← Book details Budurwar Mijina Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 32

Sashe 30

Budurwar Mijina Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yana gama zuba miyan ya kawo sakwaran ya ajiye a gabana ya dauko ruwan wanke hannu da ruwan roba ya zauna tare da tankwashe kafarsa Yana "Bismillah"

"Na koshi"

"Lubna dan Allah ki bari, fushi da zuciya bazai canza abinda ya riga da ya faru ba dan Allah ki sauke fushin nan haka haba lubna"

Ya yanko sakwaran ya kawo bakina na kau da kai

K'arfi da yaji ya dage sai ya bani a baki hakane yasa na wanke hannuna na fara cin sakwarar Kamar ana min dole,har ga Allah Kuma yamin dadi,fuskata a hade har na gama cin Wanda Zan iya ci Yana Jana da hira nidai ban tanka masa ba har na wanke hannuna na Mik'e na dauki mimi nayi Palo na zauna.

Shi ya kwaso kwanukan ba jimawa yazo palon shima ya zauna shi kadai ya ringa hirarsa da eee Aa kawai na ringa binsa bana san fushin mummy ya tabbata a kaina.

A haka har aka Kira sallah la'asar yayi alwala ya fita massallaci nima nayi sallah na sake wanka tare da canja kayan jikina nayi zamana daki na dauko wayata na kunna data na hau WhatsApp.

Grps na Shiga nake dan bin hirar mutane har ya Kuma shigowa d'akin ya zauna Yana yiwa Mimi Wasa Ina latsa wayata Ina satar kallonsa idonsa na kaina sai sauke numfashi yake, na riga da nasan duk abinda yake yiwa bana san na cigaba da dorawa.kaina zunubi Addu'a nake Allah ya bani ikon daurewa idan ya sake nemana.

Bai bar dakin ba sai da aka fara kiraye kirayen sallah magriba da ya fita bai sake dawowa ba sai da aka yi sallah Isha.

A Palo ya tarar dani a zaune idan ta nice a koshe nake,sai dai ya nemowa kansa abinda zaici.

Yana shigowa yace na tashi mu dan fita baa machine zamu fita ba a machine Mai kafa uku zamu fita ya hada da na tayashi da Addu'a akwai kudin da yake sa rai idan ya shigo zai siyi mota.

"Idan ma aure zakayi wanan damuwarka ce ba inda zani sai ka dawo"

Ya dawo gefena da sauri ya zauna Yana "Lubna ba dan halina ba dan Allah ki tashi mu tafi"

Banza na bawa ajiyarsa ya cigaba da magiya yanda ya dagemin yasa na shige daki na canza kayan jikina zuwa doguwar Riga na yane mayafin akaina.

Shi ya goya mimi da jakar goyo ta gaba sai kallona yake ni kuwa na hade rai nasan so yake yace mayafin dana yafa yayi kadan ban saurare shi ba nayi gaba har muka fita titi ya tsayar Mana da abin hawa ya fada mishi inda zai kaimu.

Wayata nake latsawa har muka iso wajen da ake Shan ice cream yasan ni mayyar ice cream ce rabon ma daya siyomin tun Ina amarya.

Nidai binsa nake kawai a baya har muka iso wajen zama na zauna, ya miko min Mimi yaje ya fada musu kalar ice cream din daya keso a kawo daga Inda nake zaunen na ringa Kare Masa kallo.

Shigar kananan Kaya na balain yi Masa kyau so nake naga muninsa,amma na shagala da kallonsa Yana k'ok'arin jiyowa na d'auke kaina da sauri ya dawo ya zauna.

Muka hada ido ya sakar min murmushi na d'auke kaina aka kawo Mana ice cream din.

Ya mik'o hannu Yana na bashi Mimi naji dadin Shan ice cream din

Ban musa masa ba na mika masa Mimi na fara Shan ice cream din a hankali,har ga Allah naji dadi a raina, amma ban nuna hakan a fuskata ba sai ma Sha da nake a hankali kamar yamin dole,da alama masoya Nan suke zuwa har nawa namiji zai kashe ya kawo matarsa nan ya faranta Mata,mazan mu basa Mana adalci haka suke ajiyemu a gida su fito nan da Yan matan su waya sani ma ko ya kakawo Hadeeza nan take na hade rai naji ice cream din na neman fita a raina.

A hankali na saci kallonsa naga yana kallon wani waje hakane yasa na juya dan naga mai yake kallo,mace da namiji ne zaune macen ta bani baya yanayin jikinta Kamar na Hadeeza take naji gabana ya Fadi,na maido da kallona Kan Mahfuz da har lokacin yake kallonsu na Kara juyawa na kallesu,a daidai lokacin da namijin yake bawa yarinya ice cream a baki hannu daya mika yasa nagane a baki yake Bata amma banga fuskar macen ba,na Kara dawo da kallona Kan Mahfuz daa yanzu yake juya cokalin ice cream din ba Kuma Sha yake ba ni kuwa na zuba masa Ido Ina karantarsa hada Ido da mukayi yasa ya sakar min murmushi da a idona na yak'e ne yace "Kiyi ki gama mu tafi dare yanayi ko Kar Mimi ta kamu da mura"

Juyawa nayi na kara kallon wajen da dazu yake kallo sai dai har lokacin namijin kawai nake gani,macen bata jiyo ba,bansani ba ko hancina ne sai naji kamar kamshin turaren Hadeeza.

Kishi wata mahfuz keyi a gabana kenan take naji raina ya b'aci Yana k'ok'arin Magana nace "Sabida kaga Hadeeza da wani shine ka hade rai Mahfuz"

Ya gwallo Ido waje Yana "Kamarya lubna akwai wacce zanyi kishinta bayan ke ne ai babu dan Allah ki daina kiramin sunan ta ki gama Sha mu tafi"

"Na Gama"

Na juya na Kara kallon bayan yarinyar da Zan so ta juyo ba ma ja Hadeeza ce kamar na kwalla Mata Kira ta juyo Wanda kake kauna kake kishi,mahfuz ganin ta da wani ne yasa ya kasa Shan ice cream din,take naji zuciyata na min zafi daya barin Kuma sai naji dadin ganin daya Mata da wani duk abinan dai ban tabbatar da itace ko ba ita bace.

"Kaje wajenta Mana mahfuz Zan jiraka a waje"

"Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun haba lubna"

Ya dan fada da karfi idona na Kan yarinya dan burina ta juyo na ganta aikuwa muryar mahfuz da taji yasaka ta juyo, gabana yayi wani irin faduwa.

Bana Jin tagani ganin mahfuz yasaka ta mik'ewa tare da gwallo ido tana mahfuz gadan gadan tayo wajen mu har lokacin bata gani ba,

Kafin ta karaso mahfuz ya daka mata wani uban tsawan daya saka ta tsayawa cak

"Karki sake ki matso kusa dani,ki fita daga rayuwata Hadeeza daga yau bani bake, matata ta isheni rayuwa ki rabu dani Hadeeza idan Kuma kika k'i duk abinda na miki ke kika jawowa kanki"

Bansan Mai yasa naji sanyi da Dadi na ratsani ba,Koda baa har zuciya MahfuZ ya fadi haka ba ya faranta min dan ya disgata a gaban katon Alhajin da tazo dashi haka ma a gaban mutane.

Ido muka hada da ita idonta ya ciciko da hawaye na sakar mata murmushi na tsinci kaina da karasawa wajen da take tsaye Ina "Idan ke din ba jaka bace Kuma karuwa mai bin mazajen mutane sai ki hakura ki daina bibiyar mijina haka banza balagaza karuwa"

So nake tayi magana na d'auke ta da mari batayi magana ba har Mahfuz yazo ya janyeni

Muka bar wajen muna fita na fusge hannuna Ina "Wlh duk kishi yasaka kayi maganar da kayi,mahfuz ni ba yarinya bace wlh kana san yarinya nan ka sakeni kawai ka aurota"

"Lubna bansan Kuma Mai kikeso na miki bayan wanan ba agaban idonki dai kina ganin kashedin dana mata duk sabida na faranta miki rai haba lubna"

Ya kuwa faranta min din banaso na nuna masa ne ban Kara ce masa komai ba har muka Isa gida.

Da isarmu gida ya ajiye ledojin da ya dan yi siyayyarsa a ciki har dasu balangu a palo ni kuwa daki na shige na canjawa Mimi Pampers na bata abincinta ta Sha ta koshi

Kafin na Shiga bandaki nayi wanka na saka kayan bacci na haye gado raina fes dan na fara yarda mahfuz dagaske yake zai rabu da Hadeeza.

Shigowarsa yasa nayi saurin lumshe idona yace "bazaki ci balangun ba"?

" A koshe.nake"

Bai Kara cemin komai ba ya fice daga d'akin ba dadewa ya dawo d'akin Ina jinsa ya rufe kofa yazo ya kwanta a gefena a hankali ya matso kusa dani yamin rada a kunne "Ina bukatar ki pls kimin wanan taimakon dan Allah"

Ban motsa ba ya juyo dani,jiki da jini Ina karbar sakonsa amma haka na kwanta kamar ruwa na d'auka yi zaiyi sai ji nayi ya dagoni idona a rufe yake Ina k'ok'arin bude Idona naji jikinsa a bakina Yana shafa kaina.

Har ga Allah abinan amai yake Sakani nayita tofe tofen yawu har garin Allah ya waye janye kaina nayi na koma na kwanta,hakane yasa ya hakura jikinsa sai rawa yake kamar Wanda tab'a sanin mace ba har ya samu nutsuwarsa naji bacci ya d'auke shi nima Ina rufe Ido bacci yayi awon gaba dani...
MG'S SKINCARE

In akaji gangami labarin kidane,sun shahara sun tumbatsa sunkai sunwuce tunanin duk wani meson Adama dashi aharkar gyaranfata d walwalinta,

Yar uwa haske ko qyalqyale kikeso kiyi Abu yaci tura?
Kyan fuskarda ko yar uwarki mace kance dama dama kikeso?
Kokuma ke kuraje d tabbuna suka lahanta mki fuska har ake ganinki d wani idon n daban,
Nankarwace tayimiki zanen kura a kyakyawar fatarki?
Kokumade Mai kikashafa be amshekiba yasa duk kika koma ruwa biyu Nan fari Nan baqi?

To duk kuzo insha Allah kudai naku y qare gdan kukazo,

Munkawo shahararrun kayangyaran jiki
Sabulu,
Man shafawa,
Man fuska,
Scrub,
Cleanser,
Glow oil,
Dukdan qawarmaku d matsaltsalunku,

Da 11k kachal zatasa kihaske kizama kalar madara qirar models,

Set 11k
Sabulu 3k
Student package:7k
Munakuma bayarwa in pieces duk afarashin mesauki.kayanmu bbu fariya ko tutiya angwada andawo,ankumayi farinciki d hkan,Kuna iya samummu d wadannan numbobin,
WhatsApp,
08062991549 or 07046881166 or 07067210195
Call only
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Idanba wadannan numbobinba to gaskiya b mg's bane, available in Kaduna and Kano only, thanks for always trusting us,our returning customers we really do appreciate wadanda sukeda burin Siya munamaku fatan alkhairi ubangiji ybaku yenda zakuyi,Allah Kuma yqaro mna dukiya me amfani ta hanyar halalinmu

*WANAN NOVEL DIN NA KUDINE BIYA 500 zuwa 2029764071 first bank nafisa Nuhu sai a tura shaidar biya zuwa ga lambar Nan 08033719070 ko katin mtn mutanen Niger Airtel Kika min SHARING bansanki ba Allah Yana kallonki na barki dashi*

*Page 22*
Chapter 30 · 0% Book details