Part ɗin Nailarh su ka koma a nan su ka kwanta.
Shiryayyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 41 min read
*WASHE GARI*
A hakimce take saman sofa mai mazaunin mutum uku a katafaren main parlor gidan, PJ ne a jikinta, laptop ɗinta na ajiye saman table ɗin dake gaban sofa, a hankali take Operating ɗinta,Joseph na zaune saman sofa mai mazaunin mutum ɗaya, ya ɗau wankan black suit,rigar suit ɗin na ajiye saman hannun sofa da yake zaune, hannushi riƙe da fils.
daga gefe chief security ɗin gidan ne sai masu kula da C C TV sai drivers ɗin Nailarh da su Luna sai chefs,gaba ɗayan maids ɗin ne Aunty sophia ce kawai babu.
Aikin ko wane ta ke bincika dan sanin abun da ya faru bayan bata nan duk da suna sanar da ita abunda ke faruwa lokacin da bata nan, drivers ɗin Nailarh ta fara tsarewa da tambayar da bata nan ina da ina su ka kai Nailarh.
Alex ne ya shiga zayyana mata inda Nailarh taje bayan bata nan,shi ke driving motar Nailarh duk za su fita kuma shine shugaban drivers ɗin gidan baki ɗaya, jinjina kai ta shiga yi har ya kammala sanar da ita, maida hankalinta tayi kan su Luna suma dai magana ɗaya ce da Alex, sallamar su tayi su koma bakin aikin su.
Masu kula da C C TV gidan ne su ka fara kora mata bayanin kaf abunda ya faru,babban cikin su ne ya sanar da ita “ma'am still Sophia's CCTV doesn't work” jin jina kai tayi tana ɗan dakatawa da aikin da take
“duk gyaran da a ka yi?”
“yes ma'am” da kamar za tayi magana sai kuma ta fasa
“u can go” ta faɗa, gabanta ɗaya daga cikin su ya zo flash ya miƙa mata kafin ya fice.
tana cikin magana da Chefs Aunty sophia ta zo,kallo ɗaya za kayi mata ka hango tsantsar damuwar dake kwance a fuskarta,gaishe da miss Malika tayi da kulawa ta amsa mata “chefs sun ce baki lafiya,how do u feel now?”
“am feeling much better”
“I'm points hope quick recovery dear”
“thank U ma'am”
Nailarh ce ta fito daga bedroom ɗinta shirt da short ne a jikinta ta ɗaure gashin kanta da ribbon, ciki parlorn ta nufo, tunda ta fito su ka kafeta da ido musamman Joseph har wani ɗaga kai yake dan ya kalleta da kyau.
tana ƙarasowa tayi hugging ɗin Aunty sophia ta baya “good morning”
“morning baby, kin tashi lafiya”
“lafiya lau” Nailarh ta faɗa tana raba jikin su
“mi ya samu hannunki?” ta faɗa yayinda take riƙo hannun Aunty sophia
“yankewa nayi da glass”
“Ayyah, sorry chefs sun ce man baki da lafiya, mike damunki”
“it was a headache,but i got better now”
“is this tumor the cause you of the headache?” ta faɗa da tsantsar kulawa
girgiza mata kai Aunty sophia tayi “bashi bane”
“sorry” Nailarh ta faɗa kamar ƙaramar yarinya
jin jina mata kai Aunty sophia tayi.
mahaifiyarta dake zaune kan sofa ta nufa, ɗan rissinawa tayi ta sumbacin lips ɗinta, saurin rintse ido Aunty sophia tayi tana jin wani irin ɗaci a ranta.
“good morning” Nailarh ta faɗa
“morning beb” malika ta faɗa tana kashe mata ido ɗaya, kusa da ita ta zauna tana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya.
“good morning boss” Joseph ne ya faɗa, amsa mashi tayi tana ɗaga mashi hannu, gaishe da ita chefs ɗin dake tsaye su ka shiga yi da kulawa take amsa masu.
sallamar chefs ɗin miss Malika tayi bayan sun gama bata amsoshin tambayar da tayi masu, sofa dake kusa da wacce Joseph ke zaune miss malika ta nuna ma Aunty sophia, zama tayi tana fuskantar ta.
Ta sowa Joseph yayi daga mazauninshi files ɗin dake hannunshi ya miƙama miss Malika, amsa tayi tana jinjina mashi kai “zaka iya tafiya,idan na kammala dubawa zan tura maka replys ta email”
“ok ma'am, have a nice day” rigar suit ɗinshi dake ajiye kan hannun sofa ya nufa,ɗaukar rigar yayi haɗe da briefcase ɗin shi dake gefe “bye” ya faɗa yana ɗaga masu hannu, jinjina mashi kai miss Malika tayi, ficewa yayi daga parlorn.
ɗaya daga cikin chefs ne ya shigo hannunshi ɗauke da madaidaicin tray wanda ya shirya masu coffee, Nailarh ya nufa ya fara miƙa mata ta ɗauka kafin miss Malika da Aunty sophia, barin parlorn yayi ya koma kitchen.
“Sophia!” miss Malika ta kira sunanta, ɗagowa Aunty sophia tayi ta fuskanceta da kyau
“William ya sanar dani har yanzu C C TV part ɗinki bata aiki, what is the problem?” ta faɗa tana kafeta da ido
“nothing, but naga is not good ace har a bedroom da bathroom an sa mana camera ba, a barshi a iya parlor kawai,bedroom and bathroom is our part of secret” tunda ta fara magana Malika ta kafeta da ido
“but if that offends u, am very sorry”
“saboda bai dace ba yasa ki ka lalata na part ɗinki?” cike da tuhuma miss Malika ta faɗa
“please momy Aunty sophia ce fa, mi kike son sani a game da rayuwarta da har sai kin sa mata C C TV, gaskiya i'm really not happy” Nailarh ta faɗa da alamar rashin jin daɗin abunda momy tata tayi
“shikenan nima ba dan komai yasa nake sawa ba sai dan na riƙa sanin halin da ku ke ciki,taking care of ur health is my responsibility”
“hakan yana da da kyau,we thank u for ur care for us” Aunty sophia ta faɗa, jin jina kai kawai Malika tayi, tashi Aunty sophia tayi ta nufi kitchen dan ta duba chefs, da kallo Malika ta bita har ta ɓacce ma ganinta.
“honestly momy baki kyauta ba, how many years Aunty sophia ke tare dake dan mi zaki sa mata C C TV a part,wannan old women ɗin mi kike tunanin zata iya aikatawa, ban da kula dani babu abunda take a gidan nan, that's why I love her,babu ruwanta”
wani kallon banza Malika tayi mata“u love her, ban gane ba?”
“yeah, ina jinta tamkar mahaifiyata wacce ta haife ni” harara Malika ta watsa mata
“ni fa?”
“u are special,ur position is different sweetheart” murmushi Malika ta saki.
❤💫❤💫❤💫❤💫❤💫❤
Tun da malika ta dawo Aunty sophia ta ƙauracema Nailarh ko part ɗin ta ta daina zuwa, iya karta ta duba masu aiki ta koma part ɗinta,duk wata hanya data san zata haɗata da malika tare da Nailarh tayi blocking ɗinta.
Yanzu ma tana kitchen ne tare da chefs tana sanar da su abubuwan da ya kamata su yi saboda celebration ɗin da za suyi bayan kammala wasan da Nailarh zata gabatar a yau, dama al'adarta ne duk ƙareshen shekara suna gabatar da wasa wanda ya fi kowane a N R T.
Duk wanda yake ji da kanshi a wasan doki zaka sameshi a ranar gasar, ƙwararrune daga yanki daban daban na ƙasar dama wasu ƙasashen ke halartar wasan, tsawan shekara biyar kenan suna gabatar da wasan har yau ba'a samu wani wanda yayi zarrar da zai zo na ɗaya a gasar wasan ko wane lokaci Nailarh dai.
A hankali ta lallaɓo masu aiki na kallonta amma ba halin suyi magana saboda gargaɗin da tayi masu,hannuwanta tasa tana rufe mata eyes ɗinta ta baya.
Murmushi Aunty sophia ta saki ta san babu wanda zaiyi mata hakan face ita, hannunta dake kan idanunta ta kama
“baby” ta kira sunanta, sakin idanunta Nailarh tayi tana ɓata fuska
“u are too quick to recognize ” ta faɗa tana turo baki, murmushi chefs ɗin suka saki
“banda abunki Nailarh waye zai yiman haka bayan ke,how was ur night,I hope u slept well?”
“fine,na biyoki har nan ne dan naji laifin me na maki ki ke avoiding ɗina tow days?”
gaishe da ita chefs ɗin su ka shiga yi,jinjina masu kai kawai tayi, shafa fuskarta Aunty sophia tayi
“baki man laifin komai ba, na barki ki samu enough time with ur momy” taɓe baki Nailarh tayi
“amma ai kin zo har ɗaki kiyi wishing ɗi na ko?”
“kema kin san zan zo, ina duba chefs ne”
“baby!” aka faɗa daga bayan su, saurin kai dubansu su ka yi ga Miss Malika dake tsaye, PJ ne a jikinta da alama daga bacci take.
Cike da girmamawa suka shiga gaishe da ita, da kulawa ta amsa masu tana nufar cikin kitchen ɗin , kama hannun Nailarh tayi “ashe kina nan ki ka bar ni sai wahalar nemanki nake”
“nazo wajen Aunty sophia ne”
“ok muje” jan hannunta tayi
“Aunty sophia sai kin zo” jinjina mata kai tayi, ficewa su kayi daga kitchen ɗin.
*ABUJA NIGERIA💫*
Shigowar su kenan daga school duk a gajiye su ke,Yumnah tun a parlor ta cire mayafin dake kanta, a saman bed ɗinta su ka yada zango.
“wallahi sis am very tired
har ƙosawa nayi a kammala lectures” Yumnah ta faɗa tana ya mutse fuska
“me too, yanzu bani da wani buri da wuce na watsa ruwa na kwanta na huta before magrib” Nainarh ta faɗa tana nufar dressing room.
kwanciya saman bed ɗin Yumnah tayi “ni gaskiya sai na tashi daga baccin tukun zan yi wanka”
Nainarh na shiga dressing room ɗin jakarta ta a jiye tukun ta cire kayan jikinta ta ɗaura towel, bedroom ɗin ta koma, Yumnah na nan kwance har bacci ya fara ɗaukarta.
toilet ta nufa ta watsa ruwa kafin ta fito, dressing room ta koma,gown ta saka mara nauyi kafin ta dawo bedroom ɗin kwanciya tayi kusa da Yumnah.
Duk yanda take jin bacci kafin ta kwanta, tana kwanciya taji kwata kwata baccin ya ƙaurace ma idonta,juyi ta shiga yi a bed ɗin Yumnah kuwa baccinta take hankali kwance.
shiru tayi tana ƙurama sailing ido, ba komai ya faɗo mata a rai ba sai photon da ta gani a part ɗin Abbah, bata san waye a photon ba amma haka nan ta kwaɗaitu da san sanin waye shi, kullum tana son tambayar Yumnah amma sai ta manta.
kallon fuskar Yumnah tayi kafin ta maida idonta akan teddy bears ɗinta dake ajiye saman head board ɗin bed ɗin.
ƙaramin tun bata da wayau mahaifiyarta ta bata shi, babban kuwa mahaifinta ya bata shi a matsayi kyautar ƙarin shekara lokacin data kai kimanin shekara goma.
Murmushi ta saki lokacin data tuna shirmenta na yarinta, haka zata tasa teddys ɗin a gaba tana faɗin ga momy ga dady,haka iyayenta za su tasata gaba suna dariya, duk tana tuna rayuwarta da iyayenta abun ba ƙaramin nishaɗi yake bata ba,amma lokaci ɗaya komai ya rushe, duk ta tuna kisan wulaƙantaki da aka yima mahaifinta da sharrin da aka da bai baye mahaifiyarta dashi sai taji wani ƙunci ya mamaye zuciyarta, ta rasa laifin mi su ka aikatama wanda yayi masu haka.
Adu'arta a kullum Allah ya toni asirin wanda yayi silar rushewar farin cikin su, shima Allah ya rusa nashi farin cikin, ya tozarta rayuwarshi kamar yanda ya tozarta ta su, sosai tayi nisa a duniyar tunani ringing ɗin wayar Yumnah ne ya dawo da ita hayyacinta, a jiyar zuciya ta sauke tana jawo jakar, wayar ta ciro, duba sunan mai kira tayi,ya Naeem ta gani.
da sauri ta ɗan bubbuga kafaɗar Yumnah “ki tashi ya Naeem na kira” juya kwanciya Yumnah tayi
“please ki ɗaga kice mashi bacci nake” picking call ɗin tayi tana kara wayar a kunenta
“Assalamu Alaikum” ta faɗa, on the other hand ya Naeem ya amsa mata sallamar
“ya Naeem ina wuni”
“lafiya lau Yumnah, kun dawo ne ko har yanzu kuna school?”
“ba ita bace, Nainarh ce” Nainarh ta bashi amsa
“yawwa Nainarh dama ke nake nema, kun dawo daga school ɗin?”
“eh” ta bashi amsa
“ok,meet me in the garden now” a sakale ta amsa mashi,mamaki ne ya cikata, neman mi yake mata
“right now” ya sake jaddada mata haɗi da rejecting ɗin call ɗin
“ni kuma, neman mi yake man” ta faɗa da tsantsar mamaki, ajiye wayar tayi ta nufi toilet, bata wani jimaba ta fito, dressing room ta nufa, hijab ta ɗauko,ficewa tayi daga ɗakin.
bata samu kowa a parlorn ba, tun daga nesa ta hango su saman chairs shi da ya Adnan a garden ɗin, waya ce kare a kunen ya Naeem ɗin da alama waya yake, tunda ta tunkaro su ya Adnan ya kafeta da ido yana kallota harta ƙaraso in da su ke, sallama tayi masu ya Adnan ne ya amsa mata ya Naeem kuwa hannu kawai ya ɗaga mata.
Cike da ladabi tana ɗan rissinawa ta gaishe da Ya Adnan ɗin, da kulawa ya amsa mata yana sakar mata murmushi ya nuna mata chair dake fuskantar wacce su ke zaune dan ta zauna, murmushi ta saki “nagode” ta faɗa tana zama.
“ya school,fatan kun dawo lafiya?”
“lafiya lau Alhmdllh” masha Allah ya faɗa, hankalin su ne ya koma kan ya Naeem dake waya
“it's a favor i'm asking for, please ka taimaka ranar birthday ɗinka ka zo,ya ɗauki ranar birthday ɗinka rana mai daraja da mahimmaci, ka daure a wannan karon ka tabbatar mashi da darajar ranar,the anger u have with him is enough, dan Allah ka kawo ƙarshen wannan guje mashin da ka ke”
ɗan dakatawa yayi da magana ya can ya cigaba
“kayi shiru ba kace komai ba, ka sa ni yanda ya ke sonka ko mu dake tare dashi baya mana son da yake maka, baka tare dashi amma duk wani abu daya shafeka baya wasa dashi,ka sani duk abunda zaiyi mana a rayuwa sai yayi maka,more than u think,wasu har gani suke kamar ya samu taɓin hankali a kan ka saboda wasu abun da yake hankali ma bazai ɗauka, please yaci albarkacin wannan ƙaunar da yake maka kayi haƙuri ka daina wannan fushin da shi” sosai ya Naeem ya kwantar da murya yana bashi haƙuri duk dan ya sauko.
zuba mashi ido Nainarh da ya Adnan su kayi, lamarin yayi matuƙar ɗaure mata kai waye wannan ake haɗashi da Allah irin haka amma yaƙi yayi abunda ake so.
“shikenan kayi duk abunda ka ke ganin shine dai dai, amma ka sani haƙƙin baƙin cikin da kake cusa mashi bazai barka ba, he's ur father, ko wane irin laifi zaiyi maka aduniya he didn't not deserve to be anger with him” yana gama faɗar haka yayi rejecting call ɗin.
haka nan Nainarh ta tsinci kanta da rashin jin daɗin abun, bata san ko waye ba amma bai kyauta ba mahaifa ba abun wasa ba ne.
“in wuni ya Naeem”
“lafiya lau Nainarh, ya school”
da Alhmdllh ta amsa ma shi
“dama akwai wasu maganganu da nake son zamu tattauna game da abunda ya faru da dadynki”
tunda ya faɗi haka yanayin fuskarta ya canza, fahimtar hakan ne yasa shi cewa
“karki damu ba wani abu bane kawai ƴan tambayoyi ne zanyi maki,in dai ki ka bani haɗin kai in sha Allah za muyi nasarar gano wanda su ka kashe shi”
“in sha Allah zan baka haɗin kai, duk wani abu dana sani zanyi ƙoƙarin sanar da kai”
“yawwa haka nake son ji,
da na so muyi maganar yanzu,but bana da time, zuwa ranar Saturday za muyi magana ko kuje can gida keda Yumnah ku same ni”
“to shikenan, Allah ya kaimu”
“Ameen ya Allah, za ki iya tafiya kawai” to tace ta na tashi daga chair, sallama tayi masu ta koma cikin gidan, ranshi ya rigada ya gama ɓaci bayajin zai iya maganar da za suyi shiyyasa kawai ya sallameta.
tunda Nainarh ta fito daga gidan ta nufo garden yake tsaye bayan pillar da waya a hannunshi, da alama video yake ɗaukar su, baƙaƙen kaya ne a jikinshi ya rufe ko ina na jikinshi banda idanun shi babu wani abu da ake iya gani daga jikinshi.
Nainarh na tunkaro ƙofar shiga gidan yayi saurin ɓoyewa yana zura wayar Aljihun wandon jikinshi, kowaye da alama leƙen asiri yake masu.
ɗan dukan kafaɗar ya Adnan ya Naeem yayi ganin ya bi Nainarh da ido
“ya dai,lafiya ka kafe yar mutane da ido ka ke binta da wannan kallon ƙurillar?”
kauda kai gefe ya Adnan ɗin yayi yana sakin murmushi
“ba komai, kawai dai tana burgeni ne she's so innocent” murmushi ya Naeem yayi
“ka tsaya dai iya haka”
dariya ya Adnan ɗin yayi yana girgiza kai “ya ku ka yi da SAM ɗin ya amince kuwa?” ya Adnan ya faɗa yana kallon fuskar ya Naeem, tsaki ya Naeem yaja
“ka kyale SAM kawai Adnan,na rasa gane wane irin bauɗaɗɗan mutum ne shi, Allah ma muna mashi laifi ya yafe mana sai shi ne bazai yafe ba, na rasa a wajen ubanwa ya gaji wannan baƙar zuciyar da idan ya juyama abu baya ya juya mashi kenan?”
“uncle Mustafa shi ka manta tashi kalar zuciyar ne?”
“uhmmm Allah gara uncle Mustafa dashi, tsawan shekara nawa kenan ana fama dashi amma ya maida mutane shashashu, ka du ba fa ka ga irin haukan da dady keyi a kan shi wannan bai isa ba ace ya yi haƙuri,bawan Allah nan sau nawa yana taka ƙafa ya bishi amma haka zai ƙaraci zamanshi ya dawo bazai taɓa ganinshi ba haba” ya ƙare maganar cikin fushi
“Allah ya kyauta, amma SAM lamarin shi sai shi, ni kaina sai na kusa haɗa shekara banji muryarshi ba” ya Adnan ya faɗa
“wallahi zanyi mashi maganin abun da ke damunshi ne” murmushi ya Adnan ya saki
“ai da yake kunfi kusa, dama da kai yake uban ba da dady ba” tsaki kawai ya Naeem yaja.
*Queen Kainart💫*
tafe take kwata kwata bata lura da mutum dake tahowa ba duk da ƙofar ta glass ce,shima hankali shi baya gaban shi yana a kan wayarshi da yake latsawa.
saurin ja da baya tayi dalilin karon da su ka yi,wayar dake hannunshi ta faɗi ƙasa, dafe goshinta da ya bigi broad chest ɗin shi tayi,wani irin zafi ne ya ziyarci kwakwalwarta, a masifance ta ɗago tana kallonshi ido cikin ido
“dallah malam baka gani ne or are u blind da ka ke tafiya baka kallon gabanka??” ta faɗa tana wani zazzare mashi ido, wani irin haushin shi da tsanar shi take ji a ranta.
kasa magana yayi saboda mamaki daya rufe shi, ta bugeshi har ta yar mashi da waya ƙasa amma ta rufeshi da faɗa kamar wani sa'anta,mamakinshi ma a ina ta samu confidence ɗin yi mashi rashin kunya.
harara ta sake watsa mashi haɗi da jan tsaki,raɓawa tayi ta gefenshi zata wuce, rai a ɓace ya fisgo Arm ɗinta, gaba ɗaya ta tafi taga taga zata faɗin, riƙota yayi sosai, idan da abunda ya tsana a rayuwarshi tsaki, ya tsani tsaki musamman ace mace ce tayi mashi shi.
Raba idanu ta shiga yi a fuskarshi, ba ƙaramin tsorata tayi da yana yin shi ba,cike da mugunta ya sake matse hannunta,saurin rintse ido tayi saboda wani zafi daya shigeta.
Murya a kausashe yace “wa ki ke ma tsaki?” banza tayi da shi ƙoƙarin ƙwace kanta kawai take daga riƙon da yayi mata, tsawa ya daka mata “tambayarki nake wa ki ke ma tsaki??” ya faɗa yayin da yake murɗe hannunta
fashewa tayi da kukan azaba, murya na rawa tace “ai ba da kai nake ba”
“dawa ki ke” ya faɗa fuska a ɗaure
“dan Allah kayi haƙuri”
“tsaran wasanki ne ni?” girgiza mashi kai tayi hawaye na bin cheek.
“bani wayata” ya faɗa yana nuna mata wayarshi dake yashe a ƙasa
“ka sakar man hannu to” sakin hannunta yayi, duƙawa ƙasa tayi ta ɗauko mashi wayar
“gashi” ta faɗa tana turo mashi baki.
amsar wayar yayi yana sake riƙe hannunta “this should be the first and last time da za kiyi gigin yiman rashin kunya if not, sai na ɓaɓɓalaki a gidan nan useless”
“IRFAN” su ka ji an faɗa a bayan su.
saurin sakin hannunta yayi yana juyawa bayanshi,dady ne da uncle hashim,tun lokacin da su ka yi karo su ke tsaye suna kallon su.
hannunta da Irfan ɗin ya riƙe ta shiga murzawa saboda zafin da yake mata
“Irfan mi ya haɗaka da ita?” dady ya faɗa
“babu komai, ina wuni Uncle”
“lafiya lau” uncle hashim ya faɗa, saurin barin wajen Irfan yayi ya nufi garden wajen su ya Naeem.
“zo nan Nainarh”dady ya faɗa yana mata alama data zo, nufo su tayi har time ɗin hawaye na bin kumatunta, hannu dady yasa ya shiga share mata hawayen
“kukan ya isa haka, mi yasa ki ka yi mashi rashin kunya?”
“babu komai”
“he's ur elder brother, kar na sake gani,kina jina ko”
“eh dady in sha Allah bazan sake ba”
“haka nake son ji, ga Uncle ɗin ku nan ku gaisa” ya faɗa yana nuna mata Uncle hashim dake tsaye yana kallonsu
“in wuni Uncle”
“lafiya lau, ya ki ke, ya school??”
“lafiya lau Alhmdllh”
“masha Allah, Allah ya taimaka”
da Ameen ta amsa tana barin wurin ta nufi bedroom ɗin su.
tana shiga bedroom ɗin saurin zame hijab ɗin jikinta tayi tana kallon hannunta da Irfan ɗin ya riƙe wurin har yayi ja.
wasu hawaye ne su sake taruwa a idonta “mugu kawai” ta faɗa tana turo baki.
*Queen Kainart*💫
“muje ko” ya dady ya faɗa yana kallon Uncle hashim
“gida zan tafi”
“tafiya dai hashim, ai ka shiga ku gaisa da Zulaihart ko?”
“A'a yaya tafiya zanyi, idan na sake dawowa mun gaisa”
dady ya faɗi haka ne kawai amma dama ya san uncle hashim bazai tsaya ba in dai dan su gaisa da mom ne
“shikenan ka gaishe da mutanen gidan”
“za su ji, sai anjima” jin jina mashi kai dady yayi yana nufar sama zuwa part ɗin shi.
ficewa uncle hashim ɗin yayi amma instead of ya fice daga gidan baki ɗaya sai ya nufi part ɗin Mamy, bai samu kowa a falonta ba, masu aiki na part ɗin su Fa'iza na gidan shi wurin Balqis.
direct bedroom ɗinta ya nufa, bai sameta a ciki ba sai ƙarar ruwa da yaji a cikin toilet alamar tana ciki.
bed ɗinta ya nufa, zama yayi yana kwantar da kanshi jikin head board, wayarta dake ajiye kan nightstand ya ɗauka, babu password a wayar hakan ya bashi damar shiga contact da messages ɗinta.
turo ƙofar toilet ɗin tayi ta fito tana yarfe hannunta da alama alwala tayi, da mamaki take kallonshi bata san yaushe ya shigo ba, mamakin ganinshi a irin wannan lokacin ne ya hanata ƙarasawa gare shi.
wayarta dake hannunshi ya ajiye yana zuba mata mayatattun idanunshi “ƙaraso mana ki ka tsaya nan” ya faɗa ganin tayi tsaye kamar an dasata.
cikin ɗakin ta nufo kamar yanda ya umarta “yaushe ka shigo, baka tsoron wani ya ganka a irin wannan lokacin??” jin jina mata kai yayi alamar eh
“eh fa kace, baka gudun yayanka ya shigo gidan?”
“tare mu ka shigo da shi, yana part ɗin shi”
“amma shine ka shigo part ɗin, baka tsoron ya shigo part ɗina??”
“wait mabaruka kinyi farin cikin gani na ko na tashi na kama gabana?” ya faɗa yana ɗan tsuke fuska alamar rashin jin daɗin tambayoyinta
“kaima ka san am really happy to see u but kawai dai bana son abunda zai jawo mana matsala”
sauka yayi daga saman bed ɗin ya nufo inda take, kama hannunwanta yayi ciki nashi
“naga hankalinki bai kwanta da zuwana ba,lee me go” ya faɗa yana sakin hannunta, saurin kamo hannunshi tayi
“tunda har kai hankalinka a kwance yake bana da wata matsala”
“are u sure?”
“really sure, kai da kazo ma baka damu ba sai ni daka iske”
a jiyar zuciya ya sauke yana wani lumshe ido
“why did u not pick my call yesterday?”
“am with u brother, ka san jiya a wajena yake”
“mi yarinyar can take har yanzu bata bar gidan nan ba?”
tsaki taja “hmmm ka bari kawai u know ur brother yanda yake da matarshi komai tayi dai dai ne a wajansa, duk wata hanya na bi dan ganin ta bar gidan nan har mama Ameenah na sanar mawa tace za tayi mashi magana amma shiru, dama nayi mashi maganar sai shata man layi yayi akan yarinyar, wani mugun sonta yake ga yarinyar da ɗan banza kilibibi, duk wata hanya data san zata bi danta samu shiga a wurinshi sai da tayi”
“alright, amma dole yarinyar nan ta bar gidan nan kema kin san da haka?”
“i know, in sha Allah zanyi iya bakin ƙoƙari na ganin tabar gidan nan” jawota yayi zuwa jikinshi, cikin wata irin shu'umar murya yace
“alright, yaushe zaki bar ya Tahir ki dawo gare ni, na gaji da wannan raba dai dan da nake dashi” ya faɗa yana wani lumshe ido
“ko a yanzu a shirye nake, umarninka kawai nake jira” sake matso da ita yayi jikinshi, hannunshi ya zura bayanta, zip ɗin rigarta ya shiga zugewa, a hankali ya furta “har yanzu burinmu bai cika ba mabaruka”
“don't worry about that, nan da wani lokacin komai zai zo ƙarshe”
“are u sure?”
“am sure, Fa'iz da Fa'iza ne kawai nake ganin za suyi man cikas”
“karki damu da wannan sun riga da sun girma, kuma ko baki nan Zulaihart zata kula da su kamar yaranta, kuma da sunyi Aure ai shikenan”
“haka ne, amma maimunatu fa kasanfa bana son zama dakai tare da kowa?”
“maimunatu is not ur problem ni na san yanda zanyi da ita” ya faɗa yana wani kashe mata ido ɗaya, murmushi ta saki itama tana maida mashi martani.
saurin manne bakinshi yayi da nata, a zafafe ya shiga kissing ɗinta ba ƙaƙautawa,sun jima a haka har ƙafafunsu suka fara gajiya, ganin tsayuwar baza tayi masu bane yasa shi sakin bakinta,ida unzipping rigartar daya fara yayi, he slipping her all and throw it away, sake manne bakinsu yayi yana ɗaukarta,a haka ya nufi bed da ita.
*UNITED STATE❤*
_*Las Vegas (Nevada)*_
*THE PRESENT DAY*
Aunty sophia da Chefs ne a kitchen suna shiri akan celebrating dinner da za suyi zuwa anjima,suke aikin tana kula da su,tunda miss Malika ta dawo ta koma kitchen duk da ba girki take ba.
“i hope Miss Nailarh enjoyed this Burger more than the previous one”
ɗaya daga cikin chefs ɗin ya faɗa,riƙe ƙugu wanda ke gaban oven yayi “i also wish this cake is better than the last celebration”
murmushin Aunty Sophia ta saki tana jin kowa da abunda yake buri
“ni dai ba komai ke burgeni ba except how we can relax today,har Adu'a nake shekara ta zagayo because of this celebration,i like how Nailarh allow us to do what we want on this day” ɗaya daga cikin chefs ɗin ta faɗa tana sakin murmushi.
Aunty Sophia na sauraron kowa sai faɗar albarkacin bakinsa yake ƙala bata ce masu ba,amma tana jin daɗin yanda su ke yabon Nailarh.
maida hankalinsu su ka yi kan aikin da suke,ƙarar fashewar wani abu su ka ji daga waje
“ba ku jin wata ƙara kamar fashewar nockout?” ɗaya daga cikin chefs ɗin ya faɗa
“ko dai sun dawo ne ,naji kamar hayaniya ƙasa ƙasa?” wani ya sake faɗa daga cikin chefs ɗin,tashi Aunty Sophia tayi daga saman chair ɗin da take zaune
“ku ci gaba da aiki,lee me check” Aunty Sophia ta faɗa tana nufar ƙofar fita.
sauran ƙiris suyi karo da luna ta shigo kitchen ɗin da gudu,da sauri Aunty Sophia taja baya tana kallonta ganin yanda ta shigo kitchen ɗin kamar wacce aka koro
“lafiya!?” Aunty Sophia ta faɗa tana leƙen bayanta ko za taga abunda ya biyota.
da mamaki Aunty Sophia ta dawo da dubanta gareta dan ba taga komai ba “are u okay?”
ƙofar fita ta shiga nuna mata tana sauke numfashi da sauri sauri alamar na wanda yayi gudu ko yaga wani abun tsoro.
“minene wai,i don't see anything?” da ƙyar luna ta fisgo kalma daga bakinta tace “Na..i..larh” zaro ido Aunty Sophia tayi,da sauri ɗaya daga cikin chefs ɗin ya miƙa mata ruwa,hannunta har rawa yake wajen amsar ruwan,kafa kai tayi ,tas ta shanye ruwan tana maida numfashi “Miss Nailarh shot Alex with a gun!”
wani mummuna faɗuwa gaban su yayi,gaba ɗaya su ka zaro ido suna kallon luna da tayi maganar,Aunty Sophia bata tsaya jin abun da luna zata sake cewa ba ta fice daga kitchen ɗin da sauri ta nufi main parlor,tana shiga parlorn Nailarh na Kunno Kai da gun a hannunta yayin da miss Malika ke biye da ita kamar mahaukaciya tana mata magiya akan ta ajiye gun ɗin.
cikin parlorn security ɗin su ka shigo da Alex hannunshi sai jini yake,ba ƙaramin tashi hankalin Aunty Sophia yayi ba,da sauri tasha gaban Nailarh “baby are u out of mind,what are u planning to do like this?”
ɗago idanunta tayi ta kalle Aunty Sophia,da sauri ta kauda kanta gefe ganin yanda idanun Nailarh su ka yi jawur wutar ɓacin rai ce kawai ke ci a cikin su, fuskarta tayi jawur musamman cheek ɗin ta.
“if u dont move of on my way,I will kill u!”
Kamar saukar aradu haka Aunty Sophia taji maganarta
“Nailarh are you saying that you will kill me?” tsawa Nailarh ta dakata mata tana zaro mata ido
“i said move or I will shoot u!” gaba ɗaya parlorn babu wanda hankalinshi bai tashi ba yau Nailarh kema Aunty Sophia tsawa har take faɗin zata kashe ta lallai ba ƙaramin ɓaci ranta yayi ba.
wasu irin hawaye ne su ka wanke fuskar Aunty Sophia cikin ƙunar rai tace“bazan matsa ko ina ba kill me Nailarh”
“sophia are out of mind or u forgot who's Nailarh when she's angry?”miss Malika ta faɗa tana zazzare ido
“babu inda zan matsa taje ta illata kanta,Nailarh just kill me if that can calm u're mind”Aunty Sophia ta faɗa babu alamar tsoro,nuna ta Nailarh tayi da gun ɗin,rintse ido Aunty Sophia tayi,wani irin wahalallan yawu miss Malika ta haɗe kamar ita aka nuna da gun ɗin.
magiya parlorn su ka shiga yima Aunty Sophia kan ta matsa amma ko gezau ba tayi ba.
hawayen da suka taru idonta tun ɗazu sai yanzu su ka samu damar zubo,wani irin Shaking jikinta ya shiga yi,canza direction ɗin gun ɗin tayi zuwa sama, crystal Chandelier ɗin dake ceilling tayi shooting,gaba ɗaya ya ruguzo ya faɗa kan center table dake parlorn,toshe kunnuwansu su ka yi in ka cire Aunty Sophia data kafe Nailarh da idanu hawaye na zuba.
hawaye ne su ka shiga sintiri a fuskar Nailarh,ita kuka Aunty Sophia kuka ga wani irin rawa da jikinta ke yi,jifa tayi da gun ɗin da gudu ta raɓa ta gefen Aunty Sophia ta nufi sama.
zubewa Aunty Sophia tayi kan gwiwoyinta,bin bayan Nailarh miss Malika da sauran masu aikin su ka yi,kallo su Alex Aunty Sophia tayi tace su tafi hospital,ficewa su ka yi dashi har time ɗin jini ke zuba.
tashi tayi tabi bayan su jiki a sanyaye dan taga halin da Nailarh take ciki,daga nesa ta hange su a home bar kasancewar glass wall ne a wurin,da sauri ta ƙarasa
a tsaye ta same su sunyi cirko cirko idanunsu a kan Nailarh dake tsaye ta ɗaga kwalbar wine tana ɗurama cikinta.
da mugun sauri Aunty Sophia ta faɗa ɗakin har tana bangaje wanda ke bakin ƙofa,a zafafe ta fisge kwalbar daga hannun Nailarh tayi jifa da ita nan take kwalbar ta fashe.
“mi yasa ki ka yi haka sophia?,atlest idan tasha zata samu relief” Malika ta faɗa, ko kallon inda take Sophia bata yi ba kamar ma bata san tana magana ba,cikin raunannar murya tace
“Nailarh idan rai ya ɓaci hankali baya gushewa,wannan abun da ki ke is not a solution,ko kin manta alƙawarin da ki ka yi man,mi yasa ki ke son maida hannun agogo baya,tell me mi ke damunki sai muyi solving matsalar tare???” cike da kulawa Aunty Sophia ta faɗa.
hannu biyu Nailarh tasa ta kama kwalar rigar Aunty Sophia,zaro ido su kayi gaba ɗayan su da mamaki su ke kallon Nailarh,Aunty Sophia ma da tsantsan mamaki take kallon Nailarh.
jijjigata Nailarh tayi cike da karaji tace “who is he,kalamanki na ranar da momy zata dawo sun tabbatar man dasa hannunki,tell me who's he??” ta ƙarashe maganar tana daka mata tsawa.
wani irin mugun tashi
hankalin Aunty Sophia yayi dan kwata kwata bata fahimci inda zancen Nailarh ya dosa ba “baby what are u talking about, please kiyi man bayani?”
“i said who is he answer me” Nailarh ta faɗa tana wani zare mata ido, hawaye ne suka wanke fuskar Aunty Sophia,girgiza mata kai ta shiga yi “believe me Nailarh ban san akan mi kike magana ba” gani tayi ɗakin na juya mata ga wani irin ciwo da zuciyarta ke mata,dafe saitin zuciyarta dake barazanar faso ƙirjinta ta fito tayi tana faɗin “my chest”gaba ɗaya ta tafi zata faɗi da sauri Aunty Sophia ta riƙota jikinta,gaba ɗaya ta faɗa jikinta
“please Aunty Sophia waye shi” Nailarh ta faɗa a hankali daga haka kuma bata sake cewa komai ba, jikinta ya saki alamar suma tayi.
fashewa Aunty Sophia tayi da kuka kamar ƙaramar yarinya..
*Ya Allah mike shirin faruwa dake Nailarh,mi ya faru a N R T*
*Back to N R T Dan muji abunda ya faru*
Track ɗin a cike yake maƙil ,ta ko ina ka duba mutane ne zazzaune a mazauninsu da aka tanada,Track ɗin ya cika Masha Allah,mutane ne daban daban daga garuruwa daban daban wasu ma ba daga ƙasar su ke ba.
kamar ko wane lokaci suna sanye da shirt da cap na track ɗin kamar yanda ya kasance al'adar wajen.
daga gefe manyan baƙi ne da, wasu daga cikin ƙasar su ke wasu kuma daga wajen ƙasar,suna zaune a mazauninsu na musamman wanda akatanadar masu,miss Malika na cikin manyan baƙi ta ɗau wankan Sheath gown kamar wata yarinya kanta sanye da haɗaɗirya hat mai net daga gabanta anyi mata ado da bird feather,su luna na daga gefenta tsaye,kiɗa da bushe bushe ne ke tashi a cikin Field ɗin.
dawaki ne aƙalla guda ashirin a cikin field ɗin,suna a killace cikin ɗan cage ɗin su a tsaye,kowa wane doki akwai mutum a saman shi,a shirye su ke umarnin fara gudu kawai su ke jira, Nailarh na daga tsakiyar dawakan saman dokinta.
wani baƙin doki ne a hannun damanta sai sheƙi yake yana ɗaukar ido,kallon wanda ke kan dokin tayi,daga yanayin shigarshi ta fahimci sabon ɗan wasa ne dan komai nasa daban yake da nasu hatta suturar dake jikinshi da helmet ɗin dake kansa,sosai ta zuba mashi ido tana kallo, banda idanunshi bata iya hangen komai daga fuskarshi,saurin kauda kai tayi ganin yana ƙoƙarin juyowa alamar ya fahimci ana kallonshi,kallon inda Nailarh take yayi,kallon ƴan seconds yayi mata ya ɗauke idonshi.
lokaci na cika aka basu damanr far gudu ta hanyar hura whistle,cike da karsashi dawakan su ka shiga gudu a cikin babban field ɗin, a tare su ka fara gudu abun gwanin ban sha'awa,sosai suke gudu kowa burin shi ya kai ga matsaya.
rarrabuwa dawakan su ka yi,shidda su ka yi gaba yayinda aka bar sha huɗu a baya,dawaki biyu ne cikin shidda su ka yi baya a dalilin karon da su ka yi da juna,hakan yasa suka koma bayan huɗu yayinda sha huɗu ke biye da su,sosai Dawakai biyu dake cikin sha huɗun su ka dage har sai da su ka cimma biyun dake gaban su suka zama su huɗu, huɗu na gaba huɗu na tsakkiya sha biyu a baya.
A wannan karan Nailarh ba tayi baya ba kamar na last wasan da su ka yi,tana cikin huɗu dake gaba,sosai ta dage dan ganin tayi nasara a wannan karon kamar ko yaushe.
Mutane kowa sai baza ido yake dan ganin yanda wasan zai kwashe,da yawan mutane na fatan Nailarh tayi nasara kamar ko wane lokaci yayinda wasu ba haka bane a zuciyar su burin su ta faɗi ko za su rage raɗaɗin kuɗaɗen su da suke asara a wajen wasan, murmushi kawai miss Malika ke saki cike da ƙwarin gwiwa take kallon wasan ta san cin galaba akan babyn tata abune mai wahalar gaske.
sosai su ka dage da gudun gashi har sun kusa isar ma matsaya amma dawakan nan uku na tare dana Nailarh, hankalin ta ne ya fara tashi ganin duk iya bakin ƙoƙarin da take dan ganin tayi masu zarra abun yaci tura, data ta samu ta kere masu sai su sake cimma mata.
duka ta kaima king dan a ganinta sakacinshi ne yasa har ta kasa tsere masu,ganin dai idan ba tayi wani abu ba komai zai iya faruwa ne yasa cike da dabara yanda alƙalan wasan bazasu lura da abunda take ba ta matsa kusa da dokin dake kusa dashi,cike da mugunta taja igiyar dake jikin dokin ta tarɗe ƙafar dokin,mahayin dokin baiyi auneba ba sai jinshi yayi ya tafi ƙasa har ya shafi dokin dake kusa da shi,gaba ɗaya su ka kifa ƙasa daga su har dawakan nasu,nan su ka shiga birgima a ƙasa,hankali tashe mutane su ka shiga miƙewa ganin abunda ya faru.
da gudu emergency officers
suka shigo cikin Field ɗin ɗauke da stretcher,ɗaukar wanda su ka samu rauni su ka yi suka ɗaura a stretcher su ka fice da su,juyawa Nailarh tayi tana sakin wani wicked smile ko a jikinta,yanzu ya rage saura su biyu daga ita sai wannan baƙin dokin,tunda yaga abunda tayi ya kafeta da ido yana kallon ta cikin helmet ɗin dake kanshi, fingers biyu yasa yayi saluting ɗinta,tsuke fuska tayi tana kauda kai.
haka aka cigaba da gabatar da wasan duk yanda Nailarh ta so yima wannan mai baƙin dokin mugunta kamar yanda tayi wacan abun ya faskara, ƙoƙarin kereta ma yake hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba gashi sun kusa isa Wining line,hankalin wasu daga cikin ƴan kallo ne ya fara tashi yayinda wasu ke fatan a karya tarihin N R T,ƙus ƙus ne ya fara tashi wasu na son sanin waye wannan dake neman yima Nailarh zarra dan da yawan mutane basu san shi ba.
hankali Nailarh sosai ya ƙara tashi, zufa duk ta wanke jikinta,tun tana ganin abun kamar wasa sai ga dokin nan ya ƙetare Wining line kamar a mafarki,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi ba shiri taci birki tana haki,abunda bata taɓa kawo ma ranta ba ya faru da ita,miss Malika ma zabura tayi daga inda take zaune tana kallon field ɗin.
Ihu da sowa ne ya fara tashi a filin wasan, mutane da dama hakan yayi masu,da gudu securitys ɗin wajen suka shigo cikin field ɗin, tai maka ma duk mahayan dawakan su ka yi su ka sauko daga kan dawakan,tsaye Nailarh tayi a wurin kamar idol, ta kasa motsawa in a shock take kallon field ɗin dan har yanzu ta kasa yarda da hakan gaskiya ne.
Murna wajen mutanen da su ka daɗe suna jin haushin Nailarh ba'a magana, dama da yawan su irin wannan ranar su ke fata gashi kuwa ta riske su.
cikin field ɗin mutane su ka fara shigowa suna nufar wannan mutumin da har yanzu yaƙi cire helmet ɗin dake kanshi haka ma Nailarh,hannu mutane su ka shiga bashi suna taya shi murna wasu kuma na hugging ɗin shi.
tunda ya sauka kan dokin idanunshi ke kan Nailarh ko ƙiftawa bayayi ganin mood ɗinta, walking majestically ya nufo inda Nailarh take still he's eyes on her kuma har time ɗin bai zame helmet ɗin dake kanshi ba,tunda ya tunkarota take kallon shi, yana da tsayi sosai dan ya kereta sosai duk da tana da tsayi, ƙaƙƙarfa ne na gaske yanada broad chest dan tana iya hangen shatin six pack ɗin shi ta jikin polo shirt ɗin dake jikin shi, ga wasu strong arms dake a murɗe, kallo ɗaya za kayi mashi ka gane gym product ne, bazaka iya tantance kalar fatar jikinshi saboda jikinshi dake a rufe.
saurin ɗauke idonta tayi daga kallonshi tana tsuke fuska, har inda take ya ƙaraso, ɗan rissinawa yayi dai dai saitin kunnenta ya kai bakinshi, whisper ya shiga yi mata, bazaka iya jin mi yake cewa ba, a hankali yake magana kamar baya son buɗe bakinshi,wani irin kishi ne ya turniƙe miss malika ta tsani taga wani ya raɓi Nailarh, wani irin kallon wulaƙancin ta shiga binsu dashi zuciyarta na wani irin tafarfasa.
sun kai five minute a haka kafin ya janye bakinshi daga kunnenta, saurin kallonshi Nailarh tayi, from head to toe yake kallonta ta cikin helmet ɗin kafin yayi saluting ɗinta a hankali yace “nice to meet u cutie,see u next time, have a nice day” ya faɗa yana ɗaga mata hannu,barin wurin yayi wani irin ƙara ɓaci ran Nailarh yayi.
da sauri Luna da sauran maids suka nufota Miss Malika na bayan su, hannu luna ta kai da nufin cirema Nailarh helmet ɗin kanta, saukar wani irin azabebben mari taji,saurin dafe cheek ɗinta tayi tana kallon Nailarh data mareta,a masifance ta zame helmet ɗin kanta tayi jifa dashi, jiki na ɓari malika ta nufota, kafin ta ƙaraso Nailarh har ta bar wurin ta nufi motocin su maganganunshi na yawo a brain ɗinta.
da sauri Alex ya buɗe mata back seat ko jiran su malika ba tayi ba tace ya kaita gida,Malika suna isowa suma motocin su suka shiga, da mugun sauri su ka bi bayan su Nailarh, a kusan tare su ka yi parking,ko gama daidaita parking driver baiyi ba Malika ta fito ta nufi Nailarh, tana isowa Nailarh na fitowa da gun a hannunta, hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, saita kanta Nailarh tayi da gun ɗin da nufin shooting kanta.
hakan ba ƙaramin sake ɗaga hankalin Malika yayi ba,umarni taba securitys da drivers ɗin dake wurin da su amshe gun ɗin, garin su amshe ne Nailarh ta harbi Alex.
*back to story*
Jijjigata Aunty sophia ta shiga yi tana kiran sunanta,miss Malika ma kamar za tayi hauka wajen kiran sunan Nailarh, ɗaya daga cikin chefs ne ya nufosu da ruwa, da sauri Aunty sophia ta amsa tana yayyafama Nailarh amma ko gezau ba tayi ba, tayi hakan kusan sau huɗu amma Nailarh bata farfaɗo ba,wani mummunan faɗuwa gaban Aunty sophia yayi haka ma miss Malika, tsoron kar ace ciwan Nailarh ne ya tashi ne ya mamaye zukatansu yaushe rabon da Nailarh ta samu Attack, dan suna kula da duk wani abun da zai ɓata ranta, komai ta buƙata yi mata su ke.
*Nailarh tunda aka haifeta take fama da haert Attack infact ma dashi aka haifeta, shiyyasa duk wani abu da zai faranta ranta miss malika na ƙoƙarin yi mata shi,haka Aunty Sophia bata wasa da lafiyar Nailarh duk wani abu da zai faranta mata tana ƙoƙarin yi mata tana kumakiyaye abunda zai ɓata ranta bare harya kai da ciwonta ya tashisai ta yi mi bata samu Attack ba dan duk abunda take so a rayuwa shi take samu*
hawaye su ka wanke fuskar Miss Malika, maids ɗin dake wurin wasu har sun fara zubar da ƙwalla
Jijjigata miss Malika ta shiga yi tana faɗin “please Nailarh wake up, I promised u to punish this man and sai ya girbi abunda ya shuka,sai yayi daya sanin shigar shi gasar nan, please wake up dear” kamar mahaukaciya haka take jijjiga Nailarh tana roƙonta akan ta tashi,Aunty Sophia banda hawaye babu abunda take.
“Please Nailarh, don't leave me, please wake up, I promised you, I promised u sai yayi daya sani,nayi maki alƙawarin zanyi mashi hukunci mai tsanani, don't leave me please wake up” Sosai take sambatu tana roƙon Nailarh,wani tausayin miss Malika ne ya rufe maids ɗin dan daga yanayin da take magana kamar bata cikin hayyacinta,da ƙar Aunty Sophia tayi ƙarfin halin faɗin
“Ma'am,I think she's on attack” Aunty Sophia ta faɗa tana share ƙwalla
ƙara rikicewa miss Malika tayi jin abunda Aunty Sophia ta faɗa.
zabura tayi da nufin ɗaukar Nailarh
“please tell Alex to bring the car, Sophia let's go to the hospital, I don't want to lose Nailarh” magana take tana ƙoƙarin ɗaukar Nailarh amma ta kasa,gaba ɗaya a gigice take har ta manta da abunda ya faru da Alex,da sauri luna ta fice dan sanar da NOAH saƙon miss malika,shima ɗaya daga cikin drivers ɗin gidan ne.
da sauri William ya ƙaraso cikin ɗakin,hannu biyu yasa ya ɗauki Nailarh,a shoulder ɗin shi ya ɗaurata,gaba ɗaya jikinta ya saki kamar mattaciya,ficewa su kayi daga cikin ɗakin baki ɗaya,miss Malika kamar zata tashi sama,Aunty Sophia kuwa sai sharar hawaye take.
NOAH har ya shiga Mota yayi mata key,jiran fitowar su kawai yake,back seat ɗin motar William ya saka Nailarh Aunty Sophia ta shiga kusa da ita yayin da miss malika ta shiga front seat,reverse yayi suka nufi main gate ɗin gidan, securitys ɗin ma shiga motocin su su ka yi harda su luna su biyu,bin bayan motar su miss malika su ka yi.
komawa bakin aikinsu suka yi sauran securits ɗin da aka bari,cikin gida chefs ɗin su ka koma wasu na jimami yayinda wasu ke sharar ƙwallar tausayin halin da Nailarh take ciki.
*Get well soon Nailarh,to be honest wannan bawan Allah baka kyauta ba😢*
*ABUJA NIGERIA*
*UNCLE MUTALLAF'S HOUSE*
saukowa yake daga saman stairs, walking gently yake taka stairs case ɗin,white suit ne a jikinshi,waya ce kare a kunnenshi.
“gaskiya I'm really happy yaya da wannan maganar,amma nayi mamaki da ban taɓa fahimtar hakan ba” saurin ɗaga kai mom fatilah dake zaune a parlor ita da Noor tayi tana kallon uncle mutallaf,kallo ɗaya za kayi mashi ka hango tsantsar farin cikin da yake ciki.
cikin parlorn ya ƙaraso,ɗaya daga cikin sofas ya nufa ya zauna “wallah da gaske nake yaya ban taɓa lura da hakan ba,kuma kasan duk rashin kunyar Noor Bata taɓa faɗa man ba” da sauri Noor ta tashi ta nufi dadynta jin abunda yace,saurin kai kunnenta tayi jikin wayar wai ko za taji dawa dadynta ke waya.
ture kanta yayi yana sakin dariya “kaji ja'iri wato shi mai kunya shine sai ya aiko maka abokinsa” ƴar dariya yayi yana gyara zaman shi
“to shikenan in sha Allah zuwa goben sai muyi magana,amma gaskiya nayi farin ciki da hakan Allah yasa ayi muna da rai,amma Abbah da yayan sun sani kuwa?”
ɗan jim yayi yana sauraron na cikin wayar can yace
“ok to shikenan Allah ya kaimu sai na shigo goben in sha Allah” sallama yayi da wanda yake wayar
“dady kai da waye ka ke waya?” Noor ta faɗa cike da shagawaɓa
“kawunki ne, maza je part ɗina ki ɗauko man glass ɗina yana Nan kan nightstand”
“to dady,amma maganar mi kuke kai dashi?”
“idan kin dawo zan faɗa maki” saurin tashi tayi ta nufi stairs case da sauri, girgiza kai kawai mom Fatilah tayi.
iska uncle mutallaf ya shaƙa tukun ya fisar,yayi ɗan shiru yana nazarin wani abu
“lafiya dai Dr?” mom fatilah ta faɗa tana leƙen fuskar shi, ajiyar zuciya uncle ya sauke kafin ya kalleta
“ya Ahmad ne ya kirani,kin san cewa Noor da Irfan soyayya su ke?” yana yin fuskar mom fatilah ne ya canza,tsuke fuska tayi
“mi ya faru,kiran mi yake maka to?”
“ya kirani ne ya sanar dani har ma sun tattauna maganar shi da su ya Ubaid, Abbah da ya Tahir ɗin ne kawai ya rage basu sanarmawa ba,amma yace zuwa gobe zai sanar da su dan a san yaushe ya kamata a sa bikin na su,amma fa nayi mamakin da ban taɓa lura da suna soyayya ba duk abun Noor ma bata taɓa sanar dani ba” tunda ya fara magana mom fatilah ta shiga binshi da wani kallon rainin wayau,Noor saukowarta kenan taji abun da dadyn nata ke furtawa,da gudu ta nufi ɗakinta ba tare da ta ko kawo masa glass ɗin da yace ta ɗauko mashi ba.
“gaskiya naji daɗin haka,kinga kafin mu tafi sai a tsaida ranar Auren na su zuwa bayan sallah sai ayi bikin,yara nata ƙara mana daƙon zumunci,saura Yazdan fatana shima ya daina wannan shashanci ya zama mutumin ƙwarai kinga sai mu haɗa su shi da Yumnah” kallon mom fatilah yayi jin tunda ya fara magana ƙalla ba tace ba
“naji kinyi shiru ba kice komai ba,magana nake kana Auren Noor f...” saurin katse shi mom fatilah tayi
“dan Allah dakata Dr,wallahi sam ba zai yiwu ba”
da mamaki yake kallonta bai taɓa tunanin wannan ce kalmar zata fito daga bakinta ba.
“fatila kin san mi ki ke faɗa kuwa?”
“na san mi nake faɗa kuma ina cikin hankalina,wannan haɗin sam bazai yiwu ba ni ba hajiya halima bace ko salima da ku ka nunama fin ƙarfi akan ƴaƴan su,ku ka nuna basu da right ɗin zaɓarma ƴaƴan su abokan zama,ni sam bazan ƴarda da wannan ba,babu ƴaƴana babu ƴaƴan Zulaihart period”
kallonta kawai uncle mutallaf keyi cike da mamaki,ko a mafarki bai taɓa tunanin wannan amsar daga gareta ba,yayi matuƙar mamakin ta duk da ya san ba su jituwa da matar yayan nashi.
“wallahi babu ƴaƴana babu ƴaƴan Zulaihart,haka kawai kuyita kwasar mana ƴaƴa kuna ba ƴaƴan Zulaihart sai kace ita kaɗai ke da ƴaƴa, gaskiya ni ban amince ba”
“amma nayi mamakin jin haka daga gareki,banyi tunanin za ki yi haka ba,miye laifin Zulaihart ne da zaki ƙi son haɗa alaƙa da ita,ai ko dan ya Tahir da farin cikin ƴarki kin amince”
tashi tayi daga inda take zaune cikin ɗaga murya tace
“wallahi bazan amince ba,haɗa dangantaka da Zulaihart wallahi bazan yi ba,ai da Noor ke faɗa man na ɗauka shashancinta ne ai ban san abun da gaske bane da wallahi tuni nayi ma tufkar hanci,haka kawai kuyi ta haɗa mu da dangin yahudawa, wallahi tun wuri kace ma ƴan uwanka baka amince ba dan Noor bazata Auri Irfan ba” ta kai ƙarshen maganar tana huci
“kin gama” uncle Mutallaf ya faɗa yana tsareta da idanu
“ban gane na gama ba,haka kawai sai inƙi faɗin ra'ayina,kowace yarinya sai ku ɗauka kuba ƴaƴan Zulaihart haka akeyi,idan su hajiya halima sun amince saboda kwaɗayin abun duniya ni wallahi bazan amince ba”
“Fatilah ina so ki san wani abu Noor da Irfan are my kids, ke baki isa ki sa na fasa abunda nayi niyya ba,Aure tsakanin Noor da Irfan Kamar anyi an gama ne in dai ni ne ubanta ba wani daban ba” ya faɗa a kausashe
“lallai Dr zaka tafka babban kuskure in dai kace sai ta Auri Irfan”
“kwarai kuwa,kije kiyi duk abunda ki ke ganin zaki iya amma Aure tsakanin Noor da Irfan Kamar anyi shi angama,ke baki isa kisa na zuba ma ƴan uwana ƙasa a ido ba,yanda aka yi na Naeem da Adnan lafiya haka za'ayi na Noor da Irfan sai dai kiyi duk abunda za kiyi”
Kwashewa tayi da wata irin dariya“haka dai kace ko,za kuwa kaga abunda zan aikata” sosai saɓani ya shiga tsakaninsu akan wannan maganar.
Noor lokacin data nufi bedroom ɗin ta,wayarta ta ɗauka tayi dialing number Irfan,har Kiran ya katse baiyi picking ba, sake kira tayi sai a na biyun ne yayi picking
“hey beb, what's up?” ya faɗa daga cikin wayar
“am really happy dear,yau dai ka cika alƙawari, i really really love u irin billions ɗin nan,i wish kana kusa da na baka warm hug of happiness”ta faɗa tana sakin dariya
daga cikin wayar tana jin yanda ya sauke ajiyar zuciya “I would like that baby,but wait farin cikin mi kike?”
“ban gane farin cikin mi nake ba,kana nufin baka sani ba?”
“am serious dear ban sani ba” ɓata fuska tayi tana turo baki
“bana son wannan wasan yaya”
“am serious Qanwata ban sani ba”
“yaya yanzu maganar Auren namuce baka sani ba” ta faɗa tana wani murguɗa mashi baki kamar irin yana kusa da ita ɗin nan
“maganar Auren fa,a ina ki ka ji?”
“yanzu naji dady na waya da Uncle Ahmad yana sanar dashi” ajiyar zuciya taji ya sauke
“Alhmdllh, gaskiya naji daɗin jin haka,am really happy dear” dariya ta saki
“wai da gaske ba kai ka faɗa mashi ba”
“da gaske nake,i think Waseef ne ya sanar dashi”
“amma naji daɗi ya Waseef ya faranta man shima Allah ya faranta mashi”
“Ameen,yanzu shikenan beb mun kusa zama husband and wife”
“yeah very soon we became husband and wifeee” ta faɗa tana jan wife ɗin,dariya su ka yi gaba ɗayan su, faɗawa tayi saman bed ɗin ta
“gaskiya dole nayi ma ya Waseef kyauta yayi abunda ka kasa tsawan shekaru”
a shagwaɓe yace “beb Ni fa kyautar”
“taka special ce husband to be”
“beb,Ina so mu haɗu Please” ya faɗa yana wani shagwaɓe murya kamar ƙaramin yaro
“ka zo gida mana”
“No beby kunyar uncle nake ji,kina so yace daga faɗa mashi har na fara mashi Zarya a gida”
“kunya fa yaya,shi fa dady ba ruwanshi”
“ni dai bazan iya zuwa ba beb,kawai ki nema mana inda zamu haɗu”
“please Ni dai ka zo, ko a compound ne sai ka tsaya ba saika shigo ciki ba”
“ok let me see idan zan iya zuwa”
“zaka iya dear”
cike da farin ciki su ka cigaba da waya,daga yanayin yanda su ke wayar zaka tabbatar suna cikin farin ciki,hayaniyar da taji ne yasa tayi saurin ce mashi tana zuwa, rejecting call ɗin tayi,da sauri ta sauka daga saman bed ɗin ta nufi ƙofar fita zuwa parlor,anan ta samu dadynta da momynta suna saɓani saboda Auren su.
cikin parlorn ta ƙarasa,fashewa tayi da kuka “momy mi yasa za kice haka akan ya Irfan,gaskiya ki daina man wannan wasan”
“sai na mareki idan ba kiyi man shiru anan ba shashasha”turo baki Noor ɗin tayi hawaye na bin cheek ɗinta
“kowa na farin ciki sai ke ce zaki tsiro da haka,ni gaskiya ya Irfan nake so kuma shi zan Aura,haka kwai burinda na daɗe ina jira zaki wani ɓ...” bata ƙarasa ba saboda saukar marin da taji,da gudu ta nufi dadynta tana fashewa da kuka.
“shashashar banza wacce bata san inda ke mata ciwo ba,ai da duk a zatona kina da hankali ashe sakaryace ke ban sani ba”
“dady dan Allah karka bari ta rabani da ya Irfan” ta faɗa tana kuka
“yi shiru Noor,karki wani tashi hankalinki ni ne dai dadynki ba wani ba,babu wanda ya isa rabaki da Irfan sai Allah,Irfan shine zaɓi na” tsaki mom fatilah taja
“zaku sha mamakina daga kai har ita” tana faɗar haka ta nufi sama,hannu yasa ya shiga goge mata hawayen dake zuba.
“yi haƙuri kukan ya isa haka,where is my glasses?” bedroom ɗinta ta nufa da sauri, glass ɗin ta ɗauko mashi,amsa yayi yana ɗan shafa kanta
“karki damu kinji” gyaɗa mashi kai tayi,ficewa yayi daga parlorn ita kuma ta koma bedroom ɗinta ranta duk a jagule bata taɓa zaton haka daga momynta ba...
*Uhmmm mom fatilah yada haka*
A hakimce take saman sofa mai mazaunin mutum uku a katafaren main parlor gidan, PJ ne a jikinta, laptop ɗinta na ajiye saman table ɗin dake gaban sofa, a hankali take Operating ɗinta,Joseph na zaune saman sofa mai mazaunin mutum ɗaya, ya ɗau wankan black suit,rigar suit ɗin na ajiye saman hannun sofa da yake zaune, hannushi riƙe da fils.
daga gefe chief security ɗin gidan ne sai masu kula da C C TV sai drivers ɗin Nailarh da su Luna sai chefs,gaba ɗayan maids ɗin ne Aunty sophia ce kawai babu.
Aikin ko wane ta ke bincika dan sanin abun da ya faru bayan bata nan duk da suna sanar da ita abunda ke faruwa lokacin da bata nan, drivers ɗin Nailarh ta fara tsarewa da tambayar da bata nan ina da ina su ka kai Nailarh.
Alex ne ya shiga zayyana mata inda Nailarh taje bayan bata nan,shi ke driving motar Nailarh duk za su fita kuma shine shugaban drivers ɗin gidan baki ɗaya, jinjina kai ta shiga yi har ya kammala sanar da ita, maida hankalinta tayi kan su Luna suma dai magana ɗaya ce da Alex, sallamar su tayi su koma bakin aikin su.
Masu kula da C C TV gidan ne su ka fara kora mata bayanin kaf abunda ya faru,babban cikin su ne ya sanar da ita “ma'am still Sophia's CCTV doesn't work” jin jina kai tayi tana ɗan dakatawa da aikin da take
“duk gyaran da a ka yi?”
“yes ma'am” da kamar za tayi magana sai kuma ta fasa
“u can go” ta faɗa, gabanta ɗaya daga cikin su ya zo flash ya miƙa mata kafin ya fice.
tana cikin magana da Chefs Aunty sophia ta zo,kallo ɗaya za kayi mata ka hango tsantsar damuwar dake kwance a fuskarta,gaishe da miss Malika tayi da kulawa ta amsa mata “chefs sun ce baki lafiya,how do u feel now?”
“am feeling much better”
“I'm points hope quick recovery dear”
“thank U ma'am”
Nailarh ce ta fito daga bedroom ɗinta shirt da short ne a jikinta ta ɗaure gashin kanta da ribbon, ciki parlorn ta nufo, tunda ta fito su ka kafeta da ido musamman Joseph har wani ɗaga kai yake dan ya kalleta da kyau.
tana ƙarasowa tayi hugging ɗin Aunty sophia ta baya “good morning”
“morning baby, kin tashi lafiya”
“lafiya lau” Nailarh ta faɗa tana raba jikin su
“mi ya samu hannunki?” ta faɗa yayinda take riƙo hannun Aunty sophia
“yankewa nayi da glass”
“Ayyah, sorry chefs sun ce man baki da lafiya, mike damunki”
“it was a headache,but i got better now”
“is this tumor the cause you of the headache?” ta faɗa da tsantsar kulawa
girgiza mata kai Aunty sophia tayi “bashi bane”
“sorry” Nailarh ta faɗa kamar ƙaramar yarinya
jin jina mata kai Aunty sophia tayi.
mahaifiyarta dake zaune kan sofa ta nufa, ɗan rissinawa tayi ta sumbacin lips ɗinta, saurin rintse ido Aunty sophia tayi tana jin wani irin ɗaci a ranta.
“good morning” Nailarh ta faɗa
“morning beb” malika ta faɗa tana kashe mata ido ɗaya, kusa da ita ta zauna tana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya.
“good morning boss” Joseph ne ya faɗa, amsa mashi tayi tana ɗaga mashi hannu, gaishe da ita chefs ɗin dake tsaye su ka shiga yi da kulawa take amsa masu.
sallamar chefs ɗin miss Malika tayi bayan sun gama bata amsoshin tambayar da tayi masu, sofa dake kusa da wacce Joseph ke zaune miss malika ta nuna ma Aunty sophia, zama tayi tana fuskantar ta.
Ta sowa Joseph yayi daga mazauninshi files ɗin dake hannunshi ya miƙama miss Malika, amsa tayi tana jinjina mashi kai “zaka iya tafiya,idan na kammala dubawa zan tura maka replys ta email”
“ok ma'am, have a nice day” rigar suit ɗinshi dake ajiye kan hannun sofa ya nufa,ɗaukar rigar yayi haɗe da briefcase ɗin shi dake gefe “bye” ya faɗa yana ɗaga masu hannu, jinjina mashi kai miss Malika tayi, ficewa yayi daga parlorn.
ɗaya daga cikin chefs ne ya shigo hannunshi ɗauke da madaidaicin tray wanda ya shirya masu coffee, Nailarh ya nufa ya fara miƙa mata ta ɗauka kafin miss Malika da Aunty sophia, barin parlorn yayi ya koma kitchen.
“Sophia!” miss Malika ta kira sunanta, ɗagowa Aunty sophia tayi ta fuskanceta da kyau
“William ya sanar dani har yanzu C C TV part ɗinki bata aiki, what is the problem?” ta faɗa tana kafeta da ido
“nothing, but naga is not good ace har a bedroom da bathroom an sa mana camera ba, a barshi a iya parlor kawai,bedroom and bathroom is our part of secret” tunda ta fara magana Malika ta kafeta da ido
“but if that offends u, am very sorry”
“saboda bai dace ba yasa ki ka lalata na part ɗinki?” cike da tuhuma miss Malika ta faɗa
“please momy Aunty sophia ce fa, mi kike son sani a game da rayuwarta da har sai kin sa mata C C TV, gaskiya i'm really not happy” Nailarh ta faɗa da alamar rashin jin daɗin abunda momy tata tayi
“shikenan nima ba dan komai yasa nake sawa ba sai dan na riƙa sanin halin da ku ke ciki,taking care of ur health is my responsibility”
“hakan yana da da kyau,we thank u for ur care for us” Aunty sophia ta faɗa, jin jina kai kawai Malika tayi, tashi Aunty sophia tayi ta nufi kitchen dan ta duba chefs, da kallo Malika ta bita har ta ɓacce ma ganinta.
“honestly momy baki kyauta ba, how many years Aunty sophia ke tare dake dan mi zaki sa mata C C TV a part,wannan old women ɗin mi kike tunanin zata iya aikatawa, ban da kula dani babu abunda take a gidan nan, that's why I love her,babu ruwanta”
wani kallon banza Malika tayi mata“u love her, ban gane ba?”
“yeah, ina jinta tamkar mahaifiyata wacce ta haife ni” harara Malika ta watsa mata
“ni fa?”
“u are special,ur position is different sweetheart” murmushi Malika ta saki.
❤💫❤💫❤💫❤💫❤💫❤
Tun da malika ta dawo Aunty sophia ta ƙauracema Nailarh ko part ɗin ta ta daina zuwa, iya karta ta duba masu aiki ta koma part ɗinta,duk wata hanya data san zata haɗata da malika tare da Nailarh tayi blocking ɗinta.
Yanzu ma tana kitchen ne tare da chefs tana sanar da su abubuwan da ya kamata su yi saboda celebration ɗin da za suyi bayan kammala wasan da Nailarh zata gabatar a yau, dama al'adarta ne duk ƙareshen shekara suna gabatar da wasa wanda ya fi kowane a N R T.
Duk wanda yake ji da kanshi a wasan doki zaka sameshi a ranar gasar, ƙwararrune daga yanki daban daban na ƙasar dama wasu ƙasashen ke halartar wasan, tsawan shekara biyar kenan suna gabatar da wasan har yau ba'a samu wani wanda yayi zarrar da zai zo na ɗaya a gasar wasan ko wane lokaci Nailarh dai.
A hankali ta lallaɓo masu aiki na kallonta amma ba halin suyi magana saboda gargaɗin da tayi masu,hannuwanta tasa tana rufe mata eyes ɗinta ta baya.
Murmushi Aunty sophia ta saki ta san babu wanda zaiyi mata hakan face ita, hannunta dake kan idanunta ta kama
“baby” ta kira sunanta, sakin idanunta Nailarh tayi tana ɓata fuska
“u are too quick to recognize ” ta faɗa tana turo baki, murmushi chefs ɗin suka saki
“banda abunki Nailarh waye zai yiman haka bayan ke,how was ur night,I hope u slept well?”
“fine,na biyoki har nan ne dan naji laifin me na maki ki ke avoiding ɗina tow days?”
gaishe da ita chefs ɗin su ka shiga yi,jinjina masu kai kawai tayi, shafa fuskarta Aunty sophia tayi
“baki man laifin komai ba, na barki ki samu enough time with ur momy” taɓe baki Nailarh tayi
“amma ai kin zo har ɗaki kiyi wishing ɗi na ko?”
“kema kin san zan zo, ina duba chefs ne”
“baby!” aka faɗa daga bayan su, saurin kai dubansu su ka yi ga Miss Malika dake tsaye, PJ ne a jikinta da alama daga bacci take.
Cike da girmamawa suka shiga gaishe da ita, da kulawa ta amsa masu tana nufar cikin kitchen ɗin , kama hannun Nailarh tayi “ashe kina nan ki ka bar ni sai wahalar nemanki nake”
“nazo wajen Aunty sophia ne”
“ok muje” jan hannunta tayi
“Aunty sophia sai kin zo” jinjina mata kai tayi, ficewa su kayi daga kitchen ɗin.
*ABUJA NIGERIA💫*
Shigowar su kenan daga school duk a gajiye su ke,Yumnah tun a parlor ta cire mayafin dake kanta, a saman bed ɗinta su ka yada zango.
“wallahi sis am very tired
har ƙosawa nayi a kammala lectures” Yumnah ta faɗa tana ya mutse fuska
“me too, yanzu bani da wani buri da wuce na watsa ruwa na kwanta na huta before magrib” Nainarh ta faɗa tana nufar dressing room.
kwanciya saman bed ɗin Yumnah tayi “ni gaskiya sai na tashi daga baccin tukun zan yi wanka”
Nainarh na shiga dressing room ɗin jakarta ta a jiye tukun ta cire kayan jikinta ta ɗaura towel, bedroom ɗin ta koma, Yumnah na nan kwance har bacci ya fara ɗaukarta.
toilet ta nufa ta watsa ruwa kafin ta fito, dressing room ta koma,gown ta saka mara nauyi kafin ta dawo bedroom ɗin kwanciya tayi kusa da Yumnah.
Duk yanda take jin bacci kafin ta kwanta, tana kwanciya taji kwata kwata baccin ya ƙaurace ma idonta,juyi ta shiga yi a bed ɗin Yumnah kuwa baccinta take hankali kwance.
shiru tayi tana ƙurama sailing ido, ba komai ya faɗo mata a rai ba sai photon da ta gani a part ɗin Abbah, bata san waye a photon ba amma haka nan ta kwaɗaitu da san sanin waye shi, kullum tana son tambayar Yumnah amma sai ta manta.
kallon fuskar Yumnah tayi kafin ta maida idonta akan teddy bears ɗinta dake ajiye saman head board ɗin bed ɗin.
ƙaramin tun bata da wayau mahaifiyarta ta bata shi, babban kuwa mahaifinta ya bata shi a matsayi kyautar ƙarin shekara lokacin data kai kimanin shekara goma.
Murmushi ta saki lokacin data tuna shirmenta na yarinta, haka zata tasa teddys ɗin a gaba tana faɗin ga momy ga dady,haka iyayenta za su tasata gaba suna dariya, duk tana tuna rayuwarta da iyayenta abun ba ƙaramin nishaɗi yake bata ba,amma lokaci ɗaya komai ya rushe, duk ta tuna kisan wulaƙantaki da aka yima mahaifinta da sharrin da aka da bai baye mahaifiyarta dashi sai taji wani ƙunci ya mamaye zuciyarta, ta rasa laifin mi su ka aikatama wanda yayi masu haka.
Adu'arta a kullum Allah ya toni asirin wanda yayi silar rushewar farin cikin su, shima Allah ya rusa nashi farin cikin, ya tozarta rayuwarshi kamar yanda ya tozarta ta su, sosai tayi nisa a duniyar tunani ringing ɗin wayar Yumnah ne ya dawo da ita hayyacinta, a jiyar zuciya ta sauke tana jawo jakar, wayar ta ciro, duba sunan mai kira tayi,ya Naeem ta gani.
da sauri ta ɗan bubbuga kafaɗar Yumnah “ki tashi ya Naeem na kira” juya kwanciya Yumnah tayi
“please ki ɗaga kice mashi bacci nake” picking call ɗin tayi tana kara wayar a kunenta
“Assalamu Alaikum” ta faɗa, on the other hand ya Naeem ya amsa mata sallamar
“ya Naeem ina wuni”
“lafiya lau Yumnah, kun dawo ne ko har yanzu kuna school?”
“ba ita bace, Nainarh ce” Nainarh ta bashi amsa
“yawwa Nainarh dama ke nake nema, kun dawo daga school ɗin?”
“eh” ta bashi amsa
“ok,meet me in the garden now” a sakale ta amsa mashi,mamaki ne ya cikata, neman mi yake mata
“right now” ya sake jaddada mata haɗi da rejecting ɗin call ɗin
“ni kuma, neman mi yake man” ta faɗa da tsantsar mamaki, ajiye wayar tayi ta nufi toilet, bata wani jimaba ta fito, dressing room ta nufa, hijab ta ɗauko,ficewa tayi daga ɗakin.
bata samu kowa a parlorn ba, tun daga nesa ta hango su saman chairs shi da ya Adnan a garden ɗin, waya ce kare a kunen ya Naeem ɗin da alama waya yake, tunda ta tunkaro su ya Adnan ya kafeta da ido yana kallota harta ƙaraso in da su ke, sallama tayi masu ya Adnan ne ya amsa mata ya Naeem kuwa hannu kawai ya ɗaga mata.
Cike da ladabi tana ɗan rissinawa ta gaishe da Ya Adnan ɗin, da kulawa ya amsa mata yana sakar mata murmushi ya nuna mata chair dake fuskantar wacce su ke zaune dan ta zauna, murmushi ta saki “nagode” ta faɗa tana zama.
“ya school,fatan kun dawo lafiya?”
“lafiya lau Alhmdllh” masha Allah ya faɗa, hankalin su ne ya koma kan ya Naeem dake waya
“it's a favor i'm asking for, please ka taimaka ranar birthday ɗinka ka zo,ya ɗauki ranar birthday ɗinka rana mai daraja da mahimmaci, ka daure a wannan karon ka tabbatar mashi da darajar ranar,the anger u have with him is enough, dan Allah ka kawo ƙarshen wannan guje mashin da ka ke”
ɗan dakatawa yayi da magana ya can ya cigaba
“kayi shiru ba kace komai ba, ka sa ni yanda ya ke sonka ko mu dake tare dashi baya mana son da yake maka, baka tare dashi amma duk wani abu daya shafeka baya wasa dashi,ka sani duk abunda zaiyi mana a rayuwa sai yayi maka,more than u think,wasu har gani suke kamar ya samu taɓin hankali a kan ka saboda wasu abun da yake hankali ma bazai ɗauka, please yaci albarkacin wannan ƙaunar da yake maka kayi haƙuri ka daina wannan fushin da shi” sosai ya Naeem ya kwantar da murya yana bashi haƙuri duk dan ya sauko.
zuba mashi ido Nainarh da ya Adnan su kayi, lamarin yayi matuƙar ɗaure mata kai waye wannan ake haɗashi da Allah irin haka amma yaƙi yayi abunda ake so.
“shikenan kayi duk abunda ka ke ganin shine dai dai, amma ka sani haƙƙin baƙin cikin da kake cusa mashi bazai barka ba, he's ur father, ko wane irin laifi zaiyi maka aduniya he didn't not deserve to be anger with him” yana gama faɗar haka yayi rejecting call ɗin.
haka nan Nainarh ta tsinci kanta da rashin jin daɗin abun, bata san ko waye ba amma bai kyauta ba mahaifa ba abun wasa ba ne.
“in wuni ya Naeem”
“lafiya lau Nainarh, ya school”
da Alhmdllh ta amsa ma shi
“dama akwai wasu maganganu da nake son zamu tattauna game da abunda ya faru da dadynki”
tunda ya faɗi haka yanayin fuskarta ya canza, fahimtar hakan ne yasa shi cewa
“karki damu ba wani abu bane kawai ƴan tambayoyi ne zanyi maki,in dai ki ka bani haɗin kai in sha Allah za muyi nasarar gano wanda su ka kashe shi”
“in sha Allah zan baka haɗin kai, duk wani abu dana sani zanyi ƙoƙarin sanar da kai”
“yawwa haka nake son ji,
da na so muyi maganar yanzu,but bana da time, zuwa ranar Saturday za muyi magana ko kuje can gida keda Yumnah ku same ni”
“to shikenan, Allah ya kaimu”
“Ameen ya Allah, za ki iya tafiya kawai” to tace ta na tashi daga chair, sallama tayi masu ta koma cikin gidan, ranshi ya rigada ya gama ɓaci bayajin zai iya maganar da za suyi shiyyasa kawai ya sallameta.
tunda Nainarh ta fito daga gidan ta nufo garden yake tsaye bayan pillar da waya a hannunshi, da alama video yake ɗaukar su, baƙaƙen kaya ne a jikinshi ya rufe ko ina na jikinshi banda idanun shi babu wani abu da ake iya gani daga jikinshi.
Nainarh na tunkaro ƙofar shiga gidan yayi saurin ɓoyewa yana zura wayar Aljihun wandon jikinshi, kowaye da alama leƙen asiri yake masu.
ɗan dukan kafaɗar ya Adnan ya Naeem yayi ganin ya bi Nainarh da ido
“ya dai,lafiya ka kafe yar mutane da ido ka ke binta da wannan kallon ƙurillar?”
kauda kai gefe ya Adnan ɗin yayi yana sakin murmushi
“ba komai, kawai dai tana burgeni ne she's so innocent” murmushi ya Naeem yayi
“ka tsaya dai iya haka”
dariya ya Adnan ɗin yayi yana girgiza kai “ya ku ka yi da SAM ɗin ya amince kuwa?” ya Adnan ya faɗa yana kallon fuskar ya Naeem, tsaki ya Naeem yaja
“ka kyale SAM kawai Adnan,na rasa gane wane irin bauɗaɗɗan mutum ne shi, Allah ma muna mashi laifi ya yafe mana sai shi ne bazai yafe ba, na rasa a wajen ubanwa ya gaji wannan baƙar zuciyar da idan ya juyama abu baya ya juya mashi kenan?”
“uncle Mustafa shi ka manta tashi kalar zuciyar ne?”
“uhmmm Allah gara uncle Mustafa dashi, tsawan shekara nawa kenan ana fama dashi amma ya maida mutane shashashu, ka du ba fa ka ga irin haukan da dady keyi a kan shi wannan bai isa ba ace ya yi haƙuri,bawan Allah nan sau nawa yana taka ƙafa ya bishi amma haka zai ƙaraci zamanshi ya dawo bazai taɓa ganinshi ba haba” ya ƙare maganar cikin fushi
“Allah ya kyauta, amma SAM lamarin shi sai shi, ni kaina sai na kusa haɗa shekara banji muryarshi ba” ya Adnan ya faɗa
“wallahi zanyi mashi maganin abun da ke damunshi ne” murmushi ya Adnan ya saki
“ai da yake kunfi kusa, dama da kai yake uban ba da dady ba” tsaki kawai ya Naeem yaja.
*Queen Kainart💫*
tafe take kwata kwata bata lura da mutum dake tahowa ba duk da ƙofar ta glass ce,shima hankali shi baya gaban shi yana a kan wayarshi da yake latsawa.
saurin ja da baya tayi dalilin karon da su ka yi,wayar dake hannunshi ta faɗi ƙasa, dafe goshinta da ya bigi broad chest ɗin shi tayi,wani irin zafi ne ya ziyarci kwakwalwarta, a masifance ta ɗago tana kallonshi ido cikin ido
“dallah malam baka gani ne or are u blind da ka ke tafiya baka kallon gabanka??” ta faɗa tana wani zazzare mashi ido, wani irin haushin shi da tsanar shi take ji a ranta.
kasa magana yayi saboda mamaki daya rufe shi, ta bugeshi har ta yar mashi da waya ƙasa amma ta rufeshi da faɗa kamar wani sa'anta,mamakinshi ma a ina ta samu confidence ɗin yi mashi rashin kunya.
harara ta sake watsa mashi haɗi da jan tsaki,raɓawa tayi ta gefenshi zata wuce, rai a ɓace ya fisgo Arm ɗinta, gaba ɗaya ta tafi taga taga zata faɗin, riƙota yayi sosai, idan da abunda ya tsana a rayuwarshi tsaki, ya tsani tsaki musamman ace mace ce tayi mashi shi.
Raba idanu ta shiga yi a fuskarshi, ba ƙaramin tsorata tayi da yana yin shi ba,cike da mugunta ya sake matse hannunta,saurin rintse ido tayi saboda wani zafi daya shigeta.
Murya a kausashe yace “wa ki ke ma tsaki?” banza tayi da shi ƙoƙarin ƙwace kanta kawai take daga riƙon da yayi mata, tsawa ya daka mata “tambayarki nake wa ki ke ma tsaki??” ya faɗa yayin da yake murɗe hannunta
fashewa tayi da kukan azaba, murya na rawa tace “ai ba da kai nake ba”
“dawa ki ke” ya faɗa fuska a ɗaure
“dan Allah kayi haƙuri”
“tsaran wasanki ne ni?” girgiza mashi kai tayi hawaye na bin cheek.
“bani wayata” ya faɗa yana nuna mata wayarshi dake yashe a ƙasa
“ka sakar man hannu to” sakin hannunta yayi, duƙawa ƙasa tayi ta ɗauko mashi wayar
“gashi” ta faɗa tana turo mashi baki.
amsar wayar yayi yana sake riƙe hannunta “this should be the first and last time da za kiyi gigin yiman rashin kunya if not, sai na ɓaɓɓalaki a gidan nan useless”
“IRFAN” su ka ji an faɗa a bayan su.
saurin sakin hannunta yayi yana juyawa bayanshi,dady ne da uncle hashim,tun lokacin da su ka yi karo su ke tsaye suna kallon su.
hannunta da Irfan ɗin ya riƙe ta shiga murzawa saboda zafin da yake mata
“Irfan mi ya haɗaka da ita?” dady ya faɗa
“babu komai, ina wuni Uncle”
“lafiya lau” uncle hashim ya faɗa, saurin barin wajen Irfan yayi ya nufi garden wajen su ya Naeem.
“zo nan Nainarh”dady ya faɗa yana mata alama data zo, nufo su tayi har time ɗin hawaye na bin kumatunta, hannu dady yasa ya shiga share mata hawayen
“kukan ya isa haka, mi yasa ki ka yi mashi rashin kunya?”
“babu komai”
“he's ur elder brother, kar na sake gani,kina jina ko”
“eh dady in sha Allah bazan sake ba”
“haka nake son ji, ga Uncle ɗin ku nan ku gaisa” ya faɗa yana nuna mata Uncle hashim dake tsaye yana kallonsu
“in wuni Uncle”
“lafiya lau, ya ki ke, ya school??”
“lafiya lau Alhmdllh”
“masha Allah, Allah ya taimaka”
da Ameen ta amsa tana barin wurin ta nufi bedroom ɗin su.
tana shiga bedroom ɗin saurin zame hijab ɗin jikinta tayi tana kallon hannunta da Irfan ɗin ya riƙe wurin har yayi ja.
wasu hawaye ne su sake taruwa a idonta “mugu kawai” ta faɗa tana turo baki.
*Queen Kainart*💫
“muje ko” ya dady ya faɗa yana kallon Uncle hashim
“gida zan tafi”
“tafiya dai hashim, ai ka shiga ku gaisa da Zulaihart ko?”
“A'a yaya tafiya zanyi, idan na sake dawowa mun gaisa”
dady ya faɗi haka ne kawai amma dama ya san uncle hashim bazai tsaya ba in dai dan su gaisa da mom ne
“shikenan ka gaishe da mutanen gidan”
“za su ji, sai anjima” jin jina mashi kai dady yayi yana nufar sama zuwa part ɗin shi.
ficewa uncle hashim ɗin yayi amma instead of ya fice daga gidan baki ɗaya sai ya nufi part ɗin Mamy, bai samu kowa a falonta ba, masu aiki na part ɗin su Fa'iza na gidan shi wurin Balqis.
direct bedroom ɗinta ya nufa, bai sameta a ciki ba sai ƙarar ruwa da yaji a cikin toilet alamar tana ciki.
bed ɗinta ya nufa, zama yayi yana kwantar da kanshi jikin head board, wayarta dake ajiye kan nightstand ya ɗauka, babu password a wayar hakan ya bashi damar shiga contact da messages ɗinta.
turo ƙofar toilet ɗin tayi ta fito tana yarfe hannunta da alama alwala tayi, da mamaki take kallonshi bata san yaushe ya shigo ba, mamakin ganinshi a irin wannan lokacin ne ya hanata ƙarasawa gare shi.
wayarta dake hannunshi ya ajiye yana zuba mata mayatattun idanunshi “ƙaraso mana ki ka tsaya nan” ya faɗa ganin tayi tsaye kamar an dasata.
cikin ɗakin ta nufo kamar yanda ya umarta “yaushe ka shigo, baka tsoron wani ya ganka a irin wannan lokacin??” jin jina mata kai yayi alamar eh
“eh fa kace, baka gudun yayanka ya shigo gidan?”
“tare mu ka shigo da shi, yana part ɗin shi”
“amma shine ka shigo part ɗin, baka tsoron ya shigo part ɗina??”
“wait mabaruka kinyi farin cikin gani na ko na tashi na kama gabana?” ya faɗa yana ɗan tsuke fuska alamar rashin jin daɗin tambayoyinta
“kaima ka san am really happy to see u but kawai dai bana son abunda zai jawo mana matsala”
sauka yayi daga saman bed ɗin ya nufo inda take, kama hannunwanta yayi ciki nashi
“naga hankalinki bai kwanta da zuwana ba,lee me go” ya faɗa yana sakin hannunta, saurin kamo hannunshi tayi
“tunda har kai hankalinka a kwance yake bana da wata matsala”
“are u sure?”
“really sure, kai da kazo ma baka damu ba sai ni daka iske”
a jiyar zuciya ya sauke yana wani lumshe ido
“why did u not pick my call yesterday?”
“am with u brother, ka san jiya a wajena yake”
“mi yarinyar can take har yanzu bata bar gidan nan ba?”
tsaki taja “hmmm ka bari kawai u know ur brother yanda yake da matarshi komai tayi dai dai ne a wajansa, duk wata hanya na bi dan ganin ta bar gidan nan har mama Ameenah na sanar mawa tace za tayi mashi magana amma shiru, dama nayi mashi maganar sai shata man layi yayi akan yarinyar, wani mugun sonta yake ga yarinyar da ɗan banza kilibibi, duk wata hanya data san zata bi danta samu shiga a wurinshi sai da tayi”
“alright, amma dole yarinyar nan ta bar gidan nan kema kin san da haka?”
“i know, in sha Allah zanyi iya bakin ƙoƙari na ganin tabar gidan nan” jawota yayi zuwa jikinshi, cikin wata irin shu'umar murya yace
“alright, yaushe zaki bar ya Tahir ki dawo gare ni, na gaji da wannan raba dai dan da nake dashi” ya faɗa yana wani lumshe ido
“ko a yanzu a shirye nake, umarninka kawai nake jira” sake matso da ita yayi jikinshi, hannunshi ya zura bayanta, zip ɗin rigarta ya shiga zugewa, a hankali ya furta “har yanzu burinmu bai cika ba mabaruka”
“don't worry about that, nan da wani lokacin komai zai zo ƙarshe”
“are u sure?”
“am sure, Fa'iz da Fa'iza ne kawai nake ganin za suyi man cikas”
“karki damu da wannan sun riga da sun girma, kuma ko baki nan Zulaihart zata kula da su kamar yaranta, kuma da sunyi Aure ai shikenan”
“haka ne, amma maimunatu fa kasanfa bana son zama dakai tare da kowa?”
“maimunatu is not ur problem ni na san yanda zanyi da ita” ya faɗa yana wani kashe mata ido ɗaya, murmushi ta saki itama tana maida mashi martani.
saurin manne bakinshi yayi da nata, a zafafe ya shiga kissing ɗinta ba ƙaƙautawa,sun jima a haka har ƙafafunsu suka fara gajiya, ganin tsayuwar baza tayi masu bane yasa shi sakin bakinta,ida unzipping rigartar daya fara yayi, he slipping her all and throw it away, sake manne bakinsu yayi yana ɗaukarta,a haka ya nufi bed da ita.
*UNITED STATE❤*
_*Las Vegas (Nevada)*_
*THE PRESENT DAY*
Aunty sophia da Chefs ne a kitchen suna shiri akan celebrating dinner da za suyi zuwa anjima,suke aikin tana kula da su,tunda miss Malika ta dawo ta koma kitchen duk da ba girki take ba.
“i hope Miss Nailarh enjoyed this Burger more than the previous one”
ɗaya daga cikin chefs ɗin ya faɗa,riƙe ƙugu wanda ke gaban oven yayi “i also wish this cake is better than the last celebration”
murmushin Aunty Sophia ta saki tana jin kowa da abunda yake buri
“ni dai ba komai ke burgeni ba except how we can relax today,har Adu'a nake shekara ta zagayo because of this celebration,i like how Nailarh allow us to do what we want on this day” ɗaya daga cikin chefs ɗin ta faɗa tana sakin murmushi.
Aunty Sophia na sauraron kowa sai faɗar albarkacin bakinsa yake ƙala bata ce masu ba,amma tana jin daɗin yanda su ke yabon Nailarh.
maida hankalinsu su ka yi kan aikin da suke,ƙarar fashewar wani abu su ka ji daga waje
“ba ku jin wata ƙara kamar fashewar nockout?” ɗaya daga cikin chefs ɗin ya faɗa
“ko dai sun dawo ne ,naji kamar hayaniya ƙasa ƙasa?” wani ya sake faɗa daga cikin chefs ɗin,tashi Aunty Sophia tayi daga saman chair ɗin da take zaune
“ku ci gaba da aiki,lee me check” Aunty Sophia ta faɗa tana nufar ƙofar fita.
sauran ƙiris suyi karo da luna ta shigo kitchen ɗin da gudu,da sauri Aunty Sophia taja baya tana kallonta ganin yanda ta shigo kitchen ɗin kamar wacce aka koro
“lafiya!?” Aunty Sophia ta faɗa tana leƙen bayanta ko za taga abunda ya biyota.
da mamaki Aunty Sophia ta dawo da dubanta gareta dan ba taga komai ba “are u okay?”
ƙofar fita ta shiga nuna mata tana sauke numfashi da sauri sauri alamar na wanda yayi gudu ko yaga wani abun tsoro.
“minene wai,i don't see anything?” da ƙyar luna ta fisgo kalma daga bakinta tace “Na..i..larh” zaro ido Aunty Sophia tayi,da sauri ɗaya daga cikin chefs ɗin ya miƙa mata ruwa,hannunta har rawa yake wajen amsar ruwan,kafa kai tayi ,tas ta shanye ruwan tana maida numfashi “Miss Nailarh shot Alex with a gun!”
wani mummuna faɗuwa gaban su yayi,gaba ɗaya su ka zaro ido suna kallon luna da tayi maganar,Aunty Sophia bata tsaya jin abun da luna zata sake cewa ba ta fice daga kitchen ɗin da sauri ta nufi main parlor,tana shiga parlorn Nailarh na Kunno Kai da gun a hannunta yayin da miss Malika ke biye da ita kamar mahaukaciya tana mata magiya akan ta ajiye gun ɗin.
cikin parlorn security ɗin su ka shigo da Alex hannunshi sai jini yake,ba ƙaramin tashi hankalin Aunty Sophia yayi ba,da sauri tasha gaban Nailarh “baby are u out of mind,what are u planning to do like this?”
ɗago idanunta tayi ta kalle Aunty Sophia,da sauri ta kauda kanta gefe ganin yanda idanun Nailarh su ka yi jawur wutar ɓacin rai ce kawai ke ci a cikin su, fuskarta tayi jawur musamman cheek ɗin ta.
“if u dont move of on my way,I will kill u!”
Kamar saukar aradu haka Aunty Sophia taji maganarta
“Nailarh are you saying that you will kill me?” tsawa Nailarh ta dakata mata tana zaro mata ido
“i said move or I will shoot u!” gaba ɗaya parlorn babu wanda hankalinshi bai tashi ba yau Nailarh kema Aunty Sophia tsawa har take faɗin zata kashe ta lallai ba ƙaramin ɓaci ranta yayi ba.
wasu irin hawaye ne su ka wanke fuskar Aunty Sophia cikin ƙunar rai tace“bazan matsa ko ina ba kill me Nailarh”
“sophia are out of mind or u forgot who's Nailarh when she's angry?”miss Malika ta faɗa tana zazzare ido
“babu inda zan matsa taje ta illata kanta,Nailarh just kill me if that can calm u're mind”Aunty Sophia ta faɗa babu alamar tsoro,nuna ta Nailarh tayi da gun ɗin,rintse ido Aunty Sophia tayi,wani irin wahalallan yawu miss Malika ta haɗe kamar ita aka nuna da gun ɗin.
magiya parlorn su ka shiga yima Aunty Sophia kan ta matsa amma ko gezau ba tayi ba.
hawayen da suka taru idonta tun ɗazu sai yanzu su ka samu damar zubo,wani irin Shaking jikinta ya shiga yi,canza direction ɗin gun ɗin tayi zuwa sama, crystal Chandelier ɗin dake ceilling tayi shooting,gaba ɗaya ya ruguzo ya faɗa kan center table dake parlorn,toshe kunnuwansu su ka yi in ka cire Aunty Sophia data kafe Nailarh da idanu hawaye na zuba.
hawaye ne su ka shiga sintiri a fuskar Nailarh,ita kuka Aunty Sophia kuka ga wani irin rawa da jikinta ke yi,jifa tayi da gun ɗin da gudu ta raɓa ta gefen Aunty Sophia ta nufi sama.
zubewa Aunty Sophia tayi kan gwiwoyinta,bin bayan Nailarh miss Malika da sauran masu aikin su ka yi,kallo su Alex Aunty Sophia tayi tace su tafi hospital,ficewa su ka yi dashi har time ɗin jini ke zuba.
tashi tayi tabi bayan su jiki a sanyaye dan taga halin da Nailarh take ciki,daga nesa ta hange su a home bar kasancewar glass wall ne a wurin,da sauri ta ƙarasa
a tsaye ta same su sunyi cirko cirko idanunsu a kan Nailarh dake tsaye ta ɗaga kwalbar wine tana ɗurama cikinta.
da mugun sauri Aunty Sophia ta faɗa ɗakin har tana bangaje wanda ke bakin ƙofa,a zafafe ta fisge kwalbar daga hannun Nailarh tayi jifa da ita nan take kwalbar ta fashe.
“mi yasa ki ka yi haka sophia?,atlest idan tasha zata samu relief” Malika ta faɗa, ko kallon inda take Sophia bata yi ba kamar ma bata san tana magana ba,cikin raunannar murya tace
“Nailarh idan rai ya ɓaci hankali baya gushewa,wannan abun da ki ke is not a solution,ko kin manta alƙawarin da ki ka yi man,mi yasa ki ke son maida hannun agogo baya,tell me mi ke damunki sai muyi solving matsalar tare???” cike da kulawa Aunty Sophia ta faɗa.
hannu biyu Nailarh tasa ta kama kwalar rigar Aunty Sophia,zaro ido su kayi gaba ɗayan su da mamaki su ke kallon Nailarh,Aunty Sophia ma da tsantsan mamaki take kallon Nailarh.
jijjigata Nailarh tayi cike da karaji tace “who is he,kalamanki na ranar da momy zata dawo sun tabbatar man dasa hannunki,tell me who's he??” ta ƙarashe maganar tana daka mata tsawa.
wani irin mugun tashi
hankalin Aunty Sophia yayi dan kwata kwata bata fahimci inda zancen Nailarh ya dosa ba “baby what are u talking about, please kiyi man bayani?”
“i said who is he answer me” Nailarh ta faɗa tana wani zare mata ido, hawaye ne suka wanke fuskar Aunty Sophia,girgiza mata kai ta shiga yi “believe me Nailarh ban san akan mi kike magana ba” gani tayi ɗakin na juya mata ga wani irin ciwo da zuciyarta ke mata,dafe saitin zuciyarta dake barazanar faso ƙirjinta ta fito tayi tana faɗin “my chest”gaba ɗaya ta tafi zata faɗi da sauri Aunty Sophia ta riƙota jikinta,gaba ɗaya ta faɗa jikinta
“please Aunty Sophia waye shi” Nailarh ta faɗa a hankali daga haka kuma bata sake cewa komai ba, jikinta ya saki alamar suma tayi.
fashewa Aunty Sophia tayi da kuka kamar ƙaramar yarinya..
*Ya Allah mike shirin faruwa dake Nailarh,mi ya faru a N R T*
*Back to N R T Dan muji abunda ya faru*
Track ɗin a cike yake maƙil ,ta ko ina ka duba mutane ne zazzaune a mazauninsu da aka tanada,Track ɗin ya cika Masha Allah,mutane ne daban daban daga garuruwa daban daban wasu ma ba daga ƙasar su ke ba.
kamar ko wane lokaci suna sanye da shirt da cap na track ɗin kamar yanda ya kasance al'adar wajen.
daga gefe manyan baƙi ne da, wasu daga cikin ƙasar su ke wasu kuma daga wajen ƙasar,suna zaune a mazauninsu na musamman wanda akatanadar masu,miss Malika na cikin manyan baƙi ta ɗau wankan Sheath gown kamar wata yarinya kanta sanye da haɗaɗirya hat mai net daga gabanta anyi mata ado da bird feather,su luna na daga gefenta tsaye,kiɗa da bushe bushe ne ke tashi a cikin Field ɗin.
dawaki ne aƙalla guda ashirin a cikin field ɗin,suna a killace cikin ɗan cage ɗin su a tsaye,kowa wane doki akwai mutum a saman shi,a shirye su ke umarnin fara gudu kawai su ke jira, Nailarh na daga tsakiyar dawakan saman dokinta.
wani baƙin doki ne a hannun damanta sai sheƙi yake yana ɗaukar ido,kallon wanda ke kan dokin tayi,daga yanayin shigarshi ta fahimci sabon ɗan wasa ne dan komai nasa daban yake da nasu hatta suturar dake jikinshi da helmet ɗin dake kansa,sosai ta zuba mashi ido tana kallo, banda idanunshi bata iya hangen komai daga fuskarshi,saurin kauda kai tayi ganin yana ƙoƙarin juyowa alamar ya fahimci ana kallonshi,kallon inda Nailarh take yayi,kallon ƴan seconds yayi mata ya ɗauke idonshi.
lokaci na cika aka basu damanr far gudu ta hanyar hura whistle,cike da karsashi dawakan su ka shiga gudu a cikin babban field ɗin, a tare su ka fara gudu abun gwanin ban sha'awa,sosai suke gudu kowa burin shi ya kai ga matsaya.
rarrabuwa dawakan su ka yi,shidda su ka yi gaba yayinda aka bar sha huɗu a baya,dawaki biyu ne cikin shidda su ka yi baya a dalilin karon da su ka yi da juna,hakan yasa suka koma bayan huɗu yayinda sha huɗu ke biye da su,sosai Dawakai biyu dake cikin sha huɗun su ka dage har sai da su ka cimma biyun dake gaban su suka zama su huɗu, huɗu na gaba huɗu na tsakkiya sha biyu a baya.
A wannan karan Nailarh ba tayi baya ba kamar na last wasan da su ka yi,tana cikin huɗu dake gaba,sosai ta dage dan ganin tayi nasara a wannan karon kamar ko yaushe.
Mutane kowa sai baza ido yake dan ganin yanda wasan zai kwashe,da yawan mutane na fatan Nailarh tayi nasara kamar ko wane lokaci yayinda wasu ba haka bane a zuciyar su burin su ta faɗi ko za su rage raɗaɗin kuɗaɗen su da suke asara a wajen wasan, murmushi kawai miss Malika ke saki cike da ƙwarin gwiwa take kallon wasan ta san cin galaba akan babyn tata abune mai wahalar gaske.
sosai su ka dage da gudun gashi har sun kusa isar ma matsaya amma dawakan nan uku na tare dana Nailarh, hankalin ta ne ya fara tashi ganin duk iya bakin ƙoƙarin da take dan ganin tayi masu zarra abun yaci tura, data ta samu ta kere masu sai su sake cimma mata.
duka ta kaima king dan a ganinta sakacinshi ne yasa har ta kasa tsere masu,ganin dai idan ba tayi wani abu ba komai zai iya faruwa ne yasa cike da dabara yanda alƙalan wasan bazasu lura da abunda take ba ta matsa kusa da dokin dake kusa dashi,cike da mugunta taja igiyar dake jikin dokin ta tarɗe ƙafar dokin,mahayin dokin baiyi auneba ba sai jinshi yayi ya tafi ƙasa har ya shafi dokin dake kusa da shi,gaba ɗaya su ka kifa ƙasa daga su har dawakan nasu,nan su ka shiga birgima a ƙasa,hankali tashe mutane su ka shiga miƙewa ganin abunda ya faru.
da gudu emergency officers
suka shigo cikin Field ɗin ɗauke da stretcher,ɗaukar wanda su ka samu rauni su ka yi suka ɗaura a stretcher su ka fice da su,juyawa Nailarh tayi tana sakin wani wicked smile ko a jikinta,yanzu ya rage saura su biyu daga ita sai wannan baƙin dokin,tunda yaga abunda tayi ya kafeta da ido yana kallon ta cikin helmet ɗin dake kanshi, fingers biyu yasa yayi saluting ɗinta,tsuke fuska tayi tana kauda kai.
haka aka cigaba da gabatar da wasan duk yanda Nailarh ta so yima wannan mai baƙin dokin mugunta kamar yanda tayi wacan abun ya faskara, ƙoƙarin kereta ma yake hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba gashi sun kusa isa Wining line,hankalin wasu daga cikin ƴan kallo ne ya fara tashi yayinda wasu ke fatan a karya tarihin N R T,ƙus ƙus ne ya fara tashi wasu na son sanin waye wannan dake neman yima Nailarh zarra dan da yawan mutane basu san shi ba.
hankali Nailarh sosai ya ƙara tashi, zufa duk ta wanke jikinta,tun tana ganin abun kamar wasa sai ga dokin nan ya ƙetare Wining line kamar a mafarki,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi ba shiri taci birki tana haki,abunda bata taɓa kawo ma ranta ba ya faru da ita,miss Malika ma zabura tayi daga inda take zaune tana kallon field ɗin.
Ihu da sowa ne ya fara tashi a filin wasan, mutane da dama hakan yayi masu,da gudu securitys ɗin wajen suka shigo cikin field ɗin, tai maka ma duk mahayan dawakan su ka yi su ka sauko daga kan dawakan,tsaye Nailarh tayi a wurin kamar idol, ta kasa motsawa in a shock take kallon field ɗin dan har yanzu ta kasa yarda da hakan gaskiya ne.
Murna wajen mutanen da su ka daɗe suna jin haushin Nailarh ba'a magana, dama da yawan su irin wannan ranar su ke fata gashi kuwa ta riske su.
cikin field ɗin mutane su ka fara shigowa suna nufar wannan mutumin da har yanzu yaƙi cire helmet ɗin dake kanshi haka ma Nailarh,hannu mutane su ka shiga bashi suna taya shi murna wasu kuma na hugging ɗin shi.
tunda ya sauka kan dokin idanunshi ke kan Nailarh ko ƙiftawa bayayi ganin mood ɗinta, walking majestically ya nufo inda Nailarh take still he's eyes on her kuma har time ɗin bai zame helmet ɗin dake kanshi ba,tunda ya tunkarota take kallon shi, yana da tsayi sosai dan ya kereta sosai duk da tana da tsayi, ƙaƙƙarfa ne na gaske yanada broad chest dan tana iya hangen shatin six pack ɗin shi ta jikin polo shirt ɗin dake jikin shi, ga wasu strong arms dake a murɗe, kallo ɗaya za kayi mashi ka gane gym product ne, bazaka iya tantance kalar fatar jikinshi saboda jikinshi dake a rufe.
saurin ɗauke idonta tayi daga kallonshi tana tsuke fuska, har inda take ya ƙaraso, ɗan rissinawa yayi dai dai saitin kunnenta ya kai bakinshi, whisper ya shiga yi mata, bazaka iya jin mi yake cewa ba, a hankali yake magana kamar baya son buɗe bakinshi,wani irin kishi ne ya turniƙe miss malika ta tsani taga wani ya raɓi Nailarh, wani irin kallon wulaƙancin ta shiga binsu dashi zuciyarta na wani irin tafarfasa.
sun kai five minute a haka kafin ya janye bakinshi daga kunnenta, saurin kallonshi Nailarh tayi, from head to toe yake kallonta ta cikin helmet ɗin kafin yayi saluting ɗinta a hankali yace “nice to meet u cutie,see u next time, have a nice day” ya faɗa yana ɗaga mata hannu,barin wurin yayi wani irin ƙara ɓaci ran Nailarh yayi.
da sauri Luna da sauran maids suka nufota Miss Malika na bayan su, hannu luna ta kai da nufin cirema Nailarh helmet ɗin kanta, saukar wani irin azabebben mari taji,saurin dafe cheek ɗinta tayi tana kallon Nailarh data mareta,a masifance ta zame helmet ɗin kanta tayi jifa dashi, jiki na ɓari malika ta nufota, kafin ta ƙaraso Nailarh har ta bar wurin ta nufi motocin su maganganunshi na yawo a brain ɗinta.
da sauri Alex ya buɗe mata back seat ko jiran su malika ba tayi ba tace ya kaita gida,Malika suna isowa suma motocin su suka shiga, da mugun sauri su ka bi bayan su Nailarh, a kusan tare su ka yi parking,ko gama daidaita parking driver baiyi ba Malika ta fito ta nufi Nailarh, tana isowa Nailarh na fitowa da gun a hannunta, hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, saita kanta Nailarh tayi da gun ɗin da nufin shooting kanta.
hakan ba ƙaramin sake ɗaga hankalin Malika yayi ba,umarni taba securitys da drivers ɗin dake wurin da su amshe gun ɗin, garin su amshe ne Nailarh ta harbi Alex.
*back to story*
Jijjigata Aunty sophia ta shiga yi tana kiran sunanta,miss Malika ma kamar za tayi hauka wajen kiran sunan Nailarh, ɗaya daga cikin chefs ne ya nufosu da ruwa, da sauri Aunty sophia ta amsa tana yayyafama Nailarh amma ko gezau ba tayi ba, tayi hakan kusan sau huɗu amma Nailarh bata farfaɗo ba,wani mummunan faɗuwa gaban Aunty sophia yayi haka ma miss Malika, tsoron kar ace ciwan Nailarh ne ya tashi ne ya mamaye zukatansu yaushe rabon da Nailarh ta samu Attack, dan suna kula da duk wani abun da zai ɓata ranta, komai ta buƙata yi mata su ke.
*Nailarh tunda aka haifeta take fama da haert Attack infact ma dashi aka haifeta, shiyyasa duk wani abu da zai faranta ranta miss malika na ƙoƙarin yi mata shi,haka Aunty Sophia bata wasa da lafiyar Nailarh duk wani abu da zai faranta mata tana ƙoƙarin yi mata tana kumakiyaye abunda zai ɓata ranta bare harya kai da ciwonta ya tashisai ta yi mi bata samu Attack ba dan duk abunda take so a rayuwa shi take samu*
hawaye su ka wanke fuskar Miss Malika, maids ɗin dake wurin wasu har sun fara zubar da ƙwalla
Jijjigata miss Malika ta shiga yi tana faɗin “please Nailarh wake up, I promised u to punish this man and sai ya girbi abunda ya shuka,sai yayi daya sanin shigar shi gasar nan, please wake up dear” kamar mahaukaciya haka take jijjiga Nailarh tana roƙonta akan ta tashi,Aunty Sophia banda hawaye babu abunda take.
“Please Nailarh, don't leave me, please wake up, I promised you, I promised u sai yayi daya sani,nayi maki alƙawarin zanyi mashi hukunci mai tsanani, don't leave me please wake up” Sosai take sambatu tana roƙon Nailarh,wani tausayin miss Malika ne ya rufe maids ɗin dan daga yanayin da take magana kamar bata cikin hayyacinta,da ƙar Aunty Sophia tayi ƙarfin halin faɗin
“Ma'am,I think she's on attack” Aunty Sophia ta faɗa tana share ƙwalla
ƙara rikicewa miss Malika tayi jin abunda Aunty Sophia ta faɗa.
zabura tayi da nufin ɗaukar Nailarh
“please tell Alex to bring the car, Sophia let's go to the hospital, I don't want to lose Nailarh” magana take tana ƙoƙarin ɗaukar Nailarh amma ta kasa,gaba ɗaya a gigice take har ta manta da abunda ya faru da Alex,da sauri luna ta fice dan sanar da NOAH saƙon miss malika,shima ɗaya daga cikin drivers ɗin gidan ne.
da sauri William ya ƙaraso cikin ɗakin,hannu biyu yasa ya ɗauki Nailarh,a shoulder ɗin shi ya ɗaurata,gaba ɗaya jikinta ya saki kamar mattaciya,ficewa su kayi daga cikin ɗakin baki ɗaya,miss Malika kamar zata tashi sama,Aunty Sophia kuwa sai sharar hawaye take.
NOAH har ya shiga Mota yayi mata key,jiran fitowar su kawai yake,back seat ɗin motar William ya saka Nailarh Aunty Sophia ta shiga kusa da ita yayin da miss malika ta shiga front seat,reverse yayi suka nufi main gate ɗin gidan, securitys ɗin ma shiga motocin su su ka yi harda su luna su biyu,bin bayan motar su miss malika su ka yi.
komawa bakin aikinsu suka yi sauran securits ɗin da aka bari,cikin gida chefs ɗin su ka koma wasu na jimami yayinda wasu ke sharar ƙwallar tausayin halin da Nailarh take ciki.
*Get well soon Nailarh,to be honest wannan bawan Allah baka kyauta ba😢*
*ABUJA NIGERIA*
*UNCLE MUTALLAF'S HOUSE*
saukowa yake daga saman stairs, walking gently yake taka stairs case ɗin,white suit ne a jikinshi,waya ce kare a kunnenshi.
“gaskiya I'm really happy yaya da wannan maganar,amma nayi mamaki da ban taɓa fahimtar hakan ba” saurin ɗaga kai mom fatilah dake zaune a parlor ita da Noor tayi tana kallon uncle mutallaf,kallo ɗaya za kayi mashi ka hango tsantsar farin cikin da yake ciki.
cikin parlorn ya ƙaraso,ɗaya daga cikin sofas ya nufa ya zauna “wallah da gaske nake yaya ban taɓa lura da hakan ba,kuma kasan duk rashin kunyar Noor Bata taɓa faɗa man ba” da sauri Noor ta tashi ta nufi dadynta jin abunda yace,saurin kai kunnenta tayi jikin wayar wai ko za taji dawa dadynta ke waya.
ture kanta yayi yana sakin dariya “kaji ja'iri wato shi mai kunya shine sai ya aiko maka abokinsa” ƴar dariya yayi yana gyara zaman shi
“to shikenan in sha Allah zuwa goben sai muyi magana,amma gaskiya nayi farin ciki da hakan Allah yasa ayi muna da rai,amma Abbah da yayan sun sani kuwa?”
ɗan jim yayi yana sauraron na cikin wayar can yace
“ok to shikenan Allah ya kaimu sai na shigo goben in sha Allah” sallama yayi da wanda yake wayar
“dady kai da waye ka ke waya?” Noor ta faɗa cike da shagawaɓa
“kawunki ne, maza je part ɗina ki ɗauko man glass ɗina yana Nan kan nightstand”
“to dady,amma maganar mi kuke kai dashi?”
“idan kin dawo zan faɗa maki” saurin tashi tayi ta nufi stairs case da sauri, girgiza kai kawai mom Fatilah tayi.
iska uncle mutallaf ya shaƙa tukun ya fisar,yayi ɗan shiru yana nazarin wani abu
“lafiya dai Dr?” mom fatilah ta faɗa tana leƙen fuskar shi, ajiyar zuciya uncle ya sauke kafin ya kalleta
“ya Ahmad ne ya kirani,kin san cewa Noor da Irfan soyayya su ke?” yana yin fuskar mom fatilah ne ya canza,tsuke fuska tayi
“mi ya faru,kiran mi yake maka to?”
“ya kirani ne ya sanar dani har ma sun tattauna maganar shi da su ya Ubaid, Abbah da ya Tahir ɗin ne kawai ya rage basu sanarmawa ba,amma yace zuwa gobe zai sanar da su dan a san yaushe ya kamata a sa bikin na su,amma fa nayi mamakin da ban taɓa lura da suna soyayya ba duk abun Noor ma bata taɓa sanar dani ba” tunda ya fara magana mom fatilah ta shiga binshi da wani kallon rainin wayau,Noor saukowarta kenan taji abun da dadyn nata ke furtawa,da gudu ta nufi ɗakinta ba tare da ta ko kawo masa glass ɗin da yace ta ɗauko mashi ba.
“gaskiya naji daɗin haka,kinga kafin mu tafi sai a tsaida ranar Auren na su zuwa bayan sallah sai ayi bikin,yara nata ƙara mana daƙon zumunci,saura Yazdan fatana shima ya daina wannan shashanci ya zama mutumin ƙwarai kinga sai mu haɗa su shi da Yumnah” kallon mom fatilah yayi jin tunda ya fara magana ƙalla ba tace ba
“naji kinyi shiru ba kice komai ba,magana nake kana Auren Noor f...” saurin katse shi mom fatilah tayi
“dan Allah dakata Dr,wallahi sam ba zai yiwu ba”
da mamaki yake kallonta bai taɓa tunanin wannan ce kalmar zata fito daga bakinta ba.
“fatila kin san mi ki ke faɗa kuwa?”
“na san mi nake faɗa kuma ina cikin hankalina,wannan haɗin sam bazai yiwu ba ni ba hajiya halima bace ko salima da ku ka nunama fin ƙarfi akan ƴaƴan su,ku ka nuna basu da right ɗin zaɓarma ƴaƴan su abokan zama,ni sam bazan ƴarda da wannan ba,babu ƴaƴana babu ƴaƴan Zulaihart period”
kallonta kawai uncle mutallaf keyi cike da mamaki,ko a mafarki bai taɓa tunanin wannan amsar daga gareta ba,yayi matuƙar mamakin ta duk da ya san ba su jituwa da matar yayan nashi.
“wallahi babu ƴaƴana babu ƴaƴan Zulaihart,haka kawai kuyita kwasar mana ƴaƴa kuna ba ƴaƴan Zulaihart sai kace ita kaɗai ke da ƴaƴa, gaskiya ni ban amince ba”
“amma nayi mamakin jin haka daga gareki,banyi tunanin za ki yi haka ba,miye laifin Zulaihart ne da zaki ƙi son haɗa alaƙa da ita,ai ko dan ya Tahir da farin cikin ƴarki kin amince”
tashi tayi daga inda take zaune cikin ɗaga murya tace
“wallahi bazan amince ba,haɗa dangantaka da Zulaihart wallahi bazan yi ba,ai da Noor ke faɗa man na ɗauka shashancinta ne ai ban san abun da gaske bane da wallahi tuni nayi ma tufkar hanci,haka kawai kuyi ta haɗa mu da dangin yahudawa, wallahi tun wuri kace ma ƴan uwanka baka amince ba dan Noor bazata Auri Irfan ba” ta kai ƙarshen maganar tana huci
“kin gama” uncle Mutallaf ya faɗa yana tsareta da idanu
“ban gane na gama ba,haka kawai sai inƙi faɗin ra'ayina,kowace yarinya sai ku ɗauka kuba ƴaƴan Zulaihart haka akeyi,idan su hajiya halima sun amince saboda kwaɗayin abun duniya ni wallahi bazan amince ba”
“Fatilah ina so ki san wani abu Noor da Irfan are my kids, ke baki isa ki sa na fasa abunda nayi niyya ba,Aure tsakanin Noor da Irfan Kamar anyi an gama ne in dai ni ne ubanta ba wani daban ba” ya faɗa a kausashe
“lallai Dr zaka tafka babban kuskure in dai kace sai ta Auri Irfan”
“kwarai kuwa,kije kiyi duk abunda ki ke ganin zaki iya amma Aure tsakanin Noor da Irfan Kamar anyi shi angama,ke baki isa kisa na zuba ma ƴan uwana ƙasa a ido ba,yanda aka yi na Naeem da Adnan lafiya haka za'ayi na Noor da Irfan sai dai kiyi duk abunda za kiyi”
Kwashewa tayi da wata irin dariya“haka dai kace ko,za kuwa kaga abunda zan aikata” sosai saɓani ya shiga tsakaninsu akan wannan maganar.
Noor lokacin data nufi bedroom ɗin ta,wayarta ta ɗauka tayi dialing number Irfan,har Kiran ya katse baiyi picking ba, sake kira tayi sai a na biyun ne yayi picking
“hey beb, what's up?” ya faɗa daga cikin wayar
“am really happy dear,yau dai ka cika alƙawari, i really really love u irin billions ɗin nan,i wish kana kusa da na baka warm hug of happiness”ta faɗa tana sakin dariya
daga cikin wayar tana jin yanda ya sauke ajiyar zuciya “I would like that baby,but wait farin cikin mi kike?”
“ban gane farin cikin mi nake ba,kana nufin baka sani ba?”
“am serious dear ban sani ba” ɓata fuska tayi tana turo baki
“bana son wannan wasan yaya”
“am serious Qanwata ban sani ba”
“yaya yanzu maganar Auren namuce baka sani ba” ta faɗa tana wani murguɗa mashi baki kamar irin yana kusa da ita ɗin nan
“maganar Auren fa,a ina ki ka ji?”
“yanzu naji dady na waya da Uncle Ahmad yana sanar dashi” ajiyar zuciya taji ya sauke
“Alhmdllh, gaskiya naji daɗin jin haka,am really happy dear” dariya ta saki
“wai da gaske ba kai ka faɗa mashi ba”
“da gaske nake,i think Waseef ne ya sanar dashi”
“amma naji daɗi ya Waseef ya faranta man shima Allah ya faranta mashi”
“Ameen,yanzu shikenan beb mun kusa zama husband and wife”
“yeah very soon we became husband and wifeee” ta faɗa tana jan wife ɗin,dariya su ka yi gaba ɗayan su, faɗawa tayi saman bed ɗin ta
“gaskiya dole nayi ma ya Waseef kyauta yayi abunda ka kasa tsawan shekaru”
a shagwaɓe yace “beb Ni fa kyautar”
“taka special ce husband to be”
“beb,Ina so mu haɗu Please” ya faɗa yana wani shagwaɓe murya kamar ƙaramin yaro
“ka zo gida mana”
“No beby kunyar uncle nake ji,kina so yace daga faɗa mashi har na fara mashi Zarya a gida”
“kunya fa yaya,shi fa dady ba ruwanshi”
“ni dai bazan iya zuwa ba beb,kawai ki nema mana inda zamu haɗu”
“please Ni dai ka zo, ko a compound ne sai ka tsaya ba saika shigo ciki ba”
“ok let me see idan zan iya zuwa”
“zaka iya dear”
cike da farin ciki su ka cigaba da waya,daga yanayin yanda su ke wayar zaka tabbatar suna cikin farin ciki,hayaniyar da taji ne yasa tayi saurin ce mashi tana zuwa, rejecting call ɗin tayi,da sauri ta sauka daga saman bed ɗin ta nufi ƙofar fita zuwa parlor,anan ta samu dadynta da momynta suna saɓani saboda Auren su.
cikin parlorn ta ƙarasa,fashewa tayi da kuka “momy mi yasa za kice haka akan ya Irfan,gaskiya ki daina man wannan wasan”
“sai na mareki idan ba kiyi man shiru anan ba shashasha”turo baki Noor ɗin tayi hawaye na bin cheek ɗinta
“kowa na farin ciki sai ke ce zaki tsiro da haka,ni gaskiya ya Irfan nake so kuma shi zan Aura,haka kwai burinda na daɗe ina jira zaki wani ɓ...” bata ƙarasa ba saboda saukar marin da taji,da gudu ta nufi dadynta tana fashewa da kuka.
“shashashar banza wacce bata san inda ke mata ciwo ba,ai da duk a zatona kina da hankali ashe sakaryace ke ban sani ba”
“dady dan Allah karka bari ta rabani da ya Irfan” ta faɗa tana kuka
“yi shiru Noor,karki wani tashi hankalinki ni ne dai dadynki ba wani ba,babu wanda ya isa rabaki da Irfan sai Allah,Irfan shine zaɓi na” tsaki mom fatilah taja
“zaku sha mamakina daga kai har ita” tana faɗar haka ta nufi sama,hannu yasa ya shiga goge mata hawayen dake zuba.
“yi haƙuri kukan ya isa haka,where is my glasses?” bedroom ɗinta ta nufa da sauri, glass ɗin ta ɗauko mashi,amsa yayi yana ɗan shafa kanta
“karki damu kinji” gyaɗa mashi kai tayi,ficewa yayi daga parlorn ita kuma ta koma bedroom ɗinta ranta duk a jagule bata taɓa zaton haka daga momynta ba...
*Uhmmm mom fatilah yada haka*