← Book details Shiryayyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 2 OF 3

part ɗin mamy Fa'iza ta nufa sai da safe Yumnah da Nainarh su kayi mata suma suna nufar bedroom ɗin su.

Shiryayyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 136 min read

Toilet Nainarh ta shiga tayi brush haɗe da alwala,kusan kullum za tayi bacci sai tayi Alwala abun ya zame mata jiki.


tana fitowa Yumnah na shiga,wanka tayi haɗe da Alwala kafin tayi brush,lokacin data fito har Nainarh ta kwanta, dressing room ɗin ta ta nufa, pajamas ta zura a jikinta kafin ta dawo bedroom ɗin.


kashe light ɗin ɗakin tayi,kwanciya tayi tana jan duvet ta rufe jikinta.

“yau ba wayar kenan?” Nainarh ta faɗa
“tun ɗazu mu kayi waya sai gobe kuma”
“Allah ya nuna mana goben lafiya” da Ameen Yumnah ta amsa.


ɗan shiru su kayi kafin Nainarh ta juyo tana fuskantar Yumnah
“wai wacece Carol da naji mom na faɗin muna kama?”
“ƙanwar mom ce” Yumnah ta bata amsa,gyaɗa kai kawai Nainarh tayi tana juya mata baya...
_*Ep 17_18*_


*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘

______________________________


*Washe Gari*


A zaune suke saman sallaya da alama basu jima da kammala sallah ba,tashi Nainarh tayi,hijab ɗin dake jikinta ta cire ta linke ta nufi bed,kwanciya tayi tana ɗan jan blanket ta rufe rabin jikinta.


yumnah na daga zaune har gari ya ɗan fara haske,tashi tayi itama ta cire hijab ɗin dake jikinta, toilet ta shiga,bata fi five minutes ba ta fito, dressing room ɗinta ta nufa,kayan jikinta ta canza zuwa gwon mai hannun armless,low bun tayi ma kanta da ƙaramin ribbon,mayafi ta ɗauka ta yafa saman kanta sannan ta fice daga ɗakin ta koma bedroom ɗin, Nainarh na nan kwance kamar yanda ta barta.


wayarta dake ajiye saman nightstand ta ɗauka ƙofar fita ta nufa,tashi Nainarh tayi zaune “sister Yumnah sai ina haka da safe?” juyowa Yumnah tayi

“wai da ba bacci ki ke ba?”
“kwance kawai nake,baccin ne yaƙi zuwa”
“ok part ɗin dady zanje na ɗauko key,za ayi gyaran part ɗin shalelen dady ne,tunda kin tashi sai ki zo muje”


“A'a sai kin dawo”
“wannan ne kuma baki isa ba,ki tashi kawai mu tafi abunda yasa ban tasheki ba nayi tunanin bacci kike,ta so mu tafi gari na waye wa bana son mu makara zuwa gidan Abbah”

saukowa Nainarh tayi daga saman bed ɗin,hijab ɗinta ta ɗauka,ficewa su kayi daga ɗakin.


direct sama su ka nufa zuwa part ɗin dady,a Parlor su ka same shi zaune saman sofa da Qur'an a hannunshi yana karatu,ciki suka ƙarasa suna mashi sallama ɗagowa kawai yayi ya kalle su ba tare da ya katse karatun da yake ba, bedroom ɗin shi Yumnah ta nufa Nainarh kuma ta zauna kan ɗaya daga cikin sofas ɗin,shiru tayi tana sauraran yanda dady ke furta ko wane harafi cikin ilimi,sai da ya kai aya tukun ya kai dubanshi gareta.


fuskar shi ɗauke da murmushi yace “ɗiyata yau kece a part ɗin na” murmushi Nainarh tayi tana ɗan rissinar da kai tace
“ina kwana dady,an tashi lafiya”
“lafiya lau Alhmdllh,fatan kema kina tashi lafiya”
“lafiya lau” ta bashi amsa
“masha Allah, Yumnah ta hanaki bacci ko?”


murmushi tayi tana faɗin “A'a dady da kaina na tashi”
“ai nayi tunanin ita ta taso ki”
girgiza kai Nainarh tayi fuskarta ɗauke da murmushi,fitowa Yumnah tayi hannunta riƙe da key's,wurin su ta ƙaraso.


“dady ka tashi lafiya?” ta faɗa yayinda take ƙarasowa inda yake side hug tayi mashi, kissing forehead ɗinta yayi fuskarshi ɗauke da murmushi
“lafiya lau,fatan kema kina tashi lafiya?”


“lafiya lau dady, key's ɗin part ɗin Autan ka na ɗauko za'aje a gyara” murmushi dady yayi yana dungure mata kai
“zaki sani idan yaji ki ne” murmushi Yumnah tayi
“taya zai sani,shida yana can”
“ai zai dawo kuma zan faɗa mashi ne”


“Allah ya Amince,nima nayi kewarsa na ƙosa naga ya zo”
“in sha Allah,yana nan zuwa”
“Allah ya kawo shi lafiya” da Ameen dadyn ya amsa,tashi Yumnah tayi tana kallon Nainarh

“muje,dady sai mungama”
“yawwa Nainarh harda sabon part ɗin yau ku shiga ku gyara shi”
“dama yau ko bakace a gyara ba sai na shiga naga abun da ka zubama shalelen naka bayan wanda kayi mashi”

“zaki kuwa gani,amma fa karki ta kallo dayawa bana son a cinye mashi kyau tun mai shi bai gani ba”

“karka damu dady,amma fa idan yafi nawa kyau tam” ta faɗa tana jinjina mashi kai
murmushi dadyn ya saki yana faɗin“dan Allah kisa su gyara da kyau kin ji”
“in sha Allah”ta faɗa suna ficewa daga part ɗin.


staircase ɗin dake can ɗan gefe da part ɗin dady su ka nufa,hawa su kayi zuwa can floor ɗin ƙarshe.

“ina so su kammala gyarannan da wuri dan mu samu zuwa part ɗin Abbah a kan lokaci” Yumnah ta faɗa dai dai time ɗin da su ke kawo bakin wata ƴar madaidaiciyar ƙofa ta glass.


wasu madannai Yumnah ta danna a jikin ƙofar
“ina tajin ana faɗin Abbah da part ɗin shi,yayan dady ne?”
“granfa ɗin mu ne, mahaifin su dady,duk ranar Friday gaba ɗaya family ɗin mu a can muke wuni,tundaga safe har dare a can muke lunch da dinner”

jinjina kai Nainarh tayi a lokacin da ƙofar ke buɗewa, wani irin katafaren parlorn ne su ka shigo,launikan dake cikin parlorn Royal blue, light brown and white color ne, an ƙawatashi da manya manyan sofas set biyu na gani na faɗa masu matuƙar taushi da daɗin zama,sai throw pillows dake kan ko wace sofa, daga tsakiyar parlorn round glass table ne an jera flower vase masu matuƙar kyau, daga saman ceiling ɗin wasu irin crystal chandeliers ne masu girman gaske , sai faskekiyar flat creen tv mai matuƙar girma sai kayan sauti dake gefe da gefen tv, sparkling floor lamps ne ajiye a ƙasa suna bada haske mai launika daban daban, ga dogayen curtains zagaye da parlorn an zuge su,daga can bakin glass wall wanda daga nan kana iya hangen main entrance ɗin shigowa part ɗin daga compound ɗin gidan,armchairs ne guda biyu ajiye daga tsakiyar su ɗan madaidaicin glass table ne,idan ka kalli ƙasan parlorn zaka ɗauka mirror ne yanda yake ɗaukar ido dan kana iya kallon kanka tsab.


Daga cikin parlorn kana iya hangen katafaren dinning room, wanda aka ƙawatashi da haɗaɗen dinning table,ƙyataccen glass table ne mai mazaunin mutum shidda,wasu haɗaɗun chairs ne kewaye da table ɗin,daga saman ceilling ɗin dinning room ɗin ƙaton bulb ne ya haskaka ko ina na dinning room ɗin,ga wata irin zungureriyar floor lamp.


cikin parlorn su ka ƙarasa Yumnah na gaba yayinda Nainarh ke biye da ita tana ƙarema parlorn kallo,tayi mamakin wannan part ɗin wanene dan yafi ko wane part dake gidan haɗuwa da tsaruwa duk da ba ko ina na gidan ta sani ba,wayar landline dake ajiye cikin parlorn Yumnah ta nufa, number kitchen ta kira,daga can ɗaya ɓangaren a kayi picking call ɗin.


“na buɗe part ɗin ku nake jira” Yumnah ta faɗa tana rejecting ba tare da ta tsaya jin amsar da za'a bata ba,wata ƙofa Yumnah ta nufa ganin haka ne yasa Nainarh binta a baya,nan ma wani parlorn ne su ka shigo wanda yafi na farkon haɗuwa,komai na cikin shi blue White and gold color ne,glass door ne guda biyu a jere sai wasu corridor guda biyu dake hannu dama da hagu can ɗan nesa da ƙofafin,wanda na hannun hagu ya kasance gym room ne ɗayan kuma wani part ne mai zaman kanshi.


ɗaya daga cikin ƙofofin dake jere Yumnah ta nufa tun kafin ta ƙarasa ƙofar ta shiga zugewa da kanta,cikin ɗakin ta kunna kai Nainarh na biye da ita a baya,wani irin haɗaɗen bedroom ne su ka shigo komai na cikin shi black,white and gold color ne, bedroom ɗin yana ɗauke da Royal bed mai matuƙar ɗaukar hankali,bed ɗin a shimfiɗe yake da tausassan bedsheet ga ƙaton blanket mai gashi gashi a jikin shi,gefe da gefen gadon nightstand ne mai ɗauke da bedside lamp,daga gaban gadon Ottoman table ne color ɗaya da bed ɗin,ƙasan ɗakin shimfiɗe yake da rug carpet mai taushi,wani irin ƙayataccen dressing mirror ne a cikin ɗakin daga gaban shi stool ne mai taushin gaske.


cikin ɗakin su ka ƙarasa,dogayen curtains ɗin dake a sake Yumnah ta shiga zugewa,kafin ta nufi wata ƙofa wacce nake kyautata zaton dressing room ne mai haɗe da bathroom, buɗe ƙofar tayi,shiga ciki tayi ta bar Nainarh nan tsaye tana ƙarema bedroom ɗin kallo baƙaramin tafiya yayi da ita ba duk da babu wasu kaya a cikin shi.


fitowa Yumnah tayi “gyaran ma bazai ɗauki wani lokaci ba saboda babu datti da yawa” jinjina kai Nainarh tayi “eh gaskiya babu wani datti sosai”
“haka ne muje na duba sauran ɗakunan kafin su Ishrat ɗin su ƙaraso” da to Nainarh ta amsa mata,ficewa su kayi daga ɗakin,ƙofar dake kusa da wacce su ka fito su ka nufa itama ta glass ce kamar wacce su ka fito.


Nan ma wani bedroom ɗin ne su ka shigo kusan duk abun da ke cikin wacan a kwaishe a nan banbancin color ne kawai shi wannan red and white color ne saɓanin wacan,mamaki gaba ɗaya ya kashe Nainarh yanzu duk mutum ɗaya keda wanann part ɗin kuma ba zaune yake a ciki ba, zata so ganin wannan shalelen dady.


curtains ɗin shi kawai Yumnah ta zuge ta duba dressing room da toilet Kamar dai yanda tayi a wacan bedroom ɗin kafin su ka fice, corridor ɗin dake hannun damanƙofofin su ka nufa,ƙofofi ne guda biyu a wurin na glass daga in da su ke tsaye suna iya hangen komai dake ciki.


tura ƙofar su kayi su ka shiga ciki,wani irin azabebben parlorn ne su ka shigo wanda ya doke gaba ɗaya falukan dake part ɗin,yafi su komai nesa ba kusa furniture's ɗin dake ciki ma kwata kwata ba irin tsarin su ɗaya da waɗancan ba,komi na cikin parlorn white color ne da ratsin gold,daga cikin parlorn kana iya hangen bedroom da swimming pool ɗin dake part ɗin ta hanyar glass wall dake mamaye da part ɗin gaba ɗaya.


bedroom ɗin Yumnah ta nufa tana faɗin “gaskiya na fara kishi da shalelen dady” murmushin Nainarh ta saki tana biye da ita ba tare da tace mata ƙalla ba sai raba ido take a parlorn kamar ba'a niger ba,kusan suman tsaye Nainarh da Yumnah su kayi a yayin da su kayi arba da makeken bedroom ɗin da su ka shigo,riƙe ƙugu Yumnah tayi tana jinjina kai alamar mamaki tunda aka gina wannan sabon bata taɓa shigowa ba sai yau da dadyn yace su shiga a gyara,gaba ɗaya bedroom ɗin a mamaye yake da glass wall.


bedroom ɗin yana da girma sosai dan tsab za'a iya gidan parlorn, bedroom, kitchen da toilet wadatattu a cikin shi,
wani irin makeken king size bed ne daga can ɗan saman stape,a shimfiɗe yake da bedsheet mai taushi gaske da blanket kafi mage taushi,gefe da gefen shi nightstand ne,bed ɗin kusan rabi da kwatar shi a cike yake da pillows ƙasan bed ɗin na fitar da wani kalar haske,daga can gefen bed ɗin sofa ce mai masifar kyau color ɗaya da gadon itama ƙasanta na fitar da haske kalar na bed ɗin.


daga cikin ɗakin kana iya hangen haɗaɗen gym room dake can ɓangaren hagu na ɗakin,wasu irin expensive machines ne a cikin shi kamar a gym center,sai toilet da shima kana hangen komai dake cikin sa.


daga ɓangaren dama sliding door ne wacce idan aka buɗe ta ƴar baranda ce,cuddler chairs ne guda biyu ajiye a wurin daga tsakiyar su round glass table ne ajiye.


jinjina kai Yumnah ta shiga yi tsarin part ɗin ba ƙaramin tafiya yayi da ita ba,wayar dake hannunta ta dannan, video ta shiga ɗaukar part ɗin,tundaga parlor har zuwa wannan yar barandar,babu in da bata ɗauka ba har toilet tukun su ka fice daga part ɗin su ka koma parlorn na biyu da su ka shigo.


tsaf tsaf yake part ɗin saboda yawan gyarawa da ake duk da ba mai zama,ɗaya daga cikin sofas ɗin su ka nufa su ka zauna,daga cikin parlorn suna hange parlorn da su ka fara shigowa ta hanyar glass wall dake mamaye da parlorn.


basu jima da zama ba Ishrat ta shigo tare da wasu masu aiki su biyar haɗi da ita su shidda kenan hannunsu ɗauke da mop da tsintsiya da detergent,in da su Nainarh su ke suka ƙaraso,cikin girmamawa su ka gaishe da su,amsa masu su kayi Yumnah na faɗin “yawwa Ishrat sai kun mai da hankali,ki fara nuna masu in da za'a fara gyarawa,yau har sabon part ɗin dady yace a gyara”


gyaɗa mata kai Ishrat ɗin tayi,kasa masu aikin tayi gida biyu,biyu tace su gyara bedrooms da gym room,biyu kuma su gyara parlors ɗin da dinning room da kitchens,ita da ɗayar kuma su ka nufi part ɗin da su Yumnah su ka fito.


babu ɓata lokaci masu aikin su ka shiga gyaran ko ina a cikin gidan,main parlorn part ɗin Yumnah da Nainarh su ka nufa, sliding door dake wurin su ka buɗe suka fita ƴar barandar dake wajen,a saman chairs ɗin dake wurin su ka zauna,daga nan in da su ke suna hangen main entrance ɗin shigowa part ɗin da compound ɗin gidan,suna iya hangen katafaren parking space dake wajen,rides ne da yawa a ciki an lulluɓe su da alama an ajiye su ne kawai.


Kasa haƙuri Nainarh tayi har sai da ta tambayi Yumnah
“wai nan part ɗin waye?,naji kina faɗin shalelen dady dama ba ke bace Auta ba,dady na da wani ƙaramin ɗa bayan ke?”


kallon Nainarh da tayi maganar Yumnah tayi tana sakin dariya

“wai dan kinji ina faɗin shalelen dady?,dady baya da wani ƙaramin ɗa ko ƴa bayan ni,ni ce Autar sa”


“ok,amma nan part ɗin waye,mi yasa ki ke ce masa shalelen dady??”


“part ɗin ya SAM ne shi ne yaron dady na uku,daga ya Naeem sai ya Adnan sai ya SAM sai ya Irfan sai Aunty Fa'iza sai ya Fa'iz sai Yumnah Auta”


yumnah ta faɗa tana sakin murmushi, murmushi itama Nainarh tayi tana faɗin

“masha Allah,Allah ya Albarkace ku ya rayama dady ku” da Ameen Yumnah ta amsa tana faɗin

“tsawan shekara 18 kenan ya SAM baya ƙasar,tun ina ƴar shekara 2 da haihuwa ya koma US wajen granny da zama”


“ikon Allah,yanzu zuwa zaiyi ne yasa dady yace a gyara part ɗin?” girgiza mata kai Yumnah tayi


“babu wanda ya san ranar da zai zo,tunda ya tafi bai sake dawowa ba,kawai dai dady yana sa a gyara part ɗin ne duk ranar friday”


“sorry kar kice na cika shiga abun da ba ruwana,amma miyasa ya tafi tsawan wannan shekarun bai dawo ba??”


murmushi Yumnah ta saki “nima ban sani ba,kawai dai na taso naga baya gidan kuma bai taɓa zuwa ba”

jinjina kai kawai Nainarh tayi ba tare da ta sake cewa komai na,amma lamarin ya bata mamaki wane irin ɗa ne zaiyi nesa da iyayen shi tsawan waɗannan shekaru ba tare da ya waiwaye su ba,haka nan taji tana son sanin dalilin barin shi gida da rashin waiwayar iyayen shi tsawan wanann shekarun,wani ɓangare na zuciyarta na gargaɗarta da shiga abun da babu ruwanta, Yumnah ce ta katse mata tunanin da take ta hanyar faɗin


“next week fa muke komawa school,ni wallahi duk na ƙagara next week ɗin tayi dan na gaji da zaman gida”

yanayin fuskar Nainarh ne ya canza da alama ba tayi farin cikin da labarin komawar ta su makaranta ba

“ya dai,baki son komawa ne?” Yumnah ta faɗa tana tsareta da idanu, girgiza mata kai kawai Nainarh tayi ba tare da tace ƙala ba,itama Yumnah bata sake cemata komai ba dan ta san dalilinta naƙi son a koma,amma ya za tayi dole tayi haƙuri ta koma komi ƴan school ɗin su za su ce.


*ASO VILLA*


Gaba ɗaya a halin gidan sun hallara a katafaren dinning room dake villa ɗin domin breakfast, Zaabith na zaune saman chair dake kallon wacce su Ammar ke zaune,sai Irfan da Waseef dake zaune kusa da juna,sun duƙar da kai,magana su ke ƙasa ƙasa idan ba kana kusa da su sosai ba ba zaka iya jin mi su ke cewa ba.

kallo Zaabith dake cikin abinci hankali kwance hajiya salima tayi

“lafiya ka fito kai kaɗai,ina kainart ɗin take,ko har yanzu jikin ne??” da sauri ya ɗago yana kallon mahaifiyar tashi da tayi magana.


“zata fito,ta tsaya wani abun ne ciki” Zaabith ɗin ya faɗa yan maida kanshi ga abincin da yake ci,wani ɗan iskan kallo Ammar da Aman su ka watsa mashi ba tare da wani ya lura da su ba.

jinjina kai hajiya salima tayi tana kai dubanta ga sarah dake tsaye


“maza ki kira man ita sarah” da to sarah ta amsa tana juyawa tabar wajen zuwa part ɗin Zaabith.


bayan kamar minti biyar sarah ta dawo “lafiya, tana ina??” hajiya salima ta faɗa tana kallon bayan sarah ganinta ita kaɗai


“gata nan fitowa ranki ya daɗe”jinjina kai hajiya salima tayi


tunda ta tunkaro dinning room ɗin ya kafeta da ido,da yake chair ɗin da yake zaune tana fuskantar ƙofar shigowa dinning room ɗin,baƙar jallabiya ce a jikinta ta lulluɓa mayafinta ta rufe rabin fuskarta da har yanzu sawun hannunshi na nan raɗau kamar yanzu ne ya mareta.


wani irin kallo ya shiga jifanta dashi wanda ita kaɗai ta san ma'anar shi,saurin kauda kai tayi kamar bata ganshi ba, murmushi hajiya salima ta saki lokacin da kainart ɗin ta ƙaraso ciki.


da sauri Zaabith ɗin ya miƙe yana ja mata kujerar dake kusa da shi,alama yayi mata data zauna yana sakar mata wani soft smile,ɗauke kai tayi kamar bata ga abun da yake nufi ba ta nufi inda su Ammar suke,tashi Aman yayi ya koma kujerar dake kusa da wacce ya tashi,murmushi ta saki tana shafa kanshi,zama tayi a tsakiyar su.


“ina kwana momy,kin tashi lafiya”
“lafiya lau Alhmdllh, kainart ya ƙarin ƙarfin jikin” da Alhmdllh ta amsa mata,da sauri sarah ta ƙaraso in da kainart ɗin take tayi serving ɗinta.


har time Zaabith na tsaye mamaki ne duk ya cika shi,kallon shi momy tayi “kai kuma lafiya kayi ma mutane tsaye a ka??”

“bakomai” shine kawai abun da yace ya koma mazaunin shi ya zauna.


“ashe baki jin daɗi Aunty kainart?” waseef ya faɗa yana kai duban shi gareta
“naji sauƙi waseef”
“Allah ya ƙara sauƙi,amma shine baki ce na zo na dubaki ba” Irfan ya faɗa yana wani ya mutse fuska.


ɗan zaro ido tayi “irfan nace ka dubani,rufa man asiri in ka ganni lahira kaini a kayi” dariya Irfan ɗin ya saki kamar ba shi ba

“nafa manta tsoron Allura ki ke”
dariya waseef ya kwashe da ita har da su Ammar
“gaskiya Aunty ya kamata ki rage wannan tsoron,akwai fa su Ammar a gabanki,amma kiyita abu sai kace farar kura” a cewar waseef.


jifar shi tayi da spoon ɗin dake hannunta saurin duƙewa waseef yayi,hakan da yayi ba ƙaramin dariya ya ba su,zuba masu ido kawai Zaabith yayi yana kallon su.


gyaran murya su kaji daga bakin ƙofar shigowa dinning ɗin saurin kai duban su ga magidancin dake tsaye cikin shigar Jogging suit launin blue black,a tsarin hallita dogo ne,launin fatar jikinshi fara ce ba irin sosai ɗin nan ba,sumar kanshi da gemun shi farare ne tas da alama rina launinsu yayi ba dan ya kai shekarun da za su koma haka ba,kunnen shi a manne yake da ear phone haka kyakkyawar fuskar shi a manne take baƙin glass.

Uncle Ahmad kenan, mahaifin Zaabith,Aunty Nadiya da Waseef,daga dady sai shi,shine President ɗin Nigeria na wannan lokaci.


da gudu Ammar da Aman su ka nufe shi saurin zame glass ɗin dake fuskar shi yayi ya tura shi a aljihun wando shi,faɗawa jikin shi su kayi suna mashi oyoyo, murmushi ya saki yana shafa sumar kansu,hannun su ya kama su ka ƙarasa cikin dinning room ɗin

“granfa shine yau ka fita ba tare da mu ba?” a cewar Aman
“bacci ku ke ne time ɗin,amma gobe idan zan fita tare da ku zan fita”
“gobe ai muna gidan big daddy tare da shi zamu fita”
“au haka ne?”


eh su ka bashi amsa,jinjina kai grandfa ɗin yayi
“shikenan idan kun dawo sai mu fita tare” ihun murna su ka saki suna koma mazaunin su.


gaishe dashi su Zaabith su ka shiga yi yana amsa masu cikin kulawa,sarah dake tsaye ma gaishe dashi tayi yayin da take matsowa domin tayi serving ɗin shi,da katar da ita hajiya salima tayi ,da kanta ta shiga serving ɗin shi.


“good morning” ta furta dai dai kunnen shi,kashe mata ido ɗaya yayi yana sakar mata murmushi, mazaunin ta dake kusa da nashi ta koma ta zauna tana sakin murmushi.


kallon Zaabith dady yayi
“zaabith ka kuwa haɗu da Muhsin??”
“A'a dady,ya dai kirani jiya yace yau su ke sa ran isowar su Mubarak”
“kai yaushe za ka tafi can kenan?”
“ƙarfe ɗaya su ke sa ran isowa,sai na tafi after Isha” wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyar kainart jin yau zai koma

“good” kawai dadyn yace ba tare da ya sake cewa komai ba,kallon Zaabith momy tayi

“yau zaka koma ne?”
“A'a,sai next week” ya bata amsa, kainart ba hakan ta so ba ta so ace tafiya zaiyi ko ta samu ta huta da uƙubar shi.


Dady da Zaabith ɗin su ka fara tashi sai Irfan da Waseef,tashi kainart tayi itama ta fice aka bar momy da su Ammar.


*Big Daddy's house*


wajen awa biyu su ka ɓata wurin gyaran part ɗin, gyara su kayi mashi na musamman ko ina ka shiga sai tashin ƙamshi yake haɗe da sanyin AC.


“sannunku da ƙoƙari Ishrat,wannan idan dady ya gani dole ya baku tukwici” murmushi kawai Ishrat ɗin ta saki

“ai ina jin ku saki curtains ɗin kawai a kashe bulbs,tunda an kammal”
da to su ka amsa mata suna nufar bedrooms da falukan dan ciki umarninta,duk wani kayan wuta da su ka san sun kunna sai da su ka kashe shi hatta AC ba su bari a kunne ba,kayan da su kayi amfani da su suka kwashe,ficewa su kayi daga part ɗin bayan sun kammala.


ƙofofin bedrooms ɗin Yumnah ta rufe tukun suma su ka fice, direct part ɗin dady ta nufa Nainarh kuma ta nufi bedroom ɗin su,bata samu dady a part ɗin ba har ya fice,key's ɗin kawai ta ajiye ta fice.


A zaune ta samu Nainarh bakin bed,da kallon mamaki ta bita
“yanzu Nainarh maimakon ki shiga kiyi wanka sai ki zauna,ni ban san mi yasa ki ke haka ba komai sai nace kiyi sai kace wata ƙaramar yarinya?”


“ba haka bane,naga ke sauri ki ke saboda fitar da za kuyi ,shine na bari idan kin fito sai na shiga”

wani ɗan iskan kallo Yumnah ta watsa mata “mi ki ke nufi da fitar da za muyi,kina nufin ban da ke??”

“haɗuwa fa za kuyi da family ku ni miye nawa na zuwa”
“gaskiya Nainarh bana jin daɗin irin wanann abun,ni kawai ki tashi ki shiga wanka karma su mom su shirya su fara jiran mu”


“yumnah gaskiya ni bazan je ba,taro ne na familyn ku, taya za ayi naje”


“wallahi sai kin shirya mun tafi kin ma ji na rantse,kullum naita fama dake kamar wata yarinyar goye” Yumnah ta faɗa tana nufar dressing room ɗin ta.


tashi Nainarh tayi ta shiga wanka ta so Yumnah ta ƙyaleta dan bata san wane irin kallo family ɗin su za suyi mata ba ganin ta shigo cikin su,ba lallai suyi maraba da ita ba.


bata jima da shiga wanka ba Yumnah ta dawo bedroom ɗin jikinta ɗaure da towel,zama tayi gefen bed ɗin, Nainarh na fitowa ta tashi ta nufi toilet ɗin har ta kai bakin ƙofa ta tsaya “kayan da zamu sa na nan na fito mana da su”
gyaɗa mata kai Nainarh tayi

ƙofar bedroom ɗin ta buɗe ta shiga, dressing room Nainarh ta nufa, dressing mirror ta nufa,zama tayi saman stool, expensive body lotion ɗin dake jere saman dressing mirror ta ɗauka,shafama jikinta ta shiga yi, simple make up tayima fuskarta Masha Allah tayi kyau abunta.


tashi tayi ta nufi kayan da Yumnah ta ɗauko masu, expensive egyptian abayas ne Black color anyi masu ado da royal blue ɗin yadi a hannun,sunji adon stones a jikin su sai sheƙi suke.


ɗaya daga cikin rigunan ta ɗauka ta zura a jikinta ba ƙaramin kyau tayi ba kamar wata balarabiya,kallon kanta tayi a gaban mirror ita kanta ta yaba da kyawun rigar a jikinta,baby ribbon ta ɗauka ta ɗaure gashin kanta,mayafin rigar ta ɗauka tayi rolling, masha Allah kawai zamu ce Nainarh Allah yayi mata wani irin sanyi kyau,ba ƙaramin haska farar fatar ta rigar tayi ba,shagala tayi da kallon kanta a mirror.


“wayyo Allah na sister Nainarh ke ce haka?,kai masha Allah kinga yanda rigar nan tayi maki kyau kuwa?, wallahi kamar mutum ya saceki ya gudu,karfa ki rikita mana samarin family a kasa gane kan su”

dariya Nainarh ta fashe da ita jin irin sambatun da Yumnah ke mata,sosai Yumnah ta shiga zuzuta kyan da Nainarh tayi,ita kuwa ban da dariya babu abun da take.


“bari nayi sauri na shirya ko na samu nayi maki pics kar wannan wankan ya tafi haka nan” ta faɗa tana nufar dressing mirror.


shaf shaf tashiga shiryawa,itama simple makeup tayima fuskarta,rigarta ta ɗauka ta zura Nainarh na daga tsaye sai Binta da ido take harta kammala shiryawa,itama ba ƙaramin kyau tayi ba abunka ga farar fata sai rigar ta sake fito da haskenta.


jinjina kai Nainarh tayi tana faɗin
“masha Allah kema ba ƙaramin kyau ki ka yi ba”
“ban kai ki ba” Yumnah ta faɗa tana ɗaukar wayarta, hand bag ta ɗauko masu mai shegen kyau tare da sunglasses mai ɗaukar ido.

bedroom su ka nufa Nainarh ta ɗauki wayarta dake saman nightstand ajiye,ficewa su kayi daga ɗakin zuwa parlor,anan su ka ɓaje kolin ɗaukar photo, photo Yumnah ta shiga ɗaukar Nainarh ba ƙaƙƙautawa,bayan nan ta kira Ishrat tayi masu a tare.


A tare su ka shigo parlorn,a bakin ƙofar su kaci burki cikin shigar shadda gezna fara ƙal sai ɗaukar ido take,kan su a sanye yake da hula, kwantacciyar sumar kan su sai sheƙi take.


fuskar shi a tsuke take kamar ko da yaushe saɓanin ta ɗan uwan shi dake ɗauke da murmushi yana kallon Nainarh da Yumnah da su ka juya ma ƙofa baya, kallo ɗaya yayi masu ya ɗauke kai yana kai dubanshi ga Ishrat dake ɗaukar su photo,wani ɗan iskan kallo ya watsa mata wanda yayi sanadiyar hautsinawar ƴan hanjin cikinta.


saurin sauke wayar tayi ƙasa har tana sake ɗaukar su wani pic ɗin ba tare da saninta ba,da mamaki Yumnah ke kallonta “Ishrat wai lafiya ki ka tsaya sauri muke,ƙara mana ɗaya kafin mom ta fito” Yumnah ta faɗa tana kallonta

cikin rawar murya Ishrat ta furta
“barkan ku da zuwa ,ina wuni” ta furta


da sauri Yumnah takai dubanta ga...
_*Ep 19_20*_


*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘

______________________________


da sauri Yumnah takai dubanta ga Irfan da Waseef dake tsaye a bayan su, murmushi ta saki
“laa ya Irfan ya waseef ku ne?” yumnah ta faɗa cikin nuna jin daɗin ganin su, wani irin faɗuwa gaban nainarh yayi jin sunan da yumnah ta ambata, idan bata manta ba shine mutumin daya shigo ɗakin su ya sameta daga ita sai towel.


wani irin takaici da kunya ne su ke rufeta ji tayi ina ma ƙasa zata tsage ta shiga,ko ƙwaƙwaran motsi kasawa tayi.


da sauri yumnah ta nufe su
“kun zo a dai dai, Ishrat yi mana photo” nainarh ta faɗa tana shiga tsakiyar su, saurin kallon Irfan da yayi kicin kicin da fuska Ishrat tayi,kasa ɗaukar photon tayi saboda hararar daya watsa mata, ƙofar parlorn mom ya nufa ba tare da ya tsaya photon ba, da kallo kawai yumnah da Waseef su ka bishi, Nainarh kuwa tsananta faɗuwa gabanta yayi lokacin da taga giftawarshi ta idonta.


taɓe baki yumnah tayi tana kallon Waseef “ya Waseef wai mike damun ya Irfan ne?”
“ban sani ba yumnah, kin san halinshi sometimes ba iya mashi ake ba”
“Allah ya kyauta,Ishrat yi mana kinji” yumnah ta faɗa, saurin dakatar da Ishrat ɗin waseef yayi yana nuna Nainarh data juya masu baya.


“wacece wannan ita bazata zo muyi photon ba”
“laa sister Nainarh zo muyi photo tare da ya Waseef” yumnah ta faɗa tana nufar Nainarh ta kamo hannunta zuwa in da Waseef ɗin yake tsaye.


“sannu pretty, muyi photo ko?” Waseef ya faɗa yana sakar mata murmushi, murmushi itama ta sakar mashi tana gaishe da shi, cikin kulawa ya amsa mata, tsakiyar su ya shiga, photon Ishrat ta shiga ɗaukar su a nan Fa'iza ta same su itama ta ɗau wankan Abaya simple makeup ne a fuskarta ba ƙaramin kyau tayi ba.


shiga itama tayi a kayi photon da ita,photona sosai su ka ɗauka Waseef sai da yasa Yumnah tayi masu su biyu shida Nainarh,Fa'iza ma sai da a kayi mata da Nainarh, sai da su kayi mai isar su tukun su ka bari a nan parlor su ka zauna suna kallon photunan.


mom ce ta fito Irfan na biye da ita, ta ɗau wankan Arabiyan Embellished open Abaya launin Royal blue tayi rolling da Veil ,babu makeup a fuskarta amma ba ƙaramin kyau tayi ba, cikin parlorn ta ƙaraso Irfan na riƙe da hand bag ɗinta.


“mom kinyi kyau sosai, dan Allah muyi photo dake kema” yumnah ta faɗa tana nufo mom ɗin
“lokaci ya ƙure Yumnah,na san mu kaɗai ne bamu je ba, ki bari sai wani lokaci” ɓata fuska yumnah tayi ba haka ta so ba.


ficewa su kayi daga parlorn gaba ɗayan su Ishrat na masu a dawo lafiya, parking space su ka nufa, motar Irfan mom da Waseef suka shiga yayin da Yumnah da Nainarh su ka shiga motar Fa'iza,key su kayi ma motocin su ka fice daga gidan zuwa gidan Abbah dake cikin Estate ɗin.


Tafiya su ka yi mai ɗan nisa kafin su ka iso gidan Abbah, katafaren luxury Villa ne na gani na faɗa,yaji kayan alatu kamar baza'a mutu ba,a katafaren parking space ɗin gidan su kayi parking Wanda yake cike da expensive rides masu matuƙar kyau.


fitowa su ka shiga yi ɗaya bayan ɗaya,a tare su ka nufi entrance ɗin shiga gidan mom da su Irfan na gaba yayin da Yumnah da su Nainarh ke bayan su, yanzu ma hand bag ɗin mom ce a hannun Irfan, bakin su ɗauke da sallama suka shiga katafaren parlorn gidan wanda aka ƙawatashi da manya manyan sofas masu matuƙar kyau da tsada.


matasan ƴan mata ne zaune saman sofa kowacen su ta ɗauka wanda Egyptian Abaya ɗaya tayi rolling da veil ɗin yayinda ɗaya kanta yake a buɗe,zallar gashin kanta ne kawai, gaba ɗaya wayoyinsu ne a hannunsu sun tasa gaba sai aikin latsawa su ke.


Kairiyyah da Noor kenan, Kairiyyah ta kasance ɗiya ga Aunty Adama Noor kuma ɗaya ce ga Uncle mutallaf.

sake ƙwaɗa sallama Yumnah tayi yayin da Irfan da Waseef su ka nufi glass elevator dake cikin parlorn.


saurin ɗago kai su kayi,riƙe ƙugu Yumnah tayi tana jijjiga jiki haɗi da kauda kai gefe,da sauri ƴan matan su ka nufo mom.


hugging ɗin ta su kayi cikin girmamawa wacce tayi rolling veil ta gaishe da mom, da fara'a mom ta amsa mata.

“lafiya lau Kairiyyah,ya school?”
“lafiya lau Alhmdllh mom”mom ta faɗa
“momy ina wuni” ɗayar ta gaishe da mom ɗin
“lafiya lau Alhmdllh,Noor zuwan yaushe?”


“jiya cikin dare mu ka zo”
“masha Allah harda dadyn ku kuka zo ne?”
Eh taba mom ɗin amsa, elevator mom ta nufa tana faɗin “bari na shiga wajen Abbah” da to su amsa mata, hugging ɗin Fa'iza su kayi cikin kulawa su ka gaishe da ita,kishi duk yabi ya cika Yumnah ganin sun ƙi kulata,kama hannun Nainarh tayi.


“mu tafi kinji sister”
da sauri Noor tabi bayan su, hugging ɗin Yumnah tayi ta baya “haba sister ba dai fushi ki ka yi damu ba?” fisgewa Yumnah tayi
“ni ki ƙyale ni”
“bazan ƙyale ki ba,sai kinyi haƙuri” murmushi Fa'iza tayi tana nufar su ita da Kairiyyah, Nainarh bin su kawai take da ido.


“sister sannu” Kairiyya ta faɗa tana kallon Nainarh, murmushi Nainarh ta sakar mata tana amsa mata sannu da tayi mata.


lallashin Yumnah Noor ta shiga yi da ƙyar su ka samu ta saki fuska,part ɗin Abbah su ka nufa gaba ɗayan su.


*MOM*💫


a second floor elevator ta sauketa, corridor da zai sadata da part ɗin Abbah ta nufa,tunda ta tunkaro ƙofar shiga part ɗin take jin muryoyin su suna fira cikin nishaɗin, a bakin ƙofar shiga ta tsaya,a hankali ta tura ƙofar ta shiga.


Masha Allah katafaren parlorn ne da yaji kayan more rayuwa, manya manyan sofas ne set uku masu matuƙar kyau da tsada ga taushi kamar audiga,haɗaɗiyar rug carpet ce shinfiɗe a ƙasa, kyakkyawan Dattijo ne mai cikar kamala cikin shigar farar Alkyabba a kishingiɗe saman rug carpet yayi matashi da tumtum yayin da ƴaƴan shi ke kewaye dashi sun saka shi tsakkiya,fira suke cike da nishaɗin.


su goma ne ƴaƴan Abbah dady shine babba daga shi sai uncle Ahmad daga su sai uncle Mustafa da uncle Ubaid daga su sai uncle mutallaf daga shi ne sai barrister Hashim da Aunty mariya daga su sai Aunty Safeenah da uncle Khamis daga su sai Aunty Adama ita ce Autar Abbah.


gaba ɗayan su ne a parlorn uncle Khamis ne kawai babu shima baya ƙasar ne tsawan shekara 19 kenan rabon shi da ƙasar,shi ka ɗai ne a cikin su baya da Aure.


Dady na daga hannun daman shi yayin da dady Ahmad ( mr president ) ke kusa da shi sai
Uncle Mustafa, Uncle ubaid da uncle Hashim, ɓangaren hagu kuma Aunty mariya,Aunty safeenah da Aunty Adama ne sai uncle mutallaf dake tsakiyar su,Irfan da Waseef na daga saitin kan Abbah zaune,gaba ɗaya hankali su na kan Abbah dake basu labarin yarintar su dady cike da nishaɗi.


sallamar mom ce ta katse masu firar da suke,gaba ɗayan su suka kai duban su gareta, murmushi ne ya bayyana akan fuskar Abbah da alama yaji daɗin zuwanta,kaf cikin surikan sa babu wacce yafi so sama da mom,tamkar ɗiya haka ya ɗauketa,idan ka cire barrister Hashim da Aunty Safeenah babu wanda baiyi farin ciki da zuwanta ba,da sauri Aunty Adama ta tashi fuskatar ɗauke da murmushi ta nufo mom.


hugging ɗin juna su kayi hakan ba ƙaramin ɓata ran Aunty Safeenah yayi ba,kauda kai tayi gefe tana jan tsaki, cike da kewar juna suka gaishe da juna,cikin parlorn su ka ƙarasa,wurin Abbah mom ta nufa fuskarta ɗauke da murmushi.


zama tayi kusa dashi “in wuni Abbah,mun sameku lafiya?”
“lafiya lau Alhmdllh,ya gidan ya kuma aiki”
“lafiya lau” Masha Allah Abbah ya furta,duban ta ta kai ga dady Ahmad cike da girmamawa ta gaishe da shi,cikin kulawa ya amsa mata yana tambayar Yumnah.


ɗaya bayan ɗayan tabisu tana gaishe da su,cike da kulawa su ke amasa mata in ka cire barrister da Aunty Safeenah da su kayi kamar ba su san da su take ba,hakan kwata kwata bai dameta ba dan idan da sabo ta saba da halin su,dady baiji daɗin hakan ba ya rasa miye matsalar ƴan uwanshi da matar shi.


“Ashe abun da ya faru da Asma'u kenan?, ubangiji Allah yayi mata mafita,Allah ya kuɓutar da ita,su kuma wanda su ka da baibaye ta da sharrin Allah yayi gaggawar tona masu Asiri” Abbah ya faɗa

da Ameen ya Allah Abbah su ka amsa banda uncle Hashim da yayi tsit kamar baya parlorn


“Allah ya kuɓutar da ita ya kyauta gaba” a cewar uncle Ahmad da Ameen su ka amsa suma,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga yi mata jaje in ka cire Aunty Safeenah data miƙe ta nufi ƙofar fita, barrister Hashim kuwa lumshe idonshi yayi kamar mai bacci .


“saffenah!!” Abbah ya kira sunanta,dakatawa tayi da tafiya ta juyo tana fuskantar shi

“ina zaki kowa na nan?”
“zan shiga wajen mama ne,naga an gama firar zumunci tunda har bare sun fara zuwa shiy...”

bata ƙarasa ba sakamakon tsawar da dady ya daka mata
“Abbahn ki ke faɗama haka?,maza ki dawo ki zauna kafin ranki ya ɓaci” murmushi kawai mom tayi bata so dady yasa baki ba.

rai a ɓace ta nufi wajen zamanta zata zauna
“jeki kawai” Abban ya faɗa,babu ko kunya ta juya ta fice,kauda kai kawai dady yayi da alama baiji daɗi ba,kallonshi Abbah yayi yana sakin murmushi haɗi da girgiza kai.

A bakin ƙofa Aunty Safeenah taci karo da su Yumnah, fuskar su ɗauke da murmushi su ka gaishe ta,ta amsa ma kowa amma banda Yumnah da Nainarh da tabi da wani irin kallo mai wuyar fassarawa.


hankali Nainarh ba ƙaramin tashi yayi ba da irin kallon da Aunty Safeenah tayi mata,duk sai taji wani iri dama ba tayi niyyar zuwa ba Yumnah ta jawota tasan dama ba dole bane dangin Yumnah su sota ba.


ganin yanayin data shiga ne yasa Fa'iza kamo hannunta cikin nata,da murmushi akan fuskarta tace “muje ko”
tura ƙofar parlorn tayi su ka shiga bakin su ɗauke da sallama,gaba ɗaya parlorn su ka kai duban su gare su.


Amsa masu sallamar su kayi in ka cire uncle mutallaf daya kafe Nainarh da ido ko ƙyaftawa baya yi uncle Ahmad ma kallon sani yake mata,har suka ƙaraso cikin parlorn uncle mutallaf bai janye idanunshi daga kanta ba har sai da Abbah yayi mashi gyaran murya tukun yayi sauri kauda idoshi daga kanta ya kalli Abban,hararar wasa Abbah ya watsa mashi.


saurin duƙar da kai yayi duk sai yaji kunyar kamashin da Abbah yayi yana kallonta yasan Abbah zaiyi tunanin wani abu shi kuwa har ga Allah kama tayi mashi da wacce ya sani.


zama su kayi kan rug carpet ɗin cikin kulawa su ka gaishe da su suna amsa masu,nuna Nainarh Abbah yayi da hannu
“in ku ka samu wannan mai kama da mariyata?” gaba ɗayan su suka kai duban su ga Nainarh sai da Abbah ya faɗa su kaga kamaninta da Aunty mariya in ka cire mom da dady dan su sunfi ganin kamaninta da Carol ƙanwar mom,sai yanzu uncle mutallaf ya fahimci da wacce take mashi kama.


kallo ɗaya Irfan da barrister suka yi mata suka kauda kai
“ƴan mata yaya sunan ki?” Aunty mariya ta faɗa tana kallon Nainarh
“NAINARH” ta bata amsa,jinjina kai Aunty mariya tayi “masha Allah, Nainarh suna mai daɗi” Aunty mariya ta faɗa, murmushi Nainarh ta saki a hankali ta furta “nagode”


juyawa Aunty mariya tayi ta kalli mom,fahimtar abunda Aunty mariya ke nufi ne yasa mom faɗin “ɗiyar Asma'u ce”

“Allah sarki” Abbah ya faɗa cike da jin tausayin Nainarh,babu wanda baiji tausayinta ba jin itace ɗiyar Hajiya Asma'u, barrister Hashim kuwa ko a jikinshi.


“sannu kinji Nainarh Allah ya kuɓutar da mahaifiyar ki” a cewar Abbah ,gaba ɗaya parlorn su ka amsa da “Ameen ya Allah” fira suka shiga yi cikin kwanciyar hankali.


Noor tunda su ka shigo Irfan ke Binta da wani irin narkaken kallo,itama tunda ta zauna hankalin ta na kanshi,wasu alamomi yake mata da ido wanda daga ita sai shi su ka san ma'anar su,sosai su ka shagala da kallon juna ƙarshe da su ka gaji tashi Irfan ɗin yayi ya nufi ƙofar fita shida Waseef ,zambur ta miƙe tabi bayan su babu wanda ya lura da ita sai Yumnah da Kairiyyah dake kusa da ita.

A parlor Waseef ya tsaya Irfan kuma ya nufi back yard,wassef na zaune sai ga Noor,nufoshi tayi cikin takun sauri “ya Waseef yana ina?”


“back yard” ya bata amsa,da sauri ta nufi ƙofar da zata sadata da back yard ɗin gidan, gyara zaman shi yayi kan sofa yana ciro wayar shi daga Aljihu.


tun daga nesa ta hango shi ya jingina da wall gaba ɗaya hannuwanshi na cikin Aljihun wandon shaddarshi, idanunshi a lumshe suke kamar mai bacci,a hanzarce ta ƙarasa in da yake tun kafin tayi magana ƙamshin turarenta ya sanar da shi isowar ta,a hankali ya buɗe idanunshi a kanta.


wani irin kallo ya shiga binta da shi yayin da ita kuma ta marairaice mashi fuska kamar zata sa mashi kuka.


“shine daka shigo kayi kamar baka ganni ba ko?” ta faɗa a shagwaɓe,buɗe mata hannuwanshi yayi alamar ta zo gare shi, ba tayi musu ba ta nufe shi,faɗawa tayi jikin shi, hugging ɗin juna su kayi tightly kamar za su koma abu ɗaya.


matso da baƙin shi yayi saitin kunnenta,magana ya fara yi mata kamar mai raɗa
“duk laifinki ne miyasa kin san tare za ku zo da dady baki faɗa man ba,kin san yanda nayi kewarki kuwa?”

“ina so nayi surprising ɗin ka ne shiyyasa”ta faɗa a shagwaɓe
“kinyi missing ɗin na?”
“sosai ma,har gani nake kamar bama sauri da muna tafiya”

“amma shine baki nemi ni ba ki ka zo part ɗin Abbah?”
“saboda na san anan zan same ka”
“da ban zo ba fa?”
“nama san bazaka ƙi zuwa ba”


raba jikin su yayi yana jan hannunta su ka nufi wasu haɗaɗun chairs dake back yard ɗin,zama yayi saman ɗaya daga cikin kujerun yana nuna mata ta kusa da shi,maƙe mashi kafaɗa tayi alamar bazata zauna ba,hannunshi ya miƙa mata babu musu ta kama jawota yayi zuwa jikinshi yayi mata mazauni akan laps ɗin shi, murmushi ta saki tana lafewa a jikin shi.


shafa doguwar sumar kanta dake a buɗe ya shigayi yayin da ita kuma tayi lamo har wani lumshe ido take.


*😳 Irfan⁉️*


idan mu ka koma parlorn Abbah,sun jima suna fira sai da lokacin zuwa masallaci yayi tukun su ka tashi,ficewa mom tayi tare da su Aunty Mariya da su Yumnah, wani ɗan corridor dake kallon parlorn Abbah su ka nufa.


wani irin hamshaƙin parlorn ne su ka shigo,yaji kayan alatu kamar a gidan sarakai,ga wasu jigunannun sofas masu rai da lafiya har set biyu.


Aunty Safeenah ce zaune saman sofa mai mazaunin mutum uku yayin da mamy ke hakimce kusa da ita ta ɗau wankan less ɗinkin riga da zani kamar ko wane lokaci zaka samu fuskarta da makeup,sofa dake kusa da su Hajiya fatilah ce matar uncle mutallaf tare da Hajiya Halima matar Uncle Ubaid sun ɗau wankan tsadadden less mai shegen kyau,fuskarnan ta su tasha makeup hannuwan su a cike su ka da ƴan hannu da zobba na zallar zinari.


Mama Ameena ce hakimce saman sofa mai mazaunin mutum biyu dake kallon ƙofar shigowa parlorn,super atamface a jikinta anyi mata ɗinkin riga da zani kalar na su na tsaffi,ta dafka uban ɗaurin ɗankwalinta kamar koda yaushe.


cikin parlorn su mom su ka nufo bakin su ɗauke da sallama,tsuke fuska mama tayi lokacin da idanunta su ka sauka kan mom,taɓe baki mamy tayi tana kauda kai.


Amsa masu sallamar su kayi in ka cire mamy dake cin ɗaci sai wani buɗar hanci take,
har gaban sofar da mama take zaune mom ta ƙara so,cikin girmamawa ta gaishe da ita,cike da izza tana wani yamutse fuska ta amsa mata a taƙaice,lamarin yaba Nainarh mamaki ita da abun ya zama sabo a idonta amma duk wanda ke parlorn yasan cewa babu jituwa tsakanin mama Ameenah da mom kwata kwata bata sonta.


Mama Ameenah matace ga Abbah,ita ta haifi Aunty Adama,ita ka ɗai ta rage a matan Abbah,kwata kwata bata ƙaunar mom.


“mun same ku lafiya?”
“ga zahiri kuwa kin gani” mama Ameenah ta faɗa tana nuna kanta da hannu, murmushi ne ya bayyana akan fuskar mamy da su Hajiya fatilah da alama abun yayi masu daɗi.

shiru mom tayi ba ta sake cewa komai ba,gaishe da mama su Yumnah su kayi, a taƙaice ta amsa masu tana sauke idonta kan Nainarh da duk tasha jinin jikinta.

“ita kuma wannan ina aka sameta?” mama Ameenah ta faɗa tana nuna Nainarh da hannu,faɗuwa gaban Nainarh yayi,gaba ɗaya parlorn duban su suka kai ga Nainarh.


“ɗiyar Aminiyata ce Hajiya Asma'u” mom ta faɗa,jinjina kai mama tayi
“ziyara ta zo maki ko mi?”
“A'a wani iftila'i ne ya faɗama mahaifiyar ta,to shine na daw...” bata ƙarasa ba mama tayi saurin dakatar da ita
“to sai aka yi yaya,zama mi take cikin zuri'ata,ita mahaifiyar ta ta bata da dangi ne da bazaki barta a hannunsu ba,?”


“ba haka bane mama,zaman...”
“dan Allah dakata mana Zulaihart, wai sau nawa zance karki sake kirana da mama,banda jaza masifa ina ni ina haihuwar dangin sheɗan wanda Allah ya tsinemawa,ko nayi maki kama wannan tsohuwar banzar mai yawo ƙwauri waje??”

ƴar dariya mamy tayi tana kallon su Hajiya gaje
“Allah ya huci zuciyarki” mom ta faɗa tana tashi, ta nufi ƙofar fita daga parlorn, Yumnah idanunta har sun cika da hawaye bakomai yasa bata son zuwa part ɗin Abbah ba idan ba ranar Friday ba sai dan saboda wannan cin mutuncin da mama kema mom,tashi tayi tana kama hannun Nainarh da duk jikinta yayi sanyi.


Fa'iza ma ranta ba ƙaramin ɓaci yayi ba,tashi itama tayi ta bi bayan su da kallon mamaki mamy tabita har ta fice daga parlorn.

rai a ɓace Aunty Adama ta kalli mama Ameenah
“gaskiya wannan abun mama da ki ke a gaban ƴaƴa da jikokin ki bai dace ba,haba dan Allah da shekarunki zaki zauna yara na zugaki kina abu irin haka”


“kamarya yara na zugata, mi kike nufi Adama?”mamy ta faɗa rai a ɓace
“da mahaifiyata nake magana ba dake ba,karki ƙara sa man baki,kuma duk abunda take akwai mai zugata sama da ku ne?”


tsantsar mamaki ne ya bayyana a kana fuskar mamy wai yau ita Adama ke faɗama haka “lallai Adama Ni kike faɗa ma haka saboda Zulaihart?”


“fiye da haka ma sai ta faɗa maki mabaruka,gaba ɗaya ku babu mai hankalin data san abun da ya kamata,mama shekarunta sun ja tunaninta baya yake komawa,maimakon ku zama masu bata shawara idan kunga za tayi abun da ba dai dai ba amma saboda son zuciya kullum cikin birkita mata tunani kuke,babu wanda yafi bani haushi a cikin kuka sama da ke Safeenah” Aunty Mariya ta faɗa rai a ɓace tana kallon Aunty Safeenah


“ni mi nayi Aunty mariya,babu ruwana fa a cikin wannan abun?”
“dama zaki ce haka mana,akwai wanda ya ɗaure masu gindin yin abunda su ka ga dama sama dake,kina ƙanwar mazajensu ko kunya bakiji”


“da Allah ya isa haka mariya,ni ya kamata Ku rufe da faɗa ba su ba,kune za ace ma ko kunya ba kuji,kun fifita bare sama da ƴan uwanku musulmai,ko da yake ke barewa ai baza tayi gudu ɗanta yayi rarrafe ba”


“ko mi zaki ce mama a shekarunki wanan abun da ki ke bai dace ba” Aunty Mariya ta faɗa tana nufar wata ƙofa,da harara mamy ta bita har ta shige ɗakin,tsaki Aunty Adama taja tana bin bayan su mom.


“aikin banza dana wofi, kullum da an taɓa wannan dangin sheɗan ɗin sai su rufe mutane da faɗa kamar wasu ƴaƴan cikin su” Hajiya Gaje ta faɗa tana sake jan wani tsaki
“gaba ɗaya zanyi maganin su ne daga su har ita” a cewar mama Ameenah


“wallahi mama karki bari yarinyar nan ta zauna,ta maidata can dangin uwarta,haka kawai zata jajubo ma mutane gayyar tsiya inji ba uwarta bace ta kashe mahaifinta ba” Aunty Safeenah ta faɗa sai wani huci take.

“rabu da ita ai Tahir ɗin zai zo ya same ni,zanji idan shi ya bata damar ajiye wanann annobar a gidan shi”


mamy ranta fes kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,dama ta san muddin mama Ameenah taga Nainarh sai tasa an koreta daga Estate ɗin gaba ɗaya.


first floor mom ta koma, bedrooms ɗin dake floor ɗin ta nufa, toilet ta shiga yayin da Yumnah da Nainarh su ka zauna saman arm chairs ɗin dake bedroom ɗin, Nainarh hankalinta duk a tashe yake da abunda ya faru a part ɗin mama Ameenah,tunaninta yanzu wace irin rayuwa za tayi idan ta koma hannun dangin mahaifinta,kwata kwata basa sonta musamman yanzu da suke zargin mahaifiyarta da kashe mahaifinta,bare ace dangin mahaifiyar ta da ba nan suke ba,yanzu ita ya za tayi kenan...⁉️ _*Ep 21_22*_


*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘


______________________________


sosai tayi nisa a duniyar tunani har mom ta fito daga toilet  yumnah ta shiga bata sani ba,prayer mat Fa'iza ta  shimfiɗa ma mom ɗin, wurin da Nainarh take ta nufo.


dafa kafaɗarta Fa'iza tayi, saurin kallon fa'izar tayi,murmushi Fa'iza ta sakar mata “ ina ta magana kinyi nisa a tunani baki ji,karki damu da maganar mama Ameenah babu in da za kije kina nan a tare da mu, ki kwantar da hankalin ki kinji”


murmushi kawai Nainarh ta sakar mata ba tare da tace komai ba, turo ƙofar ɗakin Aunty Adama tayi ta shigo,duban su suka kai gareta, cikin ɗakin ta ƙaraso, zama tayi kan chair ɗin da yumnah ta tashi tana fuskantar Nainarh, fuskarta ɗauke da murmushi tace


“kiyi haƙuri da halin kakar taku wasa take babu in da za kije,  kina nan tare da mu har Allah ya kubutar da mahaifiyarki kinji”
murmushi Nainarh ta sakar mata
“nagode sosai Aunty, Allah ya bar zumunci”
“kar ki damu,ai yanzu munzama ɗaya,  zansa yumnah ma ta kawoki gida ki zo man ziyara, ai zaki zo ko”
“Eh in sha Allah, nagode sosai Aunty”


“shikenan, tashi ki shiga toilet ki ɗauro Alwala ki zo kiyi sallah” da to ta amsa mata, tashi tayi ta nufi toilet ɗin, kusa da Yumnah ta zo ta kabbar sallah, bayan fitowar Nainarh Fa'iza ta shiga,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga gabatar da sallar zuhur, bayan da su ka kammala ne su Yumnah su ka fice aka bar mom da Aunty Adama a ɗakin.


main parlorn su ka nufa,a zaune su ka samu kairiyyah da Noor,ƙarasawa su kayi cikin parlorn, kusa da kairiyya yumnah da Nainarh su ka zauna.


suna a nan zaune parlorn Aunty Nafeesa da Aunty Nadiya su ka shigo,sun ɗau wanka Abaya maroon color yayinda Enaaya da Aneesarh su kayi ankon Pakistan dress riga da wando white color ,rigar da wandon sun sha adon sparkling stones,sunyi rolling Veil ɗin kayan a kan su,simple makeup ne a fuskarsu,  kamar ko da yaushe eyes ɗinsu manne suke da sunglasses mai shegen kyau.


basu jima da shigowa ba Laatifa da Balqis su ka shigo tare da mom maryam da mom maimunatu,  suma ankon Abaya su kayi yayinda mom maryam da mom maimunatu suka ɗau wankan tsadadden Swiss less naji da faɗa.


mom maimunatu ta so su shiga part ɗin mama Ameenah Amma mom maryam tace babu inda za ta sai dai mom maimunatu taje ita ka ɗai,duk yanda mom maimunatu ta so su shiga su gaishe da mamah ƙin zuwa mom maryam tayi sai ma tashi da tayi ta nufi bedroom ɗin da su mom su kayi sallah, itama sallah tayi.


*Queen Kainart💫*


A jere danƙara danƙaran motocinsu su ka shigo cikin estate ɗin yayinda motocin securitys Armys ɗin su suka sako su a tsakiya,katafaren parking space ɗin dake part ɗin Abbah suka nufa, daidaita parking ɗin su kayi, durowa security Armys ɗin su ka shiga yi daga motocin su,cikin girmamawa su ka shiga buɗe masu car doors, motar farko
Abbah ne ya fitowa hannunshi riƙe da sandarshi mai shegen kyau sai ɗayan ɓagaren dady ya fito, motar bayan su dady Ahmad ne da dady mustafa su ka fito bayan ta su sai tasu  Uncle ubaid da Uncle mutallaf  su ka fito daga nan sai Uncle hashim.


bayan motocin su sai na jikokin Abbah,a mota ɗaya ya Naeem da zaabith su ka fito motar  bayan su  ya Adnan da ya usman, ya Ahmer ne su ka fito bayan tasu ne sai ta su Irfan da Waseef su ka fito waseef riƙe da hannun Jamal a front seat na motar da su ka fito Aman da Ammar su ka fito su ukku sun sha ankon white jallabiya harda Arb turban a kansu ba ƙaramin kyau su kayi ba kamar ka sace su ka gudu, motar bayan su Fa'iz da Yazdan ne su ka fito sun ɗauki wankan farar shadda kamar sauran, kawunan su a sanye su ke da huluna hakan ya ɓoye tarin sumar dake kansu.


gama fitowar su kenan daga motocin su motocin her excellency salima suka kunno kai cikin estate ɗin,da katawa su kayi har motocin su ka ƙaraso parking space ɗin, sai bayan da su ka gama daidaita parking ɗin tunkun ɗaya daga cikin securitys ɗin ya  buɗe mata car door ta fito,masha Allah na furta a sanye take da lafaya white color ta yafa gyale saman kanta, fuskarta ɗauke take da simple makeup kyawawan eyes  ɗinta a manne su ke da farin shade mai shegen kyau.


wurin Abbah ta nufo cikin takun ƙasaita yayinda PA ɗinta ke take mata baya, cikin girmamawa ta gaishe da Abbah, da kulawa ya amsa mata
“ina ki ka baro man Amaryata na ganki ke ka ɗai?”
“ bata jin daɗi ne”
“subhanallah, mike damunta?”


“ta dai ceman zazzaɓi na damunta, da tare zamu zo to sai da muka shirya kuma taji bata iya zuwa jikin ya ɗanyi zafi”
“ya salam, to Allah ya bata lafiya, Allah yasa kaffarane” gaba ɗayan su da Ameen su ka amsa


“dr ya dubata kuwa?” uncle Mustafa ya faɗa
“eh dr James ya dubata”
“mike damunta yace?”
“zazzaɓin ne kawai” mom salima ta faɗa
“zazzaɓi kawai ne a wajenki?,ni dama na san Zaabith bazai iya kula man da ƴata ba,idan baza ku iya kula da ita ba ku dawo man da ita zan  sa ƙwararren likita ya duba man lafiyar ɗiyata” ya faɗa yana zaro wayar shi daga Aljihun wandon shaddar shi.

Uncle Ahmad har ya buɗe baki zaiyi magana Abbah yayi saurin dakatar da shi dan ranshi ya ɓaci ya rasa miyasa Almustafa yake mashi haka, kullum gazawar su yake gani a wajen kula da ƴarsa,gaba ɗaya zuba mashi ido su kayi suna kallon ikon Allah, Zaabith duk yasha jinin jikinshi yasa bazai wuce rashin mutuncin da yayi mata bane ya haddasa mata zazzaɓi.


dialing number dr fawar yayi, bugu biyu yayi picking “hello fawar kana hospital ne?” on the other handa dr fawar ya amsa mashi da “Eh sir, kana buƙatar wani Abu ne?”
“kainart ce ba lafiya nake son kaje ka duba man ita”
“ok sir”
“thank u” ya faɗa yana rejecting call ɗin.


“amma kasan cewa gidan gomnati ba wurin shigar kowa bane haka kawai ?” Uncle Ahmad ya faɗa yana kallon Uncle Mustafa da yayi kicin kicin da fuska


“Irfan kaje kayi mashi rakiya zuwa Villa ɗin,idan kun isa ka kira ni ina son na san mike damunta da gaggawa”
“in sha Allah Uncle” Irfan ya faɗa yana nufar ɗaya daga cikin motocin da suka dawo,driver seat ya shiga, suna anan tsaye yayima motar key ya nufi main gate ɗin estate ɗin.


babu wanda Uncle Mustafa ya kalla a cikin su ya nufi ƙofar shiga katafaren garden ɗin gidan, murmushi kawai hajiya salima ta saki,Uncle Mustafa yanda mataƙar tsaurin akan ƴaƴan sa, bai haɗa soyayyar da yake masu da komai ba, zai iya ɓatawa da kai saboda ƴaƴan shi shikuma tashi ƙaddarar kenan son ƴaƴa,shiyyasa Kainart ke mugun tsoron ya san irin zaman da suke da Zaabith dan ta san muddin ya sani  abun bazai yi kyau ba.


“bari na shiga ciki Abbah”
“to salima” Abbah ya faɗa, enterence ɗin shiga part ɗin Abbah ta nufa
“muje ko Abbah”dady ya faɗa
“kuje gani nan zuwa” da to suka amsa mashi,ƙofar shiga garden ɗin su ka nufa, dakatar da Uncle Ahmad Abbah yayi.


“zo Ahmad” dawowa yayi in da Abbah yake tsaye, kamo hannunshi Abbah yayi cikin nashi, wata ƙofar shiga garden ɗin su ka nufa daban da wacce su dady su kashiga,wasu irin shuke shuke ne a wajen masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali,ga wasu tsuntsaye masu ban sha'awa dake kai komo a cikin garden ɗin.


wasu ƙayatattun benchs dake ƙarƙashin wasu rukunin bishiyu su ka nufa,zama su kayi suna fuskantar wasu killatattun ruwa,kai tsaye baza'a kira su da swimming pool ba ga wasu tsuntsaye dake shawagi saman ruwan abun gwanin ban sha'awa.


“na san ba kaji abunda ɗan uwanka yayi maka ba,amma ina so kayi haƙuri kayi mashi uzuri” Abbah ya faɗa
“Abbah amma mi yasa kullum Al'mustafah yake ganin gazawata akan ƴar sa,ina iya bakin ƙoƙarina wajen ganin wani abu bai faru da ita ba”


“haka ne Ahmad,amma kafi kowa sanin halinshi,yanada saurin fushi ga zuciya musamman akan ƴaƴanshi shi kalar tashi ƙaddarar kenan shiyyasa nake son kuriƙa yi mashi uzuri idan yayi wasu abubuwan,yanzu na san yana can hankalinshi duk ba'a kwance ba saboda rashin lafiyar ɗiyarshi,da ƙyar yau yayi bacci mai daɗin,kayi haƙuri da ƙaddarar ɗan uwanka”


“shikenan Abbah komai ya wuce a wajena, Allah ya bashi ikon cinye ƙaddarar shi”
“Ameen ya Allah,ya fama da mutane,ina fata komai yana tafiya daidai??”


“Alhmdllh Abbah komai yana tafiya yanda ya kamata”
“masha Allah,labari yana samuna har gida daga mutane daban daban,suna kawo man labarin yanda komai ke tafiya,kuma Alhmdllh naji daɗin yanda kowa daya buɗe baki yake faɗin Alkairi a kanka,Na yarda da tarbiyyar ka da gaskiyar ka da riƙon amanarka,nasan yanda kake da tausayin talaka ina so Ahmad ka ƙara fiye da haka, kazama adalin shugaba kamar ɗan uwanka,ina fatan yanda ɗan uwanka yayi ya gama lafiya har yau ƙasar nan bata manta da ayyukan Alkairin sa ba,ina so kaima kowa ya buɗe baki ya faɗi Alkairin ka ko bayan saukar ka”


“in sha Allah Abbah zaka sameni fiye da yanda kake tunani”
“haka nake son ji,Allah yayi jagora”
“Ameen ya Allah” fira su ka shiga yi Abbah na ƙarfafa mashi gwiwa akan mulkinshi da bashi shawarwari.


Idan muka koma ɓan garen su dady wani ƙaton dinner hall su ka nufa dake cikin garden ɗin,gaba ɗaya zagaye yake da glass daga waje kana iya hangen abunda ke ciki,wasu irin zungura zunguran luxury dinner tables ne guda biyu masu ɗauke da chairs guda ashirin akan kowane table,daga saman floor ɗin wasu irin manyan crystal chandelier ne masu shegen kyau dogayen da su kamar za su sauko ƙasa,gaba ɗaya hall ɗin a zagaye yake da manyan curtains masu matuƙar kyau an zuge su.


hall ɗin an ƙawatashi da wasu tukwanan ƙasa dake ɗauke da furanni masu matuƙar jan hankali,chefs ne maza da mata da a ƙalla zasu kai su goma sai aikin jera warmers suke a saman tables ɗin,cikin hall ɗin dady su ka shigo bakin su ɗauke da sallama.


da sauri chefs ɗin su ka dakata da abunda su ke,cikin girmamawa su ka shiga gaishe su,da kulawa suke amsa masu,tunda su ka shigo suka sauke idon su a kan uncle Mustafa dake can zaune saman ɗaya daga cikin kujerun dinner table ɗin,ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya sai aikin jijjigata yake,bini bini yake kallon wayar shi haɗi da jan tsaki.


dinner table ɗin su ka nufa kwanansu kujera yaja ya zauna dady ne kawai bai zauna ba ya nufi uncle Mustafa,kujerar dake kusa da wacce ya zauna yaja ya zauna,dafa kafaɗarshi yayi,saurin kallonshi uncle Mustafa da baisan da zuwanshi wajen yayi ba.


“yanzu Mustafa duk dan saboda ƴarka ka shiga wannan yanayin?,
rashin lafiya ne ba wani abu ba amma duk kabi ka tada hankalin ka?”
“bazaka gane bane ya Tahir,ni ka ɗai na san yanda nake ji”
“taya zan gane tunda ni ban haifa ba, Al'mustafa ka rage wannan mugun son ƴaƴan da kake,duk kabi ka ɗaurawa kanka damuwa saboda ƴaƴa sai kace kai kaɗai Allah yaba ƴaƴa,akan ƴaƴanka ba kaji baka gani,haba!?” ɗan dakatawa dady yayi yana kallonshi kafin ya ɗaura da cewa


“yanzu abunda kayi ma matar Ahmad kana ganin ka kyauta kenan,karka manta yanzu kainart ta tashi daga ƙarƙashin kulawarka ta koma hannunsu,sun fika iko da ita,sannan ina so ka sani ko babu Aure a tsakanin su Ahmad mai iya riƙe kainart ne haka Zaabith,ka zamo mai kawaici a kan ƴaƴanka”


tunda dady ya fara magana ƙala Uncle Mustafa bai ce ba sai yanzu
“kayi haƙuri ya Tahir in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba,hankalina ne ya tashi ban san wane irin ciwo take na”
“koma wane irin ciwo take Adu'a ya kamata kayi mata ba abunda kayi ba”
“in sha Allah zan kiyaye,kayi haƙuri”
“shi zaka ba haƙuri ba ni ba” Dady ya faɗa,waige waige uncle Mustafa ya shiga yi ko zaiga Uncle Ahmad


“yana waje tare da Abbah,kaje ka bashi haƙuri”
“to” uncle Mustafa ya faɗa yana miƙewa ya fice daga hall ɗin.

tun suna ƙananansu suna matuƙar girmama umarnin dady har kawo yau da su ka mallaki hankalin su kuwa.


tashi dady yayi ya nufi in da su uncle Ubaid su ke ya zauna,matan ne su ka fara shigowa hall ɗin,Mama Ameenah ce a gaba yayinda su mamy ke biye da ita a baya,sai da su ka gama shigowa mom da mom maryam da mom Maimunatu su ka shigo bayan sun shigo ne yaran su ka fara shigowa.


Su Yumnah ne su ka shigo hannunta riƙe da hannun Ammar da Aman yayinda da Jamal ya maƙalƙale hannun Nainarh sai turo baki yake shi adole fushi yake yumnah bata riƙe hannunshi ba.

ɗaya bayan ɗaya su ka shiga shigowa, kowannan su ya shigo wajen zama yake nema ya zauna, table ɗin da su dady ke zaune su mom su ka zauna, kowaccen su na fuskantar mijinta yayinda mamy da su hajiya fatilah su ka cure waje ɗaya su da Mama Ameenah  bako ta mazajen na su suke ba, sai hura hanci su ke sunama mutane kallon tara saura kwata.

ɗayan Table ɗin su Yumnah su ka zauna da sauran jikokin Abbah, a tare Abbah da Uncle Ahmad da Uncle Mustafa su ka shigo, suma wajen zama su ka nema su ka zauna,saida kowa ya gama samun wurin zama ya zauna tukun chefs su ka shiga serving ɗin su, cika masu gaban su su kayi da Abinci kala kala na Alfarma.


tunda su ka shigo Aunty Safeenah ta kafe mom Maryam da kallo,wani irin kallon mamaki take binta dashi,tsaki taja tana kallon mama Ameenah


“dan Allah mama dubeta,sai wani hura hanci take kamar wani ta fi,mai Abun duniyar ma ba tayi ƙafafa ba sai ita”

“ai ni wallahi lamarin Maryam mamaki yake bani,wai ni baku lura da ita ba yanzu tafi ƙarfin zuwa ta gaishe da mama bare mu data gama rainawa mu samu arziƙin da za tayi mana magana” A cewar hajiya halima


“rabu da ita kawai zanyi maganinta ne”acewar mama Ameenah


firarsu su ka shigayi wacce banda zagin su mom ba abunda su ke, Hajiya Salima na cikin su amma kwata kwata bata saka masu baki ba haka mamy ma tunda ta zauna hankalinta na can wani waje daban,bamata san akan mi su ke magana ba,ta ƙurama waje ɗaya ido,suma da su ka gaji shiru su kayi hall ɗin yayi tsit banda ƙarar spoon da plate baka jin komai.


Noor tunda ta zauna dinning ɗin Banda juya spoon babu abunda take gaba ɗaya ta kasa cin abincin saboda rashin shi a kusa da ita duk tabi ta damu,kallonta laatifa dake kusa da ita tayi.


“lafiya dai ko Noor?” murmushin yaƙe ta sakar mata tana faɗin lafiya.
“mi yasa baki cin abincin,ko dai wannan baiyi maki ba chefs su canza maki wani??”


girgiza mata kai Noor ɗin tayi
“A'a, bana jin daɗi ne ”
“Ayyah!,sannu mike damunki?”
“jikina nake ji babu daɗi” ta bata amsa, murmushi Kairiyyah ta saki dan ta san ba komai yasa noor faɗin haka ba sai dan saboda Irfan.


Ringing ɗin wayar laatifa ne yaja hankalin mutane da dama dake hall ɗin har da dadyn ta,wani kallo ya shiga watsa mata,kwata kwata bata lura da irin kallon da yake mata ba, ganin sunan mai kiranta nata ne ya sata saurin miƙewa daga saman chair ɗin da take zaune,ƙofar fita daga hall ɗin ta nufa yayinda take picking call ɗin.


a bakin ƙofar shiga hall ta tsaya tana amsa wayar
“hello sister,kamar kin san duk ina nan na damu da rashin zuwanki” laatifa ta faɗa,on the other hand ta cikin wayar tace

“bana jin daɗi ne ƴar uwa shiyyasa ban zo ba”
“subhanallah! mike damunki naji ma muryarki wani iri, fatan dai ba wani abun ba ne ya sake faruwa ba dan naga ya Zaabith na gari”
“please sister ki zo idan babu abun da ki ke”


“wai mike faruwa ne,duk kin sa hankalina ya tashi”
“babu komai ki zo dai Please”
“ok gani nan zuwa”
“sai kinzo” rejecting call ɗin tayi,hanyar fita daga garden ɗin ta nufa ba tare da ta koma cikin hall ɗin ba,daga inda dadynta yake cikin hall ɗin yana hangen ficewar ta.


miƙewa yayi ya fito daga hall ɗin,bayanta yabi, parking space ɗin gidan ya nufa,yana isa motar ta na ficewa daga parking space ɗin,wayar shi ya zaro daga cikin Aljihu yayi dialing wata number, bugu biyu a kayi picking.


“gata nan ta fito ina son kutabbatar da in da taje” on the other hand wata irin kakkausar Muryar ce mara daɗin jin ta daki dodon kunnenshi
“angama ranka ya daɗe” rejecting call ɗin yayi ba tare da yace komai ba.


yana a nan tsaye kamar daga sama yaji anyi hugging ɗin shi ta baya tightly, murmushi gefen fuska ya saki ba tare da ya juya ba dan ya san bazai wuce ita ba ce dan babu mai mashi irin wannan rungumar idan ba ita ba.


“ai nayi tunanin sai na kira ki zaki fito?” ya faɗa cikin wani irin yanayi kamar ba barisster ba
“ni na isa, kawai jiran damar da zan fice nake ba tare da wani ya lura da ni ba”


taɓe baki yayi yana faɗin “fushi nake dake,yau wajen kwana nawa da alƙawarina amma baki ciki ba”

“kafi kowa sanin halin yayanka kwata kwata baya bani damar da zan matsa daga gidan,yanzu ina sa ƙafa na fita zaisa abi masa diddiƙin in da na tafi,kuma nasha faɗa maka ka riƙa zuwa gidan babu mahaluƙi da ya isa ya zargeka akan zuwa gidan yayanka,kuma har ka gama abun da ya kawoka ka fice ba tare da ya san ka zo ba.


hannunshi yasa ya jawo hannunta ta dawo gaban shi, ƙare mata kallo ya shiga yi tun daga sama har ƙasa kafin ya tsaida lumsassun idanunshi a kanta, wani irin shaiɗanin kallo ya shiga binta da shi,ba ita da yakema kallon ba hatta ni dake laɓe sai da naji kunyar irin kallon da yake mata.


kasa jure kallon da yake mata tayi,tafin hannunta tasa ta rufe idanuwan shi
“barisster irin wannan kallo haka, sai ka sa gaban ya faɗi” murmushi ya saki yana janye hannunta daga idanunshi,baki ta buɗe da nufin yin magana amma yayi saurin manne bakinshi da nata.


*Tashin sense Barisster Hashim,mamy 😳😳😳😳*


Zagayo da hannayenshi yayi ya riƙe ƙigunta,itama ƙanƙameshi tayi kamar za su koma abu guda,a ƙalla sun shafe tsawan five minutes a haka kafin ya raba jikin su,jan hannunta yayi su ka nufi ɗaya daga cikin motocin dake parking space ɗin,front seat ya buɗe mata ta shiga,zagayawa yayi ya shiga driver seate,Key yayi ma motar su ka nufi cikin estate ɗin.


*ASO VILLA*


Bata sha wata wahala ba wajen shiga,  saboda ita ɗin sannance a idanun securitys ɗin kuma bayan haka sun san alaƙarta da mazauna gidan.


A katafaren parking space ɗin Villa ɗin tayi parking, kusan a tare su ka fito da wani matashin ba indiye dake zaune a cikin motar shi,bai jima da parking ba tayi parking.


in da take ya nufo hannunshi ɗauke da briefcase, fuskarshi ɗauke da fara'a ya ƙaraso,murmushi itama ta sakar mashi.

“Dr fawar dama kana ƙasar?” ta faɗa da almun mamakin ganinshi, murmushi ya sakar mata cikin hausar shi da bata gama daidaita ba yace
“ina za ni, Ina nan hajiya laatifa, dama yaran irin mu na ganin ku?”


dariya ta fashe da ita wacce ta ƙara fito da ainihin kyawun fuskarta “daɗina da kai zolaya fawar, in da ka so gani na ai ka san in da zaka same ni”
“kina son dadyn ki yayi ƙarata kenan?” ya faɗa,dariya kawai laatifa tayi ba tare da tace komai ba.


juyawa su kayi da nufin barin wajen zuwa ciki, horn ɗin da a kayi a bayan su ne ya dakatar da su,parking space ɗin matuƙin motar ya nufo, parking yayi,  zuba ma motar ido su kayi dan ganin wanda zai fito.


Irfan ya fito,da sauri ya nufo su yana faɗin “sorry Dr, na san na ɓata maka lokaci” ɗan hararar shi dr fawar ɗin yayi
“haba Irfan ka san yanda tsarin gidan nan naku yake amma ka barni a tsaye a bakin gate da ba dan nayi hausar kiran Zaabith ba da tuni ina can rana na duka na”


“sorry na tsaya amsar wani saƙo ne, muje ko, Aunty Laatifa ina wuni”

“lafiya lau Irfan, kwana biyu” da Alhmdllh ya amsa mata yayinda su ke shiga cikin gidan,babu kowa sai masu aiki dake kai komo, direct part ɗin Zaabith su ka nufa, parlorn su tsit yake babu kowa sai masu aiki dake ƴan hidindimun su, gaishe da su masu aikin su kayi, a saman sofa fawar da Irfan su ka zauna yayinda laatifa ta nufi bedroom ɗin Kainart.


bakinta ɗauke da sallama ta tura ƙofar ta shiga tana ambaton “my own sis gani na ƙa...”
dakatawa tayi da maganar ganinta a kwance saman bed harda su rufa,ƙarasawa tayi bakin bed ɗin.


“Kainart lafiya?” ta faɗa tana ɗan yaye blanket ɗin data rufa,tashi tayi zaune ta jingina da head board ɗin gadon.


wani irin mummunan faɗuwa gaban laatifa yayi ganin sawun duka a saman neck ɗinta gana mari da har yayi baƙi saboda hasken fatar ta.


“kainart mi ya same ki haka, kardai kice har yanzu ya Zaabith bai daina dukanki ba??” Laatifa ta faɗa da tsantsar damuwa
“har yau Laatifa ya Zaabith yaƙi ya canza halinshi”
“kainart idan har da laifin ya Zaabith naki yafi yawa, ni banga amfanin zaman nan da kike da shi ba, mutuminnan baya sonki amma ke har yau kin kasa ganewa, so ki ke ki salwantar da rayuwarki a banza?” Laatifa ta faɗa ranta a ɓace.


“bazaki gane bane Laatifa”
“dama taya zan gane tunda soyayya ta rufe maki ido har kina shirin salwantar da rayuwarki a banza, wallahi Kainart ko ni da nake fuskantar tsangwama daga dady gara ni dake, duk ranar da Allah ya bani miji mai sona nayi Aure shikenan, amma ke fa?, karki manta zaman Aure ba zama ne na ɗan lokaci ba zama ne na har abada, kuma tuda har ya Zaabith bai sonki ko kun ɗau tsawan  shekaru tare ba ganin mutuncinki zaiyi ba, gara tun wuri kisan Abun da ya dace??”


“ina sonshi ne Laatifa shima yana sona bazaki gane ba, kuma idan na barshi ya ki ke so nayi da su Ammar?”

“matsalar ki kenan soyayya,wlh ya Zaabith baya sonki da yana sonki bazai riƙa wulaƙantaki ba, sannan su Ammar da ki ke magana, karki manta ko babu Aure tsakaninki da ya  Zaabith zai iya riƙe abun da ki ka haife barema ƴaƴan sa ne, kuma kin san cewa duk tashin hankalin da za'ayi dady bazai taɓa bari a rabaki da su ba hakama Abbah, ki nemama kanki mafita Kainart,ba kiga yanda ki ka koma ba kamar ba ke ba duk kinbi kin lalace”


“wace mafita zan nema Laatifa?” ta faɗa da alamun son ƙarin bayani daga Laatifa
“na san zaki ce bazaki iya  rabuwa da shi ba, amma ya zama dole dady ya san irin zaman da kike a gidanan”
girgiza mata kai tayi “gaskiya Laatifa bazan iya sanar da dady ba kin san halinshi, muddin ya sani ya Zaabith ya shiga uku”


“to ya shiga ukun mana ina ruwan wani, ke sau nawa yana saki a ukun” Laatifa ta faɗa a hassale da alama dai ranta ba ƙaramin ɓaci yayi ba
“bazan iya ba, ina tausayin hukuncin da dady zai yanke mashi,zanta kai kukana wajen ubangiji, in sha Allah wata rana zai daina”


“ai shikenan sai ki tashi dr fawar na nan dady ya turoshi ya dubaki” wani irin faɗuwa gabanta yayi, saurin dafe saitin zuciyarta tayi

“na shiga uku! waya faɗa mashi bana da lafiya?”

“kema kin san dole yaji ba'asin abunda ya hanaki zuwa gidan Abbah,may be mom salima ce ta faɗa mashi baki da lafiya, kin san kuma komi a kayi maku idan ba shi yayi ba baya ganin daidain shi, ki tashi kawai kije”


“amma bata faɗa mashi dr James ya dubani ba?”
“kinfi kowa sanin waye dady, kawai ki wuce kije” hijab ta ɗauka ta zura a jikinta, ficewa tayi zuwa parlorn, gefen bed ɗin Laatifa ta zauna.


A zaune ta same su saman sofa kamar yanda laatifa ta barsu masu aikin sun kawo ma Dr fawar abun motsa baki.


cikin girmamawa su ka gaishe da juna ita da Dr fawar,bayan da su ka gaisa ne ya shiga yi mata ƴan tambayoyi tana bashi amsa.


duk wani abun da ya kamata yayi mata yayi mata,baisha wahala ba saboda duk wani da zai buƙata wajen duba patient ya zo da shi,sallama yayi mata akan idan ya kammala binciken zai ba Irfan sakamakon ya kawo mata,godiya tayi mashi sosai.


sallama yayi mata su ka fice shida Irfan,a parking space yana shirin shiga motar shi uncle Mustafa ya kira dan yaji mike damunta,sanar da shi yayi zazzaɓi ne dai yanzu sai sakamakon test ɗin da yayi mata ya fito sannan ya san taƙamaimai abunda ke damunta.


godiya sosai uncle Mustafa yayi mashi kafin su kayi sallama,ficewa su kayi daga Villa ɗin motar Irfan na gaba yayinda ta Dr fawar ke bayan shi.


Estate Irfan ya koma lokacin har sun kammala lunch suna part ɗin Abbah,Noor tayi fushin tayi fushin har ta gaji,sai da ƙyar ya samu ya shawo kanta.


Barisster Hashim da mamy da su ka fita ba sune su ka dawo ba sai da yamma liƙis ana gab da kiran magrib,sai ma da suka dawo sannan wasu su ka fahimci ba sa nan.


Bayan sallar isha su kayi dinner kowa ya kama shirin tafiya gida,Ammar tunda lokacin tafiya suka fara murnar yau a gidan big daddy za su kwana Jamal ma rigima yasa shima dole ya bisu,wayau Aunty Nafisat ta so yi mashi kan ya bari idan sun koma gida dadyn shi zai kawo shi amma fir ya tubure shi dole yanzu yake son bin su duk yanda ta so ya bari sai wani week ƙin amincewa yayi dole tasa su ka haƙura.


motar su na bayan ta Irfan daya ɗauko mom,Yumnah na back seat tare da yaran yayin da Nainarh ke front seat kusa da Fa'iza dake driving.


Yumnah tun kafin su ƙarasa ta kira Ishrat ta sanar da ita zuwan su Ammar saboda su gyara masu bedroom ɗin dake kusa da na Yumnah,sosai Ishrat tayi murna da zuwan su Ammar yaran na matuƙar burgeta.


A tare motocinsu su kayi parking,a tare su ka shiga fitowa daga motocin,cikin gidan su ka nufa su Ammar na riƙe da hannun Yumnah, Jamal ma Nainarh ya maƙalemawa tunda Aunty Yumnah ta yadashi,ɗaya daga cikin security ɗin gidan ne ya shigo da kayan su Ammar.


Irfan har bedroom ya raka mom da jakatar a hannunshi mom har mamaki take miye alaƙar Irfan da son riƙe jaka,duk za su fita tare baya barinta riƙe jaka ko kau ina za su je haka zai riƙe jakarta,Fa'iza har iya shage take mashi saboda riƙe jakar mom.


Basu wani jima su ka fice shida Waseef da alama sauri suke zuwa wani waje, bedroom da Yumnah tasa aka gyara masu ta nufa da su Ammar, bedroom ɗin yana da girma sosai dan yafi na Yumnah girma ƙaton king size bed ne a cikin shi.


ruwa Yumnah tasa su ka watsa su ka shirya cikin pajamas ɗin su,a nan ɗakin su kwana harda Nainarh dan rigima su ka masu akan sai sun kwana tare da su...


_*HEART OF VEGAS CLUB AND CASINO*_

*12:00 AM*


_*HEART OF VEGAS CLUB AND CASINO*_


Ƙarfe shabiyu na dare daidai motar su tayi parking a ƙaton parking space ɗin dake club ɗin, maƙil yake da motoci kasancewar yau Friday duk wani mashahurin da yake ganin ya shahara ayawan club zaka same shi a nan.


Kamar yanda sunan ya kasance iri ɗaya haka tsarin ginin ma iri ɗaya ne,banbanci kawai wacan yafi girma sai dai ba wani sosai ba,gaba ɗaya photocopy wacan ne.


Kusan a tare su ka fito,jeans da T_shirt ne a jikin Waseef yayinda Irfan ke sanye da shirt haɗe da short iya gwiwarshi,kanshi a sanye yake da Ivy Cap idanunshi a manne su ke da baƙin shade mai shegen kyau.


Entrance ɗin shiga club ɗin su ka nufa,wasu irin jibga jibgan security guard a gaban katafariyar ƙofar shiga club,tun kafin su ka ƙaraso securitys ɗin su ka rissinar da kai alamar girmamawa a gare su,kallon in da su ke babu wanda yayi tsakanin Irfan da Waseef,bakin ƙofar su ka ƙarasa, Waseef ne ya ciro card ɗin shi daga cikin aljihu,a jikin na'urar dake jikin ƙofar ya zura card ɗin,zugewa ƙofar ta shiga yi bayan na'urar ta kammala acknowledging card ɗin.


ciki su ka kunna kai Irfan na baya yayin da Waseef ke bayan shi,tsarin club ɗin ɗaya ne dana US duk abunda ke a wancan a kwaishi a wannan banbanci abubuwa kaɗan ne, mata da maza ne ta ko ina kowa na harkar gaban shi, wasu na rawa wasu na shaye shaye,babu wanda ya lura da shigowar su har su ka isa bakin galss elevator dake club,maddanan dake jiki Waseef ya danna nan take ƙofar ta buɗe,ciki su ka shiga,sama elevator tayi da su zuwa floor ɗin ƙarshe.


fitowa su kayi bayan ƙofar ta zuge,a bakin wani office su ka tsaya,wasu nombobi dake a jikin na'urar dake jikin ƙofar ya danna,nan take ƙofar ta buɗe,ciki su ka shiga, katafaren office ne kamar ba'a niger ba komai na cikin shi extraordinary ne, Executive chair ɗin dake gaban haɗaɗɗen glass desk Irfan ya nufa,zama yayi yayin da Waseef ke jan ɗaya daga cikin chair ɗin dake gaban desk ya zauna.


mac book ɗin dake ajiye saman desk ɗin ya buɗe,babu ɓata lokaci ya shiga operating ɗin ta.


“wai yaushe Muhsin yace maka Boss zai dawo ne,akwai kayan da babu ga tarin customers da muke da su?”Irfan ya faɗa ba tare da ya ɗago daga abunda yake ba

“kasan ba kowa ke sanin lokacin tafiyar shi ba haka lokacin dawowarsa” jinjina kai Irfan ɗin yayi
“gashi Muhsin ɗin bai shigo ba,amma bari na kira wayar shi naji” ya faɗa yana zaro wayarshi daga aljihu,number Muhsin ya shiga dialing, ringing wayar ta shiga yi har kiran ya katse ba'ayi picking ba, Yana ƙoƙarin sake kira aka turo ƙofar office ɗin.


“ina jin gashi nan” Waseef ya faɗa yana kai dubanshi ga ƙofar dan ya san idan ba Muhsin ɗin ba to Boss ne su kaɗai keda lasisin shigowa ba tare da na'ura ta dakatar da su ba.

Wani matashin saurayi ne ya shigo cikin shigar ƙananan kaya,ƙaƙƙarfa ne na gaske,cikin office ɗin ya nufa, kujerar dake kusa da wacce Waseef ke zaune yaja ya zauna,hannu ya miƙa masu su kayi musabaha


“kamar kuwa kasan nemanka nake”irfan ya faɗa
“shigowata kenan naga kiranka,neman mi kake man fatan dai lafiya?”
“dama tambayarka zanyi yaushe boss zai dawo, akwai tarin customers a gaban mu”

“ka san halin yaya idan zai tafiya baya faɗa, nama yi tunanin ko kai ya faɗa maka”
“ya dai faɗa man zaiyi tafiya amma bai sanar dani time ɗin da zai dawo ba”
“ok abunda ya kamata kawai ka kirashi kaji yaushe zai dawo dan akwai tarin schedules na meeting wanda dole ya halarce su”


“ok bari na kira naji” Irfan ya faɗa yana ɗaukar wayar shi yayi dialing number boss, ringing wayar tashiga yi har sun fitar da ran za'a ɗauka akayi picking,wata irin buɗaɗiyar murya ce ta daki dodon kunnenshi.


“hello Irfan,fatan lafiya ka kira ni?” na cikin wayar ya faɗa
“lafiya lau,dama cewa nayi yaushe ne zaka dawo,kaya da yawa fa sun ƙare gashi yau muna da guest da yawa?”
“ sai next week nake sa ran dawowa ina las Vegas ne,akwai key a hannun Muhsin ku duba store na san baza'a rasa wa su a ciki ba”


“amma meeting ɗin ka fa,kasan fa dis week kayi masu alƙawari”
“haka ne,ina sane,kai nake so kayi Attending ɗin su”
“nikuma boss?” Irfan ya faɗa da alamar ruɗu
“eh,na san ai zaka iya dan ya kamata ka fara wasu abubuwan da kanka ba dole sai da ni ba”
“amma Boss kasan bana da gogewa a abun, infact ma ban taɓa Attending meeting irin wannan ba”


“karka damu idan zaka je za muyi amfani da communicative devices,zan dunga sanar da kai abunda ya kamata ka faɗa”
“ok Boss,sai ka dawo”
“thanks” Boss ɗin ya faɗa yana rejecting call ɗin.


saurin tambayar shi su kayi dan jin yaushe yace zai dawo
“sai next week” ya basu amsa
“kayan fa?” Muhsin ya faɗa
“yace akwai key a hannunka mu duba store baza'a rasa ba”
“ok,bari muje tare da Waseef,amma meeting ɗin fa?”
“ni yace nayi Attending ɗin su”


Ok kawai Muhsin ɗin yace,tashi su kayi su ka fice daga office ɗin zuwa store,maida kanshi yayi a kan mac book ɗin dake gaban shi.


*ASO VILLA*


A kwance take saman makeken gadonta ta rufe jikinta da duvet,tunda laatifa ta tafi take a kwance sallah kawai ke tashin ta.


Turo ƙofar ɗakin yayi ya shigo,Black suit ne a jikinshi looking smart,cikin ɗakin ya ƙaraso,a bakin bed ɗin ya zauna,hannu yasa ya yaye duvet ɗin da tayi rufa

in a low voice ya kira sunanta “kainart!” tsit tayi kamar batajishi ba,sake kiran sunanta yayi still bata amsa mashi ba
fuskarta ya leƙa dan yaga bacci take ko kuwa,motsi ya ga tana yi da idanunta alamar idonta biyu.


shafa fuskarta yayi da tafin hannunshi “ya jikin naki?” ya faɗa cike da kulawa,banza tayi da shi kamar bata san da ita yake ba
“kainart na san kina jina,fushi kike dani ne?” nan ma ƙin tanka mashi tayi a ranta tana faɗin “watau ma bai damu da abunda yayi mata ba har yake tambayar fushi take.

tashi yayi ganin da gaske ba kulashi za tayi ba,ƙofar fita ya nufa ɗan buɗe idonta tayi a hankali ta saci kallonshi,har ya kama handle ƙofa zai fice sai kuma ya dakata yana juyowa ya fuskance ta,saurin rufe idonta tayi.

“zan fita akwai yiwuwar sai gobe zan dawo ki kulaman da kanki” yana gama faɗa ya fice haɗi da jan ƙofar ya rufe.


a hankali ta buɗe idonta tana bin ƙofar da kallo,gaba ɗaya takaice ne ya cikata ko ina zaije da wannan tsohon daren kuma har yake faɗa mata wai sai gobe ma zai dawo,baƙin cikinta da takaicinta idan ya tashi dawowa abuge zai dawo mata ya shuka mata rashin mutunci, shikenan ita a haka rayuwarta zata ƙare.


idan tana tuna lokacin baya kafin suyi Aure sai taga kamar ba Zaabith ɗinta ba wanda kwata kwata baya son ganin ɓacin ranta,inda wani yace mata zai sauya mata bayan sunyi Aure bazata taɓa yarda ba saboda irin soyayyar da yake mata amma lokacin guda komai ya canza.


siraren hawayen da su ka zubo mata tasa hannu ta share,sauka tayi daga saman bed ɗin ta nufi toilet,alawa ta ɗauro ta zo ta kabbar sallah, nafilfilu ta shiga jerowa tana kai kukunta ga Ubangijin sammai,ta jima sosai tana Adu'a akan Allah ya shirya mata mijinta.


*UNITED STATE*


_*Las Vegas (Nevada)*_


*6:30 PM*


A kwance take saman leg press machine dake gym room ɗinta tana pressing leg ɗin ta up to down, active wears ne a jikinta vest da short Black color ta ɗaure sumar kanta da ribbon,kunnenta a manne yake da earphone tana sauraren sauti,sosai take press leg ɗinta ta haɗa uban gumi.


masu aikinta na zaune saman wasu benchs,hannun su riƙe da dumbbells,Gym room ɗin yana da girma sosai kamar gym center,babu kalar nau'in machine ɗin da babu a ciki gasu nan kala kala su exercise ball, punching bag, dumbbells,ellptical cross trainer, treadmill,bench press,step machine, trampoline, fitness cycle da dai sauran su.


Turo ƙofar Gym room ɗin a kayi,Aunty Sophia ce ta shigo cikin shigar shirt da dogon wando Black color ta ɗaure sumar kanta da ribbon black color, hannunta ɗauke jug Wanda ba komai bane a ciki sai tacaccen ruwan lemu na musamman wanda ta haɗa domin babynta, murmushi ta saki ganin yanda Nailarh ta dage bataji bata gani.


cikin Gym room ɗin ta ƙaraso,jug ɗin dake hannunta ta ajiye saman wani ɗan round table dake kusa da Nailar kafin ta nufi treadmill tahau,kunnawa tayi a hankali ta shiga running.


Nailar ta kai tsawan 30 minutes kafin ta dakata,dubanta ta kai ga Aunty Sophia, murmushi ta saki tana zame earphone ɗin dake kunnenta,alama jinjina tayi ma Aunty sophia, murmushi Aunty Sophia tayi tana maida mata martanin alamar da tayi mata.


Tashi tayi daga saman machine ɗin ɗaukar jug ɗin tayi ta nufi bench press,zama tayi,a hankali ta shiga shan lemun da Aunty Sophia ta haɗa mata, sai da tasha kusan rabin jug ɗin kafin ta ajiye,zufa har rige rigen fitowa take daga ƙofofin gashin jikinta,ɗaya daga cikin masu aikin ce ta nufo inda take da ɗan madaidaicin towel a hannunta.


goge mata gumin da tayi ta shiga yi,sai data tabbatar ta goge mata kafin ta koma mazauninsu,tashi Nailarh tayi ta nufi punching bag,boxing gloves dake ajiye saman wani table ta ɗauka ta zura a hannunta,a hankali ta fara kaima bag ɗin bugu kafin ta shiga kaimata duka da sauri sauri.


Wayarta dake hannun masu aiki ce ta fara ringing hakan ya dakatar mata da jin sautin da take da sauri mai aikin ta nufo ta,da katawa tayi, boxing gloves ɗin dake hannunta ta shiga zamewa,karɓar wayar tayi lokacin data gama zame hand glove ɗin, picking call ɗin tayi bayan ta duba sunan mai kiranta.


picking call ɗin tayi haɗi da kara wayar a kunne ba tare da tace ƙala ba,daga cikin wayar mahaifiyarta ce tace “hello baby”


shiru tayi tana turo baki kamar bada ita take magana ba, sake magana tayi tana faɗin
“baby fushi ki ke da momynki?”

still shiru tayi bata tanka mata ba, Aunty sophia dakatawa tayi da abunda take, in da nailarh take ta nufo, alama tayi mata da waye, turo baki nailarh tayi ba tare da ta bata amsar tambayar da tayi mata ba.


“please baby kiyi man magana mana, momynki ce fa?” mahaifiyar tata ta faɗa kamar zata sa mata kuka
“momy yaushe zaki dawo?” shine kawai abunda Nailarh tace mata,daga cikin wayar tana jiyo yanda mahaifiyar tata ta sauke ajiyar zuciya “kina so na dawo ne?”


“eh,gidan duk yayi baƙi saboda babuke a ciki, jina nake kamar ba ni ba saboda rashinki a kusa dani please momy ki dawo na gaji” ta faɗa kamar zata fashe mata da kuka, Aunty sophia na daga gefe tana kallonta, masu Aikin ma zuba mata ido sukai suna kallonta

“nima duk a daddafe nake saboda rashinki a tare da ni,amma ba sophia na nan ba?”
“tana nan mana, amma kin san matsayin kowa a cikinku daban a zuciyata, momy gaskiya ki dawo idan ba haka ba bazan sake zuwa Empire ba”
“baby kin cika rigima,nafa ce maki sai upper week zan dawo”


“ni dai na riga na faɗa maki bazan sake zuwa ko inaba muddin baki dawo ba”
“sorry zan dawo shikenan”
“yaushe?”ta jefa mata tambayar da son jin yaushe za tace
“yaushe ki ke son na dawo?”
“dis week”ta faɗa a shagwaɓe


“dis week yayi kusa Nailarh, ban kammala abunda nake ba fa”
“to zan biyoki”
“A'a ki bari zanyi ƙoƙarin squeezing schedules ɗina na dawo next week,hakan yayi maki?”
“Eh” ta bata amsa a shagwaɓe.


murmushi mahaifiyar ta saki tana faɗin “rigimammiyar yarinya kawai ina fatan baki manta da shipment ɗin mu ba?”
“ban manta ba”
“yawwa haka nake son ji, kiyi ƙoƙari ku isa port ɗin da wuri”
“please momy su Joseph suje port ɗin ni sai na same su a Orphanage ɗin”


“baby mi yasa ki ke son maida magana baya, na faɗa maki ke nake son kije,so nake ki koma ke ke kula da komai ba tare da wani ba”
“shikenan momy sai kin dawo”
“ok bye take care”
“bye” ta faɗa tana  rejecting kiran, dubanta ta kai ga Aunty sophia data tsareta da idanu.

shafa fuskarta Nailarh tayi tana faɗin
“lafiya ki ke mana wannan kallon?”


girgiza mata kai tayi “ina za kije?”
“port” ta bata amsa tana nufar plyometric box ta zauna
“amma miza kiyi a can?”
“yau shipment ɗin mu zai ƙaraso”
“na sani, amma su Joseph ke zuwa ba ke ba,mi za kiyi a can??”


“su ke zuwa amma wannan time ɗin ni zanje” in da take Aunty sophia ta ƙaraso kamo hannunta tayi cikin nata “please Nailarh ki bari su suje,a kwai haɗari a irin wannan wurin kuma kinga dare ne”


“momy tace ni zanje, kuma Aunty  sophi kin manta wacece ni,Nailarh ce fa, Queen, ni da nake kula da heart of vegas amsar kaya ne zai gagare ni”

“ba haka bane Nailarh, bana son wani abu ya sameki”
“ki kwantar da hankalinki babu abunda zai same ni”
“duk da haka Nailarh ko heart vegas da ki ke zuwa hankalina kullum a tashe yake, please ki bari suje da kansu” Aunty sophia ta faɗa da tsantsar damuwa tana matuƙar son Nailarh shiyyasa take tsoron wani abu ya sameta.


“nafa ce maki babu abunda zai same ni,ki kwantar da hankalin ki”
“shikenan” Aunty sophia ta faɗa ba dan ta so ba, murmushi Nailarh ta saki tana shafa gefen fuskarta

“na lura tunda ki ka ƙara tsufa tsoronki yayi yawa a kaina”
bige hannunta Aunty sophia tayi
“bana son shirme, kije kiyi wanka time ɗin dinner ɗinki yayi”


“ok muje yau kiyi man wanka da kanki” Nailarh ta faɗa tana miƙewa haɗi jan hannun Aunty sophia, saurin fisge hannunta tayi


“nailarh waike baki da kunya ne?” ɗaga mata gira tayi haɗi da faɗin
“eh” ta bata amsa a gadarance haɗi da kashe mata ido ɗaya, girgiza kai Aunty Sophia tayi

“idan ke baki da kunya ni inada ita”ta faɗa tana nufar ƙofar ficewa daga Gym room ɗin,bin bayanta Nailarh tayi tana sakin murmushi.


Part ɗin ta ta nufa,tana shiga direct toilet ta nufa anan ta samu Lara da Lolah da tun kafin ta shiga su ka san da zuwanta,babu ɓata lokaci su ka shiga abun da ya kawo su,ba su wani jimaba su ka kammala mata wankan ficewa tayi daga toilet ɗin ta nufi home of beauty ɗinta.


Aunty Sophia tana ficewa daga Gym room ɗin katafaren kitchen ɗin gidan ta nufa,tun daga waje ƙamshi abinci ya daki hancinta har sai da ta lumshe idonta,ciki ta ƙarasa,chafs ne maza da mata kowannan su ya duƙufa akan aikin haɗa dinner da su ke.


cikin girmamawa su ka shiga gaishe da ita,cike da kulawa take amsa masu tana nufar dinner table ɗin da su ka jera wermers,bubbuɗe wermers ɗin ta shiga yi tana ganin abunda su ka girka,jinjina kai ta shiga yi da alama ta yaba da aikin su.


“wannan girki haka sai kusa kunnen mutum ya tsinke tun kafin yaje bakin sa saboda daɗi,sannun ku da ƙoƙari”

washe mata baki su kayi suna faɗin “Thanks” jin jina kai tayi
“yanzu ba jimawa Nailarh zata sauko,ya kamata ku shirya dinning” da ok su ka amsa mata.


ficewa tayi daga kitchen ɗin,maza biyu daga cikin su suka shiga jidar wermers ɗin suna nufar ƙayataccen dinning room ɗin gidan,cikin ƙan ƙanin lokaci su ka kammala shirya dinning room ɗin.


Bedroom ɗin Nailarh ta nufa,direct home of beauty ɗinta ta nufa ta san bata wuce nan,tura ƙofar tayi ta shiga, a zaune ta hangota kan stool daga ita sai bathrobe Luna da Mary masu aikinta na gyara mata jiki.


cikin ɗakin Aunty Sophia ta ƙarasa,wuri ta samun saman ɗaya daga cikin chairs ɗin dake ɗakin ta zauna.

“baby an kammala haɗa dinner”
“thanks U Aunty sophi”ta faɗa tana miƙa mata hannunta,kama hannunta Aunty Sophia tayi.


har aka kammala mata gyaran jiki dana gashi hannunsu na a cikin na juna,a tare su ka fice daga ɗakin zuwa dinning room

Aunty sophia taso ta fara shiryawa amma ta nuna ba haka ba tafi son ta kammala dinner tukun.


A jere su ka isa katafaren dinning room ɗin,a zagaye yake da glass wall wanda ke waje zai iya hangen abunda ke ciki,daga sama ƙatuwar crystal Chandelier ce ta sauko ƙasa yayinda take bada wani irin haske mai ƙyatarwa, zungureren dinning table ne mai kyan gaske aƙalla yana ɗauje da 20 chairs,komai na cikin sa golding color ne
table ɗin a shaƙe yake da wasu irin warmers masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali, kai tsaye zaka iya cewa da kumfar zinari aka yi su, sai ƙyalli su ke da ɗaukar ido.


chefs ne a tsaitsaye cikin dinning room ɗin, ciki su ka ƙarasa,cike da girmamawa chefs ɗin su ka shiga rissinawa suna gaishe da uwar ɗakin na su,ciki ta ƙarasa ba tare da ta amsa masu gaisuwar da su ke mata ba, cikin kulawa Aunty sophia tayi masu alamar jinjina,murmushi ne ya bayyana a fuskarsu.


kujerar dake gaban table wacce ke facing gaba ɗaya kujerun dinning ɗin Aunty sophia taja mata ta zauna,gaban table ɗin chefs ɗin su ka ƙaraso, ɗaya bayan ɗaya su ka shiga buɗe warmers, wani irin daddaɗan ƙamshi ne ya daki hancinta har sai dai ta lumshe ido.


madaidaicin plate ɗaya daga cikin chefs ɗin ya ɗauka haɗe da serving spoon, abunda ya girka ya ɗiba ya zuba a plete ɗin,a gabanta ya ajiye mata, jinjina kai tayi tana kama hannun Aunty sophia dake tsaye kamar sauran masu chefs.

“please ki zauna mana” ta faɗa fuska a marairaice, girgiza mata kai Aunty sophia tayi
“kiyi sauri kici time na tafiya” ƙwaɓe mata fuska tayi
“kin san bana iya cin abinci ni kaɗai” ta faɗa a shagwaɓe
“baby kina da rigima”
“ni dai naji, idan kuma baza ki bani ba na tashi”


“kema kin san bazan so ki zauna da yunwa, kwantar da hankalinki” Aunty sophia ta faɗa tana jan chair ɗin dake kusa da wacce take zaune ta zauna, spoon ɗin dake cikin abincin ta ɗauka, a hankali ta shiga ɗibar abincin tana bata,har wani lumshe ido take da alama ya mata daɗi, ba ƙaramin farin ciki chef ɗin yayi ba ganin yanda take lumshe ido.


spoon biyu zuwa uku ta amsa ta kauda kai, fahimtar abunda take nufi ne yasa wani chef ɗin saurin matsowa, shima ɗibar wanda ya girka yayi kamar na farkon ya miƙama Aunty sophia, amsa tayi tana ture wacan gefe, shima spoon biyu zuwa uku tayi ta kauda, ɗaya bayan ɗaya masu aikin su ka shiga zuba na su suna ba Aunty sophia,abun gwanin ban sha'awa chefs ɗin ke kallon su kamar uwa da ƴa,a ƙalla taci kusan kala shidda kafin ta buƙaci da Aunty sophia ta bata lemu.


ɗaya daga cikin chefs ɗin ne ya tsiyaya mata lemu a wani haɗaɗɗen cognac balloon glass ya miƙama Aunty sophia, amsa tayi tana nufar bakin Nailarh da cup ɗin,sai da tasha kusan rabi tukun ta janye bakinta,tashi tayi ta nufi ƙofar fita daga dinning room ɗin, ajiye cup ɗin Aunty sophia tayi tabi bayanta.


gyaran dinning room ɗin chefs ɗin su ka shigayi da kansu, su Luna na ganin ta nufi bedroom ɗinta su kayi saurin bin bayanta, dakatar da su Aunty sophia tayi, badan sun so ba su ka dakata, kwata kwata basa jin daɗin yanda Aunty sophia ke hanasu Aikin su wani lokacin, shiyyasa su ka fi son madam na gidan ita bata shiga hurumin Aikin su duk da kuwa itace mahaifiyar Nailarh.


A tsakiyar bedroom ɗinta ta sameta
“muje ko baby” Aunty Sophia ta faɗa tana kama hannunta cikin nata, dressing room ɗin ta su ka nufa
“yau ke zaki shirya ni ne?”
ɗaga mata kai Aunty Sophia tayi dai dai lokacin da take tura ƙofar dressing room ɗin.


faskeken mirror dake ɗakin Nailarh ta nufa zama tayi kan ɗaya daga cikin chairs ɗin Aunty Sophia kuma ciki ta ƙarasa.

ɓangaren haɗaɗɗun suit ɗinta Aunty Sophia ta nufa,bata wani tsaya ruwan ido ba ta ɗauki mata wasu Black color,wurin underwears ɗinta ta nufa plunge and high waist bikini ta ɗauko mata suma Black color.


mirror ta nufa hannunta ɗauke da kayan
“tashi kisa” Aunty Sophia ta faɗa tana miƙa mata kayan dake hannunta,kallon kayan tayi haɗi da kallon Aunty Sophia
“kin san bazan iya sa kayan nan ba”


ɗan hararar ta Aunty Sophia tayi “saboda baki da hannu ko mi?”
“amma ai kin san bani ke sawa da kaina ba,kuma ki ka hana masu saman shigowa,tunda har ki ka hana su shigowa dole ki saman da kanki”


cikin muryar lallashi Aunty Sophia tace “my baby mi yasa kullum ki ke son maida kanki baya ne,ya kamata ace yanzu da kanki ki ke wasu abubuwan ko dan saboda gaba,ko so ki ke kiyi Aure a haka komai sai anyi maki,ki sani ba kowane namiji bane zai lamunci wannan sangartar taki ba”


“wa yace maki ni zanyi Aure?” Nailarh ta faɗa tana tsare Aunty Sophia da idanu,yanayin fuskar Aunty Sophia ne ya canza ta rasa mike damun Brain ɗin Nailarh kwata kwata bata tunani irin na mutane.


“kina nufin haka zaki tabbata?”
“ƙwarai ma kuwa,ni Aure baya ɗaya daga cikin tsari na,a taƙaice ma na tsani maganar shi” ta faɗa tana wani ya mutse fuska.


girgiza kai Aunty Sophia tayi
“please ko dan saboda ni ki daure kina wasu abubuwan da kanki”
“bazan iya ba!” ta bata amsa a taƙaice, marairaice fuska Aunty Sophia tayi “please Nailarh Aunty Sophian ki fa?”


“sorry Aunty Sophi bazan iya ba ne”
“shikenan,yanzu karɓi ki sa”
“bazan iya ba” ta sake faɗa,lallashinta Aunty Sophia ta shigayi Dan ta samu ta sa kayan da kanta amma fir taƙi amincewa,dan dole Aunty Sophia ta shiryata da kanta.


sosai kayan su kayi mata kyau abunka da farar fata sai ta fito a ainihin baturiyar ta, high hills masu shegen tsini Aunty Sophia ta ɗauko mata tare da wristwatch haɗe da earrings,da kanta ta saka mata wristwatch da earrings ɗin bayan ta ajiye mata hills ɗin a ƙasa,zura ƙafarta tayi a takalmin.


“baby kin yi kyau sosai” Aunty Sophia ta faɗa, murmushi Nailarh ta saki “thanks” locker ta ta nufa,ƙofar fita Aunty Sophia ta nufa tana faɗin
“baby zan jiraki a parlor” Bata tsaya jin mi Nailarh za tace ba ta fice.


murmushi Nailarh ta saki ta rasa miye matsalar Aunty Sophi da gun kwata kwata bata son kallon locker ta bare akai da abunda ke cikin ta,buɗe locker tayi ta ɗauki pistol,a ƙugunta ta soke ta tukun ta rufe locker.


jerin shades ɗinta ta nufa,Black color ta ɗauka ta zura a idonta,ficewa tayi daga dressing room ɗin, wayarta dake ajiye saman makeken gadonta ta ɗauka.


a parlor ta samu Aunty Sophia na jiranta,tunda suka shigo main parlor gidan masu aiki ke bin Nailarh da kallo baƙaramin tafiya da su wankan nata yayi ba.


russunawa suka shiga yi suna gaishe da ita,hannun kawai ta ɗaga masu,a jere su ka samu motocin da zata fita da su a compound, jiki na rawa security guard ɗinta suka shiga gaishe da ita,suma hannu kawai su ka samu ta ɗaga masu,har gaban motar da zata shiga ƙirar ACURA RDX black color Aunty Sophia ta rakata,da kanta ta buɗe mata back seat ɗin motar ta shiga ta rufe,ɗaga mata hannu tayi tana juyawa ta koma ciki.


A jere motocin su ka fice daga gidan,babban titin da zai fitar da su gaba ɗaya street ɗin su ka hau,suna karya wata kwana motocin su Joseph suka kunno kai,haɗewa su kayi da nata motocin su ka ɗauki babbar hanyar da zata sada su da ƙaton PORT dake RENO.


Tafiya su kayi mai ɗan nisa tukun su ka iso PORT,ƙaton port ne iya ganinka,ga manya manyan truck dake kai kawo ɗauke da containers,a parking lot ɗin dake port ɗin su kayi parking.


kusan a tare su ka buɗe cars door ɗin su ka fito,motar Nailarh securitys ɗin su ka nufa tare da Joseph,car door su ka buɗe mata ta fito,ya mutse fuska tayi tana kallon port ɗin kafin ta kai dubanta ga Joseph.


“ina containers ɗin su ke ne?” ta faɗa ganin tarin containers dake wurin ga wanda trucks ke ɗawainiyar ɗauka.

“sai mun fara zuwa office ɗin C G tukun”
“ok mi kake jira”
“sorry boss” ya faɗa yana ɗan rissinar da kai haɗi da nufar office ɗin CG ɗin dake cikin port ɗin,tsaki taja tana komawa cikin motar ta zauna,bata rufe door ɗin ba ƙafarta ɗaya a ciki ɗaya a waje.


Bayan kamar 5 minutes Joseph ya dawo tare da wani mutumin dake sanye da uniform white color hannunshi ɗauke da wasu takardu, bayansu matasan samari ne har su shidda suna sanye da overall orange color.


har gaban motar su ka ƙaraso, ƙarasawa Joseph yayi bakin door ɗin motar
“boss ga CBP nan,shine in charge na cargos ɗin”

zame shade ɗin dake fuskarta tayi tana kallon mutumin da tunda Joseph yayi magana yake washe baki
“ƙarasa” Joseph ya faɗa yana nuna mashi bakin door ɗin motar,ƙarasawa mutumin yayi,fuskarshi ɗauke da fara'a ya gaishe da ita cikin girmamawa.


glass ɗinta dake hannunta ta ɗaga mashi alamar amsawa, murmushi ya saki yana jin jina kai, takardun dake hannunshi haɗe pen ya miƙa mata
“CG ya sa hannu sai naki kawai ya rage”
yamutse fuska tayi tana karɓar takardun da yake miƙo mata, sign ta shiga yi a takardun ba tare da ta ko karanta abun da su ka ƙunsa ba.


miƙa mashi tayi tana faɗin “what next?”
“za muje ne kiga kayan”
“ba sai naje ba kawai su ɗauko” ta faɗa
“please madam ganin yanada amfani,kuma zaki shaida adadin containers nawa ne su ka iso”


yamutse fuska tayi tana zuro ƙafarta da nufin fitowa ringing ɗin wayarta ne ya dakatar da ita,jawo wayar tayi tana duba sunan mai kiran nata Sweetheart shine sunan daya bayyana a screen ɗin.


picking call ɗin tayi haɗi da kara wayar a kunnenta,fitowa ta yi su ka nufi cikin inda containers su ke,cike da shagwaɓa take waya da mahaifiyar ta ta data kira dan taji ya abun yake tafiya.


a gaban wani ƙaton container ship dake bakin ruwa, trucks na jidar containers su ka tsaya, Nailarh na can bayan su tana waya,nuna ma Joseph containers ɗin su da trucks su ka ɗauka har guda biyar yayi.


jinjina kai Joseph ɗin yayi
“aikin ka yayi kyau,fatan kayi waya da Madam?”
“eh tun kafin ma ku ƙaraso ta kira ni”
“ok good,muje ko” Joseph ya faɗa yana nufar Nailarh harta kammala wayar.


Juyawa tayi ta koma inda su kayi parking,motar ta shiga security daya buɗe mata ya rufe door ɗin,sallama Joseph yayi ma in charge ɗin ya shige motar shi, a jere su ka fice daga port ɗin trucks ɗin containers ɗin su na biye da su...


A jere su ka fice daga port ɗin trucks ɗin containers ɗin su na biye da su, wata hanya su ka ɗauka daban, tafiya su kayi mai ɗan nisa kafin su ka iso wani ƙaton orphanage, daga yana yin ginin zaka san cewa bana ƙana nan mutane bane,yanada girma sosai.


horn su kayi a bakin gate ɗin, can cikin bacci masu gadin orphanage ɗin su ka ji ƙarar horn ɗin, ba suyi mamakin jin horn da tsohun dare nan ba saboda mamallakan orphanage ɗin sun saba yi masu shigar dare irin haka.


ɗaya daga cikin securitys ɗin ne ya leƙo ta ƴar ƙofar dake jikin gate ɗin,kallo ɗaya yayi ma motocin ya fahimci ko su waye, a hanzarce ya koma ciki, gate ɗin ne ya shiga zugewa zuwa gefe guda, da gudu motocin su ka danna kai zuwa cikin orphanage ɗin,da sauri securitys ɗin su ka shiga motocin dake bakin gate ɗin su ka bi bayan motocin.


wasu irin gine gine na zamani su ka shiga wucewa ba laifi Orphanage ɗin yanada girma sosai, a bakin wasu manya manyan store har guda biyar su ka yi parking,fitowa su ka shiga yi daga cikin motocin su, wani matashin saurayi ne ya fito daga motar Joseph tun ɗazu sai yanzu ya fito,black American ne, neck ɗin shi yasha zanen tattoo kallo ɗaya zaka mashi ka gane riƙaƙen ɗan duniya ne.


motar da Nailarh ke ciki Joseph ya nufo, back seat ya buɗe mata, fitowa tayi a dai dai lokacin da securitys ɗin ke ƙarasowa, da sauri su ka nufeta, gaishe da ita su ka shigayi cikin girmamawa, ko arziƙin kallo basu samu daga gareta ba, trucks ɗin ta nufa umarnin a buɗe su ta bada,fitowa drivers ɗin su ka shigayi,kowace truk mutum uku ne su ka fito daga cikinta, babu ɓata lokaci su ka shiga buɗe bayan truck ɗin, wasu irin tarin kwalaye ne a bayan truck ɗin, da hannu tayima Joseph alama da ya zo, da sauri ya nufo in da take, wayarta ta miƙa mashi,da sauri yasa hannu ya amsa,video ya shiga ɗaukar kayan.


truck ɗayace ba'a buɗe ba kallon drivers ɗin tayi “wannan fa?” ta tambaya tana nuna masu truck ɗin, Joseph ne yayi saurin faɗin
“ina tunanin itace wacce madam tace kar a shiga da ita”

cike da bada umarni ta furta “ku buɗeta” da sauri Joseph yace “ba kuji ana magana” a hanzarce su ka shiga buɗe truck ɗin, wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi a lokacin da tayi arba da abunda batayi tunanin gani ba, da tsantsar mamaki take kallon matasan ƴan mata da samari dake bayan truck ɗin an rufe masu bakunansu yayinda hannayen su ke a ɗaure.


da sauri Joseph ya sauke wayar ƙasa, da mugum mamaki tashiga kallon drivers ɗin kafinta sauke idanunta akan Joseph, cike da tuhuma ta furta“miye wannan?”babu wanda ya iya buɗe baki a cikin su ya bata amsa, suma sun shiga ruɗan, sunyi matuƙar mamakin ganin yaran, wata irin gigitacciyar tsawa ta daka masu kamar ba Nailarh ba.


“tambayar ku nake miye wannan, ina aka samu wannan yaran??”
ɗaya daga cikin drivers ɗin ne yayi ƙarfin halin bata amsa “mu ma bamu sani ba kawai dai mun samu truk ɗin a cikin jadawalin da miss m...“ kasa ƙarasawa yayi saboda tsawar data daka mashi, bashi da tayima tsawar ba hatta Joseph sai da ƴan hanjin cikinsa su ka kaɗa.


gaba ɗaya fuskarta ta rikiɗe da tsantsar ɓacin rai, a fusace ta buɗe baki da nufin magana amma sai ringing ɗin wayarta ya dakatar da ita, da saurin Joseph ya miƙa mata wayar, picking call ɗin tayi ba tare da ta ko duba sunan mai kiran nata ba.


muryar mahaifiyarta ce ta daki dodon kunnenta daga cikin wayar “hello baby har kun kammala” saurin maida kiran tayi zuwa video call, back camera ta kunna ta saita wayar dai dai inda truck ɗin take.


“momy wannan container ta waye?” ta faɗa ranta a matuƙar ɓace, a kwance take saman hammock chair a bakin beach daga Ita sai bra da wani matsiyacin pant mai igiya gefe da gefe kusan rabin mazaunanta a waje,ta rufe idonta da baƙin shade hannunta a riƙe da coconut drink tana sha.


cike da bariki irin bata fahimci mi Nailarh take nufi ba tace “wace container baby?”
“wacce idanunki su ka nuna maki” ta bata amsa dai dai da tambayarta dan ba ƙaramin ɓaci ranta yayi da ganin yaran ba.
“sorry baby na manta banyi maki bayani ba,marayu ne basu da gata, gashi suna fama da wata lalura na turo su nan ne saboda suna buƙatar emergency treatment”


maida front camera tayi tana jifar mahaifiyarta ta da wani kallon rainin wayao
“amma momy kwata kwata yaran nan basuyi kama da patient ba kama suke da wanda a kayi kidnapping, momy ina ki ka samo yaran nan?” ta kai ƙarshen maganar babu alamun wasa


“baby kin fi kowa sanin mahaifiyarki ko dabba bazata iya sacewa ba bare mutum, ki yarda da ni yaran nan taimakonsu kawai nake son yi”
“idan taimakonsu ki ke son yi mi yasa baki turosu a Flight ba amma ki ka turo su a container bakunan su a rufe,mi hakan yake nufi?”

“ki yarda da ni baby taimakonsu nayi” ta faɗa cike da shagwaɓa kamar bada ƴarta take magana ba

“gaskiya banji daɗin yanda ki ka sa aka ɗaure su ba,kamar wasu dabbobi”
“sorry baby na amshi laifin hakan bazai sake faruwa ba, sorry” ta faɗa tana ɗan kama kunnenta, tsaki Nailarh taja tana rejecting kiran.


umarni ta bada akan su fito da yaran bayan ta tura securitys ɗin orphanage ɗin sun kira doctors ɗin dake hospital ɗin orphanage ɗin, ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fito da yaran sai layi su ke kamar za su kifa ƙasa da alama wani abun aka basu wanda ya gusar masu da hankalin su.


doctors da nurses dake ɗauke da stretcher ( gadon ɗaukar marasa lafiya) su ka ƙaraso wasu sun su sai hamma suke da alama daga bacci su ke, cike da girmamawa su ka shiga gaishe da Nailarh bata wani amsa masu ba ta bada umarnin a ɗauki yaran, babu ɓata lokaci su ka shiga ɗaukar yaran a gadon ɗaukar marasa lafiya suna nufar hospital ɗin, bayan su Nailarh tabi, ganin haka ne yasa Joseph bin bayan su.


cikin gaggawa likitocin su ka shiga ba yaran emergency treatment dan ganin sun dawo cikin hayyacin su, sun shafe awanni da yawa suna abu ɗaya sai da ƙyar su ka samu yaran suka farfaɗo amma sun gagara gane taƙamaimai abunda ke damun yaran.


kallon Nailar dake zaune saman waiting chair Joseph yayi, idanunta a lumshe bacci ne sosai a idonta amma saboda san ta san mike damun yaran taƙi tafiya gida, cike da tausasa murya joseph yace “boss ya kamata ki tafi gida ki huta”
“bazan tafi ba sai na san abunda ke damun yaran nan”
“am sorry boss, da dai kin tafi har yanzu bincike doctors ke yi kuma na san idan suka gama bincike har gida za su kawo maki result ɗin”

“kana ba kanka wahala Joseph babu in da zan tafi bansan abunda ke damunsu ba”
lallashinta ya shiga yi shida securitys ɗin amma babu wanda ta saurara a cikin su sai ma cewa tayi idan ba so suke suyi ta aikin su ba to karsu sake mata magana.


ganin dai da gaske ba amincewa za tayi ba ne yasa Joseph yanke shawarar kiran mahaifiyarta, number mahaifiyarta ya shiga dannanama kira amma ba tayi picking ba, canza akalar kiran yayi ga Aunty sophia, baiwar Allah tunda Nailarh ta fita bata rintsa ba, ta kasa zaune ta kasa tsaye hankalinta duk a tashe yake saboda inda Nailarh ta tafi, kiran Joseph na shiga wayarta har sai da gabanta ya faɗin, jiki na rawa tayi picking ko da ya sanar da ita dalilin kira ba ƙaramin kwanciya hankalin ta yayi ba.


“please bata wayar” ta faɗa, da sauri ya miƙa mata wayar“boss miss sophia na son magana dake” a hankali ta buɗe ido tana jifanshi da harara, saurin sadda kanshi yayi ƙasa, kauda fuska tayi gefe ba tare da ta amshi wayar ba, kara wayar yayi a kunnenshi “taƙi karɓar wayar” ya faɗa
“sata a speaker” shine kawai abunda Aunty sophia ta faɗa,ok ya furta yana sa wayar a speaker
“hello baby kina jina?” Aunty sophia ta faɗa


da wata kalar kasalalliyar muryar ta wanda bacci ke neman fin ƙarfinshi ta furata “Aunty sopei ”
“baby mi yasa baki son ki dawo gidan, kin san yanda hankali na ya tashi da fitar da ki ka yi, tunda ki ka fita ko bacci na kasa yi please ki dawo gida”


“zan dawo Aunty sopei kawai ina son na san abunda ke damun yaran”
“karki damu har gida doctor zai kawo maki result ɗin su kuma nayi maki alƙawarin tare da ni zamu zo duba su idan doctors sun kallama bin cike amma yanzu ki dawo gida”
“shikenan sai na dawo”
“yawwa ko ke fa keda na sanki babu ruwanki da shiga abunda bai shafeki ba?”
“ke ki ka fara koyaman damuwa da damuwar mutane” murmushi Aunty sophia ta saki da alama taji daɗin maganar Nailarh.


“sai kin dawo” da ok ta amsa mata, rejecting kiran Joseph yayi yana sauke ajiyar zuciya, harara Nailarh ta watsa mashi murmushi kawai ya saki, tashi tayi ta leƙa ɗakin da yaran suke kafin ta nufi ƙofar fita,har inda motocin su suke doctors ɗin suka rakata kafin sukayi mata sallama.


a guje motocin su ka fice daga orphanage ɗin, tun a hanya su ka rabu da su Joseph su kuma suka kama hanyar gida, Nailarh bata san sun iso gida ba saboda tun a moto bacci yayi awana gaba da ita, sai da Aunty sophia tasheta tukun ta san sun ƙaraso,fitowa tayi su ka nufi cikin gidan, direct bedroom ɗinta Aunty sophia ta nufa da ita, suna shiga ta faɗa kan bed ko takalman dake ƙafarta bata cire ba.


murmushi kawai Aunty sophia ta saki, da kanta ta shiga rage mata kayana jikinta, rigar suit ɗinta ta zame mata haɗe da earring ɗinta da wristwatch tukun ta zame mata takalman ƙafarta, idanunta ta sauke akan gun ɗin dake suke a ƙugunta har zata wuce sai kuma tasa gefen suit ɗinta ta zame gun ɗin, a cikin rigar ta naɗeta,dressing room ɗinta ta nufa, maida komai tayi a mazauninshi, a saman locker ta ajiye mata gun ɗin saboda bata san password ɗin locker ba kuma Nailar tafi amfani da eye I D, ficewa tayi daga dressing room ɗin ta koma bedroom ɗin, gyara mata kwanciya tayi kafin ta fice daga ɗaki baki ɗaya.


*ABUJA NIGERIA*


Nainarh da yumnah ne suka fito daga bedroom ɗin mom,less ne a jikin yumnah ɗinkin bubu ta yafa mayafi saman kanta yayinda Nainarh ke sanye da riga da skirt na atamfa hijab ne a jikinta saɓanin yumnah dake da gyale, hannunsu riƙe da na su Ammar, Aman da jamala da alama fita za suyi.


Part ɗin dady su ka nufa,da sallama a bakin suka shiga a parlor su ka sameshi shida mamy,ciki suka ƙarasa, kallo ɗaya mamy tayi masu ta ɗauke kai dady kuwa da fara'a sa yake kallon su, a saman rug carpet su ka zauna cike da girmamawa su ka gaishe da su dady kawai ya amsa masu amma mamy yi tayi kamar ma bata san da zaman su a parlorn ba.


“my friends sai ina haka?” dady ya faɗa yana kallon su Ammar, Aman ne ya bashi amsa da
“gidan papah” ɗaure fuska dady yayi “shine za ku fita ba tare da ni ba, kodai mun dai abotar ne ban sani ba?” jamal ne yayi saurin cewa “A'a ka tambayi Aunty Nainarh idan tace aje da kai shikenan” gaba ɗayan su suka kai duban su ga Nainarh da
kwata kwata hankalinta baya kansu tunda su ka shigo idanunta suka sauka akan wani ƙaton photo dake manne a bango,sosai ta shagala da kallon photon, tayi mamakin ranar da su ka shigo bata ganshi ba tunanin ta fara yi to kodai ba'a jima da sashi ba.


ɗan taɓo ta yumnah tayi “dady na magana” da sauri ta kai dubanta ga dady “Aunty Nainarh jamal yace sai kin amince za'a tafi dani, za kuje dani kuwa?” saurin sadda kai ƙasa tayi tana sakin murmushi, murmushi shima dadyn ya saki yana leƙa fuskarta “idan na fahimta wannan shirun alamace ta ba'a zuwa dani” da sauri ta ɗago tana faɗin “A'a dady zamuje da kai”


“wasa nake maku sai kun dawo ina gaishe da mutanen gidan”
tashi yumnah tayi tana kama hannun Nainarh
“za su ji in sha Allah, ku tashi mu tafi”sallama su kayi masu suka fice, taɓe baki mamy tayi tana kallon dady “wai ni kam Janar da sanenka wannan yarinyar take zaune a gidan nan?”
“wace yarinya kenan” dady ya faɗa yana kai duban shi gareta dan bai fahimci akan wa take magana ba


“wacce su ka fita yanzu da yumnah”
“wai kina magana ne akan Nainarh”
“ni ban ma san sunanta ba amma ita nake nufi”
“da sani na take zaune gidan akwai matsala ne?”
“ni gaskiya bana son zamanta a gidan nan”
“miye matsalar ki da zamanta a gidan yarinyar da ba'a kanki take ba”


“kamarya miye matsalata, gidan mijina ne fa,kawai sai mu zuba ma zulaihart ido tayi ta yin abunda taga dama, hakanan zata kwaso mana yarinya idan ta cutar damu fa??” tunda ta fara magana dady ya kafeta da ido tsantsar mamaki ne akan fuskarshi ko miye abun masifa kamar wacce ke jiran mutane
“ni gaskiya bana son zamanta gidan”
“ta kawo duk wanda zata kawo gidan mijinta ne kuma gidan ƴaƴan tanada ƴancin ajiye duk wanda ta so”


“haba Janar wai miyasa kullum kake fifita zulaihart a kaina ne, komai tayi dai dai ne a wajenka amma ni kuskure ɗaya zanyi ka ɗau mataki a kaina” ta faɗa rai a ɓace,mamaki yaƙi ɗaukewa akan fuskar dady lamarin mamy har tsoro yake bashi
“ni gaskiya bana son zamanta a gidan”
“to sai mi dan baki son zamanta a gidan, naga ba'a kanki take ba kuma gida gidana ne kuma ni na amince da zamanta dan haka bana son na sake jin kinyi tari akan Nainarh, idan ba haka ba ranki ne zai ɓaci”


“hakama za kace,kenan Zulaihart tafini?”

rai a ɓace dady yace
“Zulaihart tafiki komai mabaruka, ko ƙafarta baki kama ba, dan Zulaihart ban taɓa bata umarni ta saɓa man ba, Zulaihart bata man rashin kunya kamar yanda ki ke man,Zulaihart bata sa'insa dani,nayi mata cin mutuncin mafi muni a rayuwa amma haka nan tayi haƙuri dani take zaune da ni har kawo yanzu duk da a ƙasarta da Al'adarta bata saba ganin irin haka ba sannan ki sani Zulaihart ta fiki haƙuri mabaruka”


wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare zuciyar mamy, idan da abunda ta tsana a rayuwa taji ana yabo mom musamman dady abun na ɓata mata rai, rai a ɓace ta fice daga part ɗin gaba ɗaya, da kallo kawai dady ya bita.


Su Yumnah suna fita daga part ɗin dady ficewa su kayi daga gidan baki ɗaya,suna fitowa motar ya Naeem na kunno kai cikin parking space ɗin, ɗan dakatawa su kayi, daidaita parking ya Naeem yayi, kusan a tare aka buɗe car doors ɗin su fito,ya Naeem ne ya fito daga driver seat yayinda ya Adanan ya fito daga front seat.


Uniform ne a jikin ya Naeem yayinda ya Adnan ke sanye da suit back color, da gudu su Ammar su ka nufe su, hugging ɗin ya Naeem su kayi ɓata fuska ya Adnan yayi kamar ƙaramin yaro yana faɗin
“abun ƴar haka ce ya Naeem kawai ku ka sani, shikenan nima ai ga Autar dady nan” ya faɗa yana buɗema Yumnah hannayen shi, da sauri ta nufeshi tana sakin dariya, faɗawa tayi jikinshi tana hugging ɗin shi.


murmushi Nainarh dake tsaye ta saki, yaran mom na matuƙar burgeta Irfan ne kawai take ganinshi daban a cikin su kamar ya banbanta da su.


“dady mun fara gaishe da second father ne fa”Aman ya faɗa yana turo baki
“ba wani nan, bana dai yi daku, da Autar dady nake yi”

“ku rabu dashi kishi ne kawai” ya Naeem ya faɗa yana basu hannunshi suka tafa
“sai ina haka?” Ya Adnan ya faɗa lokacin da yake raba jikinsu
“gidan uncle Mustafa” yumnah ta bashi amsa
“a dawo lafiya muna gaishe da mutanen gidan”
“za suji in sha Allah”


kama hannun ya Adnan ya Naeem yayi yana faɗin “sai kun dawo” da sauri Nainarh ta gaishe da su ganin za su bar wajen,duban suka kai gareta
Murmushi ya Naeem ya saki “lafiya lau Nainarh, ya gidan” da Alhmdllh ta amsa mashi, ya Adnan tunda ya kafeta da idanu ƙala baice ba, duk tsawan wannan lokacin da Nainarh ta ɗauka bai taɓa ganinta ba in fact ma baisan wacece ba, ɗan taɓoshi ya Naeem yayi


“baka ji ana gaishe ka” washe mata baki yayi yana faɗin “lafiya” murmushi ta sakar mashi
“muje ko, Yumnah sai kun dawo” ya Naeem ya faɗa yana nufar ƙofar shiga gidan, ya Adnan kasa ɗauke idonshi yayi a kan Nainarh har su ka nufi motar Yumnah su ka shiga, yumnah har ta buɗe driver seat zata shiga yayi saurin jawo Arm ɗinta, bayan motar yajata.


da tsantsar mamaki take binshi da kallo, hannu yasa ya kauda fuskarta gefe “kin wani tsare ni da ido, tambayarki zanyi wacece waccan?” ya faɗa yana nuna cikin motar

“wai Nainarh?”
“sunanta kenan?”
“eh sunanta kenan, ɗiyar fa mom Asma'u ce” ɗan zaro ido waje ya Adnan yayi “amma ya akayi ban santa ba?”
“may be baka zuwa gidan ne”
“eh gaskiya bana zuwa, wajen mom ta zo?”
“ai ka san abunda ya faru da mom Asma'u to shine mom ta dawo da ita nan gidan”


“ok na tuna”murmushi Yumnah ta saki tana kallon fuskarshi
“na tafi?”
“idan kin tsaya wani abun za kiyi man ne?”
“ok sai mun dawo” ta faɗa zata bar wajen,muryar Noor ce ta dakatar da ita, da sauri su ka kai duban su ga Noor dake fitowa daga cikin mota,palazzo trouser ne a jikinta haɗe da shirt open shoulder,daga sama rigar ta kama jikinta sosai kusan rabin brest ɗinta a waje,ga wasu irin high hills masu shegen tsini tasa, ɗan siririn mayafi ne a saman kanta.


fuskarta da fara'a ta nufo su, tana ƙarasowa tayi hugging ɗin ya Adnan, saurin tureta yayi daga jikinshi rai a ɓace yace“wai Noor har sau nawa zance maki kidaina hugging ɗina, wai ke baki san cewa ni ba muharraminki bane akwai fa Aure a tsakanin mu” ɓata fuska tayi kamar zata fashe da kuka
“ya Adnan daga kawai nayi murnar ganinka”harara ya watsa mata yana kallonta tundaga sama har ƙasa


“yanzu dan Allah miye amfanin wannan suturar dake jikinki, yanzu mom Fatilah na kallonki ki ka fito a haka?”

cike da shagwaɓa tace
“miye aibun kayan dake jikina ya Adnan?”
“ban sani ba” ya faɗa haɗi da jan tsaki, bari wurin yayi gaba ɗaya ya nufi cikin gidan.


taɓe baki tayi tana kallon Yumnah “ina zaki na zo wajen ki?”
“kindai zo wajen ya Irfan kuma duk yau baizo gidanan ba”
“kefa banza ce wa yace maki wajen shi nazo, na zo gaishe da Mom ne”
“a haka?” Yumnah ta faɗa tana kallon kayan jikinta, ɓata fuska Noor tayi “wai miye matsalar kayan jikina ne?”


“ok bama kiga matsalar su ba, na so ace second father ki kayi hugging ba ya Adnan ba,da kuwa kin san matsalar kayan jikin ki”
“shikenan ni dai naji, ina zaki?”
“gidan Uncle Mustafa”
“kai Yumnah yanzu sai ki tafi duk da na zo?”


“eh mana saboda na san ba wajena ki ka zo ba, idan kuma kina zuwa to?”
“kin san halin mom Maryam ina zuwa zata rufeni da mashifa ita komai nayi rashin kunya ne”
“da gaskiyarta Noor kuma tana yi maki haka ne dan ki gyaru, ki zo muje kawai”


gyaɗa kai Noor ɗin tayi, motar Yumnah su ka nufa, back seat ta buɗe kusa da su Ammar tashiga Yumnah kuma ta buɗe driver seat, key Yumnah tayi ma motar
“sorry kinjini shiru ko,ga sister Noor nan ku gaisa” ta faɗa tana kallon Nainarh.


Juyowa Nainarh tayi “sannu, ya gida” da lafiya lau Noor ta amsa mata, gaishe da Noor ɗin su Ammar su kayi da fara'arta ta amsa masu tana tambayar “wane ɗan kasadar ne ya baku wayarshi?” ta faɗa tana kallon wayar dake hannunsu suna buga game

Aman ne ya bata amsa da
“ta Aunty Nainarh ce” taɓe baki tayi tana kai dubanta ga Yumnah

“sister Yumnah wai da gaske ya Irfan baizo ba, daga Villa nake fa can ma baya nan kuma sai kiran wayarshi nake bana samu”
“ni dama na san ba wajen mom ki ka zo ba”
“ni dai naji, dan Allah yana ina?”


“wallahi rabona da ganin ya Irfan tun jiya da muka dawo daga gidan Abbah, amma yau da safe naji sunyi waya da mom, ki gwada kiran ya Waseef na san dole suna tare”


“kin kawo shawara” ta faɗa tana zaro wayarta daga cikin Aljihun wandonta, Number Waseef tayi dialing, bugu biyu ya ɗaga


“hello Noor, ya ki ke ya gida?”
“lafiya lau ya Waseef, wai ina ka kaiman ya Irfan ne tun jiya nake faman neman number shi baya picking??”
“amma kin raina man wayo Noor wato nima na kai Irfan ɗin wani waje ko”
“eh mana” ta faɗa a shagwaɓe.


shiru taji baice komai ba, jin Waseef yayi shirune yasata faɗin “dan Allah yana ina?” muryar Irfan taji daga cikin wayar
“hello beb”

“haba ya Irfan ka san kuwa halin daka jefani ciki kuwa, sai kiraka nake bana samu dama jiya ka bani haushi shine ma ka kashe wayarka ko nayi duk abunda zanyi?”


“sorry Noor ba haka bane, kina a raina wani uzuri ne ya sani kashe wayata amma kiyi haƙuri, kina ina ne yanzu?”
“gajiya nayi da nemanka na zo gidan big dady ko zan sameka”
“ok kina can yanzu?”
“A'a mun fita tare da su Yumnah zuwa gidan Uncle Mustafa”


“sorry gani nan zuwa kinji”
“zan jiraka fa karka shanya ni?”
“karki damu zan zo kinji”
“ok sai ka zo”
“ok bye” ya faɗa yana rejecting kiran, ajiyar zuciya ta sauke tana turu wayar cikin Aljihun wandonta.


murmushi yumnah ta saki “gaskiya na kusa tona maku asiri keda ya Irfan kowa ya san abun da ke tsakanin ku” saurin kallonta Noor tayi
“ban gane abunda ke tsakanin mu ba?”
“zan fallasaku kowa ya san soyayya ku ke” ajiyar zuciya Noor ta sauke tana dafe saitin zuciyarta da “da kuwa kin kyauta min Yumnah dan na gaji da hiding ɗin da ya Irfan ke yi”


dariya Yumnah tayi “da ɗina dake fa Noor rashin kunya, yanzu ya Irfan na hiding amma ke so ki ke a faɗa ko, idan basu amince ba fa??”
“wallahi har poising zan iya sha idan har su kace za su rabani dashi” da wani mugun sauri Nainarh ta juyo tana kallonta dan kalamanta sunyi matuƙar bata mamaki.


murmushi ta sakar mata tana kashe mata ido ɗaya, saurin juyawa Nainarh tayi tana girgiza kai.

murmushi Yumnah ta saki
“za ki iya fiye da haka,dan na lura baki da hankali a kan ya Irfan”

“duk ma wanda yace maki inda hankali akan ya Irfan yayi maki ƙarya”
“Allah ya shirye ki” shine kawai abunda Yumnah ta ce yayinda take shiga compound ɗin gidan Uncle Mustafa, parking tayi
“Ameen idan da gaske ki ke” Noor ta faɗa tana fitowa daga cikin motar, girgiza kai kawai Yumnah tayi.


A tare Yumnah su ka fito ita da Nainarh, back seat Yumnah ta nufa tana buɗema su Ammar.
sojoji ne ta ko ina a harbar gidan, da gudu su Ammar su ka nufi ƙofar shiga gidan.


mom maryam na zaune a katafaren mai parlorn gidan su ka shigo da gudu su ka faɗa samanta har sai da ta ɗan tsorata
“wane mai son gamawa da duniya lafiya ne ya kawo man ku?” dariya su kayi suna faɗin “su Aunty Yumnah ne” da sauri ta kai dubanta ga ƙofar shigowa saboda sallamar su Yumnah da taji.


zambur ta miƙe tsaye tana rabka salati “innalillahi wa Innah ilaihi raji'un” wani irin mummunan faɗuwa gaban su Nainarh yayi da sauri su ka juya...
______________________________


Da sauri su ka juya suna kallon bayan su dan duk a tunanin su wani abu ta gani a bayan su.


“amma Allah wadaran naka ya lalace, yanzu ke Noor fatilah na kallonki ki ka fito haka ƙirji a waje, ubanwa zaki nunama ƙirji da ki ka fito haka” gaba ɗayansu su ka sauke ajiyar zuciya dan ba ƙaramin tsoro ta basu ba.


turo baki Noor tayi gaba“ni dama shiyyasa bana son zuwa gidan nan idan muzo”
“dama yaushe zaki so zuwa gidanan tantiriyar banza, wallahi Noor kiyi ma kanki faɗa kwata kwata wannan ba ɗabi'a bace mai kyau, kina zubar ma kanki da mutunci ne”
“haba Momy yanzu dan Allah miye laifin kayan jikina?”


baki mom maryam ta saki “shaiɗaniyar banza tambayata ma kike, kin wuce kinje ɗakin Kainart kin nemi kaya na mutuncin kin sa ko kuwa”
baki Noor ta turo gaba“ni gaskiya bazan sa wasu k...” bata ƙarasa ba saboda yo kanta da mom maryam tayi,ai kuwa babu arziƙi ta kwasa da gudu zuwa cikin gidan.

“mara kunyar banza ai dakin tsaya” ta faɗa tana nufar sofa data tashi ta zauna,dariya Yumnah da Nainarh su kayi suma suna samun wajen zama su ka zauna, cike da girmamawa su ka gaishe da ita, da fara'arta ta amsa masu tana tambayar mutanen gidan.


“suna nan lafiya sun ma ce mu gaishe ku”
“muna amsawa,wallahi ku riƙa yima yarinyar can faɗa tunda uwarta ta kawo ido ta sa mata, kwata kwata shigar da take bata dace ba, da wanan shigar sai ta rasa mijin Aure dan duk wanda ya san kanshi baizai kwashi wannan tarkacen ba, dan ni wallahi AHMER ya kwaso man mace irin wannan da sunan zai Aure sai nace ubanshi daga shi har ita”


dariya Yumnah ta kwashe da ita“mom itafa Noor zaman waje ne ya maida haka”
“ke ni dallah rabani,ku da kuke da alaƙa ta jini da turawa mi yasa baki shiga irin haka ƙarshen dai rashin kunya kenan ko, mi yasa Zulaihart bata zuba maki ido kina shigar da ki kaga dama ba,saboda ta san ciwan kanta”

murmushi kawai Yumnah tayi ta san da ace mom maryam ta san Irfan ke son Noor da ya shiga uku dan saita rabasu may be shima dalilin da yasa kenan yaƙi bari kowa ya sani.


“ku riƙa yi mata nasiha”
“insha Allah mom zamu riƙa yi mata”

“hakan shi yafi”
“mom ina papah?” a cewar su Ammar
“papah na wajen aikin, sai anjima zai dawo”
“Allah ya dawo dashi lafiya” da Amee su duka su ka amsa.

Noor koda ta shiga bedroom ɗin kwanciyart tayi saman bed ɗin ɗakin, wayarta tashi latsawa.


*Uncle Hashim's House*


Zaune suke a parlorn Uncle hashim Laatifa ce kawai babu, mom maimunatu na daga zaune saman sofa mai mazaunin mutum uku Balqis na kwance tayi pillow da laps ɗinta yayinda Uncle Hashim ke zaune saman
rocking chair hannunshi riƙe da jarida yana dubawa.


juyowa Balqis tayi tana fuskantar shi da ƴar shagwaɓa tace “dady wai har yanzu shiru maganar fara aiki na?”

“ayyah sorry my daughter, shaf na manta na faɗa maki munyi magana da ya mutallaf harma na bashi takardunki”
“na gaji da zaman gida ne”
“karki damu zuwa next week za kuyi interview”
“thanks u dady, momy nima na kusa fara fita aiki kamar Aunty Laatifa”
murmushi mom maimunatu ta sakar mata tana shafa gefen fuskarta.


“amma dady a wane hospital ya samar man aiki?”
“muna da wani hospital ne bayan namu?” ya faɗa ba tare da ya kalleta ba
“eh mana dady akwai S J Hospital, ni nafi son can”
“wane hospital ne S J”
“SAM Internati...” kasa ƙarasawa tayi saboda wani kallo da barrister ya watsa mata, dan dole ta shanye sauran maganar,maida hankalinshi yayi kan jaridar da yake dubawa yana jan tsaki.


taɓe baki mom maimunatu tayi “ni da wannan sama mata aikin da miji kasa su ka fitar ita da ƴar uwarta kayi masu Aure in yaso sunyi Aikin a ɗakin mazajensu”


“idan kin tashi Aurar da ƴarki babu wanda zai hanaki amma ni ƴata ba yanzu za tayi Aure ba”

“ban gane idan na tashi Aurar da ƴata ba, wai kai barrister har yanzu bazaka sauko daga dokin zuciyar daka hau ba ka yafe ma ƴarka?”

“bayan Balqis bana da wata ƴa a duniya, karki sake dangantani da ƴarki dan ranki ne zai ɓaci” tashi yayi yana kwashe Jaridar shi, juyawar da zaiyi yaga laatifa a tsaye bakin ƙofa kaf maganganunsu a kunenta, ɗauke kai yayi kamar ma bai gantaba ya nufi bedroom ɗinshi.


juyawa tayi da nufin barin wajen, da sauri Balqis tace“laa Aunty Laatifa yaushe ki ka dawo?” juyowa mom maimunatu tayi tana kallonta

“dawowata kenan ƙanwata, ya kike ya gida?” ta faɗa tana nufo cikin parlorn
“lafiya lau Aunty Laatifa” murmushi kawai Laatifa tayi mata tana nufar mom
“momy barka da rana ya gida?”
“lafiya lau Laatifa, harkin dawo?”


“eh mom,bari na shiga ciki na watsa ruwa duk a gajiye nake” ta faɗa yayinda take juyawa ta nufi bedroom ɗinta, da kallo kawai mom maimunatu ta bita fatan dai Allah yasa ba taji abunda Dadynta yace ba, Laatifa na matuƙar bata tausayi ta rasa miye matsalar barrister da bazai yafe mata ba.


bin bayanta Balqis tayi, lokacin da ta shiga ɗakin Laatifa har ta shige toilet mayafinta da briefcase ɗinta kawai ta samu a kan bed, wuri ta samu saman bed ɗin ta zauna.


tana shiga toilet ɗin tap ta kunna ta barshi hakanan kawai yana zuba a ƙasa,bakin bathtub ta nufa ta zauna,fashewa tayi da wani kuka mai ban tausayi, ta rasa wace irin zuciya dadynta gareshi da bazai iya yafe mata tsawan shekaru, tunani ta fara yi anya mahaifinta ne dan ta san babu wani uba da zai ƙyamaci ƴarsa kan laifi da baya da tabbaci,tasan da ace shiɗin mahaifinta ne bazai ƙyamaceta ba ko da kuwa abunda yake zargi gaskiya ne,shawara ta yanke anya baza tayi nesa dashi ba ko hakan zai sa ya yafe mata, sosai tayi nisa a duniyar tunani.


maganar Balqis ce ta dawo da ita cikin hayyacinta “Aunty Laatifa lafiya dai, tun ɗazu nake jiranki fatan dai lafiya” da sauri tayi mata gyran murya, jinjina kai Balqis ɗin tayi tana komawa mazauninta ta zauna,shaf shaf Laatifa ta watsa ruwa ta fito ɗaure da towel, murmushi Balqis ɗin ta sakar mata “inata jiranki”
“gani ai na fito, akwai labari ne?” Laatifa ta faɗa tana nufar dressing mirrow.


yanyin fuskar Balqis ne ya canza zuwa damuwa “dady ne wai dole sai a G J I hospital zai sama man aiki ni kuma na fi son S J I”
“to ni yanzu mi ki ke so nace, kawai kiyi haƙuri da in da yake son kiyi”
“haba Aunty Laatifa nazo wajenki dan ki bani shawara amma shine za kice haka?”

“to Balqis ya ki ke so nace kin dai san yanda nake da dady bare naje na roƙar maki shi, kawai kiyi haƙuri kiyi mashi biyayya”
“na san da haka,amma ai sai ki bani shawara”
“to wace shawara zan baki bayan wacce na baki?” Laatifa ta faɗa lokacin da take neman wurin zama kusa da Balqis ɗin ta zauna harta shirya cikin doguwar riga mai hannun Armless.


gyara zama Balqis ɗin tayi “kina ganin idan na sanar da big dady bazai sa dady ya amince ba?”
“too! ki gwada ki gani wataƙil ya amince”
“ni bana so naga baki bani ƙwarin gwiwa, so nake naji kince zai amince”
“to shikenan zai amince”
dariya Balqis ɗin ta saki “yawwa haka nake son naji kince” murmushi Laatifa ta sakar mata.


“yawwa Aunty Laatifa dama ina ta so na...” ringing ɗin tab ɗin Laatifa ne ya dakatar da ita, da sauri ta buɗe briefcase ɗin Laatifa ta ta ciro tab ɗin, jiki na rawa ta miƙa mata, amsa Laatifa tayi, murmushi ne ya bayyana akan fuskarta lokacin da tayi arba da sunan mai kiran nata, da sauri Balqis ta matso tana leƙen wayar,da tsantsar mamaki ta kalli Laatifa, ɗan tahalikin da kullum sai tayi maganar shi, yanzu haka maganar shi take shirin yima Laatifa sai ga kiran shi.

Wani irin annurin farin ciki ne ya bayya akan fuskar Balqis yau dai ga abunda ta daɗe tana jira
picking call ɗin Laatifa tayi, sai da tayi picking call ɗin tukun ta fahimci video call ne, amma tayi mamakin ganin duhu babu haske,ƴan dube dube ta shiga yi a wayar tana faɗin “Balqis bani glass ɗina”


da sauri Balqis ta buɗe briefcase ɗin tana miƙo mata glass ɗin,gyaran murya a kayi mata daga cikin wayar, da sauri takai dubanta ga wayar still duhu ta gani,wata irin zazzaƙar muryar ce ta daki dodon kunan su, in low voice aka furta “LAATIFA”

da sauri Balqis ta leƙa wayar amma sai taga babu kowa, murmushi Laatifa ta saki
“yau kuma ni ka ke ɓoye ma fuskarka SAM”
“ya ki ke?”shine kawai abunda aka furta mata maimakon bata amsar tambayar da tayi

“ina lafiya SAM, kwana biyu bana jinka, har saƙo na tura maka namayi tunanin baka gani ba?”
“i saw it already,ayyuka ne su kayi man yawa” Balqis sai sakin murmushi take, tama rasa inda zata sa kanta dan daɗi.


“ayyah,ya aikin?”
“Alhmdllh” ya faɗa
“masha Allah,ya su Uncle da su ALYAR?”
“suna lafiya” shiru ne ya gitta tsakanin su, gyaran murya yayi mata “lafiya ki ke dai,yana yinki kamar baki cikin walwala” murmushi ta saki tana faɗin “lafiya lau nake”
“ban yarda ba Laatifa, yanayin fuskarki ya nuna kamar kina cikin damuwa, tell me who touch u?” ya faɗa cike da tsantsar kulawa, wani irin sanyi taji a ranta tana matuƙar son yanda SAM ke nuna mata kulawa duk da basa tare,Balqis wani daɗi ne ya rufeta duk da ba ita ya nunama kulawa ba tana dai fatan ta samu kulawarshi fiye da yayarta.


“kinyi shiru, mike damunki?” saurin sakar mashi murmushi tayi “babu komai SAM lafiya lau nake,ban jima da dawowa daga wurin aiki bane,duk a gajiye nake”
“ok, idan ma akwai abunda ke damunki kiyi gaggawar sanar dani”
“in sha Allah, nagode sosai da kulawarka a gare ni” shiru taji bai tanka mata ba dama ta san ba tanka mata zaiyi ba.

SAM na matuƙar kula da ita, a duniya babu wanda take samun kwanciyar hankali da natsuwa gareshi irin SAM,duk damuwar da take ciki data sanar dashi zaiyi mata maganinta,ko momy bata bata irin kulawar da SAM ke bata duk da suna jimawa ba suyi waya ba,amma kullum ne akwai masu sanar dashi halin da take ciki musamman yasa masu bibiyar mashi rayuwarta, akwai kyakyawar alƙa a tsakanin su, tun suna yara Allah ya haɗa jininsu kaf yaran family babu wacce yake kulawa kamar Laatifa in fact ma ita kaɗai yake kulawa tana da wani matsayi a zuciyar shi,wani ɓangare na zuciyarta tunzurata take akan ta sanar dashi abunda ke faruwa tsakaninta da dady ta san zai sama mata mafita.


ganin tayi shiru ne yasashi yi mata gyran murya, da sauri ta kalli wayar “lafiya?” ya faɗa
“lafiya lau” ta faɗa tana karkata wayar zuwa fuskar Balqis dake wani noƙewa a bayanta,fuskarta ɗauke da murmushi tace
“SAM ka gane wacece wannan?” saurin sadda kai ƙasa Balqis tayi, wata irin kunyarshi take ji duk da bawai ganinshi za tayi ba, a hankali ta gaishe shi

“who is she” shine kawai abuda yace,yanayin fuskar Balqis ne ya canza tuni hawaye sun cika idanunta, yanzu duk yanda take dakon sonshi amma tashi ɗaya yace bai ganeta ba.

“Balqis ce fa ƙanwata, kana nufin ka mantata?” Laatifa ta faɗa
“i don know her,bye take care” yana faɗa yayi rejecting kiran, da sauri Balqis ta kifa kanta saman mattress, murmushi Laatifa ta saki tana dafa bayanta, kamar jira take Laatifa ta taɓata ta fashe da kuka, hankali a tashe Laatifa ta ɗago da ita
“Balqis lafiya ki ke kuka?” kuka sosai take kamar ƙaramar yarinya, lallashinta Laatifa ta shiga yi harta samu tayi shiru


“haba Balqis miye abun kuka a nan?”
“dole nayi kuka Aunty Laatifa, yanzu duk tsawan shekarun dana ɗauka ina sonshi amma yace bai sanni ba, taya ma zaice bai sanni ba bayan ni shaidace akan ya sanni”ta faɗa cike da takaici

“kiyi haƙuri abun babu daɗi,amma ta yiwu ya mantaki ne shiyyasa ya faɗi haka”
“amma Aunty Laatifa ya tsaya kiyi mashi bayani mana, amma kawai yayi rejecting saboda ko kallona baya sonyi”

“ba haka bane Balqis, kiyi mashi uzuri tsawan shekara nawa baya ƙasar ya isa ya manta da kowa tunda ba waya yake da ku ba,dan yayi rejecting ba wai dan saboda ke bane haka yake baya da son yawan magana ne, ko ni idan muna waya ya gaji da magana rejecting yake,kiyi haƙuri kinji” lallashinta sosai Laatifa tayi har ta samu ta kwantar da hankalinta.


*Queen Kainart💫*


Noor tunda ta shige bedroom ɗin Kainart bata sake fitowa har yamma tayi gashi har lokacin Irfan bai zo ba baikuma kirata ba.

Su Yumnah na parlorn tare da mom maryam fira su ke hankali kwance, mom maryam ba ƙaramin nishaɗi tasa su ba.


Uncle Mustafa ne ya shigo,Army trouser ne a jikinshi tare da farar shirt, da gudu su Ammar su ka nufe shi, saurin buɗe masu hannayen shi yayi yana sakin murmushi, ai kuwa gaba ɗayan su suka faɗa jikinshi,hugging ɗin su yayi cike da farin cikin ganinsu.

raba jikinsu yayi yana faɗin “yaushe ku ka zo gidan?”
“tun ɗazu, har munata jiranka”
ɗan zaro ido yayi “amma shine ba'a faɗa man ba, da na san zaku zo ai da ban fita ba” ya faɗa yana jan hannusu zuwa cikin parlorn.


“sai da nace Aunty Yumnah ta kiraka amma taƙi”
“kai Jamal bana son sharri yaushe ku ka ce na kira maku shi iye??” da sauri jamal ya ɓoye bayan uncle Mustafa,dariya su ka saki gaba ɗaya parlorn ganin yanda Yumnah ta haƙiƙance da kuma Jamal ɗin daya ɓoye bayan Uncle Mustafa.


“Aunty Yumnah kinyi laifi kuma dole na hukuntaki”
“wallahi ƙarya yake man dady, ni baice na kira ka ba” ta faɗa kamar zata fashe da kuka,murmushi mom maryam tayi “rabu da su kinji kowa ya san ƙarya suke”

“sai na hukuntata dole” Uncle Mustafa ya faɗa,turo baki Yumnah tayi tana dallama su Ammar harara
“in wuni dady” Nainarh ta gaishe dashi cike da girmamawa
“lafiya lau, ya gida”
“Alhmdllh” gaishe dashi Yumnah tayi, cike da kulawa ya amsa mata.


up stairs ya nufa bin bayan shi mom maryam tayi,da gudu su Ammar su ka bi bayansu dan sun san sai Yumnah taci mutuncin su saboda sharrin da Jamal yayi mata.

sun jima zaune a parlorn su kaɗai, tunda su mom maryam suka nufi sama ba su sake saukowa ba,fara kiran sallar magrib da akayi ne ya sa su ka tashi su ka nufi bedroom ɗin Kainart, a kwance su ka samu Noor har bacci yayi awan gaba da ita.


tashinta Yumnah tayi akan tayi sallah amma fir taƙi tashi da Yumnah ta dameta ma rufeta tayi da masifa akan ta ƙyaleta ita ba yanzu za tayi ba
“ke ki ka sani sai kita kwanciya idan Alkairi ce”
bathroom ɗin ɗakin su ka shiga su kayi alwala,Yumnah ta ɗauko masu carpet haɗe da hijab cikin wardrobe.

shimfiɗa masu tayi su kayi sallah, basu tashi kan sallayar ba sai da su kayi harda isha tukun, har time ɗin Noor bata tashi ba, babu ma alamun zata tashin.


duka Yumnah ta kaimata a bayanta “yanzu ai sai ki tashi mu tafi gida, idan kuma anan zaki kwana naji, wallahi kin dai san halin Mom maryam” tashi tayi tana wani hararar Yumnah,murmushi Yumnah ta sakar mata
“ai da kin kwanta” tsaki taja tana nufar ƙofar fita
“uncle dai na nan idan kuma haka zaki fita tom” dawowa tayi ta buɗe wardrobe ɗin hijab ta ɗauka har ƙasa tukun su ka fice.


A parlor su ka samu Uncle Mustafa tareda su Aman sai zuba mashi surutu su ke,gaishe da shi Noor tayi da kulawa ya amsa mata, bedroom ɗin mom maryam su ka nufa zaune su ka sameta saman sallaya tana lazimi.


“ban gane ba, na ganku tsaye?”
“tafiya za muyi mom dare yayi”
“sai ku jira kuyi dinner tukun”
“A'a mom idan muje gida za muyi”
“ke zanci mutuncinki Yumnah, sai kace wasu baƙi, ku wuce gani nan zuwa” ba dan sun so ba suka koma parlorn.


sai bayanda su ka yi dinner tukun su kayi masu sallama, har parking space mom da Uncle Mustafa suka rakasu.

“yaushe ni zaku zo man weekend kenan” a cewar Uncle Mustafa, Aman ne ya bashi amsa da “sai next weekend”
“Allah ya kaimu, zan jiraci zuwanku kuwa” haɗa baki su kayi wajen furta sai munzo, murmushi su ka saki, ƴar madaidaiciyar jaka mom maryam ta miƙama Yumnah.


“sai da safenku, ku gaishe mana da mutanen gidan”
“za suji in sha Allah mom”


ba su koma ciki ba har saida su kaga tafiyar su tukun.


Yumnah harta kama hanyar gidan Uncle mutallaf Noor tayi saurin cemata gidan big dady zata kwana, hakan yasa Yumnah kama hanyar gidan su, tun a mota Noor ta kira momynta ta sanar da ita nan zata kwana, babu yanda mom fatilah ba tayi ba ta dawo gida amma taƙi bakomai yasa bata son Noor ta kwana gidan ba sai dan saboda ta san part ɗin Mom zata kwana gashi kwata kwata basu jituwa da Mom.


Motar Yumnah na shiga harabar gidan Motar fa'iz na shigowa, kusan a tare su kayi parking,yazdan ne ya fara fitowa sai Fa'iz, jeans da t_shirt ne a jikinsu, yau babu laifi anyi shigar kirki saidai a buge su ke kamar koda yaushe,har wani gaba suke suna baya kamar zasu kifa ƙasa.


tunda suka fito su ka kafe motar Yumnah da ido har suka fito, tsaki Yazdan yaja yana faɗin “ca nake baƙi akayi ashe wannan tsamayen ne”
harara Noor ta watsa masu haɗi da murguɗa masu baki

“kaiii ashe yau zan daka wata yarinya, ke dama kin rainani ko?” A cewar Yazdan yana yo kan Noor ɗin kamar zai faɗi dama sun saba kusan kullum ne sai mom Fatilah ta rabasu, muddin su ka zo ƙasar basu barinta sakat kamar mage da ɓera haka su ke, sauƙi ma ɗaya Yazdan baya binsu shi yana Nigeria.


riƙo hannunshi Fa'iz yayi “ kai dalla rabu da ita, daga ina kuke haka?” Yumnah ta bashi amsa da “daga gidan Uncle Mustafa”

“soja marmari daga nesa ba” Yazdan ya faɗa yana saluting Fa'iz,kwashewa su kayi da dariya kamar wasu taɓaɓɓu.


su Jamal tunda su ka fito daga mota su kaga su Fa'iz su kayi saurin ɓoyewa bayan Nainarh, bala'in tsoron Fa'iz da Yazdan su ke,Nainarh itama hankalinta a tashe yake dan bata san haka su ke ba ko jiya a gidan Abbah lafiya lau ta gansu.


“kaiii wa kuke ɓoyemawa” Yazdan ya faɗa yana leƙen su Ammar daketa faman zare ido, yana layi ya nufo inda Nainarh take, wani irin duka gaban Nainarh yayi su Jamal kuwa yana ƙarasowa su ka fashe da kuka suna barin bayan Nainarh su ka nufi main entrance ɗin shiga gidan da gudu.


“kaga ƴan iskan yara” Yazdan ya faɗa yana riƙe baki,da sauri Fa'iz ya nufo inda suke, wani ɗan iskan kallon ya shiga watsama Nainarh,kamar za su faɗo mata shida Yazdan aikuwa jikinta ya hau rawa ga hawaye da su ka cika idonta “mutum ko Aljana?” Fa'iz ya faɗa yana nunata da yatsa, Yumnah ce tayi saurin ce mashi “ƙawata fa ce ya Fa'iz”


“ƙawarki, ina ki ka samu wannan kayan??” rai a ɓace Noor tace “haba dan Allah ya Fa'iz, duk kunbi kun tsoratata,ƙawar Yumnah ce fa” ta faɗa tana jan hannun Nainarh “yi haƙuri kinj, muje ko” da sauri Yazdan yabi bayan su “ke kin raina mutane ko?” saurin riƙo hannunshi Fa'iz yayi, tsaki taja tana jan hannun Nainarh suka shige gidan.


jakar da Mom maryam ta basu Yumnah ta ɗauka, bayan su tabi, part ɗin dady ta fara shiga ta sanar dashi sun dawo tukun ta fice, a bedroom ɗin mom ta samu su Noor su Jamal sun lafe a jikin mom,jakar dake hannunta ta ajiye haɗe da mayafinta.


“mom maryam na gaishe da ke”
“ina amsawa, kun barosu lafiya?”
“lafiya lau” Yumnah ta faɗa tana buɗe jakar data shigo da ita, chocolate ne kala kala haɗe da wasu expensive perfume masu daɗin ƙamshi, da sauri su Aman su ka nufota, saurin rufe jakar tayi.


“kun tsaya na baku ko” turo baki su kayi “to ba namu bane?”
“ko naku ne kunsan dai bazan tasa maku su gaba ba ku shanye su yanzu” ɓata fuska su kayi kamar za suyi kuka.


ɗiba tayi ta basu sannan ta rufe jakar “wannan sai gobe” ta faɗa tana ɗaukar mayafinta da jakar “kuzo muje ayi shirin bacci, mom sai da safe”
“a tashi lafiya” mom ta faɗa, ficewa su kayi daga ɗakin su duka, bedroom ɗin da suka koma tunda su Ammar su ka zo su ka nufa Noor kuma ta nufi na Yumnah.

tana shiga bedroom ɗin kayan jikinta ta rage ta faɗa toilet,bayan kamar 10 minute ta fito ɗaure da towel, dressing room ɗin Yumnah ta nufa, body lotion ta shafama jikinta haɗe da perfume, wardrobe ta nufa, ɓangaren PJ ɗinta ta buɗe,ƴar baby doll ta ɗauka sabuwa pink color mai haɗe da top.


rigar ta zura haɗe da top ɗin sai dai bata ɗaure igiyoyin ba, gaban rigar net ne sharara ana hangen jikinta,ribbon tasa ta ɗaure gashinta perfume ta sake fesama jikinta kafin ta fice, bedroom ɗin ta koma, kwanciyarta tayi ba tare da ta kashe bulbs ɗin ɗakin ba.


Parking Motar su suka yi a parking space ɗin gidan big dady, Waseef ne ya fito sanye da cargo pant haɗe da shirt yasa p_cap haɗe shade, Irfan ne ya fito daga driver seat,suit ne a jikinshi black color idanunshi a manne da baƙin shade.


ciki gidan su ka nufa, part ɗin dady su ka nufa, a bedroom ɗin shi suka sameshi har yayi shirin kwanciya mamy na daga gefen bed ɗinshi zaune har ta gama fushin, PJ ne a jikinta riga da wando,cikin girmamawa su ka gaishe da su, da kulawa su ka amsa masu har mamy na tambayar ya mutanen gidan, da lafiya lau su ka amsa mata.


“daga ina kuke a cikin daren nan” dady ya faɗa, Waseef ne ya bashi amsa da
“dinner bikin abokin mu”
“dinner yanzu?”
“eh dady”
“shikenan sai kun dawo, amma dan Allah ku kula kundaiga yanzu yanda zamani ya canza da mata da samari sun haɗu sai shashanci, dan Allah ku kula”
“In sha Allah dady, sai da safe”
“dare naƙarayi ku dawo, dan ma kun shirya ne yasa zan barku ku tafi”


“in sha Allah dady bazamu jimaba”
“shikenan sai kun dawo” sallama su ka yi mashi su ka fice.


bedroom ɗin mom su ka nufa harta kwanta,faɗa sosai tayi masu kamar wasu ƙananun yara kan mi za su fita yanzu cikin dare, haƙuri kawai su ka bata su ka fice,a bakin ƙofar bedroom ɗinta su ka rabu Irfan ya nufi ɗakin Yumnah saboda Noor tace mashi tana nan,parking space Waseef ya koma “kayi sauri fa kaga dare nayi” ok kawai Irfan ɗin yace mashi.


bakin ƙofar bedroom ɗin ya tsaya yana nocking amma shiru ba'a amsa mashi ba, gajiya yayi da nocking ɗin ya tura ƙofar ɗakin ya shiga, a kwance ya hangota saman bed ɗin idanunta a rufe tana jan numfashi a hankali alamar bacci.


ƙarasawa yayi bakin bed ɗin,kallon fuskarta yayi, baccinta take hankali kwance, murmushi ya saki yana shafa gefen fuskarta, motsi tayi kamar zata farka hankan da tayi ba ƙaramin tafiya yayi dashi ba, ya san da idonta biyu daya bani da ƙorafi.


a hankali ya duƙa yayi kissing forehead ɗinta ai kuwa ta buɗe ido dama idonta biyu kawai tayi kamar tana bacci ne ko nocking ɗin da yayi tana ji, sauri tashi yayi tsaye “dama ba bacci ki ke ba?”

“eh, ya Irfan wai mi nayi maka ka ke gudu na wannan time ɗin, ko dai bakayi farincikin zuwana bane??” ta faɗa a shagwaɓe

“nayi farincikin zuwanki mana”
“to mi yasa kake guduna” ta faɗa tana sauka daga saman bed ɗin ta nufo in da yake,faɗawa tayi jikinshi tayi hugging ɗin shi


“ko nayi maka wani laifi ne?” shafa bayanta ya shiga yi a hankali
“ba kiyi man laifin komai ba Noor, kawai wani uzuri ne ya riƙe ni”
“amma ai ba haka kake man ba duk muka zo, kofa zaman one hour ba muyi ba, a da da kake ɓata kowane lokacinka a tare da ni” tana a kwance saman ƙirjinshi take faɗar haka,cike da salon bariki take manna mashi ƙirjinta a nashi,hakan da take mashi ba ƙaramin jefashi a yanyi take ba,ɗago da kanta yayi yana kallon kyakyawar fuskarta,turo baki tayi kamar zata fashe mashi da kuka.


“kasan yanda nake ji kuwa saboda guduna da kake?” bai bata amsar tambayar da tayi mashi ba sai manne bakinsu da yayi waje ɗaya, ai kuwa da sauri ta kama tongue ɗinsa tana kissing dama abunda take so kenan,wasu irin hot kisses su ka shiga bama juna kamar za su haɗiye juna, cikin ƙanƙanin lokaci suka fita a hayycin su suna a wannan yanayin ne Nainarh ta faɗo ɗakin, Yumnah tace ta zo nan su kwanta kar a bar Noor ita ka ɗai.


wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi da sauri ta juya masu baya gabanta na wani irin duka kamar zai faɗo ƙasa, da sauri Noor ta tureshi tana faɗin Nainarh! , saurin kai duban shi yayi gareta,da gudu ta fice daga ɗakin...

______________________________


wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi da sauri ta juya masu baya gabanta na wani irin duka kamar zai faɗo ƙasa, da sauri Noor ta tureshi tana faɗin Nainarh! , saurin kai duban shi yayi gareta,da gudu ta fice daga ɗakin.


A jiyar zuciya suka shiga saukewa kamar wanda su kayi tseren gudu
“amma ba kince man ke kaɗai bace?” Irfan ya faɗa
“eh, ban san ya a kayi ta zo ba”

juyawa yayi ya nufi ƙofar fita,saurin kamo Arm ɗinshi tayi
“when zaka dawo,saboda kaifa zan kwana?”
“zuwa safe” ya bata amsa yana wani lumshe ido,gaba ɗaya jinshi yake a wani irin yanayi na daban ƙafarshi ma da ƙyar yake ɗagata
“shikenan saika dawo ka kula man da kanka” jinjina mata kai yayi ya fice daga ɗakin.


Ajiyar zuciya ta sauke tana kama igiyoyin rigarta ta ɗaure,switch ɗin ɗakin ta nufa ta kashe bulbs ɗin bedside lamps su ka kawo, kwanciya tayi saman bed ɗin,lumshe idanunta tayi tana jan iska haɗe da fesarwa,wani irin yanayi take ji a jikinta, kwata kwata ba taji kunyar ganinsu da Nainarh tayi ba sai ma haushin katse masu jindaɗi da tayi, tsaki taja tana gyara kwanciyarta.


Nainarh tana fita daga ɗakin da gudu parlor ta nufa tasan muddin ta koma bedroom ɗin da Yumnah take dole taji ba'asin abunda ya dawo da ita koma ta nufi ɗakin dan ganema idonta, a jikin pillar ta samu ta ɓuya, ajiyar zuciya ta sauke tunda take a rayuwarta bata taɓa jin haushin wani ɗan Adam ba kamar yanda take jin haushin Irfan da Noor a yanzu, ko wace irin taɓewace ta samesu haka,idan sun san suna son junansu danmi bazasu sanar da iyayen su suyi masu Aure ba amma zasu ɓige da neman juna ta ƙazamar hanya, ko basu san hakan babban zunibi bane, duk da take kallonshi daban da ƴaƴan mom batayi tunanin haka halayenshi su ke ba,a ido kamar mutumin kirki ko kunya basa ji yanzu da Yumnah ce ta shigo ta samesu da wane ido su ke tunanin zata kallesu.


wani irin tausayin mom da dady ne ya rufeta,mutanen kirki amma ƴaƴansu ke aikata laifuka irin haka,dady yafi bata tausayi ga Irfan ga Fa'iz mutumin ƙwarai mai riƙo da addini Allah ya jarabceshi da ƴaƴa haka, dama Allah baya barin bawansa haka ba tare da ya jarabashi ba ta hanya daban daban , ita kaɗai take sambatunta babu mai bata amsa.


tana a nan tsaye Irfan ɗin ya fito sai ƴan waige waige yake, harara ta watsa mashi kamar idanunta zasu faɗo ƙasa wani irin tsanarshi take ji a ranta,saida taga ficewarshi daga gidan tukun ta nufi bedroom ɗin ko ta kan Noor dake kwance bata biba ta juya mata baya itama Noor ɗin yi tayi kamar tana bacci.


A cikin mota ya samu Waseef har ya gaji da zaman jiranshi, yana isowa driver seat ya buɗe ya shiga kifa kanshi yayi, tunda yake a rayuwa bai taɓa jin kunyar dayaji ba yau, bai taɓa tunanin ko Yumnah ce ta ganshi zaiji irin wannan kunyar da yaji dalili ganin da Nainarh tayi masu, yayi fatan ace bata shigo ɗakin ba,damuwarshi yanzu da abun zata riƙa kallonshi za tayi mashi kallon mara kamun kai koma ta sanar da wani mussaman Yumnah.


dafa kafaɗarshi Waseef yayi
“lafiya dai?” ya tambaya
“babu komai” shine kawai abun da Irfan ɗin yace mashi
“Irfan indai irin wannan haɗuwar da kuke zata zama matsala mi yasa bazaka sanar da dady ba kana sonta,sai suyi maku Aure,bana son ku ƙetara in da bai kamataba, dan muddin ku ka cigaba a haka wata rana sai kunyi dakun sani mara amfani”


“bazan iya sanarda dady ba Waseef” Irfan ɗin ya faɗa ba tare da ya ɗago da kanshi ba
“bangane bazaka iya faɗa mashi ba, kana nufin ba sonta kake ba??”
“ina sonta mana Waseef, kawai dai bazan iya sanar da dady ba, lokuta da dama ko nayi niyyar sanar da wani a cikin su kasawa nake sai duk na rasa ƙwarin gwiwata”


“na fahimci sanar dasu ke baka wahala, ni ka bani dama na sanar da dady ko big dady nasan za suyi farin ciki da hakan”
“karka sanar da su nafi son suji a baki na”
“tayaya kenan?”
“zan sanar da su in sha Allah”
“shikenan, amma dai karka ja jiki” jin jina mashi kai Irfan ɗin yayi


“please kayi driving ɗin mu” Irfan ɗin ya faɗa yana ficewa daga motar, driver seat Waseef ya dawo shi kuma ya koma mazaunin shi dan a yarda yake jinshi zai iya watsar da su a titi, ba Noor bace damuwarshi Nainarh ce damuwarshi bai taɓa jin kunyar wani a rayuwarshi ba kamar yanda yake jin ta Nainarh yanzu,key Waseef yayi ma motar su ka fice daga estate ɗin baki ɗaya.


Heart of vegas su ka nufa saɓanin wurin dinner da su ka cema dady za su sun faɗin haka ne kawai dan su kare kansu,parking Waseef yayi,kusan a tare su ka fito shida Irfan ɗin su ka shiga ciki , a cike yake kamar kullum,third floor na club ɗin su ka nufa, wani irin ƙaton meeting room dake kusa da office ɗin Irfan su ka shiga,zungureren table ne mai ɗauke da chairs,manyan mutane ne su shidda a zaune a saman chairs ɗin zaman jiran Irfan ɗin kawai su ke, an cika masu gabansu da kayan sha kalar nasu na club, chair dake kallon duka chairs ɗin Irfan ya nufa ya zauna, Waseef ya zauna ata kusa dashi, system ɗin dake ajiye kan table ɗin ya buɗe haɗe da ɗaukar communicative device, yasa a kunnenshi.


gabatar da meeting suka shiga,cike da natsuwa Irfan yake gudanar da komai duk da baya da gogewa akan abun sai dai mubarak na taimaka mashi ta hanyar Bluetooth,sun shafe kusan Awa biyu a ɗakin meeting ɗin kafin su ka kammala around 2am


*WASHE GARI*


Ana kiran sallar farko ta farka hakan al'adarta ce tun tana gidan su, kallon Noor dake kusa da ita tayi, baccinta take hankali kwance, sauka tayi daga saman bed ɗin ta nufi bathroom, Alwala ta ɗauro, bakin bed ɗin ta dawo tashin Noor ta shiga yi, nauyin bacci gareta da ƙyar ta samu ta farka.


“ki tashi lokacin sallah yayi” ya mutse fuska Noor ɗin tayi tana juya kwanciyarta
“ki sani wannan baccin bashi da amfani,idan kin kammala sallah kina iya dawowa ki cigaba da baccinki”


“kiyi taki kawai zanyi” Noor ɗin ta faɗa, gyaɗa kai kawai Nainarh tayi, dressing room ɗin Yumnah ta nufa, kayan jikinta ta canza zuwa doguwar riga,bedroom ɗin ta dawo hannunta ɗauke da hijab da carpet, shimfiɗa carpet ɗin tayi, hijab ta zura a jikinta ta kabbar sallah, harta kammala raka'atanil fijir tayi sallah ta zauna tana azkar Noor bata tashi ba, mamakin momy Noor ne ya kamata, wace irin uwace ita da har ƴarta ke wasa da Sallah irin haka bata tsawatar mata ba, ta san da ace mahaifiyarta na kula da tarbiyarta da duk hakan bai faru ba a ganinta sakacin mahaifiyarta ne ba laifin Noor ɗin, Allah sarki ita lokacin da tana tare da iyayenta kullum mahaifinta sai ya tabbatar da ta tashi domin yin sallah yake nufar masallaci hakama mahaifiyarta bata yin sallah sai ta tabbatar da taga tashinta tayi Alwala tukun take komawa nata ɗakin tayi sallah.


wata irin kewar iyayenta ce ta kamata musamman mahaifinta a irin wannan lokacin tana part ɗin shi yana ɗora mata karatu, duk asubar duniya sai ya zaunar da ita ya bibiyi karatunta na islamiya ya koya mata abunda bata gane ba, rayuwa kenan yanzu bata da wanda zaiyi mata hakan kowane farin ciki na rayuwarta ya tarwatse.


saurin ɗago da kanta tayi dalilin dafa kafaɗarta da aka yi, Yumnah ta gani tsaye a gefenta
“lafiya ki ka zuba uban tagumi da asubar fari?”

ƙaƙalo murmushi tayi “ba komai” gyaɗa kai Yumnah tayi tana nufar dressing room ɗinta

“sister Yumnah ina ta so na tambaye ki?” Nainarh ta faɗa, juyowa Yumnah tayi tana fuskantar ta
“ina jinki?”
“wai babu islamiya ne a Estate ɗin nan?”
“akwai mana,kina so ne?”
“eh, amma mi yasa ke baki zuwa” ɗan ya mutse fuska yumnah tayi

“da ina zuwa na bari”
“saboda mi?”
“haka nan kawai”
“ya kamata ace kina zuwa, shifa karatun addini ba'a gamashi”
“zan koma amma sai idan da ke”

“karki damu,da zan samu ma wanda zai koyaman harda asuba ina so”

“in dai kina so zanyi ma dady magana, da yana koyaman na bar zuwa”
“ina so kuwa”
“shikenan idan munje gaishe shi sai nayi mashi magana”
“nagode sosai”

murmushi Yumnah tayi mata tana shigewa dressing room ɗin.

Sai da gari yayi haske sosai tukun su ka nufi part ɗin dady a zaune su ka same shi a parlor saman rug carpet,hannunshi riƙe da Qur'an yana karatu kamar kullum, zama su kayi har ya kammala, gaishe da shi su ka yi cike da kulawa ya amsa masu.


“dady dama Nainarh ke son zaka riƙa biya mata karatu da asuba” Yumnah ta faɗa, kallon Nainarh dady yayi fuskar shi a ɗan ɗaure
“shine ba zaki iya tambayata ba har sai kin sa Yumnah?”
duk sai taji kunya
“A'a dady, kayi haƙuri”
“gaskiya banji daɗi ba nima mahaifinki ne zaki iya tambayata duk abunda ki ke so”
“kayi haƙuri”
“karki damu,duk lokacin da ki ka kammala sallah ki zo zan koya maki gwargwadon abunda na sani”


“in sha Allah dady, nagode” kallon Yumnah yayi
“Auta yanzu ko kunya ba kiji ba?” saurin sadda kai ƙasa tayi tana susar kai
“ai harda ni ba ita kaɗai ba” girgiza kai kawai dady yayi, sallama su ka yi mashi su ka fice.


tunda su Nainarh su ka shigo Mamy take laɓe tana sauraronsu,wani irin haushin Nainarh ne ya sake kamata,ji tayi kamar ta fito ta shaƙi wuyanta gani take kamar neman samun gindin zama ne da neman shiga wurin dadyn yasa ta ƙirƙiro da wai tana son dady ya koya mata karatu.


tsaki taja tana fitowa parlorn, ko kallon in da dady yake ba tayi ba ta fice.


*A fter some days*


Nainarh tun ranar da su ka yima dady magana kullum da asuba sai sunje ya ƙara masu karatu ita da Yumnah,islamiya ce kawai basu fara zuwaba sun bari sai wani weekend ɗin saboda school,Noor da su Ammar tun washe garin ranar su ka koma gida,Nainarh da Yumnah ne su ka maida su Ammar gida harda Jamal.


*UNITED STATE*


_*Las Vegas (Nevada)*_


A zaune suke a saman wasu haɗaɗɗun chairs dake katafaren garden ɗin gidan,Nailarh ta miƙe ƙafafunta saman ɗan madaidaicin table yayinda system ɗinta ke ajiye saman laps ɗinta tana operating fuskarta ɗauke da murmushi,hot pant ne a jikinta haɗe da ƴar shirt da bata wuce cibiyarta ba, Aunty sophia na daga gefenta zaune hannunta riƙe da mug ɗin coffee.


kallon fuskar Nailarh dake ɗauke da murmushi Aunty sophia tayi da alama ba ƙaramin nishaɗi take samu a tattare da system ɗin ba
“da alama yau kina cikin farin ciki,ko zan iya sanin abunda yayi dalilin sa wannan kyakyawar fuskar taki farin ciki?” Aunty sophia ta faɗa


ƴar dariya ta saki tana ɗaukar mug ɗin coffee dake ajiye kan table ɗin,sai data ɗan kurɓa tukun takai dubanta ga Aunty sophia

“ba komai yayi silar shigata wannnan farin cikin ba sai wasan da zamu gabatar a N R T ranar sunday, na samu ƙarin ƴan wasa daga California,abunda yayi matuƙar burgeni da ƴan wasan, details ɗin dawakan su da su ka turo, ji da kansu yayi matuƙar ƙyatar dani, a tunanin su canza tarihin N R T abu ne mai sauƙi sai dai basu san samun dokin da zaifi KING zimma da karsashi abu ne mai matuƙar wahala” ta faɗa cike da alfahari


Murmushi Aunty sophia ta saki tana ajiye mug ɗin coffee dake hannunta “baby na lura kina matuƙar ji da kanki kema,karki manta ba kullum mutum ke nasara ba,anyi gwaraza tun talataini kuma sun shuɗe,duk yanda ki ke ji da kanki akwai wanda ya fiki kuma dole a samu wani wanda zai karya tarihin N R T, kullum ke ke hawa akan mutane kema dole a samu wani wanda zai zama sama da ke”


wani irin kallo Nailarh ta jefa mata “Aunty sophia mi yasa ki ke faɗa man haka,kina baƙin ciki da nasarar da nake samu ne?” saurin girgiza mata kai Aunty sophia tayi

“ba haka bane baby,kawai ina son kisan cewa a rayuwa ba kullum mutum ke samun abunda yake so ba”

“please ki daina faɗa man haka raina ɓaci zaiyi”
“sorry ban faɗa maki haka dan ranki ya ɓaci ba,ina maki fatan nasara kamar ko da yaushe”


murmushi Nailarh ta saki “ko ke fa,da za ki ɓata man farin cikin da nake ciki,a round 5 pm jirgin momy zaiyi landing a airport”

yanayi fuskar Aunty sophia ne ya canza zuwa tsantsar damuwa,ba dawowar mahaifiyarta ta bane bata so ba, yana yin da take jefa Nailarh ne bata so
“ya dai Aunty sophia” Nailarh ta faɗa ganin yanyin da Aunty sophia ta shiga
“ban manta ba,yanzu nake shirin tashi na duba chefs, kema ya kamata ki ajiye aikin nan ki shirya dan kije airport ɗaukota”
“yanzu zan kammala”


“ok,bari na shiga ciki” Aunty sophia ta faɗa tana ɗaukar mug ɗin coffee da take sha ta nufi cikin gidan,direct kitchen ta nufa chefs ɗin ta fara dubawa har sun kusa kammala aikin dinner da suke,ficewa tayi daga kitchen ɗin ta nufi part ɗinta dake kusa dana ma'aikatan gidan,a corridor ta tsaya,wayarta ta zaro daga cikin Aljihun rigar dake jikinta.


dialing wata number tayi,kiran har ya katse ba'ayi picking ba,maida wayar tayi cikin Aljihun rigarta ta koma kitchen.


Nailarh tana kammala aikin da take part ɗinta ta nufa shaf shaf masu aikinta su ka shiga shiryata ko sanda Aunty sophia ta shigo ɗakin har ta kammala shirinta
wani kallo Nailarh tayima Aunty sophia “dama ba tare dake zamu je ba?”
“eh Nailarh sai kun dawo” taɓe baki Nailarh tayi tana ɗaga kafaɗarta, ficewa su kayi daga ɗakin har compound Aunty sophia ta rakata sai da taga ficewarsu daga gidan tukun ta koma ciki.

Masu aikin ta fara dubawa saida ta tabbatar komai na tafiya yanda ya kamata kafin ta wuce part ɗinta, a bakin corridorn ɗazu ta tsaya number ɗazu ta sake dialing yanzu ma har kiran ya katse ba'ayi picking ba yanke shawarar turama number saƙo tayi, a hanzarce ta shiga typing message, da harshen Spanish take rubutun hakan yasa ban san abunda take rubutawa ba,tana tura message ɗin tayi saurin maida wayar Aljihun jin alamar kamar mutum a bayanta, saurin kai dubanta tayi bayanta.


ganin ba kowa ne yasata sauke ajiyar zuciya ƙofar part ɗinta ta buɗe ta shiga ina saurin na shiga dan na gane mana nida ku masu karatu amma tayi saurin murza key dan dole na tsaya a bakin ƙofa.


A round 5 pm agogon U S jirgin su yayi landing a katafaren Airport dake garin,Nailarh a zaune take ita da maƙarabanta saman waiting chairs.


Passengers ne su ka ɓullowa ta ƙofar da aka tanada domin su, momy Nailarh ce ta ɓillo a sanye take da suit black color sun bi shape ɗin jikinta, tana da diri sosai kamar matashiyar budurwa,ta rufe kanta da scarf idanunta a manne da baƙin glass,hannunta a riƙe da trolleynta, da gudu Nailarh ta nufeta securitys ɗinta na biye da ita a baya, sakin trolley dake hannunta tayi tana buɗe mata hannayenta, Nailarh na ƙarasowa ta faɗa jikinta, hugging ɗinta tayi tightly, murmushi securitys ɗin su ka saki ba Nailarh ba kawai suma sunyi matuƙar farin cikin dawowar miss MALIKA,raba jikin su tayi,kissing lips ɗin Nailarh tayi hakan ba ƙaramin ƙyatar da securitys ɗin da mutanen dake wurin tayi ba.


wani irin narkakken murmushi su ka sakar ma junansu wanda ke nuna tsantsar kewar juna da su kayi, hannun Nailarh taja da sauri securitys suka shiga rissinawa suna gaishe da ita,cike da kulawa ta amsa masu,trolley ta su ka ɗauka, in da su ka yi parking motocin su suka nufa Nailarh da miss Malika na gaba yayin da securitys ɗin ke take masu baya,Nailarh sai wani narke mata take a jiki tana zuba mata shagwaɓa kamar ba ita ba.


back seat ɗin motar da za su shiga securitys ɗin su ka buɗe masu,sai da Nailarh ta shiga tukun ta zagaya ɗayan side ɗin ta shiga,rufe ƙofar securitys ɗin su kayi,motocin su ma su ka shiga haɗi da yi masu key su ka fice daga airport ɗin.


matsowa tayi kusa da ita, kwantar da kanta tayi saman shoulder ɗinta a hankali ta furta “well come back home” ƙyataccen murmushi miss Malika ta saki tana shafa gefen fuskarta “thanks u baby” kafe juna da ido su kayi kamar za su haɗiye juna, ta cikin mirror drivern dake driving ɗin su ke satar kallon su ba ƙaramin birge shi su kayi ba, suna matuƙar mamakin wace irin soyayyace a tsakanin uwannan da ƴarta, nima dai abun ya fara ɗaure man kai. ⁉


sosai su ka shagala da kallon juna har su ka ƙaraso gida ba tare da sanin su ba,buɗe masu car doors ɗin securitys ɗin su kayi,ficewa su kayi da sauri securitys ɗin dake compound su ka shiga gaishe da ita cike da girmamawa, fuskarta da fara'a take amsa masu,cikin gidan su ka nufa a main parlor su ka samu gaba ɗaya maids ɗin gidan harda Aunty sophia, sun ja layi kamar masu jiran umarni.


cike da girmamawa su ka shiga gaishe da ita suna mata barka da dawowa,cike da tsantsar kulawa take amsa masu, ba ƙaramin farin ciki tayi ba na ganin ma'aikatanta cikin ƙoshin lafiya, murmushi tayi tana kallon Aunty sophia “na sameki lafiya, fatan babynah bata baki ciwan kai” murmushi kawai Aunty sophia ta yi ba tare da tace komai ba, murmushi itama kawai ta sakar mata.


part ɗin dake kusa da na Nailarh su ka nufa,a bakin ƙofar shiga ɗakin su ka dakata suna sake mata bangajiya ko wacce ta kama gabanta,ciki su ka ƙarasa ita da Nailarh da maid ɗin data ɗauko trolleyn ta,part ɗin ya haɗu iya haɗuwa kusan komai dake part ɗin Nailarh akwaishi a nan, a katafaren bedroom ɗinta suka yada zango,dressing room ɗinta maid ɗin ta kai mata trolley tukun ta fice.


“ki zauna mana baby” ta faɗa tana kallon Nailarh dake tsaye ta riƙe ƙugu, fuska a ya mutse Nailarh tace “zanje bedroom ɗin na,kina buƙatar hutu”
“please baby ki tsaya tare dani”
“zan dawo” ta faɗa tana nufar ƙofar fita ba tare da ta jira amsarta ba, girgiza kai kawai miss Malika tayi tana sakin murmushi.


Nailarh na ficewa daga bedroom ɗin part ɗinta ta shiga, Aunty sophia na daga dinning room ta hangi wucewarta, tana shiga bedroom ɗinta kayan jikinta ta rage da kanta,toilet ta nufa, bayan kamar five minute ta fito sanye da bathrobe, bedroom ɗinta dake can kusa da swimming pool ta nufa, a saman bed ɗinta ta kwanta, lumshe idanunta tayi kamar mai bacci.


can cikin baccin daya fara fisgarta taji kamar ana shafa jikinta, ya mutse fuska tayi ba tare da ta buɗe idonta ba ta san bazai wuce ita ba ce, dama da wuya ta iya kwanciya ba tare da ta biyota ba.


“why baki kwanta kin huta ba?” ta faɗa yayinda take buɗe idanunta da suka fara canza launi saboda baccin daya fara fisgarta, a kan miss Malika ta sauke idanunta, ƴar baby doll ce a jikinta, iya karta gwiwarta,shara shara rigar take ana hangen komai na jikinta muraran.

“baby kema kinsan bazan iya kwanciya ba tare da ke a kusa da ni ba”
“please ki tafi,ai nace maki zan dawo”
“baby ai Baki dawo ba hasalima kwanciya ki ka yi,fushi ki ke dani ne har yanxu?”
“mom..” Bata ƙarasa ba tayi saurin rufe mata Baki da tafin hannunta
“dont call me momy,call me sweetheart” ta faɗa tana wani marairaice mata fuska
ɗan rintse Ido Nailarh tayi haɗi da zuƙar iska ta fesar “ki tashi ki tafi ɗakin ki zan zo na same ki”
“baby please ki barni a nan,ko na minti ɗaya bana so nayi nesa dake,wai ke ko ba kiyi kewata bane??” ta faɗa kamar zata sa mata kuka.


“nayi kewarki,amma ki tafi zan zo”
“wai saboda mi ki ke korata ne,idan saboda yaran nan ne please kiyi haƙuri bazan sake maimaita kuskure irin wannan ba”
“nace maki bana fushi dake kuma nayi kewarki kawai I need space”

fashe mata da kukan shagwaɓa tayi kamar wata yarinya “baby ba bu in da zanje,ina nan a tare da ke,kawai dan kin ga na damu dake shine za kiyi man haka” ta faɗa yayinda take sa hannu ta shiga warware igiyar bathrobe ɗin dake jikin Nailarh,zuba mata Ido Nailarh tayi tana kallonta,kashe mata Ido ɗaya tayi yayinda ta gama warware igiyar,manne bakinta tayi Dana Nailarh.


Hot kisses ta shiga bata a gaba ɗaya ilahirin jikinta,tun Nailarh bata biye mata har abun yayi tasiri a jikinta,dama tana da matsananciyar sha'awa wanda idan abun ya motsa mata komawa take kamar mahaukaciya musamman idan Bata samu abunda take so ba,idan tana a cikin irin wannan yanayin hatta ma'aikatan gidan tsoron tunkararta su ke dan kowa tana  iya kai mashi farmaki a wannan yanayin.


Cikin ƙanƙanin lokaci su ka fita hayyacin su,baka jin komai sai sautin breath ɗin su dake tashi sama sama,murzar juna su ke basa ji basa gani,gaba ɗaya sun fice a hayyacin su.


*Queen Kainart💫*


Gajiya tayi da zaman jiran fitowar su, ganin lokacin yin dinner ɗin su na neman wucewa ne yasa ta shiryama miss Malika nata taba Luna ta kai mata ɗakinta,ita kuma ta shiryama Nailarh nata,ganin taga wucewarta part ɗinta ne yasa bata haɗe masu waje ɗaya da Malika ba.


A faffaɗan tray ta shiryamata harda banana ice cream ta haɗa mata sanin tana matuƙar sonshi,a bakin ƙofar bedroom ɗin Nailarh ta dakata,madannan dake jikin ƙofar ta Danna,nan take ƙofar ta buɗe,kutsa kai tayi ciki,ta ɗan yi mamakin ganin Nailarh bata bedroom ɗin amma sai tayi tunanin ko tana ɗaya daga cikin bedrooms ɗin nata ko bathroom.


Table ɗin dake tsakiyyar Arm chairs ɗin dake ɗakin ta nufa,sautin breathing ɗin mutanan da taji ne yasata dakatawa,saurin kai dubanta tayi ga glass door ɗin bedroom ɗin,dan daga nan take jin sautin,wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi, a lokacin da idanunta su ka nuna mata Nailarh da miss Malika Babu mai sutura a jikin shi,idanunsu sun rufe basa ji basa gani, sakin tray dake hannunta tayi ba tare da saninta ba gaba ɗaya dinner data haɗa mata ya zube a ƙasa glass cup ɗin dake kai ya fashe.


A buɗe miss Malika ta bar ƙofar lokacin data shiga hakan ne ya bata damar jin sautin su,saurin kauda idonta tayi jikinta na wani irin kakkarwa kamar wacce sanyi yayi ma mugun kamu,ko ƙarar faɗin tray da fashewar glass cup ɗin basu jiba saboda basa cikin hayyacin su.


jiki na rawa ta duƙa ta shiga kwashe abincin da ya zube da cup ɗin daya fashe tana zubawa a tray,garin sauri har yankarta glass yayi amma Bata damuba saboda hankalinta a tashe yake,ba yau ta saba ganin su ba amma yau abun yayi matuƙar ɗaga hankalinta data San Malika na ɗakin da Babu abunda zai shigo da ita kwata kwata bataga lokacin data wuce zuwa part ɗin ba.


da sauri ta fice daga ɗakin har tana haɗa hanya, kitchen ta nufa da dishes ɗin,da mamaki chefs ɗin ke kallonta ganin kayan dake hannunta a fashe ga jikinta dake kakkarwa.


“lafiya miss Sophia?” ɗaya daga cikin chefs ɗin ya tambaya,cikin rawar murya tace masu bata jin daɗi ne,kanta ke mata ciwo sannu su ka shiga yi mata,ajiye trayn tayi ta fice da sauri, da kallo kawai su ka bita har ta ɓacema ganin su.


a corridor part ɗinta ta tsaya,fashewa tayi da kuka mai ban tayi tausayi,bata taɓajin tausayi Nailarh irin na yau ba, tayi fatan ace ita ta haifeta ba Malika,kwata kwata Nailarh ba tayi dace Uwa ba, ta gurɓata rayuwarta gaba ɗaya.


Nailarh tunda ta kai kimanin shekaru 14 a duniya mahaifiyarta ke nemanta,tana amfani da pills wajen ganin ta gusar mata da hankali dan ta biya buƙatar ta da ita, tun Nailarh na gudun abunda take mata har ta koma tana jin daɗin abun,yanzu abun har ya zame ma Nailarh lalura idan abun ya motsa mata fita hayyacinta take idan ba ta samu abunda take so ba,a lokacin da Aunty Sophia ta gane ta tausaya ma Nailarh matuƙa takuma yi ƙoƙarin ganin ta ganar da miss Malika illar dake cikin hakan amma sai ta nuna mata ƴarta ce ba abun da ya shafeta bane, tana kai shekara 18 ta fara koya mata kula da club da Casino da su Joseph ke kula da su amma sai ta maida Nailarh,tunda ya koma ita ke kula dasu sai su Joseph su ka koma masu taimaka mata, a lokacin ran Aunty sophia yakai ƙololuwar ɓaci harta kasa haƙuri ta samu Malika a karo na biyu ta sake nuna mata illar sa rayuwar Nailarh a wannan tsarin kawai zata kashe mata rayuwar ne, a lokacin cin mutuncin na gidan duniya babu wanda Malika bata yima sophia ba amma hakan baisa ta daina faɗa mata gaskiya ba daga ita har Nailarh, ganin ta dage ne yasa Malika yima sophia barazanar korarta daga aiki ,da farko Aunty sophia bataƙi tabar aikin ba saida tayi tunanin taga idan kuma ta bar gidan wa zai faɗa mata gaskiya wa zai taimaki rayuwar Nailar, tana matuƙar son Nailarh da tausayinta hakan yasa tayi haƙuri ta fasa tafiya,taja bakinta tayi shiru amma abun na damunta kullum cikin yima Nailarh adu'a neman kuɓuta daga sharrin mahaifiyarta take.


ta jima a tsaye a nan, idanunta har sun kumbura saboda kukan data sha,ƙofar part ɗinta ta buɗe ta shiga.


A wannan yanayin bacci yayi awanta gaba da su, sun shigema juma kamar za su koma abu ɗaya.


sai around 11 pm su ka farka, miss Malika ta fara farkawa dalilin baƙar yunwar data addabeta tun a cikin bacci, kallon Nailarh dake kwance saman jikinta tayi, ta shige jikinta sosai ta kanainayeta kamar wani yace zai ƙwace mata ita.


A hankali ta shafa gefen fuskarta tana kiran sunanta,instead of ta tashi sai ma shake shigewa jikinta da tayi
“please baby ki tashi muyi dinner 11 tayi, idan mun kammala sai ki koma ki cigaba” maƙe mata kafaɗa Nailarh tayi
“ban jin yunwa”


lallashinta ta shiga yi da ƙyar ta samu ta tashi, toilet ta nufa da kallon Malika ta bita tana wani langwaɓar da kai, sai da ta shigewar Nailarh toilet tukun ta tashi ta fice bayan ta ɗauki rigarta ta maida.


Part ɗinta ta nufa itama wanka tayi ta shirya cikin PJ riga da wando, part ɗin Nailarh ta koma bayan ta gama shiryawa,a zaune ta samu Nailarh bakin bed bathrobe ce a jikin yanzu ma, tayi shiru kamar mai nazarin wani abu.


Zama Malika tayi kusa da ita
“baby lafiya?” ta faɗa tana ɗaura hannunta saman bayan Nailarh, ajiyar zuciya ta sauke “ba komai”
“ok tashi muje muyi dinner” ta faɗa tana tashi haɗi da jan hannun Nailarh su ka fice zuwa dinning room.


duk da kasancewar dare ne sosai chefs ɗin nan ba su tafi makwacinsu ba saboda rashin fitowar su yin dinner.

kujera tajama Nailarh ta zaune tukun itama ta zauna kusa da ita, babu ɓata lokaci chefs ɗin su ka shiga serving ɗin su,kallon chefs ɗin Nailar tayi “ina Aunty sophi?” ɗaya daga cikin su ne ya bata amsa “ta tafi part ɗinta bata jin daɗi ne”
“mike damunta”
“bamu sani ba gaskiya, amma dai tace kanta ke mata ciwo” yanyin fuskarta ne ya canza duk sai taji wani irin jin Aunty sophia ba lafiya, ta damu da ita sosai.


fatan samun lafiyar sophia Miss Malika tayima masu aikin,da kanta ta shiga ba Nailarh abincin a baki har su ka kammala,tattara dinning room ɗin chefs ɗin su ka shiga yi, Nailarh ta so zuwa part ɗin sophia ta dubata amma miss Malika tace ta bari sai da safe.
Chapter 2 · 0% Book details