← Book details Safiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 3

Gabatarwa

Safiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 1086 min read

[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹


*By*


*Maman Maama*


Daga marubuciyar:
Maimoon
A'isha Humaira
Diyam
Tagwaye
Jidda

And now..... Safiyya


*Episode One: Bon appetite!*

Breakfast is Served💔

Bismillahir Rahmanir Rahim

Ina rokon Allah ya bani ikon rubuta alkhairi, ya hana ni rubuta sharri.


Assalamu alaikum dearies ❤️

Fatan munyi azumi da sallah lfy. Allah ya karbi ibadun mu ya sa muna daga cikin yantattun bayin sa Ameen.

So, kamar yadda nayi alkawarin rubuta Safiyyah after sallah, gashi nan zanyi kokarin cikawa 😁. Ku dai ku taya ni addu'ar Allah ya bani ikon cikawar. Lol

Believe me, dama nayi niyyar yi ne on an impulse, sai daga baya kuma na fara cewa "anya kuwa?" But then na riga na fada muku and duk sanda nayi magana ina matukar kokarin ganin na cika ta, sai dai when it is beyond my control, as nobody is perfect. So, we will try insha Allah, but you will have to be patient with me idan an samu rashin update akan lokaci, ina so ku saka a ranku cewa ina iyakacin kokari na.

Kamar yadda na faɗa, littafin Safiyya hopefully zai zo a matsayin free tun daga farkon sa har karshen sa insha Allah, depending on in mun samu sponsors at least twenty, ku kuma readers ina rokon alfarmar ku bada haɗin kai wajen showing support to the sponsors dan suji dadin cigaba da siya muku littafin Safiyya kuna karantawa, idan babu sponsors, littafin Safiyya zai koma paid after the free pages.

I hope we will enjoy this journey tare da Safiyya and Gidado, it is going to be rough 😁, but I promise you a smooth landing.


*Him*👳🏻

"Tell me you love me" yaji muryar ta ta daki dodon kunnen sa kamar a yanzu ne take yi masa maganar. Ya saka hannayen sa biyu ya toshe kunnuwansa sannan ya rintse idanun sa da karfi amma sai ya zama kamar kara clearing vision and hearing dinsa yayi. Abinda ya manta shine daga cikin kansa muryar take fitowa ba daga surrounding dinsa ba. A idonsa yana ganin fuskarta, as clear as the moon when it is full. A zaune a cikin motarsa, fuskarta dauke da murmushin da ya kasance tamkar maganin dukkan damuwa a gare shi, idanuwan ta cike da soyayyar sa.

"Tell me you love me" ta fada tana saita camera din wayar ta a fuskarsa, ya saka hannu daya ya kare fuskarsa yana murmushi. "Stop it!" Ya ce cikin muryar dariya, she giggled sannan ta chanja angle din camera din zuwa inda bai kare ba a fuskarsa. "Ka fada mana to, why are you shying away from a simple question. Do you love me?"

Ya bude fuskarsa yana kokarin frowning amma ya kasa, baya iya bata rai in dai yana tare da ita. Ya jingina kansa a headrest din kujerar motar yana kallon camera din tata yace "do you need to ask?" Tace "of cause. I want to hear you say it" ya lumshe ido ya bude yace "what is with the camera then?" Tace "as evidence. I want to record you say it sannan in ajiye as evidence yadda idan nan gaba ka ce baka so na ina da shaidar da zan shigar da karar ka zuwa kotun masoya".

Yayi dariya sosai yana kokarin ture camera din tata amma sai ta matsar away from his reaching hands, ta ce "confess! Say you love me" ya ajiye hannunsa ganin bata da niyyar bashi wayar yace "common! Why do I have to say it? Me yasa ke ba zaki fada ba sai ni?" Ta daga gira tace "because I say so... Kuma duk abinda nace ina so shi nake samu. Now I want you to say you love me". Ta karasa cikin turo bakin shagwaba.

Yayi ajjiyar zuciya "you are impossible Piya. Me zan fada miki ne wanda baki sani ba?" Tace "that you love me?" Yace "you already know that ai, you just enjoy.... enjoy.....en.." ta karasa masa cikin kwaikwayon muryarsa "you enjoy teasing me " sai kuma ta yi dariya. "You are right, na san dama ba fada zaka yi ba. I only wanted to see that" ta fada tana nuna fuskarsa, ya shafa fuskar kamar mai neman wani abu yace "see what?" Tace "your face is red my dear. You are blushing" ta karasa tana sake wata dariyar.

Yayi ajjiyar zuciya "Piya! You are...." "Impossible" ta karasa masa tana sake kwaikwayon sa. Ya harare ta "stop that" ta maimaita "stop that" ya fakaice ta ya zare wayar daga hannun ta sannan ya juya camerar zuwa fuskarta. Tayi saurin rufe fuskarta da hannayen ta biyu tana dariya, yayi zooming screen din yana karewa kyawawan fingers dinta kallo. "wa na kama?" Ya fada cikin tsokana, "now, tell me you love me" ta bude fuskar ta harare shi tare da murguda baki a lokaci daya, yayi murmushi "in dai har da gaske rashin kunyar kike ji da ita ki fada min inji. Say you love me" ya karasa yana rage murya can kasa. Ta fara laluben handle din kofar. "Ni ka bude min kofa. Ni hostel zan shiga" yace "kin isa ma, ai yau sai kin fada. Kuma inyi recording din ki in ajiye, in munyi aure mun haifi yara sai in nuna musu yadda maman su ta mutu a kaina" ta juya ido "wai ma, wa ya gaya maka haka?" Yace "I know...I just know. Tun ranar da kika fara gani na you just couldn't stay away from me, kinga dan farin bafulatani kin rikice, kince in ba ni ba sai rijiya" tayi dariya "ranar da na fara ganin ka, loving you was the last thing on my mind. Bana jin ma nasan menene love ɗin " yace "huh? Shi yasa kika bar seat din ki kika dawo nawa? Admit it Piya, you were attracted to me" ta juya idonta "shi yasa naga tun daga ranar duk inda nayi sai ka bini, bita zai zai" yace "tabbas, and this is just the beginning, duk inda kika je sai na biki. Naji na yarda ni bita zai zai din ne. Kuma nan gaba zan zama 'mijin kafin ta ce'"

Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, tana jin nauyin idanuwansa a kanta, ya sauke wayar tare da yin ajjiyar zuciya yace "Please Piya, I think it is about time ki kaini gurin Daddy, har yanzu baki gama jan ajin ba wai?" Ta dago kai suka haɗa ido "sai ka lallaba ni kuma ka bani cin hanci" ya gyara zama yana shafa aljihunsa sannan yace "whatever you want, just say it, kin san cewa I can give the world to you idan da tawa ce. I can go to the ....to the..." "End of the earth " ta karasa masa, yace "yeah, right, I can go to the end of the earth for you if you want me to" ta danyi murmushi tana kallon hannun ta, da alama hankalin ta ya fara tafiya wani gurin daban kamar yadda ta kanyi a duk lokacin da yayi mata maganar aure, absent mindedly tace "but earth doesn't have an end, it is spherical" yace "I don't care. Kin dai gane me nake nufi ai. I can do anything for you" bata ce komai ba sai ta juya kanta tana kallon waje, yayin da shi kuma ya rage ido yana kallon ta kamar mai tunani sai yace "but how do you do it?" Ta juyo tana kallon sa tace "do what?" Yace "finish my sentences. You always seem to know abinda yake raina tun kafin in fada" ta danyi kyakkyawan murmushin ta idanuwan ta suna reflecting tarin soyayyar sa da take cikin zuciyar ta tace "because I am your soulmate".

****.        ****.      ****.     ****.    ****

"I am your soulmate" yaji muryar ta tayi amsa kuwwa a cikin kwakwalwar sa. Kansa yake ji kamar zai tsage gida biyu. Ya saka hannu ya dafe goshin sa amma kuma sai yaji ciwon kamar a tsakiyar kan yake, amma kuma kamar ba ciwo ba, kamar wuta ce ake hurawa a cikin kan nasa da zafin ta yake saka gumi tsiyayowa daga cikin gashin kansa zuwa fuskarsa zuwa sauran jikin sa.

Ba ciwon kan ne ya fi damunsa ba, ciwon da zuciyarsa take masa ne yafi addabarsa. Wani irin zafi take yi masa mai kama da ƙaiƙayi , gashi tana lullube a kirjinsa dan haka babu damar sosa ta. Ya saka daya hannun ya dafe zuciyar tare da yin  ajjiyar zuciya da niyyar rage azabar amma sai yaji tamkar kara kaikayin yayi. Dama wannan shine heartbreak din da ake faɗa, wannan azabar shine abinda yan social media suke wasa da shi har suke kiransa breakfast? Amma lallai duk wanda yayi wasa da wannan to bai taba shiga irin wannan yanayin ba ne ba. Bai taba jin yadda ake ji ba, ba'a taba yi masa abinda aka yi masa yanzu ba.

She was his life. For years, bai taba hango future dinsa ba tare da ita ba. Bai taba ko da tunanin cewa zata iya rabuwa da shi ba because she lead him on, ta nuna masa soyayyar da bai taba tunanin akwai algus a cikin ta ba. Ya gama shirin komai na auren ta. Ya gama plan din komai. A mind dinsa har yayan da zasu haifa yayi picturing din su da kuma irin soyayya da kulawar da zai basu. Gidan da zasu zauna ya gama shi tuntuni. Ita kawai yake jiya, green light kawai yake jira daga gare ta and then suddenly bayan tayi tafiya ta dawo she came to his office da katon ciki a jikin ta and said

"I am married. I have been married for years. I am sorry"

And then she said "it was all a misunderstanding. I never thought you love me. You never said you love me da na gaya maka cewa I am married ".

"Damn it!" ya fada da karfi tare da mikewa tsaye kamar wanda aka yiwa allura. Sai kuma ya dafa bango sannan ya koma ya zauna, bai san ya akayi ba sai ya samu kansa da murmushi. "Ka zare Muhammad" ya fada wa kansa "ta haukatar da kai. Shi kenan ta ka ta kare. Yanzu ma gashi nan kana magana da kanka" sai kuma ya daki goshinsa da tafin hannunsa "damn you" sai kuma ya sake yin wani murmushin. May be haukan will be a blessing. At least in ya haukace gidan mahaukata za'a kai shi ayi tayi masa alluran bacci har karshen rayuwar sa. Then he wouldn't have to think about her. Then he wouldn't have to miss her, miss her smile and laughter, miss the feeling of blood rushing through his body whenever he gets close to her, miss the feeling of excitement whenever his phone rang and he saw her name "Piya❤️".

He already miss tsokanar da take masa, tana enjoying tsokanar sa sosai saboda sunan kakanta ne dashi, she used to say "Malam Muhammadu dan fulani, ka ga yar kyakkyawar budurwa shine ka gudo daga riga ka zo ka makale mata"

To ko wannan ma tsokanar ce?

Yaji wani irin hope ya ratsa zuciyar sa . Cikin sauri ya fara neman wayarsa har yana zubar da wasu daga cikin takardun kan desk din, ya dauka da sauri yayi dialing number din ta sannan ya saka a speaker, a ransa yana karanto addu'ar da bai ma san addu'ar menene ba. Wayar ta shiga amma har ta gama ringing ba'a dauka ba. Ya kira daya layin nata shima ya gama ya katse bata dauka ba. Sai ya kuma kiran na farkon

"The number you are trying to call is not available at the moment....." Ya katse. "Damn it!" Ya sake kira, still the same response. Wani bangaren na zuciyarsa ya fara gaya masa cewa blocking dinsa tayi. "she just blocked you guy" ya fada a fili. "she blocked me" ya maimaita da karyayyar zuciya.

Ba wasan bane ba kenan. Ba mafarki bane ba kuma. Da gaske ne. Da gaske ne abinda tazo ta gaya masa yanzu. Abinda ya gani a jikin ta yanzu.

But how can that be? How evil can she be? Ta yaya zata kasance mai aure through out all zamantakewar su? Ta yaya zai kasa ganewa?

"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun"

Ya fada a fili. He told her that he hates her amma kuma few minutes later babu abinda yake son gani a duniya sama da ita. Babu abinda yake so sama da ita. Babu kuma abinda yake ƙi sama da ita.

Is that even possible?

****.    ****.    ****.    ****.    ****.    

*Her* 🧕🏻

Nayi kokarin dora thumb dina a ignition amma sai na kasa saboda yadda hannuna yake rawa. Na rike hannun da daya hannun da niyyar bashi support amma sai suke rawar a tare. Sai na hada su duk biyun na rungume a kirjina tare da jan dogayen numfashi sau uku ta hancina ina saki ta baki na da niyyar calming nerves dina down ko dan na samu damar driving zuwa gida, dan na tabbatar idan nayi driving a halin da nake ciki to kuwa akwai matsala ba karama ba, but part of me didn't care about matsala, a percentage of that part even hoped for matsalar, amma nasan in dai har matsalar da nake fata ta faru bisa ganganci ko son rai na to zan hadu da ubangiji na dan shine ya bani rai kuma shi kadai ne yake da ikon karbar ran nawa.

Na sake attempting kunna motar, ta tashi sannan na saka ta a drive na dauki hanyar fita daga school ɗin, a raina ina tabbatar wa da kaina cewa wannan shine ganin da zanyi wa makarantar na karshe kamar yadda na yiwa Muhammad kallon karshe a yau. Absentmindedly na dinga driving ɗin, a hankali kamar mai shiga daki, ba tare da na damu da motocin da suke ta yi min horn a baya na ba, da yawan su in sun gaji da horn din sai su yiwa kansu hanya su zo su wuce ni a guje tare da jeho min kallon banza wanda ko kaɗan bai bata min rai ba. Ni yanzu naci dubu sai ceto.

A hanya naga restaurant din da na kawo Muhammad last birthday dinsa, ranar da ta raba mu rabuwa ta har abada. Na tuna maganar da ya gaya min a lokacin.

"Wata shekarar ba zata zagayo ba Piya in sha Allah sai da ke a dakina" nayi murmushi cikin yarda da hakan "insha Allah" ya bude ido "da gaske? Da gaske kike kin gama jan ajin?" Na lumshe ido na bude tare da langwabar da kai ina kallon sa "zaren nawa naga yana kokarin tsinkewa. Besides, na ga alamar ba zaka iya rayuwa babu ni ba". Yace "exactly. Ba zan iya rayuwa babu ke ba".

Na dauke idona daga kan restaurant din ina kokarin cire tunanin ranar daga raina. In dai har na cigaba da tunanin ranar to ba zan iya karasa wa gida ba, maybe sai dai a karasa da ni.

Ina tsayawa a bakin gate, tun kafin inyi horn mai gadi ya bude gate din, nasan dai ya gaishe ni amma banji me yace ba sai kawai na gyada masa kai na shige ciki. Addu'a daya da take raina ita ce Allah yasa kar in hadu da kowa har sai na shiga dakina, bana son ganin kowa a lokacin, bana son kowa ya ganni a halin da nake ciki dan bana son tambaya.

Sai dai addu'a ta bata karbu ba, ina yin packing naga Yaya Mustapha shima yayi packing a kusa da ni. Na rufe ido na "ya Salam, not him, not now please God" amma ita ma addu'ar bata karbu ba dan yana fitowa daga motar sa direct window na ya taho, ina kallon sa through tinted glass dina ya tsaya ya gyara zaman hular kansa da kuma collar din rigar sa sannan yayi knocking glass din. Na rufe ido na tare da jingina kaina a jikin kujerar motar, "ya Rabbi" na fada a hankali "ya Rabbi give me strength" sannan na kashe motar na bude kofa da sauri na fita.

"Fiyya" ya fada yana kokarin haɗa ido da ni. "Ina kika je haka? Daddy ya tayar da hankalin kowa a gidan nan yana neman ki" sai kuma yayi shiru yana karewa fuska ta kallo "are you okay? Are you crying?"

Tambayar da yayi min ce ta saka na shafa fuskata sannan na kalli hannun, ni kaina ban san kukan nake yi ba sai lokacin na fahimci tun daga school nake kuka har gida. Ban ce masa komai ba na zagaye shi na wuce, har na shiga ciki ina jin idanun sa a kaina.

"God Please... Allah dan Allah.... Allah kasa ba shi bane ba. I cannot take it idan shine".

Sai dana dan tsaya a bakin kofa ina karewa parlor kallo ina lissafin ta inda zan bi yadda ba zan haɗu da kowa ba, duk da cewa ma dai gidan babu mutane sosai dan zuwan mu kenan gari jiya kuma gobe zamu sake barin gari. Kuma babu ma'aikata sosai a gidan tunda ba a garin muke da zama ba.

Babu kowa da na gani, dan haka na fara tafiya a hankali making sure ban making sound ba har na kusa hawa stairs, a lokacin ne naji muryar Esther. "Madam? Are you okay?"

Na runtse ido na tare da kokarin goge hawayen fuska ta amma ina gogesu wasu suka yi replacing din su. Wannan yasa ban juya na kalle ta ba nace cikin muryar da naji kamar ba tawa ba "I am fine. Don't let anyone enter my room" da haka na cigaba da hawa sama ina jinta tana cigaba da wata maganar da ban fahimci me tace ba.

Ina shiga dakina na tura kofa na murda lock sannan na jingina da jikin kofar, a hankali kuma sai na zame na zauna a gurin sannan na dira goshina akan gwuiwowina. Abinda kawai nake bukata kenan tun dazu, seclusion din da zan saki kuka na son raina ba tare da wani yayi min magana ba.

A lokacin waya ta tayi kara, da kida na musamman da na saka wa Gidado, kidan da yakan saka zuciyata cikin nishadi a duk lokacin da na jishi saboda dokin jin muryarsa. Na dauko wayar na tsaya ina kallon sunan sa da yake blinking akan screen din "Pyar❤️"

Naji wani sabon kukan yazo min "Allah sarki Muhammad" na fada a fili. "Allah ka dubi bawan ka ka bashi sassauci" na tuna da irin bakaken maganganun da ya gaggaya min daxu a office dinsa, amma mintina kadan har hana kira na. It won't be easy for him. It won't be easy for me.

Kiran yana katsewa na lalubo block button na danna wa number din sa. Abinda ban taba tunanin zan iya yi ba a rayuwa ta. Amma nasan halinsa a kaina, he won't stop calling hakan kuma yana nufin I might answer, in na amsa kuma komai ya rushe kenan.

Sai dai ina dauke hannuna kiran sa yana sake shigowa through my other line. Shima jiran sa nayi ya katse sannan nayi blocking dinsa ta chan din ma.

Abinda kawai nake hangowa a idona shine fuskar Gidado a yadda na baro shi a office dinsa da zu. I have never in my life seen someone as broken as he looked. And why won't he? Na yaudare shi iyakacin yaudara, na cutar da shi iyakacin cuta, na kuma tabbatar ba zai taba yafe min ba.

Amma a ganina hakan shine dai dai, hakan shine zai fi masa alkhairi, he will heal with time dan ban taba jin wanda yaki warkewa daga heartbreak ba, he will find someone and marry and have children kamar yadda yake da buri, and life will go on while I face my demons alone.

Na shafa cikina wanda shine silar komai, a raina ina jin ina ma dai zan iya gayawa Gidado gaskiya, ina ma dai zai iya sanin gaskiyar cikin. Maybe it will reduce his suffering na dan lokaci kadan, but it will torment him for the rest of his life. Ni kuma simplest way out nake nema masa.

Karar knocking naji a kofa, banyi magana ba dan nasan muryar ba zata fito ba, aka sake wani tare da magana a lokaci daya, muryar Safina "Fiyya na san kina ciki fa, Daddy ne yake neman ki tun dazu" na girgiza kaina, a raina nace "Daddy, Daddy na" sai kuma na mike da sauri na bude lock ɗin kofar, saurin da na tashi da shi da kuma yanayin da nake ciki ya saka jiri ya debe ni, Safina da take tsaye a bakin kofa tayi ssurin rike ni. "Fiyya? Lafiya kike kuwa? What happened again?"

Ban ce komai ba na ture hannunta daga jiki na na kama tafiya da sauri zuwa part ɗin Daddy. Safina ta biyo ni a baya tana cigaba da magana. "Magana fa nake miki Safiyya, at least ki tsaya mana kiji abinda nake ce miki. Ne yake damun ki ne? Nasan kina cikin wani hali and I sympathize with you but that doesn't gives you the right to be rude to us. Dazu naji Yaya Mustapha ma yana gaya wa Mommy cewa yayi miki magana kin share shi. Ko ba komai ai ......"

Tana ta maganganun ta ni kuma ina kallon jerin hotunan da akayi wa stairs ɗin Daddy ado da su, hotunan segments na kamfanonin sa, kamfanoni na.

A lokacin muka kawo bakin kofar part ɗin Daddy, na juyo da sauri ina kallon ta nace "what exactly do you want Safina?" Ta tsaya tana kallon na cikin mamaki, sannan kuma sai tace "I tried to help you, we, your family, are always trying to help you because we love you. At least a thank you would be....."

"Thank you" na ce mata sannan na bude kofar na shiga na mayar na rufe.

Ina shiga parlon idona ya shiga cikin nasa, Allah kaɗai yasan irin dadewar da yayi a zaune yana kallon kofa yana jiran shigowa ta. A fuskarsa naga alamun damuwa sosai, ya kalle ni ya kalli cikin jikina. Yanayin fuskarsa kadai ya isa ya saka mai karyayyiyar zuciya fashewa da kuka.

Mommy tana zaune a kusa dashi itama tata fuskar cike da damuwa.

"Am sorry Daddy" na fada tare da sunkuyar da kaina kasa ina kallon yan yatsun kafata.

"You are sorry?" Ya maimaita cikin muryar da take kara nuna halin rashin lafiyar sa.

Jirin da bai gama sakina ba ne ya sake ɗibana, na ga ya yunkura da sauri zuwa gurina sai Mommy tayi sauri ta rike shi ta zaunar da shi sannan ita ta taho gurina. Ta rike ni a jikin ta tare da fara faɗa. "Kin gani ai, zaki jawo wa kanki matsala ki jawo wa mahaifinki shima matsala, Safina me kike so ki zama ne ni Sa'adatu?"

Sai kuma ta tsaya tana karewa fuska ta kallo. "Me ya faru da ke Safina? Kukan menene kike yi haka ?"

Daddy na ga ya sake kokarin mikewa. Nayi sauri na saki Mommy na karasa inda yake na durkusa a gaban sa. Ya koma ya zauna yana kallon fuskata wadda duk da ban kalli mirror ba na san ta kumbura saboda nauyin da naji ta yi min.

Ya sauke ajjiyar zuciya. "What am I going to do with you Safiyya?" na sunkuyar da kaina kasa. "Me zan yi miki ne wai?" Ya sake tambayar no one in particular.

Ban amsa ba dan bani ya tambaya ba. Ko ni ya tambaya din ma bani da amsar da zan bashi. Mommy ta dawo ta zauna a kusa da shi. Sai naga ya juya yana kallon side ɗin sa, ni ma na juya na taya shi ganin abinda yake kallo

Hoton ta ne, tayi kyau sosai tana murmushi kamar za'a ce Safiyya ta amsa. Sai naji ina jin haushinta dan ita ce silar komai. Daddy might not know it yet but ni na sani in my bones and soul cewa ita ce silar komai. Sai dai bani da wani evidence da zan nuna masa. Bani da yadda zanyi in kare kaina.

****.    ****.    ****.    ****.     ****.     ****

Please vote, comment and share as widely as possible.

Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you….

Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on Whatsaap, Facebook, Intagram and Wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma link na social media account din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my Whatsaap, Facebook and Intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever.

Yes, we will give this a trial muga yadda zai kasance. After the 10 free pages, we will start posting as soon as we get at least 20 sponsors. Insha Allah this will be a win-win for all of us. And it will be a beginning of a beautiful journey. But if it didn’t work, though it will sadden me but Safiyya will become a “paid” novel.

I will announce kudinsa in hakan ta kasance.

So ku tayani addua cewa it will work. Lol. Cos I want all my fans to meet the amazing “Piya” and her soulmate, “Gidado” as they embark on their journey of a lifetime filled with so much love and obstacles set by their enemies, or should we call them their lovers?

Please share as widely as possible. 

For sponsorship, contact

0704 203 0419

on WhatsApp or send a dm to my Instagram page

https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ==

Save my business number

0704 203 0419

and say hi on WhatsApp dan inyi saving naku.

Please, dan Allah, abeg, ban da kira.

Sai na jiku, sai kun jini.

One Love
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹


*By*


*Maman Maama*


Daga marubuciyar:
Maimoon
A'isha Humaira
Diyam
Tagwaye
Jidda

And now..... Safiyya


*Episode Two: The Young Passengers*

Na sauke idona daga kallon hoton zuwa kasa, ita ta jawo min duk abinda yake faruwa da rayuwata na sani, amma kuma na san cewa dan Adam baya taba wuce kaddarar sa, rayuwar da tayi ita ce tata kaddarar, nima kuma halin da nake ciki shine tawa kaddarar, kuma na sani cewa addu'a tana chanja kaddara dan haka har yanzu ban gaji ba kuma ba zan taba gajiya ba wajan gyara rayuwata.

She was my role model, she has always been. Courage da determination dinta su suke hana ni giving up a lokuta da dama. Yadda ta chanja rayuwar ta from worst to best haka nima nake fatan chanjawa. Giving up has never been in her dictionary and it is not in mine. Kamar yadda Daddy yake yawan yin comment a lokuta da dama, lokutan da muke good time da shi, cewa her fire is burning in me, cewa I have her zeal, strength, bravery and stubbornness, wannan shi nake so in yi proving right.

Maganar Daddy ce ta dawo dani daga tunani na. "Safiyya, daga ina kike? gurin sa kika je ko?" Na dago kai na kalle shi, sai na yi sauri na sake sunkuyar da kaina dan ba zan iya cigaba da hada ido da shi ba.

Mommy tace "baban Mustapha, kasan dai ɓata lokacin ka da ranka zaka yi a gurin tambayar Safiyya a game da maganar nan, ba zata yi magana ba, wata nawa ana fama? Wacce irin tambaya ce bamu yi mata ba?" Yayi ajjiyar zuciya cike da damuwa yace "na sani Sa'adatu, na kasa hakura ne, gani nake kamar watarana zata tausaya min a matsayi na na mahaifin ta"

Naji hawaye na yana sauka akan hannayena da suke kan cinyata.

"Am sorry Daddy " na fada a hankali

"Sorry she said" ya maimaita. "Abinda ta iya fada kenan in anyi mata magana tace sorry" ya fada cikin kokarin daga murya, sai kuma yayi shiru yana mai da numfashi.

Mommy tace "abinda yasa kika dage da nacin sai mun biyo ta Abuja kenan ko? Kika yaudare mu mukayi tunanin you are after your father's health ashe ke kina da plan din ki da kika shirya ko Fiyya?" Na girgiza kai da sauri amma kuma part of me knows gaskiya take faɗa, except maganar daddy's health, tabbas dan in ganshi na nace sai mun tashi ta Abuja.

"Ba kuma zaki fadi ko waye shi ba ko?" Ta sake tambaya with hopelessness in her voice. Daddy yace "ba zata fada ba kin sani. Wallahi da na san zaki iya risking mutuncin ki da na family dinki ki fita ki tafi gurin sa da na ɗana miki tarko, da na saka an biki a baya an gano min ko waye shi, kuma wallahi da nayi masa abinda har ya mutu ba zai manta ba kamar yadda yayi min abinda har in mutu ba zan manta ba, da na rusa rayuwar sa kamar yadda ya rusa taki, da na....." Sai yayi shiru yana jan numfashi a kokarin daidaita numfashin sa da ya fara fita sama sama.

Na fara tracing tun sanda na fita har zuwa sanda na dawo a raina, ina so inga ko na haɗu da wani da ya san ni ko kuma na bar wani hint da zai taimaka wa Daddy yayi tracing Gidado, har sai da na tabbatar babu sannan naji hankali na ya fara kwanciya. Ba damuwa ta abinda Daddy zai wa Gidado in ya kama shi ba, cos I doubt idan zai iya yi masa komai, damuwa ta shine in akayi tracing Gidado to zai san komai, zai san gaskiyar komai and his parents will be involved too, our school management will also be involved, wannan duk yana nufin bacin sunan Gidado, sannan yana nufin goga masa baƙin fenti na har adaba. Wannan kuma shine abinda nake gudu, shine abinda zuciya ta ba zata iya dauka ba.

Ina cikin tunani na naji Daddy yana waya, "Mustapha kazo sama yanzu ina neman ka". Sai hankali na ya dawo jikina, wancan tashin hankalin ya marsa ya bawa wani sabon tashin hankalin gurin zama a cikin zuciya ta. "God, not him please" na fada a hankali ina mummurza yan yatsun hannuna cikin tsananin damuwa.

Tabbas ni nace da Daddy na amince da duk wani hukunci da zai yanke a kaina duk a kokari na ganin na rage masa radadin abinda yake tunanin nayi masa, amma kuma zuciya ta tana kakkaryewa a duk lokacin da ta hasaso hukuncin nasa, na san aure zai yi min, kuma na amince da auren amma kuma damuwa ta shine wa za'a aura min? Wanene Daddy zai zaba min a matsayin abokin rayuwata ta har abada. Shin zai zama blessing to me or a curse?

A raina nasan few choices ɗin da Daddy zai iya yi. A kokarin sa na kare mutuncina dana family din mu dole na san auren gida zai yi min. Wannan yayi limiting choices dinsa zuwa mutum uku kacal, mutum ukun da dukkan su babu wanda ba zai iya lasar tafin kafata ba in dai za'a aura masa ni, mutum ukun da duk kan su babu mai sona, mutum ukun da duk kan su babu wanda nake so. Mutum ukun da daya daga cikin su yake da hannu wajan bata tsakanina da Daddy, daya kuma yake da hannu dumu-dumu a cikin halin da nake ciki a yanzu.

Sai dai bani da tabbas ɗin who is who. Ba kuma ni da shaidar nuna wa Daddy.

But the fork is my only way out.....
If only I can find the fork.....
If only I can find it's marks....

Muryar yaya Mustapha ta katse min tunani na. Na dago kai muka hada ido sai nayi sauri na mayar da kaina kasa ina jin bugun zuciya ta yana ƙaruwa. Ya zauna a kasa nesa da ni kaɗan. "Daddy gani" Daddy yace "kaje motar Safiyya, check the dashboard camera, find out ina taje dazu, if possible, find out da wa ta hadu".

Ban daga kai na kalle su ba har ya fita, sai dai yawun baki na gabaki daya ya dauke, numfashi na ya tokare a kirjina. "Why didn't I think of the damn camera?" Na rafa lissafin way out a raina. Tabbas camera ba zata nuna Gidado ba, amma zata nuna makarantar mu da kuma dai dai inda nayi packing wato kofar building din da yake dauke da offices na some staff. And weekend ne. Few staff ne suka shiga a ranar. If police got involved zasu iya gano wadanda suka shiga a ranar and it will take Daddy closer to Muhammad.

Mara ta naji ta rike da wani mugun fitsarin tsoro. Hawayen ido na ya kafe. Na zauna zaman jira ina jina kamar akuyar da aka kai mayanka take jiran turn ɗin ta.

Bai jima sosai ba ya dawo ya sake zama a inda ya tashi. "Daddy ta kashe camera din kafin ta fita" ya fada yana kallon Daddy. Na dago kai da sauri na kalle shi. Muka haɗa ido sai ya kuma dauke kai fuskarsa expressionless ya cigaba da kallon Daddy.

Daddy yayi ajjiyar zuciya "I should have known. She is always too smart for her age, tun tana yarinya she has always been two steps ahead of mates din ta. But still ban dauka zata yi tunanin wannan angle din ba".

Mommy tace "ban taba dauka kawaye zasu yiwa mutum rana ba sai akan case ɗin Safiyya. Da ace tana da kawaye na tabbatar zamu samu wani information ko yaya ne daga gare su. Safina kuma tayi iyakacin nata kokarin"

Na tuna da kokarin da Mommy take nufin Safina tayi. A raina nace "munafuka ba" tunanin abinda tayi ɗin ya kara min zafi a zuciya ta.

But yaya Mustapha, me yake up to da zai yi wa Daddy karya? Akwai wani abun da yake bukata tabbas.

"Tashi ki tafi" Daddy yace

Na mike still idona a kasa, har na fara tafiya naji Mommy tace "ko parlor ban yarda ki sake fitowa ba sai in zamu bar gidan nan. Kuma wallahi kika fita sai ranki yayi mugun baci". Na ɗan dakata sannan na juyo ina kallon ta nace "to Mommy" a raina nace na riga na gama abinda ya kawo ni abuja ai, na gama da Nigeria ma gabaki dayan ta, bana fatan wani abu ya sake dawo dani kasar nan.

Na kai bakin kofa naji Daddy yace "kai Mustapha ka zauna, akwai maganar da zamuyi" na sake dakatawa tare da rintse ido na, sannan ba tare da na juyo ba, na yunkura na bude kofar na fita.

Kafin in shiga dakina na haɗu da Esther duk a tsorace. Ta biyo bayana "Madam am sorry, ban san an shiga dakin ki ba. Sai dana ce mata kar ta shiga. Na dakata da tafiyar ina kallon ta ina mamakin yadda ta daga hankalin ta akan karamin abu nace "it is okay Esther, relax, she is my elder sister ni kaina ba zan iya hanata yin abinda take so ba".

Na dauka Esther tana yi min maganar knocking da Safina tayi dazu a dakina ne, sai da na bude kofar dakin na shiga sannan na fahimci ba wannan bane ba.

Duk an zazzage contents ɗin cikin jaka ta akan gado, da alama wani abun ake nema sai dai ban san menene ba ballantana in san ko an samu ko ba'a samu ba. Naga wayata a yashe a gefe, na dauka naga ta nuna alamar anyi ta trying budeta an kasa. Na zauna a bakin gado ina tsince tarkace na tare da mayar da su cikin jaka. Na bude wayar using face lock ina kallon hoton da na saka a matsayin screen saver dina. Hoton hannun Muhammad Gidado ne, ya dora akan sitiyarin motar sa, da zubunan azurfa guda biyu a yatsunsa, da agogo a wrist ɗin sa.

Na tuna sanda na dauki hoton, muna cikin motarsa ne, motar da take holding most of our memories together.

****.      ****.    ****.    ****.    ****.    ****

Lokacin yana yi min korafi ne kamar kullum, yayin da ni kuma nake ƙoƙarin mayar da korafin nasa wasa ta hanyar tsoakanar sa.

"Abba yana ta yi min maganar komawa gurin sa da aiki" nace "inye, rich kid.... Irin born with a golden spoon din nan ko? Babu ruwan ka da neman aiki sai neman ka ma ake yi ko?" Ya bata rai "you know what I mean kina so ki chanja magana ko? Dazu har fushi yayi, he thought pride ne ya saka nake zaune a makarantar nan bana so inyi aiki a karkashin ss and I am hurt that he thinks that" na gyara zamana with a serious face nace "then do what he wants. You are just enslaving your self here and it is hurting me too"

Yace "you think so? Tell me in na bar makarantar nan how am I gonna be seeing you? Safiyya ko gidan ku fa ban sani ba and it has been years muna tare, i know cewa ina barin makarantar nan ko ta kaina ba zaki sake bi ba"

Nayi shiru ina kallon sa, yace "what? Ba gaskiya na fada ba?" Nace "kasan me yake damunka?" Yace "insecurity, yes, I am insecure when it comes to you, bani da wani concrete stand and I know anytime zaki iya ajiye ni a side and the thought alone is given me nightmares and...."

Nace "you once jokingly asked me me yasa nazo makarantar nan out of all the universities in the world, you jokingly said I followed you here because I cannot live without you, I laughed then amma abinda ban gaya maka ba shine gaskiya ka fada a lokacin, I came here because you mentioned ranar nan da muka hadu cewa kana nan makarantar for the time being. I wanted to be with you. I wanted to see you again. I literally threw a tantrum a gaban Daddy akan lallai nan makarantar nake son zuwa"

Na fada ina tuna yadda na kwanta ranar na ringa birgima a gaban Daddy ina kuka shabe shabe da hawaye.

Bai ce komai ba ya saki baki yana kallona, na sunkuyar da kaina na cigaba "I was hoping in mun sake haduwa zaka karbi number ta. And maybe say you love me"

Yace "Piya? Are you saying that you... " Na saka hannu na biyu na toshe kunnuwana "forget I ever said that. Lala la lala" yayi dariya amma naji relief da excitement a cikin muryar sa sosai, hankalin sa ya kwanta ya samu assurance ɗin da yake so. "Piya, you are impossible. But if that is true then ki kaini gidan ku mana please, at least let then know me yadda zamuyi all these the right way"

Na gyada kai "soon insha Allah. Na gaya maka family house din mu yana kano shi yasa ban taba kai ka ba, and Daddy bashi da lafiya yana Pittsburgh ganin likita. In yazo gari I will talk to him and he will tell me what to do. We have nothing to worry about".

Yayi ajjiyar zuciya "am sorry Piya, nasan ina ta damun ki kullum, i don't know why zuciya ta ta kasa nutsuwa, ina ta feeling restless kullum. But i promise zan gyara halina" ya fada guiltily.

Nayi kokarin chanja topic ɗin ta hanyar daukar hoton hannun sa da ya ke kan stirring "wow! rich kid! Wa ya siya maka sabon agogo? Mommy ko Daddy" na fada cikin tsokana, ya kalli agogon sannan ya kalle ni da sigar harara "ni ne rich kid ɗin? An gaya miki mina ɗan zaman kashe wando ne irin ki? Ma'aikaci ne ni if you don't know" Nace "I don't know nawa suke baka but am sure albashin ka ba zai siya maka wannan agogon ba. So, tell me the truth, I promise ba zan fada wa kowa ba. Mommy ce ta siya maka ko Daddy?" Yayi dariya "ask those who call their parents mommy and Daddy that question, misali you. Ni dan gidan Mama da Abba ne. And I don't throw tantrums idan ina son abu" na dafe kai na "shi kenan kuma na shiga uku a hannun ka. Kayi ta tsokana ta kenan har illa masha Allah " yace "tabbas, har ƴaƴan mu sai na bawa labarin yadda kika makale min kike bina duk inda na tafi" na rike bakina ina jin haushin fada masan da nayi nace "me and my big mouth" yace "you and your cute lips".

****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****

Karar knocking kofa ta dawo dani daga tunani na. Ba tare da na dauke ido na daga kan hoton ba nace "come in". Naji an bude kofa an shigo an mayar an rufe, a tunani na Safina ce, sai dai kamshin turaren da naji ya saka na dago kaina na kalli wanda ya shigo. Yaya Mustapha.

Kallo daya nayi masa na sake mayar da kaina na cigaba da aikin kallon hoton da yake kan screen din wayata. Ya zauna akan side drawer yana kallo na. Ganin bani da niyyar yi masa magana sai yayi gyaran murya yace "babu godiya ma ko?" Still ban ce komai ba kuma ban kalle shi ba. Yayi ajjiyar zuciya sannan ya mike tsaye ya tsaya a gaba na. "I just saved you and your precious love a gurin Daddy amma ko godiya ba zaki yi min ba?" Na dago kai da sauri ina jin zuciya ta tana yin zafi nace "yaya Mustapha, what do you want? Me kake bukata daga gare ni?" Ya koma ya zauna muna kallon juna yace "at least a little concern. Fiyya ni yayan ki ne and I love you with all my heart amma I can't help but feel like kin tsane ni kuma ni har ga Allah ban san me nayi miki ba. Tunda abin nan ya faru babu abinda nake yi sai kokarin ganin na faranta miki na rage miki radadin abinda yake damun ki. Only God knows how many times nayi wa iyayen mu karya dan in kare ki. I have nothing to do with abinda kika yi, I have nothing to do with decision ɗin iyayen mu na haɗa mu aure. But why are you cold toward me bayan da ba haka kike min ba?"

Na dauke idona daga kansa ina maimaita abinda yace a raina, decision ɗin iyayen mu na haɗa mu aure, so shine kenan, shi Daddy ya zaba, and he is the worst among the three.

A hankali nace "Dan Allah.... Ka tashi ka fita..."

Ya sake yin ajjiyar zuciya yace "okay zan fita. But just know that in akwai wani abu da kike bukata, just let me know "

Bance komai ba har ya mike tsaye. Ban ankara ba kawai sai ji nayi ya kwace wayar hannuna. Na mike tsaye da sauri kamar wadda aka dorawa garwashin wuta a cinya, yayi sauri ya matsa daga kusa dani yana kallon hoton yana murmushi.

"Wow. Nice hands...... And that skin...... I bet he is Arab"

Ban ce komai ba na tsaya kawai ina kallon sa zuciya ta tana tafasa.

Ya cigaba "and he is rich too..... Cos wannan wrist watch din nasa zai sayi kayan jikina kaf har da chanji"

Ya dawo yazo ya tsaya a gaba na "I feel for you dear. But it is what it is. Allah yasa haka shi yafi alkhairi".

Ya ajiye wayar akan gado kusa da ni sannan ya ce "lecturer ne ko student? Ko kuma non-academics ne?" Naji kamar in rufe shi da duka amma ko motsi ban yi ba. Ganin bani da niyyar ce masa komai sai ya daga kafada yace "okay. Whenever you want to talk I will be glad to listen"

Daga haka ya juya ya fita. Na koma na zauna na dauki wayata na fara aikin goge ta kamar wadda aka shafa wa datti. "Munafuki" na fada a fili "munafukai. Bunch of munafukai. Dukkan ku munafukai ne"

Na tuna tambayar da yayi min akan dalilin da yasa na tsane shi. Tabbas a yanzu kusan na tsani kowa amma tashi tsanar ta musamman ce. Wannan kuma yana da nasaba da sunan shi. Sunan shi aka ambata a lokacin da aka kira ni. Kiran da ya chanja dukkan rayuwar.

"Fiyya! Kina ina? Mustapha ne. Jikin Daddy ya tashi mun tafi dashi asibiti. Hurry up"

Na rufe idona ina jin maganar tana amsa kuwwa a cikin kaina. And it sounded just like him.

"Allah ya isa" na fada a fili.

*Him 👳🏻*

Ya dauki hours a cikin office dinsa dan har sai da yaga magrib ta gabato sannan ya fita, shima kuma ya fita ɗin ne kawai dan yasan rashin zuwa gidan sa zai tayar da hankalin mahaifansa. A gidan su suna da wata doka da ya fahimci cewa ta samo asali ne tun daga kakannin sa na wajen uba, dokar kuwa itace kowa must be home before magrib komai girman ka in dai kana gari, dole tare zakuyi sallah magrib da Abba, tare kuma zakuyi dinner. A dinner din ne ake discussing must of the issues da suka shafi family. A dinner din ne kuma must of the times ake matsa masa da zancen aure.

Ya dinner ɗin jiya ne yayi musu alkawarin yau Safiyya zata shigo gari, and yau din ne yake saka ran zata bashi go ahead na zuwa gurin iyayen ta.

Ya rufe office din ya sauko daga stairs din blindly ya bude motar sa ya shiga. Kafin ya tayar da motar ya dauko wayarsa for like the hundredth time ya kira layin ta. Still baya shiga. Ya kuma san ba zai shiga din ba tunda ya tabbatar tayi blocking dinsa. Amma kuma ya kasa daina kiran ta. He just couldn't let her go. Ba zai iya ba. Ya tabbatar ba zai iya ba.

Ya san cewa dating dinta da yayi a matsayin ta na matar aure ba laifin sa bane ba tunda bai sani ba, Allah kuma ba zai kama shi da laifi ba, amma kuma in ya cigaba da bibiyarta a yanzu bayan yasan tana da aure to tabbas Allah zai kama shi. Amma ya zaiyi? "I just want to confirm" ya fada a fili kamar mai kokarin kare kan sa. But confirm what? Wanne confirmation yake bukata bayan wanda ya gani a jikinta? Ciki ne fa da ita, cikin ma kuma ya kwana biyu, duk da shi ba mace bane ba amma yasan cikin zai kai around five to six months. Ciki a jikin Piyan sa.

Ya rufe ido tare da dora kansa a jikin stirring yana jujjuyawa. Me zai yi ne? Ta ina zai rarrashi kansa? Wacce amsar zai bawa Mama a yau in ta tambaye shi game da maganar da suka yi jiya? Shi dai ba zai ce mata ashe Safiyya tana da aure ba, he can only imagine irin kallon da zata yi masa idan ya fada mata haka.

Ta ina zai fara.....
Ina zai samu ruwan da zai kashe gobarar da ta tashi a cikin kirjin sa?

His worst nightmare have come to be. Safiyya ta barshi.... Bari na har abada.

Ya daga kansa ya jingina shi a jikin kujera, komai ma baya yi masa dadi. A lokacin ne yaji danshi a fuskar sa, ya saka hannu a hankali ya shafa sannan ya tsaya yana kallon abinda ya shafo. Hawaye. Sai ya samu kansa da yin murmushin takaici. Kuka? Wai shine yake yin kuka? Ba zai iya tuna sanda yayi kuka ba tunda yake a rayuwar sa. He has always been strong, emotionally and physically. Mama tayi training dinsa to be a strong man. Amma kuma dama can when it comes to Safiyya to he is the weakest man alive, a hopeless romantic.

Da ace labari za'a bashi cewa zai yi wa budurwa kuka da tabbas sai ya kusa faduwa saboda dariya. Amma kuma dama hausawa sunce duk abinda kace ba zaka iya ba to bai kama ka bane ba.

Ya bude kofar motar ya dauko ruwa ya wanke fuskarsa, there is no way da zai bada damar a gane cewa yayi kuka, ballantana a gidan su, no way.

Yana zuwa gida ya tarar har Abba ya fito zai tafi masallaci, Haidar yana take masa baya. Yayi sauri yayi packing a waje ya bisu a baya yana gode Allah daya kasance Abban sauri yake yi yasan da sai ya sha tambaya. Har suka yi sallah suka fito suka dawo gida bai yanke hukuncin amsar da zai bawa Mama ba.

A parlor suka zauna kamar kullum suka kamo tashar labarai, ya wayan ce yana ta danna waya dan baya son yin magana da kowa, gani yake in yayi magana za'a gane me ya faru a cikin voice din sa. Sai dai ba abinda yake ganewa a wayar da yake danna wa dan hankalin sa sam baya tare da shi.

Dariya yaji an kwashe da ita a parlon, ya dago kan sa sai yaga duk shi suke kallo suna dariya. "What?" Yace yana rarraba ido cikin tsoron kar dai maganar da yake yi a zuciyarsa ce ta fito fili. "Tunanin me kake yi ne haka?" Abba ya tambaya da dariya a muryar sa. "Tunanin Safiyya" Haidar ya fada shima cikin dariya. Amma maimakon Gidado ya taya su dariyar sai ya mayar da kansa ya sunkuyar ya cigaba da danna kira a layin Safiyya.

Mama da ta gama guiding Hanifa ta zauna a kujera tana kallon Gidado, fuskarta cike da damuwa. " Me ya faru?" Ta tambaya tana kallon shi. Ya ajiye wayar tare da yin ajjiyar zuciya yace "babu komai Mama. I am just exhausted ne kawai. Tun safe nake aikin marking script har yanzu kuma ban gama ba". Ta gyara zamanta tace "abinda nake gani a fuskar ka ba stress bane ba, damuwa ce, in ma da akwai aiki to akwai wani abun daban. Me ya faru?"

Ya mike tsaye yana kirkiro murmushin da ko lips dinsa bai wadatar ba yace "da gaske nake Mama. Bani da damuwa. Ko kadan. Yunwa dai nake ji" ya wuce su ya tafi dining ya zauna a kokarin sa na ganin ya gujewa cigaba da yi masa tambayoyi.

Bai jima da zama ba suma suka taho. Yayi saurin wayancewa da zuba wa kansa abinci. Yana jin Daddy da Haidar suna maganganu akan karatun Haidar ɗin, Mufida tana saka musu baki kaɗan kaɗan, yana kuma jin idanun Mama a kansa. Ya debi loma ya saka a bakinsa, ji yayi gabaki daya bakin ya gauraye da daci kamar da ruwan madaci aka dafa abincin, makogwaron sa ya toshe abincin ya kasa wucewa ciki. Haka yayi ta taunawa dan babu damar ya zubar da shi, har daga karshe ya samu ya hadiye shi da kyar.

Ya dago kai suka haɗa ido da Abba da Mama a lokaci daya, yayi sauri ya sake mayar da kansa kasa ya cigaba da juya abincin. Abba ya yi magana "Malam Muhammadu, what is it?" Ya ajiye chokalin hannunsa tare da yin kokarin bada uzurin da zai masking damuwar sa "uhmm.... Abba dama ..... Dama maganar aikin da muka yi da kai, ina ganin in ka yarda zan bar wannan din in dawo gurin ka kawai. Wannan ɗin is exhausting. Na gaji". Abba ya sake cewa "shi kenan?" Gidado ya gyada kansa kawai bai ce komai ba.

Kamar daga sama yaji Mama tace "ya maganar Safiyyan? Tazo ɗin? Kunyi maganar?" Gidado ya sake daukan chokali ya cigaba da juya abinci ba tare da ya kalle ta ba yace "bata zo ba Mama. Bata samu damar zuwa ba" tace "but am sure kunyi magana da ita a waya ko? Kasan dai next week za'a zo saka ranar Mufida, ka kuma san na jima ina fadar cewa tare zan haɗa ku" ya gyada kai "na sani Mama. Bamu yi waya ba. Zamuyi amma".

Sai kuma ya mike. "Bana jin dadi, bana jin cin abincin nan. Zan je in dan kwanta" Mufida ce tace "Allah yasa dai ba zazzaɓi zaka yi ba Hamma, fuskar ka tayi pale. Ya danyi mata murmushi yace "Ameen dear". Daga haka ya nufi hanyar da zata kai shi inda dakunan su suke. Har ya shiga ya rufo kofa yana jin idanuwan iyayensa a kansa.

Yana shiga dakin sa direct gaban dresser ya tafi, ya tsaya a gaban full mirror dinsa yana kare wa kansa kallo. Ya saka hannu ya shafa fuskarsa yaji ta dauki zafi kamar mai zazzaɓi. Sai kuma ya lura da abinda Mufida tace fuskarsa tayi fari tas kamar takarda. Sai yaji muryar Safiyya a kunnen sa yadda take tsokanar sa.

"Da wata farar fuskar ka anan"

Tana fada ne a matsayin tsokana duk he knows she is saying it as a compliment, or so he thought.

Duk sanda ta fadi haka shi kuma yakan mayar mata da cewa "da wata beautiful face dinki anan".

Ya tuna ranar da ta fara ce masa me farar fuska. Ranar da ya fara ganinta a duniya. Shekaru da dama da suka wuce. Shekaru goma da suka wuce.

He was just seventeen years old. And she was eleven years old.

****.    ****.    ****.    ****.    ****.     ****

A cikin jirgi ne, ranar da zai bar Nigeria zuwa Manchester , United Kingdom dan fara karatun degree dinsa na farko. An riga an gama yi masa komai dan haka shi kadai aka saka a jirgi ya tafi. Wannan shine karonsa na farko na yin tafiya mai wannan tsahon shi kadai. Tun yana dan karamin yaro, ya kasance yana da aerophobia ma'ana fear of flying, duk sanda ya hau jirgi ya kan ji tsoro musamman a gurin tashi da sauka ko kuma in aka shiga turbulence.

A duk sanda zasu yi tafiya tare da family yakan rike hannun Abba ko Mama, har sai jirgin ya daidaita sannan ya saki. A ranar kuma kasancewar babu Abba babu kuma Mama sannan babu kowa a seat din kusa da shi, sai ya kama handle din seat ɗin ya kankame tare da rintse idonsa. Sai dai duk da haka jiri yake ji, kansa juyawa ya ke yi.

A cikin haka ne yaji an rike hannunsa. Ba tare da ya kalli waye ba sai ya damke hannun daya rike nasa ɗin da karfi har sai da jirgin nasu ya dai daita. Ya sauke ajjiyar zuciya tare da bude idonsa a hankali, sai kuma yayi sauri ya kalli side din da aka rike hannun nasa.

Yarinya ya gani yar karama wadda ba zata fi sa'ar Mufida ba. Ta karkata kai side daya tana kallon sa fuskarta dauke da murmushi. Yayi sauri ya saki hannun ta yana yarfar da nasa hannun "You? Who are you? Where are your parents?" Ya karasa maganar yana duddubawa around them. Sai dai bai ga kowa da yayi kama da iyayen ta ba, kusan ma inda suke zaunen basu da yawa.

Ya sake dawo da dubansa kanta yace "where are your parents?" Direct tace "my mother is dead. My father is in Manchester yana jirana" ya koma ya zauna sosai "are you telling me ke kadai aka sako a jirgin nan daga wata kasar zuwa wata?" Ta daga kafada tace "there is nothing to it really. Uncle Ahmad ya kawo ni airport ya danka ni a hannun cabin crew, they will take care of me har mu sauka and my Dad will be waiting" ya tsaya kawai yana kallon yadda take zarar magana yace "awwn, rich kids, yayan Daddy da Mommy. Now if you don't mind i need to sleep. Ki koma wherever it is that you came from. I don't want any trouble".

Ta gyara zama. "i won't trouble you. I prefer sitting here" ya bata rai irin yadda yake yiwa Mufida "ke! Bar gurin nan nace miki" amma maimakon tabi umarnin sa kamar yadda Mufida take yi sai ta kyalkyale da dariya tare da kwaikwayon yadda yayi maganar "ke! Bar gurin nan nace miki" ta sake wata dariyar sannan tace "fillo". Yaji wani takaici ya kama shi kamar ya rufe ta da duka, amma maimakon haka sai ya mike tare da ɗaukan headphone dinsa da niyar bar mata gurin.

Sai dai yana mikewa jirgin su ya shiga turbulence. Ya koma ya zauna da sauri tare da mayar da seatbelt dinsa, sai da suka fita daga turbulence din sannan ya lura cewa ya kuma rike hannun ta da hannayensa biyu. Ya sake cika ta yana gyara zamansa. Tace "you have aerophobia you cannot help it. There is nothing to be ashamed of"

Ya bata rai a ransa yana tunanin wannan wacce irin yarinya Allah ya hada shi da ita yau. Yace "wai ke parents din ki basu warning dinki not to talk to strangers ba?" Ta gyada kai da sauri tace "Mommy did" yace "you just told me mamanki ta rasu" tace "yes, Mommy is my step mom. But she is more like a mother to me because she loves me so much" yace "ohh, shi yasa ba kya jin maganar ta kenan ko?" Ta yi shiru tana kallon sa da alamr bata gane me yake cewa ba.

Yace "she told you kar kiyi magana da strangers, amma gashi kina yi min magana ni" ta girgiza kai "saboda you won't harm me" ya bata rai "ya akayi kika san hakan? You don't know me" ta daga kafada tace "I don't know how I know, i just know" yadda tayi maganar yasa yayi murmushi, sannan yace "you are too smart for your own good, zaki iya cigaba da zama anan, amma kar ki dame ni da surutu" ta yarda da hakan, amma kuma bata cika alkawarin ba dan for the hours da suka dauka suna tafiya sam bata barshi ya runtsa ba, labarai dai kam ya sha su, duk yan gidan su babu sunan wanda bai ji ba, Mommy, Daddy, yaya Mustapha, Hassan, Hussain, Safina har zuwa kan yan aikin gidan su.

And he held unto her hands sanda jirgin su zai sauka. Sai bayan sunyi landing sannan yace mata "kim fada min sunan kowa a gidan ku amma baki fada min naki ba" tace "Safiyya. Sunana Safiyya Adam Muhammad. Amma yan gidan mu suna ce min Fiyya. I don't know why"

"Piya?" Ya maimaita

Tayi dariya "Fiyya. With an F and double y"

"Piya" ya sake maimaita wa

Tayi ajjiyar zuciya "fillo" ya bata rai, tayi dariya.

"In kace Piya kana nufin something totally different from my name" ya bata rai yace "me Piya din yake nufi?"
Tace "love ko beloved, in India" ya gyada kai yace "ohh"

Tace "and ina da wata super power, I can tell you your name. You are Muhammad Auwal Muhammad" yayi sauri ya kalleta da mamaki, sai ta daga masa flight ticket dinsa da ya fadi kasa bai sani ba. Tace "har ka ji tsoro, da wata farar fuskar ka anan".

****.    ****.     ****.    ****     ****.    ****

Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you….

Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah.

For sponsorship,

contact 0704 203 0419 on whatsap

or

send a dm to my Instagram page

https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ==

Save my business number

0704 203 0419

and say hi on whatsap dan inyi saving naku.

Please, dan Allah, abeg, ban da kira
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹


*By*


*Maman Maama*


Daga marubuciyar:
Maimoon
A'isha Humaira
Diyam
Tagwaye
Jidda

And now..... Safiyya


*Episode Two: The Choices*

For sponsorship,

contact 0704 203 0419 on whatsap

or

send a dm to my Instagram page

https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ==

Save my business number

0704 203 0419

and say hi on whatsap dan inyi saving naku.

Please, dan Allah, abeg, ban da kira


*Her🧕🏻*

Har dare yayi na kwanta bacci babu wanda ya kara shigowa gurina babu kuma wanda ya neme ni sai Mommy da ta shigo ta matsa min  naci abinci sannan nasha prenatal vitamins dina. Tun da na tashi da assuba kuwa nayi wankana na shirya na saka jilbab ɗin da nake fatan zai rage nuna wa mutane cikin da yake jikina. Dama kayana a hade suke ban fito da su daga jaka ba, duk abinda na fito da shi kuma nayi deciding cewa ba zan tafi dashi ba dan bani da karfi na jiki dana zuciya da zan iya yin wani abu akai.

Na koma na kwanta a kan gado na nannade jikina da jilbab ɗin, na rufe idona da fatan bacci zai dauke ni ko na samu na ɗan rage ciwon da kaina yake yi min, amma sai dai a maimakon bacci, memories ne suka yi ta overlapping a cikin kaina, memories of yarintata, memories of relationships dina da family dina a da da kuma a yanzu, memories din Gidado and all the hopes we had for a future together, and the memories of daren da ya lalata komai a rayuwa ta, daren last birthday din Gidado.

Na tashi zaune tare da dafe kaina da hannayena ina jin yana barazanar tarwatsewa. Sai kuma na daga kaina sama ina kallon hoton da yake facing ɗin gadona, hoton mahaifiyata a kwance akan gadon asibiti rike da yar jaririya a hannunta, fuskarta cike da tsantsar farin ciki. Nayi ajjiyar zuciya, ina ma dai rayuwa tana da control button, ina ma dai zan iya rewinding komai na koma yar jaririya na cigaba da jin dumin mahaifiyata, inama.......

Sai nace a fili kamar mai magana da ta cikin hoton. "you set me up to be devoured by the blood thirsty vultures, yanzu gashi sun kassara rayuwata" nayi tsaki na juyawa hoton baya, sai kuma na sake juyawa nace "I miss you though".

Knocking din da naji a bakin kofa ya saka na dawo da dubana kan kofar sannan na kalli agogo, 7:35. "Yes?" Nace ina gyara hijab dina tare da sake haɗe fuska. Sai dai kuma ana bude kofar yanayin fuska ta ya juya zuwa murmushi. At last, someone I can talk to, someone who truly loves me.

Suka shigo a tare suma fuskokin su dauke da murmushi, na bude musu hannayena amma maimakon su fada jikina kamar kullum sai suka zauna a sides dina sannan suka rungume ni a tare. Nayi ajjiyar zuciya ina kara rungumar su jikina, ina jin yadda suka kara girma duk su biyun, a tsaho yanzu duk sun kere ni.

"Yan biyun yaya Fiyya, I am glad you made it. Ina ta jin babu dadi na dauka ba zan ganku ba har mu tafi".

Hassan ya dago kansa daga kafada ta yace "kinga gudun da muka yi a mota kuwa? Mommy tace mu hakura mu zauna tunda jiya ma evening paper mukayi amma muka dage sai da muka zo dan mu ganki kafin ki tafi"

Hussain yace "Mommy tace zaki jima baki dawo kasar nan ba, haka ne? Amma zamu iya zuwa mu kai miki ziyara in mun gama waec ko?".

Na gyada kai nace "duk sanda kuke son ganin mu kuyi min magana ko kuyi wa Daddy magana, za'a siya muku ticket ku tafi. And anything you need, ko menene, ku kira ni ku gaya min".

Suka gyada kai a tare, Hassan yace "but this is not fair, Daddy is not being fair to you. Me yasa zai miki aure yanzu? Mommy tace aure zai yi miki da yaya Mustapha. Yaya Mustapha fa for God's sake. It shouldn't be. Kamata yayi a barki kiyi healing, ki kuma samu wanda kike so ku fahimci juna sannan sai kiyi aure"  na kalle shi ina murmushi nace "all that sounds so good. Amma kuma ba haka Daddy ya zaba ba, and I am sure Daddy ba zai zaba min abinda zai cutar da ni ba, da abinda ka fada ɗin shine zai fi min dai dai I am sure Daddy shi zai zaba min, you should be kinder to him".

Hussain yace "but what about you. You are obviously not happy" nace "it doesn't matter. Maybe I will be nan gaba. Hussain, a yanzu haka happiness dina kadan ne a cikin irin abinda zan iya sacrificing dan in gyara relationship dina da Daddy, zan iya bayar da komai, ko da kuwa rayuwata ce to have Daddy hug me and say 'I love you Safiyya'" na karasa maganar ina share hawaye da bayan hannuna".

Suka yi shiru gabaki daya sannan Hussain yace "he loves you, you know.  Yafi son ki akan kowa" na yi yar karamar dariya mai kama da kuka nace "my dear brother, am not sure about that. To him, I am just a big fat disappointment".

Hassan yace "no you are not. He loves you. We all love you". Nayi kokarin chanja topic ta hanyar cewa "sooo, waye yayi driving a cikin ku, naji kunce kun sharara gudu" Hussain yana dariya yace "Hassan ne" Hassan yace "i passed my driving test last week, shine yanzu na gwada skill dina" nace "yayi kyau. Amma a daina gudu da yawa. An kawo muku motocin kenan?" Hassan yace "no... Ta wani friend din mu ne" na bata rai "why? Me yasa ba'a kawo muku ba? Kun sake yiwa Uncle Ahmad maganar?" Hussain yace "munyi masa fa, sai kawai ya rufe mu da fada wai me zamuyi da personal cars bayan akwai motoci a gida"

Na fara girgiza kaina ina cewa "nasan akwai motoci a gidan ai, ni nayi niyyar zan siya muku motoci a matsayin gift na jamb da kuka ci. Zanyi masa magana. Allah yasa zai zo yau yayi wa Daddy sallama, zanyi masa magana".

Hassan yace "uhm uhm, kar ki sa yayi miki faɗa kema. Yanzu kula da lafiyar ki yafi komai muhimmanci. Ki rabu da shi kawai". Na sake girgiza kai stubbornly "zan yi masa magana".

A haka muka cigaba da hirar mu har sai da Esther ta shigo da tray din breakfast ɗina ta kuma sanarwa su Hussain da cewa nasu abincin yana kasa  sannan suka mike suka yi min sallama. Na tashi tsaye nima na rike hannayen su a cikin nawa nace "idan kunje gurin Daddy, be nice to him please, ku fada mishi maganganu masu daɗi and tell him you love him, hug him" suka tsaya kawai suna kallona amma kuma fuskokin su sun nuna cewa sun fahimci abinda nake cewa, a tare suka gyada kai, nayi musu murmushi sannan ta saki hannayen suka fita jiki a sanyaye.

Suna fita Mommy ta shigo ta kuma saka ni a gaba sai da na ci abinci, ina ci tana yi min hira. "Gwara ki ci abinci ki koshi dan ba lallai bane ki iya cin abincin jirgi. Kuma gwara ki ci abinci a daki dan ban san waye zai shigo gidan nan yau ba, ko ma'aikatan gidan ma ban yarda su san halin da kike ciki ba, dan hausawa sunce munafukin ka tabarmar ka".

Muna nan zaune Safina ta shigo ta zauna tana kallona ina shan tea din da Mommy ta hada min, tace "I will miss you little sister. Though na san ba dadewa zakiyi sosai ba. Kina dawowa kuma sai mu sha biki" ta karasa tana murmushi. Ban ce komai ba har sai da Safina ta mike zata fita sannan na daga kai nace mata "I will miss you too. Allah ya bada sa'ar karatu" tace "Ameen. Nagode" sannan ta fita.

Ban fita ba har sai da aka gama saka duk kayan mu a cikin mota, sannan Mommy tazo da kanta tace inje in shiga mota, shima sai data tabbatar jilbab din jikina ya boye cikin sannan ta kama hannuna muka fita tare.

Sai dai muna fita compound din gidan motar Uncle Ahmad tana shigowa, driver yana tukawa, Mukhtar a gaba, Uncle Ahmad a baya. Mommy ta tura ni gaba "sauri ki je ki shiga mota gani nan zuwa" amma sai na makale, ina so nayi magana da Uncle Ahmad akan maganar motocin twins. Mommy ta sake turani amma maimakon nayi hanyar motar da zamu tafi airport a cikin ta sai nayi hanyar inda su Uncle Ahmad sukayi packing.

Kafin na karasa suka fito, kallo daya Uncle Ahmad yayi min ya dauke kai, yayin da Mukhtar kuma ya taho direct gurinna yana washe baki. Sai a lokacin nayi nadamar kin jin maganar Mommy. Ya tare min hanya yayin da ni kuma nake kokarin wuce shi na tafi gurin Uncle Ahmad. Yace "Fiyya ko gaisuwa babu? Ko nayi wani laifin ne wai? Ni ina ta jin dadin zan samu na ganki ke kuma ko kallo ban ishe ki ba ko?"

Na tsaya tare da juyowa ina kallon sa. "Yaya Mukhtar, barka da zuwa, ya hanya. Nice to see you. Bye". Na juya zan tafi ya sake tarar gabana. "Dan Allah Safiyya ki tsaya. You don't have to be cold. Ki bani dama muyi magana ta fahimtar juna please. Minti biyu ya ishe ni" nayi ajjiyar zuciya ina lura da Mommy da ta bata rai a gefe tana kallon mu. Nace "ina jinka" ya gyara tsayuwa sa, na lura da yadda yake kokarin kar ya kalli cikina, yace "ina jin yau kusan shekaru biyu kenan da na fara gaya miki abinda yake zuciya ta. So kin riga kin sani. Ina so ne in gaya miki cewa babu abinda ya chanja a zuciyata a game dake duk da rejecting dina da kikayi the first time. Babu abinda ya chanja a zuciyata duk da wannan abin da kika yi" ya fada yana waving hannunsa around cikinta ba tare da ya kalli cikin ba, naji zuciyata ta tattare ta dawo wuyana, na nade hannuna a kirjina nace "what do you want, Mukhtar?" Ya dago kai yana kallon cikin idona, nima ban dauke nawa ba, yace "you know exactly what I want" nace "no, I don't. Just skip the whole preamble ka gaya min direct. Menene kake bukata daga gare ni".

Ya sauke idonsa kasa yana hadiye yawu yace "idan kin amince ..... A matsayi na na dan'uwanki na jini, ina so in kin haihu, zan taimaka miki in aure ki, har abada babu wanda zai san me ya faru. Har abada babu wanda zai san me kika yi" na kankance idona a kansa nace "Mukhtar, a tsakanin ni da kai tabbas akwai wanda yake bukatar taimako, kuma daga ni har kai mun san waye".

Na juya da sauri na bar inda yake, raina a matukar bace, blindly nake tafiya ina magana da kaina kasa kasa, ban ankara ba sai gani na nayi a gaban Uncle Ahmad, na dan ja baya sannan na gaishe shi a diririce "uhmm. Uncle. Ina kwana" yana danna wayarsa ya amsa. "Lafiya" har na wuce shi sai kuma na tuna da alkawarin da nayi wa twins dan haka na dawo da baya. "Uncle.....dama ina so zanyi maka magana ne ... Dazu munyi magana da twins akan cars din da nace a siya musu. Shine nace bara in tuna maka maybe ka manta ne".

Wani mugun kallo daya watso min ne ya saka a lokaci daya naji ina ma dai jiya da na kwanta bacci yau ban tashi da rai ba. Na ja da baya taku biyu cikin sauri dan a tunani na rufe ni zaiyi da duka amma instead sai yace cikin daga murya "Safiyya? Yanzu rashin kunyar taki har ta kai haka dama? Zamani har ya kai haka lalacewa? Ke sam baki ma damu da wannan abun kunyar da yake jikin ki kike yawo da shi ba har kina da karfin halin tsayawa a gaba na da abun kunya a jikin ki kina bani umarni?" Na juya da sauri na yi gurin motar mu ina jin kafafuwa na suna harhadewa a cikin juna, ina kuma jin idanuwan duk mutanen da suke gurin a kaina.

Kafin in kai mota hawaye sun jika fuskata, ta gefen idona na ga twins sun taho gurina amma sai nayi sauri na bude kofar gidan gaba na shiga sannan na rufe da karfi, still ina cigaba da jin muryar Uncle Ahmad yana cigaba da fadar bakaken maganganu a kaina. "Kaf dangin mu ba'a taɓa yin irin wannan abun kunyar ba. Saboda daurin gindi amma wai har tazo ta tsaya a gaba na tana gaya min maganar banza" na saka hannayena duk biyun na toshe kunnuwa na tare da kifa kaina akan dashboard ina cigaba da rusa kuka kamar wadda aka aikowa sakon Daddy ya bar duniya.

A cikin kuka na naji shigowar Mommy cikin motar ta zauna a baya tayi min magana amma banji me tace ba, sai dai na dago kaina na fara kokarin goge hawayena. Yaya Mustapha yazo ya bude daya kofar bayan ya taimaka wa Daddy ya zauna sannan ya rufe ya dawo seat din driver ya zauna. Na cigaba da ƙoƙarin tsayar da kuka na dan sam bana son Daddy ya san abinda ya faru ballantana ransa ya baci.

Sai dai yaya Mustapha yana tayar da motar naji Mommy tace "ki daina wannan kukan haka tun kafin ki saka wa kanki wata cutar kuma, ki gaya wa Daddyn ku abinda ya faru" nayi shiru ban ce komai ba, sai naji muryar Daddy yace "menene ya faru?" Na sake yin shiru amma kuma sai hawaye na ya dawo sabo. Ya sake magana cikin tsawa "magana nake miki Safiyya, menene ya faru?"

Cikin kuka nace "Uncle Ahmad ne yayi min hayaniya a cikin mutane" yayi shiru kamar bai ji ne nace ba, sai kuma yace a hankali "me yace?" Nayi shiru a raina ina jin nauyin maganar. Mommy tace "zagin ta yayi, ya goranta mata akan abinda ya same ta, a gaban duk yaran gidan nan" Daddy ya sake yin shiru, amma duk da ban kalle shi ba nasan ransa yayi matukar baci, ni kuma abinda nake gudu kenan.

Har yaya Mustapha ya ja mota sai Daddy yace "tsayar da motar nan Mustapha, zo ka kama ni in fita". Nayi sauri na juyo ina kallon sa hankali na a tashe. "Daddy please" Mommy ma ta rike hannun sa da sauri. "Dan Allah kar ka fita, dan Allah kar ka kula shi. Abinda yake so kenan dama. Mu lafiyar ka tafi mana komai. He isn't worth it. Ko babu komai yanzu mun san inda ya sa gaba".

Daddy ya karbe hannun sa da ta rike ya kama handle din kofar yana kokarin budewa. Na juya na kalli yaya Mustapha cikin tashin hankali nace "rufe lock ɗin. Ja motar mu tafi" yayi abinda nace muka bar harabar gidan a guje.

Har muka yi nisa babu wanda ya kuma yin magana. Sai daga baya naji Daddy yace "Mustapha kira min Ahmad a wayar ka ka bani shi" na dafe kaina. Ba zai hakura ba dai. Wata irin zuciya ce da Daddy da sam baya barin magana ta wuce sai ya rama. Ina kallo yaya Mustapha ya daukl wayar sa yayi dialing sannan ya saka a kunnen sa, aka dauka sai yace "Uncle Ahmad, Daddy ne yake son magana da kai" sai kuma ya mika wa Mommy wayar ita kuma ta bawa Daddy, ya karba direct yace "kar ka biyo ni airport, bana son rakiyar taka. Allah yayi min komai, bana bukatar komai daga gare ka".

Daga haka ya ajiye wayar. Mommy tace "kash. Ni dai ban so ka kula shi ba wallahi" amma a raina sai nayi mamakin abinda yasa naji kamar farin ciki a cikin muryar ta.

Bamu jima a airport ba aka kira jirgin mu, na rungume twins da suka biyo mu har airport a baya muka yi sallama, na tabbatar sunyi sallama mai kyau da Daddy sannan nabi bayan yaya Mustapha da yake tura Daddy a wheelchair zuwa cikin jirgi. Sai dana tabbatar Daddy ya zauna comfortably sannan na nemi seat dina na zauna nima tare da sauke ajjiyar zuciya. Bamu dade da zama ba jirgin ya tashi, daga can nesa dani na hango wata ta kankame hannun kujerarta. Nayi murmushi tare lunshe idona ina kallon seat din kusa dani wanda babu kowa a kan sa. Sai kuma na tuno da fuskar sa jiya. How hurt and broken he looked. Na kuma mayar da idona na rufe a fili nace "I am sorry Muhammad. Ina yi maka son da ba zan iya staining white din ka da datti na ba. Allah ya baka ikon cin wannan jarabawar. Allah ya baka wadda ta fini". Sai kuma naji ina jin kishin wadda Muhammad zai samu bayan yayi healing daga abinda nayi masa. Ina kishin rayuwar da zasu yi. Rayuwar da Gidado ya shirya mana zamu yi ni da shi, yanzu dole da wata zaiyi. Dole da wani zanyi.

Zuciya ta naji tana tafasa, gashi na kasa cire tunanin daga cikin ta. Na dauko headphone a handbag dina na saka a kunne na na kunna karatun Alkur'ani tare da rufe idona a hankali ina motsa bakina ina bin kira'ar, da fatan zai sanyaya min zuciya ta.

Ban san tsahon lokacin da na dauka a haka ba naji an taba ni. Na bude ido naga Mommy a tsaye a gaba na, tayi min murmushi sannan ta taba wuya na tana testing temperature dina. Sai kuma ta zauna a kujerar kusa dani tace "nace Mustapha yazo ku zauna tare ya debe miki kewa yace in ya zauna ma faɗa zakuyi" nayi shiru bance mata komai ba ido na a kasa. Ta cigaba "me yasa kuke rigima ne kullum wai Safiyya? Akwai abinda yake yi miki wanda ba kya so? In akwai ki gaya min ni zanyi miki maganin sa kinji?" Na gyada kai na kawai bance komai ba. Sai tace "ki je gurin Daddy, yace yana son magana da ke".

Na mike da sauri tare da cire headphone ɗin kunne na na ajiye, ta rike hannu na "ki bi a hankali kar ki fadi" na sake gyada kai sannan na wuce na tafi inda Daddy yake.

Ina zuwa ya dago kai daga karatun magazine din da take hannunsa, ya kalle ni, kallon da ya fi min ciwo akan komai sannan ya mayar da idonsa kan takardun hannunsa yace "seat" na zauna a kujerar da Mommy ta tashi daga kai ina wasa da yatsun hannuna ban ce komai ba.

Ya ajiye magazine din yace "kin dai san maganar da nayi miki akan aure ko?" Na gyada kai, yace "baki da baki?" Na amsa da sauri. "na sani Daddy" yace "good. Da nayi niyyar sai dai kawai kiji an daura miki aure, banyi niyyar sanar da ke komai a kai ba. Amma ban san me ya hani ni yin hakan ba. Ban san me yasa nake tausayin ki ba, duk da kuwa cewa ke ba kya tausayi na, ko kadan" bance komai ba, dan ji nake yi duk duniya tayi min kunci.

Jin banyi magana ba sai ya cigaba. "Ina tunanin mahaifiyar ki ce. Memory dinta ne yake hunting dina yake hanani aiwatar da duk wani hukunci da nayi niyyar yankewa a kanki. Komai nayi niyyar yi sai inyi tunanin in tana raye zata yarda? Kullum sai nayi tunanin in tana raye wanne hukunci zata dauka akan ki" ya yi ajjiyar zuciya yace "but I guess I will find out soon enough" na dago kai da sauri na kalle shi amma sai yayi sauri ya juya kansa gefe, ya cigaba "babban burina kafin in tafi din shine in ga rayuwar ki ta daidaita, yadda at least ubangiji zai rangwanta min akan  laifin negligence a kula da amanar da ya bani, yadda at least zan samu abinda zan gaya wa mahaifiyar ki idan na haɗu da ita a can".

Na goge hawayen kan kuncina a hankali na fadi kalmomin da suka zamar min kamar karatun sallah a cikin watannin nan "Daddy I am sorry".

Ya cigaba "wannan dalilin ne yasa nake son yi miki aure as soon as possible. Bana so in tafi ba tare da na yi miki aure ba Safiyya. Bana so in tafi ba tare da rayuwar ki ta daidaita ba. Wannan shine abinda nake tsoro fiye da mutuwar ita kanta" yayi ajjiyar zuciya ya cigaba "nayi magana da likitan da zai cigaba da dubaki a Germany, ya gaya min cewa zasu iya cire cikin idan yayi wata bakwai ba tare da illa ga ke ko babyn ba. Wannan shine abinda za'a yi. Ina so a rabaki da cikin nan ina raye. Sai dai kuma ban san yadda zanyi da babyn ba idan an cire shi. So for the last time ina sake tambayar ki Safiyya, waye uban cikin nan?".

Na girgiza kai na da sauri amma na san yin shiru na zai kara bata masa rai, kamar yadda nasan abinda zan fada ɗin shima bata masa ran zaiyi. "Daddy wallahi ban sani ba" na fada cikin rawar murya. Yayi ajjiyar zuciya. "I thought as much. Kamar yadda na fada, ni ina tausayin ki amma ke ba kya tausayi na. Okay let's assume gaskiya kike faɗa. Ba ki san waye ba. Amma ai na tabbatar da cewa kin san waye saurayin nan naki ko? Ko shima ba ki san shi ba" na girgiza kaina sai kuma nace "na san shi Daddy " yace "okay, let's go over the whole story kamar yadda kika bamu. Kince a ranar da abin ya faru you were with him throughout the evening, har dare kuna tare. Haka ne?" Nace "haka ne" ya cigaba "da dare you look him to an eatery. Kuka ci abinci tare daga nan sai aka kira ki, someone claiming to be Mustapha, and that's when it happened. Ko?"

A hankali nace "haka ne" yace "okay let me break it down for you maybe ko zaki iya bude idonki beyond soyayyar da kike yi masa ki ga gaskiya. You told him cewa a ranar zan zo gari. Haka ne?" Nayi tunani, tabbas na gaya masa, we were so excited saboda na gaya masa a matsayin another birthday gift da zan bashi, zan kai shi gurin Daddy idan yazo. Nace "haka ne" yace "kuma shi kadai kika gaya wa ko kin gaya wa wani?" Nayi tunani, ni bani da wasu friends da nake wata personal magana da su, na girgiza kai na "ba wanda na gaya wa" Daddy yace "good. And ya san bani da lafiya?" Nan ma na amsa in the affirmative. Ya kuma tambaya "kuma ya san kina da dan'uwa Mustapha, ya san tare zamu taho da shi?" Nayi shiru a raina bana jin dadin direction din da wadannan tambayoyin suke tafiya. Ya katse min tunani na "yes or no" nace "yes, ya sani" yayi murmushi "tambaya ta karshe. Sanda aka kira ki aka yi pretending to be Mustapha, yana zaune a gurin ko ya tashi?" Nayi shiru ban ce komai ba, zuciyata tana bugawa kamar zata bar kirjina. "Answer me!" Ya fada da muryar fada. Na tuno abinda ya faru a lokacin, muna zaune aka kira Gidado a waya, ya dauka baya jin abinda ake cewa sai ya tashi looking for network, and then my phone rang.

Na lumshe ido na a hankali nace "baya gurin, ya tafi yin waya" Daddy ya sake yin murmushi yace "and you still think ba shi ya kira ki ba? You still think ba shi bane ba?" Na girgiza kaina "Daddy bashi bane ba"

Ya dafe kansa da hannu daya, ina jinsa yana karanto addu'a a hankali, maybe addu'ar Allah ya sanyaya zuciyarsa kar ya rufe ni da duka a cikin jirgi.

Ya bude idonsa at last yace min "okay. A cikin biyu akwai daya. It is either duk wannan labarin da kike bayarwa karya kike yi, ko kuma kin san shi ɗin ne and you are doing everything in your power to protect him" na sake girgiza kai stubbornly "bashi bane ba"

"Tashi ki bani guri" Daddy ya fada cikin tsawar da nasan mutanen gurin sunji. Na mike da sauri jikina yana rawa, sai kuma yace "A cikin mutum uku ina so ki zabi daya. Ko Mustapha, ko Mukhtar, ko Abdul". Na durkusa a kusa da kafarsa ina kallon yatsun hannuna bance komai ba, tunani na yana rarrabuwa. Farko nayi tunanin already Daddy ya yanke hukuncin aura min Mustapha, tunda har shi kansa Mustapha din ya shigo dakina jiya yana min kurari akan hakan, Safina ma kuma tayi min magana akan hakan in another way, ashe su maganganun su kawai suke yi Daddy bai tsayar da magana ba, ban taba tunanin zai bani zabi ba, ban saka ran zai bani zabi ba, dan haka ban auna choices ɗin nawa ba.

Nace "ko Mukhtar ko Abdul, duk wanda zuciyarka tafi amincewa da shi Daddy, ko ba su ba ma kowane ne, anyone but Mustapha. Dan Allah banda Mustapha"

"Zauna" yace min yana sake nuna kujerar da na tashi daga kai. Na koma na zauna. Ina ganin yana kokarin daidaita numfashin sa sannan yace "me yasa kika ce banda Mustapha?" Nayi shiru ina wasa da yatsun hannuna. Ba zan iya gaya masa dalili ba, kamar yadda na zan iya gaya masa dalilin da yasa na dage akan ba Gidado bane uban cikina. Akwai wadu abubuwan da ƴa ba zata iya gayawa mahaifin ta ba, mahaifiyarta ta ke bukata, ni kuma bani da ita.

Jin nayi shiru ya cigaba. "Mahaifiyarsa tana kaunarki sosai. Ta kuma dora ranta sosai akan auren ku. Asalima dagewarta akan abun yana daga cikin dalilin da yasa na baki zaɓi dan na fara tunanin wani abu daban. Amma kuma Mustapha is like a son to me. No na bashi tarbiyya, kuma yanzu ni nake morar sa fiye da wanda ya haife shi. Shi nafi tunanin zai rike min ke amana akan sauran. Musamman yanzu after what Ahmad did to you". Jin bani da niyyar yin magana ya sake cewa "tashi ki tafi".

Na mike na koma gurin da na zauna da farko, na tarar Mommy tayi bacci, na gyara mata kwanciyar ta sannan na zauna na mayar da headphone dina ina lissafa maganganun da muka yi da Daddy. Naji dadin zancen cire wannan kaddararren cikin da yace za'a yi at seven months, meanin6ina da sauran just a month and a half tare da cikin kenan. Na biyu kuma hujjojin da Daddy yake neman kafawa akan Gidado. Daddy was right, kowanne evidence yana pointing directly at Gidado, amma bashi bane ba, na sani in my bones and soul cewa bashi bane ba, amma bani da shaida.

How I wish cewa shi ɗin ne ma. It would have made all these easier for everyone.

****.    ****.     ****.    ****     ****.    ****

Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you….

Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah.
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹


*By*


*Maman Maama*


Daga marubuciyar:
Maimoon
A'isha Humaira
Diyam
Tagwaye
Jidda

And now..... Safiyya


*Episode Four: The Choices 2*


For sponsorship,

contact 0704 203 0419 on whatsap

or

send a dm to my Instagram page

https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ==

Save my business number

0704 203 0419

and say hi on whatsap dan inyi saving naku.

Please, dan Allah, abeg, ban da kira


****. ****. ****. ****. ****. ****
Awa 8 da rabi mukayi muna tafiya kafin mu isa garin Berlin, Germany. Daddy ya zaɓi Berlin ne saboda anan ne babban abokinsa Uncle Sufyan yake zaune da iyalinsa. Akwai kuma likitan da ya kware akan ciwon Daddy wanda zai kula dashi a tsahon lokacin da zamu zauna a can. It was almost 8 o'clock pm when we landed a birnin na kasar Germany. Already muka tarar da Uncle Sufyan da dansa Abdul suna jiran saukar mu a airport. Muna haduwa da su Uncle Sufyan ya tarbe ni da murmushi "Safiyya, as beautiful as ever" na sunkuyar da kaina ina murmushi sannan na gaishe shi, duk sanda muka hadu dashi haka yake yi min, ya amsa tare da miƙa wa Daddy hannu at the same time yana cewa "duk sanda na ga Safiyya sai na tuna da Safiya, a rear gem. Har yanzu banga mace irin ta ba. Allah ya kai rahama kabarin ta". Mommy tace "Ameen ya Rabbi. Safiyya is a photocopy of her ai" Daddy ya dago yana kallo na yace "anya kuwa, sunyi kama dai a fuska, amma hali kam basu da dangantaka" na kalle shi muka haɗa ido nayi sauri na mayar da ido na ƙasa.

Abu biyu na karanta a idon Daddy a lokacin, akwai grief, wanda duk sanda akayi maganar ta sai na ga yanayin sa ya chanja, wannan yana daga cikin abinda yake kara min fahimtar irin soyayyar da yayi mata, yadda har yanzu, more than 20 years da rasuwar ta, amma bai daina jin mutuwar ta ta ba.

Abu na biyu kuma wanda yafi daga min hankali shine disappointment. Daddy was really disappointed in me. Gani yake kamar duk duniya bashi da wani disappointment da ya wuce ni.

Naji duk gwuiwowina sun sage, kamar kullum naji babu abinda nake so irin barin duniyar. A lokacin babban concern dina shine Allah ya sa hijab dina ya boye cikina tunda bani da tabbas din hosts din mu sun san da maganar cikin or not.

Daga nan muka wuce zuwa inda suka ajjiye motar su, sai da muka je na fahimci cewa motoci biyu suka zo dasu. Daddy ya juyo yana kallona yace "ki shiga motar abdul ya kai ki gidan su ki huta, mu zamu wuce asibiti" na tsaya ina kallon sa idona yana cikowa da hawaye dan naso ace na bishi asibiti anyi komai a gabana, amma kasancewar yanzu bana iya yi masa musu sai nace "okay Daddy". Na tuna da Safiyyan da, da ace seven months back ne, da zan iya rusa kukan da zai tara masa mutane a airport din idan yace ba zan bishi ba. Da ba karamin aikina bane in zauna dirshan a kasa in rike kafafuwansa ina kuka da dukkan karfina, amma yanzu sai nayi taku biyu baya na tsaya ina kallon sa ina kokarin rine kuka na. Ina kallo aka saka Daddy a bayan mota daya, Mommy ta shiga kusa da shi, yaya Mustapha ya shiga gaba sannan Uncle Sufyan ya zauna a drivers seat, aka barni a gefe ina rarraba ido.

Mommy ta sauke glass ta ce min "ki kwanta ki huta in kunje, ki sha maganin ki kuma, zan zo gidan in anjima" na gyada mata kai, Daddy kam ko kallo na bai yi ba suka tafi.

Sai da motar su ta bar gurin sannan Abdul ya ce min "okay. Daddy's girl. Nasan yanzu zaki kama kuka. Let me take you home tun kafin ki rikice min". Na goge hawayen da ya fito tare da ƙirƙirar murmushi nace "I am not crying" yace "of cause you are not. Maybe someone is cutting onions around".

Ya bude min kofar motarsa na shiga sannan ya rufe ya zagaya ya shiga side din driver muka dauki hanya. A hanya yana ta kokarin nuna min gurare amma ni bani da wani interest akan buildings and monuments dinsu, rayuwa ta kawai nake lissafa wa. Har sai da muka yi packing a gaban gidan su sannan ya juyo yana kallona yace "Safiyya, I want to use this opportunity da muke alone muyi magana. Magana nake so muyi as civilized people. Daddy na yace wai sun fara magana da Daddyn ki cewa akwai yiwuwar zasu yi mana aure" yayi shiru yana so yaga reaction daga gare ni sai yaga babu komai, ya cigaba, "so you knows about it kenan. Look, I want you to understand cewa I have nothing against you as a person, I like you. You are very beautiful and intelligent and I am very sure that akwai maza da yawa da suke layi suna son ki zabe su as your life partner. You can have any man you want. Wannan yasa na kasa gane dalilin su Daddy na bullo da wannan maganar. Gaskiya ni dai I don't want arrange marriage. Na fi son inyi aure for love. And I am sure ke ma haka. I know yadda daddyn ki yake son ki ba zai taba yi miki dole ba, and that's why I am begging you. Please idan an tambaye ki kice ba kya sona kamar yadda nima zanyi kokarin nunawa nawa daddyn haka. Let's join hands and fight this battle together. In kika yi min haka I will forever be grateful to you. I am sure kema kina da wanda kike so and I don't want to be the reason da zai saka a raba ku".

Na gado kaina ina kallon sa, part of me yana jin dadin cewa bai san maganar cikin jikina ba, part of me kuma was sad that he maybe the one da zan aura and he just told me cewa baya so na. Na ce "I understand. Kana da wacce kake so" yayi murmushi, a lokaci daya na kara fahimta dan na san irin wannan murmushin. Na hadiye wani yawu mai daci ina hango irin murmushin a fuskar Muhammad, wata irin kewar sa tana kara lullube ni, yace "Yes, ina da wadda nake so. Ban ce ta fiki da komai ba but I love her and want to spend the rest of my life with her". Nayi masa murmushi. "I understand. Kuma ina so ka sani cewa nima akwai wanda nake so, so mai tsanani. So in auren mu ya kasance sai dai in kaddarar mu ce haka. But I am not promising cewa Daddy will listen to me because things are totally beyond my control" Na bude kofa zan fita sai na kara da cewa "and I am sorry you are dragged in to this".

A gidan su na wuni ranar, mamansa mai kirki wadda dama kullum muka hadu bata da zancen sai na mamana and how close they were kafin rasuwarta. Wannan ya sa I always look forward to meeting her dan insha labaran da suka fi komai daɗi a kunnuwana amma a ranar sai na kasa zama muyi magana nace mata na gaji kwanciya nake so inyi. Ta bude min dakin da na fahimci an riga an gyara shi saboda zuwan mu, ta kuma kai min duk abinda ta tabbatar zan bukata ni kuma na karba nayi mata godiya, sai dai bata amsa ba sai ta bini da kallo kawai, and then I saw a look on her face, a look of disappointment and anger, sai dai bata ce min komai ba ta juya ta fita. But I knew it, a matsayin ta na uwa ta gane ciki ne da ni and she is disappointed in me, and angry at me, because she cared. Na zauna a bakin gado ina jin feeling ɗin da zuwa yanzu na saba da jin irinsa amma kullum intensity ɗin sa karuwa yake yi a zuciyata. Feeling na son mutuwa. Feeling na tsanar rayuwa. Na rufe ido na nayi addu'a a hankali "Allah ka ɗauki rai na a daren yau".

Sallolina na tashi nayi sannan na janyo fillow na kwanta na rufe idona tare da fatan bacci zai dauke ni ko na manta da halin da nake ciki, ko da na yan mintuna ne, amma sai dai maimakon bacci sai tunaninnikan halin da rayuwata take ciki ne suka yi ta overlapping kansu a cikin kaina. Har ban san wanda zan dauka daga ciki in duba ba, batun rabuwata da Muhammad ne ko na halin rashin lafiyar da Daddy yake ciki ko kuma na auren da za'a yi min da wanda bana so ko kuma karatuna da nayi asarar shekara uku inayi wannan alakakan cikin da yake jiki na ko kuma tunanin hanyar binciken waye uban cikin ko kuma na vultures din da suka dira akan akaina suke tsatstsagar naman jikina da rai na?

Na tashi daga kwanciyar na zauna ina lissafin rabon da inji dan cikina ya motsa tun a Nigeria. Naji wani irin relief a zuciyata "Allah yasa ya mutu" na fada a hankali tare da dora hannuna a saman cikin na dan danna da dan karfi, da karfin shima ya harbo kafa ya doke hannuna, naji wani kulukun bakin ciki ya tsaya min a makogwaro. Sannan na kara number a cikin list na abubuwan da ya kamata inyi tunani akai, "menene makomar abin da yake cikina?"

Daddy yace za'a cire shi nan da wata daya da yan kwanaki, amma shi kansa yace bai san yadda zaiyi dashi ba in an ciro shi. Ni kam ko kallon fuskarsa bana bukatar yi and I will definitely not keep it with me. Dan watarana zan iya shake shi cikin dare...

Nayi sauri na kawar da tunanin daga raina sannan na koma kan next in line, waye zan zaba a cikin choices din da Daddy ya bani? Definitely not Mustapha. I rather die than in auri Mustapha. And then Abdul dazu ya gaya min da bakin sa cewa baya sona, and bai san da maganar cikin nan ba and I don't know yadda zai dauki maganar idan ya fahimci cewa cikin shege nayi shi yasa a keso a makala masa ni, definitely he will hate me forever. Sai kuma Mukhtar. Mukhtar has been obsessed with the idea of marrying me a cikin shekarun nan. But he doesn't love me. Ni na san abinda yake yiwa, it is the same thing as abinda yasa Mommy take ta nacin a haɗa ni aure da Mustapha, Daddy ma kuma na tabbatar ya sani sai dai kokarinsa na binne abin kunyar da yake ganin nayi ne yasa yake kokarin chosing din su dan yasan zamu juya su suyi abinda muke so dan su samu abinda suke so.

Then wanne ne zan zaba daga cikin su kenan?

Naji maraici ya sake lullube ni. Babu abinda nake bukata a lokacin illa in samu someone older that I can talk to, wanda zai bani shawara ba tare da wani selfish interest a cikin shawarar ba. Naji ina kewar mahaifiyata kuma ina takaicin rashin sanin kowa a cikin danginta.

Na dauko handbag dina na bude na dauko yar karamar purse dina na bude ta itama na dauko wani tsohon hoton katin da nake yawo dashi kullum a cikin jaka. Hoton wata mata ne a zaune akan kujerar gidan daukan hoto irin na kauye, da yara yan mata su uku a jere a bayan ta. Babbar zatayi sheakara goma, mai binta takwas, yar karamar kuma ba zata fi shekaru biyar ba. Duk su ukun da ita suke kama, nima kuma da ita nake kama.

Na shafa hoton da hannuna ina lura da yadda duk su hudun suke murmushin da yake nuna yadda suke kaunar junan su, yadda suke cikin farin ciki duk kuwa da talaucin su wanda ake iya gane wa a cikin hoton ta yanayin kayan jikin su. They all had a rough life, a rough ending, but they are all fine now, they are all together now. In Janna insha Allah. Babu kuma abinda nake so a lokacin illa nima in bisu, illa in tafi gurin su.

Na dora hoton akan kirjina na rufe ido na sannan nayi kokarin mantawa da komai sai tunanin yadda rayuwar mu zata kasance a Janna tare. A haka bacci ya dauke ni

Cikin baccin naji an taba hoton dake kan kirjina. Na zabura da sauri kamar wadda za'a cirewa rai na damke hannun wadda ta dauki hoton. Ido na na shiga cikin na Mommy. Na saki hannun sannan na sauke ajjiyar zuciya na koma na kwanta na mayar da ido na na rufe. Ta juya hoton a hannunta tana kallon mutanen ciki, sai kuma ta zauna akan gadon tana kallona tace "baba Hadiza,  Saudat and the poor little Khadijah. Babu abinda Safiya take magana akai sama da su. They were her inspiration....." "And she is mine" na fada a hankali ido na still a rufe. Tayi ajjiyar zuciya sannan ta mayar min da hoton inda ta dauke shi tace "she is ours. Gabakidayan mu musamman babanku ita ce inspiration din mu. Duk hukuncin da zai yanke a rayuwa sai ya saka interest ɗin ta a ciki. What will she think? What will she say? What will she do? Kullum sune kalmomin sa. Bana kishin ta Safiyya, ban taba jin raina ya baci dan yayi considering dinta ita da bata raye before yayi considering di na ni da nake raye nake kuma matarsa ba, ban taba jin kishi ba, besides ina jin guilt ne na cewa she should be alive, ita ya kamata ta rayu ba ni ba, she should be here enjoying the empire she built with her blood and sweat. But ba haka Allah yaso ba Safiyya, and we can't question hukuncin ubangiji. I will understand if you don't like me Safiyya, maybe irin tunanin da nake yi kema kina irin sa cewa ina living the life that should be safiya's, but I cant wrap my head around the pact that you don't like Mustapha. Me yayi miki shi?"

Na bude ido na amma ban kalle ta ba kuma ban ce komai ba. Ta sauko daga kan kujerar ta zauna a kusa dani ta cigaba "Daddy ya gaya min kince ba kya son Mustapha. I won't say nayi mamaki dan tuni na fahimci yadda kike yi masa but I thought kawai kin kasa accepting dinsa ne as a brother ban dauka kin tsane shi bane ba, ban dauka zaki iya putting future din ki da kuma martabar ki in jeopardy kawai saboda mere sentiment".

Ta karasa maganar cikin daga murya. Na mayar da ido na na rufe na kuma mayar da hannuna na dora akan hoton kan kirjina. Ina jin ta tana kokarin daidaita muryarta sannan tace "am sorry Safiyya. Am sorry na daga miki murya. Amma ban taba tunanin haka daga gare ki ba. I love you with all my heart Safiyya. Haihuwar ki ne kawai ban yi ba. Idan ke baki sani ba shi mahaifinki ya sani. Soyayyar ki ce ta kawo ni gidan ku. I never expected cewa ke zaki ƙi jini na Safiyya. I never expect kuma daddy zai rufe idonsa ya goya miki. Not after all that has happened" ta sake yin shiru, nima kuma ban bude ido na ba ban kuma yi magana ba.

Naji ta kama hannuna ta rike a cikin nata, ina jin yadda natan ya dauki zafi, ta kuma cewa "Safiyya, yanzu duk duniya wa kike tunanin kina da shi da zai rufa miki asiri bayan mu? Wanne family kike da su bayan mu? Ahmad? Kina ganin dai abinda yayi miki a cikin gidan babanki ballantana in kin je gidan shi. Ko kuma Abdul ɗin gidan nan da mahaifiyar sa tun kafin in karaso gidan nan ta kira ni tana tambayar ko abinda ta gani a tare da ke gaskiya ne. Ta yaya kike tunanin zata karbe ki a matsayin sirika? Safiyya idan ma ba zaki yi tunanin yadda zanji a raina in kika yi rejecting jini na ba think of your future and the future if your unborn baby. Think ki gani ina ne kike ganin yafi dacewa da ke".

Sai ta saki hannuna ta mike ta shiga toilet. Na bude ido na ina kallon kofar toilet ɗin ina jin zuciya ta babu daɗi, tabbas Mommy tana nuna min soyayya da kulawa dai dai yadda ya kamata, bata taba cutar dani a bayyane ba, not that I know of, bata taba yi min mugunta ba tun ina yarinya har na girma, tun bata san gaskiyar wacece ni ba har ta sani. Sanin nata ya chanja abubuwa da yawa, the changes may be reality or just a pigment of my imagination dan bani da tabbas a kansu.

Abinda nake da tabbas akai shine she doesn't deserve a cold treatment from me, Safina ma haka. Mustapha is a different case duk abinda nayi masa bani da nadama amma su dai, especially Mommy ya kamata inyi kokarin kyautata mata ko dan kaunar da take nuna min. Amma kyautatawar ba zata yi involving auren Mustapha ba, in na auri Mustapha da shi zan zauna ba da ita ba and I won't subject myself to lifetime of emotional torture saboda in kyautata mata.

Ina kallon ta ta fito ta tayar da sallah nima na tashi na shiga toilet na sake alwala na fito nima na cigaba da sallolina. Sai bayan sallah asuba sannan na hau gado na kwanta bacci mai nauyi ya dauke ni. Cikin baccin naji maganganun Mommy da na Aunty Hajjo suna maganganu, nayi shiru ina son jin me suke cewa sai naji Mommy tace "to har yanzu dai bata fadi waye ba. Ko ta sani ko bata sani ba Allahu a'alam". Aunty Hajjo tace "ikon Allah. Kuma ku bakuyi komai akai ba? Kuka zauna kuka zuba mata ido?" Mommy tace "munyi iyakacin kokarin mu fa, babu abinda bamuyi ba. Munyi running duk options din mu amma ta rufe kowacce hanya da za mubi mu samo wancan yaron da muke zargi" Aunty Hajjo tace "makarantar su fa? Kun bincika ba'a can yaje ba?".

Nayi juyi kamar a lokacin na tashi. Mommy tayi gyaran murya sannan tace "ki tashi Safiyya ki ci abinci ki sha magani. Zan koma asibiti gurin Daddy". Na tashi da dan sauri na sannan nace "Mommy zan biki dan Allah. Zanje in ganshi" ta tabe baki kawai bata ce komai ba, da alama har lokacin fushi take yi dani. Na sauko daga gadon na gaishe da Aunty Hajjo, ta amsa da ɗan sakin fuska kadan ba kamar jiya ba amma kuma babu annurin da nakan gani a tare da ita da.

Da sauri na shiga toilet nayi wanka na fito jikina lullube da hijab, na debi kayana na koma toilet din babu wanda yayi min magana a cikin su, sai dana shirya na saka wani hijab ɗin sannan na sake fitowa na tarar sai Mommy ita kadai a zaune. Ina zama ta bare magunguna ta miko min tana cewa "na lura in dai bani na baki maganin nan ba ba kya sha Safiyya, ke baki damu da kanki ba ballantana ki damu da wanda ya damu da ke". Na fahimci magana take gaya min amma ban ce komai ba sai kawai na karbi magungunan a hannunta na watsa su gabaki daya a baki na hadiye. Ta tsaya tana min kallon mamaki, ta san da in zan sha magani wani lokacin sai ta kira Safina sun hadu sun danne ni sannan zasu dura min, in sun gama durawa kuma in ba sa'a suka yi ba in yi musu amai a jiki.

But now I do not care about anything anymore. Except for Daddy.

Ta ce "kinga yanzu ba zama zan ringa yi a gida tare da ke sosai ba. Ki ringa shan magani ko dan ki samu lafiya da karfin jikin da zaki rabu da abinda yake cikin ki lafiya". Na daga kafada "but I don't need it. Daddy yace I won't labour. Za'a yi aiki a cire". Ta saki baki tana kallona, na lura da bacin rai a fuskarta farko ban fahimci dalilin bacin ranta ba sai daga baya sannan na fahimta, Daddy bai gaya mata decision dinsa ba.

Ta ajiye robar ruwan hannunta tace "yaushe ne kuka yi wannan shawarar ke da shi?" Na sunkuyar da kaina "ba shawarar mukayi ba Mommy. I thought you knew. Nima gaya min kawai yayi. I am sorry. Zan ringa shan maganin".

Ta mike tsaye "ki dauki abinci ki ci ki fito mu tafi. In kuma shima abincin kunyi shawarar ba sai kin ringa ci ba shima sai ki gaya min in daina bata lokaci na akan kokarin baki. Na bar Safina ita kadai a gida, na bar twins a lokacin da suka bukata ta, and I am here a gurin da ba'a bukata ta". Ta juya ta fita da sauri

Nima da saurin na hada tea na sha sannan na bita a baya. Ina fitowa sitting room dinsu naga Abdul ya shigo da sauri, yana gani na yayi murmushi "daddy's girl, ke muke jira" ban bashi amsa ba na bishi a baya muka fita.

A asibiti muna zuwa muka shiga ciki, Mommy tana gaba ina binta a baya tunda ita tasan gurin. Muka je reception sai naji tana tambayar receptionist din da muka samu a gurin ko an shiga da Daddy gurin aikin da za'a yi masa. Na bude ido ina jin zuciya ta tana bugawa da karfi. Naji matar tace a'a ba'a fara ba an dai yi sedating ɗin sa. Ta nuna mana hanyar da zamu je dakin da aka kaishi.

Mommy ta juya zata tafi na tari gabanta da sauri nace "Mommy aiki? Wanne aiki za'a yi masa kuma?" Ta bata rai tace "ba wani major aiki bane ba fa just a minor non surgical operation zasu yi masa suyi clearing airways ɗin sa dan ya samu sauƙin numfashi. I signed the consent yesterday kafin in tafi".

Cikin daga murya nace "and why wasn't I informed?" Sai kuma na rufe bakins da hannayena biyu feeling terrible, na kama hannayen ta "Mommy I am sorry, I am very sorry. I don't know menene ya hau kaina, my emotions are all over the place. Please I am sorry" ta dafa hannuna tace "it is okay. I understand. Go and see him".

Na juya da sauri mai kama da gudu na tafi dakin da aka ce yana ciki. Ina shiga na ganshi a kwance, flat on hus back, duk da cewa naji sunce allurar bacci suka yi masa amma sai da ganin sa a haka ya tayar min da hankali. Na tsaya ina kallon sa, trying so hard not to imagine ranar da zan ganshi a haka babu rai a jikinsa. Sai naga ya mirsa hannunsa ya bude idonsa ya sauke su a kaina. A hankali naga murmushi ya bayyana a fuskarsa, irin murmushin da yake yi da idan ya ganni. Ya miko min hannunsa "Safiyya. You are here? Zo nan" na tafi da sauri na kama hannunsa da duk hannayena biyu ina jin kamar in tsaga kirjina in saka shi a ciki. Yace "I just had a dream. A very bad dream. Wai wani abu ya faru dake, something terrible. I am glad it was just a dream. I am glad you are okay" sai ya mayar da idonsa ya rufe ya koma bacci. Na kankame hannun sa a kirjina ina kuka "I am sorry Daddy. I am really sorry".

Sai da doctors din suka shiga sannan Uncle Sufyan ya fito dani ina ta kuka kamar wani major abu za'a yi masa. Da kyar ya lallashe ni nayi shiru, ina kallon Abdul yana yi min dariya but I didn't find his laughter funny. Sai da nayi shiru sannan Uncle Sufyan yace inzo muje gurin obstetric ɗin da zai ke dubani, I wanted to stay har Daddy ya dawo hayyacin sa amma yace an riga anyi appointment dole inje a ganni.


Section daban ya kaini a asibitin, yayi musu magana sai ya tafi ya barni a gurin su, suka dauki duk vitals ɗina da duk wani gwaje-gwajen da ake bukata na masu ciki suka yi recording sannan suka shigar dani gurin doctor ɗin. Shima dai tambayoyin yayi min sannan ya duba duk results din tests din da akayi min. Sai kuma yace in kwanta zaiyi scanning. Na kwanta na rufe idona, ina jin sa yana goga abin scanning din a ciki na amma ban bude ido ba. Naji yace "a healthy baby. As happy as a puppy" sai kuma yayi dariya, ni kuma ban ga abin dariya a cikin maganar ba. Ya ce "will you like to know the gender?" Nayi sauri na girgiza kai na still idona a rufe. Ya sake cewa "open your eyes and look at it" na sake girgiza kaina. Haka yayi ta tsokana ta yana jana da hira dan in saki jiki amma ni ko a jikina. Sai da ya gama na dawo na zauna sannan ya fara yi min bayanin yanayin lafiyar babyn da kuma abinda zan iya fuskanta nan gaba kafin lokacin cire babyn yayi. Ya kara tambaya ta idan da gaske ina son a cire babyn at 7 months na amsa masa da yes, ni da zasu cire shi at 6 ma so nake yi.

Har sai da ya gama yace zan iya tafiya, na mike tsaye sai kuma na dawo na zauna ina jujjuya hannu na. Ya tsayar da hankalin sa a kaina yace "is there something you want to talk to me about?" Nayi shiru kamar banji shi ba ina cigaba da jujjuya hannuna sannan na dago kai a hankali nace "when the baby is out. I want to give it up for adoption".

Yayi shiru yana kallona fuskarsa da mamaki sannan yace "are you sure? Are you sure this is what you want to do?" Na gyada kaina "I am sure" ya girgiza kansa "I have to talk to your father about this. He didn't mention something like this. I need to....." Nace "I am 21 years old. I am legally old enough to make my own decisions" ya duba file ɗina, maybe to confirm the age, sannan ya sake kallona yace "what about the baby's father. We need to have his approval as well. He needs to.." Nace "there is no father. I don't know who the father is. I was raped" kalmar rape ɗin da na fada ta saka hawaye suka fara bin fuskata, and that caught his attention. Na ga alamun tausayi a fuskarsa, sai kuma yayi dan rubutu a cikin takardu na sannan yace "I am sorry for what happened to you. But I still need you to go home and think deeply about this. If it is still what you want when you come in for your next appointment then we will take the next step. There are papers that you will need to sign. And you have to decide if you want an open adoption or closed adoption. An open adoption is when you leave all your informations so that the baby and it's adoptive parents can keep in touch with you, while a close adoption is when the baby can never be traced to you, you will have no relationship of whatsoever with the baby ......" Direct nace "closed adoption. I want to give up the baby for a closed adoption".

Ya cigaba da girgiza kansa. "Please Safiyya, reconsider. Think about this" nace "I have. I have made up my mind. This is what I want". Ya ce "okay. But this is protocol. You have to go and think about it. When you come back next week, then we will finalize your decision". Na gyada kaina. "okay. Thank you" na mike zan tafi, har sai da na bude kofa sai kuma na rufe ina kallon sa nace "one more thing please. I don't want my father to know. I don't want anyone to know.


****. ****. ****. ****. ****. ****

Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you….

Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah.
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹


*By*


*Maman Maama*


Daga marubuciyar:
Maimoon
A'isha Humaira
Diyam
Tagwaye
Jidda

And now..... Safiyya


*Episode Five: The Path of Destiny*


For sponsorship,

contact 0704 203 0419 on whatsap

or

send a dm to my Instagram page

https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ==

Save my business number

0704 203 0419

and say hi on whatsap dan inyi saving naku.

Please, dan Allah, abeg, ban da kira


Ina fita na hango Mustapha yana tsaye a corridor din yana kallon kofar office din da na fito daga ciki, na dauke kaina nayi kamar ban ganshi ba na zo na wuce shi. Ya biyo baya na yana gyaran murya. "excuse me... Akwai mutum fa a tsaye tun dazu yana jiran ki" ban kalle shi ba ban kuma tsaya ba. Ya cigaba da bi na. "Nima bani na kawo kaina ba ballantana ki wulakanta ni. Cewa akayi inzo in jira ki in kin gama in mayar da ke gida, shi yasa na taho ba dan wai ina son hakan ba, kin san ni ina jin maganar Mommy da Daddy in sun gaya min bana tsallake wa". Na tsaya da tafiyar da nake yi na juyo ina kallon sa cikin ido, yayi murmushi, sai kawai na girgiza kaina na juya na cigaba da tafiya a raina nace he is not worth it, so yake in kula shi, in na kula shi kuma na bashi abinda yake so kenan.

Ya cigaba da bi na. "excuse me??? Motar tana can side ɗin ba nan ba. You have two options here dear little sister, you can either come with me in kai ki gida kamar yadda iyayen mu suka ce or you can walk tun daga nan har gida, and in your condition, that will be very impossible". Still bance komai ba nayi hanyar inda side din da na bar Daddy dazu. Ya cigaba "okay. You have another option to get home. Maybe zaki samu wani ya baki lift. It won't be hard for you. I mean you are use to it tunda har tsaraba kika samu saboda shiga motar mutane".

Na juyo a fusace na buga masa handbag ɗina a kansa, a raina naso ace tana da nauyin da zata ji masa ciwo. Ya dafe kan "aww. Me nayi? Daga fadar gaskiya? I guess ita dama gaskiya daci ne da ita" na juya na cigaba da tafiya ganin yadda mutane suka juyo suna kallon mu. Ya cigaba da bi na yana sosa inda na dake shi. "Kar ki damu. Na yafe miki. Ni bana fushi ai kin sani. Ko da zanyi fushi ma ba zan yi fushi da 'wife' ɗina ba. We will put all these behind us. Now, you will follow me muje in kai ki gida kamar yadda Mommy tace and in turn ba zan faɗa wa Daddy inda kika je ranar nan ba, ba zan bashi labarin me Tesla ɗin nan ba. I guess it won't be hard to trace him with that kind of a car, musamman in akayi considering da rashin girman makarantar ku. I bet shi kadai yake da irin motar a cikin makarantar".

Na dakata da tafiyar da nake yi amma ban juyo ba sai da na rufe ido na na ja dogon numfashi da fatan zan hana kaina sauke mari kyakkyawa akan fuskarsa, na juyo da murmushi a tawa fuskar ina kallon sa nace "look Mustapha. Daga maganganun ka na fahimci cewa you are yet to receive the recent memo. Daddy ya fasa aura min kai, because I told him bana son ka. So stop following me around and find a life. And also stop threatening me because it is not going to work".

Daga yadda yayi da fuskarsa na fahimci cewa Mommy bata gaya masa ba. Maybe tana fatan zata yi convincing dina na amince da auren so she thought he doesn't have to know. Yace "you are lying. You have always been a little liar" na daga kafada "of cause I am a liar, na sha yiwa mutane da yawa karya, people that matters a lot to me. But I won't waste my time lying to you because you are not worth it. In baka yarda ba ka tambayi Mommy" na juya zan tafi sai dai kuma har nayi taku biyu sai na tsaya na kuma juyowa ina kallon sa nace "and about cikin jikina. Ni na yarda akwai kiyama, na san kuma ni da kai zamu je can. A can ne kuma zamu karasa maganar".

Sai da na yi nisa sannan na fahimci baya bina, kuma sai a lokacin na fahimci nayi batan kai na bi hanyar da ba ita ya kamata in bi ba. Sai da nayi tambaya sannan na gane inda na baro Daddy. Ina zuwana tarar da Mommy a zaune a waje. Na karasa gurinta ina haki saboda tafiyar da nayi kuma da sauri. Ta mike tana goge min gumin goshina da hanky din hannunta. "Ya naganki a kafa? Ina Mustaphan da na tura ya dauko ki ya mayar da ke gida ki huta?" Nace "ban san inda yake ba. Ba gida zan je ba. Ya Daddyn? Sun gama?" Ta koma ta zauna tace "eh sun gama. Na gaya miki fa ba wani abu bane za'a yi masa mai wahala ba. Bacci dai yake yi yanzu". Na wuce ta na shiga dakin, na ganshi yana ta bacci kuma ko daga yanayin yadda yake numfashi na fahimci aikin da aka yi masa ya saukaka masa numfashin sosai. Na zauna a kujerar kusa da gadon na kama hannunsa tare da sauke ajjiyar zuciya nace "I love you so much Daddy. And everything is going to be alright" amma ni kaina da na fada sai naji ban yarda da abinda nace ba, saboda a kasan zuciya ta ina jin cewa, this is only the beginning, saboda zuwa yanzu na fahimci cewa "tragedy" is another name for my family.

Har dare ina tare da Daddy, duk kuwa da yadda Mommy take ta min maganar tafiya gida amma ban tafi ba na farko saboda bana son tafiya da Mustapha, na biyu saboda ina son spending time a kusa da Daddy duk kuwa da cewa ba kula ni yake yi ba. Sai da daren sannan Daddy da kansa yace ni da Mommy mu bi Uncle Sufyan mu tafi gida, sai a lokacin na sake ganin Mustapha dan tun sa da muka rabu dashi bai dawo ba Mommy ma ina jinta tana ta cigiyar sa. Naga sun tsaya sunyi maganganun su da Mommy sannan ta taho muka shiga mota muka tafi, tunda muka shiga motar kuma bata ce komai ba har muka je gida, da muka je ma bata yi min magana ba sai suka kama hirar su da Aunty Hajjo ni kuma nayi musu sallama na shiga daki.

A dakin nayi sallah nayi shirin kwanciya bacci. Kamar kullum ina kwanciya dukkan damuwoyin da nake dasu suka saukar min, amma a daren yau abinda yafi tsaya min arai shine Muhammad. Maganar sa dazu da Mustapha yayi ta taba min bangaren da nake ta kokarin binnewa a cikin zuciyata a kwana biyun nan. Bana son in bude fejin tunaninsa dan bana jin zuciyata zata iya daukan halin da na san yana ciki a yanzu. Na cutar da shi iyakacin cutarwa. Amma kuma bana jin ko da a raina cewa abinda nayi ɗin ba dai dai bane ba. In na gaya masa gaskiya he will stick with me through thick and thin. And I am a walking and breathing tragic bomb waiting to explode. Bana son stains ɗina ya bata white ɗin sa. So nake ya tsane ni tsanar da zata saka ya manta da ni kar ya cigaba da bibiyata. So nake ya samu wadda ta dace dashi yayi aurensa ya gina kyakkyawar rayuwar sa da iyalinsa. Irin kyakkyawar rayuwar da muka fara tsarawa zamuyi ni da shi.

Na fara kokarin picturing dinsa ya yanzu, ko me yake yi? Ko yayi bacci? Na duba agogo naga karfe tara, meaning karfe takwas kenan a Nigeria. Na san bai yi bacci ba yanzu. Ten mostly yake yin bacci. A wannan lokacin mostly mukan kasance muna yin waya ne. Na fara kokarin picturing dinsa a dakin sa. Bana jin akwai wani bangare a dakin sa wanda ban sani ba saboda yawan FaceTime da muke yi idan yana dakin. Na tina da wata hira da muka taba yi a cikin irin hirarrakin mu na planning rayuwar mu.

****.     ****.     ****.    ****.    ****.     ***

"And you will look so handsome in white"

Ya bata fuska "and who told you white zan saka?" Nace "angwaye ai white suke saka wa ranar daurin aure, and I will wear white lace with golden veil and we will snap pictures, irin Mr and Mrs din nan" yayi dariya "ohh Piya, so you think I am like most people da zanyi abinda most people suke yi? I am special. I will wear something special" nace "okay to menene special ɗin, wacce color zaka saka? Pink or yellow?" Ya kyalkyale da dariya, sai kuma ya juya bayansa yana kallon kofa "kinga kin saka ni ina ta dariya a daki ni kadai, kar mutanen gidan nan suce nuts din kaina sun kwance" nace "to ka bani amsa mana. Kasan kuwa har na hango ka ka saka yellow shadda ranar daurin aure?" Ya kuma yin dariya, fuskarsa cike da nishadi dan lokacin bashi da wata matsala a duniya.

Nace "am serious fa farar shadda zaka saka" yace "to wai saboda me zan saka fara?" Na turo baki na kwabe fuska kamar zanyi kuka har da bubbuga hannuna akan katifar da nake zaune  "ni dai Allah sai ka saka fara, Allah in baka saka ba ranar kuka zanyi tayi" yace "okay okay shagwababbiyar Daddy. Naji zan saka fara, amma ba shadda ba, sai dai yadi" na danyi tunani sai kuma na gyada kai cikin nuna amincewa "okay. Allah ya taimake ka. Ranar da ka sha rigima" yace "in dai rigimar ki ce ai na saba da ita, in an tashi kawo kayan lefenki har da zanin goyo za'a saka. Dan naga alamar in kika fara wata rigimar sai na goya ki sannan zaki yi shiru".

Na rufe fuska ta ina dariya, yace "am serious fa. That's something I can do. I just can't wait for the time".

****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****.   

A cikin tunanin bacci ya dauke ni. A cikin baccin ne kuma nayi mafarki da shi. Sai dai a cikin mafarkin ba dariya yake kyalkyalawa ba, in fact fuskarsa a murtuke take da irin kallon da yayi min ranar da muka rabu dashi. Ina tsaye a kofar office dinsa hannayena biyu rike da cikina.

"I hate you" ya fada min cikin dacin murya.

"I hate you more than I have ever loved you"

"You are the worst creature that have ever walked the surface of this earth"

Sai kuma ya dauko bindiga daga cikin aljihunsa ya harbe ni da ita a kirji dai dai saitin zuciya ta. Na saki cikin da sauri na dafe kirjin. Ina cewa "I am sorry Muhammad. I am very sorry"

Ji nayi an rike kafaduna duk biyun ana girgiza ni da karfi. "Safiyya? Ke Safiyya" da muryar Mommy. Na bude ido na a firgice saura kadan in fadi daga kan gado, sai a lokacin na fahimci, mafarki nake yi, daga alama kuma maganganun da nake yi a mafarkin sun fito fili. Nayi kokarin daidaita numfashina tare da karanto addu'a, sannan na dafe kaina da hannu daya, har a lokacin ina jin amsa kuwwar muryar Muhammad. "I hate you"

Mommy tace "wanne irin mafarki kike ne haka Safiyya? Waye kuma Muhammad?" Nayi sauri na kalle ta idanuna a bude. "uhmm Muhamm... Waye Muhammad?" Na mayar mata da tambayar, tace "to ni kya tambaye ni? Ke kike ambatar Muhammad cikin baccin ki kina bashi hakuri" na girgiza kaina "ni ban san wani Muhammad ba. Mafarki ne kawai. Ni ba zan iya tuna mafarkin ma da nayi ba" sai nayi sauri na koma na kwanta tare da jan bargo na lullube har fuska ta tare da rufe idona da karfi ina sauraron yadda zuciya ta take bugawa da karfi, bakina yana furta "innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ni na san a yanzu idan Mommy da Mustapha zasu hada informations din da suke da su a guri daya, to tabbas zasu iya tracing Gidado. And I can't imagine anyi knocking gidan su gidado an gayawa iyayensa cewa yayi wa dalibar sa ciki.

Wannan mugun tunanin shi ya yanke min dukkan baccin wannan daren

****.    ****.    ****.    ****.     ****.     ****

*Him 👳🏻*

Kwanaki biyun nan suna daga cikin worse days of Gidado's life. Gabakidaya kwanaki biyun a daki yayi su, highest da ya fito shine parlor ya gaishe da Abba ya juya ya koma. In an tambaye shi me yake damunsa sai yace bashi da lafiya. Babu abinda bai ce yana damunsa ba. Yace kansa ne yake ciwo yace cikinsa, da daddare kuma da Mama ta shiga har daki ta matsa masa da tambaya sai yace kwakwalwar sa ce take ciwo.

It should be funny but it didn't sound funny to Mama, dan sosai hankalin ta yake a tashe akan halin da gudan ranta yake ciki. It also didn't sound funny to Gidado dan shi a lokacin da ya faɗa din har ga Allah ji yake yi da gasken kwakwalwar tasa ciwon take yi, sai dai kuma bai san yadda zai misalta ciwon ba.

Zuwa lokaci kowa a gidan ya fahimci halin da yake ciki, zuwa lokacin kuma kowa ya fahimci koma menene yake damunsa yana da dangantaka da Safiyya, saboda dama kowa a gidan ya san da zaman Safiyya ya kuma san da girman matsayin ta a zuciyar Gidado, har Abba.

Sai dai duk da cewa sun san abin ya shafe ta amma basu san takamaiman menene ya faru ba, wannan shine abinda Mama take ta tambaya amma ta kasa samun amsa, daga baya dai sai tayi deciding tayi involving dan'uwansa kuma abokinsa, tana saka ran zai iya gaya masa abinda su ba zai iya gaya musu ba. Bayan ta yanke wannan shawarar sai ta kira Al'ameen a waya, wanda yake aboki kuma first cousin a gurin Gidado ta kuma nemi da yazo gidan ya duba halin da dan'uwan na sa yake ciki kuma suyi magana.

Da yamma bayan ya taso daga gurin aikinsa ya zo gidan, ya gaishe da Mama ta tambaye shi lafiyar mahaifiyarsa Mami da amaryarsa Humaira, ya sunkuyar da kai yana jin kunya, sai kuma ya mike ya tafi dakin Gidado.

Ya shiga ya tarar dashi a zaune akan sallaya ya jingina bayan sa da jikin gado yana jan carbi, idonsa a rufe sai bakinsa da yake motsawa a hankali. Ya zauna a kan kujera yana kallon sa, daga inda yake yana iya lura da yadda idanuwansa suka fada ciki kuma fatar idon tayi baki.

"Muhammad" ya kira sunansa. Ya bude idon ya kalle shi sai kuma ya mayar da su ya rufe ya cigaba da jan carbin sa. Al'ameen yayi ajjiyar zuciya yace "ba tun yau ba na gaya maka. That girl is going to be the death of you" Gidado ya kuma bude idonsa yace "congratulations. You predicted right" Al'ameen ya sauko ya zauna a kusa da shi yace "ba haka nake nufi ba, believe me, I cannot say na san exactly me kake feeling right now but I know what loving a girl deeply means" bai ce mishi komai ba sai ya kuma mayar da idon ya rufe.

Al'ameen yace "me ya faru?" Yayi shiru bai ce komai ba. Al'ameen ya sake tambaya "did you guys break up?" Gidado ya a girgiza kansa yace "no" sai kuma yayi nodding yace "yes. I guess we did. I don't know" Al'ameen yace "me kake nufi da you don't know. What happened?"

Gidado yayi shiru kamar ba zai ce komai ba sai kuma yace "she is.....she said she is.....she told me that she is....... I saw that she is...." Ya hadiye yawu ya kai sau biyar amma kalmomin sun kasa fitowa. Al'ameen yayi kokarin taimaka masa "she is with someone else? She loves someone else?" Gidado ya girgiza kai "no...... Yes. I mean..." Yayi ajjiyar zuciya sannan a hankali yace "I mean she has been with someone else all along. She is married. She has been married all along ".

Al'ameen ya bude ido yana kallon sa cikin mamaki. Ya motsa bakinsa amma ya kasa magana. Gidado yace "what a fool I have been" Al'ameen ya girgiza kansa "she is lying. Karya tayi maka. Tana so ta rabu da kai ne shine tayi maka karya" Gidado ya sake girgiza kansa yace "no.... Ba karya take yi ba. I saw it da idona. She is pregnant. I saw her pregnant. She told me she has been married all along" Al'ameen ya gyara zamansa yana kare wa dan'uwan nasa kallo cikin mamaki "kai! Haba! It cannot be. Shekarar ka nawa da yarinyar nan. How can you not know? Ta yaya za'a yi ta iya boye magana kamar wannan" Gidado ya daga kafada "I don't know" Al'ameen ya sake cewa cikin fada "karya take yi fa. Ni nace maka karya take yi fake ciki ta saka a jikinta. There is no way da zaka kasa gane kana tare da matar aure for almost three years. Yadda kuke da ita there is no way da mijinta ba zai gane tana tare da wani ba. My guess is ta samu wani ne and she wants to ditch you shine tayi maka wannan karyar just to break you yadda zaka fi rabuwa da ita"

Gidado ya mayar da idonsa ya rufe yana jin ciwon kansa yana karuwa. "I don't know what to believe Ya Ameen. A yanzu haka yaki akeyi a tsakanin zuciya ta da ƙwaƙwalwa ta. Zuciya ta tana son creating all the excuses in the world dan ta kare ta. Ƙwaƙwalwa ta kuma tana kokarin sanin gaskiya. Ni kuma babban abinda nake son sani shine 'why?' idan har da gaske tana da auren me yasa tayi dating dina ta saka min gubar soyayyar ta a cikin jijiyoyin jiki na sannan ta zabi yanzu dan ta watsar da ni. Idan kuma karya take yi kamar yadda kace me yasa zata yi min karyar" Al'ameen ya dafa kafadunsa da hannayensa biyu yace "saboda kamar yadda na gaya maka ta samu wani, someone da take tunanin is better than you. Dama can ba son ka take yi ba". Gidado ya ture hannun sa daga kafadar sa yace "idan akwai abinda nake da tabbas akan shi a cikin duk wannan maganar shine Piya tana so na. I will never believe cewa ba ta so na. Something...." Al'ameen yace "haa.. this is your heart talking. Dan tana son ta. Kamar yadda kace, tana kokarin kare ta ne kawai. How can she love you and then do this to you?".

Gidado yace "i don't know. Shine abinda nake ta kokarin sani nima. Shine abinda zan iya sadaukar da komai a yanzu dan in sani. Sai dai bani da yadda zanyi in sani ɗin. Ta toshe duk wata hanya da zan bi in sani, ko kuma at least in ganta, she blocked me" ya fada yana nuna wa Al'ameen wayarsa kamar a jikin screen din ne aka rubuta haka.

Al'ameen ya karbi wayar yana kallon hoton jiki yana girgiza kai, a ransa yana matukar tausayin dan uwan nasa saboda yasan zafi da kuma zakin so, ya kuma fahimci soyayyar tayi wa Gidado mugun kamu, sai dai bai yi dace ba. So baiyi masa adalci ba.

Ya mika masa wayarsa yace "Muhammadu...... You should stop thinking about how to see or talk to her. You should start thinking about how to forget about her. Mama da Abba are very worried. She is not worth that. Nothing is worth that". Gidado yace "I can't. Ba zaka gane ba Ya Ameen. Ko da zan manta da ita ɗin ina bukatar in san gaskiya. Ina bukatar in ganta mu zauna muyi magana ta fahimtar juna ni da ita. In san ko akwai wani abu da yake damunta.."

Al'ameen ya mike tsaye, baya son yaji haushin Gidado amma kuma ya kasa hana kansa. Yace "okay taso muje gidan su sai mu tambaya" Gidado ya kalle shi bai ce komai ba dan ya fahimci bakar magana yake gaya masa, ya sake cewa "ko kuma ka kira wani a cikin yan gidan su kaji abinda yake faruwa. Ko babbar kawarta haka, ai nasan ita ma zata sani". Gidado ya jingina kansa a jikin bango yana jin kamar ya tashi ya shake Al'ameen. Al'ameen yace "ohh haka ne fa. Na manta. Baka san ko daya a cikin wadannan ba. How are you going to know the answers to those questions kuma?".

Sai kuma ya dawo ya tsuguna a gaban Gidado yace "look Muhammad, there is no way da budurwar da take son saurayi, so na gaskiya kuma na aure, zata ki kaishi gidan su, zata kuma hana shi sanin kowa nata, for over two years. A cikin biyu dole akwai daya. Ko dai rage dare kawai take yi da shi ba sonsa take ba, ko kuma kamar yadda ta gaya maka, matar aure ce take cin amanar mijinta da kai. I know it is hard Muhammad, but you must see reasons. You must be strong and accept the truth. You must let go ko ba dan kan ka ba ko dan mahaifanka" Gidado ya gyada kai, ba tare da ya bude idonsa ba yace "thank you " Al'ameen ya mike zai fita, har ya kai kofa Gidado yace "Muhammad. Kar ka gaya musu please. Kar ka gaya wa Mama".

Sai da yaji alamar ya bar dakin sannan ya bude idonsa yana kallon kofar da Al'ameen din ya fita ta cikinta, amma ba kofar yake kallo ba dan hankalin sa yana can wani gurin daban. Ya dauki wayarsa a gurin da Al'ameen ya bar ta ya kalli hoton kan screen din zuciyarsa taki amince masa da first maganar Al'ameen cewa Safiyya bata son sa tun farko, ba ya jin kuma zai taba yarda da hakan.

Ya tuna da rana ta biyu daya sake ganinta a rayuwar sa bayan haduwarsu ta farko a jirgi. Haduwar su ta biyu ta kasance ne shekara bakwai bayan ta farkon. Bayan ya gama first and second degree dinsa ya dawo yayi service. Shekaru bakwai sun wuce amma bai manta da yarinyar da ya taɓa haduwa da ita a jirgi ba. Kuma can a kasan zuciyarsa yana fatan zai kuma haduwa da ita.

****.     ****.    ****.    ****.    ****.     ****

A hankali yake tafiya a motar sa, yana juya stirring cikin nutsuwa zuciyarsa cike fal da farin cikin da bai san dalilin sa ba, amma yana tunanin akan maganar da suka yi da Abba ne dazu. Ya kunna kida kadan kadan yana tashi yana kara masa nishadi, a ransa yana lissafa rayuwarsa and how successful everything has been going for him. 

Yayi dialing number ɗin abokinsa da ya fito nema "kai ya? Gani fa a junction ɗin, ina zan juya" abokin yayi dariya yace "kai fa matsala ta da kai baka san gari ba. Abeg I can't direct you, ask Google map" ya katse wayar. Gidado yayi dan karamin tsaki "karamin dan is, sai in fasa zuwa ma" ya cigaba da driving a hankali da hannu daya dayan hannun kuma yana kokarin nemo direction din inda zai je. Ya dago kai dan tabbatar da inda yake. A lokacin ne ya ganta.

Tana tsaye a gaban mota hannunta daya rike da key din mota dayan kuma rike da jakarta. Fuskar ta a murtuke da alamar bacin rai. Ga uwar ranar da ake kwallawa a ranar. Kallo daya yayi mata ya dauke kai ya cigaba da abinda yake yi, har motar sa ta gota inda take sai kuma ya dago kai da sauri ya sake kallon ta ta mirror din motar. Gabansa ya fadi yana ganin kamar yasan fuskar. Yayi slowing down ya sake gyara mirror dinsa dan yana kare mata kallo. Yaji wani excitement ya shige shi. Komai na features din fuskarta suna nan kamar yadda yake tuna wa da su but more matured, no longer child like but lady like. More feminine. More beautiful. More beautiful than he had ever imagined she would be.

Ya tuno da ranar da suka hadu a cikin jirgi. Surutun da ta ringa yi masa, tsokanar sa da ta ringa yi, da kuma yadda suka rabu. Ita ta riga shi fita daga jirgin a ranar dan air hostess ce ta dauko mata jakarta daga inda ta barta ta taho gurinsa, ta kuma zo suka fita tare. A arrival yayi ta baza idon ko zai sake ganin ta amma bai ganta ba. He then wondered ko paths dinsu zasu sake crossing later in life.

And it did ...

Sai dai kuma bashi da tabbas din zata ma tuna da shi ballantana har ta gane shi.

Yayi reversing motar a hankali still yana kare mata kallo dan ya tabbatar da cewa ita din ce dan kar yaje yayi wa wata magana. Sai dai yana zuwa saitin ta sai ta kara yin gaba kamar bata san mota ta tsaya a gaban ta ba. Ya bude kofar motar ya fito still idonsa a kanta. Yana jin zuciyarsa wani iri dan shi dai bai taba ganin macen da ta yi masa kyau kamar ta ba, bai kuma taba tsayar da mace a hanya yayi mata magana ba.

Ta ƙara bata rai tare da juya fuskarta daya side ɗin, daga alama kallon da yake yi mata ya dame ta. Ya tako zuwa gabanta, sai ta zaro wayar ta ta fara dannawa kamar bata san dashi a gurin ba. Yayi mata sallama. "Assalamu alaikum" ta amsa, amma shi kansa da yake kusa da ita motsawar bakinta kawai ya gani amma baiji muryar ta ba. Ya danyi shiru yana tsoron kar ta wulakanta shi amma kuma yana son gwada sa'ar sa, ya dan leka fuskarta a hankali yace "Piya?"

Ta dakata da danna wayar da takeyi ta dago kai tana kallon sa da alamar tunani a fuskarta, lokaci daya kuma sai yaga recognition a fuskarta, and farin cikin da yaji a ransa was more than he thought.

"Malam Muhammadu dan fillo?"

Yayi dariya, dariyar da yaji ts wanke dukkan tsoronsa. Ta nuna shi da dogon yatsan ta "Washington DC" ya girgiza kai "no. Manchester" tace "yeah. Right. Manchester. What are you doing here? How are you here?" Yace "ke zan tambaya. Never thought I will ever see you again" tace "me too. It has been five years?" Yace "seven" tace "wow. How time flies. Kayi girma sosai" ta fada tana kallon sa tun daga kan takalmin kafarsa har zuwa yalwatacciyar sumar kansa da bai rufe da hula ba. Ya shafa kansa "ke ma haka".

Suka yi shiru duk su biyun, kowanne su trying not to look at the other. Sai kuma suka kalla a tare, suka hada ido, and then they smiled together.

"uhmm ...... Trouble with the car?" Ya tambaya yana nuna motar da take tsaye a gabanta. Ta bata fuska "wallahi... Ta mutu.... I don't know why. Ina tafiya kawai ta mutu. Na kira kuma an hada ni da mechanic har yanzu kuma bai zo ba" yace "why not leave the car here in yazo ba sai ya dauka ba. You shouldn't be here standing under the sun" ta daga mishi key din motar "sai yazo zai karbi key ai" ya girgiza kai "still sai yaje gida ya karba. You shouldn't be here alone" tayi ajiyar zuciya bata ce komai ba. A hankali yace "can I take you home?" Ta juya ta kalli motar ta, sannan ta kalle shi fuskarta kamar zata yi kuka, yace "sai in dawo wa da mechanic ɗin key din, in bai zo ba kuma I can get another one for you" ta girgiza kai "ba wannan ne damuwa ta ba. Uncle Ahmad will kill me today. Yace kar in fita da mota. Yace ban iya mota ba. Baya son a bani mota ni kuma so nayi in nuna masa na iya" Gidado ya mika mata hannu yace "mu ga key din" ta bashi, hoping motar lafiyar ta kalau itace dai bata iya din ba.

Ya bude ya shiga yayi ƙoƙarin tayar da ita amma sai yaji yana murda key din tayi wata irin kara. Ya fito yana kallon Safiyya yace "key starter din ta ta lalace. Maybe kinyi ta murda key din ne" ta fara bubbuga kafa a kasa "to ba ita ce taki tashi ba" yayi dariya "tuba take yi. Now call the mechanic and tell him key starter issues ne, tell him kuma zaki tafi gida yazo gida ya karbi key ɗin".

Tayi abinda yace sannan ya bude mata passenger's seat din motarsa ta shiga ta zauna shi kuma ya zagaya ya shiga seat din driver. Suna kama hanya ya lura duk ta zama uncomfortable, sai yayi kokarin yi mata hira "you look good. You look really good" ta danji kunya "thank you. You too" yace "so... how have the 7 years been going?" Tayi ajjiyar zuciya "like the blink of an eye" yace "na dauka ba zaki gane ni ba fa, I was praying kar ki yarfa ni" tace "nayi niyyar yin hakan fa. But sai kuma ya kasance kai ne. Ni ma nayi mamaki dana gane ka. Amma kai ya akayi ka gane ni?" Ya daga kafada "ina da saurin gane mutane. Besides, I have thought about you a lot within these years. Ke fa" tace "ina tuno da kai ne kawai idan na shiga jirgi na hadu da me aerophobia" suka yi dariya a tare.

Wayarta tayi kara, ta dauka. Shi kuma ya samu damar cigaba da kare mata kallo "Yaya Mukhtar na bar gurin fa. Na kira shi nace ya same ni a gida. Alright. Don't tell Uncle please. Thank you". Ta ajiye wayar tare da ajjiyar zuciya yace "I like the way you talk" ta juyo tana kallon sa tace "what?..." Ya maimaita "I like the way you talk. I am not sure if it is the way your lips moves or the sound of your voice or the body language, ban sani ba. I just like it. It is therapeutic" ta sunkuyar da idonta kasa tana murmushi, ya kara da cewa "and the way you smile too". Sai ta ja mayafin ta ta rufe fuskarta. Ya tsaya yana kallon dogayen yatsun hannunta.

Aka kira wayar sa, ya dauka direct yace "kai na fasa zuwa fa. And don't call me again". Ta bude fuskar ta tana murmushi tace "babu kyau karya alkawari fa" yace "ba alkawari nayi ba  fa. Besides, there is no where I would rather be then here".

Motarsa ce tayi wata yar kara sannan ta mutu. Suka juya suka kalli juna. Yayi kokarin sake tayar da ita amma taki tashi. Safiyya ta rufe fuskarta tana dariya yayin da shi kuma ransa in yayi dubu ya baci. Ta bude fuska tace "it is official. Yau da rashin sa'a na tashi" ya juyo yana kallon ta yace "ni kuma yau sa'ar dana tashi da ita bata ma misaltuwa". Tace "I am not sure. Maybe this is a sign that we are not meant to be together" ya bude kofa ya fita yana girgiza kai da sauri. "No. This is a sign that we will walk the path of Destiny together" ta fito itama tace "walking? Not driving" yace "I am ready to do it if you are" ta saka hannu tana kare rana tace "under the sun?" Ya zagayo gaban ta ya tsaya, jikinsa yayi blocking mata hasken rana yace "I will shield you".

Suka fara tafiya a hankali, side by side, enjoying each other's company, breathing in each other's scent, suna kuma updating juna akan abubuwan da suke faruwa a rayuwar su. A lokacin ne ya gaya mata karatu dama yaje yi Manchester, kuma ya gama degree dinsa na daya dana biyu, ya kuma yi service. Ya kuma sanar mata da bukatar mahaifinsa akan yaje yayi aiki a ƙarƙashin sa, da kuma shi burinsa na yayi aiki a sabuwar jami'ar da baban masa da siblings dinsa suka bude in memory of mahaifinsu ambassador Muhammad Dikko, M.D University Abuja "ina so nima in bayar da tawa gudummawar wajan kafa jami'ar".

Ta fahimta, sannan itama ta bashi nata labarin. Family dinta mazauna garin Kano ne. Ta gama Sec school dinta three years back, amma kuma sai babanta ya fara rashin lafiya. Jinyar sa ya saka bata fara jami'a ba saboda basa zama a kasar ko da yaushe suna yawon kasashe neman magani, sai yanzu ne yayi insisting dole ta dawo Nigeria ta zauna a gidan Uncle din ta anan Abuja ya nema mata admission a daya daga cikin manyan private universities ɗin da suke garin. Last week ta zo garin. Kuma already ta gaji da garin.

A lokacin suka kai karshen junction ɗin suka hau kan babban titi. Suka tsaya suna kallon juna yace "we did it. The path was rough, tiring and very sunny. But we arrived at the destination, together"

Kafin tayi magana mota ta tsaya a gabansu. Aka sauke glass din wani ya leko "Fiyya. There you are. Na kasa hakura shine na biyo bayan ki. Let's go home kafin ya dawo ya ga bakyanan" tayi ajjiyar zuciya, daga alama ranta bai so haka ba. Ta so su ci gaba da tafiya a kafa ita da shi. Duk da dai cewa a kwai wahala, but with him by her side, zata jure.

Ta juya tana kallon Muhammad tace "cousin dina ne. Gidan su na sauka. Kafin kazo dazu shi na kira na gaya masa inda nake" Ya gyada mata kai "go" tace "okay. Zamu yi magana" yace "yes. I will call you" ta danyi shiru tana kallonsa. Ya sake ce mata "go... Rana tana dukan ki. It is not good for your skin" tayi murmushi. Ya bude mata kofar motar. Har zata shiga ta kuma juyowa tana kallon sa tace "are you not forgetting something?" Yayi shiru yana tunani sannan yace "no. Me na manta?" Tayi murmushi tace "I don't know. Kawai ji nayi kamar kayi wata mantuwa" na motar ya leko. "common. Let's go sauri nake yi fa" ta shiga reluctantly ta zauna, Gidado ya ja baya tare da yi mata alamar I will call you. Ta yi murmushi.

Sai da motar tasu ta ja sannan hankalin sa ya dawo jikinsa. Sannan ya fahimci abinda take cewa ya manta. "God damnit" ya fada da dan karfi. "Damnit" Ya maimaita yana saka yatsun hannunsa duk goman a cikin gashin kansa yana jin kamar ya fincike gashin ya zubar.

Bai karbi number wayar ta ba.

****.    ****.    ****.     ****.    ****.    ****.   


Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you….

Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah.
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹


*By*


*Maman Maama*


Daga marubuciyar:
Maimoon
A'isha Humaira
Diyam
Tagwaye
Jidda

And now..... Safiyya


*Episode Six: Mother*

For sponsorship,

contact 0704 203 0419 on whatsap

or

send a dm to my Instagram page

https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ==

Save my business number

0704 203 0419

and say hi on whatsap dan inyi saving naku.

Please, dan Allah, abeg, ban da kira


Free page......


Knocking kofa ne da dawo dashi daga tunanin da yake yi. Ya mike ya koma kan kujera ya zauna yace "yes". Mama ce ta turo kofar amma sai ta tsaya daga bakin kofa tana karewa dakin kallo tace "ina Al'ameen ɗin? Ko ya fita bai yi min sallama ba" Gidado yace "ya fita, maybe ba kya kusa" ta karasa shigowa da bacin rai a fuskarta tace "ko bana kusa ai sai ya neme ni, saurin me yake yi? Ni fa na kira shi kuma sai ya tafi ba tare da na sallame shi ba" Gidado bai ce komai ba amma ya san shi ya jawowa Al'ameen wannan fadan tunda shi yace kar ya gaya mata maganar da suka yi, ya san kuma Al'ameen ya gudu ne dan baya so ta tambaye shi ya suka yi.

Ta shigo ta zauna akan gado tana kallon sa tace "ya jikin?" Ya ajiye carbin hannunsa tare da safa addu'a a fuskarsa yace "da sauki Mama, kar ki damu da ni. Zan je asibiti anjima" ta bata rai "in kaje asibitin me zaka ce musu? Ji nake dazu da na tambaye ka abinda yake damunka cewa kayi kwakwalwar ka ce take ciwo, haka zaka ce musu a asibitin? ta yaya zaka ce kar in damu? Ki yadda ka koma cikin kwana biyu, me yasa ba zan damu ba? Akan ka aka fara faɗa da budurwa ne wai?"

Gidado ya dago kai yana kallon ta, ya bude baki sai kuma ya mayar ya rufe. Shi bai san me zai ce mata ba. Baya son ya gaya mata abinda ya faru tsakanin sa da Safiyya saboda baya son ta tsani Safiyyan, duk kuwa da cewa bata san ta ba. Wannan shine zurfin soyayyar da yake yi mata.

Yin shiru sa ya saka ranta ya kara baci. "Kai ba zaka gaya min ba kuma shima dana turo ya tambaye ka ya tafi bai gaya min ba. Wani abu ne mai muni ya faru? Ko wani laifin ka aikata kake boye min?" Yayi saurin girgiza kai tare da bude ido "no, Mama babu abinda nayi fa. Babu abinda ya faru, kawai bana jin dadi ne. Kuma zanje asibiti in an jima".

Ta dauki wayarsa daga kasa ta mika masa tace "idan har babu wani abu da ya faru kira Safiyya ka bani ita mu gaisa" ya rike wayar yana jujjuya ta. "Bata kasar, kiran ba zai shiga ba" tace "WhatsApp call nko? Shima ba zai shiga ba? Ko kuma da ta tafi wata kasar a matsayin ka na mai neman aurenta bata baka layin da take amfani da shi a can ba?"

Ya ajiye wayar akan cinyarsa tare da sunkuyar da idonsa kasa, abubuwa da yawa suna yawo a ransa. Ta kuma daukan wayar and kafin ya fahimci me yake faruwa sai ta kama hannunsa ta saka fingerprint dinsa ta bude wayar. Ya dago kai da sauri yana kallon ta, trying to process abinda yaje faruwa "Mama! Mama Please don't!" Ta juyo tana kallon sa tace "ko zaka kwace wayar ne? Ko kuma akwai abinda kake boyewa ne wanda baka son in gani? I cannot just seat idle and watch you turn into this, sai dai in abinda yafi karfina ne".
Yayi shiru tare da saka hannu biyu ya dafe kansa, shi dai yasan babu wani abin ashsha da yake cikin wayarsa wanda ba zai iya budewa a gaban ta ba, abu daya ne baya so ta gani wanda kuma ya san shine abinda take after, chats dinsa da Safiyya.

Tun shekaran jiya Safiyya tayi blocking din calls dinsa, amma kuma ta manta bata yi blocking dinsa a WhatsApp ba, wanda dama shine kadai social media app din da yake yi anan ne kuma suka fi yin hira. Tun shekaran jiyan kuma yake tura mata sakonni, amma ya fahimci kamar data dinta a kashe take gaba daya dan sakonnin basa zuwa gare ta, amma hakan bai hana shi rubuta wa ba, hakan bai hana shi gaya mata duk abinda yake zuciyarsa ba, all the things that he wanted to say to her, hoping that zata bude ta karanta ko da ba yanzu ba ne ba. Ya tabbatar kuma idan Mama ta karanta sakonnin zata fahimci gaskiya abinda ya faru tsakanin sa da Safiyya, zata fahimci cewa Safiyya matar aure ce kuma har tana dauke da ciki.

Bata jima tana danna wayar ba kuwa ta ga abinda yake boyewa, tun daga expression din fuskarta ya gane ta gani.  Da sauri take karantawa harshenta har yana hardewa. Wadansu maganganun a fili wasu a zuciyarta. Har tazo kan wanda ya warware mata warware mata damuwarta ya kuma ɗora mata wata damuwar data ninka waccan.

"I only want to know me yasa kika yi min haka, me nayi miki da zaki yi min haka, how can you let me fall this deeply in love with you alhalin kina matar aure?"

Mama ta saki wayar daga hannunta ta fadi akan carpet, "Muhammad!"

Ya jawo hannayensa daga kansa ya rufe fuskarsa da su yana jin wani zazzaɓi mai zafi yana saukar masa.

"Matar aure fa Muhammad. Yanzu Gidado dama da matar aure kake tare? Matar wani?"

A muryar ta yana jin irin zafin da yake zuciyarta and how much disappointed she was in him. Ya zame daga kan kujerar ya sauko kasa "Mama.... Mama wallahi..... Na rantse miki wallahi ban sani ba" ta mike tsaye sannan ba tare da tace komai ba ta yi hanyar fita. Ya mike shima ya bita a baya da sauri "Mama, Mama" bata waiwayo ba har suka zo suka wuce Mufida a falo , Mufida ta bisu da kallo cikin tunanin abinda ya faru, har sai da ta shiga dakin ta sannan ya samu ta juyo ta kalle shi, sai dai ganin hawaye a idonta ya saka ya ji kafafuwansa sun kasa daukan sa. Ya zame ya durkusa a gabanta "innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Mama dan Allah kar kiyi kuka a kaina. Wallahi ban san tana da aure ba. Boye min tayi" ta juyo da tsawa tace masa "ka tashi ka fita ka bani guri, ka tashi in daina ganinka a gaba na kar kasa inyi maka abinda ni da kai gabakidaya zamuyi nadama" ya mike da sauri ya fita, ta turo kofa ta rufe, amma sai ya kasa tafiya ya jingina da jikin kofar sannan ya zame ya zauna a gurin, babu abinda bakinsa yake furta wa sai innalillahi wa inna ilaihir rajiun, shi kansa ya kasa tantance me yake faruwa da rayuwarsa, a cikin kwanaki biyu rayuwarsa ta juya daga good zuwa bad and now it has turned to terrible.

Tun tasowarsa he has always been Mama's boy, akwai shakuwa da fahimta sosai a tsakanin sa da ita. She raised him and his siblings with love, da soyayya ta raine su da soyayyar kuma ta tarbiyyan tar da su. Tun tasowarsa kuma ba zai iya tuna ranar da ya ganta cikin bacin rai irin na yau ba. He has always been a good boy. Da wahala yayi laifin da zata daga masa murya ma ballantana har ta kai ga zubar da hawaye a kansa. Ya tuna da maganar da Ya Ameen ya fada masa dazu, cewa Safiyya is not worth bacin ran iyayensa, a lokacin maganar bata dake shi sosai ba sai yanzu da yaga bacin ran na gaske.

Yana nan zaune har Mufida da ta ji su shiru ta taso ta biyo bayansu, a lokacin ne ta ganshi a zaune a kasa a kofar dakin Mama, hankalin ta ya tashi dan bata taba ganin yayan nata a cikin irin wannan halin ba. Ta durkusa a gabansa tare da dafa kafadarsa "Hamma? Lafiya? Me yake faruwa?" Ta fada muryar ta tana rawa kamar zata yi kuka. Ya dago jajayen idonsa yana kallon ta yace "Mufida. Kiyi min addu'a. In kinyi sallah kiyi min addu'a" ta rike kukan da yake neman kwace mata tace "kullum ina yi maka addu'a dama Hamma, amma yau zan tashi cikin dare zanyi sallah musamman dan kai, zanyi maka addu'a, insha Allah Allah zai yaye maka dukkan damuwarka".

Ranar cin abincin daren su sam bai yi armashi ba a gidan. Dan yau damuwar Gidado tafi ta kullum yawa, Mama ma kuma juya abincinta kawai take yi ba ci take ba. Daga baya ma sai ta tashi tace musu zata je ta kwanta. Gidado ba haka yaso ba, so yayi tayi masa fada, so yayi ta gayawa Abba in yaso sai ya samu damar yi musu bayani tare da kare kansa, amma maimakon haka sai ta bashi silent treatment.

Kwanan su biyu a cikin wannan yanayin. A rana ta biyun ne Gidado ya samu Mama a kitchen tana aiki tare da Mufida ya ajiye mata wayarsa. "Mama dan Allah in ba zaki saurare ni ba ma fa wayar tawa nan ki duba, ki karanta sakonnin gabaki daya zaki fahimci gaskiya ta" ta juyo ta kalle shi, zuciyarta tana yi mata zafi akan yadda dan lelen dan nata ya koma saboda mace, tace "bana bukatar duba wayarka, na riga naga abinda nake bukatar gani. Kaje kawai, zanyi addu'a akan ka zan kuma yi tunani, sannan zan gayawa mahaifinka halin da kake ciki dan ya damu da ya sani, abinda duk muka yanke a kanka kuma dole shi zaka bi". Ya gyada kai cikin amincewa. Shi indai zata daina fushi da shi to kowanne hukunci ne ya yarda zai dauka.

Washegari ya fahimci cewa ta gaya wa Abba abinda ya faru, dan sanda ya gaishe shi bayan sun dawo daga masallacin sallar asuba kin amsawa yayi, rana ta farko a rayuwarsa daya gaishe da mahaifinsa bai amsa masa ba. Wannan ya sa a ranar ko dakinsa bai koma ba anan falo ya kwanta anan falon yana jiran Abba ya shirya ya fito ya sake gwada sa'ar sa ko zai samu ya kula shi, yayi masa fada, kai ko dukansa ne ma ya yarda yayi in dai zasu daina fushi da shi.

Yana nan kwance Mufida ta fito, yaji tazo tana taba wuyansa sannan ta koma suka dawo tare da Hafeez, yana ji suna ta maganganun su sannan Hafeez din ya tafi suka dawo tare da Abba. Yaji Mama tazo itama. Ya tashi zaune yana jin sanyin acn falon tayi masa yawa a jikinsa. Abba ya aika Mufida yace ta kawo masa abinci daga nan kuma sai ya sallame su ita da Hafeez. Gidado ya dauki cup din tean da aka ajiye a gabansa ya kai bakinsa amma bai kurba ba sai ya ajiye shi, pretending kamar yasha. Mama tace "dauki ka shanye" babu musu ya dauki kofin ya shaye tas duk da kona mishi baki da yake yi.

Abba ne yayi magana yace "mamanka ta bani wani labari da ban taba tunanin jinsa ba. Tace min yarinyar da kake ta maganar za'a je nema maka auren ta, Safiyya, matar aure ce, haka ne"

Gidado ya gyada kai, har lokacin zuciyarsa ta kasa sabawa da jin sunan Safiyya tare da kalmar matar aure a hade a sentence daya. Abba yace "to me zaka ce game da haka?" Gidado yayi gyaran murya yace "ban san haka bane ba. Sai last gani na da ita take gaya min hakan" mama tace "take gaya maka me?" Yace "tace min..... Tace she is married".

Abba ya gyara zama "amma kai tun da kuke da ita ba ka taba gane cewa matar aure ba ce ba? Ta yaya? Kana me zata ninke ka a baibai tsahon lokaci baka gane ba? Wanne irin so kake mata da zai rufe maka ido from the obvious?"

Gidado yace "Abba ban san ya zanyi bayani ku gane ba. Da ace kun santa zaku fi yarda da magana ta. Babu wani alamun aure a tare da ita. Ban taba zuwa gidan su ba ballantana in gane daga nan...." Mama tace "baka taba zuwa gidan su ba? All these while har ka yi gini ka saka ni hada kayan lefe amma baka taba zuwa gidan su ba?" Gidado ya dafe kansa "how foolish he might have looked a idon iyayensa, how foolish duk wanda yaje abinda ya faru zai dauke shi, amma kuna it is easy to judge idan har abin bai faru da mutum ba.

Yace "Mama, Safiyya student ce a MD, a hostel take zaune, asalin iyayenta yan Kano ne, mahaifinta ba mazauni bane kusan ko da yaushe baya kasar. Duk sanda akayi hutu itama tana binshi whichever kasa yake a lokacin. A cewar ta kullum tana kokarin samun chance idan yazo gari ta kaini. Tace bata son kaini gurin kaninsa, wanda yake zaune a garin nan, tafi so in ganshi direct because of some family issues that she didn't mention. I didn't push sosai saboda baban bashi da lafiya, kusan ko da yaushe yana asibiti. She ......"

Mama ta katse shi "wannan shine abinda ta gaya maka? To bara in gaya maka gaskiyar magana. Babu wani gurin babanta da take zuwa. My guess is gurin mijinta take zuwa in anyi hutun. Yana kasar waje ita kuma tana nan tana karatu, in anyi hutu kuma ta tafi gurinsa. In ta dawo kuma kai gaka. Ta jefi tsuntsu biyu da dutse daya".

Gidado ya rufe idonsa yana tuno hotunan Safiyya da Daddyn ta, most of them a asibiti, ya girgiza kansa, baya son yayi tunanin abinda zuciyarsa take hasaso masa.

Abba yace "to a karshe kuma ya akayi ka sani?"

Ya bude idonsa yace "taje holiday kamar yadda ta saba, and she have been acting off for months, she came back tace tana son ganina, muka hadu a office dina, and she told me".

Abba yace "and kai me kake tunani? Do you believe she is really married ko kuma she is lying tana so ne dai kawai ta rabu da kai?"

Gidado yayi shiru because that was a million dollars question, bai san amsar ba, zai kuma iya bayar da komai dan yasan amsar. Cikin jikinta shi yake convincing dinsa akan cewa tana da aure din, amma kuma yanayin yadda tayi masa magana, da abubuwan da suka gudana kafin ranar, suna so su gaya masa cewa da akwai wata a kasa. Amma ya kasa fahimtar if those things are real ko kuma zuciyarsa da take cike da sonta ne take imagining dan ta bata kariya kamar yadda Ya Ameen ya gaya masa.

Ya dago kai yana kallon Abba yace "I don't know Abba. I don't know what to think. I don't know what to believe " yayi shiru kuma sai yayi deciding ya gaya musu all he knows, idan akwai wanda zai taimaka masa kaf duniya to su ne. Sai ya kara da cewa "she is pregnant".

Da sauri Mama tace "ita ta gaya maka?" Yace "gani nayi" tace "to wannan shine dalili, ta gaya maka gaskiyar ita matar aure ce saboda cikin jikinta. Shi ciki ai ba'a boye shi. Bata yi niyyar fada maka ba sai data tabbatar in bata fada ba ma zaka gani da idonka" Abba ya gyada kai cikin amincewa sannan yace "that will be all. Tashi kaje".

Gidado ya mike, a ransa yana jin mix feelings. Na farko yana jin dadin iyayensa sun fahimce shi duk da dai har lokacin suna ganin da laifin sa a ciki, amma kuma yana jin babu dadin yadda suka dauki maganar, a gurinsu a yanzu babu halitta worst than Safiyya.

Yana rufe kofa Abba ya juyo yana kallon Mama da bacin rai a fuskar sa yace "da ace nasan wacece yarinyar nan da ta mayar min da ɗa haka wallahi da sai na san waye uban ta a Nigeria" Mama tayi murmushin takaici tace "she can be traced, tunda daliba ce a MD, shima kansa Gidadon zai iya tracing danginta idan yayi niyya but to what end? Menene amfanin hakan? Allah zai saka masa kawai. What we should concentrate on a yanzu shine ganin ya dawo hayyacin sa".

Ya gyara zamansa yace "abinda muka yi magana akai kawai shine" tayi ajjiyar zuciya tana girgiza kanta. "I don't know dear, what works for some might not work for others. Aure kuma is a life sentence. Bana son garin neman gira mu rasa ido".

Ranar Gidado wuni yayi da wayarsa a hannun sa. Ya daina kiranta ya kuma daina tura mata messages amma wuni yayi yana kallon pictures da videos dinsu together, trying to figure out a ina hint din cewa tana da aure yake, trying to see beyond the obvious amma babu abinda ya gani sai soyayya, tsantsar soyayya. A karshe sa yaji kamar zuciyarsa zata fashe sai ya rufe wayar ya kuma rufe idonsa, a haka bacci ya dauke shi, cikin baccin ne yayi mafarki da Safiyya a tsaye a kofar office dinsa hannayenta biyu rike da cikinta, hawaye sharkaf a fuskar ta, ta mika masa hannu daya tana kiran sunan sa "Gidado please, I am sorry. Muhaammaaad...." Yayinda shi kuma ya saka hannu biyu ya hankada ta waje sannan ya rufe kofar.

*Her* 🧕🏻

Kwanaki ukun nan sun wuce wa min very slowly. Bawai ina ganin rashin saurin kwanakin bane saboda kasancewarsu event-less, a'a, abubuwa ne da yawa suke faruwa not one after the other but all at the same time, abubuwan da suka cika min kwakwalwa ta har suka sa ka bata gane komai. Mommy ta saka ni a gaba da zancen auren Mukhtar, Mukhtar ya takura min da kokarin chanja min ra'ayi a kansa, Abdul ya cigaba da rokon na akan kar na zabe shi a matsayin miji, yayin da Daddy ya cigaba ta tambaya ta akan wanene zabina.

Ni kuma a gurinta zancen aure shine least of my problems, babban matsalata shine lokaci yayi sauri yazo a raba ni da cikin jikina ko na samu freedom ɗin da zan ji daɗin jinyar Daddy, ko hakan zai bani damar rekindling relationship din mu. Sai dai kuma shi Daddy kullum maganar sa ita ce "bana son in tafi in barki a wannan yanayin Safiyya. So nake in gyara rayuwarki kafin in tafi in barki".

And through all these, Gidado weight heavily in my heart.💜 Tunanin halin da yake ciki ya kara wa wuni na tsaho, mafarke mafarken sa kuma sun hana min bacci mai nauyi.

A ranar da muka kwana biyar a garin ne na samu nayi dogon bacci da safe irin wanda na jima ban yi irin sa ba. Har Mommy ta tashi ta shirya ta tafi asibiti gurin Daddy ta barni bacci. San da na farka na danji dadin jikinta sosai, dan rashin baccin ma yana daya daga cikin abubuwan da suke toshe min tunanina. Na tashi nayi wanka na fito ina shirya wa ina tunanin yadda zan kai kaina asibitin tunda babu kuɗi a hannuna dan tunda muka zo ban yi chanjin kudi ba. Na zauna tana lissafe lissafen abun yi sai ga Aunty Hajjo ta shigo dakin. Na gaishe ta ta amsa sai naga ta samu guri ta zauna akan kujera, wannan ya saka ni feeling uncomfortable na sunkuyar da kaina, hoping cikina bai fito sosai ba. Sai naji ta fara magana "Safiyya dama ina ta so muyi magana da ke amma bana samun damar kasancewa da ke ke kadai, kuma maganar da zan yi miki da ke kadai nake son yinta.

Na cigaba yin shiru ban ce komai ba, ta cigaba "Sa'adatu ta bani labarin abinda ya faru dake, ko kuma ince abinda ke kika gaya musu cewa ya faru da ke, dan a yadda na fahimta basu yarda da labarin ba nima kuma har yau labarin bai kwanta min a rai ba. Amma kuma na kasa ganin laifinki ballantana in zauna inyi miki fada ko inji na tsane ki ko inji ina kyamar ki. Hakan kuma yana da alaƙa da mahaifiyar ki. Allah ne shaida ta har ta rasu ina yi mata kallon yaruwa ta, in fact zan iya kiranta da role model dina dan nakan kwaikwaye ta akan abubuwa da yawa musamman harkar kula da miji da kuma nuna soyayya ga yaya. Ina iya tuno da sanda ta haife ki Safiyya, ina tuno irin tarin soyayyar ki da na gani a idonta a lokacin da naje yi mata barkan haihuwar ki. Ban yi mamakin yawan soyayyar ba saboda la'akari da nayi da jimawar da tayi tana neman haihuwa kafin ta same ki, na kuma kara fahimtar soyayyar sanda ta gaya min cewa likitoci sun tabbatar mata da cewa bayan ke ba zata sake haihuwa ba".

Na saka hannu na goge hawayen da already ya fara bin fuskata, ta cigaba "ina kuma iya tuno lokacin rasuwar ta Safiyya, a gaba na aka yi mata sutura. Abinda nafi iya tunawa a lokacin shine sautin kukan ki. You were barely two years old. Kowa a gidan yayi kokarin ya rarrashe ki amma kina ta kuka kina kiran sunan da kike gaya mata 'ammi', abinda yafi tayar min da hankali a lokacin shine idan na kalle ta a kwance babu rai kuma na tuno da cewa ruhinta yana gurin kuma tana jin kukan ki amma bata da damar rarrashin ki duk kuwa da irin tarin soyayyar da take yi miki. It broke everyone's heart, musamman saboda yadda mutuwar tata ta kasance".

Ta dakata tana kokarin daidaita muryarta, daga alama kuka ne yake kokarin kwace mata. Ta cigaba "wannan shine nightmare din kowacce uwa, and I couldn't help but think about dan karamin dana Abdul Hakim, na lissafa idan nice na mutu what will happened to him? Nayi kuma tunanin taki rayuwar ya zata kasance? Tun a lokacin na fahimci kina cikin jarabawa babba kuma kin rasa wani bangare na rayuwar ki da ba za'a iya replacing ba, amma kuma ban dauka gibin da aka samu zai kai ki ga matsayin da kike ciki a yanzu ba. I offered to take you, dan inyi kokarin cike wannan gibin, bayan ni mutane da yawa sunyi kokarin daukan ki amma babanki ya hana, yaki bawa kowa ke yace shi zai raini abarsa da kansa. Ina iya tuna wata rana da muka je tare da mai gidan nan dan mu duba halin da kuke ciki, muka tarar da shi ya goya ki da zani a bayansa kina tayi masa rigima, duk da ma'aikatan da suke gidan ku amma ba zai iya bawa kowa ke ba saboda girman soyayyar da yake yi miki".

Ta sake yin shiru. Muka yi shiru baki daya sai sautin kuka na kadan kadan, ta cigaba "ban sani ba ko ma'anar labarin nan da nake baki tana fitowa, ban sani ba ko kina gane me nake nufi. But you are so precious Safiyya. You are far greater than yadda kika mayar da kanki. And you have enemies everywhere. Labaran da Sa'adatu ta bani akanki, ban san wanne ne gaskiya wannan ne akasin hakan ba. Ba zan kuma yi claiming nasan abinda yake zuciyar mutane ba. Ta gaya min cewa za'a hada auren ku ke da Mustapha idan kin haihu. Amma kuma mai gidan nan shima ya gaya min cewa suna son idan kun amince zasu hada auren ku ke da Abdul. Ban san wanne ne gaskiya ba. Amma ina son gaya miki har yanzu a raina ina da niyyar daukan ki in rike ki in dai har zan samu wannan damar. In kin zabi Abdul zan so hakan. In baki zabe shi ba kuma ina so ki san cewa I will be here for you whenever you need a mother".


****. ****. ****. ****.


Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you….

Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah.
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹


*By*


*Maman Maama*


Daga marubuciyar:
Maimoon
A'isha Humaira
Diyam
Tagwaye
Jidda

And now..... Safiyya


*Episode Seven: The Good and the Bad Choices*


A ranar ban je asibiti ba sai dare, na zauna a daki ni kadai with my thoughts thinking in nayi spending a day with my self zan iya yanke wa rayuwata shawara. Amma sai dai har daren ban zamu na yanke din ba, sai dai kamar kullum, ranar ma nayi adduoi sosai akan Allah ya dube ni ya kawo haske a rayuwata.

A ranar ne kuma na fahimci dalilin da yasa na kasa samun zabi a cikin samarin da Daddy ya lissafa min, dalilin kuwa shine Gidado. In dai har zan cigaba da yiwa aure hangen da muka yi masa ni da Gidado to kuwa sai dai in Daddy yayi zuciya ya zabar min da kansa dan ba zan iya zabar kowa ba. Amma kuma sai naji cewa ina ma dai zaiyi hakan? Da ya dauke min wani babban nauyi a kaina, da ya cire min guilty feeling da nake ji a raina a duk lokacin da nayi tunanin zabar wani ba a matsayin miji wanda ba Gidado ba.

In dai har ba Mustapha zai zabar min ba to bani da matsala.

Abdul na san idan na zabe shi bani da matsala da iyayen sa, dan maganar da Aunty Hajjo tayi min yau ta kuma tabbatar min da kaunar da take yi min, sannan Uncle Sufyan kuma zan iya kiran shi da second father dina dan duk duniya Daddy bashi da aminin da ya amince wa kamarsa. Amma kuma Abdul yana da wadda yake so kamar yadda ya gaya min baki da baki. Kuma experience dina da soyayya ya saka na fahimci cewa kowace ce ma yana kaunar ta sosai. Duk sanda nayi tunanin zabarta sai in hasaso cewa Muhammad ne sanda muke tare muke tsara rayuwar mu tare sai iyayensa su haɗa shi aure da wata saboda selfish reason ɗin su. It would have destroyed our lives. And I do not want to destroy someone else's life dan ni in samu farin ciki.

Mukhtar on the other hand yana so na, dan yana daga cikin few mazan da suka taba physically confessing soyayyar su gare ni. Mukhtar ya jima yana so na, soyayyar da ni a gurina na fara daukan ta obsession har ta fara irritating dina kuma tasa yayi loosing girmansa na yaya na a idona. In na aure shi at least zan zauna da wanda yake sona ko da kuwa ni bana son nasa amma kuma iyayensa fa? Uncle Ahmad shine dan uwa daya tilo da Daddy yake dashi a duniya, komai namu a hannunsa yake tunda Daddy ya fara rashin lafiya more than five years ago, sai dai kuma tun ina karama nake samun problem dashi da matarsa dan suna min kallon spoilt girl da bata da tarbiyya, problem din namu kuma ya karu a shekarun bayan nan, sannan ya zama worst bayan bayyanar ciki na. Zasu karbi aure na dole, and zasu iya farinciki ma da hakan, sai dai hakan baya nufin zamu daidaita dasu ko kuma zasu kasa goranta min ko nan gaba.

And Mustapha, in na zabi Mustapha rayuwa ta will be a disaster, dan ban taba tsanar mutum ba kamar yadda na tsane shi and there is no way da zan iya neman aljanna ta a karkashin sa. Sai dai kuma Mommy tayi min dukkan halaccin da mutun yake nema daga wani mutum, ba ita bama, danginta sunyi wa Ammi na halaccin da duk mutum yake bukata daga mutum, musamman wanda ba dan uwansa ba. Duk da dai nasan a yanzu ba wai dan soyayya ko halacci ne yasa suke son hadin auren mu ba, but I do not care about that, da ace zan iya 'managing' zama da Mustapha, da tabbas shi zan zaba.

Kamar kullum tunda muka zo garin, sai na samu kaina da yin adduoin istikhara da neman Allah ya bayyana min zabin sa a fili ya kuma tsayar min da zuciya ta akan zabin nasa.

Kwana biyu bayan nan, da dare ina kwance kamar kullum ina kallon ceiling na kasa bacci, a lokacin babu abinda nake nema irin abinda zaiyi taking ɗina away from my thoughts. Na tuno da twins sai naji guilty feeling dan tun da muka rabu a Nigeria bamu sake yin magana ba. Na dauko wayata na kunna ina lissafin time ɗin Nigeria amma sai na lura dare yayi sosai a can, maybe ma sunyi bacci. Amma sai nayi tunanin hawa online in duba su. Sai dai ina kunna data din wata ta naji gaba na ya fadi, sai a lokacin na tuna cewa banyi blocking Gidado from Whatsapp ba kuma na tabbatar ya neme ni ta can.

Na bude Whatsapp din na tsaya ina kallon yadda messages din suke shigowa a guje, har suka gama suka tsaya. And like I  expected, akwai da yawa daga Muhammad. Na kasa bude sakon nasa saboda tsoron abinda zan gani, zuciya ta ba zata iya daukan wasu karin bakaken maganganu daga gare shi ba. Idan kuma rokona yake ba zata iya jure cigaba da butulce wa soyayyar sa ba. Sai dai kuma a lokacin na sani har cikin zuciya ta cewa rabuwa da shi shine abu mafi alkhairi da zan yi masa a rayuwa. I couldn't stain his clean life with my dirty and tragic life. Idan ma gaya masa gaskiyar abinda ya faru da ni ba zai taɓa rabuwa da ni ba, iyayensa kuma ba zasu taɓa amincewa ya aure ni ba, nawa iyayen kuma zasu kama shi da zargin yana da hannu a cikin abinda ya sameni. So in whatever way shine a ruwa. And I rather drown myself then get him wet. Wannan shine zurfin soyayyar da nake yi masa.

Message dinsa na karshe kawai na karanta.

"please Piya, I just want to know why".

Na rufe ido na ina jin damshin hawaye na a akan kuncina na danne conversation din mu sannan na danna delete, knowing fully well that nayi deleting dukkan chats dina da shi. Sai da nayi deleting dan kar in karanta sannan na bude nayi masa reply, duk da ban san complete abin da yace ba. Na gama rubutawa na tura masa sannan nayi blocking dinsa from my Whatsapp chats.

Na saka hannu na biyu na rufe fuska ta, nayi kuka na mai isa ta sannan na bude fuskar na goge hawaye na na cigaba da scrolling through the chats ko zan samu abinda zai dan kwantar min da hankali na ko yayane. A lokacin nayi karo da messages din Yaya Mukhtar. Na bude, duk kuwa da cewa a raina na san shima wani karin bakin cikin zai kara saka wa zuciyata. Maybe ma gorin cikin jikina zai yi min. Amma kuma sai na tarar hakuri yake bani

"Fiyya ban san da wanne kalaman zanyi amfani ba in baki hakuri, daga ni har Abba na san mun bata miki, a lokacin da ya kamata mu zama mune masu share miki hawaye sai kuma muka zama mune masu saka ki kuka"

"Kin san halin Abba, it was just his temper talking not him, and he loves you shi yasa yake takaicin halin da kike ciki. Please kiyi hakuri ki yafe masa"

"And ni kuma. You of all people know what my problem is, kishi ne yake damuna ba wani abu ba. I know I shouldn't have said zan taimaka miki in aure ki because like you said, ni ne nake neman taimako a wajen ki, cos nine nake tsananin son ki. And it would be my pleasure to marry you ko da kuwa nakasa ce ta same ki. And whatever kika haifa, zai zama ɗan mu ne ni da ke babu wanda zai san abinda ya faru. This I promise you with my life"

"Please Safiyya in kinga messages ɗina ki kira ni. Ko ki kira Abba if you are still angry with me. We are worried about you. Bama samunki a waya and Daddy baya daukan kiran mu daga ni har Abba".

And the last message

"Ki gaya wa Mustapha, duk sanda ya shigo Nigeria sai yayi regretting. Na rantse sai na chanja masa kamanni".

Na ajjiye wayar tare da yin ajjiyar zuciya. Na rufe ido na ina jujjuya kalaman Mukhtar a raina sannan kuma ina tunanin abinda ya haɗa shi da Mustapha. Dama can basu fiya jituwa ba tun muna yara. Shi Mukhtar muguwar zuciya ce da shi irin ta Daddy da Abba, shi kuma Mustapha silent killer ne, da wahala kaga bacin ransa. Ga ladabi da biyayya a gurin manya. Da haka ya siye zuciyar Daddy. But only I know who he really is.

Da safe na tashi nayi wanka ina shiryawa kenan yayin da Mommy ita kuma ta shiga wanka, sai naji wayata tana kara, sai dana dan tsorata dan na manta da cewa na kunna ta. Sai kuma na fara murna ina saka ran twins ne suka kira ni, amma dana dauki wayar sai naga Uncle Ahmad ne. Nayi ajjiyar zuciya na zauna a bakin gado sannan na dauka tare da sallama.

"Abba ina kwana"

Ya amsa "lafiya lau Safiyya. Tunda kuka tafi sai yau kika kunna waya ne?" Nace "jiya da dare na kunna" yace "saboda menene? Saboda kima ganin babu wanda ya damu da ke da zai neme ki a waya? Ke kin kashe waya shi kuma Yaya na kira wayarsa yafi sau cikin charbi amma ba'a barinsa ya dauka. Na san kuma matar sa tare da wannan tsinannen yaron Mustapha. Har Mustapha ne ni zan kira Yaya ya dauka yace min wai bacci yake yi yace kar a dame shi. Ni fa?"

Na dafe kaina saboda already har naji ya fara yi min ciwo da safiyar nan. Nace "kayi hakuri Abba, in sha Allah yau in naje asibitin sai in kira ka in bashi wayar kuyi magana"

Ya danyi shiru "eh ina son magana dashi sosai, ke ma kuma ina son magana da ke. Ina son in baki hakuri akan abinda ya faru ranar nan. Na fahimci shine dalilin da yasa Yaya yake fushi da ni. Ni ba dan wani abu nayi miki fada ba sai dan ina ganin na isa inyi miki fadan ne. Uwa daya uba daya ne suka haife mu ni da Adam. Ke a matsayin ƴa kike a waje na. Ban dauka dan nayi miki fada Yaya zai dauki fushi dani har ya daina yi min magana ba. Ban dauka dan nayi miki fada zaki je ki kai kara ta gurin sa ba".

Na girgiza kai kamar yana kallona nace "Abba wallahi ban kai karar ka ba. Ba da niyyar kai karar ka nayi masa magana ba....." Ya katse ni "I know Safiyya. I understand. Wannan matar tasa ce zata hada. She have brainwashed you two ba kwajin maganar kowa sai tata. Ba kwa daukan kowa da mutunci sai ita da yayanta. Ni na san ita ce ta saka ki kike ta bina akan wai sai na dauki kuɗin ki na siya wa ƴaƴan ta motoci " na sake girgiza kaina "Uncle ba ita ta fada min ba, ni ce .." yace "ba zaki gane ba Safiyya. Ba zaki gane ba. Kamar yadda nace, she have brainwashed you". Nayi shiru ban ce komai ba a lokacin da Mommy ta fito daga toilet tana kokarin shiryawa.

Yace "in kinje asibitin ki gwada hada ni da Yaya ko Allah zai sa ya sauko muyi magana. I am not feeling comfortable with you two tare da su. Hankali na ba'a kwance yake ba" na gyada kai ina kallon Mommy da ta tsaya da abinda take yi tana kallona. Nace "insha Allah, zan yi masa magana in naje. Insha Allah, komai zai dawo dai dai" yace "good. Idan kinyi haka kin kyauta mana gabakidaya. Dan duk duniya baku da wadanda suka fi mu. Muma kuma duk duniya bamu da wanda wadanda suka fi ku".

Na cure wayar daga kunne na na ajiye ta a gefe, Mommy da har lokacin take kallo na tace "waye?" Nace "Uncle Ahmad ne " ta bata rai "Ahmad ba shi da kunya wallahi. Me kuma yake ce miki bayan irin wulakancin da yayi miki a cikin mutane? Me kuma zai ce miki?" Nayi shiru da farko, amma ganin alamar amsa take jira sai nace "yana so yayi magana da Daddy ne. Yace baya samun sa a waya" tayi tsaki, "to ba dole yaki daukar wayarsa ba. Ta yaya za'a yi mutum ya cire maka zani a kasuwa sannan kuma yazo gida yace zai daura maka? Na dauka ma maganar wannan marar kunyar yaron zai yi miki. Wannan yaron ko maye ne shi to sai dai yaci kansa wallahi dan kin fi karfin sa".

Haka ta cigaba da maganganun ta ni dai har na gama cin abinci na na kammala shiryawa ta. Sannan ita na taci muka fito muka yi wa Aunty Hajjo sallama muka tafi. Tun a mota ta bawa Mustapha labarin nayi waya sa Uncle Ahmad, ina jinsa yana bata hakuri wai kar ta sawa kanta damuwa shine maganin daga Uncle Ahmad ɗin har Mukhtar. Ni dai bance musu komai ba duk kuwa da kokarin saka ni da suke yi a cikin maganar.

Muna zuwa asibitin muka tarar an yi discharging Daddy. Sun gama bashi duk wani treatment ɗin da zasu bashi babu kuma sauran wani abu da zasu iya yi masa. Wannan shine dama mostly abinda ake yi masa a duk asibitocin da muke zuwa. Sai dai suke mana muje gida in wani symptom din ya sake bayyana ko wani ya zama worst sai mu dawo. Amma cutar sa babu magani. Har yanzu ba'a samu maganin ta ba. Sai a lokacin nake jin ashe Daddy ya saka an kama mana apartment din da zamu zauna kafin sanda za'a yi min aiki. Plan dinsa dama shine in an sallame shi mu samu gida mu zauna baki daya har sai na rabu da cikin jikina sannan zamu koma Nigeria. Damuwarsa kuma har lokacin ita ce bai san yadda zaiyi da abinda za a ciro daga cikin nawa ba and definitely baya son mu zauna tare da abinda zan haifa. Bai san already na samo solution to that ba.

Sai da na bari ya tura Mustapha ya karbo sauran magungunan da akayi masa prescribing, Mommy kuma ta fita gurin nurses zata yi making some inquiries sannan na jawo kujera kusa da shi kaina a kasa nace "Daddy, Uncle Ahmad yace yana ta neman ka a waya baya samun ka". Ya bata rai "ina ganin kiran nasa ai. Me zai ce min? Ban dauka yana daga cikin wadanda zasu goranta min a duniya idan wata kaddara ta fada min ba". Na girgiza kaina "ba gori yayi min ba Daddy. Faɗa yayi min" ya dauke kansa yace "haka yace miki kenan? Da ke yake so yayi amfani ya dawo gare ni kenan. Na riga na yanke hukunci, in Allah ya sauke ki lafiya mun koma Nigeria zan karbe komai namu da yake hannunsa. In kinyi aure lokacin your husband can take care of everything for us" naji hawaye yana taruwa a ido na. Na sake cewa "Daddy, duk duniya fa bamu da wanda ya fishi. Blood is thicker than water" yayi dan karamin murmushi "haka yace miki?" Na sunkuyar da kaina ina wasa da yatsuna ban ce komai ba. A lokacin na kammala yanke hukunci na. Na dago kai nace "Daddy na yanke shawara, akan zabin da ka bani"
Ya juyo yana kallona amma bai ce komai ba.

Nace "na zaɓi Mukhtar. Mukhtar zan aura".

****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    

A bangaren Gidado ya dan samu sauki, ba wai saukin zafin da zuciyarsa take yi masa ba sai dai yanzu iyayensa sun dan sauko duk da dai basu dawo yadda suke da ba. Still suna blaming dinsa for being negligent, for being vulnerable, for letting a small girl toyed with his emotions. Two days after zaman da suka yi dashi ne suka sake kiran sa suka gaya masa hukuncin da suka yanke a kansa.

"Ba za'a fasa haɗa bikin ka da na Mufida ba kamar yadda muka yi niyya. You are going to get married"

Ya dago kai yana kallon su, feeling confused. Abba yace "ka duba cikin yan'uwa, tun daga yalleman zuwa Kano zuwa Abuja, ka fitar da mata, cos you are getting married in the next two months".

Ya juya yana kallon Mama, hoping ko zai samu wani hope daga gare ta, amma sai ya ga taki yarda su haɗa ido kuma a duk sanin da yayi wa iyayensa duk maganar da daya yayi to dayan ma ita yake goyon baya.

Abba ya cigaba da magana "believe us Muhammad, it is going to be the best thing that has ever happened to you. Duk kan mu mun san bayan abinda yarinyar can tayi maka, it will take time for you to heal and trust women again, and from our experience, the best feeling ever is to fall in love after marriage. And it is the most easiest. To make things easier for you, mun baka zabi. Choose wadda duk kake ganin zaka iya so later on, mu kuma zamu yi wa iyayen ta magana and if bata da wanda take so, shikenan"

Gidado ya sake juyawa ya kalli Mama, ta fahimci yana bukatar ta, tayi ajjiyar zuciya tace "It is going to be okay Gidado. Wannan shine decision ɗin mu. Kuma sai da mukayi dogon tunani kafin mu yanke shi. And ba zamu taɓa yin abinda zai cutar da kai ba. Kuma in kayi biyayya a gare mu ba zaka taba nadama ba"

Ya sunkuyar da kansa kasa a zuciyarsa yana hoping ina ma dai shi mace ne, ina ma dai zai iya zama yanzu a gaban iyayensa yayi ta rusa kuka har sai sunce sun janye hukuncin da suka yanke.

Jin yayi shiru ya saka Mama ta sake cewa "ina fatan yarinyar nan bata saka dafinta a zuciyar ka har level ɗin da zai kai ka ga bujirewa maganar mu ba".

Ya dago kai yana jin zazzaɓi yana neman rufe shi yace "ɗan Allah Abba, ina neman alfarmar a bani lokaci in yi...." Mama tace "dawa zaka yi shawarar? Da ita?" Ya girgiza kai da sauri "ba da kowa zanyi shawara ba Mama. Zan dan tattauna maganar ne da zuciya ta. I just want to have some time to think " Mama ta sake cewa "babu komai a zuciyar ka Muhammad sai soyayyar waccan matar. I have seen the kind of messages da kake tura mata. I have read yadda kake begging dinta kamar wadda take rike da ranka a hannunta" ta karasa maganar cikin dacin murya and he can literally feel irin tsanar da take yi wa Safiyya.

Abba yace "tomorrow. You have until tomorrow".

Ya maimaita "tomorrow. Okay" sai kuma ya mike da sauri ya fita waje. Sai da yaje wajen sannan ya tuna babu abinda zaiyi a wajen. Babu gurin wanda zai je wanda zai iya hana iyayensa abinda suka yi niyyar yi. His grandparents will definitely back his parents up musamman in suka ji abinda ya faru, his auntie and uncles too, and then marriage proposals will start flying from alla angles. Babu irin tunanin da bai zo kansa ba. If only he can see Piya maybe he can convince her leave her husband tazo su yiwa iyayensa karyar cewa maganar da ma ba haka bace ba misunderstanding aka samu, and then get married.

Sai kuma ya dafe kansa yana tunanin ta yadda aka yi ma har yayi irin wannan tunanin. Lallai soyayya babu abinda bata sakawa dan a lokacin abubuwa kadan ne ba zai iya aikatawa ba dan ya samu Safiyya. Love yana kokarin turning the good boy he is into a bad boy. Ya dauko wayarsa and for the nth time ya kira number ɗin Safiyya.

"Common Piya" ya fada yana jin ransa yana kara baci. How can you love and hate someone so fiercely at the same time?

Ya buɗe motarsa ya shiga, ya kalli side ɗin da take zama hoping to see her appear ko da na second daya ne. Sai kuma ya dauke kansa ya tayar da motar ya fita daga gidan a guje. Sai dai kuma shi kansa bai san inda zaije ba. Bai san abinda zaiyi ba. MD University ya dosa, the first time da ya shiga tun ranar da suka rabu da Safiyya. Kamar yadda yayi tsammani babu mutane sosai a cikin makarantar saboda dalibai suna hutu, but yana hoping wanda yaje nema yana nan. Ko baya nan ma zai nemo shi duk inda yake. File din Safiyya yake so a dauko masa, address din ta yake so a bashi, kano zai je a yau yaga babanta or her husband, whatever the case maybe. In yaje sai ayi duk wacce za'a yi.

Ya dauko wayarsa da niyyar kiran wanda zai karbi informations din a hannun sa, sai dai garin neman number ɗin ya lura da notification din da ya shigo masa wanda bai ma lura da sanda ya shigo ba. A message from Piya 💝.

Wani faduwar gaba yaji, and then cikin rawar hannu ya bude message ɗin ya karanta.

"Dear Muhammad. I am very sorry for what happened. Please find it in your heart to forgive me ko ba yanzu ba. But for now, please stop trying to contact me. And don't look for me dan Allah. I have made a mistake naci amanar mijina with you. Now I have repented bana son in kara aikata kuskuren da na aikata a baya".

"Mijina bai san abinda nayi ba and I want to keep it that way. Bana son in breaking heart dinsa because I love him so much. Please, do not break up ny happy home. You will soon get over me and move on as I have gotten over you".

"Dan Allah, for the sake of the love that you have for me. Don't let my husband know".

Ya maimaita jaranta message din ya kai sau uku, sai ya rufe shi ya sake budewa hoping it will disappear amma still yana nan.

Wayar ta zame daga hannun sa ta fada kan kafarsa, yayinda shi kuma ya saka hannu biyu ya rungume kirjinsa dan ji yake yi kamar zuciyar sa zata fito. Sai kuma ya kifa kansa akan stirring motar.

Ya jima a haka kafin da dago, ya kunna motar ya jata a guje ya fita kamar yadda ya shigo a guje. Ya jima yana zagaya gari ba tare da yasan inda zashi ba, har sai da yaga rana tana neman faduwa sannan ya doshi gida, zuwa lokacin already ya yanke decision ɗin sa.

Yana shiga gida ya samu Mama a zaune a falo suna hira da Mufida. Suka bishi da kallon mamaki da kuma tausayin yanayin sa. Ya zauna daga can gefe sannan yace "Mama na yanke shawara akan maganar da kuka yi min dazu" ta gyara zama tana kallon sa tace "ba sai gobe ba?"

Yace "babu bukatar hakan. Babu bukatar jiran gobe. Babu abinda zan chanja tsakanin yau da gobe. Na amince da maganar auren da kuka yi. Allah ya sa albarka. Amma ina neman alfarma guda uku. Na farko ina so ku zaba min da kanku, bana jin zan iya zaba da kaina. Na biyu ina son dan Allah duk wadda zaku zaba ya zamanto ta amince da kanta ba takura mata aka yi ba, zan so kuma ace tana sona ne dama, at least that will make things easier. Na uku, Please, kar ku zaba daga cikin yan'uwa, nafi son bare".

Mama ta bata rai tace "why not? Me yasa bayan muna da yammata masu hankali da tarbiyya da ilimi, wadanda kuma muka yarda da su muka yarda da asalin su sai mu tsallake su mu tafi nema a wani wajen? Ta yaya gida bai koshi ba zamu bawa daji?"

Ya girgiza kai "Mama, there is a chance that this may not work. And I value zumuncin mu da yan'uwan mu a lot that bana son in zama sanadin samun sabani tsakanin mu. Please ku nema min bare yadda ko ba'a dace ba effects din ba zai zama da illa sosai ba".

Mama tace "to ni yanzu Muhammad ta ina zan fara nema maka mata a cikin dan lokacin da muke da shi. Yaushe aka samu matar har aka yi neman auren da bincike da komai?"

Mufida da take kwance tana jin su ta mike zaune tace "Mama in kin yarda akwai friends ɗina. Akwai wallahi da yawa da sun sha yi min maganar suna son sa ni kuma ban taba yi mishi magana ba saboda nasan ba kula su zai yi ba. Idan kin yarda sai in bashi pictures din su ya zaba, duk yayan manyan mutane ne, babu kuma wacce iyayen ta ba zasu iya aurar da ita a cikin wata biyu ba"

Ya sake cewa yana kallon Mufida"I don't want to choose" shi a cikin zuciyar sa gani yake yi kamar idan ya zaba yace ya zabi wance kamar yaci amanar Safiyya ne.

Mama ta kalle shi kawai tayi ajjiyar zuciya, bata jin zata daina tsinewa yarinyar nan.

Mufida ta sake cewa "to bara in nuna wa Mama ta zaba maka ita, ta san most of them already, har iyayen su ma ta sani" ta fada tana dauko wayarta. Sai kuma ta tsaya kamar wadda ta tuno wani abu tace "oh my God. Oh my God" Mama da Gidado duk suka juyo suna kallon ta. Gidado ya juya mata hannu alamar tambaya, ta koma ta zauna sosai tace "akwai wata yarinya, kusan shekara guda kenan tana yi min naci akan in haɗa ta da kai" ya bata rai yace "wacece?" Tace "I don't know her. Kawai a one of the northern blogs na Instagram naga ta tura irin hide my ID post din nan da hoton ka, wai tana cigiyar ka ko kuma wanda ya sanka, wai tana son ka. I commented cewa kai yayana ne amma already kana da wadda kake so. She followed me into my DM tana ta yi min nacin in bata ko da number din ka ne ta gwada sa'ar ta, na gaya mata ba zaka kula ta ba taki yarda, I gave her your number dan ta tabbatar da kanta. She later told me ta kira ka baka dauka ba, she sent you a message kace mata tayi hakuri kana da wacce kake so and you blocked her " Gidado yayi shiru yana tunani, ba zai iya gane wacece ba because a lot of that scenario has happened, yammata da yawa sukan gwada sa'ar su a kansa and all the times ya kan basu hakuri and then blocked them dan baya son ciwon kai.

Mufida ta cigaba "tun lokacin bata hakura ba. Har daina daukan wayarta nayi na kuma daina replying messages dinta amma bata daina kira na da kuma turo min sako ba. She even sent me some of her pictures wai in nuna maka. And she is beautiful gaskiya. Daga alama kuma yar manyan mutane ne ce. Let me see it I still have the pictures" ta fada tana bude wayarta

Gidado ya mike tsaye "unknown girl. With no link or connection to the family. She is perfect. Call her and ask her if she is still interested. And if she can get married in the next two months. Then get her information. Duk abinda ta gaya miki sai ki gaya wa Mama" ya juya ya fara tafiya zuwa bangaren sa.

Mama ta daga murya tace "haka kawai kake tunanin zamu aura maka yarinyar da ba'a san asalin ta ba, daga haduwa a social media?" Ya juyo yace "in akayi bincike za'a samo asalin ta. In asalin baiyi muku ba sai Mufida ta samo wata unknown din"

Yana jin ta tana cigaba da magana amma baya fahimtar me take cewa. Tafiya kawai yake yi yana jin zuciyarsa tana breaking into thousand pieces.

****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****.   

Assalamu alaikum masoya littatafan maman Maama, babu abinda zan ce muku sai godiya sai kuma ban hakuri. I have not been doing well with posting Safiyya na sani, and it has gotten worst. A yanzu haka kuma dole in sake baku hakuri dan zan ɗan dakata da rubutun Safiyya saboda abubuwa da yawa da suka sha kaina wadanda ba yadda zan yi da su.

Kuyi hakuri, kuyi hakuri, kuyi hakuri....

Dani da Safiyya da Gidado muna baku hakuri.

We will resume insha Allah as soon as nayi clearing issues ɗin da suke gaba na.

Please ku taya ni addu'a, I really need it because I am faced with one of the toughest challenges dana taba fuskanta so far. Allah ya bani sa'ar abinda yake gaba na a yanzu.

We will see the end of Safiyya together insha Allah.

Wadanda suka fara biyan sponsorship in suna sauri ne suyi min magana for a refund.

Nagode. Ma'assalam
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹Safiyya❤‍🩹*


*By*


*Maman Maama*


*Episode Eight: The Acceptance*


Free Episode


*Her🧕🏻*

Ya dago kai yana kallona da fuskar mamaki, nayi sauri na mayar da nawa idanuwan kasa tare da rike numfashi na dan na san abinda zai biyo baya "Mukhtar?" Ya tambaya cikin mamaki "Mukhtar fa kika ce? Are they blackmailing you? Cewa suka yi in baki aure shi ba zasu gaya wa duniya abinda kika aikata?" Na fara girgiza kaina amma ban ce komai ba, na fahimci dama tunda yana jin zafin uncle Ahmad dole zaiyi retaliating akan zabin nawa duk kuwa da cewa shi ne da kansa ya lissafa min har da Mukhtar din a cikin options dina. Amma ban dauka zai dauki zafi haka ba.

Cikin fada ya sake tambaya ta "baki bani amsa ba, are they threatening you?" Mommy ta shigo da takardu a hannun ta, ta tsaya tana kallon sa sannan ta kalle ni cikin alamar tambaya, ban ce komai ba ta mayar da tambayar ta kansa. Cikin dacin rai ya nuna ni yace "wai Mukhtar. Wai Mukhtar zata aura"

Ta zame ta zauna akan kujera tana dafe kirjin ta "na shiga uku ni Sa'adatu. I thought you hated that guy. You said it yourself several times." A hankali nace "I never hate him, he is my cousin. I just don't love him. Kuma har yanzu bana son sa. Bana masa soyayya irin ta aure amma duk kunsan cewa shi yana so na and at least that is something". Mommy ta nuna waje da hannun ta "and so does Mustapha. In dai soyayya ce Mustapha yafi Mukhtar son ki. Yafi su son mahaifin ki da yanuwanki. Yafi kowa dace wa da auren ki. Da kika ce ba zaki aure shi ba na dauka Abdul zaki aura knowing fully well cewa ba kya son auren Mukhtar. Ashe zaki iya zaben wanda kika ambata xewa ba kya so akan Mustapha? Gwara kikai kanki inda na tabbatar ba son Allah da Annabi suke miki ba akan ki zauna a inda za'a fi ko ina mutunta ki?.........."

Ta cigaba da fada muryarta har shakewa take yi yayin da ni kuma na saka hannayena biyu na toshe kunnuwana tare da rintse ido na. Da bi ar da nake yi a duk sanda ake kokarin chanja min ra'ayi akan abinda na riga na yanke shawara akan sa. Sai da naji na daina jin muryarta sannan na dube ido na ina kallon Daddy shima yana kallo na idonsa cike da mixed emotions. "Wani abun Ahmad ya gaya miki a waya sanda ya kira ki wanda ya saka kika yanke wannan hukuncin?" Ya tambaya muryarsa da sanyi akan dazu.

Na girgiza kaina tare da goge hawayen da bansan sanda na fara zubar da su ba nace "bani da wani zabin ne Daddy. Ba zan iya auren Mustapha ba. Abdul baya sona. Bazan iya auren wanda nake so ba. Bani da zabi Daddy" ya gyara zamansa "waye wanda kike so ɗin? Ki gaya min waye shi ni kuma zan aura miki shi in dai har na bincike shi naga ya chanchanta. Zan aura masa ke kuma in mayar masa da ɗan shi. Waye shi?"

Na mike tsaye "ba ɗan shi bane ba Daddy. Ba ɗan shi bane ba. Ban san waye uban ɗan ciki na ba amma ba nashi bane ba. Ba zan makala masa laifin da nake da tabbas ɗin ba shi ya aikata ba. Ba zan bata tsakanin sa da iyayensa in kuma bata masa suna a gari ba"

Ya dafa kujera ya mike shima, bacin rai yana sake dawowa fuskarsa "kina da shaidar cewa ba shi bane ba kenan? In har ba ki san waye ba zai iya zama shi ɗin ne kenan. Wato da ki bata tsakanin sa da iyayensa gwara ke kin bata da naki iyayen ko? Da ki bata masa suna gwara kin bata naki sunan kin zauna da tabo na har abada a tare da ke, gwara kin auri wanda ba kya so wanda shima kuma ba son Allah da Annabi yake yi miki ba, gwara kin zauna da ɗan da in ya girma ya tambaye ki waye ubansa baki da amsar da zaki bashi ko? Gwara kinyi watsi tare da fatali da duk sacrifices da mahaifiyar ki tayi domin ki, domin ki samu kyakkyawar rayuwa ko? She gave you everything, she gave her very life for you". Ya karasa cikin daga murya.

Nace "but I never ask for it. I never ask for any of this. I wish she didn't do what she did. I wish she let me die"

Na juya da sauri na fita daga dakin ina kuka, ina jiyo muryar sa yana kwalla min kira "Safiyya, come back here" ban waiga ba ballantana in koma.

A waje na samu kujera na zauna na kife kaina ina cigaba da rusa kuka na. Har cikin zuciya ta a lokacin fata nake ina ma dai Ammi bata yi duk abinda tayi ba. Da yanzu ban samu kaina a cikin wannan matsalar ba dan ko shakka babu abinda tayi din shine silar shiga ta halin da nake ciki.

Ina cikin kukan naji an zauna a kusa da ni. Ban dago kai ba thinking wani stranger din ne. Sai da naji an ambaci sunana "Fiyya?" Na dago kai da sauri na kalli side ɗin, duk da kuwa na gane muryar wanda yayi min maganar tun kafin in kalle shi. "Fiyya what happened. Me ya saka ki kuka har haka?" Na saka hannu biyu ina goge fuskata duk kuwa da cewa ba tsayawa hawayen suke yi ba.

"Fada muka yi da Daddy " na fada cikin sheshshekar kuka. Ya gyada kai "yes. Ina tsaye ai kika wuce ni baki ganni ba. Amma Fiyya mai zai kai ki fada da Daddy a halin da yake ciki? A halin da kike ciki? Me ya haɗa ku" ya fada yana miko min hanky. Na karba tare da kokarin tsayar da kuka na. Ya sake cewa "talk to me.... At least let it out of your chest " na girgiza kaina "ba zaka gane ba Abdul" ya gyara zaman sa "Try me. Wata kila zan gane har ma in baki shawara. And just so you know, Mama ta faɗa min komai a kanki. She told me about your situation. She said she wants me to marry you" na juyo ina kallon sa na fahimci da gaske yake abinda ya fada, but I still noticed the sadness in his eyes.

Na danyi murmushin tausayin rayuwata nace "Allah sarki Aunty Hajjo. Lallai ta cika kawai kwarai. Ammi would be very proud of her" yayi ajjiyar zuciya "yeah. I guess so" nace "but I will not marry you Abdul" ya jiyo da mamaki, nace "na riga na yanke shawara, Mukhtar zan aura. Hakan shine sanadin fadan mu da Daddy. And I am not changing my mind. Tunda ai shi ya bani options ɗin kuma na zaba" ya danyi shiru yana tunani sannan yace "but why him? Me yasa kika zabe shi? Why not me?" Nace "I am not sure why. Kawai dai nayi addu'a and naji a raina shi ya kamata in dauka. And personally, na farko I believe yana so na da gaske. Cos ya jima yana ta bina da maganar soyayya ina ƙi, nacin da yake yi min da kuma goyan bayan sa da uncle Ahmad ya fara yi shi ya saka na bar gidan su da zama a Abuja na koma hostel. Shi kuma Daddy ya goya min baya yace ba za'a yi min dole ba. Wannan shine silar fara rikici tsakanin Daddy da uncle. And secondly, ina ganin auren mu zai gyara tsakanin Daddy da dan uwansa. He needs him a yanzu. Su biyu iyayensu suka haifa, bashi da kowa sama da shi" Abdul ya gyada kai cikin fahimta "at least in yana son ki auren will be much easier on you" na ce "yes. And kai kuma abinda yasa ban zabe ka ba shine, akwai wani wanda nake so, shine dalili na biyu da yasa muka yi faɗa da Daddy. I love him so much shima haka. So ina imagining yadda muke dashi idan da ace wannan kaddarar bata fado min ba, ace kawai a gidan su a yanke shawarar cewa ba zai aure ni ba wata yar abokin babansa wadda tayi cikin shege zai aura. It would have destroyed him and me. I don't want destroy you and your girlfriend"

Yayi murmushi, I can see his love for her a idonsa, yace "thank you. I really appreciate what you did. Kin yiwa soyayya halacci. And ina ganin zabin ki shine dai dai. Amma pardon me for asking, ya labarin wancan guy din da kike so ɗin? What happened to him? Ya san halin da kike ciki?" Na yi shiru ina kallon yatsun hannuna, ban so nayi mishi magana akan Muhammad ba dan ko tunawa da Muhammad bana son zuciya ta tayi saboda irin damuwar da nake shiga idan na tuno shi, nace "I can't even imagine halin da yake ciki. Soyayya ta bata yi masa halacci ba. It destroyed him".

Waya ta tayi kara. Na dauko ta daga cikin jaka ga mamaki na sai naga number ɗin Mukhtar. Na kife ta akan cinyata tare da rufe fuskata da hannayena. Na fahimci Daddy ya hakura kenan saboda fushin da yaga nayi, har ya kira uncle Ahmad ya gaya masa zabina shi kuma har ya gaya wa dan na sa. Or not.

Ni na zaba da kaina amma yanzu a raina bana jin zuciya ta zata karbi zabin nawa, da zata so Mukhtar da tini ta so shi. "Ana kiran wayarki" Abdul ya fada yana kallo na. Na bude fuskata tare da daukan wayar na amsa kiran "hello?" Daga daya bangaren aka amsa "Hello Habibty"


*Him👳🏻*


Bai tsaya ba har saida ya shiga dakinsa sannan ya rufe kofa ya jingina bayan sa da jikin kofar tare da rufe idonsa yana jera numfashi kamar wanda yayi gudu. Sai kuma ya bude idon ya fara magana da kansa. "Yes. Wannan shawarar tayi. I will get married and I will forget about her, and fall in love with my wife and have kids like every other person. Babu wani abun da zai chanja. There is nothing special about her. She is just like every other girl".

Ya kwanta akan gado ƙafafuwan sa a kasa yana kallon ceiling, a ran sa yana jera yadda zai cigaba da tsara rayuwar sa step by step. Farko, da farkon fari kafin ya fara komai zai fara da cire Safiyya daga ransa dan in dai har tana yawo a cikin zuciyarsa babu abinda zai iya aikatawa. And to forget about her sai ya fara raba kansa da duk wani abu da yake tuna masa da ita. Ya mike zaune yana karewa dakin kallo, bata taba shiga dakin na sa ba amma kusan a kowanne angle na dakin akwai memory dinta, ko dai wani abu da ta bashi ko kuma abinda suka yi maganar sa ko ta saka ya siya da kansa. Yayi tsaki tare da yanke shawarar cewa dakin zai bari gabaki daya ya koma wani. Nan da two months ma gidan zai bari gabaki daya ya koma nasa gidan shi da matarsa. Sai dai kuma shima wancan gida babu abinda babu memories din Safiyya a ciki.

Ya sake yin wani tsakin. One step at a time. Dole zai manta da ita amma one step at a time, tunda dama ai ba lokaci daya ta shiga rayuwar sa tayi zurfi haka ba. Ya dauko wayarsa ya fara da step din farko. Numbers dinta ya nemo duk yayi blocking sannan yayi deleting. Sai kuma ya nemo dukkan messages dinsu da chats dinsu duk ya haɗa kansu ya goge.

Ya ajiye wayar tare da rufe fuskarsa da hannayensa, a ransa yana jinjinawa kansa. "You can do it" ya fada wa kansa. Ya bude fuskar tare da sake daukan wayar yana jujjuya ta. Tare ya siya musu wayar iri daya shi da ita. Too many memories. Ko dai ya ajiye wayar kawai ya chanja wata? Amma in ya ajiye ma zuciyarsa zata iya rinjayar sa wata rana ya dauko ya kunna ya duba pictures da videos dinta da suke fal a ciki. To completely forget about her dole sai ya goge wadannan ma. Ya bude wayar da sauri ya fara nemo pictures da videos din da duk take ciki yana marking, yayi marking da yawa har yazo kan wani video da bai tabbatar nata be ko ba nata bane ba sai ya bude shi dan ya tabbatar. And then he saw her face, as clear as a lokacin ne yake daukan ta video ɗin. Kuka take yi shabe shabe da hawaye a cikin video ɗin tana bubbuga kafa a kasa irin yadda shagwababbun yara suke yi. Yana jin muryarsa a ciki yana dariya

"wai da gaske kukan kike yi? La ila! Mutane fa suna kallon ki" ta turo baki tare da tabe shi, sak yar yaye, "ni wallahi ba zan daina kukan ba sai ka siya min ice cream".

Ya kife screen din wayar akan gadon tare da kife fuskarsa akan wayar yana jin zuciyarsa kamar zata fado kan gadon. Ya tuna ranar da ya dauki video din. Ranar sun haɗu a school da safe tace masa mura take yi, daya tambaye ta abinda ya saka ta murar sai ta bashi labarin cewa ruwan sama aka yi da assuba ita kuma ta shiga ciki tayi wanka. A ranar da ya kira ta da dare sai yaji muryarta har ta dashe saboda mugun kamu da murar tayi mata. Babu shiri ya dauki mota ya tafi hostel ɗin su ya dauke ta da niyyar kai ta pharmacy ya siya mata maganin mura.


****. ****. ****. ****. ****. ****.


A hanya ya lura da yadda take ta takurewa a cikin hijab dinta. Ya kalle ta yana lura da yadda idonta yayi ja. Yayi tsaki "pharmacy din nan ba zai yi ba Piya, asibiti zamu tafi, naga alamar ma harda zazzaɓi a jikin ki" ta bude ido tare da saurin sakin jikinta. "babu zazzaɓi fa. Allah babu. Mura ce kawai ita ma yar kadan" ta karasa maganar tare da yin atishawa. Ya harare ta "yar kadan? Wannan murar ce yar kaɗan ɗin? Asibiti zan kaiki. Let me call our doctor inji in da yake. Ya kamata a duba ki sosai" ya fada yana daukan wayarsa. Tayi saurin karbe wayar daga hannunsa. "Please kar ka kira shi. Ni na warke ma" yayi slowing down yana kare mata kallo, sai kuma yayi dariya "yanzu na gane matsalar ki. Tsoron allura kike yi" ta tura baki "babu wani tsoron allura, kawai ni lafiya ta kalau ne shi yasa" yayi kokarin juya steering motar "okay tunda ba kya tsoron allura muje asibitin kawai" ta saki wayar tare da saurin rike hannunsa "na shiga uku. Dan Allah kar ka kai ni asibiti" ya cigaba da yi mata dariya yana kallon yadda take zazzare ido kamar wadda za'a yanka "wannan tsoron asibitin naki Piya, duk ranar da zaki haihu bansan yadda za'a yi ba". Sai kuma taji kunyar sa ta rufe ido.

Sun jima suna rigima a mota, daga karshe pharmacy ɗin ma cewa tayi ba zata je ba sai da kyar sannan ta yarda amma da sharadin cewa ba zata shiga ba shi kadai zai shiga ya karbo mata magani ya fito. Haka da suka je ya barta a mota ya shiga shi kadai, sai dai ga mamakin sa ya na tsaye a gurin cashier sai ganin ta yayi ta shigo gurin ta shiga bangaren da suke siyar da kayan ciye ciye, jimawa kadan sai gata da manyan robobin ice cream guda biyu, ta ajiye a gaban cashier tana kallon sa tace "one for you and one for me" ya girgiza kansa "no, no, no. Babu yadda za'a yi kina wannan murar ki sha ice cream. I won't allow it ".

Ta kwabe fuska "ni Allah sai na sha. Ai naji wani doctor yace ba shan abu mai sanyi ne yake kawo mura ba, mura viral infection ce, kuma ......" Yace "oh! Viral infection? Shi yasa naga kin shiga ruwan sama kin fara mura? Ko virus ɗin a cikin ruwan saman yake?" Ya karasa maganar yana daukan robobin da niyyar mayarwa. Ta bishi da sauri "ni dai kazo ka siya min. Allah in baka siya ba ba zan fita daga shagon nan ba zama zan yi in yi ta kuka" ya juyo yana kallon ta da mamaki. "kuka? Really? To kiyi ɗin mu gani. Ni kuma I will record you and show our kids"

Ai kuwa ranar yaga rigima. Tun da ya hadu da ita dama ya fahimci shagwababbiya ce amma bai san irin girman shagwabar tata ba sai ranar. A dole sai da ya sai ice cream din nan har da karin chocolates, mai shagon yana ta yi musu dariya. Suna shiga mota ta darko roba daya ta buɗe ta fara sha. Ya zauna kawai yana binta da kallo. Tayi atishawa ta kara diban wani ice cream din ta sha. Ta juyo tayi masa gwalo. Yayi ajjiyar zuciya. "This has to change. My no has to mean no and my yes yes. Dole ki ringa jin magana ta in nayi miki ita" ta juyo tare da saluting dinsa irin yadda sojoji suke yi tace "Yes Sir!".


****. ****. ****. ****. ****. ***


"Hamma. Hamma Gidado. Yaya Gidado".

Kamar cikin mafarki yaji muryar Mufida tana kiran sunan sa, duk kuwa da yasan cewa ba bacci yake yi ba sai dai yayi matukar nisa a cikin tunanin sa. Ya dago fuskarsa ya sauke jajayen idanun sa akan Mufida da take tsaye a bakin kofar dakinsa da waya a hannun ta. Ta dan tsorata kadan sai kuma yaga tayi sauri ta rufe mic din wayar hannunta da daya hannun, tace "uhm dama waya ce aka ce in kawo maka. Amma bara in ce mata kawai you are busy zaka kira ta an jima" ya tashi ya zauna sosai ya a shafa goshin sa yace "who is it?" Tace "yarinyar da muka yi maganar ta dazu ce. Mama tace in kira ta dan a samu information ɗin ta. Shine na kira ta ita kuma tace in kawo maka" ya sauke ajiyar zuciya, with all his heart yana son yayi rejecting kiran ya fadi wani excuse ɗin amma kuma yasan bashi da wani excuse ɗin fadi. Ya san shi yayi choosing wannan option ɗin amma accepting ɗin choice din nasa yana kokarin ya zamar masa nightmare.

Ya mika mata hannu. "Give me the phone " ta bude mic din sannan ta mika masa. Yana karba ta juya ta fita. Ya zauna yana kallon timer din kiran tana cigaba da reading, sai da yayi ajjiyar zuciya sannan ya saka ta a kunnen sa, "Assalamu alaikum " yace, daga daya barin yaji ance "Ameen wa alaikumus salam Habibi" yayi shiru bai ce komai ba, sai ta sake cewa "Mufida ce ta kira ni. She told me the most wonderful news ever. Ina so ka sani cewa tunda nake a rayuwata ba'a taba gaya min labari mai daɗin wannan ba" ya sake yin shiru sai kuma ya fahimci shi take jira yayi magana sai yace "okay. I am glad you feel that way. But uhmm, this is just a procedure, I don't want to give you any false hope. Maganar aure ce and dole sai an gudanar da bincike. Am sure she told you abin yazo ne lokaci daya. I have been giving two months in fito da mata. So I am going to need some information from you and if the background check comes back okay then that's when we will celebrate" ta dan yi dariya kadan "it is going to come out okay. Everything will insha Allah be okay. And I am going to make you the happiest insha Allah. And ." Ya katse ta "Okay. Uhmm. First, menene sunan ki? Ni sunana Muhammad Lawan Muhammad. Ana ce min Gidado" tace "I know. I know a lot about you. Ni sunana Safina. Safina Ibrahim"
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹 Safiyya*❤‍🩹


By


*Maman Maama*


*Episode Nine: Safina*


Free Episode

*Him 👳🏻*

"Safina?" Ya maimaita da mamaki a muryarsa, ta ɗan yi shiru sannan tace "eh. Uhmm, ko ka san wata Safina Ibrahim ne?" Sai daya ɗan ajiye wayar akan cinyar sa ya yi tsakin jin haushin kansa, why must he relate everything to Safiyya ne wai? Kawai daga jin Safina sai ya dangantata da yar uwar Safiyya?

Ya sake daukan wayar yace "uhm. Sorry Please. Akwai wata Safina da na sani ne, in fact ita ce the only Safina dana sani. Though ita ma sunan ta kawai na sani. Yar uwarta ce wacce na sani" ya kuma ajiye wayar tare da dafe kansa "damn it. Must I talk about her?"

Ya sake daukan wayar sai kuma yayi shiru gudun kar ya cigaba da maganar Safiyya. Tace "hello? Ina jin ka. I guess you know the sister very well ko? I want to know. Tell me" yace "there is nothing to tell. Just tell me about your self, like, yar wanbe gari ce ke? Kano?" Sai kuma ya sake jin haushin kansa.

Tace "noo, not Kano. Ni yar Katsina ce" yace "really? But hausarki doesn't sound like hausar yan Katsina" ta danyi dariya "I get that a lot from people that don't know me. Bana son dialect ɗin so ina kokarin cire shi, musamman saboda duk makarantu na ba anan na yi su ba" yace "okay. Uhmm, I think that's all I need from you now. Please ki bawa Mufida number ɗin wani haka da za'a yi magana da shi, like your uncle or something. My family will contact them and do all the necessary stuff. That's all for now"

Tace "all? I thought zaka ce zaka zo muga juna ko?" Ya girgiza kai "no. My family will meet yours and do all the necessary things. I will see you idan komai ya daidaita. But now I am very busy" ya ji bacin rai a muryar ta "amma idan da zaka zo ɗin zanji dadi sosai, you have no idea how much I waiting and prayed for this. And ko suma su Abba zasu fi bawa abin muhimmanci idan suka ga kazo gurina" yace "no, zasu fi bada muhimmanci idan suka ga elders dina sun zo gurin so. I am sorry but I cannot come" tace "okay. Then how are we suppose to know and understand each other?" Yace "I will call you when I need more informations" tace "how can you call me bayan baka da number ta?" Yace "ki karbi tawa a hannun Mufida ki kira ni" tace "how can I call you bayan kayi blocking number ta " ya rufe idonsa yana jin kansa yana sarawa yace "okay. I will collect your number and unblock you. Shikenan?" Tayi murmushin da yaji sautinsa a cikin wayar "shikenan, naji dadi sosai. You have......"

Ya katse kiran ya jefar da wayar akan gadon tare da dafe goshin sa da hannu biyu. Zuciyar sa tafasa take yi, kokari take sai ta lissafo masa aibun yarinyar da suka gama waya da ita. Safina she said. But why? Upon all the names na mata a duniya why did she have to be Safina, bayan kuma Safinan ba wani suna ne irin wanda ya cika gari sosai ba. Yana ta so ya goge duk wani abinda zai ke tuna masa da Safiyya and then all of a sudden yarinyar da yace zai aura tana da sunan step sister din Safiyya. Safiyya used to talked a lot about her, ta kan ce "she is more like a sister to me, tare muka taso, a daki daya, a hannun uwa daya da uba daya".

Lokuta da dama ya kanji su suna waya, and daga yadda suke hira suna dariya ya fahimci akwai shakuwa da kaunar juna  sosai a tsakanin su.

Ya mike tsaye tare da daukan wayar ya fita. A parlor ya tarar da Mufida da Mama suna zaune suna hira, ya ajiye wa Mufida wayar a gabanta yace "ki samo wata. Na fasa wannan ɗin" Mama ta mike tsaye tana kallon sa amma sai ya dauke kai yayi hanyar fita, ta riko hannun sa ya dawo baya, tace "kai Muhammadu, dago kai ka kalle ni" ya kasa kallon nata amma sai ya samu guri ya zauna a gabanta "akan menene kace ka fasa" yayi shiru yana jujjuya kai still idonsa a kasa. Ta kara karfin muryarta "a bayanan da ta baka ne wani abu bai yi maka ba? Ko wata magana mummuna ta gaya maka wadda za'a iya fasa aure saboda ita?" Ya dago kai "Maaama! Ke ma fa ba sanin yarinyar nan kika yi ba kamar yadda ni ma ban santa ba. It wouldn't hurt anyone idan aka ce an fasa ɗin tunda dama ko maganar ba'a fara ba" ta koma ta zauna tace "I don't care much about her Gidado, in fact she lost some things a gurina tunda har ta iya fitowa social media tana neman namiji. But still that earned her something saboda hakan ya nuna tabbas tana son ka. And I do care about you a lot. I don't like hanyar da rayuwar ka take dauka akan mace. Now tell me, me yasa kace ka fasa auren ta?" Sai da ya dan yi jim sannan yace "sunan ta Safina" Mama tace "and?" Yace "sunan yar uwar Safiyya ne"

Sai da ya fadi maganar sannan ya fahimci wautar da yayi, bai kalle ta ba amma a jikinsa yana jin mugun kallon da take bin sa da shi. Yayi shiru yana jiran yaji ta rufe shi da fada amma sai kuma yaji ta sake tambayar sa "Okay, ka tambaye ta kenan ta kuma tabbatar maka da cewa ita ɗin ce?" Ya girgiza kai "ba ita ba ce ba. Ita wannan yar Katsina ce su kuma yan Kano ne". Ya cigaba da jiran fada, amma sai yaji tayi ajjiyar zuciya tace "Gidado, Allah ya kwato min kai a hannun waccan matar. Allah kuma ya saka min abinda tayi min. Tashi kaje tun kafin kasa zuciya ta ta buga. Ba za'a fasa ɗin ba. In an samo wata kuma cewa zaka yi a cikin yan uwanta akwai mai suna Safiyya. Ko in anyi auren kazo kace kai ka fasa saboda suna da makociya Safiyya. Allah ya shirye ka".

Ya mike ya fita, feeling silly. Ita Mama ba zata gane ba, shi a ganinsa wannan is enough reason to call the wedding off, dan shi duk abinda zai ke tuna masa da Safiyya gudun sa yake yi, shi kadai yasan abinda yake ji a ran sa.

Sai after two days sannan ya karbi number ɗin daga gurin Mufida, shima Mufidan ce ta dame shi da maganar cewa Safina tana tayi mata maganar, da ya karbi number ɗin ma bai kira ba har sai bayan wasu kwana biyun da Mama ta yi masa magana "idan baka kira yarinyar nan ba wai ta yaya zaku samu fahimtar juna ne? Musamman considering baku da isasshen lokaci? Idan kuma da gaske ba zaka auren ta ba dan sunan yar uwar waccan mayaudariyar ne da ita to sai ka fada mana muji in yaso mu nemo maka wata a dangi, in ma kuma auren ne ba zaka yi ba gabaki daya shima sai ka fada musan cewa bamu isa mu saka ka ba".

Da suka zo dinner da daddare ma sai da Abba yayi masa maganar" ka kira yarinyar can kuwa? Ya kuke ciki? Yaushe zaka je ka ganta?" Ya juya yana kallon Mama wacce ta tabe baki bata ce komai ba. Ya sunkuyar da kansa yace "zanje Abba, ina dan so in samu lokaci ne" Abba yace "lokaci? Lokaci kuwa ai shine babban abinda baka dashi. Shekara nawa muka baka? You have only two months my friend, ko ka je ku daidaita da wannan ɗin ko kuma wallahi kaji na rantse sai ranar daurin auren ka zaka san dawa aka daura. Stupid"

Ya cigaba da jujjuya cokali a cikin abincin, sama sama yana jin Abba suna cigaba da maganar da Mama, tana gaya masa cewa yarinyar ta turo number din uncle dinta, Abba kuma yana nuna cewa ba za'a yi contacting dinsu ba har sai sun tabbatar cewa Gidado is fully committed dan kar suje suyi magana biyu.

Gidado ya mike tsaye, Mufida ta rike hannunsa "hamma ba ka ci abincin ba" muryarta cike da damuwa, murya can ciki yace "am not hungry" sannan ya wuce ciki. Dakinsa ya shige zauna a kan kujera, staring into nothing, babu abinda yake gani idan ya rufe idonsa sai hoton Safiyya da ciki, cikin wani, waye wanin amma? Waye mijin Safiyya. Ya tuno da maganar da Mama ta fada sanda ya gaya musu cewa Safiyya tana da aure, she said wanda Safiyya take cewa Daddyn ta ne, wanda take zuwa kasar waje gurin sa, shine mijinta.

Ya san pictures din Daddy, tabbas ya haife ta ko ma wadda ta fita, amma kuma yana da kuɗi, yana da bala'in kuɗi, yammata kuma a wannan zamanin sukan auri sa'an kakansu ma saboda kuɗi. But Safiyya doesn't look like a gold digger, she never sounds like a gold digger. He just couldn't picture her and that man as husband and wife.

Yayi kokarin kawar da tunanin daga ransa dan gudun illata zuciyarsa. Ya fara mayar da tunanin kan issue at hand, issue ɗin wannan yarinyar Safina. He regretted cewa ya zabe ta. Bai san dalili ba but he just doesn't like her tun kafin ya ganta, kuma in zai gaya wa kansa gaskiya ya san aibunta kawai shine dan sunanta Safina, which is not fair to her. She couldn't possibly be Safinar Safiyya, like is not that cruel is it?

Ya tashi ya koma kan study table dinsa ya bude laptop dinsa, in da akwai inda zai samu aibun yarinyar to tabbas a social media ne, anan zai samu abinda zai nuna wa iyayen sa yadda zasu yarda a fasa auren ba tare da sun jingina fasawar da Safiyya ba. Ya bude goggle sannan ya tsaya yana tuno sunan da ta gaya masa "Safina Ibrahim" amma da ya fara typing sunan sai ya samu kansa da typing "Safiyya Adam Muhammad" "damn it" ya faɗa a fili, subconsciously yana son yin bincike ne akan Safiyya.

He saw a lot of results da basu da dangantaka da Safiyyan da yake nema, he saw her Instagram account with the few posts she made most of which na abinci ne. Yayi murmushi "acici" sai kuma yayi sauri ya fita ya cigaba da binciken sa amma bai ga wani abu da zai yi linking dinta da aure ba ko kuma ya yi directing dinsa to mijinta. Ya koma search engine din sannan yayi typing "Alhaji Adam Muhammad" a cikin results din ya ga wanda yake nema, ya gane hotonsa from the pictures dinsa da yake gani a wayar Safiyya. Anan yaga biography dinsa da aka yi publishing, ya shiga idanunsa suna searching abinda ya ke nema, anyi rubutun ne akan a lot of achievements dinsa da irin tarin arzikin da yake da shi da kamfanonin da ya mallaka, he was even listed a cikin manyan masu kuɗin Nigeria. Yayi ta wucewa har yazo kan abinda yake nema, a cikin biography ɗin nasa anyi listing spouses dinsa, sunan farko shine "Safiya" sai kuma "Sa'adatu".

Ya kife fuskar laptop din da karfin da shi kansa ya san ta lalace. Ya mike sannan yayi jifa da kujerar da yake kai a zaune. Sai kuma ya zauna akan gado tare da rintse idanunsa. "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ya furta a hankali. How much more pain does he have to endure. How much more pain can his heart take. When will this end?

Ya koma da baya ya kwanta yana kallon sama. Ba san me zai yi tunani ba, bai san me zaiyi ba, bai kuma san tsahon lokacin da ya dauka a haka ba. Daga baya ya koma ya zauna sannan ya jawo wayarsa ya bude number ɗin Safina sannan ya kira. Ba'a jima ba aka dauka "alhamdulillah. Allah shine abin godiya. Tunda nayi sallah nake zaune akan sallaya ina gaya wa Allah bukatu na akan ka. Gashi kuma ban tashi ba sai da Allah ya amsa min ya juyo min da hankalinka gare ni".

Yace "listen Safina. If we are going to do this, then we are going to do it the right way. I am really heartbroken right now. I am in love, deeply in love with someone else, someone that I cannot have. Wannan ne dalilin da yasa aka matsa min akan auren nan. Bana son shiga hakkin duk wacce zan aura, so I want you to know what you are getting yourself into. Babu rufa rufa. I will marry you saboda ina son in farantawa iyayena rai, but chances are I might never love you, or anyone else. Me kika ce? Kin amince?"

Sai da tayi shiru na wasu lokuta, daga dukkan alamu maganar ta sa ta dake ta sosai. Sannan tace "I don't know what tomorrow will present to us. Babu wanda ya san gobe. Yanzu na sani, abinda na sani a yanzu kuma shine ina son ka, ina matukar son ka. Na kuma san cewa in na aure ka zan baka dukkanin kulawar da miji yake bukata daga gurin matarsa. Na kuma san cewa ita zuciya an halicce ta ne a bisa son mai kyautata mata, so chances are high that you will love me. Maybe one day in ka tuna da waccan har sai kaji haushin kan ka ma kana tunanin what made you love her. So yes, I am going to take my chances. Na amince, a bisa alkawari guda daya, cewa you will try your best akan sauke dukkan nauyin da addini zai gindaya a tsakanin mu. Kuma ba zaka wulakanta ko goranta min soyayya ta ba".

A cikin sati biyu aka gama bincike, kuma a iyakacin abinda aka samu babu wani abu da zai hana aure a musulunci. An gano asalin ta, an kuma yi bincike akan tarbiyyar ta. Daga nan uncles din Gidado, Uncle Habib, Faruk da kuma mijin aunty dinsa Maimunatu suka je har Katsina suka nema masa aurenta, a take kuma kanin mahaifin ta ya basu auren ta. Aka saka rana sati shida yadda zai zo dai dai dana Mufida kamar yadda iyayen angon suka nema. Daga nan kuma sai aka cigaba da gudanar da shirye shirye a duk bangarorin biyu.

****.     ****.    ****.    ****.    ****     ****

*Her🧕🏻*

Sama sama muka yi magana da Mukhtar, nayi kuma iyakacin kokari na na ganin cewa banyi masa wulakanci ba tunda yanzu ni ce da kaina na neme shi, sai dai kuma na katse maganar da cewa akwai abinda nake yi amma zan kira shi idan na gama. Na mike ba tare da na kalli Abdul ba nace "zan shiga ciki, thank you for...... For listening" ya mike shima "amma da zaki ji shawara ta kar ki koma ciki yanzu, ki dan basu space ki bari su huce tukunna. Ke ma ki huce" na tsaya amma ban ce komai ba, ya mike shima "let me take you home" na juyo "ba gidan ku zamu koma ba, mun samu gurin zama for the time being" yace "I know, amma zaku dauko kayan ku daga gidan na mu ai ko? Let me take you there sai ki debo muku kayan ku".

Ban cigaba da musu ba saboda nima bana son komawa gurin Mommy da Daddy a lokacin. Muka shiga motar sa muna tafiya a hankali na jingina kaina a jikin window tare da rufe idona, hoping ina ma dai mutum yana iya hana kansa tunani? Na jima a haka sannan naji yace "Fiyya. Wata tambaya nake son yi miki. Ban san yadda zaki dauke ta ba. Please kar ki ji haushi bana nufin komai sai alkhairi. I will only ask the question dan naga yau mun samu fahimtar juna. You can choose not to answer it if you will" na dago kaina tare da bude ido nace "ina jin ka" kamar ba zai yi magana ba sai kuma yace "akan wannan da kika gaya min kina so, shine baban babyn ki?"

Nayi sauri na kalle shi. Ya daga hannu "am sorry. In ba kya son amsawa forget I ever asked it" na juya kaina na cigaba da kallon gefe, sai da na jima a haka sannan nace "ba nashi ba ne ba. But kasan wani abu? Sometimes in akayi min irin wannan tambayar I wish cewa nashi ɗin ne. It would have made everything easier for both of us. Da sai dai Daddy yayi fadan shi ya gama, maybe ma ranshi ba zai kai yanzu baci ba, shima nashi iyayen in suka ji ransu ya baci suyi fada, but duk kan su ba zasu iya disowning din mu ba saboda suna son mu, at the end zasu nema mana mafita ne, which would be to get us married, muyi aure mu rike babyn mu, and live happily ever after. The end".

Ban jima a gidan Aunty Hajjo ba na gama hada mana kayan mu, tare muka tafi da ita zuwa gidan da Daddy ya kama mana muka danyi gyare gyare kafin su Daddy su zo. Ita ta kira Mommy ta gaya mata muna tare. Da furnitures da komai a gidan dan haka kayan sakawar mu kadai muka shiga dashi, sai yan few abubuwan da naga babu nayi mana order za'a kawo mana har gida.

Tunda su Daddy suka zo daga shi har Mommy babu wanda ya kula ni, Mustapha ne ya kai shi dakin da aka shirya domin shi sannan ya shirya masa kayan sa da duk abubuwan bukatar sa. Ni dai da naga na gama abinda zan yi kuma babu wanda yake yi min magana sai na wuce na tafi dakin da yake a matsayin nawa nayi kwanciya ta.

Sai dare sannan Mommy ta shigo. "Ki tashi ki ci abinci" tace min. Na mike zaune kawai bance komai ba, sai ta zauna a bakin gadon tana kallo na tace "Safiyya wannan ita ce magana ta karshe da zanyi miki a kan auren ki. Duk da cewa yanzun ma ba wai zanyi miki maganar bane ba dan ina saka ran zaki chanja ra'ayin ki ba, zanyi ne kawai dan in nuna miki irin yadda rai na ya baci akan maganar. Ba kiyi halacci ba Safiyya, daga ke har mahaifinki ba kuyi min halacci ba wallahi. Ai na san kin san komai, duk da dai ni ban taba zama na gaya miki ba dan bana son ki dauki maganar kamar gori amma na san duniya ta gaya miki, kin san irin halaccin da nayi wa Safiya, ni na dauke ta a matsayin yar aiki sannan na mayar da ita mutum, duk abinda Safiya ta zama a rayuwar ta wallahi ni ce sila. Haka kema kuma, tun kina zanin goyon ki na dauke ki na rike tamkar nina haife ki amma yanzu ni ce abin gudu a gurin ki. Shi kuma mahaifin ki ya goya miki baya as always. Babatun sa da fadansa na banza ne in dai a kanki ne baya iya juya ki sai abinda kike so shi kikeyi. Ba'a saka ki ba'a hana ki. Kuma kowa ya dan dalilin da yasa kika samu kanki a halin da kike ciki kenan. Amma har yanzu bai dauki darasi ba. Da wasu iyayen ne ma har wanni zaɓi za'a baki? Bayan abinda kika aikata kuma ace sai an baki zabin mijin da zaki aura? Da wasu iyayen ne da tuni baki fadi uban shegen cikin ki ba? Kuma na san abinda zakuyi nan gaba, tunanin ku yanzu shine in an haifi shegen a dauko shi a kawo min ace in rike shi saboda ni ce karkatacciyar kuka mai daɗin hawa ko?. To wallahi kar ku sake ku doso ni da shi ma. Na fada miki wannan ne dan ki sani, zan cigaba da sauke nauyin ku da Allah ya dora min daga ke har mahaifin ki amma na daina going extra for any of you. Na daina saka bukatun ki a saman na ƴaƴan da na haifa da cikina. Tunda kun tabbatar min da cewa bani na haife ki ba. Kun tabbatar min da matsayina na matar uba kuma na dauki matsayin nawa".

Har ta gama bance komai ba, tana gamawa ta mike ta bar dakin ni ma kuma na koma na kwanta na cigaba da kallon ceiling. Shin da gaske na yiwa Mommy butulci?

Haka rayuwa ta cigaba da tafiyar min, har tsahon sati uku, Mommy ta janye jikinta sosai daga gare ni haka Mustapha ko magana baya yi min, nima kuma dama ba so nake yayi min maganar ba, Daddy ma kamar ko da yaushe sama sama yake min magana in dai har munyi doguwar magana to faɗa ne. Kullum dakina ne gurin zama na akan sallaya ta, anan nake sallah ta, anan nake kuka na, anan kuma nake bacci na. Na cigaba da zuwa asibiti ganin likita, na tabbatar masa da ra'ayi na na bayar da ɗan cikina for a closed adoption idan na haife shi.

A ranar da muka cika sati uku a gidan ne bayan na tashi da safe na fita da niyyar gaishe da Daddy da Mommy kamar yadda na saba kullum, ina fita parlor sai naga Daddy shi kadai a zaune akan electric wheelchair dinsa da kofin tea a hannunsa. Na karasa na gaishe shi ina lura da bacin ran da yake bayyane a fuskarsa, a raina har na fara lissafin ko nayi wani sabon laifin ne. Amma sai naji bai yi min faɗa ba bayan amsa gaisuwa ta da yayi. Na mike ina dube dube. Na shiga kitchen na fito na kuma shiga dakin su Daddy na fito amma ban ga Mommy ba. Daddy naji yace "she is gone" na juyo ina kallon sa. "Gone? Gone where?" Yana kallona shima yace "home. Sun tafi Nigeria ita da Mustapha. Wai auren Safina za'a yi. Safina ce wai aka bayar da ita ba tare da ko faɗa min anyi ba. Suka shirya tafiyar su ba tare da sun gaya min ba. Sai da safe kawai suka fito da akwati wai Nigeria zasu tafi bikin Safina. She said wai na nuna mata cewa ke ba yar ta bace ba shi yasa ita ma ta nuna min cewa Safina ba yata ba ce ba".

Not edited. Forgive the typos please.
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹 Safiyya ❤‍🩹*


*By*


*Maman Maama*


*Episode Ten: Soul Mates*


Free Episode

Na zame na zauna akan kujera cikin mamaki "aure Daddy? Safina ce zata yi aure amma ni ban sani ba? How? Why? To wa zata aura ma?"

Yace "ba ta gaya miki ba kema? Kuna magana kuma?" Na gyada kai. Na san mun dan samu falling out da Safina kwanan bayan nan, and must issue din mu na san laifi na ne saboda yadda na zama very rude to her a watannin nan, hakan kuma yan ada dangantaka da mood dina da kullum bashi da kyau. Amma ban dauka har zata iya yin aure ba tare da na sani ba. And ko shekaran jiya munyi chats da ita. We even talked about magana ta da Mukhtar.

Nace "muna magana Daddy, amma ko alama bata nuna min ba. Wa zata aura kuma?" Ya girgiza kai "ban sani ba, they didn't tell me and I didn't ask tunda sun nuna ban isa ba. Ba ki san samarin ta ba?" Na yi shiru ina tunani "Safina bata da saurayi. Ni dai ban san wani saurayi da take kulawa ba" na tuno da yadda takan takan yi min kallon zautacciya duk sanda muke tare in taji muna waya da Gidado. Tace soyayya irritating dinta take yi.

"How can she do that?" Na fada a fili. Daddy yace " ba laifin ta bane ba. Am sure Sa'adatu ce zata hana ta fada dan tana so ta bata min rai, tana so ta nuna min nata ikon" nayi ajjiyar zuciya "babu komai Daddy kar ranka ya baci, we don't need them. We can do this alone. Su je suyi mata aure, Allah ya sanya alkhairi. All we have to do now is hire someone, kamar a nurse haka that can take care of you, sai kuma mu nemi a house keeper da zata ke shigowa ko da twice a week ne tana kula da gidan, and I can drive, duk inda zamuje zan iya kai mu" yayi shiru yana kallo na da murmushi a fuskarsa, sai kuma ya girgiza kai "Safiyya kenan. Kin dauka damuwa ta kenan? Wanda zai kula da ni? Damuwa ta shine wanda zai kula da ke idan babu ni. I don't want any enmity between you and them saboda ko babu dangantaka ta jini su yan'uwanki ne, ba na son in babu ni ki rasa wanda zaki yi turning to. Ke ba yanuwan uwa ne da ke ba, and in akayi auren ki da Mukhtar yan uwans sun zama na mijin ki, ke ba older siblings ne da ke ba. In na mutu ya zaki yi?"

Na koma na zauna ina jin wani kadaici yana lullube ni. Tamkar Ni kadai ce a duniya. Ya cigaba "shi yasa da farko naso auren ki da Mustapha, at least it will strengthen the bond between you kuma ba zasu yi spilling secrets dinki ba. And you will still have Ahmad a matsayin uba ba matsayin uban miji ba, zai kuma saka ido ya ga cewa basu cuce ki ba. But now, now I don't know what to do sai dai addu'ar Allah ya kara ara min lokaci"

Na gyara zama "amma Daddy ba ka ganin wannan tafiyar da suka yi suka barmu ta nuna true intentions ɗin su? Ta nuna cewa ba soyayyar Allah da Annabi suke yi mana ba?" Yace "Allah kadai ya san abinda yake ran bayin sa. I don't know abinda ke ran Mustapha, amma na san Sa'adatu is not cruel, stupid but not cruel, she is just scared that she will loose everything" nayi kokarin gane maganar amma ban fahimta ba sai na chanja magana "I still have the twins" yayi murmushi "yes, and they are the more reasons why dole in gyara tsakanin ku kafin in bar duniya, if not, you will loose them too, dan babu yadda za'a yi su juya wa uwarsu baya saboda ke".

Daga nan na tashi na shiga kitchen na hada wa kaina smoothie na zauna ina sha ina jimamin abinda ya faru, har lokacin na kasa yarda wai da gaske Safina ce zata yi aure amma wai daga ni har Daddy bamu sani ba, kuma naji a raina babu abinda nake son sani irin wanda zata aura ɗin, waye shi? Yaushe suka hadu? A ina suka haɗu? Nayi kokarin mantawa da abin in fuskanci abinda yake gaba na amma sai naji na kasa. Na koma daki na dauko waya ta na kira Hassan, dole ai na san twins zasu sani musamman tunda suna Nigeria. Hussein ne ya sauka da murna a muryarsa ya gaishe ni "yaya da ke za'a taho? Kun fasa zama acan din? Mun dauka ai cewa kuka yi sai kin haihu zaku dawo Nigeria" nace "no Hussein ba dani za'a taho ba, kun yi waya da Mommy kenan?" Yace "eh dazu ta kira mu tace gasu nan zasu taso. I thought gaba daya zaku taho ai" nace "a'a, ita da Mustapha ne ka dai, ni da Daddy muna nan" naji chanji a muryarsa "but why? Me yasa zasu taho su barku ku kadai? Gashi Daddy babu lafiya ke ma kuma haka?" Nace "Mommy tace bikin Safina za'a yi. Kun sani?" "Bikin yaya Safina?" Ya mayar min da tambaya ta, nayi ajjiyar zuciya, basu sani ba suma, ya sake tambaya "wa zata aura?" "I don't know Hussein. Actually abinda na kira ku in tambaya kenan, daga ni har Daddy bamu san komai akan auren ba, and it hurts ne that bamu sani ɗin ba" ina jin sa yana magana da Hassan a kusa da shi, sai Hassan ɗin ya karba ransa a bace "but this is not right. Kawai tace mana zata je Katsina tun last two weeks kuma har yanzu bata dawo ba. She didn't tell us anything" nace "babu komai. In sun karaso kwa tambaye su details din sai muji" ya cigaba da fada sai na kashe wayar dan nasan idan ya fara ba dainawa zai yi, shima yayo gadon zuciya irin ta su Daddy.

Daga nan kuma sai na mayar da hankali na gurin sama mana solution ni da Daddy, na kira Abdul na nemi taimakon sa na gaya masa abinda nake bukata, ina son a samo wa Daddy nurse namiji da zai ke taimaka masa with his day to day activities, sannan kuma da house keeper macw da zata ke shigowa two times a week tana gyara gidan, ni zan iya girki da dan sauran kananan aiyuka. Shima yayi mamaki da yaji cewa su Mommy sun koma Nigeria. Zuwa yamma sai gashi nan shi da Uncle Lukman sunzo, suka zauna a gurin Daddy har dare sannan uncle Lukman ya tafi ya bar Abdul ya kwana da Daddy, sai da safe sannan nurse din da aka yi hiring yazo.

Aunty Hajjo ta kira ni tace in koma gurinta amma sai na nuna mata nafi son zama anan tare da Daddy, ina son inyi spending as much time as I can with him. Kuma naji daɗin days that follows dan na samu ina dan motsa jikina wajen zirga zirgar kula da bukatun mahaifina, abinci sai inyi masa kala biyar a rana, mu kan ci tare sometimes, in kuma yan fadan sunzo ya balbaleni da fada sai in tashi in shiga daki, daga baya sai na fahimci ganin cikin jikina ne yake triggering fadan sa, sai na koma yin iyakaci kokari na wajen ganin na saka kayan da zasu boye cikin.

Kwana hudu da tafiyar su Mommy Safina ta kira ni. Ni tunda su Mommy suka tafi ban kuma yi mata magana ba ko a chats ita ma haka. Ranar sai ga kiran ta. Kamar ba zan dauka ba dan in kara nuna mata bacin raina amma kuma curiosity ya saka na dauka. "Kinyi fushi ko kanwata?" Nace "ohh dama kina da kanwa a duniya? I thought yan Katsina ne kawai yan uwanki" tayi dariya "wallahi ba laifi na bane ba, Mommy tace kar in gaya miki dan kar ki gaya wa Daddy, tana fushi dan yaki yarda da auren ku da yaya Mustapha. Sai yanzu nace mata ni dai zan miki magana, tsakanin su daban tsakanin mu daban" cikin bacin rai nace "but how can you do that Safina. Ni ban damu da rashin gaya min da baki yi ba amma Daddy fa? Daddy fa Safina. Ace wai ba za'a gaya masa maganar auren ki ba?" Tace "na gaya miki ba laifi na bane ba" nace "but you can convince her otherwise, ko kuma kibi ta wata hanyar da za'a sanar da shi" tace "what do you want me to do? Yanzu sai kawai in kira Daddy in ce masa anzo neman aurena an saka rana?" Na girgiza kai "a gani na Daddy yafi karfin haka a gurin ki, a tunani na duk wanda zaki aura gurin Daddy zai zo ya nemi auren ki sai ya amince sannan shi zai kai shi gidan ku na Katsina" tace "to yanzu dai an riga an yi an gama. Ni dai ke zaki taya ni bawa Daddy hakuri dan Allah. Nasan in yayi fushin sa ke kadai kike sauko da shi" nace "ni ba zan shiga cikin wannan maganar ba, nima lallabawa nake yi dan laifuka na sun fi na kowa yawa a gurin Daddy".

Daga baya dana tambaye ta game da wanda zata aura sai ta bani labarin cewa a waya suka haɗu, kawai friend request ya turo mata tayi accepting shikenan cikin kankanin lokaci suka fara soyayya, ashe dama a gidan su kuma an fara matsa masa ya fitar da mata, shine ya fitar da ita. Nayi mata murna tace "I can't wait for you to meet him. I am sure you will like him".

Bayan mun gama wayar da ita na tashi na shiga wanka, bayan na fito sai na samu kaina da tsayawa a gaban mirror ina kallon kaina ina tunanin yaushe rabon da in kalli kaina a madubi? Zan iya cewa ma ni har na manta da kamanni na. Na lura da yadda nayi baki na rame sosai idunwana suka faɗa ciki, duk glow din fata ta yayi diminishing. Ga uban ciki na da sai kara girma yake yi abinsa. Na dora hannu akan cikin ina kallonsa a madubi, Allah ne kadai ya san irin azabar da cikin nan ya bani tun daga samun sa har zuwa wannan lokacin, laulayi babu irin wanda ban sha ba, ciwo babu irin wanda banyi ba, azaba ta duniya kam na ganta akan cikin nan. Na tuna da Fiyyan da da irin gatan ta da irin shagwabar ta, na hango ina ma ace da aure na samu wannan cikin, da auren Muhammad. Na lissafo irin shagwabar da zan zuba masa ina jin ko bandaki ma sai ya goya ni ya kaini, na hango irin son da Daddy zai yi wa abinda yake ciki na, watakila ma sai ya kwace min fada a gurin sa, na hango irin son da Muhammad zai yi wa cikin nan da ace nashi ne, nayi murmushi ina tuna kalamansa, kullum baya rasa aabinda zai fada da zai referring to auren mu ko yayan mu, kullum in yana so ya tsoka ne ni sai yace zai gaya wa yayan mu abinda nake yi masa. Na tuno sanda ya gane ina tsoron asibiti yace duk ranar da zan haihu za'a sha drama. I wondered idan da munyi aure da yaya haihuwa ta zata kasance a gidan sa, maybe tare zamuyi labor, ko kuma doctor ya kora shi waje dan in ina ganin sa a gurin kara rikicewa zanyi. "ai kuwa ba zai fita ba" na fada a fili, dan karamin hauka zaiyi musu. Nayi murmushi. Sai kuma na bata rai ina tuna reality ɗina, I lost everything. The person who raped me took away not only my virginity but my everything, bai barni da komai ba radadin zuciya marar misaltuwa. Ni yanzu ba komai bace ba sai fanko, an empty shell without hopes and dreams, without even a zeal to live, without hope for a future.

Karar wayata ta dawo dani cikin hayyaci na, na goge hawayen da ya sauko kan kuncina sannan na kalli screen din, sunan Mukhtar na gani. Na dauke kaina gefe ina cigaba da kallon reflection ɗina a madubi. I hate breaking his heart every time amma shi ya kasa ganewa, ya kasa fahimtar cewa dan nace na zabe shi ba wai yana nufin ina sonsa ba ne ba, na zabe shi ne dan bani da wani option left. I sometimes wondered ya auren mu zai kasance da shi, dan ni bani da burin komawa Nigeria ko da na rabu da cikin nan, too many memories.

Ya sake kira. Na dauka na saka a kunne na bance komai ba "Habibty" ya fada, nayi shiru ban ce komai ba "ko bacci kike ne na tashe ki" nace "uhm uhm" "ko ba kya jin dadi?" Nace "uhm" "okay bara in barki ki huta. I just want to check on you inji ya kuke, wallahi bana jin daɗin zaman ku ku kadai daga ke sai Daddy, so nake in taho amma Abba ya hana ni, yace in bari sai kin haihu tukunna sai in taho. And guess what? I think suna shirin zasu daura auren nan ne kina haihuwa, maybe shi yasa yace in bari, watakila sai a ango zan taho".

Naji kamar in rushe da kuka amma na cigaba da rike wayar a kunne na. Ya cigaba "ke har yanzu baki gaya min plans dinki ba for the wedding. Su Abba sunce daurin aure kawai zasu yi, ba sa son anything that will call attention na mutane kan mu, amma ni ina son ki samu everything da kike da burin yi a auren ki. Amma baki taba fada min ba ko akwai wani abu special da kike so?" A hankali nace "ni babu abinda nake so. In an daura auren kawai shikenan". Ya danyi shiru "i know ba kya so na, but this is not about me but about you. I want you to have all your heart desires. I know mata da son biki, am sure you had plans....." Na katse shi "mata daban daban ne ai, kowa da akwai abinda take so. Ni bana son biki. Bana son yin komai" na fada ina jin raina yana kara baci. Ya sake yin shiru. Sai kuma a hankali yace "I am sure da shi zaki aura da baki bata rai dan ance ki fadi events din da kike son yi ba. I am sure da Gidado ne da kin fi kowa murna........" Na mike tsaye kamar wadda aka yi wa allura "don't" na fada cikin sarkewar murya, "don't you dare mention his name ever again" ya danyi dariya kaɗan "okay, okay. Na daina. I just want you to talk kin barni ina ta magana ni kadai shi yasa na dan taɓa button ɗin da yake activating ɗin ki. Amma nima kishi na ba zai barni in kuma ambatar sunan sa ba. Kin san...."

Na kashe wayar nayi jifa da ita kan gado sannan na koma na zauna tare da dafe kaina, wani irin bacin rai nake ji, wani irin ciwo zuciya ta take yi min. Na san Mukhtar ya san Gidado kamar yadda shima Gidadon ya san shi, amma basu taba magana da juna ba kuma wani daga cikin su bai taba yi min maganar dayan ba. Ban san mai yasa jin sunan Gidado a bakin Mukhtar ya bata min rai har haka ba. Na jawo wayar tawa ina kallon hoton kan screen din. Hannun Gidado ne a ajjiye akan steering motar sa "Allah sarki Muhammad" Na fada a fili "Allah ka dubi bawanka".

Na sani, ina son Muhammad son da ba zan iya kwatanta shi ba, na kuma sani shima yana min son da ban taba ganin irin sa ba. Na tuno da haduwar mu ta uku, na tuna da yadda ta kasance.

****.     ****.     ****.    ****.    ****.    ****

Tunda muka rabu da shi a ranar da muka yi haduwa ta uku zuciya ta bata samu sukuni ba, naji haushin sa sosai a ranar, haushin rashin karbar number ta da baiyi ba, na kuma ji haushin kaina akan me yasa ni ban karbi tashi ba tunda shi ya manta bai karni tawa ba? Amma kuma ni nasan kaina, nasan pride ɗina na ƴa mace ba zai barni in karbi number ɗin saurayi ba ko kuma inyi making first attempt, na san cewa na kamu da son sa, duk kuwa da cewa a lokacin ban san so ba amma nafi so ace shine da kansa ya fara ambata min yana sona ba ni ba.

Wani lokacin kuma in ina tunanin sa sai inji haushin kaina, ina ganin kamar shi bashi ma da interest a kaina shi yasa ma bai karbi number ɗin ko kuma ya nemi address dina ba. I mean wanne saurayi ne zai ga budurwar da yake so suyi magana sosai kuma har su rabu amma bai karbi number ɗin ta ba, who does that?

Tun ina daukan abin wasa har ya zamar min gaske, kullum in ina zaune ni kadai shi nake tunawa, sai inyi ta bitar maganganun mu a raina ni kadai ina murmushi. In kuma na kwanta bacci Muhammad sai ya bini cikin bacci na, amma a baccin nawa yana karbar number ta har ya kira ni a waya muyi ta hira, ina ta murna, sai na farka sai inga ba haka bane ba.

Lokacin dama Daddy ya kawo ni Abuja da niyyar uncle Ahmad ya nema min jami'a a cikin manyan jami'o'in Abuja saboda in samu in zauna a guri daya in daina binsa ƙasa ƙasa, uncle Ahmad ɗin kuma yayi kokarin samar min admission ɗin, jira kawai yake a fara registration ya kaini inyi, a lokacin ne wata dabara tazo min.

Ina tunawa a cikin maganganun da muka yi da Muhammad ya fada min family dinsa sun bude sabuwar jami'a in honor of his late grandfather. Ya kuma shaida min yana son yin aiki a can. Duk da dai lokacin da muka yi maganar bai fara aikin ba. Sai na yanke shawarar why not in saka a nema min admission a makarantar, maybe mu sake haduwa a can. Maybe ma in ganshi a aji a matsayin malami na. Na tuna sunan makarantar "MD University". Naje na samu uncle Ahmad da maganar "uncle wata sabuwar jami'a da aka bude kwanan nan, MD University, can nake so a nema min" ya bata rai "ban gane ba. Ita kuma wannan da aka nemar miki menene matsalar ta?" Nace "babu komai uncle, kawai dai ni nafi son waccan ne, akwai kawayena da suka ce min can zasu je, kaga zan samu abokan karatu". Haka nayi ta bugawa amma uncle Ahmad yaki yarda, ranar nan ma cewa yayi in na sake yi masa maganar sai ya kwada min mari. Mukhtar yana ta yi min dariya. Ni kuma naki hakura dan gani nake makarantar ita kadai ce chance ɗina na haduwa da Muhammad again.

A haka Allah ya kawo savior dina kasar, Daddy, ai kuwa ranar da yazo da maganar na tare shi, "Daddy ni MD University nake son a nema min, ni bana son wannan da aka samu" ya juya yana kallon uncle Ahmad "wacce ce kuma MD?" Uncle Ahmad yace "kar ka biye mata yaya, wata sabuwar jami'a ce da ko kafuwa bata yi ba ballantana musan kyanta ko akasin haka. Wannan shekarar fa suka fara daukan daliban su na farko" na zamo daga kan kujera na fara kuka "ni wallahi Daddy ita nake so. Dan Allah ni dai a kaini can. Allah in ba'a kai ni ba ba zanyi karatun ba" Daddy ya fara fada "ba za'a kai ki ba ɗin. Wannan da aka samo ɗin ita zaki je".

Amma daga ni har duk wanda yake gurin mun san cewa kamar an kai ni ne an gama.

Wata guda bayan nan har na gama registration na fara zuwa lectures.

Tun daga nan kuma sai na fara abinda ya kai ni makarantar, neman Muhammad. Farko na fara neman sa a cikin malaman department din mu, amma ban same shi ba, sai na fara nema a na sauran departments amma na rasa a ina zanyi concentration neman tunda ni ban ma san me ya karanta ba ballantana in san me zai koyar. Sai na fara shiga cikin yan wani department din da ba nawa ba, in ana hira sai ince something like "ai naji labarin wannan malamin naku Muhammad Lawan, ance bashi da kirki" and they will be like "mu bamu da malami Muhammad Lawan" and I will be like "Okay ba department din ku bane ba ashe".

A haka har sai da na fara fitar da rai, thinking ko ya chanza shawara bai karbi aikin ba. Amma kuma na kasa hakura. A haka har semester ta kare aka fara shirye-shiryen exams. A lokacin ne kuma naje zanyi submitting wani assignment ɗina a office ɗin wani malamin mu. A lokacin ne kuma na ganshi.

Building din hawa biyu ne, duk offices din lecturers ne, office ɗin wanda zan kaiwa yana sama, ina hawa hawa saman idona ya sauka akan Muhammad a kofar wani office yana budewa. Sai dai bai ganni ba ya bude ya shiga ciki sannan ya mayar ya rufe. Na karasa da sauri ina jin wani irin excitement amma kuma zuciya ta tai yarda da cewa shi din ne. Naje kofar office din da ya shiga na tsaya na karanta sunan jikin office din "Muhammad Lawan Muhammad" naji wani dadi ya rufe ni kamar in taka rawa a gurin. Amma kuma what next? Gani dai gashi, katanga ce kawai a tsakanin mu amma me zanyi kenan? Shin zanyi knocking ne in ya buɗe ince hi? Ko kuma shiga kawai zanyi inyi pretending kamar batan kai nayi ba nan zan shigo ba, in yaso sai in nuna mamakin ganin sa a office ɗin. To amma kuma ai ga sunan sa nan baro baro a jikin kofar, in na shiga dole zai gane neman sa nake yi. Na dafe kaina, ga koshi ga kwanan yunwa.

A karshe haka ina ji ina gani na wuce office din ban shiga ba naje nayi submitting assignment dina na sake wucewa na koma gida. Amma hankali na ya kwanta tunda na ganshi na tabbatar yana makarantar, sai na kudiri aniyar zan san yadda zanyi ya ganni kuma ya fara yi min magana.

Daga nan na fara monitoring dinsa, na lura da sanda yake shigowa makarantar da kuma sanda yake fita. Sai na shirya plan dina. Sai da na daidaici lokacin da yake fita sannan na kwashi littattafai da takardu na tafi kan stairs din offices din nasu na baje wai ni lallai karatu nake yi. Ina zaune da uban takardu a gaba amma hankali na yana kan duk motsin da za'a yi a sama. A haka har na ji taku, na dan duba ta gefen ido na ga shine sai na dauke kai na cigaba da bude littafin gaba na amma ina jin zuciya ta tana ta bugawa da karfi. Ban ankara ba sai gani nayi yazo ya wuce ni ba tare da ko kallon inda nake yayi ba, yaje ya shiga motar sa ya tayar ya fice daga makarantar. Naji takaici ya kama ni. Amma na gaya wa zuciya ta cewa bai gane ni ba musamman saboda bayana zai gani sanda yaje saukowa.

Sai na chanja shawara.

Washegari takanas na samo kujeru guda biyu da dan karamin table na dasa a direct opposite stairs din su. Na baza takardu sannan na sawa kofar office ɗin sa ido, a haka har naga ya fito ya rufe kofa sannan ya fara saukowa, sai da naga ya kusa gama saukowa sannan nayi dabara na zubar da takardun gaba na, kamar irin iska ce ta zubar da su ɗin nan, ko bai ganni ba na san hasken takardun zai dauki hankalin sa.

Naji takunsa ya doso inda nake, ina jin kamar a cikin zuciya ta yake taka kafafunsa, sai kuma ya tsaya a dai dai sai ti na. A lokacin na tabbatar cewa ya ganni kuma ya gane ni amma ban kalle shi ba sai na cigaba da bude pages din littafin da yake gaba na. Naji Muryar sa "oh my God" still ban daga kai ba. Ya kara matsowa "oh my goodness. Piya? It is really you" na dago kai ina bata fuska, sannan na bishi da kallo tun daga kan takalmin kafarsa zuwa fuskarsa da take reflecting wani irin annuri da farin cikin da zuciyar sa take ciki.

Na bayyana mamaki a tawa fuskar "wow. Malam Muhammadu dan fillo. What are you doing here?" Ya ja kujerar da dama dan shi na ajiye ya zauna "ke zan tambaya Piya, what are you doing here? How comes? Taya kika zo nan? Shin ko mafarki nake yi ne?" Nayi murmushi ina nuna masa takardun gaba na "karatu nake yi. Anan makarantar nake. Kai fa?" Yace "I work here. Ga office dina can. I can't believe this. You have no idea yadda na sha wahalar neman ki a garin Abuja" a raina nace "taka wahalar ka sani ba ka san tawa ba".

Yace "ranar nan was the best and the worst day of my life. I can't believe I let you go ba tare da na karbi number ɗin ki ba. I went back to your car na zauna jiran mechanic dinki yazo daukan mota in karbi number ɗin ki a hannunsa, amma that good for nothing mechanic bai zo ba, anan nayi sallar la'asar da magrib" na rufe bakina ina dariya, shima yayi dariyar "stop laughing at me. Nasha wahala fa. Har dare bai zo. Da sassafe kuma dana koma gurin already har ya dauke motar".

Nace "to ai Allah ya yi yanzu, gashi mun sake haduwa" bai ce komai ba sai ya dauko wayar sa ya ajiye min a gaba na "i won't repeat the same mistake. Dauki ki saka min number ɗin ki" na dauka na saka, na mika masa amma sai yaki karba yace "save it" nace "okay, me zan saka maka yadda zaka gane. Safiyya Adam Muhammad kamar yayi tsaho, ko in saka maka Fiyya?" Ya girgiza kai "Piya. You will always be Piya to me" nayi murmushi ina jin zuciya ta fari kal. Nayi saving da Piya💝 na mika masa still sai yaki karba yace in kira, sai dana kira ya tabbatar ta shiga sannan ya karbi wayarsa. Na dauko tawa wayar a jaka nayi saving tasa number ɗin, farko na saka Muhammad, sai kuma na goge na saka "Pyar💝"

Forgive the typos

Say Hi to this number so that your number can be saved.

We are almost done with free pages insha Allah.

0704 203 0419

Yan kasuwa kofa har yanzu a bude take. Advert your markets with Safiyya and Gidado.[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹 Safiyya ❤‍🩹*


*By*


*Maman Maama*


*Episode Twelve: Twisted*


Free Episode

Masu bude telegram musamman saboda su karanta Safiyya, you guys have a special place in my heart. I really appreciate the love and support. Dan ku na kasa daina rubutu 😍💕


Gidado yayi taku biyu baya yana kallon hannun da mutumin ya miko masa, sai kuma ya kalli fuskarsa kamar mai kokarin gane wani abu "Mustapha? Mustapha kace" mutumin ya sauke hannun sa ganin gidadon bai yi shaking ba, Al'ameen yace "eh Mustapha yace, ka san shi ne?" Wani murmushi Gidado yayi, a zuciyarsa yana jin kamar an dauke masa wani babban dutse, yace "no. Ban san shi ba. At least not yet" mutumin ya mayar masa da murmushin sa yace "Yes. I believe we will soon know each other a matsayin in laws".

Yayi gaba su Gidado suka bishi a baya zuwa mota, sai a lokacin suka lura da cewa su biyu ne suka zo. Suka gaisa da dayan shima sannan suka shiga bayan motar su kuma suka shiga gaba, wanda ya kira kansa da suna Mustapha yana driving. Gidado ya juya kansa yana kallon waje yana jin daɗin iskar da take dukan fuskar ta sa, iskar yanci. Yanzu tabbas yana da tudun dafawa. Safiyya tana yawan ambaton Mustapha a maganganun ta kamar yadda take ambaton Safina. Ya kuma san cewa shi Mustapha ɗin yayan Safina ne uwa daya uba daya. It cannot be a coincidence ace wannan yarinyar sunan ta Safina sannan kuma tana da yaya Mustapha.

Ya san idan ya tabbatar wa da Mama cewa Safina yar uwar Safiyya ce to tabbas zasu yarda a fasa auren, ko ba dan komai ba ya san yanzu babu halittar da suka tsana irin Safiyya. Ya juyo da kansa, fuskarsa still dauke da murmushi, Al'ameen da yake ta kallon sa ya yi masa alamar tambaya "what?" Dan ya san ba da irin wannan fuskar suka taho ba. Amma Gidado bai kula shi ba so yake yi suje gidan ayi maganar a gaban Safina a gaban kuma Al'ameen yadda Al'ameen din zai zamo masa shaida a gurin iyayensa. Dan yanzu duk wani abun da ya shafi Safiyya ba yarda suke yi da maganar sa ba.

Basu yi nisa sosai ba suka sauka daga kan titi suka shiga wani layi sannan suka shiga wani gida. Gidado ya bude ya fito yana kallon gidan, gida ne na masu rufin asiri, not luxuriously rich but middle class rich. Daga gani kuma gida ne mai mutane da yawa a cikin sa. Wadanda suka kawo su suka yi musu jagora zuwa bayan gidan, sannan suka shigar da su wani ƙaramin parlor. Suna fita Al'ameen ya tambayi Gidado "what? Menene kake ta fara'a haka? Don't tell me daga ganin yayanta har ka matsu da ka ganta" ya karasa cikin tsokana "Gidado ya zauna ya dora kafa daya akan dayar yana jujjuya ta yace "yes, in a way zaka iya kiran abinda nake ji a raina haka. Kai dai ka jira. You will be surprised with the outcome of this visit" Al'ameen ya zauna, trying as much as he can to be comfortable akan kujerar yace "to Allah ya sa muji alkhairi".

Basu dade da zama ba wasu samari suka shigo su biyu suka fara jera musu kayan ciye ciye bayan sun gaishe su. Gidado ya yi tilting kansa yana kallon yaran kokari yake lallai sai yaga kamannin Safiyya a tare da su, sai da suka gama sannan yace "are you guys twins?" Suka juyo suna kallon sa sannan suka kalli junan su suka yi dariya. "no" daya yace dayan kuma yace "a'a. Abokina ne wannan. Dan makotan mu ne". Gidado ya koma ya jingina kansa a jikin kujera tare da rufe idonsa, yana jin al'ameen ya bawa yaran wani abu suka yi masa godiya suka fita. Sai da suka fita Al'ameen yace "kannen ta ne twins din da kake nema?" Bai bude idon ba yace "kannen Safiyya ne" Al'ameen yayi ajiyar zuciya yace "Gidado, gidan su Safina muka zo nan ba Safiyya ba. What is wrong with you" gidado ya gyara zama yace "na sani, akwai abinda nake tunani. You will understand idan ta fito.

Ba'a jima ba kuwa ta fito ɗin. Kamshin turaren ta ne ya fara iso musu kafin ta karaso. Kyakkyawace son kowa kin wanda ya rasa. Fara tas mai cikar jiki da shape mai kyau wanda ta tabbatar ya fito a cikin doguwar rigar lace ɗin da ta saka, ba irin fitowar da za'a kira da tsiraici ba amma irin fitowar da zai dauki hankalin duk wanda ya kalle ta. Fuskarta da kwalliya dai dai gwardado. Tayi daurin dankwalin da ya zauna ɗas a kanta ya kuma bayyanar da yalwataccen gashin kanta ta baya. Ta yafa mayafi a side daya ya rufe rabin kirjinta.

Ta tsaya a bakin kofa tayi sallama. Suka amsa mata a tare sannan ta shigo kanta a kasa ta zauna a kujera ta gaishe su "sannun ku da zuwa. Da fatan hanya bata gajiyar da ku sosai ba" duk suka yi shiru babu wanda ya amsa. Kowa yana saka ran dayan zai amsa. Sai kuma suka kalli juna a tare suka amsa "lafiya lau" "yauwa".

Suka sake yin shiru gabaki daya. Ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da fingers dinta, Gidado kuma ya tsare ta da ido a ransa yana son ya ga ko zai iya tuno kamannin Safinar Safiyya, maybe ko ya taba ganin ta a hoto amma ya manta, yayin da shi kuma Al'ameen yake kallon Gidado da mamakin kallon da yaga yana yiwa Safina. Al'ameen ne ya katse shirun ta hanyar yin gyaran murya tare da cewa "malama Safina ya shirye shirye?" Ya fada already feeling awkward, dan shi ba gwanin magana bane ba musamman ga wadanda bai sani ba. Ta dago ido suka hada ido da Gidado, tayi murmushi tare da sake mayar da idonta kasa sannan tace "alhamdulillah. Ya naku?" Kafin ya amsa mata Gidado yace "ina twins?" Ta sake dago ido tana kallon shi, shi kuma yayi kokarin studying fuskarta yana neman yanayin mamaki amma sai yaga confusion. "Twins kuma? Wadanne twins?" Yace "naga Mustapha shi ya dauko mu dazu, na dauka tare da twins suka zo" ta sake bata fuska tare da girgiza kai "still ban gane abinda kake nufi ba. Mustapha daga ina yazo? Ai dama yana nan. But ka san shine wai?" Yace "shi Mustaphan ba yayan ki bane ba?" Ta gyada kai still cikin nuna rashin fahimta tace "eh yaya na ne, dan kanin baban mu ne. Ka san shi ne?"

Gidado ya mayar da kansa baya tare da rufe idonsa, yana jin dutsen da ya daga daga kan zuciyarsa dazu yana komawa yana cigaba da danne ta. Al'ameen yayi saurin cewa "kamar naga kin kawo mana snacks, ɗan zuba min" ta mike da sauri ta dauki dan karamin plate ta na zuba masa samosa amma hankalin ta yana kan Gidado, ta durkusa ta mika wa Al'ameen still tana kallon Gidado tace "is he okay? Ko baya jin dadi?" Al'ameen yace "fine, he is fine, akwai serviette ne?" Ta dudduba gefe sai ta mike tace "bara in kawo".

Tana fita Al'ameen ya ajiye plate din da ta bashi ya taba kafadar Gidado yace "kai lafiyar ka kuwa? What are you doing. What is with wani Mustapha and twins" Gidado ya bude idonsa, duk annurin da ya sauka a fuskarsa dazu ya kauce yanzu, yace "Piya tana da step sister mai suna Safina, and a step brother mai suna Mustapha. When I saw that guy yace min shi yayan wannan Safinar ne kuma sunan sa Mustapha, I thought......" Al'ameen yace "Muhammad! Must you relate everything to her? Komai na rayuwa sai ka jingina da ita sannan zai baka ma'ana. Are You telling me kazo gurin yarinyar da zaka aura and the first thing da kake kokarin tambayar ta shine ko ta san dangin tsohuwar budurwar ka? Does that even makes sense to you?"

Gidado ya dauki robar ruwa ya bude ya daga ya shanye gabaki daya sannan ya ajiye robar. Yayi murmushin takaici yace "maybe I am loosing my mind. But yes. To me everything relates to her. Nothing makes sense to me in dai ba'a haɗa da ita a ciki ba" Al'ameen yace "then I don't think you are fit to marry " Gidado yace "ha! Finally someone ya fahimta. Go and tell that to Abba and Mama watakila su ma su fahimta"

A dai dai nan Safina ta dawo hannunta rike da sabuwar serviette. Ta ajiye a gaban Al'ameen amma shi kuma sai ya mike. Tace "ba ka ci samosar ba" ya kalli samosar, shi ya manta ma ta ajiye masa, yace "thank you, zan dan je waje ne inyi waya" yana fita ta zauna akan kujerar da ya tashi daga kai tana kallon Gidado cike da damuwa tace "Habibi, kamar ba ka jin dadi ko? Ko tafiyar ce ta gajiyar da kai?" Ya dan juyo ya kalle ta "am fine. Kar ki damu. Yanzu zamu ga su baban? Gwara mu gama mu zo mu tafi"

Ta dan bata rai "tafiya fa ka ambata, yanzu fa kuka zo and ko gaisawa bamu yi ba sosai musamman tunda yau muka fara haduwa. Ya kamata mu danyi hira ai ko?" Ta karasa tana langwabe kai gefe. Ya gyara zamasa yana kallon ta yace "hira? Okay what do you want us to talk about?" Tace "at least ka fada min ya ka ganni? Tunda yau ka fara ganina. Gwara in san cewa nayi maka ko ban yi maka ba. And maybe tell me abinda yake damunka, watakila ina da maganin sa" yace "does that really matter? Kina ganin ra'ayi na akan ki yana da muhimmanci?" Ta mike ta ta bi ta gabansa zuwa inda kayan abincin suke ta zubo masa juice ta hado da snacks a plate ta dawo inda yake ta durkusa a gabansa ta mika masa juice din sannan ta koma ta zauna ta dora snacks din akan cinyarta tace "ra'ayin ka a yanzu shine yafi komai muhimmanci, musamman ni a gurina. Abinda kake so shine abinda zan saka a gaba na, abinda ba ka so shine abinda zan fi ki fiye da komai" yace "tell that to my parents" ya kurbi juice din ya ajiye yace "send me your account details, zan turo miki kuɗin da zaki yi hidima, am sure kina shirya wani abu da kike so kiyi. And if you need anything, message me".

Ranta ya baci har fuskarta ta nuna, tace "yanzu dai ba zanji cewa nayi maka ko banyi maka din ba? Duk wannan kwalliyar da nayi?" Ya mike tsaye "ban boye miki komai ba Safina. And you agree to take your chance with me. Wannan shine dai dai lokacin da zaki fara hakurin da kika yi alkawarin zaki yi" ta mike ita ma "kayi hakuri. Kar ka bata rai dan Allah. Kawai dai kasan mu mata muna da son yabawa, and when I walked in I noticed kana ta kallona, I thought na samu wani bangare na zuciyar ka" ya juya yayi hanyar fita, har ya kai bakin kofa sannan ya juyo yace mata "I was looking at you because I thought you were someone else, it turned out ba ita ce". Sai ya juya ya fita.

A waje ya hango Al'ameen yana waya, ya tafi gurinsa ya tsaya har ya gama, ya fahimci cewa da matarsa Humaira (read *Aisha Humaira*) yake magana saboda yadda yake ta zabga murmushi shi kadai, love is truly the most beautiful feeling ever. Sai da ya gama sannan ya juyo yana kallon Gidado yace "wai fitowa kayi ka bar ta ita kadai?" Yace "kai ma ba fitowa kayi ka bar ni ni kadai da ita ba?" Al'ameen ya danyi dariya "guri fa na baku ku gaisa sosai" Gidado yayo dan karamin tsaki "I can't stay inside with her. It is suffocating".

Haka suka cigaba da tsaiwa a waje duk su biyun, har sai da Mustaphan da ya dauko su dazu yazo yayi musu magana sannan suka koma ciki tare, basu tarar da ita ba. Ya zauna ya saka su a gaba sai da suka dan ci abinci kadan sannan ya nuna musu toilet suma yi alwala suka zo suka yi sallah, daga nan kuma ya fita sai gashi sun dawo tare da manya su biyu, wadanda duk suka baiyana wa su Gidado kansu a matsayin wan baban Safina da kuma kanin sa, suka tabbatar musu da cewa suna goyon bayan auren suka kuma bawa Gidado assurance ɗin cewa ba zai samu matsala da Safina ba.

"Tun tana jaririya mahaifinta ya rasu. Ni na rike ta tamkar ni na haife ta, ko bayan aure gurin na zaka zo akan duk wata bukata, kar ka yarda wani daga baya ya fito yazo yace maka shine yake da iko a kanta. Mune dangin ubanta mune komai nata" Babban cikin su ya faɗa. Da zasu tashi Al'ameen ya ajiye musu kudi masu kauri yace su sayi turare

Sai da zasu tafi sannan Gidado ya tuna da sakon ta da Mama ta bashi ya kawo mata, ya mika wa Mustaphan da yake tare da su yace ya kai mata, yayi dariya "kai dai kawai kace inje in kira maka ita kuyi sallama" ya kira wata yarinya "je ki cewa Safina tazo angonta yaƙi tafiya yace sai ya ganta".

Ba'a jima ba ta fito, ta yafa mayafi sosai wannan karon ta rufe jikinta. Gidado ya mika mata ledar hannunsa "inji Mama" ta karba tana murmushi "Nagode sosai. Zan kira ta inyi mata godiya" yace "good. Mu zamu tafi. Ki turo min sakon da nayi miki magana a kansa" ta girgiza kai "no ka barshi kawai. I already made plans" ya daga kafada "okay. Alright" har ya juya ssi kuma ya dawo "I just heard cewa babanki ya rasu, you never tell me" ta daga kafada itama "you never ask" yace "maman ki kuma fa?" Tace "tana Abuja. Da ya rasu ta koma gurin sister ɗin ta a Abuja. Yanzu ma tana can. A can zan sauka lokacin bikin. A can zata yi nata taron" ya gyada kai. "Okay. Alright. Am sorry for your lost. Allah yaji kansa" ta langwabe kai "Ameen. Na kusa daina maraici ai. Insha Allah. Am sure mijina zai kula da ni sosai".

Har suka je airport basu yi magana da junan su ba, har jirgin su ya tashi ya kuma sauka a Abuja basu tattauna akan komai ba. Gidado was consumed in his thoughts yayin da shi kuma Al'ameen ɗin ya rabu dashi dan ya fahimci baya cikin mood din maganar. Sai da suka sauka suka shiga mota zasu je gida sannan Gidado yayi wa Al'ameen magana "Ya Ameen, please tell me the truth, do you think I am loosing my mind and imagining things?" Al'ameen ya rage gudun da yake yi yace "i don't think you are loosing your mind. But I believe you are overthinking everything" Gidado yace "then advise me? How can I stop thinking? How can I stop thinking about her?" Al'ameen yace "I am not expert in this thing, amma ina ganin you need to get something that will keep you busy, wani abu da zai dauke maka hankalin ka daga tunani, maybe shine dalilin su Abba na yi maka aure thinking matar zata dauke maka hankalin ka, but I advise ka samu wani abu ka dinga yi, ka daina zama kai kadai, ka gajiyar da jikin ka da ƙwaƙwalwar ka yadda ko dare ne yayi kana kwanciya zaka yi bacci. Sannan get rid of anything da zai ke tuna maka da waccan yarinyar"

Gidado ya danyi murmushi yace "I tried doing that. But she is everywhere. Har cikin bacci na take shiga. I always dream about gani na da ita na karshe. And the more I saw her a cikin mafarkin the more I feel the need to get back to her. Gani nake kamar kokarin mantawa da ita da nake yi yanzu ba dai dai bane ba. Gani nake kamar nayi betraying dinta, she needed me and I shut the door on her face" Al'ameen ya tsayar da motar ya juyo sosai yana kallon sa "I can't believe this. You betrayed her fa kace? How? I thought ita ce ta yaudare ka ta saka kuka yi soyayya alhalin tana da aure? Ko kayi bincike ne ka ga cewa bata da auren karya take yi?" Gidado yace "she is married. Wannan bani da shakku akan sa a yanzu. But ....." Al'ameen ya bude hannu yace "but what Muhammad? She is married and pregnant for her husband. Kai kace min kaga cikin da idonka. For God's sake stop creating things in your head and blaming yourself alhalin kai ne victim din" Gidado ya dago kai yana kallon Al'ameen da wani irin kallo yace "ranar da tazo gurina na karshe, ranar da ta gaya min cewa tana da aure. She looked broken, sad, and devastated. She looked like a shell of her former self. Akwai wani abu da ya faru da ita, wani abu da ya mayar da ita haka. Ba haka take ba. She was the most cheerful person I have ever seen. And sanda na kore ta daga office ɗin, ta tsaya a bakin kofa ta miko min hannu and called my name, kamar tana neman taimako daga gare ni, but i did not listen. I shut the door. And now duk sanda na rufe ido na scene din da nake gani kenan. Har cikin bacci na nake jin tana kiran sunana"

Al'ameen ya dafe kansa tare da rufe idonsa, Gidado yace "you really think I am loosing my mind, right " Al'ameen ya bude idonsa yana kallon Gidado yace "no. I think you love that girl too much, and I think you need to see a therapist, you need to see Mammy".

Gidan su Gidado suka fara zuwa, suka yi packing Gidado ya bude kofa ya fita sai kuma ya dawo ya zauna yana kallon Al'ameen yace "one more question, ka taba ganin Safiyya, do you think she loved me ko kana ganin tun a lokacin she was playing me?" Gidado yace "guy! Anya kuwa kana kallon kan ka a madubi, anya ka fahimci irin haduwar da kayi? Bana jin a duniya da akwai wata ya mace mai jini a jika da zaka ce kana so kuma ya kasance bata son ka. Tabbas a lokacin da na ganku da Safiyya tana son ka. But that doesn't matter now. Don't tell that matter".

Gidado yayi murmushi fuskarsa tana nuna jin daɗin maganar yace "thank you ɗan uwa, I really appreciate this".


Forgive the typos please

Dan Allah kar kuce yayi kaɗan 😅🤫

Littafin Safiyya is 500 naira via

0779484494
Nafisa Tafida Usman
Access Bank

Send the evidence via telegram or WhatsApp to

0704 203 0419

Posting of paid episodes will be on telegram only.

Dan Allah idan da akwai wadda ta turo evidence dinta ban saka ta a group ba should talk to me so that your message will come up.

Nagode sosai. I really appreciate all the love.
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹


*By*


*Maman Maama*


*Episode Thirteen: One Day Apart*


Free Episode

Littafin Safiyya is 500 naira via

0779484494
Nafisa Tafida Usman
Access Bank

Send the evidence via telegram or WhatsApp to

0704 203 0419

Posting of paid episodes will be on telegram only.

Kwana biyu bayan zuwan su Katsina, Gidado ya saka Safina ta turo masa address ɗin matar da aka ce yaje ya gaisar anan Abuja, sunan ta Hajiya, kuma kamar yadda Safina ta gaya masa mahaifiyar ta ma tana tare da Hajiyar a lokacin. Dan haka ya shirya ya ɗauki Haidar suka tafi tare. Tun daga gate ɗin shiga gidan suka fahimci cewa wannan gidan masu kuɗi ne, real kuɗi, tsohon kudi.

A bakin gate mai gadi ya tambaye su gurin wanda suka zo, Gidado yace "Hajiya, ina fatan tana nan ai ko. Am sure ta san da zuwan mu" maigadin yayi murmushi yace "ko sirikin na mu ne? Tun safe Hajiya tace zata yi bako, tace mai neman auren Safina ne zai zo, ai Mommyn Safina ma tana gidan. Allah ya sanya alkhairi ya sa da mu za'a yi" Gidado ya danyi shiru yana kallon sa, babba ne sosai kuma daga ganin sa kasan ya san jiya ya kuma san yau, irin masu aikin gidan nan da suka zama yan gida. Sai yayi amfani da damar sa yayi kokarin sanin wani abu akan Safina. "ka san Safina kenan sosai" mai gadin yace "sosai ma. Safina ai kamar jika take a gidan nan. Mahaifiyar ta ma a gidan nan ta tashi tun tana karama har aka aurar da ita har yau kuma nan shine gida a gurin ta. Ai yayar mahaifiyar ta ce matar gidan nan. Kuma tunda ita ta rike ta sai ta zama kamar ƴa ce a gidan. Safina kuma kaga ta zama jika ce. Kai kuma ka zama sirikin mu. Allah dai ya sanya alkhairi" Gidado yayi murmushi "na kusa zama. Not yet. Nagode Baba. Ameen. Dan Allah a sanar musu mun zo"

Mai gadin ya bude musu gate suka shiga da mota sannan ya kira wata yarinya da tazo wucewa yace ta je ta gaya wa Hajiya baƙin ta sun zo. "Saurayin safina ne?" Yarinyar ta tambaya cikin rada amma su Gidado sunji, mai gadin ya fara yi mata fada "maza ki tafi aiken da nayi miki, ku baku da aiki sai shegen tsegumi".

Su Gidado suka fito daga motar a tare, Haidar ya zagayo side ɗin Gidado yace "tana nan ne?" Gidado ya kalle shi yace "wa?" Haidar yayi murmushi "ita ɗin dai" Gidado ya bata rai "zaka koma gida wallahi" Haidar yayi dariya "wai naga sai wani bobboye ta kake yi ne. I just want to see her in lissafa mata irin abubuwan da nake so da kuma wanda bana so. Kasan ana gama bikin ku can zan koma. Though ba Safiyya bace ba amma wancan alkawarin bai karye ba. Har na zaɓi daki ma" Gidado yace "tsakanin ku ne wannan, ni ina ruwa na?" Haidar yace "to ai baka haɗa ni da ita ba dan haka akwai ruwanka a ciki, dole kai zan bawa sako ka isar mata. Ina fatan ta iya girki, ina nufin girki irin five stars standard ɗin nan".

Kafin Gidado ya bashi amsa aka yi musu magana aka ce su shiga. Suka jera suka tafi, sai Gidado ya samu kansa da murmushi yana tuno irin soyayyar da take tsakanin Safiyya da girki. She and Haidar would have been friends. She even promised him that. Ya tuna da wani lokaci da tayi wannan alkawarin.

****.     ****.     ****.     ****.     ****.    ***

Waya suka yi da safe a muryarsa ta fahimci cewa he was stressed. Da ta tambaye shi dalili sai yayi mata complain cewa aiki ne yayi masa yawa a office, har zuwa rana ma da suka kara wayar still bai kammala aikin da yake yi ba. Da yamma sai gata ta baro hostel dinsu ta dauko motar ta tazo har office ɗin sa ta kira shi a waya tace ya fito ya ga wani abu. He complain cewa aiki yayi masa yawa amma shi kansa ya san cewa ba'a cewa Safiyya "no" dan yanzu sai ta saka masa kuka. Dole ya rufe office ya fito ya same ta a mota, ta bude masa gaba tace "get in" ya shiga yana kallon ta "what?" Tace "to ka rufe motar mana so kake mutanen da suke waje su ga abinda zan nuna maka. Sirri ne" yayi ajjiyar zuciya "Piya! Aiki nake yi wallahi. Dole a yau zan gama aikin nan kuma ko rabi ban yi ba. Ko kina so a kore ni ne?" Tace "waye zai kore ka? Abba ko uncle Habib? You own dis school. Oya, close the door" ya jawo kofar ya rufe "yes ma'am" sai kawai gani yayi ta saka mota a giya ta fara tafiya, ya bude ido "what are you doing Piya? Ina zaki kai ni?" Tace "I am kidnapping you, kuma sai an biya ni ransom zan dawo da kai".

Ya gyara zaman sa yana kare mata kallo, abaya ce a jikinta da mayafin abayar a kanta. Fuskarta fes babu kwalliya, fatarta kamar kullum tana kyalli da daukan ido. Ta kalle shi ta gefen ido. "ka daina kallo na. Ko so kake inyi tuntube ne" yace "you are driving, not walking " tace "to in na buga motar fa?" Yace "tunda kin hana ni yin aiki na ba gwara in zauna inyi ta kallon ki ba, kar inyi biyu babu" tayi murmushi "believe me, you are going to enjoy this. Zaka gode Allah cewa I kidnapped you today" yace "zan rubuta a diary in ajiye wa yaran mu, in gaya musu maman su taje har office ɗina tayi man-napping ɗina" tayi dariyar kalmar da yayi amfani da ita a dai dai lokacin da suka zo gate din fita daga makarantar.

Sai da suka fita yace "seriously, ina zaki kai mu ne wai?" Tace "park. You need a rest. I couldn't take jin ka a gajiye. It doesn't suit you" ya bude ido "baby ni namiji ne fa? Dole sai nayi aiki. In banyi ba da me zan kula da ke da yaran mu?".

Sai da suka yi nisa sannan ya juya yana kallon seat din baya "wai abinci ne a bayan motar nan? Kamshi nake ji" tace "abinci ne mana. We are going to have a picnic. And I know ko lunch baka yi ba. Ya shafa cikin sa, ko breakfast din kirki bai yi ba kuma yanzu kamshin abincin ya kara masa jin yunwa. Ya juya yana kallon ta yace "you are amazing Piya. Thank you. Zan iya fara ci yanxu?" Ta girgiza kai da sauri "not in my car" ya daga hannu "nayi alkawari ba zan bata miki ba" and he knows he dare not. Dan muguwar tsafta ce da ita. A karshe dai haka ya hakura har suka je gurin. Shi yayi musu shinfida da abin shimfidar da tazo tashi, ita kuma ta jera musu abinci, sannan ta jera masa a plates ta ajiye masa a gabansa.

Farko har zaiyi mata dariyar ta zuba masa da yawa, saboda shi ba mutum ne mai cin abinci sosai ba, amma yana ci tana bashi labarin dramar da ake a hostel dinsu bai san sanda ya cinye ba sai gani yayi tana kara masa.

Ya hadiye lomar bakinsa yana jin daɗin abincin yace "Piya, duk sanda aka yi bikin mu, ina jin Haidar gidan mu zai dawo da zama" tana kallon sa itama tace "saboda me kace haka?" Ya nuna plate din abincin gabansa yace "abinci, saboda kaunar da yake yi wa abinci. Saboda ke kuma kin iya abinci" tayi murmushi fuskarta tana nuna jin daɗin maganar sa tace "bayan bacci, the second thing da na iya a rayuwata shine girki. I can cook. Irin I can really cook" yace "banda yabon kai dai. In mutum ya iya abu ai bari yake yi mutane su yaba ba wai shi ya zauna yayi ta yabon kansa ba" tace "saboda me? Abeg let me brag about my achievement tunda bani da abubuwan bragging for da yawa. I can cook. Na iya girki wato nake gaya maka" yace "there is something else da kika iya kuma ai, wanda ya kamata a baki medal a kansa" ta gyara zamanta tace "what? Tell me please, in kara shi akan list of achievements ɗina a rayuwa" yace "crying. You can cry for Africa. Ni ban taba ganin ma mai saurin kuka irin ki ba". Tayi dariya "haha. Duk kuka na ai mai dalili nake yi, is either an hana ni yin abinda nake so ko kuma an takura min sai nayi abinda bana so. In ba'a so inyi kuka kawai a barni in yi abinda raina yake so" yace "ai na fahimci haka. Kuma na fahimci laifin Daddy ne. Shi ya shagwaba ki beyond repair. Ni yanzu an barni da sabon raino. In mun haihu ban san wa zan goya ba, ke ko yaran" ta bata fuska "wanda kafi so. A lokacin zan gane matsayi na ai" yayi murmushi yana cin burger din daya ajiye masa a gabansa da zafinta, duk kuwa da cewa jin cikinsa yake yi kamar zai fashe. Yace "wai in tambaye ki Piya, yanzu in muka haihu, in yaron yana yi miki kuka ya zakiyi da shi?" Tayi shiru tana tunani sannan tace "zama zanyi nima in yi masa kuka" ya ajiye burger din yana dariya sosai, sai da ya gama sannan yace "I can't wait for that time. You will look so cute with kids" tayi murmushin ta mai kyau tace "I can't wait either. I love kids. Ban san yadda ake musu ba saboda gidan mu babu yara but I will learn. I will be the best Mom ever".

Sai da suka gama cin abincin sannan ya kira Haidar a waya. "albishirin ka. Ka kusa barin gidan Abba. Dan na tabbatar duk sa da akayi bikin mu da Safiyya gida na zaka koma" Haidar yace "saboda me?" Gidado yace "saboda ta iya girki. Kuma tana kaunar girki. She will just keep feeding you har sai ka kasa tashi. Nima abinda ya faru da ni kenan yanzu" sai kuma ya mika wa Safiyya wayar "gashi yace in baki" ta bude ido tana girgiza kai "in kuma suna tare da Mama ko Baba fa? Ai sai suce bani da kunya" yace "shi kadai ne fa" tace "to in ya basu labari fa? In yace musu munyi waya fa?" Gidado yayi ajjiyar zuciya "ba zai fada ba, zan gaya masa kar ya fada" ta langwabe kai "kayi alkawari?" Yace "yes, nayi alkawari" sai ta karbi wayar ta saka a kunnen ta, taji muryar Haidar yana dariya yace "nima nayi alkawari" sai taji kunya ta rufe fuskarta kamar yana gurin. Suka gaisa, yana ta tsokanar ta, sannan a karshe tayi masa alkawari "ka kusa dawowa gidan yayanka da zama. Kai zaka fara zabar daki a gidan. Abinci kuma sai wanda ka zaba za'a ke girkawa a gidan".

Sai da suka gama wayar ta mikawa Gidado sannan taga ashe shi kallon ta yake tayi, ta sunkuyar da kai tana jin kunya yace "you know what? I am glad you kidnapped me. And I am looking forward to you kidnapping me again. I get to look at you instead of papers.

****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****.   

Suna shiga cikin gidan wani katon parlor aka kai su. Suka zauna aka fara hidimar kawo musu fruits da snacks da drinks iri iri. Haidar zai fara ci Gidado ya harare shi sai ya koma ya zauna yana bata fuska. Basu jima ba wata dattijuwar mata ta fito tare da wata yar budurwa, yarinyar ta taimaka mata ta zauna a kasa sai su Gidado suma duk suka sauko suka zauna a kasan. Tace "bana iya zama kan kujera yanzu, ciwon kafa ya sako ni a gaba. Kun san jikin tsufa. Ko da yake ku ba zaku fahimta ba".

Suka yi murmushi sannan suka gaishe ta a tare, ta amsa musu da sakin fuska sosai tare da tambayar su mutan gida. Ta nuna Gidado tace "na gane mai gidan nawa, waccan marar kunyar ai takanas ta aiko min da hotonsa ta waya wai ta samu mijin xa yafi nawa kyau, ni kuwa na san ko a yanzu kuka jera kai da Alhaji sai yammata sun dauki Alhaji sun barka" ta karasa maganar tana dariya. Suma suka yi murmushi.

Ta cigaba "naji daɗin zuwa da kayi ka gaishe ni, hakan yana nufin ka girmama ni kenan. Ina kuma so ka dauke ni tamkar uwa ba ma kaka ba, ni uwar kowa ce. Ni ka ganni nan Allah bai bani haihuwa ba amma kuma yayi min baiwar mutane. Wannan ya sa gashi dai shekarun girma sun zo min amma bana kukan rashin yaya, yaran da na rike sun zama gata na. Yayan yanuwana da na mijina duk dauka nake yi in rike su kamar ni na haife su, sannan kuma in debo marayu in rike su suma in basu duk kulawar da ya dace iyaye su bawa yaya, ko yan aiki aka kawo min na lura basu da cikakken gata a gidajen su sai in mayar da su yayana in rike su har in aurar da su. Ba zan iya lissafa yan aikin da na rike ba, tun daga kan Safiya har zuwa wannan yarinyar ta gaba na Lubabatu. Allah sarki Safiya Allah ya kai rahama kabarin ta. Duk da bata raye amma har yanzu ina morar gatan da na yi mata".

Su Gidado suka ce "Ameen" ta cigaba "ina gaya maka wannan ne dan ka saki jikin ka, nan gidan mutane ne, kowa kuma namu ne ballantana kai da aure zai hada mu. Ka fahimta ai ko?" Gidado yayi gyaran murya yace "na gane. Na gode kuma sosai. Allah ya kara lafiya" tace "Ameen ya Rabbi. Ai an gaya min cewa kai jika ne a gurin marigayi ambassador Muhammad Dikko. Mutumin kirki. Allah ya kai rahama kabarin sa. Na san shi ai lokacin da yana da rai, na kuma san matarsa Hajiya Fatima, ban sani ba ko zata gane ni amma in kaje kace mata Hajiya Maryama matar Alhaji Nasiru Atafi tana gaishe ta" Gidado yace "insha Allah za'a gaya mata".

A lokacin wata mata ta sauko daga sama, kallo daya Gidado yayi mata ya fahimci cewa ita ta haifi Safina, kamar su daya sai dai safina zata fi ta farar fata sannan da kuma bambancin shekaru. Ta zauna akan kujera a gefen su Gidado, suka juya suka gaishe ta ta amsa musu babu yabo babu fallasa sannan tace "sai yau ka samu damar zuwa gaishe mu kenan".

Hajiya tace "menene haka Sa'adatu? Tunda yazo ba shikenan ba?" Tace "ni kinsan bana barin magana a ciki na. Amma muna gari daya ace sai few days to auren Safina sannan zamu ga mijin da zata aura? A hakan ma kuma sai da nayi waya nayi wa mahaifiyar sa korafi sannan yazo, da bai yi niyyar zuwa ba ai. Da sai dai ranar bikin muma mubi cikin mutane muna tambayar ina angon yake"

Hajiya tace "tunda dai ita amaryar ta san shi ba shikenan ba?" Sai kuma ta juya gurin Gidado tace "rabu da ita, ita in dai idonta ya ga abu sai bakin ta yayi magana, haka halinta yake, zaka saba da ita a hankali. Tana da kirki sosai sai dai zaka sha faɗa" Mommy tana daga gefe ta kuma cewa "an anyi abu ba dai dai bane ba ai nake yin fadan" Hajiya ta chanza maganar ta hanyar yi musu korafin ba su ci komai da aka kawo musu ba, su kuma suka bada uzurin cewa sunci abinci a gida kafin su fito. Amma duk da haka sai ta saka aka kwashe komai da aka kawo musu aka kai musu mota. Da haka suka yi musu sallama suka tafi.

Suna shiga mota tun kafin su bar gidan Haidar yace "I don't like wannan surikar taka" Gidado yace "that makes the two of us" bayan sun dauki hanya kuma sai Haidar ya fara dariya yace "ka san tunanin da nayi, ina ma ace tare da Aunty Hafsat muka je gidan nan matar nan tayi mana wannan mulkin" Gidado yayi murmushi yace "da anyi yaki kuwa. She will humble her. Zan so inga yadda zasu kare da bikin nan".

*Her* 🧕🏻

Kwanaki suna ta tafiya har ya rage saura sati biyu lokacin da likita ya saka za'a yi min aiki yayi, amma sai naji sam bana jin tsoron aikin da za'a yi min ban damu da cewa wai cikina za'a yanka a fito da ɗan mutum ba, ni dai kawai burina shine in rabu da mayataccen cikin nan ko na samu in shaki iska mai daɗi, ko na samu in dai na ganin disappointment a fuskar Daddy a duk lokacin da ya kalle ni, ko na samu in manta da abinda ya same ni.

Sai dai ni kaina na san cewa rabuwa da cikin ba zata taba goge abinda ya faru daga zuciya ta ba, babu abinda zai fari da zai saka in manta da abinda aka yi min. Zalincin da aka yi min. Babu kuma abinda zai saka in yafe wa wanda yayi min. Har abada.

A lissafin Daddy naji yace aiki na zai kama washegarin daurin auren Safina. Ni kam ban ma rike date din da aka saka na auren Safina ba. Dan ni ba ma na gane ranaku a yanzu. Akwai kawayen mu da yawa da suke ta yi min magana a chats akan bikin Safina, ni kuma na kan basu amsa da cewa nayi tafiya jinyar Daddy dan haka bana nan za'a yi. Safina kam sai shirye shiryen ta take yi. Ta kan turo min pictures na kaya tace in taya ta zaba, har kayan da zata saka na kowanne event da zasu yi sai da ta turo min, sometimes na kan yi ignoring dinta dan ni abinda yake gaba na yafi karfin zaban kayan sawa, sometimes kuma sai in bata amsa dan kar ta ga kamar dan nasan kudin indirectly daga gurina zasu fito shi yasa na ke wulakanta ta.

Kamar yadda nayi tunani, su yan uwan nata da ta tafi Katsina gurin su dan suyi mata aure babu abinda suka yi mata na kayan daki, haka a dole Mommy ta sauko daga fushin da tayi da Daddy ta dame shi da waya akan ya bada kuɗin da za'a yi wa Safina kayan daki, direct yace mata bashi da kuɗi, besides, ai tace masa Safina ba yar sa bace ba. Sai ta koma gurin Uncle Ahmad shi kuma yace mata ta tambaye ni amma sai ta kasa tambayar tawa ta cigaba da bin Daddy, har sai da Daddy ya tabbatar tayi laushi sannan yace da Uncle Ahmad ya bata. Haka suka yiwa uncle Ahmad bill tun daga kan kayan daki har zuwa kayan da zasu saka na fitar biki, shi kuma ya raba biyu ya basu rabi yace ba zai bayar ga baki daya ba. A lokacin ne Safina ta yi min dogon message akan maganar, wai uncle Ahmad zai saka suji kunya, wai tun yanzu ya fara nuna musu cewa su ba yanuwan mu bane ba, dan Allah inyi masa magana.

Banyi masa magana ba sai na yiwa Daddy magana, tunda na fahimci shi sulhu yake so yayi a tsakanin mu shi kuma uncle Ahmad so yake a raba gari kowa ya kama gabansa. A ƙarshe dai Daddy ya saka Uncle Ahmad ya cika musu kuɗin suka yi duk siyayyar su suka gama.

A ranar da yake saura sati daya aikina, na tashi da safe kamar yadda na saba na shiga kitchen na haɗa smoothie na sha sannan na shiryawa Daddy breakfast. Na dauka na kai masa dakinsa na tarar yana kwance idonsa a rufe amma daga gani na gane ba bacci yake yi ba. Na jawo table gabansa na dora abincin na zauna a gefe nace "Daddy ga breakfast. Ka tashi ka ci". Ya tashi zaune da kyar, na lura da effort din da ya saka yanzu gurin tashin yafi yadda yake yi da, ciwonsa yana kara cigaba a kwanakin nan fiye da yadda yake da.

Ya zauna ya debi oats din dana dama masa a hankali ya kai bakin sa, na kara lura da yadda hannunsa yake rawa sannan da kuma yadda ya hadiye abincin da kyar. Ya lura da kallon da nake yi masa yayi gyaran murya yace cikin muryar da ta kara zama weak "doctor yace nan da wata uku, that's idan na kai nan da wata uku, I will be needing a feeding tube, ba zan iya cigaba da hadiye abinci da kai na ba. Kin gane?" na gyada kai na da sauri tare da sunkuyar da kaina ina kallon ciki na da yanzu baya boyuwa a cikin riga ta. Ya kira sunana "Safiyya" na dago kai na kalle shi yace min "don't cry" na sake sunkuyar da kaina ina jin hawaye na suna zuba kan cinyata. Nayi saurin goge su. Sai ya sake kiran sunana "Safiyya" na dago kai, yace "munyi magana da Ahmad, za'a daura auren ki da Mukhtar washegarin da akayi na Safina, in anyi miki aiki da safe, da yamma za'a daura miki aure. Saboda baƙin da zasu zo na Safina ba sai sun koma ba sai a daura naki. Do you understand?"

Na sake gyada kaina ina rike hawayena. Sai na mike na yi hanyar fita, har na kai kofa ya sake kiran sunana "Safiyya " na juyo yace "kin fahimci dalilin yin auren nan ko?" Na sake gyada kaina ban ce komai ba na fita da sauri.

Daki na na wuce da sauri na rufe kofa sannan na zube a kan carpet din gaban gadon dakin na fara rera kuka. Kukan abubuwa da yawa. Kukan da ban san ranar da zan daina shi ba
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: Daki na na wuce da sauri na rufe kofa sannan na zube a kan carpet din gaban gadon dakin na fara rera kuka. Kukan abubuwa da yawa. Kukan da ban san ranar da zan daina shi ba

alamar an bude kofar dakin an shigo, ban
dago kai na ba amma a raina na san waye
saboda mu biyu ne kadai a cikin gidan,
besides, motsin wheelchair dinsa daban
yake da motsin tafiyar sauran mutane. Ban
juya na kalle shi ba amma nayi kokarin
sassauta kuka na tare kuma da kokarin goge
goge hawaye na. Ya jima anan a zaune yana
kallo na sannan yace "I knew it. Dana na san
kina nan kina kuka. But what I do not know
is kukan menene kike yi? Uhmm, fada min,
kukan me kike yi".
Na cigaba da goge fuskata da bayan hannun
rigata, ina jin yadda already fatar idon ta
kumbura. Ya sake tambaya,
"ina jin ki?
Kukan menene kike yi?" Nace "I want you to
get better. I need you to get better" yayi
shiru na wani lokaci sannan yace
"you know
it is not going to happen. Sai kuma menene
again?" Na girgiza kaina "shikenan dama.
Shine kadai abinda nake yi wa kukan" yace
"liar. You are also crying saboda maganar
auren ki. Haka ne?" nayi shiru banyi magana
ba. Ya sake tambaya ta "ba kya son auren
Mukhtar? Kina so a fasa yi da shi?" Nayi
shiru still ban ce komai ba. Ya zagayo
kujerar sa gaba na yace "Safiyya. Ina so inyi
miki aure kafin in tafi in barki. Idan na mutu
na barki babu miji this people will tear you
apart. Kuma dole in aura miki wanda ba za'a
yi bincike ba ballantana a tono abinda ya
faru da ke. Wannan ya bar ni da very limited da ke. Wannan ya bar ni da very limited
options. I gave you the options. And you
chose. Wanda kika zaba ba shi zuciya ta
take so ba, hi zuciya ta tafi yarda da ki auri
Mustapha. But you adamantly chose
Mukhtar. And now you are crying. Tell me
why".
Na dago ido na ina kalion sa "Daddy, me
yasa kake son Mustapha?" Yace "saboda a
hannuna ya tashi, ni na bashi tarbiyya.
Saboda mahaifiyarsa ce ta raine ki, ita ta
baki tarbiyya. And sometimes family means
more than blood. Sa'adatu will never harm
you. But I am not so sure about Ahmad" Na
dauke kaina gefe nace "you know what they
want" yace "and what makes you think
cewa su Ahmad ba the same thing suke so
ba?" Nayi shiru ban ba shi amsa ba sai ya
sake cewa "a rayuwa Safiyya, most of the
relationships if not all da zaki shiga, ko ta
auratayya ko business ko zamantakewa to
trade by batter ake yi, to get something you
have to give something. The best logic is ki
san abinda mutum yake so daga gare ki, and
then use that to get kema abinda kike so"
Nace "Amma Daddy Mustapha fa..." Yace
"he didn't do it. Ban san how many times
zan gaya miki ba. He didn't do it" nayi shiru
ban ce komai ba, bana son gaya wa Daddy
abinda Mustapha yayi, bana son inyi using
the only card din da nake amfani da shi
grin taming Mustapha.
Jin nayi shiru bance komai ba sai yace
"are Jin nayi shiru bance komai ba sai yace "are
you changing your mind or not?" Na goge
hawaye na tare da girgiza kaina "no. Am not.
Ina neman alfarma dai guda daya. Dan Allah
Daddy bana son komawa Nigeria. I want to
live here. Or somewhere else. Anywhere
that is not Nigeria",. Ya juyo yana kallona, sai
kuma ya juya kujerar sa yayi hanyar fita ba
tare da yace min komai ba. Har ya kai bakin
kofa sannan ya juyo yace min "about
Mukhtar, ko da ana gobe daurin aure ne in
kika chanja shawara let me know ni kuma
zan tsayar da maganar".
Ban amsa ba nima har ya fita, ban kuma bar
space a zuciya ta da zan yi tunani akan
maganar ba. Na riga na yanke shawara and I
am not going back on it, duk kuwa da zafin
da zuciya ta take yi min akan hakan. Yana
fita waya ta ta kama kida, na san waye tun
kafin ma in kalle ta dan mostly ya kan kira ni
by this time. Sai dai sam bana son daukan
wayar ta sa. Zuciya ta bata so. Sai nayi
murmushi ina mamakin rayuwa ta, yanzu na
gama ja in ja da Daddy a kan sa, akan nace
shi zan aura, amma kuma still zuciyar ba son
sa take yi ba.
4
8:00 PM
Har ta katse ban dauka ba sai da ya sake
kira sannan na dauka. Na saka wayar a
kunne na banyi magana ba yace "ko baccin
ne dai? Na ga alamar ke ba kya gajiya da
bacci" nace "na tashi, kawai dai yau na tashi
bana jin dadi ne" yace "ni kuma yau cikin jin bana jin dadi ne" yace "ni kuma yau cikin jin
dadi na tashi. Have you heard the good
news? In the next eight days you are going
to be my bride. Duk da dai su Daddy suna ta
insisting babu taron biki, but I want us to
have ko da yar walima ne haka in kin dawo
nija...
.." Nace "yaya Mukhtar, I am sorry, but I
don't want any walima dan Allah. And I also
don't think zan dawo Nigeria." Yace "why
not? Fiyya komai da ya faru ai ya wuce
kuma. Daga anyi daurin auren nan shi kenan
we will put everything behind us muyi facing
sabuwar rayuwar mu and the ways to build a
new family k0? Gashi ma Allah cikin ikonsa
we will soon have a child to start the family
with. Abeg, ki shafa min kansa ko kanta and
tell them they are already loved at home".
Abinda ya fada was supposed to made me
feel better amma sai naji raina ya baci dan a
lokacin bayan uban dan cikina babu abinda
na tsana sama da dan cikin nawa. Amma sai
na daure zuciya ta nace "kayi hakuri yaya
Mukhtar. I can't. Abun zai wuce physically,
but the trauma will always haunt me, and
the best thing to do idan mutum yana son
moving on from a traumatic experience is to
change environment. Idan na dawo Nigeria
ba zan iya bawa family na kulawar da suke
bukata daga gare ni ba" yace "kina ganin
zaki ke tunawa da shine?" Nace "not just
him, Zan ke tunawa da komai" amma a raina
na san babban abinda nake gudu a komawa
Nigeria shine Muhammad. A yanzu da na
dan saka distance a tsakanin mu gani nake
kamar na samu wata kariya daga ciwon son kamar na samu wata kariya daga ciwon son
sa, amma ina komawa Nigeria na san zanji
tamkar an rushe katangar kariyar ne, and
there is a chance na cewa zamu iya haduwa
da shi, and that would be a disaster.
A haka dai ya hakura ya bar ni amma bai ce
ya amince ba kamar yadda Daddy ma bai ce
ya amince ba, ya dai ce min zaiyi tunani a
kai.
Daga ranar sai na kara cigaba da lissafi na.
Ina lissafa ranar aiki na kuma ina lissafa
ranar daurin aure na. Safina kept calling me
har sai da na daina daukan wayarta wai taji
labarin daurin aure na and tana son mu
shirya wani abu special ni da ita tunda muna
da friends daya musamman yan secondary
school din mu. Sai da taga na nuna mata
bacin raina sosai sannan ta rabu da ni.
Mustapha ma ya kira ni ban dauka ba, sai
gashi ya turo min dogon message a
Whatsapp wai yana yi min fatan alkhairi and
he wants us to put everything behind us a
cigaba da zumunci, and whenever I need a
big brother he will be there for me. A karshe
ya kara da cewa duk sanda nake bukatar a
dan sassama min Mukhtar I should just give
him a call.
Ya rage kwana biyar daurin auren Safina ni
kuma nawa shida sai ga Mommy ta kira ni.
Na dauka na gaishe and she lost the words
to say to me, sai kuma ta kama fada "yanzu
wato da ban kira ki ba ke ba zaki taba
daukan waya ki kira ni ba ko?" Nace "kivi daukan waya ki kira ni ba ko?" Nace "kiyi
hakuri Mommy" ta cigaba "na dauka a ranar
da muka taho yarinyar nan a ranar zaki fara
nema na amma ke ko ajikin ki ma sai kika
cigaba da sabgar gabanki ko?" Nayi shiru
bance komai ba, ta cigaba "ance min nan da
six days za'a yi miki aiki. Kina shan
magungunan ki dai ko?" Na ce "eh ina sha"
amma a zahirin gaskiya rabon da insha
magani tunda ta bar kasar. Tace "good. Ki
kula da kanki. Ki kuma kwantar da hankalin
ki, kin san a haihuwa babu abinda ake gudu
irin hawan jini" na yi shiru ban ce komai ba
sai ta sake cewa
"ko ba ki auri Mustapha ba
still ke ya ta ce" nace "Nagode Mommy".
*Him*
Kwanakin sauri suke tayi a gurin Gidado, so
yake su tsaya, dan ya samu at least ya shaki
numfashi amma sun ki tsayawa and every
day there is something to do. Gidan su
already har ya fara cika da mutane
musamman saboda bikin biyu za'a hada,
gashi kuma bikin farko ne da za'a yi a gidan
na su. Wannan ya saka a dole ya rufe dakin
sa ya tattara ya koma gidan sa, gidan da aka
fara siya masa yanzu kuma da ya takura aka
sake masa wani.
8:00 PM
Babu shiri Haidar shima ya tattara nasa
kayan ya bishi, duk da hakan bai yiwa
Gidado dadi ba dan yaso ya samu these
days to himself dan in suka kare kuma shi
kenan zai shiga cikin sabuwar rayuwar da kenan zai shiga cikin sabuwar rayuwar da
bai ma san ta inda zai bullo mata ba. Yana
sane yaje ya kamawa abokansa da suka zo
gari musamman dan bikin hotel rooms duk
kuwa da cewa akwai wanna spare gidan
amma shi so yake ya zauna shi kadai. Haidar
din ma sai ya bude masa part din da ya
kamata ace shine nashi, shi kuma ya shiga
wanda ya shirya saboda Safiyya.
Ya san cewa hakan da yayi ba karamin
emotional damage zai jawo wa kansa ba
amma ya zabi hakan.
Babu komai na furnitures a gidan dan haka
sai katifu suka je dasu suka shimfida suke
kwana akai, sai kuma boxes din kayan sawan
da zasu yi amfani da su da sauran
abubuwan da zasu bukata. Kullum da safe
yake fita gurin hidimomin sa and they kept
his emotions on check har sai ya dawo gida
tukunna, shi farko ya dauka in ya gaji bacci
zaiyi saurin daukansa kamar yadda Ya
Amen ya gaya masa, amma kuma sai ya ga
shi ba hakan bane ba a gare shi. Ko ya gajin,
in ya kwanta sai dai yayi ta juyi, amma bacci
baya zuwa idanun sai gari ya kusa wayewa.
Kullum a ransa babu abinda yake yin bita sai
rayuwar sa da Safiyya, babu abinda yake so
irin ya fahimci abinda yayi missing, ya
fahimci inda hint din cewa tana da aure yake
wanda yayi missing a baya amma ya kasa
gani,
Except kin kai shi gidan su da tayi. She kept
on delaying and delaying giving all sorts of on delaying and delaying giving all sorts of
excuses. Farko excuses din nata akan cewa
tana gidan uncle dinta ne kuma uncle din zai
yi mata fada in ya ganta da saurayi because
yana tunanin cewa bata isa yin saurayin ba,
daga baya da ya fara nuna mata shi fa da
gaske aure yake son yi, aurenta yake son yi,
sai ta koma yi masa maganar rashin lafiyar
babanta and the fact that baya zama a kasar
sosai, and ranar nan da ya takura mata she
said bata son ta kaishi gurin uncle dinta sai
dai babanta, saboda uncle din yana son
hada ta aure da dan sa Mukhtar.
Ya san Mukhtar. Tun the second haduwar su
da Safiyya ya san Mukhtar, kuma tun a
lokacin jikinsa ya bashi cewa something was
going on at least a zuciyar shi Mukhtar din,
tun sanda ya ganshi din kuma yaji cewa
baya son sa. Amma kuma a zuciyarsa ya san
cewa kishi ne yake yi.
Ya san cewa kishi yana daga cikin
weaknesses din sa akan Safiyya, yana da
mugun kishin da har toro yake bawa kansa
sometimes, ya kuma san kishin nasa a
yanzu yana daga cikin abinda yake cin
zuciyarsa. The memory of her dauke da
cikin wani, knowing fully well abinda ya faru
kafin a samu cikin shine babban abinda yake
hana mishi bacci a yanzu.
A yau ma bai dawo da wuri ba sai late,
hopping to fall asleep as soon as possible,
yana shigowa ma da yay packing bai shiga
cikin gidan ba sai ya cire dogayen kayan. cikin gidan ba sai ya cire dogayen kayan
jikinsa ya bar singlet ya zagaya bayan gidan
yana jogging da niyyar karawa kansa gajiya.
A bayan ne kuma yaga wani guri da Safiyya
ta saka musamman ya ware mata bai yi
paving ba
"spices zan shuka a gurin, akwai spices din
da ba a samu sosai a kasuwa ko kuma ba
za'a samu fresh one ba, to gwara in samu
seeds din su in shuka da kaina in ringa
using".
Ya tsaya a gaban clearing din yana hakin
jogging din da yake yi. "damn you. Damn
you Safiyya" ya fada a fili, sannan ya wuce
da sauri ya cigaba da jogging din sa. Yana
cikin haka yani alamar an bude gate, ya san
Haidar ne ya dawo amma kuma baya son
kowa yayi masa magana a yanzu, dan haka
yayi sauri yayi kwana ya shige gidan ta kofar
baya ya shige dakin da yake kwana. Direct
toilet ya wuce ya kunna wa kansa shower ya
rufe idonsa yana jin dadin sanyin ruwan.
"'Komai zafi bana iya wanka da ruwan sanyi,
mura yake saka ni"
Yaji muryar ta kamar a yanzu take gaya
masa, Ya tuna da amsar da ya bata a
lokacin, "Kar ki damu, zan koya miki ne. Ita
kan ta murar sai ta hakura ta bar mu".
Ya fita daga shower din ya goge jikinsa,
yana kallon fuskarsa a mirror din toilet din, yana kallon fuskarsa a mirror din toilet din,
"Da wata farar fuskar ka anan" yayi
murmushi. "Burge ki tayi"
4
8:00 PM
Ya fito daga toilet din ya saka pajamas
sannan ya karo karfin AC ya kashe fitila yayi
addu'a ya kwanta, hoping to center his mind
on something important, anything apart
from Safiyya, amma babu abinda ya gani a
idonsa sai Safiyya da ciki a office din sa.
Babu kuma abinda yake son sani a lokacin
sai abinda Safiyya take yi a wannan lokacin,
babu abinda mind dinsa take saka masa sai
different scenarios a abinda Safiyya take yi
din. Ya mike tsaye ya kara wa kansa fanka
sannan ya koma ya kwantatare da zagaye
kansa da pillows, few minutes after that
kuma ya sake mikewa zaune ya jawo
wayarsa ya nemo number din Safina ya kira
without realizing cewa karfe sha biyu ne na
dare har da rabi.
Sai da ta dauka sannan yayi realizing
mistake din sa. "Hello Habibi. Ba ka yi bacci
ba?" Ya matsar da watar daga fuskarsa yace
"shit!" a hankali cikin jin haushin kansa.
Sannan yace "hello? Uhmm, I think I made a
mistake ba wannan number din zan kira ba"
ta danyi shiru sannan tace "wa za ka kira to?
By this time?" ya fara tunanin karyar da
zaiyi, another of his weakness shine karya,
bai iya karya ba kwata kwata. Yace "my
friend, akwai wani friend dina Sahabi shi zan kira yanzu" ta sake cewa "by this time?"
Yace "eh, baya bacci da wuri, nima haka"
tace "ko dai ita zaka kira?" Ya dan bata rai
"wa kenan?" Tace "your ex da ka fada min.
Ko ita zaka kira Allah ya sa ka kira ni" ya
danyi shiru sannan yace "I wish I can call
her, there is nothing da ba zan iya bayarwa
ba a yanzu to be able to call her. But she
blocked my number. And beg me not to find
another way to contact her. So to answer
your question, ki kwantar da hankalin ki, ba
ita zan kira ba".
Tace "okay. Because I don't want to ruin the
memory of the first time you call me da
dare. Ba na son sunan wata ya shiga cikin
memory din. It has always been a dream of
mine. In ga ina waya da kai irin yadda
yammata da samari suke y" yace "I told you
abokina...." Tace "right. At least let me
pretend ni ka kira. And since you called ya
kamata mu danyi magana ai ko? At least tell
me something about you da kake ganin ya
kamata in sani, maybe about your friends or
family ko aikin ka, anything, just talk to me "
yace "okay. Let me start with the things I
like, I like honesty, na tsani karya. I like tsafta
a lot. Bana son hayaniya, bana son mita,
bana son tsegumi ma'ana telling me
something that do not concern me. And
most importantly, I love my family, a lot"
tace "yauwa, about the family, ban san su
ba sam in banda Mufida, ita ma kuma a
waya ne kadai ko hoton ta ban taba gani ba,
ya kamata in san su ko?" Yace "zaki san su
ai. A hankali, But the immediate family basu. al. A hankali. But the immediate family basu
da yawa, daga Mama sai Abba sai Haidar
and then Mufida. I am the eldest. Akwai
cousins da yawa, I can't list them all. You will
get to know them watarana" tace "haka ne.
And your friends, aside Sahabi" yace "waye
Sahabi?" Tace "Sahabi dai da zaka kira
yanzu" yace "ohh that Sahabi, Sahabi my
friend. Yes, akwai Sahabi and the rest. Zaki
san su suma later. Now, let me call Sahabi
kafin yayi bacci".
Tayi ajjiyar zuciya "okay, shikenan. At least
we are one step ahead. Good night Habibi".
Sai dai daya ajiye wayar, maimakon ya koma
ya sake gwada baccin sai ya tashi ya zauna
ya dauko takarda da biro a cikin takardun da
Abba ya bashi zai yi cike cike na sabon aikin
da zai fara, ya juya bayan takardar kawai ya
kama zane a jiki, zanen fuskar Safiyya. Sai
da ya gama zana ta tas kamar zaka kira
sunan ta ta amsa, sai kuma ya dukunkune
takardar yayi jifa da ita ya koma ya kwanta.
Da safe bai tashi da wuri ba dan baiyi bacci
mai nauyi ba sai bayan sallar asuba, ya
manta cewa a ranar zasu fita da Abba
maganar chanjin aikin sa. He is going to take
over some parts of managerial work na
Company din Abba bayan bikin sa. Sai dai
bai tashi ba har sai da Abban yazo gidan da
kansa daukan sa kamar yadda suka shirya,
ya kuma shigo har cikin gidan har dakin da
yake kwance ya same shi yana bacci,
takardar da ya gani a kasa ya sunkuya ya. takardar da ya gani a kasa ya sunkuya ya
dauka ya warware. Sai ya samu guri a gefen
katifar da Gidado yake kai ya zauna yana
kallon zanen yarinyar da yake hannunsa.
8:00 PM
Gidado yayi juyi sannan ya bude jajayen
idonsa ya dora su akan Abba, sai kuma ya
karasa bude don da sauri tare da mikewa
zaune yana shafa fuskar sa a kokarin kore
saurin baccin da yake kansa "Abba ka
shigo? Ina kwana" Abba ya bishi da kallo
sannan ya sake kallon takardar hannun sa.
Sai lokacin Gidado ya lura da takardar, ya
kara gyara zamansa yana shafa kai tare da
kallon takardar da gefen ido.
Abba ya nuna masa zanen tare da tambayar
sa "Safiyya?" Gidado ya gyada kai bai ce
komai ba. Abba ya nannade takardar ya ajiye
a tsakanin su yace "ba ka son waccan
yarinyar, zaka aure ta ne kawai saboda ni da
mahaifiyar ka muna son kayi aure" babu
alamar tambaya a cikin maganar dan haka
Gidado bai bada amsa ba. Abba ya cigaba
da cewa "abu na farko da na san ka riga ka
sani shine we only want what's best for you.
And right now, mantawa da wannan yarinyar
shine the best thing for you" ya fada yana
nuna zanen Safiyya with bitterness in his
voice, abinda yake nun irin haushin Safiyya
da yake ji a ransa. Ya cigaba da magana,
"mun yanke shawarar aure shine babban
abinda zai taimaka maka wajen mantawa da
ita maka kayi moving forward. Sai dai daga
ni har mahaifivar ka are not perfect, kuma. ni har mahaifiyar ka are not perfect, kuma
bama ganin gaibu, zata iya yiwuwa abinda
muka zaba maka ba shine alkhairi a gare ka
ba, amma ni na san wanda yake perfect
wanda kuma ya san gaibu, Allah. Ina son zan
baka wani assignment, idan kayi shi dai dai
zaka samu reward mai girma. Ina so kuma
inyi maka wani alkawari. A cikin kwanakin
nan da suka rage kafin daurin auren ka, ina
so kayi istikhara, idan har kafin daurin auren
ka cigaba da jin a ranka cewa still ba ka son
aure to ka gaya min, ko da kwana daya ya
rage zan dakatar da abin domin ya tabbata
ba alkhairi bane ba. Amma idan kaji a ranka
cewa ka amince kana son auren yarinyar, to
sai mu cigaba da shirye shiryen mu har mu
tabbatar da faruwar abin".
Ya mike tsaye yana kallon sa yace "ka tashi
ka shirya, your new job awaits you ", Gidado ya karbi shawarar Abba sosai, dan
tun da suka yi maganar ya dukufa da yin
adduoin neman zabin Allah. Babu dare babu
rana. Ya kuma cigaba da shirye shiryen duk
da suka kamata na bikin. Yan'uwansa sunzo
na kusa da na nesa, maza da kuma mata. Da
yake Abba da Mama first cousins ne sai ya
zamana yan uwan duk daya ne babu
banbanci, duk kuma treatment daya ake
basu.
Yan'uwansa samari da suka zo gari suka
kuma fahimci a gidan da yaje ya boye kansa
duk sai suka tattaro suka dawo gidan,
sa'annin Gidado suna bangaren da yake
while sa'annin Haidar suma suka tare a
bangaren da yake. Gidado bai ji dadin haka
ba saboda an takura masa an hana shi zama
yayi hira shida zuciyarsa, shi da safiyyan shi.
Sai dai kuma a wani bangaren yaji dadin
hakan dan cikin kwanaki biyu kacal sai gashi
yana hira da dariya sosai a cikin su. Wani
lokacin idan suka nutse a cikin hira har
mantawa yake yi da cewa wai aurensa ake
yi, kuma wai baya son yarinyar da zai aura.
Sai dai kuma yana iyakacin kokarin sa gurin
danne wa dan baya son yanuwansa su
fahimta har suyi ta yayata maganar a cikin
dangi. Sai dai kuma yanuwan are making it
extra difficult for him. Casually someone
would ask him "ina yarinyar nan kuma da ka
susuce akan ta kwanan baya?" His answer
to that question was always "Allah yayi mata
rasuwa" daga haka ba sa sake tambayar sa.
In wani ma ya dauko tambayar sai a samu In wani ma ya dauko tambayar sai a samu
wani ya hana shi dan kar su taba wa angon
feelings din sa. Sometimes kuma su kan
tambaya "wannan gidan na ka ai yafi
wancan girma Gidado, me ya sa ka chanja?"
And shi kuma ya kan amsa musu da cewa
"amaryar ce tafi son wancan". Alhalin ita
amarya ko gain gidan ba ta taba vi ba sai
da masu yi mata jere suka je suka yi suka
dauko mata pictures da videos.
Gidan da za'a kai amaryar mai kyau ne, dan
sosai iyayensa suka nuna masa gata a siyan
gidan kamar yadda suke nuna masa gata a
komai. Part dinsa daban na matar daban
sannan a waje kuma akwai bangaren baki
maza sannan da part din ma'aikatan gida
(boy's quaters). A bangaren sa akwai
bedrooms biyu da parlor, a nata bangaren
akwai bedrooms uku da parlor. Part din
bakin kuma parlor ne karami da dakuna
biyu.
Kamar yadda iyayen ango suka yi kokari
wajen kure adakar su akan gidan Gidado
haka bangaren amarya su ma suka yi nasu
kokarin, dan duk dakunan da suke part dinta
babu inda ba'a cika shi da kaya ba, kaya
kuma na gani na fada wa da suka yi dai dai
kuma suka dace da tsaruwar gidan. Abin har
sai da ya bawa dangin angon mamaki, dan a
binciken da suka yi wa iyayen amarya basu
samu labarin cewa suna da irin wannan
kudin ba,
A bangaren amarya tun a week to bikin A bangaren amarya tun a week to bikin
Mommy ta tafi can Katsina suka cigaba da
kammala shire shiryen su, duk wani shiri da
za"a yi wa amarya na gyaran jiki anyi wa
Safina shi, ita kanta ta san tana da kyau, ta
kuma shirya siye zuciyar angon na ta da
wannan kyan nata da kuma duk kan wata
kissa da kisisina da Allah ya halicci mata da
ita. Ta san cewa akwai challenge a gabanta
amma kuma ta shirya karbar sa hannu
bibbiyu dai har zata samu muradin
zuciyarta. Ta yarda da kalmar hausawa da
suke cewa mahakurci mawadaci.
Mommy tayi mata shirin duk da akeyi na
gyaran amare dan taimaka musu wajen
sauke hakkin aure da zai hau kansu, amma
Mommyn ba ta san cewa ita ma da kanta
Safinar ta gama siyan duk wadannan kayan
har ma da wadanda suka fi na Mommyn. A
shirye take tsaf da yin amfani da dukkan
baiwar da Allah yayi mata wajen ganin ta
mallaki Habibin na ta.
5
+ 1 4:15 PM
anar Lahadi ta tafi garin Abuja. A ranar ne
kuma bayan kiran wayar angon sau ba adadi
kamar yadda ta saba kullum ba tare da kiran
ya shiga ba sai ta tura masa message. "Na
shigo Abuja, Dan Allah ka zo in ganka, Ina
gidan Hajiya" Sakon ya shigo masa ya
karanta ya rufe ya ajiye,
A ranar da ya rage saura five days daurin
aure ne gidan da angon ya ke ciki ya kara. aure ne gidan da angon ya ke ciki ya kara
cika fiye da kullum, yan uwan sa da suka 20
gari suma sun gayyato abokan su da suke
gari, wasu abokan kuma sun gayyato nasu
abokan. Gidan ya zama kamar wani dan
karamin biki ake yi amma na maza zalla.
Mama kuma ta daure musu gindi ta hanyar
aiko musu da kulolin abinci kala kala. Daga
nan sai hira ta balle, aka fara zancen aure da
rayuwar cikinsa da challenges din sa, masu
auren ciki suna baje fasahar experience din
su, yayin da samari suka baje kunnuwa suna
daukan darasi. Wannan ya sa angon ya
zame ba tare da sun sani ba ya fice ya bar
musu gidan. Sai da ya shiga motar sa kuma
sannan ya fahimci bashi da gurin zuwa, dan
duk friends din sa da zai iya zuwa gurin su
suna cikin gidan sa, a lokacin ne sakon
Safina ya sake shigowa. "Na gama abinda
zanyi a Abuja. Gobe aka ce in koma. Dan
Allah ka shigo".
Ya rufe idonsa yana tunani for some
seconds sai kuma ya bude ya kira number
din ta. Tana dauka yace "gani nan zuwa" bai
jira amsa ba ya katse kiran. Mintuna kadan
suka kaishi kofar gidan, mai gadi ya taho da
sauri da fara'a a fuskar sa amma sai Gidado
ya bata rai tare da daga masa hannu alamar
baya bukatar zuwan sa, sai da mai gadin ya
juya sannan kuma sai yaji babu dadi a ransa
tunda mutumin bai yi masa komai ba. Ya
dauko wayarsa ya sake kiranta "ina waje"
yace tare da sake ajiye wayar.
Few minutes sai gata ta fito. Jikinta sanye Few minutes sai gata ta fito. Jikinta sanye
da hijab fuskarta babu kwalliya. Ta bude
kofar gaban motar ta shiga ta zauna, sai ya
dauke kansa yana jin haushin ta zauna a
seat din Safiyya. Amma kuma ai shi ya kira
ta. And only God knows me Safiyya take yi
with her husband, why won't him enjoy
himself too?
Ta fara mishi magana "har na fitar da rai na
dauka ba zaka zo ba. But now I am glad
tunda kazo" ya juyo yana kallon ta fuskarsa
a matukar daure yace "me yasa kike
nemana?" Tana kallon sa tace "what's with
that face? Ko nayi wani laifin ne kuma ban
sani ba, I just wanted to see you kuma
banga abin laifi dan ina son ganin ka ba".
Yace "what's wrong with my face? I thought
ita kika gani kika ce kina so" ta sunkuyar da
kanta kasa fuskarta tana nuna damuwa tace
"na san nina ce ina son ka ba sai ka goranta
min ba. Kawai naga ranka a bace ne. Ni face
din da nayi falling in love with is always
happy always smiling" yace "you better get
use to the unsmiling face. Because you are
going to see a lot of it" suka yi shiru gabaki
daya, sai da aka jima sannan da dago kai
tace masa "dama nazo gari ne zanyi kunshi
da saloon, and da akayi min kunshin sai na
ga yayi kyau sosai, and I thought ya kamata
kai zaka fara gani, I never thought hakan zai
zama laifi".
Yace "are you telling me kin taho tun daga
Katsina zuwa Abuja kawai dan kiyi kunshi?
Duk masu kunshin da suke Katsina ba zasu. Duk masu kunshin da suke Katsina ba zasu
yi miki ba?" Ta dago kai tana kallon sa tace
"actually, na fadi haka ne kawai a gida dan
su barni in taho, Mommy like classy things
and ta san a Abuja zan fi samun taste din ta,
but in reality I just wanted to get away from
her" yayi mamakin jin haka yace "why?"
Tace "fada. Tun da taje Katsina take yi min
fada. She is not happy with this marriage
saboda bata san ka ba, she kept
complaining cewa bata san sanda muka
hadu ba ballantana sanda muka saba har
zamu yi aure. Farko bata kasar, da tazo
cewa tayi sai an daga. Da kyar ta yarda za'a
yi din" tayi shiru tana jujuya hannunta
sannan tace "she said you don't love me.
Tace ko waya bata ga muna yi ba. There is
no love vibes at all".
Ya juya fusakarsa yana kallon window, sai
kuma ya juyo yace "you know our
agreement. And you agree with my
conditions" tace "yes, I know. And ba
complain nake maka ba. I just need a little
bit of gesture from you. At least make it
easy for me". Yace "let me ask you a
question.
5
4:15 PM
Why do you agree to this? Me yasa kika
saka kanki a wannan situation din?" Tayi
shiru tana tunani sannan tace "I love you,
That is all that I know, Kuma na san I am an
easy going person, bani da matsala, You
may not love me know saboda yarinyar da
kake so, but eventually you will fall in love. kake so, but eventually you will fall in love
again. And the easiest way to make you fall
in love with me is to marry you. Yanzu misali
ita yarinyar da kake so din, I don't want to
know her name, idan da zaka samu chance
din auren ta even though bata son ka, won't
you take the chance?" Yayi shiru yana
tunani, sai kuma yayi sauri ya kawar da
tunanin daga ransa yace "she loves me, so I
can't relate to that" tace "she loves you and
she left you?"
Bai amsa ba sai ya dauke kansa gefe yana
kara jin haushin ta, amma kuma yasan
abinda ta fada gaskiya ne, shi kansa kuma a
yanzu bashi da tabbas din in Safiyya tana
son sa.
Suka sake yin shiru a motar sannan yace "if
that's all. Zan koma. I have things to do" tayi
ajiyar zuciya "Okay. Nagode da ka samu
damar zuwa. Ina neman alfarma amma guda
daya. Please ka bari in ringa kiran ka. At
least saboda hankalin Mommy ya kwanta"
ya bata
pan't you call someone and
pretend cewa da ni kike? I am a little bit
busy for phone calls" ta dago ido tana kallon
sa, kawai sai yaga hawaye yana bin fuskarta,
ta saka hannunta da ya sha kunshin amare
yayi kyau a farar fatar ta ta goge hawayen
sannan tace "okay, Na fahimta, Thank you",
Ta bude kofa zata fita sai kuma yaji babu
dadi a ransa yace "Safina wait" ta dakata
amma bata juyo ba sai dai yana jin alamar
kuka take yi yace "I am sorry, Okay, Zamu ke. kuka take yi yace "I am sorry. Okay. Zamu ke
yin waya. Sai menene kuma kike so" ta juyo
hawaye yana cigaba da zuba a fuskar ta
tace "at least stop being mean to me. Ko
baka nuna min soyayya ba ka daina
wulakanta ni. It hurts a lot. You have no idea
how much I have sacrificed for this
relationship. The least you can do is to be
nice to me".
Bai sake magana ba ta fita daga motar ta
rufe masa kofa. Sai da yaga ta shiga gida
sannan ya tayar da motar ya tafi yana jin
zuciyarsa duk tayi masa nauyi. Baya jin
da din yadda yake treating yarinyar amma
baya iya hana zuciyarsa gaya mata abinda
yake cikin ta. Kuma kamar yadda ta fada
masa, ko da bai so ta ba the least he can do
is to treat her nice. Treat her kamar yadda
yake treating sauran mutane, or more.
Albarkacin tarin soyayyar da take yi masa.
Gidan Abba ya wuce, ya tarar ana kokarin
shiga sallar magrib sai ya bisu suka yi sallar
itare
ayan sun fito daga masallacin ya
samu ya shiga ciki ya gaishe da sisters din
Mama da ya gani a parlor sannan ya wuce
cikin bedroom dinta ya gaishe ta itama. Har
ya tashi zai tafi sai ta tambaye shi ko akwai
abinda yake bukata yace a'a, sai kuma ta
sake tambayar sa "ya kuke ciki da Safina
kuwa? Kuna waya ma kuwa?" Ya dawo ya
durkusa yana shafa kansa yace "yanzu ma
daga gurinta nake. Tazo gari taje gurin
kunshi" Mama tayi murmushi, yaga alamar
jin dadin hakan a fuskarta sannan tace "to jin dadin hakan a fuskarta sannan tace "to
madalla, hakan yayi kyau sosai. Allah yayi
maka albarka" yace "Amen" a ransa yana
jin dadin abinda tace din sosai.
Tun a mota kafin ya bar gidan ya cire wayar
sa daga do not disturb din da ya saka ta
saboda Safina. Washegari da safe da ta kira
shi sai kiran ya shiga ta sanar masa cewa
zata koma shi kuma yayi mata fatan alkhairi.
Da ta sauka a Katsina ma ta sake kiransa ta
gaya masa cewa ta isa, yayi mata sannu,
sannan reluctantly yace ta gaishe masa da
Mommy.
Daga nan suka fara magana, sama sama,
yana replying messages dinta in ta kira
kuma yana amsawa. A haka har ta turo masa
hoton kunshin da aka neme shi musamman
dan a nuna masa amma yaki gani, and he
replied with "yayi kyau".
Kamar yadda aka tsara ranar alhamis aka
fara biki
akayi kamun amarya a can katsina
a gidan wan babanta. Mommy ta gaiyaci
mutanen ta sosai sun je anyi komai da su,
yan uwan ango ma an ware representatives
sunje anyi kamun a gaban su a inda kuma
suka samu tarba ta musamman daga gurin
Mommy dan sai da ta tabbatar ta fitar da yar
tata daga kunya a idon su.
A
4:15 PM
A ranar kuma aka shirya za'a yi kamun ango
shima a nan Abuja, Sai dai kuma, tun. tun a
safiyar ranar ne da samari yanuwan ango
suka tashi a gidan da suke zaune tare da shi
sai suka neme shi suka rasa, sai maigadin
gidan ne ya gaya musu cewa tun assubar
fari ya fice daga gidan a motarsa. Aka yi ta
kiran wayar sa kuma bata shiga. Wasa wasa
har rana ta yi sosai babu ango babu
labarinsa. Tun suna boyewa suna cigaba da
bincike su kadai har suka sanarwa da iyaye
halin da ake ciki. Ango ya gudu. Ana ta kiran
wayarsa kuma tana ta ringing amma baya
dauka. Farko duk wanda aka gaya wa cewa
ango ya gudu sai yayi dariya thinking cewa
wasa akeyi, sai daga baya kuma sai a
fahimci cewa babu wasa a cikin lamarin.
Neman duniyar nan akayi wa angon aka rasa
shi har lokacin kamun yayi.
A gidan kakannin su aka tsara cewa za'a yi
kamun. Amma rashin gain angon ya saka
aka tattaro aka dawo nan gidan su angon
ana ta lissafin yadda za'a yi, auntyn sa
Maimoon sai dariya take yi dan ita dai ta san
Muham had Gidado ba zai bata ba kamar
wani key din mota, yayin da Aunty Amina ta
dage sai fada take yi akan ya basu kunya
sun tara mutane ya gudu ya bar su, da ya
san ba zai tsaya kamun ba ai da sai ya fada
musu da wuri su san abin yi. Hafsat kuwa sai
kallon su kawai take yi dan dama ita bata ga
amfanin kamun nan ba, daga baya dai da
taga magana taki ci taki cinyewa sai ta kira
Al'ameen ta zare masa ido tace sai ya fadi
inda Gidado ya shiga, yayi ta rantse rantsen
cewa shima wallahi bai sani ba, sai da ta. cewa shima wallahi bai sani ba, sai da ta
fahimci da gaske yake sannan ta rabu da
shi.
Ana cikin haka Abba ya shigo, ya zauna yana
binsu da kallo yana murmushi. Amina ta
kalle shi tace tabbas yasan inda Gidado
yake tunda bai nuna ya damu ba. Yace "to ni
akan me zan damu? Tsakanin ku ne da shi ni
babu ruwa na. In kuka kama shi duk abinda
kuka ga dama kuyi masa" sai kuma ya saka
hannu a aljihu ya dauko wayarsa ya kira
number din Gidado, shi ya san indai da ran
Gidado da kuma lafiyar sa babu yadda za'a
yi ya kira shi yaki dauka.
Yana kiran nasa kuwa ya dauka din, direct
yace masa "kana ina?" Gidado yayi shiru
kamar ba zai amsa ba sannan yace "ina daki
na" yace "wanne dakin?" Yace "dakina na
gidan mu". Abba yayi shiru yana jin yadda
muryar Gidado tayi kasa sosai, and he can
almost feel halin da zuciyar dan nasa take
ciki. Yace "iyayenka suna neman ka zasu
kama ka" Gidado yace "Abba ni da ba
criminal ba me nayi da za'a kama ni?" Abba
yace "tsakanin ku ne wannan. Ni dai yanzu
ka ban amsa ta. Za'a yi ko ba za'a yi ba
mu?"
Daga Gidado har abban nasa sun fahimci
cewa ba wai maganar kamu suke yi ba
yanzu, Gidado ya sake yin shiru. Abba yace
"yau kadai ta rage maka" still bai ce komai
ba, Abba yace "ina jin ka" Gidado yace a
hankali "za'a yi. Na amince ayi". hankali "za'a yi. Na amince ayi",
Daga nan Abba ya katse wayar ya juya yana
kallon yan'uwan nasa da suka saka shi a
gaba suka tsare shi da ido. Ya kalli Amina
yace "na ga kin damu dai da cewa sai kin
jika yaron nan da nono, me zaki bani idan na
gaya miki inda yake?" Tayi shiru tana tunani
sai kuma tace "in dai ka gaya min inda yake
daga yau zan dinga gaishe da matarka ina
ce mata yaya" duk suka kwashe da dariya.
Shekara da shekaru dama suna wannan
rigimar tsakanin Amina da Zainab. Zainab
kamar kanwa take a gurin Amina amma
kuma mijinta kamar Yayan Amina ne (if you
know you know ») dan haka kowa a cikin
su ya dage lallai sai dayan ya bashi girma.
Abba ya mike tsaye yace "yana dakin sa"
sannan ya fice ya bar musu gidan. Ai kuwa
Amina ta sunkuci turaren da ta taho dashi
tayi dakin Gidadon sauran yan'uwa suna
binta, taje kuwa tayi ta gudun kofar duniyar
nan yaki budewa sai da Mammy tayi masa
magana tare da yi masa alkawarin ba za'a
zuba masa nono akai ba sannan yayi
Ami
la
A bangaren Gidado ranar tun da assuba
daya tashi ya yanke shawarar amsar da zai
bawa Abba, Saboda shine abinda yaji
hankalin sa yafi kwanciya dashi, bawai dan
yaji a ransa yana son Safina ba, but yaji a
ransa cewa auren shine abinda ya dace
dashi, shine abinda hankalin sa ya kwanta
dashi a wannan lokacin, The decision made him sad but free at the
same time. Sad that he will have to made
the final acceptance of the fact that Safiyya
ta bar shi har abada, that his life has
changed forever. Wannan yasa ya lallabo ya
shigo gidan su ya shige dakin sa ba tare da
kowa ya ganshi ba, making sure cewa ya
boye motarsa a inda ita ma ba za'a ganta
ba. Farko kwanciya yayi yayi baccin sa sai
azahar ya tashi yayi sallah sannan ya kama
yin aikin da yazo dakin da niyyar yi, aikin
tattare duk wasu kaya nasa da duk wani abu
nasa da yake da dangantaka da Safiyya,
including his phone and his laptop da suke
cike da hotuna da pictures dinta, ya hada su
ya zuba a wata locker ya rufe.
A binciken nasa ne ya dauko wata rose
flower single stem da Safiyya ta taba bashi.
Ya tuno lokacin da ta bashi din da kuma
dalilin da ya sa yake ta ajjiye da ita.
Suna tafiya ne ranar nan a hanya kamar
kullum yana yi mata korafin har yanzu bata
kai shi gidan su ba, kar yaje ayi mata miji a
gidlan su a raba shi da ita tunda ba'a san shi
she kept telling him cewa ba za'a iya
raba su ba amma a karshe yace dai shi
bama shi da tabbas din tana son sa da
gaske ba wasa take yi masa da hankalin sa
ba, suna maganar ne tayi ta tsinkar flowers a
jikin bishiyoyi tana hadawa, sai da ta tara da
yawa sannan ta cire ribbon din data daure
gashinta da shi ta daure flowers din da shi ta
bashi, tace symbol ne na son da Safiyya
take wa Muhammad, Yaji dadi sosai kuma ya. take wa Muhammad. Yaji dadi sosai kuma ya
karba, but He jokingly said "wannan ai gaibu
ne, ana jima wa zasu yi wilting su bushe su
mutu. I need something that is a forever
thing. Wanda zai nuna min matsayina is a
forever one a gurin ki. Something like zuwa
gaishe da Daddy",
A week after that, a jewelry company
delivered that rose to him. Single stem ne na
kyakkyawar red rose flower. An nannadeta
da transparent plastic sheet. A jikin sheet
din anyi rubutu da golden color in her own
handwriting.
Muhammad,
This feeling is a forever thing.
Your's
Piya
Amma abinda ya saka shi mamaki a lokacin
shine kasancewar jewelry company ne suka
yi delivering sakon. Sai da ga baya ya
fahimalalili. A kasan rose din, dan box din
da aka zura stem din rose din a ciki, was
made of gold, pure gold molded into the
shape of a heart with their initials scribbled
on it "MS".
It was too much of a gift da yaji a ransa
cewa bai kamata yayi accepting ba, that
gold is a fortune, Ya tabbatar a gida ba'a
san tayi wannan kyautar ba, Amma kuma he. san tayi wanna kyautar ba. Amma kuma he
so much love it da ya kasa mayar mata.
Wannan ya sa ya boye ta a inda yasan babu
wanda zai ganta da niyyar in sunyi aure sai
ya bata abinta.
But now it is never going to happen. Sai ya
samu kansa da jujjuya rose din a hannun sa
yana wondering me zaiyi da iya yanzu. A
karshe sai ya koma kan gado ya kwanta
rigingine ya dora rose din akan kirjinsa ya
rufe idonsa. Yana jin wayarsa tana ta kara,
kuma a ransa ya san cewa nemansa ake yi
amma haka yayi ta kwanciyar sa, sai dai
damuwar sa bata saka a ransa yaji cewa ya
fasa yin auren ba. A haka akayi la'asar ya
tashi yayi sallah ya koma ya kwanta,
deciding cewa ba zai je gurin kamun sa ba.
Duk wadanda suke kiransa yana gani, kuma
ya yanke shawarar ba zai dauka ba. A haka
har wanda ba zai iya kin daukan wayar ta sa
ba ya kira shi. Ya dauka, ta tambaye shi
game da decision dinsa kuma ya gaya masa
amsar.
Bai jima da ajiye wayar ba yaji bugun kofa da
kuma muryar Aunty Amina tana mishi
magana
filatanci "na san kana ciki, ka
bude kofar nan" ya tashi zaune yana dafe
kansa, Suka cigaba da hayaniya da kuma
bugun kofar. Bai ce musu komai ba sai ya
tashi ya kammala adana dukkan kayan da
yake bukatar adana wa including the forever
rose sannan ya tsaya a bakin kofar, a lokacin
yaji muryar Mammy tana masa magana, Yayi
murmushi ya amsa mata da fulatanci. murmushi ya amsa mata da fulatanci.
"'Amma banda nono za'a zuba min" tace "eh
banda nono" yace "kinyi alkawari?" Tayi
dariya tace "nayi alkawari" sannan ya bude
kofar, yana budewa suka feshe shi da
turaruka kala kala sannan aka dauki guda.
Duk da cewa turarukan sunyi masa karfi aka,
amma sai ya samu kansa da yin murmushi
yana jin dadin gain iyayen nasa cikin farin
ciki.
6
4:15 PM
Zuwa dare sai gashi yana hira a cikin su
harda dariya, ranar gabaki daya familyn
anan suka ci abincin dare sannan suka raba
dare suna hira, sai da bacci ya fara cin karfin
sa sannan ya zame jikinsa ya koma dakinsa
ya kwanta acan.
Da safe ya tashi da wuri kamar yadda aka
tsara ya shiga wanda, saboda da wuri zasu
tafi gurin daurin auren, yana fitowa daga
wanka da bathrobe a jikin sa sai ya ga Mama
a zaune akan gadon sa da kayan sawa na
maza a hannunta tana fesa turare a jiki. Ya
rissina ya gaishe ta yana jinsa wani iri
saboda
bu kaya a jikinsa amma sai yaga
ita ko an xinta, Ta mika masa kayan hannun
ta, fuskarta dauke da alamar damuwa, tace
."ga kayan da zaka saka nan. Dan banga ka
tanadi kayan sakawar yau ba" ya karba tare
da yi mata godiya, bata amsa ba sai tace
"kayi sauri ka shirya, baban ku har ya
shirya" ya ce "to" amma sai ua cigaba da
tsaiwa da kayan a hannun sa tunda dai ai ba
zai saka kava a cabanta ba, zai saka kaya a gabanta ba.
Ta mike a hankali kamar bata son fita. Har
takai bakin kofa sai kuma ta juyo tana kallon
sa tace "Muhammad?" Ya amsa, sai tace
"are you happy?" Yayi shiru yana kallon
damuwar da take rubuce a fuskar ta sai ya
girgiza kansa yace "no, I am not happy
Mama. But I am contented, alhamdulillah"
tace "good. That's a good start. Allah yayi
maka albarka".
Sai da ta fita sannan a hankali yace "Ameen
Mama"
Ya shirya ya saka kayan da Mama ta bashi.
Farin yadi ne tas da akayi wa aiki mai kyau
kalar ruwan toka mai haske, wanda ya dace
da hula da takalmin da ta ajiye masa. Ya
tsaya a gaban madubi yana kallon yadda
yayi kyau, shi kansa ya san yayi kyau ba
kadan ba. Ya tuna maganar Safiyya "You will
look so good in white"
Sai yayi murmushi. "Good bye Piya".
Daga nan ya juya ya fita tare da rufe kofar
dakin, kna
wing he will come back a changed
man, al
tried man. Maybe even a happy
man. Abinda bai sani ba shine a yanzun ne
zai bude babi mai cike da rikici da sarkakiya
a rayuwar sa, Yanzun ne matsalolin zasu
fara,
*Her
Ranakun gudu suke yi, musamman idan ina. Ranakun gudu suke yi, musamman idan ina
lissafa su a matsayin kwanakin da suka rage
a daura min aure da Mukhtar, amma kuma
lakaki suke yi idan na kalle su a matsayin
ranakun da suka rage ayi min aiki a raba ni
da abinda yake ciki na.
Duk shire shiryen aikin sun kammala a
asibitin da za'a yi, sun dauki dukkan vitals
dina sun tanadi dukkan abinda suke ganin
zan bukata. Sun kuma tanadi dukkan abinda
babyn da za'"a ciro zai bukata tunda zai
zamanto premature ne kuma zai bukaci
kulawa ta musamman. Yayinda ni kuma na
kammala dukkan shiryen shiryen bayar da
babyn kamar yadda na riga nayi niyya.
Sharuda na sune bana son ganin shi, bana
son Daddy ya ganshi, bana son kuma in an
samu parents din da suke son sa a basu
wani information da ya shafe ni ballantana
har nan gaba yayi amfani da information din
gurin sanin ko ni wacece.
A gida kuma kullum muna cikin rigima da
Daddy, muyi rigima yayi fushi ya sauko da
• kansa ko kuma ni inyi fushi ana jima wa
kum
sauko inje in bashi hakuri. Duk da ya
amine da maganar Mukhtar amma yaki
hakura da kokarin chanja min ra'ayi na.
Sannu kuma har yanzu bai yarda da magana
ta ta cewa ba zan koma Nigeria ba. He kept
saying akwai plans din da ya shirya min in na
koma Nigeria, But he wouldn't say what.
Mutanen kadai da nake samun fahimtar juna
da su sune twins, Kullum sai muni hirar mu
a waya. Suna kuma updating dina akan duk. a waya. Suna kuma updating dina akan duk
abinda yake faruwa a gidan. Su suka bani
labarin rikicin da ake tayi tsakanin Mommy
da Safina, a fahimtar su ita Mommy hankalin
ta bai kwanta da wanda Safina zata aura ba.
A kalaman ta kamar yadda suka fada min
"shegen girman kai ne da shi da isa kamar
wani dan sarkin Makkah"
Sun so Daddy ya bar su su taho su zauna
tare da mu amma yaki, ni na fahimci baya
son Mommy ta sake jin haushi tace ya
kwace mata su, shi lallai so yake a daidaita.
Kusan kullum kuma in muna waya sai sunyi
min maganar Hajiya, tana ta damn su da
tambaya akai na, ta damu da ni, musamman
da taji cewa za'a daura min aure.
"Kin san bata san halin da kike ciki ba.
Mommy bata gaya mata ba. Tace Hajiya
bakinta bashi da linzami"
6
2
4:15 PM
1
'"Bata gaya mata ma maganar rikicin da suka
yi da Daddy b
dasan idan da ta gaya mata
'da zata iya yi
yaya Safina kayan daki
amma kuma da kowa a gidan bikin sai yaji
labari"
Nayi murmushi, a yarda da maganar
Mommy a nan, Hajiya tana da kirki sosai,
ammà indai magana ta shiga ta kunnen ta to
sai ta fita ta bakin ta, Kuma ba wai da niyyar
munafunci ba. Haka Allah yayi ta bata san
wani abu wai shi sirri ba, Da ake zata san da. wani abu wai shi sirri ba. Da ake zata san da
zancen cikin nan nawa, zata tausaya min
sosai ta bani dukkanin kulawa, bayan ta
gamai min fada, amma kuma kowa da yake
gidan da wanda zai shigo gidan sai ya san
maganar.
Safina har da turo min pictures din gidanta
sanda aka gama jerenta, sannan tayo min
message din godiya. Ranar kamun ta ma
haka ta turo min pictures din kyalliyar da
tayi, telling me that taso ace ina nan.
Sannan sai washegari, washegari ranar
daurin aure. Ranar dama ban samu baccin
kirki ba saboda lissafin rayuwa. Haka na
gama daren akan sallaya ta. Gari yana
wayewa nace saura kwana daya. Ina nan kan
sallayar har lokacin in abincin Daddy yayi
naje na hada masa, yanzu baya iya cin
abinci mai tauri sai mai ruwa ko kuma wanda
aka dafa yayi laushi sosai.
Naje na kai masa na tashe shi zaune ya
dauka yana ci, baya son inke bashi abinci a
baki yace cin abincin da kansa ma wani
exercise ne. Yana ci yake tambayata ko na
gaml
da kaya na na zuwa asibiti nace
masa na gama, dama da yamma zan tafi, a
can zan kwana. Ya sake tambayar ko akwai
abinda nake bukata nace masa a'a. Ni kuma
na sake yi masa maganar cewa bana son ya
bini asibiti gwara yayi zamansa a gida tunda
Aunty Hajjo zata je amma ya nuna min ba zai
zauna a gida ba, Sometimes na kan yi
tunanin a gurin sa na gado taurin kaina duk. tunanin a gurin sa na gado taurin kaina duk
kuwa da cewa shi kullum cewa yake yi a
gurin Ammi ne.
Sai da nurse din shi yazo ya hada masa
ruwan wanka zai taimaka masa yayi sannan
na fita na koma parlor na zauna. Gaba na sai
faduwa yake yi. Nayi tunanin maganar aiki
na ce take damuna amma kuma ban taba
damuwa da ita ba why will I now. Ina nan
zaune har wajen azahar nurse din ya fito
yace zai je ya dawo, ni kuma na tashi na
shiga kitchen zan nema mana abinda zamu
ci da rana.
A lokacin ne wani tunani ya fado min. Twins
sunce 11am za"a daura auren Safina. Na kalli
agogo naga 12:30 ma'ana 11:30 kenan a
Nigeria. Sai nayi tunanin ko an daura? Na
shiga kitchen din na dora abincin sai na
dawo daki nayi sallah kafin abincin ya
kammala., Sai da na idar nayi adduoi na
sannan na dauko waya ta zan duba ko twins
sun turo min labari. Ina shiga kuwa naga
méssage from Hussein.
"'Yaya an daura auren Yaya Safina. We are
missing you here ke da Daddy"
Naji babu dadi a raina, nima ina missing din
su, Sai naga ya dora status, nayi sauri na
bude dan nasan pictures din daurin auren
ne,
A lokacin ne na ganshi, A lokacin ne na ganshi.
Sai da na ajjiye wayar na saka hannayena
biyu na murza idona dan in kawar da gizon
da yake min, saboda kwanan nan ba a
mafarki ba har a ido biyu gizo yake min in
ganshi kamar ya shigo gidan ko kuma inji
kamar muryarsa. Na sake daukan wayar na
sake dubawa.
Muhammad ne, Muhammad dina, yayi kyau
fiye da yadda na taba tunanin zai yi. Yana
tsaye Hussein yana tsaye shima a kusa da
shi. Hussein yayi captioning hoton with
"Nayi sabon wa"
Menene wa? Shine tambayar da na fara yiwa
kai na. Me Muhammad yake yi a gurin daurin
auren Safina?
Sai dai hoto na gaba shi yayi kokarin amsa
min tambaya ta.
Muhammad din ne dai again, this time sho
da H
an da Hussein. Hussein ya rubuta
"With the groom. Allah ya sanya alkhairi"
Naji cikina ya daure, kwakwalwa ta ta toshe.
Na sake tambayar kaina "menene groom?
Me kalmar groom take nufi?"
Hoto na gaba ne ya hau da kansa ba tare da
na tura shi ba, Muhammad ne a tsaye da
Safina a kusa da shi. Ta ci kwalliva cikin farin. Safina a kusa da shi. Ta ci kwalliya cikin farin
lace din da na siya mata. Fuskarta dauke da
tsantsar farin ciki. A kasan hoton Hussein ya
rubuta.
"Amarya da ango"
89 7
3
3
4:15 PM
Na ajiye wayar tare da girgiza kaina kamar
mai kokarin tashin kaina daga bacci, amma
kuma ba baccin nake yi ba. Na dafa gadon
da yake gaba na na mike ina jin kamar kaina
yafi dukkan sauran jiki na girma saboda
kamar dukkan jinin jikina ya tattare ya koma
cikin kan, shi kansa bugun zuciya ta a cikin
kai na nake jin sa. In dai har da gaske ba
mafarki nake yi ba, ba kuma haukacewa nayi
nake hallucinations ba, to tabbas auren
Safina da Muhammad Gidado aka daura shi.
Na dafa bango na fara kokarin fita waje sai,
kuma na dawo dakin na dauki handbag dina
da take ajjiye akan side drawer na rataya, na
cigaba da laluben hanya har na fita parlor.
"Daday!"
Na fada da karfin da bansan ina da shi ba.
Na cigaba da tafiya ina gain gaba na yana
kara duhu duk kuwa da ba dare ne yayi ba,
Sama sama naji muryar Daddy yana
magana, "Safiyya! Lafiyar ki, Me ya faru? Ina
zaki je" na juyo inda naji sautin muryarsa
nace "gida zanje, Nigeria zan tafi, Daddy
Muhammad ne fa, Wallahi Daddy shine. Muhammad ne fa. Wallahi Daddy shine.
Daddy mutuwa zanyi. Daddy zuciya ta zata
fashe. Daddy mutuwa zany" na cigaba da
fadar sauran maganganun da ban san me
nake cewa ba yayin da jiri ya debe ni nayi
kasa.
Dishi dashi naga motsin Daddy ya mike
daga kan wheelchair dinsa yayo kaina, sai
dai kafin ya karaso ya yanke jiki ya riga ni
kaiwa kasa.
Sai da kaina ya daki center table din gurin
sannan ya karasa kasa. Na hango Daddy ya
sake yunkurawa zuwa inda nake fuskarsa da
cike da tashin hankali.
"Not my daughter. God please take me
instead" ya fada a hankali. Sannan kuma da
karfi yace "who is there? help us please.
Help!"
A hankali na sake ce masa "Daddy
Muhammad ne".
Sannan na rufe ido na into
nothingness....
Longest episode ever
Shin kina son wannan episode din ya zamar
miki taliyar karshe ko kina son kari....... ....
Muhammad dai ya auri Safina, while madly
in love with Safiyya, ba tare da yasan. Shin kina son wannan episode din ya zamar
miki taliyar karshe ko kina son kari..........
Muhammad dai ya auri Safina, while madly
in love with Safiyya, ba tare da yasan
dangantakar dake tsakanin Safina da
Safiyya ba.
Ga Safiyya kuma ta dauki hanyar lahira
bamu sani ba ko zata yi rai ko akasin haka.
In bata tafi lahirar ba ma she is set to marry
Mukhtar
Yaya wanna badakalar zata kare
Yaya wadannan aurarraki zasu kasance.
Menene ainahin labarin Safiyya da
mahaifiyar ta
Menene dangantakar su da Mommy
And above all, wanene uban cikin jikin
Safiyya.
Kina son wadannan amsoshin?
Na tabbatar kina so,
Turo naira 500 dinki zuwa wannan account
din
0779484.494
Nafisa Tafida Usman
Access Bank - Safiyya'
owner
8:51 PM
Episode Sixteen: Junior
Kukan jariri ne sound din da ya fara ratsa
consciousness dina, kamar a cikin kai na aka
saka min jaririn, kamar a cikin kwakwalwa ta
yake kukan cikin kokarin sa na karasa
tarwatsa kaina. Nayi kokarin juya kan amma
naji yayi min nauyi ga kuma wani irin ciwo da
yake min. A hankali na daga hannuna da
niyyar dafe kan dan saukakawa kaina a
zabar da nake ji, k kuma in toshe kunnena
dan hana kaina jin kukan jaririn, amma sai
naji an rike hannun nawa, sai kuma naji
muryar Daddy yana magana "Safiyya?
Careful kar kiji wa kan ki ciwo. Ku fita da
wannan yaron daga nan dan Allah".
Na dan motsa idona kadan ina jin a raina ina
son in kara gain fuskar Daddy one last
time, Na samu da kyar idon da yayi min
nauyi ya bude, na sauke su akan Daddy da
yake zaune akan kujerar sa a kusa dani
hannunsa rike da nawa, ban gane inda muke
ba amma na gane Daddy na, sai dai kuma ba amma na gane Daddy na, sai dai kuma
yayi mugun chanjawa lokaci daya yayi kamar
an kara masa shekaru akan nasa, yayi ramar
da ban taba gain shi da irin ta ba duk kuwa
tsahon shekarun da ya dauka yana jinya.
Na lura bayan shi akwai likitoci da suke
tsaye a kaina blue scrub a jikin su. "Safiyya"
Daddy ya sake kiran suna na "sannu! An fita
da shi. Ki ci gaba da baccin ki"., Na mayar da
ido na na rufe na cigaba da baccin kamar
yadda ya bukata.
A farkawa ta biyu ne nayi nadamar farkawar.
Hoton Muhammad tare da Safina an rubuta
amarya da ango a kasan hoton shine abinda
ya dawo dan cikin hayyaci na, kamar yadda
shine abinda ya fitar da ni daga cikin
hayyacin nawa tun farko. "Muhammad!" na
fada ina kokarin tashi daga kan gadon da
nake kwance. Na san dai an rike ni amma
ban san waye ba, naji kuma muryar Daddy
sannan naji ta Aunty Hajjo, daga nan kuma
naga wata maaikaciyar asibiti ta shigo da
sauri ta doso ni, sannan mercifully na koma
na cigaba da bacci na.
Sanda na sake farwakawa ido na akan
agogo ya sauka, karfe biyu da minti hudu na
gani, nayi ta kallon agogon ina tunanin
abinda hakan yake nufi. Biyun yaushe?
Biyun kuma wacce rana? Nayi kokarin juya
kaina in nemi window a dakin ko zanga hint
din in safiya ce ko dare amma ban gani ba.
Sai ma kaina da yake kara yi min ciwo a
kokarin juya shi da nake yi. A lokacin na. kokarin juya shi da nake yi. A lokacin na
fahimci a dakin asibiti nake, musamman
saboda yanayin gadon da nake kai da kuma
naurorin da suke zagaye da ni. Na duba
hannuna naga drip yana shiga cikin
jijiyoyina. A gefe na naga Aunty Hajjo tana
kwance akan wata kujera, daga dukkan
alama baccin da take ba mai nauyi bane ba.
Babu Daddy a dakin.
Na mayar da ido na na rufe amma kuma sai
baccin yayi kaura daga cikin su, abinda ya
faru ya fara dawo min a cikin kaina. Yadda
rayuwata ta fara so good and perfect, lokaci
daya ta juya zuwa terrible a karshe na rasa
komai. Na rasa komai including my chance
to marry the one person I love like crazy.
Na riga na lallaba zuciyata akan ta hakura da
shi, for his own sake, duk da dai har yanzu
zuciyar ta wa bata gama amince wa da
umarnin da na bata ba, tarin matsalolin da
nake ciki sune duke danne damuwa da
rashin sa, amma yanzu, after seeing his
picture with Safina, komai ya dawo min
sabo.
Tambayar da na samu kaina da yiwa kaina
ita ce "how?" Ta yaya Muhammad da Safina
suka hadu a cikin watanni biyu da yan
kwanaki har kuma suka yi aure? Muhammad
fa? The man I thought saboda san da yake
min zai jima bayan na barshi kafin yayi aure,
the same man that kept telling me how he
can not live without me. Then he married my
sister just few months da rabuwa da ni? Ta. sister just few months da rabuwa da ni? Ta
yaya zai yi min haka?
Na tuno maganar Safina da take gaya min
wanda zai aure ta ya turo mata friend
request a social media, they get talking and
he proposed yace yana son ya aure ta in few
months. Hakan yana nufin Muhammad shi
ya nemi Safina kenan. But why and how can
he do that? Na san ya san ina da step sister
mai suna Safina, na tabbatar munsha yin
maganar ta dashi, so it was easy for him to
find her and marry her, and dalili daya zan
iya fahimta a matsayin dalilin da yasa yayi
hakan, to get back at me for yaudarar sa da
yake tunanin nayi.
32
17
6
A 9 8:52 PM
Na mayar da ido na na rufe ina jin kaina yana
kara matsanancin ciwo.
And Safina. Mun sha maganar Muhammad
da Safina. Abinda bani da tabbas akan sa
shine idan ta san shi by face or not. Na san
basu taba haduwa ba, but she must have
seen his picture a waya ta, she must have.
Babu yadda zata yi tace bata taba gain sa
ba dan hotunan Muhammad a cikin waya ta
sun fi hotuna na ni kaina yawa. Wasu
hotunan ma shi kansa bai san sanda na
dauke shi ba,
Karya take yi tace bata gane shi ba,
Duk su biyun munafukai ne
Duk su biyun maciya amana ne. Duk su biyun maciya amana ne
Duk su biyun kuma sai sun gane kuran su
akan abinda suka yi min.
I have been good, but rayuwata have turned
to bad, now I am going to be bad sai in ga in
da akwai riba a wannan bangaren. I am
going to turn into a bad girl. I am going to
destroy their marriage even if it is the last
thing I will ever do.
Na fara planning a kaina na yadda zanyi
making life difficult for Muhammad da
Safina, babu irin plan din da ban hada ba.
None of which is a good thing. But to do
that sai na koma Nigeria. Na fasa zama anan
din kamar yadda a da na ce zanyi. Nigeria
zan koma. In gasa wa Safina da Muhammad
ava a hannun su. But to do that properly, I
will have to get rid of cikin jikina first.
Wannan mayataccen cikin a jikina.
Sai a lokacin hankali na ya dawo kan cikin.
Sai a lokacin tunanin da ya chunkushe a
kwakwalwa ta yay giving way for feelings.
And I felt empty a ciki na. Na bude ido da
sauri na kalli cikin. Babu. Na daga hannuna
wanda babu komai a jiki na shafa cikin, it felt
weird, it felt as if bayan babyn har kayan
cikina ma babu su. Naji wani relief na
rabuwa da cikin ya lullube ni, sai kuma fear
ta maye gurbin relief din. Ina yake? Masu
adoption din sun karbe shi? Yanzu Daddy ya
san na bayar da shi kenan? Me Daddy zai ce
akan hakan? san na bayar da shi kenan? Me Daddy zai ce
akan hakan?
Amma kuma dazu ina bacci naji kukan jariri.
It shouldn't be. Na riga nayi signing
agreement cewa daga ni har dangina ba
zamu ganshi ba ana cire shi za'a tafi da shi.
Bana son ganin shi. Bana son duk wani abu
da ya shafe shi.
Wani alarm naji ya fara beefing a jikin gadon
da nake. Naga Aunty Hajjo ta mike da sauri
tana kallona sannan ta danna wani button da
nake tunanin na kiran likitoci ne. Sai kuma ta
taho inda nake ta dafa kaina. "Relax Safiyya,
relax. You are alright. Everything is good.
You are going to be fine".
Wata nurse ta shigo da sauri tana kallon
abinda yake yin karar tace "her VP is
skyrocketing again" da sauri aunty Hajjo
tace "then do something" ni dai ina kallon
su dan ban fahimci abinda suke yi wa tashin
hankali ba. Mutuwa ce fa ba wani abu ba.
And mutuwa a gurina idan tazo zan kalle ta
ne a matsayin mercy dan na jima ina neman
ta da ma.
Muryar Abdul ce ta sake tashina a karo na
uku.
"This baby is sooo cute Umma"
Sai kuma muryar Aunty Hajjo
"Da Allah ajiye shi haka nan. Sai faman. "Da Allah ajiye shi haka nan. Sai faman
jagwalgwalashi kake yi. Dan ma yaron me
lafiya ne ai da ba zasu barmu mu zo dashi
dakin nan ba tunda preterm ne"
Ya sake cewa "bara in dan kara rike shi
kadan. Ai ba taba shi nake yi ba. Rike shi
kawai nake yi" tayi tsaki "kai ka sani kuma.
Da ka amince da abinda nace maka ai da
yanzu kai zaka raini wanna jaririn. Amma
kaki. Kayi wa kanka ai" yace "Umma ba fa ni
naki ba, ita ce ba ta zabe ni ba" tace "bayan
ka gaya mata kana da wadda kake so?
Wacce mahaukaciya ce zata auri namijin da
ya gaya mata yace baya son ta?"
Muryar Daddy naji yayi sallama. Na juya
kaina bangaren da naji muryar ta sa sannan
na bude ido na a hankali na sauke su a
kansa, ya turo kujerar sa kusa da gado na
yana kirkiro murmushin da ni na san ba na
gaskiya bane ba. "Safiyya. Kin tashi?" Ya
fada yana shafa gashin kaina. "Sannu. Ya
jikin ki? Me yake miki ciwo yanzu?"
A hankali na bude baki da muryar da naji
kamar ba tawa ba nace "Daddy. Gida zan
tafi. Nigeria zan tafi" yace "okay, Okay. I will
get us tickets right away, Kar ki daga
hankalin ki akan hakan. Any thing you want".
14
7
8:52 PM
Na dora hannu na akan cikina ina shafawa
sai ya rike hannun "kar ki taba ciwon" na
dago ina kallon sa ban ce komai ba sai
Sending messages is not allowed in this group. sai ya rike hannun "kar ki taba ciwon" na
dago ina kallon sa ban ce komai ba sai
Aunty Hajjo ta dawo daya gefen nawa tace
"jinin ki ne ya hau. Kika fadi. Aka kira
ambulance suka dauko ki suka kawo ki nan.
Dole aka cire babyn dan a samu damar
daidaita vp din ki. Har yanzu bata zama
normal ba but it is going down
alhamdulillah".
Daddy yana kallon ta yace "I heard she had
another arrest cikin dare ko?" Aunty Hajjo ta
dan yi murmushi "kar ka damu da haka
Daddyn Safiyya. She will be okay insha
Allah" na juya ina kallon ta sai tace "they
had to admit him too. Allah ne ya kare mu.
We almost lost the both of you. Whatever is
worrying you Fiyya keep it aside. Nothing is
worth damuwar da mahaifinki ya shiga. Ko
ba kya valueing taki rayuwar I am sure ta sa
matters a lot to you",
Sai ta koma da baya ta karbo jaririn daga
hannun Abdul shi kuma ya fita sannan ta
dawo ta mika wa Daddy tace "tun jiya naga
ta yar ka kake ba ku gaisa ba" ya gada
hannu ya karba, na dauke kaina gefe in jin
hawaye yana bin kuncina. Ba zan iya cigaba
da kallon yana yin fuskar Daddy a lokacin da
ya karbi babyn ba,
Ko a mugun mafarki ban taba yin wanda na
haifi shege ba, Ban taba yin wanda Daddy
yake rike da shegen jariri daga gare ni ba.
Babu abinda ba zan iya bayarwa ba a lokacin
idan da zan samu Allah ya dauki raina a. idan da zan samu Allah ya dauki raina a
gurin. Wannan kuma yana daga cikin dalilin
da yasa na zabi bayar da jaririn.
Muryar Daddy can ciki naji ace "Allahu
Akbar. Allah mai kyauta da kari. Allah na
gode maka. Na karbi wannan kyautar da kayi
min kuma na gode maka. Allah kayi masa
albarka ka bashi rayuwa mai kyau duniya da
lahira" naji Aunty Hajjo tace "Ameen ya
Rabbi".
Sai kuma Daddy ya dan yi yar dariya yace
"yanzu kai bawan Allah, upon all the people
in this big wide world, ka rasa da wanda
zaka yi kama sai dani?" Aunty Hajjo tayi
dariya "soyayya ce yake yi maka. Kauna kai
da shi har abada. Amma jarirai ba'a iya gane
kamar su lokaci daya, sai sun yi wayo sosai
sannan kamarsu take bayyana"
Sai Daddy ya mike da jaririn a hannun sa
sannan ya dora min akan cinyata, ganin bani
da niyyar rike wa sai Aunty Hajjo ta taho da
sauri ta rike sannan ta daga gadon da nake
kai na koma kusan a zaune sai ta kwantar da
shi akan cinyar ta ta saka pillow ta tare shi.
Na runtse ido na ina girgiza kai na "bana son
ganin shi Aunty, ki dauke shi daga jikina dan
Allah"
A daidai lokacin wata maaikaciyar asibitin ta
shigo da takardu a hannun ta, suka gaisa da
Aunty Hajjo sannan tayi bayanin cewa tana
son ta cike bayanai akan jaririn da aka haifa
ne for his birth certificate. Tambayar farko. ne for his birth certificate. Tambayar farko
ita ce menene first name dinsa. Tayi
tambayar tana kallo na, nima na bita da
kallo, to in har ni zata tambaya ni kuma wa
zan tambaya kenan?
Daddy ne ya amsa "Adam. His first name is
Adam" na juya ina kallon Daddyn. Tunda na
samu cikin nan babu abinda Daddy ya tsani
gani kamar cikin, abinda har ya jawo min
nima baya son ganina. Ban taba tsammanin
zai karbi babyn ba ballantana har ya saka
masa sunan sa.
Matar ta rubuta sannan ta sake next
question wacce tafi komai ciwo a gurina "his
surname" wanda mu a gurin mu hausawa
mukan yi amfani ne da sunan uba a
matsayin surname. Still ni ta sake yi wa
tambayar. Sai na sunkuyar da kaina kasa
hawaye yana fitowa daga ido na yana zuba
akan dan jaririn da yake kan cinyata. Daddy
naji ya sake amsawa again da muryar a kasa.
"Adam Muhammad. His full name is Adam
Adam Muhammad", Matar ta rubuta sannan
ta juya ta fita.
Na rufe idona ina jin hawayen yana cigaba
da bin kuncina. Sai kuma na bude ido na
sauke su akan dan jaririn da yake kan
cinyata fuskarsa jike da hawaye na.
Yar karamar fuskarsa tana kama da ta
Daddy tabbas, yana kuma kama da ni. Wato
dai duk a kaina ya kare. Gashi kuma ya karbi
sunan Daddy. Ruwan hawayen nawa da yake. sunan Daddy. Ruwan hawayen nawa da yake
zuba a kan fuskarsa ne ya saka ya motsa a
hankali sannan ya bude idonsa ya sauke su
a kaina. Nayi sauri na mayar da nawa idon na
rufe." Aunty Hajjo dan Allah ki dauke shi
daga jiki na" tazo ta saka hannu ta dauke shi
sannan ta sake kwantar min da gadon tare
da lullube ni.
14
11
10
8:52 PM
Na rufe ido na kamar bacci zan yi, naji ta
cewa Daddy zata mayar da jaririn NICU inda
ake kula da shi.
Sai dai tunda na rufe nawa idon idon yaron
nake gani yana kallo na dasu. Ina tunanin
ranar da zai kalle ni da su yace min ina
ubansa. Ban san wanne kallo zaiyi min ba in
nace masa ban sani ba. Ko zai fahimta? Ko
kuma shima zai dora ayar tambaya a kaina
kamar yadda mutane da yawa suke dorawa,
including mahaifina.
Sai daga baya na fahimci dalilin da yasa
adoption din da nayi niyyar bayar da babyn
bai tafi daidai ba. Ambulance din da aka kira
ta dauke ni ba asibitin da nake ganin likita ta
kai ni ba, asibiti mafi kusa kawai suka nema
suka kai ni dan ceto raina. Su kuma inda aka
kaini basu san waccan maganar ba, Na
kuma fahimci anyi min aiki ne tun around
1pm na ranar juma'a, yanzu kuma 1pm din
asabar ne,
Ina jin uncle Sufyan suka shigo tare da
Abdul, suka gama magana da Daddv sai. Abdul, suka gama magana da Daddy sai
yazo kusa da ni yayi min sannu. Na gyada
masa kai kawai ba tare da na bude ido na
kalle shi ba dan ni a yanzu da naga dan da
na haifa ba tare da aure ba ido da ido sai
nake jin kamar nafi kowa abin kunya a
duniya. Na tabbatar mutanen da suka san ni
da ba zasu cigaba da yi min kallo irin wanda
suke yi min da ba.
Daga baya Aunty Hajjo ta dawo babu yaron
a hannun ta, ta hada min ruwa a toilet ta
taimaka min na tashi tsaye, sai naji kamar
iska zata kada ni, na zama kamar wata
tsinke. Sai da na shiga toilet sannan na kalli
inda aka yanka a cikina, a mark that will
forever be a reminder to me. Aunty Hajjo ta
lura da abinda nake kalla tace min "kar ki
damu, sun ce the scar won't be bad, sun
kware a aikin su ai sosai".
"It will still be
there" na fada ba tare da nasan na fada ba.
"Ko ba a jiki na ba the scar will forever be in
my heart",
Ita ta taimaka min nayi wanka yadda ba zan
fama ciwona ba, ta taimaka min na shirya
sannan muna fitowa ta bani abinci ta saka ni
naci, banyi musu ba naci saboda ina bukatar
karfin jiki na for what I have planned.
Ina cikin shan kunun da ta bani ne Daddy ya
sake dawowa dakin. Yana shigowa nace
"Daddy ka siyo tickets din? Yaushe jirgin zai
tashi?" Ya kalli Aunty Hajjo kamar mai
neman taimako a gurinta, sai ta fara magana
"Safiyya, kema kin san babu yadda za'a yi ki. "Safiyya, kema kin san babu yadda za'a yi ki
iya yin tafiya a yana yin da kike ciki. Ki bari
ki kwana biyu ayi discharging din ku daga
asibiti ke da Adam Junior in yaso sai ku tafi"
na ajiye cup din hannuna. "Ni na warke. Ni
babu abinda yake damuna. Ni Nigeria zan
tafi. Allah yau ko a kafa ne sai naje" na fara
rera kuka. Daddy ya matso "Okay, okay.
Bara in je in samu doctor muyi magana da
shi inji. In yace zamu iya tafiya shikenan"
Aunty Hajjo tace "Daddyn Safiyya ka zauna
ka huta. Zan je in turo shi nan sai kuyi
magana gabaki daya".
Likitan yazo, bayan ya gama gwaje-gwajen
sa yace zan iya tafiya tunda anfi 24 hours da
yin aikin. Musamman saboda na nuna hakan
na ke so su kuma suna son abinda zai
faranta min ne. Sai dai jaririn yace ba za'a
iya tafiya dashi ba, duk da cewa yana iya
numfashi da kansa amma yana bukatar
kulawar maaikatan lafiya 24/7 for at least 3
weeks kafin ay discharging din sa.
Bayan ya fita muka zauna shiru ni da Daddy,
sannan yace "are you sure you want to go?"
Nace "Yes" yace "okay, shikenan. Zan saka
ayi mana reserving next flight to Nigeria, But
what about him?" Na gane wa yake nufi
amma nayi shiru ban amsa ba. Ganin bana
son yin maganar sai bai kara yi ba, ya dauko
wayarsa ya kira ya gama settling maganar
tafiyar mu sannan yace min "akwai jirgi
4:00 am zai tashi. To Lagos. Yayi?" Na gyada
kai ina jujuya kofin kunun hannuna, sai ya
sake cewa "and there is something I want. sake cewa "and there is something I want
you to know kafin mu tafi. An daura auren ki
da Mukhtar dazu" na daga kai ina kallon sa
sai yayi saurin fara yi min bayani, baya son
duk abinda zai bata min rai a lokacin, yace
"an riga an saka lokaci. They couldn't get us
on phone sai suka daura. Nima sai dazu da
Abdul yaje gida ya dauko min wayata sannan
na sani" banji komai ba a raina nace a
hankali "it is okay Daddy".
11
10[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: Daki na na wuce da sauri na rufe kofa sannan na zube a kan carpet din gaban gadon dakin na fara rera kuka. Kukan abubuwa da yawa. Kukan da ban san ranar da zan daina shi ba

alamar an bude kofar dakin an shigo, ban
dago kai na ba amma a raina na san waye
saboda mu biyu ne kadai a cikin gidan,
besides, motsin wheelchair dinsa daban
yake da motsin tafiyar sauran mutane. Ban
juya na kalle shi ba amma nayi kokarin
sassauta kuka na tare kuma da kokarin goge
goge hawaye na. Ya jima anan a zaune yana
kallo na sannan yace "I knew it. Dana na san
kina nan kina kuka. But what I do not know
is kukan menene kike yi? Uhmm, fada min,
kukan me kike yi".
Na cigaba da goge fuskata da bayan hannun
rigata, ina jin yadda already fatar idon ta
kumbura. Ya sake tambaya,
"ina jin ki?
Kukan menene kike yi?" Nace "I want you to
get better. I need you to get better" yayi
shiru na wani lokaci sannan yace
"you know
it is not going to happen. Sai kuma menene
again?" Na girgiza kaina "shikenan dama.
Shine kadai abinda nake yi wa kukan" yace
"liar. You are also crying saboda maganar
auren ki. Haka ne?" nayi shiru banyi magana
ba. Ya sake tambaya ta "ba kya son auren
Mukhtar? Kina so a fasa yi da shi?" Nayi
shiru still ban ce komai ba. Ya zagayo
kujerar sa gaba na yace "Safiyya. Ina so inyi
miki aure kafin in tafi in barki. Idan na mutu
na barki babu miji this people will tear you
apart. Kuma dole in aura miki wanda ba za'a
yi bincike ba ballantana a tono abinda ya
faru da ke. Wannan ya bar ni da very limited da ke. Wannan ya bar ni da very limited
options. I gave you the options. And you
chose. Wanda kika zaba ba shi zuciya ta
take so ba, hi zuciya ta tafi yarda da ki auri
Mustapha. But you adamantly chose
Mukhtar. And now you are crying. Tell me
why".
Na dago ido na ina kalion sa "Daddy, me
yasa kake son Mustapha?" Yace "saboda a
hannuna ya tashi, ni na bashi tarbiyya.
Saboda mahaifiyarsa ce ta raine ki, ita ta
baki tarbiyya. And sometimes family means
more than blood. Sa'adatu will never harm
you. But I am not so sure about Ahmad" Na
dauke kaina gefe nace "you know what they
want" yace "and what makes you think
cewa su Ahmad ba the same thing suke so
ba?" Nayi shiru ban ba shi amsa ba sai ya
sake cewa "a rayuwa Safiyya, most of the
relationships if not all da zaki shiga, ko ta
auratayya ko business ko zamantakewa to
trade by batter ake yi, to get something you
have to give something. The best logic is ki
san abinda mutum yake so daga gare ki, and
then use that to get kema abinda kike so"
Nace "Amma Daddy Mustapha fa..." Yace
"he didn't do it. Ban san how many times
zan gaya miki ba. He didn't do it" nayi shiru
ban ce komai ba, bana son gaya wa Daddy
abinda Mustapha yayi, bana son inyi using
the only card din da nake amfani da shi
grin taming Mustapha.
Jin nayi shiru bance komai ba sai yace
"are Jin nayi shiru bance komai ba sai yace "are
you changing your mind or not?" Na goge
hawaye na tare da girgiza kaina "no. Am not.
Ina neman alfarma dai guda daya. Dan Allah
Daddy bana son komawa Nigeria. I want to
live here. Or somewhere else. Anywhere
that is not Nigeria",. Ya juyo yana kallona, sai
kuma ya juya kujerar sa yayi hanyar fita ba
tare da yace min komai ba. Har ya kai bakin
kofa sannan ya juyo yace min "about
Mukhtar, ko da ana gobe daurin aure ne in
kika chanja shawara let me know ni kuma
zan tsayar da maganar".
Ban amsa ba nima har ya fita, ban kuma bar
space a zuciya ta da zan yi tunani akan
maganar ba. Na riga na yanke shawara and I
am not going back on it, duk kuwa da zafin
da zuciya ta take yi min akan hakan. Yana
fita waya ta ta kama kida, na san waye tun
kafin ma in kalle ta dan mostly ya kan kira ni
by this time. Sai dai sam bana son daukan
wayar ta sa. Zuciya ta bata so. Sai nayi
murmushi ina mamakin rayuwa ta, yanzu na
gama ja in ja da Daddy a kan sa, akan nace
shi zan aura, amma kuma still zuciyar ba son
sa take yi ba.
4
8:00 PM
Har ta katse ban dauka ba sai da ya sake
kira sannan na dauka. Na saka wayar a
kunne na banyi magana ba yace "ko baccin
ne dai? Na ga alamar ke ba kya gajiya da
bacci" nace "na tashi, kawai dai yau na tashi
bana jin dadi ne" yace "ni kuma yau cikin jin bana jin dadi ne" yace "ni kuma yau cikin jin
dadi na tashi. Have you heard the good
news? In the next eight days you are going
to be my bride. Duk da dai su Daddy suna ta
insisting babu taron biki, but I want us to
have ko da yar walima ne haka in kin dawo
nija...
.." Nace "yaya Mukhtar, I am sorry, but I
don't want any walima dan Allah. And I also
don't think zan dawo Nigeria." Yace "why
not? Fiyya komai da ya faru ai ya wuce
kuma. Daga anyi daurin auren nan shi kenan
we will put everything behind us muyi facing
sabuwar rayuwar mu and the ways to build a
new family k0? Gashi ma Allah cikin ikonsa
we will soon have a child to start the family
with. Abeg, ki shafa min kansa ko kanta and
tell them they are already loved at home".
Abinda ya fada was supposed to made me
feel better amma sai naji raina ya baci dan a
lokacin bayan uban dan cikina babu abinda
na tsana sama da dan cikin nawa. Amma sai
na daure zuciya ta nace "kayi hakuri yaya
Mukhtar. I can't. Abun zai wuce physically,
but the trauma will always haunt me, and
the best thing to do idan mutum yana son
moving on from a traumatic experience is to
change environment. Idan na dawo Nigeria
ba zan iya bawa family na kulawar da suke
bukata daga gare ni ba" yace "kina ganin
zaki ke tunawa da shine?" Nace "not just
him, Zan ke tunawa da komai" amma a raina
na san babban abinda nake gudu a komawa
Nigeria shine Muhammad. A yanzu da na
dan saka distance a tsakanin mu gani nake
kamar na samu wata kariya daga ciwon son kamar na samu wata kariya daga ciwon son
sa, amma ina komawa Nigeria na san zanji
tamkar an rushe katangar kariyar ne, and
there is a chance na cewa zamu iya haduwa
da shi, and that would be a disaster.
A haka dai ya hakura ya bar ni amma bai ce
ya amince ba kamar yadda Daddy ma bai ce
ya amince ba, ya dai ce min zaiyi tunani a
kai.
Daga ranar sai na kara cigaba da lissafi na.
Ina lissafa ranar aiki na kuma ina lissafa
ranar daurin aure na. Safina kept calling me
har sai da na daina daukan wayarta wai taji
labarin daurin aure na and tana son mu
shirya wani abu special ni da ita tunda muna
da friends daya musamman yan secondary
school din mu. Sai da taga na nuna mata
bacin raina sosai sannan ta rabu da ni.
Mustapha ma ya kira ni ban dauka ba, sai
gashi ya turo min dogon message a
Whatsapp wai yana yi min fatan alkhairi and
he wants us to put everything behind us a
cigaba da zumunci, and whenever I need a
big brother he will be there for me. A karshe
ya kara da cewa duk sanda nake bukatar a
dan sassama min Mukhtar I should just give
him a call.
Ya rage kwana biyar daurin auren Safina ni
kuma nawa shida sai ga Mommy ta kira ni.
Na dauka na gaishe and she lost the words
to say to me, sai kuma ta kama fada "yanzu
wato da ban kira ki ba ke ba zaki taba
daukan waya ki kira ni ba ko?" Nace "kivi daukan waya ki kira ni ba ko?" Nace "kiyi
hakuri Mommy" ta cigaba "na dauka a ranar
da muka taho yarinyar nan a ranar zaki fara
nema na amma ke ko ajikin ki ma sai kika
cigaba da sabgar gabanki ko?" Nayi shiru
bance komai ba, ta cigaba "ance min nan da
six days za'a yi miki aiki. Kina shan
magungunan ki dai ko?" Na ce "eh ina sha"
amma a zahirin gaskiya rabon da insha
magani tunda ta bar kasar. Tace "good. Ki
kula da kanki. Ki kuma kwantar da hankalin
ki, kin san a haihuwa babu abinda ake gudu
irin hawan jini" na yi shiru ban ce komai ba
sai ta sake cewa
"ko ba ki auri Mustapha ba
still ke ya ta ce" nace "Nagode Mommy".
*Him*
Kwanakin sauri suke tayi a gurin Gidado, so
yake su tsaya, dan ya samu at least ya shaki
numfashi amma sun ki tsayawa and every
day there is something to do. Gidan su
already har ya fara cika da mutane
musamman saboda bikin biyu za'a hada,
gashi kuma bikin farko ne da za'a yi a gidan
na su. Wannan ya saka a dole ya rufe dakin
sa ya tattara ya koma gidan sa, gidan da aka
fara siya masa yanzu kuma da ya takura aka
sake masa wani.
8:00 PM
Babu shiri Haidar shima ya tattara nasa
kayan ya bishi, duk da hakan bai yiwa
Gidado dadi ba dan yaso ya samu these
days to himself dan in suka kare kuma shi
kenan zai shiga cikin sabuwar rayuwar da kenan zai shiga cikin sabuwar rayuwar da
bai ma san ta inda zai bullo mata ba. Yana
sane yaje ya kamawa abokansa da suka zo
gari musamman dan bikin hotel rooms duk
kuwa da cewa akwai wanna spare gidan
amma shi so yake ya zauna shi kadai. Haidar
din ma sai ya bude masa part din da ya
kamata ace shine nashi, shi kuma ya shiga
wanda ya shirya saboda Safiyya.
Ya san cewa hakan da yayi ba karamin
emotional damage zai jawo wa kansa ba
amma ya zabi hakan.
Babu komai na furnitures a gidan dan haka
sai katifu suka je dasu suka shimfida suke
kwana akai, sai kuma boxes din kayan sawan
da zasu yi amfani da su da sauran
abubuwan da zasu bukata. Kullum da safe
yake fita gurin hidimomin sa and they kept
his emotions on check har sai ya dawo gida
tukunna, shi farko ya dauka in ya gaji bacci
zaiyi saurin daukansa kamar yadda Ya
Amen ya gaya masa, amma kuma sai ya ga
shi ba hakan bane ba a gare shi. Ko ya gajin,
in ya kwanta sai dai yayi ta juyi, amma bacci
baya zuwa idanun sai gari ya kusa wayewa.
Kullum a ransa babu abinda yake yin bita sai
rayuwar sa da Safiyya, babu abinda yake so
irin ya fahimci abinda yayi missing, ya
fahimci inda hint din cewa tana da aure yake
wanda yayi missing a baya amma ya kasa
gani,
Except kin kai shi gidan su da tayi. She kept
on delaying and delaying giving all sorts of on delaying and delaying giving all sorts of
excuses. Farko excuses din nata akan cewa
tana gidan uncle dinta ne kuma uncle din zai
yi mata fada in ya ganta da saurayi because
yana tunanin cewa bata isa yin saurayin ba,
daga baya da ya fara nuna mata shi fa da
gaske aure yake son yi, aurenta yake son yi,
sai ta koma yi masa maganar rashin lafiyar
babanta and the fact that baya zama a kasar
sosai, and ranar nan da ya takura mata she
said bata son ta kaishi gurin uncle dinta sai
dai babanta, saboda uncle din yana son
hada ta aure da dan sa Mukhtar.
Ya san Mukhtar. Tun the second haduwar su
da Safiyya ya san Mukhtar, kuma tun a
lokacin jikinsa ya bashi cewa something was
going on at least a zuciyar shi Mukhtar din,
tun sanda ya ganshi din kuma yaji cewa
baya son sa. Amma kuma a zuciyarsa ya san
cewa kishi ne yake yi.
Ya san cewa kishi yana daga cikin
weaknesses din sa akan Safiyya, yana da
mugun kishin da har toro yake bawa kansa
sometimes, ya kuma san kishin nasa a
yanzu yana daga cikin abinda yake cin
zuciyarsa. The memory of her dauke da
cikin wani, knowing fully well abinda ya faru
kafin a samu cikin shine babban abinda yake
hana mishi bacci a yanzu.
A yau ma bai dawo da wuri ba sai late,
hopping to fall asleep as soon as possible,
yana shigowa ma da yay packing bai shiga
cikin gidan ba sai ya cire dogayen kayan. cikin gidan ba sai ya cire dogayen kayan
jikinsa ya bar singlet ya zagaya bayan gidan
yana jogging da niyyar karawa kansa gajiya.
A bayan ne kuma yaga wani guri da Safiyya
ta saka musamman ya ware mata bai yi
paving ba
"spices zan shuka a gurin, akwai spices din
da ba a samu sosai a kasuwa ko kuma ba
za'a samu fresh one ba, to gwara in samu
seeds din su in shuka da kaina in ringa
using".
Ya tsaya a gaban clearing din yana hakin
jogging din da yake yi. "damn you. Damn
you Safiyya" ya fada a fili, sannan ya wuce
da sauri ya cigaba da jogging din sa. Yana
cikin haka yani alamar an bude gate, ya san
Haidar ne ya dawo amma kuma baya son
kowa yayi masa magana a yanzu, dan haka
yayi sauri yayi kwana ya shige gidan ta kofar
baya ya shige dakin da yake kwana. Direct
toilet ya wuce ya kunna wa kansa shower ya
rufe idonsa yana jin dadin sanyin ruwan.
"'Komai zafi bana iya wanka da ruwan sanyi,
mura yake saka ni"
Yaji muryar ta kamar a yanzu take gaya
masa, Ya tuna da amsar da ya bata a
lokacin, "Kar ki damu, zan koya miki ne. Ita
kan ta murar sai ta hakura ta bar mu".
Ya fita daga shower din ya goge jikinsa,
yana kallon fuskarsa a mirror din toilet din, yana kallon fuskarsa a mirror din toilet din,
"Da wata farar fuskar ka anan" yayi
murmushi. "Burge ki tayi"
4
8:00 PM
Ya fito daga toilet din ya saka pajamas
sannan ya karo karfin AC ya kashe fitila yayi
addu'a ya kwanta, hoping to center his mind
on something important, anything apart
from Safiyya, amma babu abinda ya gani a
idonsa sai Safiyya da ciki a office din sa.
Babu kuma abinda yake son sani a lokacin
sai abinda Safiyya take yi a wannan lokacin,
babu abinda mind dinsa take saka masa sai
different scenarios a abinda Safiyya take yi
din. Ya mike tsaye ya kara wa kansa fanka
sannan ya koma ya kwantatare da zagaye
kansa da pillows, few minutes after that
kuma ya sake mikewa zaune ya jawo
wayarsa ya nemo number din Safina ya kira
without realizing cewa karfe sha biyu ne na
dare har da rabi.
Sai da ta dauka sannan yayi realizing
mistake din sa. "Hello Habibi. Ba ka yi bacci
ba?" Ya matsar da watar daga fuskarsa yace
"shit!" a hankali cikin jin haushin kansa.
Sannan yace "hello? Uhmm, I think I made a
mistake ba wannan number din zan kira ba"
ta danyi shiru sannan tace "wa za ka kira to?
By this time?" ya fara tunanin karyar da
zaiyi, another of his weakness shine karya,
bai iya karya ba kwata kwata. Yace "my
friend, akwai wani friend dina Sahabi shi zan kira yanzu" ta sake cewa "by this time?"
Yace "eh, baya bacci da wuri, nima haka"
tace "ko dai ita zaka kira?" Ya dan bata rai
"wa kenan?" Tace "your ex da ka fada min.
Ko ita zaka kira Allah ya sa ka kira ni" ya
danyi shiru sannan yace "I wish I can call
her, there is nothing da ba zan iya bayarwa
ba a yanzu to be able to call her. But she
blocked my number. And beg me not to find
another way to contact her. So to answer
your question, ki kwantar da hankalin ki, ba
ita zan kira ba".
Tace "okay. Because I don't want to ruin the
memory of the first time you call me da
dare. Ba na son sunan wata ya shiga cikin
memory din. It has always been a dream of
mine. In ga ina waya da kai irin yadda
yammata da samari suke y" yace "I told you
abokina...." Tace "right. At least let me
pretend ni ka kira. And since you called ya
kamata mu danyi magana ai ko? At least tell
me something about you da kake ganin ya
kamata in sani, maybe about your friends or
family ko aikin ka, anything, just talk to me "
yace "okay. Let me start with the things I
like, I like honesty, na tsani karya. I like tsafta
a lot. Bana son hayaniya, bana son mita,
bana son tsegumi ma'ana telling me
something that do not concern me. And
most importantly, I love my family, a lot"
tace "yauwa, about the family, ban san su
ba sam in banda Mufida, ita ma kuma a
waya ne kadai ko hoton ta ban taba gani ba,
ya kamata in san su ko?" Yace "zaki san su
ai. A hankali, But the immediate family basu. al. A hankali. But the immediate family basu
da yawa, daga Mama sai Abba sai Haidar
and then Mufida. I am the eldest. Akwai
cousins da yawa, I can't list them all. You will
get to know them watarana" tace "haka ne.
And your friends, aside Sahabi" yace "waye
Sahabi?" Tace "Sahabi dai da zaka kira
yanzu" yace "ohh that Sahabi, Sahabi my
friend. Yes, akwai Sahabi and the rest. Zaki
san su suma later. Now, let me call Sahabi
kafin yayi bacci".
Tayi ajjiyar zuciya "okay, shikenan. At least
we are one step ahead. Good night Habibi".
Sai dai daya ajiye wayar, maimakon ya koma
ya sake gwada baccin sai ya tashi ya zauna
ya dauko takarda da biro a cikin takardun da
Abba ya bashi zai yi cike cike na sabon aikin
da zai fara, ya juya bayan takardar kawai ya
kama zane a jiki, zanen fuskar Safiyya. Sai
da ya gama zana ta tas kamar zaka kira
sunan ta ta amsa, sai kuma ya dukunkune
takardar yayi jifa da ita ya koma ya kwanta.
Da safe bai tashi da wuri ba dan baiyi bacci
mai nauyi ba sai bayan sallar asuba, ya
manta cewa a ranar zasu fita da Abba
maganar chanjin aikin sa. He is going to take
over some parts of managerial work na
Company din Abba bayan bikin sa. Sai dai
bai tashi ba har sai da Abban yazo gidan da
kansa daukan sa kamar yadda suka shirya,
ya kuma shigo har cikin gidan har dakin da
yake kwance ya same shi yana bacci,
takardar da ya gani a kasa ya sunkuya ya. takardar da ya gani a kasa ya sunkuya ya
dauka ya warware. Sai ya samu guri a gefen
katifar da Gidado yake kai ya zauna yana
kallon zanen yarinyar da yake hannunsa.
8:00 PM
Gidado yayi juyi sannan ya bude jajayen
idonsa ya dora su akan Abba, sai kuma ya
karasa bude don da sauri tare da mikewa
zaune yana shafa fuskar sa a kokarin kore
saurin baccin da yake kansa "Abba ka
shigo? Ina kwana" Abba ya bishi da kallo
sannan ya sake kallon takardar hannun sa.
Sai lokacin Gidado ya lura da takardar, ya
kara gyara zamansa yana shafa kai tare da
kallon takardar da gefen ido.
Abba ya nuna masa zanen tare da tambayar
sa "Safiyya?" Gidado ya gyada kai bai ce
komai ba. Abba ya nannade takardar ya ajiye
a tsakanin su yace "ba ka son waccan
yarinyar, zaka aure ta ne kawai saboda ni da
mahaifiyar ka muna son kayi aure" babu
alamar tambaya a cikin maganar dan haka
Gidado bai bada amsa ba. Abba ya cigaba
da cewa "abu na farko da na san ka riga ka
sani shine we only want what's best for you.
And right now, mantawa da wannan yarinyar
shine the best thing for you" ya fada yana
nuna zanen Safiyya with bitterness in his
voice, abinda yake nun irin haushin Safiyya
da yake ji a ransa. Ya cigaba da magana,
"mun yanke shawarar aure shine babban
abinda zai taimaka maka wajen mantawa da
ita maka kayi moving forward. Sai dai daga
ni har mahaifivar ka are not perfect, kuma. ni har mahaifiyar ka are not perfect, kuma
bama ganin gaibu, zata iya yiwuwa abinda
muka zaba maka ba shine alkhairi a gare ka
ba, amma ni na san wanda yake perfect
wanda kuma ya san gaibu, Allah. Ina son zan
baka wani assignment, idan kayi shi dai dai
zaka samu reward mai girma. Ina so kuma
inyi maka wani alkawari. A cikin kwanakin
nan da suka rage kafin daurin auren ka, ina
so kayi istikhara, idan har kafin daurin auren
ka cigaba da jin a ranka cewa still ba ka son
aure to ka gaya min, ko da kwana daya ya
rage zan dakatar da abin domin ya tabbata
ba alkhairi bane ba. Amma idan kaji a ranka
cewa ka amince kana son auren yarinyar, to
sai mu cigaba da shirye shiryen mu har mu
tabbatar da faruwar abin".
Ya mike tsaye yana kallon sa yace "ka tashi
ka shirya, your new job awaits you ", Gidado ya karbi shawarar Abba sosai, dan
tun da suka yi maganar ya dukufa da yin
adduoin neman zabin Allah. Babu dare babu
rana. Ya kuma cigaba da shirye shiryen duk
da suka kamata na bikin. Yan'uwansa sunzo
na kusa da na nesa, maza da kuma mata. Da
yake Abba da Mama first cousins ne sai ya
zamana yan uwan duk daya ne babu
banbanci, duk kuma treatment daya ake
basu.
Yan'uwansa samari da suka zo gari suka
kuma fahimci a gidan da yaje ya boye kansa
duk sai suka tattaro suka dawo gidan,
sa'annin Gidado suna bangaren da yake
while sa'annin Haidar suma suka tare a
bangaren da yake. Gidado bai ji dadin haka
ba saboda an takura masa an hana shi zama
yayi hira shida zuciyarsa, shi da safiyyan shi.
Sai dai kuma a wani bangaren yaji dadin
hakan dan cikin kwanaki biyu kacal sai gashi
yana hira da dariya sosai a cikin su. Wani
lokacin idan suka nutse a cikin hira har
mantawa yake yi da cewa wai aurensa ake
yi, kuma wai baya son yarinyar da zai aura.
Sai dai kuma yana iyakacin kokarin sa gurin
danne wa dan baya son yanuwansa su
fahimta har suyi ta yayata maganar a cikin
dangi. Sai dai kuma yanuwan are making it
extra difficult for him. Casually someone
would ask him "ina yarinyar nan kuma da ka
susuce akan ta kwanan baya?" His answer
to that question was always "Allah yayi mata
rasuwa" daga haka ba sa sake tambayar sa.
In wani ma ya dauko tambayar sai a samu In wani ma ya dauko tambayar sai a samu
wani ya hana shi dan kar su taba wa angon
feelings din sa. Sometimes kuma su kan
tambaya "wannan gidan na ka ai yafi
wancan girma Gidado, me ya sa ka chanja?"
And shi kuma ya kan amsa musu da cewa
"amaryar ce tafi son wancan". Alhalin ita
amarya ko gain gidan ba ta taba vi ba sai
da masu yi mata jere suka je suka yi suka
dauko mata pictures da videos.
Gidan da za'a kai amaryar mai kyau ne, dan
sosai iyayensa suka nuna masa gata a siyan
gidan kamar yadda suke nuna masa gata a
komai. Part dinsa daban na matar daban
sannan a waje kuma akwai bangaren baki
maza sannan da part din ma'aikatan gida
(boy's quaters). A bangaren sa akwai
bedrooms biyu da parlor, a nata bangaren
akwai bedrooms uku da parlor. Part din
bakin kuma parlor ne karami da dakuna
biyu.
Kamar yadda iyayen ango suka yi kokari
wajen kure adakar su akan gidan Gidado
haka bangaren amarya su ma suka yi nasu
kokarin, dan duk dakunan da suke part dinta
babu inda ba'a cika shi da kaya ba, kaya
kuma na gani na fada wa da suka yi dai dai
kuma suka dace da tsaruwar gidan. Abin har
sai da ya bawa dangin angon mamaki, dan a
binciken da suka yi wa iyayen amarya basu
samu labarin cewa suna da irin wannan
kudin ba,
A bangaren amarya tun a week to bikin A bangaren amarya tun a week to bikin
Mommy ta tafi can Katsina suka cigaba da
kammala shire shiryen su, duk wani shiri da
za"a yi wa amarya na gyaran jiki anyi wa
Safina shi, ita kanta ta san tana da kyau, ta
kuma shirya siye zuciyar angon na ta da
wannan kyan nata da kuma duk kan wata
kissa da kisisina da Allah ya halicci mata da
ita. Ta san cewa akwai challenge a gabanta
amma kuma ta shirya karbar sa hannu
bibbiyu dai har zata samu muradin
zuciyarta. Ta yarda da kalmar hausawa da
suke cewa mahakurci mawadaci.
Mommy tayi mata shirin duk da akeyi na
gyaran amare dan taimaka musu wajen
sauke hakkin aure da zai hau kansu, amma
Mommyn ba ta san cewa ita ma da kanta
Safinar ta gama siyan duk wadannan kayan
har ma da wadanda suka fi na Mommyn. A
shirye take tsaf da yin amfani da dukkan
baiwar da Allah yayi mata wajen ganin ta
mallaki Habibin na ta.
5
+ 1 4:15 PM
anar Lahadi ta tafi garin Abuja. A ranar ne
kuma bayan kiran wayar angon sau ba adadi
kamar yadda ta saba kullum ba tare da kiran
ya shiga ba sai ta tura masa message. "Na
shigo Abuja, Dan Allah ka zo in ganka, Ina
gidan Hajiya" Sakon ya shigo masa ya
karanta ya rufe ya ajiye,
A ranar da ya rage saura five days daurin
aure ne gidan da angon ya ke ciki ya kara. aure ne gidan da angon ya ke ciki ya kara
cika fiye da kullum, yan uwan sa da suka 20
gari suma sun gayyato abokan su da suke
gari, wasu abokan kuma sun gayyato nasu
abokan. Gidan ya zama kamar wani dan
karamin biki ake yi amma na maza zalla.
Mama kuma ta daure musu gindi ta hanyar
aiko musu da kulolin abinci kala kala. Daga
nan sai hira ta balle, aka fara zancen aure da
rayuwar cikinsa da challenges din sa, masu
auren ciki suna baje fasahar experience din
su, yayin da samari suka baje kunnuwa suna
daukan darasi. Wannan ya sa angon ya
zame ba tare da sun sani ba ya fice ya bar
musu gidan. Sai da ya shiga motar sa kuma
sannan ya fahimci bashi da gurin zuwa, dan
duk friends din sa da zai iya zuwa gurin su
suna cikin gidan sa, a lokacin ne sakon
Safina ya sake shigowa. "Na gama abinda
zanyi a Abuja. Gobe aka ce in koma. Dan
Allah ka shigo".
Ya rufe idonsa yana tunani for some
seconds sai kuma ya bude ya kira number
din ta. Tana dauka yace "gani nan zuwa" bai
jira amsa ba ya katse kiran. Mintuna kadan
suka kaishi kofar gidan, mai gadi ya taho da
sauri da fara'a a fuskar sa amma sai Gidado
ya bata rai tare da daga masa hannu alamar
baya bukatar zuwan sa, sai da mai gadin ya
juya sannan kuma sai yaji babu dadi a ransa
tunda mutumin bai yi masa komai ba. Ya
dauko wayarsa ya sake kiranta "ina waje"
yace tare da sake ajiye wayar.
Few minutes sai gata ta fito. Jikinta sanye Few minutes sai gata ta fito. Jikinta sanye
da hijab fuskarta babu kwalliya. Ta bude
kofar gaban motar ta shiga ta zauna, sai ya
dauke kansa yana jin haushin ta zauna a
seat din Safiyya. Amma kuma ai shi ya kira
ta. And only God knows me Safiyya take yi
with her husband, why won't him enjoy
himself too?
Ta fara mishi magana "har na fitar da rai na
dauka ba zaka zo ba. But now I am glad
tunda kazo" ya juyo yana kallon ta fuskarsa
a matukar daure yace "me yasa kike
nemana?" Tana kallon sa tace "what's with
that face? Ko nayi wani laifin ne kuma ban
sani ba, I just wanted to see you kuma
banga abin laifi dan ina son ganin ka ba".
Yace "what's wrong with my face? I thought
ita kika gani kika ce kina so" ta sunkuyar da
kanta kasa fuskarta tana nuna damuwa tace
"na san nina ce ina son ka ba sai ka goranta
min ba. Kawai naga ranka a bace ne. Ni face
din da nayi falling in love with is always
happy always smiling" yace "you better get
use to the unsmiling face. Because you are
going to see a lot of it" suka yi shiru gabaki
daya, sai da aka jima sannan da dago kai
tace masa "dama nazo gari ne zanyi kunshi
da saloon, and da akayi min kunshin sai na
ga yayi kyau sosai, and I thought ya kamata
kai zaka fara gani, I never thought hakan zai
zama laifi".
Yace "are you telling me kin taho tun daga
Katsina zuwa Abuja kawai dan kiyi kunshi?
Duk masu kunshin da suke Katsina ba zasu. Duk masu kunshin da suke Katsina ba zasu
yi miki ba?" Ta dago kai tana kallon sa tace
"actually, na fadi haka ne kawai a gida dan
su barni in taho, Mommy like classy things
and ta san a Abuja zan fi samun taste din ta,
but in reality I just wanted to get away from
her" yayi mamakin jin haka yace "why?"
Tace "fada. Tun da taje Katsina take yi min
fada. She is not happy with this marriage
saboda bata san ka ba, she kept
complaining cewa bata san sanda muka
hadu ba ballantana sanda muka saba har
zamu yi aure. Farko bata kasar, da tazo
cewa tayi sai an daga. Da kyar ta yarda za'a
yi din" tayi shiru tana jujuya hannunta
sannan tace "she said you don't love me.
Tace ko waya bata ga muna yi ba. There is
no love vibes at all".
Ya juya fusakarsa yana kallon window, sai
kuma ya juyo yace "you know our
agreement. And you agree with my
conditions" tace "yes, I know. And ba
complain nake maka ba. I just need a little
bit of gesture from you. At least make it
easy for me". Yace "let me ask you a
question.
5
4:15 PM
Why do you agree to this? Me yasa kika
saka kanki a wannan situation din?" Tayi
shiru tana tunani sannan tace "I love you,
That is all that I know, Kuma na san I am an
easy going person, bani da matsala, You
may not love me know saboda yarinyar da
kake so, but eventually you will fall in love. kake so, but eventually you will fall in love
again. And the easiest way to make you fall
in love with me is to marry you. Yanzu misali
ita yarinyar da kake so din, I don't want to
know her name, idan da zaka samu chance
din auren ta even though bata son ka, won't
you take the chance?" Yayi shiru yana
tunani, sai kuma yayi sauri ya kawar da
tunanin daga ransa yace "she loves me, so I
can't relate to that" tace "she loves you and
she left you?"
Bai amsa ba sai ya dauke kansa gefe yana
kara jin haushin ta, amma kuma yasan
abinda ta fada gaskiya ne, shi kansa kuma a
yanzu bashi da tabbas din in Safiyya tana
son sa.
Suka sake yin shiru a motar sannan yace "if
that's all. Zan koma. I have things to do" tayi
ajiyar zuciya "Okay. Nagode da ka samu
damar zuwa. Ina neman alfarma amma guda
daya. Please ka bari in ringa kiran ka. At
least saboda hankalin Mommy ya kwanta"
ya bata
pan't you call someone and
pretend cewa da ni kike? I am a little bit
busy for phone calls" ta dago ido tana kallon
sa, kawai sai yaga hawaye yana bin fuskarta,
ta saka hannunta da ya sha kunshin amare
yayi kyau a farar fatar ta ta goge hawayen
sannan tace "okay, Na fahimta, Thank you",
Ta bude kofa zata fita sai kuma yaji babu
dadi a ransa yace "Safina wait" ta dakata
amma bata juyo ba sai dai yana jin alamar
kuka take yi yace "I am sorry, Okay, Zamu ke. kuka take yi yace "I am sorry. Okay. Zamu ke
yin waya. Sai menene kuma kike so" ta juyo
hawaye yana cigaba da zuba a fuskar ta
tace "at least stop being mean to me. Ko
baka nuna min soyayya ba ka daina
wulakanta ni. It hurts a lot. You have no idea
how much I have sacrificed for this
relationship. The least you can do is to be
nice to me".
Bai sake magana ba ta fita daga motar ta
rufe masa kofa. Sai da yaga ta shiga gida
sannan ya tayar da motar ya tafi yana jin
zuciyarsa duk tayi masa nauyi. Baya jin
da din yadda yake treating yarinyar amma
baya iya hana zuciyarsa gaya mata abinda
yake cikin ta. Kuma kamar yadda ta fada
masa, ko da bai so ta ba the least he can do
is to treat her nice. Treat her kamar yadda
yake treating sauran mutane, or more.
Albarkacin tarin soyayyar da take yi masa.
Gidan Abba ya wuce, ya tarar ana kokarin
shiga sallar magrib sai ya bisu suka yi sallar
itare
ayan sun fito daga masallacin ya
samu ya shiga ciki ya gaishe da sisters din
Mama da ya gani a parlor sannan ya wuce
cikin bedroom dinta ya gaishe ta itama. Har
ya tashi zai tafi sai ta tambaye shi ko akwai
abinda yake bukata yace a'a, sai kuma ta
sake tambayar sa "ya kuke ciki da Safina
kuwa? Kuna waya ma kuwa?" Ya dawo ya
durkusa yana shafa kansa yace "yanzu ma
daga gurinta nake. Tazo gari taje gurin
kunshi" Mama tayi murmushi, yaga alamar
jin dadin hakan a fuskarta sannan tace "to jin dadin hakan a fuskarta sannan tace "to
madalla, hakan yayi kyau sosai. Allah yayi
maka albarka" yace "Amen" a ransa yana
jin dadin abinda tace din sosai.
Tun a mota kafin ya bar gidan ya cire wayar
sa daga do not disturb din da ya saka ta
saboda Safina. Washegari da safe da ta kira
shi sai kiran ya shiga ta sanar masa cewa
zata koma shi kuma yayi mata fatan alkhairi.
Da ta sauka a Katsina ma ta sake kiransa ta
gaya masa cewa ta isa, yayi mata sannu,
sannan reluctantly yace ta gaishe masa da
Mommy.
Daga nan suka fara magana, sama sama,
yana replying messages dinta in ta kira
kuma yana amsawa. A haka har ta turo masa
hoton kunshin da aka neme shi musamman
dan a nuna masa amma yaki gani, and he
replied with "yayi kyau".
Kamar yadda aka tsara ranar alhamis aka
fara biki
akayi kamun amarya a can katsina
a gidan wan babanta. Mommy ta gaiyaci
mutanen ta sosai sun je anyi komai da su,
yan uwan ango ma an ware representatives
sunje anyi kamun a gaban su a inda kuma
suka samu tarba ta musamman daga gurin
Mommy dan sai da ta tabbatar ta fitar da yar
tata daga kunya a idon su.
A
4:15 PM
A ranar kuma aka shirya za'a yi kamun ango
shima a nan Abuja, Sai dai kuma, tun. tun a
safiyar ranar ne da samari yanuwan ango
suka tashi a gidan da suke zaune tare da shi
sai suka neme shi suka rasa, sai maigadin
gidan ne ya gaya musu cewa tun assubar
fari ya fice daga gidan a motarsa. Aka yi ta
kiran wayar sa kuma bata shiga. Wasa wasa
har rana ta yi sosai babu ango babu
labarinsa. Tun suna boyewa suna cigaba da
bincike su kadai har suka sanarwa da iyaye
halin da ake ciki. Ango ya gudu. Ana ta kiran
wayarsa kuma tana ta ringing amma baya
dauka. Farko duk wanda aka gaya wa cewa
ango ya gudu sai yayi dariya thinking cewa
wasa akeyi, sai daga baya kuma sai a
fahimci cewa babu wasa a cikin lamarin.
Neman duniyar nan akayi wa angon aka rasa
shi har lokacin kamun yayi.
A gidan kakannin su aka tsara cewa za'a yi
kamun. Amma rashin gain angon ya saka
aka tattaro aka dawo nan gidan su angon
ana ta lissafin yadda za'a yi, auntyn sa
Maimoon sai dariya take yi dan ita dai ta san
Muham had Gidado ba zai bata ba kamar
wani key din mota, yayin da Aunty Amina ta
dage sai fada take yi akan ya basu kunya
sun tara mutane ya gudu ya bar su, da ya
san ba zai tsaya kamun ba ai da sai ya fada
musu da wuri su san abin yi. Hafsat kuwa sai
kallon su kawai take yi dan dama ita bata ga
amfanin kamun nan ba, daga baya dai da
taga magana taki ci taki cinyewa sai ta kira
Al'ameen ta zare masa ido tace sai ya fadi
inda Gidado ya shiga, yayi ta rantse rantsen
cewa shima wallahi bai sani ba, sai da ta. cewa shima wallahi bai sani ba, sai da ta
fahimci da gaske yake sannan ta rabu da
shi.
Ana cikin haka Abba ya shigo, ya zauna yana
binsu da kallo yana murmushi. Amina ta
kalle shi tace tabbas yasan inda Gidado
yake tunda bai nuna ya damu ba. Yace "to ni
akan me zan damu? Tsakanin ku ne da shi ni
babu ruwa na. In kuka kama shi duk abinda
kuka ga dama kuyi masa" sai kuma ya saka
hannu a aljihu ya dauko wayarsa ya kira
number din Gidado, shi ya san indai da ran
Gidado da kuma lafiyar sa babu yadda za'a
yi ya kira shi yaki dauka.
Yana kiran nasa kuwa ya dauka din, direct
yace masa "kana ina?" Gidado yayi shiru
kamar ba zai amsa ba sannan yace "ina daki
na" yace "wanne dakin?" Yace "dakina na
gidan mu". Abba yayi shiru yana jin yadda
muryar Gidado tayi kasa sosai, and he can
almost feel halin da zuciyar dan nasa take
ciki. Yace "iyayenka suna neman ka zasu
kama ka" Gidado yace "Abba ni da ba
criminal ba me nayi da za'a kama ni?" Abba
yace "tsakanin ku ne wannan. Ni dai yanzu
ka ban amsa ta. Za'a yi ko ba za'a yi ba
mu?"
Daga Gidado har abban nasa sun fahimci
cewa ba wai maganar kamu suke yi ba
yanzu, Gidado ya sake yin shiru. Abba yace
"yau kadai ta rage maka" still bai ce komai
ba, Abba yace "ina jin ka" Gidado yace a
hankali "za'a yi. Na amince ayi". hankali "za'a yi. Na amince ayi",
Daga nan Abba ya katse wayar ya juya yana
kallon yan'uwan nasa da suka saka shi a
gaba suka tsare shi da ido. Ya kalli Amina
yace "na ga kin damu dai da cewa sai kin
jika yaron nan da nono, me zaki bani idan na
gaya miki inda yake?" Tayi shiru tana tunani
sai kuma tace "in dai ka gaya min inda yake
daga yau zan dinga gaishe da matarka ina
ce mata yaya" duk suka kwashe da dariya.
Shekara da shekaru dama suna wannan
rigimar tsakanin Amina da Zainab. Zainab
kamar kanwa take a gurin Amina amma
kuma mijinta kamar Yayan Amina ne (if you
know you know ») dan haka kowa a cikin
su ya dage lallai sai dayan ya bashi girma.
Abba ya mike tsaye yace "yana dakin sa"
sannan ya fice ya bar musu gidan. Ai kuwa
Amina ta sunkuci turaren da ta taho dashi
tayi dakin Gidadon sauran yan'uwa suna
binta, taje kuwa tayi ta gudun kofar duniyar
nan yaki budewa sai da Mammy tayi masa
magana tare da yi masa alkawarin ba za'a
zuba masa nono akai ba sannan yayi
Ami
la
A bangaren Gidado ranar tun da assuba
daya tashi ya yanke shawarar amsar da zai
bawa Abba, Saboda shine abinda yaji
hankalin sa yafi kwanciya dashi, bawai dan
yaji a ransa yana son Safina ba, but yaji a
ransa cewa auren shine abinda ya dace
dashi, shine abinda hankalin sa ya kwanta
dashi a wannan lokacin, The decision made him sad but free at the
same time. Sad that he will have to made
the final acceptance of the fact that Safiyya
ta bar shi har abada, that his life has
changed forever. Wannan yasa ya lallabo ya
shigo gidan su ya shige dakin sa ba tare da
kowa ya ganshi ba, making sure cewa ya
boye motarsa a inda ita ma ba za'a ganta
ba. Farko kwanciya yayi yayi baccin sa sai
azahar ya tashi yayi sallah sannan ya kama
yin aikin da yazo dakin da niyyar yi, aikin
tattare duk wasu kaya nasa da duk wani abu
nasa da yake da dangantaka da Safiyya,
including his phone and his laptop da suke
cike da hotuna da pictures dinta, ya hada su
ya zuba a wata locker ya rufe.
A binciken nasa ne ya dauko wata rose
flower single stem da Safiyya ta taba bashi.
Ya tuno lokacin da ta bashi din da kuma
dalilin da ya sa yake ta ajjiye da ita.
Suna tafiya ne ranar nan a hanya kamar
kullum yana yi mata korafin har yanzu bata
kai shi gidan su ba, kar yaje ayi mata miji a
gidlan su a raba shi da ita tunda ba'a san shi
she kept telling him cewa ba za'a iya
raba su ba amma a karshe yace dai shi
bama shi da tabbas din tana son sa da
gaske ba wasa take yi masa da hankalin sa
ba, suna maganar ne tayi ta tsinkar flowers a
jikin bishiyoyi tana hadawa, sai da ta tara da
yawa sannan ta cire ribbon din data daure
gashinta da shi ta daure flowers din da shi ta
bashi, tace symbol ne na son da Safiyya
take wa Muhammad, Yaji dadi sosai kuma ya. take wa Muhammad. Yaji dadi sosai kuma ya
karba, but He jokingly said "wannan ai gaibu
ne, ana jima wa zasu yi wilting su bushe su
mutu. I need something that is a forever
thing. Wanda zai nuna min matsayina is a
forever one a gurin ki. Something like zuwa
gaishe da Daddy",
A week after that, a jewelry company
delivered that rose to him. Single stem ne na
kyakkyawar red rose flower. An nannadeta
da transparent plastic sheet. A jikin sheet
din anyi rubutu da golden color in her own
handwriting.
Muhammad,
This feeling is a forever thing.
Your's
Piya
Amma abinda ya saka shi mamaki a lokacin
shine kasancewar jewelry company ne suka
yi delivering sakon. Sai da ga baya ya
fahimalalili. A kasan rose din, dan box din
da aka zura stem din rose din a ciki, was
made of gold, pure gold molded into the
shape of a heart with their initials scribbled
on it "MS".
It was too much of a gift da yaji a ransa
cewa bai kamata yayi accepting ba, that
gold is a fortune, Ya tabbatar a gida ba'a
san tayi wannan kyautar ba, Amma kuma he. san tayi wanna kyautar ba. Amma kuma he
so much love it da ya kasa mayar mata.
Wannan ya sa ya boye ta a inda yasan babu
wanda zai ganta da niyyar in sunyi aure sai
ya bata abinta.
But now it is never going to happen. Sai ya
samu kansa da jujjuya rose din a hannun sa
yana wondering me zaiyi da iya yanzu. A
karshe sai ya koma kan gado ya kwanta
rigingine ya dora rose din akan kirjinsa ya
rufe idonsa. Yana jin wayarsa tana ta kara,
kuma a ransa ya san cewa nemansa ake yi
amma haka yayi ta kwanciyar sa, sai dai
damuwar sa bata saka a ransa yaji cewa ya
fasa yin auren ba. A haka akayi la'asar ya
tashi yayi sallah ya koma ya kwanta,
deciding cewa ba zai je gurin kamun sa ba.
Duk wadanda suke kiransa yana gani, kuma
ya yanke shawarar ba zai dauka ba. A haka
har wanda ba zai iya kin daukan wayar ta sa
ba ya kira shi. Ya dauka, ta tambaye shi
game da decision dinsa kuma ya gaya masa
amsar.
Bai jima da ajiye wayar ba yaji bugun kofa da
kuma muryar Aunty Amina tana mishi
magana
filatanci "na san kana ciki, ka
bude kofar nan" ya tashi zaune yana dafe
kansa, Suka cigaba da hayaniya da kuma
bugun kofar. Bai ce musu komai ba sai ya
tashi ya kammala adana dukkan kayan da
yake bukatar adana wa including the forever
rose sannan ya tsaya a bakin kofar, a lokacin
yaji muryar Mammy tana masa magana, Yayi
murmushi ya amsa mata da fulatanci. murmushi ya amsa mata da fulatanci.
"'Amma banda nono za'a zuba min" tace "eh
banda nono" yace "kinyi alkawari?" Tayi
dariya tace "nayi alkawari" sannan ya bude
kofar, yana budewa suka feshe shi da
turaruka kala kala sannan aka dauki guda.
Duk da cewa turarukan sunyi masa karfi aka,
amma sai ya samu kansa da yin murmushi
yana jin dadin gain iyayen nasa cikin farin
ciki.
6
4:15 PM
Zuwa dare sai gashi yana hira a cikin su
harda dariya, ranar gabaki daya familyn
anan suka ci abincin dare sannan suka raba
dare suna hira, sai da bacci ya fara cin karfin
sa sannan ya zame jikinsa ya koma dakinsa
ya kwanta acan.
Da safe ya tashi da wuri kamar yadda aka
tsara ya shiga wanda, saboda da wuri zasu
tafi gurin daurin auren, yana fitowa daga
wanka da bathrobe a jikin sa sai ya ga Mama
a zaune akan gadon sa da kayan sawa na
maza a hannunta tana fesa turare a jiki. Ya
rissina ya gaishe ta yana jinsa wani iri
saboda
bu kaya a jikinsa amma sai yaga
ita ko an xinta, Ta mika masa kayan hannun
ta, fuskarta dauke da alamar damuwa, tace
."ga kayan da zaka saka nan. Dan banga ka
tanadi kayan sakawar yau ba" ya karba tare
da yi mata godiya, bata amsa ba sai tace
"kayi sauri ka shirya, baban ku har ya
shirya" ya ce "to" amma sai ua cigaba da
tsaiwa da kayan a hannun sa tunda dai ai ba
zai saka kava a cabanta ba, zai saka kaya a gabanta ba.
Ta mike a hankali kamar bata son fita. Har
takai bakin kofa sai kuma ta juyo tana kallon
sa tace "Muhammad?" Ya amsa, sai tace
"are you happy?" Yayi shiru yana kallon
damuwar da take rubuce a fuskar ta sai ya
girgiza kansa yace "no, I am not happy
Mama. But I am contented, alhamdulillah"
tace "good. That's a good start. Allah yayi
maka albarka".
Sai da ta fita sannan a hankali yace "Ameen
Mama"
Ya shirya ya saka kayan da Mama ta bashi.
Farin yadi ne tas da akayi wa aiki mai kyau
kalar ruwan toka mai haske, wanda ya dace
da hula da takalmin da ta ajiye masa. Ya
tsaya a gaban madubi yana kallon yadda
yayi kyau, shi kansa ya san yayi kyau ba
kadan ba. Ya tuna maganar Safiyya "You will
look so good in white"
Sai yayi murmushi. "Good bye Piya".
Daga nan ya juya ya fita tare da rufe kofar
dakin, kna
wing he will come back a changed
man, al
tried man. Maybe even a happy
man. Abinda bai sani ba shine a yanzun ne
zai bude babi mai cike da rikici da sarkakiya
a rayuwar sa, Yanzun ne matsalolin zasu
fara,
*Her
Ranakun gudu suke yi, musamman idan ina. Ranakun gudu suke yi, musamman idan ina
lissafa su a matsayin kwanakin da suka rage
a daura min aure da Mukhtar, amma kuma
lakaki suke yi idan na kalle su a matsayin
ranakun da suka rage ayi min aiki a raba ni
da abinda yake ciki na.
Duk shire shiryen aikin sun kammala a
asibitin da za'a yi, sun dauki dukkan vitals
dina sun tanadi dukkan abinda suke ganin
zan bukata. Sun kuma tanadi dukkan abinda
babyn da za'"a ciro zai bukata tunda zai
zamanto premature ne kuma zai bukaci
kulawa ta musamman. Yayinda ni kuma na
kammala dukkan shiryen shiryen bayar da
babyn kamar yadda na riga nayi niyya.
Sharuda na sune bana son ganin shi, bana
son Daddy ya ganshi, bana son kuma in an
samu parents din da suke son sa a basu
wani information da ya shafe ni ballantana
har nan gaba yayi amfani da information din
gurin sanin ko ni wacece.
A gida kuma kullum muna cikin rigima da
Daddy, muyi rigima yayi fushi ya sauko da
• kansa ko kuma ni inyi fushi ana jima wa
kum
sauko inje in bashi hakuri. Duk da ya
amine da maganar Mukhtar amma yaki
hakura da kokarin chanja min ra'ayi na.
Sannu kuma har yanzu bai yarda da magana
ta ta cewa ba zan koma Nigeria ba. He kept
saying akwai plans din da ya shirya min in na
koma Nigeria, But he wouldn't say what.
Mutanen kadai da nake samun fahimtar juna
da su sune twins, Kullum sai muni hirar mu
a waya. Suna kuma updating dina akan duk. a waya. Suna kuma updating dina akan duk
abinda yake faruwa a gidan. Su suka bani
labarin rikicin da ake tayi tsakanin Mommy
da Safina, a fahimtar su ita Mommy hankalin
ta bai kwanta da wanda Safina zata aura ba.
A kalaman ta kamar yadda suka fada min
"shegen girman kai ne da shi da isa kamar
wani dan sarkin Makkah"
Sun so Daddy ya bar su su taho su zauna
tare da mu amma yaki, ni na fahimci baya
son Mommy ta sake jin haushi tace ya
kwace mata su, shi lallai so yake a daidaita.
Kusan kullum kuma in muna waya sai sunyi
min maganar Hajiya, tana ta damn su da
tambaya akai na, ta damu da ni, musamman
da taji cewa za'a daura min aure.
"Kin san bata san halin da kike ciki ba.
Mommy bata gaya mata ba. Tace Hajiya
bakinta bashi da linzami"
6
2
4:15 PM
1
'"Bata gaya mata ma maganar rikicin da suka
yi da Daddy b
dasan idan da ta gaya mata
'da zata iya yi
yaya Safina kayan daki
amma kuma da kowa a gidan bikin sai yaji
labari"
Nayi murmushi, a yarda da maganar
Mommy a nan, Hajiya tana da kirki sosai,
ammà indai magana ta shiga ta kunnen ta to
sai ta fita ta bakin ta, Kuma ba wai da niyyar
munafunci ba. Haka Allah yayi ta bata san
wani abu wai shi sirri ba, Da ake zata san da. wani abu wai shi sirri ba. Da ake zata san da
zancen cikin nan nawa, zata tausaya min
sosai ta bani dukkanin kulawa, bayan ta
gamai min fada, amma kuma kowa da yake
gidan da wanda zai shigo gidan sai ya san
maganar.
Safina har da turo min pictures din gidanta
sanda aka gama jerenta, sannan tayo min
message din godiya. Ranar kamun ta ma
haka ta turo min pictures din kyalliyar da
tayi, telling me that taso ace ina nan.
Sannan sai washegari, washegari ranar
daurin aure. Ranar dama ban samu baccin
kirki ba saboda lissafin rayuwa. Haka na
gama daren akan sallaya ta. Gari yana
wayewa nace saura kwana daya. Ina nan kan
sallayar har lokacin in abincin Daddy yayi
naje na hada masa, yanzu baya iya cin
abinci mai tauri sai mai ruwa ko kuma wanda
aka dafa yayi laushi sosai.
Naje na kai masa na tashe shi zaune ya
dauka yana ci, baya son inke bashi abinci a
baki yace cin abincin da kansa ma wani
exercise ne. Yana ci yake tambayata ko na
gaml
da kaya na na zuwa asibiti nace
masa na gama, dama da yamma zan tafi, a
can zan kwana. Ya sake tambayar ko akwai
abinda nake bukata nace masa a'a. Ni kuma
na sake yi masa maganar cewa bana son ya
bini asibiti gwara yayi zamansa a gida tunda
Aunty Hajjo zata je amma ya nuna min ba zai
zauna a gida ba, Sometimes na kan yi
tunanin a gurin sa na gado taurin kaina duk. tunanin a gurin sa na gado taurin kaina duk
kuwa da cewa shi kullum cewa yake yi a
gurin Ammi ne.
Sai da nurse din shi yazo ya hada masa
ruwan wanka zai taimaka masa yayi sannan
na fita na koma parlor na zauna. Gaba na sai
faduwa yake yi. Nayi tunanin maganar aiki
na ce take damuna amma kuma ban taba
damuwa da ita ba why will I now. Ina nan
zaune har wajen azahar nurse din ya fito
yace zai je ya dawo, ni kuma na tashi na
shiga kitchen zan nema mana abinda zamu
ci da rana.
A lokacin ne wani tunani ya fado min. Twins
sunce 11am za"a daura auren Safina. Na kalli
agogo naga 12:30 ma'ana 11:30 kenan a
Nigeria. Sai nayi tunanin ko an daura? Na
shiga kitchen din na dora abincin sai na
dawo daki nayi sallah kafin abincin ya
kammala., Sai da na idar nayi adduoi na
sannan na dauko waya ta zan duba ko twins
sun turo min labari. Ina shiga kuwa naga
méssage from Hussein.
"'Yaya an daura auren Yaya Safina. We are
missing you here ke da Daddy"
Naji babu dadi a raina, nima ina missing din
su, Sai naga ya dora status, nayi sauri na
bude dan nasan pictures din daurin auren
ne,
A lokacin ne na ganshi, A lokacin ne na ganshi.
Sai da na ajjiye wayar na saka hannayena
biyu na murza idona dan in kawar da gizon
da yake min, saboda kwanan nan ba a
mafarki ba har a ido biyu gizo yake min in
ganshi kamar ya shigo gidan ko kuma inji
kamar muryarsa. Na sake daukan wayar na
sake dubawa.
Muhammad ne, Muhammad dina, yayi kyau
fiye da yadda na taba tunanin zai yi. Yana
tsaye Hussein yana tsaye shima a kusa da
shi. Hussein yayi captioning hoton with
"Nayi sabon wa"
Menene wa? Shine tambayar da na fara yiwa
kai na. Me Muhammad yake yi a gurin daurin
auren Safina?
Sai dai hoto na gaba shi yayi kokarin amsa
min tambaya ta.
Muhammad din ne dai again, this time sho
da H
an da Hussein. Hussein ya rubuta
"With the groom. Allah ya sanya alkhairi"
Naji cikina ya daure, kwakwalwa ta ta toshe.
Na sake tambayar kaina "menene groom?
Me kalmar groom take nufi?"
Hoto na gaba ne ya hau da kansa ba tare da
na tura shi ba, Muhammad ne a tsaye da
Safina a kusa da shi. Ta ci kwalliva cikin farin. Safina a kusa da shi. Ta ci kwalliya cikin farin
lace din da na siya mata. Fuskarta dauke da
tsantsar farin ciki. A kasan hoton Hussein ya
rubuta.
"Amarya da ango"
89 7
3
3
4:15 PM
Na ajiye wayar tare da girgiza kaina kamar
mai kokarin tashin kaina daga bacci, amma
kuma ba baccin nake yi ba. Na dafa gadon
da yake gaba na na mike ina jin kamar kaina
yafi dukkan sauran jiki na girma saboda
kamar dukkan jinin jikina ya tattare ya koma
cikin kan, shi kansa bugun zuciya ta a cikin
kai na nake jin sa. In dai har da gaske ba
mafarki nake yi ba, ba kuma haukacewa nayi
nake hallucinations ba, to tabbas auren
Safina da Muhammad Gidado aka daura shi.
Na dafa bango na fara kokarin fita waje sai,
kuma na dawo dakin na dauki handbag dina
da take ajjiye akan side drawer na rataya, na
cigaba da laluben hanya har na fita parlor.
"Daday!"
Na fada da karfin da bansan ina da shi ba.
Na cigaba da tafiya ina gain gaba na yana
kara duhu duk kuwa da ba dare ne yayi ba,
Sama sama naji muryar Daddy yana
magana, "Safiyya! Lafiyar ki, Me ya faru? Ina
zaki je" na juyo inda naji sautin muryarsa
nace "gida zanje, Nigeria zan tafi, Daddy
Muhammad ne fa, Wallahi Daddy shine. Muhammad ne fa. Wallahi Daddy shine.
Daddy mutuwa zanyi. Daddy zuciya ta zata
fashe. Daddy mutuwa zany" na cigaba da
fadar sauran maganganun da ban san me
nake cewa ba yayin da jiri ya debe ni nayi
kasa.
Dishi dashi naga motsin Daddy ya mike
daga kan wheelchair dinsa yayo kaina, sai
dai kafin ya karaso ya yanke jiki ya riga ni
kaiwa kasa.
Sai da kaina ya daki center table din gurin
sannan ya karasa kasa. Na hango Daddy ya
sake yunkurawa zuwa inda nake fuskarsa da
cike da tashin hankali.
"Not my daughter. God please take me
instead" ya fada a hankali. Sannan kuma da
karfi yace "who is there? help us please.
Help!"
A hankali na sake ce masa "Daddy
Muhammad ne".
Sannan na rufe ido na into
nothingness....
Longest episode ever
Shin kina son wannan episode din ya zamar
miki taliyar karshe ko kina son kari....... ....
Muhammad dai ya auri Safina, while madly
in love with Safiyya, ba tare da yasan. Shin kina son wannan episode din ya zamar
miki taliyar karshe ko kina son kari..........
Muhammad dai ya auri Safina, while madly
in love with Safiyya, ba tare da yasan
dangantakar dake tsakanin Safina da
Safiyya ba.
Ga Safiyya kuma ta dauki hanyar lahira
bamu sani ba ko zata yi rai ko akasin haka.
In bata tafi lahirar ba ma she is set to marry
Mukhtar
Yaya wanna badakalar zata kare
Yaya wadannan aurarraki zasu kasance.
Menene ainahin labarin Safiyya da
mahaifiyar ta
Menene dangantakar su da Mommy
And above all, wanene uban cikin jikin
Safiyya.
Kina son wadannan amsoshin?
Na tabbatar kina so,
Turo naira 500 dinki zuwa wannan account
din
0779484.494
Nafisa Tafida Usman
Access Bank - Safiyya'
owner
8:51 PM
Episode Sixteen: Junior
Kukan jariri ne sound din da ya fara ratsa
consciousness dina, kamar a cikin kai na aka
saka min jaririn, kamar a cikin kwakwalwa ta
yake kukan cikin kokarin sa na karasa
tarwatsa kaina. Nayi kokarin juya kan amma
naji yayi min nauyi ga kuma wani irin ciwo da
yake min. A hankali na daga hannuna da
niyyar dafe kan dan saukakawa kaina a
zabar da nake ji, k kuma in toshe kunnena
dan hana kaina jin kukan jaririn, amma sai
naji an rike hannun nawa, sai kuma naji
muryar Daddy yana magana "Safiyya?
Careful kar kiji wa kan ki ciwo. Ku fita da
wannan yaron daga nan dan Allah".
Na dan motsa idona kadan ina jin a raina ina
son in kara gain fuskar Daddy one last
time, Na samu da kyar idon da yayi min
nauyi ya bude, na sauke su akan Daddy da
yake zaune akan kujerar sa a kusa dani
hannunsa rike da nawa, ban gane inda muke
ba amma na gane Daddy na, sai dai kuma ba amma na gane Daddy na, sai dai kuma
yayi mugun chanjawa lokaci daya yayi kamar
an kara masa shekaru akan nasa, yayi ramar
da ban taba gain shi da irin ta ba duk kuwa
tsahon shekarun da ya dauka yana jinya.
Na lura bayan shi akwai likitoci da suke
tsaye a kaina blue scrub a jikin su. "Safiyya"
Daddy ya sake kiran suna na "sannu! An fita
da shi. Ki ci gaba da baccin ki"., Na mayar da
ido na na rufe na cigaba da baccin kamar
yadda ya bukata.
A farkawa ta biyu ne nayi nadamar farkawar.
Hoton Muhammad tare da Safina an rubuta
amarya da ango a kasan hoton shine abinda
ya dawo dan cikin hayyaci na, kamar yadda
shine abinda ya fitar da ni daga cikin
hayyacin nawa tun farko. "Muhammad!" na
fada ina kokarin tashi daga kan gadon da
nake kwance. Na san dai an rike ni amma
ban san waye ba, naji kuma muryar Daddy
sannan naji ta Aunty Hajjo, daga nan kuma
naga wata maaikaciyar asibiti ta shigo da
sauri ta doso ni, sannan mercifully na koma
na cigaba da bacci na.
Sanda na sake farwakawa ido na akan
agogo ya sauka, karfe biyu da minti hudu na
gani, nayi ta kallon agogon ina tunanin
abinda hakan yake nufi. Biyun yaushe?
Biyun kuma wacce rana? Nayi kokarin juya
kaina in nemi window a dakin ko zanga hint
din in safiya ce ko dare amma ban gani ba.
Sai ma kaina da yake kara yi min ciwo a
kokarin juya shi da nake yi. A lokacin na. kokarin juya shi da nake yi. A lokacin na
fahimci a dakin asibiti nake, musamman
saboda yanayin gadon da nake kai da kuma
naurorin da suke zagaye da ni. Na duba
hannuna naga drip yana shiga cikin
jijiyoyina. A gefe na naga Aunty Hajjo tana
kwance akan wata kujera, daga dukkan
alama baccin da take ba mai nauyi bane ba.
Babu Daddy a dakin.
Na mayar da ido na na rufe amma kuma sai
baccin yayi kaura daga cikin su, abinda ya
faru ya fara dawo min a cikin kaina. Yadda
rayuwata ta fara so good and perfect, lokaci
daya ta juya zuwa terrible a karshe na rasa
komai. Na rasa komai including my chance
to marry the one person I love like crazy.
Na riga na lallaba zuciyata akan ta hakura da
shi, for his own sake, duk da dai har yanzu
zuciyar ta wa bata gama amince wa da
umarnin da na bata ba, tarin matsalolin da
nake ciki sune duke danne damuwa da
rashin sa, amma yanzu, after seeing his
picture with Safina, komai ya dawo min
sabo.
Tambayar da na samu kaina da yiwa kaina
ita ce "how?" Ta yaya Muhammad da Safina
suka hadu a cikin watanni biyu da yan
kwanaki har kuma suka yi aure? Muhammad
fa? The man I thought saboda san da yake
min zai jima bayan na barshi kafin yayi aure,
the same man that kept telling me how he
can not live without me. Then he married my
sister just few months da rabuwa da ni? Ta. sister just few months da rabuwa da ni? Ta
yaya zai yi min haka?
Na tuno maganar Safina da take gaya min
wanda zai aure ta ya turo mata friend
request a social media, they get talking and
he proposed yace yana son ya aure ta in few
months. Hakan yana nufin Muhammad shi
ya nemi Safina kenan. But why and how can
he do that? Na san ya san ina da step sister
mai suna Safina, na tabbatar munsha yin
maganar ta dashi, so it was easy for him to
find her and marry her, and dalili daya zan
iya fahimta a matsayin dalilin da yasa yayi
hakan, to get back at me for yaudarar sa da
yake tunanin nayi.
32
17
6
A 9 8:52 PM
Na mayar da ido na na rufe ina jin kaina yana
kara matsanancin ciwo.
And Safina. Mun sha maganar Muhammad
da Safina. Abinda bani da tabbas akan sa
shine idan ta san shi by face or not. Na san
basu taba haduwa ba, but she must have
seen his picture a waya ta, she must have.
Babu yadda zata yi tace bata taba gain sa
ba dan hotunan Muhammad a cikin waya ta
sun fi hotuna na ni kaina yawa. Wasu
hotunan ma shi kansa bai san sanda na
dauke shi ba,
Karya take yi tace bata gane shi ba,
Duk su biyun munafukai ne
Duk su biyun maciya amana ne. Duk su biyun maciya amana ne
Duk su biyun kuma sai sun gane kuran su
akan abinda suka yi min.
I have been good, but rayuwata have turned
to bad, now I am going to be bad sai in ga in
da akwai riba a wannan bangaren. I am
going to turn into a bad girl. I am going to
destroy their marriage even if it is the last
thing I will ever do.
Na fara planning a kaina na yadda zanyi
making life difficult for Muhammad da
Safina, babu irin plan din da ban hada ba.
None of which is a good thing. But to do
that sai na koma Nigeria. Na fasa zama anan
din kamar yadda a da na ce zanyi. Nigeria
zan koma. In gasa wa Safina da Muhammad
ava a hannun su. But to do that properly, I
will have to get rid of cikin jikina first.
Wannan mayataccen cikin a jikina.
Sai a lokacin hankali na ya dawo kan cikin.
Sai a lokacin tunanin da ya chunkushe a
kwakwalwa ta yay giving way for feelings.
And I felt empty a ciki na. Na bude ido da
sauri na kalli cikin. Babu. Na daga hannuna
wanda babu komai a jiki na shafa cikin, it felt
weird, it felt as if bayan babyn har kayan
cikina ma babu su. Naji wani relief na
rabuwa da cikin ya lullube ni, sai kuma fear
ta maye gurbin relief din. Ina yake? Masu
adoption din sun karbe shi? Yanzu Daddy ya
san na bayar da shi kenan? Me Daddy zai ce
akan hakan? san na bayar da shi kenan? Me Daddy zai ce
akan hakan?
Amma kuma dazu ina bacci naji kukan jariri.
It shouldn't be. Na riga nayi signing
agreement cewa daga ni har dangina ba
zamu ganshi ba ana cire shi za'a tafi da shi.
Bana son ganin shi. Bana son duk wani abu
da ya shafe shi.
Wani alarm naji ya fara beefing a jikin gadon
da nake. Naga Aunty Hajjo ta mike da sauri
tana kallona sannan ta danna wani button da
nake tunanin na kiran likitoci ne. Sai kuma ta
taho inda nake ta dafa kaina. "Relax Safiyya,
relax. You are alright. Everything is good.
You are going to be fine".
Wata nurse ta shigo da sauri tana kallon
abinda yake yin karar tace "her VP is
skyrocketing again" da sauri aunty Hajjo
tace "then do something" ni dai ina kallon
su dan ban fahimci abinda suke yi wa tashin
hankali ba. Mutuwa ce fa ba wani abu ba.
And mutuwa a gurina idan tazo zan kalle ta
ne a matsayin mercy dan na jima ina neman
ta da ma.
Muryar Abdul ce ta sake tashina a karo na
uku.
"This baby is sooo cute Umma"
Sai kuma muryar Aunty Hajjo
"Da Allah ajiye shi haka nan. Sai faman. "Da Allah ajiye shi haka nan. Sai faman
jagwalgwalashi kake yi. Dan ma yaron me
lafiya ne ai da ba zasu barmu mu zo dashi
dakin nan ba tunda preterm ne"
Ya sake cewa "bara in dan kara rike shi
kadan. Ai ba taba shi nake yi ba. Rike shi
kawai nake yi" tayi tsaki "kai ka sani kuma.
Da ka amince da abinda nace maka ai da
yanzu kai zaka raini wanna jaririn. Amma
kaki. Kayi wa kanka ai" yace "Umma ba fa ni
naki ba, ita ce ba ta zabe ni ba" tace "bayan
ka gaya mata kana da wadda kake so?
Wacce mahaukaciya ce zata auri namijin da
ya gaya mata yace baya son ta?"
Muryar Daddy naji yayi sallama. Na juya
kaina bangaren da naji muryar ta sa sannan
na bude ido na a hankali na sauke su a
kansa, ya turo kujerar sa kusa da gado na
yana kirkiro murmushin da ni na san ba na
gaskiya bane ba. "Safiyya. Kin tashi?" Ya
fada yana shafa gashin kaina. "Sannu. Ya
jikin ki? Me yake miki ciwo yanzu?"
A hankali na bude baki da muryar da naji
kamar ba tawa ba nace "Daddy. Gida zan
tafi. Nigeria zan tafi" yace "okay, Okay. I will
get us tickets right away, Kar ki daga
hankalin ki akan hakan. Any thing you want".
14
7
8:52 PM
Na dora hannu na akan cikina ina shafawa
sai ya rike hannun "kar ki taba ciwon" na
dago ina kallon sa ban ce komai ba sai
Sending messages is not allowed in this group. sai ya rike hannun "kar ki taba ciwon" na
dago ina kallon sa ban ce komai ba sai
Aunty Hajjo ta dawo daya gefen nawa tace
"jinin ki ne ya hau. Kika fadi. Aka kira
ambulance suka dauko ki suka kawo ki nan.
Dole aka cire babyn dan a samu damar
daidaita vp din ki. Har yanzu bata zama
normal ba but it is going down
alhamdulillah".
Daddy yana kallon ta yace "I heard she had
another arrest cikin dare ko?" Aunty Hajjo ta
dan yi murmushi "kar ka damu da haka
Daddyn Safiyya. She will be okay insha
Allah" na juya ina kallon ta sai tace "they
had to admit him too. Allah ne ya kare mu.
We almost lost the both of you. Whatever is
worrying you Fiyya keep it aside. Nothing is
worth damuwar da mahaifinki ya shiga. Ko
ba kya valueing taki rayuwar I am sure ta sa
matters a lot to you",
Sai ta koma da baya ta karbo jaririn daga
hannun Abdul shi kuma ya fita sannan ta
dawo ta mika wa Daddy tace "tun jiya naga
ta yar ka kake ba ku gaisa ba" ya gada
hannu ya karba, na dauke kaina gefe in jin
hawaye yana bin kuncina. Ba zan iya cigaba
da kallon yana yin fuskar Daddy a lokacin da
ya karbi babyn ba,
Ko a mugun mafarki ban taba yin wanda na
haifi shege ba, Ban taba yin wanda Daddy
yake rike da shegen jariri daga gare ni ba.
Babu abinda ba zan iya bayarwa ba a lokacin
idan da zan samu Allah ya dauki raina a. idan da zan samu Allah ya dauki raina a
gurin. Wannan kuma yana daga cikin dalilin
da yasa na zabi bayar da jaririn.
Muryar Daddy can ciki naji ace "Allahu
Akbar. Allah mai kyauta da kari. Allah na
gode maka. Na karbi wannan kyautar da kayi
min kuma na gode maka. Allah kayi masa
albarka ka bashi rayuwa mai kyau duniya da
lahira" naji Aunty Hajjo tace "Ameen ya
Rabbi".
Sai kuma Daddy ya dan yi yar dariya yace
"yanzu kai bawan Allah, upon all the people
in this big wide world, ka rasa da wanda
zaka yi kama sai dani?" Aunty Hajjo tayi
dariya "soyayya ce yake yi maka. Kauna kai
da shi har abada. Amma jarirai ba'a iya gane
kamar su lokaci daya, sai sun yi wayo sosai
sannan kamarsu take bayyana"
Sai Daddy ya mike da jaririn a hannun sa
sannan ya dora min akan cinyata, ganin bani
da niyyar rike wa sai Aunty Hajjo ta taho da
sauri ta rike sannan ta daga gadon da nake
kai na koma kusan a zaune sai ta kwantar da
shi akan cinyar ta ta saka pillow ta tare shi.
Na runtse ido na ina girgiza kai na "bana son
ganin shi Aunty, ki dauke shi daga jikina dan
Allah"
A daidai lokacin wata maaikaciyar asibitin ta
shigo da takardu a hannun ta, suka gaisa da
Aunty Hajjo sannan tayi bayanin cewa tana
son ta cike bayanai akan jaririn da aka haifa
ne for his birth certificate. Tambayar farko. ne for his birth certificate. Tambayar farko
ita ce menene first name dinsa. Tayi
tambayar tana kallo na, nima na bita da
kallo, to in har ni zata tambaya ni kuma wa
zan tambaya kenan?
Daddy ne ya amsa "Adam. His first name is
Adam" na juya ina kallon Daddyn. Tunda na
samu cikin nan babu abinda Daddy ya tsani
gani kamar cikin, abinda har ya jawo min
nima baya son ganina. Ban taba tsammanin
zai karbi babyn ba ballantana har ya saka
masa sunan sa.
Matar ta rubuta sannan ta sake next
question wacce tafi komai ciwo a gurina "his
surname" wanda mu a gurin mu hausawa
mukan yi amfani ne da sunan uba a
matsayin surname. Still ni ta sake yi wa
tambayar. Sai na sunkuyar da kaina kasa
hawaye yana fitowa daga ido na yana zuba
akan dan jaririn da yake kan cinyata. Daddy
naji ya sake amsawa again da muryar a kasa.
"Adam Muhammad. His full name is Adam
Adam Muhammad", Matar ta rubuta sannan
ta juya ta fita.
Na rufe idona ina jin hawayen yana cigaba
da bin kuncina. Sai kuma na bude ido na
sauke su akan dan jaririn da yake kan
cinyata fuskarsa jike da hawaye na.
Yar karamar fuskarsa tana kama da ta
Daddy tabbas, yana kuma kama da ni. Wato
dai duk a kaina ya kare. Gashi kuma ya karbi
sunan Daddy. Ruwan hawayen nawa da yake. sunan Daddy. Ruwan hawayen nawa da yake
zuba a kan fuskarsa ne ya saka ya motsa a
hankali sannan ya bude idonsa ya sauke su
a kaina. Nayi sauri na mayar da nawa idon na
rufe." Aunty Hajjo dan Allah ki dauke shi
daga jiki na" tazo ta saka hannu ta dauke shi
sannan ta sake kwantar min da gadon tare
da lullube ni.
14
11
10
8:52 PM
Na rufe ido na kamar bacci zan yi, naji ta
cewa Daddy zata mayar da jaririn NICU inda
ake kula da shi.
Sai dai tunda na rufe nawa idon idon yaron
nake gani yana kallo na dasu. Ina tunanin
ranar da zai kalle ni da su yace min ina
ubansa. Ban san wanne kallo zaiyi min ba in
nace masa ban sani ba. Ko zai fahimta? Ko
kuma shima zai dora ayar tambaya a kaina
kamar yadda mutane da yawa suke dorawa,
including mahaifina.
Sai daga baya na fahimci dalilin da yasa
adoption din da nayi niyyar bayar da babyn
bai tafi daidai ba. Ambulance din da aka kira
ta dauke ni ba asibitin da nake ganin likita ta
kai ni ba, asibiti mafi kusa kawai suka nema
suka kai ni dan ceto raina. Su kuma inda aka
kaini basu san waccan maganar ba, Na
kuma fahimci anyi min aiki ne tun around
1pm na ranar juma'a, yanzu kuma 1pm din
asabar ne,
Ina jin uncle Sufyan suka shigo tare da
Abdul, suka gama magana da Daddv sai. Abdul, suka gama magana da Daddy sai
yazo kusa da ni yayi min sannu. Na gyada
masa kai kawai ba tare da na bude ido na
kalle shi ba dan ni a yanzu da naga dan da
na haifa ba tare da aure ba ido da ido sai
nake jin kamar nafi kowa abin kunya a
duniya. Na tabbatar mutanen da suka san ni
da ba zasu cigaba da yi min kallo irin wanda
suke yi min da ba.
Daga baya Aunty Hajjo ta dawo babu yaron
a hannun ta, ta hada min ruwa a toilet ta
taimaka min na tashi tsaye, sai naji kamar
iska zata kada ni, na zama kamar wata
tsinke. Sai da na shiga toilet sannan na kalli
inda aka yanka a cikina, a mark that will
forever be a reminder to me. Aunty Hajjo ta
lura da abinda nake kalla tace min "kar ki
damu, sun ce the scar won't be bad, sun
kware a aikin su ai sosai".
"It will still be
there" na fada ba tare da nasan na fada ba.
"Ko ba a jiki na ba the scar will forever be in
my heart",
Ita ta taimaka min nayi wanka yadda ba zan
fama ciwona ba, ta taimaka min na shirya
sannan muna fitowa ta bani abinci ta saka ni
naci, banyi musu ba naci saboda ina bukatar
karfin jiki na for what I have planned.
Ina cikin shan kunun da ta bani ne Daddy ya
sake dawowa dakin. Yana shigowa nace
"Daddy ka siyo tickets din? Yaushe jirgin zai
tashi?" Ya kalli Aunty Hajjo kamar mai
neman taimako a gurinta, sai ta fara magana
"Safiyya, kema kin san babu yadda za'a yi ki. "Safiyya, kema kin san babu yadda za'a yi ki
iya yin tafiya a yana yin da kike ciki. Ki bari
ki kwana biyu ayi discharging din ku daga
asibiti ke da Adam Junior in yaso sai ku tafi"
na ajiye cup din hannuna. "Ni na warke. Ni
babu abinda yake damuna. Ni Nigeria zan
tafi. Allah yau ko a kafa ne sai naje" na fara
rera kuka. Daddy ya matso "Okay, okay.
Bara in je in samu doctor muyi magana da
shi inji. In yace zamu iya tafiya shikenan"
Aunty Hajjo tace "Daddyn Safiyya ka zauna
ka huta. Zan je in turo shi nan sai kuyi
magana gabaki daya".
Likitan yazo, bayan ya gama gwaje-gwajen
sa yace zan iya tafiya tunda anfi 24 hours da
yin aikin. Musamman saboda na nuna hakan
na ke so su kuma suna son abinda zai
faranta min ne. Sai dai jaririn yace ba za'a
iya tafiya dashi ba, duk da cewa yana iya
numfashi da kansa amma yana bukatar
kulawar maaikatan lafiya 24/7 for at least 3
weeks kafin ay discharging din sa.
Bayan ya fita muka zauna shiru ni da Daddy,
sannan yace "are you sure you want to go?"
Nace "Yes" yace "okay, shikenan. Zan saka
ayi mana reserving next flight to Nigeria, But
what about him?" Na gane wa yake nufi
amma nayi shiru ban amsa ba. Ganin bana
son yin maganar sai bai kara yi ba, ya dauko
wayarsa ya kira ya gama settling maganar
tafiyar mu sannan yace min "akwai jirgi
4:00 am zai tashi. To Lagos. Yayi?" Na gyada
kai ina jujuya kofin kunun hannuna, sai ya
sake cewa "and there is something I want. sake cewa "and there is something I want
you to know kafin mu tafi. An daura auren ki
da Mukhtar dazu" na daga kai ina kallon sa
sai yayi saurin fara yi min bayani, baya son
duk abinda zai bata min rai a lokacin, yace
"an riga an saka lokaci. They couldn't get us
on phone sai suka daura. Nima sai dazu da
Abdul yaje gida ya dauko min wayata sannan
na sani" banji komai ba a raina nace a
hankali "it is okay Daddy".
11
10
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: "and there is something I want. sake cewa "and there is something I want
you to know kafin mu tafi. An daura auren ki
da Mukhtar dazu" na daga kai ina kallon sa
sai yayi saurin fara yi min bayani, baya son
duk abinda zai bata min rai a lokacin, yace
"an riga an saka lokaci. They couldn't get us
on phone sai suka daura. Nima sai dazu da
Abdul yaje gida ya dauko min wayata sannan
na sani" banji komai ba a raina nace a
hankali "it is okay Daddy".
11
10
8:52 PM
Aunty Hajjo ce da Abdul suka koma gidan da
muke suke dauko mana kayan mu da suke
ganin zamu tafi dasu, sannan kuma ta
cigaba da zama a tare da ni kafin lokacin da
zamu tafi airport yayi. A cikin lokacin ne ta
koma NICU ta kuma dauko jaririn ta dawo
min dashi gurina ta sake dora min shi akan
cinyata sannan ta kuma yi min tambayar da
Daddy yayi min dazu "sun ce ba za'a iya
tafiva da shi ba. What do you intend to do
with him?"
Na sauke idona kasa ina kallon sa, ya na ta
baccin sa ya turo dan karamin harshen sa
waje yana tsotsa, na saka dan yatsa na
shafa gefen fuskar sa inajin abinda ban taba
tunanin zanji ba, abinda tsoron sa ya saka
nayi niyyar bada shi ba tare da na ganshi ba.
Aunty Hajjo ta zauna a gefe na tana kallon
babyn ita ma tace "he is your son Safiyya.
He is your responsibility now. He is now
totally dependent on you. Dole ki zama
strong, even if not for your daddy but for
vour son". strong, even if not for your daddy but for
your son".
Ya dago dan karamin hannunsa cikin bacci
ya rike dan yatsa na da na dora a fuskar sa
ya cigaba da baccin sa. Naji hawaye na ya
dawo. Wannan innocent halittar yanzu ta
zama alhaki na, alhakin kulawa da shi da
komai na sa yana hannuna a yanzu. Duk
wani decision da zanyi will affect him
positively or negatively. Naji a raina cewa na
gama finalizing shawara ta. Na daga kai ina
kallon Aunty Hajjo nace "I wanted to give
him out. Har nayi signing him up for
adoption a wancan asibitin" ta bude ido da
mamaki amma kuma sai ta rufe da alama
bata son tayi judging dina, nace "yes, that
was a pretty dumb decision. I wasn't
thinking right, har yanzu ma tunani na ba shi
da kyau. Emotions dina are not on check.
But still I don't think the right place for him
is with me in Nigeria, at least not for now.
Zuwa da shi gida zai wargaza duk abinda
Daddy yayi sacrificing a lot to cover up. And
in Nigeria people will always tag him as a
bastard. The tag will follow him up har
karshen rayuwar sa".
Ya bude idonsa yana kallona kamar yadda
nima nake kallon sa ina jin wani nauyi a
zuciyata, Sai kuma na daga kai na kalli Aunty
Hajjo nace "Aunty kin bani wani labari
kwanan baya, labarin yadda kika so ki dauke
ni ki rike ni kamar yar ki a lokacin da Ammi ta
mutu, I don't know if you still have wannan
burin a ranki" tayi shiru bata ce min komai. bata son tayi judging dina, nace "yes, that
was a pretty dumb decision. I wasn't
thinking right, har yanzu ma tunani na ba shi
da kyau. Emotions dina are not on check.
But still I don't think the right place for him
is with me in Nigeria, at least not for now.
Zuwa da shi gida zai wargaza duk abinda
Daddy yayi sacrificing a lot to cover up. And
in Nigeria people will always tag him as a
bastard. The tag will follow him up har
karshen rayuwar sa".
Ya bude idonsa yana kallona kamar yadda
nima nake kallon sa ina jin wani nauyi a
zuciyata. Sai kuma na daga kai na kalli Aunty
Hajjo nace "Aunty kin bani wani labari
kwanan baya, labarin yadda kika so ki dauke
ni ki rike ni kamar yar ki a lokacin da Ammi ta
mutu, I don't know if you still have wannan
burin a ranki" tayi shiru bata ce min komai
ba sai na daga jaririn na mika mata "ban sani
ba ko zaki iya cika wannan burin akan
Junior? No one will know he is not yours a
Nigeria. At least not for now, Sanda zai san
gaskiya he will be old enough and strong
enough to understand". EPISODE SEVENTEEN
owner
0 11
7:39 PM
Safiyya
LTE 0
Episode Seventeen: The Wedding Crasher
Paid advert
Akwai 10% discount ga first 10 people da
suka fara ordering a cikin mutanen maman
Maama
Contact her on 08033308307
Ki gyara rayuwar aurenki tare da amfani da
ingantattun magunguna mata masu Kara
lafiya da kuzari ga rayuwar ma'aurata. Mun
tsaya mun tantance mun zabo muku herbs
da Kuma spice da suke enhancing sexually
wellness dinku. Kina fama da sanyi Kuma
kinyi magani yaki tafiya? Gwada maganin mu
(INFECTION CURE SET)na sanyi kiga iKon
Allah,sanyi ko yasa kin bude in shaa Allah in
kika yi amfani da maganin mu zaki samu
waraka. Haka Kuma dan kina bugatar
wadatacciyar niima da zaki tashi kan yallabai
to ki Nemo WETNESS PRODUCT dinmu. In
Kuma dandano kike so hajiya gidan kika. to ki Nemo WETNESS PRODUCT dinmu. In
Kuma dandano kike so hajiya gidan kika
zo, muna da SWEETNESS SET kiga aiki da
cikawa. Akwai POST-PARTUM SET a masu
jego,akwai BRIDAL SET na amare.
*Sannan ga masu son sarin kayanmu muna
da starter kit na magungunan da zaki siyar
ki samu alkhairi a ciki, kin huta da 'yar murya
akan 50k kacal*
Elevate your intimacy and ignite your
passion with our expert advice and carefully
curated products. Your journey to enhanced
sexual wellness starts here.
Tayi shiru tana kallona sannan ta kalli dan
jaririn da nake mika mata. Ta jima tana
neman haihuwa, tun daga Abdul bata sake
haihuwa ba dan tare suka yi ta neman
haihuwa ita da Ammi kafin a haife ni. Har
daga baya ta hakura ta saka a ranta cewa da
daya Allah ya rubuta mata zata samu.
Tabbas tana da shekaru amma kuma ba abin
da ya kamata ayi mamaki bane ba idan ta
haihu. Tunda in rear occasions mata masu
irin shekarunta su kan haihu. Sannan kuma
tafi shekaru uku rabon ta da Nigeria, kuma
tafi shekara rabon da wani daya santa a gida
ya kawo mata ziyara Berlin. Sai mu da muka
zo yanzu. Dan haka abu ne mai matukar
sauki tayi passing junior as her son kuma. sauki tayi passing junior as her son kuma
babu wanda zai musa. Wannan zai baya
Junior kariya daga zagi da tozarcin mutanen
mu na kasancewarsa marar ba. Idan
lokacin da ya kamata ya sani kuma yayi, shi
kadai ne ya kamata ya sani din tunda duk
wadanda abin zai shafa already sun riga sun
sani.
Ta miko hannu a hankali ta karbe shi,
muryarta kamar zata yi kuka tace "I don't
know what to say" nace "you don't have to
say anything. Except in kina ganin it's too
much of a burden" na fada ina mika mata
hannu na dan lokaci daya kuma naji kamar
ba zan iya rabuwa da shi ba. Ta matsa baya
tana rungume shi a kirjinta tace "he will
never be a burden. Kamar kuma yadda kika
fada, barin shi a gurin mu is the best thing
to do to him a yanzu. Allah ya bamu ikon rike
shi da amana. Ke kuma Allah yayi miki jagora
a dukkan sauran al'amuran da zaki
fuskanta"., Na sauke hannayena kasa ina ji
na empty, sai kuma a hankali nace "Ameen".
Bayan nan ne na gaya wa Daddy shawarar
da na yanke akan Junior, he was first
concern cewa kar mu takura musu mu hada
su da rainon jaririn da basu haifa ba, amma
bayan yayi magana da uncle Sufyan da da
aunty Hajjo sai naga ya samu relief, Dan ya
fahimci ma su murna suke yi da samun
abinda suka jima suna nema.
Sai 3am muka bar asibitin, bayan likita ya
sake duba ni tare da bani duk shawarwarin. sake duba ni tare da bani duk shawarwarin
da ya kamata ya bani, most of which ta
kunnen dama na suke shiga suna fita ta
kunnen hagu. Sai da suka gama sannan
suka rubuta mana takardar sallama ni da
Daddy, suka kuma rubuta mana report din
da zamu bawa doctor din mu a Nigeria
yadda zai cigaba da kula da lafiyar mu. Ya ja
mana kunne duk mu biyun akan gudun
abinda zai ke tayar mana da hankali, ya
kuma bamu shawara da mu kula da junan
mu.
Kafin mu bar asibitin na biya ta NICU, naje
har gaban dan akwatin da aka kwantar da
junior na daga ina kallon yar karamar
fuskarsa ta bakwaini, sannan na saka dan
yatsa na shafa fuskarsa nace "goodbye
Adam" yayi mika ya bude ido ya kalle ni
sannan ya cigaba da baccin sa.
23
15
4
A 2 7:46 PM
By 4am muna cikin jirgi, by 5 already munyi
nisa a tafiyar mu. The 8 and half hours flight
kusan in total silence muka yi shi, na lira
daddy ya ssmu bacci sosai dan daga alama
rabon da yayi bacci tun san da aka kwantar
da ni, ni kuma a nawa bangaren kokawa
muka ringa yi ni da baccin, shi yana so ya
dauke ni ni kuma ina iyakacin kokarin ganin
cewa bai dauke ni din ba, I needed to stay
awake and alert dan in samu damar planning
on my revenge on Gidado da Safina.
Ban samu bacci ba sai bayan da muka sauka
a lagos muka sake shiga wani jirgin zuwa. Ban samu bacci ba sai bayan da muka sauka
a lagos muka sake shiga wani jirgin zuwa
Abuja after waiting for 30minutes. Tun a
Lagos din naji Daddy yana ta waya da
Mustapha da kuma Mommy yana basu
labarin abinda ya faru, ya kuma gaya musu
gamu nan zuwa, sannan ya umarci
Mustapha yaje airport a Abuja ya dauke mu
sannan ya sanar da doctor din sa gamu nan
zuwa dan zai sake dubani in mun karaso. Na
fahimci su Mommy har lokacin a cikin
hidimar biki suke, a lokacin ne kuma na tuna
da cewa yau ne da daddare za'a yi dinner, a
yau din ne kuma za'a kai amarya, dan haka
na fara planning din yadda zan hargitsa
dinner din sannan in tabbatar da cewa first
night din su is the worst in history of
marriages.
Karfe biyu na rana da yan mintuna muka isa
Abuja, da kyar na iya mikewa daga kan
kujerar da nake kai saboda yadda gabaki
daya jikina yake min ciwo sannan gurin
aikina yana ta yi min zugi. Duk da ma na
kwantar da kujera ta ba wai a zaune nake
sosai ba. Ban iya tashi ba sai da wata
maaikaciyar jirgin tazo ta kama ni muka tafi
a hankali. Muna fita waje na hango Mommy
da Mustapha, Mommy ta taho da sauri inda
nake tana kare min kallo sannan ta juya
gurin Daddy shima ta bishi da kallo "me ya
same ku?" Ta tambayi no one in particular,
babu wanda ya amsa mata sai ta karbe ni
daga hannun air hostess din ta cigaba da
tafiya da ni zuwa motar da suka zo da ita.
Mustapha kuma ya cigaba da tura. Mustapha kuma ya cigaba da tura
wheelchair din Daddy. Muka karasa motar
ya taimaka masa ya zauna a gaba sannan ya
saka wheelchair din a boot din motar ya
shiga gaba mu kuma muka shiga baya ni da
Mommy. Na jingina kaina a kujerar motar ina
kallon titi da motoci da tituna da gidajen da
muke wucewa. A zuciyata nace Nigeria my
dear country, na dawo, let's see what you
have in store for me a wannan karon.
Na lura da ga Mommy har Mustapha
kwalliya ce a jikin su, kwalliyar bikin Safina.
Tun da muka shiga motar Mommy bakin ta
bai yi shiru ba tana ta fadan me yasa muka
taho a cikin halin rashin lafiya. Tace kuma
laifi na ne tunda a waya Daddy yace mata ni
ce na takura sai na dawo gida "kin san cewa
duk abinda kika fada kamar yankan wuka ne
a gurin sa, in baki damu da taki lafiyar ba ai
ya kamata ace kin damu da tasa". Ni dai ban
amsa mata ba, da ta cigaba ma sai na saka
hannayena biyu na toshe kunnuwana
sannan na rufe ido na. Can ness na jita tace
"shikenan ai" sai kuma tayi shiru.
Asibiti muka fara zuwa, muna zuwa suka
fara daukan vitals din mu a take suka sake
admitting Daddy. Ni kuma suka rubuta min
bedrest har sai sunce otherwise. A can
twins suka zo suka same mu. Suma daga
gani daga gurin bikin suke. Suka rungume ni
da murnar gani na. Ina jin Daddy yana musu
magana "careful, bata da lafiya" suka cika ni
suna kare kin kallo sannan Hassan yace
"you look terrible" nayi kokarin yi masa. "you look terrible" nayi kokarin yi masa
murmushi amma na kasa. Mommy suka fita
da Mustapha zata tura shi airport ya dauko
wasu kawayen ta da suka zo dinner din da
za'a vi yau. Suka barmu ni da Daddy da
twins.
Daddy yace musu su dauke ni su tafi da ni
gidan mu na nan garin "ba gidan bikin zaku
kai ta ba. Ba kuma gidan Ahmad ba. Ku kaita
gida ta huta, and stay with her" suka gyada
kai a tare. Har na mike zan tafi sai ya kira
sunana, "zo nan" daga yadda yayi maganar
nasan fada zaiyi min amma sai naji ban san
laifin da nayi ba kuma. Su Hassan suka fita
ni kuma na zauna a kujerar da take kusa da
gadon da yake ya sunkuyar da kaina kasa
sai ace "Safiyya. Baki gaishe da Sa'adatu
da Mustapha ba why?" Nayi shiru ina jujuya
hannuna yace "har yanzu fushi kike yi dan
sun taho sun bar mu?" Still ban ce komai ba.
21
11
1
7:46 PM
Ya sake kiran sunana "Safiyya" na amsa a
hankali, yace "Make peace with Sa'adatu
and her children. Kinji ni?" Na gyada kai na
kawai. Amsa ta bata gamsar da shi ba sai ya
sake cewa "kiyi min alkawarin ba zaki yi
rigima da su ba" na dago kaina ina kallon sa,
he looked so sick and tired, shine mutumin
da yafi sona fiye da kowa a duniya, shine
mutumin da nafi so fiye da kowa a duniya.
Nace "nayi alkawari Daddy. Ba zanyi rigima
da su ba" yace "good" na sake mikewa yace
"and one more thing" na sake dawowa na
zauna vace "wave Muhammad?" zauna yace "waye Muhammad?"
Nayi sauri na kalle shi da mamaki. Lokaci
daya mood dina ya chanza daga indifferent
zuwa tashin hankali. Yayi ajjiyar zuciya yace
"so, shine baban Adam kenan" na fara
girgiza kai na "Daddy.…... Muham.…waye
Muhammad?" Yace "oh ni kike tambaya
kenan. You call his name sau ba adadi sanda
baki da lafiya. And now you are telling me
baki san waye ba. Gashi kuma fuskar ki ta
nuna alamar rashin gaskiya karara. Na
fahimci shine baban wancan yaron. Na
fahimci kuma kina sonsa sosai shi yasa kike
cigaba da boye min shi dan kar inyi
punishing dinsa for what he did. Just tell me
who he is. I am not going to do anything to
him a yanzu. I just want to give him his son. I
just want that innocent baby to have a
father"
Na fara hawaye "Daddy ba nashi ba ne ba"
babu abinda yake tayar min da hankali a
duniya irin kin yarda da ni da Daddy yayi.
Yayi shiru bai sake cewa komai ba har
Mommy ta dawo. Na goge fuskata da sauri
amma sai da ta lura da hawayen tace "har
yanzu ana nan ana fama kenan" na kalli
Daddy sannan na gaishe ta. Ta amsa shortly.
Ina zama a mota na cigaba da kuka na.
Hussein yace "yaushe zaki daina kuka ne
wai yaya?" Ban amsa masa ba dan ni ma
ban sani ba. Na dauka xasu tambaye ni ina
baby amma sai naji duk basu tambaya ba,
and I felt bad for little Adam. No body. and I felt bad for little Adam. No body
wanted him. Not even his uncles.
Gab da magrib muka shiga gidan. Esther ta
tarye ni ta gaya min cewa dama Mommy
tace ta gyara min dakina. Na shiga dakin na
zauna twins suka shigo min da jakar kayana
da Aunty Hajjo ta hado min da ga can. A ciki
naga handbag dina, a cikin ta kuma naga
wayata da na yar a dakina a Berlin san da na
ga hoton Muhammad da Safina. Already
wayar har ta mutu charji ya kare.
Ina zaune Hassan ya dawo da tea a
hannunsa ya hado min, Hussein kuma yaxo
yace "yaya ko in hada miki smoothie irin
wanda kike sha kullum?" Na girgiza kaina
kawai ina jin babu dad yadda suke ta
kokarin kyautata min amma na kasa ko da yi
musu magana ne. Na bude jakar tawa na
dauko wani dan karamin hoto na rike a
hannuna ina kallon sa. Hoton mace da yayan
ta mata guda uku. Na shafa fuskar wacce
take mahaifiyata a cikin su ukun. She
suffered more than suffering din da nake
ciki, She lost more than abinda ni na rasa a
yanzu, She almost lost me too, but then she
gave her life for mine, Amma duk da yadda
rayuwar tata ta kasance, she never lost
hope, She kept her head high and she
achieved fiye da yadda tunanin mai tunani
zai tunano masa, Na ajiye hoton. And so will
1
Na dago kai ina kallon Hassan da ya saka ni
a gaba yana kallo kamar zai yi kuka nace. a gaba yana kallo kamar zai yi kuka nace
*karfe nawa ne dinner din Safina?" Yayi
mamakin tambaya ta amma sai ya kalli
agogo yace "7pm dai suka saka a kati.
Though sunce babu African time dan a yau
za"a kai amare bayan dinner din" na
tambaya "amare?" Yace "eh, su biyu ne ai,
akwai sister din mijin yaya Safina, tare aka
hada auren nasu" "Mufida" na fada a
hankali, yace "kin san ta ne?" Ban ce komai
ba sai na dafa gado na mike. Shima ya mike
da sauri yana kokarin rike ni. Nace "Okay.
Let's get ready kar mu makara" ya bude ido
"kar mu makara zuwa ina? Mu mun fasa
zuwa ai tunda Daddy yace mu zauna da ke.
Ke ma baki fa da lafiya ba zaki iya zuwa ba"
na kirkiro murmushi nace "dan inje dinner
din nan na taho tun daga Germany da sabon
yanka a cikina, bana jin akwaí abinda zai
hana ni zuwa",
17
11
7:46 PM
Na shiga toilet na tsaya ina kallon kaina a
madubi, saí a lokacín na kara fahimtar
abinda twins suke nufi da suka ce I looked
terrible dan da gaske I really looked terrible.
Idona ya kara fadawa kasa ya kuma loosing
all the light da suke cikin sa, fatar idon ta
yamushe tayi baki, fatar lips dina ta bushe
har tana neman tsagewa, ba zan iya tuna
rabon da in shafa mai a bakina ba, ko a
sauran jikina, Na tuna da da a gurina babban
abu mai muhimmanci shine skin care routine
dina, bana taba yadda inyi missing. Amma
yanzu da rayuwa ta nuna min shege banga
na fahimci komai ma guri yake samu. na fahimci komai ma guri yake samu.
Sanitary pad din jikina na chanja na sake
gyara kaina sannan na fito nace musu "na
shirya, ku zo mu tafi" suka kalli juna sannan
suka kalle ni, Hussein yace "yaya dinner ce
fa. Kuma dangin angon nan naga manyan
mutane ne sosai. It is going to be
extravagant ....." Na yafa mayafi na nace "ba
zuwa zanyi dan in burge kowa ba, zuwa
zanyi dan inyi wa yar uwata murnar sabon
auren ta. Wanda yaga ni ko shigata basu yi
masa ba sai dai ya rufe idon sa".
Doguwar riga ce a jikina ta yadi. Rigar aunty
Hajjo ce ta bani na saka da zamu taho
saboda tana da girma sosai kuma yadin
yana da laushi ba zai ke min famin ciwo na
ba. Rigar duk ta chukwuikuye saboda zaman
jirgi. Dankwalin rigar na daura a kaina na
rufe dankararren gashina da na manta rabon
da in taje shi. Sai kuma wani mayafi da ko
kadan bai shiga da yadin ba dana dora a
kafada ta.
Ganin basu da niyyar tashi mu tafi sai na
wuce su na ce "in kun gama ku same ni a
waje", A parlor na zauna ina jiran su, Esther
ta zo da sauri ta kunna min tv da ac, ni duk
basu dame ni ba, so nake inyi sauri inje in
aiwatar da abinda yake raina, Wajen 7:30
suka fito, still da alamar basa son inje, na
mike tsaye "kun gama?" Suma basu chanja
kayan jikin su ba, Hussain ya sake kokarin
hanani fita "yaya bedrest fa aka baki" ban
amsa ba nayi hanyar waje, sai kuma na dawo. amsa ba nayi hanyar waje, sai kuma na dawo
da baya nace musu "a ina ne gurin? Akwai
gatepass a hannun ku? Na iya mota ai zan
iya kai kaina in ba zaku kaini ba".
A dole suka fito muka shiga mota muka tafi,
sai da muka yi nisa nace musu "kar ku gaya
wa Daddy naje" basu ce komai ba.
Muna zuwa mukayi packing a inda aka
tanada, na zauna a mota ina kallon mutane
suna ta shiga gurin, ga kida har ya fara
tashi. Sai na rufe ido na ina kokarin karfafa
zuciyata. Yau zan ganshi. Amma a matsayin
mijin wata. A matsayin mijin Safina. Yayin da
ni kuma nake matsayin matar wani. Matar
Mukhtar. Sai da naga alamar gurin ya cika
sosai sannan nayi karfin halin fita daga
motar, tunda na fita naji alamar jiri yana
neman dibana amma na daure dan bana son
twins su sani, na taka a hankali naje har
bakin kofar na bayar da katin da twins suka
bani sannan na shiga. A gurin muka rabu da
su su suka tafi bangaren maza ni nayi na
mata. Dama abinda nake so kenan. Ina
kallon security din yana bina da kallo, maybe
ya dauka almajira ce, Daga can karshe na
samu guri na zauna saboda bana son wanda
ya sanni ya ganni, Duk da dai nasan a yadda
nake din nan ba kowa ne wanda ya sanni zai
gane ni ba, A haka har guri ya gama cika aka
fara gabatar da event, Ina ji aka yi
announcing zuwan iyayen su Muhammad da
Mufida, suka shigo cikin isa da burgewa.
Sannan aka shigo da iyayen angon Mufida,
suma suka wuce, sal iyayen amaryar. suma suka wuce, sal iyayen amaryar
Muhammad, wato Safina, Mommy ce a gaba
da yan uwanta suna take mata baya, nayi
ajjiyar zuciya, wato ta baro mijin nata a
asibiti ta taho dinner. Daga nan kuma sai aka
y announcing shigowar angwaye da amare.
Na mike tsaye daga inda nake ina hango
kofar da zasu shigo ta cikin ta. Su
Muhammad ne a gaba. Ido na fuskarsa ta
fara gani. Yayi kyau iyakacin yadda dan
Adam ya kamata yayi kyau. Gefensa ga
yayata nan Safina, taci kwalliya ta ajin
karshe, fuskar ta dauke da murmushi idonta
a kasa kamar mai jin kunyar mutanen gurin.
A bayan su abokan Muhammad ne, most of
which na sansu, da kuma kawayen Safina,
gabadayan su na san su. Kowannen su cikin
kwalliya ta alfarma kuma cikin farin ciki. A
raina nace gabakidayan su munafukai ne,
tun daga kan Muhammad din har zuwa kan
securities din gurin, duk munafukai ne.
25
14
7:46 PM
Sai naji a raina ina fatan ina ma dai ginin
gurin ya rushe ya fado a kan mu gabaki
dayan mu mu mutu kowa ya huta.
Ina na tsaye har suka je suka tsaya a
tsakiyar fage, aka ringa kiran iyaye suna yi
musu ruwan kudi, daga inda nake ina hango
yadda Mommy take watsi da kudi. Kudin da
ba ita ta nema ba, Sai da aka gama aka ce
suke su zauna. And those minutes daga
shigowar su zuwa zaman su, zan iya cewa
are one of the most terrifying minutes of my. are one of the most terrifying minutes of my
life.
Suna zama aka yi announcing shigowar
Mufida da angon ta. Nan da nan sai hankalin
mutane ya koma kansu. I took my chance.
Burina shine in hargitsa bikin ba tare da nayi
calling attention din mutane zuwa kaina ba,
not that I care about mutane, but bana son
Daddy ya sani. Bana son yasan komai.
Na bi ta gefen mutane har sai da na wuce
inda mutane suke zazzaune. Ina jin jiri yana
dibana amma na cigaba da daurewa. Daga
inda nake ina hango Muhammad da Safina
akan kujerun da aka tanada saboda su.
Idonsa yana kasa yana daddanna wayarsa,
ita kuma tana magana da wata kawarta
Husna. Na taka a hankali na tafi inda suke
idanuna a kansa, zuciya ta tana jera duk irin
zagin da ta iya tana yi masa. "Munafiki.
Mayaudari. Maci amana" sai dai kuma kiran
tasa zuciyar take yi, so take ya amsa, so
take ya dago ya kalli cikin idona ya gaya min
dalilin da yasa ya auri yar'uwata.
Tamkar wanda tasa zuciyar taji kiran tawa,
sai ya dago idonsa a lokaci daya suka fada
cikin nawa. Ina kallon sanda wayarsa ta
zame daga cikin yatsun hannun sa ta fadi
akan carpet din gurin. Ya mike tsaye a
hankali kamar wanda ake jansa da zare. Na
cigaba da tafiya idona a cikin nasa har sai da
naje na tsaya a gabansa tsakanin mu bai fi
taku daya ba. taku daya ba.
Sai a lokacin Safina ta ganni, ta zabura
kamar wadda aka watsawa wuta. Na dauke
ido na daga cikin nashi na mayar kanta nace
"hello dear sister. Na taho daga Germany
nazo nan gurin musamman dan ke, dan inyi
miki HML. Happy Married life to you" na
mayar da ido na kansa, har lokacin ni yake
kallo da idon da ban san yadda zan
kwatanta shi ba. Nace "and Happy married
life to you too".
Sai na juya a hankali na sauka daga kan
stage din, doing everything in my power dan
ganin na hana kaina faduwa a gurin, bana
son Daddy ya sani. Wata kofa na gani a kusa
da stage din, kamar masu rabon abinci ne
suke fitowa daga ciki. Nayi sauri na shiga, na
wuce su suna ta hidimar su, na ga wata kofa
na sake shiga sai na ganni a waje, kamar filin
bayan gurin ne. Na tsaya ina tsakar
numfashi da sauri dan in samu in daidaita
bugun zuciya ta,
Ji nayi an finciko ni da karfi an juyo dani,
saura kadan in karasa shidewa, Muhammad
na gani a tsaye a gaba na fuskarsa da yana
yin da ban taba ganin ta cikin sa ba, yanayin
da ba zan iya kwatantawa ba, EPISODE EIGHTEEN
15
> 5
3
owner
2
7:43 PM
Safiyya
Episode Eighteen: New Couples
Paid advert
*Contact Bojuwa HERBAL'S for all your*
*kayan mata for*
*Amarya*
*Uwargida*
*Bazawara*
*Mai jego*
*Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar
kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi
all from Chad.*
*Kayan gyara masu kyau da inganci kala
daban daban, special maganin sanyi for
women of class*,
*Contact Surayya HALIN YAU on*
*08032773332*, Sai da nayi amfani da dukkanin karfin halin
da rage a gare ni sannan na iya cire idona
daga cikin nasa na sauke su akan hannu na
daya rike sannan na sake kallon sa nace
"careful, ni matar aure ce" ya kalli hannun,
daga alama shi kansa bai san ya rike ba,
sannan ya sake shi da sauri yace cikin daga
murya "then what are you doing here? Me
kika zo yi nan?"
Nace "kamar yadda na fada muku a ciki kai
da matar ka, zuwa nayi in taya ku murnar
auren ku, ko kaga nayi wani abun ne bayan
haka?" Ya fara girgiza kansa "no. no. no,
nasan me kika zo yi gurin nan. Na san me ya
kawo ki. You came here to torment me. Why
me? Me nayi miki? Shin soyayya ta koma laifi
ne ni ban sani ba? After all the yaudara ta da
kika yi for years before kika ce min kina da
aure and you asked me not to contact you
again and you were pregnant and ......."
"Ya
kare min kallo "where the hell is your
pregnancy?" Ya fada looking as confused as
ever.
Nace "wrong question. You asked the wrong
question, Babu hadin ka da cikina and you
have no right to asked for it. Now I will ask
you the right question, Shin saboda kana
tunanin na yaudare ka...."
"Tunani?" Ya
tambaya "kina magana kamar baki yi ba. Kin. tambaya "kina magana kamar baki yi ba. Kin
yaudare ni kema kin sani, kin......" Na katse
shi "is that why you marry my sister?
Saboda kana tunanin na yaudare ka or do
you really love her?" Nayi masa tambayar da
ita ce take keeping dina awake all these
hours.
Ya tsaya yana kallo na kamar a lokacin ya
lura da ni a gurin. Ya bude bakin sa a hankali
"your....
." Sai kuma ya juya ya kalli hall din
da muka fito daga cikin sa "your sister?" Ya
tambaye ni kamar wanda bai ji abinda nace
ba sosai. "She is your sister" ya fada as a
statement, not as a question "she is your
Safina" ya sake fada a hankali, more like
talking to himself. And in that moment I
realized the truth. Bai sani ba. Bai san wa ya
aura ba.
And ni kaina ba zan iya cewa ga abinda naji
a zuciyata a game da hakan ba. Yes I felt a
relief, relief that he didn't intentionally do it.
And then a surge of pity, pity for him. Wani
tausayinsa naji ya lullube ni. He is innocent,
his innocence yana daga cikin dalilan da
yasa nayi deciding rabuwa da shi so that he
can continue to live his innocence life. And
now he got dragged back into it and tangled
in a web da ni bansan yadda zanyi in
warware shi and set him free ba.
Na fara girgiza kaina a hankali ina ja da
baya, sannan kuma na fara sauri zuwa bakin
titi nayi sa'ar taxi ta sauke wata na shige
ciki. Na rufe ido na ina mayar da numfashi ciki. Na rufe ido na ina mayar da numfashi
na a hankali hannuna a dage da ciki na gurin
da akayi min aiki dan ba jaramin azabar ciwo
yake yi min ba saboda tafiyar da nayi da
sauri. Sai da mai motar ya tambaye ni sau
biyu sannan na samu na bude baki na gaya
masa address din inda zai kaini.
A hanya sai na samu kaina da kasa zabar
tunanin da zanyi. Tun sanda na ga hoton
Muhammad da Safina babu irin lissafin da
banyi ba na abinda zanyi musu, a cikin jirgi
kuma babu irin plan din da ban shirya ba na
yadda zan hargitsa dinner din su. A cikin
plans din nawa har da petrol nace zan siyo
gallon daya in zazzaga a hall din in kunna
wuta. But I didn't do any of my plans. But
still I feel satisfied. My mission has been
accomplished. Dan a yadda na bar
Muhammad nasan dinner din nan ta kare a
gurin sa shi da Safina. Shi da kansa zai
hargitsa bikin nasu da kansa.
Da kyar na iya shiga gida bayan an sauke ni
saboda azabar ciwo, ina zuwa na samu na
sha magani na kwanta a parlor, har wani
gumi ne yake karyomin saboda azaba, a
haka bacci ya dauke ni. Cikin baccin naji
hayaniya, na farka amma ban bude ido na ba
sai naji muryar Mommy tana masifa,
13
7
2
1 7:51 PM
"Wallahi ba'a isa ayi mana wannan
wulakancin ba, chafdi, Basu san wace
Sa'adatu ba. Ba'a haifi wanda ya isa yayi min. Sa'adatu ba. Ba'a haifi wanda ya isa yayi min
wannan wulakancin in yi shiru in barshi ba".
Naji Muryar kanwarta da muke cewa Aunty
karama "dan Allah ki bar maganar nan
Sa'adatu. Tunda mun dauko yarinyar mun
taho ba shikenan ba, dole ai zasu bio mu
har gida su bada hakuri in dai suna so a kai
musu ita".
Na bude idona a hankali na kare musu kallo,
Mommy ce tayi kicin kicin, daga dukkan
alamu tafi awa daya tana fada, sai kanwarta
Hajiya karama da wata kawarta. Sai kuma
Safina a can gefen su ta kwanta ta kifa kanta
akan kujera, da kawarta Husna a zaune a
gabanta. Na mayar da ido na na rufe. Suka
cigaba da maganganun su, a cikin maganar
na fahimci suna fada ne akan wai tunda
Safina suka shiga da mijinta gurin dinner
suka zauna, shikenan ya tashi yayi tafiyar sa
ya barta ita kadai a zaune. Mufida tana
zaune da mijinta ita kuma Safina tana zaune
ita kadai. Anyi ta nemansa an rasa inda yayi,
anyi ta kiran wayarsa a kashe. Ita ma Safina
tace bata san inda yaje ba. Dan haka sai
concentrating bikin aka yi akan Mufida, ita
kuma Mommy ta gaji da ganin yarta tana
zaune a high table kamar decoration ta
dauko kayarta tana masifa mutane suna
bata hakuri ta fito daga gurin dinner din.
Mommy ta cigaba da fada "kuma wallahi
banga wanda ya isa ya kai min ya gidan sa
ba a yau, Idan kinga an kai yarinyar nan
gidan sa sai yazo har cikin gidan nan ya
bamu hakuri tukunna", bamu hakuri tukunna".
A yadda aka tsara bikin nasu a yau za'a kai
amare gidajen su, daga gurin dinner za'a
wuce dasu, amma Mommy yanzu tace ba
za'a kai Safina ba sai Muhammad yazo ya
bada hakurin tafiya da yayi ya barta a stage
kamar flowar decoration.
Na tashi na zauna ina jin ciwon ya danyi min
sauki sannan kuma hayaniyar su tana
kokarin saka min ciwon kai. Na gaishe su
suka amsa min babu yabo babu fallasa dan
duk rayukan su a bace suke, muka gaisa da
Husna ita ma tayi min sannu tace taji ance
bani da lafiya. Na amsa mata da "da sauki ai
sosai. The worst is over insha Allah. Na kusa
inyi getting my life back insha Allah" Na
mike nace da Mommy zan koma daki in
kwanta ta gyada min kai kawai. Ina jin Hajiya
karama tana tambayar ta "wanna yarinyar
wanne ciwo take yi ne haka Sa'adatu? Kinga
yadda ta koma kuwa?" Mommy ta tabe baki
tace "ulcer ce ta sako ta a gaba, tayi mata
mugun kamu har sai da ta kai ani mata aiki
a hanji. Yara ne kayi ta fama dasu akan suci
abinci ba zasu ci ba wai su dieting suke yi,
wai su sunfi son su rame, gashi nan ai ta
jawo wa kanta rama mai guarantee". Ni dai
na wuce na shige dakina tun kafin a fara yi
min fada akan laifin da ban aikata ba.
One thing da nake respecting mommy akai
shine ko yanuwanta da suke uwa daya uba
daya ba ta gaya wa abinda ya same ni ba,
kuma ba ta bari sun ganni da cikin ba, kuma ba ta bari sun ganni da cikin ba.
Ina shiga dakin na shiga toilet nayi wanka na
gyara jikina nayi shirin kwanciya bacci, ina
jin yunwa but I did not feel like eating
anything and did not care. Sai kawai na
kashe fitila nayi kwanciya ta, somehow I was
satisfied with tafiyar da Muhammad yayi ya
bar Safina, my bad girl part wanted more
than that but na san idan da akwai abinda
yake so kuma yake respecting a duniya sune
iyayensa, ba zai taba disrespecting dinsu a
gaban mutane ba. And at least she gets to
sleep alone in her room today, maimakon a
dakin Muhammad kamar yadda ta saka rai.
Ina nan kwance idona a rufe naji motsi an
shigo dakin nawa, sannan aka kunna fitila.
Na bude ido naga Safina a tsaye a bakin
kofa, idonta da alamun tayi kuka. Na koma
na kwanta na mayar da idona na rufe. Naji
alamar ta zauna akan gadon sannan naji
tace "Safiyya….... An samu
misunderstanding. Na san kina gain kamar
nayi miki laifi. Amma ina so in gaya miki
cewa coincidence ne. Ni ban san wanda na
aura shine tsohon saurayin ki ba. Tunda ni
dai baki taba hada ni da shi ba ban taba
ganin sa ba sunan sa kawai na sani. Suna
kuma yakan....
.." Na bude ido na na mike
zaune na zuba mata ido sai tayi shiru ta
kasa cigaba da maganar, na nuna mata kofa
nace "Safina, with all due respect, get out of
my room, Ke karyar ki ko sallah ma bata yi, it is making
me nauseous, dan Allah ki fita tun kafin
karyar ki ta saka ni aman takaici"
Ta yi shiru tana kallona. Na sake nuna kofa
"out I said. In na cigaba da ganin ki ko jin
muryar ki tabbas za'a fitar da gawar daya
daga cikin mu daga cikin akin nan". Ta mike
tsaye har takai bakin kofa kuma sai ta sake
juyowa tana kallo na tace "it is obvious kin
dauki maganar da zafi da yawa, kar ki manta
amma na farko ke a yanzu matar aure ce. Na
biyu ya gaya min ke kika yi breaking up with
him. Yes, na san yana son ki har yanzu
amma kar ki manta shi namiji ne, namiji yana
iya son yaya ya dawo kuma yaso kanwa ko
da uwarsu daya ubansu daya, ballantana mu
da babu hadin jini. And a matsayi na na
mace, making him fall in love with me is
going to be the most easiest thing ever. Ina
miki fatan alkhairi ke da naki mijin." Nayi
murmushi nace "mun gode, now go and
open your room ki shiga ki jira har sai yazo
gida ya baku hakuri sai kije ki saka shi ya so
ki din".
Na koma na kwanta na rufe idona ina jin
zuciya ta tana tafasa, da gaske idan Safina
ta cigaba da tsaya wa a gurin nan ta kuma
cigaba da kiran kanta matar Muhammad
za'a iya rasa daya daga cikin mu. Addu'a
nake a raina ta fita din, ba dan ina gudun
abinda zanyi din ba sai dan ina tunanin. nake a raina ta tita din, ba dan ina gudun
abinda zanyi din ba sai dan ina tunanin
mahaifina daya ke kwance bashi da lafiya.
Bata fita ba din kuwa sai ta cigaba da
magana. "Haka ne, zan jira shi kamar yadda
Mommy tace. Na san kuma zai zo, kamar
yadda na san cewa zai so ni kuma zai manta
da ke, musamman idan ya san abinda kika
yi, abinda na tabbatar ba ki gaya masa ba,
abinda na san kunyar gaya masa ne ya saka
kika zabi rabuwa da shi"
Na sake mikewa zaune da sauri, sai da naji
ciwona ya amsa, sannan na bude abin da na
rufa da shi na mike tsaye ina kallon ta "are
you threatening me?" Ta ja da baya, daga
alama taji tsoron irin zuciyar da nayi kuma
bata son ta karasa gawar da ba tata ba. A
lokacin aka bude kofar dakin aka shigo, duk
muka juya muka kalli wanda ya shigo din,
Mukhtar ne, kallo daya yayi yin ya juya gurin
Safina "ke! Me kike yi a dakin ta kuma? Fita
tun kafin in kai ki asibiti wallahi" ta juya da
sauri ta fita dan ita ta san ba karamin aikin
sa bane yayi decorating fuskarta da mari.
Sai da ta fita sannan ya juyo yana kallona
"Fiyya. I am so sorry" na koma na zauna a
bakin gado hawaye ya fara wanke min fuska
ta, ina jin shi ya rufe kofar dakin ya taho inda
nake ya durkusa a gaba na yana kallon fuska
ta "I am so sorry Safiyya, Bansan abinda
yake faruwa ba kenan. Sai da naje dinner
dazu na ganshi, Kuma ban san kin zo gari
ba. No body told me kin zo gari I would have ba. No body told me kin zo gari I would have
been here with you", Na rufe idona da
hannayena kuka ya sake kwace min gabaki
daya. Irin kukan da kake idan ka samu wani
wanda yayi understanding situation din ka to
some extent.
Sai ya tashi ya zauna a bakin gadon tare da
jawo ni jikinsa yana bubbuga baya na a
hankali da sigar lallashi, "it is okay. Ki daina
kuka kinji? I am here. Everything is going to
be okay" and that was all I wanted, babban
abinda nake bukata a lokacin shine wani ya
rungume ni ya gaya min cewa everything is
going to be okay. And that made me feel
safe with him. He gave me heart warming
words and a shoulder to cry on, and I did
cried on his shoulders, ban san lokacin da
na dauka ina kuka a jikin sa ba and in that
few minutes I felt the safest I have felt in
months.
The next thing da ya dawo dani back to
reality was the feeling of him trying to put
his lips on mine. Trying to kiss me. Na bude
ido da sauri ina kallon sa, ina jin safe heaven
din da na ke tunanin na samu ta dawo tana
crashing on me. Na saka hannu biyu na tura
shi baya da karfi amma saboda girman sa da
kuma rashin karfin jikina maimakon shi yayi
baya sai nice nayi baya na tafi zan fado daga
kan gadon,
Ya tare ni da hannunsa daya dan kar in fadi,
nature hannun nasa na mike tsaye jiri yana
dibana "get out!" Na nuna masa kofa "fita. dibana *get out'" Na nuna masa kota "fita
min daga daki* ya mike tsaye vana sake
kokarin rike nì, "Safyyya! I am sorry! I was
just trying to...." Ban cigaba da jin abinda
zai ce ba na wuce shi na shige toilet tare da
rufe kofa.
18
751 PM
A cikin toilet din na kwanta a kasa a akan
tiles, kukan nawa gaba daya ya dauke,
tunani na ma gaba daya ya dauke.
*Him
Ranar daurin aure....
Kamar a mafarki haka yaga any daurin
auren an gama, mutane suna ta mika masa
hannu suna yi masa murna shima yana mika
musu suna yin musabaha sannan sai mai
hoto ya dauke su hoto, amma yaki barin
zuciyarsa tayi processing abinda yake
faruwa ballantana tayi accepting. Ba zai iya
gane da wa da wa suka gaisa ba ba kuma ya
gane mai suke cewa, he just smiled at
people and answered Amen idan sunyi
masa addu'a. Ya san kuma sun shiga gidan
su Safina sunyi hotuna da ita sun kuma yi
hotuna da mutane da yawa a gidan, Kamar
kowa so yake yayi hoto da su, daga nan
suka fito suka dauko hanyar gida,
Sai da suka zo Abuja mutane suka fara
raguwa sannan ya samu damar kasancewa
shi da tunanin sa. Shi ya san shi ya zabi. auren nan a lokacin da aka bashi choice
tsakanin yin auren ko barin sa, he thought
tunda auren shine abinda ya fahimta a
matsayin zabin Allah then it is going to bring
him happiness. But me yasa instead of
happiness yake jin wani feeling a zuciyarsa
wanda ya kasa fassarawa? Ji yake kamar
akwai wani bomb da yake ticking a cikin sa
wanda yake gab da exploding ya kuma
tarwatsa shi.
Suna zuwa gida ya dauki uzuri yace baya jin
dadi zai je ya kwanta. Kuma da gaske baya
jin dadin, sai dai ya kasa tantancewa idan
zazzabi yake yi ko ciwon kai ko ciwon
zuciya? Dan haka kawai yasha maganin da
Mama ta bashi ya kwanta ya rufe idonsa.
Washegari assabar suka tashi da hidimar
daurin auren Mufida, tun da assuba bai
samu kansa ba yana ta kokarin yadda za'a
sauki bakin Abba cikin girmamawar da suka
yi deserving. Har ake je akayi daurin auren
aka yi reception duk kusan shine akan
komai, zuwa dare yayi gajiyar da a nasa
daurin auren ma bai yi irin ta ba. Ranar
Lahadi kuwa tunda yayi sallar asuba ya bar
gidan ya koma gidan da yake zama a yanzu,
yana saka ran zai kasance shi kadai tunda
yan'uwan sa should be a gidan su gurin biki
tunda biki da ma suka zo, amma bai jima da
shiga gidan ba sai gasu sunzo mota mota,
suka gaya masa ai ba gurin biki suka zo ba
gurin sa suka zo, Haka suka saka shi a gaba
da hirar aure, Yace "dan Allah ku rabu dani,
na gaya muku bana jin dadi" AbdulShakur. na gaya muku bana jin dadi" AbdulShakur
yace "baka jin dadi? Me yake damunka? Ko
tsoron auren kake ji? Babu abin toro a ciki
fa kawai da mun raka ka mun tafi sai ka
lallabata ka bata kaza da lemo, shikenan sai
ka saka ta a daki".
Gidado ya bude ido yana kallon sa "kai fa
dan iska ne" suka kyalkyale da dariya. Ayaan
yace "wait, he is telling the truth ai, in baka
saka ta a daki ba to a parlor zaka saka ta? In
kuma baka san me zaka yi mata a dakin ba
sai ka fada muyi maka bayani dalla dalla. Ga
Al'ameen nan. He have been there. Ka
zauna ka dauki darasi" Al'ameen ya gyara
zama tare da gyaran murya "I am glad you
guys realized girmana kuma kuka bani. Ni
nake da experience ni zan bada wannan
darasin". Gidado ya mike tsaye suka jawo shi
suka sake zaunar dashi. "Ka zauna a gaban
babban malami Sheikh Muhammad
Al'ameen ka dauki darasi" ya ga dai ba
rabuwa zasuyi da shi ba sai yace "to wai ku
ya akayi kuka san cewa banfi shi Al'ameen
din ilimin cikin bedroom din ba?" Al'ameen
yace "kai yaro tsaya matsay in ka. Idan
manya suna magana kayi shiru da bakin ka.
Ka bari sai zuwa nan da kamar jibi sai in fara
saka ka a ajin kusa da nawa". Gidado yace
"ka daina cika baki fa, shi wani ilimin ai ba
sai an shiga aji ake daukan karatu a kansa
ba",
A haka suka shashance har azahar, daga
nan kuma suka fita suna karasa last minute
preparations dinsu na dinner kowa yana so. preparations dinsu na dinner kowa yana so
ya kure adaka dan a samu damar yin new
catch ko kuma a burge current budurwar da
ake da ita, a lokacin ne bayan sun kebe da
Al'ameen yake gaya masa "ni fa bana son
zuwa dinner din nan" Al'ameen ya bata rai
"ai kuwa kasan baka isa ba. A ina ka taba
ganin anyi dinner babu ango?" Gidado ya
bata rai "kai kadai zaka gane halin da nake
ciki tunda kai kadai kasan gaskiyar maganar
nan, amma kuma kai ma ba zaka gane ba"
Al'ameen yace "to ka ganar da ni mana?"
Gidado yace "bana jin dadi.
21
4
3
7:51 PM
Amma ba zaka gane me yake damuna ba,
nima kaina ban san me yake damuna ba" sai
Al'ameen ya yi shiru kawai ya rabu da shi
dan bashi da amsar da zai bashi.
A motar Al'ameen suka je suka dauki
amarya, Al'ameen din ne yake tukawa Avaan
a gaba, Gidado kuma yana baya. Suna sane
suka yi haka wai dan Gidado ya zauna shi da
amaryar sa a baya, sannan kuma Al'ameen
ya saka Ayaan a gaba dan kar wata a
kawayen amarya tace zata shiga kusa da
shi, "Kar tsautsayi ya sa Humaira ta gani yau
in kwana a kofar dakin ta ina bata hakuri"
Ayaan yay dariya "kar ka bada maza mana"
Al'ameen ya girgiza kai "no.…. Babu wannan
maganar kaji, Maganin kar ayi kar a fara",
Sai da kawayen amaryar kuwa suka yi musu
mitar basu bar gurin babbar kawar amarya
ba, Sannan suka fito da amarva ta shiaa. ba. Sannan suka fito da amarya ta shiga
kusa da angonta suka tafi sauran kawayen
ta kuma duk suka shiga motocin da aka
tanada saboda su. A hanyar ne Safina tace
masa "kayi kyau sosai" ya dago kai daga
danna wayar da yake yi kamar wanda ya
manta a inda yake yace "ohh. Thank you.
You too" ta gaishe da su Al'ameen, suka
amsa mata da faraar su da tsokana, tace ta
gane Al'ameen, amma bata gane Ayaan ba.
"Ko kai ne Sahabi?" "Sahabi?" Suka
maimaita a tare, "waye Sahabi?" Al'ameen
ya tambaya, tace "abokin ku mana Sahabi, I
wanted to know his friends and he
mentioned Sahabi, har ranar nan cikin dare
yace zai kira shi a waya, sai na fahimci they
are very close" "Sahabi?" Al'ameen ya sake
maimaita wa dan baya jin akwai wani very
close friend din Gidado wanda bai sani ba,
Gidado yayi sauri yace "Sahabi mana, Ya
Amen Sahabin ka manta?" Al'ameen yace
"ohh that Sahabi, ai yayi tafiya ne shi yasa,
bai zo bikin ba".
Bayan sunje gurin event din sun jima a mota
kafin ayi musu magana su fito, already tun
kafin su shiga shi Gidado har ya gaji. Suka
fito aka gama jera su kamar zasu je
assembly a makaranta sannan aka ce su
shiga. He walk kamar har zuwa inda aka ce
su tsaya and he stood, aka yi tayi musu liki
from both his side and Safina's side, sannan
aka ce suje su zauna,
Suna zama ya dauko wayarsa ya fara
dannawa ba tare da yasan me yake. dannawa ba tare da yasan me yake
dannawar ba, just to get away from what
was happening around him. And the he felt
it.....
That feeling da ya ke ji a duk lokacin da take
kallon sa, that feeling da yake ji idan yana
tare da ita, he looked up and he saw her,
amma farkon abinda ya fara zuwa zuciyar sa
shine hallucinations yake yi. Dalili na farko
shine me zai kawo ta gurin? Dalili na biyu
kuma shine sam bata yi fitting da gurin ba.
Bata ma yi fitting da kanta ba. She looked
like yan gudun hijirar da suka shigo cikin gari
bayan spending weeks a cikin daji, sannan
aka basu kwancen kaya, kayan da suka yi
musu yawa. Shi a ganin sa ba ta yadda za'a
yi Safiyya, Piyan sa, ta zama haka. Dan ita
din first class ce a cikin yan gayun da ya
sani a rayuwar sa.
She came and stood in front of him, she
talked to Safina and then to him amma shi
duk bai ji abinda tace ba. Sannan ta sauka ta
bi ta wata hanta ta fita daga gurin. Sai a
lokacin hankalin sa ya dawo jikin sa, shin da
gaske Safiyya ce tazo ta tsaya yanzu a
gabansa ko kuma hallucinations yake yi? His
only chance of knowing the answer shine ya
bita ya gani idan da gaske ita din ce, and he
followed kofar da ta bi da sauri ya wuce
masu rabon abinci ya fita filin baya. He saw
her again and they talked or rather argued,
abinda ya tabbatar masa da cewa mutum ce
da gaske kuma Safiyya ce. A lokacin ta gaya
masa maganar da ta karasa tarwatsa. masa maganar da ta karasa tarwatsa
tunanin sa, ta gaya masa cewa Safinar da ya
aura tabbas ita ce Safina yayarta.
She left him frozen a tsaye for a moment,
and then yayi kokarin binta but was held
back by Al'ameen da ya fito neman sa
"lafiyar ka Muhammad, ina zaka je? Me kake
yi anan?" Gidado ya juya yana kallon Safiyya
da take kokarin shiga abin hawa "Safiyya ce.
She was here. She was..." Ya juya ya kalli
hall din "that bitch lied to me. Makaryaciya
ce. I was right. I was right all along and she
lied".
12
9
7:51 PM
Muhammad Al'ameen ya tsaya yana kallon
sa cikin rashin fahimta, Gidado ya juya da
niyyar komawa ciki da sauri yana cewa "I will
deal with her wallahi sai ta gane kuren ta.
Sai ta san ni tayi wa karya" Al'ameen ya rike
shi "lafiyar ka Muhammad? Maganar wa
kake yi ne?" Ya juyo yana kallon shi
idanunsa reflecting irin rage din da yake
cikin zuciyarsa yace "Safina. Karya tayi min
ashe, Ita ce yayar Safiyya, Wallahi sai na yi
mata hauka yau" Muhammad Al'ameen ya
rike shi ya hana shi shiga a daidai lokacin da
Haidar shima ya fito gurin yana kallon su da
alamar tambaya a fuskarsa, Al'ameen yace
masa "Haidar, sauri, dauko min mota"
sannan ya juya gurin Gidado yace "zakayi
mata hauka amma ba'a nan ba, Ba zaka yi
mata hauka a gaban iyayen mu da bakin su
ba". ba"
Daga haka ya saka shi a motar da Haidar ya
dauko ya ja suka bar gurin.
Gidado ya jingina kansa a jikin kujerar motar
yayi shiru, yana jin Al'ameen yana ta magana
amma baya fahimtar abinda yake cewa, ya
san dai hakuri yake bashi da kokarin kwantar
masa da hankali, ya dago kansa a hankali
yana kallon hannun sa yace "her hand looks
and feels like a stick, why?" Ya juya yana
kallon Al'ameen da bai gane tambayar me
yake yi masa ba, ya sake yi masa wata
tambayar "she was pregnant and now she
isn't". Anan Al'ameen ya fahimci maganar
wa yake yi sai yace "Gidado, masu ciki suna
haihuwa. Baka tunanin haihuwa tayi" Gidado
ya girgiza kansa "ba haihuwa tayi ba, cikin
bai isa haihuwa ba. I want to know what
happened to her. I will find out what
happened to her. And I know where I can
get my answers from".
Maman Maama
29
16
15.
EPISODE NINETEEN
owner
26
3
8:04 PM
Nafisa Tafida Usman
Safiyya
owner
Episode Nineteen: Baba Hadiza
Paid advert
*Contact Bojuwa HERBAL'S for all your*
*kayan mata for*
*Amarya*
*Uwargida*
*Bazawara*
*Mai jego*
*Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar
kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi
all from Chad.*
*Kayan gyara masu kyau da inganci kala
daban daban, special maganin sanyi for
women of class*.
*Contact Surayya HALIN YAU on*
*08032773332*. Her

Wani irin sanyin da yake ratsani ne ya tashe
ni daga baccin da bansan sanda nayi shi ba,
ban kuma san dadewar da nayi ina yin sa ba.
Na bude ido na tare da kara takurewa a guri
daya a lokacin da na fahimci cewa a toilet
nake kwance akan tiles. Sanyi nake ji har
cikin kashi na. Da kyar na iya mike wa
saboda karkarwar da jiki na yake yi. Ina
mikewar kuma sai naji gurin aikina ya fara
wani irin zugin azaba kamar wanda dinkin ya
ke budewa. Da kyar da daddafa bango na
fito daga toilet din na koma daki a daidai
lokacin da naji ana kiran assalatu. Wato dai a
toilet din na kwana.
Abubuwa ne da yawa suke faru wa da ni a
lokaci daya, azababben sanyi nake ji har
cikin kashi na, azababben ciwo nake ji a
gurin da aka yanka cikina, ga kaina yana
wani irin sarawa kamar zai sage gida biyu,
ga wata irin yunwa da nake ji wadda ta tuna
min da cewa rabona da abinci tun a Berlin
da Aunty Hajjo ta bani.
A carpet na sake kwanciya saboda
karkarwar da jiki na yake yi ya hana ni
karasawa kan gado, Na daga hannuna da
kyar na jawo blanket din da yake kan gadon
ya fado jikina. Na sake takurewa a guri daya
ina karkarwa tare da ambaton sunan Allah, a
raina kamar kullum ina fatan zai dauki raina
a ranar in huta. Bakin cikin duniya dai ai mai. a ranar in huta. Bakin cikin duniya dai ai mai
rai ne yake jin sa ko? In babu ran ba
shikenan ba?
Na fara lissafa wadanda zasu yi kewa ta idan
na tafi. Daddy na ne na farko, duk da dai
babu wanda ya san gawar fari amma ina
saka ran cewa shima ba zai jima ba idan na
mutu zai bini. Daga Daddy sai Muhammad,
saw my love burning in his eyes jiya da
daddare, daga dukkan alamu plan dina na
cire soyayya ta daga cikin zuciyarsa idan
nayi breaking heart dinsa did not work, and I
pity him for that, but na san babu abinda
time baya healing, he will get over me a
hankali musamman idan ya tabbatar da
cewa bana duniya. The last one is Junior, he
will grow up maraya, fatherless, motherless,
without even a single grandfather, or a
single relative dan na san a dangina babu
mai daukan sa ya kira shi da jinin sa, except
idan bayan mutuwa ta Daddy did to him
abinda Ammi tayi min, idan kuma hakan ya
faru da shi to kuwa tabbas sai nafi tausaya
masa akan kasancewar sa maraya. Because
the vultures will turn to feed on him a
hankali a hankali har sai sun rabashi da
komai kamar yadda suka yi min, Kamar
yadda suka raba ni da komai da yake da
value a rayuwata and then discard me to die
in the toilet,
Na tuna da gata na, da ace da ne babu
yadda za'a yi in kwana a cikin toilet kuma
wai babu wanda ya sani because no one
cared to look for me duk kuwa da cewa. cared to look for me duk kuwa da cewa
gidan a cike yake da mutanen da suke kiran
kansu da yanuwana. Bunch of munafukai.
Duk kan su munafukai ne. And every single
one of them played a role in kasancewa ta a
halin da nake ciki a yanzu. Mukhtar
included.
I chose to marry Mukhtar saboda bani da
wani zabi kamar yadda na gayawa Daddy
na. Dalilin zaban sa akan sauran kuma shine
kasancewar Mukhtar ya jima yana sona. Ya
furta cewa yana son aure na tun kafin yasan
gaskiyar wacece ni. Wannan ya banbanta
soyayyar sa da ta Mustapha and his mother.
Duk da cewa deep down na san cewa
soyayyar tasa ba ta gaskiya ba ce ba but at
least he did love me in his own way. Amma a
daren jiya ya tabbatar min da tasa kalar
soyayyar, ya tabbatar min da abinda nake
tunani a cikin zuciyata. A ganina babu
wanda zai min soyayya ta gaskiya sannan ya
tarar da ni a halin da ya tarar dani jiya
sannan har ya nemi wani abu a guri na. Wani
abu a jiki na. At least na tabbatar Gidado ba
zai taba min hakan ba.
24
16
3
A 1 8:15 PM
For all the years that we have been together
I have seen his desires of me in his eyes
more times than I can count but he never
ask me for it. Ko a waya kuma, He never
even try kissing me duk kuwa da irin
wayewar sa da kuma irin yadda rayuwa ta
zama. Abinda yayi ta tambaya kuma yayi ta. zama. Abinda yayi ta tambaya kuma yayi ta
naci akai shine aure. Abinda ni kuma naki
bashi hadin kai akai.
For all these months da nake cikin wannan
tashin hankalin na san cewa daga cikin
abinda ya saka Daddy yake daga min kafa
mai kakkarya ni ba kamar yadda Mommy ta
kan fada a lokuta da dama shine deep down
him ya san cewa akwai laifinsa akan abinda
ya same ni, sai dai bai taba furta hakan ba,
nima kuma na san akwai laifinsa akan abinda
ya same ni, amma ni ma ban taba furta
hakan ba, and for all the parts da yake nashi
ne a cikin maganar, na yafe mishi.
And na yafe wa Ammi ita ma, for she
thought she was doing the right thing for
me. And now as I lay on the floor waiting
and wishing for the hundredth time that
malakul maut will visit me and end my
suffering, I rewind my life back
Idan nace my life, sai inga cewa bata bada
ma'ana ba, dan ni din product ce of many
things, dole rayuwata ba zata tsaya tayi
zaman kanta ba sai na jingina ta da wadanda
suka samar dani, mahaifiyata da mahaifina,
saboda choices din su, losses din su and
sacrifices dinsu sune suka y making and
shaping rayuwata zuwa abinda take a yanzu,
Asalin mahafiyata kamar yadda na samu
labari daga Daddy, Mommy da kuma Hajiya. labari daga Daddy, Mommy da kuma Hajiya
sun gaya min cewa yar garin Kura ce ta jihar
Zamfara anan Nigeria. Anan tushen mahaifin
ta yake, har yau kuma yanuwanta suna can
amma kuma Daddy ya haramtamin zuwa
gurin su, yace min kuma shima wannan
wasiyya ce daga Ammi na, daya daga cikin
many wasiyyun da ta bar min. A labarin nata
na fahimci cewa mahaifiyar ta, ba yar Kura
ba ce ba, yar wani kauye ne kusa da Kurar
da ake kira kwatarkwashi, kauyen da ya
samu sunan sa daga katon dutsen da yake
kusa da shi, dutsen da ake kira dutsen
kwatarkwashi.
Sunan mahaifiyar tata Hadiza. Wadda Ammi
take kira da Baba Hadiza. Hajiya tace babu
wanda zai zauna da Safiya na awa daya bai
samu kason sa a labarin Baba Hadiza ba.
Kowa da ya san ta yasan cewa tana matukar
son Baba Hadiza.
Mahaifan Baba Hadiza Fulani ne makiyaya
masu yawo daga wanna dajin zuwa wancan
dan ciyar da shanun su, sun haifi yaya da
yawa, Baba Hadiza ita ce yar autar su kuma
sun haife ta ne a lokacin da girma ya riga ya
zo musu har sun dauka sun gama haihuwa.
Tun tana yar karama ne suka daina yawon
kiwo saboda shekarun su da suka ja, suka
bar wa manyan yayan su suka cigaba da yin
kiwo su kuma suka zauna anan garin
kwatarkwashi da niyyar karasa abinda ya
rage musu a rayuwa. Anan Hadiza ta girma,
Bata yi makaranta ba, Ta kan dai yi tallar
nono da fura, da daddare kuma taje nono da fura, da daddare kuma taje
makarantar allo inda ta koyi addini dai dai
yadda zata yi sallah ta kuma zauna da
mutane la fiya.
A tallar noon ne ta had da Alhaji Haladu
wanda babban mutum ne shi mai rike da
mukamin mai unguwa a garin Kura. Haduwar
ta su ta kasance sakamakon kadeta da yayi
a babur din sa lokacin da yake sauri zai
koma garinsa ita kuma tana sauri zata koma
gida gudun kar duhun dare ya ritsa da ita a
daji. Daga nan ya dauketa ya kaita chemist
aka duba buguwar da tayi ya kuma kaita
gidan su ya dankata a hannun iyayenta
sannan ya yi musu nasihar su daina tura ta
talla a matsayin ta na karamar budurwa
saboda gudun kar ta hadu da bata gari a
hanya.
Anan ne suka nuna masa cewa babu ce ta
saka su tura ta tallar, mahaifiyar ta tayi
girma ba zata iya yin tallar ba, mahaifin yayi
tsufa ba zai iya noma ba, sauran yara kowa
ya kama gabansa, ita din dai ita zata tatsi
nonan shanun da suka rage a gurin su taje
ta siyar tayo musu awo ta kawo musu su ci
abinci. Fahimtar hakan sai ya saka ya
tausaya musu, daga nan sai kuma yayi
alkawarin zai cigaba da daukan nauyin su
sannan kuma ya nemi bukatar su aura masa
ita. Daga farko sun ki yarda, musamman saboda
yawn shekarun sa da kuma kankantar nata
shekarun. Dan daga ganin sa sun san
kananan yayansa sune zasu yi sa'annin
Hadiza. Watanni kadan bayan wanna sai
Allah yayi wa mahaifiyar Hadiza cikawa
bayan yar karamar jinyar da Alhaji Haladu ne
ya dauki nauyin siyan magani da komai,
bayan ta rasu ma shi ya tsaya akai mata duk
kan abinda addini ya tanada a ka kaita gidan
ta na gaskiya.
Wannan ya sa mahaifin Hadiza ya ga babu
wani sauran gatan da ya rage zaiyi mata
wanda ya wuce ya aurar da ita, kuma wa yafi
dacewa ya aura wa ita wanda yafi attajirin da
yake kula da su a yanzu? A haka aka daura
auren Hadiza, baffan ta ya siyar da sauran
saniya guda daya data rage masa a gabansa
yayi mata kayan daki, sannan yanuwanta
suka zo daga gidajen su aka hadu aka kawo
ta gidan Alhaji Haladu dake garin Kura.
Gidan babban gida ne irin gidajen attajiran
kauye, katon tsakar gida da katuwar bishiya
sai dakuna a hagu da dama, sai kuma
babban zaure inda yake zama da mutanen
sa, anan kuma kofar turakar sa take.
Matan sa biyu kafin ya auri Baba Hadiza,
Inna Gaje, ita ce uwargida, kusan duk
yayanta sun yi aure sai autar ta sa'ar Hadiza,
daga ita kuma sai Inna Sa'ade, ita kuma
yaya maza Allah ya bata guda takwas,
lokacin da akayi auren Hadiza guda uku
daga ciki sunvi aure, bivu kananan suna. daga ciki sunyi aure, biyu kananan suna
gabanta, ukun tsakiyar kuma duk sun tafi
duniya neman kudi. Kusan ita ce mai kudin
gidan dan yayanta abinda suke samu a
kasuwa ya fi wanda shi kansa mahaifin nasu
yake samu.
Auren yar karamar yarinya Hadiza da Alhaji
Haladu yayi ba karamin sosa ran matansa da
yayansa yayi ba, musamman da suka duba
suka ga tsantsar kyawun fuska da kuma
kyawun surar da Allah yayi mata. A ganin su
zata iya auren duk wani matashi mai jini a
jika da take so, mai yasa ta auri mijin su?
Amsar da suka bawa kansu shine son abin
hannunsa ne ya kawo ta gidan.
A bangaren Hadiza kuwa ita ba zata ce tana
son Alhaji Haladu ba, ita ba zata ce tana son
kowa ba ma saboda ita ba zata ce ta san
menene so ba. Ita dai kawai ta san yana
kyautata wa iyayen ta, daga nan kuma taji
ance mata za'a aura mata shi, sai kuma aka
aura mata shi din aka dauko ta aka kawo ta
gidan sa aka watse aka barta daga ita sai shi
sai mutanen gidan da suke: mata kallon
hadarin kaji ba tare da tasan dalili ba. Da ace
za'a bata zabi da zata so komawa dakin
innar ta ta cigaba da kula da Inna da
baffanta, ta cigaba da zuwa tallan nonon ta
tana zuwa makarantar allon ta, Sai dai babu
wanda ya tambaye ta zabin ta, babu wanda
ya tuntube ta yaji ra'ayin ta, Hukunci kawai
aka yanke mata aka kuma barta tare da
consequences din hukuncin da ba ita ta
yanke shi ba. consequences din hukuncin da ba ita ta
yanke shi ba.
Dakin Baba Hadiza shine a farko kana shigo
tsakar gidan, katon daki ne sabon gini da
Alhaji Haladu yayi musamman saboda
amaryarsa. A ciki kuma aka zuba mata
kayan dakin da baffan ta yayi mata, gadon
karfe babba mai runfa da kuma gadon
katako karami, sai dibaida a gefe da aka cika
ta da samiru kanana da manya, tsakar dakin
kuma an shimfida leda har bakin kofa, an
kuma zagaye dakin gabaki dayan sa da
labule. Kana gain dakin kaga dakin amaryar
fulani yar gata.
Sai dai ita Hadiza bata ji duk wanna gatan
ba, tayi kewar iyayenta sosai musamman
mahaifiyarta da ta san bata duniya. A hankali
kuma sai ta fara sabawa, ta fara sabawa
sosai da Alhaji Haladu dan yana matukar
kyautata mata. Duk abinda take so shi zai yi
mata wanda kuma bata so to shima baya
son sa, baya barinta taci abincin gidan sai
dai yaje ya siyo mata a waje, abinci mai dadi
da nama, ya hado mata da kayan marmarin
da ake yayi a lokacin,
Gidan kuma kaf babu wanda ya isa yayi
mata bakar magana, in ma zasuyi sai dai a
bayan idonsa kuma yadda ba zai gane ba in
yazo, dan ko chanjin fuska ya gani a gurin ta
yayi ta tambaya kenan ko wani ne yayi mata
wani abu, ko da kuwa bata kai karar kowa ba
to sai yazo tsakar gida yayi ta masifa yana
neman wanda ya taba masa amaryar sa. Ita. neman wanda ya taba masa amaryar sa. Ita
a yarinyar ta sai ta kara daukan hakan a
matsayin soyayya da gata.
11
2
8:15 PM
Dan haka sanda mahaifinta ya rasu ma tayi
kukan rabuwa da shi amma bata yi kewa
sosai ba dan tana gain Alhaji Haladu ya
maye mata gurbin uwa da uba.
A haka Allah ya bata ciki, shima haka Alhaji
Haladu ya sha rawar kafa, dan akwai sanda
jama"ar gidan suka farka cikin dare suka
ganshi a bakin murhu yana gasa masara,
Hadiza ce tace tana son cin gasashshiyar
masara cikin dare. Idan kuwa tayi amai, haka
zasu ganshi a bakin rijiya yana wanke wa.
A hankali a hankali duk matan suka fita
sabgar sa, suka barshi shi da amaryar sa,
yayan ma kuma haka, duk suka mayar da
hankalinsu kan neman abin duniyar su.
Haihuwa ta farko Allah ya bawa Hadiza diya
mace, Alhaji Haladu ya tambaye ta sunan da
take so a saka wa yar tata, ta kalli
kyakkyawar jaririyar da take kan cinyarta mai
kama da ita tace "Safiya. Na taba jin sunan a
gurin wadansu yan birni da suka taba
tsayawa a mota suka sayi nono a gurina,
nima ina son idan yata ta girma ta zama yar
gayu irin su, ita ma ta ringa tuka mota", A
take Alhaji Haladu yay alkawarin idan yar ta
girma zai siyar da babbar gonar sa ta bakin
titi ya siya mata mota. titi ya siya mata mota.
Safiya ta ga gata, duk wani kayan yan gayu
da Hadiza ta gani zata ce a siya wa Safiya
kuma Alhaji Haladu ko tasa sutturar zai siyar
ya siya mata sai ya siya babu musu, har
keken koyon tafiya ya tafi har cikin garin
Gusau ya siyo wa Safiya Hadiza take dira ta
akai tana tura ta a tsakar gida. Babu wanda
yake tanka mata a matan gidan, ita ma kuma
a yarintar ta bata damu da su kula ta ko a'a
ba, ita dai zata gaishe da duk wacce ta san
ta girme ta ko a matan gidan ko a yayan
gidan, duk wadda bata amsa ba ma matsalar
ta ce. Ta san dai babu mai taba ko da silin
dogon gashin kanta ne.
Shekaru biyu bayan haihuwar Safiya aka
haifi Sauda. Shima sunan Hadiza ce ta zabe
shi tace sunan wata yar garin su ne da take
zuwa makarantar boko "har makarantar
kwana take zuwa kuma ta iya turanci kamar
baturiyar ingila" Alhaji Haladu yayi dariya
tare da alkawarin ita ma wanna Saudan
zata je makaranta "in ta gama makarantar
kwanan ma har kasar waje zan kaita tayi
wani karatun, sai ta hadu da turawan ingilan
a can" daga nan kuwa Hadiza ta dage, ita
lallai yar ta baturiya zata zama, A maimakon
"war" ko "zo" da ta kan fadawa Safiya in
zata kira ta, ita Sauda da "come" ta ke
kiranta, bayan da ta matsawa Dada dan
Inna Sa'ade ya koya mata "zo" da turanci,
"Saboda in fara koya mata tun yanzu, yar
boko zata zama, har ingila zata je tayl
karatu", karatu".
Sauda tana da shekaru uku aka haifi
Khadijah. Ita kuma Alhaji Haladu ne ya zabi
sunan yace "takwara zanyi miki. Amma sai
bambanta ita ace mata Khadijah. Kuma
dama gashi duk tafi sauran kama da ke".
Hadiza ta kalli yarinyar tana jin dadi, ada
bata san menene so ba, amma a yanzu ta
san shi, ta kuma san cewa duk duniya babu
abinda take so sama da yayanta guda uku.
Kamar yadda Alhaji Haladu yake nuna wa
Hadiza soyayya ido rufe haka yake nunawa
yayanta. Alhaji har tsarki yake wa yaran idan
sunyi kashi ko da kuwa uwar ba wani abin
kirki take yi ba. Wani lokacin tana can tana
shiriritar ta zai yiwa yaran wanka ya shirya
su ya fita dasu zaure su zauna tare. Idan
suna zaune kuwa duk mai abin siyarwar da
tazo wucewa sai ya siya musu musamman
idan ya fahimci suna so, kamar yadda indai
aka kawo abin kwadayin da yasan Hadiza
tana so sai ya siya mata ya aika mata dashi
cikin gida ba tare da ya tuna da sauran
matan sa ba. Idan sunyi korafi sai ya hau
fada "yanzu wannan yar karamar yarinyar
kuke kishi da ita? Yarinyar da kuka kusa yin
jika da ita?" Ko kuma yace "marainiya ce
bata da uwa bata da uba, Bata sana'a bata
kuma da manyan yayan da zasu siya mata,
Ku kuwa kudin da yake cikin zanin ku yafi na
aljihuna yawa. Abinda yayan ku suke baku
ko rabin sa basa bani ni",
Tsinuwa, bakar magana, mugun baki, Tsinuwa, bakar magana, mugun baki,
aibatawa, kyara, tsangwama babu abinda
Hadiza da yayanta ba su gani ba a gurin
iyalin Alhaji Haladu. Ita kuwa Hadiza babu
abinda ya sha mata kai da su ko abinda suke
yi. Ita a ganinta tunda dai ita bata yi musu
laifin komai ba, abinda duk Alhaji yayi musu
tsakanin su ne da shi.
15
4
8:15 PM
Hadiza tana da shekaru ashirin da uku,
Safiya tana da shekaru tara, Sauda bakwai,
Khadijah kuma hudu. Alhaji Haladu ya
kwanta bacci da daddare amma da safe bai
tashi ba. Ya mutu a cikin baccin sa. Ya mutu
yana da shekaru saba"in da hudu, ya bar
yaya ashirin da matan aure uku.
Mutuwar Alhaji Haladu ita ce dai dai junction
din da Baba Hadiza ta fara girbar abinda ba
ita ta shuka ba, ba ita ta zabi auren Alhaji
Haladu ba, ba kuma ita ta kuma ta saka shi
ya nuna mata soyayya ita da yayanta fiye da
sauran matansa ba. In fact ita bata da
hankali, wayewa da kuma ilimin da zata
banbance dai dai da rashin dai dai, Iyayen ta
da mijin ta su suka yi shuka, ita kuma ita da
yayanta suka yi girbi.
Maman Maama 4
36
24
3
2 EPISODE TWENTY
3
LTE 0
8:13 PM
Safiyya
Episode Twenty: The Tragic Family 1
Paid Advert
*Contact Bojuwa HERBAL'S for all your*
*kayan mata for*
*Amarya*
*Uwargida*
*Bazawara*
*Mai jego*
*Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar
kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi
all from Chad.*
*Kayan gyara masu kyau da inganci kala
daban daban, special maganin sanyi for
women of class*.
*Contact Surayya HALIN YAU on*
*08032773332*, Tun kafin a binne Alhaji Haladu Baba Hadiza
ta fara fuskantar cewa rayuwa ta chanja,
dan da kyar, har sai da jama'ar unguwa suka
saka baki sannan aka bar ta ita da yaran ta
da basu ma fahimci me yake faruwa ba suka
shiga gurin gawarsa suka yi bankwana da
shi. Ta zauna a gaban gawar tana kallon sa,
a zuciyarta tana yi masa addu'ar samun
rahamar ubangiji, sannan kuma at the same
time tana tambayar kanta yanzu yaya
makomar rayuwar su kenan?
Safiya wadda ita kadai ce a lokacin ta fara
fahimtar menene mutuwa, ita ce ta zauna a
kusa da Baba Hadiza ita ma tana kallon
gawar Alhaji Haladu tana kuka, sai dai ita
kukan sabo tare da alhinin rabuwa da
babanta take yi ba wai na tunanin what's
next ba. Saudat da Khadijah kam suma sunyi
kuka, sai dai a nasu bangaren, ganin
mahaifiyar su da yayarsu suna yin kuka ne
ya saka su kukan ba wai dan sun fahimci
abinda yake faruwa ba.
Daga nan Malam Jamilu wanda su Safiya
suke kira da yaya Malam saboda yana
koyarwa a makarantar primary din su,
babban dan Alhaji Haladu yazo ya kore su
daga gaban gawar "kin ganshi ai, sai ki
kwashi yayanki ku fita ku bamu guri mu
shirya shi, kin wani saka shi a gaba kuna
koke koke kamar kunfi kowa son sa" Hadiza
ta mike jiki a sanyaye tana yiwa Alhajì
Haladu kallon karshe, ganin tana cigaba da
bata lokaci ne ya saka Jamilu ya damki. bata lokaci ne ya saka Jamilu ya damki
kafadun Khadijah da na Sauda yayi waje da
su, yaran suka sa ihu saboda zafin rikon da
yayi musu, Hadiza tayi sauri ta biyo shi a
baya "dan Allah ka sake su, dan Allah" ya
ajiye su a tsakar gida ya juya yana cewa
"yanzu ba gashi nan kin fito ba" ta jawo
yaranta jikinta tana lallashin su, daga ita har
Jamilu sun san cewa Alhaji Haladu da ya ke
kwance a daki da ace da rai a jikinsa da ran
kowa sai ya baci idan aka taba masa yan
leken yayan nasa. Amma yanzu o da yana ji
babu abinda zai iya yi akai.
Akayi masa sutura aka yi masa Sallah kamar
yadda addinin musulunci ya umarta sannan
aka dauke shi zuwa gidan sa na karshe.
Hadiza yayanta suka yi masa rakiya zuwa
zauren gidan tare da sauran mata da yayan
gidan, sannan suka tsaya suka kalla yayin da
ake masa Sallah, suna kuma kallo aka dauke
shi aka tafi dashi sannan suka dawo cikin
gida knowing cewa ba zasu kara gain sa
ba,
Amma suna zama Khadijah ta jawo hannun
Hadiza "Baba Hadiza, Baba Hadiza, wai ina
Baba ya tafi ne? Ina aka kaishi?" Baba
Hadiza ta jawo ta jikinta "ya tafi asibiti ne,
bashi da lafiya shine aka kaishi asibiti gurin
likita" Khadijah ta bata rai "ni so nake ya
dawo ko kuma ke ki kaini gurin sa, zuwa
zanyi in gaya masa yaya Malam (Jamilu) ya
matse min hannu na". matse min hannu na".
Kafin Baba Hadiza ta san amsar da zata
bata sai Lami, daya daga cikin yayan Alhaji
Haladu da take zaune a kusa da su tace "ba
sai ki bishi lahirar ba ki gaya masa, kaji
yarinya yar karama da shegen munafunci irin
na gado? Da wannan munafunci ne dama
aka raba mu da mahaifin mu, muna ji muna
gani ya zamanto Baba baya jin maganar
kowa a gidan nan sai ta su" Yar'uwata
Balaraba ita ma ta karba "haba Lami, ke ma
kinsan lamarin Baba da matar nan yafi karfin
munafunci, kowa ma yasan asiri tayi masa
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: kowa ma yasan asiri tayi masa,
surkulle ne kawai irin nasu a fulanin daji
suka hada baki ita da iyayen ta suka yi masa
suka raba shi da kowa suka wahalar da
bawan Allah, yanzu dai wahalar sa ta kare
Allah ya karbi abinsa, ita kuma gata nan ga
gidan sai muga tsiyar da zata zauna a gidan
ta cigaba da ci".
Mutanen da suke gidan suka fara basu
hakuri, "haba ku kuwa, daga tafiya kai shi ko
binne shi ba'a yi ba? Ku yi hakuri ku bar
maganar nan, shi sharri ai dan aike ne duk
abinda tayi ma kanta zai dawo".
15
8
2
8:16 PM
Hadiza ta fara share hawaye "wallahi babu
abinda nayi masa, Allah ne shaida ta babu
abinda nayi masa, iyayena ma kuma sun
mutu kuma babu abinda suka yi masa" Lami
ta mike ta tsaya akan Hadiza tana nuna ta da
yatsa tace
"to in kinyi masa ma Hadiza fada
zaki vi? Mu ai duk mun san kinvi masan. zaki yi? Mu ai duk mun san kini masan
kuma babu abinda zaki fada wanda zal saka
mu yarda da ke, shi kuma ya riga ya mutu za
kuma ku hadu a lahira ke da shi, munafuka
algunguma...
." Safiya yar shekara tara ta
mike ta saka dan karamin hannunta ta tura
Lami baya "ki daina yi mata fada! Ki daina yi
mata zagi! Ki rabu da ita!"
Lami da abun yazo wa a bazata ta kaiwa
Safiya duka, Hadiza tayi sauri ta tare sannan
ta janye Safiya, bata kara yiwa kowa magana
ba ta janye yayanta suka shiga dakin su
suka turo kofa. Tana jiyo Lami tana masifa
ana bata hakuri, ta kuma yi rantsuwar sai ta
illata Safiya ko da ba yau ba.
A haka Hadiza tayi going through zaman
makokin nan, tana daki ita da yayanta sai dai
makota da sauran abokan arziki idan suna
son yi mata gaisuwa su bita daki. Ko toilet
wata daga cikin yayan idan zata je sai Baba
Hadiza ta raka ta saboda tsoron kar a taba
mata yayan ta. Idan ta fita din kuwa kafin ta
dawo sai an yar mata da magana.
Tun daga lokacin suka fara fuskantar
matsalar abinci, babu wanda yake zuba
abinci a gidan yake basu, gashi kuma ita
dama ba gwanar ajjiyar kudi bace ba ta saba
duk abinda take so Alhaji zata tambaya shi
kuma ya siyo ya kawo mata, babu kudi sam
a dakinta sai bankin Safiya da take tara
kudin tarar ta a ciki, in an bata bata kashewa
sai ta saka a ciki. Da yunwa ta ishe su shi
suka fasa Hadiza ta leka ta kira wani yaro. suka fasa Hadiza ta leka ta kira wani yaro
dan makota ya siyo musu abinci a gidan su.
To da yake matar suna mutunci da Hadiza
sai ta dawo mata da kudin ta kuma tace take
aikowa kullum ana karbar musu abinci kafin
a share makoki. To da wannan abincin suka
rayu a wannan lokacin.
A ranar bakwan ne kuma yayan Hadiza
Jabiru wanda a lokacin ya kado shanun sa
zuwa garin yaji labarin mutuwar Alhaji
Haladu sai yazo gidan gaisuwa, da shi da
matarsa da yayan su guda biyu. Hadiza taji
dadin zuwan sa sosai, saboda dama ta jima
bata ga na gida ba tun shekaru biyu da suka
wuce da daya wan nata Audu yazo shigewa
shima ya shigo gurinta shida iyalinsa. Ta kai
su dakin ta suka zauna suka yi mata
gaisuwa tare da jajanta abinda ya faru.
Anan Jabiru ya bar iyalin nasa suka kwana
biyu tare da Hadiza da yayan ta sannan ya
sake dawowa ya zauna da ita yace "yanzu
Inna da Baffa sun mutu, Alhaji Haladu ma ya
mutu, Menene kike so zaki yi yanzu?" Tayi
shiru tana tunani sannan tace "ni ban sani
ba, Ni ban taba yanke wa kaina hukunci ba.
Yanzu tunda kazo kai zaka gaya min abinda
zanyj" ya kalli su Safiya da suke gefe suna
wasa yace "ki hado kayan ki ki taho mu tafi,
kina da sauran yarintar ki wata kila Allah zai
baki wani mijin sai ki sake yin auren ki" ta
danyi tunani sai ta gyada kai da sauri
"shikenan yaya, dama nima ba jin dadin
zaman gidan nan nake yi ba, zamu hada
kayan mu sai mu biku kawai" ya girgiza kai. kayan mu sai mu biku kawai" ya girgiza kai
yana kallon ta yace "ki hada kayan ki nace
ba ku hada kayan ku ba. Wadannan yara ba
da su kika zo gidan nan ba, ki bar su a inda
kika same su nan ne gidan uban su. Ke kadai
ce nauyi na, da ke kadai zan tafi, su nauyin
dangin ubansu ne, su zasu kula da su".
Ta bude ido tana kallon sa sannan ta kalli
yaran nata da suke ta wasan doki a tsakar
daki, Safiya tana yiwa Khadijah doki Sauda
kuma tana binsu a baya. Jabiru ya mike yace
"zan kara kwana biyu a garin nan saboda ki
samu ki shirya a nutse, jibi zan shigo in
dauke ki mu tafi". Ya dauki sandarsa ya juya
ya fita.
Ta zauna ta dafe zuciyar ta tana kallon
yaranta. Kamar yadda ta fada, bata taba
yanke wa kanta hukunci ba a rayuwarta, sai
dai duk hukuncin da aka yanke mata ta bi
shi, yanzu kuma gashi an yanke mata
hukuncin rabuwa da yayanta, yaran da basu
da kowa kaf duniya sai ita. Ya zata vi ta tafi
ta barsu? A gurin wa zata tafi ta barsu? Me
zai faru da su in ta tafi ta barsu? Ita bata da
ilimi, bata san abubuwa da yawa na rayuwa
ba amma ta san cewa duk duniya babu
abinda take so sama da wadannan yaran
guda uku,
15
A
4
P
8:16 PM
Kwana biyun nan haka tayi su cikin rashin jin
da din zuciya, har sai da matar Jabiru da
take tare da ita har lokacin tayi ta tambayar. take tare da ita har lokacin tayi ta tambayar
ta abinda yake damunta amma sai ta dauka
kewar mijinta ne, a rana ta biyun Jabiru ya
dawo daukan su, ya fita da kayan iyalinsa da
suka zo dasu ya dawo yace da Hadiza ina
nata kayan? Ta girgiza kanta tana goge
hawaye daga idonta tace "bazan iya rabuwa
da su ba. Ba zan iya tafiya in bar su ba. In
har na rabu da su to a cikin makara nake
za'a kai ni kabari na, ko kuma sune a cikin
makara za'a kai su nasu kabarin" ya kalle ta,
ya kalli yaran da suke zagaye da ita suna
rike da zanin ta amma duk da haka bai ji
cewa ya kamata ya tafi dasu gabaki daya ba
shi a iya fahimtar sa ta rayuwa gani yake yi
yara, musamman yara mata dole ne su
zauna a gidan uban su, a ganinsa haka shine
dai dai.
Yace "shikenan. Ki zauna tare da su din,
amma ki sani in kina zaune a gidan nan tare
da yaran nan babu namijin da zai aure kj" shi
babbar damuwarsa akanta ita ce kar ta rasa
mijin aure, Har zai tafi kuma sai ya dauko
kudi daga aljihunsa a kulle a leda ya mika
mata sannan ya juya ya tafi. Ta bishi da kallo
tana tunanin ko zasu sake haduwa ko kuma
shikenan?
A ranar yadda Hadiza taga rana haka taga
dare da yayan ta a gabanta tana lissafin
yadda zata fara wannan rayuwar amma ta
kasa yanke shawara. In ta kalli yarn ta tuna
cewa yanzu dukkan nauyin su yana wuyanta
sai taji toro ya kamata. In sun tashi da safe
ma yanzu ita zasu ce ta basu abincin. ma yanzu ita zasu ce ta basu abincin
karyawa, da rana ma haka, suturar
sakawarsu makarantar su, magani in basu
da lafiya, ga kuma overall tarbiyyar su. Ta
kirga kudin da Jabiru ya bata "dubu goma"
su kadai ne abinda ta mallaka a yanzu. Ta
ina zata fara?
Hayaniya ce ta tashe ta da safe da yake sai
da assuba ta samu bacci, a cikin hayaniyar
ta taji ana ambaton sunanta, ta mike da
sauri taga yayanta su ma duk sun tashi suna
kallon ta fuskokin su cike da toro. Ta kuma
fahimci hayaniyar a kofar dakin ta ne, Ta
tashi ta bude kofa tare da tura yayan ta baya
tana kare su da jikinta yadda ko ma menene
ita zai sama ba su ba. Matan gidan ne da
yayan gidan mata wadanda basu koma
gidajensu ba suke ta masifa. Kusan duk a
lokaci daya suke maganganu amma ta tsinci
was daga cikin maganganun nasu
'"wallahi ba zamu yarda ba, abinda akayiwa
baban mu ba za'a cigaba da yi mana shi ba"
"tunda yan'uwan ta suka fara zuwa, Allah
kadai ya san me suke kawo mata"
"wanda yazo jiya ina kallo ya mika mata wani
abu a leda, jikina kuma ya bani asiri aka
kawo mata zata binne mana a gida mu ma ta
mallake mu"
Hadiza ta fara kokarin kare kanta "wallahi
babu abinda suka kawo min, kudi ne kika ga
ya bani", ya bani"
Amma babu wanda ya saurare ta, aka jawo
ta ita da su Safiya aka fito da su waje
sannan aka fara watso musu kayan su
wajen, tana kuka tana rokon mutanen nan
amma basu barta ba, sai da makota da
sauran yan unguwa suka shiga cikin
maganar amma aka kasa sasanta su, su
haushin duk abinda Alhaji Haladu yayi musu
ne suke kokarin hucewa akan Hadiza da
yayanta suna gain cewa sune sanadi,
bayan su kuma a nasu bangaren basu da
laifin komai musamman ma yaran.
Daga karshe dai aka tafi gurin dagaci aka
sanar da shi, ya aika aka kira su har yara
mazan dan a sasanta su amma abu yaki
yiyuwa sunce su ba zasu zauna da ita a
gidan ba, a karshe dagacin yace to ai itama
Hadiza ita da yayan ta suna da gadon Alhaji
Haladu, dan haka ya umarci limamin
unguwar su da yaje ya raba gadon Alhaji
Haladu a bawa Hadiza nata ita da yayan ta
dan su samu gurin zama da kuma abinda
zasu rike kansu.
Amma sai dai da aka zo rabon gadon sai
babban dan gidan yaya Malam yace ai Alhaji
Haladu duk ya siyar da kadarorinsa kafin
rasuwar sa yay wa Hadiza da yaran ta
hidima, yanzu abinda ya rage kawai shine
gidan da suke ciki, Wannan ya sa gidan
kawai aka raba a matsayin gado, shima
kuma gidan su ka nemi cewa a fitar wa da
Hadiza bangaren ta daga gefe dan basa son. Hadiza bangaren ta daga gefe dan basa son
zama da ita. Shima kuma limamin sai yayi
hakan dan in ba'a raba su din ba ba za'a
samu kwanciyar hankali ba.
6
3
8:16 PM
Hadiza da yayanta sun samu dakin soro,
inda nan ne da dakin Alhaji Haladu, tare
kuma da rabin soron dan su samu hanyar
shiga dakin nasu. Dakin ciki da falo ne da
bandaki a ciki, sai dai kuma matsalar shine
dakin nasa yafi ko ina tsufa a gidan, ginin
yafi na ko'"ina lalacewa. Amma duk da haka
Hadiza taji dadin samun seclusion daga
jama'ar gidan. Ta gyara dakin ta jera
furnitures dinta da kayan sakawarsu da
sauran tarkacen ta. Suna cikin gyaran kayan
nasu ne suka ga anzo da kwano irin wanda
ake rufi da shi an raba soron biyu dai dai
yadda liman ya raba musu, wato hanyar ma
ba zasu hada da su ba. Bata gama mamakin
hakan ba sai ji tayi ana buga musu wani
kwanon a windows din su wadanda suke
tsakar gidan. Wannan ya sa dakunan nasu
suka yi tsananin zafi tunda babu taga ko
daya kuma kofar ma gashi an saka musu
kwano an rufe inda iska zata shigar musu,
Kuma tunda basu da kitchen zai ya zamana
a kofar dakin su suke hada wuta suyi girki.
Wannan shima ya taimaka gurin kara zatin
dakunan.
Farko sauran kudin hannunta suka fara
cinyewa, daga nan ta koma daukan kayan
dakin ta daya bayan daya tana kaiwa gurin
dillaliya tana siyarwa a wulakance tana siya. dillaliya tana siyarwa a wulakance tana siya
musu abinci. A haka har suka cinye duk
samiru da kwallayen ta na aure, a lokacin ne
kuma ta fita daga takaba. A lokacin da take
lissafin inda zata samu wasu kudin ne Safiya
ta kawo mata shawara "Baba Hadiza ki ringa
dafa min wake da shinkafa ina yi miki talla,
sai muke samun kudi muna ajiyewa" Sauda
tace "nima zan ringa yin tallan, nima zan
¡ya" Khadijah tace "Baba Hadiza nima zan
yi".
Hadiza ta tsaya tana kallon su sai ta girgiza
kai, "ba zan dora muku talla ba, in kun tafi
talla ta yaya zan kula da ku? In wani abun ya
same ku a can kuma fa? In kuna zuwa talla
kuma a wanne lokacin ne zaku je
makaranta?" Safiya tace "in mun dawo daga
makarantar zamu ke zuwa tallan ai" Baba
Hadiza ta sake cewa "ba za kuyi talla ba" sai
kuma ta kara da cewa "ni zanyi. Zamu ringa
yin abincin siyarwa ku ku tafi Makaranta ni
kuma in tafi talla, a haka zaku yi karatu har
ku girma kuje babbar makaranta ku samu
babban aiki ku gina babban gida sai ku zo
ku dauke ni ku kula da ni, yanzu amma ni ce
zan kula da ku".
Washegari ta kira dillaliya har daki ta sayi
gadajen ta gida biyu tun na aure, ta sauke
musu katifun kasa tace sun she su kwana,
Kudin kuma da su tayi jari. Daga nan sana'ar
wake da shinkafa ta fara, kullum zata shirya
Safiya da Sauda su tafi makaranta ita kuma
ta dafa wake da shinkafa ta goya Khadijah ta
dauki abincin aka ta tafi bakin kasuwa da. dauki abincin aka ta tafi bakin kasuwa da
tasha talla, su kuma in sun taso zasu zo suci
abincin da ta ajiye musu sannan su yi wanke
wanke su gyara musu dakin su sai su tafi
makarantar islamiyya, kafin su dawo ita
kuma ta dawo sai tayi musu wanki ta
shanya akan langa langan kofar dakin su
dan ko shanya ba'a yarda ta shiga cikin
gidan tayi ba. Sannan tayo cefanen abinda
zasu dafa gobe. In dare yayi kuma anan
soron su suke shimfida tabarma su zauna
suyi ta hira tana basu labarai, wani lokacin
na babansu wani lokacin na nata yan uwan,
wani lokacin kuma lissafin abinda take so su
zama nan gaba.
Farko ba sa samun wata riba, except that
suna samu su ci abinci kuma jarin su bai
karye ba, daga baya kuma sai Allah ya buda
musu sana'a ta kankama sosai har jarin ya
ishe su suka fara yin awara da daddare a
kofar gidan. Tun a ranar da suka fara dora
kaskon awara Dauda yazo wucewa ya gani
yace "ba zaku mayar mana da kofar gida
dandali ba, ko ku sauke kaskon nan ko kuma
duk ranar da na kuma ganin sa in barar da
shi". Safiya ta tashi zata yi masa rashin
kunya Baba Hadiza ta hana ta, sai suka
janye suka koma kofar gidan makota suke yi
a can,
Shekarun su biyu a cikin wannan yanayin, a
cikin wadannan shekarun sun kuma
shakuwa da junan su sosai, Basu da wani
tension zasu ci su koshi sue makaranta
kuma suyi wasa da junan su. Basu da kudi. kuma suyi wasa da junan su. Basu da kudi
amma suna da junan su kuma suna gain su
kadai sun isi kansu.
12
8
2
8:16 PM
A lokacin ne wata rana suna tafiya a kasuwa
zasu yi cefanen abincin siyarwar su sai
Safiya ta ga gidan hoto "Baba Hadiza dan
Allah mu shiga muyi hoto muma" Baba
Hadiza tace "wanne irin hoto kuma dan bata
lokaci? Muyi sauri mu tafi gida kar lokacin
dora awara yayi azo nema bamu fara ba"
Safiya ta kara rike hannun ta "dan Allah
Baba Hadiza mu dauka, kinga yanzu Baba
ko hoton sa bamu da shi". Wannan ya karyar
da zuciyar Baba Hadiza, tabbas ko hoton
Alhaji Haladu basu da shi. Sai ta amince
suka shiga suka dauki hoton. Not knowing
wannan hoton shine zai zama memory din
su.
The first tragedy struck shekaru biyu da yan
watanni da rasuwar Alhaji Haladu, ranar
Khadijah ta tashi da mugun zazzabi lokacin
tana da shekaru shida a duniya, Baba
Hadiza ta bata magani ta kwantar da ita a
daki amma har su Safiya suka dawo daga
makaranta zazzabin bai sauka ba sai ma zafi
da jikin ya kara yi, aka sake bata wani
maganin har zuwa washegari amma zazzabi
bai sauka ba, a lokacin ne kuma suka lura
cewa wuyanta ya sankare bata iya juyashi
gefe, sannan kuma bata iya hadiyar abinci.
Sai kuka take yi "Baba Hadiza wuyana ciwo
yake yi, ki kaini asibiti" ta fada da kyar. yake yi, ki kaini asibiti" ta fada da kyar.
Babu shiri Hadiza ta kaita chemist aka duba
ta aka ce sai asibiti, suka je asibiti a take aka
kwantar da su aka ce sankarau ce ta kamata
saboda rashin wadatacciyar iska a dakin da
suke kwana. Aka rubuta musu ma gunguna
da allurai ga kuma kudin gado, babu shiri
hadiza ta fasa bankin da take fara ribar
sana'ar ta ta biya duk kudaden da ake
nema. Kwanan su biyu a asibitin jikin ya sake
ta'azzara aka tura su asibitin Gusau, a
lokacin Khadijah ko magana bata iya yi. A
can sai da duk abinda Baba Hadiza ta tara
suka kare wajen magani, dama ba wani abun
kirki ta tara din ba. Da kudin hannun ta suka
kare ta shigo mota ta dawo Kura ta ringa bin
gidajen yan uwa da yayan Alhaji Haladu
akan su taimakawa yar uwarsu Khadijah su
cece rayuwar ta amma babu wanda ya
taimaka mata, haka ta ranci kudin mota a
makota ta koma Gusau, kwanan ta biyu da
komawa Allah yayi wa Khadijah rasuwa.
Mutuwar Khadijah ta taba Baba Hadiza fiye
da sauran mace macen da akayi mata,
yayanta sune treasure din ta, zata iya bada
ranta a saboda su amma ita mutuwa bata
tambayar zabi wanda lokacin sa yayi shi
take dauka. Su Safiya sunyi kuka kamar
idanun su zasu fado kasa dan suna matukar
kaunar kanwar ta su amma Allah ya fi su
santa. Sai dai ta tafi ta bar wani rami a
zukatansu wanda babu wani wanda zai iva
cike shi. zukatansu wanda babu wani wanda zai iya
cike shi.
Daga nan kuma sai rayuwa ta komawa su
Safiya baya, babu jari babu riba babu abinda
za"a siyar a samu jarin sai tarin basussuka
da suke kansu, ga kuma kewar Khadijah. A
neme nemen jarin da Baba Hadiza take yi ne
taje gidan Hajiya Kyauta.
Hajiya Kyauta macece yar kasuwa, tana
dillancin manyan kaya kuma tana kasuwanci
zuwa garuruwa da yawa a Nigeria wani
lokacin ma har kasashen waje take zuwa.
Baba Hadiza ta nemi ta bata aron kudi ta
sake tayar da jarin wake da shinkafar ta
amma ita kuma sai ta nemi ta bata jinginar
wani abu kafin ta bata jarin. Baba Hadiza ta
gaya mata bata da komai sai tsofaffin
katifun da suke kwana akai sai kuma kayan
sakawar su. A lokacin ne Hajiya Kyauta ta
bata shawara "kina da yammatan yara
kamar wadannan, ki bani ko da babbar ne in
tafi da ita wani garin in kaita aikatau, duk
wata za'a ke aiko miki da kudin da zai isa ki
kula da kanki ki kuma kula da karamar, ita
kuma kin ga an dauke miki nauyin kula da
ita" Baba Hadiza ta juya tana kallon Safiya
da duk ta fita daga hayyacin ta saboda
wahala, tace "aikatau kuma Hajiya, Satiya ba
zata iya aikatau ba" Hajiya Kyauta tace "to ai
koya zata yi. Na kai yara da yawa kuma
sunyi arziki iyayen su ma haka. Baki san a
inda arzikin ta yake ba" Baba Hadiza ya
girgiza kanta "ba zan iya yi mata haka ba. Ba
zan dora mata nauyin kula da ni da yar uwar. zan dora mata nauyin kula da ni da yar uwar
ta ba. Ni ce mahaifiyar ta. Ni zan kula da ita.
In aikin ne ma ni ki nema min in ringa yi ina
samun kudi ina kulawa da su".
14
5
8:16 PM
Hajiya Kyauta tace "to ai in dai zan dauke ki
in tafi da ke sai dai ki barsu anan ke nan.
Kina da wanda zaki barwa su?" Hadiza tace
"bani da kowa sai Allah. In kina da hanya
dan Allah ki samar min aikatau din anan
garin yadda ba zan rabu da su ba. Sai in
ringa yin aikin ina tara kudi har in samu jarin
da zan dawo da kasuwanci na".
Haka ce ta kasance, aka samo wa Baba
Hadiza aikatau take yi a gidan wasu masu
hannu da shuni, kullum da safe su Safiya
zasu fita makaranta ita kuma zata tafi gurin
aikin ta bayan ta dafa musu abinci ta ajiye
musu, in sun dawo zasu ci abinci suyi
ayyukan su a gida sannan su taflislamiyya,
da daddare zata dawo ta taho musu da
abinci daga can. Albashin ta dashi suke
samu suke cin abinci da kudin sabulun
wanka da wanki da littattafan makaranta,
dan duk talaucin su Baba Hadiza ba ta yarda
sun daina karatu ba, Suttura kuma mostly
kwance ake basu a gidan aikin ta da kuma
makotan su, A haka suka sake yin wasu
shekaru biyun, Baba Hadiza ta dan tara jari
kadan sai ta dawo da yin awarar dare tunda
da rana tana gidan aiki babu damar tallan
wake da shinkafa.
A lokacin ne kuma second traaedv va faru. wake da shinkafa.
A lokacin ne kuma second tragedy ya faru.
Lokacin Safiya ta yi jarabawar kammala
primary school, Sauda kuma tana aji hudu.
Kamar kullum sun dawo daga islamiyya suka
yi sallar magrib sannan suka fito waje suka
hada wuta suka fara suyar awara kafin Baba
Hadiza ta dawo. Suna cikin yi Dauda yazo
wucewa ya tsaya yana kallon su yace "bana
hana ku kafa mana dandali a kofar gida ba?"
Basu kula shi ba kamar yadda Baba Hadiza
tayi musu umarni, ya sake cewa "shegu
yayan kaddara, baba dai ya cuce mu da ya
hada mana jini da ku. Gadon talauci" still
basu kula ba duk kuwa da irin zuciyar da
take cin Safiya. Ya sake cewa "ina uwar taku
take ne wai? Ko bata dawo daga karuwancin
ba?" A lokacin ne gabaki dayan su suka
mike suka yi kansa, dama haka yake bukata,
ya damki wuyan su duk su biyun ya shake a
lokaci daya.
Wani yaro dan makotan su da yazo siyan
awara ya ruga da gudu hanyar da yasan
Baba Hadiza tana tahowa, a hanya ya ganta
"Baba Hadiza ki zo Dauda zai kashe su
Sauda. Ta yar da abincin hannunta, abincin
ta na rana da ta ajiye musu zata kawo musu
suci da daddare, sannan ta ruga da gudu ta
sha kwanar da zata kai ta inda yayan nata
suke, a dai dai lokacin da wata mota ta sha
kwana ita ma a guje,
Akan don Safiya motar ta daki Baba Hadiza,
akan idonta kuma Baba Hadizan tayi sama. ta na rana da ta ajiye musu zata kawo musu
suci da daddare, sannan ta ruga da gudu ta
sha kwanar da zata kai ta inda yayan nata
suke, a dai dai lokacin da wata mota ta sha
kwana ita ma a guje.
Akan idon Safiya motar ta daki Baba Hadiza,
akan idonta kuma Baba Hadizan tayi sama
sannan ta fado direct akan titi a gaban
motar. Ta fincike daga hannun Dauda tare
da kurma ihu ta fita a guje gurin da
mahaifiyar tata ta fadi, sai dai tun kafin ta
karasa ta sani har cikin zuciyarta cewa Baba
Hadiza ta tafi ta barsu.
Maman Maama
(a) 28
27
10
6
8:16 PM. EPISODE TWENTY ONE
owner
17
edited 8:42 PM
Safiyya
LTE •
Episode Twenty One : The Tragic Family 2
Paid Advert
*Contact Bojuwa HERBAL'S for all your*
*kayan mata for*
*Amarya*
*Uwargida*
*Bazawara*
*Mai jego*
*Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar
kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi
all from Chad.*
*Kayan gyara masu kyau da inganci kala
daban daban, special maganin sanyi for
women of class*,
*Contact Surayya HALIN YAU on*
*08032773332*. Ta karasa gaban Baba Hadiza tana kallon ta
tana mayar da numfashin gudun da tayi, a
daidai lokacin da Sauda ta karaso ita ma a
guje tare da rike hannun yaruwar tata, sai
kuma ta saki hannun ta durkusa a gaban
baba Hadiza ta rungume ta "wayyo Baba
Hadiza wayyo Allah na" a take jinin da yake
fita daga kan baba Hadiza ya wanke kayan
jikin Sauda. Safiya ta tsaya tana kallon su
bata ce komai ba, a dai dai lokacin da
mutane suka fara taruwa a gurin suna ta
salati, a cikin mutanen ne Safiya taga yaya
Malam ya zo wucewa shima ya leko yana
son ganin abinda ya faru, tayi gurinsa da
sauri, desperate to get any kind of help for
her dying mother, ta kama kannunsa "Yaya
Malam dan Allah ka taimaka mana, dan Allah
kazo ka taimakawa Baba Hadiza" ta fada
cikin rawar murya da karyewar zuciya. Ya
yarfar da hannun ta yana goge nasa hannun
a jikinsa kamar wadda ta shafa wa kashi,
"kar ki kira sunana ki shafa min kashin kaj,
taimakon me zanyi muku? Ni na kade ta? Ba
zanje inyi bayani a gurin yan sanda ba
wallahi" sai ya juya da sauri ya bar gurin, sai
a lokacin ta lura bayan shi akwai yayyensu
wadanda suke uba daya su uku a wajen,
amma duk cikin su babu wanda ya taimaka
musu ko da kuwa ta hanyar gaya musu
magana mai dadi ne,
Mai motar ne yazo a rikice ya daga Baba
Hadiza daga jikin Sauda wadda gabaki daya
ta gama rikicewa, sai da Safiya ta rike ta
sannan aka saka Baba Hadiza a mota suma. sannan aka saka Baba Hadiza a mota suma
sula shiga aka tafi da ita asibiti. Haka Safiya
ta zauna a mota hannayenta biyu rije da na
Baba Hadiza, idanuwan ta akan fuskarta. A
ranta ta san ta mutu, amma zuciyar ta taki
yarda tayi accepting, so take taga ta motsa,
so take taga ko da fatar idonta ce ta motsa,
so take taji ta rike hannun ta kamar yadda ta
rike nata. Amma baba Hadiza motsi ya riga
ya kare. Sai sanyi ma da hannun nata yake
karayi with each passing second.
Gwajin farko da akayi a asibiti aka tabbatar
da cewa ta mutu. Sauda ta kara rilicewa "ka
sake dubawa, ba ka duba sosai ba, ta ji cimo
ne kadai shi yasa ta suma, suma tayi shi
yasa bata motsawa. Ku barta zata tashi.
Likita ka sake dubata".
Safiya tana nata kukan tana kuma rarrashin
Sauda, daga baya sai suka rungume junansu
a gaban gawar mahaifiyarsu jikin su jike da
jininta suna kuka. Duk wanda yake gurin sai
da yayi musu kuka tun daga kan drivern
motar har zuwa likitan da sauran majinyatan
da suke gurin.
A daren aka dawo da gawarta gida, makota
da abokan arziki ne suka yi mata suttura
anan dakin ta a gaban yayanta, sai da aka
gama shiryata ma sannan matan Alhaji
Haladu suka fito, Inna Sa'ade tace ita ba ta
ma ji labari ba sai a lokacin, ita kuma inna
Gaje tace ciwon kafa ne yake damun ta shi
yasa bata samu damar fitowa ba. Sai da
akayi sallar asuba sannan aka fita da. akayi sallar asuba sannan aka fita da
gawarta akayi mata sallah. Aka kuma
dauketa zuwa gidanta na karshe.
Baba Hadiza ta mutu tana da shekaru
ashirin da takwas a duniya, ta mutu shekaru
hudu bayan mutuwar Alhaji Haladu. A
lokacin Safiya tana da shekaru goma sha
uku Sauda kuma tana da sha daya.
Ana tafiya da ita Sauda ta juyo gurin Safiya
idanuwan ta cike da toro tace "Safiya, dan
Allah kar ki mutu ki barni, bana so ku barni
ni kadai a duniya".
Mutuwar Baba Hadiza ita ce worst
experience na rayuwar Safiya, duk wanda ya
san ta ya san har ta koma ga Allah bata
warke daga jimamin mutuwar mahaifiyar ta
ba.
Daga nan Safiya da Sauda suka bude wani
sabon babi a rayuwar su. Kowa ya tausaya
musu tabbas, duk wanda yazo gaisuwa zai
shafa kansu yace "Allah sarki yaran nan abin
tausayj" amma babu wanda yace "ku dawo
gurina ku zauna zan rike ku" saboda babu
wanda yake son responsibilities.
Tail 19
14
10
2
2
8:47 PM
Kawu Haruna, wani kanin Alhaji Haladu da
yake da rai a lokacin shi ya fara gudun
responsibility dinsu lokacin da yaga ana
kokarin lika masa. A gurin zaman makoki yaji. akayi sallar asuba sannan aka fita da
gawarta akayi mata sallah. Aka kuma
dauketa zuwa gidanta a karshe.
Baba Hadiza ta mutu tana da shekaru
ashirin da takwas a duniya, ta mutu shekaru
hudu bayan mutuwar Alhaji Haladu. A
lokacin Safiya tana da shekaru goma sha
uku Sauda kuma tana da sha daya.
Ana tafiya da ita Sauda ta juyo gurin Safiya
idanuwan ta cike da toro tace "Safiya, dan
Allah kar ki mutu ki barni, bana so ku barni
ni kadai a duniya".
Mutuwar Baba Hadiza ita ce worst
experience na rayuwar Safiya, duk wanda ya
san ta ya san har ta koma ga Allah bata
warke daga jimamin mutuwar mahaifiyar ta
ba.
Daga nan Safiya da Sauda suka bude wani
sabon babi a rayuwar su. Kowa ya tausaya
musu tabbas, duk wanda yazo gaisuwa zai
shafa kansu yace "Allah sarki yaran nan abin
tausayi" amma babu wanda yace "ku dawo
gurina ku zauna zan rike ku" saboda babu
wanda yake son responsibilities,
Ta 19
14
10
2
2
8:47 PM
Kawu Haruna, wani kanin Alhaji Haladu da
yake da rai a lokacin shi ya fara gudun
responsibility dinsu lokacin da yaga ana
kokarin lika masa. A gurin zaman makoki yaji. kokarin lika masa. A gurin zaman makoki yaji
ana zancen cewa shi ya kamata ya dauki
yaran. Nan da nan sai yayi dabarar fara furta
maganar yace yaya Malam ne ya kamata ya
daukesu '"sai ka hada su da yaran gurin ka
sa'anninsu" yaya Malam yace "haba kawu,
ni yanzu nawa iyalin ma da yaya nake rikon
su ballantana in karawa kaina da wasu?".
Daga nan sai magana ta fara, aka ringa tayin
su a cikin dangi kamar wasu kaya kowa yana
cewa baya so. A karshe dai su manyan
mazan suka dage lallai sai dai a bar su anan
gidan Inna Sa'ade ta dauki daya Inna Gaje ta
dauki daya. Suma farko suka ce ba zasu
dauka ba sai da aka hada da magiya sannan
suka dauka. Inna Gaje tace
"dama ai tun
sanda Alhaji ya gaya mana zai yi sabon aure
zai auri yarinya sai da muka gaya masa cewa
ba zai auri yarinya karama ta zazzaga yaya
shi kuma gashi girma ya dame shi a karshe
ya barmu mu da yayan mu da rikon yayan da
bamu muka haifa ba, gashi nan kuma hakan
ta faru" Inna Sa'ade tace "haka kawai mu ba
da haihuwar yaya ba yanzu an barmu da
raino, mum gama rainon namu yayan lokacin
da zamu huta yazo amma za'a kawo mana
wani rainon da ban" yaya Malam yace "Inna
ai ba rainon su zakuyi ba, yaran nan babu
wacce ba zata iya kula da kanta ba, kawai
dai su zauna a gurin ku in kunyi abinci ku
zuba musu, shikenan fa, kuma kuma ai zaku
more su tunda zasu ke taya ku aikin gida".
Wannan ne ya saka suka yarda suka dauke
su din, ba wai dan Allah ko dan suna so ba, su din, ba wai dan Allah ko dan suna so ba,
saboda su taya su aikin gida, amma kuma
aikin sai ya wuce na tayi ya koma na bauta.
Dakunan gidan gabaki daya su suke
sharewa, duk girman tsakar gidan nan shima
su zasu share shi suyi wanke wanke suyi
wankin kayan matan gidan saboda idan
basu yi musu ba ba zasu basu sabulun da
zasu wanke nasu kayan ba. Sai dai kuma a
zahiri kusan dukkan aikin Safiya ce take
yinsa da Sauda tun da Baba Hadiza ta mutu
bata dawo cikin hayyacin ta ba. Ko yaya aka
danyi motsi da wani abu sai ta tsorata, ko
yaya aka yi mata magana sai ta firgice,
kusan kullum kuma a cikin kuka take. Amma
babu wanda yake kulata ko da kuwa da
magana mai dadi ce, in tana wannan girgitar
ma sai Inna Sa'ade tayi ta fada tace ita an
hada ta da rikon mahaukaciya.
Haka Safiya zata wuni tana aiki tana kuma
rarrashin Sauda duk kuwa da cewa ita ma
tata zuciyar a karye take, amma in tace ita
ma zata zauna tayi ta kuka wa zai kula da
Sauda kenan? Babu wanda yayi maganar
komawar su makaranta ita ma kuma safiya
bata yiwa kowa maganar ba dan ta san in
ma tayi fada kawai za'a yi mata kuma ba kai
ta za'a yi ba, musamman tunda sabuwar
makaranta zata shiga dole sai an dinka mata
uniform an siya mata books, Sauda kuma a
yanayin da take ciki a yanzu bata jin zata iva
zuwa makaranta,
Watannin su hudu a hannun Inna Sa'ade da
Inna Gaje, azaba iya azaba sun shata a cikin. Inna Gaje, azaba iya azaba sun shata a cikin
watannin nan, reward din aikin bautar su
kawai shine abinci da sabulun wanka, dan na
wanki ma sai dai in Safiya ta wanke wa
matan gidan nasu ta saka nasu kayan a cikin
ta wanke musu suma.
Bayan wata hudun ne ranar nan Safiya tana
kwance a kan tabarmar da ake bata tana
kwana a dakin Inna Gaje ta jyo kukan Sauda
a tsakar gida, ta mike da sauri tana laluben
hanya saboda duhu ta fita tsakar gida tana
kiran sunan Sauda, ta amsa mata ita ma
tana laluben ta har suka hadu a tsakiya. Ta
rungume ta tana jin yadda jikinta yake
karkarwa tace "Sauda me kike yi a waje, a
cikin duhun nan?" Sauda tana kuka tace
"Inna Sa'ade ce ta koro ni waje, na kasa
bacci, toro nake ji, shine nake yin kuka,
shine ita kuma ta koro ni waje".
Safiya ta rungume ta "shikenan ya isa haka,
ki daina kukan, gani nazo taho muje mu
kwanta" ta ja ta zuwa dakin Inna Gaje inda
take kwana, suna zuwa zasu shiga Inna Gaje
ta haska su da fitila, ashe idonta biyu taji
kukan Sauda kuma ta ga sanda Safiya ta
fita, tace "mayar da ita inda kika dauko ta,
wallahi ba za'a kara min wahala ba, ba zaki
kawo min wanna mahaukaciyar yarinyar
daki na ta hana ni bacci ba" Sauda ta kara
saka kuka tana kankame Safiya "Safiya tsoro
hake ji, kar ki. tafi ki barni" Safiya tana bubbuga bayan ta
tace "babu inda zan je, taho mu je mu
kwanta a dakin mu".
A haka cikin duhu suka laluba suka tafi soro
sannan suka tura dakin Baba Hadiza suka
shiga, suka lalubi tsohuwar katifar su suka
kwanta akai tare da kankame junan su, a
haka bacci ya dauke su.
Washegari suka tashi da gyaran dakin Baba
Hadiza, suka fitar da katifun waje suka share
suka wanke bandakin sannan Safiya ta hada
duk wani abu da tasan zata iya siyarwa irin
su tsofaffin kwanuka da tukwane ta kaiwa
yan gwangwan, kudin da suka bata ta auno
waken soya ta dawo da sana'ar awarar da
suke yi da, dama kaskon ta da sauran kayan
aikin ta suna nan. Kullum in ta gama bautar
aikin gida, da yamma kuma zata soya awarar
ta a kofar gidan makotan su, da daddare
kuma zata rungume kanwarta suyi bacci du
kadai a dakin soro, Babu wanda ya tambaye
su me yasa suka dawo dakin, babu kuma
wanda suka yi wa bayani, Sai dai aikin
bautar cikin gida har lokacin bata daina shi
ba, zata yi musu aikin zasu bata abincin
rana kadai, wani lokacin da daddare tana
kallon abincin zasu kira almajirai su basu
amma su ba zasu basu ba,
Nan da nan sai sana'ar awarar ta ta kara
habaka, da ribar suke cin abincin safe da ita. habaka, da ribar suke cin abincin safe da ita
kuma ta hada ta siya wa Sauda littattafai
tace ta cigaba da zuwa makaranta. Sauda
tace "ke kuma fa? Ke ba zaki koma
makarantar ba?" Safiya tace "in Allah yayi
ina da rabon yi sai ki ga nayi watarana.
Yanzu ke zaki yi. Kiyi karatu sosai har ki tafi
kasar waje ki hadu da turawan Ingila" suka yi
dariya tare sannan Sauda tace "ina kewar
Baba Hadiza. Ina so in ganta in gaya mata
kina kulawa da ni".
A haka rayuwa ta cigaba, da safiya ta ga
kudin awara baya isar su sauran bukatun su
sai ta kara wa kanta wata sana'ar, ta shiga
gidajen makota ta gaya musu cewa ta iya
kitso, idan suna son kitso su ringa zuwa tana
yi musu suna biyan ta. Daga nan sai ta kara
da wanki, wankin kayan yaran makota duk
wanda ya ke so ya kawo ta wanke masa ya
biya ta kudi. A haka a haka Safiya har
suttura take sia musu ita da Sauda, Sauda
ta kan taya ta da wankin in an kawo, da
daddare kuma ta taya ta da suyar awara.
Gabakidaya safiya ta fita daga cikin
hayyacin ta, ta rame ta zama sai kashi,
dogon gashinta duk ya lalace ya diddige
saboda wahala, in ka ganta zaka dauka tafi
karfin shekarun ta. Ta san yadda zata samu
kudi, ta san yadda zata yi budgeting su sayi
abinda yake da muhimmanci su bar wanda
bashi da shi. Kullum zata wuni cikin wahala,
in dare yayi kuma ta rungume kanwarta suyi
bacci su kadai a dakin soro. Wannan ya kara
musu matsananciyar shakuwa da junan su. bacci su kadai a dakin soro. Wannan ya kara
musu matsananciyar shakuwa da junan su.
Watanni takwas bayan nan, lokacin da aka yi
shekara guda da rasuwar Baba Hadiza, a
lokacin ne babban dan Inna Sa'ade da yake
Kano yake kasuwanci yazo ya sa aka rushe
bangaren babar ta sa aka yi mata ginin
bulon siminti. Kafin ayi ginin sai da aka yi
ciko sosai dan dakuna suyi sama, sannan
aka jingina katangar ginin a jikin dakin da su
Safiya suke kwana aka rangada wa Inna
Sa'ade dakunan ta na bulon siminti manya
manya guda uku da kitchen din ta da
bandakin ta. A lokacin da aka gama ginin ne,
a lokacin kuma damuna ta sauka.
Tunda damunar ta sauka kusan duk ranar da
aka yi ruwa dakin su cika yake yi da ruwan
sama, a lokuta da dama sai dai su fito soro
su kwanta har sai an gama ruwan sannan su
kwashe wanda ya taru su koma ciki. Tun
Safiya tana daurewa har dai ta samu Inna
Sa'ade tayi mata maganar, sai ta bita da
mugun kallo tace "to yanzu ya za'a yi? Ko
kiran sa zanyi in gaya masa ga daya uwar ta
sa nan bai yi mata sabon gini ba ita?"
Haka Safiya ta hakura ta bar maganar, a
yarintar ta ita damuwar ta shine ruwan da
yake lalata musu kaya kuma yake hana su
bacci, bata hango babban al'amarin da
ruwan zai jawo ba,
A lokacin ne tragedy na uku ya saukar wa
Safiya. Tragedy din daya karasa tarwatsa. Safiya. Tragedy din daya karasa tarwatsa
zuciyar ta, ya kuma mayar da ita ya hade ta
zama tamkar dutse.
10
5
3
1
8:47 PM
A wani daren litinin kamar kullum bayan sun
kwashe kayan suyar awarar su sun kai daki,
suka kunna yar karamar fitilar su suka ajiye,
sannan suka yi shirin kwanciya bacci, suka
kwanta rungume da junan su suna hira, hirar
Baba Hadiza da irin burukan ta akan su,
hirar Khadijah da surutun ta, da kuma hirar
rayuwar su a yanzu. "ni dai Safiya bana so
mu rabu, ko kin girma kin yi aure ma sai na
biki gidan ki, duk inda zaki je sai na biki"
Safiya ta ce mata "babu inda zanje ai na
gaya miki. Kuma ni ba zan yi aure ba. Zan
zauna da ke har sai kin gama karatun ki, kin
samu aiki kin gina babban gida sai ki zo ki
dauke ni muje mu zauna tare" Sauda tayi
dariya "ina kewar Baba Hadiza. Ina so inje
gurin ta" suka yi shiru sai kuma tace "ni
kuma so nake in kin kara girma kin yi aure
kin haihu, ina so yar da zaki haifa ta zama
duk abinda Baba Hadiza take so mu zama.
Ta zama yar gayu mai tuka motoci masu
kyau, ta zama mai ilimi da turanci kamar
baturiyar ingila, sannan ta zama kyakkyawa
kamar Baba Hadiza" Safiya ta jawo ta ta
kwantar da ita tace "duk ke zaki zama haka,
Zan cigaba da yin wankau da suyar awara
har sai kin zama haka" Sauda ta rungume ta
tare da cusa fuskarta a wuyan ta tace "bacci
zanyi yanzu, na daina jin toro yanzu. Kiyi
mana addu'a. Sai da safe" safiya tace "to. mana addu'a. Sai da safe" safiya tace
"to
shikenan. Kiyi baccin ki. Sai da safe" sannan
ta karanta adduoin kwanciya bacci ta shafa
musu.
Da assubar fari Safiya ta farka. Amma ba wai
kiran sallar asuban ne ya tashe ta ba. Ji tavi
kamar ana kiran sunan ta cikin baccin ta, ta
zare hannun Sauda daga jikinta ta mike
zaune, sannan kuma ta tashi tsaye ba tare
da ta san me take yi ba. Ita ba ido biyu ba ita
ba a farke ba. Kamar mai sleepwalking. Ta
bude kofar dakin ta fita sannan ta cigaba da
tafiya ba tare da tasan inda take saka
kafarta ba. Sai da ta kai tsakiyar tsakar
gidan su sannan taji wata kara daga bayanta
"yif!" Karar da ta farkar da ita daga baccin
da take yi, sannan kuma lokaci daya tun
kafin ta juya bayan nata jikin ta ya bata
abinda ya far sannan kuma zuciyar ta ta
tabbatar mata da cewa Sauda ma ta tafi ta
barta.
Ta juya da sauri ta kalli dakin da ta fito daga
ciki just few seconds ago, tun daga cikin
dakin har falon har toilet din har soron
gabaki daya katangunsu sun afka ciki, sun
fada akan Sauda,
Tayi wata irin kara wadda gabaki daya
unguwar babu wanda bai ji ta ba, sannan ta
fita a guje ta hau kan tarin kasar ta fara
kokarin daga kanukan rufin da suka rufe
kasar, Kusoshi biyu ta taka a lokaci daya
amma babu wadda taji zafin shigar ta cikin
kafarta, Kuka take yi da iyakacin karfin ta. kafarta. Kuka take yi da iyakacin karfin ta
tana kiran sunan yar uwar ta "Sauda, kar ki
tafi ki barni", Makota ne suka fara shigowa,
wadansu dama already sun tashi da niyyar
zuwa masallaci, daga baya jama'ar gidan
suma suna fito, da kyar aka samu wani
makocin su ya rike Safiya, hannayensa biyu
ya saka ya rike ta gam a jikinsa yana tofa
mata adduoi sannan aka samu ta nutsu ta
tsaya a guri daya yayin da matasa suka hau
aikin hakar kasar. Gini ne irin na da katangar
mai kauri ce sosai gashi ta sha ruwa dan
haka suma mazan da kyar suke dauke ta.
Ba'a samu tono Sauda ba har sai da gari ya
waye rana ta fito sosai. Tun kafin a dauko ta
dama duk wanda yake gurin ya fitar da ran
samun ta da rai. Sanda aka fito da gawar ta
shi kansa wanda yake rike da Safiya gagara
sa tayi. Tayi kan Sauda tana wani irin kuka
mai ratsa zuciyarsa da ruhin duk wanda
yake sauraronta. Ta rungume ta kamar zata
tsaga kirjinta ta saka ta a ciki. "kar ki tafi ki
barni, dan Allah kar ki barni ni kadai"
A ranar hatta yan'uwan Safiya da basa ga
maciji da ita sai da suka zubar mata da
hawaye, Da kyar aka banbare gawar Sauda
daga jikin Safiya aka yi mata suttura aka yi
mata sallah aka dauke ta a makara zuwa
gidan ta na gaskiya, A lokacin da ake fita da
gawar kowa a gidan kuka yake yi, ba kuma
wai kukan mutuwar Sauda ake yi ba ko kuma
kukan sabo da ita ba, kukan tausayin Safiya
ake yi, da yawa mutane sun dauka ba zata yi
rai ba, sun dauka bin yaruwar tata zata yi. ake yi, da yawa mutane sun dauka ba zata yi
rai ba, sun dauka bin yaruwar tata zata yi.
A lokacin mutane da yawa sun fadi
albarkacin bakin su akan dalilin faduwar
dakin da kuma mutuwar Sauda
6
8:47 PM
'"wannan sabon ginin da akayi shi ya kashe
dakunan"
"to da ya akayi ma aka barsu suke kwana a
wannan gurin su kadai?"
"Ai ruwan cikin gidan gabaki daya cikin
katangun dakunan yake shiga"
Amma kuma babu wanda ya daga maganar
ballantana har a dauki matakin shari'a akai.
Daga nan Safiya ta sake bude wani yet
another page na rayuwa.
She became totally depressed, ta daina cita
daina sha ta daina wanka ta daina magana
da kowa, babu abinda ta so a lokacin kamar
mutuwa, da ana siyan mutuwa da tabbas
zata nemi kudi ta siya wa kanta, Ta koma
dakin Inna Gaje da kwana, tunda bata da
wani gurin zuwan idan ba can din ba, ita ma
kuma Inna Gajen ta dan sassauta mata
yanzu dan bata saka ta aikin komai kuma ko
ta saka tan ma babu tabbas din cewa zata
yi.
Wata daya bayan nan tana kwance a inda. Wata daya bayan nan tana kwance a inda
take kwanciya kamar kullum taji shigowar
yaya Malam, yazo ya shige ta ya shiga gurin
mahaifiyar ta sa a gaishe ta sai safiya taji
Inna Gaje tace "dama jira nake kazo, gwara
ka san yadda zaka yi da yarinyar can kar ta
mace min a daki azo a barni da salati" yace
"me ya same ta?" Tace "bata ci bata sha,
yadda ka ganta din nan a kwance haka take
wuni take kuma kwana. Ni fa ba zanyi jinyar
ta ba. Ku da take yaruwarku ubanku ya bar
muku wahala sai ku san yadda zakuyi da ita,
ni nayi na Allah kuma na gaji haka". Yaya
Malam yace "to Inna ni ai bani kadai ne
yayan ta ba, dan ina babba shikenan komai
sai ace ni? Ba ga su Namadi nan ba su da
suke birni ai sun fi ni arziki" Inna Gaje tace
"to ai ba zasu yi ba, in ta mutu kuma ba za'a
zage su ba kai da aka sani kai za'a zaga.
Dole ka san yadda zaka yi da ita"
Yayi shiru sannan yace "na san me zanyi a
kanta. Ni ba zan kaita gida na ba wallahi in yi
ta rigima da iyali a kanta. Aure zanyi mata.
kwai tsohon hedimastern mu da yayi retire
kwanan baya, dama ya taba yi min maganar
ta yace ko zan bashi ita sai na mayar da
maganar wasa, gwara inyi mata auren kawai
in taje gidan mijin zata warke a can. Gobe in
na hadu dashi zanyi masa magana in har
yanzu yana son ta yazo kawai ay"
Inna Gaje tace "hakan ma yayi, Kace masa
sadaki kawai zai kawo ba sai yayi hidimar
komai ba in yaso sai yayi mata kayan daki,
dan babu abinda zamu siya mata" yace "sai. dan babu abinda zamu siya mata" yace "sai
ta je itama tayi irin zaman da uwar ta tayj"
Baba Gaje tace "to Allah ya sa dai kar a
maimaita, kar taje ta kwantsama yaya shima
ya mutu ta debo yayan ta sake dawo mana
nan".
Safiya ta bude idonta, sannan ta tashi zaune
tana kare wa dakin kallo sai kuma ta mike
tana jin kamar kafafuwan ta ba zasu dauke
ta ba. Waje ta fita, taje ta hau kan tudun
kasar da yake nan ne dakin su a da, inda tayi
rayuwa da iyayen ta da yan'uwan ta. Ta
kwanta ta sake rufe idonta tana jin iskar
damuna tana kada ta, tana shakar kamshin
kasar da take kwance akai. Anan ta yanke
hukunci. Anan ta bude sabon babi a rayuwar
ta.
Ta mike kafarta ko takalmi babu tana tafiya
iska tana yawo da ita, tiryan tiryan ta taka
har gidan da tayi niyyar zuwa, gidan Hajiya
Kyauta. Hajiya Kyauta tana zaune a tsakar
gidan ta sai gain yarinya tayi kamar aljana
ta shigo mata, kafarta da ciwon kusar da ta
taka garin tono gawar yaruwarta, Hajiya
kyauta ta mike a tsorace, sai kuma ta tsaya
tana kallon yarinyar ta a tunanin a inda ta
san fuskarta,
Safiya tace "sunana Safiya, Dan girman
Allah ina so ki taimaka min" sai a lokacin
Hajiya Kyauta ta gane ta, ta koma ta zauna
tare da cewa "ke ce yarinyar nan Safiya yar
gidan marigayiya Hadiza, bana gari ta rasu,
sai da na dawo sannan aka bani labarin. da na dawo sannan aka bani labarin
abinda ya faru da ita. Ina yaruwar ta ki?"
Safiya tace "ta mutu, duk gabaki dayan su
sun mutu. Ni kadai na rage. Ni kadai suka
bari", Hajiya Kyauta taji wani iri a zuciyar ta,
yanayin yarinyar kadai ya isa ya bawa
mutum tausayi ballantana abinda ta fada,
tace "Allah sarki. Allah mai iko. Yanzu to ni
me kike so in taimaka miki da shi? Abinci
kike so ko kudi?"
fan 11
2
1
8:47 PM
Safiya ta girgiza kanta "so nake ki dauke ni
daga garin nan. Bani da sauran abinda zanyi
a garin nan. Bani da iyaye bani da yan uwa
bani da kakanni, ban san dangin uwata ba
dangin ubana kuma basa so na, aure suke
so suyi min, so suke yi in maimaita rayuwar
wahala irin wadda Baba Hadiza tayi, so suke
yayan da zan haifa su maimaita rayuwar
wahala irin wadda ni da yanuwana muka yi.
Ba zan yarda hakan ta kasance da ni ba. Ba
zan bari hakan ta kasance da ni ba. So nake
ki kaini garin da zanje in nemi kudi, kudi
nake so inyi irin wanda yayan da zan haifa
ba zasu taba fuskantar rayuwa irin wadda na
fuskanta ba, kudi nake so in yi yadda ni ce
zan zamanto mutum ta karshe a zuri'a ta da
zai san dacin talauci",
Hajiya Kyauta tayi shiru tana kallon yar
yarinyar da take gabanta tana kuma jin
yadda take zarar magana kamar wadda kae
yiwa wahayi. Tace "ke yarinya ce Safiya. Shi
arziki da talauci ai duk na Allah ne shine
kuma yake rabawa ga wanda yaso" Safiya. kuma yake rabawa ga wanda yaso" Safiya
tace "Allah kuma shine ace mu roke shi zai
amsa mana, zan roke shi ya bani, na kuma
tabbatar zai bani din".
Kyauta tace "to ke yanzu kima da jari ne? Da
me zaki nemi kudin?" Safiya tace "bani da
jari, amma ina da rai na ina kuma da lafiya
ta, da su zan nemi jarj".
Hajiya Kyauta ta sake yin tunani tace "kina
da rai da lafiya amma baki da karfi. Da ke
namiji ce sai in kai ki Kano can ne cibiyar
kasuwanci, sai in kai ki kiyi dako da
laburanci ki samu jari" ta juyo tana kallon
Safiya tace "amma ke macece, yarinyar
mace. Aikatau zan kai ki gidan masu kudi,
Abuja zan kai ki a can masu kudin suke.
Suna bada albashi kuma mai kyau in dai
zakiyi musu aiki mai kyau. Tunda baki da
nauyin kowa kinga zaki tara kudin ki ne
kawai. Daga nan zaki samu jarin da kike
nema" tayi shiru tana cigaba da kallon
Safiya, sai ta sake cewa "gidan Hajiya
Maryam zan kai ki. Yar kasuwa ce sosai
kuma bata da matsala, Zata baki ci da sha
da sutura da magani kuma zata baki albashi,
Sannan zaki koyi dabarun kasuwanci idan
kina zaune da ita, Sai dai akwai yarjejeniya
da zamuyi ni da ke" Safiya ta gyara zama
tace "kome kike so in dai ina da damar yi
miki zanyi mikj" Hajiya Kyauta tace "bana
bukatar ko kwandalar ki, zan taimaka miki ne
saboda girman Allan da kika hada ni da shi.
Amma idan yan uwanki suka kama ki kina
kokarin gudu, ko kuma bayan kinje can suka. ko kuma bayan kinje can suka
gano inda kike, babu sunana a cikin
maganar, bana son shiga cikin rigima".
Safiya tayi murmushin takaici tace "ba zasu
neme ni ba ko sunga bana nan. In sun gano
inda nake ma kuma ba zan dawo ba. In na
bar garin nan na bashi kenan har abada".[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: . EPISODE TWENTY TWO
owner
12:54 AM
Safiyya
Episode Twenty Two: A Green Snake
Bara mu bar Safiya ta huta haka nan......
Let's go back to Fiyya
Naga kunyi missing Malam Muhammadu da
"'Yaya, Yaya, Yaya!"
Naji ana fada ana kuma jijjiga ni. Duk da ban
gane muryar me magana ba amma na san
mutun biyu ne duk duniya suke ce min yaya,
either Hassan ne ko Hussain. Nayi kokarin
bude ido a amma sunyi min nauyi da yawa,
naji ina jin haushin ko ma wanene yake
kokarin tashina, I wanted to go differ into
tunanin Ammi na da yanuwanta, maybe
watakila in nazo gurin da take tafiya ta barni
zata tafi dani wannan karon,
Naji an sake taba ni, wannan karon kuma
muryar macece, muryar Mommy "Safiyya?
Bude idonki ki kalle ni, talk to me" na bude
ido na kamar yadda tace amma dishi dishi
nake ganin ta, na bude baki zanyi mata. nake ganin ta, na bude baki zanyi mata
magana kamar yadda tace amma sai bakin
ya furta "Baba Hadiza" ta kalli wanda yake
kusa da ita? Zaka iya daukan ta, go and look
for someone ko Mustapha" "Mustapha yana
gurin Daddy" ya amsa mata "Daddy " na
maimaita sunan.
Naji an dauke ni, naji kuma an saka ni a
mota, daga nan sai maganganun mutane
mostly muryar Mommy ce tana fada duk da
ban san me take cewa ba.
Sanda na dawo hayyaci na a asibiti na samu
kaina, a kwance akan dago da ruwa a jiki na.
Na kare wa dakin kallo sai naga Daddy a
gefe a zaune akan electric wheelchair dinsa
da dan karamin Alqur'ani a hannunsa. Na
jima ina kallon sa kafin ya fahimci na farko
sai ya rufe qur'anin ya karaso kusa da ni.
"hey there" na kirkiri murmushi "hey"
"ya jikin? Akwai inda yake miki ciwo ne?"
Kusan komai na jikina ciwo yake yi min
amma sai na girgiza kaina nace "babu
komai, Babu abinda yake damuna" yayi
ajiyar zuciya yana kallo na, and once more
na saka gain disappointment a fuskar sa,
Na sunkuyar da ido na kasa, "Doctor ya baki
bedrest amma baki huta din ba ko? You
were supposed to be resting 24/7 amma
shine kika fita" na da go ido na kalle shi sai
na sake mayar wa kasa, ya cigaba "yes,
twins sun gaya min kin fita, kika yaudare su
cewa gurin dinner zaki je, and you ran away. cewa gurin dinner zaki je, and you ran away
daga gurin dinner din suka neme ki suka
rasa. The poor kids have been looking all
over for you. Ina kika je?" Na cigaba da shiru
na "gurin sa kika je ko?" Still shiru.
Ya ja kujerar sa baya "ya Rabb. What should
I do. What should I do ya Rabbi. Safiyya aure
ne akan ki fa yanzu"
Mommy ta bude kofa ta shigo, Esther a
bayan ta da baskets na abinci. Ta kalle shi ta
kalle ni sannan tace "wannan ba lokacin
fada bane ba. Wannan yarinyar da kyar aka
dawo da ita duniyar mu, she called me Baba
Hadiza. Sai kace ta san Baba Hadizan" ya
juyo yana kallo na "Baba Hadiza huh? In ita
take kiran ki tell her ban gama da ke ba. She
took all her kids with her nima ina so ta bar
min tawa" ya karasa yana murmushi.
Mommy ta fara kokarin hada min abinci shi
kuma ya cigaba da magana "Safiya loved
them with everything in her. A lokuta da
dama har kishi nake yi cewa ni bata damu
da ni ba ni da nake da rai kamar yadda ta
damu da su su da basu da rai, And I was
angry at her when she chose death over life,
I thought ta zabi zama da su akan mu ni da
ke. I thought she chose to left us because
she did not love us enough, Sai da na huce
sannan na fahimci gaskiya, she lost
everything sanda ta rasa su, she couldn't
save either of them, and then she got you
and you were her everything, she could save
you so she did. I am sure she didn't even. you so she did. I am sure she didn't even
had a second thought before she jumped
into that water to save you because without
you her life would have been meaningless.
All their lives would have been meaningless.
You are their legacy. You are their dreams"
Na rufe idona ina hango fuskokin su a cikin
hoton da shine kadai abinda na mallaka na
su. Duk da talaucin su but they looked so
contented and happy a cikin hoton.
Mommy ta ajiye farfesun naman da ta zuba
a bowl a gaba na ta fara kokarin tashi na
zaune, na tashi ina rike cikina kamar mai
kokarin hana dinki na budewa. Ta bini da
kallo sannan tayi tsaki "ba kya jin maganar
Fiyya. Ji yadda kika koma dan Allah.
Skeleton ma ya fiki kyan gani. Ba zan kai ki
gidan miji a haka ba wallahi.
16
15
12:56 AM
Sai kin dawo hayyacin ki. Kuma ba zaki dawo
hayyacin naki ba sai kina cin abinci".
Mustapha ya bude kofa ya shigo tare da
sallama, Mommy ta juya kansa "daga ina
kake? Ka barni ina ta fama ni kadai, kana
sane cewa abubuwa sunyi min yawa, ga
wadannan marasa lafiyan ga baki a gida ga
surukan Safina sunce zasu zo in an jima. Ita
tana can ta rufe kanta a daki, Kai ka kama
hanya ka yi tafiyar ka yawon ka" yayi shiru
yana kallon ta har ta gama sannan yace
"Mommy ke fa kika aike ni gidan Hajiya" ta
alive flask din hannunta tace "au. haka ne fa. ajiye flask din hannunta tace "au, haka ne fa.
Then don't just stand there ka zo ka taimaka
masa ya ci abinci".
Ya karasa gaban Daddy ya zuba masa kunun
da ya gani a flask sannan yace min "sannu"
ban kalle shi ba nace "yauwa. Kai ma
sannun ka".
Mommy ta cigaba da maganganun ta ita
kadai, a ciki na fahimci cewa iyayen
Muhammad ne suka kira ta zasu zo daukan
Safina, ita kuma tace ba zata basu ita ba sai
sun zo da Muhammad ya bada hakurin
tafiya da yayi ya bar ta a gurin dinner.
Sai da Mustapha yazo fita sannan ace min
"Hajiya tace tana duba ki. Tace zata zo ta
duba ki" na gyada kai kawai. Mommy ta
bude ido "da wacce kafar zata z0 duba
tan?" Mustapha ta daga kafada "I don't
know. Sako ta bani ni dai" ta girgiza kai
"zanje gidan in na bar nan. Zan gaya mata
cewa likita yace babu dubiya. Ta bari in an
sallame ta zata je da kanta ta kaishe ta".
Sai a lokacin Daddy ya kalle ta "Sa'adatu,
ina zaki je in kin bar nan? Gida gurin surikan
Safina ko kuma gidan Hajiya?" Ta zauna tare
da yin ajjiyar zuciya "ban sani ba ni kam,
Abubuwa sunyi min yawa" yace "ki tafi gida
gurin bakin ki, Ki bar hajiya in tazo ma babu
komai. Ki basu yarinyar nan su tafi da ita.
Kar ki jawo mata rigima a gidan mijinta tun
kafin ta shige shi, Mun gode da kulawar ki.
We are going to be fine. Zaki iya tafiya ba. We are going to be fine. Zaki iya tafiya ba
wani abu"
Tun kafin ta tafi twins suka zo, sannan sai
doctor yazo ya mayar da Daddy dakinsa
yana tsokanar sa wai marar lafiya ya koma
dan zaman jinya. Nima kuma ya dawo ya
gaya min cewa ba zai sallameni ba tunda
banyi hutun da yace min inyi ba.
A gida bayan Mommy ta koma bakin nata
suka zo. Kannen baban Muhammad ne su
biyu da yayyen maman sa suma su biyu,
dukkan su mata. Mommy tai musu tarya ta
musamman suka gaisa, ta kirawo Safina ma
ta zauna daga can ness ta rufe fuska ta
gaishe su, sannan suka gabatar da bukatar
su ta tafiya da Safina.
Daya daga cikin sisters din Mama ta fara
magana "Mun fahimci cewa kinyi fushi ne
shi yasa kika dauke Safina daga gurin dinner
kika taho da ita gida. Kuma a gurin mu
fushin ki is justified. Dan haka muka zo da
kan mu zamu baki hakuri akan rashin
fahimtar da aka samu, muma kan mu lokacin
da kuka taho hankalin mu a tashe yake na
rashin ganin nasa, mun kuma yi ta kiran
wayarsa ba ma samu. Sai da ga baya muka
samu ta dan uwansa sai yake gaya mana
suna tare, wai ya shigo gurin taron da mota
shi kuma angon ya fito yin waya shine ya
dan buge shi da motar bai gani ba, Daga
nan shine suka tafi a duba kafar ko yaji ciwo,
shi yasa muka ji su shiru". Mommy tayi shiru tana kallon su, ta fahimci
su kansu da suke fadar maganar ba su yarda
da maganar ba. Tace "to ya jikin nasa? Da
fatan bai ji ciwo ba" Mammy maman
Muhammad Al'ameen tace "da sauki sosai.
Bai ji ciwo ba" Mommy tace
"Okay tare kuka
zo kenan. Yana waje?" Suka yi shiru, sai
Mammy tace "ba tare muka zo dashi ba
Hajiya. Mu a gain mu idan mu iyayensa
muka zo ai mutuntawar tafì ace shine yazo.
Muna gain idan muka turo shi muka ce
yazo kamar bamu baku muhimmancin da ya
kamata ace mun baku ba".
Mommy ta gyara zama tace "haka ne.
Zuwan naku gaskiya yafi bawa maganar
daraja. Amma abinda yasa naso ace yazo
saboda ni na kasa gane kan alakar da take
tsakanin su da Safina. Ni ban taba ganin
aure irin wannan ba. Babu shauki babu
fahimtar juna sam a cikin sa. Misali yanzu
mu dauka cewa da gaske ne abinda ya gaya
muku cewa dan uwansa ya kade shi a mota.
A matsayin Safina na amaryar da za'a kai
masa a ranar shin bai kyautu ace ya kira ta
ya gaya mata ba? Tunda dai ba unconscious
aka dauke shi ba.
13
9
g A
12:56 AM
Amma maganar da nake yi muku Hajiya tun
da muka fito daga gurin taron nan har yanzu
bai kira wayar ta ba",
Hajiya Hafsat maman Ayaan tace "na
fahimci concern dinki Hajiya, duk uwa dole. fahimci concern dinki Hajiya, duk uwa dole
ba zata so ace ta kai yarta inda ba'a daraja
ta ba, amma in muka yi la'akari da yadda
haduwar tasu ta kasance sai muga cewa
dama dole ba za'a samu shakuwa a tsakanin
su irin yadda muke bukata ba, at least not
for now"
Mommy ta bita da kallo sannan tace "ban
gane yadda haduwa ta kasance a tsakanin
su ba? Ta yaya suka hadu din?" Hafsat tace
"muma yanzu da muka matsa da bincike
akan abinda ya faru din shine mahaifiyar
Muhammad take gaya mana. Shi
Muhammad mahaifansa sun matsa masa ne
suna son ya samo mata suyi masa aure a
dalilin wani personal issue, a lokacin ne
kuma ita...
." Mammy ta katse ta "ina ganin
wannan ba maganar mu bace ba, we only
know muma saboda mun matsa sai munji
real dalilin fitar sa daga gurin dinner, amma
Hajiya Sa'adatu a shawarce kuyi magana da
Safina tunda na fahimci cewa baki sani ba,
ke ma kuma Safina ki yi magana da
mahaifiyar ki, ita ce tafi kowa dacewa da ta
baki shawara akan abinda zaki yi. Mu yanzu
zamu tafi. Yadda kuka yi sai ki sanar da mu.
Amma dai Hajiya ina tuna miki aure dai an
riga an daura, igiya uku ce yanzu ta Gidado
akan Safina".
Suka tashi daya bayan daya suka fita suka
bar Mommy a zaune cikin mamaki, ta juyo
tana kallon Safina cikin zafin zuciya tace "in
kika yi min karya sai na balla ki. A ina kika
samo wannan yaron? A yawon banza kuka. samo wannan yaron? A yawon banza kuka
hadu ko menene?" Safina ta fara kuka, ta na
jin zafin gorin da kaa fara yi mata tun yanzu,
yanzu Allah ka dai ya san a dangin
Muhammad yawn wadanda suka san cewa
ita tacevtana son shi "wallahi Mommy ba
haka bane. Kaddara ce ta fada min. Allah ne
yayi min jarabawa kuma na fadi. Daga ganin
hoton sa Allah ya jarabce ni da son sa. Shine
na nemi sister din sa na gaya mata ita kuma
ta gaya wa iyayensa, su kuma lokacin suna
nema masa mata, shine suka hada mu".
Washegari da safe ina asibiti Hajiya tazo
duba ni kamar yadda tace zata zo. Nayi
wanka kenan na shirya ina cin abinci
Mustapha ya shigo da fruit basket a hannun
sa yace ga Hajiya nan. Mommy ta dauko min
hijab ta miko min "sauri ki sa wannan,
wannan kirjin naki da ya cicciko bana son
Hajiya ta gani" na karbi hijab din na saka
pretending as if Mustapha baiji abinda
Mommy tace ba, Ya ajiye basket din ya
koma sai gasu sun dawo tare, Lubabatu
yarinyar ta tana rike da ita,
Na mike tsaye ina murmushi, har zuciya ta
ina jina dadin ganin Hajiya, tun da na samu
ciki Mommy ta hana ni zuwa gurin ta kuma
tun lokacin ban ganta ba. Ta shigo ita ma da
murmushi a fuskarta tace "babu ruwa na da
ke ai, ni nayi fushi da ke, yarinyar nan ki kira
ni a waya ma ba zaki kira ni ba. Sau nawa ina
cewa a gaya miki ki kira ni?" Ta fada da fada
amma kuma fuskar ta da murmushi, na
zauna a kasa a kusa da ita bayan ta zauna. amma kuma fuskar ta da murmushi, na
zauna a kasa a kusa da ita bayan ta zauna
ita ma nace "bani da lafiya ne Hajiya, kiyi
hakuri" tace "gashi nan kuwa ai duk kin
rame kin kode sai idanuwa kamar mujiya"
ina jin Mustapha yana dariya, ta cigaba
'"Aka ce min kuma an daura miki aure.
Sa'adatu tana ta fada wai kin ce ba kya son
Mustapha ba zaki aure shi ba, ni kuma
banga laifin ki ba yarinya, to waye zai auri
wannan abu haka kamar lagwani? Kai anya
ma kuwa kana cin abinci? Mutum sai tsaho
babu kumari makar bushashshen rake? Ni
kam ko kyauta aka bani wannan a matsayin
miji ba zan karba ba" ya sunkuyo kusa da
mu yace "auren ai ba kokawa bane ba
Hajiya. Kuma kiba ko rashin ta bashi ne yake
nuna mazantaka ba".
Hajiya ta rafka salati, yayi sauri ya mike yayi
waje, Mommy ta juyo da sauri "me yace? Me
yayi?" Hajiya ta maimaita mata abinda yace,
Mommy ta zauna akan gado "ya Rasulullah
ka kawo min agaji, wadannan yaran suna so
su kaini lahira" ni dai bance komai ba dan ni
Mustaphan da na sani zai fadi abinda yafi
wannan nauyi ma,
Hajiya ta jima tare da ni. A lokacin naji suna
maganar Safina da Mommy, na kuma
fahimci Safina still tana gida Mommy tace
bata gama yanke shawara akan ta ba
tukunna. Washegari doctor yace zai sallame mu ni da
Daddy gabaki daya, amma still yace in
cigaba da kwanciya ina hutawa kuma ina cin
abinci sosai. Kafin ya rubuta mana sallamar
ne was bakin suka sake zuwa dubani.
Umma, mahaifiyar Mukhtar, tare da
kanwarsa Salima. Mustapha ne ya shigo da
su. Suma lokacin sun tarar da Mommy a guri
na. Suka zazzauna akan kujerun da suke
dakin suka gaisa da Mommy, sai dai kallo
daya nayi wa fuskar Umma naji gaba na ya
fadi. Wannan ba fuskar umman da na sani
bace ba, umman da kusan ita ce third
mother dina dan daga Mommy a guri na sai
ita, tunda Aunty Hajjo ba haduwa muke yi ba
sai muyi shekaru ba mu ga juna ba.
Na sauko daga kan gadon da nake na
durkusa har kasa na gaishe ta, tayi min irin
amsawar da ni da nake kusa da ita ma banji
ba ballantana sauran mutanen da suke
dakin. Mommy tayi murmushi "Fiyya tana
gaishe ki baki ji ta ba maman Salim" ta juyo
tana kallona tace "naji ta mana, na amsa
mata ma, ko baki ji na masa miki ba?" Ta
tambaye ni, ban bata amsa ba sai na
sunkuyar da kaina kawai ina jin kamar zanyi
kuka. Salima ta yi min sannu na juya gurin ta
na amsa muka gaisa, sai ga Mukhtar ya
shigo, hannayensa rike da ledoji manya, ya
zo ya ajiye su a gaban Umma sannan ya
gaishe da Mommy, ta dauke masa kai itama
ta amsa masa a ciki, sai yace da Umma
"yanzu Abba yake gaya min kun taho nan. "yanzu Abba yake gaya min kun taho nan
shine na biyo bayan ku, sai na ga kun manta
wannan sakon a mota shine na shigo muku
da shi" ta harare shi sannan tayi tsaki tace
"ni ban manta komai ba, babu abinda nazo
da shi. Kai dai kawai tunda ka siyo kayan ka
zaka kawo mata shikenan sai ka bata ai
matar ka ce babu mai hana ka, amma kar ka
saka ni a ciki. Rasa kunya beran salga".
Sai kuma ta mike "to Allah ya bada lafiya"
Mommy tace "Amen, mun gode" ta fita
Salima tana binta a baya, Mukhtar ya cigaba
da zama, da ga alama ya dauka Mommy
zata je ta raka ta hanya, ganin bata da niyyar
tashi sai ya mike shima. "Ina wayarki?" Ya
tambaye ni, ban kalle shi ba na bude
hannayena alamar oho, ni na manta ma ina
da waya. Ya dan daga murya yace "ban san
baki da lafiya ba, babu wanda ya gaya min
baki da lafiya, and I should be the first to
know, I should be the one to stay here with
you" fahimtar cewa rigima yake son tayarwa
sai na dago kaina nace masa "in an jima za'a
sallame ni. Na warke already. Kaje ka raka su
Umma" kamar ba zai fita ba kuma sai ya fita
din.
Yana fita Mommy tabi bayansa da harara,
sannan tace "waccan matar ta san maganar
nan. Kin ga abinda kika jawo wa kan ki ko
Fiyya, kin fara gani ko? To wannan somin
tabi ne, ita wannan yanzu ita kika zaba a
matsayin surikar ki, ita zata zama kakar
yayan ki" ban ce komai ba ina ta jujjuya
hannu na. hannu na.
Sai kuma cewa tayi "shegiyar mata mai
kama da muciya" Mustapha ya fara dariya
sai ta nuna masa hanyar waje "fita ka bani
guri, marar kunya fitsararre".
Na dauka Mukhtar zai dawo suyi rigima da
Mustapha amma bai dawo ba, daga alama
yabi su Umma sun wuce. Har aka zo aka
bani takardar sallama, dama already an
kwashe duk kayan mu an tafi dasu gida,
Mommy ta tafi gurin Daddy ni kuma ina
hada abubuwan da suka rage mana sai da
Mustapha ya shigo dakin da nake.
Na juyo ina kallon sa shima yana tsaye a
bakin kofa yana kallona sai nace "bata nan,
ta fita" ya karasa shigowa tare da rufe kofa
ya murda key din jiki. Nayi baya da sauri ina
neman nearest makamin da zan iya kare
kaina da shi. Idanuna suka sauka akan yar
karamar wukar da aka yanka fruits da ita
dazu, na dauka da sauri na nuna shi da ita.
"get out!" Na fada sternly, "ka fita ko in cika
alkawarin da na daukar maka, the next time
you put your filthy hands on me will be the
last time you ever have hands" ya jingina da
jikin kofar tare da saka hannayensa a cikin
aljihu "na sani, I remember exactly what you
said. And I promise you that I will never
touch you again. Magana kawai nazo muyi"
Na cigaba da nuna shi da wukar ina jin
zuciya ta a bushe "I don't want to talk to you
har sai na samu evidence. Now get out tun. dazu, na dauka da sauri na nuna shi da ita.
"get out!" Na fada sternly, "ka fita ko in cika
alkawarin da na daukar maka, the next time
you put your filthy hands on me will be the
last time you ever have hands" ya jingina da
jikin kofar tare da saka hannayensa a cikin
aljihu "na sani. I remember exactly what you
said. And I promise you that I will never
touch you again. Magana kawai nazo muyi".
Na cigaba da nuna shi da wukar ina jin
zuciya ta a bushe "I don't want to talk to you
har sai na samu evidence. Now get out tun
kafin in haka ramuka a jikin ka da wannan
wukar". EPISODE TWENTY THREE
owner
16
6
8:49 PM
Safiyya
Episode Twenty Three: Unexpected
Paid Advert
*Contact Bojuwa HERBAL'S for all your*
*kayan mata for*
*Amarya*
*Uwargida*
*Bazawara*
*Mai jego*
*Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar
kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi
all from Chad*
*Kayan gyara masu kyau da inganci kala
daban daban, special maganin sanyi for
women of class*,
*Contact Surayya HALIN YAU on*
*08032773332*. Ya cigaba da tsaiwa a gurin yana kallona
kamar baiji abinda nace ba, zuciya ta fara
tafasa, he doesn't believe that I can do
anything to him, na fara takawa zuwa inda
yake still da wukar a hannuna "| mean it! Ka
fita ko kuma a fitar da gawarka" ya daga
hannu "okay, okay, zan fita. But still ina so
muyi magana, maybe inkin kara hucewa.
God knows I have been trying my best inga
mun shirya kin ki. I have made a mistake
amma na san babu wanda yake above
mistake. Har ke ma" ya karasa maganar
yana murmushi sannan ya murda key din
kofar ya bude, har zai fita kuma sai ya juyo
yana kallona yace "at least ni nawa mistake
din bai fito duniya ta ganshi ba, naki kuma
rai ne da shi ma, staying there for all to see"
yayi sauri ya karasa fita ya rufe kofar.
Na jefar da wukar sannan na zauna a bakin
gado ina kallon bangon dakin blindly, only
god knows how much na tsani Mustapha
maybe shi yasa bai kaddara zai zama mijina
ba dan da ya zama da tabbas za'a iya rasa
daya daga cikin mu. Amma kuma yanzu
concern dina ba akan Mustapha bane ba
tunda issue din auren sa ya riga ya wuce,
yanzu akan mukhtar ne, mukhtar din da na
zaba da kaina a matsayin miji, I do not love
him but I respected him, sai dai now after
what happened ranar nan da daddare, da
yawa daga cikin respect din da nake bashi
ya gushe daga zuciyata, But then mijina ne,
it wasn't wrong for him to try kissing me
islamically, but his timing was emotionally
wrong.
Sai dai kamar yadda mommy ta fada, ni na. Sai dai kamar yadda mommy ta fada, ni na
zabi kayana and now I have to live with the
consequences of my decision.
Ina nan a zaune mommy ta shigo tace an fita
da daddy in taso mu tafi. Na mike na dauki
yar karamar jakar da take gabana na fita.
Kwana biyun da nayi a asibitin naji dadin
jikina sosai, na dan samu karfi a jikina kuma
na huta sosai. Ina fita naga mukhtar yana
tahowa inda muke, mommy tayi tsaki
"wannan yaron ko maye ne sai haka" yazo
ya karbi jakar hannuna "you shouldn't be
lifting abu mai nauyi, na tabbatar sun gaya
miki haka" nace "babu nauyi ai" ya rataya
jakar a kafadar sa daya sannan ya rike
hannuna da daya hannun, na zame hannuna
da sauri "I am fine" ya tsare ni da ido "ban
yarda ba, in kika fadi kuma fa? If it was up to
me I will carry you to the car" na yi sauri na
zagaye shi na koma side din mommy wadda
na tabbatar taji abinda yace sai dai bata ce
komai ba.
Muna zuwa naga Mustapha yana taimakawa
daddy wajen shiga mota, na karasa gurin na
bari sai da ya zauna sosai sannan na gaishe
shi nayi masa sannu. Yana kallo na yace
"how are you feeling?" nace "na warke, naji
sauki sosai" ya gyada kai "good. That's
good, Shiga mu tafi", Mukhtar ya matso ya
gaishe shi shima sannan yace "zamu tafi
tare da safiyya a mota ta tunda naga kuna
da yawa anan din" na juya ina kallon yawan
namu, Mustapha ne kuma shi zai yi driving,
sai mommy sai ni sai twins amma kuma
twins da mota suka zo. Nayi sauri nace "it is
okay. Twins da mota suka zo ai, It is just me. okay. Twins da mota suka zo ai. It is just me
and mommy" mukhtar ya tsaya yana kallona
bai ce komai ba, daddy yace "ku je, zamu
hadu a gida" har mukhtar ya juya sai kuma
ya kira sunan sa, ya juyo sai yace masa
'"bata da lafiya, kar ka kaita wani guri. Gida
zaka kaita direct daga nan. I mean it" bai jira
amsar mukhtar ba yaja kofa ya rufe.
Mommy ta fara magana "sabon iyayi, ai
kuma shikenan mun shiga ukun mu.....
" ban
ji karshen maganar tata ba saboda shiga da
tayi cikin mota ta rufe kofa amma nasan har
zuje gida ba zata yi shiru ba. Nayi ajiyar
zuciya bayan sun ja motar feeling alone and
vulnerable har sai da suka fita daga building
din sannan naga tsayuwar motar yaya
mukhtar a gaba na.
14
10
8:56 PM
ya bude kofar motar yace "get in" na shiga
na zauna na rufe muka fara tafiya, ban san
me yasa ba kawai sai naji na takura, ba wai
anar ne na fara shiga motar mukhtar ba dan
gfarkon zuwana Abuja kafin uncle ahmad ya
yarda a bani mota mukhtar shine ya zama
kamar driver na to and from school, zuwa
shopping, zuwa duk was unnecessary
yawo na duk inda nace zanje to zai ajiye duk
abinda yake yi ya kaini,
"hey" naji muryarsa ta katse min tunanina,
"tunanin me kike yi ne haka?" na juyo na
kale shi sai yayi min murmushi, na sunkuyar
da kaina ina jin kamar wadda take yin abu ba
dai dai ba, somehow tafiyar da muke yi
yanzu tare da shi a mota reminded me so
much of Muhammad and mv heart feels. much of Muhammad and my heart feels
kamar ina cheating on Muhammad din ne.
na gyara zamana ban ce komai ba sai yace
"just tell me tunani na kike yi shikenan" sai
na samu kaina da murmushi, only if he
knows tunanin wanda nake yi. Ya cigaba
"bana son wannan shirun da kika koya
kwanan nan, the fiyya I know would have
break my ear drum da surutu yanzu. Na
sake yin murmushi ina tuno waccan fiyyan,
na girgiza kaina "she is gone. That fiyya is
gone. Yanzu wata ce sabuwa, and you have
to get use of this sabuwar" yayi ajjiyar
zuciya "yeah, may be. Maybe kuma I will
have to work on bringing her back to life" na
juyo in kallon sa nace "anya kuwa? Ka taba
ganin wanda ya mutu ya dawo?" yace
"wanda ya mutu baya dawowa safiyya amma
ni a yanzu idan da darasin da rayuwa ta koya
min a shine nothing is impossible, babu wani
abunda mutum zai iya cewa ba zai iya
achieving ba a rayuwa. You just have to
work hard ka kuma yi ta addua. Ban taba
tunanin akwai ranar da zan kira ki matata ba,
and today you are my wife.
Na juyar da kaina ina kallon motocin da suke
wucewa. Ita kaddara most of the times is a
complicated something, ba zaka taba gane
yadda take working ba sai ta saukar maka
tukunna, All the small pieces of every event
na rayuwar mu, all the small decisions and
choices da muke making a rayuwa, they all
work together and shape our kaddara, and
addua glued them together, Yay gyaran
murya na juyo ina kallonsa sai ya sake yi min
murmushi. "na ga alamar wannan tunanin ba. murmushi. "na ga alamar wanna tunanin ba
zai barki ba, and I really want to talk to you.
Ina son in baki hakuri about the other day.
Naga ranki ya baci sosai and I know I
shouldn't have done what I did. But you are
my wife ko? So babu laifi ai ko?"
Still ban bashi amsa ba sai najimya tsayar da
motar, na juyo da sauri ina kallonsa sai yace
"safiyya you have to say something. Ba zai
yiwu inyi ta magana da kaina ba kamar
radio, na san ni na ce ina sonki ni kuma nayi
ta naci akan hakan, amma ke kika amince da
kanki kika ce zaki aure ni then it is not a
forced marriage Kenan. Ina saka ran for you
to chose me then at least there is an ounce
of my love in your heart. Dole kuma sai kin
bani dama sannan zan gina masarautata a
zuciyarki" na kale shi cikin ido nace "banajin
dadi ne yaya mukhtar, zuciyata, jikina da
tunani na gabaki daya basa cikin hayyacin
su a yanzu. I have made a lot of bad
decisions because of halin da na samu kaina
a ciki. Some of them have caused me a lot.
Please kar ka zama one of those decisions.
need you to be the strength that I lack, I
need you to help me pass through wannan
storm din da nake ciki. This is not the right
time to discuss love and marriage, A time
will come for that"
Ya juyo sosai yana kallona ya kama hannuna
ya rike, "I will be whatever you want me to
be. In akwai abinda yake damunki tell me, in
akwai wanda ya takura miki tell me inyi miki
maganinsa. I just need you to involve me a
cikin duk abinda yake faruwa a rayuwarki,
but for that I need you to talk to me" na. but for that I need you to talk to me" na
cigaba da kallon fuskarsa, trying to study it,
sai na samu kaina da rashin son abinda na
gani a idonsa, I have seen something similar
a lokuta da dama and I do not like it. Na zare
hannuna daga cikin nasa tare da sake juya
fuskata gefe.
15
8:56 PM
Yayi ajiyar zuciya "and how do you want me
to be all what you mentioned when you
always withdraw from me" na juyo ina
kallonsa nace "what do you want to know?
Wacce maganar kake so inyi maka?" yayi
shiru yana tunani sai kuma yace "anything,
especially personal things wadanda zasuyi
creating bond a tsakanin mu. For example
let's talk about your CS, how did it go?
Where is the baby? Daga ke har daddy babu
wanda yake magana akan what happened a
Berling".
Nace "the CS went fine, anyi shi early ba a
date din da aka saka ba saboda na fara
rashin lafiya. The baby is fine, yana can a
NICU dinsu because he is preterm" ya saka
motar a gear muka cigaba da tafiya sai yace
"namiji ne kenan?" ban kalle shi ba nace eh.
Ya cigaba da tafiya "what do you intend to
do with him?" nace "I don't know, I am not
sure" ya danyi shiru sannan yace "We can
raise him together" na girgiza kaina "not an
option. That will expose him to the world.
Mutane sun san sanda aka yi mana aure
kuma sun san bamu haife shi ba" ya cigaba
da driving "ya maganar barin Nigeria da kika. da driving "ya maganar barin Nigeria da kika
taba yi min? ina ganin hakan idea ce mai
kyau, we can move out mu dauke shi and
settled somewhere" na juya ina kallon shi
bance komai ba, sai ya cigaba "that way za
ki fi healing, away from all that hurt you,
away from wadancan mayaudaran guda
biyu" na rufe ido na ina jin kaina yana fara yi
min ciwo" ya cigaba "any news a kan su? Da
akwai abinda safina ta gaya miki ne ranar
nan?" na bude idona "please yaya mukhtar
ka daina yi min maganar su. I do not want to
talk about them. Please, just take me home".
Daga nan sai yayi shiru din kuwa and we
drove in silence har muka je gida, na san
cewa su daddy already sun je gida by then
saboda tsayawar da mukayi a hanya ga
kuma dama Mustapha shegen gudu ne da
shi a mota. Muna zuwa mai gadi ya bude
mana gate muka shiga, idona yana rufe ina
sauraron yadda kai na yake sarawa. Sai naji
mukhtar yace "woaw!" yana yin yadda yayi
maganar ya saka na bude idona da sauri na
kale shi snnan na kalli inda yake kallo, and
then I saw him,
Muhammad ne a tsaye a compound din
gidan mu a jingine da jikin sabuwar lexus
dinsa, hannayensa cikin aljihunsa,
idanuwansa akan motata da take ajiye a
gefe,
Naji numfashi na ya tsaya a wuyana,
Muhammad a cikin gidan mu? Something
that I have pictured and hoped for years
amma yanzu gashi a gabana amma in an
indescribable way. Mukhtar ya taka burki
yana kallona yace "shall we go back?" ban. yana kallona yace "shall we go back?" ban
bashi amsa ba Muhammad ya juyo ya sauke
idanunsa akan mu. Na lura da yadda ya
gyara tsayuwarsa ya mike straight and his
eyes darted from me to mukhtar and then
back to me.
Mukhtar ya karasa shiga da motar muka
wuce ta gaban gidado sannan yayi packing,
ya juyo yana kallona yayin da ni kuma na
rufe nawa idanun. "do you want us to go
back?" ya sake tambaya. Na harhado
courage dina guri daya nace "what for? In
mun koma hakan zai dawo min da rayuwata
one year back? Hakan zai dawo min da duk
abubuwan da na rasa" bai amsa min ba sai
kuma ya tambaya "me yake yi a gidan nan?
Me yazo yi?" na bude ido na nace "yazo
bawa matarsa hakuri kuma ya dauke ta su
tafi" na fadi maganar da baki na amma zafin
ta yana tafasa zuciyata.
Mun jima zaune a cikin mota babu wanda ya
sake yin magana. Bana ganin Muhammad
daga inda nake amma zuciyata tana gaya
min cewa motar yake kallo har yanzu. And
here I am sitting in the car with my husband.
Na daga hannuna na kama handle din kofar
sai na ji ta a rufe, na juya na kalli mukhtar sai
yace min "don't, kar ki manta nima ina da
zuciya a kirjina, You will neither see him nor
talk to him, ever" ya fadi kalmomin daki daki
with a very serious tune. Na tsaya ina
kallonsa, and he looked dead serious,
Na juya da sauri ko zan sake ganinsa sai
mukhtar ya saka motar a gear ya fincike ta a
reverse a guje ya sake fitar damu daga. reverse a guje ya sake fitar damu daga
gidan. As we were going out of the house, I
saw Muhammad moved from inda yake a
tsaye kamar zai biyo bayan mu but he didn't.
Him
11
11
安1
8:56 PM
Ranar da ya bar gurin dinner a gidan Ya
Amen ya kwana, tun da suka je gidan
wayarsa ta fara kara dan haka ya kashe ta
dan akwai wadanda zasu kira shi kuma ba
zai iya kin dauka ba. Shi ya san yadda yake
jin zuciyarsa a lokacin, ya tabbatar da
maganar Al'ameen cewa rashin zamansa a
gurin ya fi zaman na sa alkhairi dan ba
karamar kura zai tayar da idan ya shiga.
He blamed everyone for what happened,
including Ya Amen dan har da shi akayi ta
convincing dinsa cewa he was being
delusional sanda yake tunanin cewa Safina
is related to Safiyya. Sai da Al'ameen ya
bashi hakuri sannan ya daina blaming dinsa,
ya koma blaming wadda yake ganin gabaki
daya laifin nata ne, Safina. He called her a
liar and a pretender more times than he
count a cikin dare daya,
Ya samu some of his answers, duk da dai
cewa most of the answers shi yayi
concluding kayansa, but the answers also
raised some more questions, Idan har da
gaske Safina step sister din Safiyya ce then
waye Alhaji Adam Muhammad? Baban
Safiyya ko mijinta? Idan babanta ne da
aaske to wave milin nata? And is she trulv. gaske to waye mijin nata? And is she truly
married or not? Ina cikin jikinta yake? And
the most important question, what
happened to her da ya mayar da ita yadda
take yanzu?
Al'ameen got the worst of Gidado a daren
nan, he channelled all his anger and
questions toward Al'ameen, tun yana
kokarin trying to help him figure out
wadansu answers din har ya koma yayi
tagumi ya zuba masa ido. Shi yasan
soyayya, dan haka zai iya kwatanta abinda
Gidado yake ji a ransa.
Daga baya masu kiran wayar Gidado suka
koma kiran ta Al'ameen, daga dukkan alama
sun fahimci shima baya gurin. A dole ya
dauka bayan inda inda da rashin sanin
abinda zai ce musu sai ya gaya musu cewa
ai shine ya buge Gidado da mota kuma ya
tafi da shi asibiti. Daga shi har wadda ya
gaya wa sun san cewa karya yake yi,
wannan ya saka suka cigaba da tambayar sa
gaskiya a karshe dai Maman Gidado ta
karba ta tambaye shi a wanne gidan suke ya
gaya mata suna gidan sa sai kawai ta kashe
wayar.
Ta san Gidado ba son auren yake yi ba but
she thought ya karba tunda har ya bari aka
daura, she never expects him to retreat
back ana tsakiya da biki, Ranta ya baci akan
hakan musamman da Mommy tayi kokarin
tayar da hayaniya a gurin tare da dauke
yarta, but she kept her stance har aka gama
taro aka sallami baki, amma tayi alkawarin. taro aka salami baki, amma tayi alkawarin
bata wa Gidado ransa dan suka koma gida.
Sai dai bayan an tashi daga taron ma bai
koma gidan ba, but he kept asking Al'ameen
ya kira yaji idan an kai amarya, daga baya
dai da suka yi bincike suka gano abinda ya
faru, amarya dai ba'a kaita ba, Mommy ta
mayar da ita gida kuma tace sai yaje ya
bada hakuri sannan zata bashi amarya. He
smiled, shook his head and said "zata rube
a gidan kuwa".
But he wants her to come. Yana so su
kasance shi da ita because daga bakin ta ne
zai samu dukkan amsoshin tambayoyin sa, a
yanzu ita ce link dinsa da Safiyya, link din da
ya jima yana kokarin establishing. Sai dai
zuwa yanzu ya riga yayi tagging dinta a
matsayin makaryaciya, dan haka dole zai bi
a hankali wajen gain ya samu gaskiyar
magana daga bakinta.
Washegari yaje gida, all set and ready for
fadan da yake jiransa, a kuwa ya samu
fadan dai dai gwargwado dan Mama bata yi
masa da sauki ba, Shi ya san babban abinda
zai kara triggering Mama a lokacin shine
idan ya fada mata cewa Safiyya ya gani a
gurin dinner, that Safiyya yar uwar Safina ce,
ya san idan ya fadi haka Mama sai ta
tsinewa dukkan generation din Safiyya, baya
jin akwai abinda Mama ta tsana a yanzu
sama da sunan Safiyya ba ma ita kanta ba,
Sai da ya gama karbar fadan sa, ya samu. Sai da ya gama karbar fadan sa, ya samu
auntie dinsa suka bada hakuri, sannan
Mama tayi musu bayanin dalilin da ita take
ganin ya saka shi ya bar gurin dinner, that
his mind is on some "shegiyar yarinya" da ta
shanye ruhinsa and that he doesn't love his
bride.
9
8:56 PM
Yaji dadin da aunties din nasa suma tausaya
wa lamarin sa, wasu daga cikin su har suka
yi arguing cewa hukuncin da aka yanke
nayi masa aure ba dai dai bane ba, sannan
kuma suma yi volunteering cewa zasu je su
bayar da hakurin on his behalf. He thought
that zasu taho masa da Safina and he will
get his answers that day, sai dai haka suka
dawo hannu rabbana, but da alkawarin cewa
maman Safina zata kira da kanta ko kuma ta
kawo yar tata da kanta.
Sai dai har aka kwana biyu bata kira din ba
kuma bata kawo ta din ba. And he couldn't
wait any longer. Tun a kwana na farko yaje
gidan Hajiya, tunda can ne inda ya sani, sai
dai bai bar mutanen gidan sun san yazo ba
he asked maaikatan gidan inda Safina take
and he got the address na gidan da aka ce
anan ne Safinar take a wannan lokacin
"gidan marikin ta ne, mijin mahaifiyarta, a
gurin sa ta girma ai dan haka can ne gidan
su" mai gadin nan mai surutu ya gaya masa,
Ya rubuta address din a goggle map dinsa
sannan ya sake tambaya "shine Alhaji
Adam?" Yayi shiru yana jin zuciyarsa tana
buaawa, waitina for the answer, mai aadin. Adam?" Yayi shiru yana jin zuciyarsa tana
bugawa, waiting for the answer, mai gadin
yace "eh Alhaji Adamu ba. Mutumin kirki ne
ai sosai. Ya rufe ido yana jin wani abu yana
sauka a cikin zuciyarsa.
So Safiyya didn't lie about her father, she is
not a gold digger. Babanta ne Daddy ba wai
mijinta ba. But how comes aka saka sunan
ta a matsayin matarsa?
Yayi tunanin sake using wani card din ko zai
kuma samun amsa amma kuma baya son
tsohon mai gadin ya zarge shi da wani abu.
"okay, okay na gane Alhaji Adamu, shine
baban Safiyya ko?"
To his delight sai mai gadin ya gyada kansa
"eh shine. Yarinyar kirki. Ai bata da lafiya
ma. Yanzu Hajiya ta tafi duba ta" Gidado ya
bude ido yana jin zuciyarsa tana bugawa
"me ya same ta?" Mai gadin ya daga kafada
"ban sani ba, bata dai da lafiya. Hajiya naji
tana fada".
Gidado ya saka motarsa a reverse da sauri
sai kuma ya dakata ya dauko kudi a
aljihunsa ya mika wa mai gadin, sannan ya
bar kofar gidan a guje ya doshi kwatancen
da aka bashi,
Shi kansa bai san in yaje gidan me zaiyi ba.
Zai ce yazo bawa safina hakuri ne kamar
yadda mahaifiyar ta ta nema ko kuma zai ui
pretending as if yazo duba Safiyya ne. But
that will sound odd considering the. that will sound odd considering the
situation. Har yaje gidan bai yanke shawarar
abinda zaiyi ba.
Sai dai tun daga gate mai gadi ya hana shi
shiga ya kuma gaya masa cewa masu gidan
basa nan.
"Alhaji ba lafiya, duk suna asibiti
gabaki daya" yayi shiru yana tunani, Safiyya
aka ce masa bata da lafiya ba Daddy ba, ko
dai ba gidan yazo ba?
Ya sake tambaya "Safiyya ma bata nan?"
And the rude mai gadi just said "eh bata
nan" and closed the gate. Muhammad ya
tsaya yana kallon gate din da sakakken baki.
No, this mai gadi will not stop him from
getting inside. Ya bude kofar motar ya fita
yayi knocking a gate din, mai gadin ya sake
budewa ya tsaya yana kallon sa, irin kallon
tuhumar nan, Muhammad yace "sunana
Muhammad, nine mijin Safina ta gidan nan,
na san baka sanni ba" sai yaga mai gadin
yayi murmushi "angon ne ai ashe. To ai ni
ban sanka ba. Bismillah bara a bude maka
kofa. Ai farko Safiyya kace shi yasa kaga na
ki kulaka saboda doka ce daga Alhaji kar mu
bar wani wanda bamu sani ba yazo gurin
Fiyya" Muhammad ya kirkiri murmushi, a
zuciyarsa yana adding question din why a
cikin jerin questions din da yake da su.
Amma a fili sai yace "naji ance bata da lafiya
ne Safiyya, shi yasa kaji na tambaye ka ita"
mai gadi yace "eh bata da lafiya, ita ma duk
suna asibiti, Su Hajiyan ma duk suna tare da
su a can. Hajiya Safina ce dai ban tabbatar
ko tana ciki ko kuma tana asibitin ba, ko a. ko tana ciki ko kuma tana asibitin ba, ko a
dubo maka ita?" Muhammad ya girgiza kai
"no. Zan kira ta a waya. shikenan, na gode"
Ya juya ya koma cikin motar wanting with all
that is in him ya koma ya tambayi wanne
asibitin ne amma kuma bai san me zaiyi a
asibitin in yaje ba. Ya zauna ya kwantar da
kansa akan head rest din motar yana bitar
amsoshin da ya samu so far. Da kuma
sabbin tambayoyin da amsoshin suka yi
creating. Zuciyar sa tana kwadaita masa
"she is not married.
10
9
8:56 PM
Karya tayi maka" but why will she lie? Idan
kuma da gaske kara tayi masa then da
gaske bata son sa ne tana so ne ta rabu da
shi, idan kuma haka gaskiya ne then all this
is for nothing.
Gidan Al'ameen ya koma dan har yanzu
Mama da Abba basu huce da shi ba, a can
ya sake kwana sannan washegari ya yanke
shawarar komawa neman labarin Safiyya in
the guise of neman Safina.
Ranar yana zuwa mai gadi ya gane shi ya
bude masa gate ya shiga, Muhammad yayi
packing yana kallon tangamemen gidan da
yake gabansa, gidan su Safiyya, gidan da ya
roki Safiyya ta kawo shi sau ba adadi tana
kawo masa excuses, But the house looks
empty kamar ba'a zama a cikin sa sosai. Mai
gadi ya zo har inda yake ya gaishe shi ya
kuma dava masa cewa Safina tana ciki dan. gadi ya zo har inda yake ya gaishe shi ya
kuma gaya masa cewa Safina tana ciki dan
ya ga shigar ta dazu, sannan kuma ya kara
da cewa "yan asibitin ma an sallamo su sun
dawo, yanzu aka shiga da Alhaji ciki" ya
hadiye abinda ya tsaya masa a zuciya yace
"har Safiyya?" Mai gadin yace "a'a ban ga
shigar Fiyya ba. Maybe ba'a sallamo ta ba
ita"
Sai kuma ya wuce ciki yana cewa "bara in
sanar musu cewa kazo" an jima kadan ya
dawo zai bashi amsa sai kuma ya jiyo horn a
gate, dan haka ya wuce da sauri bakin gate
din. A lokacin ne Muhammad ya ga motar
Safiyya, ya tsaya yana kallon ta, so it really is
true, duk wadannan abubuwan da yake
ganin su kamar a mafarki da gaske ne ashe,
Da gaske gidan su Safiyya ya shigo yau yake
tsaye a cikin sa but a matsayin mijin Safina.
And then he felt that feeling, and he knows
cewa ta shigo gurin. Ya juyo suka hada ido.
Ita din ce a zaune a mota da cousin dinta
Mukhtar a gefen ta, that Mukhtar that he
doesn't like, Suka wuce shi and packed a
bayan sa. Ya tsaya yana kallon motar yana
jiran yaga abinda zai faru, many questions
running through his mind, Why are they
together? And me suke yi a motar da ba
zasu fito ba? And his whole world came
crashing on him. Wani irin kishi yaji yana
kona zuciyarsa, so yake yi kawai yaje ya
finciko Mukhtar daga cikin motar yayi ta
dukan sa ba dan yayi masa komai ba. Ya fara
tafiya toward da car kenan sai Mukhtar din. jiran yaga abinda zai far, many questions
running through his mind. Why are they
together? And me suke yi a motar da ba
zasu fito ba? And his whole world came
crashing on him. Wani irin kishi yaji yana
kona zuciyarsa, so yake yi kawai yaje ya
finciko Mukhtar daga cikin motar yayi ta
dukan sa ba dan yayi masa komai ba. Ya fara
tafiya toward da car kenan sai Mukhtar din
yayi reverse da motar a guje ya fita daga
gidan kamar yadda ya shigo. Episode Twenty Four
owner
5
8:39 PM
Safiyya
el
LTE 0
Episode Twenty Four: The Interview
*Contact Bojuwa HERBAL'S for all your*
*kayan mata for*
*Amarya*
*Uwargida*
*Bazawara*
*Mai jego*
*Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar
kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi
all from Chad.*
*Kayan gyara masu kyau da inganci kala
daban daban, special maganin sanyi for
women of class*.
*Contact Surayya HALIN YAU on*
*08032773332*,
Yabi motar da kallo, contemplating on what
to do, his first thought was to follow them,
but why will he do that. As far as he knows
Safiyya matar aure ce and that guy da suke. Safiyya matar aure ce and that guy da suke
cikin mota tare is her first cousin, shi kuma
matsayin sa shine mijin step sister din ta. In
ya bisu mai zai yi musu, menene business
dinsa da su? But zafin da yake ji a zuciyarsa
kept increasing ta yadda har idanunsa sai da
suka yi ja, ji yake kamar kansa yana turiri.
Shin haka zafin kishi yake? Shin haka shi
tasa kaddarar take? Shin haka rayuwar zata
cigaba ko akwai ranar da zai daina jin
wannan zafin a zuciyarsa. Shin akwai light at
the end of the tunnel?
Mai gadi ne ya dawo daga rufe gate din da
yayi ya cigaba da kokarin yi masa magana
"yallabai ance ka shigo, bismillah" Gidado ya
kalle shi kamar lokacin ya fara ganinsa,
sannan ya kalli gate din kamar mai neman ta
inda Safiyya zata tsaga gate din ta shigo.
Sai ya girgiza kansa, not now, not like this,
ba zai iya shiga cikin gidan ba a yanzu, he is
not functioning right kuma baya so yayi
messing up position dinsa a yanzu.
Ya juya yana kallon mai gadin yace "tell
them an kira ni emergency yanzu, wani uzuri
ya taso min na fita" ba tare da ya jira amsar
mai gadin ba ya shiga motar sa da sauri ya
kunna ta, he used all his self control to keep
calm har ya fita da motar daga gidan and
then he lost it ya ci taya a waje ya figa a
guje, without knowing where he would go.
The first thought that came to his mind was
'irin wannan yanayin shi yake saka mutane
da yawa shaye shaye ko' and then 'what will. 'irin wannan yanayin shi yake saka mutane
da yawa shaye shaye ko' and then 'what will
it feel like to get something that will take
away all his pains ya dan samu zuciyar sa ta
huta' yayi sauri ya kawar da tunanin daga
zuriyar sa tare da karanto dukkan adduoin
da ya sani na korar shaidan dan yasan
sharrin sane, shi yake kokarin saka masa
wanna mugun zaren.
But then he thought that seriously dole ya
nemi wani abu da zai ke dauke masa hankali
daga wanna pain din da yake ji a zuciyarsa
kafin yayi figuring it out, or maybe kafin pain
din ya tafi. And the thought of going to the
gym came to his mind. Ya taba jin cewa
gyming relieve stress and makes the mind
more focus, kuma shi babban abinda yake
nema a wannan lokacin shine focus din.
Wani friend dinsa ya kira that is into gym, ya
tambaye shi ina ne best gym a garin Abuja
shi kuma ya lissafa masa guraren da ya sani
masu kyau da kuma addresses dinsu. Ranar
Al'ameen bai koma gida ba sai da aka fara
kiran sallar isha, ranar ko sallar magrib din
da suke yi kullum tare da Abba bai je sunyi
din ba. Sai daya gama zagaye gyms din nan
kaf ya kuma samu wanda yayi masa sannan
yayi register da su.
Yana shiga gida abinda ya fara lura dashi a
compound din shine bakuwar motar da bai
sani ba, amma kuma bai damu ba dan har
lokacin baki basu gama tafiya ba, wasu ma
wadanda basu samu zuwa bikin ba a lokacin. wadanda basu samu zuwa bikin ba a lokacin
suke zuwa suyi murna da fatan alkhairi su
tafi. Dan haka kansa daya ya shiga cikin
gidan ba tare da tunanin komai ba. Amma
sai dai yana bude palon Umma suka yi ido
hudu da Mommy, a kusa da ita a zaune a
kasa Safina, fuskarta a rufe da mayafin ta
irin yadda amare suke yi ranar da za'a kai su
gidan miji.
Yaji kamar ya juya da baya ya koma inda ya
fito, amma kuma ba zai iya yin hakan ba dan
kusan duk wadanda suke zaune a falon sun
ganshi. Ya karasa shigowa a hankali yana
lura da kallon da kusan kowa a falon yake yi
masa. Mommy tana yi masa kallon "dan
rainin hankali" Umma tanayi masa kallon "ka
bani mamaki Muhammad" Abba yana yi
masa kallon "zaka hadu da ni ne, I will deal
with you".
18
14
8:42 PM
Ya fara tunanin wanda zai fara gaisarwa a
cikin su, sai dai tun kafin ya yanke shawara
Abba yace "daga ina kake? Ina wayarka?" Ya
fara shafa aljihunsa, shi kansa bai san inda
wayar take ba, maybe a mota maybe kuma
ya yar da ita in one of the places he has
been to, Yanzu shi baya bawa waya
muhimmanci saboda rike ta a hannu yana
hana shi natsuwa, in dai zai dauki waya sai
ya tuna da Safiyya, Babu abinda yake so irin
ya ga ya kira ta ta dauka sun sha hirar su irin
yadda suka saba. Hausawa sunce sabo
turken wawa. turken wawa.
"Uhm... I don't know Abba. Maybe in the
car", "Zauna!" Abba ya fada almost cikin
fushi. Muhammad ya zauna a tsakiya yana
jin shi kamar a gaban jury, sai dai bai san
hukuncin da za'a yanke masa ba. Abba ya
cigaba da magana "ya muka yi da kai kafin a
daura auren nan? Mai kace da ni da bakin
ka?" Yayi shiru, Abba ya sake maimaita wa
"mai kace min sanda na tambaye ka for the
final time akan amincewar ka" Muhammad
ya dago kai yana kallon sa yace "cewa nayi
na amince Abba" Abba yace "okay and then
daga baya sai ka fasa amincewar? A haka
zaka girma kana yin magana biyu? Haka
kaga muna yi?" Muhammad ya girgiza kansa
"Abba ba cewa nayi na fasa ba, dazu ma ai
naje gidan nasu..
." Mommy tace "kaje,
ance ka shigo sai kuma ka sake chanja
shawara ka shiga mota ka fita". Ya sunkuyar
da kansa bai ce komai ba.
Mama tace "Muhammad ka bani mamaki
Allah. Mu dai mun yanke hukuncin mu mun
gama. Yanzu kuma mun danka hukunci a
hannun ka, Sai muga iya kacin hankalin ka.
Sai muga idan kai mutumin kirki ne ko akasin
haka. Ga Safina nan an riga an daura auren
ku da ita. Ya rage naka ka rike amanar ta
kamar yadda iyayenta da mu muka danka
maka, ya kuma rage naka kaci amanar ta ka
hadu da fushin Ubangiji. Tunda dai da
amincewar ka aka yi komai. Sannan dai dai
gwargwado munyi iyakacin kokarin mu na
ganin mun baka ilimi na zaman duniya da. ganin mun baka ilimi na zaman duniya da
lahira".
Ta juya gurin Mommy "kamar yadda na fara
fada miki Hajiya Sa'adatu, dan Allah ki kara
hakuri, na san kinyi, na kuma fahimci
concern dinki. Amma wanna hukuncin da
kika yanke na kawo mana Safina yayi dai dai.
Safina is now our responsibility. Ta zama yar
mu insha Allah. Kamar yadda ba zamu so
mijin Mufida ya wulakanta ta ba haka ba
zamu bari Gidado ya wulakanta Safina ba.
Duk abinda ya faru mu zakiyi holding
accountable" ta sake juyawa kan
Muhammad tace "kai kuma zamu gani in
zakayi upholding mutuncin mu o zaka
zubar da shi ka jashi a kasa".
Muhammad yaji gabaki daya duniya tayi
masa kunci, yaji kamar an zagaye shi da
concrete an matse shi a guri daya. Numfashi
ma da kyar yake barin kirjinsa. Yana ji Abba
da Umma suka cigaba da bawa Mommy
hakuri, suna ta lallashin Safina Mama har da
jan ta jikin ta ta rungume ta tana ta kara bata
tabbacin cewa ta zama yar ta daga ranar.
Shi dai bai saka musu baki ba har suka
gama, Sai da yaji an ambaci sunansa sannan
ya dago kai, yaji Mama tana cewa ya tashi
yaje yaci abinci "daga gain idonka tun
breakfast din safe baka ci komai ba" ya tashi
kamar robot ya je dinning table ya zuba
abinci ya diba ya kai bakinsa, ji yayi abincin
kamar ba'a saka gishiri a ciki ba. kamar ba'a saka gishiri a ciki ba.
"I can cook. I can really cook" yaji muryar
Safiyya a kunnen sa. Ya rufe idonsa a
hankali yace
"get out of my head" ya sake
jin muryarta
"zaka sha girki. Sai na koya
maka cin abinci. Sai na mayar da kai kato".
Ya cika katon cup da ruwa ya shanye sannan
ya sake cika wani ya sake shanyewa. Ya
sake jin shaidan ya kuma yi masa rada a
kunne "in da zaka samu wani abu ka sha,
zata fita daga cikin kan ka". Ya mike daga
kujerar yayi hanyar waje sai yaji Abba ya kira
sunan shi daga palo, ya juyo amma kafin ya
karaso yaji ace "kaje waje ka jira ta ta fito
ku tafi" "ya gyada kai yana kallon Safina
sannan yace "to Abba" sai ya sake juyawa
ya yi waje.
Motarsa ya bude ya zauna ya kwantar da
kansa tare da rufe idonsa. Trying so hard
not to think of anything. Bai san minutes din
da ya dauka a haka ba yaji an tayar da mota.
Ya juya bayansa sai ya ga motar da yake
tunanin a ciki Mommy tazo ce ta fita daga
gidan. Ya mayar da kansa ya kwantar tare da
sake rufe idonsa.
17
6
8:42 PM
Ba'a jima sosai ba yaji an bude kofar motar
da yake ciki an shigo,
Ya kunna ignition din motar ya tayar da ita
tare da saka reverse. Yaji tayi masa magana
"salamu alaikum" va iuva va kalle ta, ta bude. tare da saka reverse. Yaji tayi masa magana
"salamu alaikum" ya juya ya kalle ta, ta bude
fuskar yanzu amma ba gabaki daya ba but
still he saw murmushi akan lips dinta. Sai da
ya fita daga gate din gidan sannan yace
"Ameen wa alaikumus salam". Daga nan ya
cigaba da tukin motarsa.
Tunanin da ya fara zuwa masa kansa shine
gidan su fa zasu tafi ko? Gidan auren su shi
da ita. Unbelievable. Shi tunda aka gama
hidimar siyan gidan bai kuma zuwa cikin sa
ba. Ko kayan sawa ma bashi da su a gidan
ballantana kayan amfani. Duk suna daya
gidan nasa inda ya zauna lokacin bikin.
Sai da yayi circyiling around layinsu twice
kafin ya kama hanyar gidan. Zuciyar sa zafi
take yi masa amma yayi kokarin kwantar da
ita dan samun damar samun amsa daga
bakin da yayi targetting samun amsar from.
Suka cigaba da tafiya in silence sannan yaji
tace "kayi hakuri anyi maka fada saboda ni"
bai ko nuna yasan tana gurin ba. Tayi
kokarin cigaba da magana "ni ban san.....
"Please, ina kokarin driving ne zan kai mu
gida, if you continue talking to me, zamu iya
tafiya lahira instead of gida, and I do not
want to have your blood on my hands".
Daga nan bata sake magana ba har suka je
gidan, Yayi horn mai gadi ya leko sannan ya
koma ya bude musu gate, suna yin packing
mai gadin ya taho da sauri yana gaishe da
Gidado sai kuma ya lura da Safina ita ma ya
gaishe ta. Daga ganin yadda yake kallon ta. gaishe ta. Daga gain yadda yake kallon ta
kasan tunanin wacece wannan yake yi. Shi
dai yasan gidan amarya ne nan har ma anyi
jere amma ba'a kawo amaryar ba, he
expects in za'a kawo amarya za'a zo da
motoci da mutane da yawa ana guda but
wannan amaryar ita daga ita sai angon suka
20 a mota kamar masu zuwa unguwa.
Yayi sauri ya tafi yana kunna fitilun gidan, sai
da ya dawo sannan Muhammad ya tambaye
shi key din cikin gidan dan shi kansa ba shi
da su. Yazo ya bude ya shiga ciki yana
kukkunna fitilun ciki suma.
Muhammad part dinsa direct ya wuce ya
shiga toilet yayi alwala, sai a lokacin ya lura
da irin haduwar da gurin nasa yayi da irin
kudin da iyayensa suka kashe a part din
nasa. Yaji muryar Safiyya "inye! Rich kid!"
Yayi murmushi. Shi kansa ya san shi dan
gata ne, Allah yayi wa iyayen sa arziki
sannan kuma ya sanya musu kaunarsa mai
yawa a zukatan su. Shima kuma Allah ya
sanya masa kaunar su a tashi zuciyar.
Wannan shine concrete din da yaji ya takure
shi a guri daya. Duk wani hukunci yanzu da
zai dauka akan aurensa da Safiya will either
mend or destroy relationships dinsa da su.
Ya fito yayi sallar isha din da bai yi ba
sannan ya sake daukan key din motarsa ya
fice daga gidan, daya gidan nasa ya koma
ya debo kayan sa da already ya riga dama ya
hada su a waje daya tun ranar dinner, kayan
da ya san zai bukata da gaggawa, ya zuba. ya san zai bukata da gaggawa, ya zuba
su a mota ya rurrufe gidan sannan ya sake
komawa can gidan. Mai gadi ya dauki kayan
ya shigar masa da su ciki, sai kuma ya dawo
yace "ranka ya dade Madam ce tazo kenan"
bai ce masa komai ba sai ya kara da "Allah
ya sanya alkhairi" Muhammad yace Ameen
sannan ya shige ciki. Wanka ya shiga, dama
abinda ya dame shi kenan, he took a cold
shower kamar kullum sannan ya shirya cikin
kananan kaya ya fito ya doshi part din
Safina.
Yana kokarin shiga ita kuma ta a kokarin
fitowa da tray a hannun ta, saura kadan
abinda yake ciin tray din nata ya zube sai
tayi sauri ta matsa sannan ta ajiye tray din
tana kallon sa tace "abinci da ma zan kawo
maka. Naji Mama tana cewa bak aci abinci
ba"
Ya zagaye ta ya wuce ya zauna akan kujera
sannan ya nuna mata kujerar can nesa da
shi yace "sit!" Ta cigaba da tsaiwa a gurin
da take kamar bata ji abinda yace ba sai ya
mike a zuciye yana jin duk zuciyar da yake
danne wa tana dawowa wuyansa, tayi sauri
ta ja baya tare da hadewa da jikin bango jikin
ta yana karkarwa idonta yana kawo kwalla,
ya dakata few inches to her ya sake cewa
coldly "I said, sit down!"
10
6
3
8:42 PM
Ta rakabe ta jikin bango ta wuce shi sannan
ta zauna akan kujerar da ya nuna mata, zauna akan kujerar da ya nuna mata,
hawaye yana bin idon ta, ya koma ya zauna
ya dauki kafa daya ya dora akan daya yana
kallon ta yace "ki mayar da wannan
hawayen, ba zasu yi miki amfani ba. Yanxu
ina so ki fara magana, tun dazu na fahimci
dama maganar kike so kiyi. Now you can do
it. Ina so ki fara tun daga farko zuwa karshe.
I want to know everything. About you and
about Safiyya".
Ta juya hannun ta alamar confusion tace
"wacce Safiyyan? Ban gane safiyyan da
kake magana akan ta ba" ya mike zaune
sosai yace "Safina, sauran hakurin da ya
rage min bai fi cikin tsokali daya ba, please
don't make me loose it, please kar ki saka
daga ni har ke muyi nadamar sanin junan
mu, na roke ki" ya koma zaman da yake da,
kafa daya akan daya, ya sake tambaya "who
is Safiyya? Tell me about her"
Tace "wallahi Muhammad....
..... Ban gane
wacce kake magana akan ta ba. Ina da
cousin Safiyya, ina kuma da friends....."
Yace "and you have a step sister called
Safiyya, wacce kuka tashi a gida daya a daki
daya kuka je makaranta daya kuka ci abinci
from plate daya, wacce babanta ya rike ki
tamkar shi ya haife ki, let's start from her.
Tell me about her",
He saw how she was struggling with the
words sannan finally tace "she is my step
sister" sai kuma tayi shiru, yace "I know she. is your step sister, besides, ni na fara tuna
miki cewa she is your step sister. So tell me
something I don't know. Like how she
always discuss her boyfriend Muhammad
with you and how you get my picture from
her phone and send it to bloggers".
Ta bude ido alamar mamaki "your picture?"
Sai kuma ta fara juya kanta "wai kana so
kace min kai ne wanda kuke waya da
Safiyya? Wai kana so ka gaya min Safiyya ce
ex din ka da ka gaya min about?" Ta fara
wani sabon kukan. Yace "cut out that crap
please. Ke karyar ki ma ko sallah ba ta yi" ta
juyo tana kallon sa, thinking that Safiyya
used the same words to insult her three
days ago.
Ta sake gwadawa "wallahi ba karya nake yi
ba" yace "kamar yadda ba karya kike yi ba
sanda kika ce min baki san yayanki
Mustapha ba? Ko kuma sanda kika nuna min
cewa baki san wasu twins ba? Ko kuma
sanda kika ce min ke ba yar Kano ba ce ba?"
Tace "to ai gaskiya na gaya maka. Ni ba yar
kano bace ba. Both iyaye na yan Katsina ne
and
.." "And you think it is not important to
mention to the person that will marry you
that you were raised in Kano a gidan step
father dinki, Idan da kin fada min hakan tun
lokacin da muka yi waya ta farko we
wouldn't be here discussing this, Instead
you chose to lie and throw me a crap about
ba'a Katsina kika yi makaranta ba. And
Mustapha? Wannan karyar kuma fa?" Mustapha? Wannan karyar kuma fa?"
Ta yi saurin dauko wayarta, desperate to
defend herself tace "wallahi wanda kake
magana akan sa ba yayana bane ba, cousin
dina ne, ina da yaya Mustapha amma ba shi
ba ne ka gani ranar nan a airport ba. I can
show you yaya Mustapha a hoto. Ko kuma
kaje gida ka neme shi ku gaisa. Ba karya
nayi maka ba".
Ya mike tsaye yana jin ransa yana kara baci,
in ya cigaba da zama zaiyi abinda baya fatan
ya taba yi a rayuwarsa, dan gab yake daya
wanke fuskarta da mari. "Magana da ke bata
da muhimmanci Safina. You will keep lying
and lying. Ko da bashi bane ba the fact that I
mentioned yayanki Mustapha, ya kamata
ace kin nuna kina da yaya Mustapha, and
then ki nuna kina da kanne yan biyu, in dai
har da ace ke mai gaskiya ce" yayi hanyar
waje sai kuma ya juyo yace"| will get my
answers. Tunda na fahimci ba zan same su
daga gurin ki ta dadi ba then I will get them
somewhere. And I think I know where"
Har ya kai bakin kofa ta kira sunan sa da
karyayyiyar zuciya "Muhammad" ya juyo
yana kallon ta baice komai ba sai tace "she
is married" yaji kamar ta saka kibiya ta soki
zuciyar shi, dai dai gurin da hope din cewa
Safiyya karya take bata da aure yake, Yaji
hope din yana dagargajewa yana bin jinin
jikinsa. Daga yadda tayi maganar ya san
cewa yanzu ba karya take yi ba. cewa yanzu ba karya take yi ba.
07
4
1 2
8:42 PM
Ta mike tsaye suna fuskantar juna, ta
fahimci cewa maganar ta ta taba shi sosai,
ta sake maimaitawa "she is married" ya
hadiye yaw yana jika dried makogwaronsa
yace "married to who" ta cigaba da takowa
zuwa gabansa tace "who Mukhtar. Her
cousin Mukhtar. Wanda yake tamkar yaya ne
a guri na nima".
Ya ji jiri yana neman dibansa. Sai ya jingina
da jikin kofar, trying so hard to hide his
weakness from her. She saw that she got his
attention and she continued talking "ka
yarda da ni, ka yarda da rantsuwar da nayi
maka. Ban san kai saurayin Safiyya bane ba.
Nasan tana tare da wani guy da take
yaudara a school, but she never show me
you. In dai har kasan Safiyya da gaske
kamar yadda kake claiming a santa, then
you should know how secretive she is. She
never let people in" ya sake hadiye abinda
yaki tafiya a makogwaronsa yace "she let
me in" tace "really? In har da gaske she let
you in then ya kamata kaima ace ka san ni.
As her sister that she spent her entire life
with, ya kamata ace ka san ni. In har kai
baka sanni ba, me yasa zaka ki yarda cewa
ni ban sanka ba?"
Ya matsa daga jikin kofar sannan ya bude ta
ya fita. "Mukhtar" ya fada a hankali.
"Mukhtar" ya maimaita. Safiyya
••
LTE
owner
Episode Twenty Five: The Interview 2
Paid Advert
*Contact Bojuwa HERBAL'S for all your*
*kayan mata for*
*Amarya*
*Uwargida*
*Bazawara*
*Mai jego*
*Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar
kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi
all from Chad.*
*Kayan gyara masu kyau da inganci kala
daban daban, special maganin sanyi for
women of class*,
*Contact Surayya HALIN YAU on*
*08032773332*.
Not Edited
Dakin sa ya wuce direct yana zuwa ya kashe. Dakin sa ya wuce direct yana zuwa ya kashe
fitila ya kwanta ya yi addu'a ya rufe idonsa.
Baya son yayi tunani. Baya son ya saurari
maganaganun da zuciyar sa take gaya
masa. Ya kai wajen mintuna talatin a haka
sai kuma ya mike ya zauna. Kwakwalwar taki
hutawa, babu abinda take yi sai bitar
maganganun da suka yi da Safina da zu a
falon ta.
A maganganun da suka yi dazun ya kara
tabbatar da abinda ya riga ya fahimta tun
kwanaki uku da suka wuce akan Safina,
makaryaciya ce, yanzu kuma ya kara
fahimtar wani abu daban, munafuka ce, sai
dai kuma a cikin jerin karairayin da tayi masa
yau tayi mentioning something da ya fahimci
cewa gaskiya ne, that Safiyya is married.
The fact that Safiyya is married shattered all
the remnants of hope da tunanin cewa she
is not ya fara saka masa a zuciyarsa. But
saying that she is married to Mukhtar raised
another question a zuciyarsa. Ya san
Mukhtar, ya hadu da shi a lokuta da dama
amma basu taba exchanging words ba ko da
kuwa sallama ce. But Mukhtar cannot be
married to Safiyya musamman a lokutan da
suke haduwar, no real man will allow his wife
to openly have a relationship with another
man a gabansa ba tare da ya dauki wani
mataki ba, and Safiyya couldn't be married
to Mukhtar and be staying in hostel while
yana zaune a garin, yana zaune a garin.
But Safina seemed censire when she
mentioned Mukhtar's name. Kamar ba karya
take ba but it doesn't seemed right. It just
cannot be. Sun sha yin maganar Mukhtar da
Safiyya. Ya taba ma kokarin nuna mata cewa
Mukhtar yana son ta but she denied it. Sai
dai kuma ya fahimci ta san hakan ita ma da
kanta. And she later told him that Mukhtar
yana daya daga cikin dalilan da yasa ba zata
kai su gurin Uncle Ahmad ba. Sai dai ta
kaishe direct gurin Daddy.
Ya lissafa options dinsa, abubuwan da yake
da tabbas akan su kamar the fact that
Safina and Safiyya are step sisters and that
Safiyya is married, sai kuma wadanda bashi
da tabbas a kansu, kamar cewa Mukhtar
shine mijin Safiyya. And then abubuwan da
yake so ya sani kamar what happened to
cikin jikin Safiyya, shin na gaske ne ma ko
akasin hakan. And then the most important
question "what happened to Safiyya?"
Ya koma ya kwanta still yana hango fuskar
Safiyya a gurin dinner din su. She lost all her
glow, her aura, and her radiant smile. He
could tell from her eyes that she is deeply
hurt,
"Careful, ni matar aure ce"
Ya tuna kalmominta da yadda suka soki
zuciyar sa, zuciyar sa.
Ya tuna ganin da ya sake yi mata yau a cikin
motar Mukhtar, bai kalle ta sosai ba but she
still looked deeply sad kamar wadda kowa
na duniya ya juya mata baya. And sai yaji
babu abinda yake so illa ya sake ganin ta, all
he wanted a lokacin was to look deeply into
her eyes and read the truth from there. Ko
da basu yi magana ba, maybe in ya kalli
idanunta, maybe, just maybe, zai iya dauke
some of the burden from her heart ko da
kuwa hakan zai yi crumbling tasa zuciyar.
Ya tuna maganar da Safina ta gaya masa
dazu "guy din da take yaudara" and he
smiled. Yes, he had his moments of doubt
akan soyayyar da Safiyya take yi masa
especially ranar da ta yi replying all the
messages da ya ringa tura mata yana
rokonta ta bashi dama suyi magana,
messages din da har yanzu ya san su suke
haunting Mama, amma Safiyya tayi replying
with "ni matar aure ce kuma ina matukar son
mijina bana son abinda zai bata masa rai.
Amma yanzu, after she appeared a gurin
dinner dinsa looking like yar gudun hijira, ya
san cewa ko ma me take ciki a rayuwar ta a
yanzu tabbas tana son sa,
22
5
9:19 PM
Kafin yayi bacci ya yanke shawarar next step
dinsa, ya yanke shawarar gurin da zai samu
next answer dinsa, He woke up exhausted,
mentally exhausted, but also determined, mentally exhausted, but also determined.
Bai fiti daga bedroom din sa ba sai da yayi
wanka ya shirya tsaf yana tunawa kansa
cewa rabon sa da abinci tun breakfast din
jiya. Baya son ya kalli fuskar Safina da
sanyin safiyar nan ballantana ta bata masa
mood dinsa ta kuma yi tempering da tunanin
sa, dan haka addu'ar sa sanda zai bude
kofar bedroom din ita ce kar Allah ya hada
fuskokin su har sai ya bar gidan.
Sai dai kuma fuskar tata ita ce abinda ya
fara gani yana bude kofar dakin. Tana tsaye
a gaban dining table dinsa tana ta aikin
arranging and rearranging dishes. Ta ci
kwalliya cikin doguwar rigar da ta kama
jikinta sosai ta bayyana shape da cikar
cikakken kirjinta, ta kuma tsaya iyakacin
gwiwarta, gashin kanta ya sha gyara daga
gani yaci kudi. Ta dan tsorata da ganin sa,
maybe bata yi tunanin fitowar sa a lokacin
ba. Ya hade rai ya zuba mata ido da kallon
tuhuma, Falon nasa sai kamshin turaren
wuta, turaren jikinta da kuma abinci yake yi.
Ta danyi murmushi tana jujjuya hannunta,
yadda ya sha kunun ya hade rai ba karamin
kyau yayi mata ba, His face looking as fresh
and handsome as always,
"Good morning
Habibj" ta fada tana langwabe kai gefe. "Wa
yace ki shigo min daki?" Ya fada da
busashshiyar murya, "ta fara takowa zuwa
inda yake da yanayin tafiyar da yake motsa
duk wata halitta ta jikinta, "ba wanda yace in
shigo, na ga dakin mijina ne shi yasa na
shigo, bana bukatar iznin wani kafin in shiga. shigo, na ga dakin mijina ne shi yasa na
shigo, bana bukatar iznin wani kafin in shiga
dakin mijina" Wulakantaccen kallon da yake
bin jikin nata da take nuna masa dashi, tun
daga gashin kanta har zuwa kafafuwanta,
irin kallon da yan gayu su kan yiwa abincin
da suke ganin ko zasu mutu ba zasu iya ci
ba, like "God forbid bad thing
Ta dakata tare da sauke idonta kasa, feeling
necked and degraded, ji take yi kamar ta
rushe da kuka, kalma daya bai gaya mata ba
amma kallon da yayi mata sai da taji dama
duka ya saka ta a gaba yayi mata. Ya dauke
idonsa daga kanta ya karasa inda ya ajiye
key din motarsa ya dauka ya cigaba da
tafiya zuwa hanyar waje, ta juyo tana kallon
bayansa tace "Fita zaka yi? I thought an
baka hutu a gurin aiki. You should be resting
by now" bai ce mata komai ba ta cigaba
"Abinci fa? You haven't eaten tun jiya.
Please ka tsaya ka ci abinci kar ka fita da
yunwa. Nayi maka abinci fa dan Allah ka
tsaya ka ci abinci, tun kafin sallar asuba na
tashi dan inyi maka shi, dan Allah ka tsaya",
Sai da ya kai bakin kofa ya kama handle din
sannan ta kira sunansa "Muhammad
Gidado" ya dakata sannan ya juyo "don't!
Please continue with your Habibi din da kika
fara tunda bansan sunan waye ba but
Muhammad Gidado is my name, and you are
not worthy of pronouncing it",
Daga gida wani eatery da ya gani a hanya ya
shiga yaci abinci, sannan ya karasa sabon. shiga yaci abinci, sannan ya karasa sabon
gurin akin sa, one of the branches of oil
company of his father, in da a yanzu shine
yake jan ragamar gurin while Abba yana
cigaba da rikon head office din su, akwai
kuma sauran branches da yake dasu in
almost all the states of the country. Sai dai
tun ranar da suka zo da Abba aka gama cike
ciken takardu aka kuma gama introducing
dinsa a gurin ma'aikatan gurin sai kuma aka
bashi hutun aure, one month Abba ya rubuta
masa da hannunsa, but a yanzu Gidado yayi
deciding fasa yin hutun da kuma durfafar
aikin da gaske.
Wannan yana daga cikin matakan daya
dauka na ganin ya rage wa kansa tunane
tunane ya kuma kare kansa daga hudubar
da shaidan yake yi masa. A office din ya
wuni har 5pm sannan ya tashi, shima kuma
dan dai shine lokacin tashi a office din
amma ba dan haka ba zai iya cigaba da
zama a can. A wuni dayan da yayi kadai a
office din shi kansa ya san already da yawa
daga cikin ma'aikatan gurin sun tsane shi
saboda yadda ya azabtar da su, bai huta ba
kuma bai bar kowa ya huta ba.
13
3
3
2
9:19 PM
Da yamma yana fitowa gidan su Safiyya ya
dosa, ya gama shirya abinda zai yi a can din.
A bakin gate ya tsaya yayi horn sannan ya
jira, mai gadi ya leko ta yar karamar tagar shi
ya ganshi sai Gidado yayi masa alamar yazo,
ya bude karamar kofa ya fito tare da gaishe
da Gi
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Da yamma yana fitowa gidan su Safiyya ya
dosa, ya gama shirya abinda zai yi a can din.
A bakin gate ya tsaya yayi horn sannan ya
jira, mai gadi ya leko ta yar karamar tagar shi
ya ganshi sai Gidado yayi masa alamar yazo,
ya bude karamar kofa ya fito tare da gaishe
da Gidado "yallabai sannu da zuwa" Gidado. da Gidado "yallabai sannu da zuwa" Gidado
yay masa murmushi, something that tun
safe bai yi ba. "Ya aikin?" Ya tambaya "lafiya
lau yallabai. Ka shigo da motar ciki mana, su
Hajiyan duk suna nan aj" Gidado yace "no,
ba shiga zanyi ba" mai gadi ya bude baki
"yallabai Hajiya fa ranar nan tayi fada da ka
tafi" Gidado yace "yau ai ba zata san nazo
ba ko?" Maigadi ya gyada kai yana
murmushi yace "ba zata sani ba yallabai, me
ake bukata?" Gidado yace "dama twins nake
nema, na bar daya waya ta a gida bani kuma
da number din su a wannan wayar. Suna
ciki?" Mai gadi ya girgiza kai "sun fita
yallabai, tun safe basa nan. Kasan kananan
samari, ballantana anyi sababbin mota,
kullum suna yawo ba sa zama a gida" ya
karasa maganar yana murmushi, Gidado
yayi murmushin shima "na gane. Just in sun
dawo ka gaya musu nazo ina neman su" mai
gadi ya dauko wayarsa daga aljihunsa yace
"to in baka number din daya daga cikin su
mana, sai kawai ka kira su, watakila neman
gaggawa kake musu" Gidado ya dauko
wayarsa yace "Okay, hakan ma yay"
maigadin ya nemo number din "bara in baka
ta Hassan, anfi samun sa a waya, Hussein
shi yanzu haka ma yabar tasa wayar a gida",
Ya karanto masa numbers din Gidado ya
rubuta sannan yayi masa godiya, ya saka
hannu a aljihu ya dauko kudi ya mika masa
hannu suka yi musabaha ya bar masa kudin
a cikin hannun nasa, ya lura da yadda fuskar
mai gadin ya yi haske da murmushi, shi ma
ya mayar masa da murmushin sannan ya ja. ya mayar masa da murmushin sannan ya ja
motarsa ya tafi.
Gidan su ya zarce, babban damuwarsa a
cikin duk wannan abin shine ya ga ya gyara
tsakanin sa da iyayensa. Sai da ya jima a
mota yana shakar numfashi da niyyar
daidaita fuskarsa, baya son ya cigaba da
bayyana damuwa ga iyayen sa, baya son ya
cigaba da saka su damuwa. Ya shiga gidan
da sallama, lokaci daya yaji yana missing
Mufida da ya duba inda take yawan zama ya
ga bata nan. Mama tana zaune da dan
karamin Alqur'ani a hannun ta, suna haka
ido yayi mata murmushi, sai da ta aki aya
sannan yace "sannu da hutawa Mama" ta
bishi da kallo kawai sai ya mike ya doshi
hanyar dinning "akwai abinci? I am starving"
tace "daga ina kake?" Ya na cigaba da tafiya
yace "office, yau a can na wuni, I bet Abba
will be impressed" tace "office kuma? Na
dauka hutu kake yi, kuma ba gidan ka ya
kamata ka tafi ya huta kaci abinci ba? Ni
banyi girki da kai ba" ya juyo ya zagayo ta
bayan kujerar ta ya sunkuyo yayi mata kiss a
goshi, "I just miss you ne shi yasa na zarto
nan. Kuma ina son inci abincin ki, at least dai
once a day ai ba za'a hana ni ba" ya ga
murmushi ya bayyana a fuskarta, shine
dama abinda yake aiming for, ya sanya farin
ciki a zuciyar mahaifiyar ta sa.
Sai gata ta taso da kanta ta zo ta zuba mishi
abincin "me yasa ka koma aiki?" Ta
tambaya, "so nake Abba yaji dadi, ya jima
yana son in karbi aikin nan, and naga babu. yana son in karbi akin nan, and naga babu
wata gajiya a tare da ni tunda an kwana biyu
da gama bikin". Ta zauna tana kallon sa yana
cin abinci "ka ringa samu kana cin abinci
sosai Muhammad, duk kayi baki ka rame" ya
ajiye cokalin hannunsa yana kallon fatar
hannun nasa kamar mai tabbatar da bakin
da tace yayi, sai kuma ya jingina hannun a
jikin fuskarta yace "still na fiki fari Mama" ta
girgiza kai "ina! Ban yarda ba, ai fuska dama
bata kai jiki fari ba" ta jingina hannun ta a
jkin nasa "see? Na fika fari" yayi dariya.
Su kan yi wanna musun lokaci zuwa lokaci
shi da ita, ya fita fari amma bata yarda, in ya
matsa sai ta ce shekaru ne suka saka tayi
duhu.
Sosai yaga ta sakar masa fuska tana yin
murmushi, ya kuma ji dadin hakan. Suna nan
tare Abba ya shigo tare da Haidar, ya taso
yazo ya gaishe shi ya fara kokarin bashi
labarin zuwan da yayi office yau amma sai
yaji har labari ya iske Abban. Anan suka yi
sallar magrib are sannan suka sake komawa
cikin gida, ya fahimci suma iyayen nasa
sunyi missing zama suyi hira da shi.
11
9:19 PM.
sunyi hirar aiki sosai da Abba sannan sunyi
hirar Mufida da Mama, Sai da akayi sallar
isha Mama ta fara korar shi gida "ka bar
yarinya ita kadai tun safe, Ka tashi ka tafi,
Akwai abinda kuke bukata ne a gidan?" Ya
girgiza kai, "no I don't think so, but zan
tambaye ta inji" ya ga alamar Mama taj
da din hakan, amma duk da haka sai ta kara. dadin hakan, amma duk da haka sai ta kara
da "kar ka manta dai Muhammad, yarinyar
nan amana ce a gurin ka, idan ka zalunceta
sai Allah ya saka mata".
Daya bar gidan ma ba gidan nasa ya tafi ba,
gym din da yayi register da su jiya can ya
tafi, baya son ya koma gida sai ya zama too
exhausted to even think, baya son ya bawa
kwakwalwar sa damar yin tunani,
musamman tunanin Safiyya da Mukhtar a
matsayin mata da miji.
Bai koma gida ba sai da aka rufe gym din by
11. Yana zuwa gida ya wuce bedroom dinsa
direct ya shiga wanka, a cold shower as
always, ya fito da bathrobe a jikinsa da towel
a kansa ya ganta. Tana zaune akan kujera a
gaban mirror hannun ta rije da wayar ta tana
jujjuya wa, idanuwan ta a kansa. Jikinta
sanye da riga da wando silk na bacci, kana
gani kasan babu komai a cikin kayan. Ya
tsaya kawai yana kallon ta yana jin murnar all
accomplishments din sa na yau tana tafiya
tana barin zuciyarsa.
Ta mike tsaye,
"sannu da dawowa. Ina ta
kiran wayarka tun safe ba ka dauka ba" yaji
ransa ya kara baci ya zo da sauri ya wuce ta
ya bude kofa "get out of my room! Wai ke
wacce irin dakikiya ce? Wai in tambaye ki
ma, anya sanda akayi rabon aji irin na mata
kinje kin karba kuwa? Ko kuma dai masu
rabon ba su baki bane ba saboda sun san
you did not deserve it?" Ta juyo tana kallon
sa, fuskarta kamar zata yi kuka tace "ka sa, tuskarta kamar zata yi kuka tace
"Ka
gaya min duk maganar da ka ga dama. Ko
me kayi min nina jawo wa kaina. Amma aikin
gama ya gama, ni da kai yanzu mata da miji
ne until you say otherwise, and I bet ba zaka
iya saying otherwise din ba because your
parents will disown you......
..." Yace "disown
me? Akan ki? Me kike daukan kanki ne wai?
Okay let me tell you something, you are here
because I want you here, you are here as
nothing but a ladder da zan taka in kai ga
inda nake son kai wa. And don't think
shamelessly exposing that thing you call a
body to me will get to me. Now get out, and
this will be the last time da zaki shigo min
daki".
Bata fita din ba still, ta cigaba da tsaiwa a
inda take "you promised..... You promised
me ba zaka wulakanta ni ba and you
promised you will perform all your duties as
husband, akan wannan promise din muka yi
aure" yace "I made that promise to
someone that I thought I can accept as a
wife, someone that you pretend to be, kuma
I intended to keep that promise, Amma daga
ranar da na fahimci cewa ke ce, daga ranar
kika yi loosing wannan alkawarin. Now
please, don't open that mouth of yours
again, out of my room I said" tana sake bude
bakin nata kuwa ya koma da baya ya damko
hannunta and dragged her zuwa bakin kofa
sannan ya hankada ta waje yadda ya san ba
zata ji ciwo ba ya mayar da kofar sa ya rufe. Ya jima a tsaye a tsakiyar dakin idanunsa a
rufe, wannan yarinyar bata da class sam, shi
bai taba gain tsiraici physically irin wannan
ba. Na kammala shirin kwanciya baccin sa
ya kashe fitila ya kwanta, sai a lokacin ya
dauko wayarsa yay going through tarin
missed calls da tarin messages din da akayi
masa through out the day. Sai a lokacin yaga
missed calls din Safina, sannan da message
da ta tura masa da rana.
"Ban san inda ka tafi ba, amma ina kewar ka.
Allah ya kare min kai ya dawo min da kai
gida lafiya. I love you".
Yayi tsaki zai ajiye wayar kenan ya ga wani
message din nata ya shigo, kamar a lokacin
ta turo shi.
"Wallahi Muhammad ni ba yar iska ba ce ba,
kuma ni ba mace marar aji bace ba. Idan da
ace ka san ni kafin wannan lokacin ba zaka
taba tunanin wani namiji zai yi min irin
wulakancin da kake yi min ba. Kaddara ce ta
fada min, kaddarar son ka da Allah ya
jarabce ni da shi, Da ace zan iya cire wa
kaina da bamu zo wannan gurin ba, Amma
na yafe maka, Saboda ina sonka kuma ina yi
maka fatan rahamar Ubangiji",
Ya kashe wayar ya ajiye sannan yayi addu'a
ya rufe idonsa. Washegari just like jiya, sai da ya gama
shiryawa tsaf sannan ya fito daga akin sa.
Yana fitowa wanna karon ma ita ya fara
gani a zaune a kan kujera a falon sa. Ya
tsaya kawai yana kallon ta yana tunanin anya
kuwa akwai zuciya a kirjin yarinyar nan?
Already har ta gama shirya masa breakfast
akan dinning ta kuma shirya jikinta cikin
doguwar rigar atampar da aka yiwa dinki mai
kyau kuma dai dai jikinta, ta yi dauri da
dankwalin atampar, kijinta da abincin ta
suna kamshi.
"Ina kwana Habibi" ta fada, idanuwanta a
kumbure, daga dukkan alama ta kwana tana
kuka, bai amsa mata ba ya dauki key din
motarsa yayi hanyar waje. Ta bishi a baya da
sauri ta sha gabansa. "Whether kayi
alkawari, ko ka fasa yin alkawari, ka riga ka
karbi aurena. Kuma dukkan nauye nauye na
yana kanka" ya zagaye ta ya wuce, har ya
fita ya rufe kofa kuma sai ya dawo ya watsa
mata kudi a jikinta yace "cook dinner, I am
bringing guests".
Da rana yana office ya kira number din
Hassan da ya karba jiya. Hassan ya dauka
sai Gidado yace "sunana Muhammad
Gidado" Hassan yace "yaya good afternoon,
ina yaya Safina?" Yace "tana lafiya lau, tana
ta missing din ku, ina Hussein?" Yace "gashi
nan. Yana lafiya lau. Ni ai bani da number din
ka" Gidado yace "I know, shi yasa ni na nemi
taka na kira ka, kuna kanne na amma ace
bamu wani san juna sosai ba. I want to invite. bamu wani san juna sosai ba. I want to invite
you two to dinner today, in babu abinda
kuke y" Hassan da sauri yace "babu abinda
muke yi. Zamu zo insha Allah" Gidado yace
"good. Allah ya kaimu. Ina jiran ku",
Ya ajiye wayar yana murmushi. He can't wait
to see what information he can get out of
these two guys.
Ranar da wuri ya tashi ya je gida gurin mama
yaci lunch, ranar ma sai da tayi masa gorin
gidan sa ya kamata yaje ya ci amma sai ya
gaya mata cewa zai ci dinner a can din ai,
kawai baya son yayi missing girkin ta ne.
Daga nan gym ya wuce and spent da rest of
the day there. Sai da yayi sallar magrib
sannan ya tafi gida, ya shiga yayi wanka ya
chanja kaya ya fito a dai dai lokacin da
motar Hassan take shigowa gidan. He
watched them from his window a lokacin da
suka jera suna tahowa cikin gidan suna hira,
he remembered seeing them ranar daurin
auren sa a Katsina, but they are not the
boys he saw ranar da ya fara zuwa katsinan,
but that doesn't change the fact that Safina
lied.
Gabansa ne ya fadi, kar dai yarinyar nan
baya yi abincin nan ba? Cos he thought zata
kawo part din sane, baya son shiga part
dinta amma kuma baya so ya bata lokaci da
su, zata iya shirya musu abinda zasu fada
masa. Ya bude kofar part din nata ya shiga
da sallama, suna zaune akan kujeru su biyun
suka juyo a tare suna kallon sa, Hassan yace. suka juyo a tare suna kallon sa, Hassan yace
"wow" Hussein ya dan dake shi yace
'"masha Allah ake cewa" Gidado yayi
murmushi yace "Amen wa alaikumus salam
ake cewa" duk suka yi dariya a tare sannan
suka amsa masa sallamar sa.
Ya zauna a kusa da su yana kallon dining
table dinta, babu alamar abinci a gurin, yace
"ina take ne" suka daga kafada duk su
biyun. "Muna ta sallama shiru" ya dauko
wayarsa ya nemo number dinta and for the
first time tunda aka daura musu aure ya kira
ta, tana ta ringing bata dauka ba. Ya ajiye
suka cigaba da hira da su Hussein, hirar
mota da hirar school, nothing personal, yana
son sai tana zaune zai musu personal
questions dan ya ga response din ta.
Ganin bata da niyyar fitowa kuma ya san
shine ya kamata ya shiga ya kira ta ya saka
dole ya mike, sai dai bai san ina ne dakin ta
ba, and he really doesn't want to enter her
room, Dakin farko ya fara zuwa yayi
knocking sau biyu sannan ya tura kofar
kadan yace "muna jiran ki fa. Ko wankan
chanja fata kike yi ne?" Hussein yayi dariya.
Gidado ya tura kofar sosai amma babu
alamar mutum a cikin dakin. Ya rufe kofar ya
koma daya dakin da yake can karshe, ya yi
knocking shima sannan ya tura kofar da
sallama, Tana tsaye a gaban mudubi da dan
karamin towel a jikinta wanda bai wuce na
goge fuska ba, Rabin kirjinta da rabin
mazaunan ta duk a bayyane suke, da
kwalbar turare a hannun ta tana fesawa, ta. kwalbar turare a hannun ta tana fesawa, ta
juyo tayi masa wani kasalallen murmushi
tace
"minti biyu. Ina zuwa",
10
3
1
P
9:19 PM
Yayi sauri ya ja da baya, sannan ya jawo
kofar da sauri yana jin zuciyarsa tana
bugawa da sauri. Wannan wacce irin masifa
ce ya debo ya kawo gidan sa?
Bai jima da zama ba ta fito, har da dogon
hijab a jikin ta, sai kuma ta tsaya tana kallon
twins da mamaki, suka hada baki "surprise!"
Tayi dariya tana kallon Gidado "wai kune
bakin dama? Kuma nufin ku nayi slaving
kaina in the kitchen for?" Suka yi dariya
suma, Hussein yace "Allah ne ya kamaki,
dama ba kya yi mana girki, yau kuma zamu
ci albarkacin yaya"
Ta zauna suka gaisa sosai sannan ta
tambayi inda zata kai musu abinci, Gidado
ya daga kafada "ko ina ma" ta tashi tare da
jan hannun twins "nayi muku girki ba zan
kawo muku ba, ku zo muje kitchen ku dauko
da kan ku" Gidado yayi sauri ya dawo dasu
baya tare da girgiza kai "not gonna happen.
They are my guest and will be treated as
such" suka dawo suka zauna, Hassan har da
daukan kafa daya ya dora akan daya yana
mata dariyar mugunta,
Amma ita ssi yanayin fuskarta duk ya
chanja, zuwa lokacin ta tabbatar da cewa
Gidado is up to something. Tana so ta kebe. Gidado is up to something. Tana so ta kebe
da twins ta gaya musu suyi minding tongue
din su amma babu dama. Haka ta debo
warmers din abinci ta jera a kan dining
sannan tayi musu magana suka taso, kuma
tayi serving din su.
Suka fara cin abincin in silence, Gidado yayi
noticing how tasteless the food is, sai
kamshi da ya cika gidan. Ya ajiye cokalin sa
yana kallon Hassan, ya ga alamar yafi
Hussein magana yace "to ya gida? Tell me
about every one at home. Tunda ni ma na
zama dan gida yanzu" Hassan ya gyara
zama yace
"a gidan mu dai the first rule is to
never cross Mommy. In ta fara yi maka fada
har sai kayi bacci ka tashi bata gama ba"
Hussein yace "but she barks more than she
bites. Fadan ne kawai da ita baya iya yi mana
komai. Musamman ma mu yan autan ta"
suka kalli juna suka yi dariya, Hassan yace
"she is so loving, tana son mu sosai, she
can put her life on the line for us" Hussein
yace "amma Daddy! Kar ka sake ka bata wa
Daddy rai, Zai babballaka ne kamar rake"
Hassan yace "ka tuna wata damka da ya
taba yi min? Sai da allon kafada ta ya goce"
suka sake dariya, Muhammad kuma yayi
murmushi. They are just like Safiyya have
described to him.
Muhammad ya rungume hannun sa a kirjinsa
yace "and Safiyya? Should I cross her or
not?" Safina ta ajiye spoon din hannunta ta
zuba masa ido. Hassan yayi murmushi, from
his smile ma zaka gane irin son da yake yiwa. his smile ma zaka gane irin son da yake yiwa
Fiyya, yace "Fiyya is the nicest of us all. She
is stubborn though" Muhammad yayi
murmushi. Sai kuma yace "wow! You just
said nicest. Meaning kunfi sonta akan
Safina? Zaku fitar min daga gida na yanzu"
Hussein yana kallon Safina yace "ita ma ai ta
sani. Muna sonta ita ma amma munfi son
Fiyya saboda ta fi son mu" Muhammad yace
"koma dai menene, since they are both
married now, mazajensu are now included in
the competition, ni kuma zan kwato u daga
hannun mijin Safiyya. Waye shi ne wai? I
should know him also" Hassan ya dan bata
rai "yaya Mukhtar ne. He is our cousin. I do
not like him. So na baka winner a
competition din tun kafin a fara" Hussein
yace "wannan mutumin bana jin ma zai bar
mu muje gidan su in akayi bikin. He doesn't
like us. Da shi da babansa".
Muhammad ya juya ya kalli Safina da itama
shi take kallo, ya sake kallon yan samarin da
suke gabansa yace "in akayi bikin? You
mean ba'a yi bikin su ba?" Hassan yace
"ba'a yi ba ai, ka dauka anyi? Kwana daya ne
tsakanin daurin auren ku da nasu, any naku
Friday akayi nasu Saturday, Bata da lafiya
shi yasa ba'a yi bikin ba sai ta warke"
Muhammad yaji gumi yana tsatstsafowa
daga cikin gashin kansa, Ya sake maimaita
wa "you mean, last weekend akayi daurin
auren Safiyya?" "Yes" suka amsa a tare.
Ya mike tsaye ya zagaye table din amma ya. Ya mike tsaye ya zagaye table din amma ya
rasa abinda yake nema, sai kuma ya bude
fridge ya tsara a gabansa yana jin sanyin
fridge din yana dukan sa, he wants to hold it
together, he doesn't want to loose it, he
wants to know more ....
9
> 1
9:19 PM
Ya dawo ya zauna ya zuba ruwa a cup ya
shanye, sannan yace "lallai Safiyya is truly
an amazing woman, aure biyu kenan tayi in
her young age" suka kalle shi with confusion
a fuskokin su, "aure biyu kuma? Wannan
shine auren ta na farko, Bata taba yin aure
ba, Wa yace maka tayi aure?"
Yaji wani abu yana kokarin tokare numfashin
sa, but he couldn't stop asking, Yace "ita ta
gaya min, I met her ranar nan, About four
months ago, She was pregnant, We talked,
And she said she is married",
Ya fada yana kallon fuskokin su and
immediately he mentioned pregnant he saw
yadda gabakidaya yanayin su ya chanja,
Suka kalli juna sannan suka kalle shi, they
looked terrified kamar wadanda suka aíkata
babban zunubi, Sannan suka hada baki suka
ce "ba ita bace" "maybe wata ka gani" ya
girgiza kansa, trying to press them more "ita
ce, I am very sure of that",
Hassan ya kalli Safina kamar mai neman
taimakon ta, jin bata ce komai ba saí ya xe
cikin rawar murya da inda inda "maybe
she…she…... was pretending" ya taba. she....
...She..... was pretending" ya taba
Hussein "kasan yaya tana pretending to be
pregnant was lokuta".
Hussein ya mike tsaye "ya kamata mu tafi
kar Daddy yace muni dare. Yaya
Muhammad thank you for the invite. Yaya
Safina thank you for the food " Hassan ya
mike shima "yes, we should go. Thank you.
Sai da safen ku".
Daga Gidado har Safina babu wanda yace
musu komai har suka fita daga falon. Bayan
sun fita din ma sun jima a haka a zaune
sannan lokaci daya Gidado ya mike ya dauki
jug din glass din da yake gabansa ya rotsa
da kasa. Ya dauki plate din da aka zuba
masa abinci a ciki shima ya buga shi da jikin
bango ya tarwatse.
Ya tsallake mess din da yayi creating yayi
hanyar waje a kokarin sa na hana kansa
tarwatsa Safina ita ma da take zaune a
gurin. Sai da ya kai bakin kofa sannan ta kira
sunansa, ya juyo yana kallon ta da idon da
take ganin kamar ba nashi bane ba tace
"that answer you are looking for, you will
find it in dai zaka cigaba da nema. But
sometimes ignorance is merciful".
Bai amsa ta ba ya bude kofa ya fita. Yes he
will keep looking for the answer even if it will
kill him. And he knows exactly where to look
for it next. It is time to meet Daddy. Yes, a
matsayin sa na surikin Daddy, ya kamata ya
je ya gaishe shi. find it in dai zaka cigaba da nema. But
sometimes ignorance is merciful".
Bai amsa ta ba ya bude kofa ya fita. Yes he
will keep looking for the answer even if it will
kill him. And he knows exactly where to look
for it next. It is time to meet Daddy. Yes, a
matsayin sa na surikin Daddy, ya kamata ya
je ya gaishe shi. Nafisa Tafida Usman
Safiyya
owner
Episode Twenty Six: Face to Face
M
Paid Advert
Contact Lame(07036662633)for all your
costumes both oriflameand other special
products that will make ur skin glow and
flawless
Kayanmu lamba daya ne wajen kyau da
farashi daidai da aljuhun kowa.
Muna Kano, muna aikawa kowanne gari.
Muna tayaku zaben mayukan da zasu dace
da fatarku.
Sensitive skin
Oily skin
Dry skin,
Haka nan duk yadda spots da pimples suka
bata muku skin da zarar kun yi amfani da
kayanmu zaku hue wanna takaicin da ikon
Allah,
Kayanmu tested & trusted,
Skin care for exclusive women,
Contact Aysha lame on My heart and thoughts are with my fans
from Maiduguri, Allah ya shiga lamarin ku
ya fitar da ku daga halin da kuke ciki. Allah
ya mayar muku da ninkin abinda kuka
rasa. Allah ya saukaka muku wannan
rayuwa tare da mu baki daya.
You are in my prayers always A
Not Edited
Motar shi ya shiga ya tayar ya fita daga
gidan ba tare da ya san inda za shi ba.
Babban abinda ya fahimta a maganganun da
suka yi da twins shine karyar da Safiyya tayi
mishi. Ranar da taje office dinsa ranar da
tayi breaking up with him she lied to him
cewa tana da aure a lokacin. She said "I am
married. I have been married all along".
Idan da ace haka kawai tazo ta gaya masa
wannan maganar da ba zai taba yarda ba,
da direct zai ce mata karya take yi, amma
cikin da ya gani a jikinta a lokacin and the
fact that sun kasance tare tsahon shekaru
biyu da watanni amma bata taba kai shi
gidan su ba duk kuwa da nacin da yake yi
mata shine abinda yay convincing dinsa to
some extent cewa da gaske take yi ita matar
auren ce, But now, out of nowhere, he
learned that karya tayi masa, But why?
Sannan cikin da ya gani a jikinta kuma fa?
Ya tuna da yadda yanayin fuskokin twins ya Ya tuna da yadda yanayin fuskokin twins ya
chania the moment da yayi mentioning ciki,
and then they lied that ai pretending take yi.
Karyar ta su ma ko ma'ana bata yi ba. Why
will she pretend to be pregnant just to break
up with him? Zuciyar sa ta gaya masa amsar
amma sai yayi sauri ya girgiza kansa, he
refused to believe cewa bata sonsa, he
refused to believe cewa yaudarar sa tayi, he
refused to believe that Mukhtar take so a
duk wannan tsahon lokacin.
And even if, in the slightest chance that bata
son nasa, me yasa tazo gurin dina din su
looking and sounding so hurt. Ya tuna
kalaman da ta gaya masa cikin dacin rai
"you married my sister" she wouldn't be
that hurt idan da bata son sa.
Ya kuma tuna da kalaman Safina na karshe
kafin ya bar gidan "sometimes ignorance is
merciful" ya sake girgiza kansa, he doesn't
want that mercy, he want to know, not
knowing why is what is hurting him the most
a cikin duk wannan drama din.
Sai da ya lura kusan shi kadai ya rage a titi
sannan ya juya zuwa gida, ya san cewa ba
lallai ya samu baccin da yake bukata ba dan
haka yana zuwa alwala yay ya tayar da
sallah, asking God to put an end to his
suffering and grant his heart peace, And
then he found himself praying for Safiyya,
for God to be with her and guide her akan
dukkan lamurran ta. dukkan lamurran ta.
Washegari weekend, bai tashi da wuri ba sai
around 12, da ya tashi kafin ya shirya ya fito
ya gama dukkan plans dinsa for the day.
Matsalar sa ta farko kafin komai ita ce
abinci, baya son yake zuwa gida gurin Mama
cin abinci always saboda baya son ko kadan
ta fahimci bai ji maganar su ba akan Safina,
sannan kuma baya son cin abincin siyarwa,
shi kuma ba girki ya iya ba. And there is no
way da zai ke cin abincin Safina. Shi bai taba
jin ma ya tsani mutum kamar yadda ya tsani
yarinyar nan ba.
Fita yayi wani mall a kusa da su ya lodo
kayan kusa da baka. Kayan tea, cereals iri iri
da dai duk abinda ya san zai iya ci without
having to enter the kitchen. Ya zo ya lode su
a cabinet din dining set din sa. Sai a lokacin
ya lura da abincin da yake jere akan table
din. Ya bude yaga farfesun kifi da kuma
masa, ya tsaya yana tunani, shi bai taba
ganin inda aka hada masa da kifi ba.
11
10
7
5
9:16 PM
Gaya tea flask ya bude ya ga tea ne a ciki
mai kayan kamshi, sai yaji kamar ya zuba ya
sha amma kuma sai ya rufe, a fili yace
"wannan mayyar fa zata iya zuba min asiri a
abinci, dan naga alamar babu abinda ba
zata iya ba",
Ya dauko kettle a cikin kayan da ya siyo ya
dafa ruwan zafi ya hada abinci yaci, a ransa
yana mamakin yau bai ga mayyar ta shigo. yana mamakin yau bai ga mayyar ta shigo
ba duk kuwa da cewa bai fita da wuri ba. Sai
da ya gama ya dauko wayarsa sannan ya ga
missed call din Mama, ya kira ta suka gaisa
tace "na kira ai ashe baka tashi ba, sai na
kira Safina. Dama ce maka zanyi tunda yau
weekend ka shirya ka dauki Safina ku je ku
gaishe da iyayen ka kuyi musu bangajiyar
biki, sun sha hidima" yayi shiru yana jin
plans dinsa suna tarwatsewa a gaban
idonsa, yace "shikenan Mama, ina ganin
gobe sai muje, yau da akwai wani gurin da
zanje kuma already na riga na gaya musu
zanje, suna jira na" ta dan yi shiru sannan
tace "shikenan, Allah ya kaimu, amma Safina
bata san zaka fita ba ko? Dan yanzu muka yi
waya da ita har ta gama shiryawa kai take
jira, tana ta murna zata fita yau" ya ji
haushin zakewar Safina a gurin iyayensa
yace "eh ban gaya mata zan fita ba, tunda
ban san da wannan plan din ba" Mama tace
"shikenan, ka je can din, cika alkawari ai
yana da muhimmanci ga cikar mutuntaka.
Amma ko gidan Mommy ne kuje kafin ka tafi
din, in yaso sai ka bar ta a can ka tafi uzurin
ka. Kaga Mommy bata ganta ba har yau,
kuma maman Khausar ma naji tace gobe
zasu koma Ankara, Turkey",
Baya son ya kara cewa Mama no, dan haka
yace "okay shikenan, zamu je can din".
Amma a ransa sam baya son zuwa, baya son
abinda zai distracting dinsa daga babban
abinda yake gabansa, sai dai kuma ya san
babu abinda yake gaban nasa wanda yafi. babu abinda yake gaban nasa wanda yafi
biyayya ga abinda iyayensa suka ce. Sai da
ya zauna a mota sannan ya danne horn din
motar ya cika gidan da kara. Ba zai sake yin
kuskuren shiga part din ta ba ballantana har
ya shiga dakin ta da sunan neman ta. Shi ya
san abinda ya gani jiya. And baya fatan sake
gani. Yasan kuma tana sane ta nuna masa.
Ya sake danne horn din, ya san har makota
in bacci ma suke yi sun farka. Ta leko ta
window "gani nan fa" amma tana rufe
window din ya sake danne horn din. Ta fito
da sauri ta a gyara mayafin ta. Lace ne a
jikin ta riga da skirt da suka sha stone work,
ta yafa mayafin da ya shiga da lace din, haka
ma jakar hannun ta da takalmin kafar ta. Ta
bude gaban motar ta shiga tana haki, "you
could have at least called me kace in fito" ya
watsa mata wani mugun kallo ya tayar da
motar.
Ta fara magana "Mama tace...
..." Yace
"Please just shut it. Idan har kinsan abinda
zai fito daga wannan ramin na tsakiyar
fuskar ki ba answer din da nake bukata bace
ba, to ki rufe shi, Bana son jin komai daga
gare k", Tayi shiru ta juya kanta tana kallon
side din titi yayin da suka dauki hanya. Sai
kuma ta juyo fuskarta tana nuna bacin ranta
tace "you know abinda nake gaya wa kaina
kullum in kana min wanna wulakancin?.....
Ya daga hannu "Please spare me. I don't
know, I don't want to know and I don't care"
ta kara jin haushi "okay, Kana da options
guda biyu, ko dai ka sauke ni anan in kira guda biyu, ko dai ka sauke ni anan in kira
Mama in gaya mata ka ki kai ni ko kuma kaji
abinda zan gaya maka" ya kunna kida a
motar tare da kure volume ya cigaba da
tukin sa. Ta saki baki tana kallon sa, she
never thought him to be this petty. Gidadon
da taso was so warm and nice. This one is a
monster that has no empathy. But she still
loves him kamar ta mutu.
Bata sake magana ba har suka je gidan.
Gidan kakannin Gidado na bangaren uba.
Suna shiga ya fara bin motocin da suke
gidan da kallo, yana tantance su waye da
waye a gidan, ga mamakin Safina sai ta ga
ya juyo ya kalle ta yana murmushi yace "I
know what? I am glad we came. Yau zaki
tantance banbancin aya da tsakuwa,
ma"ana, banbancin kaya masu daraja da
kuma kayan bola".
Ya bude kofa ya fita ya barta tana lissafin
menene kayan bolan? And tun kafin ta shiga
din sai taji ina ma bata zo din ba.
13
9
A
9:16 PM
Ita ma ta lura gidan a cike yake da motoci,
shin mutum nawa ne a gidan suka san cewa
ita tayi cigiyar sa a social media tace tana
son sa? Mutum nawa ne a cikin su suka san
cewa baya son ta ya aure ta ne dan ya
farantawaiyayensa?
Ta bude kofar motar ta fita tana karewa
gidan kallo, ba ta san ma ta kofar da zata. shiga gidan ba, and every thing in the house
is screaming money and class.
Ta hango Gidado yayi wajen wani magidanci
da yake tsaye yana magani da wani
teenager. Tun kafin Gidado ya karasa gurin
su yace "Abdallah! I missed you kamar zan
mutu" yaron yayi murmushin sa mai kyau
amma sai taga maimakon ya amsa wa
Gidado da kalmomi sai taga yana yi masa
signing da hannu, amma daga alama Gidado
ya gane me yace dan dariya yayi sannan ya
karasa ya rungume shi a jikinsa, ita dai bata
taba gain Gidado cikin wannan farin cikin
ba. Sai kuma taga ya gaishe da magidancin
"'uncle Faruk zamuyi kewar ku in kuka tafi".
Ta tsaya tana tunanin taje ne itama ta gaishe
su ko kuma ta shiga cikin gidan? A karshe
dai ta wuce bata gaishe su ba ta shiga kofar
da take tunanin nan ce hanyar shiga. A ranta
tana cewa maybe ma baki ne ba wadanda ya
dace ta gaisar ba ne ba.
Sai da Gidado ya gama hirar sa da uncle
dinsa Faruq wanda yazo kasar ne dama dan
attending bikin kuma yanzu zasu koma
Ankara shi da matar sa Huda, amma yar su
guda daya Khausar zata sake bin Aunty
Hafsat ne zuwa UK inda take karatu yanzu a
can tare da cousin dinta Bassam dan
Mammy kanin Al'ameen da kuma sauran
yayan Aunty Hafsat, amma su sai next week
zasu tafi, sannan ya shiga cikin gida.
Falon ya tarar a cike, mostly da yammata da. Falon ya tarar a cike, mostly da yammata da
samari, har Haidar yana nan shima. Ya ji a
ransa kamar ya fasa zuwa inda yayi niyya ya
zauna cikin yan'uwansa amma kuma baya
son samun any slack a cikin plan dinsa, ya
zauna a cikin su suka gaisa sannan ya
tambayi Khausar ina Mommy take ta gaya
masa tana dakin ta "tare da amaryar ka"' ta
karasa maganar tana dariya. Sauran suna
suka yi dariya. Ya mike shima ya tafi dakin
Mommy din, kakar sa ta wajen uba. Ya tura
kofar da sallama ta amsa masa, ya shiga
yana jin dadin kamshin dakin da sanyin acn
da ta cika shi. Tana zaune akan gado ta dora
kafafuwanta akan cushion din da aka ajiye
mata a gaban gadon saboda haka. Idanunta
sanye da eye glasses, completely
immaculately dressed kamar wadda zata fita
unguwa. Safina tana zaune a kasa daga
gefenta kanta a kasa.
Ya shiga yana karewa dakin kallo "wow. Wai
ke kullum cikin gyaran dakin nan kike? Sai
kace wata amarya?" Ta bishi da harara "ina
ruwanka to? Ko ka kawo gudummawar ka a
gyaran dakin na wa?" Yayi murmushi "ai ni
akayi wa gyaran na sani. Kuma na gani na
yaba, Baki da problem, gurinki special ne a
zuciya ta" ta kalli Safina da take gefenta ta
tabe baki tace "ni kuma na ga haka, Zaka yi
min dadin baki, Dama neman ka nake yi zo
ka zauna anan" ta fada tana nuna gabanta,
Ya karaso ya zauna yana jan yatsun
kafafuwan ta", "Good afternoon momma, ya
tsufa?" Ta rankwashi kansa, ya dafa gurin
yana dariya, sai kuma ya ga ta kara bata. yana dariya, sai kuma ya ga ta kara bata
fuska tana kallon Safina tace "amarya bamu
guri zamu yi magana. Ki je ga iyayen ki can a
sama ki gaishe su" Safina ta kalle shi, and
he can already see yadda fuskarta ta yi
loosing all the excitement da ta shigo gidan
da shi"
Tana fita Mommy ta bi bayan ta da wani
kallo da Gidado ya san ma'anar sa sannan ta
tabe baki tace masa "kai kuma bawan Allah
duk iyayin ka anan ka kare? Anya wannan
sangamemiyar matar ta ka bata fi karfin ka
ba? Ina zaka kaita? Nonon ta daya yayi nawa
duk biyun sanda ina budurwa".
Gidado ya mike da sauri yana jin kamar ya
fita daga dakin a guje dan kunya, ta jawo
hannun sa, "dawo ai ban gama ba" ya dawo
ya zauna ta cigaba "gaya min, a ina ka samo
ta? na tambayi babarka tace min sun ce ka
zaba a yan'uwa kace ba ka son yar'uwa.
Kace kai kafi son bare. Me yasa?" Ya gyara
zama yace "bani na samo ta ba ai Mommy,
su suka samo ta, sai dai suyi miki bayani"
yayi murmushi yana son chanja maganar
"kar ki damu, ina da ke ai, And you are the
most beautiful woman ever" ta tabe baki "ba
ka son ta, I can see it in your eyes baka son
ta, Da sake gaskiya,
17
9
9:16 PM
Ba zan bari ta tsotse ka ba. Wannan
dirkekiyar yarinyar sai ta zuke katas" ya kalli
agogon hannun sa "zan iya tafiya yanzu? I. agogon hannun sa "zan iya tafiya yanzu? I
have an appointment" ta dan ima tana
tunani sannan tace "ie ka, I will think about
your situation".
Yana dawowa falo yaji shiru kamar babu
kowa, sai da ya karasa shiga sannan ya
gansu gabaki daya sun zagaye Abdallah shi
kuma sai labari yake basu da hannunsa,
kowa ya saki baki yana bin bayanin nasa,
Gidado ya jingina da bango yana kallon su,
wato Abdallah da yana da baki da kunnuwan
su sun shiga uku fan a haka ma bai barsu
sun huta ba, a cikin labarin ya fahimci hirar
new abubuwan da ya tarar sun faru a gida
wannan hutun da yazo yake basu, a ciki har
da labarin amaryar yaya Gidado da yadda ta
wuce bata gaishe da uncle Faruk ba. Sai
kuma zancen Humairan Al'ameen tana da
ciki Basma ma tana da ciki.
Gidado yayi gyaran murya yace "Abdallah da
kai mace ne mun shiga uku da tsegumi" duk
suka juyo suka kalle shi suka yi dariya,
banda Abdallah da bai ji me yace ba tunda
lokacin da yayi maganar baya kallon sa, sai
ya fara tambayar sa "what did you say"
Gidado ya wuce shi yana murmushi bai
bashi amsa ba, ai kuwa ya mike ya biyo shi
har mota wai lallai sal ya gaya masa abinda
yace, sai da Gidado ya tayar da motar
sannan yace "in ka matsu ka zo gida na kayi
kwana biyu, sai in gaya maka".
Gidansa ya sake komawa ya sake shiryawa a
tsanake. Yay shiga mai kyau ta alfarma irin. tsanake. Yayi shiga mai kyau ta alfarma irin
wadda kullum yake da burin yi idan zai je ya
gaishe da Daddyn Safiyya. Ko ta na nan? Ko
zai ganta? Sai dai shi kansa bai san me zai
cewa Daddyn idan ya ganshi ba. But he will
surely ask some questions wadanda ba za
suyi raising suspicious ba, and he will surely
get some answers.
A bakin gate yau ma kamar kullum mai gadi
ya bude masa, sai kuma ya tsaya ya
tambaye shi idan shigowa zai yi ciki ko kuma
a waje zai tsaya. Ya gaya masa ciki zai shiga,
bayan ya shiga ne kuma ya tambayi mai
gadin idan Daddy yana nan. Mai gadin yace
"Alhaji yana nan. Kasan bashi da lafiya. Bai
fiya fita ba in dai yana gari sai dai in dole"
Gidado ya gyada kai, indai har ciwon da
Safiyya ta gaya masa yana damun Daddyn
ta shine da gaske, then he should be in a
wheelchair by now. Sai yaji wani tausayin
Safiyya ya kara kamashi, in Daddy ya tafi
zata zamanto babu uwa babu uba, and he
should be the one to replace them all for
her.
Ya gaya wa mai gadin cewa gurin Daddy
yazo, yazo ne zai gaishe shi. Sai maigadin ya
shiga yace bara yayi masa magana, Ya jima
sannan ya dawo yace "yace ka dan jira
kadan, yana ciki yanzu, in ya fito falo sai ka
shiga" har yayi gaba kuma sai ya juyo yace
da Gidado "kar ka sake guduwa amma"
suka yi dariya tare, Sai maigadin ya koma
cikin inuwa kan kujerar sa ya zauna. Gidado
ya bishi yaje ya zauna a kusa dashi yace "no. cikin inuwa kan kujerar sa ya zauna. Gidado
ya bishi yaje ya zauna a kusa dashi yace "no
gidan nan kullum na shigo sai in ganshi
kamar dry, kamar babu mutane a cikin sa"
maigadi yace "eh ai ba zama suke ba masu
gidan. Tunda Allah yayi wa Hajiyar mu ta
farko rasuwa Alhaji baya son zaman gidan
nan sam. Sanda ya auri wannan Hajiyar ta
yanzu kuma sai suka koma Kano da zama
gabaki daya. Dama shi dan can ne" Gidado
ya gyada kai "kana nufin mahaifiyar Safiyya
kenan ko?" Mai gadin yace "eh ita fa. Anan
suka tare ai tun farkon auren su. Anan aka
haifi Safiyya, anan kuma Allah yayi mata
rasuwa. Daga baya ya auri mahaifiyar Safina,
su ai zuwa tayi dasu ita da Mustapha, kamar
yan'uwa suke ai da mahaifiyar Safiyya da ta
Safina, ban san dai dangantakar tasu ba
amma tun waccan Hajiyar tana da rai
wannan tana zuwa sosaj" Gidado ya bude
baki zai sake next question dinsa sai ya ga
wani dogon saurayi ya fito daga cikin gidan
ya doso inda suke da murmushi a fuskar sa,
Tun kafin ya karaso Gidado ya gane waye
shi, suna yanayi da Safina da kuma twins,
sai dai kamar yadda Safina ta fada, ba shine
wancan Mustaphan da ya gani a Katsina ba
amma still hakan ba wai yana nufin tana da
gaskiya ba,
13
9:16 PM
Ya karaso ya mika wa Muhammad hannu
"Muhammad Gidado, welcome, ya
amaryar?" Gidado ya kirkiri murmushi "lafiya
lau, tana gaishe ku. Tayi missing din ku". lau, tana gaishe ku. Tayi missing din ku"
Mustapha ya girgiza kai "ahh! I doubt much,
yarinyar can ba zata yi missing din mu yanzu
ba. Lokaci daya ta birkice mana ita aure ta
ke so ita kai take so" ya karasa yana dariya
amma Muhammad bai yi ba. Sai kuma yayi
gyaran murya yace "Daddy yace ka shigo"
suka juya suka jera zuwa cikin gidan, a
hanya Mustapha ace "sunana Mustapha,
kuma ni yayan Safina ne uwa daya uba
daya" Gidado yace "I know" daga nan bai
sake cewa komai ba. A kofar falon Mustapha
ya tsaya, Gidado ya shiga shi kuma ya koma
da baya
Yana shiga falon Daddy abinda Gidado ya
fara gani shine hoton wata mata yana facing
dinsa, kallo daya yayi mata ya gane wacece,
ya gane cewa ta jikinta Safiyya ta zo duniya.
Tana tsaye da dan katakon award a
hannunta, da murmushi a fuskarta, a jikin
katakon ya karanto sunan ta "Safiya Khalid"
yaji gabansa ya fadi, ya tuno sunan da ya
gani a cikin biography din Daddy, wannan
Safiyan suke nufi ashe.
Ya sauke idonsa kasa ya sauke su akan
Daddy, yana zaune akan kujera yana kallon
sa, he looked just like pictures dinsa da yake
gani a gurin Safiyya, except that he looked
smaller and older now, daga alama ciwon
nashi ya kara tsanani, Yayi kokarin tattara
nutsuwar sa sannan ya durkusa daga dan
nesa kadan da Daddy ya gaishe shi "Daddy
barka da yamma" ya fada yana jin zuciyarsa
tana matsewa with emotions, this has. tana matsewa with emotions, this has
always been his dream a cikin shekaru biyu
da suka wuce, now gashi a gaban Daddy
amma kuma a matsayin mijin Safina ba wai
saurayin Safiyya ba.
Daddy ya amsa masa yana studying dinsa
da sharp eyes dinsa da suka yi making
Gidado uncomfortable "ya mutan gidan?"
Gidado yace "lafiya lau Daddy" Daddy yace
"Sa'adatu ta ce min ai kai jikan marigayi
Muhammad Dikko ne ko?" Muhammad yace
'"eh. Kakana ne shi" "mutumin kirki ne"
Daddy ya fada, Gidado yayi murmushi yana
jin dadi a ransa. Sai kuma ya tambayi Daddy
"'ya saukin jikin?" Daddy yace "alhamdulillah
Allah shine abin godiya. Never thought zan
kawo yanzu, gani nan kuma har yanzu,
sannan ban san yawan kwanakin da Allah zai
kara ara min nan gaba ba".
Daga nan sai Daddy ya cigaba da yi masa
tambayoyi kamar inda yayi karatu da inda
yake aiki yanzu da muka sauran affairs na
rayuwa. Gidado da yazo da niyyar yin
tambayoyi sai aka koma shi ake yiwa
tambayoyin kuma yana amsawa da dukkan
gaskiyar sa, Sai da ya gama sannan Daddy
yace "nayi mamaki, Sa'adatu was
complaining about you, Maybe you started
on a wrong foot with her. Daga abubuwan
da ta gaya min sai nayi picturing dinka a
matsayin arrogant, rude and spoiled dan
masu kudi, But you look and sound
different. Na gamsu da tarbiyyar ka gaskiya.
lyayen ka sunyi kokari. Allah yayi maka. lyayen ka sunyi kokari. Allah yayi maka
albarka" Gidado yaji kamar an bashi award,
ya amsa da "Amen Daddy, Nagode. Allah
ya ja kwana ya kara maka lafiya".
Ya sake daga kai ya kalli hoton Safiya, sai
Daddy yace "she was my first wife. Ta rasu.
Safiya sunan ta" Gidado ya sunkuyar da
kansa yace "Daddy na dauka kanwar Safina
ce Safiva. Ashe suna ta ci" Daddy yayi
murmushi, he looked proud and in love.
Yace "suna ta ci. Sanda na aure ta mun jima
muna neman haihuwa Allah bai bamu ba.
Mun zaga duniya neman haihuwa Allah bai
bamu ba. Har mun fitar da rai. Sai kuma
lokaci daya Allah ya bamu Safiyya. Sanda ta
haife ta na bata zabin cewa ta saka mata
sunan da take so. She spent entire two days
thinking, ko bacci bata iya yi, har cikin dare
maganar sunan yake yi, she wanted to name
her Hadiza sunan mahaifiyar ta but then she
had a sister called Khadijah kuma in ta saka
Hadiza wai waccan Khadijan ita ma zata ce
an saka sunan ta, and then there is the other
sister Sauda, wai Saudan zata ce ita ba'a
saka sunan ta ba",. Daddy yayi dariya "she
was so dramatic. Duk sun mutu fa. Wai a
lahira ne za'a yi wannan rigimar idan sun
hadu. So I saved her the stress na dauki
yarinya nayi mata huduba da sunan ta,
Safiyya, nace ta gaya musu cewa ni na fi
sonta akan su baki daya",
13
5
9:16 PM
Suka yi shiru baki daya. Sai Gidado ya samu
kansa da cewa "Allah yayi mata rahama, yayi. Suka vi shiru baki daya. Sai Gidado ya samu
kansa da cewa "Allah yayi mata rahama, yayi
wa abinda ta bari albarka" Daddy ya gyada
kai yace "albarka kam alhamdulillah. Dama
ita mai albarka ce. Duk abinda ta taba
albarka ce da shi. You know how some
people are just blessed beyond measure,
but then they get tested kuma up to their
breaking point. In aun ci jarabawowin then
they emerge stronger and wiser, in kuma
sun fadi then they crumble and turned to
dust". Gidado yayi shiru yana kallon Daddy
cikin rashin fahimta, ya kasa gane yana
magana ne akan waccan Safivan ko kuma
abin da ta bari din "Safiyya".
Muhammad yay kokarin throwing one of his
questions "jiya ai muna tare da twins, su
suka wayar min da kai akan Safiyya. I
thought ta jima da yin aure a" Daddy ya jiyo
yana kallon sa kamar mai studying dinsa, sai
Muhammad yaji duk ya tsargu, har yayi
tunanin Daddy ba zai amsa question din
tasa ba sai kuma yaji ya yi magana "last
weekend aka dauka mata aure. Yau sati
guda chif kenan. Though ta jima ta na son
yin auren. Ta jima tana yiwa Mommyn su
magana, har daga baya ta ajiye kunya tayi
min magana da kanta. But 1 had plans for
her sai naki bata goyon baya" yayi ajjiyar
zuciya "komai da da lokacin sa., Yanzu ne
lokacin auren nata yay" Gidado yayi shiru
yana digesting maganar,
Sai kuma Daddy ya ajiye waccan maganar,
daga alama ya tuna da wa yake magana, sai daga alama ya tuna da wa yake magana, sai
ya dauko nasiha akan zaman aure da
hakkokin mata da suke kan mijinta. Yace "ba
ka da matsala da Safina, tana da hakuri
sosai, bata da gardama musamman kuma
tunda ita tace tana son ka tabbas zata yi
maka biyayya iya kacin iyawarta. Da dai
Safiyya ce.." Sai kuma yayi murmushi "ita
wannan taurin kai ne da ita. She is always a
handful" ya fada amma fuskarsa tana
reflecting soyayyar da yake wa Safiyya.
"'Amma Safina ban taba jin abokin fadan ta
ba, ko da Safiyya ban taba jin suna fada ba.
Bata ma da surutu sosai. Amma Safiyya in
tana gida sai ta damu kowa a gidan. In kaji
Sa'adatu tana fada to da Safiyya take y" ya
sake yin murmushi sannan yay ajiyar zuciya
"those are the good old days".
Jin yayi shiru sai Gidado yace "ya jikin nata?
Safina tace min bata da lafiya" Daddy ya
juyo yana kallon sa "me tace maka yana
damun ta?" Gidado ya danyi shiru yana
tunani, Daddy sounds defensive, sai yace
"she didn't say. Na dai ce bamu taba
haduwa ba sai tace min bata da lafiya shi
yasa" Daddy yace "eh, amma taji sauki
sosai" and out of nowhere sai kuma ya dauki
wayarsa yace "bara in kira maka ita sai ku
gaisa, Tunda tafiya zamu yi*,.
Gidado yay shiru yana saurarar Daddy yana
magana, he was great full bai kira shi da
matsayin mijin Safina ba yace dai kawai tazo
za'a duba ta, Maybe da ba zata fito ba, But
then kuma tunanin sa yana kan maganar. then kuma tunanin sa yana kan maganar
tafiya da yaji Daddy yace zasu yi? Ina zasu
je?
Daga nan suka cigaba da magana, ya
fahimci Daddy baya iya hada sentence biyu
a tare ba tare da sunan Safiyya ya fito a ciki
ba. Mostly labarin yarintar Safiyya da Safina
ne.
Suna cikin magana aka bude kofar da
Gidado yake tunanin cikin gida ta shiga aka
shigo. Sai kuma takun ya tsaya daga bakin
kofar bai karaso cikin falon ba. Gidado ya
daga kai, duk da wata zuciyar tana gaya
masa not to look, matar aure ce, but he did
looked and saw her.
Tana tsaye a bakin kofa jikinta sanye da
dogon hijab, kumburarrun idanuwan ta a
kansa. She looked very thin and fragile,
kamar in aka taba ta zata balle, and the
eyes, the eyes are a clear testimony that she
have been crying a lot.
Yaji kamar ya mike ya je ya jawo ta jikinsa ya
tambaye ta abinda yake damunta, he can do
anything, anything, to take her pain away.
Her
A guje Mukhtar yake tafiya da mita yana
ratsa traffic, gashi dama yanma ce gari ya
cika da motoci, and in my heart hoping nake
zai je ya buga motar a wani guri duk mu
mutu, ko kuma ni in mutu, Amma bai buga mutu, ko kuma ni in mutu. Amma bai buga
din ba. Ransa har lokacin a bace yake ina
kallon yadda yake fitar da numfashi sama
sama.
15
6
9:16 PM
Ni ban san me yake yiwa gudu ba, tunda dai
Gidado ba biyo mu yayi ba ballantana yace
shi yake gujewa. Na goge hawayen fuska ta
ina tuno da Gidado a gidan mu a tsaye a jikin
motar sa. Ni na san ba guri na yazo ba, to
menene ma hadi na dashi da zai zo gurina?
Gurin matarsa yazo, zuwa yayi ya bawa
Safina hakuri kamar yadda Mommy ta nema
sannan ya dauke ta su tafi gidan su. Fully
accepting the marriage.
Naji duniya ta kara yi min zafi, I have went
through the heartbreak of rabuwa da
Gidado through I have always bottled up my
feelings na kasa barin kaina inyi tunanin
ciwon da zuciya ta take yi akan rabuwa da
shi. But now I have to accept rabuwa da shi
din and also accept him as mijin Safina. Mijin
Safina for God's sake. Ta yaya zan jure ganin
su tare a matsayin mata da mij? Ta yaya zan
iya mantawa da shi bayan dole zan cigaba
da ganin sa around?
Na kara duba possibility din barin Nigeria,
But can I? Dana barta ma da farko haka na
hado kayana na dawo da kaina, Yanzu ma in
na tafi dawowar zan sake yi, Besides, it is a
fool's choice to run from the battle field, Na
juya ina kallon Mukhtar, what is he running
from? juya ina kallon Mukhtar, what is he running
from?
Na sake gofe wahaye na nace "he is not
following us, gudun me kake yi?" Yace
"bashi na ke gudarwa ba. I do not give a
P**** about him, kai na nake gudarwa, dan
in ya tsaya yana kallon ki zan iya karya shi
wallahi'" nace "ba guri na yazo ba, kuma ka
sani, gurin matarsa ya z0. And I doubt idan
zaiyi min magana ma ko da mun hadu" ya
girgiza kai "ko da bai yi miki magana ba I
can't stand having the two of you together
in the same place. Zuciya ta ba zata tsaya
guri daya ba. And I may do something that
all of us will regret".
Nace "now, you are doing something that
you will regret. Daddy yace ka kaini gida
straight. And I am sure yanzu ya tabbatar ba
gida muka tafi ba, or yaji labarin mun shigo
mun fita. Or really don't want to cross
Daddy" yayi slowing down yace "ba zai ce
dai ya fasa aura min ke ba ko?" Nace "yes,
zai iya cewa" ya danyi murmushin da ban
gane ma'anar sa ba yace "I think you are
forgetting cewa an daura, Ke a yanzu iko na
ce ba tasa ba" naji raina ya fara baci nace
"igiyar aure ba zata taba limiting Daddy
from me ba, Now, ka mayar da ni gida in ba
haka ba Daddy zai fahimtar da kai abinda
nake nufi idan baka gane ba".
Ya juya kan mota ya dauki wani titin yace
"not now. Har sai na tabbatar wancan
banzan ya bar gidan can" naji raina ya kai. "not now. Har sai na tabbatar wancan
banzan ya bar gidan can" naji raina ya kai
kololuwar baci nace "sauke ni a nan" yayi
kamar bai ji ni ba na sake maimaita Wa
"Mukhtar ka sauke ni anan nace. I don't
want to be in your car one more second"
yace "saboda nace masa banza? You think
ba banzan bane ba? Shashasha irin sa"
Na kama handle din kofar na bude shi
sannan na tura kofar a lokacin da motar take
cigaba da tsalala gudu. Cikin seconds
abubuwa da yawa suka faru, iska ta fincike
ni waje sai kafafuwana ne kadai a ciki yayin
da motocin da suke kan titi suka cika titin da
horn. Mukhtar ya saki stirring motar ya baro
seat dinsa gabaki daya sannan ya damko
rigata ya rike da karfi ya hana kaina reaching
kan titin, tare da kokarin tsayar da motar ta
hanyar dauke kafarsa daga kan accelerator,
sakin stirring da yayi ya saka motar mu ta
sauka daga kan lane din mu ta hau daya lane
din sannan ta gangara gefen titi.
Sai a lokacin ya samu nasarar tsayar da
motar ta hanyar taka break a hankali,
sannan ya jawo ni ya dawo dani sosai kan
seat dina, Ya tsaya yana kallona yana mayar
da numfashi da sauri, na koma na kwanta a
jikin seat dina tare da rufe ido na. Cikin fada
yace "what?! What just happened? You want
to kill yourself saboda na zage ship" Ba tare
da na bude ido na ba nace "now you know"
ya daki motar cikin dacin zuciya "why? Just
tell me why kika zabi aure na when you
know you love him this much, Me yasa ba know you love him this much. Me yasa ba
zaki gaya wa Daddy directly cewa shine
uban dan ki ba and have Daddy get you two
married. Me yasa kika zabi dragging me into
this mess?" Na bude ido ina kallon sa dusu
dusu saboda kaina da yake juyawa nace
"saboda ba shi ba ne ba.
12
9:16 PM
And I will never stain his white" ya bude baki
cikin mamaki "to ni kuma fa? Nine uban dan
kike nufi ko menene? Why choose me?"
Nace "saboda nayi addu'a and kai na
fahimta a matsayin mijin da Allah ya zaba
min. Now you have to accept me as I am or
reject me".
Sai yayi shiru yana kallona kawai, fuskarsa
tana nuna tsananin bacin ransa. Na kwantar
da seat din sannan na kwanta na juya masa
baya, at that point ban damu da yaushe zai
mayar da ni gida ba. In yaga dama mu
kwana a motar shine a ruwa ba ni ba.
Naji ya zura hannunsa ta sama na ya jawo
kofar ya rufe ta. Sannan ya tayar da motar
muka cigaba da tafiya, ban bude ido a ba
ballantana in san inda muke tafiya kuma ban
damu ba, Abinda na sani kawai a lokacin
shine dole in koma asibiti in cigaba da
karbar anti depressants din da aka taba min
prescribing watannin baya when I tried
something like this,
Sai da naji an bude gate sannan na bude
idona, na fahimci gida muka dawo, na mayar idona, na fahimci gida muka dawo, na mayar
da ido na na rufe har muka yi packing
sannan naji yace "ki tashi ki shiga ciki". Na
tashi na bude kofa na fita, na gane dabarar
sa, so yake ya ajiye ni kawai ya tafiyar sa
yadda Daddy ba zai ganshi ba ballantana
yayi masa fadan dadewar da muka yi. Bance
komai ba na juya nayi hanyar cikin gida shi
kuma ya fara kokarin bude mota kenan naji
muryar Mustapha yana yi masa magana
"hey, Daddy yana kira" na wuce Mustapha
na yi shigewata a raina ina tunanin su
Muhammad da Safina sun tafi tunda banga
motar sa ba.
Sai dai ina shiga falo naga Safina a zaune,
Mommy ma tana zaune ranta a bace, daga
ganin ta kasan tayi fada har ta gaji. Ta juyo
kaina "da aka ce kar kuje ko'ina ba ku ji ba
kenan? Idan shi ba shi da hankali kema ba ki
da shi?" Ban ce komai ba na samu guri na
zauna, ina son in tafi daki in zauna ni kadai
da tunani na ina kuma son inji yadda aka
kare da Safina da Muhammad. Muna zaune
Daddy ya shigo tare da Mustapha, shima
nashi ran a bace, yana kallona yace "me na
gaya muku kafin ku taho" bance komai ba
Mommy tace "kai ma kasan laifin waye ai,
kasan wa zaka yiwa fada ba ita ba" yace "ai
nayi masa nasa, Ita ma da laifin ta. To ki
shirya ki hada kayan ki, gida zamu koma,
Kano zamu tafi dan ba zan yarda ya cigaba
da zuwa yana batan rai na ba, Idan kin huta
sosai kin warke sai a saka ranar biki" ni dai
bance komai ba, sosai kin warke sai a saka ranar biki" ni dai
bance komai ba.
Mommy tace "ni ban ma fara tunanin nata
bikin ba tukunna, wannan da akayi bikin ita
ce nake so mu san matsayin ta first. Ni na
kasa gane matar aure ce ita ko kuma
budurwa?" Bai ce komai ba ya juya kujerar
sa zai fita, Mommy tace "ba ka ce komai ba
fa?" Ya juyo still da fada a muryarsa yace
"cewa fa kika yi ba ya ta bace. Da bakin ki
kika gaya min cewa bani na haife ta ba. Me
kike so ince kuma? Kika dauki yarinyar kika
kai ta inda basu san mutuncin ta ba suka vi
mata auren da babu mutunci a ciki, sai
yanzu kuma da abu ya kwabe zaki tambaye
ni mai za'a vi? Ke zaki san abinda zaki yi a
kai. Ko kuma ki mayar musu da ita katsinan
su san me zasu yi. Ni ba zan saka baki a ciki
ba" tace "'wato yanzu dan ni da kai mun yi
hukunci ba dai dai ba cikin fushi shikenan
sai yara su zama sune zasuyi paying price?
Ni da ka nuna min bani na haifi Safiyya ba
shikenan sai in ce na daina shiga lamarin ta
kenan?" Yace "ke dai kika yi ba dai dai ba.
No babu abinda nayi ba dai dai ba, saboda
ban yarda cewa takurawa yarinya ta auri
wanda ta fada ta sake fadar cewa bata son
shi shine dai dai ba, Ko da ke kika haife ta ba
zan bari ki takura mata ba" ya juya cigaba
da tafiya, ni a lokacin damuwata ita ce
lafiyar sa, maganganun da yake tayi sunyi
draining dinsa, muryar shi tayi can kasa
sosai. Sai da ya kai bakin kofar komawa part
dinsa sannan ya juyo yace mata "ki dauke ta
ki kaiwa iyayensa ita, ki danka musu ita ki kaiwa iyayensa ita, ki danka musu ita
amana a hannun su, hukunci kuma ya rage
nasu. Tunda an riga an daura ba zamu
cigaba da rike ta a hannun mu ba. Ke
kuma.." ya fada yana nuna Safina "duk
abinda ya faru bayan nan sai ki kira mu ki
gaya mana. Idan yafi karfin iyayensa sai mu
sani, idan munga akwai cutarwa sai mu
shigar da shari'a ciki" ya juya ya karasa fita
13
6
9:16 PM
Anan dai Mommy ta zauna ta cigaba da fada
zuwa lokacin na fahimci a gurin Mommy
babu marar tarbiyya kamar Muhammad.
Safina bata ce komai ba nima ban ce komai
ba. Daga baya dai naga Mommy ta yanke
shawarar yin abinda Daddy yace tace da
Safina taje su shirya su tafi. Ina nan zaune
har ta shirya ta fito cikin shiga irin ta amare,
ina kuma zaune Mommy ta sa aka fitar da
duk sauran kayan Safina da suka rage a
gidan ta ce in ta kai Safina gidan iyayen
Muhammad zata kai mata kayan nata
gidanta, sannan suka yi min sallama suka
fita,
Na cigaba da zama anan kamar mutum
mutumi har Mommy ta dawo, tana kallo na
tace "na kai ta, Ai naga iyayen nasa sunyi
masa fada sosai, Ya dauke ta ma sun tafi",
Na mike na shiga daki na na rufe kofa, Daren
was one of the longest dare in the history of
my life, Kuka dai nayi shi har na gode Allah,
Kwana biyun da suka biyo baya were one of
the terrible days of my life. Nayi kuka Kwana biyun da suka biyo baya were one of
the terrible days of my life. Nayi kuka
iyakacin iyawa ta. A daren kwana na biyun
ne ina shirin kwanciya bacci twins suka fado
min daki hankalin su a tashe, na bisu da
kallo sannan na kalli kofar da suka shigo
"lafiya? Jikin Daddy ne?" Suka girgiza kai,
Hassan yace "daga gidan yaya Safina muke"
na zauna a gakin gado ina kallon su, trying
to guess what happened. Hussein yace
"dama kin san mijinta?" Na rufe ido na na
bude nace "me ya faru? Me yace?" Hassan
yace "tambayoyi ya ringa yi mana. I think
mun saki baki da yawa. We told him an
daura miki aure da Mukhtar last week" naji
kaina ya sara jiri yana neman dibana, ban ce
komai ba Hussein yace "He said wai auren ki
biyu kenan, muka ce daya ne, and then he
said.
." Sai yayi shiru, but na san karashen
maganar, Hassan ya karasa "he said kin
gaya masa kina da are three months ago,
kuma ya ganki da ciki three months ago".
Nayi shiru ina tauna maganar a raina sannan
nace "and Safina? Me tace masa?" Hassan
yace "bata ce komai ba, bata yi magana ba"
na gyada kai na "alright, It is okay, Kar ku
damu kanku, I will call her sai muyi maganar
Na jima a zaune bayan sun fita ina going
over maganar sannan a fili nace "what are
you up to Muhammad? Me kake yi?" I was
terrified cewa he is closer to the truth, but
also relieved that yana yi min son da zai
zauna yana magana ta a gaban matarsa. zauna yana magana ta a gaban matarsa.
Duk da na san son ba zaiyi min amfanin
komai ba, shima ba zaiyi masa amfanin
komai ba. Tunda ni matar wani ce. Shi kuma
mijin wata.
But sai kuma anxiety ya fara kamani,
Muhammad is digging, yana haka rami ban
kuma san a wanne bangaren yake hakar ba.
Ban san ta ina ramin nasa zai bullo ba. Ina
tsoron kar ya haka ramin da zai rufta da shi.
Washegari ina zaune da yamma akan sallaya
ta bayan nayi kuka na na gama kamar
kullum, sai Daddy ya kira ni yace inzo ga
bako nan yazo zai duba ni. Na tashi na tafi
da kumburarrun idanuwa na da dogon hijab
din sallah ta. Ban san waye bakon Daddy din
ba and I do not care what I looked like.
Amma ga mamaki na ina tura kofa sai ganin
Muhammad nayi a zaune a gaban Daddy, a
picture that has always been my dream.
Daddy and Muhammad together suna hira
suna murmushi, But now he is here as min
yar'uwata Safina, not as saurayina da zai
aure ni,
Maman Maama. Nafisa Tafida Usman
Safiyya*
owner
Episode Twenty Seven: Safiya
@
43
Paid Advert
Contact Lame(07036662633)for all your
costumes both oriflameand other special
products that will make ur skin glow and
flawless
Kayanmu lamba daya ne wajen kyau da
farashi daidai da aljuhun kowa.
Muna Kano, muna aikawa kowanne gari.
Muna tayaku zaben mayukan da zasu dace
da fatarku.
Sensitive skin
Oily skin
Dry skin.
Haka nan duk yadda spots da pimples suka
bata muku skin da zarar kun yi amfani da
kayanmu zaku huce wannan takaicin da ikon
Allah.
Kayanmu tested & trusted.
Skin care for exclusive women,
Contact, Aysha lame on. Safiya
Wani bangaren na zuciya ta ya cigaba da
gaya min in koma da baya, kar in karasa
shiga, bangaren da ya kasance cike da tsoro
da fargabar outcome din wanna haduwar,
amma kuma dayan bangaren yana nuna min
cewa zuwan nawa gurin zainiya dakatar da
duk wata annoba da rashin zuwan zainiya
haifarwa.
Ban san ne suke magana a akai ba ban
kuma san me zasu ce ba har sai an karasa
gurin tukunna zan sani. Gabakidaya zuciyar
tawa kuma yana yabawa boldness irin na
Muhammad, ko kuma dan bai san cewa da
ace Daddy ya san ko shi waye da tuni wata
maganar ake yi daban.
Ta ja kafarta a hankali ta karasa shiga ciki,
still idonta akan Muhammad, so take ta
tambaye shi me yake yi anan kuma me yake
gayawa Daddy amma kuma babu dama. Sai
dai ganin da tayi babu chanji a fuskar Daddy
ya dan kwantar mata da hankali ta fahimci
bai gaya masa wata magana da ta shafe su
ba, Ta durkusa a kusa da kafafuwan Daddy
tana fuskantar Muhammad amma kuma ta
juya yadda Daddy ba zai kalli fuskarta ba
tace cikin maganar motsa baki yadda Daddy
ba zai jiyo ba "don't! Please",
Bata sani ba ko Muhammad din ya fahimci
abinda tace ko kuma bai fahimta ba, ta dai ga ya dauke idonsa daga kaina sannan ya
mayar da su kasa yana kallon yatsun
hannunsa, muryar Daddy ta ratsa falon
"Safiyya, mijin Safina ne yazo duba mu, ba
ki gaishe shi ba" na dan gyara muryata dan
farki nayi tunanin ba zata fito ba nace
"barka da zuwa. Ya iyalin?" Ya dago daga
kallon hannun nasa ya kalle ni, yanayin
fuskarsa gabakidaya ya chanja, ya danyi
gyaran murya sannan yace "lafiya lau. Ya
jikin?" Na sunkuyar da kaina kasa nima ina
yin duk kan kokari na na daina kallon sa
nace '"da saukj" sai kuma muka yi shiru
gabakidayan mu.
Sallamar Mommy ce ta ratsa shirun falon,
ban dago na kalle ta ba shima kuma
Muhammad haka. Ta ratsa ta tsakanin mu ta
zauna a kan kujerar gefen Daddy sannan
tace "da gaske ne kuwa ashe, Mustapha
yace min kazo kana nan nace anya kuwa?"
Ya gaishe ta ba tare da ya dago kai ba
"Barka da yamma" tace "lafiya lau. Ka
kyauta kuwa da kazo ka duba Daddy tun
kafin mu tafi. Ina so dama in cewa Safina ta
gaya maka hakan kuma ban fada ba ashe
kana da niyya dama", Ya dago kai muka
hada ido nayi sauri na dauke kaina gefe,
bana son ganin emotions din fuskarsa, it
breaks my heart,
Ya fara kokarin mikewa "Daddy zan koma,
Allah ya kara lafiya ya kaiku lafiya, Mommy
Allah ya tsare hanya" Mommy tace "a'a,
baka shiga ciki ba ai, ko ruwa ba ka sha ba". baka shiga ciki ba ai, ko ruwa ba ka sha ba"
vace "babu komai Mommy, next time insha
Allah" sai kuma ya tsaya yana kallona.
"Safiyya ban sani ba ko zaki iya zuwa mota,
akwai sakon ki da Safina ta bani in baki" na
dago kai da sauri ina kallon sa cikin mamaki,
his boldness is really on another level. Ya
cigaba da tsaiwa yana kallona yana jiran
amsa, Mommy tace "zata iya zuwa mana, ai
dama ance ta ringa motsa jikinta. Safinan
Safiyya kenan tsakanin su sai Allah".
Naga bashi da niyyar tafiya sai na mike, sai
da ya tabbatar na taho sannan yayi gaba na
bishi a baya. Ina fita na ganshi a tsaye a
bakin kofar, muka jera a muna tafiya a
hankali amma babu wanda ya kalli wani
ballantana yayi magana har muka je gaban
motarsa muka tsaya.
Wani tunani ne yazo min nayi ssuri na kalli
hanyar gate. Na dawo da idona kansa naga
ni yake kallo with his full attention, kamar
mai kokarin karantar soul dina.
8
6
2
9:07 PM
"What are you afraid of?" Ya tambaye ni
murya can kasa, ban ce komai ba sai ya
bawa kansa amsa "kina tsoron kar ya shigo
ya ganmu ne? Mukhtar kike jin toro?" Na
cire idona daga cikin nasa na sauke su kasa
nace "he is my husband" yace "just as
Safina is my wife" ya karashe maganar tare
da huro numfashi daga bakin sa, a kokarin
sana daidaita emotions dinsa. "I am so sorry Muhammad" na fada a
hankali. "I have hurt you fiye da kowa a
duniya, ban yi maka adalci ba" yace "yes,
you have hurt me real bad Piya, but I am not
here for the apologies, maybe zan iya
accepting apologies din naki nan gaba, but
now I am here for the truth. Did you or did
you not lie to me about being married and
being pregnant?"
Na goge hawayen daya fara taruwa a gefen
ido na nace "yes, I was lying. Karya nayi
maka. Ni makaryaciya ce" ya girgiza kansa
"you are not a liar......" Na katse shi "haka
ne, bana yi maka karya. Amma a lokacin nayi
maka. I lied to you. Bani da aure a lokacin
nace maka ina da shi".
Yayi shiru yana cigaba da nazari na. "A cikin
wata hudu, you have moved from single to
married and then back to single, then to
married twice and then to married once.
Wannan zan dauka Safiyya? Wanne zan
yarda da shi? Okay assuming you were lying
a lokacin, me yasa kika yi min karyar? And
don't give me the crap about ba kya so na
dan a lokacin ne zan kara tabbatar wa da
cewa karya kike sake yi min".
Na dago kai ina kallon shi, I saw bacin rai
vividly written on his face, sannan nace "ina
son ka Muhammad, more than you will ever
know. But somethings are not just meant to
be....." Ya katse ni "and who told you we are. know. But somethings are not just meant to
be..." Ya katse ni "and who told you we are
not meant to be? With whom are we
supposed to be? Who am I supposed to be
with? Safina?" Ya fadi Safinan da dacin rai,
Na girgiza kaina "I don't know. Somethings
are hard to explain. Dan Allah kayi hakuri",
Ya girgiza kansa "I just can't believe this.
You just told me you love me, and then you
say we are not meant to be, in yi hakuri. Ni
ban gane ba Piya. Ki gaya min what's going
on. What happened to you? Please ki gaya
min. Whatever it is we can get through it
together. Let me share the burden with you
please" na kasa cigaba da kallon sa na
sauke ido na kasa, na bude baki da niyyar
magana amma ita ma sai na kasa. A karshe
sai na kare da cewa "I can't. I am sorry",
Ya zagaya ya bude motar sa kamar zai shiga
sai kuma ya buga murfin motar da karfi ya
sake zagayowa inda nake, he looks very
frustrated, daga dukkan alamu neman
abinda zai daka yaji dadi yake yi. Na sake
cewa "I am sorry" na nuna ni "if you say
sorry one more time....." Sai kuma yayi shiru
yana kallona na "just look at you. Duba ki
02
gani yadda kika zama. And you won't tell me
me yake faruwa. You won't tell me me yasa
kika yi breaking up with me. And you won't
let me ask Daddy questions da zasu
bayyana min gaskiya, You won't let me tell
Daddy gaskiya, But then you said you love
me., All I have to do now is guess, And you
know what my guess is? My guess is that. know what my guess is? My guess is that
guy Mukhtar ne ya shirya wani abu, shi ya
saka akayi forcing dinki a gida akan lallai sai
kin aure shi, shi yasa kika yi min karyar aure
da ciki kika rabu dani because you are been
threatened by him to do so. Ni kuma ba zan
kyale shi ba. I will find out the truth
whatever it is and I will.
......
." Na mika hannu
kamar zan rike shi sai kuma na mayar da
hannun na rungume su a jiki na nace "'it is
not Mukhtar. Shima auren nan ba plan din sa
bane ba it just happened" ya dakata da
maganar da yake yace "you are defending
him? Idan ba shi bane ba to babansa ne, you
once told me ba kya son inje gurin sa
because he wants you to marry his son. Shi
ya shirya wanna kenan? Ko kuma Safina?
Safina can do something like this because
she is a liar and a hypocrite" na girgiza kaina
"'] don't know. I don't have answers a yanzu.
Amma na yadda a hankali komai zai bayyana
to me. Wannan ita ce kaddarar mu
Muhammad, wannan ita ce jarabawar mu. I
am ready to face mine. Kayi mana kokari
dan Allah kayi facing ta ka. I believe ubangiji
yana da dalilinsa na saka wa abubuwa su
kasance haka".
8
15
9:07 PM
Yace "are you telling me to accept Safina as
my wife?" Nayi shiru ina jin ciwon ambaton
sunan Safina da kuma wife da yayi a
sentence daya, Sai kuma nace "I don't
know, Kai kayi making decision na auren
Safina, you deal with it", Safina, you deal with it"
Muka yi shiru na dan lokaci sannan nace
"you should go. We shouldn't be standing
like this. Ni matar aure ce. It is islamically
wrong",. Bai ce komai ba kuma ban kalle shi
ba ballantana inga abinda zuciyar sa take
ciki, na kara da cewa "I wish you best of
luck. Good bye" still bai ce komai ba na juya
ya koma cikin gida.
Direct sama na wuce zuwa dakina, na daga
labule kadan na ganshi still yana tsaye a
inda na bar shi idonsa yana kan kofar da na
bi. Sai kuma ya zagaya ya shiga motar sa ya
ci taya ya bar gidan.
Na saki labulen ina jin idanuna a bushe, a
zuciya ta ina fatan kukan ya kare dan ni
kaina na gaji da yinsa. Na zauna akan gado
ina kallon carpet din dakin, my mind blind.
Sai kuma na daga kai na kalli picture din da
yake facing gadon nawa, picture din Ammi
rike da ni a hannun ta akwance akan gadon
asibiti, fuskar ta dauke da matsanancin farin
ciki, Daddy ya taba gaya min cewa it was
the happiest day of her life. Sai na samu
kaina da mamakin yadda ta iya shiga cikin
wannan farin cikin bayan duk abinda ya faru
a rayuwarta? Bayan duk abinda ta rasa? Sai
na tambayi kaina shin nima watarana zan iya
kasancewa cikin irin wannan farin cikin
nata? Ko shikenan na gama samun nawa
share of farin cikin a rayuwa?
Na sake daga kaina ina kallon ta nace a fili Na sake daga kaina ina kalion ta nace a fili
"how do you do it? How do you looked
beyond your sadness and find happiness?"
Sai na lura da amsar tambaya ta a hannun
ta, Ni, nice farin cikin ta a lokacin, she
looked passed her past and into her future,
sai na fahimci wani abu guda daya, idan har
ina son samun farin ciki sai na daina hanging
onto my past nayi planning future dina, and
to plan my future sai na nutsu na daina kuka
nayi making bold decisions. Just like she
did. Sai na yi taking control of my life, just
like she did.
Na tuno da labarin da ta bawa Daddy, shi
kuma ya bani, labarin decision din da ta
yanke na barin garin su, na barin kowa nata,
na barin komai nata, and starting a new life
a inda babu wanda ta sani, babu wanda ya
santa. But sometimes strangers are better
than blood relatives.
O
Kafin Safiya ta bar gidan Hajiya Kyauta sai
d
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Episode Twenty Eight: The Beginning of a
New Life
Paid Advert
Contact Lame(07036662633)for all your
costumes both oriflameand other special
products that will make ur skin glow and
flawless
Kayanmu lamba daya ne wajen kyau. Sai washegari sannan ta samu damar
assessing situation dinta da kuma mutanen
da take tare da su. Yaran da suka taho dasu
daga Gusau suma kananan yammata ne
kamar ta. Biyu daga cikin su ma basu kai ta
ba. Ta kuma fahimci cewa yanzu ta bar duk
mutanen da ta sani, duk wasu wadanda
suke da dangantaka da uta ta kusa ko ta
nesa, yanxu ta shigo cikin mutanen da basu
santa ba ita ma bata san su ba, babu kuma
wanda ya san tana tare da su, hakan yana
nufin zasu iya cutar da ita ta kowacce hanya
in suka yi niyya. But she didn't care. It was a
great risk, a bold step in her life, but she
took it.
Tasan cewa abubuwa biyu ne zasu iya
faruwa a wannan gari na Abuja, ko dai
rayuwar ta ta juya daga marar kyau zuwa
mai kyau ko kuma ta chanja kalar rashin
kyau din. Sai dai kuma Safiya bata ji toro a
ranta ko kadan ba, wanne kalar shege ne
rayuwa bata nuna mata ba? Bata jin akwai
abinda zai far da ita wanda zai girgiza ta
kuma. And she was ready to face whatever
is coming her way,
Ita dama ta saba making decisions a
rayuwar ta, ta saba taking responsibilities,
tun Baba Hadiza tana da rai sai da yawa
Safiya ce take cewa ayi kaza ko kar ayi kaza
and most of the times Baba Hadiza tana bin
maganar ta ta ne dan ita din ta saba da bin umarnin wasu a tata rayuwar, dan haka
yanzu Safiya bata da damuwar daukan
responsibility and risks a rayuwar ta as she
had nothing more to lose except her life,
and to her, her life doesn't have much value.
Sai da suka ci abinci a gidan suka yi wanka
suka chanja kaya sannan Hajiya Kyauta ta
zauna dasu ta fara yi musu bayanin aikin da
za'a kai su suyi, wadansu daga cikin yaran
already sun taba yin aikin a wani guri dan
haka sun saba, Safiya kuma da bata taba
aikatau na kudi ba itama ta saba da wahalar
rayuwa dan haka bata jin cewa aikin zai
gagare ta.
"Babban abu mai muhimmanci da zaku rike
a aikin nan shine tsafta, kunga mutanen nan
yan gayun nan suna son tsafta ba sa son
kazanta ko kadan, amma kuma basa son su
wahala, dan haka babban aikin ku a gidan
shine ku tabbatar da tsaftar gidan. Aikin da
za'a baku ya danganta da gidan da suka
dauke ku, wasu masu shara da wanke
wanke kawai suke nema, wasu mai kula da
yara, wasu mai wankin kayan yara da guga,
wasu, wasu kuma mai girki. Ya danganta da
hannun wadda kuka fada. In munje a
gabanku za'a yi cinikin kudin da za'a ke
baku, amma kuma ba ku za'a ke bawa ba, ni
za'a ke bawa ina kaiwa iyayen ku. Duk Duk
abinda ya faru a gida ni zan lira a sanar
muku, kuma Icuma dulk abindia ya faru da lau
ni za"a kira a gaya min. Duik wadida tayi sata
ko munafunci ko zalunci za'a kore ta ta
koa garin su babu ruwa na".
Ita dai Safiya tana jinta amma a ranta tasan
babu wani abu da zai mayar da ita garin su,
ba zata koma ba ko da kuwa zata ke kwana
ne akan titi
Bayan sun shirya suka fita gabaki dayan su.
Tun a gidan farko da suka je Safiya ta kara
tabbatar wa da cewa ta shigo birnin tarayya,
dan ita dai bata taba gain irin wannan
gidan ko kuma makamancinsa a garin su ba.
Suka shiga falon gidan suka zauna, sai da
suka yi jira na gurin awa daya sannan matar
gidan ta sauko daga sama, sai a lokacin ta
tashi daga bacci. Ta zauna tana ta bata
fuska da daga hanci sama kamar wadida aka
ajiye mata kashi a gabanta.
10
9
115 AM
"Hajiya Kyauta nace miki ki ringa saka yaran
nan suna yin wanka sosai in zaki zo dasu
gidan nan. Ni zuciya ta saurin tashi take yi
wallahi". Hajiya Kyauta tace "ai kam sunyi
wanka Hajiya, duk babu wadda bata yi
wanka ba, sai dai kawai ace rashin turare
kuma gashi mun shiga rana". Ta fara bin su da kallo daya bayan daya
kamar mai zaben atampa a kasuwa sai ta
nuna Safiya. "Waccan zaki bani. Tafi kvan
gani'"., Hajiya Kyauta ta kalli Safiya tace
"wannan banda ita, akwai yar'uwar ta a
garin nan ita ta aika ni kauyen su takanas na
dauko mata ita" Hajiyan ta bata rai "to ai
kinji, ni duk sauran basu yi min ba gaskiya.
Duk sunyi min kazanta da yawa" Hajiya
Kyauta tace "to ai da sun kwana biyu anan
zaki ga sun gyaru sun koma yadda kike so.
Yanzun rashin kulawa ne ya saka suke haka"
ta sake girgiza kai" gaskiya basu yi kin ba, in
kin koma kya samo min wadansu wadanda
suka fi wadannan kyan gani".
A haka suka tashi suka fita, sai safiya ta
samu kanta da tambayar kanta me vasa
matar ta zabe ta bayan duk sauran yaran
sun fita kyan gani?
Suna fita Hajiya Kyauta ta kuma samar musu
abin hawa tace "gidan Hajiya Maryama
zamu fara zuwa gaskiya, in ba haka ba
wahala zamuyi ta sha, in dai sun ganki cewa
zasuyi ke suke son dauka" Safiya ta
tambaye ta "me yasa?" Hajiya Kyauta tace
"saboda kina da kyau. Shi ido yana son abu
mai kyau, kuma shi abu mai kyau in yana
guri yana disashe kyawun abubuwan da
suke zagaye dashi", Sai Safiya ta samu kanta da mamakin haka,
ita bata taba tunanin kanta a matsayin mai
kyau ba, ita ba zata iya ma fasalta kan ta ba,
ita ba ma zata iya tuna last time da ta kalli
kanta a madubi ba. Ta san dai Baba Hadiza
da Sauda da Khadijah suna da kyau. Sune
mafiya kyawun halitta da ta sani a
rayuwarta.
Daga nan suka tafi gidan Hajiya Maryaman
da aka jima ana gaya wa Safiya. Tun daga
bakin gate din gidan Safiya ta fahimci gidan
ya banbanta da daya gidan da suka baro.
Shi wancan babu kowa sai mai gadi shi
kadai, shi kuma wannan maza ne sun kai su
hudu a bakin gate din suna hira. Daga can
gefe ga wasu samari nan suna buga ball, a
can karshen katanga kuma ta hango wata
mata tana shanya kayan wanki. Wannan ya
tabbatar mata da abinda Hajiya Kyauta ta
fada cewa gidan mutane ne.
Yanayin gidan katon gida ne a tsakiya, sai
kanana a gefe da gefe, inda daga baya
Safiya take fahimtar gurin yan aiki ne maza
da mata. Suka gaisa da mutanen gurin
sannan suka shige ciki. A cikin Safiya ta
tsaya tana kallon haduwa da tsarin gurin,
kujerun falon kadai abin kallo ne haka fentin,
ga kuma sanyin ac da kamshin da ya ratsa
su suna shiga,
Yammata ta gani guda uku a falon a zaune suna kallo a tv, biyu akan kujera daya a
zaune a gabansu, a shekaru ba zasu fi
sa'annin ta ba amma a jiki sun kusa ninka ta
saboda hutu da yanayin cimar su da ta
banbanta. Yammatan suka tsaya suna kallon
su kamar yadda suma suke kallon su, daya
daga cikin su tace "lafiya? Daga ina? Kawai
zaku shigo wa mutane gida ku tsaya musu
aka kuna kallon su?"
Hajiya Kyauta tayi murmushi tace "Hajiyan
tana kusa? Munyi magana da ita tace min
tana gida" dayar ta kan kujerar tace "tana
nan, amma dan Allah kuje waje ku jira ta, in
ta sauko sai ayi muku magana". Suka juya a
jere suka fita kamar yadda suka shigo a jere.
Suka je kuma suka jeru a baranda. Sun jima
a haka sannan Hajiya Kyauta tace '"bara dai
in kira ta a waya in gaya mata nazo, ba zamu
yi ta zaman jiran tsammani ba" Jamila, daya
daga cikin yaran da suke tare tace "to wai
Hajiya su wadannan da suka koro mu waje
yayan ta ne?" Hajiya Kyauta ta girgiza kai
"sai dai yayan yan'uwa ko kanne, Allah bai
taba bata haihuwa ba".
Tayi ta kiran Hajiya bata same ta ba, har duk
suka kosa, sai ga matar da suka gani tana
shanya nan ta zagayo inda suke, suka gaisa
da Hajiya Kyauta sai tayi mata bayanin cewa
Hajiya suke son gani, matar ta shiga ciki sai
gata sun fito tare da yarinyar da suka gani a
zaune a kasa a ciki, matar ta fara yi mata fada "kina kallon mutane sunzo suna son
ganin Hajiya sai ki bar su anan a zaune? Ba
zaki shiga ciki ki duba musu ba? Kin fiso ki
biyewa su Sa'adatu kuyi ta yiwa mutane
rashin kunya ko? To wallahi kin san
15
5
1:15 AM
halin Hajiya ko ki shiga hankalin ki ki kama
kanki ko kuma ta sallame ki zuwa gidan
iyayen ki".
Yarinyar ta zumburi baki tana kunkuni ta
koma ciki. Safiya ta fahimci yarinyar yar aiki
ce. Bata jima ba ta sake dawowa tace "tace
tana zuwa" matar ta ce "to ko ke fa? Yanzu
ba ya fi ba? Amma wulakanta mutum ai
babu dadi" sai kuma ta koma ta kawowa su
Safiya ruwa, suka karba suka yi godiya,
dama duk kishi suke ji.
Matar ta cigaba da zama tare da su tana
taya su hira, sai a lokacin Safiya ta san
sunan sauran yammatan da suka taho tare
dan babu wata maganar kirki da ta hada su
a hanya. Suna nan zaune har Hajiyan ta
sauko. Tun daga inda suke zaune a waje
suka fahimci ta sauko saboda maganar ta da
suka jiyo.
"Waye ya bar remote akan kujera? Sai am
zauna akan sa an balla shi"
"Aka ce nayi baki, Ina bakin nawa suke?" "Aka ce nayi baki, Ina bakin nawa suke?"
"Me suke yi a waje a cikin ranar nan?"
Sai ga yarinyar dazu ta fito da sauri tace su
shiga. Hajiya Kyauta ta dakatar da su Safiya
tace su jira ta fara shiga suyi magana
tukunna. Ta shiga suka gaisa sosai da Hajiya
Maryama, "Hajiya ya kasuwa? Ya kuma fama
da jama'a" Hajiya Maryama tace "lafiya lau.
Ya taki kasuwar da naki jama'ar? Ina fatan
dai kin kawo min yarinya mai hankali, kinga
wannan Lawisan?" Ta fada tana nuna
yarinyar da ta shigo da Hajiya Kyauta "rashin
samun wata ne ya saka har yanzu nake
zaune da ita, bata jin magana kuma bata
girmama mutane, babu abinda ta sani sai
kula maza, duk mazan can na waje samarin
ta ne" yammatan da suke zaune akan kujera
suka yi dariya, ta juya tana kallon su tace
"ku tashi ku bani guri, ina magana kuna bin
bakina da kallo kuna haddace abinda nake
cewa" suka tashi sum sum suka shige ciki,
ita ma yarinyar da aka kira da Lawisa ta tashi
ta bisu.
Bayan sun ta shiga ciki ne Hajiya Kyauta
tace "na kawo miki yarinya Hajiya,
musamman saboda ke na taho da ita Abuja"
Hajiya Maryama ta gyara zama tace
"alhamdulillah. Tana da hankali kenan sosa"
Hajiya Kyauta tace "tana da hankali da
nutsuwa, amma ba wannan ne dalilin da yasa na kawo miki ita ba, na kawo ta nan ne
saboda ita marainiya ce ke kuma na san ke
uwar marayu ce. Bata da uwa bata da uba,
bata da danuwa shakiki ko daya, ba kuma ta
da dangin uwa ko daya, sannan dangin
ubanta basa kaunarta" sai ta bata labarin
abinda ta sani a daga rayuwar Safiya.
Hajiya Maryama tayi shiru tana tunani sai
tace "kira ta in ganta inyi magana da ita
tukunna" Hajiya Kyauta ta leka ta kira Safiya.
Safiya ta shigo kanta a kasa tana kallon
yadda kafafuwanta suke nutsewa a cikin
carpet din falon da ta kasa tantance da me
aka yi shi. Kamar da katifa kamar kuma da
gashin rago.
Ta durkusa daga nesa da su ta gaishe da
Hajiya, Hajiya tace mata "ya sunan ki?" Tace
"Safiya" Hajiya ta kalli ciwon da yake kafar
Safiya tace "ya akayi kika ji ciwo haka
Safiya?" Safiya ta dago kanta tana kallon ta
tace "kusa na taka guda biyu, lokacin da
nake kokarin tono yaruwata da katangar
dakin mu ta fada mata".
Duk hajiyoyin biyu suka bude baki, thinking
about the trauma, dan itama Hajiya Kyauta
bata san yadda mutuwar Sauda ta kasance
ba, Hajiya Maryama tace "ina yar'uwar taki
take to yanzu? An fito da ita?" Safiya tace
"ta mutu. An fito da gawarta daga karkashin kasa, sal aka sake mayar da ita aka binne a
kasan wata kasar a makabarta" suka sake
yin shiru baki daya, sai kuma Hajiya ta sake
tambaya "mamanki fa? Me ya faru da ita?"
Safiya tace "Baba Hadiza, Mota ce ta kade
ta, sanda take gudu zata cecemu ni da
Sauda daga hannun Dauda" suka sake yin
shiru, safiya ta kara cewa "Dauda din yayan
mu ne" ba tare da sun tambaye ta ba,
Sai Hajiya Maryama taji tana son jin cikakken
labarin Safiya, ta tambaye ta, ita kuma ta
bata labari tiryan tiryan a yadda rayuwar ta
ta kasance tun daga kan abinda ta sani na
labarin auren iyayen ta har zuwa rasuwar
Alhaji Haladu da kuma tragedies din da suka
biyo baya.
16
1:15 AM
Bata san tana kuka a labarin nata ba sai da
ta gama taga audience din nata suna share
hawaye sannan ta share nata ita ma. Ta
cigaba da magana "so nake in samu hanyar
da san zamu jari in fara sana'"a, shine naje
grin Hajiya Kyauta ita kuma tace min zata
kawo ni nan in yi aikatau sai in tara kudin da
zan yi jari dasu, Hajiya dan Allah ki dauke ni
aiki, zanyi miki aiki sosai kuma zan ringa
girmama mutane yadda ba zaki kore ni ba, in
na tara kudi sai in gina wa Baba Hadiza
masallaci in roki Allah ya gina mata gida a
aljanna da ladan masallacin". Hajiya ta sauko daga kan kujerar da take ta
durkusa a gaban Safiya tace "zan dauke ki
aiki kinji? Kuma ba zan kore ki ba ko da kinyi
laifi, in kinyi laifi zanyi miki fada in baki
tarbiyya kamar yadda uwa ya kamata ta
bawa yar ta tarbiyya. Kin zama yata daga
yau kinji? Ina fatan nima Allah zai gina min
katon gida a aljanna da ladan rikon da zanvi
miki"
Hajiya Kyauta ta share nata hawayen tace
"Amen Hajiya. Dama nasan zaki karbe ta.
Banyi tunanin kowa ba sai ke. Allah ya dubi
niyyar ki ya baki ikon sauke wannan babban
nauyin da kika dauka" Hajiya tace "Ameen.
Ke ma Allah ya baki ladan taimakon da kika
yi mata da zuciya daya. Da baki dauko ta ba
da yadda zuciyar ta ta bushe din nan
gudawar zata yi ko da kuwa an daura mata
auren ne, kuma kinga da ba'a san hannun
wanda zata fada ba".
Ta juya gurin Safiya tace "zan dauke ki aiki,
zan ke baki albashi kamar yadda bake bawa
sauran yan aikin gidan nan, zanyi hakan ne
saboda ki samu ki cika burin ki na gina wa
mahaifiyarki masallaci da gumin ki, amma ba
zan rike ki a matsayin yar aiki ba, zan rike ki
a matsayin yata, Kuma ina so ki saki jikin ki,
duk wata magana da kika san zaki iyayi da
Baba Hadiza ki zo kivi da ni, in wata shawara
kike nema ki zo gurina, duk wani abinda ya
shige miki duhu ki tambaye ni, duk wani abu da kike bukata ki tambaye ni. Kinji?" Safiya
ta gyada kai tana share hawayen ta, rabon
da ayi mata magana with motherly concern
irin haka tun Baba Hadiza tana da rai, hakan
yasa ta tuna irin yadda take missing
mahaifiyar tata.
Daga nan sai Hajiya ta dauki wayarta ta yi
kira, "Sa'adatu zo ina neman ki". Jimawa
kadan sai ga daya daga cikin yaran da aka
kora dazu ta fito daga ciki ta zauna a kusa
da Hajiya tace "Hajiya ganj" Hajiya tace
"ga
yar'uwa kun samu ke da A'isha, ta zama
kanwar u daga yau" Sa'adatu ta kalli Safiya
ta a yatsina fuska tace
"Hajiya yar'uwar mu
kuma? Ji nake sabuwar yar aikin da aka
kawo miki ce?" Hajiya tace "shi dan aiki ba
mutum bane ba kenan? Ba zai zama dan
uwa ba? So nake kuje ku samar mata kayan
sawan da suka yi muku kadan a cikin kayan
ku, da duk sauran kayan da kuka san zata
bukata kafin in fita in siyo mata. A dakin ku
zata zauna tare da ku saboda ina son ku
kula min da ita, duk abinda tayi ba dai-dai
ba ku gyara mata har ta gane ta saba da irin
rayuwar nan. Kin gane?"
Sa'adatu ta ce "eh" amma daga ganin
fuskarta kasan bata ji dadin maganar ba,
Hajiya ta kara sa da cewa "saura kuma kije
kiyi tayi mata wannan fadan naki da baya
karewa". Ta juya kan Safiya tace "wannan kanwata ce
uban mu daya sunan ta Sa'adatu, daga
yanzu ta zama yayarki. Zata ke kula dake
kamar yadda yaya zata kula da kanwarta. Sai
dai tana da fada" ta karashe maganar cikin
tsokanar Sa'adatu da har lokacin take zaune
fuskar ta a bace. Hajiya tace "ku je ki nuna
mata dakin ku.
Ta juya gurin Hajiya Kyauta tace "to sai
kuma a bani yar aikin"
Sa'adatu ta mike Safiya ta bi bayanta
hannunta rike da ledar da hotan su yake ciki,
wannan ledar ita kadai ce abinda Safiya ta
shiga da shi gidan Hajiya.
Wani dan corridor suka bi sannan suka yi
kwana, sai suka tarar da kofofin dakuna
guda biyu da kuma toilet a tsakiya. Sa'adatu
ta bude kofa daya ta shiga sai Safiya ta bita
amma sai ta tsaya a bakin kofa kanta a kasa.
Babu abinda bata so a rayuwar ta irin a
wulakanta ta, ta kuma lura kamar yammatan
suna da wulakanci. Kallon dai suke cigaba
da yi a dakin a tvn dakin. Daya yarinyar tana
zaune a kan gado, Lawisa tana zaune a
kasa,
6
3
1:15 AM
Sa'adatu ta zauna akan kujerar dakin tace
"Fati ga bakuwa nan inji Hajiya, tace zata
zauna anan a wajen mu. Kuma zata zama kanwar mu" wadda aka kira da Fati ta kalli
Safiya sannan tace "yar'uwar ku ce?"
Sa'adatu tace "ni dai ban san ta ba, ban san
a ina ta samo ta ba, tace kuma mu bata
kayan sawa da abubuwan bukata" Lawisa da
take zaune a kasa tace "yar aiki ce fa, na
ganta tare da wannan matar da tazo"
Sa'adatu tace "ina ruwan ki? Bana hanaki
muna magana kina saka mana baki ba?
Tashi ki fita?"
Lawisa ta taso saura kadan ta bangaje
Safiya sai ta bata guri ta wuce. Tana nan dai
a tsaye Sa'adatu ta bude wardrobe din dakin
ta fara debo kaya tana ajiyewa akan dago,
sai data bata kaya sunfi set goma, har da
mayafai da hijabs, sannan ta bude drawer ta
bata sabulun wanka, tooth brush da paste,
da kuma man shafawa da roll on da turare.
Ta tsaya tana kallon ta sai ta kalli Fati tace
"kuma fa kyakkyawa ce. Gyara kawai take
bukata" Fati ta kalle ta ta tabe baki tace
"fatan dai ba nan dakin zaki ajiye ta ba. Sai
dai ki kata can dayan dakin" Sa'adatu bata
ce komai ba ta saka hannu ta kwashi kayan
tace "debo sauran mu tafi" Safiya ta debi
sauran kayan suka fita suka shiga dayan
dakin. Ta lura kamar dakin ba'a amfani da
shi kamar wancan, amma kuma shima
exactly kamar wancan din yake, Sa'adatu ta
ajiye kayan akan dago tace "ga kaya nan na
baki, ki zuba a cikin wardrobe din nan ki ki zuba a cikin wardrobe din nan ki
ringa sakawa, ga kuma kayan gyaran jiki
suma na baki, kin iya amfani da su?" Safiya
bata ce komai ba sai Sa'adatu ta nuna mata
yadda zata yi amfani da komai, sannan ta
nuna mata yadda zata kunna kayan
electronics din dakin, sai kuma suka fita ta
nuna mata yadda zata yi amfani da toilet,
daga nan ta mayar da ita falo.
Sanda ta koma falo already Hajiya sun gama
maganganun du da Hajiya Kyauta, Safiya ta
fahimci Hajiya ta dauki Jamila aiki itama a
gidan, amma instead of cikin gida da aka
shiga da ita sai aka hada Jamila da Dije,
matar da suka gani a waje, ta tafi da ita
bangaren yan aiki mata.
Hajjya ta tambayi Safiya in ta samu duk
abinda take bukata, Safiya tace "ta bani
kaya masu yawa, Nagode sosai Allah ya kara
arziki" Hajiya tace "Ameen. Tana da kirki ai
da kyauta, sai fada fal cikinta" Sa'adatu ta
tura baki tana kunkuni.
Daga nan suka yi sallama da Kyauta da
sauran yaran, Kyauta tayi mata alkawarin
duk sanda ta shigo Abuja zata je zuwa tana
ganin ta, Ta tsaya tana kallon su har suka
fita daga gate sannan ta juya ta koma ciki, A
lokacin Safiya tana da shekaru goma sha
hudu a duniya, dai dai da shekarun Baba
Hadiza sanda aka aura mata Alhaji Haladu. A hankali Safiya ta fara adjusting to rayuwar
gidan duk da dai ba xata ce babu challenges
ba amma tana jin dadin changes din sosai.
Ita kadai take kwana a dakin da Sa'adatu ta
kai ta, and all the nights she misses her
mother and siblings, wishing suma rayuwa
ta basu irin wanna damar ta kwanciya a irin
wannan gadon da kwana cikin ac a
lafiyayyen dakin da baya zuba ballantana ya
fada a kansu. Kullum ita take fara tashi a
gidan, kafin kuma mutan gidan su tashi ta
gyara duk inda take da access to, tun daga
dakin da take kwana har falo har kitchen da
duk wani daki da ya ke bude ko da kuwa
babu kowa a ciki. So take ta nuna wa Hajiya
irin gwanintar ta dan Hajiyar ta san bata yi
kuskuren daukan ta aiki ba. Satin ta daya a
gidan Hajiya ta dinka musu sababbin kaya
ita da Jamila, sai dai na Safiya yafi na Jamila
yawa.
Ta lura su Sa'adatu suna zuwa makaranta,
kullum da safe zasu tashi su shirya, Dije zata
hada musu breakfast su ci tare da wasu
samari biyu suma data fahimci rikon su ake
yi a gidan, in sun gama driver zai kai su
school, ita kuma zata je ta gyara musu dakin
da suka kwana a ciki sannan ta wanke toilet
din da suka yi amfani da shi,
Farko ta samu challenges kafin ta iya aikin gidan, sai da Dije ta zauna tayi mata bayanin
yadda ake yin amfani da komai sannan ta
iya, a hankali kuma har ta kware. Ta fahimci
cewa Fati yar kanwar mai gidan ce, ita kuma
Sa'adatu kanwar matar gidan.
9
4
1:15 AM
Ta kuma fahimci cewa daga mai gidan har
matar gidan yan kasuwa ne kwararru dan
har sunayin muamala sosai da kamfanonin
kasashen waje.
And she wished that one day she will be like
them....
Jinin su yafi haduwa da Sa'adatu akan Fati,
saboda Sa'adatu tafi fada amma tafi son
mutane, Fati tana da rainuwa musamman da
ta kara fahimtar cewa da gaske Safiya ba
yar uwar Hajiya bace ba.
A gurin Hajiya ma kuma tana samun kulawa
ta musamman dan ko da yaushe in dai suka
hadu sai ta tambaye ta "kin ci abinci? Akwai
abinda kike so? Ki ringa yin bacci sosai kina
hutawa ko kya samu ki dan yi kiba, ga
Sa'adatu nan sai hawa take kamar fulawar
da aka saka wa yeast". In Sa'adatu taji haka
sai ta kara kumbura,
Ranar nan tana dakin da su Sa'adatu suke
tana yi mata tsifa, sun kulla kallo a tv suna yi
ga wayoyi ana ta chatting da kawaye ana ga wayoyi ana ta chatting da kawaye ana
shirya irin hidimar da za'a yi a birthday din
wata kawar su da yake zuwa soon. Hajiya ta
shigo ta tsaya a bakin kofa tana kallon su
tana kuma jin irin hirar da suke yi ba tare da
sun ga shigowar ta ba. Sai da suka gama
sann6ta karasa shigowa ta kuma kama fada.
"Kun ganku yaran nan sai kunyi wa kanku
fada fa. Rayuwa ba zata tafi muku yadda
kuke so a haka ba. Ku baku da tunanin
komai sai na jin dadin duniya? Ya kamata
ace zuwa yanzu kun fara tunanin yadda
zaku ke juya biyar tana komawa goma.
Rayuwa bata da tabbas. Kamata yayi ace
kun fara tunanin wata sana'ar hannu ko wani
kasuwanci da zaku iya fara wa tun kafin ku
gama secondary school. Hausawa sunce da
zafi zafi ake dukan karfe"
Sai duk su biyun suka kwashe da dariya
"haba Hajiya, wacce sana'a ce zamuyi ne
wai? Sai kace wasu maza" "mu kam ai sai
dai a nemo a kawo mana. Soft life kawai"
Hajiya ta bude baki "soft life? Kawai dai
kuce min cima zaune na tara a gida na. To
Allah ya sawake muku. Amma dai sai kun
sake tunani tun kafin lokaci ya kure muku,
Ko irin dan cin cin din nan ne da zobo ku
ringa yi mana kuna tafiya da shi makaranta
kuna siyarwa" Sa'adatu tace "cin cin fa kika
ce Hajiya? Haba dai! Wuce nan mana""Safiya dai bata ce komai ba har Hajiya ta
fita, sai data gama tsefewa Sa'adatu kitson
ta sannan ta fita tana neman inda Hajiya
tayi, a falon ta na sama ta same ta waya da
dealer din da zai kawo mata abayas. "A
sabon shagona zan saka su, kaga kuma
zuwa nan da two weeks nake son bude shi.
Dan Allah kar saba min alkawari".
Safiya ta zauna a kasa sai da ta gama wayar
sannan ta kalle ta cikin kulawa tace "Safiya?
Kina bukatar wan abu ne" Safiya ta gyara
zama tace "maganar sana'a da naji kina
yiwa su Sa'adatu. Kina gain nima zan iya
yi?" Hajiya ta gyara zamanta tace "ba su
Sa'adatu nake yiwa maganar sana'a ba, har
da ke kema, gabaki dayan ku nake yiwa. Da
akwai sana'ar da kike gain zaki iya farawa
yanzu?"
Safiya tayi shiru tana tunani sannan tace
"a
garin mu dai tun bayan rasuwar Baba ni da
Baba Hadiza muna yin awara da kuma wake
da shinkafa muna siyarwa, ban sani ba ko
anan zasu siya?" Hajiya ta dan yi shiru tana
tunani sai tace "gaskiya bani da tabbas din
zaki yi cinikin wake da shinkafa anan, Amma
ina saka ran zaki vi na awara tunda abin
sha'awa ce." Ta sake yin shiru sai kuma tayi
murmushi tace "kin san wani abu. I have a
plan for you. Ki rubuta min duk abinda kike bukata na yin sana'ar awara ni kuma zan
siyo miki. Zaki iya yin aikin dahuwar awarar a
can filin baya, sai mu aika duk makota zan
kuma yi miki talla a gun customers dina, sai
a ringa sakawa a robobi ana aikawa ko'ina"
Safiya tayi murmushi tana jin dadi "Nagode
Hajiya, Nagode sosai " hajiya tace "and that
is not all, zan bude sabon shagon da zan
ringa siyar da fabrics na mata, da sauran
ado na mata, zan dauke ki aiki a matsayin
sales girl din shagon, zan hada ki da
yarinyar da already na riga na dauka sai kuyi
akin tare ki koyi harkar yadda ake gudanar
da business" Safiya tayi shiru tana kallon ta
tace "amma Hajiya already kin riga kin
dauke ni aiki anan gidan ai, ko kora ta kika yi
daga akin gidan?" Hajiya tace "ban kore ki
ba kuma ba zan kore ki ba, ko baki san ana
yin aiki biyu a lokaci daya ba? And also
concerning aikin gidan nan, Dije tace min
kusan komai ke kike
14
1:15 AM
yi, maybe shi yasa har yanzu kika gagara yin
kiba, daga yau na ware miki aikin ki,
bedroom dina da nan falon su kadai ne naki.
In kika yi kika gama sai ki tafi zaman shagon
ki, in kin dawo da yamma sai ki dafa awarar
ki, are you up to the task?" Safiya tayi shiru
dan bata gane karshen ba, Hajiya ta
maimaita mata "zaki iya yin hakan?" Da sauri ta gyada kai "zan iya Hajiya, sosai ma".
And that was how it began.
Ana bude shagon Safiya ta fara aikin zaman
shago, kullum da assuba tana tashi zata hau
saman Hajiya, dama kuma Hajiya ba'a dakin
ta take kwana ba tana dakin Alhaji. Dan haka
dakin nata bashi da datti gyaran sa babu
wahala, cikin kankanin lokaci Safiya take
gamawa sannan ta sauko ta gyara nata
dakin tayi wanka ta shirya taci abinci ta debi
na rana ta tafi shago. A can take wuni sai
la'asar take dawowa gida sannan tazo ta
dora dahuwar awarar ta. Ta kan dafa da
yawa wani lokacin ta yi freezing sai take
daukowa tana soyawa ana zuwa ana siya
daga gida gida. Yadda take cinikin awarar
har mamaki yake bata. Tana kuma diyar da
danya, idan mutum yafi so ya soya da kansa
a gida. Har a shago idan customers sunzo
takan yi musu tallan awarar ta, daga baya
sai ta fara soyawa tana tafiya da ita shagon
ma tana siyarwa a can.
Da lokacin albashi yayi Hajiya ta lissafa
kudin albashin ta na aikin gida ta bata a
hannunta, Sannan ta sake lissafa kudin
albashin zaman shago ta sake bata, Sai ta
tsaya tana kallon kudin kawai dan dai ita
bata taba gain kudi masu yawan wadannan
ba. A garin su ko masu aikin gwamnati jin suna daukan wanna kudin. Ta tashi ta je ta
dauko kudin ribar awarar ta da take tarawa
ta kara su akan albashin nata. And the first
thing that came to her mind was wacce
hanya zata bi ta juya wadannan kudaden su
kawo mata wasu?
Maman Maama
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Episode Thirty: Safiya Khalid


Not Edited
Kwana biyu bayan nan Adam ya dawo da
duk takardun da zasu tabbatar da
yarjejeniya, Hajiya still bata amince ba sai da
ta dauki Safiya suka tafi a motar Adam din
zuwa gurin lawyer din da yake gudanar
musu da most legal services din su ita da
Alhaji.
Adam yana driving Safiya tana gefensa
Hajiya tana baya sai ya fara yiwa Hajiya
korafi. "Shekara nawa muna business da ke
Hajiya, amma duk nuna wa kike yi kamar
baki yarda da ni ba. Ni ma fa zan saka kudi
na acikin harkar nan, wallahi in kika ji yawan
kudin da zan saka sai kin yi mamaki, I only
want to make sure cewa the whole 30%
comes from me bana son wani ya shiga cikin
maganar yayi hijacking komai daga gare ni
shi yasa nake nema a cikin mutane na"
Hajiya tana murmushi tace "na gaya maka
ba kai ne ban yarda da kai ba, su ne ban
yarda da su ba. Kuma idan da ace kudi na ne
da bazan tayar da hankali na akai ba, but
that girl sitting beside you is the most
hardworking person da na taba gani a
rayuwata. She went through a lot, more than
abinda mutane da yawa zasu iya dauka a rayuwa. Ta sha wahalar rayuwa ba kadan ba,
ta kuma sha wahala wajen gain ta tara
wadannan kudaden da ta basu. Shekarar ta
goma ko baccin kirki ba ta yi saboda ta
cimma burinta, and I won't let her effort go
to waste" yana kallon Safiya yace "I don't
understand the ta sha wahala da kike fada,
ba ta yi kama da wadanda suke cikin wahala
ba, plus she is born rich ba irin mu da muka
fara kasuwa from the scratch ba" Hajiya
tace
"oh, you are judging a book by it's
cover. Wannan yarinyar da kake gani
marainiya ce, babu uwa babu ba babu
dangin uwa babu dangin uba, ko kuma in ce
useless dangin uba, sanda ta shigo Abuja
kayan da suke jikinta ma bata su aka yi ta
saka ba nata bane ba. Ko kwandala bata da
ita. And she worked and pulled herself up.
Duk kudin da kaji ta ambata da bakinta cewa
tana da su da gumin ta ta hada su".
Ya dan yi slowing down yana kallon Safiya
suka hada ido sai ta juya kanta tana kallon
window. Yace "I thought yarki ce fa, ko niece
haka" Hajiya ta gyada kai "yata ce a yanzu.
She is the closest thing I have to a
daughter" tun daga nan jikinsa yayi sanyi
kuma ya fara thinking twice akan maganar.
Suna yin packing a gaban office din lawyer
din da zasu dauka ya juyo yana kallon Safiya
"do you still want to go ahead with this ko
kin chanja shawara?" Ta dan kirkiri
murmushi, ta lura maganganun Hajiya sun
sagar masa da guiwar sa sai tayi kokarin
lightening up the atmosphere, tace "kar ka zama ragon maza mana Adamu, fargaba aka
ce asarar namij" ya bude ido "wannan
wanne irin sabo ne, Adamu fa kika ce, Adam
sunana ba Adamu ba" tace "Adamu zan ce
nikam. And remember I am your partner now
dan haka you should get use to Adamu"
yace "gaskiya ki samu ruwa a kusa ki
kuskure bakin ki ki hada da istigfari, sunan
Annabi guda kike bata wa, ko kin taba jin
ance annabi Adamu?".
Hajiya da take baya tace "kunga, ni ina da
abinyi, ku taho muje muyi sauri mu gama
abinda ya kawo mu. A office din lawyer din
aka sake maimaita bayanai ya karbi katardun
da Adam yayi drafting ya yi modifying using
legal terminologies kowa ya amine sannan
aka saka hannu. Da aka zo rubuta suna ne
Safiya ta fadi sunan ta "Safiya Haladu"
Adam ya yi dariya ta tsaya tana kallon sa
tana tunanin menene abin dariyar, yace "no
wonder! Yanzu na gane dalilin da yasa kika
ce min Adamu. Ashe ashe bakin ne ya riga
ya saba" ta bata rai "sunan baban nawa
kake yiwa dariya?" Ya girgiza kai "ke nake
yiwa dariya da baki iya fada dai dai ba.
Khalid ake cewa ba Haladu ba",
Ta juya tana kallon lawyer "kaga rabu dashi,
dan na ce masa Adamu shine yake ramawa.
Rubuta min sunana ka bani in saka hannu"
lawyer yace "amma fa nima ina goyon
bayansa. This is a new beginning, a new life,
it warrants a new name" ta girgiza kai "
have been using Haladu all my wife, credentials dina duk haka ne a jiki, I cannot
change it for this only, in na chanja sunan I
have no evidence to claim cewa nice"
lawyer ya gyara zama yana kallon ta proudly
yace "daga dukkan alama kin manta a office
din wanda kike.
6
3
9:04 PM
I can do all that for you in kina so" ta juya ta
kalli Hajiya alamar shawara, Hajiya tayi mata
murmushi tace "Safiya Khalid suits you
more, kuma it is still his name" ta juya ta
kalli lawyer din tace "ubuta" sannan ta kalli
Adam da yayi sauri yace "yes!" Tace "ba dan
ka fada bane ba fa, dan Hajiya ta fada ne.
And you are still Adamu".
A cikin sati biyu komai ya kammala. Aka
gama duk cike ciken da za'a yi Adam da
Safiya suka hada kudi jointly suka sayi 30%
share na kamfanin mining and processing of
gold wanda a lokacin ko official suna bashi
da shi. And with their share kamfanin suka
sami permit din da suke bukata dan fara
operating a Nigeria. But sun gayawa Adam
dama cewa it will be a long journey kafin
komai ya daidaita. Yanzu babu abinda Adam
da Safiya zasu yi sai dai su jira, su kuma
cigaba da addu'a.
Wannan contract din was what firstly
brought them together, amma kuma ita din
kawai agent ce da Allah ya aiko gare su, for
they are meant to be together. Tun daga ranar da Safiya ta shiga falo ta ga
Adam a gaban Hajiya, tun daga ranar
rayuwar ta ta kuma taking another turn.
Bayan turn din tattara kudin ta da tayi ta
bashi blindly, sai kuma turn din yadda shi
kuma ya makale mata kamar cingam. Da
farko ta dauka he is just after the money, so
yake a gama hidimar signing contracts din
and he will go back to his life ya barta sai
kuma in wani abin ya sake tasowa da yake
bukatar ta a matsayin ta na partner din shi.
But she was wrong. Tarkon da bata san
sanda ta dana shi ba ya riga ya kama Adam,
and he wasn't even trying to escape, he was
comfortable and even glad cewa tarkon ya
kama shi. And ga mamakin ta bata ji
repulsion din6da takan ji ba a duk sanda
wani namiji ya gwada irin abinda Adam yake
gwadawa yanzu a kanta. She was glad that
tarkon na ta ya kama shi.
Gidan Hajiya ya zama gidan zuwan Adam,
Abuja ta zama gurin zamansa duk kuwa da
cewa most of his businesses a Kano suke.
Kullum in yaje gidan sai ya fara kame kamen
yazo zai kara yi mata bayani ne akan
yarjejeniyar da suka kulla, in yana fadawa
Hajiya haka sai kawai tayi ta nodding kai
tana jin sa, in ya gama tace "haka fa" daga
baya dai ranar nan da yazo yana ta yi mata
dogon bayani da ta bashi wani bombastic
side eye sai yaja bakin sa yayi shiru mid
sentence, amma kuma fuskarsa dauke da
murmushi dan ya fahimci ta gane inda ya dosa, tace "Please Adam spare me da
wannan dogon bayanin, idan kazo gurin
Safiya l am sure you have her phone
number, call her kuje can akwai gurin da
yamma tan gidan suke saukar samarin su ku
zauna a can. Spare me please" yana cigaba
da murmushi yace "okay, to bara in kira ta"
sai ya tashi ya fita waje.
An jima kadan sai gata nan itama ta fito, ta
zauna a gaban Hajiya tana lissafa yatsun
hannunta "Hajiya dama,......
. Adamu ne
yazo…………yace wai akwai wata takarda.....
Hajiya ta nuna mata waje "tashi kije yana
waje yana jiranki. Wai ni yaran nan me suka
mayar da ni ne? Yarinya karama suke son
mayar da ni ko me?" Sa'adatu da tun
shigowar Adam take kwance akan kujera
tana danna wayarta ya juyo tana yiwa Safiya
dariya tace "business partner din ne yazo?
To manyan yan kasuwa maza aje a cigaba
da tattaunawa akan business" Safiya ta
harare ta ta fita tana murmushi.
A gaban motarsa ta same shi a tsaye, ya
taho shima suka hadu a hanya yace "ina
yake?" Tace "me?" Yace "zobo na" tace
"yau ba zobo zan baka ba, yau konon aya
nayi maka mai dankaren dadi, amma sai ka
kawo kudi" ta fada tana mika masa
hannunta da yasha zanen lalle. Ya fara
laluba aljihun sa sai kuma yayi ajjiyar zuciya
"a bani bashi. Zan biya" ta bata fuska "ni
bana bada bashi, amma tunda dai sunan ka
Adamu zan baka, amma sai ka rubuta sunan ka ka saka hannu ka kuma rubuta ranar da
zaka biya" yace "ko na rantse zan biva ma
ba za'a bani ba? I promise you zan biya ki.
Wata rana. Ke dai ki jira kawai ki gani".
5
1
9:04 PM
Watanni suka wuce. Safiya bata yi folding
arms dinta tana jiran maganar kamfani ta
tabbata ba, ta cigaba da managing sauran
30% na kudin ta da Hajiya ta tabbatar bata
zuba all her eggs in one basket ba. Ta
cigaba da zaman shago, ta cigaba da
hustling musamman yanzu ba bata Zuwa
makaranta tana da all the 24 hours to
herself. Sannan kuma gashi yanzu tana
samun shawarwari da kuma ideas daga
gurin Adam. And sometimes manly taimako.
Yanzu indai yana gari yana taimaka mata da
shiga kasuwa da sauran guraren da yake
ganin are too risky for her.
Wasa wasa soyayya mai karfi ta kullu a
tsakanin su. Kamar yadda safiya bata taba
yiwa kowa karya akan asalin ta ba haka
shima Adamu bata yi masa karya ba, cikin
lokaci kankani ya san komai a kanta, labarin
Baba Hadiza kuwa sai da ya bawa wani dan
duk zuwan da zaiyi sai ta bashi kuma duk
wayar da zasu yi sai ta ambace ta,
Abinda ya kara karfin soyayyar su kuma
shine fashion da suke da shi iri daya, fashion
for business, Yes, suna soyayya amma
mostly hirar su ta harkar business ce suna sharing ideas suna bawa juna shawara.
Zuwa lokacin ita ma ta san abubuwa da
yawa akan sa. Ta san dan kano ne shi kuma
he started his business from the scratch. Ba
wai haihuwar sa aka yi into the money ba. A
yadda yake gaya mata abinda ya fara
siyarwa a duniya shine rake, rake ya fara
siyarwa a layin su tun yana dan primary
school, daga wanna sana'ar ya koma
waccan daga waccan ya koma waccan har
wani abokin babansa ya dauke shi jiran
shago a kasuwar sabon gari. And that was
where his gold business started.
Shi wanda yake jire wa shagon sarkokin gold
yake siyarwa, a hankali ya fara koyan
business din shima, kuma yayi sa'a
ubangidan nasa bashi da son bakin hali and
he showed him the way har shima ya samu
nasa jarin ya fara. Farko a cikin dan akwati
yake zuba sarkokin sa yana yawo dasu yana
siyarwa, daga baya ya fara samun
connections da matan manya yana kai musu
har gida suna siya, gari gari babu inda baya
zuwa, gidajen yan siyasa da duk masu
kwandala ya sani kuma he talked his way
into the houses ya kuma siyar musu da
kaya. A haka ya samu fada sosai a tsakanin
manyan da yake business da su, a haka ya
bude nasa shagon ya saka kaninsa Ahmad a
ciki shi kuma ya cigaba da yawo gari gari,
daga baya yawon nasa ya koma kasa kasa,
he opened his next shop in Kaduna, wanda
yana daga cikin abubuwan da ya siyar to get
the contact, and another one in Abuja, Shagon da Hajiya tayi wa Safiya bargaining a
bata partnership a ciki. Sai dai a yanzu
Safiya bara san inda zata samu kudin da
zata saka a cikin shagon ba.
Adam bai yi karatu mai zurfi ba amma yana
da gogewa sosai saboda yawn muamala da
yake yi da mutane. Ya iya mu'amala da
mutane. Kuma Safiya ta fahimci cewa he is
very smart, principled and trustworthy. Yana
da gaskiya sosai. And she felt safe with him.
Sai dai kuma watanni bayan haduwar su he
stated growing impatient akan maganar
kudaden su da suka bawa kamfanin da ko
takamaiman suna bashi ba shi.
"'Safiya tsoro na ke ji. What if Hajiya ta fi mu
gaskiya? What if suka gudu da kudin mu?
Yaya zanyi kenan?" Safiya tayi dariya "then
we will work and get another money. Kudi ne
fa ba wani abu ba" yana girgiza kai yace
"kudi kuwa sune wani abu. Kin manta duk
wahalar da kika sha kafin ki same su? Ji
nake da kanki kike bani labarin yadda kike
dashi tun kafin asuba ba kuma zaki koma
bacci ba sai dare yay nisa?" Tayi ajjiyar
zuciya tace "ka san me? Da gaske naso yin
kudi, but I never thought zan yi din, Actually,
a ranar da Sauda ta rasu I never thought zan
sake kwana a duniya. Daga nan kuma sai na
koma tunanin ba zan kai shekara ba, and
now shekara goma kenan har da watanni da
mutuwar Sauda and I am still alive. Duk a
cikin wadannan shekarun I was just living kamar a mafarki. Har yanzu ji nake kamar
zan iya farkawa at any moment in tarar cewa
mafarki nake yi ashe. I am living a far better
life than I have ever imagined. So for me, I
am just waiting for the death to catch up
with me" yayi sauri yace "kowa ma a duniya
haka ne. Duk ita muke jira.
) 2
9:04 PM
So ke kina so ki ce min baki da wani plan for
the future? What were you aiming at sanda
kika fara sana'a?"
Tayi shiru tana kallon bango, deep into her
thoughts, sannan tace "Ina da dream for a
future. A future were I will have a legacy, a
legacy in form of kids, princes and
princesses that I will raise with love and
protect with my life. A cikin wannan
mafarkin my kids will lake for nothing, they
will never know fear, they will never know
loneliness, and they will never know poverty.
Ina so in haifi yaya, lots and lots of yaya"
Adam yayi gyaran murya, ta juyo tana kallon
sa sai kuma taji kunyar cewa tana maganar
haihuwa a gaban sa, ta rufe fuskarta da
hannunta, yayi murmushi "yanzu dai kina
nufin in kara zage damtse kenan gurin
neman dukiyar da zan kula da ke da
wadannan princes and princesses din da
za' a haifa min" ta bude fuskar ta tace "don't
worry, we will take care of them together"
ya girgiza kai "no. Idan muka yi aure kina da
damar neman all the halal money that you can get, but it will be my duty to take care of
you and all the kids we will have"
Wasa wasa magana tayi karfi tsakanin Adam
da Safiya, har ya fara maganar taking their
relationship to the next level, ma'ana aure.
Sa'adatu Safiya ta tura ta gaya wa Hajiya,
Hajiya ta nuna jin dadin ta sosai dan dama
tun sa da ta gane abinda yake tsakanin su
taji dadin hakan dan tasan Adam mutum ne
mai hankali da nutsuwa da kuma kokarin
neman na kansa. Ta fahimci sun matukar
dacewa shi da Safiya.
Aka bawa Adam damar a turo kuma ya turo
din, sai dai bayan maganar da mahaifansa
suka yi da Alhaji sai suka nuna cewa suna
son zuwa suga asalin dangin Safiya. Anan
ne kuma rigimar ta tashi, dan ana gaya wa
Safiya abinda suka ce tace ta fasa auren.
Wannan ba karamin daga hankalin Adam
yayi ba. Babu shiri ya baro Kano ya taho
Abuja. "Safiya dan Allah. Kawai so suke yi
suje suri tracing asalin ki shikenan. Ba wai
acan za'a nemi auren ba, Alhaji zai iya bamu
auren, amma Baba ya dage sai an je can
tukunna" tace "saboda me?" Yace "saboda
gaba. Aure zamuyi, Zuri'a muke da burin
samu. Dole zasu bukaci sanin asalin
mahaifiyarsu" ta girgiza kanta da sauri "idan
ka gan i a garin nan to gawa ta aka kai. Idan
ka ga yayana a garin nan to bana duniya.
And ko bana duniya I want you to promise
me ko hanyar garin ba zasu bi ba". Yace "ba zasu je ba in ba kya so. Ke ma kuma ba zaki
je ba tunda ba kya so. Su Baba zasu je
amma. I just don't want them to go ba tare
da na gaya miki ba shi yasa na gaya miki din.
Kin amince su je din?"
Tayi shiru tana kallon sa, wata zuciyar tana
gaya mata ta hakura da shi gabaki daya,
wata zuciyar tana gaya mata ta hakura da
auren ma gabakidaya. But when she opened
her mouth she heard herself saying "idan
nace kar su je zasu bari ayi auren ba tare da
sunje din ba?" Ya girgiza kai "I am afraid no"
And love over powered Safiya's hatred for
her family, she let them go.
Hajiya ce ta yi magana da Hajiya Kyauta, ita
kuma while still insisting bata son a san ita
ta dauki Safiya, ta basu address din gidan
baban Safiya a garin Kura da kuma gidan
kanin baban ta., Suka je har can din suka yi
tambayoyin da suke bukata suka tabbatar
da kasancewar ta yar garin kuma yar Alhaj
Haladu sannan suka dawo suka cigaba da
neman aurenta a gurin Alhaji Nasiru,
A hankali hidima ta kankama, aka kawo duk
abubuwan al'ada dai da gwargwado aka
saka rana aka gama komai. Adam ya samu
gida ya kama musu rent anan Abuja dan
baya son ya rabata da kasuwancin ta, shima
kuma yanzu yafi mayar da hankali akan
shagon sa na nan Abuja, na kanon mostly
kaninsa Ahmad ne yake handling.

Suma kuma su Hajiya Maryama da Alhaji
Nasir sunyi namijin kokari wajen zubawa
Safiya kayan daki na fitar kunya, yayin da
Sa'adatu ta shiga ta fita ta tabbatar cewa
bikin ya tsaru ya zama very unique and
classy babu wanda zai kushe sai dai idan
hassada ce yake yi.
3
2
9:04 PM
Safiya ta so ta fitar da kudi ta yiwa kanta
gata, amma Hajiya Maryama tace babu
abinda zata yi wa kanta "wannan auren da
zamuyi miki shine last gatan da zamuyi miki,
daga wannan karon kin bar hannun mu
kuma bama fatan ki dawo. Kin koma hannun
mijin ki, amma still ina son ki sani cewa
muna nan anan gidan babu inda zamuje a
duk sanda kike bukatar wani abu ko wata
sharawa ki zo muna maraba lale da ke".
Safiya tamkar ya take a gurin Hajiya
Maryama. In har ba maganar kuka taba yi da
ita ba ba zaka san ba uta ta haife ta ba. Duk
wasu harkokin ta ita take dorawa akai. Duk
inda zata je da ita take zuwa. Ranar nan ma
da zata je gidan ambassador Muhammad
Dikko, da ita taje,

Anan gidan Alhaji Nasiru aka daura auren
Safiya, shine waliyyin ta. Da dare kuma aka
kai Safiya gidan mijinta. A lokacin tana da
shekaru ashirin da biyar a duniya, A ranar
Safiya tayi kukan da rabon da tayi irinsa tun
kafin zuwan ta Abuja. Kukan rabuwa da
Hajiya da kuma Sa'adatu, ta yiwa Hajiya Safiya ta so ta fitar da kudi ta yiwa kanta
gata, amma Hajiya Maryama tace babu
abinda zata vi wa kanta "wannan auren da
zamuyi miki shine last gatan da zamuyi miki,
daga wanna karon kin bar hannun mu
kuma bama fatan ki dawo. Kin koma hannun
mijin ki, amma still ina son ki sani cewa
muna nan anan gidan babu inda zamuje a
duk sanda kike bukatar wani abu ko wata
sharawa ki zo muna maraba lale da ke".
Safiya tamkar ya take a gurin Hajiya
Maryama. In har ba maganar kuka taba yi da
ita ba ba zaka san ba uta ta haife ta ba. Duk
wasu harkokin ta ita take dorawa akai. Duk
inda zata je da ita take zuwa. Ranar nan ma
da zata je gidan ambassador Muhammad
Dikko, da ita taje.
Anan gidan Alhaji Nasir aka daura auren
Safiya, shine waliyyin ta. Da dare kuma aka
kai Safiya gidan mijinta. A lokacin tana da
shekaru ashirin da biyar a duniya. A ranar
Safiya tayi kukan da rabon da tai irinsa tun
kafin zuwan ta Abuja. Kukan rabuwa da
Hajiya da kuma Sa'adatu, ta yiwa Hajiya
kuma adduoin da sai da suka saka ita kanta
hajiyan kuka tare da duk wanda yake gurin,
A haka Hajiya ta rungume ta ta kaita dakin
mijinta tana matukar jin dadi a ranta, ita ta
san Safiya a gurin ta investment ce,
investment din da ba a duniya zata samu
ribar sa ba, a lahira ne,[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: A big sorry to those that waited for
Safiyya yesterday
owner
A big thanks to those that checked up on
me
Some things cannot be explained.
21
6:49 AM

Safiyya
Episode Thirty One: The Legend
Safiya became very emotional tun da aka
kaita gidan miji, tun daga kukan rabuwa
da Hajiya kuma shikenan sai ta zarce
kullum kuka ta bar ango da aikin rarrashi,
amma shi ya fahimci zuwa lokacin ba wai
auren take yiwa kukan ba ko kuma
rabuwa da Hajiya ba, loneliness ne yake
damunta, tana missing din familyn ta
sosai. Ta koma kullum sai ta yi hirar su,
kuma da ta fara sai hawaye, Adam ya
fahimci abin nata har da survivors guilt, a
zuciyarta tana feeling guilt na cewa su
sun mutu ita kuma tana raye, and she is
living the life that idan da ace suna raye
ba lallai ne ta samu wannan rayuwar ba.

One week after the wedding ya tashi da
safe ya neme ta a dakin su ya rasa, yayi ta
zagaya gidan yana neman ta sai can ya
samo ta a backyard dinsu tana zaune a
kasa ita kadai tana kallon flowers din
gurin, ya je ya zauna a kusa da ita ba tare
da yace mata komai ba. Sun jima a haka
sannan ta juyo tana kallon sa da idanunta
da suka kumbura saboda kuka tace "da
kai aka je Kura ko su Baba ne suka je su
kadai?" Yace "da ni aka je" ta juya ta
cigaba da kallon flowers din sannan a
hankali tace "ina so zan je. In ka yarda".
Ya saka hannu ya jawo ta kan kafadarsa
sannan ya zagaye ta da hannunsa guda
daya yace "of cause we will go in kina son
zuwa, just tell me yaushe kike so muje" ta
kara kwanciya a jikinsa tace "jibi" suka
saka yin shiru zuwa wani lokaci sannan
yace "I saw the rooms, na ga dakunan da
suka fadi. Kasar tana nan har yanzu" tace
"I want to see it".
Kwana biyu bayan nan suka dauki hanyar
Zamfara da sassafe, dan tun kafin asuba
tayi suka fita sai a hanya suka tsaya suka
vi sallah. Su kadai kuma babu wanda suka
gaya wa. The drive was joyous as well as
emotional for Safiya saboda tana jin dadin
companion dinta amma kuma tafiyar tana
tuna mata tahowar da tayi zuwa Abuja
over 11years ago, a hanya hirar da kawai
take bashi, ranar har da hirar Baba and
the little she can remember about him musamman irin soyayyar da ya nuna mata
ita da yan'uwan ta. They talked about
yadda irin auren Alhaji Haladu da Baba
Hadiza yake random a cikin al'ummar mu
da kuma yadda irin auren yake affecting
zumunci a tsakanin yan gida daya. It is
halal tabbas, amma wata halal din ana
barin ta ko dan kunya da abinda zata
haifar nan gaba. Wani ma sai yayi retire,
da kudin gratuity dinsa zsi je ya auro yar
karamar yarinya ta zo kuma ta fara
haihuwa bayan sun gama girma matansa
kuma sun manyanta, sai kuma yazo ya
biye mata yayi ta yarinta yana bakanta ran
matansa da yayansa, wannan kuma sai ya
kara hura wutar kiyayyar amaryar da
kuma yayanta a zuciyar wadancan. A
karshe ya mutu ya bar baya da kura.

Su kuma yayan da aka haifa basu da laifi,
amma a karshe sune suke paying price
din abinda ba su suka siya ba.

Karfe 10 na safe a Gusau tayi musu, anan
suka tsaya suka samu wani eatery suka ci
abinci sannan suka dauki hanyar Kura.
Few minutes after that suna garin Kura,
Tun da suka shiga yayi slowing down yana
tafiya a hankali ita kuma tayi shiru tana
karewa garin kallo, nothing much has
changed tun barinta garin, except for few
houses da taga an gina an ld wadansu an
sake musu fasali zuwa na zamani amma babu wani major change a garin, dan haka
tar take gane hanya tiryan tiryan har kofar
gidan su.
Abinda ta fara gani shine tarin kasar da ta
kasance ita ce dakin da tayi spending
most of her childhood in. She could still
feel the moist, dark and suffocating
nature of the rooms, their laughter
together ita da kannnenta da Baba
Hadiza, sheshshekar kukan su idan suna
cikin bakin ciki, ta rufe idonta tana tuno
sound din kukan Khadijah sanda bata da
lafiya "Baba Hadiza ki kaini asibiti bani da
lafiya". Ta bude idonta tana jin echo din
hun Sauda a lokacin da mota ta kade
Baba Hadiza.
Ta juya da sauri ta kalli gurin, a idonta
tana gain gizon sanda motar ta daki
Baba Hadiza ta tashi sama sannan ta fado
kan kwalta. Ta tuna da yadda jini ya ringa
fita daga kan ta, yadda jinin ya jika ta ita
da Sauda. Ta bude tafin hannun ta tana
kallo, kamar mai kokarin gain jinin a jikin
hannun.

Adam ya saka hannun sa cikin nata yana
kallon yadda hawaye yake bin fuskarta
yace "kina so mu koma?" Ta girgiza kan ta
"no" sai ta cire hannun ta daga cikin nasa ta bude kofar ta fita.
Sai a lokacin ta lura da cewa mutanen
unguwar kusan kowa da yake gurin a
lokacin motar ta su yake kalla, irin anga
bakuwar mota ta tsaya kuma ba'a san
waye a cikin ta ba. Ta juya tana kallon inda
suke suyar awarar su ita da Sauda, a kofar
gidan makota, saboda basu isa su yi a
kofar gidan su ba.
Ta taka a hankali zuwa kofar gidan ta
shiga soron, yana nan shima yadda ta
sam shi sai dai ya kara lalacewa, katangar
duk ta tsatstsage, rufin ya taho zai fadi sai
itace aka saka aka tokare shi. Langa
langar da aka saka aka raba soron gida
biyu babu ita, haka jakankunan kayan su
da ta bari a wajan babu su suma. Daga
dukkan alama soron ma ba'a amfani da
shi yanzu dan dakunan su da suka fada
kuma ba'a gyara ba sun saka gidan ya
zama bashi da takamaiman mashiga.
Ta shiga tsakar gida tana bin gidan da
kallo, daga dakin da yake farko, dakin da
nan ne inda yake na Baba Hadiza sanda
Alhaji Haladu yana da rai, dakin da a ciki
aka haife ta taga wata mata da bata sani
ba ta fito ta a kallon ta "'baiwar Allah
lafiya? Daga ina?" Bata amsa mata ba ta cigaba da bin gidan da kallo.
Babban abinda ya ja hankalin ta a
chanjawar da gidan yayi shine bedroom
din Inna Sa'ade da taga ya rushe shima.
Sabon dakin da aka yi mata ginin bulon
siminti aka jingina shi a jikin nasu na kasa
har yayi sanadiyar lalacewar nasun kuma
yayi sanadiyyar rayuwar Sauda, shima ya
fadi, kuma daga alama ya jima shima da
faduwar, amma kuma kamar nasu shima
ba"a gyara gurin ba yana nan a bude, sai
ginin kasa da aka yi aka toshe kofar
tsakanin cikin dakin nata da falon ta.
Safiya ta wuce matar da har yanzu take yi
mata magana ta doshi kofar falon Inna
Sa'aden, kafin ta daga labule taji murya a
bayan ta, muryar yayanta Dauda "ke
wacece ne wai ana ta yi miki magana kinyi
wa mutane shiru?" Ta juyo da sauri ta
sauke rinannun idanun ta akan sa, ya ja da
baya kadan kamar wanda yayi gamo,
"Baba Hadiza?" Ya fada, sai kuma ya
chanja "Safiya?"

Bata amsa masa ba sai ido da take binsa
da shi. Muryar sa tana nan yadda take
bata manta ta ba, ta tuno sanda yace "ina
uwar ta ku? Ko bata dawo daga yawon
karuwancin ba?" Amma kuma kamannin
sa gabaki daya sun chanja, ya rame ya sirance yayi baki, kana ganin sa ka ga
wanda shaye shaye yayi wa kamun mutu
ka raba.
"Lantana! Lami!" Ya fara kwalla kiran
sunan yayyen su wadanda suke yaya ne a
gurin Inna Gaje. Lami ta fito daga dakin
Inna gaje da sauri tana gyara daurin zani.
"Kai lafiya kake min irin wannan kiran
mafarautan? Ba dai zan baka rancen wani
kudin ba dan. .
...." Sai kuma ta tsaya tana
kallon Safiya.
"Safiya" ta kira ta direct
"Safiya ke ce haka? Ke ce a gidan nan?"
Safiya ta tuno ta sanda take zazzagin
Baba Hadiza tana kuma kokarin dukan ta
a dai dai lokacin da aka dauki gawar Alhaji
Haladu. Ta kuma tuno ta sanda suke yi
musu watsi da kaya a waje suna cewa sai
sun bar musu gida, Baba Hadiza tana ta
kuka tana bin su tana rokon su.
Ta juyo sosai tana kallon ta ta kira sunan
ta ita ma "Lami" duk kuwa da cewa Lamin
da haife ta dan tana da yaya sa'annin ta.
Sai kuwa Lami ta rafka salati "jama'a ku
fito. Safiya ce a gidan nan jama'a. Ashe
tana raye. Jama'a ku fito ku ganta dan in
tabbatar ba gamo nayi ba" Dauda yace
"gani nima ina ganin ta kuwa? Wanne irin
gamo? Zamuyi gamo ni mu biyu?" Ta
watsa masa kallon banza "kai dalla can,
kai me idon ka yake gani in banda kwaya?
Ina kiran mutane masu hankali ne su zo su
taya ni gani" nan take sai masifa ta kaure a tsakanin su.

Safiya ta wuce su ta shiga dakin da take
ta hari tun da ta shigo gidan. Sai dai tun
da ta daga labule taji dakin yana wari,
wani wari kamar warin mushe. Ga duhu
tamkar dakin su na da saboda tagogin
dakin duk a rufe suke. Sai da ta dan jima a
tsaye a gurin sannan idon ta ya washe, a
lokacin ne ta ga mutum a kwance a kan
katifa a tsakar daki.
14
6
3
6:52 AM
Sama sama take jin murya tana kiran
sunan ta "Safiya? Safiya ke ce? Safiya" ta
durkusa a gaban halittar da take kwance
a gabanta tana kallon ta. Ta rame ta
motse ta yamushe, Inna Sa'ade ce.
Kafafuwanta duk guda biyun babu su an
yanke su. Daga jikin ta da kuma katifar da
take kwance a kai ne warin yake fitowa.
Sai dai bakin ta yana nan tas, kuma daga
dukkan alamu tana cikin hayyacin ta.
"Safiya daki na ne ya fado min ina kwance
ina bacci, kafafuwana duk duka kakkarye
sai da aka yanke su, Balarabe yayi
hatsarin mota ya mutu, sauran yaya na
duk sun gaji da kulawa da ni suna can
gurin matayen su, Sai Dauda shi kuma
babu abinda yake sai shaye shaye, komai nawa ya sace ya siyar ya sayi kayan shaye
shayen sa..
..." Ta cigaba da magana non
stop, kamar neman wanda zata yiwa
magana da ma take yi, kamar ta jima ba ta
yi magana da kowa ba.
Safiya ta mike tsaye ba tare da ta ce mata
komai ba ta doshi kofa. Sai da taje bakin
kofa sannan inna Sa'ade ta sake kiran
sunan ta "safiya"Safiya ta dakata sannan
ta juyo tana kallon ta, tace "ki godewa
Allah da Sauda mutuwa tayi ba ta zama iri
na ba. A wani lokaci mutuwa rahama ce,
ni yanzu neman ta nake yi taki zuwa".
Har ta koma tsakar gida ana cigaba da
rigima tsakanin Lami da Dauda. Ta wuce
su again ba tare da tace komai ba ta shiga
dakin Inna Gaje. Tana zaune akan
tabarma ita kadai tana ta maganganu
kasa kasa, har Safiya taje gabanta ta
durkusa bata san ta je ba, kuma Safiyan
bata gane me take cewa ba. Maganganu
kawai take yi marasa ma'ana. Ga tsufa ita
ma ta koma kamar tsumma. "Da yazo ya
dauki kazar sai suka tafi cikin ruwan
sama, kuma saniyar bata da ilimi, Allah dai
ya tona asirin takalmi, Amen Ameen"
Safiya ta mike tsaye tana cigaba da kallon
ta sannan ta saka hannu biyu ta share
hawayen fuskarta ta juya ta bar dakin.
Tana fita Lami ta sske kokarin tarar gabanta, ta lura yayan lamin suna zagaye
da ita, da alama zawarci take yi. "Safiya
ina kika je tsahon shekarun nan. Munyi ta
neman ki bamu same ki ba. Mun dauka
ma ba kya duniya" Dauda yace "ina taje
kuwa in banda yawon duniya, namiji ne fa
yanzu ya kawo ta a katuwar mota, a ina
Safiya zata samu shiga irin waccan motar
in dai ba yawon duniya take yi ba?" Lami
tace "dalla yi mana shiru, ka kalle ta mana
ka gani? Ko dan shaye shaye ya toshe
kwakwalwar ka. Bata yi kama da abinda
kake fada ba, kama take yi da matan
masu kudi. Ka sani ko mijinta ne? Ko aure
ta yi? Safiya kiyi min magana mana ina ta
yi miki magana".

Still Safiya bata ce komai ba, ta wuce ta
tsakiyar su taje ta hau ta kan kasar da
shekaru suka saka ta zaizaye ta zama
bata da yawa, ta fita daga gidan ta koma
mota inda ta bar Adam.

Yana tsaye a jikin motar yana kallon cikin
gidan, daga dukkan alamu hankalin sa
ba'a kwance yake ba, yana gain ta fito
yayi ajiyar zuciya sannan ya bude mata
kofa ta shiga ta zauna a dai dai lokacin da
yaya Malam ya kawo kai yana kokarin
shiga gidan, ya tsaya yana kallon motar
daga alama bai gane wacce ta shiga cikin
motar ba, Safiya ta bishi da kallo, yana
nan kamar yadda ta san shi, ssi dai
shekaru da suka karu akan na da, sai
kuma shekarun suka saka taga yayi mata
kama da baban su. Ta rufe ido tana
kokarin tuno wa da fuskar Baba, suna
kama sosai da yaya Malam, ta bude idon
tace da Adam, "Drive, please" ya taka
motar a dai dai lokacin da yaya Malam ya
gane ta yace "Safiya?" Amma bata amsa
masa ba kamar yadda bata amsawa kowa
a gidan ba.
Gidan Hajiya Kyauta tayi masa kwatance
suka je, Hajiya Kyauta tayi murnar ganin
su sosai dan dama bata samu zuwa bikin
nasu ba saboda bata jin dadi sosai. Suka
zauna suka yi hira da ita sannan suka ci
abinci. A lokacin ne take bawa Safiya
labaran abubuwan da suka faru a gidan
su, yayan ta Balarabe wanda Inna Sa'ade
take ji da shi a cikin yayanta ya mutu, ita
kuma kasar da ta kashe Sauda ita ce ta
lalata nata ginin na zamani sannan babu
zato babu tsammani dakin ya fado mata
ita ma cikin dare, abinda yayi sanadiyyar
kafafuwanta biyu duk sai da aka yanke su.
15
8
4
6:52 AM
Ita dama bata da yaya mata, yaya mazan
suka fara jinyarta kamar gaske daga baya
duk kowa ya kama gabansa sai Dauda da
yayi aure yanzu yake zaune a asalin dakin Baba Hadiza. Su sauran yayan daudan
suke aikowa kudi wai ya kula da
mahaifiyar ta su, shi kuma sai ya cinve
kudin. Hatta fitsari da bahaya a lokuta da
dama sai dai tayi su a kwance.

Inna Gaje on the other hand tsufa yazo
mata da tabin kwakwalwa, kanta ya kwace
bata gane kowa bata gane komai. Lami da
lantana duk suna gida suna zawarci. Anan
Safiya ta gaya wa Hajiya Kyauta abinda
yake ran ta. "Hajiya Kyauta ina son siyan
gidan mu idan zan samu. Ina son ki samo
min wanda zai siya da sunana dan ba lallai
su siyar ba idan suka ji ni zan siya" Hajiya
Kyauta tace akwai dan ta zai iya. Safiya ta
cigaba "so nake ya bisu daya bayan daya
yayi musu tayin siyan gidan, tunda gidan
gado ne nasan da yawa zasu siyar, ina da
takardun bangaren mu har yanzu a
hannuna, idan da zan samu ko da rabin
cikin ne sai in hada da inda muke da shi
ina son gina wa Baba Hadiza masallaci a
wajen. In kuma sunki siyarwa sai a samu
wani filin daban a siya ayi ginin" Hajiya
Kyauta tace "zasu siyar ma, Gabaki dayan
su fa a kone suke talauci yayi musu
katutu, babu wanda za'a yi masa tayin
kudi yaki karba, Wadanda kawai suke
cikin gidan sune babu tabbas din zasu
siyar, amma kuma sauran sunfi su yawa".

Bayan sun ci abinci sunyi sallah anan
gidan sai suka dauki hanya suka koma
Abuja.

Zuwan su Kura ya taimaka wa Safiya sosai
gurin samun composure da ajiye past
dinta a gefe ta kuma fuskanci future. Cikin
dan kankanin lokaci cinikin gidan su ya
kammala, kuma kamar yadda Hajiya
Kyauta tayi predicting haka ne ya
kasance, kusan kowa a gidan ya siyar da
kason sa, hatta Dauda ya siyar da nasa da
kuma na Inna Sa'ade, yayan Inna Gaje ma
sun ce a siyar da nata a basu kudin, Lami
da Lantana ne kadai su ka bijire dan basu
da gurin zama, sai Safiya tace a kara
musu kudin yadda zai ishesu su sami
gurin zama, bata son shiga hakkin kowa
ba kuma ta son takurawa kowa.
Ganin cewa in sunki siyarwa ma kason
subbashi da yawan da zai ishe su su
zauna a ciki sai suka hakura suka siyar
suka nemi rent din wani gidan suka tafi da
mahaifiyar su. Safiya kuma a bisa
amincewar hakimin garin ta fara cika burin
ta na gina katon masallacin da sunan
mahaifiyarta a matsayin sadakatul jariya a
gare ta. Gini aka tsara mai kyau irin na
zamani, tun daga harabar masallacin har
cikin sa abin sha'awa ne, Sai kuma Adam
vavi furnishina masallacin va saka duk abinda ake bukata tun daga kan fankoki
da mic da Alqur'anai da sauran littattafan
addini har carpets, ya kuma yi borholes
guda uku a zagaye da masallacin duk da
sunan Baba Hadiza. Bayan an kammala
komai sai suka danka masallacin a hannun
Haruna dan Hajiya Kyauta saboda
maintenance, suka ce duk abinda ya
lalace ko kuma abinda ake bukata sabo a
ciki ya kira ya fada musu.
And then life goes on. Suka koma back to
their various kasuwanci. Shekara guda
bayan auren su Safiya ta bude awara joint
a Abuja, tace ba zata bar sana'ar awara
ba. A shekarar ne kuma suka yi handing
over na shago da Hajiya, shagon ya dawo
completely na Safiya ne. A karshen
shekarar ne kuma kamfanin gold din da
suka yi investing in ya gama kammala ya
fara functioning, har zuwa lokacin dai
bass samun komai daga gare shi amma
kuma hankalin su ya kwanta tunda sun
zama confirm share holders na kamfanin.
Da shekara ta sake zagayowa ne aka fara
basu profit, Safiya sai da ta girgiza da
adadin kudin da ta gani a rubuce kuma
wai nata ne ita kadai a matsayin riba kawai
bayan jarin ta da still yake ciki. Adam ma
yayi mamakin nasa, tun farko ya san cewa
akwai alkhairi a cikin abin amma bai dauka zai kai haka ba. A take Safiya ta sake
mayar da ribar ta cikin kamfanin ta kara
girman share dinta, while Adam used his
own profit ya siya musu gidan zama a
Abuja. Dama ya gaji da biyan rent.
23
9
6:52 AM
The house was huge and it was all Safiya
have imagined as aljannar duniya. The
first thing she did a gidan shine enlarging
picture din su ita da Baba Hadiza da su
Sauda ta kafe a babban falon gidan.
Together, they furnished the house to
their exotic taste. Babu ce kawai babu a
cikin gidan. Sai kuma yaya.
Tun bayan auren Safiya take saka ran
ganin ciki amma shiru, duk wata sai tayi ta
addu'a ta kuma yi ta sadaka amma a
karshen watan ta sai taga period. Tun
tana tura maganar to the back of her
mind har ta fara fito da ita tana furtawa.
And Adam kept saying lokaci ne bai yi ba
that their princes and princesses are on
their way, amma shiru basu karaso ba. Sai
dukiya ce take zuwa. Her story and
marketing strategies became a legend,
Kullum cikin signing business contract
take yi da different companies wasu
neman shawara suke yi daga gare ta wasu
aiki suka bata to market their products
wasu kuma ambassador suka bata na

brand dinsu. Wasa wasa duk kamfanin da
ta fara hulda da su sai suga cigaba sai
wasu kamfanin suma su fara neman ta.
A shekaru uku na farkon auren Safiya tayi
signing business contracts babu adadin,
at a point, she even had to have her own
lawyer da zai taimaka mata wajen tace
contracts din kar taje tayi signing akan
abinda yake illegal. A lokacin Safiya tafi
Hajiya da Alhaji gabakidayan su kudi.
Ranar nan ta dawo daga wani taro a
gajiye, babu tunanin abinda take yi sai na
zuwa gida ta samu tayi wanka ta kwanta
ta yi dogon bacci. Sai dai tana tsayawa a
bakin gate ta ga mutane a zaune a kasa
dirshan, Allah ne kadai ya san dadewar su
a gurin. Sai dai duk da gajiyar da take ciki
da kuma rashin kyawun yanayin su, ta
gane su. Yaya Malam ne da Lantana.
Taji kamar ta saka reverse ta fita da motar
a guje, amma kuma gidan ta ne wannan
ba nasu ba, ita zata kore su ba su zasu
kore ta ba. Sai dai babbar tambayar anan
ita ce "ya akayi suka san gidan? Me kuma
ya kawo su", Tayi kamar bata gansu ba ta
danna horn. Mai gadi ya taso da sauri ya
bude mata gate a lokacin da suma suka
taso da sauri suka taho wajanta, yaya
Malam kamar zai fadi. ta danna motar cikin gidan a guje, tana packing ta hango
su suna rigima da mai gadi, yana kora su
waje yana kokarin rufe gate su kuma suna
kara cuso kai. Bata ce komai ba har sai da
ya gama rufe gate din sannan ya taho
inda take "Hajiya sannu da zuwa.
Wadansu ne tun safe suka takurawa gidan
nan, na rasa yadda zanyi dasu, babu irin
zagi da tsoratarwar da bani musu ba
sunki tafiya" ta bude kofa ta fito tana jin
zuciyar ta tana zafi, mai gadin ya cigaba
da magana
"sunce su yayyen ki ne, wai
daga Kura suke" ta juyo da sauri tana
kallon sa tace "ka gaya musu na basu
minti goma, ko su bar kofar gidan nan ko
in saka a rufe min su, ka gaya musu nan
Abuja ce ba Kura ba, in na rufe su babu
mai fito da su har abada".
Daga haka ta shige ciki ta rufe kofa. Sai
dai baccin kasa yiyuwa yayi duk kuwa da
wankan da tayi ta kuma kwanta a
lallausan gadon ta. She have forgiven
them, amma ta kasa manta irin abubuwan
da suka yi musu da kiyayyar da suka nuna
musu, bata fatan wata mu'amala ko da ta
magana ne ta shiga tsakaninsu. Tana nan
a kwance Adam ya dawo daga tasa
hidimar, Ya tsaya a bakin kofar dakin ta
yana kallon ta, yace "baccin yamma babu
kyau" tayi juyi "yaki zuwa ma baccin, I am
extremely tired" yace "I know. How did the meeting goes?" Tace "just like we
expected, wai suna son in je musu taro ne
a Beijing, kuma inyi magana a matsayin
representative din su" yace "okay. Sai mu
shirya zuwa china kenan" ta tashi zaune "I
didn't say yes, nace sai nayi magana da
kai first" yace "to ni na ce miki yes. It is a
golden opportunity, zaki hadu da mutane
da yawa a can. Kawai kiyi amfani da
marketing strategies dink and win their
hearts, daga nan zaki samu connections
da zasu kaiki next level in life".
Bata ce komai ba har ya karaso ya zauna
a bakin gadon yana kallon ta. Sai yace
"akwai baki a falon kasa" ta tashi tsaye da
sauri, ta fahimci bakin da yake nufi "I will
not see them" ta fada matter of factly" ya
gyada kai "then I will see them.
24
6:52 AM
Ba zan iya barin su a waje ba knowing
jinin ki ne su, and they refuse to go, kuma
sun taho tun daga Zamfara sannan basu
san kowa a Abuja ba bai kamata mu ki
ganin su ba".
Ta sake maimaita wa "I will not see them.
will have nothing to do with them" shima
ya maimaita "then I will see them". Ya juya kuma ta mike ta fita daga dakin itama. A
kan barandar da ta zagaye babban falon
gidan, wadda kuma ita ce zata kai ka
dakunan sa da nata, anan ta tsaya tana
kallon bakin nasu a zaune a kasa suna ta
kalle kalle, tana kallon yaya Malam ta tuno
sanda mota ta kade Baba Hadiza yayi
tafiyarsa ya barsu rungume da gawar ta,
sai a lokacin ta lura har da bagkon kaya
suka taho. Ta ga Adam ya bude dakunan
da suke kasa sannan yazo guri su yace
"tace ba zata gan ku ba, ta kuma ce in
kuka sake dawowa zata dauki matakin
shari"a a akan ku, amma nayi mata
magana, ga dakuna nan ku shiga akwai
duk abinda kuke bukata a ciki, za a kawo
muku abinci, ku kwana anan, gobe zan
bawa maigadi kudin mota ya baku ku
koma inda kuka fito"

Yaya Malam ya mike daga zaunen da yake
a kasa ya koma kan kujera ya zauna yace
"'wai kai in tambaye ka, uban waye ya
daura muku aure da ita? Shin wai auren
ma kuke vi o kuma zaman dadiro kuke
yi? Saboda ni dai ban daura mata aure ba
kuma kaf dangin mu babu wanda ya
daura mata aure, Zan kai ku kotun shari'ar
musulunci in yaso sai inga wanda zai
daure wani tsakanin ni da ku".

Maman Maama
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA❤️‍🩹
Episode Thirty Two: The Legacy

Not Edited
Safiya ta bar inda take ta sauko kasan da
sauri kamar wadda ake hankada ta, tazo
ta wuce su da sauri tana jin Adam yana
cewa tunda ba da mutunci suka zo ba ya
fasa basu dakin, ya juya yana rufe kofar
dakin da ya bude, Lantana ta fara kokarin
yiwa Safiya magana amma bata amsa
mata ba ta fita waje, tana fita sai gata sun
dawo tare da maigadi ta tsaya a tsakiyar
falon tana bin su da kallo tana lura da
yadda yaya Malam yake kokarin washe
mata baki "gata nan ta dawo ma ai,
kanwata ce, baban mu daya ni da ita" ta
juya tana kallon mai gadin tace "anan
kusa akwai irin matasan nan yan shaye
shaye wadanda basa jin tsoron uban
kowa?" Mai gadin ya fara fahimtar me
take nufi yace "babu anan layin Hajiya,
amma akwai anan layin bayan mu, neman
su kike yi?" Tace "ka zagaya dan Allah da
sauri ka samo min kamar guda biyar, ina
son su zo su fitar min da wadannan daga
cikin gidan nan ba ta hanyar mutunci ba,
kai kuma ka gane fuskokin su, in na fita
gobe zan sivo maka bindiga, duk wanda ya kuma dawowa a cikin su ka harbe shi a
kata ni na saka ka", Mai gadin ya gyada
kai da sauri "to shikenan Hajiya, bara in yi
sauri in kirayo su, harbi kuma sai dai in
ba'a bani bindiga ba, duk wanda aka kora
yaki tafiya kam ai barawo ne......
...." Ya fita
yana cigaba da maganganun sa
Safiya ta juya ta koma sama da sauri
kamar yadda ta sauko da sauri. Yaya
Malam ya kira sunan ta "Safiya..... Safiya
yanzu ni zaki ce a kira wo wa yan shaye
shaye suyi min korar kare daga gidan ki?
Ni zaki ce a harba idan na kuma zuwa
gidan ki? Uba daya ne fa ya haife mu ni da
ke. Wa kike dashi a duniya da ya wuce
mu. Mu kadai zaki gani ki kira da yan'uwa
kaf duniya" ta dakata a saman stairs din
ta juyo tana kallon su kamar zata yi
magana, duk suka tsaya suna jiran abinda
zata ce, sai kuma ta kuma juyawa ta hau
kan baranda suka daina gain ta.
Suka juya suka kalli juna
"ato magana
ma bamu isa tayi mana ba, wato bamu isa
ma tayi musayar yawu da mu ba, lallai
duniya mai abin mamaki, wai Safiya?
Safiya dai yarinyar da in nazo gida take
wankewa yaya na kashi take yi musu
wanka idan sunci abinci sun rage su bata
taci ita da kanwarta, wai ita ce yanzu take
yi mana korar kare da ga gidan ta". Yaya Malam ya koma ya zauna akan
kujera tare da yin tagumi da hannun sa
"duniya kenan. Ance fa kudin da take da
shi yafi dukkan tunanin mai tunani. Amma
ruwa yarinyar nan ba zata bamu musha ba
kenan take nufi?" Lantana taji an taba
gate ta zabuwa "yaya ka tashi mu tafi,
wanna yarinyar mai idanu a tsatstsaye
wallahi in bamu bar gidan nan ba ba
karamin wulakanci zata yi mana ba, ka ga
fa ta tura a dauko mata yan daba. Ka tashi
mu tafi" ta fada tana jan rigarsa" ya ture
hannunta "mu tafi ina wai? Kina da kudin
motar komawa gidan ne?" Tace "bani da
shi amma zan nema a waje, wallahi ba zan
zauna a nakasta ni a banza ba, wannan
katon gidan ko kashe mu ta saka akayi
tana da gurin da zata binne mu babu
wanda zai sani. Kazo mu je ko gidan
abokin na ka ne mu kwana a can"

Ya mike yana kallon been da Safiya ta
hau sannan yayi kwafa "zamu sake
haduwa ne" Lantana tace "kai dai kazo
mu tafi. Da mun sani mun lallaba mijin ta
naga kamar ya fita saukin kai shi zamu iva
samun wani abu a gurin sa, ko kuma ya
lallaba mana ita ta saurare mu, amma
yanzu kayi mana wasa da damar mu.........
Suka fita suna cigaba da maganganu kasa
kasa.

Safiya ta bisu da kallo har suka bar falon
sannan ta juya ta koma daki ta kwanta a
kan gado tare da jan bargo ta rufa. Ta san
babu wasu yan daba a unguwar, shima
mai gadin ya san babu, kuma yadda suke
din nan ko mai gadin shi kadai ta saka zai
iya daukan su aka ya fitar da su daga
gidan ballantana akwai sauran ma'aikatan
gidan, amma tana so ne ta nuna musu
how far she can go akan hana su shiga
rayuwar ta. Kuma yanzu from
maganganun su kadai ta san abin da ya
kawo su, ba komai bane ba sai kudi, kuma
ta rantse ta kuma rantsewa, kwandalar ta
ba zasu ci ba.
23
A
00
3
10:03 PM
Adam ya shigo dakin yana kallon ta, ya
san idonta biyu, yace "naso ace da
mutunci suka zo, da ko kudin mota sun
samu. Now they are stranded in Abuja
basu da ko kudin da zasu koma gida" ta
mike zaune tana kallon sa tace "da in
basu kudi na gwara na bude window na
watsa kudin waje, watakila almajirai su
dauka suyi amfani da shi. They are after
my money, my hard earned money, kuma
wallahi kwandala ta ba zan basu ba".

Adam ya zauna a bakin gadon ya rike
hannunta yace "wannan shine Zuwan su
na farko gidan nan, ina so ki fahimta kuma
ki saka a ranki cewa it won't be the last,

they will come back. Kudi suke so kuma
na yarda da ke idan kika basu they will
want more and more kuma tunda akwai
kiyayya a tsakani they will use every
means possible to get it" taji ajjiyar
zuciya"to yanzu ya zan yi? How can I get
rid of them? Ko gida zamu chanja ne?"
Yace "yadda suka gano wanna gidan
idan mun chanja ma haka zasu gano shi.
But we will take security measures for
protection"
Sun jima suna magana akai sai ya fita, ta
koma ta kwanta, sai ta tuno da maganar
Hajiya Maryama years back, ta sake tashi
ta zauna, yanzu idan ta mutu bata haihu
ba duk abinda ta tara a duniya su yaya
Malam ne zasu gada? Except for 1/8 da
za"a cirar wa Adam.

Three weeks after that maganar tafiyar su
Beijing ta tabbata. Wani taron karawa juna
sani ne na wani international organization
na yan kasuwa, anan ne aka bawa Safiya
dama tayi magana da yawn small scale
entrepreneurs na Nigeria da kuma irin
kalubalen da suke fuskanta. A cikin
bayanan nata ne ta bada labarin ta da
yadda ta rasa iyayen ta da yanuwanta da
kuma yadda ta fara kasuwancin ta hanyar
suyar awara a kofar gidan su har zuwa
matakin da take kai a yanzu,

Bayanan nata sun taba zuciyoyin mutane
da yawa a fadin duniya baki daya, aka
bata award suka yi pictures da mutane da
dama, mutanen da ada take gain sunyi
mata nisan da ko hanya ba zasu hada da
ita ba. And kamar yadda Adam ya gaya
mata, she got a lot of contracts and
connections, a ciki wanda tafi jin dadin sa
shine na wani textile industry da suka yi
mata alkawarin zasu zo su bude branch a
Nigeria and she will be their lead. Ita zasu
bawa contract din tun daga selection na
site din da zasu yi ginin industry din har
aikin ginin, siyo machineries da kuma
daukan ma'aikata. Bata dauka da gaske suke ba sai da suka
dawo Nigeria taga sun kira sun cigaba da
maganar. Nan da nan ta hau hidima tare
da taimakon Adam. She got an
opportunity and she used it wisely. Ta
tsaya tayi musu aiki akan gaskiya da
gaskiya and she got their trust har suka
sakar mata kudi sosai. Ta kuma yi amfani
da damar wajan kyautatawa du wadanda
suka yi playing major roles a rayuwar ta,
kusan aikin tun daga farkon sa har
karshen sa da Alhaji Nasir da Hajiya
Maryama aka yi shi. Cikin shekara daya
aiki ya kammala, a gurin kananan
ma'aikata ta bawa mutanen ta dama sosai, a lokacin ta samu fada sosai a gurin
yan'uwan Adam dan ta dauke su sosai har
sai da Adam yayi mata magana yace sunyi
yawa, ta aika wa da Hajiya Kyauta slots ita
ma tace in tana da wadanda take so a
bawa aiki ta turo su ayi musu interview,
Hajiya Kyauta kuwa ta turo yayanta da
jikokin ta sosai kuma kowannen su aka
bashi inda ake ganin ya dace da
qualifications dinsa da kuma experience
din sa. She then send slots to makotansu,
wadanda suka taimakawa Baba Hadiza a
lokuta da dama sanda tana raye, bayan
rasuwar ta ma kuma they were kind to
them, suma suka aiko samari biyu a gidan
kuma Safiya ta basu aiki suma.

A lokacin ne ta sake yin baki.

Ranar tayi baccin safe ba ta tashi da wuri
ba, Adam kuma yana Kano suna shirye
shiryen bikin kaninsa Ahmad da aka kusa
yi. Ta tashi ta shirya tsaf da niyyar zuwa
gidan Hajiya gurin Sa'adatu, tana
saukowa daga stairs idanunta suka sauka
akan yaya Malam da Dauda a zaune a kan
kujerun ta na falo, Ta tsaya tana kallon su,
suma kuma motsinta ya saka suka juyo
suna kallon ta, sai suka mike a tare suna
washe mata baki, Dauda yace "ga antin
namu nan ta sauko, An sha bacci" yaya
Malam yace "ba dole tayi bacci ba,
wanna hidima haka". A dai-dai lokacin da daya daga cikin
ma'aikatan gidan ta shigo ta ajiye musu
drinks da fruit a cikin plate. Tana mikewa
Safiya ta kira sunan ta "Hassana, waye ya
shigo da wadannan cikin gidan nan?
Dawo kizo ki duke min lemo na ki mayar
da shi fridge ko kuma ki bawa almajirai a
waje" yadda tayi maganar cikin fada yasa
yarinyar ta rikice, dan basu saba jin
Hajiyar ta su ta daga murya ba. Ta dawo
hannu yana rawa zata dauka Dauda ya
mike "ke! Zan kwarfe ki anan gurin in kika
taba wallahi" ta ja da baya a tsorace tana
kallon Safiya.
Safiya ta nuna mata hanyar waje "kira min
mai gadi" har yarinyar tayi hanyar waje sai
kuma tace "barshi ma, zo kiyi tafiyarki", ta
tuna cewa ba wancan mai gadin bane ba,
su biyu ne masu gadin nasu kuma shifting
suke yi, so wanna bai san yaya Malam
ba, and the girl was greatful to go.

Ta tsaya at the foot of the stairs ta
rungume hannayen ta a kirjinta tana
kallon yadda suke rige rigen cin abinda
aka ajiye a gabansu, "Safiyan Baba
Hadiza kenan, Safiyan Baba, kai Allah dai
yaki kan Baba, Baba zai ji dadi idan da ace
zai ganki a yanzu, kinyi kyau abinki, Baba zai ji dadi idan da ace zai gan mu a yanzu
tare da ke, yayye sun kawo wa karamar
kanwarsu ziyara. Kai zumunci yayi",
Ta saka hannu a jakarta ta dauko wayarta
ta nemo number din dpo din police
station da take kusa da su. Wancan
zuwan da su yaya Malam sukayi a cikin
matakan da suka dauka ita da Adam
akwai reporting issues din to the police
station nearest to them cewa akwai
wadanda sue bibiyarta kuma suna tsoron
kar su cutar da ita, sai dpo din ya rubuta
case din kuma ya basu number din sa
akan cewa in suka sake zuwa ta kira shi
direct.
Ta danna kira ta saka a kunnen ta still
idonta yana kan su Dauda, yana dauka
tace "hello dpo" suka gaisa ta fara yi
masa bayanin ta yace ya gane ta ai. Sai
tace "the people I once lodge a complain
about are here again, they are threatening
my life and frightening my house staff.
Okay. Thank you. Ina jiran ku" and she
hing up and continued standing up and
staring at su yaya Malam.

Dauda yana kallon ta shima ya taba yaya
Malam yace "yaya me take cewa ne, kai
ka dan fini iya turancin" yaya Malam
shima yana kallon ta fuskarsa cike da takaici da mamaki yace "yan sanda ta kira
mana, tace su zo su kama mu wai munzo
zamu kashe ta" Dauda ace "kut...... To
ke idan kashe kin zamu yi ai da tuni kina
lahira wallahi. Shikenan ba zamu zo gidan
ki muyi zumunci da je ba sai ki ce zamu
kashe ki? Da tun kina jaririyar ku bamu
kashe ki ba sai yanzu?" Still bata ce komai
ba sai ma gyara tsayuwar ta da tayi ta
cigaba da kallon sa, yaya Malam yace "ko
magana fa bamu isa tavi mana ba. Bamu
isa tayi magana da mu ba. Lallai kudi
masu gidan rana. Ko ba zakiyi magana ba
na san ai kina jina tunda ke ba kurma ba
ce ba, mu yan uwanki ne uba daya ya
haife mu kuma munzo neman taimako
gurin ki. Safiya ko abincin da zamu ci
bamu da shi amma ke kina nan kina
rabawa mutanen gari wanda babu dangin
¡ya babu na baba manyan aiyuka, kina
zaune a wanna katon gidan, kalli irin
abincin da kike ci...'
" Ya fada yana nuna
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Dauda yana kallon ta shima ya taba yaya
Malam yace "yaya me take cewa ne, kai
ka dan fini iya turancin" yaya Malam
shima yana kallon ta fuskarsa cike da takaici da mamaki yace "yan sanda ta kira
mana, tace su zo su kama mu wai munzo
zamu kashe ta" Dauda ace "kut...... To
ke idan kashe kin zamu yi ai da tuni kina
lahira wallahi. Shikenan ba zamu zo gidan
ki muyi zumunci da je ba sai ki ce zamu
kashe ki? Da tun kina jaririyar ku bamu
kashe ki ba sai yanzu?" Still bata ce komai
ba sai ma gyara tsayuwar ta da tayi ta
cigaba da kallon sa, yaya Malam yace "ko
magana fa bamu isa tavi mana ba. Bamu
isa tayi magana da mu ba. Lallai kudi
masu gidan rana. Ko ba zakiyi magana ba
na san ai kina jina tunda ke ba kurma ba
ce ba, mu yan uwanki ne uba daya ya
haife mu kuma munzo neman taimako
gurin ki. Safiya ko abincin da zamu ci
bamu da shi amma ke kina nan kina
rabawa mutanen gari wanda babu dangin
¡ya babu na baba manyan aiyuka, kina
zaune a wanna katon gidan, kalli irin
abincin da kike ci...'
" Ya fada yana nuna
abinda aka kawo musu,
"amma mu hatsin
da zamu dama wa yaran mu kunu su sha
safiya gagararmu yake yi. Inna Gaje ta
rasu. Inna Sa'ade tana bukatar taimako
kuma kina da halin da zaki taimaka mata,
zaki iya kaita asibiti ayi mata kafar katako
ko ki siya mata keken guragu ko kuma ki
daukar mata mai kula da ita, duk zaki iya.
Mu kuma ki sama mana aikin yi Safiya. Ga
yayanki nan Dauda ko gidan da zai ajive iyalinsa ba shi da shi a yanzu sai gida
matar ta shi ta koma. Ki daure ki bashi ko
da aikin gadi ne. Ga su Haruna nan da
badamasi duk basu da wan takamaiman
aiki. Ga danki nan Salisu shima ya gagara
yin aure saboda rashin aikin yi. Ki taimaka
mana kamar yadda Allah ya taimake ki ya
mayar da ke yadda kike din nan".
Ko motsa bakinta bata yi ba ballantana
tace masa kala. Ya mike tsaye zuciya tana
cinsa yace "lallai yau kin tabbatar min da
abinda nake zargi a kanku, cewa ku shegu
ne ba yayan baban mu ba.
12
9
4
10:03 PM
Dan babu dan uwan da zai viwa dan
uwansa irin wannan wulakancin, jini ai ba
wasa bane ba" Dauda shima ya mike ya
doso ta "tunda tace kashe ta muka zo yi
gwara in kashe ta din ai shikenan kowa ya
huta" yaya Malam ya rike shi "kar ka taba
ta. Tarko ta dana mana so take mu taba
su taji dadin rufe mu. Kar ka jefa mu a
tarkon ta, Wanna yarinyar shaidaniya Ce"
Dauda ya kwace daga hannu sa ya karasa
gabanta suka tsaya suna kallon juna, ko
motsawa bata yi ba, sai kuma yayi
murmushi yace "an gaya mana ai, an fada
mana cewa ke juya ce ba kya haihuwa. Ki cigaba da tara mana dukiya kinji? Kina
mutuwa zamu zo mu kwashe tas. Allah ne
ya bamu", Ya juya ya saka kafa yayi ball da
drinks din da aka ajiye musu sannan ya
fita yaya Malam yana bin sa a baya.
Sai da suka fita sannan ta saki numfashin
da ta rike tun sanda Dauda ya kira ta da
juya, a take jikinta ya dauki kyarma har
saida ta kasa cigaba da tsaiwa ta zauna a
kasa tana ruke da kirjinta, zuciyar ta zafi
take yi mata. A haka police din da ta kira
suka karaso suka same ta, ba ta iya tayi
musu bayanin komai ba sai yarinyar ta
Hassana ce ta zo tana kwatanta musu
kamannin wadanda suka zo din da kuma
kayan jikin su, aka kira mai gadi shima
yayi bayani sai kuma ya kara da cewa
"sun gaya min su yanuwanta ne daga
garinsu suke shi yasa na barsu suka
shigo, kuma naga suna kama, kama irin ta
jini".

A ranar Adam yana jin labarin abinda ya
faru ya juyo daga Kano, yana zuws ya
zarce dakinta da sauri yaje ya rungume
ta, sai da taji dumin jikinsa sannan ta saka
kuka. Ya bar ta tayi kukan ta ta gama
sannan tace "sunce ni juya ce ba na
haihuwa, sun ce ina mutuwa zasu zo su
kwashe duk abinda na tara. And they will
do that idan na mutum" ya girgiza ta "and who told you zaki riga su mutuwa? Waye
ya san gawar fari? Kuma waye ya gaya
miki ba kya haihuwa?" Ta bude hannun ta
"to ina yayan suke? Gaya min suna ina?
Nuna min su" ya girgiza kai "'it has been
just four years. Babu wanda zai ce bama
haihuwa dan muni shekara hudu bamu
haihu ba. And if it will put your mind at
rest zamu iya zuwa orphanage muyi
adopting baby, baby sabuwar haihuwa
yadda babu wanda zai ce bamu muka
haife shi ba. Wannan zai dakatar da su
daga irin wadannan threats din". Ta sake
girgiza kai. "We can fool them. Amma
Allah yasan ba namu bane ba kuma ba shi
da gadon mu" yace "Okay then. We can
start fertility treatment in kina so, duk da
dai ni nasan lokaci ne bai vi ba. Ga Sufyan
nan da matarsa Hajjo sun riga mu aure
amma basu haihu ba suma har yanzu.
Akwai couples da na sani da suka yi
shekaru ashirin basu haihu ba daga baya
kuma suka haihu. We should just be
patient Safiya, muyi ta gayawa Allah zai
dube mu ya share mana hawayen mu".

Wannan maganar ta kara kusanci mai
karfi tsakanin Hajjo da Safiya, they
understood each other irin tunda suna
cikin the same situation, a hankali har
suka koma kawance, daga baya kuma
suka koma aminci yadda kowa ta san komai na kowa. They support each other
through ups and downs.

Exactly a year later matar Ahmad kanin
Adam ta haihu, wata goma bayan bikin su,
ta haifi dan ta namiji aka saka masa suna
Mukhtar. A shekarar ne kuma finally
Sa'adatu ta gama ruwan idonta ta zabi
miji, kamar yadda ta jima tana mafarki,
babban mutum ta zaba, wani dan majalisa
acan garin su Katsina amma anan Abuja
ya sama mata gida zata zauna a matsayin
ta na amarya, matar sa kuma ta farko tana
Katsina. Aka yi bikinta, Safiya tayi mata
zumunci sosai ta tare a gidan mijinta.
Daga nan suka cigaba da zumuncin su.

A shekarar ne kuma ta sake yin baki daga
Kura. Wannan karon ba maza bane ba
mata ne. Lami da Lantana. Ranar ta dawo
daga unguwa mai gadi ya gaya mata tayi
baki mata, bata yi tunanin komai ba
saboda akwai wadanda take expecting
kuma dama ta gaya wa security din gidan
cewa wasu mata zasu zo neman ta, wani
program ne take leading a lokacin na wani
ngo da zasuyi training mata a bangaren
catering,
19
3
10:03 PM
Sai dai tana shiga sai ta tarar ba matan da
take tunani bane ba. Lami ne da Lantana
da kuma mata duburwar yarinya da take Safiya ta gane ta saboda ta sha wahala a
gurin rainon ta sanda tana baby. Ta tsaya
kawai tana kallon su a zazzaune akan
kujerun ta. Lantana tana yiwa yarinyar
magana a hankali can kasa yadda ba dan
falon yayi shiru ba da Safiya ba zata iya ji
ba "kin dai gane duk abinda muka gaya
miki ko? Mu mun san abinda zamu ce
mata yanzu ta karbe ki, in dai har muka
samu ta yarda kika zauna a gidan
shikenan mun samu abinda muke bukata"
Sai kuma Lami tace "wai ni a ina kike
ganin yarinyar nan ta samu wannan uban
kudin ne?" Lantana tace "kin manta an
tabbatar mana da cewa Hajiya Kyauta ce
ta fitar da ita daga gari? Kin manta kuma
safarar yammata dama take yi? Ai kasar
waje take kai su suyi karuwanci su samu
kudi, an ce fa a wajen har karnuka ake
hada su da su sai kuma a basu miliyoyin
kudi"

Cikin bacin rai Safiya ta kwala kiran mai
gadi, ranar duk masu gadi biyun ne a
gidan, suka taho a guje cikin tashin
hankali, ta nuna su Lami "waye ya shigo
min da wadannan mutanen cikin gida
na?" Daya yace "Hajiya bakin ki ne da kika
ce zasu zo, su suka ce mana su bakin ki
ne" tace "wadannan fa sune bakin da na
ce kar a sake bari su zo min gida,
wadanda nace in sun dawo a harbe su"
mai gadin ya bude baki cikin mamaki "Hajiya wallahi bamu gane su ba. Gidan
nan mutane suna shiga suna fita kullum,
ba zamu iya gane kowa ba" ta dauko
wayarta daga cikin jaka ta juya gurin su
Lantana tace "ku dan kalle ni kadan" suka
juya suna kallon ta sai ta dauke su a hoto,
ta juya gurin masu gadin tace "ga hoton
su nan zan tura muku, kuyi ta kallon hoton
har ku gane kamannin su, ko su ko masu
kama da su bana son gani a jikin gidan
nan ballantana cikin gidan nan. Idan kuma
kuskure irin haka ya sake faruwa zaku
rasa aikin ku"

Ta juya da sauri ta doshi stairs Lami ta
mike da sauri ta rike hannunta "haba
kanwata, wai me muka yi miki haka mai
zafi ne. Ubangiji yana son zumunci kuma
yana son masu sada shi, sannan kuma
baya son masu yanke shi. Mu kadai kike
dasu kaf duniya. Bana son yadda kike
zaune a garin nan baki da kowa naki a
tare da ke. Shi yasa muka kawo miki yarki
ta zauna a gurin ki dan mu gyara
zumuncin da yake tsakanin mu. Allah yaji
kan mahaifin mu",

Wani mugun kallon da Safiya take binta
da shi ya saka ita da kanta ta saki hannun
ta fara ja da baya tana girgiza kanta. Lami
tace "duk kiyayyar da kike yi mana ba zaki
taba cire jinin mu da ga jikin ki ba, ba zaki
taba cewa mu ba vanuwanki bane ba" Safiya ta juya tana kallon security dinta
"'ku je ku kunto karnukan nan daga cikin
kejin su ku hada su dasu su fitar da su in
ku ba zaku yi ba" ta kalle su tace "maybe
in suka hadu da karnukan zasu fahimci
wahalar da ake sha kafin ayi kudi" a take
suka fara rige rigen fita daga falon har
suna yin tuntube da juna. Sai dai har sun
kai bakin kofa Lami ta juyo tana kallon ta
tace "lokacin da zamu dawo yana nan
zuwa, ko bama raye zamu bar wa yayan
mu wasiyyar su zo su karbi gadon ki in
kika mutu. Kuma dole zaki mutu, dole
kowa zai mutu".

Shekaru biyu bayan auren Sa'adatu ta
haihu ta haifi namiji aka saka masa
Mustapha, a lokacin kuma matar Ahmad
ita ma ta kuma haihuwar namiji aka saka
masa sunan Adam. Sanda suka je barka
ita da Adam sai Ahmad ya kawo masa dan
"yaya nayi maka takwara, idan an yaye shi
ni da mamansa muni alkawarin bar muku
shi tunda babu yara a gurin ku" yayi shiru
yana kallon su sai kuma ya kara da "kafin
ku samu naku" suka sake yin shiru sai ya
sake cewa "in kuma Mukhtar kuke so sai
mu baku shi tun yanzu, tunda yayi wayo
already" Safiya tayi ajjiyar zuciya tace
"mun gode sosai Ahmad, Yaran ai duk
namu. Allah ya raya du yayi musu
albarka" Shekara daya bayan nan Allah ya
albarkaci Sufyan da haihuwa shima ya
samu namiji, aka saka masa Abdul Hakim.
Haihuwar Abdul ta dan daga hope din su
Safiyya, sai kuma a lokacin ta yarda suka
fara fertility treatment.
15
8
10:03 PM
Ita duk tsahon lokacin nan tashin hankalin
ta shine kar taje asibiti ayi mata
confirming cewa ba zata taba haihuwa ba,
without knowing she was holding on to
hope cewa zata haihu watarana.

Shekaru suka cigaba da tafiya, har Safiya
da Adam suka shekara goma da aure,
babu ciki babu labarin sa, sai war dukiya
da take ta ninka kanta both a side din
adam dana Safiyya. Ita kanta kudin da
take dashi toro yake bata in ta zauna
tana lissafin sa, a anniversary dinsu na
shekara goma da aure ne suka bude their
first personally owned textile factory, two
years after that suka bude na takalma da
jakankuna and that was in addition to all
the other companies da suke da manyan
hannayen jari a ciki, one of the major one
of which is the gold company wanda har
yau Safiya ba ta taba taba share dinta ta
ciki ba, it just kept growing, Safiya tayi charity da yawa a tsahon
rayuwar ta, most of which tana yi ne da
sunan mahaifiyarta, wasu kuma tana yi da
niyyar neman haihuwa. And deeply in her
tana jin wani assurance na cewa adduoin
ta ba zasu tafi a banza ba, that she will
one day get a child.

Five years haihuwar Mustapha Sa'adatu
ta sake haihuwa ta haifi mace ta saka
mata Safina. Safiya ce ta kaita asibitin
haihuwar kuma a hannunta aka haifi
Safina. Sa'adatu tana labour tana yiwa
Safiya addu'ar samun haihuwa har Safiya
tana tsokanar ta cewa bata in ciwon
haihuwar shi yasa. Ranar suna aka saka
wa yarinyar Safina, Sa'adatu tace wa
Safiya "sunan ki fa na saka a wayan ce,
bana son saka mata Safiya Hajiya ta saka
ni a gaba tace dan kudin ki na saka mata
sunan ki, kin san Hajiya gani take kamar
nafi kowa son kudi a duniya" Safiya tayi
dariya tana kara rungume yarinyar "Safina
is my daughter, ko taci suna na ko bata ci
ba".

Sam yan'uwan Safiya basu barta ba, an
sha gaya mata cewa an ga Dauda ko wani
daga cikin su around unguwar su, sai da
suka kai pictures dinsu duk gurin yan
sandan da suke kusa da su sannan suka
kara security din gidan. Gidan ya koma
duk wamda zai shiga sai any waya cikin Sam yan'uwan Safiya basu barta ba, an
sha gaya mata cewa an ga Dauda ko wani
daga cikin su around unguwar su, sai da
suka kai pictures dinsu duk gurin yan
sandan da suke kusa da su sannan suka
kara security din gidan. Gidan ya koma
duk wamda zai shiga sai any waya cikin

And then two years later all of a sudden
Safiya became pregnant. Ranar da taje
asibiti suka yi confirming pregnancy dinta
wuni tayi tana kukan jin dadi, da daddare
kuma kasa rufe idonta tayi dan gani take
kamar tana rufe idon zata farka ta ga
cewa ashe mafarki take, sai ta raya daren
wajan godiya ga Allah a bisa wannan
kyautar bazata da yayi mata. Mutane sun
kasa gane tsakanin Adam da Safiya waye
yafi murna da cikin nan, waye kuma yafi
son cikin, su kan su basu sani ba.

In celebration of samun cikinta ta shirya
bikin bude sabon gidan gonar ta data
sanya wa suna "The Oasis",. Gidan gona
ne da yake da bangarori daban daban,
akwai bangaren kiwon kaji layers akwai na
broilers, akwai gurin kiwon raguna akwai
kuma na kifi, sannan ga side din exotic
animals wadanda aka saka su dan su
kawara gurin kuma su zama ababen debe
kewa. Sai kuma aka yi shuke shuke shuke na
different varieties of fruits. Aka dauki
masu aikin gidan gonar aka yi musu
dakunan su a gefe.
Kusan a cikin The Oasis akayi renon cikin
Safiya, dan tunda aka bude gidan gonar
Safiya ta dauki son duniya ta dora masa
kullum acan take wuni. Sometimes har
kwana suke yi a dakunan da suka ware
saboda hakan. A haka har cikin ya girma
kuma ya isa haihuwa, da kyar Adam ya
raba ta da Nigeria ya kaita america ta
haihu a can saboda yana son babyn ya
samu citizenship na can. "For the rainy
days" ya fada a kokarin sa na convincing
dinta.
Sai dai ita a lokacin concern dinta shine
gender din abinda zata haifa. Adam yace
"kina nufin saboda ba kya son yan'uwanki
su gaje ki ba kya son ki haifi mace?" Ta
girgiza kai "ko me a haifa zan so shi fiye
da raina.
q
10:03 PM
Amma idan suka ji na haifi namiji zasu fita
daga rayuwa ta, shine kawai abinda nake
bukata" sai kuma ta kara da "'kuma in na
mutu ba zasu ci kwandala ta ba". Adam
yaji ransa ya baci "wai ke baki da magana
sai ta mutuwa? Why do you always want
to torment me with maganar zaki mutu?" Tayi murmushi "duk zamu mutu. Kowa zai
mutu"
Ranar da Safiya ta haihu was the happiest
day of her life. Ba ta taba dauka cewa a
duniya akwai farin ciki irin wannan ba. A
lokacin shekarun su goma sha biyar da
aure. Ita kuma shekarar ta arba'in a
duniya.

Ta rungume jaririyar tana kallon ta
hawayen farin ciki yana fita daga idonta,
tana kallon Adam yana yi musu pictures,
ta shafa fuskar yarinyar tace "she looks
just like Baba Hadiza, dan Allah Adam ka
saka mata Hadiza" ta dawo kusa da ita
yana kallon jaririyar yace "she looks just
like you, na baki wuka da nama, ki zaba
mata duk sunan da kike so" ta fara murna
kamar zata vi rawa "Hadiza zan saka
mata, Baba Hadiza zata ji dadi sosai idan
taji nayi mata takwara" ta sake dariya "na
san Khadijah ma cewa zata yi sunan ta
ne" sai kuma ta bata fuska tana tunani
"Sauda ba zata ji dadi ba, ita rigimammiya
ce ga saurin kuka, zata ce ita ban saka
sunan ta ba" Adam yayi dariya "kina da
abin dariya wallahi, Yanzu a lahirar ne har
za'a yi rigima da kuka?"

Sai da ga mamakin sa har cikin dare da ya
farka yaga Safiya tana zaune tana feeding baby ya zo ya zauna a kusa da ita sai
cewa tayi "sunan Sauda kawai zan saka
mata, maybe idan nayi haka zata yafe min
fitar da nayi na barta a daki ita kadai"
Da safe kuma "na fasa saka Sauda Hadiza
za'a saka, sai a ringa ce mata Kubra, ka
ga ai ba sunan kowa bane ba" ya saka
hannu ya dauki jaririyar daga cikin gadon
ta ya zauna akan kujera yayi mata huduba
sannan ya mayar da ita ya kwantar yace
"nayi mata huduba da sunan ki. Because I
love you so much, kinga yanzu babu
zancen explanation".

Shikenan yarinya taci sunan mamanta, sai
dai aka chanja sunan ya koma Safiyya
instead of Safiyya, a hankali kuma sai aka
sake mayar mata da shi Fiyya.

Sai da Fiyya tayi sati biyu a duniya sannan
suka dawo Nigeria bayan uwa da yar sun
huta sosai. A lokacin Safiya ta fahimci irin
yawan mutanen da take dashi da irin
soyayyar da mutane suke yi mata, dan har
sai da ta rasa inda zata saka kayan baby,
mutane kuwa kullum gidan a cike yake da
yan zuwa barka tare da fatan alkhairi.
Hajjo da Sufyan ma sunzo daga Berlin
inda suke zaune tare da little abdulhakim
sunga baby. Sa'adatu kuwa kamar ita ta
haihu dan tattaro yayanta tayi suka dawo
gidan Safiya sai tazo zaman jego. Babu
wanda ya isa ya taba yarinyar nan, ganin ta ma sai dai mutum ya leka a hannun ta
ya gani amma ba zata bayar ba sai dai in
anfi karfin ta. Sam Safiya bata jin kewar
wai bata da yan'uwa a duniya, ita
mantawa ma take yi cewa bata da
yan'uwa.

Sai dai wata daya da haihuwar tata aka
aiko mata da sako a cikin envelope. Ta
dauka masu aiko da barka ne wadanda
suke jin nauyin bayarwa hannu da hannu.
Ta karba ta bude sai taga takarda ce da
rubutu marar yawa a ciki, ta karanta

"Muna taya ki murna. Ashe munyi ya,
Allah ya raya ta. Muna nan muna jira, ko
bamu samu ba yayan mu zasu cigaba da
bibiya har zuwa ranar da zasu samu.
Kowa zai mutu, sai dai ba kowa ne zai
haifi namiji kafin ya mutu ba".

Ta ajiye takardar tare da kafa wa jaririyar
hannunta ido. Ta gane daga ina takardar
ta fito ta kuma gane abinda sakon yake
nufi. And in one minute ta yanke hukunci.
A daidai lokacin Adam ya shigo dakin,
Yana kallon fuskarta ya san something is
wrong, Ya karaso da sauri yana duba
lafiyar Fiyya sannan ne ya lura da takardar
da take gabanta ya dauka ya karanta, Yayi
zagi kasa kasa tare da juyawa da sauri zai
bi baasin wanda ya kawo takardar sai sai ta
dakatar da shi "don't bother. Kwandala ta
ba zasu ci ba. Ina son magana da kai" ya
dawo ya zauna yana kallon ta sai tace
"na
yanke shawara, ina fatan kuma zaka goya
min baya" ya gyara zama "wacce
shawarar ce?" Tayi murmushi tana shafa
fuskar Fiyya "all what I did a rayuwata, tun
bayan mutuwar Sauda, duk wani decision
da na dauka a rayuwata all the struggles
all the wealth and all the tears were
25
11
4
10:03 PM
for her. Duk dan Fiyya nayi komai. She is
my dream and my legacy. She is
everything I have ever hoped for. She is
my future, and the future of my family"
cikin rashin fahimta yace "still ban gane
me kike nufi ba. Menene shawarar da kika
yanke?" Ta dago kai tana kallon sa tace "I
am going to transfer everything I have, I
mean everything down to the last kobo, to
her name".
Ya bude ido yana girgiza kai "that is not
possible" tace "it is. Babu abinda yake
not possible a rayuwa, Ita kadai ce ya ta
kuma daga kanta ba zan kuma haihuwa
ba. All what I need to do is to get my
lawyers to change everything daga Safiya
Khalid to Safiyya Adam Muhammad,
shikenan"

Ya rike hannun ta "is it about maganar
gadon nan wai? Shin wai ba sai mutum ya
mutu ba sannan za'a ci gadon sa? Are
You sick? Akwai abinda yake yi miki ciwo
ne?" Ta girgiza kai "babu abinda yake
damuna. In fact I have never felt as
amazing as I am feeling right now. Na riga
na yanke shawara all I need is your trust
and support" yace "amma Safiya I am
afraid for Fiyya, what if suka ji abinda kika
yi and they harm her and then you? Babu
abinda mutanen can ba zasu iya yi akan
dukiyar nan ba, babu abinda mutane da
zasu iya yi akan dukiya ba".

Ya sunkuyar da kanta tana kallon Fiyya da
ta bude ido ita ma take kallon ta, she then
smiled and say "no body will harm her
saboda yaci dukiyar ta. Nobody will harm
my daughter" ta fada tana shafa gefen
fuskar Fiyya sai kuma ta dago kai tace "I
will sign another contract with my
lawyers" Adam yace
"na menene kuma?"
Tace "if anything is to happen to Safiyya
Adam Muhammad wanda zata rasa
rayuwar ta, be it natural death ko
suspicious death kafin ta samu magadan
ta, everything in her name will go to
charity".

Adam ya bude baki da hanci yana kallon
Safiya da mamaki, but she had that
stubborn look da yasan cewa ta riga ta
gama magana.

Ta cigaba da cewa "ina so ka tabbatar
kowa da yake kusa da ita ya san da
wannan maganar, that way, people will
take care of her and make sure babu
abinda ya same ta, ko ba dan Allah ba ko
dan dukiyar ta".

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA❤️‍🩹
Episode Thirty Three : The Oasis

(U
6
Paid Advert
Yar uwa kinsan illar dake tareda infection
kuwa,to bari kiji kadan daga cikin illar da
infection yake da ita, kinsan cewa
infection yana hana haihuwa,yana hana
ma'aurata jindadin mu amala,yanasa warin
gaba kowane irin tirare kika sa bazai hana
wannan warin fita daga jikin kiba fitar
farun ruwa kaikayin gaba tusar gaba duk
suna daga cikin illar da infection yakewa
Ifyr ki.
Ina masu fama da ulcer, Asthma,sickle,
ina matar dake fama da fibriod, matsalar
rashin haihuwa ko bushewar jiki da fata
haddake mai son hibs da breas ina uwar
gida maison faranta ran oga a othe room
kema ba abarkiba jawarawa da yanmata
ku garzayo kuma ku kwada ku gani
munada feminine wash,garlic oil da dai
sauransu munada VIP chair akwai blood
circulatory machine ga kuma data1g250
cikin sauki da rankwame da rahusa kedai
kira number nan domin karin bayani
07035275119, 08038098317


Adam yayi shiru yana kallon ta yana kuma
nazarin maganganun ta, a karshe sai yace
"you can gift dukiyar ki to her, but you
cannot give a will na cewa idan ta mutu
kafin ta samu yaya a kai dukiya charity, it
is not islamically possible. In dai kin bata
then you no longer have the right to
dictate yadda zata yi da ita. Zata iya duk
abinda ta ga dama da ita. And ko da ita
din ma, bata da damar cewa ga abinda
za"a yi da dukiyar in ta mutu, tana dai da
damar tayi abinda taga damar yi da ita
idan tana da rai, kamar yadda ke ma
yanzu zaki yi abinda kika ga damar yi da
ita yanzu da kike da rai".
Tayi shiru tana tunani, ta san cewa
gaskiya ya fada, ta dago kai tana kallon
sa, she still had that stubborn look a tare
da ita "bana son ta zama target na
mutane saboda dukiyar ta, bama so
mutane su cutar da ita saboda dukiyar ta.
In haka ta faru na zalunce ta" ta danyi
shiru sai kuma tace "I will still sign the
contract" yace "how? Zaki ketare iyakar
ubangiji kenan?" Tayi murmushi "no. I will
forge the contract. Zamu gayawa mutane
cewa munyi agreement da lawyers din da
suke kula da dukiyar cewa zasu bayar da
ita ga charity idan Safiyya ta rasa ranta
kafin ta haihu. We will make them think
and believe that. While in reality ba
zamuyi hakan ba. We will make them take care of her ko dan su amfana da dukiyar
ta, knowing idan wani abu ya same ta
zasu rasa both ita and the money",
Adam yace "I don't know why you are
saying "they', Mu zamu kula da yar mu
and we will raise her together. Su kuma
wadanda kika yi haka saboda will never
get close to har ballantana har su kula da
ita. Ban fahimci suwa kike nufi ba" tace
"every body. In nace 'they' ina nufin
everyone. Akan issue din Fiyya da dukiyar
nan ban yarda da kowa ba sai kai sai
Hajiya. Ko Sa'adatu ban yarda da ita ba,
ban yarda da yan'uwan ka ba, ban yarda
da duk wanda zai zo kusa da ita ba. Ba
wai cewa nayi su ba mutanen kirki ba ne
ba, but money can change people or
sometimes it brings out their true color. It
can corrupt even the most purest of
hearts sai wanda Allah ya kare. Yana daga
cikin challenges da masu kudi suke
fuskanta cewa basa iya gane wanda yake
son su saboda Allah da kuma wanda yake
son kudin su. Kana ganin da bani da kudin
nan yan'uwanka zasu yi shiru a lokacin da
nayi shekaru goma sha biyar a gidan ka
ba tare da na haihu ba? Har kuma su
dauki babyn da suka haifa suce sun bani
kyauta?" ya yi kokarin defending dan
uwansa "Ahmad have been managing
businesses din mu for ears, bamu taba samun matsala ba" tace "saboda akwai
masu monitoring shige da fice da kudi. Ka
fahimce ni, ba nace ina zargin Ahmad ba
ko kuma nace shi ba mutumin kirki ba ne
ba, am just saying kudi most of the times
shaidan ne. It can corrupt him.
Musamman yanzu idan za'a yi wannan
transfer of ownership din dole zai sani
saboda yana managing bangarori da yawa
na dukiyar.
20
14
9:19 PM
Ahmad bashi da gado na but in na bawa
Fiyya na matso da kudin toward him, I
want him to believe idan wani abu ya
same ta nobody is getting anything, I
want everyone that will ever come close
to her to believe that, ko nan gaba zaka yi
aure zaka haifi wasu yayan I want the wife
and the children to believe that, ko ta
girma zata yi aure I want the husband to
believe that".
Adam ya dafe kansa yana jin yana sara
masa, shi kansa duk ciwo yake yi masa
with all these lissafi marar tishe da take yi.
She is alive and well, babu amfanin
wadannan lissafe lissafen, Yace "Okay,
please stop talking as if kina bankwana da
duniya ne, kina saka wa ina kasa gane
komai. You have been talking and now it is time for me to respond. Macanar for you to have a peace of mind cewa
mutanen Kura ba zasu karbi kudin nan ba.
And maganar charity bla bla bla, shima
zaki iya yi tunda kince ba yarjejeniyar
gaskiya zaki yi signing ba. But magana
daya zan kara akai, Koma me kika yi I do
not want Fiyya to know. I want her to have
a normal childhood and grow up to be
stronger than even you. I don't want her
to grow up with this burden on her
shoulders. Har sai ta girma ta mallakin
hankalin kanta ta kuma samu ilimin yadda
zata kula da kyautar da kika yi mata
sannan zata sani. If you agree to this than
everything else is fine with me".

And that was how the agreement was
concluded and within months aka gama
komai. Everything da Safiyya ta mallaka
wanda yake da takardar shaidar mallaka
sai da aka chanja sunan ya koma Safiyya
Adam Muhammad. Tun daga kan shares
dinta in factories din su ita da Adam har
kan wadanda take da outsiders, har aka
sauko kan personal belongings dinta su
sarkokin ta da motocin ta and every other
valuable possession,

Da Ahmad akayi komai, dan haka tun a
lokacin ya sani, kamar yadda kuma a
gabansa tayi signing takardar bogin da ta komai. You have been talking and now it
is time for me to respond. Maganar
transfer of ownership na yarda kiyi, just
for you to have a peace of mind cewa
mutanen Kura ba zasu karbi kudin nan ba.
And maganar charity bla bla bla, shima
zaki iya yi tunda kince ba yarjejeniyar
gaskiya zaki yi signing ba. But magana
daya zan kara akai. Koma me kika vi I do
not want Fiyya to know. I want her to have
a normal childhood and grow up to be
stronger than even you. I don't want her
to grow up with this burden on her
shoulders. Har sai ta girma ta mallakin
hankalin kanta ta kuma samu ilimin yadda
zata kula da kyautar da kika yi mata
sannan zata sani. If you agree to this than
everything else is fine with me"

And that was how the agreement was
concluded and within months aka gama
komai. Everything da Safiyya ta mallaka
wanda yake da takardar shaidar mallaka
sai da aka chanja sunan ya koma Safiyya
Adam Muhammad. Tun daga kan shares
dinta in factories din su ita da Adam har
kan wadanda take da outsiders, har aka
sauko kan personal belongings dinta su
sarkokin ta da motocin ta and every other
valuable possession,

Da Ahmad akayi komai, dan haka tun a
lokacin ya sani, kamar yadda kuma a
gabansa tayi signing takardar bogin da ta rubuta da kanta cewa if anything is to
happen to Safiyya Adam Muhammad
komai in her name will go to charity. And
after doing all that, Safiya became
happier and more relaxed. Ta mayar da
hankalinta kachokam kan kula da jaririyar
yar ta wadda tafi so fiye da rayuwar ta.
A cikin watannin ne kuma kaddara ta
saukar wa Sa'adatu. Mijinta uban yayan ta
yayi accident ya mutu. Wannan mutuwa
ba karamin daga hankalin Sa'adatu da
duk wanda yake tare da ita tayi ba. Ya tafi
ya barta da 8 years old Mustapha and 2
years old Safina. And Safiya was there for
her, a kan kafadun ta Sa'adatu tayi kukan
rashin mijinta, a gidan ta kuma tayi
spending most of her moaning period.
Sai dai kuma tun kafin ta fita daga takaba
efcc suka dira a gidan ta suka kore su
daga ciki suka garkame gidan da sunan
yana under investigation. Sannan kuma
suka yi freezing account din mijin.
Shawarar da Safiya ta fara bata sanda
tazo gidan ta tana kuka tana gaya mata
abinda ya far shine ta koma gidan Hajiya
ita da yaran for the mean time kafin a
warware problem din amma Sa'adatu ta
girgiza kanta "ba zan iya komawa gidan
Hajiya ba, ga yara" Safiya tace "me zai
hana? Hajiya tana rike wadanda bata da hadi da su ma ballantana su Mustapha da
suke kamar jikoki a wajenta" Sa'adatu ta
sake girgiza kai "duk wanda ya riga ya
wuce age din zama a gida ya riga ya
wuce. Ina komawa raini ne zai shiga
tsakani na da mutanen da suke gidan"
Safiya tace "to ki zauna anan, akwai
isassun dakunan da ba zaku takura ba
daga ke har yara" shima Sa'adatu ta ki
yarda tace "ba zan zo in zauna miki a gida
ba ga mijinki yana gidan".
A karshe sai ta tattara kudin duk da take
da shi a account dinta ta kama rent din
gida a nan Abuja duk kuwa da yadda
Safiya ta nuna kin amincewar ta da
maganar. "In kika karar da kudin hannunki
akan rent da me kuma zaki biya wa yara
kudin makaranta da me kuma zaki cigaba
da rayuwa? Wannan kudin da hannun ki
kamata yayi ki juya shi, this is the right
time to fold up your sleeves and start
earning something ko dan future din
yayan nan.
28
4
9:19 PM
Amma Sa'adatu taki "in na gama takaba
zamu zauna da family dinsa na Katsina,
akwai gidaje da yawa yana da su, akwai
sauran kadarori, idan an raba an bamu
namu sai mu shiga kasuwar da su. Yanzu ke zaki biya wa yaran kudin makaranta, ki
kuma bamu abinda zamu rike a hannun
mu kafin komai ya warware.
And that was what happened, Safiya ce ta
saka musu furnitures da komai a gidan da
suka yi renting din sannan ta ajiye musu
kayan abinci ta kuma biya kudin
makaranta sannan ta basu kudin
kashewa. Ba haka ta so ba. Ba wai dan
bata son yi din ba sai dan tana son
Sa'adatu ta fahimci situation din da take
ciki a yanzu, she have been there, she
knows the probable outcome.

Ai kam dai sanda aka raba gadon Alhaji
Ibrahim sam abinda Sa'adatu ta saka ran
zata samu ba shi ta samu ba daga ita har
yaran. Sunce suma efcc ta kwace da
yawa daga abinda yake hannun su, a cikin
abinda ya rage gida kadai suka samu ita
da yayanta a Katsina. And the first thing
da tayi tun kafin ma ta gaya wa kowa
abinda ta samu shine ta saka gidan a
kasuwa ta siyar. Sanda Hajiya taji ba
karamin fada tayi mata ba "kina da
kananan yaya ciki har da namiji amma ki
siyar musu da gidan gadon su? Ba zaki
bar shi yayi musu amfani nan gaba ba?"
Tace "to Hajiya idan ban siyar ba da me
zan rike su? Kudin da zan siya mana
kayan abinci ma fa bani da shi" Hadiya tace "ki dauko su ku dawo nan gidan ku
zauna kinga baku da matsalar abinci
kenan. Zan baki jari kuma ki fara sana'a.
Kudin gidan da kika siyar kuma ki sayi ko
wani ne acan da ba zai siya miki gida anan
ba, ko kuma fili, ko ki sayi gold ki ajiye,
amma whatever you do kar ki kashe su".
Sai dai wanna hukuncin bai yiwa
Sa'adatu dadi ba. Sam bata son zaman
gidan Hajiya gani take tafi karfin haka a
yanzu. Kuma abinda ya kara koma mata
rai shine ire yaran da Hajiya ta yi daga
makarantar da suke zuwa mai dan karen
tsada ta dawo dasu wacce zata iya biya
musu. Ita Sa'adatu gani take yi abin kunya
ne kawayen ta suga tana zaune a gidan su
kuma yayanta suka karamar makaranta.
She went to Safiya for help amma Safiya
tace ba zata iya tsallake abinda Hajiya
tace ba. "Tunda ta cire su daga
makarantar idan na mayar da su nayi
mata ba dai dai ba. Kiyi hakuri, watarana
ke da kanki zaki mayar da su. Yanzu ki
kawo kudin hannunki akwai wata dama da
zata shigo min kwanan nan sai in saka
kudin naki a ciki, ki basu kamar shekaru
uku kadai ki gani yadda kudin zasu zama.
Ko kuma kiyi daya daga cikin shawarwarin
da Hajiya ta baki",

Amma Sa'adatu ba tayi haka ba. Sai ta bar
kudin a cikin account dinta "for security
purposes, zama babu kudi a hannu kudin a cikin account dinta "for security
purposes, zama babu kudi a hannu
tsautsayi ne", And a year later ko
kwandala babu a cikin kudin. Safiya da
Hajiya sun bawa Sa'adatu jari iya adadin
da su kansu basu san yawan saba, amma
da sun bata an kwana biyu za ta ga babu
shi babu alamun sa, kudi kamar ta
tsakanin yatsun hannunta ta yake
wucewa, bata taba koyon yadda zata
hade yatsun ta hana kudin fita ba.
Akwai lokacin da Safiya ta bata wasu kudi
sai ta mayar mata da su tace "ki juya min
su ke da kanki. Kiyi min abinda kika yiwa
kanki. Ni ribar kawai zaki ke bani ki rike
E3
war" safiya tayi dariya tana mamakin
halin Sa'adatu tace "ranar da bana duniya
kuma fa? Waye zai juya miki ya baki ribar
kawai. Dole sai kin koya. Nobody will take
care of you except you". Amma Sa'adatu
a ranta ta san wanda zai kula da ita da
yayanta. Ta san abinda take bukata. Wani
mijin take bukata mai kudin da zai rike ta
ita da yayanta. She was not born to suffer
like this. She was not born to take care of
herself and her children. She was born to
be taken care of,

Present days...….

"Fiyya?"

Naji an kira sunana kamar daga sama. Na
dauke idona daga kan fuskar mahaifiyata
na juyo na kalli mai kiran sunana, Mommy
ce. Tace "me kike yi ne ke kadai a zaune
kamar gunki?" Sai kuma ta kalli hoton da
ta lura shi nake kallo, tai ajjiyar zuciya ta
karaso cikin dakin ta zauna a bakin dago
tana cigaba da kallon hoton tace "I miss
her too....
.. She was so smart.
21
12
3
9:19 PM
The smartest human being I have ever
seen" ta danyi murmushi "na taba
tambayar ta cewa anya kuwa ba da aljanu
take aiki ba? Cos she will be like
"Sa'adatu idan kika yi this, this and that
ne zai faru amma idan kika yi that, that
and that ne zai faru" and abinda duk ta
fada din shine abinda yake faruwa sai dan
banbanci kadan, and then she will be like
"I told you so, ba kya jin magana
Sa'adatu"

Ta danyi dariya sai kuma muka cigaba da
yin shiru awkwardly, Ganin dai still bani da
niyyar yin magana sai ta sake cewa
'"dama zuwa nayi in taya ki hada kayan ki.
Kin san gobe zamu tafi. Gwara in shirya
miki kayan ki tun yanzu" na dan yi gyaran murya sannan nace "thank you Mommy,
Esther ta gama hada min ai. Nagode
sosa'" muka cigaba da yin shiru sannan
Mommy ta mike tace "okay then. In kina
bukatar wani abun dai just let me know".
Da haka ta fita.
Na bi bayanta da kallo har ta fita sannan
na girgiza kaina a hankali nace "ki je ki
hada kayan mijinki mana, me yasa ba zaki
hada mishi kaya ba sai ni zaki hada wa"
na yi dan karamin tsaki nace "bunch of
munafukai"
Na juya na cigaba da kallon hoton Ammi
na. She was the smartest just like Mommy
just said, and that means if she were here
with me right now she will not let me sit
here alone in my room crying like a
coward, she would tell me to put my past
behind me and take control of my future.
And that is exactly what I am going to do.
cannot be her, but I am going to be the
daughter she would have been proud of.
Kafin safe na gama yanke hukuncin duk
abinda zanyi.

After subh prayer ban koma bacci ba sai
na zauna nayi azkar dina sannan nayi duk
adduoin neman yarda Allah akan
abubuwan da na saka a gaba da kuma neman guidance dinsa akan abubuwan da
suka shige mun duhu, nayi wa Ammi
addu'ar samun rahamar ubangiji sannan
nayi wa Muhammad addu'ar Allah ya
sanyaya masa zuciyarsa ya bashi ikon
karbar kaddarar sa. Sai da gari ya gama
wayewa sannan na tashi na shiga toilet
nayi wanka, taking care kar in fama
ciwona, and seeing the scar sai na
tambayi kaina ko ya yake ciki? How is he?
Amma kuma ni na san ba zan iya kiran
Aunty Hajjo in tambaye ta shi ba.
Na fito daga wanka na shiga closet dina,
somewhere that I have not been in for a
while, a ciki naje na bude wata wardrobe
da tun da Daddy da kansa ya zuba kayan
ciki ban taba bude ta ba. Partly because I
was not emotionally ready. Sai dai na san
kayan ciki kamar sauran kaya na are been
well cared for by Esther.

Na tsaya ina bin kayan da kallo tun daga
sama har kasa, kayan Ammi ne, bayan
rasuwar ta Daddy took duk kayan ta da
yasan zasu yi lasting years har zuwa
lokacin da zan iya saka su ya adana su
safely, bai bani ba sai two years ago on
my 20th birthday, ranar da ya gaya min
maganganu da yawa da suka hargitsa
rayuwa ta,

And for the two years they have been with
me ban taba taba su ba ballantana in
saka. I doubt idan zasu yi min dai dai ma.
Na saka hannu na shafa su yadda suke a
jere ina jin texture din su sannan hannuna
ya sauka akan wani lace cream mai laushi
a hannu. Na jawo shi na fito da shi sannan
na warware, duguwar riga ce da aka yi
mata aiki mai kyau a wuya, simple dinki ne
irin wanda nake so wanda ba zai takurawa
mutum ba. Ga mamaki na material din
babu abinda yayi, daga gani an kashe
kudi a gurin siyan sa.

Na daga kayan na kai hancina hoping ko
zan ji wani scent da zsi iya tuna min da
memory dinta amma banji komai ba sai
kamshin wardrobe balls. Na saka undies
dina sannan na saka rigar, tsahon kamar
an auna da ni amma kuma wuyan ya dan
yi min yawa kadan, ko dai ta fini fadi ko
kuma ramar da nayi ce ta saka haka.
43
Na jawo dan karamin akwatin da yake
kasa wanda Daddy ya rufe da pin, na saka
3 9 pin din na bude na tsaya ina kallon
O
O
contents din ciki, sarkokin ta ne, sarkoki
na. A jere a cikin boxes din su. Tun da ta
rasu Daddy ya kai su ajjiya banki sai on
my 20th birthday ya karbo su ya bani
together with a lot of things. Na dauko
wata na bude box din ina kallon ta, na gane ta, ita ce a wuyanta a pictures din
ranar suna na. Na cire dan kunnen na
saka sannan na saka sarkar ita ma. Na
mike tsaye ina kallon kaina a madubi,
23
9:19 PM
I looked very different from Fiyya. I looked
more like Safiya.
Na daura dankwalin sannan na yafa
mayafina da ya shiga da kayan na rufe
komai na fita. A daki na dauki jaka ta tare
da key din mota ta na fita na kuma rufe
kofar dakin. Ina fita muka hadu da Esther,
ta tsaya tana kallona da mamaki amma
bata ce komai ba, nayi mata murmushi
"'ina Daddy?" Ta nuna kasa da hannun ta
"he is downstairs, they are all downstairs.
Shi yace in kira ki kuyi breakfast" nace
"okay. Please get me my banana
smoothie" tayi murmushi, ina ganin farin
ciki a fuskar ta tace
"yes ma'am" ta juya
da sauri and I heard her say "finally!"

Na gyara zaman wuyan rigar a jikina
sannan na fara sauka daga stairs din a
hankali, making sure cewa takalma na
suna making sound, and as I expected,
ina zuwa point din da zasu ganni na ga
gabakidaya suna kallon side dina. A lokaci daya all their jaws dropped.

Suna zaune a kan dining table, Mommy
da Mustapha da Hassan da Hussaini.
Daddy kuma yana zaune akan wheelchair
dinsa a gefen su alone like an island. Suna
cin abinci shi kuma yana karanta
newspaper. Newspaper din ta zame daga
hannun sa ta fadi akan cinyarsa. Hassan
yace
"woW" Hussain yace "masha Allah"
Mommy tace "dama sarkar nan tana
nan?" Na wuce su dukkan su na tafi
gaban Daddy da har lokacin ya kasa furta
komai. Na durkusa a gaban sa fuska ta da
murmushi nace "good morning Daddy"
sai kuma na dago na yi kissing cheeks
dinsa kamar yadda nake yi sanda ina
yarinya. A lokacin Esther tazo da
smoothie na a dogon mug ta miko min.
Hassan yace "the smoothie is back!" Nayi
murmushi tare da daga masa cup din
nace "yes dear, I am back" sai kuma na
gaishe da Mommy da tun da ta mike tsaye
sanda na shigo bata zauna ba. Ta amsa
har lokacin da mamaki a fuskarta tace
"you look a lot like her" nayi murmushi
"thank you"., Sai kuma na juya na gaishe
da Mustapha da yake ta jujuya cokalin
hannunsa tunda na shigo,

Na jawo kujera kusa da Daddy na zauna,
har lokacin kallo na yake, na fara shan
smoothie na still ina cigaba da bin mutanen gurin da kallo, har lokacin dai
kallo na suke yi. Na yi musu murmushi
daya bayan daya, sai da na shanye abin
da yake cikin cup din tas sannan na ajiye
na juya ina kallon Daddy nace "Daddy ina
son magana da kai, and it is important" ya
yi ajjiyar zuciya yace "she wore that
necklace ranar sunan ki" nayi murmushi
tare da rike hannunsa, ya sake cewa
"thank you for wearing it" na sauke ido na
kasa ina kallon hannunsa nace "thank you
for keeping it" yayi murmushi for the first
time tunda na shigo gurin sannan yace
"wacce magana ce zamu y" na dan daga
£3
murya dan ina son kowa yaji abinda zance
nace "dan ka amince Daddy, I want to
take over" his smile brightened, na san ya
fahimci abinda nake nufi amma sai ya
sake tambaya, maybe to make sure "take
over what?" Nace "take over every thing"
and I saw farinciki a idonsa, na cigaba "in
ka amince I want you to call Uncle Ahmad
da duk wani wanda wani abu yake hannun
sa, saboda su fara preparing everything, I
want to take over as soon as possible" ya
cigaba da murmushi "good, very good"
Mommy tace "finally! Kai amma naji dadin
wannan labarin. Na gaji da mulkin da
Ahmad yake mana dama a gidan nan,
komai muke so sai mun tambaye shi
kamar kudin sa" ban ce komai ba na mike na ajiye cup din hannuna akan table din a
gaban Mustapha, Hassan yana cigaba da
kallo na yace "kinyi kyau sosai yaya" nace
"'tukunna ma Hassan" na juya ina kallon
Mommy nace "Mommy zan dan fita
please" tayi murmushi, daga alama taji
dadin tambayarta da nayi tace "ina zaki
je? Kin san dai in an jima zamu tafi ko?"
Nace "zan je gyaran jiki ne, ina son in
wanke kaina in kuma yi manicure and
pedicure, flight din ai sai yamma" tace
"kiyi dai a hankali, kin san ciwon ki bai
warke ba" na gyada kai kawai, a raina ina
tuna cewa Ammi bata hakura ta zauna a
guri daya tana kuka ba, she walked
barefooted many kilometers da ciwo a
kafar ta dan tayi securing good future for
me.
O
21
12
9
9:19 PM
Na dauki jaka ta da car keys dina nayi
hanyar waje, sai da na kai bakin kofa na
juyo, har lokacin ni suke kallo, sai na fadi
abinda nayi tunanin Daddy zai yi
retaliating to, ina sane na bar maganar a
293 Marshe "na manta Daddy, also want to
re-open The Oasis. In kin amince" nayi
shiru ina jiran no daga gare shi, but he
kept on smiling and said "good luck"


Maman Maama✍🏻[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA❤️‍🩹
Episode Thirty Three : The Oasis

(U
6
Paid Advert
Yar uwa kinsan illar dake tareda infection
kuwa,to bari kiji kadan daga cikin illar da
infection yake da ita, kinsan cewa
infection yana hana haihuwa,yana hana
ma'aurata jindadin mu amala,yanasa warin
gaba kowane irin tirare kika sa bazai hana
wannan warin fita daga jikin kiba fitar
farun ruwa kaikayin gaba tusar gaba duk
suna daga cikin illar da infection yakewa
Ifyr ki.
Ina masu fama da ulcer, Asthma,sickle,
ina matar dake fama da fibriod, matsalar
rashin haihuwa ko bushewar jiki da fata
haddake mai son hibs da breas ina uwar
gida maison faranta ran oga a othe room
kema ba abarkiba jawarawa da yanmata
ku garzayo kuma ku kwada ku gani
munada feminine wash,garlic oil da dai
sauransu munada VIP chair akwai blood
circulatory machine ga kuma data1g250
cikin sauki da rankwame da rahusa kedai
kira number nan domin karin bayani
07035275119, 08038098317


Adam yayi shiru yana kallon ta yana kuma
nazarin maganganun ta, a karshe sai yace
"you can gift dukiyar ki to her, but you
cannot give a will na cewa idan ta mutu
kafin ta samu yaya a kai dukiya charity, it
is not islamically possible. In dai kin bata
then you no longer have the right to
dictate yadda zata yi da ita. Zata iya duk
abinda ta ga dama da ita. And ko da ita
din ma, bata da damar cewa ga abinda
za"a yi da dukiyar in ta mutu, tana dai da
damar tayi abinda taga damar yi da ita
idan tana da rai, kamar yadda ke ma
yanzu zaki yi abinda kika ga damar yi da
ita yanzu da kike da rai".
Tayi shiru tana tunani, ta san cewa
gaskiya ya fada, ta dago kai tana kallon
sa, she still had that stubborn look a tare
da ita "bana son ta zama target na
mutane saboda dukiyar ta, bama so
mutane su cutar da ita saboda dukiyar ta.
In haka ta faru na zalunce ta" ta danyi
shiru sai kuma tace "I will still sign the
contract" yace "how? Zaki ketare iyakar
ubangiji kenan?" Tayi murmushi "no. I will
forge the contract. Zamu gayawa mutane
cewa munyi agreement da lawyers din da
suke kula da dukiyar cewa zasu bayar da
ita ga charity idan Safiyya ta rasa ranta
kafin ta haihu. We will make them think
and believe that. While in reality ba
zamuyi hakan ba. We will make them take care of her ko dan su amfana da dukiyar
ta, knowing idan wani abu ya same ta
zasu rasa both ita and the money",
Adam yace "I don't know why you are
saying "they', Mu zamu kula da yar mu
and we will raise her together. Su kuma
wadanda kika yi haka saboda will never
get close to har ballantana har su kula da
ita. Ban fahimci suwa kike nufi ba" tace
"every body. In nace 'they' ina nufin
everyone. Akan issue din Fiyya da dukiyar
nan ban yarda da kowa ba sai kai sai
Hajiya. Ko Sa'adatu ban yarda da ita ba,
ban yarda da yan'uwan ka ba, ban yarda
da duk wanda zai zo kusa da ita ba. Ba
wai cewa nayi su ba mutanen kirki ba ne
ba, but money can change people or
sometimes it brings out their true color. It
can corrupt even the most purest of
hearts sai wanda Allah ya kare. Yana daga
cikin challenges da masu kudi suke
fuskanta cewa basa iya gane wanda yake
son su saboda Allah da kuma wanda yake
son kudin su. Kana ganin da bani da kudin
nan yan'uwanka zasu yi shiru a lokacin da
nayi shekaru goma sha biyar a gidan ka
ba tare da na haihu ba? Har kuma su
dauki babyn da suka haifa suce sun bani
kyauta?" ya yi kokarin defending dan
uwansa "Ahmad have been managing
businesses din mu for ears, bamu taba samun matsala ba" tace "saboda akwai
masu monitoring shige da fice da kudi. Ka
fahimce ni, ba nace ina zargin Ahmad ba
ko kuma nace shi ba mutumin kirki ba ne
ba, am just saying kudi most of the times
shaidan ne. It can corrupt him.
Musamman yanzu idan za'a yi wannan
transfer of ownership din dole zai sani
saboda yana managing bangarori da yawa
na dukiyar.
20
14
9:19 PM
Ahmad bashi da gado na but in na bawa
Fiyya na matso da kudin toward him, I
want him to believe idan wani abu ya
same ta nobody is getting anything, I
want everyone that will ever come close
to her to believe that, ko nan gaba zaka yi
aure zaka haifi wasu yayan I want the wife
and the children to believe that, ko ta
girma zata yi aure I want the husband to
believe that".
Adam ya dafe kansa yana jin yana sara
masa, shi kansa duk ciwo yake yi masa
with all these lissafi marar tishe da take yi.
She is alive and well, babu amfanin
wadannan lissafe lissafen, Yace "Okay,
please stop talking as if kina bankwana da
duniya ne, kina saka wa ina kasa gane
komai. You have been talking and now it is time for me to respond. Macanar for you to have a peace of mind cewa
mutanen Kura ba zasu karbi kudin nan ba.
And maganar charity bla bla bla, shima
zaki iya yi tunda kince ba yarjejeniyar
gaskiya zaki yi signing ba. But magana
daya zan kara akai, Koma me kika yi I do
not want Fiyya to know. I want her to have
a normal childhood and grow up to be
stronger than even you. I don't want her
to grow up with this burden on her
shoulders. Har sai ta girma ta mallakin
hankalin kanta ta kuma samu ilimin yadda
zata kula da kyautar da kika yi mata
sannan zata sani. If you agree to this than
everything else is fine with me".

And that was how the agreement was
concluded and within months aka gama
komai. Everything da Safiyya ta mallaka
wanda yake da takardar shaidar mallaka
sai da aka chanja sunan ya koma Safiyya
Adam Muhammad. Tun daga kan shares
dinta in factories din su ita da Adam har
kan wadanda take da outsiders, har aka
sauko kan personal belongings dinta su
sarkokin ta da motocin ta and every other
valuable possession,

Da Ahmad akayi komai, dan haka tun a
lokacin ya sani, kamar yadda kuma a
gabansa tayi signing takardar bogin da ta komai. You have been talking and now it
is time for me to respond. Maganar
transfer of ownership na yarda kiyi, just
for you to have a peace of mind cewa
mutanen Kura ba zasu karbi kudin nan ba.
And maganar charity bla bla bla, shima
zaki iya yi tunda kince ba yarjejeniyar
gaskiya zaki yi signing ba. But magana
daya zan kara akai. Koma me kika vi I do
not want Fiyya to know. I want her to have
a normal childhood and grow up to be
stronger than even you. I don't want her
to grow up with this burden on her
shoulders. Har sai ta girma ta mallakin
hankalin kanta ta kuma samu ilimin yadda
zata kula da kyautar da kika yi mata
sannan zata sani. If you agree to this than
everything else is fine with me"

And that was how the agreement was
concluded and within months aka gama
komai. Everything da Safiyya ta mallaka
wanda yake da takardar shaidar mallaka
sai da aka chanja sunan ya koma Safiyya
Adam Muhammad. Tun daga kan shares
dinta in factories din su ita da Adam har
kan wadanda take da outsiders, har aka
sauko kan personal belongings dinta su
sarkokin ta da motocin ta and every other
valuable possession,

Da Ahmad akayi komai, dan haka tun a
lokacin ya sani, kamar yadda kuma a
gabansa tayi signing takardar bogin da ta rubuta da kanta cewa if anything is to
happen to Safiyya Adam Muhammad
komai in her name will go to charity. And
after doing all that, Safiya became
happier and more relaxed. Ta mayar da
hankalinta kachokam kan kula da jaririyar
yar ta wadda tafi so fiye da rayuwar ta.
A cikin watannin ne kuma kaddara ta
saukar wa Sa'adatu. Mijinta uban yayan ta
yayi accident ya mutu. Wannan mutuwa
ba karamin daga hankalin Sa'adatu da
duk wanda yake tare da ita tayi ba. Ya tafi
ya barta da 8 years old Mustapha and 2
years old Safina. And Safiya was there for
her, a kan kafadun ta Sa'adatu tayi kukan
rashin mijinta, a gidan ta kuma tayi
spending most of her moaning period.
Sai dai kuma tun kafin ta fita daga takaba
efcc suka dira a gidan ta suka kore su
daga ciki suka garkame gidan da sunan
yana under investigation. Sannan kuma
suka yi freezing account din mijin.
Shawarar da Safiya ta fara bata sanda
tazo gidan ta tana kuka tana gaya mata
abinda ya far shine ta koma gidan Hajiya
ita da yaran for the mean time kafin a
warware problem din amma Sa'adatu ta
girgiza kanta "ba zan iya komawa gidan
Hajiya ba, ga yara" Safiya tace "me zai
hana? Hajiya tana rike wadanda bata da hadi da su ma ballantana su Mustapha da
suke kamar jikoki a wajenta" Sa'adatu ta
sake girgiza kai "duk wanda ya riga ya
wuce age din zama a gida ya riga ya
wuce. Ina komawa raini ne zai shiga
tsakani na da mutanen da suke gidan"
Safiya tace "to ki zauna anan, akwai
isassun dakunan da ba zaku takura ba
daga ke har yara" shima Sa'adatu ta ki
yarda tace "ba zan zo in zauna miki a gida
ba ga mijinki yana gidan".
A karshe sai ta tattara kudin duk da take
da shi a account dinta ta kama rent din
gida a nan Abuja duk kuwa da yadda
Safiya ta nuna kin amincewar ta da
maganar. "In kika karar da kudin hannunki
akan rent da me kuma zaki biya wa yara
kudin makaranta da me kuma zaki cigaba
da rayuwa? Wannan kudin da hannun ki
kamata yayi ki juya shi, this is the right
time to fold up your sleeves and start
earning something ko dan future din
yayan nan.
28
4
9:19 PM
Amma Sa'adatu taki "in na gama takaba
zamu zauna da family dinsa na Katsina,
akwai gidaje da yawa yana da su, akwai
sauran kadarori, idan an raba an bamu
namu sai mu shiga kasuwar da su. Yanzu ke zaki biya wa yaran kudin makaranta, ki
kuma bamu abinda zamu rike a hannun
mu kafin komai ya warware.
And that was what happened, Safiya ce ta
saka musu furnitures da komai a gidan da
suka yi renting din sannan ta ajiye musu
kayan abinci ta kuma biya kudin
makaranta sannan ta basu kudin
kashewa. Ba haka ta so ba. Ba wai dan
bata son yi din ba sai dan tana son
Sa'adatu ta fahimci situation din da take
ciki a yanzu, she have been there, she
knows the probable outcome.

Ai kam dai sanda aka raba gadon Alhaji
Ibrahim sam abinda Sa'adatu ta saka ran
zata samu ba shi ta samu ba daga ita har
yaran. Sunce suma efcc ta kwace da
yawa daga abinda yake hannun su, a cikin
abinda ya rage gida kadai suka samu ita
da yayanta a Katsina. And the first thing
da tayi tun kafin ma ta gaya wa kowa
abinda ta samu shine ta saka gidan a
kasuwa ta siyar. Sanda Hajiya taji ba
karamin fada tayi mata ba "kina da
kananan yaya ciki har da namiji amma ki
siyar musu da gidan gadon su? Ba zaki
bar shi yayi musu amfani nan gaba ba?"
Tace "to Hajiya idan ban siyar ba da me
zan rike su? Kudin da zan siya mana
kayan abinci ma fa bani da shi" Hadiya tace "ki dauko su ku dawo nan gidan ku
zauna kinga baku da matsalar abinci
kenan. Zan baki jari kuma ki fara sana'a.
Kudin gidan da kika siyar kuma ki sayi ko
wani ne acan da ba zai siya miki gida anan
ba, ko kuma fili, ko ki sayi gold ki ajiye,
amma whatever you do kar ki kashe su".
Sai dai wanna hukuncin bai yiwa
Sa'adatu dadi ba. Sam bata son zaman
gidan Hajiya gani take tafi karfin haka a
yanzu. Kuma abinda ya kara koma mata
rai shine ire yaran da Hajiya ta yi daga
makarantar da suke zuwa mai dan karen
tsada ta dawo dasu wacce zata iya biya
musu. Ita Sa'adatu gani take yi abin kunya
ne kawayen ta suga tana zaune a gidan su
kuma yayanta suka karamar makaranta.
She went to Safiya for help amma Safiya
tace ba zata iya tsallake abinda Hajiya
tace ba. "Tunda ta cire su daga
makarantar idan na mayar da su nayi
mata ba dai dai ba. Kiyi hakuri, watarana
ke da kanki zaki mayar da su. Yanzu ki
kawo kudin hannunki akwai wata dama da
zata shigo min kwanan nan sai in saka
kudin naki a ciki, ki basu kamar shekaru
uku kadai ki gani yadda kudin zasu zama.
Ko kuma kiyi daya daga cikin shawarwarin
da Hajiya ta baki",

Amma Sa'adatu ba tayi haka ba. Sai ta bar
kudin a cikin account dinta "for security
purposes, zama babu kudi a hannu kudin a cikin account dinta "for security
purposes, zama babu kudi a hannu
tsautsayi ne", And a year later ko
kwandala babu a cikin kudin. Safiya da
Hajiya sun bawa Sa'adatu jari iya adadin
da su kansu basu san yawan saba, amma
da sun bata an kwana biyu za ta ga babu
shi babu alamun sa, kudi kamar ta
tsakanin yatsun hannunta ta yake
wucewa, bata taba koyon yadda zata
hade yatsun ta hana kudin fita ba.
Akwai lokacin da Safiya ta bata wasu kudi
sai ta mayar mata da su tace "ki juya min
su ke da kanki. Kiyi min abinda kika yiwa
kanki. Ni ribar kawai zaki ke bani ki rike
E3
war" safiya tayi dariya tana mamakin
halin Sa'adatu tace "ranar da bana duniya
kuma fa? Waye zai juya miki ya baki ribar
kawai. Dole sai kin koya. Nobody will take
care of you except you". Amma Sa'adatu
a ranta ta san wanda zai kula da ita da
yayanta. Ta san abinda take bukata. Wani
mijin take bukata mai kudin da zai rike ta
ita da yayanta. She was not born to suffer
like this. She was not born to take care of
herself and her children. She was born to
be taken care of,

Present days...….

"Fiyya?"

Naji an kira sunana kamar daga sama. Na
dauke idona daga kan fuskar mahaifiyata
na juyo na kalli mai kiran sunana, Mommy
ce. Tace "me kike yi ne ke kadai a zaune
kamar gunki?" Sai kuma ta kalli hoton da
ta lura shi nake kallo, tai ajjiyar zuciya ta
karaso cikin dakin ta zauna a bakin dago
tana cigaba da kallon hoton tace "I miss
her too....
.. She was so smart.
21
12
3
9:19 PM
The smartest human being I have ever
seen" ta danyi murmushi "na taba
tambayar ta cewa anya kuwa ba da aljanu
take aiki ba? Cos she will be like
"Sa'adatu idan kika yi this, this and that
ne zai faru amma idan kika yi that, that
and that ne zai faru" and abinda duk ta
fada din shine abinda yake faruwa sai dan
banbanci kadan, and then she will be like
"I told you so, ba kya jin magana
Sa'adatu"

Ta danyi dariya sai kuma muka cigaba da
yin shiru awkwardly, Ganin dai still bani da
niyyar yin magana sai ta sake cewa
'"dama zuwa nayi in taya ki hada kayan ki.
Kin san gobe zamu tafi. Gwara in shirya
miki kayan ki tun yanzu" na dan yi gyaran murya sannan nace "thank you Mommy,
Esther ta gama hada min ai. Nagode
sosa'" muka cigaba da yin shiru sannan
Mommy ta mike tace "okay then. In kina
bukatar wani abun dai just let me know".
Da haka ta fita.
Na bi bayanta da kallo har ta fita sannan
na girgiza kaina a hankali nace "ki je ki
hada kayan mijinki mana, me yasa ba zaki
hada mishi kaya ba sai ni zaki hada wa"
na yi dan karamin tsaki nace "bunch of
munafukai"
Na juya na cigaba da kallon hoton Ammi
na. She was the smartest just like Mommy
just said, and that means if she were here
with me right now she will not let me sit
here alone in my room crying like a
coward, she would tell me to put my past
behind me and take control of my future.
And that is exactly what I am going to do.
cannot be her, but I am going to be the
daughter she would have been proud of.
Kafin safe na gama yanke hukuncin duk
abinda zanyi.

After subh prayer ban koma bacci ba sai
na zauna nayi azkar dina sannan nayi duk
adduoin neman yarda Allah akan
abubuwan da na saka a gaba da kuma neman guidance dinsa akan abubuwan da
suka shige mun duhu, nayi wa Ammi
addu'ar samun rahamar ubangiji sannan
nayi wa Muhammad addu'ar Allah ya
sanyaya masa zuciyarsa ya bashi ikon
karbar kaddarar sa. Sai da gari ya gama
wayewa sannan na tashi na shiga toilet
nayi wanka, taking care kar in fama
ciwona, and seeing the scar sai na
tambayi kaina ko ya yake ciki? How is he?
Amma kuma ni na san ba zan iya kiran
Aunty Hajjo in tambaye ta shi ba.
Na fito daga wanka na shiga closet dina,
somewhere that I have not been in for a
while, a ciki naje na bude wata wardrobe
da tun da Daddy da kansa ya zuba kayan
ciki ban taba bude ta ba. Partly because I
was not emotionally ready. Sai dai na san
kayan ciki kamar sauran kaya na are been
well cared for by Esther.

Na tsaya ina bin kayan da kallo tun daga
sama har kasa, kayan Ammi ne, bayan
rasuwar ta Daddy took duk kayan ta da
yasan zasu yi lasting years har zuwa
lokacin da zan iya saka su ya adana su
safely, bai bani ba sai two years ago on
my 20th birthday, ranar da ya gaya min
maganganu da yawa da suka hargitsa
rayuwa ta,

And for the two years they have been with
me ban taba taba su ba ballantana in
saka. I doubt idan zasu yi min dai dai ma.
Na saka hannu na shafa su yadda suke a
jere ina jin texture din su sannan hannuna
ya sauka akan wani lace cream mai laushi
a hannu. Na jawo shi na fito da shi sannan
na warware, duguwar riga ce da aka yi
mata aiki mai kyau a wuya, simple dinki ne
irin wanda nake so wanda ba zai takurawa
mutum ba. Ga mamaki na material din
babu abinda yayi, daga gani an kashe
kudi a gurin siyan sa.

Na daga kayan na kai hancina hoping ko
zan ji wani scent da zsi iya tuna min da
memory dinta amma banji komai ba sai
kamshin wardrobe balls. Na saka undies
dina sannan na saka rigar, tsahon kamar
an auna da ni amma kuma wuyan ya dan
yi min yawa kadan, ko dai ta fini fadi ko
kuma ramar da nayi ce ta saka haka.
43
Na jawo dan karamin akwatin da yake
kasa wanda Daddy ya rufe da pin, na saka
3 9 pin din na bude na tsaya ina kallon
O
O
contents din ciki, sarkokin ta ne, sarkoki
na. A jere a cikin boxes din su. Tun da ta
rasu Daddy ya kai su ajjiya banki sai on
my 20th birthday ya karbo su ya bani
together with a lot of things. Na dauko
wata na bude box din ina kallon ta, na gane ta, ita ce a wuyanta a pictures din
ranar suna na. Na cire dan kunnen na
saka sannan na saka sarkar ita ma. Na
mike tsaye ina kallon kaina a madubi,
23
9:19 PM
I looked very different from Fiyya. I looked
more like Safiya.
Na daura dankwalin sannan na yafa
mayafina da ya shiga da kayan na rufe
komai na fita. A daki na dauki jaka ta tare
da key din mota ta na fita na kuma rufe
kofar dakin. Ina fita muka hadu da Esther,
ta tsaya tana kallona da mamaki amma
bata ce komai ba, nayi mata murmushi
"'ina Daddy?" Ta nuna kasa da hannun ta
"he is downstairs, they are all downstairs.
Shi yace in kira ki kuyi breakfast" nace
"okay. Please get me my banana
smoothie" tayi murmushi, ina ganin farin
ciki a fuskar ta tace
"yes ma'am" ta juya
da sauri and I heard her say "finally!"

Na gyara zaman wuyan rigar a jikina
sannan na fara sauka daga stairs din a
hankali, making sure cewa takalma na
suna making sound, and as I expected,
ina zuwa point din da zasu ganni na ga
gabakidaya suna kallon side dina. A lokaci daya all their jaws dropped.

Suna zaune a kan dining table, Mommy
da Mustapha da Hassan da Hussaini.
Daddy kuma yana zaune akan wheelchair
dinsa a gefen su alone like an island. Suna
cin abinci shi kuma yana karanta
newspaper. Newspaper din ta zame daga
hannun sa ta fadi akan cinyarsa. Hassan
yace
"woW" Hussain yace "masha Allah"
Mommy tace "dama sarkar nan tana
nan?" Na wuce su dukkan su na tafi
gaban Daddy da har lokacin ya kasa furta
komai. Na durkusa a gaban sa fuska ta da
murmushi nace "good morning Daddy"
sai kuma na dago na yi kissing cheeks
dinsa kamar yadda nake yi sanda ina
yarinya. A lokacin Esther tazo da
smoothie na a dogon mug ta miko min.
Hassan yace "the smoothie is back!" Nayi
murmushi tare da daga masa cup din
nace "yes dear, I am back" sai kuma na
gaishe da Mommy da tun da ta mike tsaye
sanda na shigo bata zauna ba. Ta amsa
har lokacin da mamaki a fuskarta tace
"you look a lot like her" nayi murmushi
"thank you"., Sai kuma na juya na gaishe
da Mustapha da yake ta jujuya cokalin
hannunsa tunda na shigo,

Na jawo kujera kusa da Daddy na zauna,
har lokacin kallo na yake, na fara shan
smoothie na still ina cigaba da bin mutanen gurin da kallo, har lokacin dai
kallo na suke yi. Na yi musu murmushi
daya bayan daya, sai da na shanye abin
da yake cikin cup din tas sannan na ajiye
na juya ina kallon Daddy nace "Daddy ina
son magana da kai, and it is important" ya
yi ajjiyar zuciya yace "she wore that
necklace ranar sunan ki" nayi murmushi
tare da rike hannunsa, ya sake cewa
"thank you for wearing it" na sauke ido na
kasa ina kallon hannunsa nace "thank you
for keeping it" yayi murmushi for the first
time tunda na shigo gurin sannan yace
"wacce magana ce zamu y" na dan daga
£3
murya dan ina son kowa yaji abinda zance
nace "dan ka amince Daddy, I want to
take over" his smile brightened, na san ya
fahimci abinda nake nufi amma sai ya
sake tambaya, maybe to make sure "take
over what?" Nace "take over every thing"
and I saw farinciki a idonsa, na cigaba "in
ka amince I want you to call Uncle Ahmad
da duk wani wanda wani abu yake hannun
sa, saboda su fara preparing everything, I
want to take over as soon as possible" ya
cigaba da murmushi "good, very good"
Mommy tace "finally! Kai amma naji dadin
wannan labarin. Na gaji da mulkin da
Ahmad yake mana dama a gidan nan,
komai muke so sai mun tambaye shi
kamar kudin sa" ban ce komai ba na mike na ajiye cup din hannuna akan table din a
gaban Mustapha, Hassan yana cigaba da
kallo na yace "kinyi kyau sosai yaya" nace
"'tukunna ma Hassan" na juya ina kallon
Mommy nace "Mommy zan dan fita
please" tayi murmushi, daga alama taji
dadin tambayarta da nayi tace "ina zaki
je? Kin san dai in an jima zamu tafi ko?"
Nace "zan je gyaran jiki ne, ina son in
wanke kaina in kuma yi manicure and
pedicure, flight din ai sai yamma" tace
"kiyi dai a hankali, kin san ciwon ki bai
warke ba" na gyada kai kawai, a raina ina
tuna cewa Ammi bata hakura ta zauna a
guri daya tana kuka ba, she walked
barefooted many kilometers da ciwo a
kafar ta dan tayi securing good future for
me.
O
21
12
9
9:19 PM
Na dauki jaka ta da car keys dina nayi
hanyar waje, sai da na kai bakin kofa na
juyo, har lokacin ni suke kallo, sai na fadi
abinda nayi tunanin Daddy zai yi
retaliating to, ina sane na bar maganar a
293 Marshe "na manta Daddy, also want to
re-open The Oasis. In kin amince" nayi
shiru ina jiran no daga gare shi, but he
kept on smiling and said "good luck"


Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹


Episode Thirty Four: The Oasis 2


Na shiga mota ta na tayar, sannan na
dauko sunglasses din da nakan ajiye a
cikin motar na saka a idona, remembering
cewa the last time da na shiga cikin ta
shine ranar da naje office din Muhammad.
Nayi saurin kawar da tunanin sa daga
zuciyata, tun jiya da na gama deciding to
be strong na fahimci cewa shine kadai zai
zamo weakness dina, babban kuma
makamin da zanyi amfani da shi in yaki
wannan weakness din shine inyi nesa da
shi. Wannan yasa na kuma tabbatar wa da
kaina cewa tafiya Kano tare da Daddy
shine alkhairi a gare ni a yanzu. But
before that I need to go to the oasis, I
need to see it,
Na san a inda yake, duk kuwa da cewa sai
daya na taba zuwa gurin da wayo na,
shima kuma Uncle Ahmad ne ya taba
kaimu ni da Mustapha da Safina wani
zuwa da muka taba yi Abuja hutu gidan
sa. Shima kuma bamu dade a ciki ba ya
dauke mu muka fita saboda lokacin gurin
a cike yake da ciyawa. A lokacin ban san
menene gurin ba, ban kuma san me ya
faru a gurin ba.
Na kara gudun motar dan gurin da dan
nisa kuma bana so lokaci ya kure ban
dawo gida ba ran Daddy ya baci, a haka
har na karasa unguwar da gidan gonar
yake. It looks more congested then I can
remember. Wannan ya sa hanyar ta bace
min har sai da na fito daga motar nayi ta
tambaya "dan Allah wani tsohon gidan
gona nake nema anan unguwar yake" sai
dai mutane da yawa basu gane ba, sai na
fahimci yanzu it is no longer gidan gona
dan haka mutane da yawa ba zasu sanshi
a matsayin gidan gona ba.

Sai da kyar na samu wani mai babur din
haya yace ya san gurin, ya tafi gaba na
bishi a baya har muka bar cikin gidajen
mutane sannan muka fito wani filin ball
sannan na hango gidan gonar. Na sallami
mai babur din na karasa nayi packing na
fito na tsaya ina kallon gate din, it looked
old and rusty, it looked like an jima ba'a
bude ta ba dan har kasa ta taru a kasa,
except for karamar kofar da naga a bude take ma. Karafunan da aka saka a saman
gate din in shape of the alphabets THE
OASIS duk sun kakkarye wadansu ma
babu su a gurin, and my bet is yan
gwangwan ne suka sace.

Na tura karamar kofar a hankali na shiga,
babu komai sai kukan tsuntsaye sai dai
kallo daya na yiwa harabar gurin na
fahimci akwai mutane a ciki, daga can
bangaren da akayi dakunan ma'aikatan
gurin naji kukan baby, na doshi gurin
sannan na dan daga murya nayi sallama.
Naji muryar namiji ya amsa min, sai kuma
naga wani ya fito daga daya daga cikin
dakunan biyu yana kallona yana magana
"waye ?" Nayi shiru ban ce komai ba har
ya sauko daga kan barandar gaban
dakunan sai kuma ya tsaya yana kallona,
then I saw the realization as it hits him.
"Hajiya Safiya?" Maficin hannunsa saura
kadan ya fadi kasa.

Nayi murmushi ina jin wani stick of pride
yana strengthening spine dina, ina jin
23 pride duk sanda mutane suka ce ina kama
da ita, to me it is a great honor. "Hajiya
Safiyya" na gyara masa,
"Safiyya??" Ya
fada sannan ya karasa sakin maficin
hannun nasa ya rufe bakin sa da hannun,
sai kuma hawaye ya fara bin fuskarsa. Na cire glass din idona na cigaba da kallon
sa, ya goge hawayen idonsa "kiyi hakuri
Hajiya, sannu da zuwa. Da na ganki na
dauka ita ce. Sai na tuno da da, sai na
tuna da yadda muke da. Allah yaji kan
mahaifiyar ki Allah yayi mata rahama"
Nace "Ameen" yace "bismillah Hajiya, ki
shigo.…." Ya fara nuna min hanyar dakunan
da ya fito daga ciki, na girgiza masa kai
'"na gode, amma ba zama zanyi ba, zan
dan zagaya ne kadan, ina so in ga gurin
ne saboda za'a zo ayi aiki nan ba da
dadewa ba, za'a cigaba da duk abinda
ake yi a ciki" ya rufe bakinsa cikin farin
ciki "alhamdulillah, alhamdulillah. Allah
maji rokon bayinsa, Allah na gode maka.
Hajiya shekara ashirin kenan da rufe
gidan nan kuma shekara ta ashirin kenan
ina zaune har yau ban samu wani
tsayayyen aiki ba, dan ma Alhaji Ahmed
yace in cigaba da zama anan da iyali na
da na san zuwa yanzu ko gidan zama ba
zan samu ba. Allah ya tabbatar mana da
wannan magana" na wuce shi na bi
hanyar da na fahimci ciki ta shiga a raina
ina yaba yadda aka fitar da tsarin gurin. 22
14
2
1
10:32 PM
Ya biyoni a baya yana yi min bayanin ko
ina da abinda yake a gurin a da. Nayi
kokarin tunowa amma ban tuno komai ba.

Kafin mu gama zagayen har na gama
yanke hukuncin duk changes din da zanyi
da kuma abubuwan da zan kara a gurin.
Bayan mun gama ne kuma na tsaya ina
kallon sa nace "thank you for showing me
around" ya gyada kai, "nine da godiya
ranki ya dade" na danyi shiru ina kallon sa
sannan nace "ina reservoir din take? Ina
son ganin ta" nan take naga fuskar sa ta
chanja, "Hajiya??" Ya fada da rawar
murya, nayi kokarin kirkirar murmushi
"'babu komai. Kawai so nake in ganta" ya
~ juya reluctantly ya fara tafiya ina binsa a
baya har muka je inda katon tankin ruwan
gidan yake, na daga kai ina kallon
girmansa, da ruwan cikinsa ake bawa
dabbobin gidan ruwa da shi kuma ake
bawa shukokin gidan ruwa, na sunkuyar
da kaina kasa ina kallon inda mutumin ya
tsaya, a kusa da kafafuwan sa akwai wata
kofa ta karfe a rufe da padlock. Kofar
reservoir.

Yawn bukatar ruwan gidan ya saka bayan
tankin aka yi katuwar reservoir a kasa ake
tara ruwa a ciki, yadda in ruwan tankin ya
kare za'a ja wani daga reservoir din zuwa
cikin tankin sannan a kara cika reservoir
din. Na durkusa na dora hannu na akan kofar karfen da ta rufe gurin, na rufe ido
na ina kokarin forcing kaina to remember.
Ina so in tuno wani memory din nata, ko
yaya ne, ko wannan ne. Na bude ido na na
dago ina kallon mutumin da yake tsaye a
kusa da ni fuskarsa cike da damuwa. "Ina
key din?" Na tambaye shi, ya girgiza kai
bai ce komai ba sai na sake tambaya "ina
key din? Dauko min" na fada a matsayin
umarni ba shawara ba. Ya tsaya kamar ba
zai tafi ba sai kuma ya tafi da sauri.
Na sake rufe ido na trying so hard to
remember. And I can almost heard my
little self calling her "Ammie. Ammieme"
ya bude ido na ina murmushi. Na tuna
yadda nake kiran sunan ta idan muna
wasa "Ammieme" she was my best friend
ko minti daya bana son yi ba'a tare da ita
ba.

Bayan ta haife ni she gave up alot of her
ambition ta koma zama a goda tare da ni.
She would tell me stories most of which
ba gane wa nake yi ba, she would sing me
songs most of which ita take hadawa da
kanta, she would play with me kamar
sa'ata, muyi wasan ni iri iri, sanda na fara
way favorite wasan mu shine hide and
seek, zan je in buya a bayan kujera ko
wani grin inyi ta kyalkyala dariya. "Hide
Ammieme" nake kiran wasan, Ita kuma idan ta buya na duba ban ganta ba sai in
saka kuka in kwanta a kasa ina bori sai ta
fito sai in kama ta inyi ta dariya.

Babban abokin wasa na bayan Ammi
shine ruwa. Lokacin ina matukar kaunar
wasan ruwa, duk inda na ga ruwa sai nayi
wasa da shi, in me yawa ne kuma a bude
sai na shiga ciki. Sai da aka koma boye
ruwa a gidan mu saboda ni, tun ina rarrafe
na iya bude fridge in dauko ruwa in a
bude yake in kwara wa kaina shi komai
sanyin sa. Ko a cup a ka bani ruwa sai in
karba in kwara a kaina ince "water!!" Duk
wanda ya san ni a lokacin ya san ni da
wasan ruwa.

Mai gadin gidan ya dawo da sauri da key a
hannun sa sannan ya durkusa a kusa da
ni ya bude padlock din jikin kofar, I saw
his hands shaking as he was opening it.
Nace masa "thank you" sai kuma ya
matsa ya tsaya a bayana, maybe tunani
yake yi in yabar gurin zan fada ciki ne. Na
juya ina kallon sa nace "dan bani guri dan
Allah" sai da yayi dan jim kadan sannan ya
tafi, so nake a bar ni ni kadai, so nake in
kasance daga ni sai tunani na.

Na cire lock din daga jikin kofar sannan
nayi kokarin daga ta, it was so heavy that
sai da na saka hannu biyu sannan na daga
ta. Daga cikin kofar akwai sprina wanda ya rufe, idan ka bude kofar kuma all the
way akwai hook da yake rike ta a kasa ya
hana ta komawa. Na makale kofar a jikin
hook din sannan na mayar da ido na cikin
reservoir din ina kallon ta, it was filled
with water har bakin ta. It looked dark,
deep and cold. Sai naji wani chilly feeling
na toro ya shige ni. She jumped inside
with out a second thought so save me,
she died inside.

Twenty years ago...
16
9
8
10:32 PM
Haihuwar Fiyya ta saka Adam da Safiyya
sun kara zama closer than ever, sunyi
putting duk wani not so important
business din su on hold dan su samu suyi
raising yar tilon yar su together.
Abubuwan kuma da ba zasu iya putting
on hold ba sai suka yi scheduling dinsu
yadda zssu yi fitting sababbin tsare-
tsaren su. A cikin tsare-tsaren akwai
spending every weekend at the oasis, duk
Friday evening sue tahowa basa komawa
gida sai Sunday evening ko kuma ma
Monday morning. Idan sunzo suna zama
ne su kadai without visitors without
business discussions, just enjoyments
and playing with their Fiyya.

And that fateful weekend shima suka z0
kamar ko yaushe, Safiya ta dauki Fiyya
suka shiga ciki suka yi changing into
kananan kaya yayin da Adam shi kuma
yake cike da dokin zuwa yayi testing
sabon dokin da ya siyo. Safiya tana ta yi
masa dariyar idan ya hau zai fado tunda
ba iya wa yayi ba, dan haka sai yayi
deciding waje zai fita da dokin ya hau, ba
zai hau a cikin gidan ba kar ya fado tayi
masa dariya. And they watched as he and
ma"aikatan gidan guda biyu suka fita da
dokin waje suka turo gate din.

Suna fita Fiyya ta sauko daga hannun
Safiya ta fara gudu akan pavement din
wajen "hide Ammieme, hide Ammieme"
Safiya tayi dariya, ta gane wasa Fiyya take
so suyi, ta bita a baya, pretending kamar
ita ma gudun take yi, watching how Fiyya
take kokarin tsere mata da yan kananan
kafafuwanta. Tace "run run little one,
don't let me catch you".

Fiyya ta kara karfin gudun ta zuwa wasu
shuke shuken flowers da suke a gaban su
ta shige ciki tana kyalkyala dariya wai ita
lallai buya tayi, Safiya tazo ta wuce gurin
tana neman ta "where are you...... Don't
let me catch you...." Fiyya ta cigaba da
dariya ganin Safiya ta wuce ta, ita a
ganinta bata san tana gurin ba.

Sai da Safiya ta gama zagaye gurin
sannan ta saka hannu cikin flowers din ta
dauko ta.
"I got you" duk suka yi dariya
tare, safiya ta jefa ta sama ta cafe ta.
Fiyya ta fara tutture ta har saida ta sauke
ta kasa sannan ta tura ta baya tare da rufe
idonta da hannayenta "hide Ammieme,
hide Ammieme" Safiya ta gane me take
nufi, so take ta buya ita kuma ta nemo ta,
ta tafi da sauri ta buya a bayan wani dan
karamin daki da ake ajiye abincin
dabbobin gurin, Fiyya ta fara tafiya tana
neman ta tana kiran sunan ta "Ammi .
Ammieme.....
." Ta cigaba da kiran sunan
kamar mai waka tana zagaye a gurin har
tazo kasan tankin ruwan, a lokacin ne
kuma taga reservoir din, wide open, and
she saw the water.

Farin ciki ya bayyana a karamar fuskarta,
a hankali tace "water!!!" Sai kuma ta
karasa gurin da sauri ta leka tana kallon
43
sa, sai kuma ta sunkuya tana kara leka
0?
ramin gurin kamar mai auna zurfin sa, sai
kuma ta saka hannu daya ta taba ruwan
dan tabbatar wa cewa ruwa ne da gaske,
farin ciki ya sake cika zuciyar ta,
"water!!!" Ta sake fada cikin jin dadi, ga
ruwa ga shi kuma babu mai hana ta wasa
dashi, dan haka ta zura dukkan hannayen
ta biyu ciki tana jujjuya su tana watsi da ruwan zuwa jikin ta, and as she bent over
more dan taji dadin wasan, she slipped
and fell inside.

Safiya tana tsaye a mabuyarta tana jin
muryar yarta tana kiran ta cikin waka
'"Ammie, Ammieme....." Sai kuma ta ji tayi
shiru, tayi murmushi tana jiran taji ta fara
kuka dan trick dinta kenan in ta kasa
samo ta, amma kuma sai taji shiru bata ji
tayi kukan ba. She waited shiru. Nan take
zuciyar ta ta gaya mata cewa Fiyya was
distracted, maybe ma ta manta wasa
suke. And only one thing ne zaiyi
distracting Fiyya daga wannan wasan.
Ruwa. And she remembered the reservoir
and her heart stopped. Sai dai ta san
cewa the reservoir has always been
heavily closed amma bata bari wannan
tunanin ya tsayar da ita ba.

She got to the area a dai lokacin da Fiyya
tayi leaning over, and she saw her fell into
the water. She screamed and called
Adam, amma kuma sai ta tuna with a
sinking feeling that Adam baya cikin
gidan, that su kadai ne a cikin gidan.
19
6
4
10:32 PM
She could have run to the gate and call
for help but she didn't. She could have
run to their room ta dauko wayar ta ta kira Adam but she didn't. Ta san kowanne
second daya data bata zai iya making
different between life and death for her
daughter. And her daughter's life is
something da bata saka a kasan komai
ba.

She ran to the reservoir and looked
inside, she saw Fiyya sinking down the
clear water, her small hands and legs
kicking the water, her eyes wide, her body
jacking as she kept on breathing in the
water. And without a second thought
Safiya took a deep breath and jumped
inside.

Bata iya swimming ba, but she went down
and grabbed her daughter. Sannan kuma
ruwan yayi sama da su tare, she was
relieved and terrified at the same time,
terrified that she was too late, that
something bad had happened to her
daughter,

Tayi amfani da dukkanin karfin ta ta turo
Fiyya's little body waje, and she was so
relieved lokacin da taga Fiyya ta fara tari
tana fito da ruwa daga hancinta da bakin
ta, trying to get air into her lungs. Ta fara
kokarin fit da kanta daga cikin ramin,
garin kokarin ne ta dafa murfin, and it got released from the hook da ya rike shi a
kasa, spring din da yake jikinsa ta ciki ya
jawo shi da karfi. It went swiftly and
heavily, and hit her on the head.

She was sanda murfin ya taho kanta, and
she knew she was going to die. Her life
flashed before her eyes and ga mamakin
ta sai taga bata da regrets, amma kuma
tana burika masu yawa, babban unfulfilled
wish dinta shine na ganin yarta ta girma
ta samu rayuwa mai kyawun da take yi
mata fata. And as the metal hit her head,
just before she lost consciousness, she
wondered what her daughter's life would
be without her, and she prayed for God to
be with her.

As she lose consciousness, she sank to
the bottom of the reservoir yayin da
murfin ya rufe ta a ciki, the drawn. She
died


Twenty years later.…..
Present days.....….

Na saka hannuna daya cikin ruwan ina
wasa da shi tare da kokarin jera numfashi
dan kawar da abinda ya toshe min
makogwaro, dan hana kaina kuka kamar yadda nayi alkawari. "She drawn" na fada
wa kaina a hankali, trying to console
myself. "She drawn" na sake fada.
"Shahada tayi, She is in Janna".

Na sake jera wadansu numfarfashin
sannan na mike tsaye ina kallon reflection
dina a cikin ruwan. A hankali nace "rest in
peace mother. Rest in peace legend".

I was all emotional when I left the farm
house, amma hakan bai hana ni zuwa
saloon din da nace zanje ba. Nayi wa
kaina alkawarin not letting me emotions
get the hold of me. Saloon din da na saba
zuwa ne and they gave me the special
treatment da suka saba bani, naji kunya
sanda aka wanke min kaina saboda irin
dattin da yayi amma ana gama wa naji
iska tana shiga ta ta ko'ina, aka gama min
komai na fita, feeling as fresh as ever.

Ban koma gida ba sai da na biya ta
shagon da na saba siyayyar kayan skin
care dina, and I bought all abubuwan da
nake using before and more. Na riga na
daura niyya kuma babu gudu babu ja da
baya.

Ina komawa gida nayi sallah sannan nayi
joining su Mommy muka ci lunch tare.
Abinda ta fara tambaya ta shine "wai dama sarkar nan tana gurin ki?" Nayi
kamar ban fahimci abinda take nufi ba
nace "acce sarka kenan Mommy?" Tace
'"wannan ta wuyan ki. Sarkar Safiya ce. I
thought Daddyn ku ya siyar da ita or
something all those years ago. I was
surprised to see it with you today" na
ajiye spoon dina na gaya mata gaskiyar
lamarin. "Bai siyar ba, ya ajiye ne a banki.
Sai two years ago ya dauko su ya bani.
Suna nan a dakina. Ban taba buda su ba
sai yau" ta bude baki tana kallona da
mamaki, sai kuma rage yayi replacing
mamakin" I cannot believe it. I cannot
believe Adam yana boye min maganganu
irin wadannan. Ke ma kuma kina boye min
maganganu irin wadannan. Me zanyi da
sarkokin idan kun gaya min suna nan? But
at least ya kamata ace na sani. Wannan
boye boyen yafi komai bata min rai a
lamarin ku. Misali yanzu tunda kuka dawo
babu wanda ya gaya min ina babyn nan
yake ko take. I don't even know me aka
haifa. Bayan da ni aka yi komai" a hankali
nace "Mommy you didn't ask.
17
8
5
1
10:32 PM
Ni kuma naga ba dai dai bane in yi miki
maganar sa" tace "ohh namiji ne kenan?
Amma kin zauna da cikin sa ai a gaba na
amma ba zaki iya yi min maganar sa ba"
na so in bar maganar haka in koma quit mode dina but the new Fiyya in me
wouldn't let go sai nace
"Mommy ke kika
gaya min da kanki cewa you don't want
anything to do with the baby, kika ce kar
in doshe ki da shi" tayi shiru tana kallona
sai kuma a karshe tace "I was angry" na
dauki spoon dina na cigaba da cin abinci
na.

Muna gamawa naga an fara fita da kaya, I
asked abinda yasa zamu tafi da wuri and
Hassan ya gaya min wai za'a biya ne ta
gidan Safina Daddy da Mommy suga
dakin ta sannan muyi mata sallama. Muna
shiga mota Mommy tace "kema ai baki ga
gidan Safina ba, kwa samu ku gaisa
sosai".

Tun sanda aka ambaci gidan Safina na
nemi farin cikin da nake faking na rasa, it
was so hard to even fake a smile. Tunanin
nake kawai hanyar da zan bi in yi dodging
zuwa gidan Safina amma kuma na san
abu ne mai wahala hakan ta kasance. Har
muka je muka yi packing a kofar gidan
ban samu mafita ba and on impulse I
used the only way da nake ganin zata fitar
da ni "ban jin dadi, ku shiga ku fito kawai
zan jira ku a mota" duk suka juyo suna
kallona cikin mamaki har Daddy. Mommy tace "wanne irin ba kya jin dadi kuma? Ga
gidan a gabanmu taku goma ya isa ya
shigar da ke har ciki amma ki ce ba zaki
shiga ba? Menene yake damun ki ma to?"
Na nuna cikina "ina jin fitar da nayi dazu
ce ta gajiyar da ni. Ji nake kamar ciwona
zai bude" ta bini da kallo amma a fuskar
ta naga alamar ba ta yarda da abinda
nace ba, amma sai kawai ta bude kofa ta
fita tana magana kasa kasa ni banji me
tace ba, Mustapha da yake driving ya fita
shima zai dauko kujerar Daddy a boot, a
lokacin Daddy ya juyo yana kallona, na
sunkuyar da kaina kasa sai yace "ki tashi
ki shiga" ban ce komai ba na bude kofar
na fita na tsaya ina kallon gidan. Ba gidan da na sani a matsayin na
Muhammad bane ba, and hakan ya saka
naji dan dama dama a zuciya ta. My heart
can't take Safina da Muhammad living a
gidan da nayi planning zamu yi rayuwa da
Muhammad. But this one too is beautiful in dai zan
ajiye kishin da yake zuciya ta. I realized
akwai parts biyu a gidan, maybe daya
nasa ne daya na ta, sai kuma wasu
dakuna da nake tunanin na bakin sa ne
daga gefe. Ta fito da gudunta, daga
dukkan alamu ta san da zuwan mu, taje ta É dukkan alamu ta sai ua zuwan mu, taje ta
rungume Mommy sai kuma ta fara sharar
kwalla. Nan da nan hankalin Mommy ya
tashi ta fara tambayar ta in akwai matsala
amma sai tace mata kawai tayi missing
dinta ne.

Muka shiga ciki muka zazzauna, su
Hassan suna ta zagaya gidan wai wancan
xuwan nasu basu samu damar zagayawa
° ba amma ni sai na zauna akan kujera na
fara daddanna wayata naki ma dago kaina
ballantana in ga abinda zai hana ni bacci. I
was relieved sanda naji tana gaya wa
Daddy cewa Muhammad baya gida, "yaje
gidan su, bai san zaku zo ba, na manta
ban gaya masa ba" and I sensed she was
lying.

Ta nemi muje dining mu ci abinci, Mommy
tace "ai na gaya miki dama kar kiyi mana
abinci ba zama zamuyi ba, ganin ki kawai
zamuyi mu wuce, sai kuma Allah ya dawo
da mu gari. Amma bana jin zamu dade
bamu dawo ba ai tunda ga bikin Safiyya
zamu fara planning sannan kuma ga
wannan aikin da ta baro mana" na dago
kai ina tunanin wanne aiki ne na baro din,
sai naji ta fara bata labarin maganar da
nay dazu ta taking over all that is mine.
Sun jima suna hirar su, Daddy da
Mustapha suna dan jefa albarkacin bakin
su, daga baya kuma sai Daddy yayi mata fadan da bai samu damar yi mata ba na
yin biyayya ga aure, hakuri da sauran su,
sai kuma yayi mana nasihar mu hada kan
mu muyi zumunci da junan mu. Ni dai ban
ce komai ba har aka gama.
Har mun tashi zamu tafi sai Safina ta rike
hannuna "20 mana Safiyya, akwai magana
fa" Mommy tayi murmushi fuskarta tana
nuna jin dadin ta amma sai tayi fada
"wacce magana ce ba zaku yi a waya ba?
To kuyi sauri dai dan ba jiran ku zamuyi
ba". Suka fita suka bar mu mu biyu.
28
5
10:32 PM
Na karbe hannuna daga rikon da Safina
tayi masa na rungume su a kirjina ina
kallon ta cikin ido. Nasan maganar and I
was ready for her. Suna fita fake
murmushin fuskarta ya bace tace
"Mommy ta gaya mun jiya mijina yaje
gida, ta gaya min yace wai na bashi sako
ya kawo miki, Me yace miki?"

Saura kadan maganar ta ta bani dariya
amma sai nayi murmushi nace "do you
really want to know?" Bata amsa ba
instead sai tace "ina fatan dai baki manta
ba cewa ke matar aure ce shi kuma mijina
ne. If you continue seeing him I will have to tell our parents. So this is a warning. Ki
fita harkar mijina Safiyya, idan ba haka
ba....." Na katse ta "idan ba haka ba zaki
gaya wa Mommy da Daddy, gasu can a
waje, go and tell them please" muka yi
shiru muna kallon juna, sai kuma naji bai
kamata in bar maganar haka ba, not the
new me, na cigaba "You first asked me
me yace min, na tambaye ki if you really
want to know amma baki bani amsa ba to
bari in amsa miki nevertheless. Yaje ya
sake jaddada min how much he loves me
and how much he hates you. Ya kuma
gaya min cewa he hates you saboda cin
amana ta da kika yi....
.." Ta fara girgiza
kanta, fuskarta tana nuna tsananin bacin
rai '"ban ci amanar ki ba, ban san cewa
saurayin ki bane ba" nace
"explain that to
him, not to me because I don't believe
you.....
." Ta katse ni "| don't care what you
believe Fiyya. I just want you out of our
lives. Ki fita daga rayuwar mijina shine
kawai abinda nake bukata" ta fada tana
nuna hotonsa da yake makale a bangon
falon,

Na daga kai ina kallon hoton, ina jin bugun
zuciya ta yana tsayawa a guri daya
saboda kyawun da yayi min, nace
"mijinki.... Safina let me give you the first
and the final warning. Na daga miki kafa ne a cikin maganar nan ba wai dan ke ba
sai dan shi da kuma dan ni kaina, bana
son mu kasance masu sabon Allah har
Allah yayi fushi da mu. Wannan shine
dalilin da ya saka zan ja baya daga gare
shi ba wai dan kina matsayin matarsa ba"
na kara taku daya na tsaya daf da ita nace
"but don't push it. Don't force my hands.
In kika sake gangancin tsayawa a gabana
kina yi min irin wadannan maganganun
banzan zaki gane really wacece ni. Kinga
wannan mijin naki?" Na fada ina nuna
hoton nasa, sannan na nuna mata tafin
hannu na "a tafin hannuna yake. Duk
abinda nace masa yayi to tabbas zaiyi shi.
Idan da ina bukatar ki koma gidan ku da
zama ba ma sai na bude bakina nayi
magana ba, I just have to make a sign
with my hands and boom!!!! Zaki ganki a
gidan babana a dakin Mommy a matsayin
bazawara, ko kuma ki ganki a katsina inda
yafi dacewa da ke. In baki yarda ba ki
gwada ki gani. Nonsense"

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Thirty Five: Petty


Yar uwa kinsan illar dake tareda infection
kuwa,to bari kiji kadan daga cikin illar da
infection yake da ita, kinsan cewa
infection yana hana haihuwa,yana hana
ma'aurata jindadin mu amala,yanasa warin
gaba kowane irin tirare kika sa bazai hana
wannan warin fita daga jikin kiba fitar
farun ruwa kaikayin gaba tusar gaba duk
suna daga cikin illar da infection yakewa
Ifyr ki.
Ina masu fama da ulcer, Asthma,sickle,
ina matar dake fama da fibriod, matsalar
rashin haihuwa ko bushewar jiki da fata
haddake mai son hils da breas ina uwar
gida maison faranta ran oga a othe room
kema ba abarkiba jawarawa da yanmata
ku garzayo kuma ku kwada ku gani
munada feminine wash,garlic oil da dai
sauransu munada VIP chair akwai blood
circulatory machine ga kuma data1g250
cikin sauki da rankwame da rahusa kedai
kira number nan domin karin bayani
07035275119, 08038098317 k kiyi
joining group dinmu dan gani da ido09
si kunzo ngdhttps://chat.whatsapp.com/
LqcXIrhogcQC1iLdGGNJcZ hitps://
chat.whatsapp.com/

I watched as the hurt on her face turned
to rage, na juya zan fita ta kara kamo
hannu na ta rike, da alama maganar ba ta
ishe ta ba tace "gori? Gorin uba kike yi kin
Fiyya. Do you really want to play the gori
game? Ko kin dauka ban sani ba? Na san
komai fa" na juyo ina kallon ta nace
"Kamar yadda nima na san komai. Yes, let
play the gori game please. Nayi throwing
first card ina jiran naki. Menene abinda
zaki goranta kin akai?"

Tayi shiru yana girgiza kai, obviously
trying to compose herself tace "ba yanzu
ba Safiyya, time will come amma ba
yanzu. Zan goranta miki ne kamar yadda
kika yi min amma ba samda muke mu biyu
ba, sai lokacin da yake tare da mu, I want
to see the look on his face sanda zai san
wacece ke, I want to see the look on your
face sanda zai kalle ki idonsa cike da
tsanar ki. But for now ina kara tuna miki
cewa ni matarsa ce, shi mijina ne, and
that's a relationship that you guys will
never have. We live in the same house,
sleep in the same room, share the same
bed.....

Na dan yi kar karamar dariya, trying so
hard not to show her kishin da yake kona
zuciya ta, not to let her know my
weakness nace "still with the threats. Zaki
sha mamaki kuwa a ranar da kika gaya masa din. A lokacin da kika gaya masa a
lokacin ne zaki fahimci dalilin da yasa ban
gaya masa ba. A lokacin ne kuma zaki
fahimci the depth of his love for me. And
maganar gida da daki da gado, ke karyar
ki ai arniya ce bata sallah saboda ganin da
nayi wa Muhammad jiya, da ganin da nake
yi miki yanzu, plus maganganun da suke
fitowa da ga bakin ki masu tabbatar da
how desperate you are sun tabbatar min
da cewa baku taba hada daki ba
ballantana gado. Maybe only in your
dreams" na karasa ina flashing mata
hakorana in an ear to ear smile.

Ta kara kufula, a lokacin nasan zata iya
bada komai nata dan ta samu damar
dukana but she couldn't. Tace "haka kika
ce? Haka kike tunani? To ni kuma zan
nuna miki karya kike yi wallahi. Ki bani
wata biyu zuwa uku zan je har gida in
nuna miki result din kwanan da muke
akan gado daya, a lokacin zaki tabbatar
da karya yake miki yana kuma miki wasa
da hankali, sannan,…..

Mustapha ya bude kofar falon ya shigo,
daga alamu aiko shi aka yi ya kira ni, sai
kuma ya tsaya yana kallon mu "me yake
faruwa?" Ya fada yana kallon hannuna da
ta rike gam, ta saki hannun ta ja baya, ya
sake tambaya cikin fada "me yake faruwa
nace, are you guys fighting?" Na watsa masa mugun kallo sannan nazo na wuce
shi da sauri half expecting him to drag me
back, half thinking cewa we are back to
when we are younger, when they will
team against me. Amma kuma sai na tuna
cewa da da yanzu ba daya bane ba,
abubuwan da suka faru a da ba zasu taba
faruwa a yanzu ba.
WhatsApp.com
GHT team one marketing
33
WhatsApp Group Invite
18
11
2
8:25 PM
Da sauri na bude kofar motar na shiga
tare da rufe kofar da karfin da banyi niyya
ba. Mommy ta juyo tana kallona "lafiyar
ki?" Ban ce mata komai ba sai na kwantar
da kaina a kofar motar na rufe idona, ta
fahimci ba zanyi magana ba, ta san kuma
idan ta cigaba da magana zan saka
hannayena in toshe kunnuwana da su,
tayi karamin tsaki "Allah ya shirya".
Mustapha ya fito shima da sauri ya shiga
motar yayi driving muka tafi. Har muka
tsaya a airport din ban bude idona ba, ina
ta yaki da tunani na trying so hard to stop
picturing Safina and Muhammad akan
gado daya,

Sai dai ashe wan bacin ran yana can yana
jirana a airport dan ina bude idona muka hada ido da Mukhtar a tsaye a kusa da
Uncle Ahmad. Uncle Ahmad fuskarsa cike
da fara'a shi kuma Mukhtar tasa kamar an
aiko masa da mutuwa, Nayi ajjiyar zuciya
"God, give me patience" dan yanzu ba
strength nake bukata ba patience nake so
to limit and contain my strength, in ba
haka ba zan hada Mukhtar din da Uncle
Ahmad din da koma wanene zai tare da ni
da wata magana in dura musu yar garin
su Safina, Sai dai kafin in bude kofa in fito daga
Mukhtar din har uncle Ahmad din sun
taho inda nake, maimakon su fara zuwa
gurin Daddy su taimaka masa ya fito daga
cikin motar, Nayi sauri na karasa fitowa
kafin daya daga cikn6su yayi magana na
bar gurin na koma kofar da Daddy yake
kokarin budewa na bude masa sannan na
taimaka masa ya dafa ni ya fito daga cikin
motar, a lokacin Mustapha ya zagayo da
kujerar Daddy a hannun sa ya bude ta
sannan muka zaunar da shi a kai. Zuwa
lokacin twins suma sun karaso gurin, su
suka fara gaisar da uncle Ahmad ya amsa
musu kamar baya so sannan ya karaso ya
gaishe da Daddy, Mukhtar ma yazo ya
gaishe shi, Na dauke kaina pretending as
if bana ganin kalion da yake yi min, nima
na gaishe da uncle Ahmad sai na koma na jingina da jikin mota ina jiran su gama
gaishe gaishen su mu shiga ciki.

Mukhtar ya matso kusa da ni "hey, babu
gaisuwa?" Nayi masa kallo daya na dauke
kai nace "good afternoon" ya jingina da
motar shima a kusa da ni yace "fushi fa
nake yi, ko baki ga fuska ta ba? Nace
'"'hima haka, ko baka ga tawa ba?" Yace
('"na gani mana. Fuskar ki ita ce abinda
/nake kallo tun da kuka shigo gurin nan,
and kinyi kyau sosai. I noticed some
changes daga shekaran jiya zuwa yau.
You look different and sound different"
naga jama"ar mu sun fara tafiya na bi
bayan su da sauri, glad to cut off the
conversation, amma ina yin taku biyu na
jishi a gefena.

"Ya Rabbi, give me patience" na sake yin
addu'a a zuciya ta. Ya cigaba da magana
"'baki tambaye ni fushin me nake yi ba"
ban kalle shi ba nace "do I have anything
to do with it?" Yace "of course, yanzu kaf
duniya akwai wanda yake da things to do
with me kamar ki? Duk, abinda ya shafe ki
ya shafe ni kuma duk abinda ya shafe ki
ya shafe ni, We are bounded together"
ban ce komai ba na bi bayan Mommy
zuwa lounge din da zamu jira lokaci ya
karasa, Mukhtar ya shigo after me, ina zama ya zauna a kujerar kusa dani.

Na dauko Wayata daga cikin jaka na fara
danne dannen iska, ya saka hannu ya zare
wayar daga hannu na yana kallon ta yace
"so your phone is with you amma in na
Kira ki bana samu. Why?" Na daga kafada
"it was switched off, sai dazu na kunna"
yace "liar. Jiya ta shiga ai baki dauka ba
dana sake kira dai naji a kashe" nayi
ajjiyar zuciya "na kuna ta briefly, ba
charge kuma sai ta mutu, ban sake
kumnawa ba sai yanzu" ya cigaba da juya
wayar a hannunsa sannan yace "still lying.
Ba kya son magana da nine. Just say it
with your full chest shikenan. When I
accept to marry you I know fully well what
1 am getting myself into." Ya miko min
wayar yana yi min murmushi "and 1 am
ready for it all. You will fall in love with me
Safiyya I promise you that. One day zaki
yi mamakin me yasa tun farko baki so ni
ba. Because I am going to treat you like a
queen, I have so many things da nayi
mana planning for our lives together. And
I cannot wait long kafin in cika wadannan
burikan nawa a kanki,
17
16
8:25 PM
Wannan yasa na yanke shawara, na gaya
wa Abba and I am sure maganar da suke
yi da Daddy kenan" na dago kai na kalli inda Daddy yake zaune, naga uncle
Ahmad a zaune a kusa da shi suna
magana, daga alama magana mai
muhimmanci suke yi. And at the other
side Mommy da Mustapha suna zaune
looking back and forth between us and su
Daddy.

Na yi ajjiyar zuciya. This family of mine is
full of drama. Mukhtar a kusa da ni yayi
dariya kasa kasa, amma duk mutanen
gurin sun ji shi dan gabakidaya sai suka
juyo suna kallon mu, sai kuma yayi sauri
ya rufe bakinsa da hannunsa tare da kifa
fuskarsa akan kafada ta, nayi saurin
matsawa daga kusa da shi ina kallon
Daddy da shima yake bina da kallo sai
kuma naga ya juya sun cigaba da
maganganun su da uncle Ahmad.

Mustapha ya mike ya bar gurin da sauri,
Mommy tayi tsaki, na tabbata zuciyarta a
makogwaronta take a lokacin and I pity
wanda zai taba ta a lokacin. Kamar abin
baki sai ga innocent twins sun shigo gurin
da ledoji a hannayensu, daga dukkan
alama wani abun suka siyo a waje, ai kuwa
suna shigowa Mommy tayi kan su da fada
"daga gidan uwar wa kuke? Kowa yana
nan a zaune ku kun kama hanya kun fita?
Uban me kuka siyo?" Suka tsaya kawai
suna kallon ta sun kasa neman uzurin
kare kan su.

Mukhtar ya gyara zaman sa ya juyo yana
facing dina, stylishly covering the
distance dana saka a tsakanin mu. Ya ce
"na gaya wa Abba ya yi wa Daddy
maganar ina son ayi bikin mu in the next
two weeks" na juyo da sauri ina kallon sa
and he winked at me, nayi saurin dauke
kaina daga kansa ina girgiza kai ne "it is
not possible kai ma ka sani. Bani da lafiya,
Daddy yace sai na warke tukunna" yace
"and who says ba zaki iya warkewa a
gidan ki ba? I need to take care of you inyi
jinyarki ki warke a hannuna" ya fada yana
kama hannuna, nayi saurin karbe hannuna
ina yarfarwa a gefe tare da rarraba ido
kamar marar gaskiya "ka bari, ka daina
haka dan Allah yaya Mukhtar. Su Daddy fa
suna gurin nan" ya sake yin dariya
"SO
nake Daddy ya yarda da maganar da
Abba yake gaya masa ai. I need to be with
you" ya fada almost in my ears.

Na mike tsaye da sauri na rataya jakata
nayi hanyar fita, ya mike shima ya wuce ni
ya tsaya a bakin kofa yayi folding
hannayensa, completely blocking my way,
still da murmushi a fuskarsa, na bata rai
nace "ka bani guri in wuce" yace "sai
kince kin amince da abinda nace, dan
yanzu in na barki kuka tafi ba waya ta zaki dauka ba kuma ba gain ki zanyi ba. So l
need to know amsa ta yanzu even if I
have to kiss you here" na juya na koma na
zauna, ignoring zuciya ta da take gaya
min in wanke fuskarsa da mari.

Ina zama shima ya zauna a kusa da ni. Na
kalli Daddy naga shima ni yake kallo, his
face looked worried. Mukhtar yace
'"'believe me idan aka yi bikin ke kanki zaki
fi jin dadi, zaki samu ki huta sosai, ki
samu nutsuwa ta jiki da ta zuciya, away
from all this ...
...…..hayaniya" ya fadi
hayaniyar yana waving at side din da
Mommy har lokacin take yi wa twins fada.

Na juya ina kallon sa raina a matukar bace
"don't talk like that about her" ya daga
hannu '"shikenan, na daina. Yar gidan
Mommy"

Uncle Ahmad ne ya dan gada murya ya
kira sunana "Safiyya, come here my dear"
na tashi na je inda yake zan durkusa sai
ya nuna kujerar kusa dashi "seat" na
zauna ina kallon sa and I noticed that 1
have never seen him this happy, shi
mutum ne marar fara'a wanda tun ina
karama nake tsoransa, fadan sa ba irin na
Mommy bane ba, Mommy will bark and
bark but she will never bite, fadan ta ya
kai har bamu da mu ba in tana yi, like I can literally fall asleep a lokacin da take yi
min fada. But shi ko kallon ka yayi you will
feel your insides shaking.
Amma lokacin he was smiling from ear to
ear for me. Ya sunkuyar da kaina kasa ina
kallon yatsun hannu na, I was ready for
his fada, na dauka zai sauke min balai ne
idan Daddy ya gaya masa abinda nace,
and I already made plans for that. But he
was smiling. And it threw me off balance.
22
12
8:25 PM
Yace "yaya ya gaya min sakon ki, and I am
very happy with your decision. I would
have said nan da next two weeks
everything will be ready for you but your
husband is pressuring me cewa nan da
two weeks yake so ayi bikin su, and I
cannot do two things at the same time"
nayi shiru ban ce komai ba sai ya cigaba
"mun riga munyi magana da yaya mun
kuma yanke hukunci, amma ke ya kike
gani? I want to know your opinion" na
dago kai na kalli Daddy, bana son in fadi
abinda ba shine abinda ya yanke din ba
amma sai naga ya gyada min kai, I took it
to mean in fadi abinda yake raina, Nace "if
you can make the arrangements within
two weeks din shikenan sai ayi wannan
din first, Bikin sai a kara lokaci" ya kalli
Mukhtar da yake zaune a inda na taso yana kallon mu, maybe trying to guess
abinda muke cewa, sai yace "hmmm, your
husband isn't going to like that. Amma sai
dai yayi hakuri. Kamar yaushe kenan kike
so a saka bikin?" Na ji ina feeling very
uncomfortable. Ba zan iya maganar bikina
da iyaye na ba. Sai na juya na kalli
Mommy nace "Mommy uncle Ahmad
yana magana" sai na dawo da idona
O
kansa nace "Mommy will take care of
that. Maganar ta ce ba tawa ba" and I
instantly saw bacin rai a idon uncle
Ahmad. Amma kuma na lura hakan yayi
wa Daddy dadi.

Ta taho ta zauna a kusa da Daddy tana
tambayar sa menene, Daddy ya fara yi
mata bayani, nan da nan tace "at least
wata uku za'a saka" uncle Ahmad yace
"wata what?" Ni dai na mike na bar su da
wannan.

Mercifully tun kafin in zauna aka shigo
aka gaya mana mu fito, Ban jira komai ba
nay hanyar waje twins suka bi bayana
suka tsaya a sides dina muna tafiya tare,
Hassan yace "it was too hot in there, and
all the acs are working" Hussain yace
"zafinai bana gari bane ba, Mommy tana
ciki, uncle Ahmad yana ciki, how can it
not be hot?" Suka yi dariya a tare, na saka
both hannayena da daki jeyoyinsu a tare, Suka sake yin dariya sannan Hussain ya
miko min ledar hannunsa yace
"ga ice
cream ki sha ki sanyaya zuciyar kj" na
karba ina jin dadi a raina nace "thank you,
I really need this".

Sai bayan da na shiga na zauna na bude
ice cream dina zan fara sha sannan na
tuna ko kallon inda Mukhtar yake banyi ba
ballantana muyi sallama, and I didn't care.
Mommy ta shigo ta zauna a kusa da ni ta
cigaba da mita "wai sati biyu, kiji fa wani
rainin hankali. Ko yar tsana ai ba za'a yi
bikinta a cikin sati biyu ba. Da akwai
kayayyakin da ba zamu same su a Nigeria
ba sai munyi order, akwai mutane da
zamu gaiyata da suke bukatar noticed
tunda wasu ba'a kasar nan suke ba, ga
shi ba'a jima da bikin Safina ba mu kan
mu bamu huta ba, gashi......
." Na kwantar
da kaina ina kallon ta nace "Mommy relax.
You already had your dream wedding a
bikin Safina, Ni bana bukatar taro a nawa,
there is no going to be a dinner or any of
those bridal things, Sai dai in ku iyaye
zaku yi naku, Amma ni babu abinda zanyi"
ta ce "kina nufin kin amince da sati biyu
kenan?" Na girgiza kaina "no, Ba dai sati
biyu ba, Ina da abubuwa da yawa a gaba
na. Ina bukatar in huta kuma, Duk watannin da kike ganin sunyj" ta tabe baki
"na fahimci manufar Ahmad ai. Zancen
karbar dukiyar da kika yi shine ya jawo
wannan sati biyun, kinga yana nufin ko kin
karba zaki koma hannunsa ne daga ke har
abinda kike da shi. Ni na riga na gane duk
tactics dinsa, watarana kema zaki gane.
Fata na dai kawai ki gane da wuri tun kafin
ya zama late. Dan daga kun fara haihuwa
magana ta kare. And wannan marar
kunyar dan nasa......... Na tabbatar da
Adam lafiyar sa kalau, da ace da ne da sai
ya wanka masa mari yayi resetting brain
din dan iska...
Ta cigaba da surutan ta ni kuma na
kwanta na rufe ido na ina jujjuya maganar
ta da ta dauki hankali na. "Zancen karbar
dukiyar da kika yi shine ya jawo wannan
sati biyun, kinga yana nufin ko kin karba
zaki koma hannunsa ne daga ke har
abinda kike da shi" shin wannan shi ya
saka bai nuna damuwa ba kamar yadda
nayi tsammani ko kuma da gaske bai
damu ba din? In dai kuwa har abinda ta
fada shine plan din sa then he is really in
for a surprise, They all are really in for a
surprise,

Him
©️
22
10
2
8:25 PM
Sanda ya bar gidan su Safiyya his mind
was running in all different directions. Ya
kasa tsayar da tunanin sa guri daya. Ya
kasa fahimtar me ya faru. Ya kasa
fahimtar me ya far ballantana yayi
preparing for menene zai faru next. He
just saw Safiyya and they talked, more
calmly now then last haduwar su. But still
the calmness was from Safiyya not from
him. Ta hana shi cigaba da magana da
Daddy, and obviously that means bata
son Daddy ya sam tsakanin su and his
mind is telling him cewa dalilin ta is
deeper than him being her step sister's
husband or she being married. Akwai
wani dalili mai karfi aside those. And yana
so ya san menene dalilin.

And then she told him she loves him.
Kalmomin da suka ratsa fata, tsoka, katsi
da bargon sa suka shiga jinin dake
gudana a jijiyoyin jikinsa sannan suka
sauka a zuciyarsa, Casually ta fade su,
Maybe she didn't even think much before
saying them but sun yi matukar tasiri a
gun shi. He needed those confirmatory

words. Tunda abin ya faru lalube kawai
yake yi cikin duhu, thinking, analyzing and
making assumptions amma yanzu ya
samu tabbas. She loves him
Sai dai kuma sanin haka ya kara jefa shi
cikin rudani, menene ya faru da zai saka
ta ki auren sa duk da son da take masa ta
auri wanda da bakinta ta fada cewa bata
so? Menene ya faru da yayi stripping
dinta of all that makes her?
He just kept driving and passing
unguwanni without knowing exactly ina
zai je, idan yana cikin irin wanna yanayin
yana son yin driving especially a outskirts
of town inda babu traffic, it clears his
mind and increases the dept of his
thoughts.

Ya samu amsoshi da yawa a binciken sa
amma kuma a karshe ya hadu da dead
end, Safiyya ta toshe duk kofofin binciken
0?
sa, She said she wants him to accept and
face his fate, Amma kuma sai ta nuna
kishin ta a fili da ya ambaci sunan Safina a
matsayin fate din nasa, It is obvious cewa
auren sa da Safina yana damunta sosai.
Shima kuma yana damunsa sosai, sai dai
his hands a tied a yanzu, In dai har ba ya samo wata hujja kwakwkwara ba bashi da
damar rabuwa da Safina dan hakan zai
shafi alakar sa da mahaifan sa sosai. Yana
bukatar wani abu da zai presenting to
them a matsayin dalilin da yasa ba zai iya
zama da Safina a matsayin matar sa ba.
Kiraye kirayen sallah ne ya dawo dashi
hankalin sa ya juya kan motar zuwa
hanyar gida. Sai da yayi packing sannan
ya ga dauko wayarsa, sai a lokacin yaga
missed calls din Safina guda 5. Yayi tsaki,
shi ya ma manta da ita a gidan Mommy.
Yanzu kuma Mama zata ce sai yaje ya
dauko ta. Watakila ma already har ta kira
Mama tace mata ta neman sa bata same
shi ba.
Ya jira sai da yaga Abba da Haidar sun fito
zasu tafi masallaci sannan ya bude motar
ya fita ya bisu suka je suka yi sallah tare
suka koma gida, Yana zama a falo Haidar
ya fara tsokanar sa "anya kuwa wannan
amaryar ta iya girki? Kullum sai kazo ka ci
mana abincin gidan mu?" Yaji ranshi ya
baci duk kuwa da cewa ba abin bacin rai
Haidar din ya fada ba, Mama ta karaso
inda suke da charbi a hannun ta tana
cewa "muryar wa nake ji ne anan, Gidado no banga amfanin wayarka ba wallahi.
Gabakidaya yanzu ka chanja hali sai a
kiraka sau goma ba zaka amsa ba, idan
kuma emergency ne ya faru fa? Mutum ya
ajiye iyali amma baya daukan waya?" Bai
vi kokarin kare kansa ba sai ya gaishe ta,
ta amsa sannan tace "dazu Safina ta kira
ni tana tambayar ko kana nan nace mata
ba ka nan, ta kira wayarka baka dauka ba
ni ma na kira ka baka dauka ba" yaji
haushin Safina ya karu a zuciyarsa, yace
"'ai ta san ina tare da mutane, niyya ta in
zan tafi gida in biya in dauke ta mu tafi"
Mama ta bishi da kallo tana lura da yadda
ransa yake a bace. Sai tayi shiru bata
sake cewa komai ba. Abba yace "ka bata
waccan motar ta ka da baka hawa mana,
ka huta da kaita unguwa da kuma
daukota" "to"' kawai Muhammad yace ya
sake yin shiru zuciyar sa tana burning a
kirjinsa, so yake kawai ya samu abinda zai
daka yaji dadi. Mama ta sake cewa "tun
dazu ta kira ni wallahi, da yake tana da
kunya shi yasa bata gaya min jiransa take
yaje ya dauke ta ba ta dai ce min ta kira
number din sa bata same shi ba,
19
12
2
8:25 PM
Kuma tunda bata saba da mutanen gidan
ba kamar she sounds uncomfortable".

Muhammad ya mike da sauri ya dauki key
din motar sa yayi hanyar waje, Mama tace
"ka fasa cin abincin ne? All through yau fa
ina jin baka ci abinci ga idanunka nan duk
sun fada" ya juyo "na fasa cin abincin
tafiya zanyi. It seems like you people
don't want to see me here anymore.
Gwara in tafi in bar muku gidan ku".
Gabakidaya suka saki baki suna kallon
shi, bai taba yiwa Mama magana irin haka
ba. Sai kuma yayi realizing da wa yake
magana yaji wani iri a zuciyarsa. Ya dawo
a hankali ya koma ya zauna tare da dafe
kansa. Abba yace "Gidado lafiya kake
kuwa? Menene ya hau kanka yau?" Mama
kuma tace "Muhammad waye a bata
maka rai haka?"

"Am sorry" ya fada a hankali sai kuma ya
sake tashi ya tafi dinning table ya fara
zuba abinci not knowing me yake zubawa
ma. Mama ta biyo shi ta karba tana zuba
masa sai ya koma ya zauna, ta ajiye masa
plate din a gabansa sannan tace "me
yake damun ka Muhammad? Talk to me"
ya fara jujjuya spoon din hannunsa yana
kallon ta, shi ya san the moment da ya
ambaci sunan Safiyya gabaki daya sai
rayukan su sun kara baci, maybe ma cewa zata yi akai shi gidan malamin ruaya ayi
masa.

Ta sake tambaya "Safina ce? Are You not
happy with her?" Ya sake yin shiru yana
tunanin iyakacin abinda ya kamata ya
gaya mata, at the end yace "I just don't
like her" tayi ajjiyar zuciya
"Muhammad...
..... Don't you think it is a
little bit too late for that? Tun kafin a fara
maganar nan sai da aka turo maka
pictures dinta ka ganta, and then you
went to gidan iyayen ta ka sake ganin ta
face to face sannan kace ka amince
sannan aka fara maganar nan. Abban ka
yace har a day to daurin aure sai da ya
tambaye ka idan ka amince ace masa ka
amince. Sai yanzu bayan an daura har ta
tare sai kace bata yi maka ba kuma? Will
it be fair to her and to her parents idan
muka ce an fasa kuma yanzu? Ko wata
behavior tayi maka yanzu da ta saka kaji
haka?"

Bai bata amsa ba Abba da Haidar suka zo
gurin, Abba yana kallon sa yace "kaga
dan lelen mamansa, ta zauna tana ta
lallaba shi kamar wani jariri. Ko Mufida
ba'a lallabawa haka" Haidar yace
"'ballantana ni" daga Muhammad har
Mama babu wanda yayi magana, Muhammad ya fara cin abincin da ta zuba
masa yana hadiye wa kamar mai shan
magani ita kuma tayi tagumi tana kallon
sa, babban tashin hankalin ta a duniya
shine taga yayanta cikin damuwa, babban
burinta shine yayanta suyi living a happy
and fulfilling life. And she is determined to
get that for them in all the possible halal
ways.….

Suka gama in abincin sannan suka dawo
falo suka zauna, ganin basu sake yi masa
maganar ya tafi ba sai yayi kwanciyar sa
akan kujera yana jin dadin presence din
iyayen sa a yare da shi da kuma muryoyin
su suna tattaunawa akan random issues,
har akayi sallar isha, ganin bashi da niyyar
tashi kuma bata son matsa masa sai
Mama tace
"Haidar tashi ka dauki mota
kaje gidan Mommy ta dauko Safina ka
taho da ita nan gidan"., Muhammad yana
jin ta fadi haka sai ya gyara kwanciyar sa
aka kujera ya chanza tasha a tv, amma
maimakon yayi kallon sai ya mayar da
idonsa ya rufe,

Yana nan a kwance har yaji tsayuwar
motar Haidar ya dawo, yaji shigowar sa
sannan yaji sallamar Safina, ta gaishe da
Abba sannan ta gaishe da Mama, Yaji
Abba yayi musu sallama ya shiga ciki, sai
kuma yaji Mama tace "sannun ki, kin sha kuma yaji Mama tace "sannun ki, kin sha
zama" Safina tace "babu komai Mama"
and he noticed muryarta tayi kasa sosai.
Mama ta fara kokarin tashin sa
"'Muhammad Gidado" ta fada tana shafa
kafarsa, sai kuma ta danyi dariya
nervously "yayi bacci. Abin mamaki.
Muhammad baya bacci akan kujera. In dai
kinga yayi bacci to sai yayi wanka ya
chanja kaya ya kwanta akan gado, ba'a ko
ina yake yin bacci ba. Kinga mai bacci nan
a ko'ina. Shi wannan ko akan siminti ne
kwanta yayi bacci" ta fada tana nuna
Haidar, Haidar yace
"haba Mama kar ki
tona min asiri mana" Mama ta sake taba
Muhammad "Muhammad ka tashi fa, dare
yana kara yi" Safina tace "maybe he is
exhausted" Mama tace "ai kuwa dolr ya
tashi, wannan kwanciyar ai sai jikinsa yayi
ciwo. Muhammad!" Ta fada da dan karfi
tare da taba fuskarsa.
24
6
4
8:25 PM
Yana bude ido suka hada ido da Safina, ya
dauke idonsa daga nata sannan ya tashi
zaune, Mama tace "ka tashi ka bar yarinya
tana ta hamma ta gaji" ya mike tsaye
sannan involuntarily yayi mika. Haidar yayi
dariya "wai! Wa yaga zangina ba da sunan
wani ba" Mama tace "tubarkallah"
Muhammad ya juyo yana kallon sa ya
hade rai yace "yaushe na fara wasa da kai?" Sai kuma yayi wa Mama sallama
sannan ya dauki key din motar sa yayi
waje ba tare da ya kalli inda Safina take
ba.

Yaje ya kunna motar ya kunna kida
sannan yayi zamansa a ciki, yana kallon ta
ta fito ita kadai ta taho zata bude kofar
motar sai yayi locking sannan ya dauke
kansa gefe kamar bai san tana gurin ba.
Tayi knocking window din motar sai ya
kara volume din kidan da ya saka. Ta ja
gefe daya ta tsaya kusan five minutes
sannan ta zagayo side din da yake ta sake
knocking, ba tare da ya kalle ta ba ya
bude lock din sannan ya nuna mata kofar
da hannun sa, sai da ta sake zagayawa
sannan ta bude ta shiga. Tana shiga kafin ta gama rufe wa ya ja
motar, tayi sauri ta rufe kofar tana kallon
sa da mamaki, sai a lokacin ya lura da
cewa kuka take yi, hawaye ne shabe
shabe a fuskarta, Suna daukan hanya
tace "ka kaini gidan mu" bai kalle ta ba
yace "sai dai in ajiye ki anan ki samu
motar da zata kaiki tasha ki tafi Katsina"
tace "ai ba'a Katsina ka dauko ni ba" ya
juya yana kallon ta yace "actually ba'a ko
ina na dauko ki ba, Ke kika zo da
kafafuwan ki. In zaki tafi ma da kafafuwan ki zaki tafi" tayi shiru bata sake cewa
komai ba suka cigaba da tafiya, sai kuma
yace "nan gurin yayi ko in kara gaba? A
ina ne inda zaki fi samun abin hawa? Ko in
ajiye ki zaki karasa da kafarki" ta goge
hawayen fuskarta da yaki tsayawa tace
"why do you have to this mean? Da me
kake so inji Muhammad? Kana so in mutu
ne wai?"

Yace "you bought it da kudin ki. Da kudin
ki kika saka kika sayi duk abinda nake yi
miki, and I will keep delivering what you
bought har sai ke da kanki kince ya ishe ki
haka kin koma gidan ku"

Ta cigaba da kukan ta "Mommy tace min
kaje gidan mu, and you said wai na baka
sako ka bawa Fiyya. Ashe dama wajanta
zaka je kace wani business issues ne?
Muhammad matar aure ce fa. Ba ka
tsoron abinda Allah zaiyi maka akan
hakan? Baka tsoron abinda Allah zai yi
maka akan abinda kake yi min?" Yace
"point of correction, Dazu naje gidan su
Piya ba gidan ku ba, Why are you
associating yourself with them bayan you
didn't consider them important enough
kiyi mentioning dinsu to wanda zaki aura?
Ke fa kika ce min ke yar Katsina ce. Ta ya
akayi kuma gidan da yake Abuja ya zama gidan ku?" Bata amsa ba, ya sake cewa
'"kina son jin maganar da muka yi ne?"' Ta
dauke kanta gefe "kaji tsoron Allah. Allah
yana kallon ka, and kayi tunanin abinda
Mama da Abba zasu ce idan suka sanj" ya
taka burki da saurin da sai da ta kusa
buga kanta a jikin dashboard, ta juya tana
(
kallon sa ta ga ya hade rai kamar bai san
kalmar imani ba yace "this will be the first
and the last time da zaki yi threatening
dina, and dazu will be the first and the
last time da zaki kai magana ta gurin iyaye
na. I don't joke with my parents and I
swear you will regret knowing me idan
kika yi trying hada ni da su".

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹


Episode Thirty Six: The Boss Lady


(©️
243
X
Wani tsoron sa taji ya kamata, ta dauke
idlonta daga cikin nasa ta sauke su a kasa,
ya maimaita cikin tsawa "do you
understand?" Ta gyada kai da sauri tana
jin wasu sabbin hawaye suna biyo cheeks
dinta. Ya ja motar suka cigaba da tafiya
yana jin ransa yana kara baci, yarinyar nan
ba karamin raina masa hankali ma tayi ba
wallahi, wai har shi zata yi threatening
cewa zata gaya wa iyayensa maganar
Piva?
Amma kuma a kasan zuciyar sa ya san
toro ne ya kara masa bacin ran, he just
couldn't imagine bacin ran da Mama zata
shiga idan taji cewa har yanzu bai rabu da
Safiyya ba duk kuwa da irin rabuwar da
suka yi da kuma kasancewar ta matar
aure, duk kuwa da auren da suka rufe ido
suka yi masa shima, Maybe ranar kwana
zata yi tana kuka, And he will never let
that happen ko da kuwa a mafarki ne.
Ian Safina kuwa tayi gangancin faruwar
hakan to tabbas sai dai taje asibiti a saka
mata hakoran roba dan sal ya zubar da wadanda suke cikin bakin ta.
Babu wanda ya sake cewa komai a cikin
su har suka shiga gida suka yi packing.
Sai kuma duk suka zauna a motar basu
fita ba. Ya juya ke nan zaiyi mata bala'in ta
fita ta bashi guri sai ita ma ta juyo tana
kallon sa da kumburarrun idanun ta tace
"Kayi hakuri Habibi, na ga ranka ya baci
sosai akan maganar su Mama. I will never
do abinda ba ka so. Ko da kuwa kai zaka
cigaba da yi min abinda bana so ne" ya
girgiza kansa cikin mamaki "you are one
darm manipulative woman. Ba zakiyi
abinda bana so ba kika ce. And the first
thing da kika yi a rayuwar mu da ke was
abinda na gaya miki point blank cewa
bana so, and it turned out to be the only
thing da kika iya yi, karya. You are a liar
and it seems like you will always be a liar"
ta saka yatsun hannunta da har lokacin
suke duke da lallen bikin ta ta goge
hawayen fuskarta tace "you are really
hurting my heart. Allah shine shaidata. Ni
banyi maka karya ba" yace "get out of my
car" ta bude kofa ta saka kafafuwanta a
waje zata fita sai kuma ta juyo tana kallon
sa tace "wannan amsar da kake ta nema,
It looks like ba ka same ta ba yau ma, And
knowing kun hadu da ita tells me cewa ta
toshe hanyar samun amsar ta ka kenan,
Meaning she lied to you again, And here you are shouting at poor Safina cewa ba
ka son karya" ta karasa fita daga motar
dan kallon da yayi mata anything can
happen in ta cigaba da zama kusa da shi.
Amma maimakon ta rufe kofar ta tafi sai
ta cigaba da magana daga waje "na san
amsar, amma ba zan gaya maka ba
saboda dalilai uku. Na farko saboda ina
sonka bana son abinda zai bata maka rai.
Na biyu saboda ka riga kayi tagging dina a
matsayin makaryaciya dan haka ko na
fada ma ba zaka yarda ba, gwara ka ji a
wani gurin. Na uku kuma because you did
not ask me nicely, try asking me nicely,
watakila in gaya maka" sai kuma tayi sauri
ta juya ta yi cikin gida har tana hardewa
saura kadan ta fadi. A ranta tana jin dadin
ko babu komai yadda zata kwana da
takaici haka shima zai kwana da shi.

Ya bita da kallo har ta shige ciki ta mayar
da kofa ta rufe, a zuciyarsa yana mamakin
audacity irin na Safina. Ya tabbatar ba
dan gudun bacin ran iyayensa ba da ace
zuciyar sa zai bi da either Safina ta kwana
a asibiti ko kuma a gidan babanta, or
better put, gidan baban Safiyya,

Ya jima a zaune a motar kafin ya tashi
shima ya shiga nasa part din. Kamar
yadda Safina tay target, duk su biyun ba su samu nutsatstsen bacci ba. Part of him
knows that gaskiya Safina ta fada cewa
Safiyya tayi masa karya, amma ya rasa
dalilin da yasa baya daukan karyar tata a
matsayin babban laifi kamar yadda yake
daukan ta Safina. Yana yi mata uzuri
saboda yana son ta, yana son ta sosai. Sai
ya fahimci cewa babban weakness dinsa
a rayuwa shine Piya. Ya tuna sanda suke
tare sau da yawa yana gaya wa kansa
haka, yana gaya wa kansa cewa idan suka
yi aure dole ya san yadda zai ringa
tankwara ta akan abinda yake ba dai dai
ba., Amma a zamanin soyayyar su duk
abinda tace shikenan magana ta zauna ko
da kuwa a zuciyarsa ya san ba hakan ya
kamata ayi ba.

Ya tuna watarana da tazo office din
sa………

"Yaya Muhammad"

Ya dago kai da sauri tare da sakin baki
yana kallon ta, Ta sake maimaitawa

"'Yaya Muhammad dina"

Ya ajiye biron hannunsa yana dariya

"Wonders will never end in this world, Yau
kuma Yaya na koma? Ina kika bar Malam
Muhammadu dan fillon and the rest of the
names you used to call me"

Ta zauna akan kujera tare da langwabe
wuya ta turo baki. Yayi tagumi da hannu
daya yana kallon ta fuskar sa da
murmushi, ya lumshe idonsa yace "those
lips
........ I wonder what they taste like" ta
mayar da su da sauri sannan ta mike ta
dauki jakarta tayi kamar zata fita, yana
dariya yace "sorry fiyyan Daddy, na daina
tsokanar ki, zo ki gaya min me ya faru" ta
tsaya a bakin kofa, dama kuma bata yi
niyyar fita ba barazana ce kawai. Sai ta
juyo ta nuna shi ta ce "zan rama, Ka
rubuta ka ajiye" yace "ba damuwa, Bana
jin tsoro, Ina nan ina jira" ta koma ta
zauna tana kallon sa tana jujjuya
hannunta, yace "uhumm, ya akayi?
What's up with all the lallabawa and the
Yaya Muhammad" tace "dama wan labari
zan baka, Kana ji ko? Uhmmm, biki ne za'a yi next weekend a gidan su Safina
yace "your step sister?" Tace "yes, to
za'a yi bikin half sister din ta. Shine
Mommy tace mu shirya mu tafi muyi sati a
can. Zasu z0 su dauke ni this weekend sai
mu wuce" tayi shiru, ya gyara zamansa
yana juyi akan kujera yana studying dinta,
she looked disturbed, ta jima sannan ta
karasa maganar a hankali '"'I don't want to
go" ya ajiye pen din hannunsa yana kallon
ta yace "then tell Daddy. Ki gaya masa ba
kya son zuwa shikenan" ta kwabe fuska
tana shirin sa kuka tace "na gaya masa ai,
sai yayi min hayaniya a waya wai sai naje"
yace "okay then go. Menene abin
damuwa a ciki? You guys have been living
together for years. Kun saba. And Daddy
wants you to go da haka yana da dalilinsa.
Kiyi masa biyayya mana ki je" "I don't
want to go" ta sake maimaitawa. Yayi
ajiyar zuciya, ya san wanna fuska, ba
zata je ba. Yace '"to yanzu menene nawa a
ciki? What's with the Yaya Muhammad
thing" tayi murmushi tare da gyara
zamanta tace "yauwa. Dazu na gayawa
Daddy cewa ina da test har guda four a
next week, amma sai yace karya nake yi
tunda already na gaya masa bana son
zuwa" yace "and he is right" tace "yes,
but I want him to believe cewa da gaske
nake" ya sake cewa "ni fa har yanzu ban gane role dina a wannan maganar ba"
tace "so nake ka rubuta takarda, using
the school's letter heading and stamp,
cewa next week satin c.a ne dan haka ana
bukatar kowanne dalibi ya kasance a
present, wanda baya nan ba za'a yi masa
make up c.a ba".

Ya bude ido "Piya? What's lying and
forgery, it can cost me my job" tace
'"makarantar ta su waye?" Yace "ohh, kina
nufin uncle Habib will take it lightly with
me idan ya kama ni da wannan laifin?"
Tace "it is not as if zamu kafe takardar ne
a notice board, Daddy kawai zan turawa a
waya ya gani shikenan" ya girgiza kansa
am not going to do it Piya. Ba zamu hada
baki muyiwa Daddy karya ba. In ya gane
ba zai ji dadi ba kuma ba zai kuma yarda
da maganar mu ba" desperately tace
"please 🥺"' ya sake cewa "no. And I
mean no. Magana ta kare".

Ta cigaba da zama tana hararar shi shi
kuma ya jawo system dinsa yana
daddanna wa pretending as if bai san
hararar sa take yi ba, Sun jima a haka
sannan tace "dama ni damuwa ta shiga
cikin bikin ne. Naga sun shirya a lot of
dinners and parties, I just don't want to mingle with mazan gurin. Ka san samari in
suka ga yammata sababbin fuska......
Amma tunda ba zaka yi min ba I will just
have to go and mingle with them" ya
danyi murmushi sannan ya dago yana
kallon ta, ta dauke kai gefe alamar tayi
fushi, yace "I understand what you are
trying to do. You are trying to get to me
and I will not let you" ya cigaba da danne
dannen sa. Ta juyo tana kallon sa ta sake
cewa "Please mana Yaya Muhammad,
haba mana" ya sake cewa "no! We will
not do it"
20
16
2
10:12 PM
But five minutes later har ya gama rubuta
takardar yayi printing, tana tsaye a kusa
da shi fuskarta kamar gonar auduga, ya
dauko biro yayi signing a inda ya kamata
ayi signing a grin. Ta miko hannu zata
karba "thank you, thank you so much" ya
janye takardar "uhmm uhmm. I am not
going to give it to you" ta bata rai sai va
wuce ta zuwa dan karamin board din da
yake kafe a office din nasa ya dauko pin
ya makala takardar a jiki sannan ya dauki
wayarta da take ajiye akan desk dinsa,
fingerprint dinsa yana iya budewa kamar
yadda nata yake bude wayarsa, ya bude
wayar sannan ya dauki hoton takardar da
take makale a jikin board din. Ya mika mata wayar, "Send the picture to him, sai
kice masa a notice board aka kafe muku"
ya yage takardar da ya kafe ya yayyagata
ya zuba a waste bin.
Ta cigaba da murna, yace "it is still a risk,
idan bai zama convinced ba he can get
worried and start to investigate" ya danyi
murmushi kuma sannan yace "but on a
positive note, in aka kamu mu I may finally
get to meet Daddy. Shi yasa mana saka
signature dina" ta bude ido "what??" Ya
daga mata gira yana murmushin "yes! It is
an invitation. And you will be the one to
take the risk of sending it".

But his invitation wasn't accepted. Daddy
believed Piya and didn't investigate. Now
here they are one year later. She married
to her cousin and him married to her step
sister.

** . . . . **

Ganin baccin ba zai yiwu ba and the
burning in his heart yana karuwa sai ya
tashi yay alwala ya kama sallah dan ya
sanyaya zuciyar sa, Washegari yana tashi
yayi ordering for gym equipments, sannan
ya fito with the help of maigadi suka
kwashe kayan da suke spare room dinsa
suka saka a store sannan suka yi getting the room ready to be his private gym. And
it became his solace during the evening
hours and on weekends. On work days
kuma ya mayar da hankali sosai akan
aikinsa har sai da Abba da kansa ya yaba
masa, but shi duk yanayin wadannan ne
to keep his head straight and his mind
occupied.

Her🧕


First two weeks din mu a Kano nayi
spending din sune wajan taking very good
care of myself, care of my physical and
mental health. Tun two days da zuwan mu
gari naje asibiti na ga Dr Salma na gaya
mata what have been happening so far
and I also told her about the car opening
scenario with Mukhtar. SHe wasn't as
concerned as I thought she would be. Ta
fada min cewa ina healing sosai tunda har
nazo da kaina na bata labari, and she also
noticed chances a confidence dina tun
daga yadda nake yi mata magana. Sai ta
bani antidepressants to help me control
my emotions sannan kuma ta bani
sharawar inyi avoiding anything that will
trigger my emotions,

Sai dai wannan ne kuma nake ganin
kamar da wuya, Because I am surrounded
bv emotional beinas, Mommv kullum cikin korafi take akan maganar biki na "wannan
ai son kai ne wallahi. Kiri kiri sun nuna dan
su suke so basu damu da ke ba. Shikenan
dan yace ga ranar da yake so a akai mishi
ke sai kawai a dauke ki kamar wata yar
tsana a kaki? Shi kuma Daddy yaki cewa
komai. Ni kuma ko sama da kasa zasu
hade ba za'a bikin nan a kasa da wata
biyu ba". And Daddy was always like "ki yi
kokarin gyara tsakanin ki da Sa'adatu da
yayanta. Sune family dinki a yanzu. Bana
son duk wani abinda zai jawo baraka a
tsakanin ku. And then in na kebe kaina to
get away from them, sai tunanin
Muhammad ya addabi zuciya ta, tunanin
Muhammad da Safina a gida daya, daki
daya kuma akan gado daya. And that
thought kept my nights long.
On the other hand kuma ga Mukhtar da
ya addabi rayuwata, sometimes I even
find myself questioning my decision to
marry him, amma kuma in ba shi ba wa
zan aura? Daddy has limited my options.
A raina ina jinjina girman kaddarar da take
tunkaro ni, Kaddarar zama da Mukhtar a
gida daya a daki daya a kan gado daya,
And that thought kept my days long, Daga baya dai Mommy ta gaya min sunyi
reaching agreement da su uncle Ahmad
akan tariya ta, sun saka six weeks from
ranar da muka taho daga Kano. Daga nan
kuma sai ta zama busy, ita ce Abuja ita ce
Lagos ita ce Kano, ranar nan mace min
tayi Maiduguri zata je. "Akwai turaruka da
kayan gyaran jiki na amare da zanje in
karbo miki, akwai friend dina da na saka
tayi min order dinsu daga chadi, ita ta
kawo wa Safina ma a lokacin bikinta" nace
"Mommy ai ba sai kinje ba. She can send
it to you ai" ta girgiza kai "gwara inje dan
in tabbatar an hada min komai. Bana son
mistake". Sai na fahimci ba wai dan ba
za'a iya kawo mata sakon bane ya sa zata
5 je ba, ita kawai bata iya zama ne a guri
daya.
Kamar yadda muka yi da uncle Ahmad,
two weeks da zuwan mu Kano suka zo
gabaki dayan su. Duk wanda yake da
ruwa da tsaki (stakeholders) a cikin affairs
din dukiyar Ammi yazo kano a ranar.
Dama tun two days to the day uncle
Ahmad ya kira ni ya sake tabbatar min da
zuwan nasu, muna gama waya da shi sai
kuma Mukhtar ya kira ni shima ya gaya
min cewa uncle Ahmad ya nemi ya shirya
su taho tare "I just want to let you know ni
zuwa zanyi dan in ganki, I have no
business with taron da zaku y", Muna
gama wayar na zauna ina murmushi ina kuma juya wayata a hannuna. People are
so predictable.

Ranar da zasu zo din ban tashi da wuri ba
sai da nayi dogon bacci dan in samu
nutsuwar da nake bukata. Ina tashi
Mommy ta shigo tace Daddy yace a gaya
min bakin sun fara zuwa. Na tashi navi
wanka na shirya in another of my
mother's attire, ba wai dan bani da
wadanda suka fi su ba sai dan ina bukatar
ta a tare da ni, anything that belongs to
her gives me courage. Na dauko wata
sarkar ta itama na saka, dan karamin
43
pendent ne with matching earrings, it is
simple, classy and unique. Na saka rings
guda biyu a yatsun hannuna sannan na
yafa mayafi na na fito. Ina fita naga
Mommy a zaune tana kallon hanyar da
zan fito, muna hada ido tayi murmushi
tace "you look good, sai dai baki ci abinci
ba" nayi mata murmushi nima nace "| am
fine Mommy, in na dawo sai in ci" dan a
lokacin ji nake yi abinci ba zai iya wucewa
daga makogwaro na ba,
Na sauka kasa cikin tafiya ta nutsuwa ina
kara tattaro courage dina sannan na bude
kofar falon Daddy inda anan na san bakin
zasu zauna,

Ina bude kofar duk suka juyo suna
kallona, naji kamar in mayar da kofar in
rufe sannan in ruga da gudu in koma daki
in lulluba a cikin bargo and become the
little girl I once was. Sai dai na san hakan
is not possible. Na san cewa wancan
lokacin ya riga ya wuce ni. And then I
understood gatan da Daddy yayi min da
ya boye min all these maganganu ya barni
nayi normal childhood dina. Bai bari na
sani ba sai lokacin da yake tunanin I am
old enough to handle it. That I am old
enough to understand. Lokacin da na cika
shekara ashirin a duniya. Few months
after his diagnosis.

*. *. *. *. ***

2 years ago…..

Ranar birthday na ne, ranar da na cika
shekaru ashirin a duniya. Daddy ya shirya
min dan karamin birthday party and I was
O?
so happy saboda shi ba mutum bane mai
irin wadannan abubuwan, abu in dai na
bidi'a ne da shagali to aikin Mommy ne,
But that day shi yayi min komai kuma naji
dadin hakan sosai, iyakocin mu yan gidan
ne kawai yan partyn nawa, sal
photographers da suka zo suka yi kin pictures, suka kuma dauke ni tare da yan
partyn nawa su Safina da Mustapha da
Mommy da twins da kuma Daddy.
Amma kuma ga mamaki na sai naga uncle
Ahmad yazo shima, daga alama kuma tun
daga Abuja yake, a tare da shi kuma
akwai wadansu mutane su biyu. They all
smiled and nodded at me amma kuma sai
zuwan nasu ya saka ni na zama
uncomfortable. Ina tunawa cewa sanda na
yanka cake dina na gutsira naji dadin sa,
the first thing that came to my mind was
Muhammad, a take na yanke shawarar
zan yanki cake din in yi masa preserving,
in zan koma makaranta in tafi masa da
shi.

Bayan na gama ne Daddy yace a zo a
zauna ayi min addu'a. Muka zazzauna
gabaki dayan mu har bakin da ban sani
ba. Uncle Ahmad yayi min addu'ar tsahon
rai da rayuwa mai albarka muka shafa sai
naji Daddy ya fara magana.
17
8
10:12 PM
"Alhamdulillah, Allah shine abin godiya,
Tun muna lissafawa Safiyya kwanaki a
duniya har muka koma lissafa mata
watanni sai kuma aka fara lissafin shekaru yanzu gashi har tayi ashirin. She is now a
big lady"
' '"'gir'" na fada ina dariya, yayi
murmushi shima yace "big girl. Ita bata
son ta girma. Tafi son kullum tayi ta zama
a yarinya tana ta yi mana shawaba muna
lallaba ta. But it is not going to continue
like that. Dole ki mike ki karbi girma ki
kuma karbi nauyin da Allah ya dora miki.
Nauyin da mahaifiyar ki ta dora miki"
Jin ya ambaci mahaifiyata sai ya fahimci
he was talking about something else,
something serious. And then he said it.
'"Bayan haihuwar ki, she transfered
everything da take dashi to you, as a gift.
Everything" nayi shiru ina kallon sa,
analyzing and deciding menene
everything din. Kayan dakinta? Kayan
sakawarta? Maybe her car and a little
change da take da shi a bank?

And then one of the men da suka zo tare
da uncle Ahmad said it "wannan ya hada
da half of all your father's companies, a
share in The Glitters Gold Company, a
share in ........
," He kept talking and talking
har sai da naji kaina yana ciwo, naji my life
tana turning upside down, naji bana
fahimtar komai, Sai da yayi shiru sannan uncle Ahmad ya
cigaba "wannan abubuwan da aka lissafa
was at the moment of the transfer of
ownership, bayan rasuwar ta mahaifinki
yayi making some changes, an siyar da
abubuwan da muke gain ba zasu yi miki
amfani ba kamar motoci da sauran
kananan kadarori, an kuma siyar da
wadansu daga cikin kananan hannayen
jarin da muke gain babu riba mai kyau ta
long term a tare da su sai aka hada da
cash din da yake hannu a lokacin aka kara
akan wadanda muke gain sun fi long
term benefits. Wadannan sun hada da
kamfanonin mahaifin ki guda biyu da
kuma gold company din can. Karin da aka
yi sai ya saka tun a lokacin share din ki a
lokacin ta fi ta mahaifin ki yawa a cikin
both of the companies.
Na saki baki ina kallon shi tun da ya fara
har ya kai aya, sai kuma naji Daddy ya
cigaba, na juya na cigaba da kallon sa
shima,

"It has been 18 years now da akayi
making wadancan changes din, and a lot
of things have also changed daga lokacin
zuwa yanzu, Her shares have increased
massively, while mine have reduced. A
yanzu da nake muku magana Safiyya
owns.……." Sai ya juya yana kallon daya
mutumin da bai yi magana ba, mutumin ya bude takardar gabansa ya duba
sannan yace "91%" ya rufe yana kallon na
directly yace '"91% of everything"

Daddy yace "yes, everything. Except for
wannan gidan da muke ciki da motocin da
muke hawa da kuma gidan mu na Abuja.
Those are mine."

Uncle Ahmad yace "yes, and she also
have the sole ownership of The Oasis"
mutumin da yayi magana da farko ya sake
bude takardun gabansa yace "bayan The
Oasis tana da gona guda uku da land
guda biyu daya a Kano daya a Abuja and
other personal items"

Daddy yace "wadannan ba sune damuwa
ba. Tunda sole ownership ne, damuwata
shine wadanda muke tare da ita, I want to
clear everything with the rest of my family
members tunda ba'a san gobe ba. I want
her, my wife and my other kids to know
dan gudun samun rashin fahimta nan
gaba, tunda..."

Dariyar Mommy ce ta katse masa
maganar sa, duk muka juya muna kallon
ta, sai da ta gama dariyar sannan ta
girgiza kai tace "wato wannan shine plan
dinka kenan Adam, wannan ita ce sakayyar da kake gain zaka yi min kenan
ko?" Daddy yace "mind your tongue
Sa'adatu. Wanne plan kuma? I didn't plan
any of this. Abinda Allah ya tsara mana
dole shi zamu karba. I have...."
.." Tace "you
have always love Safiyya fiye da kowa da
komai a duniya. You have never cared
about me and the kids I birthed for you
ballantana wadanda ba naka ba. Na dauki
duk discrimination dinka saboda nasan
cewa ita marainiya ce shi yasa kake bata
special treatment dan kana gain kamar
ni bana kulawa da ita yadda mahaifiyar ta
zata yi mata. I have accepted that but I
will never accept this. Ba zan taba yadda
dan ciwo ya same kaka dauki komai da
kake da shi kace nata ne ba. Mu kuma fa?
Yayan ka maza kuma fa?"
13
13
10:12PM
Yace "ba dauka nayi na bata ba. Dama
nata ne. You already know. Tun mahaifiyar
ta tana da rai kin san cewa ta bata dukiyar
nan" Mommy tace yes, na san ta bata
abinda take da shi a lokacin. But kaima ai
da akwai naka a ciki, Na ka ma yafi nata
yawa, Yaya za'a yi kuma ace min nata ya
karu naka ya ragu bayan tare ake juya
kudin, bayan tare ake raba ribar, Me yasa
nata zai karu har ya kai 91% kai kuma
naka ya ragu har ya koma 9%. Wanne irin lissafi ne wannan kamar ana so a nuna
mana ba muje makaranta ba?"
Daddy yace "Okay, tunda kin nemi bayani
bara inyi miki gwari gwari. Nata yayi
wannan karuwar ne saboda for over 20
years da muka hada kudi muka bude
wadannan kamfanini bata taba ciran ko da
kwamdala daga ciki ba. Sai ma karawa da
akayi bayan rasuwar Safiya. Duk ribar da
aka samu a cikin tsahon shekarun nan
akan jarin ta ake kara mata. Ni kuma fa?
Kudin nan da su nake yin komai da su
nake yi muku komai. All the extravagant
spendings, all the holiday vacations da ba
kya yin watanni uku cikakku baki fita wata
kasar ba daga cikin kudin ne, all the cars
the latest gadgets, the bukukuwa duk a
cikin kudin ne. All the kudin makarantar
yara da ba kya so a saka su a kowace
makaranta sai wadda tafi kowacce tsada,
Mustapha da kika dage sai a kasar waje
zaiyi karatu duk a cikin kudin ne. I have
ER
used all the money you are asking about
to take care of you and the kids. Yanzu
abinda ya rage min bai fi wanda zan rike
ku zuwa sanda ciwon nan zai karasa ni
ba. And that's idan kin ajiye wannan life
style a gefe",

Tace "okay, yanzu laifi na ne kenan? Laifi
na ne that we know have nothing?" Uncle
Ahmad yayi gyaran murya yace
"Wadannan maganganun are private
issues, muna tare da baki so let's calm
ourselves mu gama abinda ya kawo su, in
sun tafi sai mu tattauna sauran batutuwa"
Daddy yayi ajjiyar zuciya yace "as you all
know yanzu bani da lafiya, and it is a
terminal illness da zai cigaba da cina till I
am no more. So for now, every affair will
be handed by Ahmad, abinda ya shafi
dukiyar Safiyya da abinda ya rage min duk
zai koma hannun sa zuwa sanda Safiyya
zata mayar da hankali ta gama makaranta
sai ta karbi abinta"
Mommy ta cigaba da magana "wallahi da
sake. Wannan abin da kuke fada abu ne
da ba zai yiwu ba ko a mafarki. Chafdi"
Babu wanda ya kula ta. Sai naga daya
daga cikin bakin ya taso yazo gabana ya
durkusa yana kallon fuskata yace "it is
really nice to see you again Safiyya Adam.
I knew and worked with your mother tun
tana yin unique mix, da special awara" yayi
murmushi "tun tana Safiya Haladu kafin ta
koma Safiya Khalid, She is an amazing
woman, And you are going to be an
amazing woman too, I am looking forward to working with you as well" sai ya dauko
wani card a aljihunsa yayi rubutu a bayan
sa ya ajiye min a gaba na yace "this is my
complimentary card, akwai duk
information dina a jiki, ga kuma private
phone number dina nan itama. You can
call me anytime you want in kuna da wata
tambaya ko wani legal issue concerning
wannan maganar or any other one".
Na dauki card din sannan na dago na kalle
shi, for the first time tun da aka fara
maganar nayi magana nace "thank you"
ya mike ya koma inda yake ya sake zama.
Mommy ta sake cewa "chafdi. Babbar
magana" still babu wanda yace mata
komai.
Uncle Ahmad yace "akwai mai tambaya?
Safiyya? Do you have any question?"
Kowa yayi shiru babu wanda yace komai,
zuwa can sai Mustapha yayi magana "ina
da tambaya" uncle Ahmad yace "okay,
muna jin ka" yace "duk wadannan lissafe
lissafen ban gama gane su ba tukunna, I
need a figure, how much is Safiyya really
worth, In figure" uncle Ahmad yace
"menene naka a ciki?" Daya mutumin ya
fara bude takardu yana dubawa sai wanda ya kira kansa da lawyer yace "hold on. Shi
waye mai tambaya din? because this is a
security issue ba wai kowa akewa
disclosing that information to ba"
Mustapha yace "I am her brother, and I
have the right to ask" uncle Ahmad yace
"step brother. Her step brother"
14
13
10:12 PM
Mommy tace "au gorin ya fara kenan, tun
yanzu?" Daddy yace "just tell him. It is
okay" mutumin ya karasa bude takardar
sannan ya ambaci figures din da babu
wanda bai tsorata ba a falon. Including
uncle Ahmad. A fuskar sa na fahimci
shima bai san kudaden sun kai haka ba.

Falon yayi tsit na some seconds, sannan
Mustapha yace "tashin sense"

Mommy tace "wallahi da sake, wai an
bawa mai kaza kai" Daddy ya zuciya
"waye mai kazar kenan? Ke? Where were
you sanda Safiya take neman kudin ta?
Tare kuke soya awarar ko tare kuke shiga
cikin kasuwanni sarin kaya? Where were
you sanda take bi aji aji a makaranta tana
musu tallan abaya? Tare kuke shara da
wanke wanken ko tare kuke zaman
shagon",.

Tayi shiru bata ce komai ba. Hassan that
was 15 years then ya daga hannu "ina da
tambaya" uncle Ahmad yace "muna jin
ka" yace "yanzu in muna son kudi wa
zamu tambaya kenan? Daddy ko yaya?"
Mommy ta daka masa duka a baya
'"'banza sakarai wanda bai san me yake
masa ciwo ba. Zaka rufe min baki ko sai
na fasa maka shi?"
OC
Taron da aka fara shi cikin farin ciki da
annushuwa, sai aka kare shi cikin
mabanbantan yana yi. Sai da kowa ya tafi
ya barni a falon a zaune ni kadai.
Rewinding and unwinding maganganun
da akayi. Daga nan kuma nabi Daddy har
dakinsa na gaya masa cewa ni bana son
abinda Ammi ta bani, na bar masa, ya
cigaba da rikewa a hannun sa ya kuma
cigaba da kula da mu baki daya. And he
sat me down and talked to me. He told
me about Baba Hadiza and Ammi and her
siblings, he told me about it all.
And then after two years and going
through hell and coming back, I finally
decided to accept what was given to me. Na sauke ajiyar zuciya sannan nayi taking
first step a cikin falon, ga mamaki na sai
naga duk sun mike tsaye irin mikewar da akeyi to show respect to manyan mutane.
I held my head high and walked through
them, zasu kai su ashirin roughly, na ga
uncle Ahmad na kuma ga Mukhtar,
sannan na ga Daddy. Na lura da mutane
biyun da suka zo wancan zuwan but all
the rest are new faces. Uncle Ahmad yayi
wa Mukhtar magana "matsa mata nan
kusa da kai ta zauna. Wannan shine
mijinta. This is her husband" ya fada wa
mutanen gurin. But I walked pass then na
je gurin Daddy wanda shi kadai ne a
zaune na zauna a kusa da shi.
I wanted to create a very good first
impression with them all. Ina son inji
displaying confidence, smartness,
intelligence and power to them. Bana son
su ke kallo na a matsayin naive little girl.
Kuma daga dukkan alama na basu
wancan impression din. But even with all
the displayed power, nayi kokarin gaishe
su dan bana son power din tawa tayi
overwriting tarbiyya ta.
Daddy ne ya bude taro da addu'a, and he
made the effort of including Ammie a
cikin addu'ar tare da roka mata rahamar
ubangiji, Daga nan sai uncle Ahmad ya
fara kokarin yi min introducing mutanen
gurin, Na girgiza kaina sannan na mike
tsaye ina kallon su daya bayan daya nace "I am going to see them all uncle, amma
ba'a nan ba. Zan ga kowa one after the
other and talked to kowa privately in
daddy's office" a fada ina nuna office
din Daddy da yake da kofa ta cikin falon. I
looked at Daddy and I saw the look da na
bOd
jima ban gani ba a fuskar sa, the look of
pride.
Naga chanji a fuskar Uncle Ahmad ya
kama hannuna ya jani gefe "this is a bad
idea Safiyya, wadannan mutanen ni na
san su na san kowa, i have delt with them
for years.
..." Nace "and now I am going to
43
learn how to deal with them too" yace
"but at least take your husband with you"
na juya na kalli Mukhtar da na fahimci
ransa a bace yake nace
"no uncle. I am
going to do this alone. Ko Daddy ban ce
masa ya shigo ba. Da ina son shiga da
Mukhtar da ni da kaina zan ce masa ya
zo".

Na wuce shi na bude office din na shiga,
na wuce can ciki na zauna akan kujerar
Daddy sannan involuntarily na shafa
pendent din Ammie da yake wuyana a
hankali nace "alright Ammie, you want me
to do this? I will do this",

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹


Episode Thirty Seven: The Eyes


Daya bayan daya suka ringa shigowa
kamar yadda na bukata. Most of them sun
haife ni, others sun girme ni sosai. Kowa
d
in ya shiga zai yi min introducing kansa da
mukamin da yake rike da shi sannan ya
bani brief breakdown of what has been
going on a bangaren da yake rike da shi.
Duk abinda suka fada min in recording a
43
karamar recorder din da na ajiye a gurin.
Duk wanda ya gama kuma sai ince yaje ya
rubuto duk bayanin da yayi min in written.
Dalilin yin hakan shine dan in yi
comparing said and written words din
inga in zany detecting something.
Abinda na fahimta shine kowa a cikin su
yana kokarin cusa kansa ne a waje na,
every one of them was trying to impress
me. Some were even black painting
others a kokarin su na buda wa kansu
hanya a gurina, Wannan yasa nayi using
dama ta, kowa idan ya gama sai in ce
masa "naji dadin bayanan ka sosai, Kuma
na fahimci cewa you are a good and
hardworking person, I am glad you are part of my company. In babu damuwa ina
son ka zama special adviser na, I want
you to be my eyes and ears a duk inda
bana nan, and I will appreciate it if you will
report to me duk abinda kake gain ya
kamata in sani" wanna kalaman suna
saka su farin ciki sosai. And it mostly
made them spill one or two information
da da suka boye. Then kafin su fita sai in
kara da cewa "aikin da na baka is
confidential. Bana son kowa ya sani, daga
ni sai kai".
And that was how I tied them all to me.
Kowa yana gain kansa a matsayin
special somebody a gurina. And kowa
yana yi min aiki secretly ba tare da sauran
sun sani ba. A zama dayan nan na samu
informations masu yawn da banyi
tunanin samu ba.
Sai bayan da na sallami kowa sannan
kuma muka zauna da uncle Ahmad da
barrister Umar da kuma daya mutumin da
na fahimci shine account manager na.
Anan aka chanja all the signatories zuwa
signature dina aka cire ta uncle Ahmad,
sannan yayi min handing over all the
necessary documents and then muka
shirya cewa zamu yi going on a tour a
nuna min ko'ina and komai,

Bamu fara fita a ranar ba saboda duk mun
gaji, ga wata uwar yunwa da nake ji. Na
samu dai a karshe suka ce zan iya tafiya,
washegari zamu cigaba. Ina son in je inci
abinci amma kuma ina son gain Daddy,
ina son magana da shi. Sai na tafi dakinsa
dan tun da na fara gain stakeholders din
ya shiga dakinsa ya kwanta dan ba zai iya
zama a cikin wanna hayaniyar ba.

A kan gadonsa na same shi a kwance
kamar mai bacci, na jima a tsaye ina
kallon sa sai na juya zan fita dan bana son
tashin sa, na kai bakin kofa kenan sai naji
ya kira suna na.
"Fiyya" ya jima bai ce min
Fiyya ba, for months yanzu Safiyya yake
ce min. Na juyo ina kallon sa sai yace "kun
gama?" Ya gyada kai "mun gama da
stakeholders din sun tafi. Dama taron is
just to let them know I have taken over, so
daga gurina zasu ke karbar duk wani
directives" yace "then why do you have to
see them one by one?" Nayi ajiyar zuciya
na zauna a kan gadon a kusa da
kafafuwansa nace "ina kokarin fahimtar
su ne kawai, trying to know their
personality saboda in fahimci yadda zanyi
dealing with them" ya danyi gajeren
murmushi "and you think you can
understand their personality in one
sitting?" Nayi shiru bance komai ba, yace
"you did right, ba wai ina tuhumar ki bane
ba, at least you have shown them power and instilled a bit of fear in them, kowa zai
shiga taitayinsa. But I don't want you to
be the boss that is fearful, I want you to
be the boss that is loved. Ki saka musu
son ki ta hanyar kyautatawa and at the
same time ki zama strict with them" na
gyada kai "insha Allah Daddy. Dama ina
son ne in samu informations daga gurin
su, and I got some" sai kuma nayi shiru,
yana kallona yace "what information?" Na
girgiza kaina deciding not to tell him now
nace "I am not sure now. Zan dai kara
bincike first" yayi ajiyar zuciya "there is
something about information Safiyya. If
you keep looking for it to tabbas you will
get it. Ko dai ki samu true information ko
kuma ki samu false information. Amma
tabbas zaki samu. Matsalar zata fara ne
idan kika samu false information.
20
14
10:09 PM
Musamman idan kina da kudi. People will
only tell you abinda suka san kina son ji
dan su samu wani abu a hannunki. Very
few people will look you in the eyes su
gaya miki abinda suka san ba zaki ji dadin
shi ba".

Sai na gaya masa hanyar da na fara bi for
now. "Kowa zai ke kawo min nashi report
din, kowa zai saka wa kowa ido, so l am
hoping I can get the truth that way" muka
yi shiru ina tunanin ta yadda zan gaya masa mafi girman information din dana
samu, sai dai kafin inyi magana sai naji
yace '"I am sure sun fada miki something
about Ahmad? What are you going to do
with him? Wanne hukunci zaki yi akan
sa?" Cikin mamaki nace "so you know
what he has been doing? Ka sani all this
while?"
Yace "I already know the truth of it. An
riga an gaya min ai ba tun yanzu ba. I
even talked to him about it yayi min
alkawarin zai mayar da kudin da ya dauka
amma har yanzu bai mayar da kudin ba.
Ya jima yana daukan kudade yana keeping
it aside for himself. Just a month ago aka
sake gaya min ya kuma daukan wadansu,
and that was bayan kin amince zaki auri
dansa".

Nayi ajiyar zuciya nace "yanzu ai ba zai
sake dauka ba. Yanzu bashi da damar
daukan ko kwandala kuma" yace "shi
yasa ya dauka ai, saboda ya san in kika
karbi aikin ki ba zai samu damar dauka
ba. Yanzu me zakiyi akan wadanda ya
9?
dauka already?" Nace "I don't know
Daddy, abinda ya sa na shigo gurinka
kenan, Nasan kullum in zaka yanke
hukunci kana tunanin abinda Ammie zata
yi, me kake tunanin zata yi idan ita ce a
matsayi na?" Yayi shiru yana tunani sai
yace "your mother had been a great woman. Ta iya zama da mutane sosai.
Tana da dabarun da take amfani da su ta
juya mutane ba tare da sun san tana juya
su ba" yayi murmushi "just like yadda kika
fara yanzu, you are so much like her" nayi
murmushi nima. Ya cigaba "she warned
me about Ahmad, she said money is
sometimes evil and can change people's
behavior, Ahmad ya bautawa business
dina tun lokacin da shago daya kawai
nake da shi, shi nake bari yana jire min
shagon a lokacin da ni kuma nake
pursuing higher ambitions. Yes, tun
lokacin yana kara kudi akan kaya ya siyar
dan shima ya samu ta sa ribar kamar
yadda duk masu irin wanna harkar suke
yi, amma bai taba daukar min kudi ba. As
the shop turned into shops and then into
an industry he started becoming greedy
and possessive. I think mistake din da
nayi making with him shine na danka
masa ragamar komai a lokacin da na fara
rashin lafiya, I did that to strengthen trust
dan in na bar ku ya kyautata rikon da zai
yi muku, but it made him more greedy
and more possessive. Yaji zakin dukiyar
baya son rabuwa da ita, shi yasa ya dage
akan ki auri dansa tun farko, he thought
auren zai hana ki karbar dukiyar daga
hannun sa, after you refused the offer sai
ya fara daukan kudin yana ajiyewa for
himself, daga baya kuma you chose auren
dan nasa, he then became comfortable cewa ko kin karba daga hannun sa dan sa
zaki saka a kai ko kuma shi ki barshi ya
cigaba da juyawa. He was devastated
today after you took it from him and cast
the son aside" yayi shiru yana kallon na,
waiting for me to say something.
100
Nace "that was why ka nuna baka son
zabar Mukhtar da nayi?" Yace "yes. If I
was the one given the choices I would
have chosen Mustapha, idan kuma aka
cire Mustapha daga cikin options din
gwara in zabi Abdul din da ban gama sani
ba sosai akan Mukhtar"

Na girgiza kaina feeling stubborn "Daddy
ba ka san Mustapha ba, the Mustapha
you know is different from the one I know.
And I don't think Mukhtar is as bad as you
think. He is my friend. Kuma ba lallai ne ya
san plans din baban sa ba".
Ya gyara kwanciyar sa yace "you are
wearing your mother's clothes and acting
3
83
like her. But you are still a child",
Na bar part din sa na shiga cikin gida da
niyyar in ci abinci in huta, a raina sam na
manta da Mukhtar yana gidan saboda
gajiyar da nayi, Ina shiga na bada umarnin
a kai min abinci dakina dan ba zan iya zama a dining in ci ba.
23
5
10:09 PM
Kai na tsaye na bude kofar dakina na
shiga na ajiye jakar hannu na sannan na
cire mayafi na shima rataye shi, na tsaya
a
gaban mirror ina kokarin cire dan kunne
na kawai muka hada ido da shi a kwance
akan gado na. Na firgita saura kadan in
kwalla kara sai kuma na rufe bakina da
hannu na gudun kiran attention din
mutane.
Ya tashi zaune yana kallona yana dariya "I
always knew ke farar kura ce saboda
toro" na juyo ina kallon sa har lokacin iiki
na yana karkarwa "me kake yi anan
Mukhtar? Menene hakan? Me yasa zaka
shigo min daki ba tare da izini ba?" Ya
tashi tsaye "gurin wa zan nemi izinin
shiga dakin matata? Koke baki da damar
hana ni shigowa dakin nan a yanzu. Abba
yace anan zamu kwana so I decided ni
anan zan kwana" ya fada yana nuna
gadon da ya tashi daga kai,
©️? Na dauki jaka ta tare da mayafi na nace
"'bani da ikon hana ka shigowa dakin nan
ka ce ko? Amma ai ina da ikon bar maka
dakin ka zauna a cikin sa kai kadaj" na
fada ina yin hanyar fita daga dakin, Cikin
taku biyu ya kamo hannu na ya dawo dani
baya, saura kadan in fada jikinsa nayi regaining stand dina, raina a matukar
bace na nuna shi da daya hannun nace
"ka sake ni Mukhtar, I am very serious" ya
saki hannun yana kallon fuskata "why are
you so difficult ne. Relax. You are so
tensed. Ba wani abu zanyi miki ba I just
want to sit down with my wife and have a
talk" Nace "zaka fitan ne ko ni in fita. I just
want to be alone ne yanzu. I want to rest,
na gaji da yawa".
Maimakon ya fita sai ya ja kujerar gaban
mirror na ya zauna yace "a problem
shared is a problem half solved. Zauna ki
gaya min abinda ya saka kika zama this
edgy" na zauna a bakin gado ina kallon sa
"I don't want to talk about it, I just want to
be alone and think about it" yace "okay.
Pretend kamar bana nan. Kiyi harkokin ki
kawai. I will just sit here and enjoy your
presence".
Nayi shiru ina kallon sa bance komai ba,
yayi murmushi "you were about to
undress before you saw me. Continue
from there" na girgiza kaina "ban san
sanda ka zama haka ba Mukhtar. You
were decent a sanin da nayi maka. And I
like the former version of you better" yace
"nima haka, I like the former version of
you better, The former Fiyya that was
always free and kind with me. Not this one da take nuna kamar ta tsane ni".
Ban bashi amsa ba aka yi knocking aka
shigo, yarinyar da na ce ta kawo min
abinci ce, tazo ta kama jera flasks din
abinci nace mata "ni fa ba cewa nayi ki
cika min daki da abinci ba, a plate kawai
nace ki zu bo min wanda zan ci ki hado da
drink da spoon ki kawo min" tace
"Mommy ce tace a kawo miki gabakidaya
ki zuba wanda kike so" nayi ajiyar zuciya
sannan nace ta zuba min shinkafa da
miya, sai kuma na kalli Mukhtar da yake
zaune still ya zuba min ido nace "zaka ci
abinci?" Yace "I thought ba zaki yi min
tayi ba" yarinyar da take zuba abincin ta
dan tsorata saboda bata lura yana dakin
ba sai muryar shi kawai ta ji. Nace mata
'"'barshi kawai, tashi kije, in ya gama kya
dawo ki dauke, ta tashi da sauri ta fita
tana juyowa tana kallon shi.
Nace "kaga ka tsorata yarinyar mutane,
yanzu zata je tana wondering me kake yi
anan" yace in ta tambaya sai a bata amsa,
a gaya mata dakin matata ne. Na dauki
plate din da ta fara zuba min abincin na
karasa zubawa sannan na koma na zauna
na fara cin abinci na saboda yunwa da
nake ji. Ya sauko daga kan kujerar shima
ya zuba abincin ya fara ci sannan yace
"So, how is he?" Na ajiye spoon din hannuna nace "how is who?" Yace "The
boy, what name kika bashi ne wai? Dole in
zaki cike information din sa acan sai kin
saka suna, so definitely kin saka masa
suna. Wanne sunan kika saka masa?"
Nayi shiru ina kallon sa sannan nace "why
do you want to know?" Ya dauke idonsa
daga nawa ya daga kafada yace "is it now
a crime idan mutum ya nuna damuwa da
abinda ya shafi matar da yake so? Yanzu
na gama gaya miki cewa you are edgy,
abu kadan yake bata miki rai" na cigaba
da cin abinci na '"'I don't want to talk about
him" yace "okay, shikenan" sai kuma ya
chanja topic ya fara yi min maganar
gyaran gidan da yake yi da lefen da yake
hadawa.
22
10:09 PM
"Da tuni duk an gama komai ba dan
Mommyn ki ta kwafsa mana ba. Banga
abinda zaki anan wanda ba zaki yi a can
ba. Sai ma abinda zakiyi acan wanda ba
zaki yi anan ba" ya karasa yana kokarin
hada ido da ni. Nayi kamar banji me yake
cewa ba na cigaba da cin abinci na har
muka gama gabaki daya, Sai ya dauko
wayarsa ya dawo kan gadon ya zsuna a
kusa dani "I want to show you the new
design da aka chanja wa kitchen din nan,
you will like it na sani, na san how much kike son kitchen" na karba nayi scrolling
through pictures din, ban wani gane
designs din sosai ba dan kaina ciwo yake
yi na gani sosai. Na mika masa wayarsa
'"ni fa ba gane wa nake yi ba wallahi. Na
gani later. I just want to rest yanzu" ya
mike "okay, bara in barki ki huta. We will
talk later".

Har zai fita sai ya ga wayata a ajjiye a
kusa da jaka ta, sai kawai ya saka hannu
ya dauka "you need to change this
phone" ya fada yana juya ta a hannun sa,
nayi shiru ban ce komai ba dan ni kawai
so nake ya fita ya bani guri, sai kuma naji
yace cikin murya mai kaushi "who is
this?" Na juyo na kalle shi sai ya nuno min
hoton screen din waya ta. Na dauke kai
nayi kamar ban gani ba na fara kokarin
gyara gurin da muka ci abincin "who is
this na ke tambayar ki?" Ya fada yana
doso ni da wayar a hannunsa "oh ba zaki
bani amsa ba?" Na fara jin tsoron yanayin
sa, he looked like he did sanda yake gudu
da mu a mota, na dauke ido na daga cikin
nasa "you already know who is that, kuma
hoton ya jima a screen din I didn't get the
time to change it" "you didn't get the time
to change it or you don't want to change
it? Whatever the case, I will change it for
you" yana fada sai yayi jifa da wayar, ta
daki bango ta fado kasa ta tarwatse, Na mike tsaye ina kallon sa "you broke my
phone" na fada cikin mamaki, ya wuce ni
ya je inda wayar ta fadi ya saka kafar sa
me sanye da takalmi ya take wayar, yace
"yes I did. And this is the last time da zan
kuma gain anything related to that guy a
gurin kj" na tsaya kawai ina kallon sa, ya
dawo ya tsaya a gabana, blocking my
view with his big body, yace "ina sonki
matukar so Safiyya.
Na bi bayansa da kallo har ya fita, ina jin
raina yana kara baci. Ba wai wayar da ya
fasa ce damuwa ta ba, I was surprised
and concerned that he had that kind of
temper. What if nan gaba ba waya zai
fasa ba? Na karasa inda wayata take a
ruguje a kasa na durkusa ina tattare ta,
ina tunawa da cewa Muhammad ne ya
siya min ita, tare ya siya mana iri daya ni
da shi.
Washegari da safe ina tashi sai ga sako an
kawo min any wrapping dinshi, Na ksrba
na bude sai ga sabuwar waya a ciki with
an "am sorry" card, ban karanta rubutun
ciki ba dan na fahimci daga gurin wanda
yake, a bayan card din yayi rubutu,

"Am sorry darling. I promise to never
loose my temper again"

Na mayar da card din cikin wrap din na
ajiye. Su Hassan suna shigowa na aika su
suka siyo min wata wayar dan nasan za'a
yi ta nema na.

Har Mukhtar ya koma Abuja ban kara yi
masa magana ba duk kuwa da bada
hakurin da yayi ta yi min. Satin ya zo min
cikin sauri sosai dan kullum kusan a waje
nake wuni. We had an extensive tour tare
da uncle Ahmad wani lokacin har da
Daddy da Mukhtar ko Mustapha. Sai a
lokacin na kara fahimtar dalilin da yasa
Daddy ya kafa min takunkumin yin karatu
mai zurfi dan ni kaina sai da naji na raina
ilimi na, abubuwa da dama in anayi min
bayani sai inji ban gane ba, amma bana
nuna ban gane din ba sai dai kawai inyi
taking note, duk abinda ban gane ba
kuma bana yanke hukunci akan sa sai na
je gida nayi research akai kuma na
tambayi Daddy ya kara yi min bayani
sannan in yanke hukuncin da nake ganin
ya dace da abin,
Ina lura da yadda uncle Ahmad yake
cigaba da kokarin cusa Mukhtar a duk
abinda muke yi, ina kuma lura da yadda
shi Mukhtar din baya so, shi yayi
concentrating ne akan gain mun shirya yayin da ni kuma na ki bashi damar hakan.
Har kuma muka gama tour din yi wa uncle
Ahmad maganar abinda ni da shi duk
mukasan yayi ba saboda har lokacin ban
gama yanke shawarar hukuncin da zan
dauka ba.
18
10
10:09 PM
Bayan sun koma kuma sai nayi
concentrating on revamping the whole
industry, akwai chanje chanje da dama da
nake son making wadanda nayi magana
da Daddy kuma ya amince. Kullum ina
cikin meeting, duk da dai wadanda na
gayyata gida suke zuwa su same ni amma
still kullum a gajiye nake and that gajiya
helped me a lot wajen rage tunanin
abubuwan da suke gudana a rayuwata.
Tunani biyu ne yafi damuna idan nazo
kwanciya bacci, na Muhammad dana
Junior. I always wondered how they are
doing. How they are coping with their
fate. A raina nasan Junior is doing well
but I was not sure about Muhammad.
Sai da na gama da tour din na kuma yi
setting a lot of things in motion sannan
kuma na zauna meeting da family na, I
told them straight forward "daga yanzu a
gidan nan there will be no more free
money. Every one will have to work to take care of himself"
Mommy tace "ban gane ba, aiki zamu
ringa yi miki kenan a gidan?" Nace
"Mommy ai ni ban isa ince zaki yi min aiki
ba, ina magana ne da samarin gidan nan"
tace "twins dai karatu zasu yi, karatun
zasu fasa su zauna yi miki aiki?" Na tara
tattaro patience dina dan kar in gaya mata
magana nace "bani za'a yi wa aiki ba,
kowa kansa zai yi wa aiki. Mustapha, zan
baka list of vacant positions da muke da
su in the company sai ka zabi wanda kake
so and the job will be yours" ya daga
hannu "] don't need it. Na riga nayi
submitting cv na zuwa gurare da dama, I
will soon get a job" nace "your choice" sai
na juya gurin twins nace "kai Hassan
tunda harkar engineering kake sha'awa
zaka yi joining team of engineers din mu
in the factory, zaka fara aiki da su kana
koyon yadda suke gudanar da aiyukan su
kuma kana yi musu kananan aiyuka"
Mommy tace "I don't believe this,
laburanci zaki tura shi? Kanin naki?"

Ban bata amsa ba na juya kan Hussain
"kai kuma tunda naga you have daddy's
business mind, you will join the marketing
department, kai ma zaka koyi aiki za kuma
ka taya su aiki, Zakuyi aikin zuwa sanda
zaku samu admissions and even kun fara karatu we will still find a way for you to
continue your job part time zuwa sanda
zaku kammala karatu then you will take it
full time" na bisu da kallo naga yadda duk
suka yi shiru suna kallo na, nace "any
question?" Hassan ya daga, nace "dama
na san kai zaka fara magana, menene
tambayar ka?" Yace "nawa ne salary din?"
Daddy da yake zaune yana jin mu yayi
dariya, Hussain yace "yaushe zamu fara
aikin?" Nace "as soon as you can get[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Daddy da yake zaune yana jin mu yayi
dariya, Hussain yace "yaushe zamu fara
aikin?" Nace "as soon as you can get
yourselves to your various departments.
You will discuss your salaries with the
heads of your departments" suka juya
suka kalli juna sannan suka yi murmushi,
Hassan yace "shagali, duniya sabuwa"
Daddy yana kallon Mommy yace "see?
They are happy. This maybe the best
decision da aka taba making a rayuwar
su" amma Mommy still kamar abin bai yi
mata dadi ba, ita a son ranta shine a nemi
makarantar da tafi kowacce tsada a
Nigeria ko kuma wata babbar makaranta a
waje a saka su, a kuma cika musu
accounts din su da kudi,
Sai ta juyo tana kallona "saura ni kuma, a
wanne department za'a saka ni?" Nayi
murmushi duk da na san bakar magana
take gaya min nace "ai ke Mommy Allah ya riga ya baki aikin ki, permanent aiki,
aikin kula da Daddy, all your expenses will
be taken care of, duk abinda kuke bukata
a gida ko na personal use din ku will be
provided" naga fuskar ta tayi relaxing
alamar hankalin ta ya kwanta, sai na kara
da '"but not in cash. Except when
necessary. Duk abinda kuke bukata will
be provided directly".
And that was a story for another day. Tafi
sati tana mita akan hakan. But I stood my
ground.
Da taga ba zan chanja shawara ba, ta
kuma tabbatar Daddy baya na yake bi sai
ta koma shirye-shiryen biki, ta rubuto min
dogon list na abubuwan da za'a siya da
kudaden su and I was like "what?" Na
fahimci ita bata jin wahalar ambatar kudi
komai yawansa, ni kuma yanzu da na fara
wannan role din kudin da nake bukata na
siyan abubuwan da za'a bukata ne gurin
gyare-gyaren da na tsara za'a yi wa
factories ne, Da nace mata no sai ta tafi ta
kai kara ta gurin Daddy.A dole nayi mata
signing taje ta karbi kudi ta cigaba da
hidimar ta,
22
10:09 PM
Duk wani abu da za'a bukata a gida ta siya, har abubuwan da ba za'a bukata ba
ma ta siya. She spent more money a
kayan dakina then she did a kayan dakin
Safina. Kullum kuma in ta je hidimarta ta
dawo ta ringa loda min karkacen
magunguna kenan.
'"Wannan da madara zaki ringa damawa
kina sha, wadannan kuma su zaki mayar
ruwan shan ki kiyi ta sha daga yanzu
zuwa bikin. Wanna kuma a tsarki ne
duk da dai cs akayi miki amma dole sai
anyi miki gyara sosai" in ta bani sai in
nemi deepest corner of my room in ajiye,
sai na shan ne takan takura min ta zaunar
da ni ta ce sai na sha "dan ke nake so inyi
miki wanna gyaran ba wai dan wancan
mara kunyar yaron ba. Kin san se da na
korawa uwar nan ta sa bakaken
maganganu wanna zuwan da nayi
Abuja? Naje zan karbi key din gidan nasa
zamuje muyi aune aune, matar nan tana
ta wani kumbura kamar an saka mata
yeast, ni kuwa na gaya mata boldly cewa
dan ta da ubansa su suka kawo kansu
kuma suka dage sai anyi, su suke nema
ba mu ba, in tana ganin ta isa kuma ta
hana gani, Akwai da yawa suna jira suyi
replacing dan nata" tayi shiru tana jira in
yi magana, jin bance komai ba sai ta kara
da "Allah ne kadai ya san me suka yi miki
ma har idonki ya rufe kika zabe shi, Dan ni ban yarda da wanna lamarin ba".
Daga nan kuma sai ta bani labarin Safina.
'"Naje gidan Safina. Ni fa wannan auren
nata ban yarda da shi ba har yanzu. Kin
ga yadda yarinyar nan ta kare ta lalace
kamar ana yankar naman ta ana ci? Nayi
ta tambayar ta kuma kin san halin Safina
da hakuri ta ki gaya min komai, in na
tambaye ta sai tace babu komai. Ni ban
san yadda zanyi ba wallahi. It breaks my
heart to see her like that. Wannan mijin
nata ni sam ban yarda da shi ba, har
yanzu hankali na yaki kwanciya da shi".
Da naga ba zata daina zancen Safina da
mijinta ba sai nayi excusing kaina na tafi
daki dan bana son jin duk abinda ya shafe
su, but through out that night I kept
wondering what was happening with
them.
Saura sati biyu biki aka kawo lefe, Daddy
ya gaya musu baya son attention dan
haka babu mutane sosai kuma da yake
abin na gida ne masu kawowar dai sune
kuma masu karbar. Aka gama ganin kayan
anan sannan Daddy yace a zuba su a
mota a kai su Abuja in za'a je jere gidan
Mukhtar sai a tafi dasu kawai can tunda
ba amfani zanyi da su anan ba, Amma duk
da haka sai da Mommy ta dauki set din akwati daya cike da kaya tace na rabo ne.
"'Yan uwa zaa rabawa da abokan arziki. Ke
menene shire shiryen ki ne? Ni ban ga
kina yin dinkuna da siyayyar kayan fitar
biki ba, ki kira Safina ta hada ki da tailor
din da yayi mata dinkunan bikin ta, na ga
ya iya sosai"
Na girgiza kaina "ni na gaya muku babu
abinda zanyi Mommy, ba zan rasa kayan
da zan saka ranar kai amarya ba.
Shikenan" ta girgiza kai "ba zai yiwu ba ai
ba auren dole ake yi miki ba, ke kika zaba
da kanki" haka ta saka ni na sake fitar da
wasu kudaden na bata tayi min dinkunan
fitar biki.
Mun dan shirya da Mukhtar na fara
daukan wayarsa bayan na tabbatar cewa
ya gane kurensa, sai dai kuma bani da
tabbas din cewa he won't be that violent
in the future.
Ten days to biki. Already Mommy ta gama
tsare-tsaren ta, za'a yi kamu anan gidan
mu sannan zata kama event center tayi
mother's eve, shikenan sai a tafi Abuja a
sake yin wani yinin acan wai Saboda su
Hajiya da sauran kawayen ta da ba zasu
samu zuwa nan ba, Sai kuma akai amarya,
Ni dai ina ta jin ta ban saka mata baki ba.

A ranar I had a very long meetings with
engineers din mu akan sababbin machines din da za'a siyo, bamu dama ba
sai late afternoon sannan na samu na
shigo gida naci abinci nayi wanka na
chanja kaya into pajamas da niyyar ba zan
sake fita daga daki na ba sai safiya. Sai da
na gama komai na zauna sannan na
dauko waya ta da niyyar duba wani
message da nake saka ran za'a turo min.
Sai dai ina budewa na ga message daga
Abdul. Nayi murmushi na bude message
din and I saw a lot of pictures wadanda
tun kafin in bude su na fahimci na waye.
Abdul din ya rubuta "mun girma fa.
Getting big and ready for big brother's
wedding" na tuna Mommy ta gays min an
saka bikin sa za'a yi two weeks after
mine.
23
10:09 PM
Nayi murmushi sannan na bude pictures
din.
Da gaske yayi girma din his skin looking
smooth, babu wrinkles irin na premature
babies, fuskarsa ta ciko tayi kiba har da
kumatu, his facial features more
pronounced than sanda aka haife shi,
yanzu kamannin sa da Daddy sun ragu ya
zama yana looking more like me than
Daddy, Hotunan suna da yawa, har da
short videos of him smiling, wadansu
pictures din a asibiti wadansu kuma a gida. Wadansu tare da Abdul wadansu
tare da Aunty Hajjo. Daga alamu Abdul is
very fond of Junior.
Ina cikin scrolling nazo kan wani picture,
anyi zooming fuskarsa sosai and he was
calm and looking directly at the camera,
with a serious face. And my heart
stopped for a second. Na kife wayar tare
da dafe kirjina ina jin wani irin ciwo a cikin
zuciyata. Sai da nayi ta ambaton sunan
ubangiji sannan na sake daukan wayar na
kuma kallon hoton. His eyes looked
exactly like his. Kamar shine yake kallo na
whenever he is serious.
Na sake ajiye wayar tare da rufe fuskata
da hannayena guda biyu "it is not him. It
cannot be him" amma kuma naji har a
cikin bargon jikina that it is truly him.
Na bude fuskata ina jin hawayen da na yi
alkawarin a daina suna betraying dina,
sannan wani irin rage yana mamaye
zuciyata da duk kan bargon jikina,
Na sake daukan wayar ina cigaba da
kallon hoton sannan na je na lalubo wasu
pictures dinsa da ya turo min just a week
ago. I chose wanda ya kalli camera sosai
and looked serious, sai na hada su side by side da hoton Junior and the eyes looked
exactly the same, kamar na mutum daya.
Tun bayan da na haifi Junior na dawo
Nigeria, it looked as if komai ya wuce,
babu wanda yake maganar babu wa da
yake kokarin bi mini hakkina. Hatta Daddy
ma tunda na bar asibiti bai sake yin
maganar ba, kokarin sa kawai ya aurar da
ni ya binne maganar abin kunyar da yake
ganin na jawo mana. I have been trying to
bury it for the time being as well. Amma
ba wai na manta bane ba, it was
something that can neither be forgotten
nor forgiven.

He took my life away from me, and
doomed Junior's life. And now, I will take
his life as well…

Amma ta yaya zanyi hakan?

Junior's eyes looking like his is not
enough proof na cewa shine babansa. Ko
da court zan je ba zasu karbi wannan a
matsayin shaida ba dan yaya suna iya
dauko wani abu na dangin su na can nesa
ma ballantana shi da yake first cousin
dina,

I need to have something better than that.
Zan iya samun another shaida if I can get
to see him naked. If I can see the marks I need to have something better than that.
Zan iya samun another shaida if I can get
to see him naked. If I can see the marks

Naji zuciya ta tayi min wani irin nauyi
when the realization hits me. Tunda abin
ya faru nake karar da dare na da rana ta
gurin gaya wa ubangiji and begging him
to find a way out for me, and he chooses
MUKHTAR as my husband because He
knows that sai na aure shi sannan zan ga
abinda nake nema.

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Thirty Eight: A Night to
Remember


Na cigaba da zama a guri daya kamar
statue, ina jin bacin rai yana cigaba da
mamaye dukkan ilahirin jijiyoyi da bargon
jikina. Mukhtar has always been a friend
to me, more like babban yayan da
Mustapha ya kasa zame min. I always run
to him for consolation tun sanda ina
yarinya, he has always been the first
person da nake nema in ina bukatar
taimako ko a way out of my mischief. He
is one of the few people da nake feeling
comfortable around, nake iya being
myself around. Ko gidan su naje da shi
nake wasa instead of su Salima da Salim
da suke kusan mate dina. Da na kara
girma kuma in dai naje Abuja to ya zama
driver na, yawo lungu da sako na Abuja
babu inda baya kaini. Zai iya siya min abu
bai siyawa Salima ba ballantana Safina da
dama can ba shiri suke yi ba.

Ko da wasa ban taba tunanin shine ba....
1
have always thought Mustapha ne, idan
kuma ba shi bane ba sai dai wani can
daban. Wani wanda ba Muhammad ba, Duk da yadda Daddy ya dage wajen
kokarin convincing dina cewa Muhammad
ne amma ni na san ba shi ba ne ba
saboda na farko Muhammad yana sona,
he could never have hurt me that way.
Idan ma har yana son aikata haka da ni he
could have easily seduce me or maybe
emotionally blackmail me to get it tunda
ya san ina sonsa but not rape me, not in
that cruel way.

*. *. **. *.

Muhammad ya jima yana ta putting
pressure on me about going next level
with our relationship kusan tun a shekarar
mu ta farko a makaranta. Tun ina chanja
topic in yana yi min maganar har na fara yi
masa karya hakan kuma ya sa ya kara
damuwa, saying ba son shi nake da gaske
ba. On the other hand Daddy have
warned me strictly akan maganar saurayi
tun farkon shiga ta jami'a. "idan na ganki
da saurayi Safiyya, you are living that
school ko zaki yi kukan jini. You are there
to study and become what your mother
sacrifices a lot for you to become not to
be distracted by something not
important", Shi bai san saboda saurayin
ma naje makarantar ba,

Yadda yake tsaurara min akan kar inyi saurayi ne ya saka da kansa ya dauke ni
daga gidan uncle Ahmad ya mayar da ni
hostel a lokacin da Mukhtar yace yana so
na. "karatu zaki yi ba soyayya ba. Lokacin
da zakiyi aure zai zo, and even then, zan
saka ido in tabbatar da wanda zaki kula ya
chanchanta kafin in barki ki kula sh'" shi
yana gain ya dauke ni daga gurin
Mukhtar, not knowing gurin wani saurayin
ya kaini da kansa.

And later after he broke the news of my
mother's gifts to me, sai na fahimci dalilin
da yasa ya dage akan karatu na kuma ya
tsaurara akan maganar saurayi, amma ni a
tunani na maganar sa bata da tushe, I can
manage my wealth and study at the same
time, a gefe kuma ina soyayya da
Muhammadu na. Right?

Amma bai yarda ba, ya kara buga min
warning akan soyayya. "Especially now
that this news is out, you will find it hard
to differentiate between true love and
fake love". Naso inyi masa bayani ai
wanda nake so bai san duk wannan ba
ballantana yayi faking, but na san yana jin
labarin already ina soyayya zai raba mu.

A lokacin ne kuma fake love din ya fara
bayyana, Mustapha ya chanja toward me
and became kind and soft spoken and a karshe ya gaya min wai yana so na. I
laughed out loud when he said it. And I
understood more of what Daddy meant.

As I continued hiding Muhammad, our
relationship grew stronger and stronger
each day yadda ni kaina na fahimci auren
na ke so ba karatun ba. And Muhammad
ya cigaba da takura min da zancen inyi
introducing dinsa a gida, tun ina yi masa
karyar Daddy baya nan har na gaji na
samu Mommy da maganar, a tunani na ko
zata iya lallaba Daddy ya ga Muhammad
ko yaga iyayen sa just to prove to him
cewa ba yaudarar sa nake yi ba, in yaso
sai in cigaba da karatu na kamar yadda
Daddy yake so.
33
11
12:01 AM
Amma sai Daddy ya kira ni yace "I will go
to your school and withdraw you tunda ba
karatun kike ba, sai in sama miki
makaranta a waje ki tafi can kiyi karatun,
dama ke kika nace wannan kike so" da
kyar na samu na lallaba shi ya hakura ya
bar ni in cigaba da karatun a nan bayan
nayi masa alkawarin babu ni babu kula
wan saurayi har sai nayi graduating. And then two years into my studies, muna
exams din gama level two zamu shiga
three, I decided to take a bold step in kawo Muhammad gidan mu duk da babu
amincewar Daddy sai in ga yadda drama
din zata yi unfolding.
anar birthday din Muhammad ne, he was
turning 27 years. Ranar ne kuma Daddy
zai shigo Abuja shi da Mustapha. Ya kira
ni ya gaya min cewa ni zanje airport in
dauko su idan sun sauka. Saukar dare
zasu yi. And I planned on spending time
with Muhammad har zuwa lokacin saukar
ta su sannan sai in tafi da shi airport din
mu dauko su Daddyn tare. I was scared of
what will happen amma kuma I was
determined.
So I took Muhammad to the restaurant
and celebrated his birthday, a gurin kuma
nayi masa alkawarin a ranar zai ga
mahaifina. He was so happy...
I was so happy…….

And then as muna tsaka da cin abincin
mu, his phone rang, ya dauka
"hello, who
is this?" Sai ya ajiye "bana ji.....
.." Nace
"hope it is not important" ya kalli wayar
"new number, ban san waye ba", Muka
cigaba da magana, and he was already
planning on yadda zai siye Daddy na da
dadin baki, "He is a difficult person, I am
not sure idan zai yarda da dadin baki" ya
daga kafada "I am use to difficult people,
Don't worry, he will like me ko da baya so, But I suggest you go alone to the airport
ni kuma sai kiban address din gidan da
zaki kai shi sai inje in jira ku a can. He may
not like seeing us together a titi"
Na gyada kai, agreeing with him. Wayar
sa ta sake kara yayi ignoring nace "ka
dauka, maybe it is important" ya dauka
wayar "bana ji ai, kamar network din is
bad hear" ya saka a kunnen sa "hello?"
Sai kuma ya mike tsaye yayi min
murmushi tare da yi min alamar zai je
waje da hannun sa, I nodded and smiled
back at him and watch as he goes out.
Yana fita na dauki fork dina na cigaba da
cin abincin gaba na ina lissafin yadda
haduwar shi da Daddy zata kasance da
challenges din da zan fuskanta. Na saka
abincin a bakina kenan kira ya shigo tawa
wayar, na kalli screen din and I saw an
unknown number, without thinking about
anything na dauka na saka a kunne na
"hello?" And I heard a voice that sounded
so much like Mustapha's

"Fiyya! Kina ina? Mustapha ne. Jikin
Daddy ya tashi mun tafi dashi asibiti.
Hurry up"

Na mike da sauri gabaki dayan jikina yana
daukan karkarwa "hello, yaya Mustapha?
Mustapha?" But watakara kawai nake ji on
the other side ban kuma jin magana ba. I
cut the call and called again aka kuma
dauka but still bana ji "Mustapha? Kun
shigo gari? Kuna ina?" Still static, and
then another sound "hurry up" na saka
hannu na dauki handbag dina cikin sauri
nayi waje a hankali ina magana da kaina
cikin tashin hankali "Daddy.
.....
• Wayyo
Daddy na...... Wayyo Allah na…....
" Nayi
waje a rikice hawaye yana bin fuskata.

Ina fita na cigaba da kokarin trying
number din da aka kira ni da ita amma
kiran baya tafiya, zuwa lokacin sam na
manta ma da cewa tare muke da Gidado
ballantana in neme shi gabakidaya hankali
na yayi kan mahaifina da yake fama da
rashin lafiyar da already likitoci suka fara
lissafa masa lokacin da ya rage masa. Da sauri na doshi mota ta babu kowa a
gurin motar sai securities da suke daga
can bakin gate, na san asibitin da Daddy
yake ganin likita in yana gari, sai da naje
gaban motar na fara kokarin bude ta
sannan na lura da fork din da nake cin
abinci da shi a hannu na, ban san ma na
fito da shi a hannu na ba, Ina zaro key din
motar naji saukar hannu a fuskata ya
toshe hanci da bakina a lokaci daya, toshe hanci da bakina a lokaci daya,
tunanin da ya fara zuwa kaina shine
kidnappers ne, wani matsanancin toro ya
shige ni, zuciya ta ta buga da karfi making
my whole body weak, duk da haka sai da
nayi kokarin fighting amma sai aka hada ni
da jikin motar aka matse sannan aka kara
matse min hanci da baki aka hana ni
25
6
3
12:01 AM
numfashi, weakening my body more. I
started to paint, and I felt tsining allura
yana huda fata da tsokar kafada ta, and
then I lost consciousness.

Tsananin azabar zafi ne ya farkar da ni.
Zafin daga kasa na yake farawa sannan
yay vibrating through dukkan gabobin
jikina, blocking every line of thought,
destroying everything that made me who
I was and stealing every dream I ever had.
The strokes did not only took my virginity,
they took away my life.

An dare min idanuwana very tightly,
babu abinda nake gani sai duhu. At first
pain din da duhun ba su barni na gane
abinda yake faruwa ba, I later realized
what was happening and I was
devastated, I started fighting, trying to hit
the man above my with the little bit of
energy that I had, at the same time kuma ina kokarin bude idona but allurar da aka
yi min har lokacin ba ta bar jikina ba, and
also karfi na was no match for karfin
namijin da yake tare da ni.

A cikin kokawar da nake yi ne hannu na ya
sauka akan something metallic a gefe na,
ina dauka na fahimci fork ne from it's
shape, fork din da yake hannuna lokacin
da na fito daga restaurant din. In seconds
na dauka sannan da dukkan karfina na
soka wa wanda yake tare da ni.

I didn't think zai huda jikinsa but it did,
yayi sauri ya matsa daga jikina and I felt
his blood on my hand. Nayi sauri na fara
kokarin kunce daurin da aka yi wa idona
duk kuwa da zafin da nake cigaba da ji a
kasana. But an saka karfi sosai gurin yin
daurin and my hands and my whole body
was shaking violently, amma kuma a
lokacin babu abinda nake son gani sai
fuskar wannan azzalumin, fuskar wanda
ya dauki rayuwata,

Amma kafin in samu damar kunce ko da
dauri daya ne he came back and held
both my hands in one of his hands and I
felt another allura pierced the flesh of my
arm,

" will kill you!" Na fada "I will kill you" na
maimaita and then I lost consciousness
again.

Sanda na sake farkawa I was alone, lying
at the back seat of my car completely
dressed. Jaka ta, wayata, and mayafi na
all together akan seat a kusa da ni. Motar
a kunne, with the AC on. Nayi kokarin
mikewa zaune amma gabakidaya jikina
ciwo yake yi, kafafuwana har karkarwa
suke yi. Har lokacin ina jin alamar allurar a
jiki na, dusu dusu nake gani, hatta
kunnuwa na jin su nake yi kamar ruwa ya
shiga ciki ya toshe su.

Sannan ga bakin cikin da ya toshe
makogwaro na ya hanani numfashi. Na
kama kujerar gaba for support sannan na
mike zaune da kyar jikina gabaki daya
yana karmarwa, kokari kawai nake yi in
samu in leka waje ko zan ganshi, ko zan
ga wanda ya dauki rayuwata.

Duhu na gani a wajen, na kalli agogon
cikin motar naga 12:30 na dare. Wajen
yayi duhu sosai except for the street light,
da street light din kuma na gane inda
nake, layin gidan mu ne, just two houses
away from gidan mu, Na dauki waya ta na
duba and I saw several missed calls daga
Muhammad da Daddy da kuma
Mustapha, Mustapha,

I was 70% sure it was Mustapha because
of the encounters I had with him before
that, because of his name and his voice
that was used, and because of how him
and his mother reacted ranar da Daddy
yayi revealing my wealth. And also
because of how they treated me before
su san kudin da nake da shi and after sun
san kudin da nake da shi.

Na bude kofar motar na fito zuciya ta tana
tafasa, duk da ban ga fuskarsa ba but I
was sure Mustapha ne. Babu abinda nake
so a lokacin irin in nemi nearest makami in
Illata dan iska,

Sai dai ina fitowa dana cikin motar na
yanke jiki na fadi a gurin. Na sake mikewa
nayi taku uku zuwa hanyar gidan mu na
sake faduwa ina jin kaina yana juyawa
ganina yana gushewa. Sai da na huta
sannan na kuma mikewa still not giving
off, a haka na ja kafa har kofar gidan mu
sannan na sake faduwa a gurin ina jin
kaina kamar zai tsage.

Na ga an haske ni da fitila, na saka
hannuna na kare, naji muryar mai gadin
gidan mu "Safiyya?" Sai ya koma da sauri
ina jin sa yana magana "yallabai! Ga
Safiyyan da naji ana nema" sai kuma gasu fara kokarin dagani "Fiyya? Are you okay?
Lafiyar ki kuwa?" Na fara ture shi "karrrrr
ka tabbba ni.
14
9
2
12:01 AM
Dan isssska. Allah yaaaaa isaa na" and I
realized cewa irin maganar yan shaye
shaye nake yi.

Sai naga ya sake ni ya tsaya yana kare
min kallo, and he said the words "are you
drunk?" A lokacin Daddy ya fito da sauri
kamar zai fadi "Safiyya? Daga ina kike
haka?" Nayi kokarin tafiya gurinsa cikin
tangadi "daddddy" and I fall down again a
kusa da kafafuwan sa. "She is drunk"
Mustapha yayi concluding,

Avi hakuri da wannan.

*. *. *. *. *

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Thirty Nine : A Trap


Kunga ji da neman indazaku samu kayan
tsabtace muhallinku da kamsa sawa duk
awuri daya to this is ur bustop El Wada's
sun tanadar maku da komi d kuke bukata
cikin Amin ci.
Munda turarukan wuta irin su
Sandaliya Arab
Exclusive hawii
White House Kajiji
Special flasks
Habeel florals
Brown humra
Classic
VIP white humra
Soulmate da sauransu
Toilet cleaner
Mopping mist
Air fresheners
Ceramic/ tile cleaner and more
https://chat.whatsapp.com/
IHHSMB9AyPcEDUMpYkJh4a

Muna marabada masu siyen daya ko sari.

Not Edited

A gigice Daddy ya fara kokarin daga ni.
Na kama shi na mike amma saboda ba shi
da karfi shima sai muka tafi kamar zamu
fadi, Mustapha ya taho da niyyar taimaka
mana sai na tura shi baya da hannuna.
"kar ka taba ni na gaya maka" na fada
cikin murya irin ta yan maye. Daddy ya
ture shi shima yace "kar ka taba ta tunda
bata so" Mustapha ya matsa gefe yana
kallon mu sai na zagaye hannayena a
wuyan Daddy na cusa fuskata a wuyansa
na fara kuka, feeling safe at last.

A haka ya tafi da ni ciki, muna ta tangadi
tare kamar zamu fadi amma ya hana
Mustapha kama ni saboda nace bana so,
har muka shiga ciki sannan ya kwantar da
ni akan kujera yana kallona fuskarsa cike
da tashin hankali. Ya juya gurin Mustapha
yace "call the doctor, da sauri" sannan ya
juyo gurina "Safiyya?" Yace yana kallon
cikin ido na "what happened to you?"
Kafin inyi magana Mustapha da yake
tsaye a gefe yace "wallahi Daddy wannan
yarinyar a buge take, kalli idonta ka gani"
Daddy ya mike a fusace "zaka je kayi
abinda na aike ka kayi ne ko zaka cigaba
da tsayawa a kaina kana gaya min
maganar banza?" Mustapha ya juya da
sauri ya fita,

Daddy ya sake juyowa inda nake ya tsaya
yana kallona, a hankali yace "inna lillahi
wa inna ilaihir rajiun" na daga kai nima ina
kallon sa sai naga kamar jujjuyawa yake yi
ba'a tsaye yake a guri daya ba. Hatta
bangon falon da kujerun gani nayi suna
motsawa kamar wadanda suke yawo a
cikin ruwa. Mustapha ya sake dawowa ya
ajiye kayana na cikin mota a gabana
"Daddy na ga motar ta a waje, kofar a
bude, ga jakarta da wayarta nan ta bari a
cikin motar, na shigo da motar ciki.....
Daddy ya sake rufe shi da fada "I don't
care about the car. Ka kira Dr din ko baka
kira shi ba? And call the police as well"
Mustapha yace "police kuma Daddy?"
Daddy yace "yes, police" Na mayar da ido
nana rufe, a take bacci ya sake daukata.

Cikin baccin naji Daddy yana ta magana
da karfi "I need the lab result now!" Na
bude ido na kadan na ganshi a tsaye tare
da doctor din da yake duba mu a Abuja,
doctor din yace "kayi hakuri Alhaji ka
zauna, ka ga ba lafiya ce da kai ba. Na
dauki jininta ai gobe da safe zany duk
tests din da suka dace a kai" Daddy ya
girgiza kai "ba gobe da safe ba. Yanzu
nake so kay running analysis din, in ba
zaka yi ba in kira wani yayi" yace "za'a yi
Alhaji. Zanje in bude lab din yanzu inyi, In zargin mu na cewa a buge take gaskiya
ne zamu gani a jinin ta and then sai
musan matakin da zamu dauka"

Bayan ya fita Daddy ya lura da cewa na
farka sai ya sake dawowa inda nake
"Safiyya, wake up! Tashi ki gaya min
abinda ya faru da ke? Daga ina kike? Me
ya same ki? Tashi ki gaya min" nayi
kokarin tashi amma naji na kasa, ko'ina na
jiki na ciwo yake yi min amma kuma ciwon
da yake cikin zuciyata yafi da jiki na
damuna.

Maimakon inyi magana sai na kama kuka,
I should have told Daddy there and then
what happened to me amma sai naji
maganar tayi min nauyi da yawa inyi da
mahaifina, and I missed my mother a
ranar fiye da kowacce rana. Akwai
maganganu da yawa da ya mace ba zata
¡ya yi da babanta ba sai dai da mahaifiyar
ta, ni kuma bani da mahaifiyar, and the
woman that is suppose to be my mother
figure is the mother of the person da nake
zargi da laifin rusa rayuwata,
WhatsApp.com
EL WADA'S GLOBAL VENTURES
EM
WhatsApp Group Invite
13
9
4
7:19

I had to switched off my phone saboda
kiran da Muhammad yake ta yi min, and
my heart broke for him dan nasan yana
can cikin damuwa akan tafiya da nayi na
barshi, yana kuma tunanin cewa ta
tabbata yaudarar sa nake yi kuma karya
nake yi masa da nace zan kawo shi gurin
baba na.

A falon muka kwana daga ni har Daddy,
but I doubt shi yayi bacci ma throughout
the night. Sanda na tashi da assuba naji
allurar ya dan sake ni dan ina iya gani
sosai sai dai ciwo da kaina yake yi sosai,
sannan kuma jiki na gabaki daya yayi
tsami. Na tashi da kyar na shiga dakina na
hada ruwa nayi wanka and I cried kamar
idanuna zasu fito lokacin da nake yin
wankan, I felt like a used and discarded
rag. I have heard about rape and read
about some cases of rape online amma
ban taba tunanin cewa haka feeling din
yake ba, bakin cikin is undescribable in ba
wanda ya shiga cikin matsalar ba, which
bana yi wa kowa fatan ya shiga din, babu
wa da zai fahimci abinda ake ji a cikin
zuciya,

Har lokacin kaina a toshe yake, dan haka
ban samu nayi zurfin tunani akan komai
ba ballantana in yanke wani hukunci mai
ma'ana. Ina fitowa na saka riga a jikina
kenan naji knocking a kofar dakina and muryar Mustapha, "Ki zo inji Daddy", Naji
wani bacin rai ya tokare min kirjina, tsanar
sa tana kara ninkuwa a cikin zuciyata.
Ina saukowa naga Daddy a zaune. Na
cigaba da tafiya a hankali ina dafa bango
da kujera dan har lokacin kafafuwana
karkarwa suke yi. Daddy ya bini da kallo,
shi a tunanin sa har lokacin a cikin maye
nake shi yasa nake irin wannan tafiyar. Na
zauna a kasa ina kallon sa amma na kasa
cewa komai. Ya sake tambaya ta "daga
ina kike jiya da daddare? Me yasa muka yi
ta kiran wayar ki ba kya dauka?" Na
sunkuyar da kaina hawaye suna sake
cigaba da bin fuskata. Na bude baki na
wajen sau uku amma kalmomin sun kasa
fitowa. Shin cewa zanyi Daddy I was
raped yesterday ko kuma me zan ce? Na
san dole zan fadi abinda ya faru ko dan a
bi mini hakkina amma ba xan iya gayawa
Daddy ba.

Muna haka doctor din jiya ya shigo tare
da Mustapha, ya zo ya gaishe da Daddy
yana kallona sannan ya mikawa Daddy
wata farar takarda, Daddy bai karba ba
yace "tell me, Gaya min kawai" likitan ya
dan yi gyaran murya yace "akwai
percentage mai yawa na hard drug a cikin
jinin ta" Daddy ya dafe fuskarsa da
hannayensa biyu "innalillahi wa inna ilaihir
rajiun" na dago kai na kalle shi, na jima
banga tashin hankali a fuskar Daddy irin wannan ba.

"Shaye shaye kike yi Safiyya?" Ya
tambaye ni muryar sa cike da
disappointment. Na kara karfin kuka na
"Daddy wallahi ban sha komai ba, ka bari
zanyi maka bayani" ya mike tsaye yayo
kaina "yi min bayanib mana to inji, idan ba
ki sha komai ba menene ya kawo hard
drug cikin jinin ki?" Nayi shiru tare da rufe
idona, maganar tana yin kuna a cikin
zuciyata amma bakina ya kasa furtata.

A lokacin ne naji abinda ban taba ji ba a
rayuwata, saukar kyakkyawan mari akan
kuncina, na bude idona a tsorace ina
kallon Daddy, kafin in ankara wani marin
ya kuma sauka wanda ya fi wancan karfi a
daya kuncin. Karfin marin ya saka mayafin
kaina ya kunce, sai ya kama gashina da
hannunsa ya finciko ni fadi a tsakiyar falon
"ba zaki gaya min gaskiya ba?", Doctor
din da Mustapha suka taso da sauri suka
rike shi, shima kansa neman faduwa yake
yi. Na kwanta a inda ya jefar da ni ina kuka
matsananci, Daddy bai taba duka na ba
tunda aka haife ni duk kuwa da tarin
laifuffuka na, amma yau gashi ya dake ni
akan laifin da ban aikata ba,

A lokacin naji sallamar wasu sun shigo
gurin, na cigaba da kuka na ban tashi ba har suka zauna suna gaishe da Daddy
amma bai amsa ba dan kamar magana ta
dauke a bakin sa, a lokacin na fahimci
police ne and I remembered Daddy
mentioning police jiya cikin dare.
Sai da Daddy ya gama mayar da
numfashin sa sannan yace musu "ina so
ku bincika min inda yarinyar nan take a
jiya da dare. Ta dawo min gida a buge and
something is telling me that there is
something or someone behind that. Da
akwai abinda ya faru wanda taki fada min"
sai ya dauki passport size picture dina a
aljihunsa ya mika musu "a M.D University
take zaune a hostel. Ku fara binciken ku ta
can.

See if you can get their cctv ku ga sanda
ta bar makarantar and if possible, with
who"
Nayi kokarin mikewa zaune ina jin wani
sabon tsoron yana kamani. Muhammad
ne yaje makaranta ya ajiye motarsa a can
sannan muka fita tare a tawa. Kamar
Daddy yaji abinda nake tunani sai yace da
Mustapha "show them her car, su dauki
hoton ta da details dinta",
Sai da duk suka fita sannan ya dawo
gurina yace min "in na tarar kina boye min
wani mugun abu ko Safiyya, sai na babballaki".
E3
Police din basu jima ba suka dawo suka yi
reporting findings dinsu back to Daddy.
Sunje MD din sunyi magana da security
kuma sun basu access to cctv din gate
din su, sannan kuma sunga fita ta daga
makarantar "ba ita kadai ta fita ba, tare da
wani suka fita a motar ta, but we couldn't
get his face from the camera. Amma
zamu cigaba da bincike, duk abinda muka
samo zamu gaya maka". And Daddy
almost lost his mind after that information
"ku koma makarantar, press the security
su baku more information, su gaya muku
waye yake zuwa makaranta yana fitar min
da yarinyar da na basu amana" sai kuma
ya juyo kaina "waye shi? Waye a cikin
motar ki jiya? Shi ya baki kwaya kika sha?
Ina kuka je? Menene hadin ki da shi?" And
by that time I knew gaskiya ta will mean
nothing to Daddy. Duk ta inda na zaga ya
na zagayo, Muhammad ne a ciki.

*. *. *.

Present days........

Muryar Mommy ce tayi cutting through
tunani na. "Safiyya? Me kike yi ke kadai a
zaune a cikin duhu?" Na juya na kalli side
din da maganar take fitowa, side din kofar shigowa dakina. Sai a lokacin na lura da
duhun da dakin yayi gani kuma a zaune a
bakin gado. Ta lalubi switch ta kunna fitila
dakin ya cika da haske. Na daga kai ina
kallon ta. I have known her all my life, she
have been and still is a mother figure in
my life. Idan na d tana so na kamar yadda
take son yayan ta tabbas nayi karya ita
ma kuma in ta fadi haka tayi karya,
saboda soyayyar uwa ga yayanta daban
take, sai dai kuma a duk tsahon shekarun
nan ni dai ba zance ga lokacin da ta cutar
da ni bayyananniyar cutarwa ba, in ma
tayi a boye to bani da tabbas except for
sanda ta boyewa kowa including ni kaina
maganar cikina, though she claimed that
tayi ne to protect me from myself.
1 have never been a fan of her when
growing up saboda tana da fada ni kuma
ina da rashin jin magana. I have always
been daddy's girl, akaina Daddy bai yarda
da kowa ba including her. Wannan ya
kawo musu sabani a tsakanin su sosai, in
dai za'a ta ba ni sai Daddy yayi magana,
ba ita ba ko waye, ita kuma komai
kankantar abu idan nayi to bakin ta ba zai
yi shiru ba ta dinga yi min fada kenan, But
she does that to everyone, kawai dai ni
dan na fi sauran fitina ne shi yasa nawa
fadan ya fi na sauran yawa. A fahimta ta wannan sabanin da suke
yawan samu a kaina shine silar rashin
jituwar muni da Mustapha. In dai har
zamu keve daga ni sai shi to sai ya ci
zalina yace min munafuka, amma in a
gaban mutane ne musamman a gaban
Daddy to zsiyi6ta lallaba nine kamar wani
babban wa na. Amma da sun juya bayan
su zai dungume min kai ko yayi min wata
muguntar, sometimes a gaban Safina, sai
dai ko na kai kara in aka kira Safina shaida
sai ta goyi bayansa ta ki fadar gaskiya. Ni
kuma Mommy tayi ta min fada.
A saboda irin haka har saida Daddy ya
chanja min makaranta lokacin da muna
primary school. Ya ware min makaranta ta
daban driver na daban. Ai kuwa a kan
hakan ma sai da suka yi rigima da Mommy
tace zai raba kan mu saboda ina gaya
masa karya. And then as we grow up,
muguntar Mustapha sai ta chanja salo.
As for Mommy, relationship din munya
samu babbar baraka ne lokacin da Daddy
ya ambata cewa nice nake da mallakin
kusan duk abinda take tunanin ya
mallaka, A lokacin ta chanja min kwata
kwata daga ita har yayanta. Suka daina
min magana suka daina shiga harkata
except for twins da suke zagayewa ba tare da ta sani ba suyi min magana, suma
in ta gansu sai randu ya baci.

Babu inda ba ta je ba akan ayiwa Daddy
magana ya rushe waccan maganar, tana
ganin anyi mata ita da yaranta rashin
adalci, duk wanda ta san Daddy yana jin
maganar sa sai da taje ta kai kara gurinsa,
sai da ta tabbatar magana dai haka take
babu chanjawa sannan kuma ta hakura
and I guess they moved to plan b, wanda
a cikin sane ta jawo ni jikinta take nuna
min soyayya da kulawa fiye da kowa a
duniya, watakila a tunanin ta hakan zai
saka in raba kudin da su ko kuma in
daddy ya mutu in cigaba da kula da su.
Sai kuma ga Mustapha of all people ya
zagayo ya zo yace min wai yana so na
yana son ya aure ni. Can you imagine the
audacity? I rejected him outrightly. And
few months after that I was raped and
framed for shaye shaye, and the first
thing Mommy did sanda maganar taje
kunnen ta shine bada shawarar cewa ayi
min aure, a aura min Mustapha. But that is
a story for another day, Shin ta yaya ba
zan ki taba? Ta yaya kuma ba zan zargi
Mustapha akan abinda aka yi min ba?

Amma kuma yanzu dan zargina akan
Mukhtar ya tabbata hakan na nufin cewa they are innocent of that crime. Hakan na
nufin maganar Daddy gaskiya ce da yace
Mommy is not cruel.

Ta karaso ta zauna a kusa da ni tare da
rike hannuna a cikin nata tace "dole
wanna rayuwar ta chanja Safiyya, ko so
kike ki samu mental issue ne? Ta yaya
zaki mayar da zama a cikin duhu tare da
dogon tunani dabiar ki?" Na juya fuskata
gefe tare da kokarin goge hawayen da
yake jikin ta dan kar ta gani, and she said
"and you have been crying too. Kukan
nan ba zai kare ba ne ba wai?"

Na goge hawayen tate da gyara murya ta
sannan nace "nima na dauka na gama
kukan. Ashe da saurana. Rayuwa keeps
throwing things at me tun kafin in Zo
duniya ma. I thought na kai karshe, I
thought babu abinda zai sake bani
mamaki ashe akwai saura na Mommy, ban
kuma san menene rayuwa have in store
for me nan gaba ba".

Tayi ajiyar zuciya tace "nima haka, Ba zan
iya ce miki menene zaki fuskanta nan
gaba ba, amma kuma zan iya ce miki you
are strong enough to face koma menene,
because you are your mother's daughter,
You are as hard as a stone".

Sai na yi murmushi na mike na je na tsaya
a gaban wani hoton mu ni da Ammi da
yake dakin, a Oasis ne ta jefa ni sama ta
mika hannu zata cafe ni, gabakidayan mu
muna dariya. Na tsaya a gaban hoton
sannan nace "no mommy, stone ana iya
fasa shi with something as common as a
hammer, I am harder than that. Ba kuma
zan ce as hard as a steel ba, dan shima
something as common as oxygen and
water can destroy it" na juyo ina kallon ta
nace "no Mommy, I am as hard and as
precious as a diamond. Nothing, I mean
nothing, can break a diamond, not even
fire, except another diamond of cause"

Tayi shiru tana kallona bata ce komai ba,
sai na tambaye ta "saura kwana nawa biki
na?" Ta yi mamakin tambayar amma sai ta
amsa "kwana goma" nace
"good. Very good “


Amma a raina na ga kwana goman kamar
sunyi min yawa, I have waited nine
months amma yanzu zuciya ta naji ba
zata iya jiran ten days din ba kafin in kama
wanda yay min wanna babban zaluncin.
Shaidar kamannin ido ba zata ishe ni a
court ko a gurin iyayen mu cewa Mukhtar
ne yayi min wannan zaluncin ba, I need to
request for a DNA test, and even that

bana jin Mukhtar will just go willingly ya
bada sample for the test, idan kuma na
dauki sample din from him ba tare da
saninsa ba zai iya denying yace it is not
from him. Dan haka ina bukatar shaidar
da zan tunkari iyayen mu ko hukuma da
ita wadda zata saka su matsa masa ya
bada sample openly for the test, and to
get that dole in tare a gidan sa.
Bayan na gama shirin kwanciya na
kwanta, duk da nasan ba lallai in samu
bacci mai kyau a wannan daren ba, sai ga
kiran mukh6ya shigo wayata kamar yadda
ya saba yi a yanzu kusan duk dare. Ganin
sunan sa kawai da nayi sai naji wata irin
tsanarsa tana cika dukkan ilahirin jikina.
Wani irin rage that I have been bottling up
for months yana cika zuciyata. Gani nake
yi babu abinda zai bani satisfaction idan
da ace kisa ba haramun bane ba irin in
samu wuka mai kaifi in soka a
makogwaron sa sannan in jawo ta kasa
har cikin marar sa.

Sai dai kuma wannan tunanin sai ya saka
na fara tunanin anya tarewa ta a gidan sa
shine mafita? Kar fa inzo in aikata abinda
zai rusa dukkan kokarin da nake yi dan
ganin na gyara rayuwata. Kiran ya katse wani ya sake shigowa sai na dauka, trying
to force myself to play along zuwa sanda
zan samu abinda nake nema.
Ina dauka yace "maman boy, ko har kinyi
bacci ne?" Sai na kara fahimtar wani abu
da ban fahimta ba da, he have been
asking for junior tunda na saka kafata a
kasar nan. Pretending cewa saboda
soyayyar da yake yi min ne ya saka yake
son abinda na haifa ba ta hanyar aure ba.
Nace "me kace?" Yayi sauri yace "cewa
nayi amaryata" nace
"ba haka kace ba, ka
fadi abinda ka fara fada daga farko" yace
"na fasa fadar wancan din ai, dan yanzu
kin zama hukuma sai lallashi. Lallabawa
nake yi har Allah ya dube ni ya cika min
zuciyar ki da soyayya ta". Nayi kokarin
bashi amsa ma ko da bakar magana ce
amma naji zuciya ta ta toshe makogwaro
na maganar ta ki fitowa. Ya cigaba "but
seriously, you need to call them and ask
them halin da yake ciki ko? You can't just
leave him in the NICU, na san zuwa yanzu
ya warware ya kamata ma ace sunyi
discharging din sa. Ina zasu kai shi
kenan?" Nayi gyaran murya nace "and
how is that any of your concern? Idan ni
ban damu da shi ba kai menene naka?"
Yace
"sorry....
.. Na san za'a vi haka dama.
Relax, na daina maganar sa. So, ya yau din?"

Na katse kiran tare da ajiye wayar. Me
yasa wai tun farko ban fahimci inda
mutumin nan ya dosa ba. But how could
he did that to me? Why? Me nayi masa?
Kawai sai na rungume pillow na fara rusa
kuka ina jin ciwon abin yana dawo min
sabo a zuciya ta.
Washegari na tashi da kumburarriyar
fuska da edgy mood, kowa a gidan sai da
yayi receiving kason sa na bacin raina.
Mustapha asked me me yake damuna and
I told him to mind his business ko in bude
file dinsa yanzu. Bai kara ce min komai ba.
Hatta Daddy sai da ya tambaye ni abinda
yake damuna sai nace masa bana jin dadi
ne kawai. Sai kuma na nemi ayi
postponing duk was pending businesses
da suke bukatar attention dina till further
notice. Naga Daddy ya damu da hakan
amma a zuciya ta sai nace zai fahimta ne
nan gaba, I then turned to Mommy na
gaya mata she should count me out of
every event na biki da ta shirya, suyi
kayan su amma ni ba zanje ba because
my mood was so messed up a lokacin na
san in naje zan iya zagin mc ana tsakiya
da biki

Daddy ya kira ni har dakin sa ya tambaye
ni menene yake damuna nace masa babu
komai, he was worried ya ga kamar na
koma yadda nake a watannin baya, but i
assured him babu komai kawai ina
bukatar time ne alone to process the
whole marriage thing da yake doso ni.
And he seemed to understand that.
Har na tashi zan tafi sai ya kira sunana, na
juyo ina kalion sa sai yace "kuna waya da
Hajjo?" Na girgiza masa kai, yace "muna
wata da Sufyan ina jin halin da yaron can
yake ciki, ya gaya min an sallame shi daga
asibiti, wannan weekend din ma zasu taho
Nigeria gabakidaya. Kin sam za'a yi auren
Abdul" na cigaba da shiru ban ce komai
ba sai ya sake cewa "kina son ki ga hoton
sa?" Nayi sauri na girgiza kai sannan na
fita.

A bangaren Mukhtar yayi ta neman waya
ta baya samu, sai kawai ya dauko mota ya
taho Kano. Ina daki na ina kan sallaya ina
gayawa ubangiji matsaloli na kamar
kullum sai gashi ya bude kofa ya shigo
kan sa tsaye. Na daga kai na kalle shi, nan
take zuciya ta ta fara aiyana min shi yana
aikata min abinda aka yi min, na rufe
idona kawai sai ga hawaye yana bin
fuskata. Ya karaso da sauri ya tsuguna a
gabana "innalillahi.
., Safiyya kuka fa kike
yi? What happened? Nayi ta kiran ki bana
samun ki? Me yaje damun ki?" And his concern broke my heart more, like how
can you pretend to love and care for
someone and then hurt them like that?
What kind of a human being does that. Na goge hawaye na and I told him abinda
dama na riga nayi planning gaya masa
just to see how he would react and dan ya
rabu dani ya daina damuna tun kafin inyi
masa illa "they called me from the
hospital, the boy is dead". And he reacted
just like I expected. Saura kadan ya fadi daga tsugunnon da
yayi, and his face shows it all, his
reactions cleared dukkan sauran wasiwasi
na, "What?" Yace cikin daga murya "what
did you just said?" Ban maimaita ba na
cigaba da kallon sa. "Yaushe suka gaya
miki hakan? Ta yaya zasu fadi haka? Are
they sure ya mutu? Ta yaya ya mutu?" Na
cigaba da yin shiru ina kallon sa. Ya mike
tsaye "we should go there, muje mu
tabbatar, mu kai shi wani asibitin suyi
double checking, How can he be dead
now" Na gyara zamana ina kallon fuskar
munafiki azzalumin da yayi min babban
zalunci, already har na fara planning
hanyoyin da zan rama, duk hanyoyin da nake planning din kuma babu mai kyau a
cikin su. Calmly na kira sunan sa
"Mukhtar" ya kalle ni bai amsa ba amma
sai nace "he is dead. Ba kuma a kasar nan
bane ba ballantana mu dauki mota mu
tafi. He is dead, magana ta Wuce".

Sai ya zauna akan kujera kamar wanda
aka hankada, sannan ya saka hannu biyu
ya dafe kansa, and I understood ya
mugun dora ransa akan yaron da ko
ganinsa bai taba yi ba. Sanda ya dago kai
ya kalle ni idonsa ya kada yayi ja, yace
"how can you let this happened? Tun
farko me yasa zaki barshi shi kadai a wata
kasar ke ki taho wata kasar? I am sure
negligence ne ya kashe shi" a nutse na
sake yi masa magana "me yasa ba zan
taho nan in barshi a can ba? Kar ka manta
he is a bastard. Ba shi da uba. I was
gruesomely raped, a sanadiyyar haka na
samu cikin sa, maybe ka manta ne.
Maybe I need to remind you that he is not
your son. Ko naka ne?"

Yayi shiru yana kallona and then he
blinked and brought back the mask of
munafuncinsa,
"haka ne, I am so sorry
Safiyya. I shouldn't have shouted at you.
Kiyi hakuri. What can I do to help?" Ya
fada yana saukowa daga kan kujerar
trying to hug me "na daga masa hannu tare da bata rai "Please no. You can help
me by leaving ne alone, let me morn him
in peace dan Allah. Kuma ina so duk wata
hidima da ka shirya ta bikin nan ka cire
nina ciki please, the goal is for me to
marry you kuma an riga anyi, so kawai
abinda nake jira shine akai ni gidan ka"

Yayi ajjiyar zuciya tare da zama a kusa da
ni. "Na fahimta. I am sorry Safiyya. Kiyi
hakuri kinji?....…. Next year by now insha
Allah da dan mu a hannun mu. And ina
ganin ma wannan abin da ya faru is for
the best for you and the boy. Allah ya sa
mai ceton iyayensa ne" nace "Allah ya sa
mai ceto nane. I am his only parent" yace
"yes, right, haka ne. Ameen ya Rabbi. But
still zan so ace kin barni na zauna tare da
ke. I don't want to leave you alone a
wannan yanayin" na girgiza kaina "I want
to be alone" ya mike "okay .... Alright. Zan
tafi, but sai gobe zan koma Abuja" ban ce
masa komai ba sai ya juya, har ya kai
bakin kofa na kira sunan sa, ya juyo nace
"I will appreciate it idan maganar mutuwar
yaron nan zata tsaya a tsakanin mu. Bana
son mutane suyi ta min maganar" ya
gyada kai cikin fahimta, ") understand,
and thank you for letting me know",

Yana fita na goge hawayen na sannan nace '"bakin munafuki Da sannu zaka girbi abinda ka shuka “

But na samu abinda nake so, peace and
quite to make my plans, and I did made
plans in batches, akwai plan A, akwai B
akwai kuma C. Kuma a hankali duk na
nema kuma na samu abubuwan da nake
bukata to work the plans. Sai dai damuwa
ta guda daya ita ce, the marks may have
faded tun da wata tara kenan da faruwar
lamarin, sannan kuma takamaimai ban
san a ina zan duba a jikinsa inga marks
din ba. Saboda ban san a ina na same shi
ba. But my guess was cinyarsa ko kasan
bayan sa. But koma a ina ne in dai yana
nan sai na ganshi.
Mommy taje Abuja suka gama jeren su, ta
dawo tana ta labarin yadda gidan yayi
kyau, harda kara kawo min wani list din na
abubuwan da ta lura in aka saka zasu kara
wa gidan kyau, na karba kawai na ajiye
nace zan siya amma ni bani da niyyar yin
ko da sati daya ne a gidan ballantana har
in damu da kyan sa ko rashin kyansa.
Ranar kamu suka zo ita da wasu cousins
din Daddy suka gama hidimarsu suka fesa
min turare suka tafi,

Ranar da ta saka zata yi taron ta tazo, tayi taron ta a event center din da ta kama,
and I have no idea wanne uzuri ta bawa
mutanen da suka je gurin ha rashin zuwan
amarya. Daga nan kuma sai aka fara shirin
tafiya Abuja, twins suna ta tsokana ta wai
zasu ga kukan rabuwa da Daddy amma
ko kwalla banyi ba, shine dai kamar zaiyi
kukan, ya zauna yayi ta min nasihar bin
miji da hakuri da kiyaye dokokin Allah da
sauran su amma ta kunnen hagu suke
shiga duna fita ta kunnen dama. Sai da
zan tafi sannan naje gabanss na durkusa
na rike hannunsa nace "Daddy, for all the
pain I have caused you, kayi hakuri, ka
yafe min. Insha Allah, I will make
everything okay, ko ba dan ni ba ko dan
kai" ya dago ni jikinsa ya rungume ni yace
cikin karyayyiyar murya, "na yafe miki
Safiyya. Nima ki yafe min. You went
through everything because of my wrong
decisions, because of my weakness" sai
na dago daga jikinsa nay kissing cheeks
dinsa sannan na juya na tafi.
A abuja muna zuwa muka tarar da Safina
a gida, sai dana ganta sannan na fahimci
abinda Mommy take fada, ta chanja
gabakidaya and she looks somewhat
depressed. Har da akwatin ta tace kwana
biyu zata yi a gida wai mijinta baya nan
yayi tafiya. Mommy ta fara fada "tun
tafiyar da kika ce yayi har yanzu bai dawo ba?" Safina ta kalle ni na dauke kai sai
tace "ya dawo, sake komawa yay" and I
knew she was lying",
O
Yan bikin Abuja ne dai suka samu ganina
tunda a gida aka yi, amma a daki na wuni
sai dai duk me son ganin amarya ya hau
ya ganni ko kwalli babu a ido na ya juya ya
tafi. Sai da Hajiya tazo sannan na sauka
gurinta saboda ba zata iva hawowa
saman ba kuma tana da matsayi mai
girma a gurina ba zan iya cewa ba zata
ganni ba. Na sauka ita ma ta zauna tavi ta
min nasiha da kuma bani labaran Ammie,
a lokacin ne nayi kuka, shima ba kukan
auren ba ne ba kukan kewar mahaifiya ta
ne, ko yaya rayuwata zata kasance da ace
tana da rai? Sai nayi kwanciya ta a jikin
Hajiya anan falon har aka ce ga masu
daukan amarya nan sun zo sannan
Mommy ta kama ni muka koma sama.
Haka tayi ta aikin shirya ni, ta shafa min
wancan ta goga min wancan ta barbada
min wancan. Ta zubo wani abu a kofi ta
bani ta saka na shanye "kayan nan fa sai
kina amfani da su na gaya miki, na fahimci
ba son amfani kike yi da su ba. Kinga
Safina har ta karar da nata yanzu zan
bada order a kawo mata wasu, mazan ne
sai da irin wadannan dabarun, ballantana nata mai shegen taurin kaj" sai na mike na
fake da shiga bandaki just to get her to
stop talking about mijin Safina in dai ba
ina so wanna kai amaryar ya tarwatse
ba.
A haka aka dauke ni, na dauka gidan
Mukhtar din za'a kaini sai naga an fara
kaini gidan uncle Ahmad, sai a lokacin na
tuna ko su Salima ban gani a gidan mu ba
ballantana Umma. Aka zaunar da ni a
gaban Umma Mommy ta fara jawabin
bada amana ta "dama yar ki ce. Daga
gida ta taho ta kuma zo gida. Ba dan ma
Allah yayi haka ba ai da ke ce mai daukan
ta ki kai ta dakin miji" sai Umma tace
"'haka ne. Allah ya riga yayi babu yadda
zamuyi. Jarabawa ce Allah yayi mana
Allah bamu ikon cin ta baki daya" Mommy
ta ce "wacce jarabawa kuma kike magana
a kanta? Yarinya dai yarki ce kuma matar
danki, kuma war jikokin ki nan gaba. In
kin rungume ta kanki kika yiwa in kin
watsar da ita ma haka. Abinda ma sani dai
Safiyya bangon sikari ce duk wanda ya
jingina da ita sai ya ji zaki, idan make ba
ki jingina ba to an riga an jinginar miki
kuma kin dandani zakin ta" da kyar aka
lallaba Mommy tayi shiru, Umma tana ta
cewa ita ba wani abu ta fada ba Mommyn
ce tayi mata rashin fahimta.

Ni dai kawai ina jin su. Ko Umma ta karbe
ni ko kar ta karbe ni dama ba zama zanyi
ba. Mutanen da suke gurin sai suka dauka
rigima ce kawai su Mommy suke yi irin ta
faccaloli.

Daga nan sai gidan Mukhtar, gida ya cika
da kamshi mai dadi da kuma sanyin ac.
Aka wuce da ni bedroom din da suka ce
C
shine nawa akan zaunar dani masu nasiha
nayi masu tsokana nayi ni dar ina lullube
ina jin su, ina kuma Allah Allah su tafi su
bani guri dan maganar Umma ta kara
dada min tsanar auren da kuma dan nata
baki daya. A haka har aka watse, saboda ban
gayyaci kawayena ba ya sa Mommy tace
Safina ta zauna da ni kar a barni ni kadai.
Amma suna tafiya na bude fuskata ina
kallonta tana danne danne a waya nace
mata "zaki iya tafiya" ta mike tsaye ta
dauki jakarta "dama ai ba zaman kaina
nake ba, saka ni aka yi, kuma ina da gidan
miji nima wanda yafi wannan ma" nayi
murmushi "shi yasa naga kin bar gidan
mijin naki kin taho gida, in har gidan mijin
da dadi kiyi zamanki mana a can?" Ta yi
murmushi sannan tace min "lallai rashin
sani hausawa suka ce yafi dare duhu. Amma babu komai, nan gaba kadan zaki
sani ai, zaki gane irin dadin da nake ji a
gidan mijina. Ko kuma ince zaki gani da
idonki" ta karasa maganar tana shafa
marar ta, na kalli marar sannan na kalle ta
ina jin zuciya ta tana kuna, tayi kamar zata
tafi sai kuma ta sake juyo wa tace "fata na
shine dan da zan haifa yayi kama da shi
sak, at least kya rage zafi idan mun hadu
kin ganshi. Before then, enjoy your own
husband. Ina yi muku fatan zaman lafiya
da zuri'a mai albarka".

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Forty: The Trap 2


Not edited please,

Nayi kokarin danne zuciya ta da already
dama a kusa take, amma sai hakan ya ki
yiwuwa, I guess komai yana da limit dinsa,
space din pretending hakuri ya kare a
zuciya ta. Nace "babbar matsalar ki a
rayuwa Safina shine kina da cutar karya,
ke makaryaciya ce....." Ta girgiza kai tana
murmushi "yes, I am a liar. But not this
time Safiyya. Not about this. Idan baki
yarda ba call him and ask him, that is idan
zai daga kiranki. Dan ba ma shi da
number dinki a yanzu, ko zaki gwada? In
baki da number din in baki watakila ya
gaya miki how crazy he is into me. Ohh na
manta fake matar aure ce ko waya ba
zaki iya yi da shi ba. Well good luck
driving your own husband crazy"

Na mike da sauri sai tayi sauri ta fita daga
dakin, ban hakura ba na bita har falo sai
tayi sauri tayi hanyar fita har tana
hardewa kamar zata fadi. Na kira sunan ta
'"Safina!" ta tsaya sannan ta juyo still da
murmushi a fuskar ta, nace "ba zan tambaye ki abinda nayi miki a rayuwa kika yi min abinda kika yi min ba, ba kuma zanyi miki fatan ayi miki abinda kika yi min
ba because that will be mercy for you,
amma ki jira ni ina nan zuwa gare ki, da
kaina zan dauki fansa a kanki ba zan jira
karma ba, and when I am done with you,
you will regret the ranar da kika dora idon
ki a kansa".

Na juya na koma dakin da na fito na koma
na zauna a gurin da na tashi. Amma kuma
zaman sai ya kasa yiwuwa. I kept rocking
back and forth and kept fisting and
unfisting my hands. Nasan da Dr Salma
ES
zata ganni a wannan yanayi da tabbas
gado zata bani. Zafin da nake ji a zuciya
ta ko makiyi na bana yi masa fatan ya ji
irinsa. Na san cewa Safina makaryaciya
ce tun muna yara, amma sai na rasa
dalilin da yasa yau na bari kalamanta suka
taba ni har haka, me yasa na kasa yarda
cewa karya take yi yanzu? Me yasa nake
tunanin gaskiya ta fada? Me yasa rayuwa
zata zo min da haka? Me yasa nake
fuskantar jarabawa ta kowanne bangare
na rayuwata? Me yasa nake yiwa
Muhammad irin wannan zazzafar
soyayyar alhalin yana mijin yar'uwata ni
kuma ina matar wani,

Ban san mintuna ko awannin da na kwashe a haka ba sai ji nayi an bude kofar dakin an shigo, ban kalla ba amma na riga na san ko waye, and for the uncountable
time naji ina fatan ace kisan kai halal ne
da yau Mukhtar ba zai kwana a duniya ba.

Ya karasa shigowa ya zagayo gabana ya
tsaya. Ya sha kwalliya irin wacce ban taba
ganin shi a cikin ta ba, fuskarsa dauke da
farin cikin da ban taba gain shi a cikin sa
ba. Ya ajiye ledojin hannunsa "amarya ta"
na daga jajayen idanuna ina kallon, and I
guess the eyes scared him dan lokaci
daya naga murmushin fuskarsa ya bace,
but he still tried to continue keeping his
composure. Ya jawo kujera gaba na ya
zauna yana cigaba da kallon fuskata. "Are
you okay?" Ya tambaya cike da concern.

Na girgiza kaina "no, I am not okay. I am
not even close to being okay" na fada da
murya mai cike da daci. Ya danyi gyaran
murya, a fuskar sa ina ganin emotions da
02
yawa, a cikin su har da fear. "Me ya faru
kuma? Talk to me. You can tell me
anything" nace "anything?" Ya danyi
karamin murmushi "yes, anything",

Na gyara zamana na cire mayafin da yake
jikina na ajiye nace "okay, Let me start from the most important thing. Kana son
sanin abinda ya faru da ni? I was raped"
na fada ina locking gaze with him, yayi
saurin dauke idonsa daga cikin nawa sai
na saka hannu na juyo da fuskar sa zuwa
gare ni "anar 13th of last july, someone
called me lokacin ina tare da Muhammad
a restaurant yayi min karyar Daddy ba shi
da lafiya, ya kira kansa da suna Mustapha
kuma yayi faking muryar Mustapha, sanda
na fito he almost suffocates me ta hanyar
toshe min hanci da bakina sannan yayi
min allura ta kwaya mai saka bacci, he
kidnapped me and took me to......." Nayi
shiru ina tunanin sannan nace "I don't
even know where the hell he took me to,
do you know why?".

Ya hadiye yawn tashin hankali a
makogwaronsa and I can already see
streaks of gumi a goshinsa. "Why are you
telling me this Safiyya? I don't want to
know" ya fada yana kokarin tashi tsaye sai
na kama hannun sa na rike gam sannan
nima na mike "ohh but you have to know.
You are my husband remember? Dole in
gaya maka kuma dole ka sani. Ta yaya
zamu fara aure da boye wa juna
maganganu irin wadannan? That man
took me somewhere that I do not know
because ya daure min idanuna, ya daure min idanuna so tight that skull dina kamar min idanuna so tight that skull dina kamar zai tsage, he then raped me" ya kwace hannunsa tare da saka su ya rufe
kunnuwan sa "na gaya miki bana son ji. I
know you said something like that
happened. But I do not want to know the
details. Me yake damun ki ne wai?" Ya
fada almost shouting but I didn't flinch.

Na sake matsawa gabansa not minding
banbancin girman jikin sa da nawa na
cigaba da magana "he RAPED ME
Mukhtar. And with that rape he took away
everything da nake da shi a rayuwa ta,
everything, including abubuwan da ban
riga na samu ba ma. He killed me that day
dan a yanzu babu abinda yayi saura a tare
da ni sai bakin ciki da zafin zuciya da
tunanin tarin abubuwan da na rasa" na
fada hawaye yana zuba daga ido na
kamar an bude fanfo. Cikin rawar murya
Yace "am sorry Safiyya, am sorry that
happened to you" nace "no you are not.
Not yet. Ai ban gama baka labarin ba. Ya
sake min wata allurar ai, he did not even
care if jini na ba zai dauka ba ko kuma
kwakwalwa ta zata buga , ko zan zama
addict sanadiyyar hakan ko kuma na zan
rasa raina ba ki daya, no, he did not care,
ya sake yi min wata allurar, After he raped
me sai ya dauko ni cikin maye ya dawo
dani gidan mu ya yasar da ni a bakin hanya like a used and discarded rug, and
wannan abin cost me my father's trust,
har yau Daddy bai yarda cewa ba shaye
shaye naje nayi ranar ba, kamar yadda bai
yarda cewa ba zuna na aikata na samu
ciki ba. Yes, rape din ya zama sanadiyyar
da na samu ciki, sanadiyyar da na haifi da
ba tare da aure ba, and that alone is a
trauma beyond measures" ya rufe idonsa
tare da jingina kansa a jikin bango, gumi
yana bin goshinsa zuwa fuskarsa, sannan
ya sake tambaya "why are you telling me
this Safiyya?" Nace "kai ka tambaye ni.
You asked me what happened to me shi
yasa na ke baka labari" yace '"I did not
wish to know all this, please stop telling
me this" sai ya juya da sauri yayi hanyar
fita daga dakin, na bishi nima da ssuri6naje ya sha gaban sa na tsaya muka cigaba da kallon juna, na tabbatar ya hango tarin tsanarsa da take cike a cikin
idanuna kamar yadda ninma na hango
tsoro da rashin gaskiya da suka cika nasa
idon. Murya can kasa nace masa "but
don't worry my husband. Ko waye ya
aikata min hakan I promised him tun a
lokacin da yake aikatawar that I will find
him, and when I do, I will kill him. I will
take his life just like he took mine".

Na sauke idona kasa sannan na matsa na
bashi hanya, bai kara cewa kala ba ya bude kofa ya fita. Na saka hannu na rufe kofar na murda key sannan na dawo na koma inda nake zaune na cigaba da zama
idona akan frame dim da aka yiwa dakin
ado da shi. I knew I messed up. I messed
up big time, dan yanzu ya tabbatar na
gano shi kuma zaiyi dukkan kokarin sa ya
ga cewa ya kare kansa. But I didn't care
because I let my anger out and I felt good.

Na sauko daga kan gadon na jawo ledojin
da ya shigo da su, kaji ne a leda manya
manya masu zafi, daya kuma drinks ne
masu tsadar gaske, sai dayar kuma fruits.
Wato ya shirya celebrating wanna rana
sosai. Na jawo kaza daya na bude sannan
na dauko drink daya, ba zan iya planning
the ways to get out of this mess cikin
yunwa ba. Da safe tun kafin in bar kan sallaya ta naji
tashin motar sa, and I wondered ina zai ie
da sassafe? To ko guduwa zai yi ne? But I
doubt idan zai gudu, not yanzu da yake
ganin ya same ni, Wajan karfe goman safe sai ga Salima ta kawo mana abinci, Ta shigo har bed room
muka zauna tana ta y min hira, a lokacin
na fahimci kamar su basu san abinda ya faru da ni ba, basu san zancen ciki na ba,
kamar iyayen ne kadai suka sani sai
Mukhtar kuma. Tace "na dauka Umma
zata so auren nan sosai saboda yadda
take son ki, and she was in support
before, yanzu sai naga duk tayi wani iri
bata wani excitement, but she will get
over it very soon tunda muna son ki mu
da yaya" ta karasa tana winking at me, na
kirkiri murmushi "and I love you too, kuma
1 appreciate the food dan ko kitchen din
gidan nan ban san inda yake ba" ta mike
tsaye tare da jan hannuna "tashi muje mu
zagaya to, yaya bai zagaya da ke ba? And
where is he by the way" nace "ya fita,
something emergency. And thank you,
kiyi zamanki kawai, zan zagaya later.
Yanzu na gaji" she smiled ta koma ta
zauna "amarya amarya, dole ki sha gajiya
yarinya" nayi kamar ban fahimci abinda
take nufi ba. Ban zagaya gidan ba kuma
bani da niyyar zagayawa, dan da ace ban
bar emotions dina sunyi getting the better
of me ba da yanzu ina hanyar gidan
iyayena. Bana jin har in bar gidan Mukhtar
zan dora tukunya.

Sai wajen zuhr ya dawo, sai a lokacin ni
kuma na zauna ina cin abincin da Salima
ta kawo min. Naji shigowar sa amma ban
waiga ba sai ya zo ya zauna a kan kujera a
kusa da ni, na juya na kalle shi and I saw a
smile on his face "am sorry na fita na bar kike kadai, I had to go and see some of
my friends up, dama jiya suna ta yi min
mita ban shigo da su sunga amarya ba, ni
kuma na san you will not like that" na
cigaba da shan kunun madarar da yake
cikin kofi a hannu na ba tare da na kalle
shi ba.

Ya jawo basket din abincin ya bude yace
"Salima tace min dama zsta kawo mana
abinci. She did well. Dama ko breakfast
ban yi ba. Jiya ma ko dinner ban ci ba" na
cigaba da yin shiru na har ya gama zuba
abincin sa ya dawo ya zauna sosai yana ci
sannan yace "Safiyya. I am glad we talked
about that issue yesterday. I am glad you
felt free to talk to me about that. Maganar
ta fahimtar da ni abubuwa da yawa. It
hurts me that you are hurting that way
and there is nothing I can do about it. Da
ace zan iya goge miki wannan bakin cikin
da tabbas zan goge miki wanna memory
din da tabbas na goge miki shi, but ba
zan iya ba, abinda zan iya kawai shine a
matsayi na na mijin ki a yanzu in tabbatar
na baki dukkan kariyar da ta dace dake a
yanzu, yadda babu wani abu da zai kuma
samunki ko da wanda bai kama kafar
wancan bane ba, I will protect you ko da kuwa a ce da rayuwa ta ne, I will make sure baki sake zubar da wani hawayen ba sai dai na farin ciki". Naii kunun da nake sha ya tsaya a wuyana ya ki wucewa, idan da akwai abu guda daya da na fahimta game da Mukhtar
wanda duk tsahon shekarun da na sanshi
ban fahimta ba sai yanzu shine he is a
narcissist, he will gaslight you, sweet talk
you out of blaming him and then hurt you
physically and emotionally.

Na ajiye cup din hannu na ina kallon sa
nace "don't worry my husband, kar ka
samu damuwa, I got emotional ne jiya shi
yasa har nayi wadancan maganganun but
maganar ta riga ta wuce" Na danyi
murmushi "yesterday was suppose to be
our first night and I ruined it. I am sorry
yayi murmushi and I expected a hug a
even a kiss but he didn't do any. I kept
expecting physical touch from him amma
still shiru har ya gama cin abincin ya tashi
ya dauke ya dauke kayan gurin bai taba
ko da hannu na ba.

Da dare ya fita da kansa sai gashi ya
dawo da abinci yace inji Umma, ya zauna
ya gama cin kayansa kawai sai ya mike
"good night darling, zan kwanta da wurj"
yayi hamma "i am actually very
exhausted, gobe kuma I have an
appointment" ya sunkuyo yayi kissing
cheek dina sannan ya shiga kofar da nake tunanin dakin sane a gurin. Na ajiye waya
ta da take hannu na ina kallon kofar, lallai
ma wanna mutumin. He is definitely
planning something, amma me yake
shiryawa? Mutumin da tun da aka daura
auren nan baya iya cire dauke hannun sa
daga jikina in dai muna tare shine yanzu
zanyi kwana na biyu a gidan sa ba tare da
ko hannu na ya rike ba? Washegari ma ya sake fita da safe, Salima suka dawo tare da Yaya (kanin Mukhtar
mai sunan Daddy) suka kawo mana abinci, sannan ta kwashi kayan jiya ta tafi dasu tana ta sauri dan Yaya yace ba zai jira ta ba in dai ta dade tafiya zai yi ya bar
ta. Basu jima da tafiya ba nayi bakuwa,
the most unexpected bakuwa, Aunty Hajjo.

Akayi knocking a tashi daga kwanciyar
da nake akan kujera naie na bude half
expecting Salima ce ta dawo, dan da
Mukhtar ne yasan kofar a bude take
shigowa kawai zai yi, Ina budewa muka
hada ido, tayi murmushi ganin yadda
fuskata ta cika da mamakin ganin ta. A
rataye a gaban rigarta baby carrier ce, a cikin ta kuma akwai baby. Nayi iyakacin
kokarin hana kaina kallon babyn. Nayi
kokarin rungume ta sai ta jani ta gefe tace
"zaki matse bawan Allah yana baccin sa"
nayi dariya "sannu da zuwa Aunty, ya
akayi kika san gidan nan?" Tace
"Mommyn ki na kira ta bani address,
munzo gari ai tun last weekend, naso
shiga gidan ku ranar bikin ku but I didn't
want to go with Junior" sai kuma ta fara
kalle kalle "ke kadai ce dai ko?" Nayi
murmushi tare da bata hanya ta shigo
sosai "ni kadai ce" amma tana shigowa
sai na rufe kofar na kuma murda key dan
bana son Mukhtar yayi surprising dina yaji
wani abun da ba zan so yaji ba. Ta zauna
tare da ajiye katuwar baby bag din da
take hannun ta sai kuma ta kunce baby
carrier din ta sauko da shi ta kwantar
dashi a kan kujera. "Sarkin son jiki, yanzu
zaki ga ya tashi indai ya daina jin dumin
mutum a jikin sa" na bishi da kallo, yayi
girma sosai fiye da yadda na gani a hoto,
ba zaka taba tsammanin preterm aka
haife shi ba. And he looked more cute in
real, ya turo harshen sa waje yana tsotsa
kamar yadda yake yi ranar da na fara
ganinsa. Na dauke idona daga kan sa
sannan na gaishe ta. Ta amsa "ya taro?
An sha biki. Allah ya sanya alkhairi. Naso
zuwa ai to kuma Abdul yana busy shima ranar ballantana ya zauna min da Junior,
and I didn't want to go with him saboda
Sa'adatu" nayi shiru ban ce komai ba sai
tace "zaki yi mamaki in na ce miki people
actually believe cewa ni na haife shi" tavi
dariya "har gida ake zuwa yi min barka,
har da masu kawo min kayan barka" ta
dauko wani set din toys daga cikin jakar
gabanta tace "kinga wannan ma dazu
kafin in fito wata makociyar mu anan garin
ta shigo ta kawo masa, suna ta tsokanar
Abdul wai sai da zaiyi aure sannan aka yi
masa kan'" na sake yin shiru kaina a kasa
ina wasa da yatsun hannuna, ta cigaba
"amma na san Sa'adatu tana gain sa
zata gane shi. Kuma ban sani ba ko kun
gaya mata yana wajena. Tunda dai ta san
sanda ta baro ni babu ciki a tare da ni
kuma watannin sa wasu yi dai dai da
haihuwar ki. Za kuma ta ¡ya gane
kamanni" na sake kallon sa, he really
looked like a mixture of me and Daddy,
amma kuma in dai ba kana tunanin haka
ba zaka kawai kalle shi ka fadi haka ba, sai
dai in dama kana zargi. And I wondered if
Mukhtar will recognize him. Kamar amsar tambaya ta sai naji an buga kofa, na mike ina jin faduwar gaba na je na leka naga shine, amma kuma ai ba zai
kawo komai ba dan ya ganni da bakuwa mai jariri, right? Na bude kofar na bashi
hanya ya shigo "you locked the door? Ke
da waye?" And he saw Aunty Hajjo a
zaune. Nace "matar abokin Daddy ce" a
fuskarsa naga alamar bai san ta ba. Ya
gaishe ta ta amsa sai ya wuce zuwa dakin
sa. Ina zama tace min "me zaki zauna kiyi,
tashi ki bishi. Bara in hada wa yaron nan
madara naga yana kokarin tashi" ta dan
lakuce masa fuska "a cici" na wuce ta na
shiga inda Mukhtar ya shiga, wani dan
corridor ne da kofofi guda biyu, na bude
daya sai naga falo ne kuma yana da kofa
daga waje, na rufe na bude daya kofar sai
na ganshi a ciki yana kokarin cire rigarsa,
na tsaya a bakin kofar muna kallon juna, I
half expected him to put it back on amma
sai naga ya karasa cire wa yana kallo na
expression din sa unreadable. Ya ajiye ta
akan gado sannan ya fara kokarin cire
dogon wandon jikinsa, zuciya ta ta fara
dukan tara tara, ina jin toro dan ban tana
ganin babban namiji yana cire kaya a gaba
na kuma daga ni sai shi a daki ba, sannan
kuma there was anticipation of maybe
zan ga abinda nake nema, abinda nazo
gidan dan in gani. Ya cire wandon ya ajiye shi shima, ya zama daga shi sai singlet da gajeren wando.

Na fara bin jikin sa da kallo a hankali tun
daga kan kafadar sa zuwa rabin cinyoyin
sa da suke a waje zuwa kafafuwansa. Sai
da na kai kasa sannan na sake dawowa
sama. A lokacin muka hada ido and he
was smiling, na dauke kaina daga
fuskarsa na kalli gefe, yayi dariya "to ya?
Are you satisfied with abinda kika gani or
should I show you more" nayi gyaran
murya "yau ma ka sake fita da wuri baka
ci abinci ba, ina kaje?" Na fada a kokari na
na chanja topic din, ya fara tahowa inda
nake, sai naga ya kara yin girma, almost
scaring me amma na rike stance dina naki
motsawa har ya karaso inda nake "will you
like to see more?" Ya fada da
daskararriyar murya, na kalle shi cikin ido
nace "oh yes, I can't wait. But ina da
bakuwa a falo. So zany reserving show
din for another time" sai nayi sauri na
bude kofa zan fita sai ya saka hannu ya
mayar da ita ya rufe, na juyo muka sake
hada ido and the look in his eyes scared
me. "What if I said now, your bakuwa can
wait" nayi kokarin tura shi baya amma ko
motsi bai yi ba "no, she cannot wait, Sauri
take yi, tafiya zata y" yayi kokarin hada
bakin sa da nawa sai na zame ta kasan
hannunsa na koma cikin dakin,

Ya juyo yana kallona tare da jingina
bayansa da jikin kofar yana murmushi
"okay…..okay .. na yarda, let reserve the
show for another time. But, in kina son
fita daga dakin nan you have to kiss me
first, sai in baki hanya ki fita, I promise,
just a kiss shikenan" na girgiza kaina. I
planned on kissing him, on doing anything
to get to see what I want to see, but not
here, not in his room, not when he is 10x
stronger than me.

Wayata da take hannuna tayi kara number
din Mommy, nace ina kallon wayar
"kaga tana kira na, har ta gaji da jira, dama ta ce
min tafiya zata yi" sai kuma yayi ajjiyar
zuciya ya matsa daga bakin kofar ya koma
ya zauna a bakin gado "shikenan, you can
go. Babu dadi a bar bakuwa tana jira" na
wuce shi nayi hanyar fita, half expecting
zai tashi ya kama ni because the lost I
saw in his eyes ba kadan ba ce ba. And
something in my mind told me ba dan
bakuwa ya bar ni na fito ba. Ina komawa falo na tarar da ita har gama feeding dinsa ya saka shi a kafadar ta, na wuce kitchen na hado mata anything da
na san zata so na kawo mata, tayi min
godiya sannan tace "ba zama zanyi ba
ma, naga mijin ki ya dawo, But I was hoping zan bar miki shi a gurinki inje unguwa in dawo" ta fada tana murmushi, sai na fahimci ba wai dan zata je unguwar
ba ne ba tana so ne kawai ta bani dama
inga Junior sosai, amma sai naji bana son
hakan especially with Mukhtar a gidan.
Amma kuma ina so ....

Na girgiza kaina "I cannot do it, kar inje
inyi masa wani abu ba dai dai ba. I have
never been around babies. What if in na
dauke shi ya zame ya fadi? Ko in ya fara
kuka ya zanyi masa? Me zan bashi in yaji
yunwa?" Tayi murmushi ganin yadda duk
na rikice "you will do just fine. I want you
to be with him ko da for an hour ne or
two, yanzu zan dawo. Akwai wata friend
dina Zainab Aliyu, tun secondary school
muke tare da ita, kwanan baya tayi bikin
yayanta har guda biyu ban samu zuwa ba
shine yanzu xan leka inyi mata Allah ya
sanya alkhairi. Ba dadewa zanyi ba. Zan
kuma nuna miki yadda zaki yi komai" na
gyada kai ina jin excitement, I have never
been around babies kamar yadda na gaya
mata, tun ina five years aka haifi twins
dan haka ba zan iya tuna komai akan
jarirantakar su ba, daga kan su kuma
babu inda aka sake haihuwa a cikin
gidajen da nake zama, Gidan uncle
Ahmad ma Salim da Salima ne auta,
shekara daya kuma na basu,

Ta miko min shi, yadda zan dauke shima
sai da ta nuna min and he felt heavier
than I expected. Ya fara mutsu mutsu na
zaro ido "zai fadi, Aunty ki karbe shi zai
fadi" tayi dariya sosai amma sai naga na
gyara rikon sa da kaina ba tare da ta
gyara min ba. Sai ta nuna min yadda zan
hada masa madara idan ya ji yunwa da
kuma lokacin da ya kamata ace aji
yunwar.

Ta nuna mun yadda zanyi wearing baby
carrier din ajikina in kuma saka shi a ciki
idan zaiyi bacci, ta nuna min yadda zan
chanja masa diaper da kuma favorite toy
din sa.

Tana tafiya na kwashe shi da kayan sa na
tafi da shi guest's room dina. Na rufe kofa
sannan na kwantar da shi a kan gadon
dakin ina kallon sa, ya kura min ido yana
kallona, maybe yaga fuskar da bai sani
ba. Na shafa hancinsa da dan yatsa na
nace "hey you, how have you been?" Sai
kawai naga ya kai wa yatsan na wa
wawura, ya kama shi da hannu biyu
sannan ya ja shi zuwa bakin sa ya kama
tsotsa yana kallona, na bude ido "da
gaske ne kenan abinda ake gaya min akan
ka? Da gaske ne kenan kai acici ne" sai
kuma na fara jin tsoro, what if hannun
nawa akwai germs a jiki, what if ya dauki
cuta a jikin hannun nawa. Nayi kokarin
zare dan yatsa na daga bakin sa da
hannun sa but he held it tighter da karfin
da ban dauka yana da irin sa ba. Nace
"hey, me aunty Hajjo taje baka ne kake da
karfi haka. Give me back my finger" ban
ankara ba sai ji nayi ya gatsa min cizo,
nayi sauri na zare hannuna pretending
kamar naji zafi "me nayi maka? Never bit
the hand that feeds you" sai naga yayi
dariya, dariya da bakin da babu hakori ko
daya and I smiled, thanking Aunty Hajjo
for giving me this moment.

Anan muka yi bacci tare ni da shi. Ina
tashi naji Mukhtar ya sake fita. Na dauko
waya ta nayi order abinci online sannan
naje nayi sallah kafin in idar har ya tashi
ya fara rigima, a rikice na hada masa
madara na bashi sannan na chanja masa
diaper da kaya, I then took some pictures
of him, of him and me and then my heart
breaks sanda naji sallamar aunty Hajjo. I
cursed the man da ya saka ba zan zauna
da da na ba. I cursed my society

Kafin su tafi mukayi maganar bikin Abdul,
ta sake tambaya ta "kin gaya wa Sa'adatu
maganar yaron nan?" Na girgiza kai, har yau na kasa gayawa Mommy saboda ina
son Junior sosai and I planned on
protecting him with everything in me, ita
kuma Mommy har yanzu ban san
matsayin da zan ajiye ta ba. A karshe sai
nayi deciding in barwa destiny tayi
deciding for me. Nace mata "ban gaya
mata inda yake ba, don't tell her, amma in
ta gano da kanta shikenan".

Abinda ya faru da rana ya saka nayi
tunanin something will happened tsakani
na da Mukhtar da dare but it did not. Ya
dawo gida da dare har da balangun sa
cike a leda ya zauna ya baje a falo yana
tayi min hirar friends dinsa and how they
reacted to him getting married babu
dinner. Ya gama ya tashi ya karkade
rigarsa yace "good night dearest, kiyi
bacci mai dadi" na mike tsaye ina jin raina
yana baci, bana son sake spending
another night breathing under the same
roof with him, nace "what about the
show? You promised me a show tonight"
yay murmushi "don't worry sweetheart,
zaki samu show dinki but not tonight, da
mace miki nayi another time, bance miki
tonight ba" na matsa kusa da shi tare da
saka hannu ina kokarin balle buttons din
rigarsa, "why not? What are you waiting
for?" Ya ture hannuna '"'I promised to take
care of you didn't I? And yanzu baki da lafiya, your stitches are still raw and you are not emotionally ready for this" na kama hannun sa na fara kokarin jan sa ta
karfi "but I am ready, I am more than
ready. Kazo muje dakina and I will show
you how ready I am" ja daya yayi ya zare
hannun sa daga cikin nawa still yana
murmushi yace "good night sweetheart",

Washegari na sake yin wata bakuwar,
Mommy, tazo zata yi min sallama zasu
koma Kano. Tayi ta tambaya ta ko ina da
problem ko kuma da akwai abinda nake
so, "you look drained....... Kamar ba
amarya ba. Kina samu kiyi bacci kuwa
sosai ki huta? Kina cin abinci ki koshi?"
Nayi dariya, tayi ajjiyar zuciya "to ni dai
aurar da yaya bai karbe ni ba. Ni dai na
san in akayi aure a zamanin mu daga
amaryar har angon kana ganin zu zaka
gane, har kyalli zaka ga suna yi saboda
samun nutsuwar zuciya, amma ke ji bi
idonki yadda yayi rami, ita kuma waccan
gata can kamar na bawa mayu ajjiyar ta
suna lasar ta kullum" sai ta yi shiru, and I
knew I was into trouble dan nasan labarin
Safina zata bani, na fara tunanin abinda
zan fada in chanja topic amma kafin in fada already ta

fara "ko da yake na gane lafiya ce bata da
ita kwana biyu, ga mijin baya nan. Nace
taje asibiti kuma taki zuwa. Ina tunanin
kamar ciki ne da ita. Na dai tura mata Dr
Abbas ya duba ta, nace yayi mata pt,
tunda su ba zasu kula min da yar ba ni
zan kula da abata" nayi shiru yayin da ni
kuma na rufe ido na, trying so hard not to
think about maganar da take yi, ta cigaba
"na daukar mata dai yan aiki biyu su
sannan na dauko mata wata yar uwarta
daga Katsina ta taya ta zama, at least ta
ringa samun wadda zata ke magana da
ita. Yanzu kawai damuwata rashin mota
da bata da ita, ga motocinsa nan a gidan
ya ajiye amma wai bai bar mata key din ko
daya ba, shine nace. ." Na juyo tana
kalion na, and 1 already know abinda zata
tambaya sai dai yanayin fuskata kadai ya
tabbatar mata ba zanyi abinda take so din
ba. Ta chanja layi "shikenan kawai. Zan
bata tawa motar ni ai ba zan rasa motar
hawa ba" still bance komai ba sai kuma ta
sake cewa "yauwa Safiyya, nay magana
da Safina kema kuma yanzu zanyi
magana da ke. Na rasa me yake damun
ku. You two don't act like sisters, farko
nasan it was because of what happened
to you, you grew distant from every one,
amma yanzu na ga kamar kin dawo dai
dai, kamar kin shirya da kowa amma
banda Safina why?" Nace "babu komai Mommy, kawai dai dan bama tare ne"
tace "to ai yanzu kuna tare, ga ku Allah ya
kawo ku aure gari daya, ku daure kuyi
zumunci dan Allah. Be each other's
keepers. Ku ringa haka wa kuna binne wa
tare, duk wacce take da problem ku hadu
ku samo solution ba tare da mu iyayen ku
mun sani ba ma. I want you to be kamar
yadida muke ni da Safiya in our days. Kinji
Safiyya?" Na gyada kai "okay Mommy" ta
sake cewa "a gaya mata next weekend
tazo nan ku wuni tare, in kin samu dama
ke ma sai ki je ki wunar mata" na sake
amsa mata.

Ranar da dare na shirya yin abinda banyi
niyyar yi ba a da. Sai da na tabbatar da
komai nawa yana in place sannan na
shirya with only a pant and bra na dora
rigar da take da ita da babu duk daya na
zauna jiran Mukhtar. Bai dawo ba sai dare
sosai, Ina jin shigowar sa na tashi na bude
kofar dakin da nake ciki na tsaya a bakin
kofa. Ya bude kofa sannan ya rufe, na lura
a hankali yake yi a tunaninsa nayi bacci.
Yana juyo wa muka hada ido and he
dropped his car keys ya saki baki yana
kallona, Na gyara tsayuwata feeling very
awkward nace "come to bed, husband".

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Forty One: "Goodbye
Husband"


Al'ummar jihar Jigawa da kewayenta har
ma da jihohin kusa . Haifa foods and
pastries ta zo muku da kayan maqulashe
kala kala irin su yogo fura wanda babu
kamar sa ga dadi ga qoshi ga gardin shi
badaganan©️ wani abun saima ka
dandana. Ga irin su milk cake (sunan
wani abu wai farfesun madara) wanda
babu kamar shi ga sauqi ga dadi,
cocunut milk wanda har getare babu
kamar shi da kuma uwa uba Yogo fruits
wanda ze gara muku Ify. Zaku sami kayan
HAIFA har kofan gidajenku in kuna so ga
komai na HAIFA a farashi mai sauki yake
ku garzaya ku dandana kayan dadin Haifa 0812 536 8737 https://www.instagram.com haifa_foods_and_pastries iigsh=NHYyN2k1eTlhenBt&utm_ source=gr

*. *. *. *.

Ina kallon sanda ya hadiye wani mugun
yawu sannan ya fara girgiza kansa, "What
are you doing Fiyya. Na gaya miki baki da
lafiya. I don't want to hurt you" na fara cat
walking zuwa inda yake tsaye "really?
Even if that's the case then we will be
careful. I know you will not hurt me. I trust
you" na tsaya half way from him, studying
yadda yake bina da kallon, yadda
idanunsa suke juyewa, and I hated myself
for doing that. But I have already started
dan haka sai na karasa.

Na saka hannu na sauke kafadar rigar
jikina guda daya, it slid down my arms and
exposed more of my skin, he started
taking steps toward me and I gave him a
look da nake tunanin is seductive and
turned around, signalling him with my
hand to follow me sannan cikin tafiyar da
na tabbatar ba zai iya resisting ba na
koma dakin da na fito daga ciki.

Ina shiga na kalli gadon da sauri making
sure cewa the handcuffs I kept locked at
each side of the bed suna nan but
completely hidden sai dai in kasan da
zaman su, na san cewa wasa nake da
wuta kuma probability is very high that
wutar zata kona ni but I was ready to get
burnt in dai zan samu abinda nake
bukata, Sai dai kuma zuciya ta da gangar
jiki na cike suke da tsoro, kayan ciki na har karkarwa suke yi.

Naji shigowar sa nayi sauri na juya dan
bana so in dauke ido na daga gare shi
even for a second. Ya tsaya a bakin kofa
yana cigaba da kallo na, and akwai wani
murmushi da na kasa fahimta a lips din
shi. Ya karasa shigowa "you are seducing
me" ya fada directly, but daga muryarsa
na san I got him right where I wanted him.
Nayi kokarin yin magana but abinda kawai
yake kwakwalwa ta was that night, the
pain, the darkness, the fear, the........
"Are you sure you know what you are getting
yourself into?" Ya sake fada, bitting his
lips. Nayi taku biyu zuwa gareshi "is it a
crime idan mata tayi seducing mijinta? I
am not made of stone and I have a
husband. Besides, you promised me a
show ranar nan, I want to see the
complete show".

Ya karaso gaba na, looking down at me
"you want a show? You really want a
show? You will have a show" ya fada
muryar sa a cikin kirjin sa sannan ya dora
hannayensa akan kafaduna tare da
kokarin jawo ni closer to him at the same
time trying to kiss me. All | wanted a
lokacin was to scream on top of my voice,
to scream out all my anger and hatred for
him, to stab him in one place or two, amma instead sai na zame daga gare shi na koma kan gado na zauna, close to the spot da na makala one of my handcuffs.

Ya juyo yana kallo na, sai kuma ya tafi
gurin light switch ya dora hannunsa akai
da niyya kashewa. Na mike da sauri,
"Please, no, I hate the dark. It scares me"
and I meant that har cikin raina. Ya juyo
yana kallona and I saw him shakes his
head sannan yace "no!" Na kara matsowa
"please leave the light on" sai ya matsa
daga kusa da ni ya sake cewa "no" na
tsaya kawai ina kallon sa, na fahimci
guduwa yake shirin sake yi ya juya min
baya da sauri trying to stop looking at me
"no, you are sick, and we shouldn't do
this sai kin warke" yana gama fadar haka
yayi hanyar fita da sauri. Na bishi nima da sauri na kama hannun sa da hannu daya sannan na juyo da fuskar sa da daya hannun "i am not sick, come,
will show you that I am fine" and then he
smiled at me, a smile that confirmed all
my suspicious "not tonight, sweetheart"
sannan ya juya ya fita.

Na koma da baya har sai da kafafuwa na
suka ta ba gadon dakin sannan na zauna akan sa. Yanzu shikenan? I have belittled
myself for nothing?

Amma kuma sai naji wani relief a wani
bangaren zuciya ta, I wasn't sure my plan
A will work and wannan abinda ya faru ya
tabbatar min da cewa plan A is off.

Dama na shirya plan A din ne saboda
akwai remnants of shakku a zuciya ta na
cewa shi ya aikata min wancan laifin. Bana
son in dauki alhakin sa idan shi innocent
ne and I risked everything to avoid that.
Amma yanzu, the way he rejected me
bayan na san babu abinda yake so irin to
have me, ya tabbatar min da cewa shi din
dai shine.

Ba fariya ba, yadda Allah ya tsara jikina,
dan ma dai har yanzu ban dawo yadda
nake ba, ba Mukhtar da ya jima yana
lusting for me ba, bana jin akwai namijin
da zan bude masa jikina kamar yadda na
bude wa Mukhtar yau, sannan mu shiga
daki daga ni sai shi, sannan ga igiyar aure
uku a tsakanin mu, kuma ace yayi
rejecting dina yayi tafiyarsa.

Wannan ya kara tabbatar min da abu uku,
na farko Mukhtar ne yayi raping dina, na
biyu kuma ya san ina zargin shi, na uku
and the most important thing shine the
scar is there,

A yadda na bashi labarin daren da akayi
raping dina in details ya tabbatar masa da
cewa ina cikin hayyacina sanda na ji masa
ciwo, and the way that I tried seducing
him tonight bayan halin ko in kula da nake
nuna masa kafin in tare ya tabbatar masa
da cewa shaida nake nema a kansa, kuma
wannan scar din ita ce shaida. Wannan
realization din kuma sai yay unblocking
another fear in me, he will now try to get
rid of the scar ta kowanne hali. Tunda a
ganin sa ita kadai ce shaidar da zata
tabbatar min da kuma duniya cewa shine.
Musamman tunda yana tunanin Junior ya
mutu. And that was where I had upper
hands in the matter, na kuma gode Allah
da yasa nayi wancan tunanin dan in da
yasan Junior yana raye kuma ya san ina
zargin sa zai iya kokarin ma kawar da ni
daga duniya to cover his crime.

Wannan daren shine ya kawo karshen
plan A dina. My plan A was to seduce him
to my bed, handcuff both his hands idan
na dauke masa hankali da jikina, and then
check his body for the scars. It was risky
but worth a trial considering bani da
tabbas din shine dan haka bana son cutar
da shi.

Yanzu kuma it is going to be an eye for an
eye. Dan yanzu zamu shiga plan B.

Sai dai kuma daga alama shima Mukhtar
ya chanja takunsa gabaki daya. Dan ganin
shi ma daga ranar gagara ta yayi. Da
asuba yake fita, sai cikin dare kuma yake
dawowa, wani lokacin ma in ya tashi
dawowa ta can daya kofar falonsa yake
shiga zuwa dakinsa sannan in zai fita ma
ya fita ta can. Mun koma kamar mage da
bera a cikin gidan auren mu. And that
frustrate me more than anything.
Kamar yadda nayi alkawari ba zan yi girki
a gidan Mukhtar ba, ban taba dafa ko da
noddles ba, order abinci nake yi kuma a
kawo min har gida. Shima kuma bai taba
tambaya ta abinci ba, ban san kuma inda
yake zuwa ya ci ba. And I didn't care. Bai
taba kawo abokansa gidan ba, nima kuma
ban gayyaci kawayena ba duk kuwa da
korafin da suka ringa yi min a waya cewa
anyi bikina amma ban gayyace su ba
kuma gidan nawa ma ban gayyace su ba, I
told them suyi hakuri abin ne yazo min
lokaci daya amma na yi musu alkawarin
shirya musu walima wata rana. Amma na
fada musu hakan ne dan su rabu da ni inyi
concentrating akan abinda yake gaba na.
Sati biyu da biki na aka yi na Abdul. Tun
kafin bikin na kira shi a waya nayi masa murna tare da lallaba shi da kyar ya turo min account details dinsa and I sent him heavy da sai da uncle Sufyan da kansa ya kira Daddy and Daddy said babu ruwansa
ni nayi niyya kuma tsakanin mu da Abdul
ne. Lokacin bikin Abdul Mommy tazo gari,
dama munyi waya da ita tace min in shirya
zata zo muje gidan bikin tare ni da ita da
Safina, and I wasn't looking forward to
that. Nayi ta neman hanyar da zan zame
in fasa zuwa na rasa kuma gashi ina son
zuwa din ko dan Aunty Hajjo, na san zata
ji dadi sosai idan naje. But I was in no
mood to neither meet nor talk to Safina.

Sai dai cikin ikon Allah ranar da Mommy ta
zo gari take gaya min Safina ba zata samu
damar zuwa ba, bata da lafiya,
"gashi shi kuma mijin nata har yanzu bai dawo ba,
ina tunanin da ita zan koma Kano gaskiya,
gwara in san a gabana take, ko kuma in je
gidan iyayen nasa inji me zasu ce, amma
wannan ai ba aure ba ne ba" ban ce
komai ba kuma banyi niyyar cewa komai
ba, sai kuma tace "ya kamata dai kije ki
duba ta" nace "insha Allah". Amma sai
naji dadin cewa ba zan hadu da Safina ba,

Ranar yini Mommy tazo ta dauke ni muka
je tare. I kept thinking ko zamu ga Junior?
Ko zata gane shi? Amma da yake a event
center akayi bikin I guess Aunty Hajjo
bata tafi da shi ba dan duk baza ido na
ban ganshi ba. Washegari da dare muka
sake zuwa dinner. Aunty Hajjo taji dadin
ganin mu sosai kuma ta karrama mu
sosai, naje har gurin ango da amarya na
taya su murna and they looked so happy
and so in love with each other. Abdul yayi
introducing dina a grin amaryarsa muka
gaisa sosai, yana tsokana ta wai ina ango
na. Sai ganin su naji ya fama min wani
ciwo a zuciya ta da nake ta ajjiye da shi,
and as I sat down looking at them I
thought about him, ko ina yake? Ko me
yake ciki? And I so much wanted to
unblock his phone number and call him,
maybe inyi pretending kamar babu abinda
ya faru and say '"tsokanar ka fa nake yi
Yaya Muhammad. It was all a prank. I miss
you so much", I remembered the sound of
his voice over the phone, the deepness of
it and how it has always reach deep into
my heart "hey Piya, you have no idea how
much I miss you" na sunkuyar da ido na
kasa ina jin hawaye yana taruwa a idona, a
hankali nace "I miss you too Yaya
Muhammad".

A lokacin ne naji Mommy tana taba ni
"Kinga mother in law din Safina, Ashe ta san su Sufyan" nayi sauri na dago kai and
I saw her tana tafiya zata zauna. Ban taba
ganin ta ba amma na tabbatar ko da kuwa
Mommy bata nuna min ita ba zan iya gane
ta idan na ganta. Kana ganin ta indai
kasan Muhammad to zaka san cewa ita ta
haife shi.

Mommy ta ja hannuna "zo muje ku gaisa
da ita" na zame hannu na tare da
langwabe kai "Mommy please" tace "ke
fa matsalar ki kenan ba kya son mutane,
ai sai kiyi ta zama" ta tafi ta barni. Nayi
ajiyar zuciya na cigaba da kallon Mama
da ga nesa, naki zuwa ne saboda ina jin
toro, ban sani ba ko ta taba ganin hotona
a wayar Muhammad ko something like
that, ina tsoron kar ta gane ni, duk da dai
na san karin maganar hausawa da suke
cewa idan kere na yawo zabo na yawo
watarana dole za'a hadu.

Wasa wasa dai sai naga Mommy ta samu
kujera a can ta zauna sun cigaba da hira.
Ni dai ina zaune a guri daya har aka gama
sannan Mommy ta zo muka tafi. Tun kafin
mu fita na san cewa I was in for hirar
Safina da mijinta har muje gida, ai kuwa
dai muna shiga mota ta fara "mutanen
nan suna da son kansu wallahi, kinji wai
basu san Safina babu lafiya ba, wai bata
gaya musu ba shima bai gaya musu ba,
Amma dai munyi magana tace zata je gidan ta dauke ta ta mayar da ita can
gabanta su zauna tare kafin mijin ya
dawo. Ai ce mata kawai nayi tafiya zanyi
da Safina Kano inyi jinyar ta a can" naji
kamar in toshe kunnena irin yadda nake
mata in bana son jin maganar da take yi
sai kuma na fasa, tunda na mayar da
zargina kan Mukhtar a fara sassautowa
akan Mommy. Sai kuma tayi ajjiyar zuciya
tace "ni tausayi take bani yarinyar nan,
Allah ya sassauta mata wanna lamarin.
Ko babu komai iyayensa masu kirki ne".
Ranar daurin aure ma muka sake komawa
gidan Aunty Hajjo, ranar ni na fara fita a
motata naje na dauki Mommy sannan
muka wuce, muna yin packing na dauko
envelope din dana taho da ita da kudi
masu kauri a ciki na mika wa mommy
nace "gashi Mommy ko zaki bawa Aunty
gudummawa" ai kam taji dadin haka sosai
"kai amma kin kyauta Safiyya, dama ina ta tunanin abinda zan bata na rasa" nayi
murmushi kawai na fita.

Ranar babu mutane sosai tunda daurin
aure ne, sai yan uwansu na jiki sai kuma
few close friends kamar mu. Muka zauna a falo Mommy ta samu wata yar uwar
Aunty Hajjo itama mai surutu suna ta
zance ni kuma na koma gefe ina ta rubuta
wani sabon plan da nake shiryawa akan
maganar reopening Oasis da nake son yi
as soon as I get rid of Mukhtar.

Muna nan sai ga wata yarinya ta shigo
falon da Junior a hannunta, tazo ta zauna
opposite din su mommy ta na bashi
madara shi kuma yana ta rigima yaki sha
sai dawo da ita yake yi. Na ajiye waya ta
akan cinyata ina kallon su. Kanwar Aunty
Hajjo ta juya gurin su itama tace "ke
Husna yaron nan fa ya koshi, daga alama
bacci yake ji ki goya shi mana" wadda aka
kira da Husna ta kwabe fuska kamar zata
yi kuka tace "na goya shin fa yaki yin
baccin wallahi. Wannan yaron rigimamme
ne" Mommy ta juya tana kallon su ita ma
sai tace "ki kaiwa maman sa shi mana to,
maybe goyon ne baki iya ba" yarinyar
tace "to ai maman tana gurin mutane, ita
tace in rike shi" Mommy ta mika mata
hannu "bani shi in gani, watakila diaper
za'a chanja masa ko kuma kaya ne suka yi
masa yawa" yarinyar ta zo ta mika mata
shi ta karbe shi and she laughed and said
"wow, ina karbar yaron nan sai naga
kamar twins sanda suna babies" ta sake
jujjuya shi a hannunta and she looked at
me, muna hada ido na sunkuyar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna, ta sake
kallon sa ta kalle ni a take na fahimci ta
gane shi.

Ta juya tana kallon yarinyar tace "dan
waye?" kanwar Aunty Hajjo da suke tare
tace "au wai kema baki san ta haihu ba?
Dan Hajjo ne fa. Matar nan babu wanda ta
gayawa tana da ciki kawai sai kiran mu
tayi tace ta haihu. Kin san in aka girman
nan in Allah ya kawo rabo sai kiga ana jin
kunyar fada ana gain kamar abin kunya
ne" Mommy ta mika wa matar shi tace
"haka ne. Allah ya raya shi", Matar tace
ameen sannan ta tashi ta jefa shi sama ta
chafe shi, naji kamar zuciyata zata fado
kasa, shi kuma ya takarkare ya chanyara
kuka, sai kuma ta rungume shi a kirjinta
tana dariya sai tace "yaron nan ajebo ne,
bai san cika masaki ba. Bara inje in yi
masa wanka in goya shi, bacci yake j"
tana tafiya Mommy ta juyo tana cigaba da
kallona, fuskarta na nuna alamun bacin
rai. Sai kuma ta mike tayi hanyar waje
tana cewa da sauran mutanen gurin "na
tafi. Allah ya bamu alkhairi, idan Hajjo ta
shigo kuce mata na tafi" na mike nima da
sauri na dauki jakata da waya ta nabi
bayanta.

A hanyar fita muka hadu da Aunty Hajjo
tana shigowa cikin gidan, ta yiwa Mommy
magana amma Mommy ko kallon ta bata
yi ba, muka kalli juna ni da ita and she
understood what happened sai ta bi mu a
baya "Sa'adatu naga sako na gode Allah
ya bar zumunci, Allah kuma ya huta
gajiya, sai munyi waya insha Allah" stil
bata ce mata komai ba ta shiga mota, na
russuna nace "Aunty mun tafi Allah ya
sanya alkhairi" sannan nima na zagaya
drivers seat na zauna na tayar da motar
muka fita fully knowing that mai raba
Mommy da ni ranar sai Allah. Amma sai
naji tayi shiru bata ce komai ba. Fuskarta
cike da bacin rai. Sai naji babu dadi, na
saba da in nayi mata laifi zata yi ta min
fada ne ba wai tayi fushi da ni ba.

Har muka je gida bata ce min komai ba,
nayi packing sannan na juyo ina kallonta
nace "Mommy am sorry" ta juyo tana
kallona tace "no, don't be. Ba laifinki bane
ba ai. Laifi na ne" sannan ta bude motar
ta fita. I thought about following her
inside in sake bata hakuri but sai na
chanja shawara na juya mota na fita, dan
bana cikin mood din bata hakuri ina
tsoron kar in sake kwafsawa again.
Washegari ta koma Kano gurin Daddy, A haka ranaku suka cigaba da wucewa,
satittuka suka shude, har aka yi six weeks
da bikin mu da Mukhtar amma ya ki bani
damar aiwatar da plan B dina a kansa.
And for my plan B ina bukatar getting
close to him. Akwai ranar da nayi niyyar
zuwa dakinsa ma cikin dare in ritsa shi
yana bacci amma sai na tarar ashe kofar
dakin ma rufe ta yake yi. Wato bashi da
niyyar taking any chance with me. Ya kan shigo gurina kusan kullum da assuba, ko da safe idan bai fita da assuba ba, amma a bakin kofar dakina yake
tsayawa "good morning sweetheart. Hope
babu abinda yake damun ki. Aiki ya matsa
min a office ki dan kara yi min hakuri,
soon everything will be over kinji? I will
soon plan us a vacation"

Ko da wasa baya shigo wa cikin dakin,
and da ga na taso zuwa gurinsa zai juya
ya fita. He never let me gets two meters
close to him. Abinda na fahimta bayan
rashin gaskiyar sa shine muguwar
sha'awa na damunsa, and he chose to
avoid me akan yay letting his guard
down. I knew he was trying to get rid of
the scar and duk ranar da ya samu yayi
hakan he will come for me. Wannan kuma shine abinda yake keeping me up wide awake at night.

A cikin six weeks din abubuwa da yawa
sun faru. Har lokacin Mommy fushi take yi
da ni, dan in ba ni na kira ta a waya ba ta
daina kira na. Daddy kuma ya matsa min
lallai in koma bakin aikina, na fahimci he
was worried about me and the way da
yake jin sound of my voice a cikin waya
yana ganin in na koma aikin it will keep my
spirit up, gani yake kamar zaman bana yin
komai ne ya jawo nake cikin damuwa. Na
ce masa ya dan kara hakuri kadan na kusa
komawa, but he didn't believe me sai
gashi ya turo uncle Ahmad har gida wai
yazo yayi min magana in cigaba da
abubuwan da na fara a office. Na gaya
masa shima soon zan dawo, akwai abinda
nake jira ne.

Sai da ya tashi tafiya sannan yace
"Safiyya wannan gidan naku yayi muku
kadan. Ya kamata ku samu babba ku siya
ku koma tunda in kika koma bakin aikin ki
ai mutane zasu ke zuwa gurinki, manyan
mutane, this house shouldn't be
presented as yours" nayi mamakin
maganar sa amma sai nace masa "okay
babu komai. Za'a sayi wani insha Allah" ya yi murmushi '"a fara duba muku?" Na
girgiza kaina "later.…. In lokacin siyan yayi i
will talk to you".

And then one fateful day, ina zaune akan
sallaya ta da daddare na gama shafa"I da
wutiri ina adduoina naji shigowar motar
Mukhtar, ban wani mai da hankali akan
hakan ba dan nasan ba lallai ne ma ya
shigo ta nan falon ba, amma ga mamaki
na kawai sai ji nayi an bude kofar dakin da
nake ciki, na dan tsorata kadan dan ban
saka ran shigowar sa ba, nayi sauri na
shafa adduar na juyo na ganshi a tsaye a
bakin kofa, ya rungume hannayensa a
kirjinsa with that smile that I now so much
understand a fuskarsa.

Naji kirjina ya buga da karfi, tsoro ya
kamani but I tried as much as I can to
keep my face neutral, nace "you scared
me, me kake yi anan kuma yau?" ya gyara
tsayuwarsa "hello sweetheart, sorry na
baki tsoro, laifi ne dan miji ya shigo dakin
matar sa da dare?" na fara dauke kayan
sallata nace "au dama ni matar ka ce, ai ni
har na manta ma. Thank you for
reminding me" yayi dariya tare da karaso
wa cikin dakin "kiyi hakuri, I know I
haven't been a good husband, but believe me things are going to change a gidan
nan from today" na jawo drawer,
pretending kamar sallaya nake sakawa a
ciki, na dauko abinda zan dauka a ciki na
boye a cikin hijab dina na juyo tare da
bata rai nace "ka riga kayi wasa da
damarka ai Mukhtar, I gave you a golden
opportunity ka debi kasa ka watsa min a
fuska, yanzu mun riga mun wuce wannan
stage din" na fada meaning every word of
what I said. Ya fara tahowa zuwa inda
nake "na san nayi ba dai dai ba, and
believe me it hurt me more than it did
you, why do you think na daina zama a
gida? It was because I couldn't get that
site out of my head, it drove me crazy, it
is still driving me crazy. Bana son in
hurting dinki, especially after what you
went through shi yasa na baki chance dan
ki warke sosai. But get ready" ya fada
smirking "because I am ready".

Na yi getting ready din kuwa exactly like
he said, but not in the way he meant, and
I watched him come closer har yazo
gabana ya tsaya idonsa yana bin jikina da
kallo duk kuwa da cewa still akwai hijab a
jikin nawa, ya tsaya so close har ina iya jin
saukar numfashinsa a fuskata yace "I have dreamt about this night Safiyya, fiye
da adadin da zan iya lissafawa, I have
planned for this night Fiyya more times
than I can remember, for years na yi
dakon soyayyar ki a raina mai tarin yawan da ban san adadin ta ba. And tonight, finally, burina zai cika, I
am finally going to make you mine, tawa
ni kadai, har abada".

Na mayar masa da murmushinsa, sannan
nace "I also have been planning for this
night Mukhtar, amma not for years but for
weeks"
And then just as I said that, allurar da
nake rike da ita a cikin hijab dina ta huda
hijab din nawa, ta huda kayansa, ta huda
tsokar cinyarsa sannan na juye masa
abinda yake cikin syringe din a jikin sa.

It happened in seconds, and it was done
before he realize what was happening.
The next second na matsa da sauri away
from him nayi hanyar bakin kofa na tsaya
ina kallonsa, ready to run dan jininsa yafi
karfin allurar,

Ya juyo yana kallona hannunsa rike da
cinyarsa, fuskarsa cike da mamaki " Safiyya!" ya ambata idanunsa suna juyewa,
"What have you done?" yayi taku
biyu zuwa inda nake yana miko hannunsa
gare ni, sannan yayi taku daya baya, na
dawo cikin dakin na karasa gaban shi na
tsaya daf dashi sannan nace "| am giving
you the taste of your own medicine" sai
kuma na saka hannayena biyu da karfi na
tura shi ya fada kan gadon da baya, and
he lost consciousness a lokacin.

My thought was drugging Mukhtar will be
the hardest part of plan B, amma sai
bayan da na same shi unconscious akan
gado na sannan na fahimci it was the
easiest. My plan was to use my handcuffs
in daure hannayensa a both sides of the
bed and then strip him naked in duba
abinda nake nema. Zan daure
hannayensa ne saboda ban san karfin
jinin sa ba ina tsoron kar ya tashi kafin in
gama abinda nake yi.

Amma sai lokacin na fahimci cewa karfi na
bai fi cikin cokali ba, ba karamar wahala
na sha ba kafin in jashi zuwa position din
da zai bani damar dare hannayensa duk
biyun. Kuma nayi hakan ne cike da tsoro
ina gain zai iya farkawa anytime. Bayan
na gama sai da na tabbatar handcuffs din
sunyi locking hannayensa completely
sannan na zauna na huta na sha ruwa sai na fara next task dina na checking his body for the scar, target dina dama shine bayan sa da cinyoyin sa, sai kuma a
lokacin na fahimci cewa ba zan iya cire
masa rigar ba saboda yadda hannayen sa
suke daure, so I got a razor blade and cut
it, na yanke ta daga jikin sa sannan na
yanke singlet din ciki, and it took me a
whole lot of another energy to roll him to
his side dan in samu ganin bayan.

1 already had a mental picture of yadda
marks din zasu zama, zasu zama size din
tsinin fork guda hudu a jere, distance din
tsakanin su kuma zai zama even. I
checked, bayan fitilar dakin da kuma
bedside lamp da na kunna har sai da na
kara da fitilar waya ta but banga komai
makaman in hakan ba.

Wannan ya saka na koma next gurin da
nake suspecting, cinyoyin sa, na zare
wandon jikinsa na barshi da gajeren, I
wasn't looking forward to cire masa
gajeren wando for my own mental health,
but at the end I had to cut them too, na
yanka sides dinsu but leaving the rim and
the middle covered dan bana san ganin
abinda zai kara min trauma akan wacce
nake facing already.

Amma babu marks babu alamun su. And
then just as I was about to give up I saw
something, a scar, a can saman cinyarsa
ta hagu kusa da hip bone dinsa, amma
kuma wannan sabon tabo ne and it looks
nothing like tabon fork. It looks like an
yanke a gurin deep yanka wanda har sai
da aka yi dinki a gurin. Na sake haska fitila
ta sosai sai naga tsahon yankan dai dai
fadin yatsun fork ne. It looked new, bana
jin zaiyi wata biyu.

A lokacin ne na tuna cewa da hannun
dama na ji masa ciwon, meaning tabon
should be a bangaren hagun sa.

Sai na fahimci abinda ya faru, na ja da
baya na zauna akan side drawer ina kallon
sa cikin bacin rai. Tabbas shine. And that
tabon stitches da na gani shine dai dai
gurin da ya kamata ace naga tabon fork,
but bayan na kwafsa ranar da aka kawo ni
na nuna masa alamar cewa ina zarginsa,
he got rid of the original scar by creating
another one a dai dai inda waccan take.
He cut himself. He cut himself deeply and
took himself to hospital yayi musu wata
karyar suka yi masa dinki a gurin. Wannan ya sa ya ja baya da ni, giving himself time to heal, giving the new scar time to form and cover the old one.

And that got me furious, really furious
that karfin addu'a he kawai ya rike ni ya
hanani hallaka Mukhtar a cikin daren nan.
Plan B ya kare. My plan B was to get
Mukhtar close and drug him ya zama
unconscious, in daure shi yadda ba zai
farka yayi harming dina ba, and check for
the scar. In na gani kuma in hada kaya na
inyi gidan mu and then sue him for rape.

Sai dai wannan discovery din ya tabbatar
min da cewa to get justice from him dole
sai na shiga plan C and I wasn't looking
forward to it, duk wannan wahalar da
nasha da risking rayuwata was to avoid
the plan C. Bana son in shigar da Junior
cikin maganar, idan da zan samu yadda
nake so, bana son ko sau daya Mukhtar
ya dora idonsa akan sa. But now he must
come in to get justice for the two of us.

Har lokacin Mukhtar bai tashi ba, ya
kamata ace hankali na ya tashi amma bai
tashi ba, sanda ina neman drug din I
asked for mai matsakaicin karfi with low
risk dan bana son jininsa a hannuna duk
kuwa da cewa chances are higher na
cewa jinin sa zai fi karfin maganin but it
now seems like jinin na sa bashi da karfi.
While waiting sai na dauko red permanent marker din da na ke ajiye da ita a cikin
jaka ta na koma kan gadon nayi masa
rubutu manya akan goshinsa "RAPIST"
sannan na sauko.

Na dauko karamar akwati ta da hada duk
abubuwan da na san ina bukata, dama
kayan sawa kusan duk wadanda suke
dakina a Abuja ban dauko ko set daya ba
suna can, akwatinan lefe na kuwa har
yanzu ko buda su banyi ba. Na ajiye
akwatin a gefe na jawo kujera na zauna na
saka Mukhtar a gaba ina jiran ya tashi. Sai
da sanyin asuba ya fara kadawa sannan
ya fara motsi, I saw him trying to open his
eyes, sai da kyar ya samu ya bude su
sannan ya sauke su a kaina. I smiled and
said "hello husband" nan da nan naga
toro ya cika fuskarsa, da sauri ya kalli hip
dinsa na hagu gurin da scar din yake and
then tried to get up. Sai lokacin ya lura da
cewa a daure yake "safffiyya" ya fada
muryarsa cike da tsoro, "what have you
done? Me kika yi min?" Na gyara zama na
nace "well, first I drugged you like you did
me. But unlike you, I didn't rape you,
couldn't even bring myself to look at it.
But I saw it, I saw what I was looking for"
ya sake kallon gurin sannan ya kalle ni
"what? What are you talking about? Wacce maganar kike yi haka? Are you crazy? Get me out of this things?" Ya fada yana jan handcuffs din but he was still
very weak bashi da karfi sam.

Na mike tsaye na taka gadon da kafa daya
looking down at him nace "stop trying, ba
zaka fita daga cikin handcuffs din nan ba
sai na gama da kai, and am not yet done
with you. I don't need a confession out of
you saboda already na riga na tabbatar
kai ne. You may have temper with the
evidence but believe me you are going
down one way or another. I promised you
dama didn't I? I promised I will take your
life just like you took mine. And that's
exactly what I am going to do".

Ya girgiza kansa pretending to not
understand maganganu na "me kike
magana akai ne Safiyya? Are you saying
ni kike zargi for that? How can you even
think that?" Na koma inda na ke zaune na
sake zama nace "ba zargin ka nake ba
Mukhtar, na tabbatar kaine, kaima kuma
kasan na san kaine, that was why you try
to get rid of the scar by cutting yourself.
So kake in cigaba da zama da kai a
matsayin mijina even after knowing what
you did to me, So kake in rasa hujjar da
zan raba aure na da kai in kuma rasa
evidence din da zany convicting dinka in the court of law. But I am already two
steps ahead of you Mukhtar" na fada
sannan na sake mikewa na dauko
handbag dina yayin da shi kuma ya kama
rantse rantse "wallahi Safiyya ba ni bane
ba. How can you even think nine? I can
never hurt you ke ma kin sani because I
love you. I love you more than anything
Safiyya please ki yarda da ni. Wallahi......

And his words stopped in his throat sanda
ya ga abinda na fito da shi daga jaka ta. A
brand new scissors. Na bare shi daga
cikin ledar sa sannan na saka hannu na
nayi testing kaifin sa, na juya ina kallon sa
and I have never seen anyone looking as
scared as he did, idonsa kamar zasu fado
kasa. He tried to get up amma jikin sa was still
weak, he tried to get his hands out of the
cuff amma shima ya kasa, "Safiyya? Are
you crazy? What are you doing? Ki dawo
cikin hankalin ki Safiyya. Don't do
something stupid out of anger" ya fada
yana kokarin juya wa, trying as much as
he possibly can to hide the thing in
between his legs,

Na dawo inda yake na dora kafata daya
akan gadon still hannuna rike da
almakashin, "why are you afraid? Tsoron
me kake ji? The pain? Har yanzu ina tuno
da pain din da naji, har yanzu in na rufe
ido na ina jin pain din har cikin kwakwalwa
ta" '"don't do this Safiyya" ya sake fada
frantically trying to free himself, ha cigaba
da cewa "relax, I am doing you and the
world a favor, in na cire kaga shikenan
matan duniya sun huta da hali irin naka,
kai ma kuma ka huta da shan wahalar
finding your next victims. This is justice
for all the girls you have defiled".

Cikin tashin hankali Yace "wallahi, I have
never touched any girl except you. Only
you" na tsaya ina kallon sa "only me? Why
me?" Ya fahimci cewa yayi confessing, ya
kara rikicewa "I can explain. Please
Safiyya ki kunce ni. Ki tsaya muyi magana.
Dan Allah Safiyya" a mayar da almakashi
na cikin ledar sa nace "i am not going to
use this, at least not today and I don't
need your explanation. You can explain to
Daddy and to the judge" na mayar da
almakashin cikin jaka ta, naga yadda
hankalin sa ya kwanta, na fahimci sosai
yana son toy din nan na sa.

Yace "we don't need to do this Safiyya. I
have already regretted more than you
know, I want to make it up to you, I will make it up to you Safiyya. I will love and
take care of you forever. Dan Allah......
You are my wife now Safiyya.... Dan
Allah....... Nobody need to know" ban
saurare shi ba na cigaba da abin da nake,
na gama rufe jakata na rataya na kama
handle din ta kayan na rike nace
"goodbye Husband" ya cigaba da kokari
"get me out of these cuffs mana, don't
leave me naked and like these" har na
juya zan fita sai kuma na juyo nace "you
know what? I have been trying to change
from good girl to bad girl, amma har
yanzu na kasa, I am good and will always
be good. Dan haka zan baka options, ka
zabi wanda zan kira maka ya cire ya bude
maka cuffs din" na fada ina jefar da keys
din a kasa a bakin kofa, na cigaba
'"tsakanin Abba, Umma, Yaya, Salim ko
Salima, ka zabi daya" ya girgiza kai da
sauri "not them... not like this ... Ki dauki
waya ta ki kira friend dina Mus'ab. Ko ki
bude ni da kanki. Dan Allah Safiyya…...
Dan zumuncin da yake tsakanin mu. Don't
let them see me like this" na sake
dawowa ina kallon sa nace "like what?
Naked and in shame? You drugged me,
raped me and took me home to my father.
Har yau bai sake yarda da ni ba. Har yau
bai yarda cewa ba shaye shaye nake yi
ba, Har yau bai yarda cewa ba yawon banza nayi na samu ciki ba. And you don't
want yours to see you naked?" Ya girgiza kai "Please believe me Safiyya,
ban dauka abin zai kai haka ba. Ban san
zai gane ba. Ban san zai dauka a buge
kike ba. Ban san zaki samu ciki ba. Dan
Allah ki yarda, dan Allah ki tsaya muyi
magana" ya fada hawaye yana bin gefen
fuskar sa.
na hadiye dacin da yake makogwaro na
nace '"ba ka san zai faru ba, but ya faru,
and nothing will change that, nothing will
bring me back what you took" na dauko
waya ta nace "are you going to choose or
should I choose for you? Maybe Umma? I
bet she will be very happy that her son is
a rapist. You have three seconds.. 1, 2...".

Da sauri yace "yaya, call yaya" na mayar
da wayar jaka nace "sai nayi bacci na
tashi tukunna" sannan na juya na kai
bakin kofa ya sake kira na, na tsaya ban
juyo ba, yace "think about this one last
time, do you really want to do this? It is
going to be my words against yours" na
juyo da fuskata ina kallon sa nace "'no
husband, it is going to be your

words against yours"

Maman Maama✍🏻[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Forty One: "Goodbye
Husband"


Al'ummar jihar Jigawa da kewayenta har
ma da jihohin kusa . Haifa foods and
pastries ta zo muku da kayan maqulashe
kala kala irin su yogo fura wanda babu
kamar sa ga dadi ga qoshi ga gardin shi
badaganan©️ wani abun saima ka
dandana. Ga irin su milk cake (sunan
wani abu wai farfesun madara) wanda
babu kamar shi ga sauqi ga dadi,
cocunut milk wanda har getare babu
kamar shi da kuma uwa uba Yogo fruits
wanda ze gara muku Ify. Zaku sami kayan
HAIFA har kofan gidajenku in kuna so ga
komai na HAIFA a farashi mai sauki yake
ku garzaya ku dandana kayan dadin Haifa 0812 536 8737 https://www.instagram.com haifa_foods_and_pastries iigsh=NHYyN2k1eTlhenBt&utm_ source=gr

*. *. *. *.

Ina kallon sanda ya hadiye wani mugun
yawu sannan ya fara girgiza kansa, "What
are you doing Fiyya. Na gaya miki baki da
lafiya. I don't want to hurt you" na fara cat
walking zuwa inda yake tsaye "really?
Even if that's the case then we will be
careful. I know you will not hurt me. I trust
you" na tsaya half way from him, studying
yadda yake bina da kallon, yadda
idanunsa suke juyewa, and I hated myself
for doing that. But I have already started
dan haka sai na karasa.

Na saka hannu na sauke kafadar rigar
jikina guda daya, it slid down my arms and
exposed more of my skin, he started
taking steps toward me and I gave him a
look da nake tunanin is seductive and
turned around, signalling him with my
hand to follow me sannan cikin tafiyar da
na tabbatar ba zai iya resisting ba na
koma dakin da na fito daga ciki.

Ina shiga na kalli gadon da sauri making
sure cewa the handcuffs I kept locked at
each side of the bed suna nan but
completely hidden sai dai in kasan da
zaman su, na san cewa wasa nake da
wuta kuma probability is very high that
wutar zata kona ni but I was ready to get
burnt in dai zan samu abinda nake
bukata, Sai dai kuma zuciya ta da gangar
jiki na cike suke da tsoro, kayan ciki na har karkarwa suke yi.

Naji shigowar sa nayi sauri na juya dan
bana so in dauke ido na daga gare shi
even for a second. Ya tsaya a bakin kofa
yana cigaba da kallo na, and akwai wani
murmushi da na kasa fahimta a lips din
shi. Ya karasa shigowa "you are seducing
me" ya fada directly, but daga muryarsa
na san I got him right where I wanted him.
Nayi kokarin yin magana but abinda kawai
yake kwakwalwa ta was that night, the
pain, the darkness, the fear, the........
"Are you sure you know what you are getting
yourself into?" Ya sake fada, bitting his
lips. Nayi taku biyu zuwa gareshi "is it a
crime idan mata tayi seducing mijinta? I
am not made of stone and I have a
husband. Besides, you promised me a
show ranar nan, I want to see the
complete show".

Ya karaso gaba na, looking down at me
"you want a show? You really want a
show? You will have a show" ya fada
muryar sa a cikin kirjin sa sannan ya dora
hannayensa akan kafaduna tare da
kokarin jawo ni closer to him at the same
time trying to kiss me. All | wanted a
lokacin was to scream on top of my voice,
to scream out all my anger and hatred for
him, to stab him in one place or two, amma instead sai na zame daga gare shi na koma kan gado na zauna, close to the spot da na makala one of my handcuffs.

Ya juyo yana kallo na, sai kuma ya tafi
gurin light switch ya dora hannunsa akai
da niyya kashewa. Na mike da sauri,
"Please, no, I hate the dark. It scares me"
and I meant that har cikin raina. Ya juyo
yana kallona and I saw him shakes his
head sannan yace "no!" Na kara matsowa
"please leave the light on" sai ya matsa
daga kusa da ni ya sake cewa "no" na
tsaya kawai ina kallon sa, na fahimci
guduwa yake shirin sake yi ya juya min
baya da sauri trying to stop looking at me
"no, you are sick, and we shouldn't do
this sai kin warke" yana gama fadar haka
yayi hanyar fita da sauri. Na bishi nima da sauri na kama hannun sa da hannu daya sannan na juyo da fuskar sa da daya hannun "i am not sick, come,
will show you that I am fine" and then he
smiled at me, a smile that confirmed all
my suspicious "not tonight, sweetheart"
sannan ya juya ya fita.

Na koma da baya har sai da kafafuwa na
suka ta ba gadon dakin sannan na zauna akan sa. Yanzu shikenan? I have belittled
myself for nothing?

Amma kuma sai naji wani relief a wani
bangaren zuciya ta, I wasn't sure my plan
A will work and wannan abinda ya faru ya
tabbatar min da cewa plan A is off.

Dama na shirya plan A din ne saboda
akwai remnants of shakku a zuciya ta na
cewa shi ya aikata min wancan laifin. Bana
son in dauki alhakin sa idan shi innocent
ne and I risked everything to avoid that.
Amma yanzu, the way he rejected me
bayan na san babu abinda yake so irin to
have me, ya tabbatar min da cewa shi din
dai shine.

Ba fariya ba, yadda Allah ya tsara jikina,
dan ma dai har yanzu ban dawo yadda
nake ba, ba Mukhtar da ya jima yana
lusting for me ba, bana jin akwai namijin
da zan bude masa jikina kamar yadda na
bude wa Mukhtar yau, sannan mu shiga
daki daga ni sai shi, sannan ga igiyar aure
uku a tsakanin mu, kuma ace yayi
rejecting dina yayi tafiyarsa.

Wannan ya kara tabbatar min da abu uku,
na farko Mukhtar ne yayi raping dina, na
biyu kuma ya san ina zargin shi, na uku
and the most important thing shine the
scar is there,

A yadda na bashi labarin daren da akayi
raping dina in details ya tabbatar masa da
cewa ina cikin hayyacina sanda na ji masa
ciwo, and the way that I tried seducing
him tonight bayan halin ko in kula da nake
nuna masa kafin in tare ya tabbatar masa
da cewa shaida nake nema a kansa, kuma
wannan scar din ita ce shaida. Wannan
realization din kuma sai yay unblocking
another fear in me, he will now try to get
rid of the scar ta kowanne hali. Tunda a
ganin sa ita kadai ce shaidar da zata
tabbatar min da kuma duniya cewa shine.
Musamman tunda yana tunanin Junior ya
mutu. And that was where I had upper
hands in the matter, na kuma gode Allah
da yasa nayi wancan tunanin dan in da
yasan Junior yana raye kuma ya san ina
zargin sa zai iya kokarin ma kawar da ni
daga duniya to cover his crime.

Wannan daren shine ya kawo karshen
plan A dina. My plan A was to seduce him
to my bed, handcuff both his hands idan
na dauke masa hankali da jikina, and then
check his body for the scars. It was risky
but worth a trial considering bani da
tabbas din shine dan haka bana son cutar
da shi.

Yanzu kuma it is going to be an eye for an
eye. Dan yanzu zamu shiga plan B.

Sai dai kuma daga alama shima Mukhtar
ya chanja takunsa gabaki daya. Dan ganin
shi ma daga ranar gagara ta yayi. Da
asuba yake fita, sai cikin dare kuma yake
dawowa, wani lokacin ma in ya tashi
dawowa ta can daya kofar falonsa yake
shiga zuwa dakinsa sannan in zai fita ma
ya fita ta can. Mun koma kamar mage da
bera a cikin gidan auren mu. And that
frustrate me more than anything.
Kamar yadda nayi alkawari ba zan yi girki
a gidan Mukhtar ba, ban taba dafa ko da
noddles ba, order abinci nake yi kuma a
kawo min har gida. Shima kuma bai taba
tambaya ta abinci ba, ban san kuma inda
yake zuwa ya ci ba. And I didn't care. Bai
taba kawo abokansa gidan ba, nima kuma
ban gayyaci kawayena ba duk kuwa da
korafin da suka ringa yi min a waya cewa
anyi bikina amma ban gayyace su ba
kuma gidan nawa ma ban gayyace su ba, I
told them suyi hakuri abin ne yazo min
lokaci daya amma na yi musu alkawarin
shirya musu walima wata rana. Amma na
fada musu hakan ne dan su rabu da ni inyi
concentrating akan abinda yake gaba na.
Sati biyu da biki na aka yi na Abdul. Tun
kafin bikin na kira shi a waya nayi masa murna tare da lallaba shi da kyar ya turo min account details dinsa and I sent him heavy da sai da uncle Sufyan da kansa ya kira Daddy and Daddy said babu ruwansa
ni nayi niyya kuma tsakanin mu da Abdul
ne. Lokacin bikin Abdul Mommy tazo gari,
dama munyi waya da ita tace min in shirya
zata zo muje gidan bikin tare ni da ita da
Safina, and I wasn't looking forward to
that. Nayi ta neman hanyar da zan zame
in fasa zuwa na rasa kuma gashi ina son
zuwa din ko dan Aunty Hajjo, na san zata
ji dadi sosai idan naje. But I was in no
mood to neither meet nor talk to Safina.

Sai dai cikin ikon Allah ranar da Mommy ta
zo gari take gaya min Safina ba zata samu
damar zuwa ba, bata da lafiya,
"gashi shi kuma mijin nata har yanzu bai dawo ba,
ina tunanin da ita zan koma Kano gaskiya,
gwara in san a gabana take, ko kuma in je
gidan iyayen nasa inji me zasu ce, amma
wannan ai ba aure ba ne ba" ban ce
komai ba kuma banyi niyyar cewa komai
ba, sai kuma tace "ya kamata dai kije ki
duba ta" nace "insha Allah". Amma sai
naji dadin cewa ba zan hadu da Safina ba,

Ranar yini Mommy tazo ta dauke ni muka
je tare. I kept thinking ko zamu ga Junior?
Ko zata gane shi? Amma da yake a event
center akayi bikin I guess Aunty Hajjo
bata tafi da shi ba dan duk baza ido na
ban ganshi ba. Washegari da dare muka
sake zuwa dinner. Aunty Hajjo taji dadin
ganin mu sosai kuma ta karrama mu
sosai, naje har gurin ango da amarya na
taya su murna and they looked so happy
and so in love with each other. Abdul yayi
introducing dina a grin amaryarsa muka
gaisa sosai, yana tsokana ta wai ina ango
na. Sai ganin su naji ya fama min wani
ciwo a zuciya ta da nake ta ajjiye da shi,
and as I sat down looking at them I
thought about him, ko ina yake? Ko me
yake ciki? And I so much wanted to
unblock his phone number and call him,
maybe inyi pretending kamar babu abinda
ya faru and say '"tsokanar ka fa nake yi
Yaya Muhammad. It was all a prank. I miss
you so much", I remembered the sound of
his voice over the phone, the deepness of
it and how it has always reach deep into
my heart "hey Piya, you have no idea how
much I miss you" na sunkuyar da ido na
kasa ina jin hawaye yana taruwa a idona, a
hankali nace "I miss you too Yaya
Muhammad".

A lokacin ne naji Mommy tana taba ni
"Kinga mother in law din Safina, Ashe ta san su Sufyan" nayi sauri na dago kai and
I saw her tana tafiya zata zauna. Ban taba
ganin ta ba amma na tabbatar ko da kuwa
Mommy bata nuna min ita ba zan iya gane
ta idan na ganta. Kana ganin ta indai
kasan Muhammad to zaka san cewa ita ta
haife shi.

Mommy ta ja hannuna "zo muje ku gaisa
da ita" na zame hannu na tare da
langwabe kai "Mommy please" tace "ke
fa matsalar ki kenan ba kya son mutane,
ai sai kiyi ta zama" ta tafi ta barni. Nayi
ajiyar zuciya na cigaba da kallon Mama
da ga nesa, naki zuwa ne saboda ina jin
toro, ban sani ba ko ta taba ganin hotona
a wayar Muhammad ko something like
that, ina tsoron kar ta gane ni, duk da dai
na san karin maganar hausawa da suke
cewa idan kere na yawo zabo na yawo
watarana dole za'a hadu.

Wasa wasa dai sai naga Mommy ta samu
kujera a can ta zauna sun cigaba da hira.
Ni dai ina zaune a guri daya har aka gama
sannan Mommy ta zo muka tafi. Tun kafin
mu fita na san cewa I was in for hirar
Safina da mijinta har muje gida, ai kuwa
dai muna shiga mota ta fara "mutanen
nan suna da son kansu wallahi, kinji wai
basu san Safina babu lafiya ba, wai bata
gaya musu ba shima bai gaya musu ba,
Amma dai munyi magana tace zata je gidan ta dauke ta ta mayar da ita can
gabanta su zauna tare kafin mijin ya
dawo. Ai ce mata kawai nayi tafiya zanyi
da Safina Kano inyi jinyar ta a can" naji
kamar in toshe kunnena irin yadda nake
mata in bana son jin maganar da take yi
sai kuma na fasa, tunda na mayar da
zargina kan Mukhtar a fara sassautowa
akan Mommy. Sai kuma tayi ajjiyar zuciya
tace "ni tausayi take bani yarinyar nan,
Allah ya sassauta mata wanna lamarin.
Ko babu komai iyayensa masu kirki ne".
Ranar daurin aure ma muka sake komawa
gidan Aunty Hajjo, ranar ni na fara fita a
motata naje na dauki Mommy sannan
muka wuce, muna yin packing na dauko
envelope din dana taho da ita da kudi
masu kauri a ciki na mika wa mommy
nace "gashi Mommy ko zaki bawa Aunty
gudummawa" ai kam taji dadin haka sosai
"kai amma kin kyauta Safiyya, dama ina ta tunanin abinda zan bata na rasa" nayi
murmushi kawai na fita.

Ranar babu mutane sosai tunda daurin
aure ne, sai yan uwansu na jiki sai kuma
few close friends kamar mu. Muka zauna a falo Mommy ta samu wata yar uwar
Aunty Hajjo itama mai surutu suna ta
zance ni kuma na koma gefe ina ta rubuta
wani sabon plan da nake shiryawa akan
maganar reopening Oasis da nake son yi
as soon as I get rid of Mukhtar.

Muna nan sai ga wata yarinya ta shigo
falon da Junior a hannunta, tazo ta zauna
opposite din su mommy ta na bashi
madara shi kuma yana ta rigima yaki sha
sai dawo da ita yake yi. Na ajiye waya ta
akan cinyata ina kallon su. Kanwar Aunty
Hajjo ta juya gurin su itama tace "ke
Husna yaron nan fa ya koshi, daga alama
bacci yake ji ki goya shi mana" wadda aka
kira da Husna ta kwabe fuska kamar zata
yi kuka tace "na goya shin fa yaki yin
baccin wallahi. Wannan yaron rigimamme
ne" Mommy ta juya tana kallon su ita ma
sai tace "ki kaiwa maman sa shi mana to,
maybe goyon ne baki iya ba" yarinyar
tace "to ai maman tana gurin mutane, ita
tace in rike shi" Mommy ta mika mata
hannu "bani shi in gani, watakila diaper
za'a chanja masa ko kuma kaya ne suka yi
masa yawa" yarinyar ta zo ta mika mata
shi ta karbe shi and she laughed and said
"wow, ina karbar yaron nan sai naga
kamar twins sanda suna babies" ta sake
jujjuya shi a hannunta and she looked at
me, muna hada ido na sunkuyar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna, ta sake
kallon sa ta kalle ni a take na fahimci ta
gane shi.

Ta juya tana kallon yarinyar tace "dan
waye?" kanwar Aunty Hajjo da suke tare
tace "au wai kema baki san ta haihu ba?
Dan Hajjo ne fa. Matar nan babu wanda ta
gayawa tana da ciki kawai sai kiran mu
tayi tace ta haihu. Kin san in aka girman
nan in Allah ya kawo rabo sai kiga ana jin
kunyar fada ana gain kamar abin kunya
ne" Mommy ta mika wa matar shi tace
"haka ne. Allah ya raya shi", Matar tace
ameen sannan ta tashi ta jefa shi sama ta
chafe shi, naji kamar zuciyata zata fado
kasa, shi kuma ya takarkare ya chanyara
kuka, sai kuma ta rungume shi a kirjinta
tana dariya sai tace "yaron nan ajebo ne,
bai san cika masaki ba. Bara inje in yi
masa wanka in goya shi, bacci yake j"
tana tafiya Mommy ta juyo tana cigaba da
kallona, fuskarta na nuna alamun bacin
rai. Sai kuma ta mike tayi hanyar waje
tana cewa da sauran mutanen gurin "na
tafi. Allah ya bamu alkhairi, idan Hajjo ta
shigo kuce mata na tafi" na mike nima da
sauri na dauki jakata da waya ta nabi
bayanta.

A hanyar fita muka hadu da Aunty Hajjo
tana shigowa cikin gidan, ta yiwa Mommy
magana amma Mommy ko kallon ta bata
yi ba, muka kalli juna ni da ita and she
understood what happened sai ta bi mu a
baya "Sa'adatu naga sako na gode Allah
ya bar zumunci, Allah kuma ya huta
gajiya, sai munyi waya insha Allah" stil
bata ce mata komai ba ta shiga mota, na
russuna nace "Aunty mun tafi Allah ya
sanya alkhairi" sannan nima na zagaya
drivers seat na zauna na tayar da motar
muka fita fully knowing that mai raba
Mommy da ni ranar sai Allah. Amma sai
naji tayi shiru bata ce komai ba. Fuskarta
cike da bacin rai. Sai naji babu dadi, na
saba da in nayi mata laifi zata yi ta min
fada ne ba wai tayi fushi da ni ba.

Har muka je gida bata ce min komai ba,
nayi packing sannan na juyo ina kallonta
nace "Mommy am sorry" ta juyo tana
kallona tace "no, don't be. Ba laifinki bane
ba ai. Laifi na ne" sannan ta bude motar
ta fita. I thought about following her
inside in sake bata hakuri but sai na
chanja shawara na juya mota na fita, dan
bana cikin mood din bata hakuri ina
tsoron kar in sake kwafsawa again.
Washegari ta koma Kano gurin Daddy, A haka ranaku suka cigaba da wucewa,
satittuka suka shude, har aka yi six weeks
da bikin mu da Mukhtar amma ya ki bani
damar aiwatar da plan B dina a kansa.
And for my plan B ina bukatar getting
close to him. Akwai ranar da nayi niyyar
zuwa dakinsa ma cikin dare in ritsa shi
yana bacci amma sai na tarar ashe kofar
dakin ma rufe ta yake yi. Wato bashi da
niyyar taking any chance with me. Ya kan shigo gurina kusan kullum da assuba, ko da safe idan bai fita da assuba ba, amma a bakin kofar dakina yake
tsayawa "good morning sweetheart. Hope
babu abinda yake damun ki. Aiki ya matsa
min a office ki dan kara yi min hakuri,
soon everything will be over kinji? I will
soon plan us a vacation"

Ko da wasa baya shigo wa cikin dakin,
and da ga na taso zuwa gurinsa zai juya
ya fita. He never let me gets two meters
close to him. Abinda na fahimta bayan
rashin gaskiyar sa shine muguwar
sha'awa na damunsa, and he chose to
avoid me akan yay letting his guard
down. I knew he was trying to get rid of
the scar and duk ranar da ya samu yayi
hakan he will come for me. Wannan kuma shine abinda yake keeping me up wide awake at night.

A cikin six weeks din abubuwa da yawa
sun faru. Har lokacin Mommy fushi take yi
da ni, dan in ba ni na kira ta a waya ba ta
daina kira na. Daddy kuma ya matsa min
lallai in koma bakin aikina, na fahimci he
was worried about me and the way da
yake jin sound of my voice a cikin waya
yana ganin in na koma aikin it will keep my
spirit up, gani yake kamar zaman bana yin
komai ne ya jawo nake cikin damuwa. Na
ce masa ya dan kara hakuri kadan na kusa
komawa, but he didn't believe me sai
gashi ya turo uncle Ahmad har gida wai
yazo yayi min magana in cigaba da
abubuwan da na fara a office. Na gaya
masa shima soon zan dawo, akwai abinda
nake jira ne.

Sai da ya tashi tafiya sannan yace
"Safiyya wannan gidan naku yayi muku
kadan. Ya kamata ku samu babba ku siya
ku koma tunda in kika koma bakin aikin ki
ai mutane zasu ke zuwa gurinki, manyan
mutane, this house shouldn't be
presented as yours" nayi mamakin
maganar sa amma sai nace masa "okay
babu komai. Za'a sayi wani insha Allah" ya yi murmushi '"a fara duba muku?" Na
girgiza kaina "later.…. In lokacin siyan yayi i
will talk to you".

And then one fateful day, ina zaune akan
sallaya ta da daddare na gama shafa"I da
wutiri ina adduoina naji shigowar motar
Mukhtar, ban wani mai da hankali akan
hakan ba dan nasan ba lallai ne ma ya
shigo ta nan falon ba, amma ga mamaki
na kawai sai ji nayi an bude kofar dakin da
nake ciki, na dan tsorata kadan dan ban
saka ran shigowar sa ba, nayi sauri na
shafa adduar na juyo na ganshi a tsaye a
bakin kofa, ya rungume hannayensa a
kirjinsa with that smile that I now so much
understand a fuskarsa.

Naji kirjina ya buga da karfi, tsoro ya
kamani but I tried as much as I can to
keep my face neutral, nace "you scared
me, me kake yi anan kuma yau?" ya gyara
tsayuwarsa "hello sweetheart, sorry na
baki tsoro, laifi ne dan miji ya shigo dakin
matar sa da dare?" na fara dauke kayan
sallata nace "au dama ni matar ka ce, ai ni
har na manta ma. Thank you for
reminding me" yayi dariya tare da karaso
wa cikin dakin "kiyi hakuri, I know I
haven't been a good husband, but believe me things are going to change a gidan
nan from today" na jawo drawer,
pretending kamar sallaya nake sakawa a
ciki, na dauko abinda zan dauka a ciki na
boye a cikin hijab dina na juyo tare da
bata rai nace "ka riga kayi wasa da
damarka ai Mukhtar, I gave you a golden
opportunity ka debi kasa ka watsa min a
fuska, yanzu mun riga mun wuce wannan
stage din" na fada meaning every word of
what I said. Ya fara tahowa zuwa inda
nake "na san nayi ba dai dai ba, and
believe me it hurt me more than it did
you, why do you think na daina zama a
gida? It was because I couldn't get that
site out of my head, it drove me crazy, it
is still driving me crazy. Bana son in
hurting dinki, especially after what you
went through shi yasa na baki chance dan
ki warke sosai. But get ready" ya fada
smirking "because I am ready".

Na yi getting ready din kuwa exactly like
he said, but not in the way he meant, and
I watched him come closer har yazo
gabana ya tsaya idonsa yana bin jikina da
kallo duk kuwa da cewa still akwai hijab a
jikin nawa, ya tsaya so close har ina iya jin
saukar numfashinsa a fuskata yace "I have dreamt about this night Safiyya, fiye
da adadin da zan iya lissafawa, I have
planned for this night Fiyya more times
than I can remember, for years na yi
dakon soyayyar ki a raina mai tarin yawan da ban san adadin ta ba. And tonight, finally, burina zai cika, I
am finally going to make you mine, tawa
ni kadai, har abada".

Na mayar masa da murmushinsa, sannan
nace "I also have been planning for this
night Mukhtar, amma not for years but for
weeks"
And then just as I said that, allurar da
nake rike da ita a cikin hijab dina ta huda
hijab din nawa, ta huda kayansa, ta huda
tsokar cinyarsa sannan na juye masa
abinda yake cikin syringe din a jikin sa.

It happened in seconds, and it was done
before he realize what was happening.
The next second na matsa da sauri away
from him nayi hanyar bakin kofa na tsaya
ina kallonsa, ready to run dan jininsa yafi
karfin allurar,

Ya juyo yana kallona hannunsa rike da
cinyarsa, fuskarsa cike da mamaki " Safiyya!" ya ambata idanunsa suna juyewa,
"What have you done?" yayi taku
biyu zuwa inda nake yana miko hannunsa
gare ni, sannan yayi taku daya baya, na
dawo cikin dakin na karasa gaban shi na
tsaya daf dashi sannan nace "| am giving
you the taste of your own medicine" sai
kuma na saka hannayena biyu da karfi na
tura shi ya fada kan gadon da baya, and
he lost consciousness a lokacin.

My thought was drugging Mukhtar will be
the hardest part of plan B, amma sai
bayan da na same shi unconscious akan
gado na sannan na fahimci it was the
easiest. My plan was to use my handcuffs
in daure hannayensa a both sides of the
bed and then strip him naked in duba
abinda nake nema. Zan daure
hannayensa ne saboda ban san karfin
jinin sa ba ina tsoron kar ya tashi kafin in
gama abinda nake yi.

Amma sai lokacin na fahimci cewa karfi na
bai fi cikin cokali ba, ba karamar wahala
na sha ba kafin in jashi zuwa position din
da zai bani damar dare hannayensa duk
biyun. Kuma nayi hakan ne cike da tsoro
ina gain zai iya farkawa anytime. Bayan
na gama sai da na tabbatar handcuffs din
sunyi locking hannayensa completely
sannan na zauna na huta na sha ruwa sai na fara next task dina na checking his body for the scar, target dina dama shine bayan sa da cinyoyin sa, sai kuma a
lokacin na fahimci cewa ba zan iya cire
masa rigar ba saboda yadda hannayen sa
suke daure, so I got a razor blade and cut
it, na yanke ta daga jikin sa sannan na
yanke singlet din ciki, and it took me a
whole lot of another energy to roll him to
his side dan in samu ganin bayan.

1 already had a mental picture of yadda
marks din zasu zama, zasu zama size din
tsinin fork guda hudu a jere, distance din
tsakanin su kuma zai zama even. I
checked, bayan fitilar dakin da kuma
bedside lamp da na kunna har sai da na
kara da fitilar waya ta but banga komai
makaman in hakan ba.

Wannan ya saka na koma next gurin da
nake suspecting, cinyoyin sa, na zare
wandon jikinsa na barshi da gajeren, I
wasn't looking forward to cire masa
gajeren wando for my own mental health,
but at the end I had to cut them too, na
yanka sides dinsu but leaving the rim and
the middle covered dan bana san ganin
abinda zai kara min trauma akan wacce
nake facing already.

Amma babu marks babu alamun su. And
then just as I was about to give up I saw
something, a scar, a can saman cinyarsa
ta hagu kusa da hip bone dinsa, amma
kuma wannan sabon tabo ne and it looks
nothing like tabon fork. It looks like an
yanke a gurin deep yanka wanda har sai
da aka yi dinki a gurin. Na sake haska fitila
ta sosai sai naga tsahon yankan dai dai
fadin yatsun fork ne. It looked new, bana
jin zaiyi wata biyu.

A lokacin ne na tuna cewa da hannun
dama na ji masa ciwon, meaning tabon
should be a bangaren hagun sa.

Sai na fahimci abinda ya faru, na ja da
baya na zauna akan side drawer ina kallon
sa cikin bacin rai. Tabbas shine. And that
tabon stitches da na gani shine dai dai
gurin da ya kamata ace naga tabon fork,
but bayan na kwafsa ranar da aka kawo ni
na nuna masa alamar cewa ina zarginsa,
he got rid of the original scar by creating
another one a dai dai inda waccan take.
He cut himself. He cut himself deeply and
took himself to hospital yayi musu wata
karyar suka yi masa dinki a gurin. Wannan ya sa ya ja baya da ni, giving himself time to heal, giving the new scar time to form and cover the old one.

And that got me furious, really furious
that karfin addu'a he kawai ya rike ni ya
hanani hallaka Mukhtar a cikin daren nan.
Plan B ya kare. My plan B was to get
Mukhtar close and drug him ya zama
unconscious, in daure shi yadda ba zai
farka yayi harming dina ba, and check for
the scar. In na gani kuma in hada kaya na
inyi gidan mu and then sue him for rape.

Sai dai wannan discovery din ya tabbatar
min da cewa to get justice from him dole
sai na shiga plan C and I wasn't looking
forward to it, duk wannan wahalar da
nasha da risking rayuwata was to avoid
the plan C. Bana son in shigar da Junior
cikin maganar, idan da zan samu yadda
nake so, bana son ko sau daya Mukhtar
ya dora idonsa akan sa. But now he must
come in to get justice for the two of us.

Har lokacin Mukhtar bai tashi ba, ya
kamata ace hankali na ya tashi amma bai
tashi ba, sanda ina neman drug din I
asked for mai matsakaicin karfi with low
risk dan bana son jininsa a hannuna duk
kuwa da cewa chances are higher na
cewa jinin sa zai fi karfin maganin but it
now seems like jinin na sa bashi da karfi.
While waiting sai na dauko red permanent marker din da na ke ajiye da ita a cikin
jaka ta na koma kan gadon nayi masa
rubutu manya akan goshinsa "RAPIST"
sannan na sauko.

Na dauko karamar akwati ta da hada duk
abubuwan da na san ina bukata, dama
kayan sawa kusan duk wadanda suke
dakina a Abuja ban dauko ko set daya ba
suna can, akwatinan lefe na kuwa har
yanzu ko buda su banyi ba. Na ajiye
akwatin a gefe na jawo kujera na zauna na
saka Mukhtar a gaba ina jiran ya tashi. Sai
da sanyin asuba ya fara kadawa sannan
ya fara motsi, I saw him trying to open his
eyes, sai da kyar ya samu ya bude su
sannan ya sauke su a kaina. I smiled and
said "hello husband" nan da nan naga
toro ya cika fuskarsa, da sauri ya kalli hip
dinsa na hagu gurin da scar din yake and
then tried to get up. Sai lokacin ya lura da
cewa a daure yake "safffiyya" ya fada
muryarsa cike da tsoro, "what have you
done? Me kika yi min?" Na gyara zama na
nace "well, first I drugged you like you did
me. But unlike you, I didn't rape you,
couldn't even bring myself to look at it.
But I saw it, I saw what I was looking for"
ya sake kallon gurin sannan ya kalle ni
"what? What are you talking about? Wacce maganar kike yi haka? Are you crazy? Get me out of this things?" Ya fada yana jan handcuffs din but he was still
very weak bashi da karfi sam.

Na mike tsaye na taka gadon da kafa daya
looking down at him nace "stop trying, ba
zaka fita daga cikin handcuffs din nan ba
sai na gama da kai, and am not yet done
with you. I don't need a confession out of
you saboda already na riga na tabbatar
kai ne. You may have temper with the
evidence but believe me you are going
down one way or another. I promised you
dama didn't I? I promised I will take your
life just like you took mine. And that's
exactly what I am going to do".

Ya girgiza kansa pretending to not
understand maganganu na "me kike
magana akai ne Safiyya? Are you saying
ni kike zargi for that? How can you even
think that?" Na koma inda na ke zaune na
sake zama nace "ba zargin ka nake ba
Mukhtar, na tabbatar kaine, kaima kuma
kasan na san kaine, that was why you try
to get rid of the scar by cutting yourself.
So kake in cigaba da zama da kai a
matsayin mijina even after knowing what
you did to me, So kake in rasa hujjar da
zan raba aure na da kai in kuma rasa
evidence din da zany convicting dinka in the court of law. But I am already two
steps ahead of you Mukhtar" na fada
sannan na sake mikewa na dauko
handbag dina yayin da shi kuma ya kama
rantse rantse "wallahi Safiyya ba ni bane
ba. How can you even think nine? I can
never hurt you ke ma kin sani because I
love you. I love you more than anything
Safiyya please ki yarda da ni. Wallahi......

And his words stopped in his throat sanda
ya ga abinda na fito da shi daga jaka ta. A
brand new scissors. Na bare shi daga
cikin ledar sa sannan na saka hannu na
nayi testing kaifin sa, na juya ina kallon sa
and I have never seen anyone looking as
scared as he did, idonsa kamar zasu fado
kasa. He tried to get up amma jikin sa was still
weak, he tried to get his hands out of the
cuff amma shima ya kasa, "Safiyya? Are
you crazy? What are you doing? Ki dawo
cikin hankalin ki Safiyya. Don't do
something stupid out of anger" ya fada
yana kokarin juya wa, trying as much as
he possibly can to hide the thing in
between his legs,

Na dawo inda yake na dora kafata daya
akan gadon still hannuna rike da
almakashin, "why are you afraid? Tsoron
me kake ji? The pain? Har yanzu ina tuno
da pain din da naji, har yanzu in na rufe
ido na ina jin pain din har cikin kwakwalwa
ta" '"don't do this Safiyya" ya sake fada
frantically trying to free himself, ha cigaba
da cewa "relax, I am doing you and the
world a favor, in na cire kaga shikenan
matan duniya sun huta da hali irin naka,
kai ma kuma ka huta da shan wahalar
finding your next victims. This is justice
for all the girls you have defiled".

Cikin tashin hankali Yace "wallahi, I have
never touched any girl except you. Only
you" na tsaya ina kallon sa "only me? Why
me?" Ya fahimci cewa yayi confessing, ya
kara rikicewa "I can explain. Please
Safiyya ki kunce ni. Ki tsaya muyi magana.
Dan Allah Safiyya" a mayar da almakashi
na cikin ledar sa nace "i am not going to
use this, at least not today and I don't
need your explanation. You can explain to
Daddy and to the judge" na mayar da
almakashin cikin jaka ta, naga yadda
hankalin sa ya kwanta, na fahimci sosai
yana son toy din nan na sa.

Yace "we don't need to do this Safiyya. I
have already regretted more than you
know, I want to make it up to you, I will make it up to you Safiyya. I will love and
take care of you forever. Dan Allah......
You are my wife now Safiyya.... Dan
Allah....... Nobody need to know" ban
saurare shi ba na cigaba da abin da nake,
na gama rufe jakata na rataya na kama
handle din ta kayan na rike nace
"goodbye Husband" ya cigaba da kokari
"get me out of these cuffs mana, don't
leave me naked and like these" har na
juya zan fita sai kuma na juyo nace "you
know what? I have been trying to change
from good girl to bad girl, amma har
yanzu na kasa, I am good and will always
be good. Dan haka zan baka options, ka
zabi wanda zan kira maka ya cire ya bude
maka cuffs din" na fada ina jefar da keys
din a kasa a bakin kofa, na cigaba
'"tsakanin Abba, Umma, Yaya, Salim ko
Salima, ka zabi daya" ya girgiza kai da
sauri "not them... not like this ... Ki dauki
waya ta ki kira friend dina Mus'ab. Ko ki
bude ni da kanki. Dan Allah Safiyya…...
Dan zumuncin da yake tsakanin mu. Don't
let them see me like this" na sake
dawowa ina kallon sa nace "like what?
Naked and in shame? You drugged me,
raped me and took me home to my father.
Har yau bai sake yarda da ni ba. Har yau
bai yarda cewa ba shaye shaye nake yi
ba, Har yau bai yarda cewa ba yawon banza nayi na samu ciki ba. And you don't
want yours to see you naked?" Ya girgiza kai "Please believe me Safiyya,
ban dauka abin zai kai haka ba. Ban san
zai gane ba. Ban san zai dauka a buge
kike ba. Ban san zaki samu ciki ba. Dan
Allah ki yarda, dan Allah ki tsaya muyi
magana" ya fada hawaye yana bin gefen
fuskar sa.
na hadiye dacin da yake makogwaro na
nace '"ba ka san zai faru ba, but ya faru,
and nothing will change that, nothing will
bring me back what you took" na dauko
waya ta nace "are you going to choose or
should I choose for you? Maybe Umma? I
bet she will be very happy that her son is
a rapist. You have three seconds.. 1, 2...".

Da sauri yace "yaya, call yaya" na mayar
da wayar jaka nace "sai nayi bacci na
tashi tukunna" sannan na juya na kai
bakin kofa ya sake kira na, na tsaya ban
juyo ba, yace "think about this one last
time, do you really want to do this? It is
going to be my words against yours" na
juyo da fuskata ina kallon sa nace "'no
husband, it is going to be your

words against yours"

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹


Episode Forty Two: Shattered Desires

Not Edited.

Ina fita na shiga mota ta na tayar a dai dai
lokacin da mai gadin gidan yake kokarin
yin alwala, ya ajiye butar hannunsa da
sauri ya taho inda nake "Hajiya..... Allah
dai ya sa lafiya" nace "lafiya lau, zan yi
tafiya ne kuma jirgin mu in an jina kadan
zai tashi" ya gyada kai cikin fahimta
amma kuma sai yace "ai da mai gidan ya
raka ki Hajiya, garin ne kin san yanzu sai a
hankali. Ina ji miki tsoron fita ke kadai" na
kirkiri murmushi nace "nayi addu'a. Now,
bude min gate" na karasa maganar da
authority a voice dina, ya juya da sauri
yaje ya bude gate din na ja mota ta na fita.

Gidan mu na zarce direct, na tarar mai
Eta gadin mu ya davo daga masallaci kenan
yana shirin bude gate sai ya ga mota ta,
ya gane motar amma sai ya fasa bude
kofar ya dawo da baya yana kara kokarin
ganin wanda ya ke cikin motar, na sauke
tinted glass din windon motar dan saukaka masa gani na. Yayi sauri ya sussuna "sannu da zuwa ranki ya dade" ban ce komai ba sai na mayar da window
na rufe, ya ruga da sauri ya bude gate din
ni kuma na shiga da motar ciki nayi
packing dinta a gurin da dama nan ne
inda nake ajjiye ta. Na sauke ajjiyar zuciya
sannan na bude kofa na fito, mai gadin ya
karaso inda nake yana kallo na da hasken
alfijir da ya fara haska gari, "sannu da
zuwa, da assuba haka? Babu kowa amma
a cikin gidan" nace "ina Esther?" Yace
"taje gida suna biki. Sai yau zata dawo"
ssi kuma ya koma dakin sa da sauri ya
dauko key ya kawo min. "ga keys ta bari
da ma ko za'a yi bako" na karba nace
'"'shikenan. Nagode Baba Ya'u".

Na juya na shiga cikin gida amma ina jin
sa yana kallo na. Na bude kofa na shiga,
falon da duhu sai na kunna fitilar wayata
da niyyar zan haska hanya ba sai na
kunna fitilu ba. Ina haska fitilar sai ta
sauka akan hoton Baba Hadiza da
yayanta. Na karasa gaban su na tsaya ina
kallon su, they all looked happy and kuma
kamar ni suke kallo, Na saka hannu na
shafa fuskar Ammie "hey Ammieme" sai
kuma na wuce hoton na tafi hanyar da
zan hau stairs zuwa dakina, Ina shiga dakin na kunna fitila, sai na ga Esther ta rufe komai na dakin da yadi dan kar yayi kura, atmosphere din dakin was
suffocating tunda komai a rufe yake, na
ajiye jakar hannuna na bude windows din
akin sannan na yaye yadin da ta rufe
gado da shi na bude closet na dauko
bedsheet na zo na shimfida akan gadon
sai kuma a shiga toilet nayo alwala na
fito nayi sallah. Ina idarwa na mayar da
windows din na rufe sannan na kunna ac
na saka waya ta on silent mode na bi
lafiyar gado na kwanta, and I slept like a
baby, irin baccin da tun da naje gidan
Mukhtar ban yi irin sa ba.

Him👳🏻‍♀️

Three Months ago……

Kamar wani engine haka Muhammad
Gidado ya mayar da kansa, daga ina kake
aiki ina zaka je aiki me yi aiki, Abba da
kansa had to tell him to slow down and
take things easy. Within the first few
weeks da ya fara yiwa abba aiki ya yi
securing musu business deals da yawan
da Abba bai yi tsammani ba. He takes
risks and he no send anybody, Nan da
nan sunan shi ya fara shiga bakunan
business partners din su and they tried to
make deals with him, wadansu deals din
ya karba wadansu kuma yayi watsi da su, A gida kuma yana iyakacin kokarin sa na ganin cewa hanya bata hada su da Safina ba. Saboda idan bai ganta ba yakan
manta da wasu abubuwan amma da zarar
ya ganta zai ji duk damuwowin sa sun
dawo masa sababbi fil. Sannan kuma
babu yadda za'a yi su hadu din bata gaya
masa maganar da zata tuna masa cewa
ita yayar Safiyya ce and Safiyya is now
someone else's wife. Wannan knowledge
din kuma shine abinda yake fin komai
dagula masa lissafi ya kuma bata masa
rai. Idan kuma ran nasa ya baci sai yaje ya
huce akan punching bag din da ya saka a
cikin gym dinsa. Wannan punching bag
din da ace mutum ce da babu kashin da
ba zai karye a jikin ta ba saboda irin
dukan da take sha a gurin Muhammad. A zuciyarsa yana son ya cigaba da digging labarin Safiyya kamar yadda ya fara, amma kuma yana dakatar da kansa
dan yana gudun sabawa ubangiji, ya
tabbatar Safiyya a yanzu matar aure ce
tunda babanta da kansa ya gaya masa,
cigaba da bibiyarta kuma a matsayin ta na
matar aure haramun ne kuma zai iya jawo
masa fushin ubangiji. A gefe daya kuma ya san the more he hold on to her the more soyayyar ta take karuwa a zuciyarsa wanda shima hakan ba dai dai bane ba kuma bai san inda hakan zai kai shi ba.

Ya tuna da abinda tace masa, she said he
should accept his fate kamar yadda ita
ma tayi accepting kuma take facing na ta,
ya tuna da tambayar da yayi mata akan
tana nufin yayi accepting Safina? And she
couldn't answer that, sai dai fuskar ta ta
nuna tsantsar kishin sa da take yi akan
Safina.

Safinan kuma ita ce babban problem din
sa a yanzu. Ya tsane ta. Ya tsane ta ba
kadan ba. Ya kasa cire tunanin cewa tana
da hannu a cikin koma menene ya samu
Safiyya, koma menene ya chanja da
Safiyya from a cheerful soul to a
sorrowful soul. Gani yake yi kamar Safina
ce tayi mata wani abu dan ta raba su ita ta
same shi. Dan irin soyayyar da take nuna
masa is scary, it is obsession. Ko kadan
©️? bata yin zuciya da shi ko tayi masa fushi
duk kuwa da irin trailer trailer ta rashin
mutunci da yake sauke mata. Sai dai tayi
kuka ta gama ta cigaba da ga inda ta
tsaya,

Ko da sau daya bata taba fashin yi masa
girki ba, zata yi breakfast ta kawo masa
za kuma tayi dinner, ranar da taga yana
gida bai fita ba har lunch take yi masa
amma bai taba yin ko da loma daya ba.
Sometimes he wondered me take yi da
abincin idan bai ci ba? Shi kuma yana
iyakacin kokarin sa wajan ajiye mata kudi
a kusa da abincin da ta kawo din, a
ganinsa ya rage wa kansa nauyin ta na
ciyarwa. Amma kuma a kasan zuciyar sa
ya san ba wannan ne kadai nauyin ta da
yake kansa ba. But he couldn't even think
of sauke dayan nauyin. God forbid….

Sai dai ita kuma a nata bangaren tana yin
duk kan kokarin ta na taga cewa ya sauke
wancan nauyin da yake gudu din, tunda
ita lissafin ta shine sauke wancan nauyin
shine kadai hanyar da zata bi ta ga ta juyo
da hankalinsa gare ta. If only he will come
to her bed……. If only he will let her go to
his bed. Amma san babu hanya kuma
babu fuska,

Ta sha gwada shiga dakinsa, amma babu
abinda take samu a cikin dakin sai
wulakanci da bakar magana, Ta sha
gwada yaudarar sa zuwa nata dakin,
amma tun shigar da yayi ranar da su twins suka zo bai sake shiga ba. Sai ta chanja salo, har a falon nashi ba ta kyale shi ba duk inda yayi in dai yana gidan sai ta bishi ta nuna masa jikinta with any opportunity
da ta samu.

And then one day, three weeks after
komawar su Safiyya Kano, about a month
kenan da bikin su. Muhammad ya tashi da
assuba yayi sallah sai ya shiga gym dinsa
kamar kullum ya fara gudu akan treadmill,
dama yanzu al'adar sa kenan kullum
bayan sallar asuba zai shiga yayi exercise
in ya gama kuma sai yaje yayi wanka yayi
breakfast ya fita, exercise din yana sa ya
zama more focused and more productive
a gurin aikin sa.

Kamar kullum ranar ma ya toshe
kunnuwansa yana jin kida while running,
his mind focused on the lyrics. A lokacin
ne yaji kamshin turarenta and yaji haushin
kansa for forgetting to close the door.
Dan yanzu ya zama shi da gidan sa amma
bashi da ikon barin kofa a bude sai ta
shigo ta takura masa, Ya cigaba da
abinda yake yi, knowing fully well abinda
zai gani dan ya kalli inda take and he
wasn't looking forward to it. Amma bata
hakura ba sai da ta taho ta zagaya ta tsaya a gaban treadmill din.

Wando ne a jikin ta three quaters length
wanda ya kama ta sosai dan Muhammad
ya tabbatar sai da ta sha wahala kafin ta
saka shi, da kuma half vest wadda ko
rabin cikinta bata rufe ba kuma babu
brazier a cikin ta. Tayi packing gashin
kanta a gefe daya ta zubo shi kan kafadar
ta daya, fuskar ta babu kwalliya sai
murmushi da yake kwance a lebenta. Yayi sauri ya sauka daga kan treadmill din
dan saura kadan ya fadi "damn it" ya fada
cikin tsawa tare da dafe kansa "what the
hell are you doing here?" Tayi magana
amma bai ji ba saboda kunnensa da yake
toshe. Ya cire abin kidan sannan ya sake
cewa cikin tsawa trying as much as he
can to not look at her "Malama ki fita ki
bani guri, Wai ke wacce irin mutum ce?
Are you insane? Haka aka koya miki
tarbiyya a gidan ku?".

Ta saka hannun ta daya tana shafa gashin
kanta zuwa kafadar ta tace "gidan mu
sunyi min tarbiyya sosai, Na kuma gode
musu. Ban ga abin rashin tarbiyya dan na
gaishe da miji na ba, Ina fatan ka tashi
lafiya" yace "to be frank with you, lafiya lau na tashi and I was looking forward to this day saboda ina da muhimman abubuwan da nake da su a gaba na, but
now I am not so sure. You destroyed my
morning with your presence. Now get out
of my site".

Amma maimakon ya ga bacin ran abinda
ya fada a fuskarta sai yaga murmushi ta
cigaba da yi. "I am sorry Habibi. Na san
ma bata maka morning dinka tunda yanzu
na tabbatar in kaje office babu abinda
zaka iya yi sai tunani na. And that's
exactly what I want. I want you to think
about me, and know that I am yours, and I
am here a cikin gidan ka a matsayin matar
ka and ….
..." Ya nuna mata hanya "ki fita
nace miki tun kafin in chanja miki
kamannin ki. You have no idea how much I
have been trying to control my temper
around you. Ki kwashe wadannan
kafafuwan na ki ki dauki sauran mutuncin
da ya rage miki ki fita. You have no idea
how much I hate the site of you" amma
maimakon ta fita din kamar yadda ya
bukata sai ta durkusa a gaban sa fuskar
ta a kasa, "Muhammad. You can hate me
all you want, amma kasan cewa ni ina son
ka. Bana jin akwai wata mace kaf duniya
da zata yi maka irin son da nake yi maka, Kuma......
."Bai jira sauran maganar ta ta
ba ya juya ya fice ya bar mata gym din,
yana shiga dakin sa ya mayar da kofa ya
rufe dan gani yake yi zata iya biyo shi nan
din ma. Bayna ya rufe kofa sai da ya
jingina kansa a jikin kofar tare da rude
idonsa yana mayar da numfashi, wannan
wanne irin tashin hankali ne .... Yarinyar
nan ta wuce duk inda yake tunani a rashin
aji. Abinda kuma ya tabbatar wa kansa
shine ba zata hakura ba. Dan da zata
hakura da tuni ta hakura. Da tana da
zuciya da tuni tana gidan su.
A ranar a office ya yanke wata shawara.
Kasar zai bari. Akwai wasu tafiye tafiye
dama da ya fara tunani akai amma kuma
bai yanke shawara ba, wadansu tarurruka
ne na oil marketers da za'ayi a kasashe
uku cikin watanni uku masu zuwa,
kowanne wata daya za'a yi taro daya a
kasa daya, he was thinking of going to
one of the countries, amma ranar kawai
sai ya dauko takardu ya cike duk kasashe
ukun. Yana bukatar hutu gaskiya. Yana
bukatar time away from everything and
everyone musamman wanna halittar da
take gidan sa.

A ranar ya fara processing tafiyar, yadda
ya tsara shine in ya tafi ba zai dawo ba sai
an gama dukkan tarukan, daga kasar
farko zai wuce ta biyu sannan kuma ya wuce da uku. Ana tashi daga office ya tafi
gida ya fara yiwa Abba bayani, Abba ya
fahimta sosai kuma yaji dadin yadda yake
kokarin gain cigaban business din su.
Amma kuma sai ace "amma da matar ka
zaka tafi" Gidado yaji kamar Abba ya
kwada masa mari, yace "Abba business
trip ne fa? Ta yaya zan ringa yawo da ita a
cikin mutane? Ita kanta ba zata ji dadin
tafiyar ba" Abba yace "zata ji dadi mana.
And who told you ba zaka iya zuwa da
matarka business meetings ba? She is
your wife, you can take her anywhere.
Muhammad ya dafe kai yana jin kamar
zaiyi kuka.

Sai bayan da Abba ya tashi sannan Mama
ta dawo kusa da Muhammad tace "you
want to run away from your
responsibilities ko?" Ya gyara zaman sa
yace "haba Mama, wanne run away kuma
sai kace wani yaro. I just want a little
peace" tace "tana vi maka wani abu ne a
gidan that is not peaceful?" Yayi shiru bai
ce komai ba, bai sani ba ko tsayawa a
gabansa almost naked can be counted as
"not peaceful" ta cigaba "ni ina ganin ka
dauke ta ku tafin Muhammad, you both
need the trip,

Maybe tafiyar zata yi clearing issues din
ku ta samar muku fahimtar junan da kuke
lacking" yace "Mama. I planned the trip to
get away from her. How can I then carry
her along on a trip that is meant to get me
away from her" Mama tayi shiru tana
kallon sa, daga alama bata gane ba,
shima kan sa bashi da tabbacin yana
making sense or not.
O
Ganin duk ba zasu fahimce shi ba sai ya
mike zaiyi mata sallama ya tafi. Tana ta
kallon sa tace
"you are still thinking about
that girl ko?" Ya tsaya bai ce komai ba
kuma bai juyo ba, tace "wannan abin da
kake yi kana tayar da hankalin ka kaki ka
kwantar da hankalin ka kayi concentrating
on what God has blessed you with duk
saboda Safiyya ne ko?" Ya juyo yana
kallon ta amma bai ce komai ba, he can
see the hurt on her face amma kuma ba
zai iya ce mata ba saboda Safiyya bane
ba saboda shi ya san saboda itan ne.
Bai koma gida direct ba, sai da yayi yawo
a gari a mota dan ya danyi clearing brain
dinsa ya kuma nemawa kansa mafita.
Yana jin haushin kansa for loving Safiyya
too much, yana jin haushin Safiyya for
making him go through this dan a ganinsa
ita tayi causing komai, Sai da dare yayi
sosai sannan ya dauki hanyar gida, Sai dai
kuma to add to his troubles yana zuwa kofar dakin sa ya saka key zai bude sai yaga kofar ta bude, and he saw her standing a tsakiyar dakin tana jera pillows
akan gado. Ya fahimci kamar ta chanja
beddings din ne. Ya tsaya yana kallon ta,
ta gama jeran pillows, ta dauke wannan ta
juya wancan tayi straightening wannan
har ta gama sannan ta dauko turare tana
fesawa akan gadon.

Ya na daga bakin kofa yace "cire su ki
mayar da su inda kika debo su" ta juyo
tana kallon sa, daga alama ba ta san da
zuwan sa ba. Ta dan yi murmushi "yayi
kyau ko?" Bai ce komai ba ya sake hade
rai. Ta cigaba da murmushi "yayi min kyau
sosai, saboda na ka ne" ya sake maimaita
abinda yace "ki kwashe min su daga kan
gado ki mayar da su inda kika debo su".
Bata yi hakan ba sai ta tako ta taho inda
yake tsaye, rigar bacci ce a jikinta with a
very low neckline da yake bayyanar da
kusan rabin kirjinta.

Ta tsaya a gaban sa suna kallon juna.
"get out" ya fada cikin muryar da take nuna
tsananin tsanar ta. Tace "Muhammad.
Dan Allah ka tsaya muyi magana ko da
sau daya ne. Ka bani da ma at least kaji
abinda yake zuciya ta" ya saka
hannayensa a aljihunsa yace "okay,
Menene a zuciyar taki, That is in kina da
zuciyar kenan" ta langwabe kai tace '"babu mutumin da Allah yake halitta babu zuciya a kirjin sa, kamar yadda Allah yake rubutawa kowa kaddarar sa, ni tawa
kaddarar ita ce soyayyar ka" yace "wrong
answer. The only words I want out of you
is a confession. Ki gaya min yadda kika
saci saurayin kanwarki, and yadda kika yi
crawling into my life" ya girgiza kanta
"wallah ban san kai saurayin ta bane ba.
Ban san sau nawa zan rantse maka akan
hakan ba. Bani da hannu sam akan
rabuwar ku. I only know ina son ka.
Soyayyar ka ita kadai ce abinda na sani a
cikin duk wannan maganar. And I will do
anything for you. Duk abinda kace inyi
maka wallahi zanyi maka indai bai sabawa
ubangiji ba. Saboda ina son ka. Ina sonka
sosai Muhammad".

"Get out" ya sake fada, tayi kamar zata yi
kuka "please Muhammad ko yaya ne ka
yarda da ni mana. You have no idea how I
am hurting akan abinda kake yi min. o da
ba zaka so ni yanzu ba ka bani dama in
nuna maka tawa soyayyar. Na tabbatar
maka wata rana you will look back and
thank God for separating you from
Safiyya and giving you me"

Ya ja kofar akin da hannunsa daya yace
"how dumb are you? Menene baki gane
ba wai? Get din ko kuma out din? I said get out" har tazo zata wuce shi kuma sai
yace "wait" ta dakata with hope a fuskar
ta sai ya nuna gyaran gadon da tayi yace
"take your trash out with you",
Haka ta koma ta nannade duk shimfidar
da tayi ta rungumo kayanta a hannun ta
tazo zata wuce shi, sai a lokacin yaga
hawayen da yake bin fuskarta, ta tsaya a
bakin kofa tace "kamar kullum dai. I am
sure you will come around one day. Akwai
anar da zaka fahimci banbancin soyayyar
karya da ta gaskiya, and when that day
comes, I will be here to wipe away your
tears".

Washegari ya cigaba da shire shiryen
tafiyar sa, the first meeting is in a weeks
time, wannan ya bashi idea din yadda zai
yi ditching Safina ya ki tafiya da ita kamar
yadda iyayensa suke so. "She doesn't
have a visa, da kyar na samu tawa nima,
amma zan cigaba da processing tata from
there, I have someone da yake harkar visa
din nan. He will help", Farko Abba yaki
y yarda da shi amma da ya yi masa bayani a
nutse na cewa sunansa ne kawai akan
invite din meeting din, sannan kuma
tunda ba ta amfani da sunansa dan haka
it is hard to convince them cewa matarsa
ce, Daga baya dai Abban ya yarda, amma Mama ta san yana sane, sai dai kawai tayi
shiru ta rabu da shi.

And then two days to ranar tafiyar ta sa,
ya dawo gida da daddare kamar kullum,
ya shiga part din sa ya rufe kofa, ya kalli
kan dining table dinsa ya ga abinci kamar
kullum, ya karasa ya tsaya yana kallon
abincin and he saw a note a kusa da
plates din da ta jera "for all the hurtful
words you said to me, na yafe maka tun
kafin ka nemi yafiyar because I love you,
dan Allah yau dai kadai kaci abincina" ya
bude yaga tuwon shinkafa ne miyar
taushe. Ya mayar ya rufe sannan ya jona
electric jug din da yake dafa tea a ciki ya
shiga daki ya fara shirye-shiryen sa. A
ranar yake so ya hada kayansa, ya koma
dining ya zubo tea din sa ya dawo dakin
yana aiki yana shan kayansa har ya gama,
ya zuba kudi masu dan yawa a envelope
ya ajiye da niyyar ranar da zai tafi zai
ajiyewa Safina with a note saying in ta gaji
da zama ta tafi gida.

Yana gamawa yayi wanka yayi shirin bacci
ya kwanta, Sai dai me? Baccin ne ya
gagare shi, Wani irin yanayi yake ji da bai
taba jin irin sa ba, Farko ya dauka zazzabi
ne zai kama shi dan yadda jikinsa ya dauki
zafi gabaki daya, amma kuma maimakon
sanyin da ake ji in ana zazzabi shi zafi yake ji, wani irin zafi kamar babu iska a dakin, ya tashi da niyyar karo karfin ac amma sai yaji marar sa tayi wani irin
daurewa, ji yayi kamar jinin jikinsa
gabakidaya ya tattara ya dawo marar sa
ya tare. Kanshi yayi nauyi sosai yana sara
masa kamar zai tsage. Ya kwanta ya
lulluba da bargo sai kuma ya yaye bargon,
ya cire rigar jikinsa ya ajiye amma still zafi
yake ji. Da kyar ya tashi ya shiga toilet ya
sakar wa kansa ruwan sanyi, ya jima yana
jin dadin saukar ruwan sanyin a jikin sa
sannan ya fito ya koma ya kwanta ba tare
da ko ruwan jikin sa ya goge ba.

A haka bacci mai nauyi ya dauke shi. Cikin
baccin yaji motsi kamar an shigo dakin sa,
ya tashi da sauri yana jin ciwon kan yana
sake dawowa, a dai dai lokacin da Safina
ta fito daga toilet dinsa jikinta daure da
karamin towel din sa, kamar daga wanka
ta fito. Cikin takaici da mamaki yace
"what? What the hell are you doing
here?" Tayi pretending kamar ta tsorata ta
yar da towel din jikin ta, sai kuma ta
sunkuya ta dauka ta mayar ta daura "am
sorry Habibi na baka toro, zafi nake ji
kuma shower din toilet dina ta lalace" bai
iya ce mata komai ba har ta fita.

Ya koma ya kwanta rigingine yana kallon rufin dakin, kusan five minutes yana a haka sannan ya mike and went straight to part dinta straight to her room, kofar a
bude take fitila ma kuma a kunne, tana
kwance akan gadon ta wearing silky
doguwar rigar bacci with nothing inside.
He went in an switched off the light.

Sanda ya fito daga dakin he banged the
door with so much anger kamar zai karya
kofar, bai kuma koma bacci ba instead sai
ya tafi gym dinsa and punched the living
light out of his punching bag. Ji yake yi ya
tsani kansa, ya tsani Safina ya tsani kowa
including Safiyya.

Washegari da safe, for the first time in
history na auren su Safina bata kawo
masa breakfast ba but ko kallon inda
dakinta yake bai yi ba. Ya san ya kamata
ya duba ta, a matsayin sa na mijinta
especially after what happened between
then the night before, amma bai je ba ya
tafi office dinsa, sai da ranar aikin
gagarar sa yayi, a duk iyakacin kokarin sa
na ganin ya cire abinda ya faru tsakanin
sa da Safina da daddare amma ya kasa
¡ya cirewa,

A karshe sai ya tattara takardun sa yayi. wa mutanen sa sallama akan cewa tafiyar
da zaiyi ce ta saka zai tashi da wuri dan
yaje ya kammala shire shirye. Sai dai
yana zuwa gida part dinta ya dosa, bata
falo and he went straight to her room,
yana shiga ya tarar da ita ta fito daga
wanka, kallo daya tayi masa ta san abinda
ya kawo shi, sai da kayan cikin ta suka
kada saboda toro dan a lokacin ma da
kyar take daga kafarta. Amma sai ta
kirkiro murmushi, a gurin ta wanna wata
babbar nasara ce, maybe he will
appreciate her now.

But after he did what he came to do, buga
mata kofar da yayi yafi na daren jiya ma
karfi. Ta koma ta kwanta tana jin hawaye
yana bin fuskarta. He is everything she
had hoped and more, but this is nothing
she had imagined. Instead of love and
passion, what he gave her was anger and
hate. She expected hugs, kisses, smiles
and snuggles with a little touch of
passionate words. But she did not get
any. And when she draged her self out of
her room sai ta ga envelope a kuss da tvn
ta, with a handwritten note.

"Forget about what happened, Nayi
tafiya. If you cannot stay you can go"

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹


Episode Forty Three : Plan C


A ranar bai kwana a gidan ba sai ya tafi
daya gidan sa ya kwana a can. Ko kuma
muce ya kwanta a can. Dan baccin
gagarar idanunsa yayi. Shi ya san abinda
yayi ba laifi ya aikata ba but at the same
time it felt so wrong. Ya san ya bude wani
fejin da bai san yadda zai yi ya rufe shi ba.
He thought he had everything under
control zai cigaba da keeping Safina a
gidan sa har zuwa lokacin da zai samu
hujjar da zai gabatarwa da iyayensa
yadda zasu amince masa ya sallameta, ko
kuma ita zata gaji ta nemi sallama, shi
kenan komai zai kare with no strings
attached. But now he have attached the
strings. Amma shi kansa bai san ta yadda
ya kulla wannan zaren ba. Ta yaya? How? Why?

Kwata kwata ba zai iya bayanin ya akayi
hakan ta faru ba. Shi dai yasan yana da
lafiya a wannan bangaren, sosai, bai taba
vi ba but he have all the feelings na
mazantaka toward wacce yayi burin bude
wannan babin da ita, wanna yana daya daga cikin dalilan sa na matsa mata akan
maganar aure, but then one thing lead to
another and he found himself married to
Safina. And he lost all the feelings,
especially idan ya tuno da dangantakar ta
da Safiyya ko kuma idan tayi kokarin yi
masa tallan jikin ta. It disgust him. Rashin
class dinta yana daga cikin abinda ya
saka baya kallon ta a mace. The more da
take zubar da ajinta a gurin sa the less
yake mata kallon mace. Shi yaso ace idan
zai samu wannan abin sai ya nema
sannan a bashi da kyar bayan an gama ja
masa aji.

But that doesn't change the fact that shi
namiji ne ita kuma mace, and dole yana
da bodily urges wadanda yake kokari
wajan keeping on check. His desires have
always been under control and he was so
sure of himself yana ganin ba gida daya
ba ko daki daya ne zai iya kwana da matar
da baya so kuma ya tashi ba tare da yaji
ko gezau ba.

But what happened yesterday wasn't
normal. It wasn't natural. He had never
felt anything like that before in his entire
life, bai kuma taba tunanin akwai wani abu
irin wannan ba. It was scary, And totally
disappointing at the end. Desire din was
huge but the satisfaction was close to zero, wannan shi ya saka shi yayi wanting more but the more was even more disappointing. Ba zai iya kwatanta abin
ba, kamar karin maganar da Hausawa
suke cewa ga koshi ga kwanan yunwa.

Shi dai yasan dole akwai abinda yarinyar
nan ta yi mishi, yafi kuma tunanin cewa
asiri ne dan irin yadda take naci akan sa
tabbas zata iya yi masa asiri dan ta same
shi. Duk da dai ya san shi baya wasa da
addu'a, amma kuma asiri babu wanda ba
zai iya kamawa ba.

Abinda ya faru dai ya riga ya faru, yanzu
saura ya san menene zaiyi akan hakan.
Shin wannan abin da ya faru yana nufin ya
karbi auren sa da Safina kenan? But just
the thought gave him shivers, ba zai iya
imagining spending his entire life with
Safina as his life partner ba. Amma kuma
in ya sake ta babu laifin tsaye babu na
zaune even after what happened anya
Allah ba zai saka mata ba? Especially if
she is saying the truth about not having a
hand in rabuwar su da Safiyya.

But all that decisions will come after ya
gano what happened with him the other
night, idan har da gaske wan abun tayi
masa unnatural then ya tabbatar babu
abinda ba zata iya ba kenan. Wannan
kuma zai kara masa tsanar ta and may lead to their separation.

Washegari ya je gida yayi wa mahaifansa
sallama sannan Haidar ya kaishi airport ya
tafi.

And it has been over two months now da
tafiyar sa. Sau daya bai taba daga
wayarsa ya kira Safina ba. Tayi kiran har ta
gaji baya dauka. She sent him messages
zai karanta yay ignoring. She sent him
voice notes, sometimes crying and
expressing herself amma kamar da dutse
take. Abinda ya fahimta shine kamar after
what happened between them her
obsession with him increased. In one of
her vns ne ta gaya masa cewa bata da
lafiya and she thinks she is going to die.
Daga nan ya daina sauraran vn din ko ta
turo, ya fahimci tana son tayi gaslighting
dinsa to make him feel guilty. Yana aika Haidar ya kai mata kayan abincin duk da ake bukata a gida, ya
kuma bata kudin kashewa. On the other
hand kuma ya mayar da hankalinsa sosai
kan abinda ya kai shi. Sanda yayi watanni
biyu a can ne Mama ta kira shi tana yi
masa fadan wai ashe Safina bata da lafiya
amma duk wayar da suke yi kullum bai taba gaya mata ba, ta ce sai a bakin Mommyn safinan ta ji a gidan biki. Sai kuma ta fara zancen zata tafi da Safina
gurin ta ta zauna tare da ita har lokacin da
zai dawo. Dama tana ta kewar Mufida.
Wannan maganar ba ta yi masa dadi ba,
shi gani yake ciwon munafunci ne Safina
take yi dan ta ja hankalin sa da na
iyayensa kanta, yanzu gashi tayi nasarar
jan hankalin Mama kuma bai san irin
kissar da zata vi wa maman ba a zaman
da zasu yi tare kafin ya dawo. Wannan ya
sa ya fara rounding things up dan ya
samu ya dawo din amma abubuwa suka ki
yin sauri. Kullum a ransa tunanin Mama da
Safina yake yi together, kar taje ta gaya
mata wata maganar, kar taje tayi mata
wani abun.

Still har Safina tayi sati biyu a gidan su bai
samu dawowa ba.

Her🧕🏻

Ban san awa nawa na dauka ina yin
wannan baccin ba. Sanda na farka daga
yanayin hasken gari na fahimci cewa rana
tayi sosai. Na jawo waya ta da take gefena
na duba lokaci 1:30pm. Na tashi zaune
tare da jera adduoin tashi daga bacci
sannan na sake daukan wayar tawa na duba naga several miss calls, wadansu daga grin Daddy wasu kuma daga gurin Uncle Ahmad. Nayi ajiyar zuciya. This is going to be a very long short day for me.

Na koma na kwamta rigingine ina kallon
saman dakin, thinking, saboda nayi bacci
mai nauyi sai naji kwakwalwa ta ta ware
sosai and every thing looks clear to me.
Na gama planning din abinda zanyi.
Babban matsala ta shine Daddy, bana son
ransa ya baci ko kadan kuma na san dole
ran nasa zai baci, I wasn't looking forward
to breaking the news to him dan na
tabbatar it will break him down. Yes, baya
son Mukhtar amma kuma Mukhtar dan
dan uwansa ne. Kuma babban abinda zai
kara masa damuwa in all this shine the
fact that bai yarda da ni ba when I told
him I was raped, in fact har yau bai yarda
cewa I was raped din ba.

Na tashi zaune ina murmushin jin dadin
halin da na bar Mukhtar a ciki. Na san
zuwa yanzu jikinsa yayi tsami ba kadan
ba, amma kuma na sam duk tsamin da zai
yi ba zai kai yadda nawa yayi a lokacin da
ya aikata min abinda ya aikata min ba. Sai
dai kuma nay mamakin kiran uncle
Ahmad da na Daddy da na gani. Kar dai
ace har sunje gidan sin ganshi? Ba zanji
dadi ba idan haka ta kasance saboda ina sane na barshi yayi hours a daure dan ya dandana yaji, kuma ina son in zama wadda zata yi breaking news din to them.

Na lalubo number din Yaya a waya ta duk
da yadda the nutty part of me yana zuga
ni in kira Umma ko Abba. Na yi dialing
number din bai jima ba ya dauka "hello
Fiyya, ina kuka shiga ne ke da mijin ki?"
Ban amsa tambayar ta sa ba nace "kana
i ina ne?" Dan naji kamar a hanya yake,
yace "ina hanyar gidan ku. Abba ne yace
inje in duba ku wai ana ta kiran wayoyin
ku ba'a samu" nace "alright. Shikenan
ma. Da ma zance maka kaje gidan ne
gurin Mukhtar. Ni bana nan naje gida. In
kaje don't bother knocking kawai ka
shiga" daga nan na katse kiran dan nasan
tambayoyi ne zasu biyo baya.

Daga nan sai na kira Daddy, shima tana
shiga ya dauka and his sick voice sounds
worried "Safiyya? Ina kika shiga? Malam
Ya'u ya kira ni tun da zu yace wai kinzo
gida da asuba, Kuma nayi ta kiran wayoyin
ku ke da Mukhtar baku dauka ba. Allah ya
sa dai lafiya kike" na sassauta murya ta
sosai "Daddy lafiya lau nake, kar ka damu
da ni" yace "damuwa kam ta zama dole
Safiyya, as parents it is our job to worry
about our children. Musamman make. Me kike yi a gida? Me yasa kika fita daga gidan mijinki da assuba? Da wani abun ya same ki fa? Ko fada kuka yi?"

Na yi shiru ina jujjuya maganganun a
raina, bana son gaya masa a waya dan
bansan yadda zai yi reacting ba, bani da
tabbas din kuma akwai wani a tare da shi.
Nafi son muyi magana face to face da shi
yadda zanfi iya controlling emotions din
sa nace "Daddy lafiya ta kalau. Kuma ina
gida kamar yadda Baba Ya'u ya gaya
maka. Ka tuna abinda nace maka ranar da zan
bar Kano? Nace maka everything will be
okay? To akan maganar ne, things are
beginning to be okay. In anjima kadan
uncle Ahmad zai kira ka, Please Daddy
duk abinda zai gaya maka kar ka tayar da
hankalin ka, kamar yadda na gaya maka I
am okay kuma I am safe a gida. Zamuyi
maganar as soon as I come to Kano"

Ya yi shiru, farko na dauka ma kiran ya
katse sai kuma naji yace "kar ki fita daga
gidan, I will be on the next flight to Abuja".
Sai ya katse kiran, Na ajiye wayar tare da
dafe kaina, Kamar yadda ya fada haka ne
it is parent's job to worry about their
children, but I don't want him worrying about me, especially in his condition.
Amma kuma na san a karshe idan aka
gama maganar ya fahimci komai
damuwarsa zata ragu sosai zai ji dadi
sosai dan zai gane cewa ban aikata
abinda yake tunanin na aikata ba, zai
kuma kara fahimtar cewa I am capable of
taking care of myself ko da bayan baya duniya.

Na tashi na shiga wanka, ina wankan ina
jin waya ta tana ta kara amma I took my
time nayi wankana a nutse dan na san ba
Daddy bane ba, na fito na shirya nayi
sallah sannan na bude dakin na sauka
kasa, ina sauka naga Esther, ta taho
gurina da sauri tana gaishe ni tare da bani
hakurin rashin samunta da banyi ba a
gida, I smiled at her and asked her to get
me something to eat, bata jima ba ta
dawo, daga alamu ta yi dama already tun
kafin in tashi.

Na zauna a kasan hoton Ammi naci abinci
nana koshi, sannan na kuma dauko waya
tana duba, missed calls from Yaya, uncle
Ahmad da kuma shugaban marasa kunyar
duniya, Mukhtar, Banyi returning kowanne
call ba na kunna tv na cigaba da zama na
a falo yayin da Esther take aikin gyara min
dakina. Har la'asar sannan na tashi na
koma saman na tarar da gyara komai dakin sai kamshi yake yi. Navi sallah na
sake fitowa na tarar har ta gama lunch
tana jerawa a dining. Nayi mata sannu sai
ta ce min ai Mommy ta kira ta a waya tace
gasu nan zasu taho. Na koma na zauna
kawai ina kallon hoton Ammie, wato har
yanzu Mommy bata huce da ni ba tunda
bata kira ni ba sai ta kira Esther.
Ina da zaune a gurin sai ga kiran
Mustapha, na dauki wayar ina kallon
number din sa, yaushe rabon da muyi
waya da Mustapha? Bazan iya tunawa ba.
Na dauka na saka a kunne na "Fiyya
Daddy yace kar ki ce zaki zo daukan mu,
zamu taho da motar airport" "to" kawai
nace masa na ajiye wayar ina jin wani iri a
raina. He sounded just like the voice that
called me that day. Shin da bakin sa a
cikin maganar nan ko kuma he is innocent
framing dinsa Mukhtar yayi?

Tun yarintar mu na san Mukhtar da
Mustapha ba sa shiri, in dai suka hadu sai
sunyi fada kuma lokuta da dama a kaina
ne suke yin fadan dan Mukhtar ya fahimci
cin zalina da Mustapha yake yi shi kuma
tunda ya fi shi karfi sai ya rama min, daga
baya bayan sun girma sai suka dore a
haka, not just about me basa jituwa sam,
they disagree on everything. Bana jin
zasu samu agreement on raping me, it
iust doesn't make sense. musamman yadda a dai dai lokacin da abin ya faru Mustapha da Mukhtar sun cikin heated rivalry akan son aure na.

Nayi ajjiyar zuciya tare da ture tunanin da
ga zuciyata, ko ma menene Mukhtar zaiyi
bayani da bakin sa dalla dalla.

Ina nan dai zaune naji an bude gate
sannan naji tsayuwar mota. Na mike tsaye
ina kallon kofar. Mustapha ne ya fara
shigowa, ya tsaya yana kallona kamar
yadda nima nake kallon sa, kamar zai ce
wani abu sai kuma ya juya ya koma da
sauri. Yana fita Mommy ta shigo, sannan
Mustapha ya sake dawowa tare da Daddy.
Gabakidayan su yanayin su ya nuna cewa
suna cikin damuwa. Mommy ce ta fara
magana "Safiyya me ya same kike kuwa?
Da gaske ne abinda Ahmad ya gaya mana
wai kin tozarta mijinki irin haka? Ki tube
mutum tsirara ki daure shi akan gado?
Mijin ki fa Safiyya?" Muka hada ido da
Mustapha and I saw yadda yake kokarin
hana kansa dariya, nayi kamar ban ganshi
ba na fara kokarin yiwa Daddy magana
"Daddy sannu da zuwa" ya juya kujerar sa
zuwa hanyar part dinsa ace "zamuyi
magana in an jima, Sa'adatu kar ki tayar
da maganar nan", Mommy ta bishi da kallo sai da ta
tabbatar ba zai ji ta ba sannan tace "yaya
zanyi kuwa ba zan tayar da magana ba. Ni
na san da akwai wata a kasa kuma dole in
bincika inj'" ta juyo kaina" Me yayi miki?
Yanzu muma sauka naji Ahmad yana yi
masa waya wai ga abinda kika yi wa mijin
ki, kaninsa yaya ne yaje ya ganshi a hakan
ya kira iyayen. Gaya min inji me yayi miki".

Uncle Ahmad ne ya shigo falon kamar an
jefo shi. Yana shigowa muka hada ido and
he gave me just the look that I expected
him to give me sannan ya fara magana
"ina Yaya? Ina bukatar ganin sa yanzu
yanzun nan?" Babu wanda ya amsa masa
sai yayi hanyar shiga part din Daddy,
Mommy ta daga murya "dakata dakata,
yace kar wanda ya shiga gurin sa
tukunna. Yanzu muka sauka hutawa zai yi
sai anjima za'a yi maganar" ya juyo a
fusace yana nuna ta da yatsa "ke
Sa'adatu ki fita daga ido na. Ke kin isa zan
ga danuwana ki gaya min yaushe zan
ganshi ko yaushe ne ba zan ganshi ba?"
Kafin tayi magana Mustapha ya tsaya a
gabanta yana kallon Uncle Ahmad yace
"sauke wannan hannun da ka daga"
Uncle Ahmad ya saki baki da mamaki,
daga alama bai taba tsammanin haka daga Mustapha ba yace "ni kake kallo
cikin ido kake cewa in sauke hannun na?"
Mustapha yace "exactly. Kana mamaki
ne?" Uncle Ahmad yace "idan ban sauke
ba kuma fa? Me zai faru?" Mustapha yace
"sauke maka shi zanyi kawai. Shine
abinda zai faru" Uncle Ahmad yace "lallai
yaron nan ka cika marar kunya. Ni lake
gaya wa magana irin haka? To wallahi
kasan ina da yayan da da hannu daya
zasu iya karya min kai kamar rake"
Mommy ta fara jan Mustapha "rabu dashi
Mustapha. Neman wanda zai huce a
kansa ya ke yi kar ya huce a kanka" Uncle
Ahmad ya taba kofar Daddy yaji a rufe sai
kuma ya dawo yazo inda nake ya nuna ni
da hannu "ke kuma!" Sai kuma ya girgiza
kansa "ban ma san me zance miki ba. Kin
bani mamaki" daga haka sai ya juya ya
fita.

Mommy ma tazo ta wuce ni ta hau sama
tana cigaba da mita "haka kawai. Zaka 20
kana mana hayaniya a ka. A bari mana a
tambayi yaran aji menene ya hada su?"

Ni dai na koma na zauna tare da rufe
idona. It has started. Ban san kuma
yaushe zata yi ending ba, Ina bude ido na
muka hada ido da Mustapha, yana tsaye a
jikin kofa yana kallona. Na mike na dauki
jaka ta zan hau sama sai ya kira sunana "Fiyya" na tsaya amma ban juyo ba sai
yace "da gaske ne abinda aka ce kin yi
masa? Da gaske ne kin rubuta masa
"RAPIST " a goshinsa?" Na juyo ina kallon
sa sai ya daga kafada yace "haka naji
Daddy da uncle Ahmad suna fada a waya"
ya dawo da baya ina kallon sa nace
"menene naka a ciki? Huhh? what do you
want?" Ya gyara tsayuwa
"nothing.….…..kawai dai kin san ni yayan ki
ne and I care about you duk da kiyayyar
da kike yi min. I know we have had our
share of problems a tsakanin mu. Ki gaya
min abinda yayi miki, kin san Daddy yanzu
cewa zai yi kiyi hakuri, ni kuma in kika
gaya min nayi miki alkawarin zan dan
farfasa masa baki ko hakora uku ne in ciro
in kawo miki. Maybe to make up for my
mistakes" na nuna shi "nothing will make
up for your mistakes" ya daga kafada
"okay okay, don't shout. Naji. Allah ya
gani ina kokarin ganin mun daidai ta ke
kuma kin ki. Any time you need me just
call me" ya juya zsi fita, Har ya kai bakin
kofa sai kuma wani tunani yazo min and I
called his name "Yaya Mustapha" ya juyo
and I saw a smile on his face, na taka
zuwa gabansa na tsaya muna kallon juna
nace "I want to ask you something. Ansar
da zaka bani kuma zata yi matukar tasiri
gurin gyaran tsakanin mu. Ranar da kuka
dawo daga Cyprus kai da Daddy, ranar da ka yi min sharri kace ina yin shaye shaye,
ka kira ni a waya kace in zo Daddy bashi
da lafiya?" Ya dan bata fuska yana kallona
yace "kamar kin taba yi min wannan
tambayar, ko kuma Daddy ne? Ni ban kira
ki a waya ba, ta yaya zan kira ki a waya
alhalin ina cikin jirgi tare da Daddy?" Na
gyada kai na "are you sure? This is very
important" yace "I am sure. Menene wai?"
Na koma da baya na zauna akan kujera
nace "kasan wata hanyar da za'a iya bi a
kwaikwayi muryar mutum a waya?" Ya
dawo tsakiyar falon ya a kallo na yace
"technology yanzu babu inda bai je ba
Fiyya. Ba murya ba har kamannin mutum ana iya
cloning, why are you asking this
questions" na dora kafa daya akan daya
nace "on the 13th of sep last year, around
karfe takwas na dare, someone called me
with a new number and called himself
Mustapha, ya kuma yi magana da irin
muryar ka sak, da na fito he attacked me,
drugged me, kidnapped me and
•.........
Nayi shiru ido na yana kallon sa ban
karasa ba, ya sauke rungumar da yayi wa
hannayen sa fuskarsa tana nuna fahimtar
magana ta, ya karasa min "and raped
you" na gyada masa kai ina jin hawaye
yana zuwa ido na. Yayi shiru yana kallon hawayen ido na daga gani one and one
yake hadawa a kansa and I saw sanda
labarin ya gama haduwa a cikin
kwakwalwar sa "that bastard!" Ya fada da
dan karfi. Nayi sauri na mike kar ya hada
min mutane, ya cigaba "it was Mukhtar.
That bastard. Shine and he tried to frame
me. He used my name and my voice
saboda ya san bama shiri dan kiyi zargi
na. He knows Daddy bashi da lafiya he
probably knows ranar zamu zo gari. He
raped you and framed me. Wallahi sai
naci kan bu** ub* sa" yayi hanyar waje da
sauri ni kuma na bishi na jawo rigarsa tare
da tare hanya.
"me kike yi haka? You still
want to defend him?" Nace "no.... Babu
abinda nake bukata yanzu irin justice for
what he did to me. Za su zo in an jima.
will have my Justice then you can do
whatever you want with him. Kar kaje
yanzu kayi masa illar da zata bashi damar
playing the victim card. Let me finish with
him first then you can have him".

Yayi shiru yana kallona, sai kuma ya gyada
kai, Fuskarsa tana nuna tsananin bacin
rai. Na matsa na bashi hanya ya wuce
sannan nima na koma dakina,

Ina dakina har aka yi sallar magrib nayi
sallah sannan na cigaba da zama ina kallon agogo. A lokacin kiran Mukhtar ya
sake shigowa cikin waya ta, na bishi da
kallo har ya katse wani kiran ya sake
shigowa, a haka har ya kira sau biyar sai
kuma ya tiro min message "please Safiyya, we can still fix this. Kar muyi wannan maganar a gaban iyayen mu. I still love you with all my heart dan Allah" na
karanta na mayar na ajiye wayar.
Har na fara fitar da ran za'a zo kirana sai
ga kiran Mommy ya shigo wayata. Na
daga na saka a kunne na sai tace "ki zo
muna falon Daddy" na tashi dama da
hijab din da nayi sallah da shi a jiki na na
dauki jakata making sure abinda nake
bukata yana ciki sannan na fita daga
dakin.

Ina shiga falon na gansu gabakidayan su a
zazzaune. Daddy, uncle Ahmad, Mommy
da kuma Umma. Sai Mukhtar a kasa a
kusa da kafafuwan Umma, ya dago kai ya
kalle ni sannan ya dauke kansa. Nayi
sallama na shiga na zauna nima a kasa
kusa da Mommy, Ban gaishe da kowa ba,
Shiru babu wanda yace komai na dan
wani lokaci sai kuma Umma ta fara
magana "wannan wanne irin wulakanci
ne? Babu yadda da ma banyi ba akan kar
ayi auren nan amma aka nuna min ni bare
ce wai za'a rufa wa yan uwa asiri, gashi nan kum rufa mata asirin ita kuma ta bankada muku naku a duniya. Dama ba sa'ar auren sa bace ba. Tafi shi kudi ta
fishi budewar ido da wayewar duniya.
Babu bangaren da idanun ta basu bude akai ba. Yanzu gashi ." Mommy tace "yanzu gashi magana ta dawo baya. Tunda ta kira shi da rapist kuwa ai
magana ta dawo baya. Yanzu ba mu da
tabbas din wanda aka rufawa asiri da
wanda kuma ya rufa wa wani asiri. Sai mu
tsaya mu saurare ta muji abinda ya saka
ta gaya masa haka....".

Daddy yayi gyaran murya "zaku tsaya muyi magana ne ko kuma ku zaku vi maganar? Idan ba zaku yi shiru ba ku fita" na daga kai jna kallon sa and he looked
older than I knew, kamar shekaru sun
karar masa akan wadanda yake da su. Sai
naji banji dadin putting him through
wannan ordeal din ba amma kuma dole ce
ta kawo hakan.

Ya kalli Mukhtar yace "kai be babba. Me
ya faru?" Mukhtar ya dago kai yana
kallona,. Na dauke kai na kalli gefe sai naji
ya fara magana "kun san dama ba so na
take yi ba, Dole ce ta saka ta aure na, To
tunda akayi auren da ma
bata……..bata…..…..batayarda…………da……..daniba,
Na fahimci hankalin ta yana kan wani
tsohon saurayin ta da take so. To sai jiya….

nayi kokarin gain mun daidaita auren mu
mun samu fahimtar juna ita kuma taki
yarda, sai nayi kokarin gain na fahimtar
da ita, ashe ta ajiye allurar bacci a tare da
ita, shine tayi min allura" ya fada tare da
fito da syringe din da nayi masa allura da
shi ya ajiye a gaban Daddy. Ya cigaba
"daga nan ban san me ya faru ba sai farka
wa nayi na ganni ni kadai a dakin cikin
halin da Yaya ya tarar da ni. Ban san ma
tayi min rubutu a fuska ba ban kuma san
dalilin da yasa tayi haka ba". Umma tace "to kunji dai
Dama ai an gaya mana tana shaye shaye, shine ta tafi
da kwaya tayi masa allurar ta. In ba yi take
yi ba a ina ta samu? A ina za ta samu?" Mommy tace
"munji bangare daya saura daya bangaren. Kiyi shiru dai tukuna kar kizo kiji kunya. Wannan shawara ce na
baki kyauta" Umma tace "Mukhtar dai
wannan wallahi na san tarbiyyar da na
bashi kuma ko a gaban wa zanyi shaidar sa.....
." Mommy tace "ni ma na san tarbiyyar da na bawa Safiyya amma ba zanyi shaidar ta a gaban mutane ba sai dai in barta tayi proving tarbiyyar tata da
kanta. Ba'a shaidar yayan zamani, Wannan ma wata shawarar ce na baki kyauta".

Cikin fada Uncle Ahmad yace "kunji kunya
dai kam wallahi. A gaban yayan ku kuna
fada kamar kaj'" sai ya juyo ya kalle ni
'"muna jin kike kuma. Ga abinda mijin ki
yace. Me zaki ce akan hakan?" Kafin inyi
magana Mukhtar ya cigaba "Abba ni dai
ina son matata. Duk abinda ya faru
kuskure ne da rashin fahimta a tsakanin
mu. Ina rokon a bamu dama mu tattauna a
tsakanin mu mu daidai ta. Ni dai ina son
matata kuma na yafe mata abinda tayi"
Umma ta rafka salati "la ha ila ......
... Kaji shanyayye" Mommy tayi dariya "kunya ta
farko ta tabbata" Daddy yayi magana "ba
zaku yi shiru din ba kenan? In ba ku ji
maganar mu ba ta yaya kuke tunanin su
zasu ji maganar mu?" Uncle Ahmad ya sake ce min "muna jin ki Safiyya, kinji abinda mijinki yace, ko zaki
iya kare kan ki?" Na mike tsaye na dawo
tsakiyar su sannan na juya ina kallon
Mukhtar nace "na gaya maka tun a jiya. It
is going to be your words against yours
not mine" sai na dauko wayata daga
jakata and I played the audio of
maganganun da muka yi da shi that I
recorded, maganar ta fara ne tun sanda ya farko "safffiyya. Me kika yi min . And it ended with "no, it is going to be your words against yours"

Duk da akwai maganganun kunya a ciki
amma banji kunyar su ba haka na bari
suka ji komai. Suna gama ji na dauki
wayata na koma inda nake zauna na
zauna. Mommy ta kama salati "la haula
wala..Yau naga abinda yafi karfina ni
Sa'adatu" Uncle Ahmad ya mike tsaye
"Mukhtar! Ka gaya min cewa ba kai bane
ba kake magana a cikin wayar can, gaya
min cewa ba kai bane ba" Umma tace
"'uhm uhm. Ku barshi yayi magana dan
Allah, na tabbatar yana da bayanin da
zaiyi mana. Na tabbatar akwai explanation
to all these" Mommy tace "wanne bayani
bayan wanda muka ji? Ko kuma ba
muryarsa bace wannan? Ji nake yanzu ya
gama cewa shi da ya farka ma bai ganta a
gidan ba already ta tafi. Ko cikin bacci
suka yi wannan maganganun?"

Mukhtar gabaki daya ya rikice, ac ce a
falon amma gumi yake hadawa kamar anyi
masa wanka "Abba wallahi. ...... Daddy ka
tsaya kaji ... Umma na rantse ....."
''Wallahi me? Fadi abinda zaka ce mana" yace
"Abba she drugged me, Yarinyar nan ta
wuce duk inda kuke tunani. Trap ta hada
min. She threatened me. Scissors fa ta dauko tace zata yi min illa, kuna jin ta fa a cikin maganganun. I told her what she want to hear dan kar ta illata ni. Amma
karya take yi min Abba. Ni ban san komai
akan abinda ya faru da ita ba. Dan Allah
Abba ka yarda da ni".

Na rufe ido na ina jin zuciya ta tana
tafasa, na bude na kalli Daddy naga yana
zaune ya dafe kansa sai maimaita salati
yake yi shi ya kasa ma magana. Na sake
kallon Mukhtar naga yadda ya dage yana
ta jera wa iyayensa karya da fatan lallai sai
sun yarda da shi. Sai naji Abba yace "biri dai kam yayi kama da mutum. Idan har abinda ya faru da ita
kenan da tuntuni me yasa ba ta fada ba
tun a lokacin sai yanzu tukunna? Me yasa
ba ta ce tana zargin sa ba sai ta amince ta
aure shi dan ta makala masa wannan
sharrin? Me yasa da farko da yace yana
son ta ta ki shi sai daga baya kuma da
kanta tace tana son auren sa, ya kamata
mu duba wannan maganar, Yaya ya
kamata muyi dogon bincike kafin mu
yanke hukunci",

Mommy tace "amma me yasa yayi karya?
In yana da gaskiya me yasa yace bai ma
san sanda ta bar gidan ba bayan gashi munji sai da suka yi maganganu kafin ta fita?"

Suka cigaba da maganganun su yayin da
ni kuma na kwantar da kaina kawai akan
kujera ina jin su, na fahimci iyayen
Mukhtar gabaki daya kokari suke yi sai
sun kare dan su sun ce sharri nayi masa,
ni kuma nawa ban ya kasa cewa ma
komai saboda rashin lafiya sai fuskar sa
da take nuna tsananin damuwa, sai
Mommy ce kawai bakin ta yaki yin shiru
sai kokarin mayar wa da su uncle Ahmad
maganganun su take yi. Na bude ido na
ina kallon su, a raina nace plan C it is.

Sai na jawo jakata ba tare da sun lura ba
na dauki scissor dina na boye a cikin hijab
dina na mike tsaye na fara magana. "okay
shikenan. Yanzu kunce sharri nayi masa.
Gashi kunji da bakinsa ya fada amma
Umma tace "me muka ji ya fada? Dauko
wayar ki sake kunnawa. Ni dai banji inda
ya amsa yayi wanna mummunan abun
ba" nace "ba zaku yarda ba dama. Ni na
san ba zaku yarda ba. Wai kuma a haka
Daddy yana da rai kenan. Idan babu shi
kuma fa? Me zai faru idan babu shi?"
Uncle Ahmad ya mike a zuciye "ke
Safiyya ki shiga hankalin ki, kar ki gaya
mana maganar banza. An gaya miki kudi
hauka ne da zaki saka mu a gaba kina daga mana murya da maganar banza alhalin mu iyayen kine?",

Na girgiza kaina ina jin hawaye yana bin
fuskata "maganar banza. Maganar banza
kake cewa uncle" na juya ina kallon
Mukhtar da dacin rai nace "you took
everything from me. Duk abinda na
mallaka, duk abinda nake takama da shi
sai da ka raba ni da shi, mutunci na a
matsayi na na ya mace, daraja ta a cikin
al'umma, soyayya da amincin iyayena, my
confidence, my good image, saurayina xa
nake so fiye da komai sai da ka raba ni da
shi saboda abinda kayi min, you almost
took my sanity dan sai da na kusa
zaucewa saboda bakin cikin abinda kavi
min and I promised you tun a lokacin
kuma yanzu ma a gaban iyayen mu ina
maimaita maka, i will take away
everything from you too ko da kuwa duk
abinda na mallaka zai kare akan hakan.
Bayan na gama nawa kuma I will make
sure you get the highest sentence da za'a
¡ya yiwa rapist a Nigeria".

Gaba daya duk sunyi shiru suna kallo na,
ni kaina ban san cewa da karfi nake
maganar ba sai da nayi shiru. Hawaye ne
kawai yake bin fuskata ina zagaye su, Sai
na saka hannu na share hawayen fuskata
a dai dai lokacin da na tsaya a saman kan
Mukhtar da yake zaune a kasa a gaban mu.

Ba tare da sun lura da abinda yake faruwa
ba kawai sai na durkusa na damki gashin
kan Mukhtar na yanka da almakashin
hannuna, making sure na dan yanke shi
kadan. Ya zabura saboda zafi ni kuma na
mike da gashin sa a hannuna. Na nuna
masa almakashin hannuna nace "I told
you zanyi amfani da shi dama. Ga abinda
zan yanka nan" na koma inda na ajiye
jakata na bude na dauko ledar da na ajiye
a ciki ta ziplock na saka gashin a ciki
sannan na ajiye ta a tsakanin uncle
Ahmad da Daddy nace "zan kawo muku
na yaron da na haifa. Run a DNA test ku
gani idan ba nashi bane ba. Idan kunyi
baku yarda ba ku sake asibiti ku sake yi
and I assure you ko sau dari zakuyi zaku
ga 100% compatibility. Dan sa ne".
Mukhtar ya mike yana kallona, daga
dukkan alama maganar da da nayi ta
mantar da shi zafin yankar sa da nayi,
yace cikin kidimewa "you told me he is
dead" na daga kafada "I lied" na koma na
zauna, Daddy yayi magana murya can
kasa "wanne irin dead kuma? Yaushe?
Jiya mana ganshi on a video call". Mukhtar ya zame saura kadan ya fadi sai ya zauna akan kujera tare da dafe kansa, cikin karyewar zuciya ya sake cewa "you
told me he is dead" na sake maimaita wa
nima "I lied", Daddy ya saka hannu ya
dauki gashin Mukhtar da na ajiye a gaban
su, sannan ya dago kai yana kallon
Mukhtar din fuskar sa cike da emotions
da ba zan iya kwatantawa ba yace "idan
har ta tabbata kaine Mukhtar. Idan har ta
tabbata kaine, wallahi, wallahi, sai na
tabbatar da cewa kayi nadamar zuwa duniya".

Ya zame daga kan kujerar da yake kai ya
sauko kasa, in ka ganshi zaka dauka
sanarwar cewa Umma ta mutu aka kawo
masa. Ya bude baki ya kai sau biyar amma
ya kasa furta komai. A karshe sai yace
"Daddy..... Abba ..... Dan Allah.…”

Na mike ina kallon sa nace "I will see you
in court" har zan fita kuma sai na juyo na
nuna uncle Ahmad nace "kai kuma ka
dawo min da kudin da ka sata nan da one
week ko kuma ka kawo min resignationletter din ka".

Na juya na fita, Yes, I know that last part
was petty and uncalled for but I didn't
care. I was beyond caring.

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹


Episode Forty Four : Betrayed


Not edited….

Dakina na koma da sauri kamar wadda
ake hankada, ni raina a matukar bace. Yes
na san dama iyaye suna son yayansu and
it is only natural for iyaye to choose yayan
su over every one else, but that should be
on something not as serious as this.
Sanda abin ya faru da ni musamman
sanda maganar cikina ta bayyana every
hand was pointing toward me akan abinda
ni nasan bani da laifi akai amma babu
wanda ya yarda da ni, to me yasa yanzu
ba zasu juya hannun su nuna wanda yake
da laifin ba sai suke neman shield din da
zasu kare shi da shi? Me yasa ni lokaci
daya aka yarda nayi laifin amma shi ba
za'a yarda yayi ba?

But they are all in for a surprise.

Zasu sha mamaki na ba kadan ba.

Dan tabbas Mukhtar sai ya girbi abinda ya shuka sai dai in lahira zasu kai shi su boye shi. In can din ma suka kaishi walakiri yana can yana jiran shi, dan ban yafe masa ba kuma ba zan taba yafe masa ba.

Na shiga dakin na koma na zauna akan
kujerar da na tashi daga kanta ina mayar
da numfashi. Babu wanda zai fahimci
abinda nake ji a zuciya ta sai wanda ya
taba shiga cikin irin halin da nake ciki.
Babu kuwa wanda nake yiwa fatan ya
shiga irin halin da na shiga a rayuwata. Na
sha wahala. Na wahala ba kadan ba. The
pain and trauma of the rape was the
easiest part, sharrin shaye shaye da
Mustapha yayi min, kin yarda da ni da
Daddy yayi da kuma yadda maganar ta
fara kokarin juye wa zuwa kan
Muhammad duk ba sune worst abinda ya
fi bakanta min ba. My life got totally
destroyed lokacin da na fahimci ina da ciki.
. . . . .


11 months ago

Immediately after the night to
remember…..

Ba makaranta ba, a Abuja ma Daddy bai
barni ba ya dauke ni muka koma Kano tare, a lokacin babban tashin hankali na
shine Muhammad, na san yana can cikin
damuwa akan bacewar da nayi na barshi a
ranar da na saka masa rai na kuma yi
masa alkawarin zan kaishi wajen
mahaifina. I tried calling him amma sai na
kasa saboda babu abinda na wuni a ranar
ina yi sai kuka, muryata har dashewa tayi,
kuma yadda muke da fahimtar juna ni da
shi na tabbatar yana jin murya ta zai san
wani abu ya faru da ni, ni ma kuma na san
ina jin muryarsa zan sake wani kukan dan
it will remind me of all the love and the
promises da muka yi wa junan mu. Dan
haka sai na tura masa text, na gaya masa
cewa bayan ya fita aka kira ni cewa Daddy
sun zo amma jikin sa ya tashi, shi yasa na
tafi na barshi dan hankali na ya tashi. And
I forgot my phone in the car shi yasa ban
dauki kiran sa ba. Nace masa kuma da
muka kwana a asilitin jikin baiyi dadi ba
sai muka sake fita dashi da ga kasar, shi
yasa ba zai same ni a waya ba ko ya kira.
Daga nan na rufe dukkan sims dina yadda
ko ya kira ba zai samu ba. But I cried after
that, just the thought of him yana kara
sakani bakin ciki da bacin rai. Tun a
lokacin naji na fara tunanin rabuwa da shi.
A ganina bai yi deserving a used rug like
me ba, Tun kafin muje kano Mommy ta samu
labarin wai na zo gida a buge kuma
bincike ya nuna cewa saurayi ne yaje makarantar mu ya dauke ni ya fita da ni. Na kuma san wanda ya bata labarin....

Abinda ta fara saka ni a gaba da tambaya
muna zuwa gida shine waye saurayin
nawa?

"'Wanda kika ce zai zo gurin Daddyn ku
ne? Dama ba mutumin kirki ba ne ba
Safiyya? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun,
abinda kika zama kenan Safiyya?"

And then…..

"Na gaya maka dama baban Mustapha,
yarinyar nan aure za'a yi mata kaki yarda.
Tun da ta nuna auren ta ke so to ai auren
ya kamata ayi mata. Ga Mustapha nan
yace yana son ta amma daga kai har ita
kun nuna ba kwa son abin. Gashi nan ai ta
fara kula wadanda ba mutanen kirki ba.
Bayan ga wannan wanda kai kayi tarbiyyar
sa da kan ka". Naji kamar zuciyata zata kama da wuta,
Wata irin tsanar Mustapha tana kara shiga
ta. A zuciya ta ina kara tabbatar wa da kaina
cewa shi ya aikata min wannan aika aikan dan ya cimma burinsa, dama ya jima yana
nema ya ga tabbas ba zai sa mu ba, ya
shigo da maganar aure ba dam yana so
na da gaske ba sai dan kudin da yaji an
ambata a matsayin nawa, shima kuma ya
ga babu nasara ta wannan bangaren shi
yasa yayi min wannan abun, sannan kuma
ya kala min sharrin shaye shaye, dan a
matsamin dole in aure shi shikenan ya
samu riba biyu. Ni kuma tun a lokacin nayi
rantsuwa a raina cewa ko mazan duniya
zasu kare ba zan aure shi ba. Na kuma
rantsuwa cewa sai na tona mass asiri.
Amma kafin in tona masa asirin ai dole sai
na bayar da labarin abinda ya faru da ni
sannan in shigar da maganar wanda nake
zargi. Amma kuma maganar tayi min
nauyi da yawa a bakina, a zuciya ta. A
cikin first few weeks da faruwar abin na
gwada bude bakina in fada yafi sau a
kirga amma sai dai in mayar da bakin in
rufe ba tare da na fada din ba saboda
maganar taki fitowa, Magan6ce da bazan
iya yin ta da Daddy ba duk kuwa da
shakuwar da take tsakanin mu, ita kuma
Mommy da ya kamata inyi maganar da ita
dan ta nake zargi da aikata min wannan
abun dan haka ita ma sai ma kasa bude
bakina in gaya mata,

Sai dai kuma tun da abin ya faru sai na rasa lafiya. Farko tsananin
ciwon jikin da ma dangantashi da abinda
ya faru, sai kuma ciwon kan da nayi
tunanin tashin hankali ne da bakin ciki ya
saka min shi, daga nan bayan sati biyu sai
abin ya wuce ya zama zazzabi. Mommy ta
kaini asibiti suka yi min gwaje gwaje suka
bani magunguna har da su karin ruwa,
kwana na biyu aka sallame ni na dawo
gida na fara pretending kamar na warke
saboda yadda nake tsoron allura, amma
kuma sam ban warke ba din, tun ina boye
ciwon har na kasa na cigaba da bayyana
shi aka sake mayar da ni asibiti, suke
typhoid suce malaria haka dai muka yi ta
fama. Haka na cigaba da zama a gida ina jinya
ta ina kallon Safina tana zuwa makarantar
ta ni kuwa an rabo ni da tawa makarantar
kuma babu ma zancen komawa ta ko
kuma sake min wata. Daga cikin tashin
hankalin da nake ciki a lokacin shine
maganar Muhammad, ga mamaki na ya
yadda da karyar da nayi masa, da na
samu mukayi online call ma he sounded
so genuinely concerned about jikin Daddy
har yana tambayar in akwai abinda zai iya
yi to help. Sai kawai na saka masa kuka,
ina tausayin sa ina kuma tausayin kaina.
Ina kuma jin haushin kaina akan karyar da
nake ta shirga masa, amma abinda ya faru
da ni abu ne da budurwa ba zata iya bude baki ta gaya wa saurayin ta ba.

Through all these emotional rollercoaster
da nake ciki I missed my period ba tare da
na fahimta ba sai one week after lokacin
da ya kamata in ga period din, ranar da
nayi realizing na shiga toilet ne da niyyar
yin wanka na shire kayana kenan and I
noticed change a kirjina, farko ban yi wani
giving much thoughts to it ba sai daga
baya bayan na fito daga wanda ina shafa
mai sannan na sake fahimtar chanjin and
my first thought was abinda akayi min ne
ya saka naga wanna changing amma
ban kawo ciki ne ba, sai bayan nazo saka
kaya sannan na ga pad a cikin drawer and
it occured to me that ya kamata a ce nayi
period. Na dauko waya ta da sauri na duba app
din da make tracking period dina da shi
and it shows 8 days late. Sai da ma yanke
jiki na fadi. Allah ne kasai ya saka banji
ciwo ba amma na jima ban dawo cikin
hayyacina ba amma tashin hankalin da na
shiga ciki ba xai misaltu ba.
"Allah, Allah, Allah" kawai nake maimaita
wa, na ma rasa me zan roki Allahn, na
rasa me zan ce masa. Kukan ma a ranar
bai zo ba. Hijab dina kawai na saka na
dauki jaka ta tare da key din mota na fita
da sauri, Safina da take falo tana kallon series hankalin ta a kwance tayi ta min
magana amma ni ba ma jinta nake yi ba
na fice da sauri. Abinda nake lissafi kawai
shine inda zan je in tabbatar da zargin da
nake yi sannan kuma in ya tabbata in fitar
da shi. A lissafi na sati biyar kenan dan
haka bai kai matsayin da zai zama laifi in
na zubar da shi ba, sannan kuma na taba
jin waazin da aka ce idan rape case ne irin
nawa malamai sun yi saasauci akan
hukuncin zubar da shi. Sai dai o bayan da na fita daga gidan da mota ban san inda zan dosa ba. Ni dai na
san ba zanje gurin likitan gidan mu da
wannan zancen ba dan idan yaji to kamar
Daddy yaji ya gama ne, ni kuma zan iya
bayar da raina a lokacin dan kar Daddy
yaji wannan maganar.

Haka nayi ta yawo da mota a titinan garin
kano ban san inda zan je ba. Cikin ikon
Allah kawai sai naga signboard din wani
asibiti a bakin titi, I followed the directions
sai gani a kofar asibitin, dan karamin clinic
ne haka, Na shiga na je reception din su
na nemi gain likita suka ce sai na bude
file na bada kudi suka bude min na cike
info din da duka nema amma ko kadan
ban saka addres dina na gaskiya ko
number wayar wani a gidan mu ba.

Daga nan naje na hau layi, babu abinda
nake yi sai salati da istigfari a zuciyata ina
rokon Allah yasa kar zargi na ya tabbata, a
haka layi yazo kaina na shiga gurin likitan
direct na gaya masa pt nake so ayi min.
Ya tambaye ni symptoms dina na fada
masa sai ya rubuta min test din yace inje
lab suyi min, na je lab din suka dauki jini
na, for the first time in my life aka huda jiki
na ban ma san an huda ba dan zafin da
nake ji a raina ya ci uban zafin allurar.

Ina zaune dai har aka gama, zuwa lokacin
na tabbatar an fara nema na a gida dan
dai har lokacin layi na a kashe yake da an
fara kira na. Hankali na idan yayi dubu ya
tashi. A haka aka rubuta min result din
aka ce in mayar wa da Dr. Ban mayar din
ba na samu guri na zauna na bude
takardar da sauri ina bin rubutun da kallon
ina neman kalmar positive, and I saw it,
and it was the worst news I have ever
received in my life,

Tashin hankalin da ma shiga baya
misaltuwa, dan yafi ma na ranar da aka yi
raping dina, kawai hango kai na nake yi a
gaban Daddy da ciki a jiki na, musamman
a yanzu da na san in dai ba miracle ba ba
lallai ya yarda rape ba ne ba, and then sai
na hango Muhammad, na hango Muhammad idan labari ya iske shi cewa Piya ta yi cikin shege. Naji na tsani kaina, na tsani rayuwata, na tsani duk wan abu
da ya shafe ni and most importantly na
tsani cikin jiki na. Zuwa lokacin magrib
tayi na tabbatar cewa in na koma gida ina
cikin matsala but still ban koma din ba.
Dan matsalar da nake ciki ta fi ta kaiwa
dare a waje

Na rufe takardar na juya na koma office
din Dr na kai ma sa sannan na zauna ina
kallon sa har ya gama karantawa, ya dago
kai yana yi min murmushi "well,
congratulations madam. You will soon
become a mother" na gyara zamana ina
kallon sa directly nace "ina so zan zubar
da shi, kuma yi?" Ina kallon yadda
murmushin ya bar fuskarsa sannan ya
fara yi min wani irin kallo mai cike da
zargi, a karshe yace "mu mutanen kirki ne
a asibitin nan, ba ma yin irin wannan aikin asshan….." Ban jira sauran maganar ta sa ba na mike na dauki jaka ta na fita.Sai da na koma mota sannan na kife kaina na kama kuka, nayi kuka kamar raina zai
fita. Me zance da Daddy in ya ganni da
wannan cikin? Me zance da Muhammad, I
couldn't imagine yadda wanna maganar
zata yi breaking heart dinsa. He doesn't
deserve this. Na tuna da sauran yan'uwa na da kawayena wanne irin tunani zasu yi a akaina, probably most of them zasu yi min irin kallon da wancan dr din yayi min ne. Yar iska, tayi yawon banza tayi cikin shege

Na kuna mota ta amma maimakon in
koma gidan still sai na cigaba da yawo ina
neman wani asibitin. Ni tunda na tashi ban
taba zuwa asibiti da kaina ba, muna da
likitan da yake zuwa ya duba mu in bamu
da lafiya, in ciwon yayi karfi kuma a kaimu
asibitin sa, duk ban san was formalities
na harkar asibiti ba.

Bayan tsahon lokaci na kuma gain wani
asibitin na sake shiga, sai suka ce min Dr
din ba ranar yake zuwa gain patience ba
sai dai nurse, na je gurin nurse din and I
told her directly ga abinda nake son yi, a
take ta fara yi min wa'azi har da janyo aya
da hadisi, ban barta ta sauke wadda ta
janyo ba na dauki jakata na fita na bata
guri. Zuwa lokacin na san dole ne in koma
gida ko dan gudun kara wa kaina laifi akan
wanda already nake da shi. Da kuma
lafiyar Daddy. Haka na ja mota nayi gida, idanuwa na har sun kumbura saboda kuka. Ina zuwa kofar
gate kuwa naga karamin munafikin,
Mustapha, kafin mai gadi ya bude min kofa ya zo window na "daga ina kike?" Ko
kallon sa bani ba na ja mota a guje na
shiga, ina shiga kuwa na hango Daddy a
tsaye a kofar shiga side dinsa, ina yin
packing ya taho gurin motata, a dai dai
lokacin da Mustapha shima ya karaso,
Daddy ya tambaye ni "daga ina kike?" Na
fara kokarin furta karyar da na shirya zan
fada idan an tambaye ni "gidan su kawata
na je na karbo sako" ya na kallon fuskata
yace "karbo sakon ne ya saka ki wannan
kukan?" Na yi sauri na shafa fuskata, a
hannu ma naji alamun ta kumbura.
Mustapha ya warce jakar hannuna
"Daddy gwara a duba a ga wanne irin
sako ne ta karbo" ya fada yana kokarin
bude jakar, Daddy ya dakatar da shi "kar
ka bude mata jaka" amma kuma sai shi ya
karba "bani inga" na gode Allah da ban
karbo takardar lab result dina ba, Daddy
ya bude jakar ya duba kayan ciki sannan
ya miko min yace "je kivi sallah ki zo ki
same ni a daki" ya juya ya koma ciki.

Na juya nima zan shiga ciki Mustapha ya
biyo ni a baya "Allah ya taimake ki. Amma
wata rana za'a kama ki ne" na juyo a
fusace "za'a kama ni ko za'a kama ka? Ka
jira karshen ka Mustapha. Wallahi karshen
ka ba zata yi kyau ba". A ranar Daddy har cikin bedroom dinsa yayi kira na muka zauna "Safiyya, me
yake damun ki? Ki gaya min in kina da
wata damuwa. Wani abun aka vi miki?
Wani ne a gidan nan yake takura miki?"
Amma in na bude baki sai in mayar in
rufe, duk yadda naso in gaya masa sai na
kasa gaya masa and I missed Ammie
sosai da sosai.

A karshe dan ya bar tambaya sai na ce
masa "bana son zancen aure na da ake yi
da Mustapha. Bana son sa" Daddy yayi
ajjiyar zuciya "shikenan damuwar? Ke
waye yace miki za'a aura miki Mustapha?
Dan kinji mahaifiyarsa tana maganar ai
hakan ba yana nufin maganar ta tabbata
bane ba har zaki zauna kina irin wannan
kukan. Ni bani da niyyar yi miki aure
yanzu. Idan kuma lokacin auren naki yayi
bani da niyyar yi miki auren dole, ke zaki
zabi wanda kike son aura ki kawo min shi,
idan na ga ya cancanta sai in bashi ke,
kinji? Ki daina da mun kanki" na gyada kai
kawai na tashi zan tafi, har na kai kofa sai
yace "kuma karki sake fita ba tare da kin
gaya wa Sa'adatu ba".

Amma damuwa fa a lokacin ne ma na fara
yin ta. Yadda nake gain rana haka nake
ganin dare, burina kawai shine in samu
yadda zanyi in raba kaina da cikin da yake
jiki na dan with each passing day na san
lokaci ne yake cigaba da kure min. Kuma sai a lokacin sannan laulayi ya kara saka ni a gaba. Wannan ya sa a daki nake wuni ni kadai kuma haka zan wuni ina zaryar amai a toilet. Ranar nan dai na je nayi wa
Mommy karya "Mommy akwai kawata
Sharifa, kin tuna ta? Mun jima ba mu hadu
na kuma na rasa number dinta, ina so
zanje gidan su mu gaisa" sao naga taji
dadin haka "yauwa ko ke fa? Ai gwara ki
fita ki dan ga gari kiji dadi amma ace
kullum mutum yana kwance a daki" har na
fara murna sai cewa tayi "sai ku tafi tare
da Safina". A haka plan dina ya rushe. Ina ji ina gani
haka naje nayi zumuncin da banyi niyya
ba. Muka wuni muka dawo gida babu
yadda zanyi.

Ranar nan ma na sake satar kafa naje
wani asibiti da nake gani a hanya muna
wuce wa shima nay demanding abortion,
suma suka ce min basa yi tare da hada wa
da yi min wa'azi, sai na fito na tafi wani
Asibitin da naga kamar ba musulmai ne
suke running dinsa ba dan kar suyi min
wa'azi amma suma sai suka ce is against
there their religion and medical ethics, har
da gaya min wai Jesus yana sona yana
kuma son abinda yake ciki na. Haka na
fito suma ban samu abinda nake so ba. A lokacin da cikin ya kai wata biyu ne na
yanke shawarar neman sunan abortion pill
din online sai inje in siya. Nayi searching
ma samu sunan wani da naga a review
dinsa kamar yana da kyau, haka nayi ta
yawo shima na rasa chemist din da zasu
siyar min sai suke wai sai da saka hannun
likita. Daga baya na fahimci cewa duk
inda nake zuwa gurare ne na mutane
masu mutunci, abinda kuma nake bukata
ba abu ne da ya shafi mutunci ba. Ni kuma ko kawaye da zan iya yiwa irin wannan tambayar bani da su. Dan haka na dauki mota na tafi kasuwar sabon gari,
haka nayi ta yawo a kasuwar nan da kyar
na samu chemist na shiga na basu kudi
da yawa suka bani wani magani suka ce
inje gida in sha. Amma hatta shi mai
chemist din sai da yayi warning dina cewa
akwai ciwo kuma zan zubar da jini but I
didn't care,

Ina zuwa gida na shige dakina na rufe
kofa sannan na debi maganin na watsa a
bakina na bisu da zuwa. A ranar ban
dauka cewa zan sake kwana a duniya ba,
Ban taba jin ciwo irin wannan ciwon ba, Ji
nayi kamar allura aka samu ake caccaka
min a mara ta. A take kuma jini ya tsinke
min, jinin da na zubar na dauka jinin jikina
gabaki daya ya kare kenan, dan ban ma dauka akwai adadin wanna jinin a jikin nawa ba.

Ban sani ba azabar ciwo ne ko kuma
yawan jinin da na zubar ne ya dauke ni ba,
ni dai na san na fadi a cikin toilet.

Sanda na farka akan gado na na ganni a
kwance, a gefe na kuma Mommy da
Safina, Mommy ta ci kuka idonta yayi ja,
hannun ta rike da packet din maganin da
na sha. Na mayar da idona na rufe ina in
duniya gabaki daya tayi min kunci, yanzu
shikenan Mommy ta sani, shikenan Daddy
zai sani, shikenan na shiga uku, me yasa
ban mutu ba.

Mommy ta fara magana "yanzu sakayyar
da zaki yi mana kenan Safiyya? Reward
din mu kenan na duk tarbiyya da kulawar
da muka baki? Innalillahi wa inna ilaihir
rajiun" na kasa bude ido na sai hawaye
kawai da ya ke bin fuskata. Naji Mommy
tace da Safina "je ki ce masa ta farka"
nayi sauri na bude ido ina kallon kofar
shigowa kirjina yana dukan tara tara, daga
dukkan alama dama yana kusa da dakin
nawa dan bata dade da fita ba ya shigo,
fuskarsa kawai na kalla na fashe da kuka,
hannayensa nannade da belt din da ban
san ma a ina ya samo shi ba, amma sam
ban ji ina jin tsoron ya dake ni ba, ni
damuwata shine din da na gani a fuskarsa. Na zamo daga kan gadon na zube a kan kafafuwansa ina kuka,
maimakon dukan da ya shigo da niyyar zai
yi min shima sai ya durkusa a kusa da ni
mukayi ta kukan tare, kukan sa ya fi komai
tayar min da hankali, ban taba ganin sa
yana kuka ba. Mommy ma ta zauna a
kusa da shi ita ma tana yin nata.

Sai da ya gama kukan sannan kuma ya
tashi ya fita da sauri, jimawa kadan sai
gashi nan ya dawo hannunsa rike da wata
katuwar wukar da ban san inda ya samo
ta ba.

"Kashe ki zanyi yau. Yau sai na raba kanki
ga gangar jikin ki. Ni zaki nuna wa iyaka ta
a duniya? Ni zaki tozarta ki ciwa mutunci
Safiyya? Lahira zan tura ki kije can kiyi
bayani. Wallahi ko ki gaya min wanda yayi
miki wannan aika aikan ko kuma yau a
lahira zaki kwana dan uban ki"

Ko motsawa banyi ba daga inda nake dan
ni da zai tura ni lahirar ma da sai nafi jin
dadi. Mommy ta tashi da sauri ita da
Safina, Mommy ta rike hannunsa tana
salati "mun shiga uku, menene haka? Kayi
hakuri zata fada, zata fada mana ai, Kawo
wukar kar kaji wa kan ka ciwo da ita" ni
dai ko kallon su bana yi har su ka gama
abinsu ina dunkule a guri daya. Sai na
sake jin muryar Daddy a saman kai na "Safiyya! Waye yayi miki ciki? Waye yayi miki ciki na ce?" Ya fada cikin tsawa duk da rashin lafiya ta saka muryarsa bata
fitowa sosai.

Na daga kaina na kalle shi da idanuwa na
wanda da kyar nake iya bude su.
"Daddy..... Wallahi........ Ban sani ba" na
fada cikin karyayyiyar murya, ni kaina da
na fadi maganar na san ba yarda zai yi da
ita ba kuma wanna shine abinda yafi
komai damuna.

"Baki sani ba?" Suka tambaya a tare shida
Mommy '"baki sani ba fa kika ce" na
mayar da ido na na rufe ina fatan Allah ya
dauki raina. "Zaki yi magana ne ma, zaki
bude idon nan kiyi magana ne" ya fada
cikin haki, kafin in ankara naji saukar belt
din da ya shigo da shi dazu a hannunsa a
bayana, azabar dukan har cikin kwakwalwa ta saboda ni ba dukana ake yi ba, ko a makaranta ba duka na aka taba yi ba, Na kwanta a gurin tare da dunkule wa
a guri daya, ban san adadin bulalar da
yayi min ba, ban kuma sani ko zafin dukan
ne ko kuma tsananin tashin hankalin da
nake ciki ba, ni dai na san na fita daga
hayyacina, Sanda na sake farkawa a asibiti na ganni,
ina kwance da karin jini a hannuna. Gefe naga Mommy nan a zaune ta rafka tagumi tana kallo na. Na bude ido ina neman Daddy amma ban ganshi ba. Tace
"yana gida. Na san shi kike nema. Yana
gida ba shi da lafiya. Kin sani sarai ai
bashi da lafiyar amma kika he kika jawo
mana wannan abin kunyar Safiyya. Wai ke
yanzu har kin san kiyi cikin shege ki kuma
sayi abortion pill ki zubar da shi. An
tambaye ki uban sa kuma kince ba ki sani
ba. To a ruwa kika sha? Ko kuma saboda
yawansu ne ya saka baki san mana waye
a cikin su ba?......" Na jawo hannayena
biyu na toshe kunnuwana da su sannan
na rufe ido na.

Kwana na biyu a asibitin aka sallame ni.
Bleeding din ya tsaya kuma anyi min karin
jini sannan an bani magunguna, sai dai
har muka tafi ban sani ba ko asibitin sun
san abinda ya faru da ni ko kuma wata
maganar daban Mommy ta fada musu.
Har aka sallame ni Daddy bai zo ba. Ranar
da aka sallame ni din ba gida muka tafi ba
sai naga Mommy ta kai ni wani asibitin da
ban, Muka shiga office din dr din muka
zauna sai tace "yarinya ce tayi abortion,
so nake a duba ta a gani in ya fita gabaki
daya ko kuma in akwai saura" wannan shi
ya kara tabbatar min wancan asibitin basu
san abinda ya faru ba. Likitan mace ce, ta saka na kwanta akan gadon da yake kusa da ita tayi scanning
mara ta sannan tace da Mommy "ya fita
gabaki daya. Amma yanzu zan bata wasu
magunguna da zata ringa sha wadanda
zasu kara wanke mahaifar ta sosai su
kuma taimaka mata gurin healing" na ji
dadi ya kama ni kamar an saka ni a
aljanna. Na sauko daga gadon na zauna sai ta
debo magunguna masu yawa ta bawa
Mommy ta kuma yi mata bayanin duk
yadda za'a sha su. Ta juyo tana kallona
tace "akwai possibilityn cewa period din
ku ba zata dawo da wuri ba, har sai komai
ya daidaita a mahaifar ki sannan period
zata dawo" na gyada kai da sauri cikin
amincewa, who period help? In dai cikin
ya fita ai shikenan.

Muna zuwa gida Mommy ta kaini wajen
Daddy yana kwance a dakin sa, tsananin
damuwa a tare da shi. Na zauna a
gabansa na fara kuka. "Daddy am sorry"
ya mike zaune yana kallo na da irin kallon
da ban saba ganin yana yi min irinsa ba
yace "Safiyya, cikin waye kika zubar?" Na
fara goge hawayena dan nasan amsar da
zan bashi ba zata gamsar da shi ba amma
haka na fade ta "Daddy wallahi ban sani
ba" ya koma ya jingina da jikin kujera yana
cigaba da kallo na "kina gaya min cewa
haka kawai kika ga ciki a jikin ki ba ki san yadda aka yi ya zo jikin naki ba?" Nayi shiru bance komai ba sai yayi min tsawa "answer me!" Na bude baki cikin rawar
murya nace "na sanj" yace "to waye?"
Nace "Daddy ban san waye ba. Daddy
dan girman Allah ka yarda da ni. Wallahi
ban san waye ba. Amma ni Mustapha
nake zargi" ya bude ido cikin mamaki
"Mustapha? Wanne Mustaphan?" Nace
"yaya Mustapha na gidan nan" ya gyara
zama "kina da hujja? Me yasa kike zargin sa?"

Sai na bashi labarin abinda ya faru ranar
da ya dawo daga Cyprus, tun daga farko
har karshen abinda na sani. Sai da na
gama yace "shi waye saurayin naki da
kuka fita tare?" Navi shiru ban ce komai
ba ina jin daci a raina, yace "ba zaki fadi
waye ba?" Na girgiza kaina "Daddy ba shi
ba ne ba" yace "kuma kika ce baki san
waye ba. To ya akayi kika san ba shi bane
ba?" Nace "Daddy wallahi ba shi ba ne ba".

Yayi shiru kamar ba zaiyi magana ba
sannan a karshe yace "you just
desperately want to protect him. Har kina
neman ki halaka kanki, Har kina neman ki
yi wa wanda bai ji ba bai gani ba sharri"
nace "Daddy Mustapha fa......" Yace
"shut up! You are very stupid. Kina so ki
raina min hankali. Ranar da kike magana akai muna tare da Mustapha. Nine shaidar
Mustapha. Lokacin da kike magana muna
jirgi tare. Ko daga jirgin ya yi tsuntsuwa
yazo yayi kidnapping din naki?" Na girgiza
kaina "ban san yadda yai yazo ba. Ni dai
na san ya kira ni a waya yace ....." "Shut
up " Daddy ya sake katse ni "kar in sake
jin kin ambaci sunan Mustapha a wannan
maganar. Uwar sa tana iyakacin kokarin ta
a kan ki. Kar ki yarda taji wannan
maganar" Har zan fita sai yace "ki shirya kayan ki.
Zan je India gain likita. Dake zan tafi. I
am never taking my eyes off you again".

Haka na shirya muka tafi India da ni da shi
da Mommy da Mustapha, kullum Mommy
sai ta bani magunguna na nasha
religiously dan har alarm ne da ita na shan
magani na, ni kuma ban yaba saka komai
a raina akan maganin ba haka nake shan
kayana in ta bani, ina kuma jin dadi a
zuciya ta duk da na san tsakani na da
Daddy yayi bacin da miracle ne kadai zai
gyara amma tunanin na rabu da cikin shi
yake saka min kwanciyar hankali, at least
it is over, at least zan iya regaining dignity
na a hankali,

Watannin mu biyu a can sannan muka
dawo Nigeria. Zuwa lokacin har na fara tunanin dabarar da zanyi in sake dawo da
Muhammad cikin rayuwata ya zo a
matsayin wan daban ba wancan saurayin
da Daddy yake zargi ba, dan shi kansa
Muhammad din nasan zuwa lokacin yasan
karya . A lokacin ne kuma sauran buruka
nana rayuwa duk suka tarwatse a gaban
ido na. Ina kwance a falo kawai naji kamar
motsi a ciki na. Farko na dauka iska ce,
but then the movements became very
distinct. It felt like wani abu ne a cikin
nawa yake yin motsi.

Kwana biyu na cigaba da ji, kuma motsin
kamar karuwa yake yi. And then ranar nan
na tsaya a gaban mirror and really looked
at cikina, and I saw it. Mara ta ta daga
sosai kamar ace naci abinci na koshi
sosai. Ni kuma ba me tumbi bace ba. Duk
koshin da zanyi cikina baya taba kai haka
girma. Na ji gaba ma yayi mugun faduwa,
na dora hannu na akai a hankali na taba
cikin sai naji shi yayi tauri kamar wadda
aka kifa wa wani circular abu a cikin.

Na koma da baya na zauna akan gado
cikin tashin hankali. Menene wannan din
kuma? How? When? Na sauko waya ta na
fara googling ciki da yadda yake and it all
showed me cewa ciki na yana nan babu
inda yaje. And it occured to me that wayo
Mommy tayi min. Duk wahalar da nasha
wata biyu da suka wuce cikin bai fita ba ashe ya hada baki da wannan Dr din suka

nace mata ciki ne da ni ina son zan cire
shi. Ta fara yi min fada ita ma kamar
sauran doctors din tare da gaya min su
basa yin haka a asibitin sai kawai na dauki
jaka ta zan fita.

Tace min "wait" na dakata na dawo na
zauna tace min "watansa nawa?" Nace
"hudu" "ina babansa?" Nace "bashi da
shi" tace "yayi girma, akwai risk mai yawa.
Duk wanda zaki je ya cire miki wannan
cikin ba magani kadai zai baki ko allura
ba, sai anyi miki aiki an cire fetus din.
Akwai at least 70% chance na cewa zaki
mutu" na daga kafada nace "I don't care"

Ta cigaba da kallo na. "Ina iyayen ki?"
Nace "babata ta mutu babana ba shi da
lafiya" tayi ajjiyar zuciya tace "okay, zan yi
miki, amma kamar yadda na gaya miki
akwai risk sosai. Kuma ba zan yi miki a
nan ba akwai private hospital dina can
zaki je sai in cire miki a can. Kuma akwai
tsada, zaki iya biya?" Na bude jaka ta na dauko sarkar da na dauko a cikin kayana, set ne da dan
kunnen ta da abin hannu, na ajiye mata a
gaban ta nace "wannan zai yi? In ba zai
isa ba I can get some money too" ta dauki
sarkar tana kallo "this is gold" ta fada
cikin mamaki, ban amsa mata ba nace "zai isa payment din?" Ta dauka ta saka a
cikin jakar ta sannan ta miko min card din
ta tace "ga address nan, ki same ni a can
da weekend" na karba nayi mata godiya
sannan na tafi.

Da weekend din na shirya, har da leka
dakin Daddy da niyyar ko da ban dawo ba
na mutu to nayi masa kallon karshe,
sannan na kunna mota ta na tafi address
din da ta bani. Ina zuwa tace a shiga dani
wani daki. Ta kara maimaita min bayanin
aikin da risk din sa na kuma tabbatar mata
da cewa ni ban damu ko in mutu ba ko
kuma inyi rai, burina shine in rabu da cikin
jikina. Sai ta bani form na cike a matsayin
consent form na cewa na yarda da kuma
amincewa ta za'a yi komai,

Sai kuma ta dauko wata takardar ta bani,
a ciki naga inda zan saka phone number
din wani nawa, na nuna damuwata a kan
hakan, "bana son kowa ya sani" tace "'it is
just protocol, saboda idan wani abun ya
faru da ke, idan aikin ba'ayi nasara ba sai
mu kira gidan ku su dauki gawar ki, Ko ba
kwa so su yi miki sallah su binne ki?"' Nayi
shiru ina tunani sannan bayi deciding ina
so su binne ni.

Amma kuma sai na rasa number din wa
zan saka. Definitely not Daddy. Mommy kuma munafuka ce as far as I was concerned. Ni kuma bani da wani wa da zan ce a kira. Sai kawai na saka number
din Mukhtar.

Da kaina naje na kwanta akan gado
sannan na rufe idona lokacin da naga ta
dauko allura zata yi min. A raina ina
lissafin ko dai in farka a duniya ko a lahira.
Amma in a duniya din ne na san zan farka
ne ba tare da wanna mayataccen cikin
ba.

Sai dai ga mamaki na sanda na farka din,
ina duniyar, kuma cikin still yana tare da
ni, bayan shi kuma akwai iyaye na. Naji
wani rage ya kama ni, wannan likitan ta
yaudare ni. Naji muryar ta tana magana
"this girl is severely depressed. She is
suicidal. She is going to kill herself"
Mommy tace "ki daina fadar haka dan
Allah" likitan tace "but it is true. Idan ba
dan nayi mata wayo ba zata cigaba da
neman wanda zai cire mata ne har ta
samu, za kuma ta iya rasa ranta. Babu irin
tsoron da ban bata ba amma bace ita
bata damu ko ta mutu ko tayi rai ba. Dole
ku chanja approach din ku a kanta or else
you are going to lose her".

Na bude ido na, wanda na fara gani a
kusa da gado na shine Mukhtar. Sai
Daddy da Mommy da uncle Ahmad a can gefe tare da dr din. Naji wani irin bakin ciki, shikenan Mukhtar yasan abinda ya faru dani. Wannan wanne irin abin kunya ne.

Nayi sauri na mayar da ido na na rufe.
Bayan an ima kadan naii uncle Ahmad
yana fada "wannan yarinya ta jawo mana
abin kunya da bamu taba gani ba a dangi.
Yaya aure ya kamata ayi mata. Tana
haihuwa ayi mata aure. Ga Mukhtar nan,
dama ya jima yana son ta kai da ita ne
kuka ki amincewa. Tana haihuwa sai a
daura musu aure kawai"

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹


Episode Forty Five: Love


Na juya baya na na fara kuka feeling
totally betrayed. Ina jin Mukhtar yana yi
min magana amma ban ma fahimci me
yake cewa ba. I felt betrayed by everyone,
Mommy da ta boye kin cewa ciki na bai
zube ba, Dr Salma da ta yaudare ni tace
zata zubar min da cikin, Mukhtar da na
saka number dinsa kuma ya kira iyaye na.
Naji tamkar kowa da kowa na duniya ya
tsane ni nima kuma naji na tsani kowa,
Especially kaina.

Uncle Ahmad ya cigaba da fada, ta inda
yake shiga ba ta nan yake fita ba. Blaming
Daddy da Mommy wai su duka bata ni
bana jin maganar kowa babu wanda ya isa
ya juya ni yanzu ga abinda na zama.

Har sai da Daddy ya cire alkunya yayi
masa magana yace ya rabu dani,
musamman saboda abinda Dr tace dan
haka fada ba zai yi maganin komai ba sai
dai a lallaba ni. Sai uncle Ahmad yayi fushi
ya fice daga dakin, Ina jin Mukhtar yana
cigaba da yi min magana, making me promises na cewa babu abinda ya ragu a zuciyarsa na son da yake min kuma kamar yadda baban sa already ya fada shi ma ya yarda zai aure ni duk kuwa da abinda nayi.

Ganin bani da niyyar kula shi sai ya tashi
ya fita.

Daga baya Dr Salma ta dawo ta zauna
dani ta yi ta kokarin inyi mata magana
amma na ki kulata, haushin ta nake ji ba
kadan ba. Ashe wai she is a psychotherapist as well as a gynecologist dan haka Daddy ya bude min file a gurin ta wai zan ke zuwa duk sati ina ganin ta.
Daga nan aka sallame ni bayan uta ma ta
bani wasu magungunan. Muna komawa
gida na kwanta a falo na rufe idona
pretending kamar bacci nake yi sai naji
Daddy da Mommy suna rigima, Daddy
yana ta fada sosai muryar sa har makale wa ta ke

"How can you do this! Ta yaya kin san
cikin nan bai fita ba amma zaki ja bakin ki
kiyi shiru? Menene hujjar ki ta yin hakan?"
Tace "kana ganin da ta san da cikin da
zata barshi?" Yace "nima da nasan da shi
da ba zan barshi ba ballantana ita, Ke
yanzu da kika barshi me zai yi miki?" Tace
"I don't care about cikin, but I do care
about her. Ni na san halin da na tarar da ita a ciki a wancan karon da tayi kokarin
zubar da shi kuma in no way zan kuma
barinta ta saka kanta a wanna halin.
Likita ta gaya min cewa those pills are
effective kuma Safiyya overdose din su
tayi ma. Still kuma cikin bai fita ba. In dai
har ta sake sha zata iya rasa ranta
maimakon ta rasa cikin. In dai ta kashe
kanta ta mutu kafura fa kenan, ba gwara
ta haihu mu san yadda zamuyi da dan ba
sannan kuma sai a guji gaba, ayi mata
aure. Shi yasa na nuna mata cewa ya fita
dan ta hakura har zuwa sanda cikin zai
girma yadda dole ta hakura da zubar da
shi. Ba a kanta aka fara ba ai. Ni dai ta
bangare na nobody will know. Haka ta
bangaren yaya na. Amma yanzu da su
Ahmad suka shigo cikin maganar i am not
so sure akan rufuwar asirin"

Daddy yace "but you could have told me.
Tare dani da ke ya kamata mu zauna muyi
wannan shawarar. I should have had a say
in what goes on with my daughter's life.
Idan da kin gaya min abinda likitan tace a
lokacin I would have take her to duk kasar
da nasan suna da likitocin da zasu cure
mata cikin successfully, Ko a Nigerian nan
ma ba za'a rasa likitan da zai cire cikin
few weeks ba tare da complications ba.
Kuma kin san da haka. Amma kika bar
marainiyar Allah da ciki a jikinta har ya kai
lokacin da cire shi ya riga ya zama haramun. Wato kin bar mu da choice din ko dai mu aikata sabo wajen cire cikin ko kuma mu barta ta haifi shege and then we
will have no choice then to get her
married and cover up abinda ya faru,
shine target din ki ko?"

Mommy ta hau "how can you say that?
Kana ganin zan cutar da Safiyya dan ta
auri Mustapha? Abinda kake nufi kenan? I
made the decision for you dan nasan duk
abinda ya shafi Safiyya idonka rufe wa
yake yi ba ka ganin gaskiya, duk laifin da
tayi you will cover it up and find someone
to blame for it. Yanxu ma kuma abinda
kake yi kenan. Kana so ka juya laifi zuwa
kaina ba yan kasan laifin ka ne. Ka riga ka
bata yarinyar nan iyakacin bata wa. Yanzu
kuma da lokacin karbar sakamako yayi
you are looking for someone to blame". Daga lokacin rayuwa ta kara chanja min, duk da uzurin da Mommy ta bayar amma ban kuma jin cewa na yarda da ita ba,
abinda na saka a raina shine ta vi ne
saboda a matsa min lallai in auri
Mustapha, Wannan kuma sai ya kara min
zargin cewa Mustapha ne uban ciki na, za
kuma ta iya yiyuwa cewa Mommy ta san
da haka, sun hada baki ne dan su ci kudina.

Daddy a bangaren sa ya rage yi min
hayaniya sosai. Amma kuma ni kaina bana
jin dadin zama a gabansa dan wannan
bond din da yake tsakanin mu sam babu
shi, bana o son kallon idonsa dan
disappointment kawai nake gani a cikin
su. Yayi kokarin nuna min ba komai, har
sabuwar wayar da ake yayi a lokacin ya
siyo min wai inyi keeping in touch with my
friends tunda ba ma tare, amma ni na san
yayi hakan ne kawai dan yana gudun zan
sake kokarin halaka kai na.

Idan nace I was depressed a lokacin sai
inga kamar na rage wa abinda naji girma.
Babu anar da ba zanyi wa kaina addu'ar
mutuwa ba. Abu daya ne ya hanani
loosing hankali na completely shine sallah
da na rike na koma ga Allah. Kullum ina
dakina akan sallaya, anan nake kuka na
anan nake baccina anan nake wuni. Sai
dai Mommy ta shiga ta loda min uban
magunguna in shanye ta bani abinci in ci,
Safina ma tana shigowa, amma sau da
yawa in ta shiga gurina ko kallo bata ishe
ni ba ballantana har muyi magana dan
haushin mahaifiyarta da dan uwanta ya
shafe ta ita ma. Twins suna boarding suna
kokarin rubuta jarabawar kammala
secondary school dan haka bani da tabbas din sun san halin da nake ciki ko basu sani ba.

Ciki na kuma tun daga sanda na fahimci
yana nan shikenan sai ya cigaba da
girman sa kamar wanda ake hura shi
kullum, tun riga tana boye shi har ya fara
fitowa a cikin rigar ma sai dai in na saka
babba ko kuma na saka babban hijab.

A haka Daddy ya yanke wata shawara ya
kira ni ya gaya min "akwai asibitin da aka
yi min maganar sa a Berlin, likitocin su
sun kware akan kula da masu ALS, zan je
can, zan kuma tafi da ke ki zauna tare da
Sufyan da matarsa har sai kin haihu. She
is a good woman and a good friend of
your mother's. Na san ba zata tona
asirinki ba. Kafin nan kuma dole ki gaya
min uban dan saboda in kai masa
kayansa. And you, kina haihuwa zanyi miki
aure dan ba zaki kara min wani abun
kunyar ba. Besides, my time is running
out and I want to see you settled before I
go"

Na fara kuka amma bai chanja shawarar
sa ba sai ma yace in tashi in bashi guri, na
shiga daki na cigaba da kuka na and I
knew it was time to let Muhammad go....
Dole in hakura da shi. Tunda na san ba
zan aure shi ba. Na san Daddy zaiyi
kokarin aura min wanda in aka tashi auren ba za'a vi bincike ba ballantana a gano
abin kunyar da nayi. Sai dai kuma na rasa
yadda zan yi in rabu da shi din. Me zance
masa? Dole in gaya masa wani abu da zai
saka ya hakura da ni dan idan nayi
ghosting dinsa just like that ba zai hakura
ba zai cigaba da nema na ne har sai ya
same ni, kuma ina tsoron garin neman
nawa kar ya binciko abinda nayi.

Kafin tafiyar mu tafi sai na yanke shawara.
It wasn't the best shawara nima na sani
but I wasn't on my right senses sanda na
yanke ta. Ni da mahaukaciya banbancin
mu kadan ne. Amma kuma a raina ina son
in sake ganin sa, ko da sau daya ne.

A lokacin tafiyar mu ne naci sa'a jirgin mu
ta Abuja zai tashi, Daddy yaso sai ranar
tafiyar mu zamu je Abuja amma sai nace
"Daddy muje mu kwana mana, tunda ba
ka da lafiya ka samu ka dan huta ba wai
muna sauka kuma mu shiga jirgi mu tafi
ba" It has been long rabonda na saka baki
in ana magana, maybe shi yasa Daddy ya
bi shawarata to encourage me to talk
more, Ni kuma plan dina shine in samu
damar zuwa ganin Muhammad, Ina ganin
ya yarda na tura wa Muhammad sako
cewa na shigo Nigeria, mu hadu a office
din sa, akwai magana mai muhimmanci da
zamu y" Muna zuwa Abuja kuwa bayan
an shigar da kayan mu na shiga daki kamar zan kwanta in huta ne sai na dauki key din mota na faki ido na fice.

**. *. *. *. ***.

Present days…..

And now, all the possible tablets have
turned in all the impossible directions Mommy ta bude kofa ta shigo dakin. Ta
tsaya a bakin kofa tana kallo na, sai kuma
tayi ajjiyar zuciya "zaman cikin duhun dai
yana nan" sai ta kunna fitilar dakin sannan
ta karasa shigowa. Ta tsaya tana kallona
sai kuma ta zauna a kusa dani. "Safiyya?"
Ta tafa da karyayyiyar murya, sai na dora
kaina a kafadar ta tare da sakin kuka. Ta
juyo ta rungume ni sosai "Safiyya. Kiyi
hakuri. Ya isa kukan haka nan. You have
cried enough. Ya isa haka" ta fada cikin
sigar lallashi. Na daga kaina ina cigaba da
sheshshekar kuka. Ta kama hannuna "kiyi
hakuri Safiyya. Ni ban san da wanne bakin
ma zan baki hakuri ba, Daddyn ki ma
haka, Kiyi hakuri dan Allah ki yafe mana
rashin fahimtar ki da bamu yi ba, Wallahi
yanzu dukkan mu mun yarda, ba ma
bukatar ma da test din abinda muka ji da
kuma yanayin Mukhtar kadai ya gamsar
da mu. Mun yarda da ke. And it breaks my heart yanzu da na fahimci cewa you went through all that kuma you are innocent. Sannan kuma mu iyayen ki mun ki yarda
cewa you are innocent. Kiyi hakuri dan
Allah".

Na gyada kai na tare da share hawaye na
da hannu biyu. Sai kuma nace "ke ma kiyi
hakuri, I have been disrespectful to you a
lot of times" ta girgiza kai "babu komai. Ni
ban taba rike ki ba. Most of the times in
kinyi abu Daddyn ki nake hucewa a kan
sa" sai kuma tayi murmushi "yanzu kam
shima duk jikinsa yayi sanyi. Na san
kunyar hada ido zaiyi da ke. In kinje gurin
sa you should use kind words to ease
guilt feelings din sa" nace "to Mommy
sai kuma tace "su Ahmad sun tafi. Sunce
zasu bincike shi sosai. But sum jikin su
yayi sanyi. Uwarsa ko magana ba ta sake
yi ba har suka fita. Da kyar ma ta iya
mikewa da ga inda take zaune. I guess he
will confess sooner or later" muka vi shiru
gabakidaya sai kuma tace "kai! Allah ya
isa wallahi. Raina zafi yake yi. Ji nake
kamar in bisu in je gidan in zazzaga musu
masifa, Wannan wanne irin zalunci ne?"

Na dan yi murmushi nace "you don't need
to go to them, zasu dawo ne da
kafafuwan su suna begging for
forgiveness and then you can talk to them in all manners da kike bukata".

Sai washegari sannan a koma gurin
Daddy da safe na gaishe shi kamar yadda
nake gaishe shi duk safiya. Ya amsa
sannan yayi shiru, nima nayi shiru kaina a
kasa sai da muka jima a haka sannan na
mike da niyyar bashi guri tunda naga
kamar baya son muyi maganar sai kuma
ya kira sunana, na dawo na zauna sai
yace "me yasa?" Na dago kai da mamaki
"Daddy me yasa me?" Yace "me yasa kika
zabi auren Mukhtar bayan kuma kina
zarginsa da wannan mugun abun? Me
yasa tunda kika fara zargin sa baki zo kin
same ni kin gaya min ba? Ko dan kina
ganin I dismissed you sanda kika ce min
kina zargin Mustapha? Haka ne? Idan da
Mukhtar kika ce I would have given it
more thoughts than Mustapha. Me yasa
baki fada min ba?"

Na sake sunkuyar da kaina nace "Daddy
nima ban fara zargin shine ba sai bayan
da muka dawo Nigeria, bayan da aka riga
aka daura auren, Tun lokacin ya fara nuna
min ya damu da abinda na haifa and I
found that suspicious, Daga baya kuma
saw some kind of resemblance tsakanin
sada…...da.... Junior, Shine nace masa ya
mutu, and he acted kamar uban da aka ce
masa dan sa ya mutu" Daddy ya sake girgiza kai "but still you should have come to me ai. Da sai in dakatar da bikin in kashe auren in kuma bincike shi. Bai
kamata ki saka kanki in danger ta hanyar
tarewa a gidan sa alhalin kina zargin sa da
wannan maganar ba. Zai iya yi miki komai
dan ya rufa asirin kansa, zai iya daukar
ranki ma. Akwai rapist da yawa da suke
kashe victims din su dan gudun kar su
tona musu asiri. Da kin gaya min sai mu
tuhume shi in yaso in yaki sai mu dauko
Junior ayi dna din, shikenan".

Nayi shiru ina wasa da yatsun hannu na,
ina jin kunyar Daddy sosai akan duk wata
magana da ta shafi Junior, amma wannan
magana ce da ya kamata muyi. Nace
"Daddy I did all that for Junior. I was
trying to avoid doing the DNA. Ina tsoron
dna test din will blow off Junior's cover,
Mukhtar zai san shi sauran yan'uwa zasu
san shi, mutane zasu gane cewa ba dan
Aunty Hajjo ba ne ba. I was trying to
protect him from people and from the
reality of his life. Na san zai sani watarana. Amma nati son in zai sani din ma sai ya zama strong
enough to accept it, yadda ko ma me
mutane zasu fada din ba zai affecting
ginin rayuwarsa ba".

Daddy yace "so you were trying to
protect him by putting your own life in
danger? By risking your life?" Na gyara
zamana ina kallon sa nace "Ammie
jumped to her death to protect me. She
went through a lot of things dan taga na
samu rayuwa mai kyau. Wannan shine
version na motherhood da na sani.
Wannan shine irin uwar da nake so in
zama".

And I saw him smile. It has been 20 years
amma babu yadda za'a yi a ambaci sunan
ta ba tare da zuciyar sa ta russuna ba.
Babu yadda za'a yi ayi labarin ta ba tare
da yayi murmushi ba.

He said "shikenan. Allah ya bada sa'a yayi
jagora. Allah kuma yayi miki albarka.
Ahmad ya roka cewa a basu lokaci da
Mukhtar, zamu jira shi muji abinda zai ce
da kuma abinda zaiyi. Idan kuma bai yi
abinda ya dace ba, mu zamu yi abinda ya
dace".

And then the waiting began ………. Muka fara
zaman jiran hukuncin da Uncle Ahmad zai
yanke,

Kwana na uku a gida ranar nan muna
zaune a falo da Mommy muna ta hirar twins and how they are coping with aikin su sai ga Safina ta shigo. Naji gabaki daya mood dina ya chanja. Har da gudun ta taje ta fada jikin Mommy tana murna.
Mommy ta ture ta tana dariya. "ke dalla
saukar min a jiki kar ki balla ni" Safina ta
fara shagwaba "haba Mommy, na rame
fa" Mommy ta kalle ta "kin rame tabbas
amma yanxu ai naga kin fara dawo da jikin
ki, kin murmure ba laifi. I guess your
inlaws are treating you right ko?" Safina
ya gyara zamanta sosai tana kallo na tace
"suna da kirki sosai. Mama is the best
mother in law in the whole world" Mommy
tace "uhumm. Sai shine bashi da kirki
kenan. Bai yi gadon halin kirki ba gaskiya"
Safina ta bata rai "kai Mommy, baya... "Baya gari ne fa
. " Mommy ta karasa tana kwaikwayon muryar ta. "Zancen kenan kullum baya gari. Ni ba zan ki fadar
gaskiya ba fa. Mijin ki bashi da kirki. Ko a
gaban sane ko a gaban iyayensa zan fada
ballantana a gaban ki. Bashi da kirki ko
kadan. Yanzu ji nake bikin Safiyya aka yi
ko waya baiyi mana yace Allah ya sanya
alkhairi ba ballantana ya kawo mana
gudummawa. A haka kuma kullum kice
wai aiki yayi masa yawa shi yasa baya
zama a kasar, To ya dauke ki ya tafi da ke
inda yake zuwa mana in da gaskiya ne……”

Ta cigaba da wanke Muhammad ni dai na
mayar da hankali na kan waya ta bance
musu komai ba.

Sai daga baya Safina ta mike ta ajiye
mayafin ta tare da cewa "Mommy me
kuke da shi abinci a gidan nan? Ina Esther
take? Ta zo ta jefa min danwake, shi nake
son ci da manja"

Mommy tace "ke zauna tukuna ba
maganar dan wake ake yi ba. Wai baki ga
Safiyya ba? Ko bata baki labarin abinda
yake faruwa ba? Ki zauna ki jajanta mata
mana" Safina ta koma ta zauna tana
kallona sannan tace "me ya faru?"
Mommy ta fara bata labari "zancen cikin
ta, ashe dai da na Mukhtar ne...." Ina jin
su ta bata labari tiryan tiryan tun daga
farko har karshe. Na lura da yadda
yanayin fuskar safinan yake nuna tsananin
tashin hankali,

A karshe Mommy tace "to yanzu dai
maganar da nake miki zaman jiran
hukuncin da iyayenku maza zasu dauka
muke yi. Bamu san dai abinda zasu ce ba
amma abinda na tabbatar shine auren
Safiyya da Mukhtar ya kare" Safina ta yi sauri ta kalle ni and I smiled brightly at her. Ta dafe kirji cikin tsananin tashin hankali "innalillahi wa inna ilaihir
rajiun. Hasbinallahu wa niimal wakel"
Mommy tace "dole kiyi salati yar nan..
wannan abin tashin hankali ai ya kai inda
ya kai. Sai dai kawai muyi mata addu'a
Allah ya musanya mata da wanda ya fishi
alkhairi" Safina ba ta yi magana ba sai ni
nace "Amen Mommy. Nagode"

Mommy ta mike, bara inje in gano ko
baban ku ya tashi daga bacci in taimaka
masa...." Ta cigaba da magana tana tafiya,
tana fita na sake yiwa Safina murmushi
"Hi dear sister.... Kinga ikon Allah ko? Har
na kusa gamawa da dayan saura ke, ina
gamawa da shi zan dawo kan ki kamar
yadda nayi miki alkawari. I will not wait for
karma to catch you. I will come for your
head as soon as na gama da wancan
munafikin. Kuma ba zan yi miki da sauki ba Safina, ke
da kanki zaki ciro kan naki kiyi min serving
din sa on a tray, You will regret sanda kika
dora don ki a kan Muhammad".

Tayi shiru tana kallo na, fuskar ta da
idonta sunyi ja, ta bude baki amma ta
kasa magana, daga dukkan alamu duk
karerayin ta da mugayen maganganu ta sun kare, a karshe sai tace "he is my husband. And Daddy will never let you marry my husband and iyayen sa will
never let him marry kanwar matar sa.
Ballantana kuma someone with your
reputation".

Na mike tsaye ina kallon ta nace "har
yanzu ko shekara ba'a yi ba da fara
wannan dramar, and abubuwa da yawa
sun faru most of which a shekarun baya
nake kalla as impossible. Misali ke a
matsayin matar Muhammad. Hakan yana
nufin cewa God can change impossible to
become possible through the most
impossible way. Just wait and see, zaki
sha mamaki. Ban san yadda abubuwa
zasu kasance ba but na san cewa the
moment da mijin ki yaji labarin aure na ya
mutu he will run back to me as fast as his
legs can carry him. And the rest will be
history".

Da niyyar kwana Safina tazo gidan amma
bata iya kwanan ba, haka ta dauki mayafin
ta ta dauki motar Mommy ta tafi da ita.
Yanayin ta gabaki daya ya koma tamkar
wadda aka cewa Mommy ta mutu, ita
Mommy duk ta dauka labarin abinda ya
fari da nine yayi affecting dinta hakan
bata san ita Safina abinda ya faru da ni ko
a jikinta ba dan ko jajanta min bata yi ba, ita tsoron ta kawai shine zan kwace mata mijinta.

Ni kuma a lokacin ba zan ce Muhammad
baya gaba na ba, dan in nace bana son sa
nayi karya, amma na fadawa Safina
wadancan maganganun ne dan in bata
mata rai. Amma ni kaina na san akwai
obstacles da yawa a tsakanin mu.

Daga nan na cigaba da zaman jiran
hukuncin da za'a yanke, ko dan ance aski
in yazo gaban goshi yafi zafi? Sai naji
yanzu nafi damuwa akan duk dadewar da
nayi ina jiran bayyanar gaskiya. Mukhtar
da yake kunya bata ishe shi ba haka yayi
ta zabga min kira da messages a waya
akan wai yana son muyi magana, naki kula
shi sam, nayi blocking kiran sa na bar
messages din duk wanda ya turo sai inyi
screenshotting in ajiye ko zasu zamar min
evidence.

A haka har na kwana biyar a gida. Ranar
ne ina zaune a dakina ina aiki akan system
kawai naji an bude dakin an shigo sannan
an mayar da kofar an rufe, na san mutum
daya ne yake yi min hakan amma kuma
ranar na san bashi ba ne ba, na juyo da
sauri sai naga Mukhtar a tsaye ya jingina
da jikin kofar yana kallo na. Kallo daya
zakayi masa kasan cewa rayuwar sa
gabaki daya a upside down take.

Nayi sauri na saka hannu na a kasan gado
inda nayi ajjiyar sabuwar wuka ta
musamman saboda Mustapha, na juyo na
nuna shi da ita nace "fita, ko a fitar da
gawar ka" maimakon ya fita sai ya zame
ya zauna a wajen yace "kill me, idan
hakan shine abinda kike bukata" na
karaso na tsaya a gabansa fuskata cike da
tsanarsa hannu na rike da wukar nace
"zan kashe ka wallahi, in kashe banza a
banza kuma babu abinda za'a yi min".

Yace "zaki iya yin hakan. Ko kuma zaki iya
tsayawa ki saurare ni. Wata kila mu samar
da mafita a cikin maganar da zamuyi"
nace "bana bukatar wata mafita wadda ta
shafe ka. I already know what I want kuma
shine abinda zan samu. I want to see you
locked up in prison for as long as
possible" ya dago ido yana kallo na,
fuskarsa kamar ba ta Mukhtar din da na
sani ba. Yace "I don't care about going to
prison Safiyya. I care about more
important things than my freedom" nayi
shiru ban ce komai ba, trying to control
my heart da take zugani a kan in soka
masa wukar hannu na,

Ya cigaba "Umma ta fadi, tana asibiti
kwanan ta biyu bata san waye a kanta ba.
Abba yace babu shi babu ni har abada,
And you" Cikin tsawa nace "don't
talk about me. Kar inji sunana a cikin
bakin ka. I don't care me iyayen ka suke
ciki ko me suka yi maka. Ni ka damu da
halin da nawa iyayen suka shiga a sanadin
abinda kayi min? a damu da halin da na
shiga a saboda abinda kayi min? Ka cuce
ni Mukhtar! Ka cuce ni! Kayi min cuta ta
har abada. Allah ya isa! Allah ya isa! Allah
ya isa tsakani na da kai". Na fada ina kukan da har sai da wukar ya fadi daga hannu na. Ya kife fuskarsa akan
guiwar sa yana kuka shima, jikinsa har
rawa yake yi. Na zauna a kasa nima na
jingina da jikin gado ina jin wani tarin
tsanarsa tana kara yawa a zuciya ta. Gani
nake yi da ace Mustapha ne yayi min
wannan abun da ba zan tsane shi kamar
yadda na tsani Mukhtar a yanzu ba.

Ya dago fuskar sa yana kallo na yace "
want to confess a gaban iyayen mu su
yanke min hukuncin da zasu yanke min,
but before then I want to tell you why I did
it" nace "I don't want to know, I don't
care"

Yace "I know. But I want to tell you
anyway. I did it because I love you. Ban
taba son wani abu ba a duniya kamar
Manna nake con ki Safivva Tin kina taba son wani abu ba a duniya kamar
yadda nake son ki Safiyya. Tun kina
karama nake sonki. I tried duk yadda
zanyi inga kin so ni amma kika ki, babu
yadda banyi ba, ke ma kin san babu
yadda banyi ba. I even tried involving
iyayen mu amma Daddy ya goyi bayan ki.
Meanwhile you got some guy and you
kept rubbing him on my face. I wanted to
have you. I wanted you so bad...." Ya fada
miko hannunsa zuwa gare ni, na janye
jikina out of his reach nace "in ka sake ta
bani sai na cire hannun ka. You are
insane" ya ajiye hannun sa a gefe yace "I
thought in na same ki ta wannan hanyar
zan daina jin zafin soyayyar ki da take ci
na. I thought in nayi miki haka maybe zaki
rabu da wancan saurayin and might
consider me. I thought maybe in iyayen
mu suka fahimci abinda ya faru they
might consider aura min ke. I never
thought you will get pregnant. I never
thought anyone will notice. But believe
me Safiyya wallahi I regretted it tun a
lokacin, sharrin shaidan ne da sharrin
zuciya ta da na kasa controlling a akan ki.
Na kai ki gida and I watched you har kika
shiga gidan, thinking za'a yi miki fada ne
kawai for staying out late and shikenan",

Yayi shiru, maybe jira yake inyi magana,
jin bani da niyyar yi sai ya cigaba "I was
wrong. Maimakon abinda nayi ya rage min son ki da bukatar ki sai kara min ma da
yayi. I waited inji kin rabu da wancan
saurayin kinyi kokarin shiryawa da ni but
you didn't. I thought kin manta ma da
abinda ya faru and you have moved on,
sai kuma ga kira daga asibiti that you
went kina so zaki zubar da ciki, tun a
lokacin na san cewa nawa ne. And I
thought I hit the jackpot, nasan dole ki
rabu da wancan saurayin naki and
chances dina na auren ki ya karu. when
you chose to marry me kuma sai naji
kamar nafi kowa sa'a a duniya, I thought
chance ne Allah ya bani na rectifying
mistakes dina by taking care of you and
abinda zaki haifa. Allah kuma sai ya saka
min son sa shima a zuciya ta kamar yadda
ya saka min ya kuma kara min naki. Ban
san cewa tarkon kamani ne Allah ya dana
min ba".

Ya goge hawayen fuskarsa "I know all this
doesn't matter. It doesn't change
anything. Amma ina so ne kawai in gaya
miki cewa I love you and I never meant to
hurt you" idona yana rufe nace "and yet
you did" yace "yes, amma nayi nadama
tun a lokacin, you have no idea how it
haunted me" na bude ido ina kallon sa
nace "da kayi nadama da tun a lokacin
you will turn yourself in, zaka kawo kanka
gurin iyayen mu ko gurin hukuma ka nemi ayi maka hukunci. But you stood by and
watched me suffer, hoping to have me
again. No Mukhtar, ba ka yi nadama ba,
not yet. I trusted you but You are just a
selfish and entitled bastard with no single
atom of imani a cikin zuciyarka. Your
reason, duk a wadannan maganganun
naka is just cewa kana so na, and who
told you dan kace kana sona sai nima
lallai na so ka? And let me tell you, ka cire
kalmar so daga bakin ka. Kai baka sona,
baka sona ko kadan. Ni na san menene so
and it neither look nor sound like what
you just described"

Na gyara zamana nace "ina da wanda
nake so kuma yake so na. And what I did
sanda wanna musibar ta same ni shine
na rabu da shi duk kuwa da son da nake
yi masa, saboda na san cigaba da
kasancewa tare da shi zai shafa masa
bakin fentin da maybe har abada ba zai
¡ya goguwa ba. Babu abinda Daddy bai yi
min ba, amma naki ko da kuwa ambatar
sunan sa, duk kuwa da nasan maybe da
na ambaci sunan na sa da yanzu ina gidan
sa a matsayin matar sa.

But I couldn't hurt him that way, I can
never hurt him in any way because I love
him. Wannan shine love"

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya😥❤️‍🩹

Episode Forty Six: Decision Making


Na tashi na koma inda nake zaune kafin
ya shigo na zauna sannan nace "idan ka
gama maganar da zaka yi ka kuma gama
kukan zaka ¡ya fita" nayi kamar na cigaba
da aikin da nake yi a system.

Ya jima a gurin a zaune sai kuma ya mike
yace "I know you have recorded all that I
said, kamar yadda na san kinyi
screenshot na messages dina, but you
won't need them. Kamar yadda na gaya
miki I am going to confess, ba kya bukatar
wadansu shaidu tunda zan amsa laifina
da bakina. Amma abu daya ne ba zanyi ba Safiyya, abu daya ne ba zan iya yi ba. Ba
zan iya rabuwa da ke ba. You and my son
are mine".

Naji kamar ya soki zuciya ta na mike "your
what? Did you just say your son?" Ya
daga kafada "Allah ne kadai yasan dalilin
da ya sa yaron ya zo duniya but I am
greatful for him, maybe a saboda shi you
will learn to love me, maybe he is meant
to bring us back together"

Na nuna shi da hannu nace "don't you
ever call him your son again. Ba dan ka
bane ba, ba shi da hadi in whatever way
da kai. And I will never like you ballantana
love, da da nake maka kallon mutumin
kirki ma ban so ka ba Mukhtar ballantana
yanzu da na san the kind of monster that
you are? Get out of my room tun kafin in
tara maka mutanen gidan nan".

Ya bude kofa sannan ya sake juyo wa
yana kallo na. Na fahimci maganar yake
so ya cigaba sai na juya na shige toilet na
rufe kofa. Na zauna dirshan a cikin toilet
din na jingina da jikin bango, zuciya ta
tana yi min zafin ambatar Junior as son
da Mukhtar yayi. In da ace zan samu
yadda nake so Mukhtar will never lay his
eyes on Junior har karshen rayuwarsa.

Sai da na tabbatar ya tafi sannan na fito,
na sauka kasa muka ci abinci tare da
Mommy, na lura ba ta san Mukhtar yazo
ba dan da ta sani zata yi min maganar,
Mustapha yazo shima ya zuba abincin
yana ci suna magana da Mommy akan
wadansu abokan babansa an siyasa da
ya kaiwa takardun sa zasu sama masa
aiki. Sai da suka gama maganar su ta
tashi sannan yace min "can I kill him
now?" Na girgiza kaina "not yet. Saura
kadan" yayi ajiyar zuciya "I don't even
know why I am listening to you, you of all
people, after wulakancin da kika yi min a
gidan nan" na juya ina kallon sa nace 'I
thought you said you wanted to make it
up to me?" Ya mike tsaye ya saka hannu a
aljihu yace "yes, I want to do something
for you dan in gyara tsakanin mu and dan
in yi making up for my mistakes, but case
din that bastard is my case dan haka
babu ke a ciki. Kawai na baki time da shi
ne out of the goodness of my heart,
amma sai ya raina kansa wallahi, he tried
to frame me Allah ne ya kare ni. I will
return the favor to him, ni kuma in na haka
masa nawa ramin muguntar ba zan jira shi
ya fada ba ni zan je in hankada shi da
kaina".

Nayi murmushi bance komai ba sai ya
juya zai fita. Na mike tsaye na kira sunan
sa ya tsaya yana kallona, na je gabansa na
tsaya nace "in har da gaske kana son
gyara tsakanin mu then accept the job I
offered you. Let's work together and take
care of our parents" yace "so that ki
samu damar yi min gori with every
opportunity da kika samu?" Nace "in kace
haka ba kayi min adalci ba, when na taba
yi maka or anyone a gidan nan gori?" Ya
danyi shiru sannan yace "I will think about
it" nayi masa murmushi "that will be
good"

Mommy ta fito daga hanyar kitchen sai
kuma ta tsaya tana kallon mu, Mustapha
ya juya da sauri ya fita ni kuma na dawo
cikin falo, na lura da yadda farin ciki ya
cika fuskarta and I hoped 'she is not
thinking what I think she is thinking'

Sai da nayi sati daya a gida sannan uncle
Ahmad ya dawo. Ranar da yazo ina
kitchen naje zan dauko ruwa in sha naji
muryarsa ya shigo gidan, sai nayi zama na
a kitchen din naki fitowa har sai da Esther
ta shigo tace Mommy tazo tana nemana
wai in je inji Daddy, Na koma sama na
dauko hijab na saka sannan na tafi falon
Daddy, Ina shiga na gansu gabaki daya
kamar ranar nan, Umma ce kadai babu.
Na je in da na zauna ranar nan na sake zama nayi shiru, yau ma ban gaishe da kowa ba. Uncle Ahmad ya danyi gyaran murya sannan ya fara magana a hankali, na lura yayi loosing duk zafin kansa da takamar
sa. Yace "ban san abinda zan fara fada a
wannan zaman ba, kawai dai na san ni ne
ya kamata in fara magana a matsayi na na
baban ku gabaki daya. Musamman tunda
yaya bashi da lafiya. Amma abinda na sani
shine nayi nadama babba a rayuwata,
nadamar da nayi kuwa ita ce ta haihuwar
ka Mukhtar " ya fada yana nuna Mukhtar
"da nasan wanna ranar zata zo min da
ma shake ka tun kana jariri ka bar duniya
dan ubanka"

Ya karasa maganar cikin daga murya, na
kalli Mukhtar na ga yadda ya takure a
waje daya fuskarsa tana kallon kasa, and I
wondered me yasa yazo gurin. Mommy
tace "babu zancen yin dna test din
kenan? Har na fara binciken asibitin da
suka kware a wanna bangaren" Uncle
Ahmad ya juyo yana kallon ta yace "na
san farin ciki kike yi da wannan maganar,
wannan kuma ya kara tabbatar min da
who you really are. Wannan maganar ba
abin murna ba ce ba. Abinda ya kamata
mu zauna gabaki daya mu jajanta sannan
mu nemi mafita akai ce" Mommy tace "wancan satin da aka zauna ai baka jajanta ba. Kin yarda ma kayi. Ka fara kokarin kare dan ka. Kuma ni ba murna
nake yi ba amma bana jajantawa, na riga
na jajanta na kuma zubar da hawayena
tun a lokacin da aka zalunci yarinya,
yanzu kuma da lokacin karbar mata
hakkin ta yayi in banyi murna ba ma ai ba
zan jajanta ba" Yace "babu wanda yafi karfin kaddara ta saukar masa..... Mommy tace "Allah ya raba mu da
mummunar kaddara...””


Daddy yayi gyaran murya yace "yanzu
menene abinda kazo zaka ce Ahmad?
Kace a baka lokaci da yaro zaka tuhume
shi kaji gaskiyar magana da ga bakin sa.
Mun baka lokaci. Ka dawo. Fada mana
abinda ka jiyo daga bakin nasa" uncle
Ahmad yace "ni dai godiya daya da zan yi
wa Allah a cikin wanna maganar ita ce da
ya azurtani da wadansu yayan bayan
Mukhtar, ina kuma saka ran insha Allah
Allah ba zai hada min lalatattun yara irin
sa ba" ya juya yana kallon Daddy yace
"yaya, Mukhtar ya fada min da bakin sa
cewa ya aikata laifin da yarinyar nan ta ce
yayi. Mukhtar ne yay'" ya fadi maganar
kamar zai yi kuka,

Sai kuma yayi shiru yana kokarin daidaita
muryar sa sannan yace "farko na ce masa babu ni babu shi har abada, sannan kuma kunyar ka da kuma kunyar yarinyar nan ta hana ni zuwa in gaya muku abinda ya ce min din. Amma kuma yanzu sai naga
rashin zuwan nawa kamar kara wa laifina
girma zaiyi a gurin ka. Kai yaya na ne, duk
duniya bani da kamar ka".

Ya sake juyawa wajen Daddy "yaya, dan
Allah, kayi hakuri ya yafe min" Daddy bai
ce komai ba yana dai kallon sa amma
yanayin fuskar sa yana nuna tashin
hankali da rudanin da zuciyar sa take ciki.
Uncle Ahmad ya cigaba "yaya ka yafe min
dan Allah. Ba wai Mukhtar nake nema wa
yafiya a gurin ka ba dan nasan abinda yayi
abu ne da zai yi wahalar a yafe masa
lokaci daya, ni nake nema wa kaina yafiya
a gurin ka saboda na gaza gurin tarbiyyar
yaron nan. Amma Allah shine shaidata
kuma kuma zaku iya zamar min shaida ko
a lahira ne. Nayi iyakacin kokari na gurin
tarbiyyar yaron nan" yayi shiru yana
mayar da numfashi sannan ya cigaba "da
nace babu ni babu shi har abada, amma
kuma sai na ga hakan ba zai cire jini na
daga jikin sa ba, Idan har zai iya aikawa
wanna mummunan abun alhalin yana
tare da mu me zai hana shi aikata abin da
yafi wannan muni idan baya tare da mu?" "Gashi nan yaya na kawo maka shi. Kayi masa duk hukuncin da kake gain ya dace da shi".

Falon yayi shiru, sai zuwa can Mommy
tayi magana "chafi. Lallai duniya ta zama
abin toro. Wai dan uwanka shi zai vi
maka wannan cin mutuncin". Aka sake yin
shiru zuwa can sannan Daddy yace
"Mukhtar"' Mukhtar yayi shiru bai amsa
ba. Kamar wanda yake kokarin shigewa
cikin kujerar da yake zaune a gabanta.
Daddy ya sake cewa "Mukhtar kai ne ka
aikata wanna mummunan aikin? Kai ka
cutar da kanwar ka Safiyya irin wannan
cutarwar mai girma?" Mukhtar ya sake yin
shiru bai yi magana ba. Daddy yayi kamar
zai tashi daga kan kujerar sa cikin tsawa
yace "answer me!" Mukhtar ya dago kai
sannan ya fara jan guiwarsa zuwa gaban
Daddy "Daddy dan Allah kayi hakuri..
Wallahi ina son ta ne....…. Wallah sharrin shaidan ne..........Ina sonta ne bana son in rasa ta, Dan Allah Daddy kayi hakuri ka yafe min".

Daddy ya koma ya zauna yana kallon sa
yace "kana son ta kake ce min Mukhtar.....
Kayi mata wannan wulakancin sannan
kace kana son ta? A haka ake soyayyar?
An taba yin soyayya dole ne?" Mommy
tace "zancen soyayya ma bata taso ba. Baka son ta Mukhtar ko kadan ba ka son yarinyar nan. Dan ko makiyin ka sai wanda kiyayyar tayi zurfi sannan zai iya aikata maka wanna mummunan abu. Karya
kake yi wallahi Mukhtar" ya juyo gurinta
"Wallahi Mommy da gaske nake.... Wallahi
ina son ta. Tun tana karama nake son ta
ita kuma tace bata so na" Mommy tace
"tun tana karama? Kace Allah ne ya kiyaye
mu da tun tana karama zaka aikata mata
wannan aikin kenan tunda kai irin version
of soyayyar ka kenan. To wannan ba
soyayya bace ba bari kaji in gaya maka.
Wannan sha'awa ce. Mummunar sha'awa
ma kuwa irin mai cutarwar nan. Inda auren
ya dore ma akwai yiyuwar zaka cigaba ne
da cutar da ita kana kuma cigaba da gaya
mata kalmar so, wannan shi ake kira da
toxic love. Yanzu kuwa tunda Allah ya toni
asirin ka mun gane halin ka to sai dai ka ci
kanka ka sha bakin ruwa. Wannan
yarinyar kai da ita sai hange daga nesa.
Kai daga nesan ma ba zaka ganta ba".

Mukhtar ya cigaba da kneeling a gaban
Daddy, "Daddy dan Allah kayi magana,
Wallahi nayi nadama" ya fada tare da
fashewa da kuka, Still Daddy bai ce komai
ba, Mommy tace "nadama tukunna
Mukhtar. Baka yi nadama ba zaka yi dai",

Uncle Ahmad yace "na yarda da ke a wannan karon. Nadama ai ba yanzu zaka yi ta ba tukunna. Kuma wannan kukan munafunci kake yi bana gaskiya ba. Kar
kuma ka dora wa shaidan, sharrin zuciyar
ka ne kawai da ka saka mata tunane
tunane marasa kyau a cikin ta. Kuma shi
da kake bawa hakuri ai ba shine wanda
kayi wa laifin direct ba. Ga wacce kayi wa
laifi can kaje ka durkusa ka bata hakuri".

Mukhtar ya tashi daga gaban Daddy ya
dawo gabana ya durkusa "Safiyya, na san
na cutar da ke cuta mai girma. Na san
nayi miki laifin da babu abinda zai taba
goge miki shi daga cikin zuciyar ki. Amma
wallahi nayi nadama. Dama kawai nake so
a bani in gyara kurakurai na. Safiyya dan
girman Allah da soyayyar da kike yiwa
annabin rahama kiyi hakuri ki yafe min"
Mommy tace "Sallallahu alaihi Wasallama".

Ban dago kai na kalle shi ba ballantana
inyi magana. Uncle Ahmad yace "to
alhamdulillah. Sai ka godewa Allah tunda
ya baka ikon neman yafiyar ta tun kuna da
rai duk ku biyun. Dan Allah baya taba yafe
laifin da akayi wa wani har sai in shi wanin
ya yafe da kansa" sai kuma ya juya gurin
Daddy yace "yanzu dai yaya da Mukhtar
nan da Safiyya, dukkan su yayan ka ne.
Ka yanke hukuncin duk da kake ganin ya dace da abinda ya faru a tsakanin su". Daddy ya danyi shiru yana bin mu da kallo sannan yace "yanzu Ahmad misali ace na bar maka wannan hukuncin. Nace ka
yanke duk abinda kake gain shine dai dai. Me zaka yanke a kai?"

Uncle Ahmad ya juyo yana kallon mu daya
bayan daya sannan ace "to yaya.
Wannan dai wani lamari ne mai sarkakiya.
Lamari ne da ya shafi mutuncin ba su
kansu yaran ba har da mu har da sauran
yanuwansu da kuma yayan da zadu haifa
nan gaba. Mutunci dai Mukhtar ya riga ya
zubar mana da shi, abinda ya rage mana
shine mu tattara wanda ya rage mana mu
cigaba da kare shi. Irin wannan idan ya
faru ko da ba'a cikin dangi daya bane ba
kokari ake yi a rufe dan kare martabar
dukkan bangarori biyun. Abunda akanyi
idan an samu yaro takadiri irin Mukhtar ya
haikewa yarinya irin haka to sai a matsa
masa akan ya aure ta dan a kare martabar
ta, shi kuma a bashi damar gyara
kuskuren sa. Ballantana kuma yanzu da
ya kasance har da rabo a tsakanin su,
dole in mun tashi yanke hukunci mu duba
har shi yaron da aka haifa. Muyi kokarin
kare mutuncin sa da kuma rufe wa
mutane hanyar da aka bi aka same shi ta
hanyar tabbatar da aure a tsakanin iyayen
sa. To alhamdulillah a wannan case din already ma akwai aure a tsakanin su. Already ubangiji ya riga ya rufa asirin abin. Duk hukuncin da za'a yiwa Mukhtar ayi masa amma a shawarce Yaya abar auren
da yake a tsakanin su dan kare martabar
yarinyar da dan da ta haifa da kuma bawa
Mukhtar shima damar gyara kuskuren da
ya aikata. Wannan shine nawa hangen.
Amma abinda kace duk shi za'a yi".

Tunda ya fara magana zuciya ta take zafi,
ikon Allah ne kawai ya saka banyi magana
ba har yaje karshe. Sai nayi shiru ina jiran
inji abinda Daddy zai ce, zuciya tana
bugawa tana bugawa da kaifi ina tsoron
kar Daddy ya goyi bayan maganganun
uncle Ahmad dan it will break my heart to
say no to him

Sai naji yace "na gane maganar ka
Ahmad. Kuma na fahimci manufar ka.
Sannan na yarda kana da gaskiya, dan
kusan abinda ake yi kenan a cikin
mutanen mu idan aka samu issue irin
wannan, kokari ake yi a binne dan a kare
martabar iyalin. Sai dai kuma matsalar
guda daya ita ce, Safiyya is not like all the
other girls da ake yin hakan akan su".

"Tun Safiyya tana yarinya, tun bayan
rasuwar mahaifiyar ta, loka6da na fara
bata tarbiyya. Kai da Sa'adatu da sauran
mutane da yawa kun sha gaya min cewa
tarbiyyar da na ke bata ba irin wadda aka
saba yi a kasar hausa ba ce ba, kuna
ganin kamar ina lalata tarbiyyar ta ne ta
hanyar bata freedom, musamman
freedom of speech. Kunce sai abinda take
so nake yi mata bana tursasa ta akan
abinda ni nake son tayi. To yau zan gaya
muku dalili. Za kuma ku fahimci result din
tarbiyyar tawa. Ina bawa Safiyya zabi ne
akan duk abinda ya shafe ta komai
kankantar sa saboda ina so ta koyi
making decisions a rayuwar ta dan nasan
zata fuskanci kalubale da yawa, duk da
ban hango mata wanna masifar ba
amma na san zata fuskanci kalubale da
yawa kuma dole zata bukaci courage din
saying yes or no as a final decision. Na
san kuma ba zan zauna tare da ita ba har
abada. A yanzu kuwa ku kan ku shaida ne
cewa Safiyya doesn't need anybody to
make her decisions for her. Namu shine
mu bata shawara a matsayin mu na
wadanda muka fita hangen nesa, But the
final say is hers" ya juyo yana kallo na
yace "Safiyya, Talk to us, Ga abinda
Mukhtar yace ga kuma shawarar da uncle
dinki ya bayar. Me kika ce"

Na dago kaina for the first time sannan na
gyara zamana ina kallon su daya bayan
daya, na sauke ido na akan Mukhtar nace
"Mukhtar. Naji ka bani hakuri. Amma
kuma ban karba ba. Ba zan iya hakura ba.
Mukhtar ba zan iya yafe maka ba har
abada. Ko da nace na yafe maka to ka
tabbatar karya nake yi maka". Ya fara
matsowa zuwa gaba na "Safiyya
please.….. dan Allah" na cigaba "Abu
daya zaka yi min in yafe maka" da sauri
yace "menene? Anything you want" nace
"ka je ka kai kanka kotun musulunci a
yanke maka hukuncin da addini ya
tanadar wa duk wanda ya aikata irin laifin
ka. Idan kayi haka zan yafe maka.
Ubangijin ma zai yafe maka tsallake
iyakarsa da kayi" nan take naga yanayin
fuskarsa ya chanja, ya juya ya kalli
mahaifinsa sannan ya sake juyowa ya
kalle ni. Nayi murmushi "na san ba zaka je
ba. Saboda kamar yadda Mommy ta fada
nadamar karya ce kake yi. You just want
to emotionally blackmail us and blame
shaidan for your actions, you want to eat
your cake and still have it. You want to
just say sorry to me and shade fake tears
and you expect everything to just
disappear, Sai a dauke ni a mayar da ni
dakin ka kamar wata unwanted akuya".

Na juya gurin Uncle Ahmad nace "uncle I
am not sorry for saying this, ba zan koma gidan Mukhtar ba. Ba zan cigaba da
zaman aure da Mukhtar ba ko da kuwa shi
kadai ne ya rage a matsayin namiji a
duniya. Tabbas abinda ka fada shine
abinda ake yi wa mata da yawa a kasar
hausa. Namiji yay raping mace sannan ayi
forcing dinta to leave with him a matsayin
mij for the rest of her life. Wannan zalunci
ne ba karami ba. I was raped. Ni nasan irin
tsanar da nake ji a zuciya ta ta wanda yayi
raping dina, dan haka na san yadda
wadannan matan suke ji a zuciyar su a
game da mazan da ake matsa musu suyi
zaman aure da su. Amma suna yin shiru
su zauna dan basu da bakin magana
kamar yadda Daddy yace. They are just
yes girls. They just do what they are told and live a
miserable life cikin kunci zuciya, hatred
toward their husbands da kuma cigaban
cin zali daga mazajen na su. Dan duk
namijin da zai iya raping yarinya to tabbas
cikakken azzalumi ne, kuma chances are
he will continue to rape her day after day
a cikin rayuwar auren nasu, Chances are
high that she will never know what true
marriage really feels like. Ga raping, ga
auren dole sannan ayi sentencing dinta to
life time of torture. And all for the crime
that she didn't commit. Amma shi wanda yayi laifin sai reward ma da aka bashi na auren ta, babu wani hukuncin da za'a yanke masa saboda a rufe maganar kar aji kunya".

Na girgiza kaina "no. Not me. That will
never happen to me. Not in thousand
years...…." Na juya kan Mukhtar nace "na
baka shawara naga baka yarda ba. Okay
in ba zaka yi hakan ba kana da wani
option din again. You will go to jail. You
will go to jail for as long as its legally
possible for someone with your crimes.
You will never go free, ba yan'uwan ta ka
ba ko uwa daya uba daya muke da kai. I
will make an example of you Mukhtar,
maybe sauran mutane zasu yi following,
maybe sauran mata zasu fara breaking
this chain of torture suna reporting
mazaje masu irin halin ka".

Ya fara girgiza kai "Safiyya dan Allah. Na
baki hakuri fa Safiyya nine fa Mukhtar.
Wallahi ban san maganar zata yi karfin
haka ba" ya juya gurin su Daddy "Daddy
dan Allah ka bata hakuri. Abba dan Allah
ka saka baki, Wallahi nayi nadama,
Wallahi ban san zata samu ciki har ta sha
wannan wahalar ba" Mommy tace "Allah ne ai ya kama ka shi yasa ta samu cikin. Da babu cikin da
maybe har abada babu wanda zai san
abinda ya faru sai dai tayi ta rije bakin ciki
a cikin zuciyar ta har mutuwar ta" na juyo
ina kallon ta nace "yes Mommy. Na
tabbatar akwai mata da yawa da aka taba
raping amma har su mutu babu wanda zai
san anyi, sai dai abun yayi ta cin su a
zuciyoyin su saboda fadar ma ya zama
abun kunya. In mace ta fada ita za'a vi wa
tambarin while culprit din will be free, ko
kuma ma ace sharri tayi masa"

Na mike tsaye ina kallon Mukhtar da yake
ta hada uban gumi nace "I will see you in
court" na juya zan fita sai uncle Ahmad ya
mike ya kira suna na "Safiyya!" Na juyo
ina kallon sa idanu na a bushe "what
about you? Idan kin kai maganar nan
court dole sunan ki yana ciki, ke yanzu
babbar mace ce a cikin al'umma dan haka
sunan ki zai yi tambari. Yes, za'a yanke
masa hukunci a rufe shi ke kuma sunan ki
zai baci. Shin ba zaki yi considering
wannan ba?" Na juyo na dawo tsakiyar
dakin nace "suna? Wanne irin suna ne ya
rage min uncle? Wanne bacin suna zanyi
wanda yafi wanda nake ciki yanzu? Maybe
maidan maganar ta fita cewa I was raped
in samu sympathy na sensible mutane.
mean cikin shege fa nayi uncle, I already
have a bastard child uncle, wanne mutunci ne kuma ya rage min?"

Na fada with raising anger. Mommy ta mike "still Safiyya…... Nima yanzu na fara
goyon bayan uncle din ki. You still have
your reputation to protect Fiyya. A yanzu
babu wanda ya sani sai gidajen nan guda
biyu. In kika fitar da magana kuwa duniya
gaba-daya zata sani" nace "for how long
Mommy? For how long maganar zata
tsaya a tsakanin mu? Safina will say it the
first chance she gets. And someday aure
zai iya taso min a garin bincike wani da ya
ga wani abu zai iya gaya wa wani shima ya
gaya wa wanj and then everyone will
know, abinda kuma zasu sani sannan
zasu fada shine Safiyya Adam
Muhammad tayi cikin shege. No body will
mention sunan Mukhtar a ciki. All fingers
will point at me. The innocent me"

Na ga duk still sun cigaba da kallona,
daga alama babu wanda yake goyon
bayana a cikin su sai na juya daga hanyar
zuwa cikin gida nayi hanyar waje., Mommy
ta rike hijab dina, "ina zaki je kuma
Safiyya? Kar ki fita a wannan yanayin" na
juyo ina kallon ta nace "zanje gidan radio
da television da duk wata media channel
that I can get to, zan je in bada labarin
how my cousin raped me, and how my
family are trying to cover it up dan su
"kare martaba' ta, martabar da already aka riga aka zubar min. And I am also going to write an article inyi
publishing on the Internet, in saka sunana
da nasa, in bada labarin abinda ya faru
sannan inyi tagging all the humanitarian
organization da zasu kwato min hakkin da
kuke kokarin hana ni karba"

A falon babu wanda yake zaune sai
Daddy, daga dukkan alamu duk na hada
musu zafi. Uncle Ahmad ya rike hannuna
shima "Safiyya. Yata ki nutsu ki dawo ki
zauna. We will talk about this. Zamu sake
magana. We will find a way out kinji?".
Mommy kuma tana cewa "ba dai jail kike
so ya tafi ba? Zai je jail but don't go and
publish your name a duniya.…...." Suna ta
maganganun su naji Daddy ya kira sunana
"Safiyya!" Ya juya ina kallon sa yace "ki
koma gida, Zamu yi magana in an jima" na
karbe hannaye na daga gurin su nayi
hanyar cikin gida, sai kuma Daddy ya juya
yana kallon su yana murmushi yace "na
tabbatar yanzu kun fahimci abinda nake
nufi, She can stand up for herself, Ba ta
tsoron uban kowa. Yanzu bani da
damuwa, Ko yau na mutu na san she will
take care of herself".

A ranar na zauna da daddare na rubuta
labari na da duk abinda ya far da ni.
Including names and places da komai.
Banyi publishing ba amma sai a barshi
sai naji abinda Daddy zai ce. Amma har
cikin zuciya ta bana jin damuwa wai dan
nayi publishing sunana a matsayin rape
victim.

Washegari da safe naje gaishe da Daddy
sai yace in zauna zamuyi magana. Ina
zaune har Mustapha ya gama taimaka
masa yaci abinci sannan ya fita ya bamu
guri

Daddy yace "naji maganganun ki jiya"
nayi shiru ina sauraron sa sai na ji shima
yayi shiru. Nace "Daddy to me zaka ce
akai?" Yace "I don't know Safiyya. Ni na
san zafin da nake ji a zuciya ta a
matsayina na mahaifin ki ballantana kuma
ke da abin ya faru da ke. Kuma zan so ace
Mukhtar ya samu hukunci wanda yafi
kowanne hukunci tsanani akan abinda
yayi miki. Zan ji dadi sosai idan hakan ta
faru ko dan ya zama izna ga yan baya"
nace "good, Then kana goyon bayan in
shigar da kara court kenan?" Yace "yes,
zan so hakan, Amma kamar yadda Ahmad
yace what about you?" Na girgiza kaina "I
don't care about me Daddy. I have no
honor left. Bani da wani sauran mutuncin
da zan kare " yace "kina da shi Safiyya. Kina da shi sosai. Idan kuma kamar yadda
kika ce you don't care about yourself
what about Junior? What about other
children da muke saka ran zaki yi aure
nan gaba ki haifa? What about their
reputation?" Nayi shiru ina kallon sa ina jin
raina yana baci sai ya cigaba "ke uwa ce
Safiyya. Just last week kika zauna anan
kike gaya min yadda kika saka rayuwar ki
a danger to protect martabar Junior. In
kika ce zaki watsa labarin nan a duniya kin
zubar da waccan maganar kenan
gabakidayan ta, duk abinda kika yi kinyi in
vain. And not only him, yayan duk da zaki
haifa nan gaba will also be tagged with
that. Zaki haifi dan halak nan gaba amma
mutane will also call him shege saboda
basu san wanne ne shegen ba. They will
tag all your children as bastard. Duk inda
kika je kika boye Junior sai anje an binciko
shi. Ba karamin aikin mutanen mu bane ba
ki ga pictures din sa suna yawo a social
media together with your story ko kuma
ma a kara wata karyar akai".

Naji hawaye yana bin fuska ta "to yanzu
shikenan Daddy? Shikenan ba za'a
hukunta Mukhtar ba" yace "za'a iya
hukunta shi Safiyya. But bata hanyar da
kika dauko ba" na share hawaye na nace
"ta wacce hanyar to, Daddy me zan yi? Ya
zanyi?" Ya daga kafada "I don't know, But I know something. Your mother is the
smartest person I know when it comes to
decision making. And you are smarter
than her. You are her modern version. Na
tabbatar you will make the smartest
decision"

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Forty Seven : The Decision


*Free baking master class*
I'll be sharing delightfully delicious
recipes including how to make soft and
fluffy doughnut for *free* it's completely
free A-Z
Click the link below to join
Females only
https://chat.whatsapp.com/
DN5w2VPGPhE0gf3700F9k0
0704248974
Zan koyarda snacks kala 8 kyauta
acikinsu akwai yadda zakiyi doughnut me
laushi da dadi classes dinnam kyauta ne
daga farko har karshe
Danna wannam link kiyi joining
Mata kawai
Or contact
07042486974
To be added
https://chat.whatsapp.com/
DN5w2VPGPhE0gf3700F9ko

Safiyya.....

Ranar kwana nayi banyi bacci ba ina saka
da warwara, a fahimci abinda Daddy
yake nufi, amma sai dai kuma fahimtar ta
sa ta toshe min hanyar da na biyo kuma
na kasa ganin wata hanyar da zata bulle
da ni xuwa destination dina. Na tashi nayi
sallah na gaya wa Allah bukata ta na roje
shi ya bani mafita tunda dai ni bani da ita.
Sai wajen asuba na kwanta akan sallayar
nayi bacci, bayan anyi sallah na tashi nayi
sallah sannan na koma kan gado na
kwanta bacci mai nauyi ya dauke ni.

Ban farka ba sai da rana tayi sosai. Na
tashi nayi wanka na shirya ina jin kaina
yana yi min ciwo duk kuwa da cewa nayi
bacci mai nauyi amma na san damuwa ce
ta saka min ciwon kan. Na dauko waya ta
ina dubawa sai na ga sako daga Abdul
yana yi min mitar bana neman su sai in
sun neme ni "munyi fushi" ya turo tare da
hoton Junior ya bata rai ya turo baki, Sai
na samu kaina da yin dariya, He looks so
cute and innocent and doesn't deserve all
this, Na shafa fuskar sa ta cikin wayar sai
nace a hankali "hey you, It is going to be
okay. You are going to be okay, I promise"

Nayi replying Abdul tare da tsokanar sa
ina tambayar sa labarin amarya. Sai kuma na tashi na tafi part din Daddy dan gaishe
shi. Ina shiga na tarar da shi a falon sa
tare da Mustapha suna gwada wani
machine da aka siyo masa da zai taimaka
masa wajen zama da tashi ba tare da an
rike shi ba. Na zauna a gefe ina kallon su.
Mustapha might be a bad person but he
takes care of Daddy and I am greatful to
him for that.

Sai da suka gama sannan na karasa gurin
sa na gaishe shi sannan nace '
"sai yanzu na tashi. I slept in" ya zauna yana haki
saboda movements din da yayi sannan
yace min "maybe baki yi bacci da dare ba
ne ba ko?" Na sunkuya da kai nace "haka
ne Daddy. Ina ta tunani ne. I am still not
sure what I will do" yace "kin ci abinci?"
Na girgiza kai "no, shigowa nayi da ma mu
gaisa sai inje inci abincin" yace "good. Sai
kuma yayi shiru ya kwantar da kansa tare
da rufe idonsa,

Har na fara tunanin tashi ina gain maybe
bacci ya dauke shi sai kuma na ga ya
bude ido yana kallona yace "na taba baki
labarin siblings din Ammien ki?" Na gyara
zama, ina son labarin Ammie ko a gurin
waye ballantana a gurin Daddy, A gurin sa
da sauran mutane na hada labarin ta.
Nace "wanne labarin da ga ciki? Na yadda
suka yi sanadin rasuwar baba Hadiza da su Sauda ko kuma na yadda suka biyo ta
nan suka takurawa rayuwar ta?" Ya girgiza
kai yace "na abinda ya faru da su bayan
rasuwar ta" nace "Daddy you never talk
about anything related to rasuwar Ammie.
Labaran ka duk na sanda tana raye ne ba
ka taba bani labarin lokacin rasuwar ta ko
abinda ya far bayan rasuwar tata ba".

Yayi shiru yana kallon tv amma ba wai tvn
yake kalla ba. Ya dan jima sannan yace
"tabbas yan'uwa Safiya sun tsane ta ita
da yan'uwan ta, tsanar da har ta kaisu ga
aikata abubuwa da dama wadanda suka
zama sanadiyyar da Safiya ta rasa kowa
nata. Sannan kuma sai Allah ya daukaka
ta fiye da yadda bata yi tunani ba, fiye da
yadda suma ba su taba mafarki ba, and
they came back, zuciyoyin su still cike da
tsanar ta, they threatened her life, suka
kira ta da juya, suka kuma bita da
mugayen maganganu na sharri".

"A lokacin a irin daukakar da Safiya take
da shi idan da taga dama zsta iya batar da
su a duniya baki daya, idan da taga dama
zata iya kai su kara ta lissafo irin
abubuwan da suka aikata mata and she
can get a good lawyer da zai iya rufe mata
duk wanda yake da hannu a cikin abinda
ya same ta. But she didn't do that. She said sanda ta shiga gidan su yaga yadda Allah ya mayar da su ita kuma ta ga yadda Allah ya mayar da ita sai ta san
cewa Allah has already fought her battle
for her. Bata bukatar revenge. Ya riga yayi
mata. Amma sai ta ja jikinta daga gare su
dan gujewa sharrin su. Ko sanda suke
zuwa gidan nan. A cikin gidan nan sun
taba gaya mata ido da ido cewa tunda ita
juya ce bata haihuwa suna jira be ta mutu
su ci gadon ta. She could have sue them
a lokacin, but she didn't. She said taga
abinda Allah yay musu wancan karon,
wanna karon ma shi take jira yayi mata
komai. She just took some protective
measures and leave them with God".

"And then she died"

"Washegarin da ta rasu suka zo gidan
nan, Bus guda suka yo shata daga Kura
suka taho mazan su da matan su, yara da
manya, Sanda suka zo aka gaya min sai
nace a barsu su shigo, Na saka aka basu
dakuna biyu, maza aka basu daya a waje
mata kuma aka basu daya a cikin gida,
Amma tun a lokacin sai suka tayar da rigimar su dakunan ta suke so a bude musu a sama su a dakin ta zasu sauka. Lokacin kina ta koke koken ki na neman
mahaifiyar ki Sa'adatu da sauran mutane
suna ta fama da ke amma su ko a kin su.
Hajiya ta san ba alkhairi ne ya kawo su ba
dan haka ta hau saman ta rufe dakunan ta
rike key a hannun ta. Shikenan sai rikici.
Suka kafa maganganu na rashin mutunci
da izgilanci suke yiwa Hajiya, Sa'adatu
kuma da sauran mutane suka shiga ciki,
sai rigima ta tashi a gidan gaisuwa"

"Ni ina can ina cikin matsananciyar
damuwar abinda ya faru naji hayaniya. Ina
ji dama na san sune. Nan take na kira
police suka zo suka kwashe su
gabakidaya suka tafi dasu. Sai da suka
kwana a can. Ahmad ne yayi ta zirga-
zirga sannan daga baya nace a sake su
amma kar su dawo min gida. Su barni inji
da abinda yake damuna".

"Suka tafi din, amma basu hakura ba
ranar sadakar bakwai sai gasu sun dawo,
Mutane sun taru ana yi mata sadaka da
adduoin neman rahamar ubangiji amma
tun daga bakin gate suka fara zage zage,
wai suna so suga uban da zai hana su
shiga gidan, ai gidan ma yanzu nasu ne, ai
ance musu dama gidan tane kuma su ne magadan ta dan haka sun zo karbar gadon su. Har nayi niyyar sake kiran police sai Alhaji Nasir ya hana ni. Ya aika
aka shigo da su ya zaunar da su yace su
zauna avi mata addu'a tare da su sannan
sai a saurari maganar da suka zo da ita".

"Aka gama zaman addu'a aka tashi. Suka
sake zama da Alhaji Nasiru suka gaya
masa sun zone karbar dukiyar da ta mutu
ta bari, har da list din su a hannu na
abubuwan da aka gaya musu ta mallaka.
Alhaji Nasiru ace babu komai dama ai shi
gado Allah ya riga ya raba shi. Su je su
samo malamin da zai raba gadon sai su
zo a raba a basu. Suka ki tafiya, dan
sunce ko kudin motar da zasu koma kura
basu da shi jira suke sai an basu su samu
na mota a ciki, Alhaji Salisu ya sama musu
gurin zama, sannan ya nemo alkalin da zai
raba gado ya kawo ya hada su dashi,
sannan ni kuma aka ce in bayar da abinda
ta bari wanda za'a raba".

"Ban je gurin ba dama nace ba zan je ba,
sai na tura barrister Umar da sauran
lawyers din ta suke managing affairs dinta
suka je, suka gabatar da lissafin
abubuwan da ta mutu ta bari wadanda
suke nata. Wadannan sun hada da
wadansu daga cikin kayan sskawarta, sauran tarkacen irin na mata, da kuma kudin da yake cikin account din ta. Ko mota bata da ita. Nan take sabuwar
rigima ta rikice dan ma Allah yasa na gaya
wa barrister su tafi da security dan babu
abinda ba zai iya faruwa ba. Ai kam dai
ance Dauda wuka ya fitar yace sai ya illata
barrister Umar".

"Nan take suka shigar da kara Court akan
an cinye musu gadon yar'uwar su data
mutu ta bar musu. Zama daya aka yi wa
shari'ar alkali ya kori karar tunda basu da
hujjar cewa wadannan kadarori da suka
lissafa nata ne. Dan ga takardu lawyers
din mu sunje da su da suke nuna duk
kadarorin nan naki ne ba nata bane ba.
Daga nan suka sake kai kara kotun
musulunci. Sunce waccan kotun kafurci
ake yi a ciki. A wannan zaman court din
ne naje, na kuma yiwa alkali bayanin duk
abinda Safiya tayi sanda tana da rai kuma
cikin koshin lafiyar ta. Ta baki kyautar komai da ta mallaka kuma ke ce kadai yar ta a duniya. Na kuma nuna masa abinda ta mutu ta bari a matsayin
nata. Sannan nace ni da ke mun yate
gadon Safiya, abinda ta bari din mun bar
musu su rike"

"A take alkali ya tabbatar musu da cewa
Musulunci ya yarda da abinda Safiya tayi,
dan haka abinda na nuna musu din shine
kawai abinda za'a raba a matsayin gadon
ta, sannan kuma yace ni da ke musulunci
bai bamu damar cewa mun yafe gado ba,
ba'a yafe gado, dole sai an bamu sai dai
in an bamu mu bayar in bama so"

"Still sai suka tayar da rigimar wai ai kayan
sakawa kadai na fito da su banda kayan
daki, su sun san cewa kowacce mace
tana da kayan dakin ta a gidan mijinta dan
haka sai na fito da su gado da kujeru da
sauran su ai suma kayan ta ne. Ni kuma
na san sanda na sayi gidan nan na saka
aka zuba komai a cikin sa, tabbas safiya
ta sai abubuwa itama amma ba ma
zanniya ware abinda ta siya da wanda na
siya ba dan haka nace su zo su dauka.
Ahmad yana ta bala'i nace ya barsu suzo
su dauka. Na zo gida na kwashe duk
abinda na san mai daraja ne kuma ta baki
tun tana da rai, irin su gwala-gwalai da
manyan suturu da designer perfumes din
ta duk na adana a bangare na, Duk abinda
yake bangaren ta kuma nace azo a dauka,
Hatta carpet da labule ba'a bari ba sai da
suka cire, Hatta cutlary set sai da suka
dauke daga kitchen. Cokali basu bari ba,
Har da mugunta, abinda aka ga ba zai
dauku ba sai a fasa shi. Ban ce komai ba
dan ni ta kaina nake yi. Duniyar ma ta fita daga kaina ballantana kayan da suke cikin
ta. Suka kai alkali aka yiwa kaya kudi aka
fitar da nawa da naki sauran aka basu. Ni
dai ban sake komawa court din ba.
Abinda aka bamu ma nace da Ahmad yaje
yayi sadaka da su Allah ya kai mata ladan
kabarin ta. Daga lokacin naji gidan gabaki
daya ya fita daga kaina ba zan iya cigaba
da zama a cikin sa ba. It holds a lot of
good and bad memories for the both of
us dan kema a lokacin kamar kinfi kukan
neman ta in muka shigo gidan. A lokacin
ne na yanke hukunci komawa Kano da
zama to ease the pain for us".

Yayi shiru yana hutawa, idon sa yayi ja,
har yanzu mutuwar Ammie tana damun sa
sosai and I couldn't imagine going
through the pain of loosing her at the
same time kuma da wannan bacin ran na
yan'uwan ta. Ga kuma ni da na saka shi a
gaba da rigima kullum.

Muka cigaba da yin shiru sannan nace
"Daddy to ba ka gaya min ba" yace "ban
gaya miki me ba?" Nace "sanda zaka fara
magana kace zaka bani labarin abinda ya
faru da su bayan rasuwar ta. Menene ya
faru da su?" Ya dan yi gyaran murya yace
"a labarin da aka bani, Tun a gaban alkalin
da ya raba gadon suka fara rigima akan
abinda aka basu, matan suna ta zabar
kayan sakawa daga cikin kayan da suka samu. Sai babban su, Yaya Malam, ya kwace komai daga hannun kowa yace su bari sai sun je gida sai suyi nasu rabon.
Ya dauko shatar motar diban kaya aka
kwashe duk kayan aka zuba a ciki, cash
din kuma ya karba ya rike a hannun sa, su
kuma suka shiga mota suka koma Kura
gabakidayan su"

"Daga baya Jamilu dan marigayiya Hajiya
Kyauta, shi yake bani labarin abinda ya
faru da su. Yace bayan sun je gida suka yi
ta jiran motar kaya tazo shiru shiru mota
bata zo ba. Tun suna tunanin matsala
motar ta samu a hanya har suka fara
tuhumar yaya Malam akan inda kaya suka
makale, da farko yayi ta basu uzurirruka
masu cike da karaiyayi. Daga baya bayan
an debi tsahon lokaci ba tare da kaya sun
zo ba sai suka hada kai suka je gidan sa
suka ritsa shi suka ce lallai sai ya fadi inda
kaya suke, a nan ne yaga babu sarki sai
Allah sai yace musu kaya dai ya siyar da
su, kudin kuma ya biya lawyer din da ya
dauka ya tsaya musu a court, kudin
hannunsa kuma da su ya biya kudin
shatar motar da suke je suka dawo da
kuma motar da aka dauki kayan, Dan haka
babu wani abu da ya rage wanda zai basu”.

"Wannan maganar ta bata musu rai sosai,
a take Dauda ya cire wuka ya soka wa yaya Malam a kahon zuci, a take ya fadi ya mutu, yan sanda kuna suka kama Dauda, bayan anyi shari'ar sa sai aka
yanke masa hukuncin daurin rai da rai". Ya sake yin shiru yana kallon expression din fuska ta. Ban taba tunanin wannan ne abinda ya faru da su Dauda ba ban kuma taba damuwa da lallai sai na san wani abu
a game da su ba. Lallai Allah mai yawan
hikima ma a cikin dukkan al'amuran sa.
Daddy yayi murmushi yana lura da yadda
labarin ya taba ni sai yace "ina fatan kin
gane abinda nake so ki fahimta a cikin
wannan labarin. When you leave all your
battles in God's hand, God will fight all
your battles for you. Za kuma ki samu
justice din da baki taba zata ba, justice
din da in ke kika yi fighting battle din to ba
zaki samu irin su ba.

Na sunkuyar da kaina ban ce komai ba,
Duk tunani na ya kara dagule wa. Har sai
da nayi masa sallama zan tafi sai ya kira
ni. Na juyo ina kallon sa sai yace "idan
kina son zuwa kura ba zan hana ki ba,
Duk da Safiya tace kar in barki ki je dan
tana gudun kar su biyo ki da sharri kamar
yadda suka yi mata. Amma ni ba zan hana
ki ba. Saboda na yarda cewa ba duk aka taru aka zama daya ba. Ba duk yayan Alhaji Haladu ne tantirai ba, tabbas ba za'a rasa na gari a cikin su wadanda zaki ¡ya yin zumunci da su ba".

Ranar haka na wuni da Ammie a cikin
zuciyata. Naji ina ta missing dinta sosai.
Da yamma sai na dauki mota na tafi gidan
Hajiya, a duk sanda kewar mahaifiya ta ta
dame ni gurin ta nake zuwa in ji sanyi a
raina. Ai kuwa munsha hira sosai har
saida bakina ya fara ciwo saboda dariya,
ta kuma ii dadin zuwa na fiye da yadda
nayi tunani. Da zan tafi sai ta bata rai
"Adamu bai kyauta min ba, bayan ya
dauke min Safiya ke ma kuma ya raba ni
da ke" na dawo gaban ta na durkusa nace
"Daddy bai raba mu ba Hajiya, abubuwa
ne suka dan yi min yawa a yanzu. Idan
komai ya warware zaki ke gani na sosai
insha Allah" ta bata rai "kullum haka kuke
cewa ai. Yaushe ne komai zai daidaita? Su
fa matsalolin duniya ba sa kare wa
Safiyya, in kin gama da wasu ma wasu ne
zasu taso, Just seize your moments
Safiyya, be happy when ever you can,
Enjoy your life saboda ita kuruciya guda
daya ce in ta tafi bata dawowa. Don't let
anyone snatch away your youth and your
happiness from you", Na zauna sosai ina
kallon ta nace "kin san wani abu Hajiya? I
think we need to spend more time together. Zan shirya mana zuwa Umrah insha Allah very soon daga ni sai ke. Muyi spending at least two weeks together
muna ibada. It is going to be fun" Hajiya
tayi murmushi tana jin dadi amma sai tace
"ni ina zan iya zuwa Umrah da wannan
kafar tawa Safiyya? Da yaya zanyi
dawafin?" Nace "don't worry zan tura ki a
kujerar guragu", Muka yi dariya tace "ai
kuwa zanji dadi in hakan ta kasance.
Dama nayi missing ka'aba sosai".

A ranar da daddare na yanke hukuncin
abinda zanyi, kamar yadda Hajiya ta bani
shawara, ba zan bar kowa yayi snatching
happiness dina from me ba, sannan kuma
kamar yadda Daddy ya bani shawara I
won't jeopardize the future of Junior and
my unborn kids for vengeance.

Sai dai ban yanke shawarar ba sai da na vi
istikara nayi addu'a sosai akai. Sannan na
gaya wa Daddy nace ya kira su uncle
Ahmad su zomu sake zama.

Ranar da suka zo da aka kira ni sai na
shiga gurin na tsaya a bakin kofa ina
kallon su, deciding a raina that that day is
going to be the last day da zamu zauna
meeting akan wannan issue din dan ma
basu karbi hukunci na ba sai da su cigaba
da yin meetings din su kadai ban da ni.

Dana shiga sai na zamu kujera na zauna
akai instead of kasan da nake zama. A
raina ina hoping da saka glasses dina but
I didn't because of Daddy. Umma ta samu
zuwa ita ma yau, kana gain ta kasan ta
sha jinya. Ban gaishe su ba ranar ita ma.
Ina zama uncle Ahmad ya mike ya zo
gaba na ya ajiye min wata farar takarda
akan cinyata yace "my resignation letter,
as you requested" sai naji raina yayi min
babu dadi but i didn't let that distract me
from abinda na saka a gaba na.
Daddy yana kallona yace "kin ce Mukhtar
yazo kina da magana da shi, gashi nan ya
zo tare da mu bakidaya. Wacce maganar ce zaki yi?" Na gyara zamana na kalli Mukhtar da yake can gefe
daya a zaune sai na dauko waya ta na
nemo number din barrister Umar a kira
shi tare da sakashi a speaker na kuma
ajiye wayar a kan dan table din da yake
gaba na,

Bata jima tana ringing ba ya dauka, na
gaishe shi ya amsa cikin kulawa, And then
I said "barrister Umar, ranar nan kace min
I can come to you whenever nake da any
legal issue" yace "tabbas, duk matsalar da kike da ita data danganci law kiyi min
magana, even if I cannot handle it I will
guide you to the right channel" nace
"good. Yanzu tambaya ce da ni. Ina so inji
menene hukuncin rape a Nigeria" cikin
nuna damuwa yace "rape kuma Safiyya? I
hope you are okay?" Nace "I am fine
barrister, we will discuss more on it if the
need arises" Yace "Okay. It depends
gaskiya. Ya danganta da circumstances
da abin ya faru a ciki, ya kuma danganta
da how good the lawyer representing the
case is. But the minimum is 10 years. The
maximum is life imprisonment. Ana iya
yanke hukuncin kisa ma in some cases
idan rape din yayi leading to death,
especially of small children" nagyada
kaina ina kallon Mukhtar wanda shima ni
yake kallo fuskar sa cike da damuwa nace
"okay na gane. Thank you. This rape case
da yasa nayi maka wannan maganar bai yi
leading to death ba, but it also involves
kidnapping, drugging, torturing and then
raping. How many years kake ganin za'a
samu?" Ya danyi shiru sannan yace
"gaskiya kin lissafa manya manyan
criminal offenses, any of which babban
offense ne. Like I said, it depends, but my
guess is a minimum of 30 years and
maximum of life imprisonment if the
lawyer is good and akwai evidence sosai" nace "akwai evidence, plenty, I even have
a recording of the culprit confessing the
crimes and emotionally blackmailing the
victim. And don't worry about the lawyer,
I can get a SAN" ya danyi dariya "you are
sounding so much like your mother. Of
course you can get a SAN. And a SAN can
get the culprit locked up for life" nace
"good. Then we are getting a SAN" nayi
kokarin katse kiran sai naji yace "I am
worried about you Safiyya are you okay?
Case din waye wannan?" Nace "Nagode
barrister, and don't worry about me I am
okay. Zamu yi magana later".

Na katse kiran ina kallon su, trying to
study them. Definitely Mukhtar da
¡yayensa sun tsorata, a raina nace "oh,
kace kuma ba ka tsoron a rufe ka,
mayaudari" ya gyara zama ya kai sau
biyar, Umma ce ta fara magana "Safiyya,
ni ban damu da rufe Mukhtar da zaki yi ko
ma me zakiyi masa ba, amma idan kika
fitar da maganar nan ba Mukhtar ka dai
zata shafa ba har damu baki daya, har da
kannen sa da basu ji ba basu gani ba, har
da abinda kika haifa da abinda zaku haifa
nan gaba. Martabar gidan gabaki daya
zaki rusa. Wannan shine zai zama
tambarin gidan nan na har abada. " na
juya ina kallon ta nace "martabar gidan
gabaki daya Mukhtar ya rusa a lokacin da ya aikata min abinda ya aikata. Dan haka
shine da laifin ba ni ba" Mommy tace
"haka ne, ni zan fi kowa ma son a rufe
Mukhtar har tsahon ransa dan shi ba
karamin mugun mutum bane ba amma ba
shi zaki duba ba. Bamu zaki duba ba.
Innocent yaron can zaki duba. Da kuma
sauran yaran da zasu zo nan gaba. Think
about it Safiyya" na gyara zama na nace
"nayi tunani akan maganar Mommy, i have
been thinking a lot about it. Na duba
innocents din kamar yadda kika ce.
Wannan shi yasa na kira ku yau a gaban
ku zan bawa Mukhtar options. It is either
this...." Na fada ina nuna waya ta, or two
other things"

Uncle Ahmad da sai a lokacin yayi
magana yace "what other things?" Nace
"na farko zai rubuta min takardar saki ya
bani. Na biyu zamu yi signing wani
contract ni da shi" duk suka yi shiru suna
kallo na sai nace "Yes, i am my mother's
daughter and I like signing legal
contracts" uncle Ahmad ya sake tambaya
"wacce irin contract ce?" Nace "farko I
will report to my team of lawyers and
informed them about what happened to
me. Zan rubuta komai in basu cewa on so
so date I was raped by an unknown
person har ma kuma na samu ciki na haihu on so so date. I will give them the details of everything, Ba zasu shigar da kara ba tunda babu
suspect. And then Mukhtar and I will sign
a contract na cewa he will never look at
me or my son ever again. Bana son ganin
shi a ko da kilomita goma daga inda ni ko
dana muke. Ballantana har ya bude baki
ya kira shi da sunan dan sa. He is not his
son. Ko a musulunci bashi da hadi
whatsoever with him. A duk kuwa ranar
da ya ambace shi a matsayin dansa, it
means my lawyers will have a suspect
and a take zasu shigar da kara and he will
be sentenced probably for life kamar
yadda kuka ji an fada yanzu. Ambatar
yaron da sunan dansa yana nufin yayi
confessing publicly to all the crimes da na
lissafa. Wannan contract din zata zauna
har bayan raina for as long as shi yana raye".

Na juya na kalli Daddy and I saw him
smiling. Na sake juyawa gurin su uncle
Ahmad nace "wannan shine decision
dina, at least maybe you will know that I
did all I can to protect the dignity of the
family, Ba kamar wasu ba",

Na koma na jingina da bayan kujera ta ina kallon su. Like I expected, Mukhtar ya fara
retaliating, "Abba wallahi ina sonta ba zan
iya rabuwa da ita ba. Ni gwara a yanke
min hukuncin, na yarda a rufe ni din. Ina son yaron shima... " Abba ya tashi ya wawwanke fuskar sa da mari, Umma ta kama fada ita ma, Mommy ma haka. I sat and watched…

As ina kallon su sai na fara lisssafin roles
din kowa a cikin su a kan wannan
maganar. Mommy have stood as my
mother tun ina yarinya but masifar son
kudin ta ya saka har yanxu na kasa
tantance gaskiyar son da take yi min. Son
kudin ne ya saka tayi ta kokarin cusa min
Mustapha a matsayin miji, har yanzu
kuma na ga alamar ba ta hakura ba. Son
kudin ne ya saka take prioritizing duk
abinda ya shafe ni over even Daddy, tana
ganin kamar hakan ne zai saka ko babu
ran Daddy in cigaba da kulawa da su ita
da yayan ta. Sai dai zuwa yanxu na
tabbatar bata fa hannu akan abinda ya
same ni, Umma have been good to me while
growing up, tana bani kulawa dai dai
gwargwado duk sanda naje gidan su hutu,
A lokacin da na fara makaranta a nan
Abuja ma da na zauna a gidan su ta bani
kulawa sosai. Sannan lokacin da Mukhtar ya fara cewa yana so na ta nuna amincewar ta da maganar dan har irin alkunyar nan ta fara nuna min ta surukai.
Da na ki karbar soyayyar sa, a bar gidan
su, sai dangantakar mu ta ragu sosai and I
did not blame her, babu uwar da zata so
ace ba'a son danta. But I thought she will
get over it with time. Sai kuma gani da
ciki, cikin shege, and sai kuma na zabi
Mukhtar din a matsayin wanda zan aura
to cover the cikin shegen da nayi. I think
kowacce uwa will do abinda Umma tavi ko
ma fiye da haka. Na fahimce ta. Wannan
kuma ya saka bani da grudges
whatsoever on her. And then uncle Ahmad. Uncle Ahmad bayan Daddy bani da wani father figure
kamar sa. Babu kuma wand aya
hidimtawa dukiyar Ammie da Daddy
kamar shi. He spent his entire life yana
aiki a karkashin su though not free tunda
duk abinda ya ke da shi daga gare su ne
but he gave it his best, Ita kuma dukiya
tana da zaki, mutane kadan ne zasu so
rabuwa da ita bayan sun dauki shekaru
suna juya ta. Wannan shi yasa ya nuna
goyon bayan saga aure na da Mukhtar
tun a karon farko, wannan kuma shi yasa
har a last zaman da muka yi ya ke cigaba
da kokarin cusa min Mukhtar din dan yana gain aure na da Mukhtar zai saka ya cigaba da juya dukiyar kuma ko babu ransa to dansa da jikokin sane akan
dukiyar, in babu raina ma sune zasu gaje
ni. Amma kuma bashi da hannu a cikin
abinda Mukhtar din yayi. Nayi kokarin dawo da hankali na kansu, har lokacin suna ta tafka rigima da
Mukhtar, na lura cewa ba karamin maruwa
fuskar Mukhtar tayi a gurin Uncle Ahmad
ba dan fuskar har tayi ja ta fara kumbura,
amma da yake ba shi da kunya still bai yi
shiru ba. Na juyar da kaina gefe na daina kallon su.
Na dauka uncle Ahmad zai cig6da
dagewa a kan abar aurena da Mukhtar, sai
kuma na lura cewa yanzu ya fahimci
hakan ba mai yiyuwa bane ba ya hakura.
And by submitting his resignation letter
yana nufin ya sallama komai ya kuma
hakura da komai. Da gaske uncle Ahmad huce haushin sa yake yi akan Mukhtar, dan bayan marikan
da yake zuba masa har da kafa ya saka ya
ke dukan sa. Ni dai sai na mike tsaye nayi
cikin gida na barsu anan. Na gama kuma
da wannan shafin. Ban yafe wa Mukhtar
ba kuma bana jin zan yafe masa. Amma na bar shi da Allah, na kuma san hukuncin da zai yanke masa yafi wanda alkali zai yanke masa idan na kai shi court.

Maman Maama✍🏻

Ina yan soyayya? Next post zamu tabo
muku Malam Muhammadun ku insha
Allah. Allah ya sa kar ya bada ku kuma😅[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Forty Seven : The Decision


*Free baking master class*
I'll be sharing delightfully delicious
recipes including how to make soft and
fluffy doughnut for *free* it's completely
free A-Z
Click the link below to join
Females only
https://chat.whatsapp.com/
DN5w2VPGPhE0gf3700F9k0
0704248974
Zan koyarda snacks kala 8 kyauta
acikinsu akwai yadda zakiyi doughnut me
laushi da dadi classes dinnam kyauta ne
daga farko har karshe
Danna wannam link kiyi joining
Mata kawai
Or contact
07042486974
To be added
https://chat.whatsapp.com/
DN5w2VPGPhE0gf3700F9ko

Safiyya.....

Ranar kwana nayi banyi bacci ba ina saka
da warwara, a fahimci abinda Daddy
yake nufi, amma sai dai kuma fahimtar ta
sa ta toshe min hanyar da na biyo kuma
na kasa ganin wata hanyar da zata bulle
da ni xuwa destination dina. Na tashi nayi
sallah na gaya wa Allah bukata ta na roje
shi ya bani mafita tunda dai ni bani da ita.
Sai wajen asuba na kwanta akan sallayar
nayi bacci, bayan anyi sallah na tashi nayi
sallah sannan na koma kan gado na
kwanta bacci mai nauyi ya dauke ni.

Ban farka ba sai da rana tayi sosai. Na
tashi nayi wanka na shirya ina jin kaina
yana yi min ciwo duk kuwa da cewa nayi
bacci mai nauyi amma na san damuwa ce
ta saka min ciwon kan. Na dauko waya ta
ina dubawa sai na ga sako daga Abdul
yana yi min mitar bana neman su sai in
sun neme ni "munyi fushi" ya turo tare da
hoton Junior ya bata rai ya turo baki, Sai
na samu kaina da yin dariya, He looks so
cute and innocent and doesn't deserve all
this, Na shafa fuskar sa ta cikin wayar sai
nace a hankali "hey you, It is going to be
okay. You are going to be okay, I promise"

Nayi replying Abdul tare da tsokanar sa
ina tambayar sa labarin amarya. Sai kuma na tashi na tafi part din Daddy dan gaishe
shi. Ina shiga na tarar da shi a falon sa
tare da Mustapha suna gwada wani
machine da aka siyo masa da zai taimaka
masa wajen zama da tashi ba tare da an
rike shi ba. Na zauna a gefe ina kallon su.
Mustapha might be a bad person but he
takes care of Daddy and I am greatful to
him for that.

Sai da suka gama sannan na karasa gurin
sa na gaishe shi sannan nace '
"sai yanzu na tashi. I slept in" ya zauna yana haki
saboda movements din da yayi sannan
yace min "maybe baki yi bacci da dare ba
ne ba ko?" Na sunkuya da kai nace "haka
ne Daddy. Ina ta tunani ne. I am still not
sure what I will do" yace "kin ci abinci?"
Na girgiza kai "no, shigowa nayi da ma mu
gaisa sai inje inci abincin" yace "good. Sai
kuma yayi shiru ya kwantar da kansa tare
da rufe idonsa,

Har na fara tunanin tashi ina gain maybe
bacci ya dauke shi sai kuma na ga ya
bude ido yana kallona yace "na taba baki
labarin siblings din Ammien ki?" Na gyara
zama, ina son labarin Ammie ko a gurin
waye ballantana a gurin Daddy, A gurin sa
da sauran mutane na hada labarin ta.
Nace "wanne labarin da ga ciki? Na yadda
suka yi sanadin rasuwar baba Hadiza da su Sauda ko kuma na yadda suka biyo ta
nan suka takurawa rayuwar ta?" Ya girgiza
kai yace "na abinda ya faru da su bayan
rasuwar ta" nace "Daddy you never talk
about anything related to rasuwar Ammie.
Labaran ka duk na sanda tana raye ne ba
ka taba bani labarin lokacin rasuwar ta ko
abinda ya far bayan rasuwar tata ba".

Yayi shiru yana kallon tv amma ba wai tvn
yake kalla ba. Ya dan jima sannan yace
"tabbas yan'uwa Safiya sun tsane ta ita
da yan'uwan ta, tsanar da har ta kaisu ga
aikata abubuwa da dama wadanda suka
zama sanadiyyar da Safiya ta rasa kowa
nata. Sannan kuma sai Allah ya daukaka
ta fiye da yadda bata yi tunani ba, fiye da
yadda suma ba su taba mafarki ba, and
they came back, zuciyoyin su still cike da
tsanar ta, they threatened her life, suka
kira ta da juya, suka kuma bita da
mugayen maganganu na sharri".

"A lokacin a irin daukakar da Safiya take
da shi idan da taga dama zsta iya batar da
su a duniya baki daya, idan da taga dama
zata iya kai su kara ta lissafo irin
abubuwan da suka aikata mata and she
can get a good lawyer da zai iya rufe mata
duk wanda yake da hannu a cikin abinda
ya same ta. But she didn't do that. She said sanda ta shiga gidan su yaga yadda Allah ya mayar da su ita kuma ta ga yadda Allah ya mayar da ita sai ta san
cewa Allah has already fought her battle
for her. Bata bukatar revenge. Ya riga yayi
mata. Amma sai ta ja jikinta daga gare su
dan gujewa sharrin su. Ko sanda suke
zuwa gidan nan. A cikin gidan nan sun
taba gaya mata ido da ido cewa tunda ita
juya ce bata haihuwa suna jira be ta mutu
su ci gadon ta. She could have sue them
a lokacin, but she didn't. She said taga
abinda Allah yay musu wancan karon,
wanna karon ma shi take jira yayi mata
komai. She just took some protective
measures and leave them with God".

"And then she died"

"Washegarin da ta rasu suka zo gidan
nan, Bus guda suka yo shata daga Kura
suka taho mazan su da matan su, yara da
manya, Sanda suka zo aka gaya min sai
nace a barsu su shigo, Na saka aka basu
dakuna biyu, maza aka basu daya a waje
mata kuma aka basu daya a cikin gida,
Amma tun a lokacin sai suka tayar da rigimar su dakunan ta suke so a bude musu a sama su a dakin ta zasu sauka. Lokacin kina ta koke koken ki na neman
mahaifiyar ki Sa'adatu da sauran mutane
suna ta fama da ke amma su ko a kin su.
Hajiya ta san ba alkhairi ne ya kawo su ba
dan haka ta hau saman ta rufe dakunan ta
rike key a hannun ta. Shikenan sai rikici.
Suka kafa maganganu na rashin mutunci
da izgilanci suke yiwa Hajiya, Sa'adatu
kuma da sauran mutane suka shiga ciki,
sai rigima ta tashi a gidan gaisuwa"

"Ni ina can ina cikin matsananciyar
damuwar abinda ya faru naji hayaniya. Ina
ji dama na san sune. Nan take na kira
police suka zo suka kwashe su
gabakidaya suka tafi dasu. Sai da suka
kwana a can. Ahmad ne yayi ta zirga-
zirga sannan daga baya nace a sake su
amma kar su dawo min gida. Su barni inji
da abinda yake damuna".

"Suka tafi din, amma basu hakura ba
ranar sadakar bakwai sai gasu sun dawo,
Mutane sun taru ana yi mata sadaka da
adduoin neman rahamar ubangiji amma
tun daga bakin gate suka fara zage zage,
wai suna so suga uban da zai hana su
shiga gidan, ai gidan ma yanzu nasu ne, ai
ance musu dama gidan tane kuma su ne magadan ta dan haka sun zo karbar gadon su. Har nayi niyyar sake kiran police sai Alhaji Nasir ya hana ni. Ya aika
aka shigo da su ya zaunar da su yace su
zauna avi mata addu'a tare da su sannan
sai a saurari maganar da suka zo da ita".

"Aka gama zaman addu'a aka tashi. Suka
sake zama da Alhaji Nasiru suka gaya
masa sun zone karbar dukiyar da ta mutu
ta bari, har da list din su a hannu na
abubuwan da aka gaya musu ta mallaka.
Alhaji Nasiru ace babu komai dama ai shi
gado Allah ya riga ya raba shi. Su je su
samo malamin da zai raba gadon sai su
zo a raba a basu. Suka ki tafiya, dan
sunce ko kudin motar da zasu koma kura
basu da shi jira suke sai an basu su samu
na mota a ciki, Alhaji Salisu ya sama musu
gurin zama, sannan ya nemo alkalin da zai
raba gado ya kawo ya hada su dashi,
sannan ni kuma aka ce in bayar da abinda
ta bari wanda za'a raba".

"Ban je gurin ba dama nace ba zan je ba,
sai na tura barrister Umar da sauran
lawyers din ta suke managing affairs dinta
suka je, suka gabatar da lissafin
abubuwan da ta mutu ta bari wadanda
suke nata. Wadannan sun hada da
wadansu daga cikin kayan sskawarta, sauran tarkacen irin na mata, da kuma kudin da yake cikin account din ta. Ko mota bata da ita. Nan take sabuwar
rigima ta rikice dan ma Allah yasa na gaya
wa barrister su tafi da security dan babu
abinda ba zai iya faruwa ba. Ai kam dai
ance Dauda wuka ya fitar yace sai ya illata
barrister Umar".

"Nan take suka shigar da kara Court akan
an cinye musu gadon yar'uwar su data
mutu ta bar musu. Zama daya aka yi wa
shari'ar alkali ya kori karar tunda basu da
hujjar cewa wadannan kadarori da suka
lissafa nata ne. Dan ga takardu lawyers
din mu sunje da su da suke nuna duk
kadarorin nan naki ne ba nata bane ba.
Daga nan suka sake kai kara kotun
musulunci. Sunce waccan kotun kafurci
ake yi a ciki. A wannan zaman court din
ne naje, na kuma yiwa alkali bayanin duk
abinda Safiya tayi sanda tana da rai kuma
cikin koshin lafiyar ta. Ta baki kyautar komai da ta mallaka kuma ke ce kadai yar ta a duniya. Na kuma nuna masa abinda ta mutu ta bari a matsayin
nata. Sannan nace ni da ke mun yate
gadon Safiya, abinda ta bari din mun bar
musu su rike"

"A take alkali ya tabbatar musu da cewa
Musulunci ya yarda da abinda Safiya tayi,
dan haka abinda na nuna musu din shine
kawai abinda za'a raba a matsayin gadon
ta, sannan kuma yace ni da ke musulunci
bai bamu damar cewa mun yafe gado ba,
ba'a yafe gado, dole sai an bamu sai dai
in an bamu mu bayar in bama so"

"Still sai suka tayar da rigimar wai ai kayan
sakawa kadai na fito da su banda kayan
daki, su sun san cewa kowacce mace
tana da kayan dakin ta a gidan mijinta dan
haka sai na fito da su gado da kujeru da
sauran su ai suma kayan ta ne. Ni kuma
na san sanda na sayi gidan nan na saka
aka zuba komai a cikin sa, tabbas safiya
ta sai abubuwa itama amma ba ma
zanniya ware abinda ta siya da wanda na
siya ba dan haka nace su zo su dauka.
Ahmad yana ta bala'i nace ya barsu suzo
su dauka. Na zo gida na kwashe duk
abinda na san mai daraja ne kuma ta baki
tun tana da rai, irin su gwala-gwalai da
manyan suturu da designer perfumes din
ta duk na adana a bangare na, Duk abinda
yake bangaren ta kuma nace azo a dauka,
Hatta carpet da labule ba'a bari ba sai da
suka cire, Hatta cutlary set sai da suka
dauke daga kitchen. Cokali basu bari ba,
Har da mugunta, abinda aka ga ba zai
dauku ba sai a fasa shi. Ban ce komai ba
dan ni ta kaina nake yi. Duniyar ma ta fita daga kaina ballantana kayan da suke cikin
ta. Suka kai alkali aka yiwa kaya kudi aka
fitar da nawa da naki sauran aka basu. Ni
dai ban sake komawa court din ba.
Abinda aka bamu ma nace da Ahmad yaje
yayi sadaka da su Allah ya kai mata ladan
kabarin ta. Daga lokacin naji gidan gabaki
daya ya fita daga kaina ba zan iya cigaba
da zama a cikin sa ba. It holds a lot of
good and bad memories for the both of
us dan kema a lokacin kamar kinfi kukan
neman ta in muka shigo gidan. A lokacin
ne na yanke hukunci komawa Kano da
zama to ease the pain for us".

Yayi shiru yana hutawa, idon sa yayi ja,
har yanzu mutuwar Ammie tana damun sa
sosai and I couldn't imagine going
through the pain of loosing her at the
same time kuma da wannan bacin ran na
yan'uwan ta. Ga kuma ni da na saka shi a
gaba da rigima kullum.

Muka cigaba da yin shiru sannan nace
"Daddy to ba ka gaya min ba" yace "ban
gaya miki me ba?" Nace "sanda zaka fara
magana kace zaka bani labarin abinda ya
faru da su bayan rasuwar ta. Menene ya
faru da su?" Ya dan yi gyaran murya yace
"a labarin da aka bani, Tun a gaban alkalin
da ya raba gadon suka fara rigima akan
abinda aka basu, matan suna ta zabar
kayan sakawa daga cikin kayan da suka samu. Sai babban su, Yaya Malam, ya kwace komai daga hannun kowa yace su bari sai sun je gida sai suyi nasu rabon.
Ya dauko shatar motar diban kaya aka
kwashe duk kayan aka zuba a ciki, cash
din kuma ya karba ya rike a hannun sa, su
kuma suka shiga mota suka koma Kura
gabakidayan su"

"Daga baya Jamilu dan marigayiya Hajiya
Kyauta, shi yake bani labarin abinda ya
faru da su. Yace bayan sun je gida suka yi
ta jiran motar kaya tazo shiru shiru mota
bata zo ba. Tun suna tunanin matsala
motar ta samu a hanya har suka fara
tuhumar yaya Malam akan inda kaya suka
makale, da farko yayi ta basu uzurirruka
masu cike da karaiyayi. Daga baya bayan
an debi tsahon lokaci ba tare da kaya sun
zo ba sai suka hada kai suka je gidan sa
suka ritsa shi suka ce lallai sai ya fadi inda
kaya suke, a nan ne yaga babu sarki sai
Allah sai yace musu kaya dai ya siyar da
su, kudin kuma ya biya lawyer din da ya
dauka ya tsaya musu a court, kudin
hannunsa kuma da su ya biya kudin
shatar motar da suke je suka dawo da
kuma motar da aka dauki kayan, Dan haka
babu wani abu da ya rage wanda zai basu”.

"Wannan maganar ta bata musu rai sosai,
a take Dauda ya cire wuka ya soka wa yaya Malam a kahon zuci, a take ya fadi ya mutu, yan sanda kuna suka kama Dauda, bayan anyi shari'ar sa sai aka
yanke masa hukuncin daurin rai da rai". Ya sake yin shiru yana kallon expression din fuska ta. Ban taba tunanin wannan ne abinda ya faru da su Dauda ba ban kuma taba damuwa da lallai sai na san wani abu
a game da su ba. Lallai Allah mai yawan
hikima ma a cikin dukkan al'amuran sa.
Daddy yayi murmushi yana lura da yadda
labarin ya taba ni sai yace "ina fatan kin
gane abinda nake so ki fahimta a cikin
wannan labarin. When you leave all your
battles in God's hand, God will fight all
your battles for you. Za kuma ki samu
justice din da baki taba zata ba, justice
din da in ke kika yi fighting battle din to ba
zaki samu irin su ba.

Na sunkuyar da kaina ban ce komai ba,
Duk tunani na ya kara dagule wa. Har sai
da nayi masa sallama zan tafi sai ya kira
ni. Na juyo ina kallon sa sai yace "idan
kina son zuwa kura ba zan hana ki ba,
Duk da Safiya tace kar in barki ki je dan
tana gudun kar su biyo ki da sharri kamar
yadda suka yi mata. Amma ni ba zan hana
ki ba. Saboda na yarda cewa ba duk aka taru aka zama daya ba. Ba duk yayan Alhaji Haladu ne tantirai ba, tabbas ba za'a rasa na gari a cikin su wadanda zaki ¡ya yin zumunci da su ba".

Ranar haka na wuni da Ammie a cikin
zuciyata. Naji ina ta missing dinta sosai.
Da yamma sai na dauki mota na tafi gidan
Hajiya, a duk sanda kewar mahaifiya ta ta
dame ni gurin ta nake zuwa in ji sanyi a
raina. Ai kuwa munsha hira sosai har
saida bakina ya fara ciwo saboda dariya,
ta kuma ii dadin zuwa na fiye da yadda
nayi tunani. Da zan tafi sai ta bata rai
"Adamu bai kyauta min ba, bayan ya
dauke min Safiya ke ma kuma ya raba ni
da ke" na dawo gaban ta na durkusa nace
"Daddy bai raba mu ba Hajiya, abubuwa
ne suka dan yi min yawa a yanzu. Idan
komai ya warware zaki ke gani na sosai
insha Allah" ta bata rai "kullum haka kuke
cewa ai. Yaushe ne komai zai daidaita? Su
fa matsalolin duniya ba sa kare wa
Safiyya, in kin gama da wasu ma wasu ne
zasu taso, Just seize your moments
Safiyya, be happy when ever you can,
Enjoy your life saboda ita kuruciya guda
daya ce in ta tafi bata dawowa. Don't let
anyone snatch away your youth and your
happiness from you", Na zauna sosai ina
kallon ta nace "kin san wani abu Hajiya? I
think we need to spend more time together. Zan shirya mana zuwa Umrah insha Allah very soon daga ni sai ke. Muyi spending at least two weeks together
muna ibada. It is going to be fun" Hajiya
tayi murmushi tana jin dadi amma sai tace
"ni ina zan iya zuwa Umrah da wannan
kafar tawa Safiyya? Da yaya zanyi
dawafin?" Nace "don't worry zan tura ki a
kujerar guragu", Muka yi dariya tace "ai
kuwa zanji dadi in hakan ta kasance.
Dama nayi missing ka'aba sosai".

A ranar da daddare na yanke hukuncin
abinda zanyi, kamar yadda Hajiya ta bani
shawara, ba zan bar kowa yayi snatching
happiness dina from me ba, sannan kuma
kamar yadda Daddy ya bani shawara I
won't jeopardize the future of Junior and
my unborn kids for vengeance.

Sai dai ban yanke shawarar ba sai da na vi
istikara nayi addu'a sosai akai. Sannan na
gaya wa Daddy nace ya kira su uncle
Ahmad su zomu sake zama.

Ranar da suka zo da aka kira ni sai na
shiga gurin na tsaya a bakin kofa ina
kallon su, deciding a raina that that day is
going to be the last day da zamu zauna
meeting akan wannan issue din dan ma
basu karbi hukunci na ba sai da su cigaba
da yin meetings din su kadai ban da ni.

Dana shiga sai na zamu kujera na zauna
akai instead of kasan da nake zama. A
raina ina hoping da saka glasses dina but
I didn't because of Daddy. Umma ta samu
zuwa ita ma yau, kana gain ta kasan ta
sha jinya. Ban gaishe su ba ranar ita ma.
Ina zama uncle Ahmad ya mike ya zo
gaba na ya ajiye min wata farar takarda
akan cinyata yace "my resignation letter,
as you requested" sai naji raina yayi min
babu dadi but i didn't let that distract me
from abinda na saka a gaba na.
Daddy yana kallona yace "kin ce Mukhtar
yazo kina da magana da shi, gashi nan ya
zo tare da mu bakidaya. Wacce maganar ce zaki yi?" Na gyara zamana na kalli Mukhtar da yake can gefe
daya a zaune sai na dauko waya ta na
nemo number din barrister Umar a kira
shi tare da sakashi a speaker na kuma
ajiye wayar a kan dan table din da yake
gaba na,

Bata jima tana ringing ba ya dauka, na
gaishe shi ya amsa cikin kulawa, And then
I said "barrister Umar, ranar nan kace min
I can come to you whenever nake da any
legal issue" yace "tabbas, duk matsalar da kike da ita data danganci law kiyi min
magana, even if I cannot handle it I will
guide you to the right channel" nace
"good. Yanzu tambaya ce da ni. Ina so inji
menene hukuncin rape a Nigeria" cikin
nuna damuwa yace "rape kuma Safiyya? I
hope you are okay?" Nace "I am fine
barrister, we will discuss more on it if the
need arises" Yace "Okay. It depends
gaskiya. Ya danganta da circumstances
da abin ya faru a ciki, ya kuma danganta
da how good the lawyer representing the
case is. But the minimum is 10 years. The
maximum is life imprisonment. Ana iya
yanke hukuncin kisa ma in some cases
idan rape din yayi leading to death,
especially of small children" nagyada
kaina ina kallon Mukhtar wanda shima ni
yake kallo fuskar sa cike da damuwa nace
"okay na gane. Thank you. This rape case
da yasa nayi maka wannan maganar bai yi
leading to death ba, but it also involves
kidnapping, drugging, torturing and then
raping. How many years kake ganin za'a
samu?" Ya danyi shiru sannan yace
"gaskiya kin lissafa manya manyan
criminal offenses, any of which babban
offense ne. Like I said, it depends, but my
guess is a minimum of 30 years and
maximum of life imprisonment if the
lawyer is good and akwai evidence sosai" nace "akwai evidence, plenty, I even have
a recording of the culprit confessing the
crimes and emotionally blackmailing the
victim. And don't worry about the lawyer,
I can get a SAN" ya danyi dariya "you are
sounding so much like your mother. Of
course you can get a SAN. And a SAN can
get the culprit locked up for life" nace
"good. Then we are getting a SAN" nayi
kokarin katse kiran sai naji yace "I am
worried about you Safiyya are you okay?
Case din waye wannan?" Nace "Nagode
barrister, and don't worry about me I am
okay. Zamu yi magana later".

Na katse kiran ina kallon su, trying to
study them. Definitely Mukhtar da
¡yayensa sun tsorata, a raina nace "oh,
kace kuma ba ka tsoron a rufe ka,
mayaudari" ya gyara zama ya kai sau
biyar, Umma ce ta fara magana "Safiyya,
ni ban damu da rufe Mukhtar da zaki yi ko
ma me zakiyi masa ba, amma idan kika
fitar da maganar nan ba Mukhtar ka dai
zata shafa ba har damu baki daya, har da
kannen sa da basu ji ba basu gani ba, har
da abinda kika haifa da abinda zaku haifa
nan gaba. Martabar gidan gabaki daya
zaki rusa. Wannan shine zai zama
tambarin gidan nan na har abada. " na
juya ina kallon ta nace "martabar gidan
gabaki daya Mukhtar ya rusa a lokacin da ya aikata min abinda ya aikata. Dan haka
shine da laifin ba ni ba" Mommy tace
"haka ne, ni zan fi kowa ma son a rufe
Mukhtar har tsahon ransa dan shi ba
karamin mugun mutum bane ba amma ba
shi zaki duba ba. Bamu zaki duba ba.
Innocent yaron can zaki duba. Da kuma
sauran yaran da zasu zo nan gaba. Think
about it Safiyya" na gyara zama na nace
"nayi tunani akan maganar Mommy, i have
been thinking a lot about it. Na duba
innocents din kamar yadda kika ce.
Wannan shi yasa na kira ku yau a gaban
ku zan bawa Mukhtar options. It is either
this...." Na fada ina nuna waya ta, or two
other things"

Uncle Ahmad da sai a lokacin yayi
magana yace "what other things?" Nace
"na farko zai rubuta min takardar saki ya
bani. Na biyu zamu yi signing wani
contract ni da shi" duk suka yi shiru suna
kallo na sai nace "Yes, i am my mother's
daughter and I like signing legal
contracts" uncle Ahmad ya sake tambaya
"wacce irin contract ce?" Nace "farko I
will report to my team of lawyers and
informed them about what happened to
me. Zan rubuta komai in basu cewa on so
so date I was raped by an unknown
person har ma kuma na samu ciki na haihu on so so date. I will give them the details of everything, Ba zasu shigar da kara ba tunda babu
suspect. And then Mukhtar and I will sign
a contract na cewa he will never look at
me or my son ever again. Bana son ganin
shi a ko da kilomita goma daga inda ni ko
dana muke. Ballantana har ya bude baki
ya kira shi da sunan dan sa. He is not his
son. Ko a musulunci bashi da hadi
whatsoever with him. A duk kuwa ranar
da ya ambace shi a matsayin dansa, it
means my lawyers will have a suspect
and a take zasu shigar da kara and he will
be sentenced probably for life kamar
yadda kuka ji an fada yanzu. Ambatar
yaron da sunan dansa yana nufin yayi
confessing publicly to all the crimes da na
lissafa. Wannan contract din zata zauna
har bayan raina for as long as shi yana raye".

Na juya na kalli Daddy and I saw him
smiling. Na sake juyawa gurin su uncle
Ahmad nace "wannan shine decision
dina, at least maybe you will know that I
did all I can to protect the dignity of the
family, Ba kamar wasu ba",

Na koma na jingina da bayan kujera ta ina kallon su. Like I expected, Mukhtar ya fara
retaliating, "Abba wallahi ina sonta ba zan
iya rabuwa da ita ba. Ni gwara a yanke
min hukuncin, na yarda a rufe ni din. Ina son yaron shima... " Abba ya tashi ya wawwanke fuskar sa da mari, Umma ta kama fada ita ma, Mommy ma haka. I sat and watched…

As ina kallon su sai na fara lisssafin roles
din kowa a cikin su a kan wannan
maganar. Mommy have stood as my
mother tun ina yarinya but masifar son
kudin ta ya saka har yanxu na kasa
tantance gaskiyar son da take yi min. Son
kudin ne ya saka tayi ta kokarin cusa min
Mustapha a matsayin miji, har yanzu
kuma na ga alamar ba ta hakura ba. Son
kudin ne ya saka take prioritizing duk
abinda ya shafe ni over even Daddy, tana
ganin kamar hakan ne zai saka ko babu
ran Daddy in cigaba da kulawa da su ita
da yayan ta. Sai dai zuwa yanxu na
tabbatar bata fa hannu akan abinda ya
same ni, Umma have been good to me while
growing up, tana bani kulawa dai dai
gwargwado duk sanda naje gidan su hutu,
A lokacin da na fara makaranta a nan
Abuja ma da na zauna a gidan su ta bani
kulawa sosai. Sannan lokacin da Mukhtar ya fara cewa yana so na ta nuna amincewar ta da maganar dan har irin alkunyar nan ta fara nuna min ta surukai.
Da na ki karbar soyayyar sa, a bar gidan
su, sai dangantakar mu ta ragu sosai and I
did not blame her, babu uwar da zata so
ace ba'a son danta. But I thought she will
get over it with time. Sai kuma gani da
ciki, cikin shege, and sai kuma na zabi
Mukhtar din a matsayin wanda zan aura
to cover the cikin shegen da nayi. I think
kowacce uwa will do abinda Umma tavi ko
ma fiye da haka. Na fahimce ta. Wannan
kuma ya saka bani da grudges
whatsoever on her. And then uncle Ahmad. Uncle Ahmad bayan Daddy bani da wani father figure
kamar sa. Babu kuma wand aya
hidimtawa dukiyar Ammie da Daddy
kamar shi. He spent his entire life yana
aiki a karkashin su though not free tunda
duk abinda ya ke da shi daga gare su ne
but he gave it his best, Ita kuma dukiya
tana da zaki, mutane kadan ne zasu so
rabuwa da ita bayan sun dauki shekaru
suna juya ta. Wannan shi yasa ya nuna
goyon bayan saga aure na da Mukhtar
tun a karon farko, wannan kuma shi yasa
har a last zaman da muka yi ya ke cigaba
da kokarin cusa min Mukhtar din dan yana gain aure na da Mukhtar zai saka ya cigaba da juya dukiyar kuma ko babu ransa to dansa da jikokin sane akan
dukiyar, in babu raina ma sune zasu gaje
ni. Amma kuma bashi da hannu a cikin
abinda Mukhtar din yayi. Nayi kokarin dawo da hankali na kansu, har lokacin suna ta tafka rigima da
Mukhtar, na lura cewa ba karamin maruwa
fuskar Mukhtar tayi a gurin Uncle Ahmad
ba dan fuskar har tayi ja ta fara kumbura,
amma da yake ba shi da kunya still bai yi
shiru ba. Na juyar da kaina gefe na daina kallon su.
Na dauka uncle Ahmad zai cig6da
dagewa a kan abar aurena da Mukhtar, sai
kuma na lura cewa yanzu ya fahimci
hakan ba mai yiyuwa bane ba ya hakura.
And by submitting his resignation letter
yana nufin ya sallama komai ya kuma
hakura da komai. Da gaske uncle Ahmad huce haushin sa yake yi akan Mukhtar, dan bayan marikan
da yake zuba masa har da kafa ya saka ya
ke dukan sa. Ni dai sai na mike tsaye nayi
cikin gida na barsu anan. Na gama kuma
da wannan shafin. Ban yafe wa Mukhtar
ba kuma bana jin zan yafe masa. Amma na bar shi da Allah, na kuma san hukuncin da zai yanke masa yafi wanda alkali zai yanke masa idan na kai shi court.

Maman Maama✍🏻

Ina yan soyayya? Next post zamu tabo
muku Malam Muhammadun ku insha
Allah. Allah ya sa kar ya bada ku kuma😅
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹


Episode Forty Eight: Busted!


Not Edited and typed when tired😴, so
expect a lot of typos

Him👳🏻‍♀️

Duk da kokarin Gidado na ganin cewa ya
dawo Nigeria da wuri amma hakan bai
samu ba sai da ya yi wata uku da barin
kasar, sai dai watan karshe yayi shine ba
cikin kwanciyar hankali ba dan sam bai
amince da idea din zaman Safina tare da
mahaifan sa ba. Yasan yarinyar is very
conniving and manipulative, yana tsoron
sharrin ta. Dan haka lokacin da zai dawo
din ma he tried to emotionally prepared
himself for koma menene zai tarar a gidan.

A ransa yayi ta lissafa scenarios, yana
hasaso sharrin da Safina zata iya shirya
masa a gurin iyayensa, duk yawancin
tunanin sa akan Safiyya ne, gani yake zata
iya creating karerayin da zasu kara bata
Safiyya a wajen su Mama, dan yasan dai
shi bata isa tayi masa karya a gurin
¡yayensa ba dan idan tayi ma tana yi zasu
san karya take yi. And that would be the worst mistake ever da zata yi a rayuwar auren su.

Ranar da zai zo already ya gaya wa Abba
da Mama, ya san kuma zai samu tarba ta
musamman daga Mama dan sai tambayar
sa take yi wanne kalar abinci yafi missing
tayi masa "ga Safina nan sai ta taya ni
muyi maka" yaji abincin har ya fita daga
kansa tun kafin a dafa shi yace "Mama
yarinyar nan ba iya girki tayi ba, in kika
bata zata bata min abinci ne" Mama tayi
dariya "na sani. Bata iya girki ba but she is
trying to learn, kusan kullum in ana abinci
a gidan nan sai ta shiga kitchen ta zauna,
kullum kuma tana tambayar abincin da
kafi so tana mayar da hankali a kai. Dan
dai ma bata da lafiya ne shi yasa dole ta
hakura da shiga kitchen din" yayi shiru bai
ce komai ba, shi baya son wannan zancen
rashin lafiyar Safina da Mama take yi
masa kullum, he doesn't want to talk
about it, he doesn't want to think about it.
Sai ta kara da cewa "yarinyar nan tana
son ka Muhammad" ya chanja topic "ba
sai kun aiko a dauko ni ba, muni magana
da Ya Amen zai zo ya dauke ni".

Har a jirgi lissafin abinda rayuwa tayi
keeping in store for him a Nigeria yayi ta
yi. Abinda ya riga yay coming in terms
with shine the fact that soyayyar Safiyya ita ce jarabawar rayuwar sa, yana kuma iyakacin kokarin sa na ganin cewa ya ci wanna jarabawar.


Kamar duk sanda ya hau jirgi, wannan
karon ma sai da ya tuna da ranar da suka
fara haduwa a jirgin, she was the most
sweetest girl and he was just a teenager.
There was nothing romantic about
haduwar ta su but it was the most
memorable thing about their relationship.

Yana sauka ya fito daga jirgi hasken rana
ya haske masa ido, ya daga hannu ya kare
fuskarsa and again ita ce ta fado masa a
rai with her collection of sun shades, a
cikin jakarta a cikin motarta a ko'ina take
ba ka raba ta da shades, tace suna kare
idonta daga hasken rana sannan suna
kare ta daga yan sa ido.

A cikin mota ya samu Al'ameen already
yana jiran sa. Ya bude boot din motar aka
saka wa Muhammad kayansa sannan
Muhammad din ya zagaya ya shiga motar
still yana kare rana da hannunsa,
Al'ameen ya tsaya yana kallonsa da
budadden baki "this one that you are
doing as if baka saba da rana ba so kake
a dauka cewa kai ba dan nan bane ba ko
me?"

Muhammad ya ajiye hannunsa ace "allah
Ya Amen ba ka ji ranar nan ba, har cikin
kwakwalwa ta nake jin ta" Muhammad
al'ameen ya tayar da motar yace
"welcome back to Nija" gidado yayi ajiyar
zuciya yace "home sweet home" sai dai
kuma a ransa bashi da tabbas din how
sweet the home will really be for him.

Al'ameen ya dan kalle shi yace "you look
good, you look really good, har wata kiba
naga kayi fa, and with that skin dole ka
nuna baka san rana ba" gidado ya dan
daga hannunsa yana kallon skin din
sannan ya tabe baki yace "change of
weather, just take me home kaji? Ka kaini
inga rabin rai na ko na san na dawo
Nigeria" Al'ameen yace cikin tsokana
"kaga angon Safina wanna doki haka?
ana ta missing amarya ko? Tunda ka bata
rabin ran ka mu babu komai zamu raba
the other half din" Gidado ya jefa masa
wata harara yace "Safina kuma? a'a ba
Safina ba Sa'adatu" Alameen yace
"wacece kuma saadatu? Kar dai kace min
new catch kayi" Muhammad yayi dariya sosai sannan yace "uwar safina nake nufi, sunanta Sa'adatu" Al'ameen yayi dariya shima yace "wallahi baka da kirki
Muhammad, warta fa kace, yanzu sunan
sirikar taka kake ambata kanka tsaye?"
Muhammad ya daga kafada yace "kai ka
jawo mata, why will you say she is my
rabin rai?" Alameen yace "then who is
your rabin rai? Am sure you are not
talking about that married girl k0? Ko har
yanzu bamu wuce gurin ba?" Muhammad
yace "I was talking about Mama. Mama is
my rabin rai please. And don't mention
that girl's name. let the sleeping dog lay"
Muhammad Alameen bai ja maganar ba
kamar yadda gidado ya bukata, sai suka
koma hirar humaira da sauran family
members, daga nan kuma suka yi maganar various businesses din su da yadda suke adjusting to their
responsibilities.

Ana bude musu gate mama ta bude kofa
ta tsaya tana kallon su har suka yi packing
suka fito a tare, Gidado yana fadada
murmushin sa yace "Mamana" sannan ya
karasa inda take da sauri ya rungume ta,
gabaki dayanta iya kirjinsa ta tsaya.
Alameen ya karaso sai ta saki Muhammad
tana amsa masa gaisuwar sa tare da
tambayar sa lafiyar Humairah, bai amsa
ba ya sunkuyar da kai yana shafa keya
cikin nuna jin kunya, mama tace "Allah dai
ya sauke ta lafiya, Allah ya sauke su lafiya baki daya" Alameen ya amsa a hankali sannan yayi musu sallama yace zai koma office, Mama tayi kokarin ya shigo yayi
lunch amma yaki yace sauri yake yi.

Suna shiga ciki Muhammad ya zauna
akan kujera cikin nuna gajiya tare da fara
unbuttoning shirt din jikinsa, "akwai zafi
mama" mama ta karo karfin ac sannan ta
zo ta zauna tana kallonsa fuskarta cike da
farin cikin yanayin da ta ganshi a ciki "you
look good Muhammad. I was worried ko
baka samun abinci kana ci sosai" yayi
murmushi "ba sosai nake cin abincin ba
fa, ina ta missing abincinki, kawai dai ina
samun bacci ne sosai and the weather
there is good. Shine kawai. Ina abba?"
tace "yana office shi da Haidar" ta kalli
agogo "but they will soon be on their way".

Yaran gidan suka fara hidimar ajiye masa
kayan ciye ciyen da mama ta tanadar
masa. Ya zuba drink a cup yana tasting
sanyin sa sai yace da daya daga cikin
yaran "get me ice, saurj" mama tace "kai
dai kana son sanyi, ka sha ruwan sanyi ka
sha kankara kayi wanka da ruwan sany"
ya danyi murmushi bai ce komai ba. He
sometimes feels as if his blood is too hot
shi yasa yake cooling din sa down. Abu
mai sanyi yana calming dinsa kuma baya
saka shi ciwo.
Aka ajiye bowl of ice din a gabansa tare
da diba aka zuba a cikin drink din da
already ya riga ya zuba a cikin cup, ya
dago kansa suka hada ido da mai zuba
masa ice din. Ta sha kwalliya kamar ranar
ne zaa kai ta gidan miji. Jikinta sanye da
doguwar riga ta shadda da ta sha aikin
stones sai kyalli take yi, fuskarta with all
the make up possible, daga dukkan alamu
ma gidan kyalliya taje musamman aka yi
mata kwalliyar aka kuma daura mata
dankwalin kanta, hannayenta sun sha
both bakin lalle da ja. Fuskarta dauke da
murmushi.
Ta miko masa kofin tare da cewa "sannu
da zuwa" ya karba, amma maimakon ya
sha sai ya ajiye akan table din gabansa
tare da cewa "yauwa, sannunki". Ya juya
gurin Mama "Mama bara inje inyi sallah
tukunna" tace "gaskiya kam, kar ka ci
abinci jikin ka yayi nauyi ka kasa tashi.
Jiya na saka aka gyara maka dakin ka
dama. Yana bude" ya wuce da sauri zuwa
dakin nasa.

A can ya shiga toilet ya watsa ruwa ya
chanja kaya zuwa jallabiyya da wando
sannan yayi sallah azahar da laasar din da
yaji already an fara yi. Sai kuma ya dawo
falo, mama bata nan sai safina a zaune ta
dasa wa hanyar da zai fito ido, yayin mata kallo daya ya dauke kai yana jin gabansa yana faduwa, ta chanja, she looked a bit like abinda baya son ya ambata ko da
kuwa a zuciyarsa ne, she cannot be. It is not possible. Amma shi ya san cewa it is very possible kawai yana so yay denying ne to protect his heart. Ya dauki wani cup din, ignoring wancan da safina ta taba, ya sake zuba ice sannan ya zuba drink a kai ya zauna yana
jujjuyawa a hannunsa har sai da yayi masa
sanyin da yake so sannan ya daga ya
shanye ya kuma hada wani ya ajiye. Ta
sauko daga kan kujerar da take kai zuwa
gabansa tace "me za'a zuba maka?
Akwai.... " Ya katse ta "I know menene
akwai, so just shut your hole please. And
please get out of my site ina son zama da
family na" ta gyara zaman ta a gabansa
tace "I am your family" ta shafa marar ta a
hankali tace "we are your family" ya mike
tsaye yana jin kamar yayi ball da kayan da
suke gabansa. "goddammit" ya fada a
hankali, almost inaudible dan yasan ko da
wasa mama taji yana yin zagi sai ransa ya
baci.

A lokacin abba ya shigo, haidar yana
binsa a baya da briefcase a hannunsa,
duk su biyun suka saki murmushin ganin Muhammad, ya juya gurinsu shima yana
kirkirar murmushi duk kuwa da yadda
hankalinsa gabaki daya yake a tashe. Ya
je ya rungume abba sannan kuma ya
russuna ya gaishe shi, ya rungume haidar
shima, haidar yana kare masa kallo yace
"amma bread kake ci a can ko? Naga
kamar wanda aka saka maka yeast?
Mama da ta fito daga sashen ta da charbi
a hannunta jikinta sanye da hijab, daga
alama sallah tayi tace "tubarkallah". Abba
yayi dariya shima yana jin dadin ganin dan
nasa yace "zai zazzage ne ai, akwai aiki
da nake ta tara masa yana nan yana jiran
sa"
Safina da take zaune a gefe ta gaishe da
abba ya amsa mata tare da tambayar ta
jikin ta, bata ce komai ba ta sunkuyar da
kai tana murmushi, Haidar ya fara
tsokanar ta "yau da ya dawo, tagumi ya
kare. Nace wannan ciwon nata har da
rashin yaya" ta dan harare shi cikin wasa
amma bata ce komai ba sai mama tace
"kinyi sallah kuwa safina? Dan miji ya
dawo kuma sai ki zauna ki saka shi a gaba
kina kallo ba zaki je kiyi sallah ba?" safina
ta mike da sauri ta shiga wani daki da
yake cikin falon.

Suna zama sai ga mufida ta shigo gidan
da gudunta, tazo ta rungume Muhammad tana dariya, ya daga ta daga jikinsa hana murmushi, yana kin dadi a zuciyarsa "yar autar Mama, ke da nace miki zan zo har gida ina same ki?" Ta bata rai "da zaka
tafi ma cewa kayi zaka je muyi sallama
kuma ba ka je ba. Shi yasa naki jiran ka
yanzu" yace "ayi hakuri, nayi niyyar zuwa
wallahi sai abubuwa suka duke min
hankali, sai da na shiga jirgi na tuna" tace
"zanyi hakurin but I need one more
squeeze" ta fada tana kara rungume shi.

Bayan Mufida ta gaishe da kowa sai suka
hadu gabaki daya suka tafi dining suka
fara zuba abinci, tun kafin su fara ci sai ga
Safina ta dawo, fuskarta tana nan da
kwalliyar ta, tana shiga gurin Mufida tace
"hey in law! I was about to ask about you
sai na manta" Safina tace "nayi fushi ai.
Tunda kinga yayanki ai dole ki manta da
ni'" Mama ta juyo tana kallon Safina tace
"Safina wannan fuskar kuwa kin wanke
ta? Ta yaya kika yi alwala da wannan
kwalliyar?" Safina ta dan yi murmushi
nervously "Mama nayi, ai ba zata fita ba
dama" Mama ta girgiza kai "ai kuwa dai in
bata fita ba alwala ba tayi ba. Ki koma ki
wanke ta tas ki sake alwala ki sake Sallah.
Ai ya ga kwalliyar taki" Safina ta dan bata
rai "Mama nayi alwala kafin inje kwalliyar
fa" Mama tace "tun safe kenan? Alwala
tun safe har la'asar ai ya kamata a hakura da ita ko?" Safina ta juya ta koma ciki,

Mama ta gyara zaman ta tana cigaba da
zuba wa Abba abinci. Haidar yayi dariya,
Mufida tace "Mama kin ba da Safina a
gaban Haidar, a gaban kuma mijinta"
Mama tace"ga Abban ku nan a zaune
shima ai. Dole mu gyara mata mata
tarbiyyar ta ai, ko mijin nata ne yayi ba dai
dai ba dole a gyara masa ballantana ita,
she will soon become a mother, idan babu
tarbiyya ai mun shiga uku baki daya".

Muhammad ya kware da abincin da yake
ci. Abba ya zuba masa ruwa ya mika
masa, ya karba ya sha amma still yaji
abincin ya tsaya masa a makogwaronsa
ya ki wucewa, wani zafi yaji jikinsa ya
dauka. Ya fara panning fuskarsa da
hannayensa sai ya lura kowa na gurin shi
yake kallo. Abba yace "lafiyar ka kuwa?"
Muhammad ya sake daukan cokalin ya
debi abincin yace "lafiya lau.
I am not feeling good ne kawaj" Mama
tace "kace lafiya lau kuma kace you are
not feeling good, Wanne ne kenan? Kar fa
mu je ko heat stroke zaka samu dan tun
dazu kake complain din zafi" Haidar ya
mike tare da kara karfin ac sannan shima
ya tambaye shi "are you okay Yaya?" Muhammad ya kirkiri murmushi tare da gyada kai, yana jin babu dadin yadda duk suka shiga damuwa lokaci daya saboda
shi.

"It is okay. I am okay yanzu" ya fada yana
sake kai lomar abinci bakinsa duk da
waccan lomar har lokacin bata wuce ba. A
zuciyarsa ya san abinda duk wadannan
maganganun suke nufi amma ya kasa
barin kwakwalwarsa ta yarda. Mama tace
"'in ka cigaba da jin zafin dai kayi magana
aje asibiti, tun kafin abun ya zama babba"
ya gyada kai kawai tare da kokarin cigaba
da cin abincin da yake gabansa.

Sunanan zaune Safina ta sake dawowa, ta
wanke fuskar tas yanzu, daurin dankwalin
ma daga dukkan alama an kwance shi an
sake, Mama tace "yauwa, ko ke fa, yanzu
har kinfi kyau ma" ta danyi murmushi tana
sunkuyar da kanta kasa, Mama ta nuna
mata kujerar kusa da Mufida daga right
dinta tace "zauna to ke ma kici abinci, tun
safe banga kinci komai ba kina ta
kwalliya" sai ta zagaya ta zauna a left din
Mufida, kujerar da take kusa da
Muhammad. Ta zuba abinci ta fara ci,
yana jin idanunta a kansa amma bai ko
kalli inda take ba, he tried as much as he
can to not ruin the moment for his family.

Suka yi ta hirar su suna bashi labarin gida
yana basu labarin can. Bayan sun gama
kuma sai suka sake dawowa falo ya zauna
yana ta yiwa Abba bayanin tarukan da
yayi attending da matsayar da aka samu a
tarukan and what they mean to their business.

Suna nan tare har magrib, suka je suka yi
sallar suka sake dawowa suka cigaba da
hirar su, zuwa lokacin Muhammad ya dan
ware, trying not to look at side din da
Safina take zaune duk kuwa da cewa yana
jin yadda ta zuba masa ido a jikin sa.

Daga baya sai ga mijin Mufida yazo
daukan ta, shima ya shigo yayi joining
hirar ta su, sai kuma suka yi dinner tare
sannan Abba yace kowa ya zo ya tafi
gidan sa. Mufida ta fara tsokanar Safina
"Safina ki kara wa Mama ko sati biyu ne
mana" Mama tace "ina fa, ta tafi gidan
mijinta ya cigaba da jinyar a can. Tun dazu
dama na saka an kai yan aikinta gidan dan
su gyara musu kafin su tafi"

Babu kunya sai ga Safina ta jawo akwatin
kaya ta fita da su waje, tana ganin
Muhammad ya tashi kuwa tayi wa Mama
sallama, dama Abba ya riga ya shiga ciki,
ya fita ta riga Muhammad din shiga motar
ta zauna, maybe tana tsoron kar yayi
mata irin na ranar nan. Ya tsaya yana kallon ta kawai a ransa yana tunanin da ace daya motar tana nan da ita zai je ya shiga yayi tafiyar sa ya barta anan ya ga
yadda zata yi. Amma kuma Mama tana
tsaye a bakin kofa tana kallon su, yayi
sallama da su Mufida ya zo ya shiga
motar yana bata wuta Mama ta leko tace
"ka tafi a hankali fa, ban da gudu, kai a
guje dama kake driving dinka sai kace dan
tsere" yayi murmushi "to Mama, ba zanyi
gudu ba" tace "Allah ya sa" ya ja motar a
hankali suka fita daga gidan, amma ana
rute gate ya fige ta a guje saura kadan
Safina ta hantsula, tayi sauri ta gyara
zamanta tare da saka seat belt.

Suka fara tafiya da farko in silent, Allah
Allah yake yi suje gida ba tare da tayi
magana ba ballantana tayi confirming
abinda yake suspecting. Har ya fara
murnar ba zata yi ba sai kuma tayi din "ya
hanya?" Yayi kamar bai ji ta ba ya kara
gudun motar sa, sai kuma tace "you run
away, gashi kuma ka dawo" ya dan daga
kafarsa ya juyo yana kallon ta yace
"excuse me? Me kika ce?" Ta maimaita
"cewa nayi ka gudu, gashi kuma ka dawo"
yace "ban gane na gudu ba? Gudun me
zanyi? Run away from what?" Tace "you
run away from me" yace "and why will I
do that?" Tace "because you found out
that you cannot resist me. Shi yasa ka gudu"

Sai da ya danyi karamar dariya "you are
delusional. You and I know that that thing
that you think happened…….." Ta katse shi
"that I think happened? Kana nufin bai
faru kenan ba. Kana nufin I imagined it?
Okay wanne bangaren nay imagining the
first round or the second" yaji kamar yaje
ya jefa su a rami gabakidaya su mutu
kowa ya huta. Yana girgiza kansa cikin dacin rai yace "I wanted to not talk about it now, amma
tunda kin kawo topic din let me spell it out
for you. Na farko I did not run away from
you or from anything, na riga nayi
planning tafiya ta before that thing you
think is something happened. So idan
kina tunanin it means something to me ki
daina, it means nothing, you mean
nothing and will never be anything to me.
Abu na biyu kuma mafi muhimmanci
shine ni da ke gabakidaya mun san cewa
what happened that day wasn't natural,
you did something to me, I don't know
what amma ke kin sani kuma you are
going to tell me one way or another. Me
kika yi min?" Ya fada almost shouting.
Tayi kokarin matsawa daga kusa da shi
yadda ransa ya baci gani take kamar zai
kai mata duka.

"'Ba zaki fada ba?" Ya sake yi mata tsawa.
Ta rufe fuskarta da hannayenta da suka
sha lalle tace "ni banyi maka komai ba. Ni
babu abinda nayi maka". Yayi horn a bakin
gate mai gadi ya bude masa kofa ya shiga
da motar yaje yayi packing ya juyo yana
kallon ta "Ke munafuka ce Safina. Baki da
gaskiya ko kadan. Kin aikata abinda kika
aikata and you have the guts to spill out
trash from that hole in your face kina gaya
min maganar banza? You did something
to me ke ma kin sani, you thought idan
naje gadon ki I will fall in love with you ko?
Haka kike tunani? To abinda baki sani ba
shine what you did made me hate you the
more, made me despise you the more,
your gutter behavior and your trash of a
body disgust me. I am going to find out
what you did and I am going to use it as a
pass to my freedom from you". Ya bude
motar ya fita sannan ya buga kofar motar
da karfi.
Chapter 1 · 0% Book details