki daya hostle din ya dauki ihu, musamman makafin da suke jin kukan kare da Akuya, tare da mage. Su Umma da wasu mata uku suka tashi kusan dalibai dayawa sun tashi a cikin su har da masu barnan aka je kallon abin da ya faru, Rahilah kasa rike dariyar tayi ganin yadda Prefect Zainaru take kerma, tana zabura........
[29/05, 5:42 pm] usmanlauratu71: Barin dakin sukayi, tare da dariyar mugunta kamar zasu kifa, asalin dariyar yaki tsayawa, musamman Rahilah da ta kasa barin dariyar har garin yayi tsit. Washi gari da asuban fari suka fara bin layin wanka, suna ganin ta fito suka cure wuri guda, kamar munafukai suna dariya kasa ƙasa cigaba da dariya, bayan sun shirya suka nufi dinning suka amshi abinci suka ci, sannan suka wuce makarantar. Haka Yaran nan suka gallabi Prefect duk da ana cin Ubansu amma haka bai saka sun daina fitina ba, sai ma kara kai mi da suke yi. Har lokacin visiting ya zagayo, babu Abuturab ga kowa na Sa'ade yazo amma babu shi, sai leke leke tana niman sa babu shi, sai Sadeeq da ya kawo mata kayan provision kamar yadda Abuturab din yake mata. Lokacin da ya kawo ya mika mata, kallon shi tayi tana motsa bakin ta, sannan ta amshi kayan tana kyakyafta idanu alamar hawaye ne zai zubo mata. Rike hannun shi tayi tana kara kallon shi. Dan dukawa yayi yana faɗin. "Yace zai zo ki jira shi" so take ta tambaye shi, ina ya tafi, amma ba halin haka, hawaye ne ya zubo mata. Ta share tana gyad'a kanta, ya labartawa su Zakaria abin da ya faru, sannan sun yi mishi fatan Alkhairi sosai.
***
A bangaren Hajiya Daulah zubwa Dr Sharif da dansa idanu, amma tsabar masifar bata iya saukewa akan su ba, sai akan Taufik da Afiyyah, kullum sai sun sha masifa, babu yadda ta iya dasu tunda haka likita ya ce. Har ta hakura haduwarta da Hajiya Nazirah, sai ga magana ya kuma dawowa sabo fil, wanda har maganar ta girma an fara zancen aure. Ko uban bata gayawa ba. Sai dai ta samu Kannen shi biyu kawu Nura da Laminu, suka shiga maganar suma dake munafukai ne bin bayan ta suka yi har sai aka kai sadakin shi da Sophia. Ranar Laraba. Yau ta kama monday, Dr Sharif yana gidan Aunty Fareedah. Shigowa dakin Aunty tayi cikin ladabi ta zauna a bakin gadon sa. Tana kallon shi, kamar bai manyan ta ba domin ya hadu da hutu da kulawa kamar ba shi ya haifi Abdul Hakim ba, "Madam kina kallon kyakyawan saurayi ne kar ka fita mata su kware min ko?" "Tabjam a wannan shekarun naka wacece kwailar ce zata iya da majinarka " ta fada tana dariya, "kuma haka ne, amma me ya kawo ki nasan kina kitchen ne?" Jim tayi tana kallon shi, kafin ta mike tare da ɗaukar links ta fara kokarin daura mishi a hannun rigar ya ce mata."kuma kika yi shiru" "hmm dama akan Abdul ne ashe kun kai sadakin shi?" Kura mata idanu yayi, cike da mamaki amma sai yayi ta maza ya ce mata. "Eh na manta ne ban gaya miki ba, amma mun kai." Ya fadi haka domin bayan son abin da zai tab'a mutuncinsa. Balle yadda matar sa ta rena na shi. "Allah ya sanya alkhairi" ",Amin Ya Allah Nagode sosai, muje ki ba ni abin karyawa." "Tow muje dama kai yake jira" haka suka fito yaba gaba tana baya har wurin zaman su, duk da yayi kokarin hàdiye abin da Hajiya tayi amma ya kasa manta wannan al'amarin. Har ya gama karyawa ya bar gidan. Ba ƙaramin danne bacin sa yayi ba, ya tafi wurin aiki daga nan ya wuce gidan Hajiya. Yana isa ya same ta a falo ita da Abdul ya zauna a kasa, kamar me niman gafara. "Ashe har an kai sadakin Babana?" Ya tambaye ta, ganin yadda tayi maganar so calm, a take jikinta yayi sanyi ta zuba mishi idanu. "Na zata ranka zai ɓaci ne?" Murmushi yayi wanda zaka fahimci kawai na karfin hali ne, "A'a ai da kai da kayan duk mallakar wuya ce, akan me zan yi fushi Allah ya nuna mana lokacin lafiya" "Amin Ya Allah" duk fada da zafin da yazo da shi sai gashi baki ɗaya yayi sanyi, domin yadda yaga Abdul din a gabanta sai yake ganin kamar idan yayi magana laifin kan Abdul zai sauka. Haka yasa gara ya barta tayi yadda take so, domin yasan do kile wata rana zata zo gabbar da dole sai magana. Dole akwai lokaci yanzu ba damar magana, a kyale ta tayi yadda take so, ba wai a hana ta ba tunda ba mamaki tana da nata dalilin da uzurin don haka ya mata uzuri tayi yadda take so, daga haka ya wuce dakin sa yayi abin da zai yi ya fito. Amma a matsayin shi na shugaba a gidan sa, ya dace tayi gaban ta kenan? Duk sai yaji kansa yayi wani irin girma, kawai bai ce kome ba, amma zai ajiye zancen har zuwa lokacin da ya dace ya mata magana. yana gama abin da ya kawo shi ya bar gidan, yana ganin yadda Abdul yake kallon sa. Duk sai ya bashi tausayi.
---
Kwara
Zuwa yanzu hankalin Badi'atul Noor ya kwanta, asalima kallon kowa take kar bata san me suke yi ba, tana kwance Mama Hajja ta shigo, cikin girmamawa ta ce mata. "Ranki shi dade, Sultan yana son ganin ki" bude idanu tayi tana kallon Mama Hajja. Murmushi tayi sannan ta ce mata. "Ki ce mishi ina barci" shiru tayi tana kallon kasa, duk da idanun ta a rufe, ta ce mata. "Ina sane ki tafi ki gaya mishi ina barci" "amma sultanah" "Ni nace ki gaya mishi ina barci" "shi kenan " ta juya ta fita har bangaren Sultan, duk mutanen gidan suna zaune, ta shiga cikin falon. "Allah ya baka nasara, tana barci " "Ko dai ta ce miki ki gaya mishi tana barci ne" "A'a Sultanate " shiru falon ya dauka, mikewa yayi zai fita Hajiya Mariya ta ce mishi. "Kuma zuwa zaka yi?" Banza yayi da ita. Ya bar falon, bai sake ya bi ta hanyar waje ba, ta hanyar baya ya bi har ɓangaren ta. Tana kwance a falon sama, da sallama ya shiga falon, kasa ƙasa ta amsa, a hankali yaji wani irin nutsuwa ya shige shi. Ga sanyi da dadin da ya cika ko'ina na falon. Ya zuba mata ido, ta zube sosai kamar ba ita ba. A hankali ya ji kamar wani abu yana mintsinin shi, "Badi'atul" bude ido tayi ta zuba mishi. "Me yasa na kira kika saka tayi karya?" " Ba karya tayi ba, nice nace ta gaya maka ina barci laifi ne?" Zama yayi ya kura mata idanu, "but" "kawai bana son magana ne" "but why?" "Kawai bana son magana ne" "akan wani hujja?" Zama tayi sosai tana hamma, ta ce mishi. "Kawai" "tow laifin me na miki? Ban san meye nayi ba, kike min haka na san dai nayi kokarin adalci ne, Yarana kuwa nayi haka ne domin su samu salama bayan nan me kike so nayi miki? Kin haramta min kanki, wannan a ajiye shi a gefe, kin haramta min duk wani abu me muhimmanci don Allah me kike so nayi!" Wani irin kallo ta mishi kafin ta ce mishi. "Yanzu kai ko kunya baka ji ba , kake irin wannan zancen? Hmm ku dai maza baku da kunya wallahi" kura mata idanu yayi, "ok kina son na cigaba da niman hakkina da karfi ne," hannayen ta ta kai baya ta duniya dogare tana kallon shi. "Kuma dake ni yarinya ce sai na zuba maka idanu ka turmusa. Allah ya baka lafiya." "Ciwo nake da kike faɗin Allah ya bani lafiya?" "Kafi kama da me jinya ai, kai baka san ka girma ba ne?" "Eh amma ba shi ya kawo ni ba, nazo magana ne akan me yasa kike disrespect dina?" Kallon shi tayi baki sake. "Kasan me? Idan rigima kake ji ka tafi akwai masu iya taya ka, ni bani da lokacin magana da kai" "kenan kin mai dani mahaukaci kika mai dani?" "An zo wurin " ta fada tana gyara zama, "kamar ya an zo wurin?" Ya kuma tambayarta. "Ai ni lokacin da nake binka ina rokon ka kyale min Yaro bai da lafiya ya shigo ka sauraren Ni? Asalima share ni kayi don haka zaka iya tafiya, kuma ina ganin zancen auren mun tara shi a gefe sai bayan binciken abin da ya faru ya kammala zaka zauna muyi magana irin ta gaskiya. Amma yanzu ni ba matar ka ba ne" "wallahi baki isa ba, baki isa ba nace miki " " na isa wallahi na isa nayi tsaroro, kuma kana ji kana gani idan gaskiya tayi halin halin ta zan buga zawarci me tsada nayi aure ba bar maka gidan ka" kaman wanda ta yarfa mishi wuta haka yaji maganar banbarakwai, "lallai baki da hankali na kuma yarda yau baki da hankali sam baki san me ya dace ki fada ba, ko nace baki da lissafi, me lissafi baya abin da kike yi, aure kuwa yanzu aka fara domin wallahi ba zan tab'a rabuwa da ke ba." Fahimtar maganar rabuwar ya bata mishi rai, ta kuwa shiga maimaitawa aure zata yi har da zawarawa kuma kamar yadda Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce tayi idda a ɗakinta haka zata yi, bawan Allah nan ya shiga bala'i kamar zai rufe ta da duka...
Tsuntuwa=₦400
Ashraf=₦800
Sanin Gaibu=1000
08130269641
[30/05, 11:21 am] usmanlauratu71: Haka Ummi ta gama zurma shi ya bar sashinta a fusace, kamar zai hada sama da kasa ya tashi, koda ya isa bangaren sa wuce su yayi. Da idanu suka bishi domin sun san ya fita lafiya, gashi ya dawo a fusace, kenan ta bata mishi rai bari ya zo ya sauke kuncin sa a kan sa, wanda haka ya b'atawa Sultanate rai ta mike itama ta fita, don bakar jaraba, ta tsaya iya wurin ta mana, a'a kawai matar nan ta nufi bangaren Sultanah, tun daga bakin kofar take ruwan Bala'i da masifa, sultanah tana fara jin hayaniyar ta, dole ta sauko tana faɗin."Allah ya baki lafiya da nisan kwana an yi miki wani abu ne?" Kamar wacce aka gaya mata magana, ta shiga masifa. "Ki ce na mutu kawai, meye Abdurrhmanu ya miki?" Tab'e baki tayi ta nufi wurin zama tana faɗin. "Babu abin da ya haɗa mu, kawai yana jin rikici ne a ransa" sake baki Sultanate tayi tana faɗin. "Kenan haka kawai yake kunci bayan nan yazo kika dagula mishi lissafi, Badi'atul kiji tsoron Allah fa" wani shan mur Ummi tayi tana fadin. "Ki tambaye shi meye nayi mishi da zai kai kara na wurin? Lallai ma zai zo ya same ni?" Zaro idanu Sultanate tayi tana kara rike sandarta tace mata. "Me zaki mishi? Iyeee me zaki mishi nace?" Shiru tayi bata ce mata uffan ba, domin bata jin tayi iya magana. "Idan ma saboda Yaranki kike haka to ki sani sun tafi kenan gara su zauna a can, ina dalili ke ranki ke kadai kin haifi Yara zama uku, kowa a gidan nan Yaransa maza daya biyu, ke da an kyale ki wasu Mazan zaki haifa bayan matan nan tow wallahi ahir dinki " "Sultanate kenan saboda na haifi Yara maza shi yasa aka watsa min kan su?" Shiru Sultanate tayi tana nazarin katobarar da tayi, a hankali ta ce ."Eh tow, ga zahiri tunda kin saka shi a gaba idan ya mutu fa?" Karewa Sultanate kallo tayi tabbas sakon daga kasar zuciyar ta ne, ba daga saman bakinta yake ba. "Kwanan shi ne ya kare, hmm" domin nade taburman kunyar ta da hauka, ai kuwa ta hau masifa da bala'i, kamar zata daki sultanan, ita dai idanu ya zuba musu har ta gama masifar ta, ta bar gidan. Tana fita ta kira Maina, sun jima suna magana akan Abuturab ya gaya mata har yanzu jikin yaki dad'i, ya ki kuma a kai shi asibiti yana kwane a gida da ciwon. "Idan ka koma ka bashi wayar muyi magana" "in sha Allah Ummin mu" Duk sai taji bata jin wani dadi domin bata san yadda suke bashi kulawa ba, da tana kusa ne zata fi bashi kulawa yadda ya da ce, sama da yadda suke ba shi. Ko ya yake oho? Ta fada a ranta tana tagumi. Kasa hakuri tayi ta kira shukriya matar Maina din tasan tana gida. "Barka Ummin mu!" "Yawwa shukriya, ya jikin Baba karami?" "Alhamdulillahi, Ummin mu yaki zuwa asibiti wallahi" ta fada a dame. "Ok kai mishi wayar yana ina ne ma tukun?" "Yana dakin da, tare da Latifah yar kawu Khamal " "shi kenan kai mishi " kashe wayar tayi, can ta kuma kiran su. "Auta na!" "Ummina!" Ya kira sunan ta. "Ummi mutuwa zan yi?" "In sha Allah ba zaka mutu ba, sai naga Ƴaran ka. Kamar yadda naga na yan uwanka." "Ummina me yasa suka kashe min Babe?" "Kwananta ne ya ƙare? Kayi hakuri sai kace ba namiji ba, kana son ka nuna cewa ba kai Allah bai isa yayi ikon sa bane? Don Allah ka hakura akwai abubuwa da ya dace ka sani ban gaya maka ba, gudun haka gara ka daura damara domin isa inda ya dace. Allah ya muku albarka." "Amin Ya Allah " ya faɗa, daga nan ta daura da nasiha, tare da jan shi da hira. Kamar yadda take son haka yayi ta amsa mata, yana kara tabbatar mata da in sha Allah zai tafi asibitin. Da haka suka yi sallama. Ta zubawa kofar ɗakinta idanu, Sultan ne tsaye kamar ba shi ne ya bar dakin ba minti arba'in da suka wuce ba, ga shi ya kuma dawowa. Mikewa zata yi wuce bakin daki ya riko hannunta. "Me yasa ba zaki tsaya muyi tsayayya magana ba.?" Tab'e baki tayi sannan ta ce mishi. "A gani na, ai mun wuce zancen nan ko? Tow kuwa babu amfanin dawo da shi baya " "amma meye gaskiyar zaki kashe aurenki?" Galala tayi tana kallon shi. "Lallai ma akan wannan ka dawo dama? Hmm" ta wuce bakin daki ta saka key abinta a ranta tana faɗin 'aiki ne bai ishe ka, da ya ishe ka ba zaka zo tambaya ba, Allah na tuba ko mutuwa kayi ai na gama aure balle da ranka, kaji yadda ake ji ne kai ma'
**
Birnin London.
A hankali ya fito Latifah tana rike da hannunsa, gefen shi Saraki ne. Ya mishi duk abin da zai yi na ganin likita, Na'ima matar Saraki na gefe tana mishi sannu. Kamar su mai da shi cikin su, duk wani zirga-zirga Saraki yayi, koda ya samu ganin likitan bashi gado suka yi aka shi kula da shi kamar me. A hankali sai da ya kwashe kwana biyar, ana kula da shi kafin suka sallame shi, ya dawo gida. Bai yarda da kowa ba, sai matan Yayunsa suma don suna Yayun Mansurah ne, a wannan karon ko Zuwairah kin bata fuskar yayi ya mai sa hankalin shi akan abin da yake gaban sa. Sai dai ya sauya sosai, idan ba a gaban ummin sa ba, ya ajiye wannan shegen shagwab'ar, ya juye ya koma namiji sak. Tun lokacin da yaji labarin mutuwar Mansurah baki daya ko hira haka bayi da lokacin yi da kowa sai ma Ƴaran Yayunsa idan suka ga ya bata shiru zasu biyo shi daki su dame shi da surutu, haka zai zuba musu idanu har su gama. Ya sakawa kansa shirun dole, musamman idan ya tuna yadda mahaifin su ya ki amincewa Ya bar shi ya shiga cikin gidan su, wannan abin yana burning dinsa very crazy, zai yi wuya ka fahimci yadda yaƙe. Tun tasowar sa ake son hada shi da mahaifinsa amma ba a cikin nasarar haka ba, sai akan mutuwar a bar kaunar sa, idan ka kalli fuskar shi kamar bai tab'a dariya ba, ba hmm ba uhmmm. Ai kuwa wani irin yanayi ne mara daɗi ga shiru kamar kurma, kai baki daya Abuturab ya masifar sauyawa wanda hakan ya sa dole yan uwan suka kira mahaifiyar su suka gaya mata halin da ake ciki, a cikin kasa da wata guda. Ya zama sai a hankali, jin haka yasa ta d'aga hankalin ta, domin tsoron kar kunci yasa shi hàdiye zuciyar shi ya mutu, sai da suka kai ruwa rana kafin Sultan ya barta tazo, tare da drive uncle Khamil suka tafi daukota, lokacin da ta iso cikin babban ma shigar, baza idanu tayi tana nimansa, cikin ikon Allah ya d'ago mata hannu. Lokacin da ta ganshi sai da jikinta yayi sanyi, da sauri ya nufe ta. Tare da amso kayanta yana kallon ta. "Abuturab kashe kanka zaka yi ne? " Ta fada tana kara mamakin sa. Wato baki daya tsoro ya bata, bata tab'a zatan al'amarin ya kai har haka ba, sai yau domin duk gaya mata da Maina ko Saraki suke gani take kawai sun kasa fahimtar shi ne, sai yau da ta ganshi da Idanunta. Jikinta yayi sanyi sosai haka suka nufi har gida, idan tayi mishi magana sai dai yayi mata yake, haka suka isa gidan. Shi ya kwashe kayan. Ita can part din Dan uwanta ta sauka anan tayi wanka ta huta can sai ga su Zawairah da Jalilah, Matar Khamal dake irin mutanen nan ne masu wuyar sha'ani, bata yarda da kowa ba sai danginta bata sake da su Zuwairah ba, ganin yadda suke mata sintiri tacewa Ummin su ."Badi'atul nifa mahadimanki wallahi haka kawai ban.yarda da su ba, tsoro suke bani." Dariya Ummi tayi tana faɗin. "Tun rasuwar Khatoon kika kasa yarda da hadimai tow idan Allah yasa ya Khamal zai zama.sarki ya zaki yi hala turawa zaki kwaso mana a gida?" Dariya ta saka ta ce mata. "Ni Kudirat ta ya zan kwaso turawa, kawai jini na ne yaki yarda da duk wani wanda zai fito daga cikin gidan sarautar nan, tun bayan mutuwar Khatoon nake jin a jikina basu da gaskiya duk wanda yake cikin masarautar nan " shigowar Abuturab yasa ta zuba mishi idanu."Son kaga yadda ka tara kasumba kuwa? Don Allah jeka a maka askin ka dawo kai ma ai zaka huta da wannan yanayin." "Yes Ma " ha fada yana barin falon. "Kudirat haka ya koma?" "Eh baki gani ba, kaf idan ya akwai wanda yake kulawa tow na miki karya domin duk nace na Mimi haka ta bar sa, baya magana daga Yes sai Ok, iya su ke hada shi da yan uwansa, don ko shekaranjiya sai da Daddy ya mishi fada, na dai ji suna cewa zai koma makaranta, idan ya shiga cikin jama'a dai dan samu karfin fada da kansa domin kuwa a halin yanzu ya kasa fada da kansa ne, zuciyar shi taci karfin shi ne da zai iya yaki da ita tow da wasu abubuwan zasu yi sauki. "Gani nake kamar ba Abuturab dina ba, ya sauya sosai." "Ki cigaba da addu'a domin shi yake bukata wannan shirun na shi, ai ba kanta" inji Hajiya Kudirat, "haka ne kan zan kara kaimi kafin na koma zamu tafi Saudiya da shi ko zai samu sauki wasu abubuwan in sha Allah." Abinci taci kaɗan, can kuwa sai gashi ya kuma shigowa fuskar tayi kyau. Zama yayi ta zubo mishi abinci. "Ummi i'm ok" watsa mishi harara tayi. "Oya bude baƙi, ba dole ka lalace ba, babu walwla babu cin abinci mutum ya kare kamar kudin guzuri." Ta shiga bashi abinci yana ci, tana rarrashinsa. Shigowa Latifah tayi ta same su a haka, sai ta ji sun masifar burgeta, ta zauna me bude bakinta itama ana saka mata abincin. Duk da yamma tayi sai da Ummi ta saka su a gaba suka fita. Abubuwan da suke damun sa, har da nauyin Sa'ade da bai sauke ba, gani yake bai kyauta ba, da bai nime ta ba bai gaya mata gaskiya waye shi ba, ga Mansurah ta tafi ta bar shi, yanzu yasan tazarar da take tsakanin su. Ba zai bata damar ganin shi ba, na cewa zai dawo. A hankali ya fara sake jikinsa domin ummi, amma ba dan kansa ba. Duk da haka sai da Ummi ta shirya mishi ganin likita na musamman. Ta kai shi. Likitan ya dube shi bayan sun gaisa da junan su. Sannan ya ce mishi. "Mr Ali. Meke damun ka?" Shiru yayi yana kallon window kasancewar su suna lokacin zafi ne . "Mr Ali ina jinka?" Kallon Likitan yayi sannan ya ce mishi. "Babu kome!" "Babu kome gashi Mahaifiyar ka ce ta kawo ka." "Eh babu kome Dr" "ka tab'a shiga mugun yanayi ne a rayuwar ka? Ko ka tab'a jin babu dad'i a wani abu da ya faru da kai?" Murmushi yake yayi sannan ya ce mishi. "Babu bana jin dadin rayuwa ne kawai" "kamar ya?" Shiru yayi yana cup na coffee da aka ba shi. "Tun ina yaro na taso tare da ita ne, ban tab'a barin wani abu ya cutar da ita ba, sai da aka mana baiko ta rasu, shi ne nake jin babu dad'i " kallon shi Dr din yayi. "Kenan mutuwar ta shi ya saka ka shiga kunci da damuwa?" "Eh tow bana ce ba, amma kuma ina kewar ta." "Amma addinin musulunci ya baku wasu abubuwan da matukar naku ya mutu kuna mishi ai, ko kai baka yi ne?" D'ago kai yayi yana kallon likitan, sannan ya yi murmushin dole ya ce. "Dole ne wannan." "Tow me yasa ba ka manta da ita ka nime auren wata ba?" Kurban shayi yayi sannan ya ce. "Niman auren wata ba sauki, domin sai ka fara jin qarfin yin soyayya kafin har akai da zancen aure, kaga kenan duk yadda zaka yi dole sai an dauki wani mataki na rayuwa kafin a cimma wani mafita " ........ Yau kan na sallame ku, idan kuka min comments na kuma yin wani da yamma idan babu ku huta na huta.🤣🙄🚶
08130269641
[31/05, 9:04 am] usmanlauratu71: "Amma ai da ka jarabawa, idan baka manta ba, akwai mutanen da suke dakon jiran haka a tare da kai, cikin su har da Mahaifayar ka, ko kafi son ganin ta cikin kunci da damuwa ne?" Murmushi yayi yana kallon ruwan coffee ɗin ya ce. "Ba ni da burin saka su damuwa, sai dai zuciyata tayi nisan da ba zata ji kira ba, idan lokaci yayi kome zai sauya. Kome zai koma muhallin sa na ainihi, amma yanzu bani da karsashin da zan iya tunkarar mace domin nasan daga ni har ita wahalar da kan mu zamu yi toh me zai saka mu bawa juna wahala." Shiru likitan yayi kafin ya ce mishi. "Bayan yarinyar da ka rasu ka taba haduwa da mace?" Shiru yayi kafin ya girgiza kai, "Ban hadu da wata mace ba, sai wata yarinya karama da na tsaya muka kai ta makarantar nakasassu." Kallon shi likitan yayi. "Yarinya kuma? Zata kai shekaru nawa?" Ajiye kofin yayi yana faɗin. "Ka gama ko akwai saura?" Yadda ya mike sai ya bawa Likitan dariya, yayi murmushi sannan ya mika mishi hannu suka kara musabaha suka fito, suna kara tattaunawa, sannan likitan ya kalle shi na wani lokaci kafin ya ce. "Baka da matsalar kome, matukar ba bad nightmares kake ba, sannan damuwar ka bata da yawan da zata hana barci, kewar ta ne bai fita a ranka ba. Amma yana da kyau kana dan fita shan iska, kamar kallon kwallon, yan tafiye-tafiye yawon buɗe ido, ko zuwa bakin beach, idan ta kama shiga kungiyoyin agaji da taimako yana da kyau domin zai rage maka damuwar ka, zaka ga kamar kai ba damuwar ce da kai ba, akwai wad'ada nasu tafi naka, ka kula sosai idan kasamu hali ka kara tuntubana." "Ok " ya fada bayan ya fito, Ummi da Latifah ne zaune suna jiransa. "Ka fito auta?" "Eh ummina " "Ummin mu dai ko Ummi?" Murmushi tayi, sannan ta wuce wurin likitan, suka wuce cikin office din shi. "Sannu Ma, Ali bai da matsalar ko me, sai ta kewar yarinyar da ta rasu, sannan a hiran da muka yi da shi, akwai wata Yarinyar da ya hadu da ita, ina ga ba mamaki idan da zai zauna kusa da ita tow walwalar shi zata dawo sosai" "wacece ita haka? Kuma me yasa ka fadi haka?" Gyara zama likitan yayi, sannan ya a labarta mata yadda suka yi da Abuturab, shiru tayi, kafin ta ce mishi. "Yanzu babu maganin da za a daura shi a kai?" "Babu, shi da kansa zai bawa kansa magani, domin yakin ba na kowa ba ne na kansa ne, shi da kasan zai yaki kansa matukar ana son ya dawo daidai sai ya tsaya tsayin daka ya bawa kansa kome, babu wanda ya isa mishi wannan fadar kin fahimta, ko wacce yarinyar da ya sako a zancen shi ba wai ya sako don yana da wani abu da ita ba ne, asalima kamar yana jin babu dad'i ya tafi ya bar ta, ba tare da ya ce mata good bye ba. Amma idan ya kasance haka ne zai iya nimanta har ya mata sallama." "Na gode sosai likita, bayan bayan nan babu wani abu?" "Eh tow na gaya mishi abubuwan da ya dace yayi domin samun sauƙin shi." Anan ya zayyano mata abubuwan da ya dace su. Tayi mishi godiya suka bar asibitin, tun daga lokacin Ummi ta lashi takobin ba zata bar shi ba, sai ta saka shi ya daina kuncin nan. Kuma haka ne, haka suka ta cigaba da tafiya da shi, haka ta dauke shi su je nan, su je can. Idan ta kama kallon kwallo ne a tare suke tafiya, a cikin wannan yanayin suka tafi umra, babu laifi ya sake sosai, sai dai rashin magana ne kamar ba shi ba, duk da yadda Latifa take makale mishi, kuma itama Ummi ta yaba da halin ta, yasa duk inda zasu tana me janyo hankalin yarinyar, tana dakyau ga hankali uwa Uba bata da hayaniya kamar na sauran yan matan, kuma sai ta ga dacewar su da shi Abuturab din domin yarinyar bata da fitina da kiriniya. Haka suka cigaba da mishi addu'a da kulawar da suke ba shi ba na wasa bane, haka yasa shi dole yake sakewa ko dan Umminsu. A can gida Nigeria kuwa, tun Sultan yana dauke kai idan aka mishi maganar abin da Sultanah Badi'atul Noor tayi har ya kasa hakuri, domin dai tunda ta bar musu gidan tace kowa ya ci kansa, yake cikin damuwa, duk abin da za ayi baya burge shi, asalima yayi ta fada kenan, sun rena shi sun biyewa Badi'atul Noor suna mishi abin da ransu yaso, don haka kar ya ga kafar kowa a bangaren shi, yau kusan sati hudu ake nima da tafiyar ta, yana zaune shi kadai a dakinsa. Ya bude idanun ya zubawa wani karamin hoton ta idanu da yake gefen gadonsa idanu. Hoton tayi shi tun da kuruciyar ta ne, don haka ya saka shi a wannan wurin domin dakin bai zama a cikin sa, kuma ba a cikin yake kwana da matan shi ba. Yana son Badi'atul Noor matsalar ta cika rashin kunya ne, kuma tun can baya haka take, wayar shi ya janyo sha biyu saura, kiran layinta tayi a kashe don Allah ya kira Layin Maina ya same shi. "Assalamu alaikum, Barka da dare Abba" "wa'alaikumunsalam Barka dai, amma kunyi hankali da kuka rike min mata ta? Akwai adalci a cikin wannan al'amarin? Fisabilillah idan bata yi tunanin dawowa ba, ku ba zaku tuna mata zaman aure take ba, sai ta zauna a tsakanin ku tana kalle muku mata idan ba a muku daidai ba, ta hau masifa an mallake mata Yara?" Yadda yake fada zaka rantse da Allah wani abu aka mishi, yana gama fadar Maina ya bashi hakuri, yana tari. "Mura ya kama ka baka je asibiti ba?" "Eh amma zanje in sha Allah, bai wani jima da kama ni ba " da haka sukayi sallama, washi gari da safe, Maina ya da ya shiga cikin gidan Kawunsu ya ce mata. "Ummina yaushe zaki koma gida ne?" Kallon shi tayi kafin ta haɗe rai ta ce. "Abban ku ya kira ka ne?" Shiga nutsuwar shi yayi sannan ya ce mata. "Eh ki kira shi" nan ma ya fara tarin, "yaushe mura ya kamaka, naga zafi ake yi?" "Eh zan je asibiti na ga likita" "Allah ya baka lafiya" "Amin Ya Allah, zan tafi wurin aiki" "Allah ya bada abin da aka je nima, ya kuma bada sa'a" "Allahumma Amin." Haka ya bar gidan yana girmama rigimar da za ayi tsakanin iyayen su, bayan fitar shi ta kira Layin Sultan. Dauka yayi cikin niman rigima ya fara sauke mata halin uwar shi, sai da ya gama jidalin shi , ta ce mishi. "Kasan Allah ka kuma sako min Yarana cikin maganar mu sai dai wata ba ni ba, ka tab'a jin labarin mace ta sake namiji? Tow a kaina za a fara, wallahi ka fita Idanuna na rufe ba zan dawo ba, da kake cewa matan Yarana zan saka musu ido waye ya gaya maka ina da wannan halin, babu abin da ya dame ni da su, idan matan su, sun so su dafa su babu abin da ya dame ni. Kai da kake da mata me zaka yi da akwala irina. Aure kuma idan nace bana yi babu me min dole ka fahimta?" "Amma Badi'atul Noor fisabilillahi tun tuni baki yi yaji ko fushi ba, sai yanzu da jikoki suka miki kawanya? Na zata idan nayi kuskure zaki zauna dani a haka ne, don Allah ki dawo dakin ki ina bukatar ganin ki a haka, bana jin dadin rayuwata." Baki daya yadda yake kalaman in romantic da rarrashi yasa jikinta yayi sanyi ya ce mata. "idan ma ni kike son gani nazo daukar ki, in sha Allah jibi ina hanyar zuwa, don Allah kar ki ce min a'a, kin ji Nur" shiru tayi kamar zata ce mishi ba sai ya zo ba, amma ta nunawa uwar shi da Matan shi ita fa mijin su ya dama, shi yasa suke bin shi, ita kuma Sultanate danta babu yadda zata yi da shi Allah ya kulla sai tayi hakuri. "Ok kazo ka ɗauke ni" "da gaske?" Ya tambaye ta? "Eh da gaske mana, na tab'a maka wasa ne?"
"In Sha Allah zaki ganni." Ya fada cikin zumudi, ai dama ba cewa tayi bata son shi ba, rashin fahimta ce kawai da kuma shiga makiya a tsakanin su yake haifar musu da rashin zaman lafiya, da za a tsaga jikinta jinin shi yake yawo lungu da sakon jikinsa, bata jin zata yi butulci akan zaman su, tunda kome ka gani mukaddari ne, daga rabbil alamina, sannan zata iya daukar haka a matsayin kaddaran ta ce, babu wani abu da zata iya sauyawa akan rayuwar ta ko na Yaranta, shi yasa take kara zage damtse sosai wurin tsayawa Yaranta da shi kansa Sultan din. Koda Sultan din ya bayyana tafiyar shi London, abin bawa Kowa mamaki duba da yadda Badi'atul Noor tayi tafiyar dutse a hannun riga yasa baki daya haushi ya kama Mariya da Badariyyah uwa Uba Turai ai gani suke su da basu kai ta girma ba, baya wannan azarbabbin balle ita da ta girma, wani irin munafikin jiki ne da ita wallahi baya nuna girman ta, kai ko irin tumbin nan bata da shi balle har ka ga alamar girmanta, a iya gashin kanta ne zaka fahimci haka da muryanta amma bayan haka gyara jikinta take ba Bala'in, bata wasa da gyaran jiki hatta cimarta ba irin tasu bane, ba kome take zubawa cikin ta ba, wani abin da basu sani ba, har abin motsa jiki tana da shi a ɓangarenta, su kuwa kowa ka gan shi ya zama rusheshe. Kuma su masu aiki ke kula da cikin su, ita kuwa taki yarda da haka. Ita ke sarrafa kome nata shi yasa take kara haukata Sultan babu abin da ya dame ta. Haka suka gama ihun su, itama Sultanate ta gama mitar ta, ta hakura tunda bata da yadda ta iya, sai dai tana kan bakanta har abada Yaran Badi'atul Noor ba zasu tab'a zama cikin masarautar ba, domin ta lura baki daya so suke su raba danta da muka mishi sa, ita ba zata ma iya daukar wannan ganganci ba, zata ci mutuncin su daga Sultan din har Badi'atul Noor tunda ta lura yarinyar bata da mutunci so take kimar shi ta b'are. Zata yi maganin ta.
***
Wannan karon visiting din ya zo babu dad'i, duk kiriniyar Sa'ade daga ranar tazo zata koma wani kalar tausayi, ga Sadeeq shima an dauke shi a Sokoto, ya koma gombe duk sai ta koma kamar mareniya. Babu Abuturab babu Sadeeq, kallon yan uwanta maza da mata tayi, tana son tambayar su Inna amma bata san yadda zata fahimta ba, riko hannun Yusuf tayi tana kai hannunta goshi, "me yasa innar mu bata zo ba?" ........ "Muna cikin rashin wuta ayi maneji" Top-notch 08130269641
[01/06, 4:36 pm] usmanlauratu71: 30807
A haka harsu ya faru a lokacin domin Rahilah kuka tayi ta musu ba zata tafi gida ba, da a zava barta tow da ta zauna a makarantar, amma babu hali. Duk da sauran na murnan komawa gida amma ban da ita, ganin yadda take takure ne yasa Sa'ade itama shiga cikin damuwa, domin ko da ta tambaye ta meke damunta. Cewa tayi babu kome, har suka gama jarabawa, baka gane kanta. Kwanakin da suka biyo baya kawai, suna tare ne amma babu dad'i. Kamar an musu mutuwa, ranar da zasu yi hutu kuwa kwana suka yi suna hira. Washi gari suna cancad'a kwalliya aka zo aka ɗauki kowa, Sa'ade da Rahilah karshe, shi yasa da aka zo daukar ta, taki tana son ta ga tafiyar Rahilah. Haka kuwa ya faru, wurin karfe biyu na rana aka zo daukar ta, suna rike da hannun juna, haka suka yi ta kuka. Dakyar aka raba su. Sannan suka tafi cike da kewar junan su...
***
Abdul Hakim.
Biki budiri bured'ed'e,, anyi bikin da ba a tab'a yi ba, domin Ƴaran iyayen su manyan ne masu kumbar susa. Anyi wasa da dukiya kamar ba a aso. Anyi barna da almubazzaranci, sai dai muyi fatan Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a dayyiba. A bangaren ango kuwa babu abin da saka ce ya karu da shi a auren sai ciwon kai da kuma barazanar da ciwon shi yake kan yi na alamar zai tashi. Haka ya wuce gidan shi da yake bayan gidan Hajiyar shi. Anan suka tare, kullum Afiyyah da Taufiq suna gidan. Tun bikin da Aunty Faridah tazo, taga irin matar da aka aura mishi sam yarinyar bata mata ba, domin tana da Bala'in reni da rawan kai don ko da aka ce mata ga matar Babansa ta zo, wani kallon shekeke ta mata, haka yasa baki ɗaya take tausayin rayuwar Abdul din irin matar da uwar shi take so kenan, bayan biki da kwanaki ya kaita gidan Aunty Fareedah, ba laifi ta samu tarba na musamman, har kunya sai da ya kama yarinyar nan domin yadda ake mutunta kuwa. Daga nan gidan Iyayenta ya kaita. Har zuwa lokacin babu wani abu da zata ce na aure ya shiga tsakanin su, sai ma ƙara lalacewa hakan domin tsakanin su ina kwana, baya iya kome asalima baya dawowa gidan akan lokaci koda ya dawo ba zai shiga ba. Haka ya faru ne sakamakon shigar da take yi a gidan, idan ya ce zai dauka tow zai iya mutuwa, a cikin kwanakin akwai abin al'ajabi da ya faru, ya fito wanka ta shigo dakin. Duk da ya so kauce Mata. Amma dake yarinyar wayo da ita, haka ta saka shi a gaba bai san yadda aka yi ya biye mata ba. Sai da yaji kamar ana zare numfashin da daga jikin shi, saboda yana kokarin motsa jikin sa ya sarrafa amma abin yaci tura ƙarshe suma yayi a wurin, faruwar haka yasa ta nufar gidan Hajiya ta gaya mata suka fito aka kai shi asibitin, dalilin wannan yanayin yasa dole Hajiya ta dawo da Sophia gidan ta, don a yadda likita ya mata bayani danta matukar aka ce sai wani abu ya faru a tsakanin su tow zai mutu. Gani take kamar karya ne anyi haka ne domin a rufe ta. Shi yasa tun da Abdul ya farka ta haushi da masifa da bala'i kamar zata rufe shi da duka. Inda take shiga, ba nan take fita ba abin tausayi, sunkuyar da kai yayi yana rike da Kirjinsa. Har ta gama Bala'i bai ce mata cikanki ba, a haka ya samu awa uku, ta matsa lallai a sallame sa. Haka aka suka sallame shi, suka nufi gidan Hajiya.
***
Maikulki.
An samu cigaba yadda ba a zato ba tsammani, domin ta ko ina ka shiga zaka samu mutane suna kokarin fitar da yaran su zuwa makarantu har cikin sunkuru, makiyaya da manoma suna kokarin fito da yaran su niman ilimin zamani da na addini, sau tari mutane zaka samu suna yiwa Malam Aminu ba'a da cewa, yar da aka nime kaita bara yau ita ce tayi mana sanadin da yaran mu suke samun karatu da ilimi, tun abin baya damu n shi har ya kai ya fara damunsa, ya daina fita waje ko sallah ma a cikin gidan shi yake, a hankali abin da ya shika ya fara girban sa, domin yadda ya tsangwame Sa'ade sai gashi shima da girmansa mutane sun tsangwame shi har da mishi habaici da bakaken magana ake cisga mishi wanda yasa shi shiga kunci da damuwa, yana ji yana gani depression ya sako shi a gaba. Yau juma'a yana son ya fita sallar juma'a amma tsoron abin da zai iya faruwa yasa shi ƙwanciyar shi a dakin shi. Yana tunanin yadda yayiwa Sa'ade shima yau gashi duniya ta mishi daurin goro. D'aga labulen dakin sa Inna tayi tana kallon shi, yadda ya koma yasa ta shiga dakin tana faɗin. "Yanzu yau juma'a rana me falala da albarka malam kana kwance a dakin ka? Wai na tambaye ka Malam meke faruwa ne?" "Babu kome, hmm" ya fada yana kallon kofar dakin. "Ya zaka ce babu kome bayan gashi nan ana iya hango damuwa karara bisa fuskar ka. Meke faruwa ne?" "Ina yaron nan Aliyu da yake zuwa?" Ya tambaye ta kansa a sunkuye. "Ina jinka" "hmmm dama na sayar masa da Sa...." Kura mishi idanu tayi tana kallon sa. "Ka sayar mishi da Sa'ade ba? Ai na jima da sanin haka, Allah ya kyau yanzu yasa ka shiga damuwa?" "Hmmm ban san inda yake ba, na nime shi na bashi kudin sa ne ya dawo min da ita ban gan shi ba, karshe ma Mai gari ya tabbatar min ya bar garin nan, ina tsoron kar sanadin abin da na aikata rayuwar ta ya lalace " "Allah ya kyauta tunda ka sayar mishi da ita ai kasan ya saye ta, Allah na tuba ko bawa an daina sayar da su, balle yarinyar da Allah ta jarabce ta, da lalura irin na Sa'ade. Ina imanin ka da tausayi suke da zaka sayar da yarinyar da ko magana bata yi, Allah sarki Ubangiji kenan ya kyauta " daga haka ta juya ta koma wurin girkinta har abada ba zata tab'a gaya mishi inda Sa'ade take ba, balle har yayi wani kazamin tunani akanta ba, Allah ya tsare mata Sa'aden ta domin ko wancan satin da Iro yazo ya tabbatar mata da sun yi hutu, shi yasa take hada mata kayan komawa kafin lokacin yayi. Don ma Allah ya bata yara masu tausayi da jin kan junan su, Allah shi ya bata su kuma sai ya sanya mata su a matsayin sanyin idaniyarta, musamman Mazan da Allah ya fifita su ya musu albarka a cikin niman su da sana'ar, matan ma suna kokarin turo mata abubuwan da suka samu, sai dai samun da namiji da na ya mace akwai banbanci. Amma tabbas duk abin da suka samu suna kokarin kaiwa mahaifiyar su. Yanzu Babban abin da yake d'agawa Malam Aminu hankali yadda ake kara cewa ana ganin Abuturab ba dan Najeriya bane, wani abu ya kawo shi kuma ya gama ya koma kasar su, wannan abin ya saka Malam Aminu a cikin tashin hankali da damuwa, domin har ga Allah ciwon tsatsaye yake, ga yawan zurfaffa tunani, wanda haka yasa shi zubewa duk da daman can ba kibar ce da shi ba.
***
Kamar yadda Sultan ya yi alkawarin ai kuwa hakan ce ta faru, karfe goma na daren juma'a ya sauka a garin london. Maina da Saraki, suka je tarbo shi. Idan ja ganshi yau babu manyan kaya, shiga ce irin ta zamani. Hannun shi daya riƙe da sandar dogarawa, ba wai dogarawa ta lalura ba. A'a ita kanta rike sanda a hannu sunnar annbawan Allah, kuma basaske don haka kusan kwalliyar sarakai ne rike sanda a hannun su, haka yasa shi fitowa dass da shi. Loggers din shi Maina ya amsa. Yana murmushi domin sun bar Ummi ana mata henna, jiya zuwa yayi aka mata gyaran gashi, shi ne ma ya ajiye ta a wurin saloon din, yana jin Shukriya matar shi tana cewa no wonder mai Sultan yake fadar sun rike mishi mata, kawai tsabar kulawa ce da lafiyar jiki da kuma abincin sa. Domin kafin a fara mata lallen sai ta ta gama daura kome sauran su Shukriya zasu karasa. "Ina baba karami?" Kallon juna suka yi da Saraki, kafin suka san yadda zasu kare dan autan su. "Ya tafi makaranta" "wani irin makaranta yaushe ya fara?" Tarin da Maina ya fara yasa suka zuba mishi idanu. Tari har da rike kirjin shi. "Ka je asibiti kuwa?" Gyada kai yayi yana sauke numfashi, fita yayi da sauri ya samu irin babu mutane ya zubda bakin majina me had'e da jini. "Maina anya kaje asibitin ban yarda da kai ba ne wallahi" "wallahi na je har hoton kirjin aka min amma babu kome sun ce ina shan ruwan sanyi ne!" Cikin b'acin rai Sultan ya kalle shi ya ce mishi."hala kai yaro ne da za ace kar ka sha ruwan sanyi, ka kula da lafiyar ja da rayuwar ka, yau ko babu mutuwa akwai tsufa dole idan ma gaji da mulkin nan kai zan bawa ko Saraki?" "Haka ne Abba " ya kalli Maina yana dariya. Girgiza kai Maina yayi ya zauna a gefen shi Direba Saraki yana jan motar, "Abba mulkin kwara ta me zafin nama ne da sanin halin mutanen cikin sa, Allah ya gani bana sha'awar mulki sai dai ko Saraki" wani wawan burki saraki ya taka. "Kasan me ka fada?" " Na sani mana, ni fa jikina yana bani, cewa rayuwata ba ta da tsawo." Gaban Sultan ne ya fadi. Kallon Maina saraki yayi ya ce mishi. "Like me nima ina jin kamar bani da sauran tsawon shekaru da rayuwa." "Dan kun ganni ne kuke gaya min zaku mutu ku bar ni?" "Afwa Abba"suka fada kusan dukkan su lokaci guda. Haka suka isa gidan jikin su a sanyayye. Har ɓangaren baki suka kai Abban su, an gyara wurin tass. Maina ya wuce cikin gidan, daurewa yake daman yana shiga dakin sa ya saka key, ya cire rigar shi Wasu irin rashes ne a gefen hakarkarinsa, sunyi jajjur. Haka ya shiga ban dakin yayi ta kwara ruwa, yana gamawa tari ya ce gani, ashe dama bai yi ba da sai yanzu tari har da jini ta hanci ta baki. Sai da yayi sosai fuskar shi tayi wani irin fayau, kamar babu jini a jikin shi. Yana gamawa ya wanke fuskar shi da ruwan zafi, ta yi ja domin idan ba hakan ba zai d'agawa iyayen shi hankali. Shi kuma baya son ya d'aga musu hankali, kusan asibitoccin da suke garin nan babu inda bai je ba, an rasa gane ciwonsa. Har gwanjin Cancer sai da aka mishi amma babu wani Cancer ciwo ne dai kawai. ALLAH YA MANA MAGANIN CIWON DA BAMU SANI BA...
[02/06, 6:46 pm] usmanlauratu71: Ciwo ne da ba asan kanshi ba, shi yasa shima ya boyewa iyayen shi, wannan al'amarin babu wanda ya sani shi daya yake ta yawo da shi, bayan ya fito ya huta kafin ya nufi part din baki. A can suka hadu baki daya aka bude shafin hira ban da Abuturab da yayi b'atar dabo. Hira sosai aka yi sai magarib aka watse maza suka nufi masallaci, mata kuma suka wuce bangaren su. Sai wajen goma saura Abuturab ya shigo gidan, suna zaune a falo ana hira, ya shiga ya gaida kowa sannan ya kalli Ummi hankalin shi yana kan agogon hannun shi."sai da safen ku, Ummi ki min addu'a gobe muna da interview." Daga haka ya bar falon yana i mamakin ina Abban su. Bai wani damu ba domin ya b'ace ne a gidan don baya son wani abu ya haɗa su, don har yau yana jin zafin Abban su. Hango inuwar mutum yayi kamar mara gaskiya, shan jinin jikinsa yayi akwai wani abu da yake faruwa. Bin inuwa yayi kicibis suka yi da Zuwairah. Kallonta yayi sosai sannan ya ce mata. "Me kike yi a wurin?" "Hmm dama dama, kukan mage na ji nace bari na duba" juyawa yayi bai ce mata kalla ba, bayan tambayar da ya mata. Wucewa dakin shi yayi ya tura zai shiga, yaji motsi a dakin dan dakatawa yayi kafin yayi kasadar shiga, Sultan ya samu a cikin dakin yana duba wasu abubuwan Abuturab din, "Ubana nayi laifi shi ne aka ko zuwa dauko ni?" Yar murmushin yaƙe yayi ya ce."A'a ina niman karamin aiki ne na fita saboda zan koma makaranta." Juyawa yayi sosai ya zuba mishi idanu, baki daya ya sauya daga Aliyu da ya sani. Sai karkad'a key yake. "Na dame ka ko?" "A'a Abba" yasan waye Abuturab, a fusace yake kuma abin da ya dakatar da shi, don shi ne ya haife shi da ace wani ne ya mishi haka, zai ga danyen kai. Nad'e hannu yayi a kirji yace masa. "Kana jin zafina ko?" Dauke kai yayi yana girgizawa. "Tow me yasa?" "Abba na gaya maka gaskiya na tafi." "Abuturab kenan ai nasan halin ka, akwai lokacin da zaka fahimci abinda yasa nayi haka, kai da Mahaifiyar ku, kuna min kallon mara adalci ba? Hmm ka kula da y'an uwanka Maina yana fama da tari, don Allah ka saka idanu akan sa, gobe zamu wuce Nijar daga can zamu wuce gida ne" "Allah ya tsare hanya" takowa yayi a hankali yana kallon yadda kome yake zaune a muhallin sa. "Allah ya muku albarka." "Amin Ya Allah " ya fada a sanyayye, fita Sultan din yayi Abuturab ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya, sai ya ji ya shaƙi iskar yanci. Haka kuwa ya faru da safe suka bar kasar, cike da farin ciki.
***
Hutu ya kare, kowani dalibi yana kallon ranar komawa makaranta a matsayin ranar fara damuwa, a gefen Rahilah wani irin farin ciki take cike da shi, ga magana da farin ciki amma ta rasa inda zata fadi haka. Da sassafe Aunty tayi sammako daga gidan ta, ta same ta a dakin su zaune kamar mayya. "Kin gaji ko? Kina son ki koma makarantar ko?" Ta tambaye ta, dake tayi koyarwa a makarantar kafin ta bar aikin ta fara wani. Girgiza kai tayi tana sunkuyar da kai kasa. Tab'a ta tayi tana ce mata. "Taso muje" ta riko jakan Ghana most go dinta, tana kallon yadda yarinyar ta sukurkuce, Mahaifiyar Aunty ce ta fito tana rike baki. "Yanzu sai ki tafi bamu gaisa ba, Auntyn su." "Mama sauri nake zan mai da ita makaranta ne, kuma zamu makara". "ai shi kenan sai ki ta tafi tunda bamu isa ki shigo wurin mu ba" a gaggauce ta shiga dakin Mahaifiyar ta, tasan halin ta sarai, "fisabilillahi tun yaushe nake kiran wayar ki baki dauka ba, amma dake aikin wahala ne kin taso zaki daurawa kanki, bayan Baban ku ma cewa yayi aurar da ita zai yi ya huta" gyara zama tayi sannan ta ce mata. "Mama lokacin Baffa yake raye shi ya rike hannuna har na kai matakin da nake, na rantse da Allah, ba zan iya barci yar shi tana cikin kuncin rayuwa ba, shi yasa na kaita makarantar irin su tunda na lura Baffan mu bata ita min yake ba. Ni dai ina baku shawara kar ku dauka babu rayuwa bayan mutuwa ne akwai domin kuwa Allah yana sane. Kuma ya ji." "Tashi ko ki kaita, Kafin ji fara mana wa"azi alaramiya, sai ku tafi ai" Mamanta ta fada tana aikawa Rahilah harara. Ita dai sunkuyar da kai tayi suka fita da daga gidan. "Kiyi hakuri zaki ji dadin haka wata rana," gyada kai tayi tana mata alamar godiya. Haka suka bar gidan. Tare da nuna mata ledar bagco da ta sako mata kayan abinci da su sabulu, tayi kokari ba laifi don ma sun sake mata nauyin Rahilahn ne ai da ba haka ba, "Allah ya jikan mahaifan ki" domin ba haka suka yi mata ba, yau gashi yar su tana watangaririya. Suna shiga cikin makarantar ana kawo Husnah, ai nan suka kacame da murna, bayan an gama musu kome suka wuce hostle, awa biyu da dawowan su, sai ga Sa'ade. Anan aka bude sabon shafi na farincikin. Washi gari aka kawo Kubrah, suna ganinta aka fara halin niman magana kamar yaran bera. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya da yan matan nan, yau fari gobe tsumma. Ga kokari sai dai a bangaren Sa'ade bata fasa zuba idanun ganin yaushe zai zo ba, tun kawayen basu fahimci akwai abin da yake damunta har suka fara gano ta, idan aka ce yau ranar visiting ne zaka ganta tana kallon bakin get ko zata ganshi.
***
Abdul Hakim.
A bangaren shi da mahaifiyar sa, ba a cewa kome, hatta Sophia ta fahimci bai da wani kuzari, haka ya janyo wani irin wawan gibbi a tsakanin su, domin reni take da shi. Duk abin da ya mata shi take yi, idan a gidan su ne, a gaban Hajiyar shi kuwa kamar ta cinye shi danye. Duk da yana kokarin boye damuwar shi haka ya janyo mishi ciwon sa ya fara kokarin tashi a kai akai don ma yana Bala'in tsoron Hajiya domin cewa take karya ne ba ciwo bane gulma ce an saka shi ya mata renon hankali ne. Ganin yadda yake kara samun koma baya a kan lafiyar shi, babu shiri Mahaifin shi ya nima mishi mafita, ta hanyar tura shi karatu PhD domin tausayin d'an na shi yaƙe, yasan idan baya nan zata kyale shi, bata san da tafiyar ba sai bayan tafiyar shi Dr Sharif ya gaya mata, domin nan ya bar mata Sophia.
***
Kwara.
Tunda Badi'atul Noor da Sultan suka dawo, aka gansu tare hankalin sauran matan ya tashi babu kamar Badariyyah, domin ta iya munafinci, amma a ruwan sanyi. Haka tayi ta bin sa akan ya shirya musu tafiya Umra, ya share kamar bai san tana yi ba. Yau girkin Badi'atul Noor ne, duk da taki yarda da zancen haka amma yadda ya kafa ya tsare yasa ta amsar girkin babu yadda ta iya, kuma ta ce mishi ba zata zo ba, tunda ita ba yarinya ba ce. Ya ce ya ji ya gani shi zai je. Akan haka sai da Baffanta Junaidu ya shigo cikin lamarin domin rigima aka tadda shi, matan shi da goyon bayan Sultanate, ita kuwa ta ce bata iya ji ba. Ganin zasu ja mishi salalalar tsiya ya ce musu. " Na amince ni zan na zuwa bangaren ta, su kuma duk wacce ba zata zo ba, tayi zaman ta." Wannan abin ya bakanta ran Sultanate. Don haka babu shiri kowacce ta ce ta amince shi kenan. Shi yasa ake zauna lafiya, shi kansa lallaba Badi'atul Noor yake kamar yana jin Bala'in tsoron ta. Tun sallah isha ya wuce bangaren ta, suna falon sama suna hira kafin su kwanta. Kwankwasa kofar falon aka yi Mama Hajja ce. "Shigo Mama Hajja" ta bada izinin ta shigo. Cikin ladabi ta shigo ya ce mata. "Sultanah Hajiya Badariyyah tana son ganin Sultan" " ta shigo" ta fada tana gyara zaman dan kwalinta. "Tow" ta juya ta fita can sai gata ta shigo bayan cancad'a kwalliyar da tayi. "Barka da Hutawa Sultanah" "Yawwa Mamana Arif, ya Yara?" "Lafiyar su lau, ya labarin su Baba karami da su Maina?" "Suna lafiya lau " ta mai da hankalinta kan tv. "Badi'atul Noor ko zaki taimaka min da madubina a saman bedside" "tow " ta fada tana me barin falon, juyawa yayi ya zuba mata ido. "Me ya kawo ki? Ita tana muku haka ne? Tashi ki tafi" "babu inda zani wallahi sai ka kai mu umra kamar yadda kake yawo da ita." Kamar ya rufe ta da duka, ya rasa me zai ce don takaici. Dawowa Badi'atul Noor ya sa shi amsar madubin. "Ummin baba karami, ki saka baki ya biya mana umra fisabilillahi aiki babu adalci yana fifiko, ban da kowa yasan matsayin sa ai da Allah kadai yasan me zai faru. Wallahi Sultan baya mana adalci, idan ba zai iya zama da mu ba, ya sallame mu mana." Shiru tayi kallon ikon Allah. Ita da aka kora mata yaranta baki daya a gidan bata yi ihu ba. Murmushi tayi irin ta manya ta ce mata. "Shi kenan idan dai Umra ce ai kin kawo kuka inda ya da ce. Don Allah zaku ba iya umra ba har Dubai zaku." "Bani da kudi." Ya fada a gatsale. "Ah zan baka aro ko bashi." "Ba zan karba ba, na gaya miki bani da shi idan na samu zan biya musu su tafi lokacin Ramadan " "tow Allah ya hore maka" "Amin Ya Allah." Ya fada yana barin falon. Kallon Badariyyah tayi cikin tausasshen harshe ta ce mata. "In sha Allah zaku tafi, ki kara hakuri zan kokarta miki koda dukkan ku baku tafi ba, amma ke da yaranki zaku tafi." Gyada kai tayi tana faɗin. "Ya dai ji tsoron Allah, babu adalci a cikin lamarin shi " " a kara hakuri dai" haka tayi ta mita har ta bar falon, idan ta fahimta ita yake fifutawa akan su, murmushi tayi. Wucewa ɗakinta, tayi wanka da sallah shafa'i da wutiri tayi addu'a sannan ta wuce dakinsa. Yana zaune yana aiki. "Barka da hutawa." "Yawwa " zama tayi tana kallon shi. "Kin ga bana son rigima fadi abin da yake ranki" "ka biya musu Umra kawai a wuce wurin" "ai na gaya miki gaskiya bani da shi" "me yasa kake haka ne? Su gani suke ka fititani." "Eh su fadi abin da ya musu ma" "amma sai ka biya wallahi" "Badi'atul" "Na'am bani da shi" " Allah kana da shi ka biya musu kawai" "idan nace zan biya dukkan ku hudu zan biyawa." "Na yafe ka biya musu ai ni Yarana suna biya min." "Shi kenan zan duba" "ka kyauta" ta wuce ta kashe wutar dakin ta kwanta abin ta. Washi gari bayan yan sallah la'asar ya tura musu Ibrahim baban dan hajiya Mariyah ya amso passport dinnsu. Sai wurin isha da ya shiga cikin gidan ya bawa Sultanate takardun su, domin har da ita a a cikin masu zuwa umran. Ai kuwa saka albarka kamar harshenta zai tsinke da saka mishi albarka take. Ya mata sallama ya bar ta tana murna. Haka ta turawa matansa da suke karkashin inuwar ta, anan Badariyyah take musu burga da cewa ita tace mishi ya biyawa Sultanate Umra shine ya ce a'a su tafi tare, wayyo da tasan bala'in da ta jangwalo ba zata fadi haka ba, domin dai Sultanate ta ce bata zuwa umran tunda ita ta nima nata Alfarman zuwa ba shi yayi niyya ba, dama kuma tana da rikicin tsufanta yar batalikan nan ta haɗa kowa ta ci mutuncin sa. Dakyar aka samu ta sauko kuma abin dariya Badi'atul Noor din nan dai ita ce ta rarrasheta kafin ta sauko da sharadin sai dai su tafi abin su ita ta tafi aikin hajji da kyar aka kashe wutar suka tafi Umran.
*After Four years ago*
UK..... 08130269641 top-notch
[03/06, 8:10 pm] usmanlauratu71: Shekaru hudu.
_2013_
Ga Yaran Ummi kamar azaba ce, domin a cikin shekarun Abuturab ya farga da halin da Maina yake ciki, domin da farko ya manta yadda suka yi da iyayen su akan ya kula da Maina da suke ganin bai da lafiya, baki daya ya sha'afa sai shekara da suka wuce ya fahimci haka, sakamakon faduwar da Maina yayi a wurin aikin sa aka wuce da shi asibiti. Anan suka fahimci yana fama da mugun mura, da wasu kuraje masu tadda hankali. Duk yadda yaso daurewa sai da ya kasa, domin daga kirjin Maina zuwa bayan shi kurajen ne da suka watsa ƴaƴan su masu bala'in azaba da ciwo, amma karfin hali irin na shi haka yake kokarin ganin babu wanda ya gane, Allah ya taimaka lokacin da ya fadi Abuturab aka kira domin sun yi magana da Abuturab din ya fada, haka yasa aka samu last call din Maina. Koda ya zo asibitin shi kasa ya sha mamakin ciwon da magungunan da yake sha. Koda Maina ya fara abu daya ya nime Abuturab yayi ya bar maganar iya su, don Allah kar ya d'agawa Iyayen su hankali da matar shi da yan uwan su. Babu yadda Abuturab bai yi be yi ba amma haka Maina ya hana shi fadar ciwonsa. Tun daga lokacin Abuturab ya kasa zaune ya kasa tsaye wurin niman magani da haduwa da manyan kwararrun likitoci. Kullum cikin binciken ciwon Maina yake, haka yasa wani professor a Berlin na Germany ya bashi shawaran ya kai Maina Abubakar China domin suna da sani akan magunguna da ciwo, da wannan shawarar Abuturab suka tafi sai dai ance mai nima yana tare da samu, haka ce ta faru domin dai sun sami magani ba laifi amma kuma ba wai an san ciwon ba ne, sun ba shi magani da zai taimaka mishi akan rage radad'in da yake fama da shi, sai kuma na fatar shi, da aka bashi magani yana sha yana shafawa. Za a iya cewa Alhamdulillahi tunda dai har ya samu sauki babu laifi tunda lafiyar ce ta tabu dole sai a hankali sauƙin. Exactly shekara biyu kenan, a cikin wannan shekaru hudun duk shekara Zuwairah da Jalilah suka zuwa Nigeria ba don kome ba sai don dangin su, kuma a wannan zuwan da suke babu wanda ya tab'a sanin halin da Maina yake ciki, domin sun boye babu wanda ya sani sai shi da Abuturab. A gajiye Saraki ya shigo domin kwana biyu baya samun damar hutawa, har Asabar yana wurin aiki sakamakon yadda ake gab da yin bikin jikan sarauniyar Ingila. "Abuturab ina Maina kwana biyu bana ganin shi?" Hankalin shi yana kan aikin da yake s jikin laptop ya amsa mishi. " Ya tafi Beijing amma yau nake saka ran zai dawo" fitowa matar shi Aneesah tayi dauke da ruwan sanyi ta mika mishi, "Barka da dawowa ya aiki?" Ta amshi jakar aikin shi. Kurba yana kallon Abuturab. "Auta sai nake ganin kamar Maina bai da lafiya" da sauri Abuturab ya kalle shi, ya bude baki zai magana wayar tafi da gidan ka landline yayi kara, Aneesah da take kokarin shirya table saboda mijinta, ta dauki wayar. "Hello " "Muna magana da iyalan Mr Maina ne?" "Eh nan ne?" "Yana asibit ne bai da lafiya" "what?" Mikewa suka yi daga Abuturab har Saraki. "Ok ga mu nan zuwa " "wai Hamma Maina ne bai da lafiya ya fadi a airport amma sun wuce da shi asibiti " "innalillahi wa'inna illahi raju'un." "Muje kar ki bari Hamdiyah ta ji" suka fita daga shi har Abuturab, sun samu babu halin a shiga wurin shi, kiran Baban Latifah Alhaji Khamal...
***
A cikin shekaru hudu nasara da cigaba an samu a rayuwar Sa'adatu Aminu Fulani, wacce take jerin daliban Ss1, yau saura kwana biyu bikin yaye daliban Ss3, don haka sosai hankalin su ya koma su da yan Ss2 da Ss3, abubuwan sun sha kan su, domin tun safe suka tashi sai dare suke komawa sallah da cin abinci yake dauke su daga wurin, saukowa tayi tana kallon Husnah da take kishingid'e kasar bishiyar da suke daura yadin zare kalar tutun nigeria. "Malam tashi mu tafi" lumshe idanu Husnah tayi, tana murmushi. Tashi tayi tana karkad'e jikinta. "Ina tunanin Ya muhsin ne!" Ta fada bayan ta zanen heart a hannu. Zaro idanu Sa'ade tayi tana b'ata yar karamar baby face din ta, tare da cizon lips dinta. Kyakyafta mata idanu Husnah tayi, tana tambayar ta me nene? D'aga kafada tayi tana juya idanun ta, (ana kiran salon wannan maganar da Morse code) ba kowa yake fahimtar ba, amma kurame suna yin shi musamman wadanda suka samu koyarwar shi yana da saukin isar da sakon da ba kowa yake fahimtar ba, a cikin daliban makarantar bai wuce su goma sha bakwai suka iya Morse code ba, a cikin daliban da suka fito da excellent Sa'ade ce ta biyu, sai wani Yaro ke bin ta sai Husnah. Rahilah da Kubrah cewa suka yi su Sign languages din ma ba kowa yake yi ba, sai masu saukin fahimta. Haka yasa iya su goma sha bakwai suke koyan lession din, wani abin da ba kowa ya sani ba. Shi kan shi Morse code yare ne na security agent jami'an tsaro sirri suke amfani da shi, musamman wurin isar da sakon da suke bukata, musamman idan aka kama su, kamar misalin idan yan ta'adda suka kama jami'an tsaro sirri, suka fito da su domin suyiwa gwamnati barazanar a sake su, tow kwararru a cikin jami'an suna iya isar da sako na musamman inda suke da kuma adadin mutanen da suke wurin. Ya samo asali ne daga wani Samuel Morse, shi yasa ake kiran shi da Morse code, sannan bayan haka yana da hanyoyi daddama wurin isar da shi, na farko akwai yin rubutun shi in alphabetical, sannan akwai yin amfani da shi da finger's, sannan akwai yin shi ga idanu. Waɗannan sune hanyar isar da shi. Yana da kyau. Wannan shi ne asalin yadda Sa'ade ta fara koyan yaren idan muka tuna farkon labarin inda take magana da idanu Inna Laminde ke iya fahimta, shi yasa da ta fahimci irin talent dinta, ta koyo hanyar fahimtar karatu da shi, sannan a bangaren ilimin Sign languages ma ba laifi tana kokari sosai, haka yasa baki daya ta daura ragamar tafiyar rayuwar ta akan. A hankali suke tafiya suna ratsa filin makarantar har zuwa hostle din su, Rahilah suka hango tana zaune saman barandar dakin su. Kubrah tana shan garin kwaki. Kallon su tai ta dauke kai tana tsaki. Haka ta gama cusa garin ta mike. Riko hannunta Rahilah tayi ta mata alamar ta zauna, idan ka zaka duba zaman su, hakuri suke da Kubrah don ma Rahilah bata daukar reni. Yanzu zata ci Ubanta a zauna lafiya. Dawo da ita tayi su fahimci juna. Wai fada aka yi akan Sa'ade, Kubrah da Husna duk shirun Husnah sai da ranta ya ɓaci tayi fada, sam Sa'ade bata iya rigima ba, sai dai idan tayi fushi abin baya kyau. Akan kayan abinciin Sa'ade ne da ya kare. Su uku kayan su a haɗe yake, suna haka ne saboda Rahilah haka Kubrah ta haɗa kayan ta da nasu, Ashe tana lura da kome da zarar kayan abincin Sa'ade ya kare ko Rahilah zata kwashe nata, dama na Sa'ade ake fara tab'awa tayi ta bakin hali kenan, dake tana masifar tsoron Rahilah da Husnah bata iskanci da renin hankali sai ta ga basu nan, tow nan zata yi ta bakin hali har Sa'ade tayi fushi taki cin abincin su. Rahilah da Husnah basu sani ba, sai yau da safe sun amso kunu Sa'ade ta bude locker zata dibi Sugar kawai Kubrah ta mike tana kallon duk abin da sa'ade take. Shine ta mike take tambayar ta "Meye yasa duk lokacin da zan debi abinci kike tsaya min a kaina?" Shi ne ta mike ta fara fada da ihu, kamar wani abu ya faru. Abin ya bawa Sa'ade haushi ta bar mata kunun da sigar zata fita suka hadu da Husnah tare ta, tayi tana tambayar ta lafiya? Shine ta fashe da kuka sosai har jikinta yana rawa. Ganin haka Husnah ta shiga dakin a fusace ta samu Kubrah tana raba kayan zata cire ta. Ai kuwa ita da ta fita hauka ta kwashe kayanta ta watsa mata su, ta rufe locker. Shine cikin fushi itama ta mike take nuna mata wato don tana gadaran ubanta me kudi ne shi ne zata watsar mata da kaya, akan wata yar kauye da iyayenta kauye suka fito, da ta daina kula Sa'ade da yafi ta bar sa'ade da Rahilah sune rayuwar su iri daya. Sake baki Husnah tayi ta ce mata. "Ban yi mamakin jin haka daga bakin ki ba, domin zaki fadi abin da yafi haka, ke ko kunya baki ji ba. Daga yau kar ki kuma shiga harkan mu ki je da halin ki. Barauniya kawai " shi ne fa dambe ya kacame a dakin dakyar Rahilah ta raba su bata san me ya faru ba, ita kuwa Husnah ta juya ta bar dakin. Tun da suka tafi take bin Rahilah sau da kafa saboda kar ta tambayi dalilin rigimar su , itama ta juya mata baya. Don sai da tayi fadar ta fahimci ba karamin son Sa'ade suke ba. Hango su da tayi, ba kome bane taburman kunya a nad'e shi da hauka tayi. Don kar a tadda zancen ne, su kuma sun manta sun yi fadar ma. Sa'ade tana shiga dakin su daukar bokiti zata yi ta gan shi cike da ruwa, kallon Rahilah tayi da take zaune. A gefenta tana murmushi. Dauka tayi zata fita Rahilah ta amsa mata, ta wuce ban daki ta tsaya a wurin. Har ta fito tana kallon ta. Sai da ta zo kusa da ita ta tambaye ta me ya faru ɗazun. Girgiza kai ta yi tana dariya ta mata alamar ya wuce a bar shi kawai..
***
Daga Hajiya Daulah ba zaka gane waye ya fi wani murnan dawowar Abdulhakim ba, sai ma yadda suke rawan jiki, dake shekara biyu da suka wuce Dr Sharif ya tura mishi ita, domin ta zauna da shi kafin a mishi aikin shi wanda ya rage saura watanin ne a mishi. Sai dai kuma bata kai wannan lokacin ba ta dawo gida, idan ta matso sai ta tafi wurin shi, har aka yi aikin. Ganin gari ba nasu ba, zata fara yawo ya dawo da ita tare da fadawa mahaifin sa kar ta kuma zuwa shi zaizo. Nan ma Hajiya Daulah ta cika tayi makil. Ko lokacin da za a mishi aikin karshe dole Dr Sharif ya ajiye aiki ba don kome ba, sai don rayuwar dan shi, sai da aka yi aikin har ya fara takawa suka dawo gida ya gama jinya yana gamawa ya lura zasu takura shi. Shi ne ya gudu inda ya fito. Yanzu ma abun da ya kawo shi bikin Afiyyah da za ayi kwanan nan ne, da kuma ya ga cigaban da kamfanin simintin Mahaifiyar shi yake samu, bayan nan ƙaddara ta kuma janyo shi izuwa sokoton Shehu.....
08130269641 Top-notch Addah Ramlat....
[05/06, 8:14 am] usmanlauratu71: Kamar mara gaskiya haka ya shiga cikin falon Hajiyar su yana yake, duk da dai lafiyar har zuwa yanzu sai godiyar Ubangiji, amma ba laifi, tunda rayuwar auratayyar shi da Sophia da sauki, domin daga yadda take rawan jiki zaka fahimci lallai kome lafiya lafiya, daga kan fuskar Hajiya Daulah zaka fahimci zallar farincikin da take ciki, musamman da suka yi ido biyu da Abdul din, wani yalwataccen Murmushi yake kwance a bisa fuskar ta, "Sannu Ubana,anya kaso dawowa kuwa?" Murmushi yayi yana me zama gefenta. "Hajiyata gani nan a gaban ki" "da ina fushi da kai amma yanzu na huce ya can inda kake? Ka bar min kamfanina sai a hankali. Amma Alhamdulillahi ya lafiyar ka?" "Alhamdulillahi hajiyata" ya faɗa kamar.me tsoron kar wani abu ya faru, don yasan hajiya wata birkitacciyar mace ce. "Ka je ka huta daga akwai maganar da zamu yi da kai mai muhimmanci ka ji" Hajiya Daulah tana lallaba shi ne saboda karfen da aka saka mishi a kirjinsa amma ba don haka ba, da ruwan masifa zata tarbe shi. Gidan sa ya wuce ya samu cike da yan mata kawayen Afiyyah. "Sannun ka da zuwa Ya Abdul" "Yawwa sannu ku Afi ya shirye-shiryen bikin?" "Alhamdulillahi, Masha Allah Ubangiji ya baku zaman lafiya" yana gama fadar haka ya wuce sama abin sa, domin Kawayenta kamar su cinye shi danye. Shi kuwa baya ciki da irin wannan kallon da suke mishi. A bakin kofar dakin sa ya hadu da Sophia. "Ina saurin na isa gidan Hajiya na dauko ka, ashe ka tawo?" "Eh gani" ya fada yana kokarin bude kofar, da dan sauri ta buɗe mishi kofar suka shiga. Yasan halinta yanzu zata iya damun shi. "Sophia" "shiiii, kayi shiru kawai It's my duty" ta fada tana taimaka mishi, har sai da yayi wanka tsaf. Sannan suka fito, itama a jiken. Fita tayi ta nufi dakinta, ta sauya kaya sannan ta nufi down stairs ta haɗa mishi abinci ta kawo mishi, idan ka cire azabar yawo Sophia bata da matsalar kome sai shegen yawo kamar wacce ya ci miyan shanshani. Kafin wani lokaci sun ci abinci an fada duniyar su iya su suke gane yanayin ko nace iya ita domin baki daya shi a bangaren shi baya wani dauki ko murnan haka. Wurin karfe shida suka sauko fess da su, wucewa masallaci yayi, Dr Sharif ya hango a kofar masallacin zaune rike da katin gayyata. "Sannu Abba, katin gayyata ne na bikin?" "A'a ƙatin bikin yaye daliban makarantar Raji special school ne" amsa yayi yana kallon katin. "Naga kamar jibi ne?" "Eh gashi nan sun gayyace ni" "Zan raka ka" murmushi yayi sannan ya ce mishi. "Allah ya kai mu" "Amin Ya Allah"
***
UK..
Kallon Hamdiyah Alhaji Khamal yayi bako daya ya kasa yarda da abin da take fada. "Taya shekaru hudu mijin ki yana fama da ciwo irin wannan ki ce baki sani ba?" Cikin kuka ta ce mishi. "Na rantse da Allah ban sani ba, asalima kullum da rigar shi yake kwana" "Ina ga bai dace da ka tambaye ta irin wannan zancen ba, yayi nauyi da yawa" inji Abuturab da yake tsaye a wurin. Fitowar Latifah daga cikin dakin sa, kasancewar ta ɗaliba me sanin makaman aiki a bangaren likitanci, ta cire facemask ɗinta. A hankali ta saka a cikin aljuhun rigar labcoat. "Mimi ya dai?" Hàdiye yawu tayi tana faɗin. "A cigaba da addu'a" ta wuce Office din likitan da yake rike da case din shi. "Newbie's kin ga halin da yake cikin? Bana son na fad'awa familyn ki ne domin naga kamar kun fito daga Noble family." Gyada mishi kai tayi tana faɗin. "Eh daga Babban gida muka fito, wani hali yake ciki?" Mika mata x-ray din yayi yana faɗin. "Huhunsa dukka biyu sun lalace, shi yasa yake haki, dalilin da yasa kurajen da suke wurin hakarkarinsa kenan suka feso." Hàdiye yawu tayi cikin wani irin tsoro. "Me ke kawo ciwon?" "Eh toh sai dai mu tsannanta bincike, domin dai ban ga wani abu ba." "Please doctor kayi wani abu, shi ne next Crown princes" rike bakinsa yayi sannan ya ce mata. "Oh My God, bari na tura lab a diba mana ruwan ciwon hakarkarinsa da kuma jinin sa." Mikewa suka yi, suka fita baki daya, kafin kace me an dibi jinin an fita da shi. Daga Abuturab har Saraki da Alhaji Khamal. Suna tsaye a wurin sai shiga da fita su Latifa suke. Fitowar da Latifah tayi cikin mutuwar jiki ta kalle su. "Ku shiga wancan dakin zaa baku kaya ku saka sai ku shiga yana son magana da ku." Tana gama fadar haka ta wuce. Tana share hawayen da yake zubo mata. Riko arm dinta Abuturab yayi domin ya lura da yadda take kuka. "Gaya min meke faruwa?" "Babu kome Hamma" ta juya zata tafi ya kuma janyota suna kallon juna. "Me yasa mu Abubakar?" "Kaje yana son ganinka karka b'ata lokaci" "Mimi gaya min meke faruwa?" "Please ka kyale ni mana" ta kwace rikon da ya mata, ta zura da gudu. Ai bai tsaya sauya kaya ba, ya wuce dakin. Idanun Maina yana kan kofar, hannun shi cikin na Saraki. "Kayi hakuri Saraki ka kula min da kanka" ya fada yana rike da hannun shi. Juyawa yayi yana kallon matar shi. "Idan kika ji kewa da maraici akwai Saraki da Abuturab, akwai Rumaisah da Zakiyyah, da Ummy Aymana, ga Ummin mu da Abban ki. Ba zasu tab'a barin kiyi maraicina ba." Wani irin kuka ta sake tana me juyawa zata fita. "Auta baka saka kayan kariyar ba? Zo auta ina son baka wani matsayi na musamman. Ku bamu wuri" ya fada yana tari. Rike shi Saraki yayi. "Ku bamu wuri babu Ummin mu auta zo nan kafi mu jin duminta zo ka bani jikinka naji dumi" wucewa yayi Alhaji Khamal ya bashi facemask ya saka, mika mishi hannu Maina yayi, ya d'an d'aga shi sannan ya zare pillow da yake kai, ya jingina Maina a jikin shi. "Hammmm" ya sauke ajiyar zuciya.
***
Kwara.
Barcin la'asar kowa yasan babu kyau, ita kanta Ummin ta sani, amma yadda barci yake cin idanunta kamar ta kwana bata yi ba. Asalima yau tun tashinta da suka yi waya da Maina yake mata wasu irin magana. Takaici yasa ta kashe wayar. Tun safe bata kuma jin duriyar kiran shi ba, shi ne ta kira Saraki ya tabbatar mata baya ganin shi kwana biyu. Ai kuwa ya sha fada kamar ta shiga wayar. Har yamma tana kiran su layikan su a kashe. A hankali barci yayi gaba da ita, tafiya take ta gefen makabarta, ta ga an tone kabari biyu, ana shirin tone na ukun ta isa wurin tana tambayar su. "Kabarin su waye haka tonawa?" Juyawa mutanen suka yi daya daga ya ce mata. "Ga me kabarin can zuwa" juyawa tayi itama tabbas ba gizau bane Maina ne sanye da farin jallabiya, sai sauri yake, Saraki yana bin bayan shi a hankali kamar baya son zuwa, shi kuwa sai sauri yake kamar zai tashi sama. Yana isowa ya kalli Ummin su ya ce mata. "Kin ga yayi miki kyau ko? Kin ga yadda labarin yake, gaskiya yafi ko ina kyau da aminci. Ummina na gode sosai bari na kwanta." "Innalilahi wa'inna laihil raju'un Ubangiji ka raba mu da mugun ji da mugun gani." Ta farka tana zufa kamar wacce tayi gudun faffalaki.
***
UK..
Fita suka yi suka basu wuri, "Abuturab don Allah ka roka min Ummina da Abbana su yafe min, ga Annur da Nur, kasan wani abu? Duk da wannan yanayin na jinya she is pregnant. Naki barin ta fahimci ciwon ne domin bana cire kayana, kome na kamar mara gaskiya nake yi, duk da naso na sake ta, sai dai tana bani tausayi. "Abuturab kayi hakuri zan tafi na barka da nauyin da ya dace na dauka." Ya fada yana kwantar da kan shi a kirjin Abuturab. Tari ya fara sosai yanayi yana amai kamar zai juye kayan cikin sa, sai kokarin aman yake. "Bari a kira likita" "girgiza kai yayi sannan ya rike Abuturab. Yana wani irin yunkuri, haka yaui ta aman guda-gudan jini, yayi yana rike hannun Abuturab da karfi kamar zai balla mishi kashin hannu, "La'ilallah halillah Muhammad Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama." Shi ne kalmar da yake fada yana nanatawa, Abuturab yana taya shi. Yanayi yana firgita, yanayi yana kara rike dan uwansa, rungumar shi sosai Abuturab yayi ko ba a gaya mishi ba, yasan yau Abubakar yana amsa kiran mahaliccin sa, a hankali yake jin wani irin tsoron Allah, yana shiga cikin zuciyar shi, imani da Allah yana kara samun muhalli a cikin kokon tanshi, a hankali yake kallon yadda Abubakar Maina yake shure-shure yana salatin, kafin ya shiga maimaita kalmar shahada, a hankali Abuturab yana taya shi har ya daina jin muryan shi, sai dai al'amar yana yi, karshe ya daina ganin alamar ma. Sai dai ya dauki lokaci yaji ya sauke ajiyar zuciya, jikin shi yayi nauyi. Rungumar Maina yayi sosai cikin wani irin kewar dan uwansa, soyayyar dan uwan yana kara cika mishi zuciya, yau itace farkon da yaga mutuwa a idanun shi, mutuwar ma ta dan uwan shi. A hankali ya kwantar shi, sannan ya gyara mishi kwanciya ya rufe mishi idanu, kafin ya kofar fita suna kallon shi yadda jikin shi ya b'aci da jini. "Aliyu!" Saraki ya kira sunan shi. Kallon shi yayi a hankali ya nemi wuri ya zauna. Ciro wayar shi yayi, yana ganin Latifah da sauran likitocin zasu shiga dakin ya ce "da kun koma ya rasu ma" ya fada yana saka wayar shi a kunne kamar ba shi yayi maganar ba, ko mantawa yayi ne, sai jin faduwar Hamdiyah suka yi. Baki daya ya manta tana wurin, da idanun ya bita da shi kamar yana kallon sabuwar halitta, ya ce. "Latifah ku kaita maternity ciki ne da ita" kafin ya mai da hankali kan wayar. "Abba, muna hanyar zuwa don Allah ka lallaba Ummin mu, Abubakar ya amsa kiran mahaliccin mu, please ka lallaba Ummi." "Innalilahi wa'inna laihil raju'un Ubangiji ya Jikan Abubakar Maina, Ina Saraki?" Sun wuce da Hamdiyah maternity in sha Allah gobe zamu taso jibi zamu iso kasan gawa ce dole sai an cike cike" "Allah ya maka albarka, ka tsaya akan kome Aliyu " "shi kenan Abba" kallon Alhaji Khamal yayi yana faɗin. "Abba mu karasa sauran abubuwan da ake bukata " mikewa suka yi shima Baban Latifah jikin shi yayi sanyi. Haka suka ta shige da ficce, aka tura gawar mutuare, sannan suka wuce Office din Embassy na Nigeria dake nan British, suka gama kome, airport suka wuce aanan ma sai da suka dauki lokaci. Kafin suka dawo gida, kusan duk yawon da suke a babu wanda ya samu arzikn cikin abinci, sai jigila kawai suke akan yadda za a fitar da gawan zuwa Nigeria.
***
Bayan sallah ishe Sultan ya isa falon Sultanah da take kwance akan abin sallah. Zama yayi yana kallon ta. Kafin ya zauna shima. "Tunanin me kike ina ta sallama?" Tashi tayi zaune tana murmushin karfin hali domin jikinta baki daya babu kwari. "Ina tuna ranar da na haifi Maina ne, sai da yayi kwana uku bai sha nono ba, saboda daga ni har shi bakin juna ne. Ranar da ya fara sha, ina kuka yana sha. Baki daya abin dariya yake bani" matsawa yayi jikinta sosai. Ya riko hannunta, "eh haka al'amarin, musamman da yazo lokacin ana rikicin ba a sona" murmusa mishi tayi, sannan ta zare hannunta zata kwanta. "Badi'atul Noor" bude idanu tayi tana kallon shi. "Waye ya halicce ki?" Bakinta yayi matukar nauyi ta ce. "ALLAH" "su Ƴaran ban waye ya baki su?" "Allah" "Ina iyayen ki?" "Allah ya amshe su?" "Idan Allah ya amshi abin da ya baki ya zaki ji?" "Da zafi kan amma kuma ai shi ya halicci kayan sa, kuma Ya bamu aron shi ya kuma karba a lokacin da yaso, babu amfanin tashin hankali sai dai muce tsarki ya tabbata ga makagin halittun farko da ba karshe." Rike hannun ta yayi. "Alhamdulillahi, Allah ya amshi Abubakar Maina." D'ago kai tayi tana kallon shi, wani irin zazzaɓi ne ya rufe ta, bata san lokacin da ta sulalle kasa ta kwanta ba, "Badi'atul Noor." "Ba kome zazzaɓi nake ji, dan rufa min bargo" ...... *In sha Allah zuwa dare zan kara muku. 08130269641*
[05/06, 6:59 pm] usmanlauratu71: .Kamar wacce aka lullube ta da danyen nama haka take jin ta, baki daya kanta wani irin juyawa yake, kafin taji har cikin Idanunta juyawa yaƙe. Rintsa idanun tayi da karfi tana faɗin. "Maina ya rasu ka ce min ko?" "Eh Badi'atul Noor" ajiyar zuciya ta sauke tana faɗin. "Alhamdulillahi" ta kuma lumshe idanunta, na wani lokaci kafin ta bude ta ce mishi. "Yaushe zasu iso?" "Jibi in sha Allah" murmushi tayi, ta kwanta a wurin. Wayarta ne ya fara kara, ya dauko tana ji amma bata da wani kuzarin daukar wayar. Ummy Aymana ce ta fara magana cikin kuka."Ummin mu Hamma Maina" "ba ita bace." "Abba Hamma Maina ya rasu" "ki mishi Addu'a" daga haka ya kashe wayar duk tana jin shi, kafin kace kwabo labarin mutuwar Maina ya kara watsuwa cikin Masarautar, jikin kowa ya mutu, mutum me hakuri da sanin darajar na kusa da shi, Maina bai da abokin fada babu ruwan shi da fankama da dabi'un yaran sarakuna. Yana da kirki sosai kamar me ga iya mu'amala da mutane. A hankali barci yayi gaba da ita bayan zazzaɓin ya saukar mata a falon Sultan yayi Sallah isha, ana idarwa Rumaisah tana shigowa, can sai ga Zakiyyah, bata zauna ba Ummy Aymana ta shigo itama, suka saka mahaifiyar su a gaba suna kuka, sai da Sultan ya musu nasiha sosai, kafin suka daina kukan. Suna zaune a wurin Sultanate ta shigo, duk kiyayyar ta da Ƴaran Badi'atul sai da ta yi kuka musamman Maina da yake da hakuri duk abin da tsanar su da take, bai hanata kuka ba. "Ayya mutuwa me yasa zaki dauki bawan Allah ko bar mutanen banza? Mutuwa me yasa ba ki dauke marasa kunyar dakin Badi'atul Noor ba?" Babu wanda ya kulata, kafin wani lokaci dakin Ummi ya cika sosai da jama'a har wurin goma na dare kafin aka watse. Sai wurin karfe biyu Ummin ta farka, ta zauna tana kallon yaranta da suke zaman gadinta. A hankali ta tashi zaune ta zuba musu idanu. Wani abu ta ji ya taso ya tsaya mata a kirjin ta, fiyye da yadda bata tsammani ya tsaya mata, a hankali ta zare jikinta zuwa ban daki, kunna ruwa yana zuba a tsakiyar kanta. Kuka take son yi amma ta kasa yin kukan sai ma jin wannan abin da ya mata bake-bake. Haka tayi wanka da alola ra fito , sannan ta shimfida abin sallah. Ta sauke Isha da yake kanta da shafa'i da wutiri. Tana idarwa ta zauna a wurin baki daya wani irin tausayin shi take ji, tausayin d'a da Uwa, tausayin irin na jin kan D'a da uwa, har lokacin so take tayi kuka domin zuciyar ta kamar an hura mata wuta ne, tana zaune a wurin tsawon daren gani take kamar gari ba zai waye ba, a rayuwar ta bata tab'a ganin dare mai tsawon wannan daren ba, abu daya yake yawo a ranta, shi ne ranar da ta haife shi, yadda aka daura mata shi a kan cinyarta. Abu na biyu ranar da ya fara shan nono, abu na uku ranar da ya fara mata dariya, wadannan abubuwan bata iya mantawa da su har ta koma ga Allah. Ba zata iya manta su ba, har ta daina numfashi. Anya akwai abin da ya kai mutuwar D'a girgiza? Bayan na iyayenta bata ji mutuwar da ya hana ta barci ba, sai mutuwar. Ko ta lumshe idanunta Maina take gani yana dariya, baki daya zuciyarta a cushe yake da dinbin tashin hankali, so take taji ko da gaske ne, mutuwar ce, yakushin kanta tayi, ta ji zafin a fatar da ranta. "Alhamdulillahi" ta furta, yadda ta ga rana haka ta ga dare, wurin uku saura ta tashi zuwa ban daki ta kuma dauro alola taso ta fara nafilla har aka yi aka kira sallah farko, ta gabatar da raka'atul fijr, tana cikin Addu'a, su Rumaisah suka farka ganinta kan abin sallah ya basu mamaki, amma basu yi mamaki ba domin ita din Ma'abociyar ibada ce, haka suka wuce kowacce tayi alola ta fito suka yi sallah, kafin suka juya gare ta. "Ummin mu ina kwana? Ya karin hakuri Allah ya mishi rahama!" "Lafiya lau, Alhamdulillahi Amin Ya Allah " ta fada fuskar ta a sake, haka suka mata ta'aziyar dan uwannsu sanan suka zauna har gari ya fara haske kafin suka kama aikin gyaran ɗakinta, Rumaisah ta wuce kitchen din da yake saman ta mata abin karyawa. Tana aikin ta ji muryan Abban su, ya shigo katse kome tayi ta fito ta Gaishe sa. Sannan ta koma tea tayi da pan cake,ta kawo ɗakinta Ummin, ya ajiye mata. Har lokacin abban su yana falon suna tattaunawa akan zuwan su. "Ina ga ayi jana'izar shi a fada kamar yadda akewa kowa, domin waziri ya bukaci idan aka kawo shi ayi wani binciken, ni kuma ina ganin a bar shi kawai a mishi suturan shi a wuce da shi gidan shi na gaskiya" kura mishi idanun tayi kafin ta ce mishi. "Ban gane ayi wani binciken ba, dama jinya yayi ne?" Gyada mata kai yayi, cikin sanyin murya ya ce mata. "Jinya yayi sosai tsawon shekaru huɗu yana jinya tun komawar Abuturab can." A hankali ta janye hannunta cikin nashi ta kura mishi idanun kafin ta ce. "Allah ya gafarta mishi yasa jinya ta kankara zunubi" "Amin Ya Allah " haka ya mike yana kallon ta. "Zauna ka karya mana" ta ce mishi, girgiza kai yayi, yana murmushi. "Bana jin yunwa" sai a lokacin ta lura da wani irin rama da yayi fuskar shi ta fitar da tsufar shi abin da da bai da shi, haka ya fita kamar wanda aka mishi duka. Can wurin karfe goma Sultanate ta shigo tana kallon Ummy Aymana da take saka turaren wuta. "Sannu sara me bakar takashi, so kike na gaishe ki?" Banza da ita Ummy Aymana tayi tana cigaba da aikin ta. "Dama kune kuka mutu aka bar min Buba Maina" "idan bamu mutu ba, sai ko.kashe mu yar renin hankali" ta fada kasa-kasa. "Kika zagi uwata Aimana?" Sultanate ta fada cikin d'aga Murya salon kowa yaji abin da ta fada. "Kyaji da halin ki" "innalillahi wa'inna illahi raju'un, wayyo Allah na yau ni ake zagi ko tausayi min rashin Buba maina yar nan bata yi ba take zagina ciki da waje." Ta fashe da kuka, "Aymana me yasa baki jin magana.ne? Baki ga halin da ake ciki ne? Fisabilillah sai kin saka jinin Ummi ya hau ne?" "Tow Didih don Allah me na mata? Ta gaya muku me na mata?'" wani kallon banza ta watsawa Sultanate, ta wuce. "Kuyi hakuri Sultanate " "Ai dole nayi tun da Buba Maina ya mutu sai ku min abin da ranku yake so, shi daya ne yake sona da gaskiya wayyo mutuwa me yasa baki dauke ni ba" ta fada tana rushewa da kuka, maganar gaskiya mutuwar Maina ya daki Sultanate, duk da tsanar da take mishi bata kawo cewa zai tafi very soon ba, ita kawai tafi ganin cewa gara ta nisan ta su ga thrones na masarautar sama da ta tab'a lafiyar su, duk da takun sakar da suke yi da Uwar su, duk abin da Sultanate tayi Maina Uzuri yake mata, ya kance soyayyar danta ne yake janyo take musu wulakanci da cin zarafin su, yana yawancewa akwai wani boyayyen al'amarin da Sultanate tayi yasa take tsoron kar ya shafe su. Shi yasa take kare danta, sannan ya tab'a gayawa Rumaisah cewa Son da take musu yasa bata son ganin suna cikin masarautar domin za a iya cutar dasu saboda mahaifin su, ta gaya mishi haka ne lokacin da ya je mata sallama zasu bar kasar. Ire-iren waɗannan abubuwan yasa take kin su, duk da ta sha gaya mishi. "a duk lokacin da kasan laifin da nayi da hannunka zaka kashe ni har lahira kafin hakkin ya fara bibiyar ku, domin nasan ba iya kaina da Mahaifin ku zai tsaya ba. " Hawaye ne ya zubo daga idanun Rumaisah tunawa da tayi da kalaman sa, tabbas akwai wani abu da yake faruwa a cikin masarautar tun.kafin a haife su, "tow meye shi?" Kalaman Sultanate taji tana faɗin. "Allah na tuba, Allah ka yafe mana"
***
Colleague na wurin aikin Maina su. Zo da boss dinsu, musamman yan uwa musulmai da suke aiki tare, kowa ya ji mutuwar shi. Haka gidan baya ya kasance da masu zuwa gaisuwa. Tun ranar da ya rasu Likitan da yake kan shi ya kira Latifah da dadare ya bata file din ciwon Maina, ra firgita kamar zata mutu, tsoro ya hanata sakat wani abin da ya kara furgitatta shi ne sakon da ake turo mata. *Nasan zuwa yanzu babu wanda yasan ciwon da ya kashe Maina! Ki kula da rayuwar mahaifin da ta Mahaifiyar ki, ko na shi wanda kike Haukar kina, ko ita Badi'atul Noor bata wuce ayi lomar tuwo da ita ba, balle ke kiyashi. Ki kona file din nan awa 72 kafin ki shigo nigeria ko kuma hmm Yarinyar zaki gani da idanun ki, layin ya fara sauka akan Maina ko waye next?* Ta matukar kaduwa da ta ga sakon hakan yasa taki haduwa da kowa gani take kamar ma zasu fahimci barazanar da ake mata shi yasa taki fitowa.
***
Sa'ade tunda suka gama jarabawar su, Yusuf ya zo ya tafi mata da kayan ta, sauran ya bari ranar da suka yi hutu sai ta tawo da sauran. Yasa baki daya take takure. Don ma tana amfani da kayan Husnah da Rahilah, wani irin soyayya suke mata, kuma babu hassada ko Kyashi zaman su akwai dadi da fahimtar juna, ganin Kubrah zata kawo musu rigima yasa suka watsar da lamarin ta, gobe ne bikin yaye daliban aji shida, yasa suke ta kintsa kayan su, saboda su ranar zasu bar makaranta, yayinda wasu sai juma'a. Haka suka yi ta shiri ba, gefe guda wasu sun kafa hira wasu gulma. A cikin yan gulma har da Kubrah. Ganin tun shekaran jiya da suka yi fada da Sa'ade bata kuma shiga harkata ba, yasa ta koma gefe tana zaginta Ita da wasu Kawarta me suna hajiyayye. Ita kanta Hajiyayyen ba wani abin arzikn yake haɗa su da Kubrah sai cuta, domin kuwa kwashe mata kayan abinci take da wayo, wai a haka tafi su Sa'ade kaunarta.... Top-notch 08130269641
[06/06, 8:36 am] usmanlauratu71: 29.. Ganin yadda ta sauya tsarin Rayuwar ta, yasa suma suka watsar da ita, washi garin da za ayi taron tun wuri suka gama shirin su, daga nan wurin taron zasu wuce gidan su Husnah, domin yawo zasu yi kafin raka Rahilah gidan su. Daga nan ta wuce gida itama, sai dai wannan karon tayi alkawarin zata Maikulki ganin Innarta ta gaji da zaman sai tazo ganin ta. Komawa yayi ta kwanta tana dafe kanta. Tab'ata Rahilah tayi tana tambayar ta lafiya? Yar karamar murmushi tayi sannan ta mike zaune tana dafe kirjin ta. Janyo jakar makarantar ta, tayi ta zuge zip din. Wani littafi karami pink colour me zanen butterflies, sai hoton daya daga cikin barbe tana tashi sama. Dariya suka fara mata, bude littafin tayi ta zaro pen din da yake zuwa da littafin ta, ta fara rubutu cikin gangariyar turanci akan wasu yanayi na shauki da take ji, tare da matsanancin kewar Hamma Abuturab da take kwana da shi take ta shi da shi. ```'I feel bad'

I feel like crying in vain,

I don't know how to end this pain,

coz I am missing you so much,

your words and your thought,

please come back in my life my dear,

I really don't have any reason to cheer,

please come back oh dear!``` kwace littafin Husnah tayi, ta ware idanun tana kallon Rahilah ta juya tana kallon ta, hawaye ne ya cika Idanunta, ta fita da gudu tana shaƙar iskar da yake kad'awa, lumshe idanunta tayi tana shaƙar iskar, haka kawai take jin kuka da kuma farin ciki mara iyaka. (🤣😂😹 Yanzu sai su kwashe min albasa me lawashi😭😂 i found love) fitowa Rahilah tayi tana me riko hannunta. Suka dawo cikin dakin. "Da gaske kin yi missing din shi har haka ne? Ko dai ko dai?" Zare idanu tayi tana girgiza kai, alamar a'a ba haka ba ne, da hannun Husnah tambaye ta, "tow meye nufinki na rubuta wannan tsadaddun kalmomin masu tsada da kwarjini, ni kin sani ma na ji ina son na ruhutawa Ya Muhsin " sake mata duka Rahilah tayi akan cinya tana nuna musu lokaci ya tafi, a wrist watch ɗinta. Mikewa tayi domin sha daya ake nima, suna shirin fita Kubrah ta shigo ita ɗaya, ta cancad'a kwalliya kamar zata wani wurin biki. Babu wanda ya ce mata, tattara kayan su, suka yi a wuri guda suka rufe sannan suka fita. Suna hira.
***
Karfe sha goma da arba'in da tara, jirgin Maxi air, ya sauka babban airport din Lagos. Sanye yake da wando kaftani sage green sai rigar jamfa ce Ivory colour, hannun shi na sweater coat, kasancewar sun tsaya a Island, sakamakon matsalar da jirgin taso samu, haka suka nime kayan sanyi domin yanayin garin akwai dan ƙaren sanyi. Hannun shi na hagu rike da Annur, a hankali kowa yake saukowa, suka nufi inda zasu zauna su jira jirgin da zai wuce da su kwara. Idanun shi toshe yake da bakar madubi na sunglass, ya saka ne domin hana mutane gane halin da yake ciki ba. Wurin karfe sha daya da rabi aka fitar da gawar Maina aka mai da ita cikin jirgin da zata wuce da su, sai da aka gama shiri sannan suka dauki hanya zuwa kwara, idan ka ga yadda jikin su yayi sanyi musamman Saraki da yake jin kamar bai da lafiya ta cikinsa. Sai Hamdiyah da take ta kuka, gwanin ban tausayi, wurin karfe aha biyu da arba'in da biyar suka isa kwara, manyan jami'an gwamnati da manyan a cikin emirate council suka zo taran su, har suka isa fada garin ya cika da mutane. Kafin ka ce me an samu an shigar da gawar Falourn Sultan. Akan lokaci likitoci da forensic suka shiga nasu binciken. A can bangaren Sultanah Badi'atul Noor, tunda Hamdiyah ta shigo ta kwanta a jikinta tana kuka tana faɗin. "Ummina na zama marainiya, Maina shi ne Uwata shi ne Ubana, shi ne abokina bani da kawa sai Maina, Ummi Maina ya tsaya min nayi achieve din abubuwa, yana shirin kara min kwarin gwiwa ya mutu, Ummina Yaran mu" "Allah yana sane da Al'amarin ku" haka tayi ta shafa bayan ta, lokacin da Abuturab ya leko dakin ya cika makil, daga nesa ta hango shi, murmushi ta sakar mishi na kwarin gwiwa. A can Falourn Sultan kuwa, waziri Dawud ne akan binciken ana gamawa ya saka a briefcase dinshi ya cire babban rigar shi ya nad'e kafar wandon shi da hannun rigar shi, tare da Saraki. Zasu wanke gawar Sultanate ta shigo tana kuka da kururuwa. A bayan ta Abuturab ne. "Ya isa haka mamaci bai son kuka da kururuwa." "Ungo naka nace maka dan banza mara kunya yo ai da kai ka mutu ko kuka ba zan yi ba" yasan duk da tsufa da rikici amma baya tunanin ko gawar sa ta gani sai tafi haka haukacewa domin wallahi asalin rigimar su da fadar su soyayya ce, laifin yadda Ummi tayi ta haihuwa su maza ne yake bata haushi. Domin da jimawa sun yi haka da ita, da ya ce mata. "Wai ke me yasa kika tsane mu?" "Banza halin uwarka da tayi ta zazzage ku maza uku, ina laifin tayi maza biyu Allah ya raya su, shine don munafinci ana son a kashe min Yarona shi ne ta haife ka da idanun a tsakar ka." "Kina nufin zuwa na ya hanaki rawan gaban hantsi ne?" "Dan banza mara kunya, kai ban da kana da sauran shan ruwa ai da ka jima da mutuwa dan farka me rantalelan kai" ajiyar zuciya ya sauke, fitar da ita yayi tana kuka tana dukar shi. Haduwa suka yi a hanya da su Abdulrashid da Hajiya Suhailah sai Yarta autar ta Sahra. Kallon juna suka yi na wasu dakikai. "Aliyu ya hakuri" "ungo naki Suhailah ai ko babu kome kya kira shi da Baba karami, tunda sunan Uban Mijinki ne." Shiru tayi bata kula Sultanate ba, "Abuturab ya hakuri, ashe kuma Maina ya tafi?" "Eh wallahi Babban Yaya " ya ja hannun Sultanate. "Baby prince ya hakuri? Ashe Hamma Maina lokaci yayi." "Eh Sarah " ya fada yana barin wurin. "In ji Hamma Abdulkarim wai na mika maka sakon ta'aziyar shi, in sha Allah zai zo kafin ayi Seven " "Allah ya kai mu, Allah ya kawo shi." Haka ya kai ta ɓangarenta, sai kuka take. "Kin gan ni ba zan iya rarrashin ki ba, wanda yake rarrashin ki kenan ya amsa kiran mahaliccin sa, don haka ki daina kuka domin ba zan yarda ji daurawa Abba wani damuwa ba. Ki kula da kanki " takaici yasa ta rufe shi da duka, jikinta yana rawa. Tabbas mutuwar Maina ya girgiza Sultanate. Ba zai ce ba amma kuma yadda ta firgice abin yana bashi mamaki da daura ayar tambaya akanta. Mikewa yayi zai fita ta riko hannun shi. "Kar ka sake ka yarda da kowa, ka gayawa Saraki kar ya ci abincin kowa ko ya sha ruwan sadaka, idan kuna jin yunwa ga wannan key din store na ne" kallon ta yake cike da mamaki yana kuma kara jin wani abu a ransa. Durkusawa yayi a gabanta ya zuba hannun shi akan gwiwar ta. "Me kika nufi?" "A'a bana nufin kome ka san dai abin da yake faruwa a gidan nan kawai ku kula da kan ku." Haka ya mike tare da ajiye mata key dinta a kan cinyarta. "Ga kayan ki." Ya juya ya fita. Ba tare da ya kuma mata magana ba, domin hankalin shi ya koma kan Saraki. Yana zuwa falon Sultan ya samu sun gama wanka ana shirya shi Abdulrashid yana goge falon, koma cikin gidan yayi ya dauko turaren wuta aka saka a falon, lokacin an gama shirya gawan. "Saraki jeka dauko mahaifiyar ku da matar shi, da matar shi." "Tow Abba " har a lokacin Abuturab na kallon abin kamar a mafarki. "Abuturab ko zaka dauko mana Sultanate ne?" "Abba kyale ta depression zai mata yawa domin kusan sai a hankali kamata yayi a tura mata likita ya duba ta." "Kaci kaniyar ka, gani da kafana ba dawo. Wai ni mutuwa me yasa baki dauke dan banza me taurin zuciyar nan ba, kika dauke Buba Maina." Ta fada tana sakar mishi duka a baya, zuwa tayi ta zauna a gaban gawan Maina. "Buba Maina haka min ? Haka zaka min baka zuba min kasa ba, nice zan zuba maka kasa? Buba Maina me yasa zaka tafi lokacin da Badi'atul da Abdurrhmanu suke buƙatar ka?" Ta fada tana kuka, jikin kowa yayi sanyi domin kuwa kowa yasan yadda ta tsani Yaran Badi'atul Noor. Shigowar su Ummi, yasa ta kallon su. "Sannu Badi'atul Noor." Murmushi Ummin tayi tana isa kan gawar Maina, dafa kan shi tayi tana mishi Addu'a, tana gamawa ta sumbaci goshinsa. "Abubakar Ubangiji ya amshi bakuncin ka, Rabbana ya haskaka ya haska kabarin, Allah ya baka ikon amsa tambayoyin ka, Ubangiji ya raba ka da azabar kabari, Ya Allah nayi tawassali da sunayenka tsarkaka ka jikan Abubakar ka mishi rahama, ka yafe Mishi kura-kuran sa. Ya Allah ga bawan ka nan" ta fada haka, mikewa tayi ta ce. "Ina ga sun gama ku mika shi makwancinsa na gaskiya " tana fadar haka, wani irin duhu ya lullube idanunta, Allah yasa Saraki na bakin kofar, yadda ta jefa kafar ta, sai komawa tayi zata fadi, baki daya Yaran suka tare uwar su, da sauri Suka kwantar da ita. Numfashi ta yana sama da kasa. "Ku kai shi gidan shi na gaskiya" "Ummy Aymana ina kayan aikinki" Saraki ya tambaye ta, "yana sama bari na dauko" shigowar Latifah, dama yadda ta ga Ummin ta fito daga falon ta, tasan za ayi haka. Shi yasa da ta ji an bakin kofar na faɗin Sultanah Badi'atul Noor ta fadi ta koma ta dauko kayan ta, akan lokaci ta shiga kokarinta, baki daya Ummy Aymana gani take kamar bata taɓa rike ko da safar hannu ne, baki daya ta rikice ta fice, fita da gawar Maina aka yi a falon, aka tafi jana'izar shi, "Saraki muje da kai, Abuturab ka koma ka duba su idan da hali ku wuce asibitin." Duk yadda yaso yaga kabarin Maina haka ya hakura, yana zuwa yaga babu wani cigaba shawara ya basu aka wuce da ita asibiti. (Ya Allah ka jikan iyayen mu da sauran al'ummar Musulmi baki daya)
***
Wurin sha biyu aka fara taron, Tsohon Kwamishinan ilimi, Dr Sharif ya samu halartar taron tare da Abdulhakim. Ana cikin taron wayar Abdulhakim tayi ta ruri dole ya fita daga cikin rumfar ya nufi wajen makarantar. A hankali yake takawa yana duba me kiran shi, kasancewar makarantar babu kowa ana can wurin taron, irin bugawa karfen da yake kirjin shi yayi, a hankali ya rike wurin tare da durkusawa kasa, yana haki jini ne ya shiga fita ta hancinsa. A hankali ya sulalle kasa ya fadi. Sa'ade ta fito daga hostle saboda mantuwa da tayi ta koma ta dauka, tana son ta koma inda suke zaune, har ta wuce shi sai ta kuma dawowa, a hankali ta isa kanshi, tana kallon shi. Dishi -dishi yake hangota. Sake bude idanun yayi tana girgiza kai. Dulum ya daina ganin a hankali ya rufe idanun shi. Wayar shi da ta gani a yashe shi ta dauka. Ta fara juyawa shi bata san yadda ake amfani da shi ba, kira ne ya shigo wayar baro-baro ta ga an rubuta My Super hero. Da sauri ta katse kiran ta shiga call din, sake kiran aka yi ta katse, tunda bata da yadda zata yi magana, sako ta turawa layin. *Wannan me wayar gashi nan yayi collapse* ta tura da sauri. Can aka kuma kiran shi. Katsewa tayi ta ce. *yana harabar makarantar ba zan iya magana ba* can kuwa sai ga wasu daga cikin malamai da shi kan shi tsohon Kwamishinan ilimi, tana durkushe a gaban shi, isowa wurin suka yi. "Sir bai da lafiya ne?" "Ina ga" godiya suka mata, Malam Dalhat ya tambaye ta yadda abin ya faru ta gaya masa, shi ya musu bayani, sannan suka sallame ta......08130269641 Top-notch 🙄 🚶🏽‍♀️🚶🏽‍♀️😹🤣😂😹😂 Chaiiiiiiii ye... Mu hadu a intermission babu dual typing daya ne kawai Yasin
[07/06, 10:53 am] usmanlauratu71: 30... Sam ita bata dauki abin da ya faru da wani babban al'amari ba, domin ita abin da yake gabanta ya fi karfin ajiye faduwar shi a ranta, tana shiga wurin taron baki daya ta manta da wani, suna zaune a wurin har aka tashi, sannan suka nufi dakin su. Suka dauki kayan su, suna fitowa bakin get suka hadu da Ya Muhsin dan Yayan Baban Husnah, abin dariya a madadin ta shiga gaban motar, sai ta koma tana rab'e rab'e kamar ba zata shiga ba, su kuwa suka wuce baya suna mata dariya, tun sanya shiga gaban motar ta kifa kanta a saman cinyar ta. Sai dariya yake yana mamakin kunyar Husnah haka ya ja su, har gidan su Husnah suka wuni zuwa yamma aka wuce da Rahilah gidan uban goyonta a kofar gidan aka sauke ta tana d'aga musu hannu. Suna tafiya ta shiga cikin gidan. Yayan Babanta ta gani da manyan baki, bata san su ba. A dan tsorace ta gaida su. Ya fatota yayi da hannun shi. Ya nuna mata wani mutum. "Wannan dan uwan mamanki ne. Sun zo daga Yola ne ganin ki" wato da ta fashe da wani irin kuka, ta rungume shi, shi kasan kasa rike kukan a'a yayi yana shafa bayan ta, kuka take tana girgiza kai. Shafa bayan ta ya shiga yi. "Alhaji Zailani zan tafi da ita Yola." Cikin yar taburman kunya ya ce. "Allah sarki idan ka tafi da ita kar kace zaka rike min 'Ya da ita nake tuna dan uwana da matar sa." "Ba zamu rike ta ba, zan dawo da ita idan Hutu ya kare." "Ai shi kenan " ya fada yana kallon yadda take kara rike hannun Kawunta. Cikin gidan ya ce ta shiga gobe zai zo daukar ta. Dakyar ta amince. "Allah sarki da alamu tana kewan iyayen ta ne." "Eh barista. Alhaji zamu tafi sai goben in sha Allah." Haka suka yi sallama. Tana shiga cikin gidan, Mama ta dauke kai kamar bata ganta ba, bata kula ta ba ta shiga dakin su ta fara gyaran dakin tana mita a ranta. Har ta gama ta share dakin sannan ta fito ta ja ruwa a rijiya ta wuce wanka, tana fitowa. Yayan Babanta yasa aka kira ta. Sannan ya mika mata kayan da dan uwan Mamanta ya kawo mata, ta karba tana alamar godiya. Ta bar wurin dakin su ta koma ta fara bude kayan a dakin su. Tasan bata da rabon abincin rana, kuma bata saka kanta ba. Tsarabar da aka kawo mata shi ta ci ta koshi sannan ta wuce ban daki tayi alola domin lokacin la'asar yayi.
***
Abdul Hakim, sai wurin karfe biyar na yamma ya bude idanun shi, ganin shi kwance a saman gadon asibiti. Yasa shi mikewa zubur, yana kallon Mahaifiyar shi da take zaune tana duba jarida. "Hajiya Ina yarinyar da ta zo kaina?" Ajiye jaridar tayi tana kallon shi kafin ta ce mishi. "Babu wata yarinya, tashi kayi lokacin sallah ya wuce maka" "Hajiya yarinyar" "ka wuce kayi sallah, bana son magana. Sai da nace kar ku tafi tare ina son ganinka shi ne ka bi shi. Yanzu kuma ka je ka kwaso aljanu zaka saka ni gaba" ta fada cikin matsanancin masifa, bai kula ta ba sai ma wucewa ban dakin da yayi, ya dauro alola. Sallah azhar da la'asar ya sauke tare da fatan Allah yasa ba aljana ba ce, "sai ka tashi ka ci abinci." Yasan idan ya ce ya koshi jidali ce, don Allah ya tashi ya karbi abincin da ta zuba mishi, har ya fara cin abincin ta wurgo mishi wata mahaukaciyar tambayar da ta sanya shi kwarewa. "Wai kai da matar ka waye bai da lafiyar haihuwa ne?" Tari ya fara, mika mishi ruwa tayi. "Eh jika nake so kai ne baka da lafiyar haihuwa ko ita ce, idan kai ne sai a sallame ta idan kuma ita ce sai ka kara aure wannan shi ne gaskiyar maganar " shiru yayi yana kallon kasa. "Hajiya lafiyar mu lau " "ungo naka nace Abdulhakim! Sai na zabga maka Mari" shi dai bai ce mata kome ba, ta cigaba da masifa" inda na tabbatar kai ne sai kaci kaniyar ka, domin ba zan yar da na zauna ina kallon ka a idanun kamar me lafiya amma a bad'ili kafin kowa matsala ba" hàdiye yawu yayi yana kallon abincin sa. Wacce irin tsana Hajiya take mishi haka? A hankali ya ajiye plat din ta daka mishi tsawa. "Dauka ka cinye min ko ranka ya b'aci" kamar yaro karami haka ya dauki abincin yayi ta cusawa kamar zai yi amai, shigowan Dr Sharif da Aunty Faridah yasa shi sake ajiyar zuciya yana kallon su." Cinye min ko na sab'a maka" "idan ya koshi a kyale shi mana" inji Dr Sharif yana amsar plat din. "Yaya ya jikinka?" Inji Aunty Fareedah. "Da sauki sosai Aunty Mom." Mikewa Hajiya tayi tana tsaki." Zan tafi sai a baka nono" babu wanda ya ce cikanki har ta fita. "Abba akwai yarinyar da tazo." "Auya sunanta Sa'adatu Aminu Fulani." Wani irin abu yaji tun daga tafin kafar shi har tsakiyar kan sa. Murmushi yayi ya ce. "Abba tana cikin masu gama makarantar ne?" Murmushi shima yayi yana girgiza kai. " Yar aji hudu ce." Murmushi ya kuma, shi daya sai murmushi yake ya d'ago zai magana Aunty Fareedah ta ce. "The charm prince met cendirellah." Wani irin blush tayi yana ji wani irin kunya. "And kana sonta" wani irin yanayi yake ji na wanda bai san mai zai ce ba. "Fiye da so!" Dafe kirjin shi yayi daidai bugun zuciyar shi ya ce. "Tun da na hango ta daga can nesa naji zuciyata ta daina bugawa," bai san ya aka yi yake sake magana haka ba, sai dai yasan sakon daga zuciyar shi ce, ya kasa control din kan sa. Su kansu dariya suke mishi domin ya samu abin da yake so. "Amma ka sani kurma ce." Murmushi yayi ya ce. "Abba nima bani da lafiya, gara it kurma ce ni fa? Rayuwata tana tsakanin mutuwa da rayuwa, gara ita zata iya rayuwa mai tsawo da farin cikin, nifa? Babu tabbacin zan kai har haka. Domin kullum da ciwon karfen nake kwana." Jikin su yayi mugun sanyi sosai.
----
Tunda Husnah suka sauke ta shiga cikin gidan, ganin Inna Larai yasa ta daka tsalle ta rungume ta. Suna dariya yayin da Rabi da Harirah suka rufa mata aka shiga farin ciki. Tambayar su tai me ya kawo su?
"Baffa bai da lafiya yana Asibitin koyarwa na Udut. "me yasa me shi?" Watsar da hannu suka yi suna fada mata basu sani ba. Dakin Aunty Ummy ta shiga tana tambayar ta, me yasa mu Baffa.
***
Kwara.
Idan Allah ya tashi jarabtar ka, babu tsumi babu dabara, haka ne ya faru domin baki daya kowa yana mai da hankalin shi gidan rasuwar, yayinda aka bar Ummy Aymana da Latifah a asibitin wurin Ummi wacce bata san inda kanta. Haka suka cigaba da da zama, har zuwa dare da Ummin ta farka. Fita Ummy Aymana tayi ta kira likita. Koda likitan yazo ya gama dubata. Sannan ta mata wani allura ya ce musu. "Zata farka jikin da sauki gobe, amma don Allah kar a d'aga mata hankali ko abin da zai d'aga mata hankalin. " Gyad'a mishi kai suka yi, har ya fita babu wanda ya iya magana, sai can dare Abuturab ya kira su, ya tambayi jikinta suka ce da sauki. Washi gari. Da asuba ta farka tana farkawa kuwa ta tubure a sallame ta, babu yadda suka iya dole suka sallame ta, tana isowa jikinta ya dauki rawa, tabbas akwai wani bakon al'amari da zai faru, idan har lissafin ta daidai ne, kasa cigaba da ta kawa tayi tana kallon yan zaman makokin, kai tsaye ta wuce falon Sultan. "Ina Umar Saraki?" "Badi'atul me yasa zaki ce a sallame ki?" "Ina Umar Saraki?" "Ya ce kin kira shi, kin ga inda yake zaune kika kira shi ko ?" Da wani irin azama ta fito da gudu daidai shigowar Ambulance cikin gidan, cak ta tsaya tana kallon motar, wani irin rawa jikinta ya dauka. "Ina Abuturab?" Ta tambaye su jikinta yana sake daukar wani irin rawa. Kamar makauniya haka take bin motar tana shafa shi. "Sarakina yana nan, me yasa kuka bar shi ya fita?" Wasu mutane biyu suka fito daga motar bayan sun bude motar, baki daya suka yi bayan motar, Umar saraki ne a kwance kafar shi sanye da takalmin shi kafa daya, babu kafa ɗaya. Rufe baki Sultan yayi, bai tab'a ganin tashin hankali irin na yau ba, a hankali ya taka har gaban gawar ya bude yana kallon Umar saraki kwance, gaban goshinsa ya lutsa, jini yana fita ta hancinsa da kunnen shi. "Ku saka hannu anan." "Me yasa mishi a ina kuka same shi ina motar shi?" "Muma kiran mu aka yi, yayi hatsari a yadda aka gaya mana, motar shi ce tayi faci, shi ne ya fito zai sake taya. Wata motar daukar yashi ta zo da gudu ta make shi." "Sun kashe min d'a na biyu." "Badi'atul wannan wani irin zance ne, Abuturab zo ka taimaka mana a wuce da shi." "A'ah a'ah bar shi na boye shi kar su same shi, shima iya shi ya rage min " ta riko hannun Abuturab suka wuce can cikin part dinta, yadda zaka tabbatar da a gigice take, baki daya ta fita hayacinta. Kokarin niman maboya take tana son saka shi. Bude wardrobe tayi tana kokarin shiga tana cewa. "Zoka boya babu me ganinka " rungumar ta yayi yana kuka, "A'a Ummi, kij manta ko a cikin ki kika mai dani mutuwa zata bibiye ni? Ummi Ina yarda da kaddaranki yake? Ina imaninki yake? Yaushe zaki yi ta boya saboda mutanen da baki sani ba? Kar ki manta basu cutar da kowa ba, kema baki cutar da kowa ba, Ummi wallahi bana raba daya biyu su din bayin Allah ne, kuma kowannen su bana cire tsammanin yan aljanna ne, don Allah ki daina kokarin gudun matsalar ki." "Dole ka bar garin nan, ka tafi can can ka tafi su nime ka su rasa, ka nisanci masarautar don Allah." Tayi kamar zata durkusa mishi , rike ta yayi yana kallon yadda ta firgice. "Zauna " ta fada mishi, ba musu ya zauna yana kallon yadda take kokarin ganin ya zauna domin kar wani abu ya same shi. "nasan Ummina jarumar Uwa ce, wacce take tsayawa domin kare maslahar ta, idan har Ummina ta juya a guje waye zai tallafi rayuwar Sultan? Wannan yakin ba iya ke daya bace, har da Sultan ne karki manta suma Yaran sa ne waye zai rarrashe shi a rashin da yayi na manyan yaran shi a cikin kwanank tsakani? Idan har Ummin da na sani ce tow wallahi ba zata zauna domin wasu da manufarsu ba, ku barni na tsaya akan gawar dan uwana, kin ga sai buga mana kofar ake. Please Ummina nasan ke me hakuri ce da yarda da duk abin da Allah ya ƙaddara miki " "tow naji kar ka kula kowa." "Na yarda" dakyar ya fita ta bar ta da yan uwansa, har zai sauka Zakiyyah ta kwaila mishi kira, dukkan su uku haka suka tawo da gudu suka rungume shi, wani irin nauyi yaji ya karu mishi, kamar ya cire zuciyar shi ya huta. Dole yayi aure ko don taya Ummi ɗaukar nauyin yaran yayun shi. "Kun rike ni, kar na kai gawar Saraki kenan?" "Tsoro muke ji kar wani abu ya same ka" murmushi yayi sannan ya ce musu. "Idan na mutu gaku nan " ya fada yana janyewa daga jikin su, yayi tafiyar shi domin baya son suga karaya da hawayen da yake cikin idanun shi, kusan tunda ya tafi falon Sultan gawar na ajiye babu wanda ya tab'a, shi ya isa ya dauki Almakashi ya yanke rigar, yana cire kayan hawaye na zuba daga idanun shi. Sai kallon shi duk dattawan suke. Shi kan Sultan yaƙe yadda hawayen bai hana shi kome ba, a falon aka wanke Umar saraki, aka shirya shi, Abdulrashid da Abdulkarim da yazo suka fara gyare-gyaren falon, a lokacin aka kira Aneesah wacce ta kasa ki kuka sai ajiyar zuciya, "Abuturab kashe min mijina suka yi, wallahi kashe shi aka yi. Maina ma kashe shi suka yi, ka binciko duk me hannu a cikin kisan su ka hukunta shi, duk wanda ya kashe su shi ya kashe Mansurah dole a hukunta su." Abu daya ne ciwon mutuwar mijinta ne yasa take surutu. Koda aka kawo Ummi sai idanu bata ko iya magana abin tausayi. Sultanate kan tsabar tashin hankali sumarta uku, tana kuka tana cewa don Allah mutuwa me yasa bata dauke ta ba, ta bar Yaran da babu ruwan. Haka aka tafi aka sallaci gawar. Bayan an kai shi aka dawo sabon zaman makoki aka cigaba da yi, duk da a ranar Maina ya cika kwana uku, ana sallah la'asar aka mishi Addu'a. Haka kwanaki suka tafi, har aka Addu'oin bakwai maina da Addu'ar ukun Saraki a rana guda, daga nan aka watse.
Bayan sati biyu.
Ummi ta saka Abuturab ya bar ƙasan, ya koma Ingila da Baban Latifah zai koma suka koma, abin tausayi ranar da ya koma yayi kuka kamar ta cire zuciyar shi ya huta. Domin kuwa yadda kome yake dawowa akan idanun shi kamar yanzu abin yake faru. Ya manta da Sa'ade da farko yayi alƙawarin idan kome ya lafa wato bayan rasuwar Maina zai je yaga yadda take, sai dai Mutuwar Saraki yasa baki daya ya manta da ita. Yanzu gani Nigeria yake like hell. Ya tsani Nigeria baya jin zai kuma taka kafar shi kasar.
***
Sokoto.
A cikin sati biyu Abdulhakim ya hana kansa sakat akan Sa'ade sai damun mahaifin sa yake yaje a yi Maganar da manyan don Allah. Uban yace mishi auren dole yake nufi a mata, ya nime soyayyar Sa'adatu Aminu Fulani, ya shirya tsaf zai tafi niman ta, amma ta ina zai fara niman ta.. *intermission*
Abuturab ya tsani Nijeriya, Abdulhakim yana can yana haukar niman soyayyar abar kaunar shi, ita kanta bata san halin da ake ciki. Yawwa yanzu zan ja zaren yadda labarin zai bada citta.... Ku tanadi tissue paper 🤧
[08/06, 9:18 am] usmanlauratu71: 31... Kawun Rahilah ya dauke ta, suka tafi Yola. Tun daga Sokoto suka dauki mikati babu bata lokaci. Kallon hanya take tana jin nutsuwa a ranta, babu abin da yafi dangin Uwa dadi, haka suka bar sokoton a fatar ta ma, ta tafi kenan amma idan ta tuna bata cewa su Husnah da Sa'ade goodbye ba, sai ta ji kamar bata kyauta ba. Kuma bata cancanci tafiya babu sallama ba, haka yasa ta kwantar da kai. Tana lumshe idanun ta, tana kewan kawayen ta babu laifi. Musamman Sa'ade don haka ta kwantar da kai tana jin barci yana fisgar ta,
***
Kwara
A can kuwa ba karamin ciwo Sultanah Badi'atul Noor tayi ba, domin wallahi mutuwar Yara biyu a kwanaki kusan daya yasa ta ta gigita, sai dai dake akwai Yaranta a jikinta yasa ta fara samun sauki, domin kuwa suna ƙoƙarin gano abin da zai sakata farin ciki.
Chapter 1 · 0% Book details