Gabatarwa
Shiryayyar Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 176 min read
𝑃𝑒𝑟𝑓𝑒𝑐𝑡𝑙𝑦 𝑝𝑒𝑛'𝑠..... ✍💫
🎀
_*🔥🔥SHIRYAYYIYAR ƘADDARA 🔥🔥💫*_
_*Season one*_
_*FREE*_🔥
*_KING AND QUEEN WRITING CHAMBER_*🤴 👸
𝑄𝑢𝑒𝑒𝑛 𝐾𝑎𝑖𝑛𝑒𝑟𝑡..... ✍💫
𝑇ℎ𝑒 𝑤𝑟𝑖𝑡𝑒𝑟 𝑜𝑓 𝐷𝑜𝑐𝑡𝑜𝑟 𝑆ℎ𝑎𝑧𝑖𝑚 𝑎𝑛𝑑 𝑛𝑜𝑤 𝑠ℎ𝑖𝑟𝑦𝑎𝑦𝑦𝑎𝑟 𝑘𝑎𝑑𝑑𝑎𝑟𝑎
_*Episode 1_2*_
_*Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ma ɗaukakin sarki mai kowa mai komi da ya bani ikwan rubuta wannan littafi.*_
_*Ya ubangiji al'arshe kabani ikwan rubuta abin da zai amfani muslinci da muslmai, ka bani ikwan rubuta abun da zai amfaneni duniya da lahira 🙏*_
❌❌❌❌❌❌❌
_*Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na littafin nan ba ta kowace hanya ba tare da an nemi izni a wurina ba.*_
_*idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi min haƙƙina!*_
_*Wannan labari ƙagegen ne ,sannan ban rubuta shi ba da niyyar muzanta wani ko cin zarafin wani ba, duk wanda ya ga wani abu yayi shige da halayyar shi to arashi ne ba da nufi ba*_.
*A big big hug to Khadija Sabi'u yahaya A.k.a Nainarh kd Nkds*
*special thanks to Ameenatu Muhammad Yakasai A.k.a oum Yasmeen the writer of Binta ƴar jagaliya*
_*Dedicated to my family*_
*@Kainaat1733*
*Wattpad*
_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ_
1:30 am
*Sydney,Australia*
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
______________________________
Can cikin bacci taji ana nocking window ɗakin da su ke,a hankali ta buɗe idanuwanta da su kayi mata nauyi.
sake nocking ɗin window a kayi, gabanta ne ya ɗan faɗi dan duk a tunanin ta a mafarki ne taji nocking ɗin ba gaske ba.
jin an dage da nocking ɗin ne yasa tayi saurin kallon gefanta, baccin shi yake shara abun shi hankali kwance, magidanci ne da a ƙalla zai kai kimanin shekaru 60 a duniya,baƙi ne kyakyawan gaske matar dake gefan shi itama zata kai kima nin shekaru 46 zuwa da 8 a duniya.
fara ce kyakyawa ajin farko, kai tsaye idan ka kalleta ba zaka ce zata kai kimanin wannan shekarun ba.
ɗan bubbuga pillow da yake kwance ta shiga yi tana kiran sunan shi cikin muryar raɗa
“ranka ya daɗe! ranka ya daɗe!!” a ƙalla sai da ta kira sunan shi kusan sau uku ba tare da ya farka ba still ba'a fasa nocking ɗin da ake yi ba.
ƙara sautin kiran sunan shi tayi cikin harshen hausa take faɗin“dan Allah ka tashi, inajin fa babu lafiya yau a ɗakin nan” ko gezau baiyi ba gashi wanda yake nocking yanzu ƙoƙarin buɗe window yake ta ƙarfin tsiya ya shigo.
cikin muryar kuka ta fara haɗa shi da Allah akan ya tashi
“dan Allah yallaɓai ka tashi , babu lafiya”
can cikin baccin shi yaji shashekar kukan ta, firgigit ya faraka, jin dai da gaske kukan take ne yasa shi tashi da sauri yana faɗin“lafiya mi yasa ki ku ka??”
window ta nuna mashi cikin yin ƙasa da murya tace“wani ke ƙoƙarin shigowa ta window” duban shi ya kai ga sliding door dake ɗakin,wacce mutum idan yaje gabanta ko ya buɗe zai iya hangen cikin garin sydney da harabar hotel ɗin.
zuro ƙafar shi yayi daga kan bed ɗin ya sauko wurin window ya nufa, ɗan saurarawa yayi,bugun windowa yaji anyi da ƙarfin gaske can yaji sautin kukan mace cikin harshen turanci tana faɗin“please open the door, help please!”
ɗan ja da baya yayi yana mamakin wacece kuma mi ya kawo ta window ɗakin su duk yawan ɗakunan dake cikin hotel ɗin tarasa in da zata zo sai na su, banda zare ido babu abunda matar dake zaune kan bed take.
ƙara ƙarfin kukan tayi da dukan window tana cigaba da faɗin“please help me,open the door please”
shahada kawai yayi ya nufi window, hannu yasa ya yaye curtain ɗin dake jikin window,matashiyar baturiya ce ya gani tsaye da uban ciki haihuwa yanzu ko anjima,da ƴar madaidaiciyar jaka rataye a kafaɗar ta, a ƙalla zata kai kima nin shekaru 25 a duniya.
fuskar ta sharkaf da hawaye idanunta sunyi jawur hakama hancinta da kumatunta, kyakyawa ce ajin farko tana da manyan idanuwa da tsayayyen hanci har baka sai ɗan ƙaramin baki mai ɗauke da red lips tana da tsayi dai dai misali.
baƙar duguwar riga ce a jikinta, har ƙasa rigar ta kai mata, ta rufe kanta da mayafin rigar.
ganin yayi shiru ya zuba mata idano ne yasa ta sake fashewa da wani kukan tana sake roƙon shi da ya taimake ta.
tasowa matar dake zaune kan bed tayi ta nufo bakin window, kallon baturiyar dake tsaye tayi daga sama har ƙasa.
“yallaɓai mu taimake ta” ta faɗa tana kallon mijin nata dake tsaye.
hannu yasa ya buɗe door, kamar jira take ya buɗe da mugun sauri ta shigo cikin ɗakin kamar zata faɗin,sakin jakar dake rataye a kafaɗar ta tayi, da sauri matar ta taro ta tana faɗin ki kula cikin harshen turanci.
kamata tayi har zuwa cikin ɗakin, jakar data yarda mutumin ya ɗauka yana bin bayan su,sofa da ke ɗakin su ka nufa, zaunar da ita tayi, a gefanta ya ajiye mata jakar, nufar wani ɗan table dake ɗauke da robar ruwa da cup matar tayi, ɗaukowa tayi ta dawo wurin sofar.
tsiyaya mata ruwan tayi a cup ta miƙa mata, hannunta har rawa yake wurin amsar cup ɗin, kallon mijinta dake tsaye matar tayi wani irin tausayin baturiya ne ya kamasu daga gani ba ƙaramar wahala tasha ba.
da sauri ta dafe ƙaton cikinta tana ɗan rintse ido da fatin “Auch, oh my god”
ƙoƙarin miƙewa take saboda wani ciwan mara daya taso mata lokaci guda, da sauri matar ta ajiye cup ɗin hannunta sannu ta shiga yi mata tana sa hannu ta taro ta.
ƙara baturiya ta fasa tana faɗin matar ta kaita toilet,matar kamar zata fashe da ku ka ta kalli mijinta tana faɗin“haihuwa ce za tayi”ɗan zaro ido yayi
“ya za muyi kenan?”
“nima ban sani ba, da ace a gida muke ina da komai da zamu buƙata”
“haka ne, yanzu babu wani taimako da za ki iya yi mata?”
“akwai sai dai su kasan basa son haihuwa a gida sai a hospital”
“yanzu tana a wannan halin ina ruwanta da inda zata haihu, tunda dai Allah yasa ke dr ce kawai kiyi mata abun da ya dace”
“shikenan”matar ta faɗa,barin wurin mijin matar yayi ya koma can nesa da su sosai.
tai makon gaggawa matar ta shiga bata, banda kuka da kiran sunan mahaifiyar ta babu abun da baturiyar nan ke yi.
sannu matar ke mata tana bata haƙuri, ba ƙaramar azaba baturiyar ke sha ba matar na iya bakin ƙoƙarin ta ganin ta taimake ta.
mijinta ma dake can nesa da su adu'a yake tayi Allah ya sauƙeta lafiya.
wahala sosai take sha gashi har yanzu haihuwar sai a hankali, barin wurinta matar tayi ta nufi mijinta fuskarta duk tayi jagajaga da hawaye
“yallaɓai ina tunanin dole fa sai mun kaita hospital”
“saboda mi?”
“nayi iya yanda zanyi amma haihuwar sai tazo sai ta koma”
“dr yanzu ya zamuyi?, kinga nan ba ƙasarmu bace fita da ita daga cikin hotel ɗin nan haɗari ne, gashi daga gani yana yin data shigo wani ne ya biyota, kuma na san wanda ke binta duk in da yake yana nan cikin hotel ɗin”
“to yanzu ya za'ayi kenan?”
“shine nima ban sani ba”
“ko zaka nemi alfarma wurin dr mark sai yazo da nurses su dubata”
“anya dr kina ganin barin wani ya san halin da ake ciki ba zai jaza matsala ba kinga nan ba ƙasar mu bace kada daga timako mu jefa rayuwar mu cikin haɗari”
“to yallaɓai ya ka ke so muyi?”
ko rufe baki matar ba tayiba kukan jariri ya cika ɗakin da mugun sauri ta juya ta koma can cikin ɗakin, a durƙushe ta samu baturiyar nan riƙe da jaririya a hannu ga wata sabuwar naƙuda da ta taso mata.
da sauri matar ta nufeta tana amsar jaririyar dake hannunta, towel ta ɗauka ta lulluɓe jikin jaririyar ta kwantar da ita saman sofa a hankali,gaban baturiyar ta dawo tana mata sannu haɗi da bata taimakon daya dace,ko minti ɗaya ba'ayi ba ta sake santolo wata jaririyar fara ƙar da ita kyakyawar gaske kamar wacce ta fara haihuwa sai dai wannan bata numfashi kwata kwata babu alamun rai a tattare da ita.
da sauri matar ta karɓi yarinyar ta shiga jujjuyata,kusa da ƴar uwarta daketa tsala kuka ta matsa ta kwantar da ita,ɗaukar mai ran tayi ta shiga goge mata jikinta bayan ta gama ta gogema ɗayar jikin itama,baturiyar tana daga in da take durƙushe ta kafe kyawawan yaran nata da kallo fahimtar ɗaya bata numfashi ne yasa ta tashi a hankali ta nufi jariran,shafa fuskar yaran ta shigayi can kuma ta fashe da kuka tana tambayar matar bata da rai ne.
jinjina mata kai matar tayi hawaye na bin kumatunta dan ba ƙaramin tausayi baturiyar ta bata ba,kuka sosai baturiyar ta fashe dashi matar na lallashinta har ta samu tayi shiru.
ɗaya bayan ɗaya matar ta shiga da yaran toilet ta wanke su a cikin jakar da mahaifiyar tasu data shigo da ita kayan jarirai ne harda su teddys,wasu riga da wando na saƙa farare ta sama yarinyar,gawar kuwa lulluɓeta tayi da farin towel ta kwantar saman sofa kusa da ƴar uwarta,taimaka ma mahaifiyar tasu tayi zuwa toilet danta gyara jikinta,ruwa ta haɗa mata da duk wani abu da zata buƙata tukun ta fice daga toilet ɗin ta bata wuri,cikin ɗakin ta dawo ta gyara wurin kamar wani abu bai faru ba sannan ta nufi wurin jariran,ɗaukar jaririyar daketa faman kuka tayi ta nufi mijinta ta miƙa mashi, hannun biyu yasa ya amshi jaririyar
“masha Allah, Allah ya rayata” ya faɗa
“Ameen,ƴaƴa biyu ne sai dai ɗayar ba ta zo da rai ba”
“Allahu Akbar, Allah ya raya mata wannan ɗin”
“Ameen”
“mahaifiyar ta su fa?”
“Alhmdllh ta haihu,tana toilet ma yanzu haka”ta bashi amsa
“masha Allah, amma ya ki ke ganin za muyi da ita duba da yanda ta shigo gashi kuma time ɗin tafiyar mu na ƙurewa?”
“yanzu dai mu bari ta fito na sake duba lafiyarta sannan sai mu tambayeta daga ina take”
“shikenan ba damuwa” amsar jaririyar tayi daga hannunshi
Zama su kayi kan sofar dake kusa da su
“yallaɓai yarinyar kyakyawa ce ina ma ace ni na haifeta”
murmushi yayi yana kallon fuskar matar ta shi“da kuwa munyi farin cikin da bamu taɓa irin sa a ruyuwar mu ba”
“da sai mun tara shagali irin wanda ba'a taɓayi ba a duniya ko da a finafinai da littafi”matar ta faɗa tana sakin murmushi da shafa kumatun jaririyar, shima mijin shafa kumatun yarinyar yayi da fara'a a fuskar shi.
“yallaɓai dan ma ba kaga ɗayar ba,kyakyawa ce itama ta ƙarshe da ka ganta kaga ƴar uwarta sai dai tafi kama da mahaifiyar su kamar an tsaga kara”
“zan so kuwa na ganta”
sun jima a nan zaune suna jiran fitowar mahaifiyar jaririyan daga toilet amma su kaji shiru har lokacin bata fito ba
“yallaɓai anya lafiya?, naji shirun nata yayi yawa”
“haka ne gashi time na ƙure ma na, ko za kije ki dubata?” tashi matar tayi ta miƙa masa jaririyar da tayi shiru tayi lamo a hannunta.
tun kafin ta ƙarasa bakin ƙofar toilet ɗin gabanta yayi wani mugun faɗi, fara fahimtar a kwai abun da ke shirin faruwa ko ma ya faru tayi, ba ta sake tabbatar da hakan ba sai da taga babu gawar jaririyar data bari,da ƙarfi ta ƙwala ma mijinta kira
“yallaɓai!yallaɓai!!” ta kira sunan shi har sau biyu, a hanzarce ya iso in da take , sofa ta nuna mashi da sauri ya kai dubansa zuwaga sofa amma sai yaga ba komai
“mi ya faru ne?”
“babu gawar jaririyar” ta faɗa cikin rawar murya tana zare ido
“to ina mahaifiyar tasu?”
“tana toilet”
“to kila ita ta ɗauketa”
“anya kuwa?” ta faɗa tana zaro ido
“fara dubata ki gani tukun” a hankali tayi nocking ƙofar toilet ɗin shiru taji, sake nocking tayi nan ma shiru taji babu almun mutum,deciding tayi ta tura ƙofar toilet ɗin ta shiga kawai, tura ƙofar tayi ta shiga wayam taga toilet ɗin ba kowa kamar ma ba'ayi amfani da shi ba, gabanta ne yayi wani mummunan faɗuwa da sauri ta fice tana ambaton Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.
“lafiya?” mijin ya tambaya da alum ruɗu
“ba kowa,bata ciki” ta bashi amsa bakinta na rawa
“ya salam, to ina ta tafi?”
“nima ban sani ba” dube dube su ka shiga yi cikin ɗakin wai ko ta shiga wani wuri har bakin window data shigo mijin matar ya nufa yana leƙa wajen ko ta nan ta fita amma bai ga alamun ta nan ta fita ba, hankali su ne yayi ƙololuwar tashi.
“yallaɓai anya matar nan ba aljana bace?”
“wane irin aljana ana zaman lafiya”
“idan ba aljana ba, taya za ace ta fita bamu sani ba kuma da yarinya a hannunta”
“koma dai minene zama nan bai kama mu ba,mu haɗa kayan mu kawai mu tafi Airport dama lokacin tafiyar ya gabato dan hankalina bai kwanta da wannan lamarin ba”
mijin ya faɗa yana kwantar da jaririyar dake hannun shi saman sofa sai a sannan ya lura da ƴar guntuwar takarda da wani ɗan madaidaicin teddy bear a jikinshi an rubuta mommy a kan sofa.
da sauri ya ɗauki takardar ya duba rubutu ne a jikin takardar cikin harshen turanci, fara karantawa yayi da sauri matar ta nufo shi ganin pepar a hannunshi kusan a tare su ka gama karanta abun da ke cikin takardar, da sauri su ka kalli juna
“anya yallaɓai wannan lamarin akwai tsoratar wa, taya uwa za tayi kyauta da ƴarta daga haihuwarta ba tare da ta ko san wanda ta ba”
“gaskiya abun akwai ban tsoro sai dai yanzu abun da za'ayi kawai mu tafi Airport ɗin idan ya so ma kirata tunda ga number waya nan ta rubuta”
“to shikenan” matar ta faɗa tana cigaba da haɗa masu kayan su cikin ɗan madaidaicin trolly, tana gama haɗa kayan ta ɗauki teddy ta saka cikin bag ɗinta sannan ta ɗauko mayafi mai ɗan girma cikin kayanta ta lulluɓe jaririyar a kafaɗa ta saɓa jaririyar mijinta kuma yaja trollyn su ka fice daga ɗakin....
*Abuja_Nigeria*
_*COURT*_
Mutanene ta ko ina a harabar court ɗin ƴan jaridu ne ƴan gidan radio da television , ƴan social media gasu nan birjik a harabar kowa burinshi ace shine na farko wurin ɗaukar rahoton yanda shari'ar zata kaya.
mutane dake kai kawo a harabar da wanda suke zaune sai faɗin albarkacin bakin su suke wasu na iƙirarin idan har hukuncin koto baiyi masu yanda suke so ba to babu abun da zai hanasu ɗaukar doka a hannun su sai dai duk abun da zai biyo baya ya biyo.
mutanen dake bakin gate security sun hanasu shigowa kansu abun kallon ne wasu galan galan na fetur ne a hannun su yayin da wasu tayoyi ne a hannun su duk yan ɗaukar doka ne a hannu idan court batayi masu adalci ba.
Wasu danƙara daƙaran motacine na gidan television suka dunfaro court ɗin tun kafin su ƙaraso police ɗin dake wurin suka shiga kora mutane gefe dan su basu hanya.
A ƙalla motocin gidan tv zasu kai guda biyar huɗu baƙaƙe ne ƙirar reng rover yayin da suka sako tv broadcasting van car white color a tsakiyar su da gudun gaske suka nufo court ɗin,ganin irin gudun da suke ne yasa mutane darewa suka basu hanya, tuni security's sun buɗe masu gate suna ƙarasowa ciki suka shige , sai da suka gama dai daita parking tukun suka shiga fitowa kowanen su sanye yake da journalist jacket black color a gaban rigar anyi rubutu da farin paint inda aka rubuta press da mayan haruffa.
ba ɓata lokacin suka shiga fito da kayan aikin su cameras ne yan uban su dan duk yan jaridar dake wurin babu masu nagartatun kayan aiki masu tsada kamar na su.
cikin ƙanƙanin lokaci suka gama dai daita kayan aikin su bayan sun gama daidaitawa ne aka buɗe back seat na motar dake gaban tv broadcasting van car, wata matashiyar budurwa ce tafito sanye take da pant suit white color tayi roling da black ɗin veil,high hills ne a ƙafarta black color,fara ce kyakyawar gaske wurin cameras ɗin ta nufo cikin takun ƙasaita.
Kallo fa ya koma sama gaba ɗaya hankalin mutane ya dawo kan su sai ƙus ƙus ke tashi a wurin.
wannan matashiyar budurwar ce ta fara gabatar da shirin nasu cikin harshen hausa amma saboda zaƙin muryar ta kamar bada hausa take magana ba
“masu kallon mu barkan mu da sake saduwa acikin shirin mu mai farin jini GANI YA KORI JI, a inda muke kawo maku shari'ar hajiya Asma'u wacce ake zargin dasa hannunta a kisan mijinta wato CP ( commissioner of police ) na wannan jaha ,masu kallon mu idan baku manta ba a wancan lokacin koto ta ɗaga sharia'ar zuwa goma ga wanta febrairun shekarar da muke ciki bisa ga wasu dalilai, a yaune adadin kwanakin da koto ta yanke dan zartar da hukunci suka cika , ku biyo mu dan jin yanda shari'ar zata kaya”
tana gama faɗa ma'aikatan suka kashe kemarorin, wani daga cikin ma'aikanta ne yace “good job BALQIS babu wanda zaice ba LAATIFA ba ce” ɗan ya mutse fuska tayi tana faɗin “thanks” tana komawa back seat ɗin motar data fito, jinjina kai kawai yayi,yana sakin murmushi tana shiga cikin motar wayarta dake ringing ta ɗauka picking call ɗin tayi haɗi da kara wayar a kunnenta, muryar mai kiranta ne ya daki dodon kunnan ta
“ hello balƙis ya aikin yake tafiya?”
ya mutse fuska tayi tana faɗin “wallahi bawani abun duk wahala ne, kuma ni banga amfanin bin wannan shari'ar ba”
“haba balqis miye abun wahalar aciki, na kalli live kuma naga kinyi ƙoƙari, ke da yake ba yar jarida bace shiyyasa zaki ce haka”
taɓe baki tayi tana faɗin “ni dai wallahi kin haɗani da Aiki Aunty laatifa”
“kai balƙis miyasa za kice haka bana jin daɗi kina faɗin haka sai naga kamar na takura maki ne ba da son ranki ki kayi ba” jin abun da laatifa tace yasa balqis cewa “ni baki takura man ba, dan nayi niyya ne yasa na zo”
“shikenan sai kin dawo amma dan Allah kar kice ma dady ni na nace kizo please”
“zance mashi ni nayi niyya ba ke ki ka sani ba,amma kin tabbata zaki cika man alƙawari na?”
“nagode ƙanwata sai kin dawo karki damu”
“ok sai na dawo” balƙis ɗin ta faɗa tana rejecting kiran iska ta fesar daga bakinta,wayarta ta shiga shafawa tana kallon wallpaper wayar tana sakin murmushi,sai sakin murmushi take tana aikin shafa wayar, matso da wayar tayi zuwa fuskarta kissing screen ɗin wayar tayi tana faɗin
“am eager to see u my hero,i miss u”
tana cikin wannan shauƙin taji hayaniya tayi yawa ga kuma jiniyar motocin security Army's da yake glass ɗin motar da take ciki na gaba a buɗe yake,tsaki taja tana faɗin
“i hate this sound gaskiya Aunty latifa baki kyauta man ba” ta faɗa tana ɗan jan tsaki, nocking ɗin ƙofar motar taji anyi da sauri ta juya tana kallon mai yin nocking ɗin ranta a haɗe tace “what?”
“sorry dama cewa zanyi ki fito ga BARRISTER ZULAIHAT nan ta ƙaraso” ya mutsa fuska tayi tana faɗin ok
fitowa tayi daga motar sai wani sa hannu take tana kare fuskanta saboda zafin rana.
wasu jibga jibgan motacin sojoji ne ke shigowa cikin court ɗin gaba ɗaya sun cika court ɗin da ƙarar jiniyar su yayin da tsakiyar su wasu expensive bullet proof latest car ne masu nufashi guda biyu fara da baƙa.
Anan compound ɗin court ɗin su kayi parking,security Army's ne suka fara fitowa daga cikin motacin su hannuwan su riƙe da manyan bindigu ga wasu soke a ƙugun su.
farar motar su ka nufa, wani jibgegen security guard ne ya buɗe back seat ɗin motar.
wata kyakyawar baturiyar mata ce ta fito daga back seat ɗin a ƙalla zata kai kimanin shekara 50 a duniya, kyakyawa ce ajin farko ƴar gayu kai tsaye idan ka kalleta ba zaka ce tayi waɗannan shekarun ba a duniya,sanye take da fararen flat pant suit a jikinta ta yafa farin mayafi a kanta,tana da dara daran idanu farare wanda cikin su ya kasacen Ash ne a manne su ke da farin medical glasse,fuskarta ɗauke take da ni'imceccen murmushi.
𝑏𝑎𝑟𝑟𝑖𝑠𝑡𝑒𝑟 𝑧𝑢𝑙𝑎𝑖ℎ𝑎𝑡 𝑘𝑒𝑛𝑎𝑛 𝑓𝑖𝑟𝑠𝑡 𝑤𝑖𝑓𝑒 𝑜𝑓 𝑡ℎ𝑒 𝑓𝑜𝑟𝑚𝑒𝑟 𝑝𝑟𝑒𝑠𝑖𝑑𝑒𝑛𝑡 𝑜𝑓 𝑛𝑖𝑔𝑒𝑟𝑖𝑎,𝑤𝑎𝑐𝑐𝑒 𝑚𝑢𝑡𝑎𝑛𝑒 𝑘𝑒𝑚𝑎 𝑙𝑎𝑘𝑎𝑏𝑖 𝑑𝑎 𝑙𝑎𝑢𝑦𝑎𝑟 𝑎𝑙'𝑢𝑚𝑚𝑎ℎ.
daga front seat na motar security guard ce ta fito hannunta riƙe da black coat da white hand bag sai briefcase rataye a ƙafaɗar ta wanda nake kyautata zaton na barrister ne.
wani daga cikin security guard ɗin ne ya buɗe back seat ɗin baƙar motar dake bayan wacce barrister zulaihat ta fito,ƴan mata ne guda biyu su ka fito, dukan su baƙar abayace a jikinsu anyi mata aiki da golding stones sai sheƙi da ɗaukar ido su ke, sunyi roling da glenta,fuskar ɗaya sanye take da niƙab,ɗayar kuwa sunglasses ne manne a fuskarta dake ɗauke da fara'a,hannunta riƙe da ƴar madaidaiciyar bag ta company Gucci golding color,tana matuƙar kama da barrister zulaihat kamar an tsaga kara.
cikin tafiyar ƙasaita balqis ta ƙaraso wurin su tana sakin murmushi,tana isowa hugging ɗin barrister tayi tana faɗin “good morning mom” raba jikin su barrister tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace
“morning balqis, yau kece da kanki?” murmushi balqis tayi tana faɗin “ayyuka ne su ka yima Aunty laatifa yawa shine tace nazo nayi attending wannan shari'ar dan bata so tayi missing”
“good,laatifa ba dai aiki ba” barrister ta faɗa,ƴan matan nan ne suka ƙaraso wurin su, mai niƙab ɗin ce ta gaishe da balqis yi tayi kamar bata san da ita take ba,saima kyauda kai da tayi tana kallon gefe, yamutse fuska mai kama da barrister tayi tana faɗin “Abun ma yar haka ce ko Aunty balqis” murmushi balqis tayi kamar ba ita ba tana faɗin
“miye kuma yumnah shagwaɓa” bubbuga ƙafa wacce aka kira da yumnah ta shiga yi tana turo baki da faɗin
“mom kina jin Aunty balqis ko, ba zata daina ce man haka ba”
“bana cike da wannan shiritar taki yumnah,balqis nayi ciki”
barrister ta faɗa tana yin gaba, bin bayanta yumnah da wannan budurwar dake sanye da niƙab su kayi yummah na cigaba da shagwaɓarta security guard ɗin na biye da su.
murmushi kawai balqis tayi tana komawa wurin aikinta.
Yan jarida na ta so suyi magana da barrister amma security guard ɗin ta sun ƙi ba su dama,amma saboda ƙwaƙwa irinta ƴan jarida ana ture su amma suna jefoma barrister tambayoyi.
A bakin ƙofar office ɗinta security
su ka tsaya macen dake ɗuke da jakarta da rigarta ce ka ɗai ta shiga ciki sauran securitys ɗin kuma su ka zagaye office ɗin yanda ko ƙuda bai isa ya gitta ba tare da sun ƙwamushe shi ba.
Wani irin haɗaɗen office ne naji da faɗa, yasha expensive desk da leather chair's masu shegen kyau ,barrister zulaihat kujerarta ta nufa ta zauna,akan desk ɗinta securityn ta ajiye mata hand bag ɗinta sannan ta rataya mata coat ɗinta jikin office suit hanger,wasu files ta ciro daga cikin briefcase ɗinta ta shiga dubasu tana ƙarasa haɗa hujjojine kafin lokacin shiga court ɗin yayi.
saman sofa dake cikin office ɗin yumnah su ka nufa su ka zauna sai a lokacin ne ɗayar ta yaye niƙab ɗin dake fuskar ta, masha Allah na furta da ganin kyakyawar fuskar matashiyar budurwar wacce a shekaru bazata wuce sha tara ko ashirin ba kusan sa'anni ne da yumnah.
damuwace ƙarara akan fuskarta, murmushi yumnah tayi tana faɗin
“yanzu dan Allah da ki ka cire wannan abun ba kiji daɗi ba?” kallon yumnah kawai matashiyar tayi ba tare da tace komai ba
“zaki fara wannan shirun naki ko, mom kiyi mata magana mana ta saki jiki da ni ko dan taga na damu da ita” yumnah ta faɗa tana wani ɓata fuska, girgiza kai kawai barrister tayi tana cigaba da aikin dake gabanta ba tare da tace ma yumnah komai ba.
“mom kema shirun zaki man?” ta faɗa tana turo baki kamar zata fashe da kuka
“yumnah wai miyasa ke baki san lokacin da mutum ke son magana da lokacin da bai so ba, baki san halin da take ciki bane zaki dameta?”
a hankali ta kama kunnenta tana faɗin “sorry mom, zama da damuwa bashi ke maganin matsala ba, that's why nake son ta ɗan saki jikinta” kallon matashiyar tayi tace
“sorry NAINARH idan na takura maki, inaso ki saki jiki ne kawai”
murmushi wacce aka kira da nainarh ta saki
“karki damu baki takura man ba, nagode da kulawar ki a gare ni”
martanin murmushi yumnah ta mayar mata tana buɗe hand bag ɗin data shigo da ita, ciro wayarta ƙirar iPhone 14 pro max tayi dialing wata number,waya ta shiga yi cike da shagwaɓa.
miƙewa barrister tayi da sauri security ta matso tana harharɗa files ɗin dake kan desk ɗin tana maidawa cikin briefcase, ganin haka ne yasa su yumnah miƙewa da sauri nainarh na maida niƙab ɗinta tana ɗaurawa, kallon su barrister tayi tace “ina zaku?” yumnah tace “mom ba time yayi ba”
“eh, ku zauna anan duk yanda shari'ar tayi za kuji” duƙar da kai nainarh tayi alamar ba haka taso ba
matsowa barrister tayi ta dafa kafaɗar “sorry nainarh ba dan wani abu yasa nace ku zauna nan ba sai dan tsoron abun da zai biyo baya acikin court, nan sai kin fi samun tsaro”
“shikenan mom,amma ba za'a neme ni ba?” nainarh ta faɗa
“babu mai neman ki, idan yiwuwar hakan ma ta taso za'a zo a tafi dake ne, fatana dai ki kwantar da hankalin ki” gyaɗa mata kai kawai tayi.
Komawa su kayi su ka zauna barrister kuma su ka fice,security tunda su ka ji alamun buɗe ƙofar office ɗin su ka gyara tsayuwar su tana fitowa su ka nufi cikin court ɗin har lokacin yan jarida basu daina binta da jefo mata tambayoyi.
ciki su ka ƙarasa security guard biyu ne suka shiga cikin court room haɗi da macen sauran su ka tsaya a waje, lokacin da su ka shiga court room ɗin a cike take,duk wani mai ruwa tsaki ya hallara suna zaune a mazaunin su yan jarida sun saita kamarorin su jiran a fara kawai su ke, balqis na daga zaune saman chair daga can baya,Attorney tables da aka tanada domin su ta nufa zama tayi security na ajiye mata briefcase ɗinta daga gefenta su ka tsaya,gaishe da ita attorneys ɗin su ka shigayi tana amsa masu cikin kulawa , mutum biyu ne a cikin su ko kallon in da take ba suyi ba,wata macece da wani namiji,fuskar ko wanen su a haɗe take kamar an aiko masu da saƙon mutuwa, namijin ya jingina da head board ɗin chair ɗin da yake zaune hannunshi riƙe da ƙwallon wasan chess yana wasa da ita saman desk,murmushi saki tana faɗin “good morning BARRISTER HASHIM” sai a time ɗin ya juyo masha Allah na faɗa kyakyawa ne na gaske fatar jikinshi chocolate color ce, kallonta yayi da wasu lumsassun idanuwanshi, kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kai yana faɗin “morning” kamar irin anyi mashi dolen nan,girgiza kai kawai tayi tana buɗe briefcase ɗinta ta fito da files da laptop ɗinta dake ciki......
_*Episode 3_4*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
_________________________
Prison officers ne su ka shigo su biyu sai mata guda biyu ma'aikatan prison sun sako wata mata a tsakiyar su yayinda police maza gudu biyar ke a bayan su kowanen su riƙe yake da bindigar sa,uniform ɗin prison ne a jikin matar inda a gaban rigarta aka rubuta number 106 da farin fenti’ black ɗin hulace a kanta,hannunta a sanye yake da handcuff, kanta a duƙe yake har su ka ƙarasa cikin court ɗin, kusa da brisster zulaihat matar ta zauna yayin da police ɗin su ka tsaya a bayan su.
ƙus ƙus ne ya fara tashi a cikin court room ɗin wasu na tausaya ma matar yayin da wasu ke kiranta da munafuka in sha Allah asirinta sai ya tonu.
shiru su kayi sun kafe juna da ido kowa na so yayi ma ɗan uwansa magana amma ya kasa daga brisster har mata,ƙwalla ne ya taru idon matar da sauri brisster ta miƙa mata handkerchief tana faɗin “karki kiyi kuka, in sha Allah yau gaskiya za tayi halinta” jinjina mata kai matar tayi tana goge hawayen dake zuba a idonta, brisster ma dauriya kawai take amma itama kukan take son yi kawai ta daure ne dan karta ƙara karyama matar zuciya.
A hankali matar tace “ina nainarh?”
“suna office ɗina ita da yumnah, na hanata shigowa nan ne dan ban san wani abu ya faru da ita” jinjina kai kawai matar tayi da ka ganta ka san tana cikin matsananciyar damuwa.
ɗaya daga cikin prison offices ɗin ne yace “hajiya za mu iya tafiya?” miƙewa matar tayi su ka nufi in da aka tanada domin zaman su,zama tayi matan su ka sata a tsakiya.
miƙewa su kayi gaba ɗayan su saboda shigowar alƙali,saida alƙali ya zauna tukun suma suka zauna,bayan koto tayi tsit, miƙewa judicial Assister yayi ya gabatar da ƙara bayan ya kammala ne alƙali ya buƙaci da lawyer masu ƙara ya fito.
Cikin ƙwarewar aiki clerk yake typing duk wani abu da ake furtawa a cikin court kama daga sunaye mutane har zuwa yanda shari'ar ke tafiya ga DAR (digital Audio recording ) box a gefenshi tana ɗaukar komai.
miƙewa tsaye brisster hashim yayi wasu files dake gabanshi ya ɗauka yana ajiye chess ball ɗin dake hannunshi, fitowa yayi daga inda yake zaune yana wani gyara zaman coat ɗin dake jikinshi,papers ɗin dake hannunshi ya miƙama judicial Assister, juyawa yayi ya miƙama alƙali.
“my lord wannan rahoton gawar marigayi ne wanda ƙwararon likitoci su ka gudanar tare da horoton cctv camera dake gidan shi, sai bincike da ƴan sanda su ka gudanar akan shatin hannun hajiya Asma'u da aka samu a jikin bindigar da aka kashe marigayi da duk wasu wayoyi daya amsa kafin faruwar abun,sai sunayen witness”
yana gama faɗa ya koma mazauninshi ya zauna yana ɗaukar ball ɗin shi ya cigaba da juyata saman table.
miƙewa mom tayi cikin taƙon kamala ta fito tsakiyar court,ɗan rissinar da kai tayi tana kallon alƙali alamar girmamawa, jinjina mata kai alƙalin yayi,takardar dake hannunta ta miƙama judicial Assister tana faɗin
"my lord wannan sune jadawalin shedo da nayi ma court alƙawarin kawowa"
tashi judicial Assister ɗin yayi ya miƙama alƙali takardar, amsa alƙalin yayi yana ɗaukar glass ɗin shi ya manna a ido, ya ɗan ɗauki tsawan lokaci yana duba duka takardun harda wanda brisster hashim ya bada kafin yace“zaki iya tafiya” godiya tayi mashi tana komawa ta zauna.
“idan malam Aisha tana kusa ta matso gaban koto” Alƙali ya faɗa, a hankali matar ta miƙe daga cikin mutanen dake zaune saman chair, jikinta sai rawa yake daga ganin yana yinta bata cikin natsuwarta,ƙarasowa tayi ta tsaya a cikin witness stand, tashi mom tayi ta nufi in da matar ta tsaya.
ƴan jarida nan su ka fara ɗaukar komai, tasowa balqis tayi ta dawo inda mutane su ke hannunta riƙe da abun magana,juyawa tayi saitin da attorney su ke karab idanunta su ka haɗu da na brisster hashim wani ɗan iskan kallo ya watsa mata wanda yasa ƴan hanjin cikinta kaɗawa ita kaɗai ta san ma'anar wannan kallon daya watsa mata , da sauri ta duƙar da kai tana juyawa ta bar wurin da sauri, gyaɗa kai yayi yana maida hankalinshi ga Alƙali.
Rantsuwa Alƙali ya fara sa Aisha tayi akan zata faɗin gaskiya, kafin ya ɗaura da cewa “court na san sanin cikaken tarihin ki?”
kasa magana tayi saboda wani irin rawa da jikinta yake har sai da Alƙali ya sake magana “kina ɓata ma koto lokaci" da ido mom tayi mata alama data kwantar da hankalin ta, magana ta fara cikin rawa rawar murya dake nuna rashin natsuwarta
“suna na Aisha Usman shekaruna 42 ni ƴar asalin garin faskari ce dake jahara katsina,nazo Abuja ne ta dalilin wata ƙanwar mahaifiyata itace sanadiyyar fara aikina a gidan marigayi”
“malama Aisha tsawan wane lokaci ki ka san marigayi da matar shi hajiya Asma'u?”
“tsawan shekara goma sha biyar”
“ko zaki iya faɗa ma court yanda zamantakewar gidan take tsakaninki da masu gidan?”
“mutanene masu karamci da san al'ummah ko da kuwa ya kasance na ƙasa da su ne, duk tsawan shekarun dana ɗauka tare da su basu taɓa nuna man cewa wai ni ƙasa nake da su ba, hajiya Asma'u ta ɗauke ni tamkar ƙawarta kuma ƴar uwarta,haka marigayi tamkar ƴar uwarshi ta jini haka ya ɗauke ni”
ƴan rubuce rubuce Alƙali yayi kafin ya ɗago yana faɗin “ko zaki iya bama court labarin yanda kisan marigayi ya....” tun kafin Alƙali ya ƙarasa magana tayi saurin ƙatse shi jikinta na rawa tace “wallahi ni ban san komai a game da kisan marigayi....”
desk Alƙali ya buga yana faɗin “nan court ce, ki san yanda zaki riƙa magana, laifi ne Alƙali na magana ka tari numfashin shi, ki kiyaye”
“tuba nake” ta faɗa
tunda Alƙali ya fara magana gaban matar nan ke faɗuwa, tama kasa ɗagowa ta kalli Alƙalin ko mutanen dake cikin court ɗin,brisster hashim kuwa da wannan matar tunda Alƙali ya fara gabatar da ƙara ya mida hankalin shi kan Alƙali ko motsin kirki ba yayi ƙwallon chess ɗin dake hannunshi ma ajiyeta yayi.
tambayar Alƙali ya sake jefa mata, kawai sai gani a kayi tafashe da kuka abun yayi matuƙar ɗaurema brisster kai hajiya Asma'u kuwa jikinta sanyi yayi zuciyarta ta karaya, ta san da wahala ta ƙubuta, Aisha ka ɗaice shedar da take ganin zata iya taimakawa wajen faɗar gaskiya.
wicked side smile brisster hashim ya saki, yana kallon macen dake kusa da shi su ka kashe ma juna ido, da yawan brisster's ɗin dake wurin sun jin daɗin yanda abun ke tafiya ƙalilan ne abun ya taɓa zuciyar su.
sai da ta gama kukan mai isarta tukun Alƙali yace“koto na saurarenki”
“wallahi ni ban san komai ba, hasalima bana garin abun ya far.....”
da sauri brisster zulaihat ta tari numfashin matar tana faɗin
“my lord!, shaidata ta shiga halin ruɗani, tana tsoron magana a gaban court sabo....”
da sauri matar tace “babu ruɗanin da na shiga, kuma ba wai ina jin tsoro ba ne , gaskiya ce nake faɗa, bana nan abun ya faru” matar ta faɗa with full confidence,mamaki kamar ya kashe mom, saboda Aisha tana Abuja komai ya faru amma a gaban koto tace bata nan, brisster hashim har ƙara gyara zama yake abun yana tafiya yanda yake so.
“laifi ne katse shaida yayin bada amsar da Alƙali ya tambaye shi, brisster ki kiye”
“tuba nake” ta faɗa
“ina ki ka je a lokacin da abun ya faru?” Alƙali ya jefa mata tambaya
“naje garin mu domin duba jikin ɗana da ke fama da ciwan daji ( cancer ), kuma hajiya Asma'u da kanta ta bani izinin tafiya ita da mijinta”
“ A ranar yaushe ki kayi tafiyar?”
“na tafi garin mu ranar laraba a washe garin ranar Alhamis nake samun labarin abun da ya faru”
“mi yasa baki dawo ba da ki ka samun labarin abun da ya faru da ubangidan na ki?”
“saboda lalurar ɗana, jikinshi ne yayi tsanani shiyyasa ban samu damar zuwa ba”
ƴan rubuce rubuce Alƙali yayi kafin yace “zaki iya komawa ki zauna, kotu za tayi bincike akan bayanan da ki ka bata, lawyer masu ƙara ko kana da tambayoyin da za kayi ma malam Aisha” miƙewa brisster hashim yayi yana gyara zaman coat ɗin shi, cikin takun ƙasaita ya nufi tsakiyar koton, cikin maganar ƙasaita yake faɗin “my lord, ina so zanyi ma shaida wasu ƴan tambayoyi”
izini Alƙali ya bashi
“godiya nake” ya faɗa yana matsawa in da Aisha take tsaye
“malam Aisha ina so zanyi maki wasu ƴan tambayoyi,ya zamantakewar iyayen gidan naki take, shin kafin mutuwar cp ko a kwai wani saɓani da ya taɓa shiga tsakaninshi da uwar ɗakin ki, ko akwai rashin jituwa tsakaninsu, wasu dai Abubuwa maka mantan haka???”
“babu yallaɓai,a kwai fahimta a tsakaninsu, marigayi yana matuƙar kyautata ma matar shi hatta mu ƴan aiki ya ɗauke mu da matuƙar daraja”
jinjina kai brisster hashim yayi yana faɗin “ita fa uwar ɗakin taki, ya nata halayen su ke, bata da wasu ɗabiu marasa kyau wanda baku jin daɗin su???”
ran brisster zulaihat ne ya fara ɓaci da irin tambayoyin da brisster hashim kema Aisha
“gaskiya babu”
“koda a ɓoye bata da su?” ya sake mata tambayar, miƙewa brisster zulaihat tayi rai a ɓace “objection my lord”
“sustained”Alƙali ya faɗa yana bata izini
“lawyer masu ƙara kamar yana son tursasa witness ɗina akan dole sai ta faɗi abun da bashi ba”
“brisster hashim ka kiyaye” jinjina kai brisster hashim yayi
“malam Aisha a ra'ayin ki ne ki ka tafi gida ko kuwa uwar ɗakin kice ta nuna dacewar tafiyar ki a wannan lokacin?”
“Itace tace ya kamata na tafi na duba jikin shi , da tace man haka sai nace mata zan shirya ranar juma'a ko asabar naje amma sai tace na shirya gobe na tafi da farko naƙi amincewa da tafiyar a washe garin nace kawai zan tura masu kuɗin su fara amfani dashi kafin zuwa ranar juma'ar na tafi, amma sai ta zaunar dani ta nuna man dacewar na tafi a goben shine na amince”
“da tace ki tafi a lokacin ba kiyi wani tunani ba ko akwai dalilin da yasa tace kije?”
Miƙewa brisster tayi tana ɗan dukan table ɗin dake gabanta “objection my lord”
“Overruled”Alƙali ya faɗa
komawa tayi ta zauna tana cizon yatsa na rashin bata dama da Alƙali yayi, side smile brisster hashim ya saki
amsar tambayar da brisster hashim yayi mata ta bashi
“banyi tunanin komai ba, saboda idan ahalina suna cikin matsala ta kan fini shiga damuwa akan halin da nake ciki,shiyyasa banyi zargin komai ba”
jinjina kai brisster yayi “mudi mai gadi ya sanar da koto cewa akwai wani matashin saurayi dake yawan zuwa wurin uwar ɗakin na ki, baki taɓa tunanin mike kawoshi wajenta ba , ko miye alaƙarta da shi ???"
“sunan sa Abid, ɗan ƙanwarta ne dake zaune a ƙasar waje, yana yawan zuwa wurinta duk lokacin da yazo suna samu saɓani da marigayi saboda kwata kwata jinin marigayi bai haɗu dana Abid ba, saboda Abid yaro ne mara tarbiya baya girmama na gaba da shi , gashi duk lokacin da yazo sai ya takura ma yarinyar su , hakan yasa marigayi baya son yana zuwa gidan, ita hajiya sai ta nuna ba taji daɗi ba kan nuna kyara da tsangwama da yake akan yaron, a ranar da mu kayi magana kan tafiyata ya zo gidan har saɓani ya shiga tsakanin shi da marigayi ya dake shi, abun yayi matuƙar ɓata ran hajiya har su ka samu saɓani da marigayi, bayan mungama magana da ita naje ɗakina na wanke kayan da zan tafi da su na zagaya baya zanyi shanya na hangesu ita da Abid suna tattauna wasu maganganu wanda ban san mi su ke tattaunawa ba, nayi ƙoƙarin naji abun da su ke faɗa amma abun ya gagara saboda tazara dake tsakanin mu,bayan na koma ɗakina cikin dare naji Abid ɗin yana waya a bayan ɗakina kamar yana faɗama wanda suke waya saɓanin da su ka samu da marigayi bana jin mi na ciki wayar ke faɗa masa na dai ji yana faɗin a cikin satinnan ya kamata suyi aiki a kanshi ko zai daina mashi shiga hanci da ƙudindine, na tsorata da jin abun daya faɗa har na kasa bacci , washe gari tunda safe na samu hajiya da maganar amma sai ta nuna kar na damu da abokan kasuwancin shi yake waya”
tunda Aisha ta fara jera wannan jawabin gaban hajiya Asma'u ke faɗuwa bata taɓa sanin komai dake faruwa a gidan Aisha na sane ba sai yanzu.
“abokan ka suwanci, ko kin san wane irin ka suwanci yake?, sannan wane saɓani ya shiga tsakanin shi da marigayi?”
“gaskiya ban san kasuwanci da yake ba, amma na taɓa jin labari a wurin mai gadi cewa yaron yana harkar kayan maye , kuma dukiyar da yake juyawa ta hajiya Asma'un ce ”
jinjina kai brisster yayi
“wane saɓani ne ya shiga tsakanin shi da marigayi?” ya sake maimaita mata tambayar
“gaskiya ban sani ba”
juyawa brisster hashim yayi ya kalli Alƙali “my lord , tun ranar da mai gadin gidan ya ba police duk wasu bayanai akan yaro suka tsaurara bincike sai dai kash bayan kwana biyu da fara binciken na su aka samu gawar shi yaron a cikin gidan shi anyi mashi kisa makamancin na marigayi,hakan na nufin hajiya Asma'u ta tura Aisha gida ne dan ta samu damar aiwatar da shirinta ba tare da wani ya ganota ba,sannan ta sallami ma'aikatan gidan dan kar su ga abunda zai faru,Abid ya ƙi bata haɗin kai ne shiyyasa ta tura makasan da su ka kashe cp su ka kashe shi dan kar ya zame mata matsala”
“Objection my lord”
jinjina mata kai Alƙali yayi alamar amincewa
“my lord lawyer masu ƙara na son tabbatar da laifi akan wacce nake karewa ba tare da ƙwararan hujjoji ba”
“brisster hashim ka kiyaye”
“tuba nake”
jinjina kai Alƙali yayi kafin ya ɗauki pen ɗin shi yayi ƴan rubuce rubuce
“lawyer masu ƙara ko kana da sauran wasu tambayoyi da za kayi ma malam Aisha”
“su kenan tambayoyin da nake son yi mata” brisster hashim ya faɗa, tsaki brisster taja a zuciyarta tana faɗin
“ko ina amfanin wannan tambayoyin”
“lauyan wanda ake ƙara ko kina da wasu tambayoyi da za kiyi ma malam Aisha?”
miƙewa brisster tayi “eh my lord” dama Alƙali ya bata, fitowa tayi brisster hashim kuma ya koma mazauninshi.
“malam Aisha a bayanan da hajiya Asma'u ta bada da kuma binciken da muka gudanar ya tabbatar mana da cewa kina a gidan a ranar da abun ya faru , hasalima kece ki ka fara sanar da su zuwa mugayen mutanen da su ka shigo gidan”
“wallahi brisster bana garin ita da kanta tace naje, munyi maganar da ita yau washe gari tunda safe na tafi”
murmushi gefen fuska brisster ta saki tana faɗin “ƴan uwan naki su su ka bada shedar cewa a ranar ba kije garin naku ba sai a washe garin ranar da abun ya faru”
shiru Aisha tayi ba tare da tace komai ba
“malama Aisha ke koto ke saurare?”
“ranar na tafi sai dai ban samu isa garin ba sai cikin dare,hakan yasa basu san da zuwa na ba sai washe gari”jinjina kai brisster tayi tana juyawa ta kalli Alƙali
“my lord malama Aisha ta sanar da koto cewa bata nan abun ya faru, a binciken dana gudanar ya tabbatar man da tana a cikin komai ya faru”
“binciken koto zai tabbatar da hakan, kina da sauran wasu tambayoyi da za kiyi mata”
“babu sauran wasu tambayoyi da zanyi mata”
“malam Aisha zaki iya komawa mazauninki kafin binciken koto ya kammala”
“godiya nake” ta faɗa tana ɗan rissinar da kai,barin witness stand ɗin tayi ta koma mazauninta ba tare da ta bari sun haɗa ido da brisster ba ko hajiya Asma'u.
brisster wurin zamanta ta koma itama,haka shari'ar ta cigaba da tafiya duk wasu jadawalin sunayen witness ( sheda) sai da Alƙali ya kira su gaban koto yana masu tambayoyi bayan ya kammala masu ya ba brisster's dama suma suyi masu nasu tambayoyi, ko wane sheda da kalar amsar da yake ba dawa a kan kisan marigayi CP,hajiya Asma'u tun tana sa ran kuɓuta har ta sadaƙata tasan bazata taɓa kuɓuta ba daga yanayin amsoshin da shedun ke ba court,brisster ma gwiwowinta sun sage bata taɓa shari'a irin wannan ba tana shari'a akan kisa amma kuma bata taɓa rashin nasara ba amma wannan shari'ar na neman tafi ƙarfinta , shedun da take taƙama dasu gaba ɗaya sun juya mata baya,duk wanda aka kira a cikin su abu ɗaya su ke faɗi hajiya Asma'u ta kashe mijinta kuma suna bada ƙwararan hujjoji wanda dole koto ta yarda .
brisster hashim kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha yasan zaiyi wuya yau bai yi nasara akan brisster zulaihat ba abun da ya daɗe yana jira kenan tsawan shekaru.
Magana Alƙali ya fara, tsit kotun tayi kowa na sauraron hukuncin da court zata yanke “binciken kotu ya tabbar da malam Aisha bata nan a ranar ashirin da ɗaya ga watan biyar”
Ajiyar zuciya Aisha ta sauke tana dafe saitin zuciyarta, brisster wani mugun faɗuwa gabanta yayi hajiya Asma'u kuwa tuni hawaye sun taru a cikin idanunta
“bayan kammala haɗa duk wasu hujjoji da binciken koto dana likitocin dake kula da gawar marigayi CP ya tabbatar da hajiya Asma'u itce ta kashe CP” tunda Alƙali ya fara magana brisster hashim ke sakin murmushi, brisster zulaihat kuwa banda faɗuwa babu abun da gabanta ke yi.
“kotu ta yanke ma hajiya Asma'u hukuncin kisa ta hanyar rataya tare da biyan tara ta naira milayan hamsin”
Wani irin murmushin farin ciki barisster Hashim ya saki yana kallon ƴan uwan shi wanda hukuncin yayi masu dai dai,a ɗayan ɓangaren kuwa barisster Zulaihart wani irin tashin hankali mara misaltuwa ta tsinci kanta, da dama mutanen dake Court ɗin abun yayi masu daɗi yayin da wasu ke tausaya ma Hajiya Asma'un.
ana cikin jimamin hukuncin da court ɗin ta yanke sai ga saƙo daga fadar shugaban ƙasa na nemama Hajiya Asma'u sassaucin kotu daga rataya zuwa ɗaurin rai da rai tare da biyan tara ta nera miliyan ɗari saɓanin hamshin.
Ran barisster hashim idan yayi dubu ya ɓaci ba haka yaso ba yaso hukuncin kisa aka yanke mata ta hanyar rataya bai so ɗaurin rai da rai ba amma idan ya tuna ba wai zata fito bane sai hankalishi ya kwanta, mom ta ɗan ji sassauci da ba kisa bane ɗaurin rai da rai ne sai dai idan ta tuna halin da hajiya Asma'u da nainarh za su shiga hankalinta na tashi.
wasu daga cikin mutane kwata kwata ba su so haka ba gani suke kamar wata maƙarƙashiya ce ake ƙullawa.
Miƙewa Alƙali yayi gaba ɗaya su ka miƙe,ƙofar office ɗin shi ya nufa kamar jira a ke Alƙali ya fita koto ta ɗauki haya niya kowa da abunda ke fitowa daga bakin shi,can compound ɗin curt ɗin kamar zai fashe saboda haya niyar mutane, mom tunda Alƙali ya fita ta kifa kanta saman desk ko motsin kirki ta kasa yi,matsowa wannan security guard ɗin tayi tana bata haƙuri, miƙewa brisster hashim yayi yana wani gyara zaman rigar shi fuskarshi ɗauke da murmushin mugunta, ɗaya bayan ɗaya mutane su ka fara fita daga cikin kotun suna tofa albarkacin su.
hanyar fita prison officers suka nufa da hajiya Asma'u, da ƙyar take taka ƙafafuwanta suna zuwa tsakiyar court ɗin ta yanke jiki ta faɗi a sume, salati mutanen da su ka rage a ciki su ka rabka da sauri mom ta miƙe kusan a tare su ka isa inda hajiya Asma'u ke yashe a ƙasa ita da wasu mata guda biyu, amma kafin su ƙaraso ma'aikatan gidan yarin sunyi mata rumfa mom ka ɗai su ka bari ta ƙarasa in da take, jijjigata ta shiga yi tana kiran sunanta amma ko gezau ba tayi ba, ɗaya daga cikin prison officers ne ya miƙoma mom ruwa,a hannu ta zuba ruwan ta shafa mata a fuska, tayi hakan kusan sau ba adadi amma bata farfaɗo ba mom bata san lokacin da ta fashe da wani matsanancin kuka ba,doctors ɗin gidan yari ɗaya daga cikin jami'an gidan yarin ya kira, ba'ayi five minutes ba sai gasu sun ƙaraso, nurses huɗu mata ne su ka kamata su ka ɗaura saman stretcher,ficewa su kayi da ita daga cikin court ɗin bayan su mom tabi tana goge hawayen dake zarya saman kumatunta, a hanzarce security guard ɗinta tabi bayan ta har zuwa in da su kayi parking Ambulance,ganin fitowar mom ne yasa sauran security guard ɗin nufota da sauri saboda mutane da ƴan jarida da suka fara jefa mata tambayoyi harda na hauka, wasu ma a fakaice magana su ke gaya mata,buɗe Ambulance ɗin ɗaya daga cikin officers ɗin yayi ciki su ka saka hajiya Asma'u,maganganu mutane ke jifa ma mom,tana jinsu amma tayi kamar bata jin mi suke cewa tana nan tsaye har sai da taga ficewar Ambulance ɗin daga cikin court ɗin tukun ta juya da nufin ta koma office ɗinta, juwar da za tayi taga brisster hashim tsaye ya harɗe hannuwa saman chest ɗin shi, wani ɗan iskan murmushi ya sakar mata yana tunkaro in da take tsaye, bashi hanya security guard ɗinta su kayi da alama dai shima ba ƙaramin mutum bane.
zuba mashi ido tayi har ya ƙaraso inda take, murmushi ya saki cikin wata irin murya kalar ta ƴan duniya yace
“ya dai lawyer Al'ummah?, yau ina goyan bayan Al'ummar taki yake?”
ɗauke kai mom tayi wani ƙululun baƙin ciki na tokare mata maƙoshi, dariya brisster hashim ya saki
“see u next time” ya faɗa yana kashe mata ido ɗaya, barin wurin mom tayi securitys ɗinta su ka bi bayanta, da kallo brisster hashim ya bita har ta ƙarasa inda su kayi parking motocin su,duk Abun da ke faruwa balqis na tsaye tana kallo,hawaye ne su ka taru a idonta ta rasa dalili rashin jituwar brisster hashim da mom, juyawa tayi ta nufi motocinsu ta shiga barin court ɗin su kayi baki ɗaya.
wannan lawyer ce ta nufo brisster hashim dake tsaye
“brisster na lura so ka ke baƙin ciki ya kashe brisster zulaihat a yau ” ta faɗa tana sakin murmushi, martanin murmushi ya sakar mata yana
faɗin “yanzu ta fara gani in dai ni ne”
“Allah ya shirya ka, gaskiya baka kyautawa matar yayan ka ce fa”
“na tsaneta bana son ganinta” ya faɗa yana barin wajen, bin bayan shi lawyer tayi.
waya brisster ta ɗauka tayi dialing number yumnah bugu ɗaya tayi picking “ku fito ina parking space ku same ni” tana gama faɗa tayi rejecting ba tare da ta tsaya jin mi yumnah za tace.
miƙewa yumnah tayi tana kallon nainarh data zuba uban tagumi, girgiza kai tayi tana nufar ta, dafa kafaɗar tayi firgigit nainarh tayi ta miƙe a tsorace har sai da gaban yumnah ya faɗin
“yumnah an gama shari'ar ne?” nainarh tajefa mata tambaya
“ban sani ba, amma dai mom tace mu sameta waje ban sani ba ko an gam....” tun kafin ta ƙarasa nainarh ta nufi hanyar fita da sauri, bin bayanta yumnah tayi.
tana fitowa ƴan jarida su ka yo mata caaa, sai jefa mata tambayoyi su ke marasa kan gado, ruɗewa tayi ta rasa in da zata dosa hawaye har sun fara zuba daga idanuwanta,ganin halin da take ciki ne yasa securitys ɗin nufarta, zagayeta su kayi suna tutture ƴan jaridar, in da mom ke tsaye tana jiran su suka nufa,maganganun mutane ne su ka fara ɗaukar hankalinta da irin kallon da suke binta da shi
“itace ɗiyarta ko kunya ba tajiba ta kashe ma yarinya ubanta saboda neman duniya kawai”
“ai hukuncin da kotu ta yanke mata bashi ya kamata da ita ba hukuncin kisa ne dai dai da ita”
“saboda brisster zulaihat yasa ba'a yanke mata hukuncin kisa ba, kasan suke da ƙasar sai yanda su kayi da talaka” maganganun dake fitowa daga bakin mutane kenan, tunda ta fara sauraronsu gabanta ke faɗuwa.
bayan su yumnah ta biyo sai turo baki take kamar zata fashe da kuka,da sauri nainarh ta nufi mom hawaye na fita daga idanunta “mom ina ummah?” shine tambayar data jefa ma brisster, juyawa mom tayi ta shige motar ta ba tare da tace mata komai ba, motar da ke bayan wacce brisster ta shiga security guard ɗin ya buɗe ma nainarh da nufin ta shiga, a masifance ta maida marfin ƙofar ta rufe tana juyawa zata nufi cikin court ɗin, da sauri brisster ta fito tana faɗin “kar ku barta ta wuce”
umarnin mom su ka bi, duk yanda nainarh ta so shiga cikin court room ɗin hanata security su kayi ƙarshe data gaji zubewa tayi ƙasa tana fashewa da wani matsanancin kuka,kamata mom tayi ta miƙar da ita tana lallashinta su ka nufi mota, itama daurewa kawai take yumanh da yake saurin kuka ne gareta har ta fara matse ƙwalla abun tausayi, motar da su ka zo ita da nainarh ta shiga nainarh kuma a tare su ka shiga da brisster, kuka take kamar ranta zai fita tun brisster na daurewa har itama ta kaida zubar da ƙwalla, a tamanin security guard ɗin su ka shiga motocin su, da gudun gaske su ka fice daga court ɗin.
tun daga farkon shigowa anguwar zaka tabbatar da anguwa ce ta manyan mutane masu faɗa aji a cikin ƙasa,manyan gine gine ne ta ko ina,tun daga nesa ƙarar jiniyar motocin su ka cika anguwar,da wani irin matsiyacin gudu su ka shigo anguwar, miƙe titin su kayi shantal sai da su ka kusa kai ƙarshen shi tukun suka karya kwana,tun daga farkon street ɗin da su ka shigo check point ne na sojoji,kowanen su ƙatuwar bindigace a hannunshi yayin da wasu ke soke a ƙugunansu, tun kafin motocin su ƙaraso sojojin dake zaune bakin ɗan gate ɗin da su ke sawa su ka buɗe masu, suna isowa babu jira suka wuce,tafiyar kusan minti goma sha biyar su kayi a ƙalla sun wuce check point na sojoji da ƴan sanda kusan guda goma kafin su ka kawo bakin wani ƙatafaran gate,ba sojojin dake gadin gate ɗin ba shi kanshi gate ɗin abun kallo ne, wani irin zungureren gate ne ƙaton gaske.
ga wasu irin manya manyan sojoji dake gadin shi, kwata kwata babu ɗigon imani a fuskar su,sojojin dake zaune saman bench ne suka miƙe da sauri lokacin da motocin su ka ƙaraso bakin gate ɗin,wani mahaukacin horn akayi da motar dake gaba da sauri wani soja ya danna wani abu dake hannunshi mai kama da remote nan take gate ɗin ya shiga zugewa zuwa gefe ɗaya,da gudun gaske suka danna kan hancin motocin zuwa ciki, masha Allah na furta a yayin da nayi arɓa da ƙaton Castle ɗin da su ka shigo,gidajene a cikin shi na alfarma hagu da dama aƙalla za su kai kimanin guda hamsin kusan a jere suke sai dai akwai tazara mai ɗan yawa a tsakanin ko wane gida, security guard ne ke yawo a cikin Castle ɗin ta ko ina,babu abun da babu a ciki kama daga clinic ne sport center, garden babu abun da babu a ciki, duk wani abu na more rayuwa a kwaishi a cikin estate ɗin.
a ƙalla sunyi tafiyar kusan minti biyar kafin su ka kawo bakin wani ƙaton luxury Villa wanda yafi ko wane gida dake cikin estate ɗin girma haɗuwa da tsaruwa, yana yin shi ma da ban yake da gidajen dake ciki shi ba'a jere yake da sauran gidajen ba yana a tsakiyar su yana fuskantar gate ɗin estate ɗin, water falls ne masu matuƙar kyau da ban shawa'a a bakin villa ɗin da a ƙalla ya kai hawa biyar, parking motocin su kayi...
_*Episode 5_6*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
___________________________
A zaune take saman royal sofa mai mazaunin mutum uku dake a katafaren main parlorn dake villa ɗin,faɗa maku tsaruwa da haɗuwar parlorn ɓata lokaci ne,royal sofas ne a cikin shi kusan set shidda, komai na cikin parlorn white and golding color ne,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke tashi a cikin parlorn haɗe da sanyi AC,parlorn iya haɗuwa ya haɗu.
duguwar rigar lace ce a jikinta ɗinkin bubu,wuyanta yasha adon sarƙar gold hakama hannuwanta da ƴan yatsunta da suka sha ƙunshin jan lalle sunsha zobunan gold masu tsadar gaske, fara ce mata ƴar duma duma ba laifi kyakyawa ce,gashin attachment ne a kanta ya zubo har gadon bayanta,wani daddaɗan ƙamshine ke fita daga jikinta wanda ya haɗe da na fresheners ɗin dake parlorn ya bada wani ni'imtaccen sanyin ƙamshi.
tsadaddiyar wayarta ƙirar company Samsung ce kare a kunenta da alama waya take,cikin maganarta ta ƙasaita da isa take faɗin
“nayi matuƙar jin daɗin wannan daddaɗan labarin daga gareka”
bana iya jin mi na cikin wayar ke faɗa, murmushi ta saki tana cigaba da faɗin
“kar ka damu in dai nice zaka samu harda gyara ma, fatana dai sirrin mu ya cigaba da ɓoyiwa”
jin jina kai tayi har ta buɗe baki za tayi magana ƙarar dirar motocin su ya katse ta, da sauri ta miƙe daga saman sofa ta nufi bakin window cikin taƙun izza da ƙasaita, yaye curtains ɗin dake jikin window tayi,a hankali ta sauke idanunta a compound ɗin gidan,kusan a tare aka buɗe motacin dake tsakiyya, brisster zulaihat ce ta fito ɗayan ɓangaren kuma nainarh ce ta fito dafe da kai yayin da yumnah ta fito daga bayan motar dake bayan ta su,daga ganin yanayin fuskarta ba ƙaramin ku ka tasha ba.
main entrance ɗin gidan su ka nufo wannan security guard ɗin ce ta shiga gaban su yayin da mazan su ka rufa masu baya har bakin entrance ɗin villa ɗin,wani ɗan card security guard ɗin ta ciro daga aljihun wandonta ta zura a jikin wata ƴar na'ura dake jikin ƙofar , cikin ƙanƙanin lokaci ƙofar ta shiga zugewa,zare card ɗin tayi, kama Nainarh mom tayi, ciki su ka kunna kai ban da security guard ɗin maza, juyawa su kayi su ka koma in da su ke zama.
Taɓe baki matar tayi tana sakin curtain ɗin ta juya zuwa cikin parlorn, ya mutse fuska tayi
“sorry kaji ni shiru, dangin yahudawan ce ta dawo, matar nan akwai ɗan banzan taurin kan tsiya,babu abun da ta rasa a rayuwa amma saboda tsabar zubar ma da kai aji ina ita ina aikin lawyer dukiya mulki babu wanda Allah bai bata ba, daga gidan mijin har gidan iyaye da ƴaƴa amma ta zaɓi wannan aikin wahalar”
jinjina kai tayi can ta kwashe da dariya tana faɗin
“no ba haka nake nufi ba, kaima ai kafi ƙarfin shi kawai ra'ayi ne irin naku kai da ita”
dariya ta sake saki tana faɗin “ok bye bye, take care of ur self for me sai na sake jinka” tana gama faɗa ta janye wayar daga kunnenta, mazauninta ta koma ta zauna tana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya tana wani jijjiga ƙafarta dake manne da chain na gold, ƙafar sai sheƙin ƙunshin jan lalle take.
tana a nan zaune su ka shigo parlorn bakin su ɗauke da sallama, daga yanyin da su kayi sallamar zaka tabbatar da rashin natsuwar da su ke a ciki, yumnah har time ɗin kuka take,miƙewa matar tayi tana nufar su fuskarta ɗauke da wani shu'umin murmushi, tana ƙarasowa gabansu tace
“Ashe haka shari'a ta kasan ce?” banza mom tayi da ita kamar bada ita take ba
“dama duk wanda yace tukunyar wani bazata tafasa ba to tabbas tashi ko zafi ba za tayi ba,to Allah dai ya kyauta na gaba”
ta faɗa tana sakin murmushi,wucewa mom tayi ba tare da ta tanka mata ba ta nufi elevator,bin bayan ta su yumnah su kayi.
dariya matar ta saki tana faɗin
“ita ƙarya dama ai fure take bata ƴaƴa,salihan bayi kullum a cikin nasara suke, tsinanne kuwa baya taɓa nasara akan masu daraja”
mom na jinta amma tayi kamar bata san tana yi ba, wasu madannai ta dannan a jikin elevator, buɗewa ƙofar tayi su ka shige ciki,wata ƴar iskar dariya mata ta sake saki
“Allah ya la'anci yahudawa da nasarawa, duk wanda ya kasance cikin wa ƴannan da Allah ya la'anta yayi asara, Allah mungode maka da kayo mu cikin jinsi mafi daraja da ɗaukaka kayo mu a muslmai ba sabon tuba ba” dariya ta saki tana bin su mom da kallo har suka yi sama.
juyawa tayi da nufin komawa mazauninta,wata kyakyawar budurwace tsaye a bayanta fara ce sai dai ba irin sosai ɗinnan ba,gown ce a jikinta white color ta ɗan wuce gwiwarta yayinda kanta ke sanye da hular saƙa baƙa,manya idanunta farare ƙar ta zubama matar, tsuke fuskarta matar tayi tana wani yamutse fuska tace “miye ki ka wani tsare ni da idanu uwata?” girgiza kai tayi cikin ƙunar rai da takaici tace
“MAMY gaskiya abun da ki ke baki kyautawa, miyasa kullum ki ke son zubarma kanki da mutunci ne?, yanzu dan Allah abun da ki ka yima mom kin kyauta?, gaskiya mamy ki dai na wannan ba hali bane mai kyau,kina jawo ma kanki abun kunya damu kan mu”
“ehyye!,sannu uwata, nace sannu uwata faɗa za kiyi man?” ta faɗa kamar zata rufeta da duka
“mamy ba faɗa zanyi maki ba, ina faɗa maki gaskiya ne a matsayina na ƴar ki, hakan bai dace ba”
“to bana so” mamy ta faɗa
“mamy dole na faɗa maki gaskiya,idan har DADY ya san baki daina wannan ɗabiun ba bazai taɓa raga maki ba kin dai san halin shi, a kullum mom tana son ku zauna lafiya amma ke baki son haka, kullum burinki ki tada fitina, kuma mamy da ki ke mata gori kema fa ba rawa ki kayi Allah ya hallice ki muslmar ba sai kiga tafiki dacewa ita data shiga muslincin daga baya sama dake da aka haifa a cikin s...”
bata ƙarasa ba mamy ta daka mata tsawa tana faɗin “FA'IZA! ni ki ke faɗama wannan kalaman dan uwarki?”
“kiyi haƙuri mamy gaskiya ce”
riƙe haɓa tayi “ah gaba gaba duka zaki fara kaiman idan banyi wasa ba”
“Allah ya tsare ni da kai maki duka mamy, amma ki sani wallahi sai na sanar da DADY baki dai na cin mutuncin mom ba, kuma ma ai ya hanaki zama main parlor,kin dai san sauran idan har yazo ya sameki”
tana faɗar haka ta nufi elevator da su mom su ka hau da sauri dan ta san zamanta a wurin bazai haifar da ɗa mai ido ba, madannan dake jiki ta danna.
“ina zaki uwar iyayi?” mamy ta faɗa tana ɗan ɗaga murya
“zanje na lallashi mom ne”
baki mamy ta saki har fa'iza ta ɓace ma ganinta, jinjina kai tayi tana faɗin
“zan kama ki ne dan ubanki, sai naji uban dake zugaki kina faɗa man magana san ranki” ta faɗa tana nufar elevator dake ɗayan ɓangaren parlorn ta shiga, dan ta san muddin dady ya shigo ya sameta a main parlorn ranta idan yayi dubu to sai ya ɓaci.
ƙofar elevator ne ya buɗe, zuro ƙafarta tayi ta nufi wani ɗan corridor,wata ƙofa ta shiga,wani haɗaɗen parlor ne ta shigo,ya fi na ƙasan da su ka baro kyau da tsaruwa, komai na cikin shi ya kasance gloding color ne,set ɗin sofa biyu a cikin shi.
Wata ƙofa ta nufa wacce nake kyautata zaton kitchen ne,tura ƙofar tayi ta shiga makeken kitchen ne gari guda babu wani da babu a ciki,ma'aikata ne su shidda gaba ɗayan su mata ne, kowaccen su na sanye da uniform ɗinta riga da wando, rigar fara ce yayin da wandon ya kasance baƙi, kowannen su aikin gaban shi yake, bakinta ɗauke da sallama ta shiga, gaba ɗaya su ka ɗago suna kallonta, amsa mata sallamar su kayi suna ɗan rissinawa su ka gaishe ta, cikin kulawa ta amsa masu tana ƙarasawa cikin kitchen ɗin, ɗaya daga cikin su ce tace
“Aunty Fa'iza mi ki ke buƙata, ai da kin kira waya ba sai kin zo da kanki ba?”
dish rag ta nufa tana faɗin “karki damu ISHRAT zan ɗauka da kaina, kawai dai ina so ku haɗa ma su mom lafiyayyan abinci mai rai da lafiya”
“in sha Allah yanzu za'a kammla” jinjina kai tayi tana ɗaukar plate mai ɗan girma ta nufi fridge,kayan ci da sha ne shaƙe a cikin shi, duk wannan kayan ƙwalam da maƙulashe dake ciki ruwa da lemu kawai ta ɗauka ta ɗaura saman plate ɗin,ƙofar fita ta nufa ɗan dakatawa tayi.
“kina buƙatar wani abun ne?” ishrat ta faɗa
“A'a, wai yaushe ummah za ta dawo ne?”
“tace man yau ko gobe amma ba tabbas” ishrat ɗin ta faɗa, jinjina kai fa'iza tayi tana ficewa daga kitchen ɗin.
parlorn data shigo ta koma wata ƙofa ta nufa nan ma wani madaidaicin parlor ne, anan ta samu yumnah da nainarh,nainarh har lokacin kuka take yumnah kuwa ta dafe kanta da hannunta ɗaya yayin da idanunta ke a lumshe hawaye na fita,wannan security na zaune gefen nainarh tana lallashinta
“Assalamu Alaikum” ta faɗa tana ƙarasawa cikin parlorn,
“good morning ma” security guard ɗin ta faɗa
“morning”fa'iza ta faɗa tana nufar in da suke ,trayn dake hannunta ta ajiye saman table, zama tayi kusa da nainarh, dafa ƙafaɗarta tayi
“ba kuka ya kamata kiyi ba Nainarh, Adu'a ya kamata kiyi in sha Allah komai yayi farko zaiyi ƙarshe, in sha Allah babu abun da zai faru da momyn ki,zata dawo gareki in sha Allah”
lallashinta fa'iza ta shigayi tana faɗa mata kalamai masu daɗi, shiru nainarh tayi tana sauke ajiyar zuciya, kallon yumnah fa'iza tayi
“Autar dady da mom kukan ya isa haka sai kisa zuciyarta ta karaya, ki daina kinji” jin jina mata kai kawai yumnah tayi
“ku shiga ɗaki sai ku kwanata ku huta kunji, ga breakfast can nasa su ishrat su haɗa maku” da to su ka amsa mata, suna tashi itama
miƙewa tayi tana faɗin “mom na ciki ne?” da eh yumnah ta bata amsa.
trayn ta ɗauka,ƙofar dake kallon dama ta nufa, a hankali ta tura ƙofar bakinta ɗauke da sallama,masha Allah na furta a yayin da nayi arba da katafaren bedroom ɗin data shigo,expensive furniture's ne a cikin shi na alfarma,royal bed ɗin dake ciki kawai abun kallo ne,yasha blanket da bedsheet masu tsadar gaske, bed ɗin a cike yake da pillows, bedroom ɗin ba wani cike yake da kaya ba, bed ne kawai sai nightstand dake ɗauke da bedside lamps sai dressing mirror,sai sofas guda biyu dake can bakin sliding window sai ɗan round table dake tsakiyar su.
Cikin ɗakin ta ƙarasa yayin da take yin sallama, a tsaye ta hango brisster zulaihat bakin window hannunta riƙe da curtains,girgiza kai fa'iza tayi cike da tausayawa ta nufi in da brisster take, sallama ta sake yi dan a tunaninta bata jita ba,kafe garden ɗin dake bayan villa ɗin tayi da ido yayin da hawaye ke sauka daga idanunta, a zahiri kallon shuke shuke dake cikin garden ɗin masu ɗaukar hankali take amma a zahirin gaskiya hankalinta kwata kwata ba'a kan su yake ba,babban tashin hankalin ta a wane hali yanzu aminiyarta take ciki sannan ya rayuwar nainarh zata kasance ba tare da mahaifiyarta ba, da sauri ta juyo jin an dafa kafaɗar ta.
kallon fa'iza dake tsaye a bayanta tayi
“Fa'iza yaushe ki ka shigo?”
“mom yanzu na shigo ina ta ƙwala sallama ba kijini ba, mom dan Allah ki daina sa damuwa a ranki kar wani abun ya same ki, in sha Allah momy zata fito”
ajiyar zuciya ta sauke,hannu fa'iza tasa ta shiga guge mata hawayen dake zuba daga idonta tana sake bata haƙuri, jan hannunta tayi su ka nufi sofas ɗin dake wurin.
Zama su kayi suna fuskantar juna
“mom in sha Allah zata fito, mom kinfi kowa sanin yanke mata hukuncin ɗaurin rai da rai ba shike nuna gaskiya baza tayi halinta ba,ba kuma shi ke nuna ba zata iya fitowa wata rana ba, dan Allah ki kwantar da hankalin ki”
“Nagode fa'iza” shine kawai abun da brisster tace
“mom kinfi ƙarfin haka a waje na fatana dai ki rage damuwar a zuciyar ki, sannan nayi maki Alƙawari mom zan tayaki da Adu'a Allah ya bayyanar da gaskiya”
“Ameen fa'iza”
“sannan mom ina mai baki haƙuri akan abun da mamy tayi maki, bata kyauta ba dan Allah kiyi haƙuri”
murmushi brisster ta saki yarinyar akwai shiga rai ta na matuƙar burgeta
“fa'iza kenan idan da sabo ai yaci ace na saba da hakin mamyn ku, karki damu abun da tayi man kwata kwata bai ɓata man rai ba”
“shikenan mom amma duk da haka ina mai baki haƙuri a madadinta” murmushi brisster ta saki
trayn data shigo ta nufa, ruwa ta tsiyaya mata a cup
“mom gashi kisha, na sa chefs su haɗa maku breakfast dan na san haka ku ka fita bakuci komai ba”
”nagode fa'iza Allah ya biyaki da mafificin Alkairi”
“mom dan Allah ki daina gode man”
“ya zama dole ne fa'iza”
“ni dai dan Allah ki daina gode man, nifa ƴarki ce kuma mom kin san cewa babu godiya tsakanin iyaye da ƴaƴansu” murmushi brisster ta sake saki tana zubama fai'za ido, fa'iza badai iya tsara kalamai masu daɗi ba.
Turo ƙofar bedroom ɗin a kayi, da sauri su ka kai duban su ga ƙofar
a tsaye ya ke ya harɗe hannuwan shi a ƙirji,Army green ɗin shirt ce a jikinshi haɗe da Army trouser wanda ya tsaya mashi iya gwiwa , babban mutum ne da a ƙalla zai kai kimanin shekaru 56 zuwa da 8 a duniya, dogo ne sosai yana da jiki, ƙaƙƙarfa ne na gaske kamar ba dattijo ba, a ido idan ka kalleshi baza kace shi ke da waɗannan shekarun ba,fari ne kyakyawa kallo ɗaya za kayi mashi ka hango kamaninshi da fa'iza da yumnah,da gudu fa'iza ta nufe shi, faɗawa tayi jikinshi
“good morning dady”
murmushi ya saki yana jan kumatunta “har yanzu baki san kin girma ba ko fa'iza?, kina abu sai kace yumnah” ɓata fuska tayi kamar ƙaramar yarinya “dady nice ma yumnah” zuba masu ido brisster tayi tana kallon su baƙaramin birgeta suka yi ba, raba jikin su yayi yana faɗin
“ƙwarai ma kuwa”
cikin ɗakin ya ƙarasa, ƙofar fita fa'iza ta nufa tana faɗin
“mom sai na dawo, dady ka barta ta kwanta ta huta ta gaji” ta faɗa tana jan handle ɗin ƙofa
“na lura fa'iza kin raina ni da yawa” dariya tayi tana jan ƙofar ta fice, murmushi kawai mom tayi tana girgiza kai.
bakin bed dady ya nufa,zama yayi yana zuba ma barrister ido, ɓata fuska tayi kamar zata fashe da kuka ta nufeshi, tana ƙarasowa gabanshi faɗawa tayi jikinshi tayi hugging ɗin shi,hannu biyu yasa ya zagaye bayanta,shafa doguwar sumar kanta ya shiga yi
“Barrister lafiya?”
saukar hawayenta yaji a saman chest ɗin shi, da sauri ya ɗago da fuskar ta yana kallo,hawaye ya gani suna zarya a kumatun ta.
hannu yasa ya shiga share mata su “gaskiya ƙarshen wannan aikin naki ya zo,bazaiyu a riƙa sa man mata kuka ba, dole ki ajiye wannan aikin dama ba so nake ba saboda kin dage kina so ne kawai yasa na barki”
“sir kar kace haka,wannan aikin da nake ban san iya adadin ladar da nake samu ba, zaka so ka zama sanadiyyar yankewar wannan ladar?”
“amma kullum sai su riƙa sa man ke kuka, bana jin daɗin hakan?”
“ba laifin su bane kukan ne dole nayi, ina ji ina gani na kasa taimakon Aminiyata kotu ta yanke mata hukunci ba tare da ta aikata laifin ba”
“karki damu,in sha Allah komai zai daidaita yanke mata hukuncin ai ba yana nufin shikenan ba,ki dai na kuka kinji bana so”
wasu hawayen ne su ka sake zubuwa, ɗan bubbuga bayanta ya shigayi “ya isa haka, idan ba nima nawa hawayen ki ke son gani ba”
hannu tasa tana share hawayen “na daina”
“yawwa ko ke fa,ina ita yarinya Asma'un?”
“dama ina so na nemi wata Alfarma a wurin ka”
“Alfarma kuma?”
“Eh,dangin mahaifiyarta sun so tafiya da ita amma nace A'a saboda karatunta zata zauna anan in yaso sai su riƙa tafiya tare da yumnah,kuma dai gaskiya ina son ta zauna a tare da ni sai tafi samun kulawa sama da can, zata iya zama nan ba matsala?” jinjina kai yayi
“dama makarantar su ɗaya da yumnah ne?”
“eh school ɗin su ɗaya”
“shikenan ba damuwa, zata iya zama a nan ɗin ai kema tamkar mahaifiya ki ke a gareta”
“haka ne, nagode sosai Allah yasa da Alkairi”
ɗan ɗaure fuska yayi
“ni ki ke ma godiya zulaihat?”
“eh mana, idan an kyautata maka sai ka gode ai ba wani abu bane”
“to bana so, nan ɗin gidan ki ne kina da ikon ajiye duk wanda ki ke so, idan kuma ki ka sake godeman to ni da ke ne” murmushi tayi tana kwantar da kanta saman shoulder ɗin shi
“zuwa anjima ina so zanje prison dan na duba jikinta,his excellency yanke jiki fa tayi ta faɗi na shiga tashin hankali matuƙa a lokacin”
“Allah ya kaimu anjimar sai mu tafi tare, Allah ya bata lafiya”
“Ameen ya Allah”
𝑄𝑢𝑒𝑒𝑛 𝐾𝑎𝑖𝑛𝑒𝑟𝑡..... ✍💫
Baƙar motar ce ƙirar benz ta tukaro gate ɗin estate ɗin,sanin halin mamallakiyar motar ne yasa tun kafin motar ta ƙaraso sojojin dake gadin gate ɗin su kayi hanzarin buɗe mata ƙofa,babu ɓata lokaci ta danna kan hancin motar zuwa ciki,ɗaya daga cikin gidajen motar ta nufa,a parking space ɗin duplex ɗin data nufa tayi parking,dai daita parking tayi, kafin aka buɗe motar ƙafarta ta zuro kafin ta fito gaba ɗayanta,iska ta shaƙa ta fesar, hannu ta zura ta ɗauko hand bag ɗinta, main entrance ɗin duplex ɗin ta nufa bayan ta rufe motar, sai ya mutse fuska take alamar ta gaji.
Wani madanni ta danna jikin ƙofar, nan take ƙofar ta buɗe, ciki ta kunna kai,mash Allah na furta a yayin da nayi arba da haɗaɗɗen parlorn data shigo, komai na cikin shi ya kasance light brown, faɗa maku haɗuwa da tsaruwar parlorn ɓata lokaci ne,babu kowa a parlorn sai mai aiki dake ƴan goge goge,jin ƙarar buɗe ƙofa ne yasa mai aikin ɗagowa, ganin wacce ta shigo ne yasa ta nufota da sauri,hannu ta miƙa da nufin amsar jakar dake hannunta tana faɗin
“good Afternoon ma” wani ɗan iskan kallo mai haɗe da harara ta watsa ma mai aikin, saurin sadda kai ƙasa mai aikin tayi tana ja da baya,tsaki taja tana nufar stairs case dake parlorn.
da kallo kawai mai aikin ta bita har ta ɓacce ma ganin ta,taɓe baki tayi tana komawa kan aikin dake gabanta, a bakin ƙofar wani ɗaki ta tsaya, tura ƙofar tayi ta shiga,wani haɗaɗeb bedroom ne ta shigo komai na cikin shi ɗan dai dai babu haya niya, ciki ta ƙarasa tana kiran sunan
“Aunty laatifa! am home where are u” matashirya mata ta hango zaune kan study chair yayin da laptop ke a saman desk tana operating.
“Aunty nah sarkin aiki,a gidan ma baki huta ba, gaskiya mijinki ya shiga shiga uku na san a daren ku ma nafarko kwana za kiyi kina aiki, shiyyasa momy ke ce maki agogo sarkin aiki”
juyowa tayi masha Allah na faɗa da ganin wannan madarar kyan, laatifa kyakyawa ce ajin farko,riga da wando ne a jikinta masu taushi, kanta babu ɗan kwali tayi parking gashinta a tsakiyar kai, medical glass ɗin dake idonta ta cire.
“ƙanwata idan ban yi aiki ba mi ki ke so nayi?”
“gaskiya kina aje wa kina hutawa”
“shikenan, ya gajiyar aiki?” ya mutse fuska tayi yayin da take samun wuri bakin bed ta zauna
“aiki babu daɗi” murmushi laatifa ta saki wanda ya ƙarama kyakyawar fuskarta kyau
“gaskiya Balqis kin cika raki, miye abun gajiya a wannan aikin ke da kina bayan mota kina shan iskar Ac”
“haka za kice mana tunda ke kin saba, duk ranar dana sha court za kice haka”
“ba wai zan ce ba haka ne ma, kawai dai kin cika raki”
“shikenan naji ina alƙawari na?”
“yanzun nan na gama tura mashi saƙo ta email kin san baya ɗaukar kira ba tare da ka fara tura mashi saƙo ba”
“haka ne, amma ai ke naga kuna waya”
“wannan ai shi ke kirana, amma duk lokacin da ni nake son magana da shi sai na fara tura mashi saƙo tukun” taɓe baki Balqis tayi
“shi dai komai nashi na daban ne”
“classic boy ake faɗa maki dole komai nashi ya kasance unique,ke dai kawai ki dage da Adu'a dan akwai aiki a gabanki”
“ni kaina na sani Aunty laatifa abun har tsoro yake bani”
“karki damu nima zan tayaki da adu'a ”
“in sha Allah, bari na tafi ɗakin momy bata san na dawo ba, nan na fara shigowa”
“ok anjima zaki bani labarin yanda ƙarar ta kasance”
“kin ma tuna man, wallahi dady ya ganni ba kiga harar da ya watsa man ba kamar ƴan hanjin ciki na su faɗo” dafe ƙirji laatifa tayi
“nashiga uku!! dan Allah da gaske ki ke”laatifa ta faɗa da tsantsar tashin hankali
“wallahi kuwa na san dole yaji ba'asin abun da ya kaini, amma zanyi duk yanda zanyi ganin bai gane ke ki ka tura ni ba”
“yawwa dan Allah kice ra'ayi ki ka yi ba ni nace kije ba”
“in sha Allah karki damu”
“yawwa na gode” ƙofar fita Balqis ɗin ta nufa tana ƙara jaddadamata karta damu.
zama tayi bakin bed dafe kanta“ya Allah” ta furta,da alama hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba jin dadyn su yaga Balqis.
Balqis tana fita daga ɗakin wani ɗan corridor ta nufa, wani ɗan madaidaicin parlor ta shiga,a zaune take saman sofa mai mazaunin mutum biyu les ne a jikinta ɗinkin half bubu da zani, hannunta da wuyanta sun sha adon zinari, wayace kare a kunenta da alama waya take
“lamari ai baiyi daɗi ba, in sha Allah anjima idan Barrister ya dawo zan tambaye shi naje nayi mata jaje ai abun ayi jaje ne” murmushi Balqis ta saki tana ƙarasawa cikin parlor.
faɗawa tayi saman jikinta“momy na dawo” da sauri ta janye wayar daga kunenta “ja'irar banza kin girma amma baki san kin girma ba, ba ki gani waya nake, karya ni ki ke son yi?” tashi tayi zaune tana turo baki“momy daga nayi kewarki zaki rufe ni da faɗa”
“an rufeki da faɗa, dan gidan ku haka ake kewa kina shirin karya ni”
“ke momy haka ki ke daga abun arziƙi sai ki rufe mutum da faɗa na san da dady ne bazai ce man komai ba”
"ai shi ki ka ce ƙashin shi ƙwari ne gare shi” ficewa Balqis ɗin tayi daga parlorn tana gungunai.
Mai da wayar tayi a kunne “kina jina da wannan ja'irar yarinyar tana neman karya ni”bana jin mi na cikin wayar ke faɗa
“to shikenan idan Allah yasa mun haɗu anjimar to shikenan, idan kuma bamu haɗu ba sai ranar friday kenan idan mun haɗu a part ɗin Abbah” jinjina kai tayi kafin daga bisa ni su kayi sallama.
*UNITED STATE*
_*Las Vegas (Nevada)*_
_*Nailarh Racing Track (N.R.T)*_
Ƙaton track ne gari guda wanda girmanshi zai kai girman wani babban ƙauyen,kallo ɗaya zaka ma wurin ka hango tsirarar dukiyar da aka kashe wajen gina shi,
ta ko ina ka duba mutane ne zazzaune a saman chairs gaba ɗaya hankalin su naga wasan da ake gabatarwa,kowa burinshi nashi yayi nasara,duka mutanen dake wurin suna sanye ne da polo shirt white color wacce a gabanta a kayi rubutu da ɓakin fenti in da aka rubuta QUEEN da manya haruffa daga saman shirt ɗin logo ne na sunan center ɗin ( N R T) sai p_cap da hat wanda suma aka rubuta QUEEN a jikinsu kamar na shirt ɗin,maza ke sanye da p_cap yayin da mata ke sanye da hat wacce aka yi mata kwalliya da gashin tsintsaye a samanta, Al'adar wurin wasan ce duk wanda zai shiga sai an bashi wannan shirt da cap ya sa wanda kyauta ce daga mamallakiyar wurin wasan.
dawakai ne kyawawan gaske ke gudu a tsakiyar filin,yayin da mamallakansu ke saman su jikin su sai salƙi yake yana ɗaukar ido,color uku ne dawakan wasu brown yayin da wasu su ka kasance baƙaƙe doki ɗaya ne a wurin ya kasance white color,daga yanayin tsarin dokin zaka san na musamman ne, a jere su ka fara gudun,cikin ƙwarewa da karsashi dawakan ke gudun abun gwanin ban sha'awa,abun dai sai wanda ya gani,rabuwa su ka fara yi da junan su, dawakai uku ne su kayi gaba yayin da su ka bar sauran a baya harda wannan farin dokin yama fisu yin baya sosai sama da sauran dawa kan,sosai su ke gudu dan kaiwa ga matsaya,miƙewa tsaye mutane su ka fara yi da alama dawakan nan gudu uku na daban ne, mutane na da buri a kan su.
Wasa fa ya fara ɗaukar zafi dawakan kansu su ukun sun rabu da juna yanzu biyu ne a gaba ɗayan a baya.
“da alama dai yau tarihin N R T zai canza, ban taɓa ganin wasa irin wannan ba” cewar wani bature dake zaune cikin ƴan kallo, murmushi gefen baki mace dake gefen shi ta saki tana faɗin
“ba abu bane mai yuwuwa canza tarihin N R T cikin sauƙi, a ko wane lokaci da sabon salo take zuwa, kana tunanin wannan baya bayan da tayi babu wata a ƙasa?” taɓe baki yayi yana ɗaga kafaɗa
“i don think,tazarar tayi yawa duba kiga in da su Ryder su ke kalli in da king yake”murmushi matar ta saki
“dear sai kace yau ka fara zuwa kallon wasan N R T”
“ba yau na fara zuwa ba, but wasan yau ne ban taɓa ganin irinshi ba”
“to ka zuba ido za kace na faɗa maka”
“okay” ya faɗa yana mai da glass ɗin shi daya cire.
ran wani magidanci ne daga cikin ƴan kallo ya fara ɓaci,sign matar wannan baturen tayi mashi, duban shi ya kai ga mata da majin
“bazan taɓa ƙyale Anthony ba idan har kuɗina su ka lalace” ya faɗa da alamar ranshi ya ɓaci“but why?” matar shi ta tambaya
“babu alamun zanyi nasara,kin kuma san dama ba da san raina na zuba kuɗi na a wasan nan ba, idan har kuɗina su ka salwanta bazan ƙyale shi ba”
“just bcox of five hundred thousand dollars kake wannan maganar akan brother nah?”
kallonta yayi da mamaki“its not a money?”
“no it's money, but ai kafi ƙarfin su, kuma banyi tunanin zaka iya furta wannan maganar akan Anthony ba”
“it's not my concern,kuɗina kawai na sani”
“sai ka bari idan kaga ba kayi nasara ba sai ka faɗi duk abun da zaka faɗa,ai har yanzu wasan ake”
murmushi takaici mutumin ya saki
“oh wai kina nufin har yanzu kuna da sa rai a wannan wasan,ƙazamin tunani kawai” ya faɗa yana kauda kanshi gefe, haɗa ido su kayi da wannan matar da mijinta, a tare su ka sakar mashi murmushi suna ɗaga mashi hannu, shima hannun ya ɗaga masu yana maida kanshi ga wasan.
Murmushi matar tayi“mi na faɗa maka kowa ya san cewa canza tarihin N R T ba abau bane mai sauƙi, ka dai ji wance magidanci ya saduda ta ƴan kuɗaɗen shi kawai yake” ta faɗa tana sakin murmushi, murmushi shima mijin nata yayi yana jinjina kai da faɗin“na tabbata...
_*Episode 7_8*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
_____________________________
Murmushi matar tayi“mi na faɗa maka kowa ya san cewa canza tarihin N R T ba abau bane mai sauƙi, ka dai ji wance magidanci ya saduda ta ƴan kuɗaɗen shi kawai yake” ta faɗa tana sakin murmushi, murmushi shima mijin nata yayi yana jinjina kai da faɗin“na tabbata”
mai da hankalin su su kayi akan wasan,wasan ne ya fara canza salo kamar walƙiya sai ga dokin dake baya sama da ko wane doki ya zama shine a tsakiyar dawakai biyun dake gaba, kamar a mafarki masu kallon wasan ke kallon ikon Allah,tashi wannan magidanci yayi yana jan tsaki ya kalli matar shi
“kin dai ji abun dana faɗa maki sisi na ban yarda tayi ciwo ba” yana gama faɗa ya bar wurin gaba ɗaya, taɓe baki matar tayi ita har a lokacin ba taga wani alamar rashin nasara ba tunda dai ba'a gama wasan ba.
fita dokin yayi daga cikin jerin dawakai biyun daya shiga ya zama shine ke biye da dokin dake gaba sai dai akwai ƴar tazara a tsakaninsu,sosai dawakan ke gudu cike da karsashi suna tunkarar matsayar wasan in da ya kasance nan ne ƙarshe duk wanda ya riga isa shine ya lashe gasara.
hankalin mutane dake sa ran cin gasar ne yayi matuƙar tashi, tuni zufa ta shiga wanke wasu daga cikin su saboda maƙudan kuɗin da su ka zuba wanda suke ganin suna gab da yin asara,seconds Biyar ya rage a kammala wasan,bai wuci taku kaɗan ya ragema dokin dake gaba ya isa matsayar wasan, kamar walƙiya wannan farin dokin ya gita ta gabanshi ya riga shi isa matsayar, da sauri ma hayin dokin yaci birki rai a ɓace ga ci yana gani amma ya rasa.
Ihu da sowa ne ya fara tashi a wurin wasan haɗe da kiɗe kiɗe, a fusace ɗai ɗai kun mutane su ka fara tashi suna barin wurin wasan,birki dokin yaci cike da kuzari mamallakin dokin ya sauko, da sauri wasu matasan ƴan mata su biyar suna sanye da riga da skirt iya gwiwar su, rigar white color yayin da skirt ɗin ya kasance black color aƙalla kowace a cikin su zata kai kimanin shekara 28 zuwa 30,cikin filed ɗin su ka nufa a gaban wannan dokin su ka tsaya ɗaya na riƙe da water bottle yayin da wata ke riƙe da ɗan ƙaramin towel wacce tafi kowa girma a cikin su ce take goye da backpack sauran biyu babu komai a hannun su sai sakin murmushi su ke, wani matashi sauarayi ne ya amshi dokin, helmet ɗin dake kanta wacce aka rubuta Queen a jikinta ta zame tabarakallahu ahsanul kaliƙin na furta da ganin wannan maƙurara kyan.
fara ce tas doguwa kyakyawar gaske wacce idan akace kyau to fa anazuwa kanta an rufe babin kyau,tana da idanuwa masu matuƙar jan hankali launin Acme white grey sai sheƙi su ke ga zira ziran eye lashes ɗinta da su ka ƙara ƙawata su,tana da siraran laɓɓa launin light pink masu matuƙar taushi tana da ɗan tsayin fuska hancinta a tsaye yake kem,tana da cikar gashin gira sai dai ba sosai ba,kanta ta ɗan girgiza yayin da take zame ɗan ƙaramin ribbon ɗin data ɗaure gashin kanta nan take wavy hair ɗinta launin light golding brown ta tarwatse a gadon bayanta ,tana da shape mai matuƙar ɗaukar hankali skin ɗinta sai sheƙi take tana salƙi kamar hasken rana bai taɓa raɓarta ba.
kissing neck ɗin dokin tayi tana ɗan sakin murmushin gefen baki har sai da dimples ɗinta su ka lotsa sosai murmushin ya ƙarama kyakyawar fuskarta kyau
“madam water”ɗaya daga cikin matan ta faɗa tana miƙa mata water bottle ɗin dake hanunta mai kyan gaske wacce a jikinta aka rubuta Queen, ya mutse fuska tayi ba tare da ta ko kalli in da matar take ba,wacce ke riƙe da towel a hanunta ce ta matsa kusa da ita daddaɗan ƙamshin turaren ta ne ya daki hancin matar har sai da ta lumshe ido duk da zufar da tayi haka bai hana dawwamamman ƙamshinta fita ba, a hankali ta shiga goge mata zufar da tayi,jefi jefi mutane su ka shiga ƙarasowa cikin field ɗin suna mata congrat yayin da take ya mutse masu fuska ba tare da ta amsa masu ba hakan bai dame su ba saboda sanin halinta sunma samu sa'a yau da har ta tsaya harma take yamutse masu fuska.
barin wurin matashi yayi da dokin, ɗaga ma dokin hannu ta shiga yi tana faɗin“ i miss u” murmushi matan su ka saki,fly kiss ta ma dokin tana sakin murmushi,bata bar wurin ba har sai da ta daina ganin dokin tukun ta bar wurin yayin da matan ke biye da ita har gaban wasu motoci guda bakwai,guda shidda rang robbers ne yayinda su ka saka wata farar Rolls Royce tsakiyar su sai ɗaukar ido take,body guards ne tsaye a bakin motocin Aƙalla za su kai su biyar ban da drivers ɗin da da su kayo driving motocin,cikin girmama su ka shiga gaishe da ita suna tayata murnar lashe wasan, babu wanda ya samu arziƙin data amsa mashi sai ma nufar wannan fara rolls royce ɗin dake tsakiyar motocin tayi, da sauri ɗaya daga cikin su ya buɗe mata back seat ta shiga,komawa su kayi cikin motocin harda wannan matan,a jere su ka hau wani dogon titi a cikin wurin wasan.
A kishingiɗe take a cikin motar ta lumshe idanunta yayin da sanyin Ac ke ratsata, tafiya mai ɗan nisa su kayi kafin su ka nufo wani katafaren gate ga wasu irin jibga jibgan security guard a bakin shi, horn driver dake gaba yayi, babu ɓata lokaci security guard ɗin su ka buɗe masu gate,da gudu motocin su ka kunna kai ciki security guard ne ke kai kawo ta ko ina na wurin, titi ne su ka sake miƙewa shantal, wani ɗan ƙaramin gate na ɓakin ƙarfe wanda ya kasance shara shara kana iya hange ciki su ka nufo, wani remote driver dake gaba ya danna nan take gate ɗin ya buɗe ciki su ka kutsa kai ciki.
masha Allah na furta da ganin irin haɗuwar wurin ,ƙatafaren luxury skyscraper ne iya ganinka, ta ko ina ka kallah a jikin ginin gilasai ne masu matuƙar ɗaukar ido A ƙalla yana da sassa guda shidda,harabar gidan kanta abun kallo ce lion water fall ne a tsakiyar gidan yayin da yake fitar da ruwa da styel daban daban, security guard ne ke kai kawo a ko ina na harabar gidan.
A bakin skyscraper ɗin su kayi parking da sauri ɗaya daga cikin security guard ɗin ya fito ya buɗe mata car door,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fitowa,gaba ɗaya matan gaban motar da take ciki su ka zo su ka tsaya, a hankali ta zuro ƙarta kafin ta fito gaba ɗaya, security guard ɗin dake kai kawo ne su ka shiga rissinawa suna gaishe da ita, hannu kawai ta ɗaga masu kafin a hanzarce ta nufi gidan matan nan na take mata baya,a bakin main entrance ɗin gidan suka tsaya,wata irin haɗaɗiyar ƙoface ta glass,sai ta fuskarta tayi a jikin wata na'ura dake manne jikin ƙofar wacce nake kyautata zaton face ID ne magana na'urar ta fara cikin harshen turanci
“welcome back home miss NAILARH”
zugewa ƙofar ta shigayi, kutsa kai su kayi ciki, wani katafaren parlorn ne su ka shigo,painting cikin shi sliver glod ne, an ƙawatashi da manya manyan sofas jigunannun gaske masu matuƙar taushi da daɗin zama set huɗu sai throw pillows dake kan ko wace sofa, daga tsakiyar parlorn round glass table ne an jera flower vase masu matuƙar kyau, daga saman ceiling ɗin ginin crystal chandeliers ne golding color masu girman gaske an ƙawata su da kwalliya, sai faskekiyar flat creen tv mai matuƙar girma ta mamaye kusan rabin bangon da take sai kayan sauti dake gefe da gefen tv, sparkling floor lamps ne ajiye a ƙasa suna bada haske mai launika daban daban, ga dogayen curtains wanda aka ƙawata da zanen furanni kewaye da parlorn an zuge su,idan ka kalli ƙasan parlorn wanda ya kasance na glass wasu irin kifaye ne masu launika a jikin su suke shawagi.
komai na cikin parlorn golding color ne hatta stairs case ɗin dake ciki,A ƙalla floor ɗin na ɗauke da parlor biyar harda wannan wanda ya kasance shine babba a cikin su kuma yake a tsakiyar su, daga cikin parlorn zaka iya hangen sauran falukan dake floor ɗin,masu karatu ba ƙaramar dukiya aka kashe a wajen haɗa wannan parlorn ba idan nace sai na fayyace maku komai dake cikin shi to tabbas anan book one zai ƙare,kawai ku ida ƙissma sauran a zuciyar ku.
ma'aikata ne ke kai komo a cikin parlorn, zubewa su ka shigayi akan gwiwowunsu suna kai gaisuwa gareta, ko kallon in da suke ba tayi ba.
glass elevator su ka nufa,ɗan yatsanta tasa a jikin na'ura dake jikin ƙofar elevator nan take ƙofar ta buɗe, ciki ta shiga tana lumshe idanunta alamar gajiya,mara mata baya ma'aikatan su kayi,ɗaya daga cikin ma'aikatan ce ta danna wasu madanni dake ɗauke da nombobi a jikin su,ƙofarce ta shiga zuge, sama elevator tayi da su, daga ta ciki zaka iya hangen manya manyan parlor kan da suke wuce masu matuƙar kyau wanda tsayawa fayyace su har littafin ya ƙare ba'a gama faɗar kyawu da haɗuwar su ba, tsayawa elevator yayi da alama sun kawo in da za su tsaya, ƙofar ce ta shiga zugewa,sai data gama zugewa tas tukun tasa kai ta fice ma'aikatan na biye da ita kamar wasu jela.
nan ma wani katafaren parlorn ne su ka shigo wanda yafi na farkon haɗuwa sai dai bai kaishi girma ba,ma'aikatan ne nan ma ke kai kawo, take su ka shiga zubewa ƙasa suna gaishe da ita, hannu kawai ta ɗaga masu yayin da take yin gaba, a bakin wata katafariyar ƙofa su ka dakata, ɗaya daga cikin matan ce tayi saurin miƙa mata wayarta dake hannunta, amsa tayi yayin da take ɗaura tafin hanunta saman na'urar dake jikin ƙofar, zanen hannunta ne ya fito a jikin na'urar ,scanning hannunta na'urar ta shigayi na tsawan secon biyar kafin na'urar ta fara magana kamar ta ƙofar da su ka fara shigowa yayin da ƙofar ke zugewa.
sai da ƙofar ta gama zugewa tas tukun ta kunna kai zuwa ciki yayin da matan guda biyu ke biye da ita sauran su ka kama gaban su, wacce ke ɗauke da backpack ce ta bi bayanta sai ɗaya wacce take riƙe da towel ɗin data goge mata jiki.
wani irin katafaren bedroom su ka shigo a ƙalla girman shi ya isa ayi ɗan ƙaramin plat house saboda girma da faɗin shi, bedroom ɗin yana ɗauke da king size bed light golding, gadon na shimfiɗe da tattausan bedsheet da ƙaton blanket mai azabebben taushi ga jerin pillows wanda su ka kusa cinye kwata gadon,
gefe da gefen gadon nightstand ne mai ɗauke bed sides lamps daga gaban gadon ottoman table ne mai ɗauke da drawer chest a jikin shi daga saman shi anyi mashi kwalliya da wasu stones masu sheƙi an mamman a jikin shi.
daga ƙasan gadon wani haɗaɗɗe rug ne mai gashi gashi a jikin shi tsabar taushin shi har bacci mutum zai iya a kanshi ba tare da ya fahimci ba'a katifa yake ba,idan ka kalli saman ɗakin wani irin ƙaton chandeliers ne,daga hannun dama na ɗakin glass sliding door ce wanda nan ma wani bedroom ɗin ne sai dai komai na cikin shi white color ne, daga ɗayan ɓangaren kuma wani haɗaɗen stairs case ne can ma saman wani bedroom ɗin ne sai dai bai kai wannan dana kusa da shi girma ba, daga ɓangaren haggun ɗakin wasu ƙofofi ne guda uku a jere ɗaya bathroom sai spa and saloon wanda yake haɗe massege spa sai ɗaya ƙofar dressing room ne wanda idan ka shiga cikin shi zaka ɗauka boutique ne.
wacce ke goye da back pack ɗin ce ta nufi laundry room,ɗurƙusawa ɗayar tayi a gabanta takalamin ƙafarta ta shiga cire mata, zama tayi saman ɗan stool hakan ya bata dama wurin cire mata takalmin, bayan data gama cire takalmin,sama nailarh ta ɗaga hannunta hakan yaba matar damar cire mata rigar dake jikinta tayi ta barta daga ita sai bra ta ajiye gefe kafin ta koma kan wandon, wandon shima zame mata shi tayi shantala shantalan cinyoyinta ne su ka bayyana farare tas da su sai sheƙi su ke kai kace haske rana bai taɓa ratsasu ba,kwashe kayan matar tayi ta nufi laundry room da su,a tare su ka fito daga laundry room ɗin ita da wacce ta fara shiga sallama su kayi mata su ka fice daga ɗakin.
A kasalance ta shiga taka ƙafafunta tana nufar ƙofar toilet, tafiya take kamar bata son gaka ƙasa tana tafiya ko ina na jikinta na juyawa musamman ƙugunta da zanen rose flower na tattoo ya ƙarama fatar bayanta kyau,tun kafin ta ƙaraso bakin ƙofar ta shiga zugewa kutsa kai tayi ciki,wani irin bathroom mai girman gaske komai na cikin shi expensive ne,harda silver bed mai ɗauke da rober mattress mai haɗe da pillow sai daga jikin bangon toilet ɗin glass drawer ce mai girman gaske an rarrabata gida gida wanda bakomai ne a cikinta ba sai tarin shower gels,soaps,shampoos, towels, bathrobes,sponges da flip flops.
ƙofa biyu ce a toilet ɗin da wadda ta shigo sai wata dake can ɗayan ɓan garen , silver bed ɗin ta nufa kwanciya tayi rub da ciki tana sauke ajiyar zuciya,wasu irin abubuwa ne a jikin ɗayar ƙofar masu kama da bulbs haske su ka shiga kawowa suna fitar da wani irin sauti can kuma su ka daina suna sanar da isowar lolah da larah,a hankali ta furta open ba tare da ta ɗago ba, zugewa ƙofar ta shiga yi, wasu matan turawa ne su ka shigo manya da su kamar ƴan wrestling,baƙin mini skirt ne a jikin su tare da farar shirt ajikin rigunan su an rubata sunayen su da wani irin style, haka shigar ma'aikatan gidan take.
in da take su ka ƙaraso gaishe da ita su kayi suna ɗan rissinawa,bata amsa masu ba hakan bai dame su ba idan da sabo sun saba da halin uwar gidan ta su,lolah ce ta nufi glass drawer ɗin nan, buɗewa tayi ta ɗauko shower gel tare da soap da shampoo da sponge,a saman wani ɗan table mai ƙafafu ta ɗaura, maida ƙofar drawer tayi ta rufe turo table ɗin tayi zuwa gaban bed ɗin, ɗaukar shampoo larah tayi, buɗe marfin tayi ta shiga tsiyayama Nailarh shi a kai, bayan data gama ne tashiga cuɗa mata kan sai data tabbatar ya wanku tukun ta jawo hand shower ta shiga wanke mata kan, bayan data gama ne ta ɗauki shower gel ta shiga zubawa a ko ina na jikin Nailarh,sponge sock lolah ta saka a hannun ta larah na gama zuba shower gel ɗin ta shiga mulka mata mashi a ko ina na jikinta, ko motsi Nailarh ba tayi kamar matatta su ke juyata yanda su ke so dan su wanko ko ina na jikinta.
sangarta da gata ne yasa Nailarh ko wanka bata ma kanta ba wai dan bata iya ba isa ce kawai da lalacewa tasa bata iya yi da kanta musammusam ta ajiye lolah da larah dan su riƙa yi mata wanka wanda aikin su ke nan a gidan, daga wankan ta da yi mata massege sai gyaran jiki babu abun da su ke iya aikin su kenan.
ta ɗauki tsawan lokaci tana cuɗa mata jikinta sai data tabbatar ko ina na jikinta ya wanku tukun larah ta jawo hand shower ta shiga wanke mata jikin bayan data gama ne ta ɗauko hairdryer ta shiga busar mata da gashin kanta bayan data kammala busar mata da kan ta nufi glass drawer ɗin nan ta ɗauko bathrobe da flip flops ta dawo a bakin bed ɗin ta ajiye mata, a kasalance Nailarh ta sauko daga saman bed ɗin,flip flops ɗin ta zura a ƙafarta, miƙa mata bathrobe ɗin tayi , ƙarɓa tayi da kanta ta zura kafin ta cire hook ɗin bra ɗin dake jikinta ta ciro a ƙasa ta yarda ita kafin ta warware igiyar pant ɗin shima nan ƙasa ta sake shi, igiyar bathrobe ɗin ta ɗaure ƙofar fita ta nufa ba tare da ta ko kalli ɗaya daga cikin su ba.
bra da pant ɗin lolah ta kwashe ta nufi dustbin ta saka Nailarh tana da wata ɗabi'a ta rashin maimaita sutura idan har kaga ta maimaita sutura to ba ƙaramin sonta take ba bra da pant dama su daga idan ta cire su to sun zama wasted bata ƙara amfani da su,gyra toilet ɗin su kayi su ka maida komai mazaunin shi sannan su ka wanke toilet ɗin duk da ba datti yayi ba bayan da su ka gama ƙofar da su ka shigo su ka nufa tun kafin su isa ƙofar ta buɗe alamar an basu izinin fita, ficewa su kayi.
Nailarh tana fita daga toilet ɗin wannan sliding glass door ɗin ta nufa tana isowa ƙofar na buɗewa, ciki ta kutsa kai sai wani lumshe ido take, nan ma bedroom ne komai na cikin shi white color ne , babu wata hayaniya a cikin shi bed ne sai nightstand dake ɗauke da bedside lamps sai rug mai taushi dake shimfiɗe a ƙasa sai chaise lounge chair dake bakin wata ƙatuwar glass sliding door wacce da an buɗeta zata sadaka da ƙyataccen swimming pool wand kusan haɗe yake da ɗakin ƙofar ce kawai ta raba su sai ruwan da suke a kewaye daga bakin swimming pool ɗin lounger chairs ne guda biyu suna fuskantar juna sai daga can ɗan nesa da su ball chair ce daga gabanta ɗan madaidaicin glass table ne.
nightstand ɗin ta nufa ear phone ɗin dake ajiye ta ɗauka tare da eye mask,bed ɗin ta dawo a kune ta sa ear phone ɗin kafin ta rufe idonta da mask ɗin, faɗawa tayi saman bed ɗin ta ɗaura kanta saman pillow tana saka ɗaya tsakankanin cinyoyinta yayin da ta rungume ɗaya a haka bacci yayi awan gaba da ita yayin da waƙar data kunna a ear phone take ratsa ƙwaƙwalwarta, Al'adarta ce bacci tana sauraron sauti.
_*ABUJA . NIGERIA*_
_*G J I ESTATE*_
momy da laatifa ne zaune saman sofa da alama fita za su yi,momy ta ɗau wankan swiss lace maroon color ta yafa mayafi saman kanta, wayace kare a kunenta da alama waya take laatifa na daga gefenta zaune saman sofa mai mazaunin mutum ɗaya ta ɗau wankan black abaya tayi rolling da gyalenta simple make_up ne a fuskarta sai medical glass ɗinta dake ƙarama kyakyawar fuskarta kyau,wayar tace riƙe a hanunta tana aikin latsawa, janye wayar momy tayi daga kunenta tana ɗan jan tsaki
“du kace zaka fita tare da Balqis sai ta ɓata maka lokaci,gaskiya tafiya zanyi na barku ni driver ya kaini idan ta gama shiriritar kun ta ho”
momy ta faɗa tana miƙewa tsaye ta ɗauki hand bag ɗinta, tashi laatifa tayi itama tana ɗaukar hand bag ɗin ta “baza ki tafi ki barni ba momy, tare zamu tafi ita driver ya kaita
“gani nan bama sai an tafi an barni ba” Balqis ta faɗa yayin da take taka stairs case tana nufo parlorn, Abaya ce a jikinta tayi rolling gyalen kamar yanda laatifa tayi tana riƙe da hand bag a hannunta fuskarta tasha uban make_up ba ƙaramin kyau tayi ba.
harara momy ta watsa mata tana nufar ƙofar fita daga parlorn, murmushi Balqis ta saki yayin da ta ƙarasowa cikin parlorn, bin bayan momy su kayi,a parking space su ka sameta har ta buɗe back seat na wata ɓakar Acura ta shiga,ƙarasowa su kayi laatifa ta shiga driver seat yayin da Balqis ta buɗe front seat kusa da laatifa ta shiga, babu ɓata lokaci laatifa tayi ma motar key haɗi da reverse, cikin Estate ɗin su ka nufa tafiya su kayi mai ɗan nisa, parking space ɗin gidan dady su ka nufa, parking laatifa tayi haɗi da kashe motar, momy ta fara fitowa sannan sai Balqis, momy bata tsaya jiran su ba ta nufi main entrance ɗin villa ɗin,fitowa laatifa tayi a tare su ka jera zuwa entrance ɗin a lokacin da su ka ƙaraso har ƙofar ta buɗe alamar an basu izinin shiga.
a tare su ka kutsa kai, babu kowa a parlorn sai jefi jefin ma'aikata dake kai kawo, gaishe da su su ka shiga yi cikin kulawa momy da laatifa su ka shiga amasawa yayin da Balqis ko kallon banza ba su isheta ba, glass elevator dake parlorn ta ɓangaren mom su ka nufa,laatifa ta danna nombobin dake jikin elevator ɗin,zugewa ƙofar tayi, momy ta fara shiga kafin su ka bi bayanta rufewa ƙofar tayi elevator tayi sama da su.
ba su samu kowa a main parlorn mom ba hakan yasa su ka nufi ɗayan parlorn,yumnah da fa'iza su ka samu zaune a parlorn kowacce ta tasa waya a gaba sai aikin latsawa take ba su jima da dawowa daga prison ba duba jikin mahaifiyar nainarh, bakin su ɗauke da sallama su ka ƙarasa ciki, ɗagowa su kayi suna amsa masu sallamar da gudu yumnah ta taso ta nufi momy faɗawa tayi jikinta tana faɗin oyoyo, murmushi momy ta saki tana shafa bayanta.
“sannu da zuwa momy, ina wuni , yanzu mom ta shiga ciki”
“lafiya lau Alhmdllh ya hutu” da Alhmdllh yumnah ta amsa yayin da take raba jikin su gaishe da momy fa'iza tayi cikin kulawa momy ta amasa mata tana faɗin
“yan hutu, shine har yau banga ƙafarku ba ko” sunnar dai fa'iza tayi tana sakin murmushi
yumnah da sauri ta nufi laatifa buɗe mata hannuwa laatifa tayi tana sakar mata murmushi da sauri ta ƙarasa gabanta faɗawa tayi jikinta tana faɗin
“nayi missing ɗinki sosai Aunty laatifa” murmushi laatifa tayi tana shafa bayanta
“nima nayi missing ɗinki, ya hutu”
“hutu ya kusa ƙarewa” yumnah ta faɗa yayin da suke raba jikin su, taɓe fuska Balqis tayi tana nufar ƙofar bedroom ɗin mom yayin da take faɗin
“ni bari nayi ciki tunda babu wanda yayi missing ɗin na dama banyi na mutum ba” dariya gaba ɗayan su ka saki saboda sun san bakomai yasa Balqis faɗin haka sai tsabar kishi saboda babu wanda yayi mata oyoyo
“Aunty Balqis ai ni mun haɗu a court shiyyasa ban yi maki oyoyo ba” yumnah ta faɗa, murmushi fa'iza ta tayi tana faɗin “ke nan dai wannan faɗan dani ake, to Allah ya huci zuciyarki ƴar uwa nayi kewarki ya ki ke”
ya mutse fuska Balqis tayi tana faɗin “lafiya” dariya gaba ɗayan su suka saki ganin yanda ta amsa bayan abun da take so kenan, girgiza kai momy tayi tana nufar sofa ta zauna, ƙofar bedroom ɗin mom Balqis ta buɗe ta shiga,zama laatifa da Yumnah su kayi fa'iza itama zama tayi yayin da take gaishe da laatifa, cikin kulawa ta amsa mata, fira su ka shiga taɓawa.
Mom ce ta fito hannunta riƙe dana Balqis dake sakin murmushi, da sauri laatifa ta miƙe sakin hannun Balqis mom tayi tana buɗe ma laatifa hannuwanta alamar ta zo gareta, laatifa ba tayi ƙasa a gwiwa ba ta ƙarasa ga mom ɗin, hugging ɗinta tayi fukarta ɗauke da murmushi
“mom ina wuni, mun same ku lafiya”
“lafiya lau agogo sarkin aiki” mom ta faɗa yayin da take raba jikin su, ɓata fuska laatifa tayi tana faɗin “mom kema haka za ki ce”
dariya Balqis tayi tana faɗin
“wallahi mom gaskiya ki ka faɗa Aunty laatifa bata saurarama aiki” momy na daga zaune,murmushi ta saki a ranta tana faɗin sarakai za ku fara
“ai ba sai kin faɗa ba Balqis na santa ne” mom ta faɗa
“shikenan mom tunda kema haka za kice” laatifa ta faɗa tana komawa mazauninta
“wasa nake maki laatifa ai aiki abu ne mai kyau” murmushi laatifa ta saki jin mom wasa take mata itafa babu abun da ta tsana sama da ace mata ta cika nacema aiki.
sofa da momy take zaune mom ta nufa, tashi momy tayi su kayi hugging ɗin juna kafin su ka raba jikin su fuskokin su ɗauke da murmushi, gaishe da juna su ka shiga yi cikin kulawa yayin da suke samun wurin zama su ka zauna,masu aiki fa'iza ta kira dan su kawo ma su momy abun sha ta hanyar landline ɗin kitchen.
fira sosai su ka shiga yi a tsakaninsu momy na jajanta ma mom abun da ya faru da aminiyarta hajiya Asma'u,tambayar mom momy tayi ina ɗiyar hajiya Asma'u take
“tunda mu ka dawo daga prison wajen mahaifiyarta ta shige ciki bata jin daɗi,yumnah je ki kira man ita” mom ta faɗa, har yumnah ta miƙe fa'iza tayi saurin tashin tana faɗin “bari na kira ta”ta faɗa tana nufar corridor da zai sada ka da bedroom ɗin yumnah, tura ƙofar bedroom ɗin tayi ta shiga bakinta ɗauke da sallama.
bedroom ɗin yana da girma sosai, king size bed ne a cikin shi mai matuƙar kyau gefe da gefen shi nightstand ne mai ɗauke da bedside lamps,daga saman headboard ɗin bed ɗin ƴar rumfa ce mai haɗe da sparkling bulbs,sai ƙaton dressing mirror an cika gaban shi da body lotion da perfume masu dadda ɗan ƙamshi da tsadar gaske, tsakar ɗakin shimfiɗe yake rug carpet.
daga bakin sliding door glass balls chairs ne guda biyu suna kallon juna, daga wajen door ɗin ƴar baranda ce mai ɗauke da chairs guda biyu tsakiyar su round table ne daga nan kana iya hangen cikin estate ɗin da swimming pool dake cikin garden ɗin gidan.
A kwance fa'iza ta hangota saman makeken gadon ta rufe jikinta da duvet, bakin bed ɗin fa'iza ta ƙarasa pillow da take kwance ta ɗan bubbuga tana kiran sunanta, a hankali ta shiga buɗe idanuwanta da su kayi mata ɗauyi ga wani irin azabebben ciwo da kanta yake yi mata
“ki tashi mom na parlor tana kiran ki”pro khaki eyes ɗinta ta sauke akan fuskar fa'iza da tayi maganar,eyes ɗin sun ɗanyi jajja jajja saboda baccin data fara ga ciwan kai.
A hankali ta tashi zaune hanunta dafe da kanta, matsawa fa'iza tayi tana bata hanya dan ta samu damar saukowa, a hankali ta zuro da fararen ƙafafunta ƙasa,rober gown ce a jikinta ,rigar ta kamata ta bayyanar da surar jikinta,kanta babu ɗan kwali, water wave hair ɗinta har gadon bayanta ya sauka, gashin duk ya ɗan yamutse saboda bai samu gyara kwana biyu ba,sannu fa'iza ta shiga yi ma mata yayin da take binta da kallon ba ƙaramin tafiya da ita kyan nainarh yayi ba yarinyar ce Allah ya zuba mata kyau ko mace ƴar uwarta ta kalleta sai ta sake kallon, hijab ɗin ta dake kan bed ɗin ta ɗauka ta zura a jikinta.
“muje”fa'iza ta faɗa, gaba nainarh tayi fa'iza na biye da ita, a hankali take taka ƙasa kamar zata faɗi saboda rashin ƙwarin jikinta,tunda su ka shigo parlor momy da laatifa ke bin nainarh da kallo har su ka ƙaraso ciki, wurin mom nainarh ta nufa tana faɗin mom gani, momy ta nuna mata tana faɗin “ga momyn su laatifa nan kun gaisa” sai a sannan nainarh ta kai dubanta ga momy.
gaishe da ita tayi cikin kulawa momy ta amsa mata tana faɗin“ ya jikin ki naji ance ba ki jin daɗi”
“da sauki Alhmdllh” ta faɗa, gaishe da laatifa tayi cikin kulawa laatifa ta amsa mata Balqis tunda su ka shigo parlorn kallo ɗaya tayi ma nainarh ta ɗauke kai
“amma kin sha magani kuwa?” laatifa ta faɗa cikin nuna kulawa
“A'a” nainarh ta faɗa tana nufar rug carpet zata zauna saboda wani jiri da take ji, da sauri momy ta nuna mata kusa da ita tace ta zauna.
sannu su ka shiga jera mata mom na faɗin“bari idan IRFAN ya shigo ya duba ki, yumnah kira man shi a waya kice nace idan ya taso daga aiki ina son ganin shi”
da to yumnah ta amsa tana ɗaukar wayar ta ta shiga contact, number Irfan ta shiga nema, dialing number tayi ringing ta shiga yi har ta katse bai ɗaga ba, sake kira tayi sai da ta kusa katsewa ta samu sa'a yayi picking,sallama tayi tana gaishe da shi babu wanda ya amsa mata daga ciki sai cewa yayi“ lafiya ki ke man irin wannan kiran?”
shagwaɓe fuska yumnah tayi kamar tana a gaban shi
“dama mom ce tace idan ka ta so daga aiki ka shigo gida tana son ganinka” rejecting kiran yayi kawai ba tare da yace komai ba, taɓe baki yumnah tayi.
masu aiki ne su ka shigo hannun su ɗauke wooden tray, soft drinks ne da ruwa masu sanyi haɗe da glass cups, cikin parlorn su ka ƙaraso bakin su ɗuke da sallama, amsa masu sallama su kayi,ajiye tryas ɗin su kayi saman glass round table ɗin dake parlorn, ficewa su kayi, fa'iza ce ta shiga zuba masu ruwan da lemu ta miƙa masu.
masu aikin suna fita daga parlorn ɗaya kitchen ta nufa yayin da ɗaya ta nufi elevator, da sauri ƴar uwarta tace“munirat ina za kije?”
“part ɗin mamy ”wacce aka kira da munirat ta faɗa, girgiza kai wacce ta kira munirat ɗin tayi tana faɗin
“munirat ina rabaki da kiwan kyalla kina akuya ta haihu, wallahi ki daina shishige ma mamy, dan wallahi za kiyi da kin sani dan ita ba'a mata gwaninta ina guje maki ranar da zata shuka maki rashin mutunci”
“banji bakin ki ba, kuma ni bani ke shishige mata ba itace ke jana a jiki”
“na dai faɗa maki dan idan baki san abun da ya faru da baaba jummai ba gara tun wuri ki sani”
“ni dai naji,yanzu zan dawo” ta faɗa tana daddana madannan dake jikin elevator, girgiza kai kawai ƴar uwar tata tayi tana nufar kitchen...
_*Episode 9_10*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
______________________________
A kishingiɗe take saman makeken king size bed ɗinta ta ɗauki wankan rantsatsiyar shadda white color anyi mata aiki da red color ɗin zare, fuskarta tasha make_up a ko wane lokaci zaka samu hannuwanta da wuyanta da ƙafarta cikin adon gold ko zinari, kanta babu ɗan kwali gashin Attachment ɗin dake kanta ya sauka har gadon bayanta,wayarta ce a hannunta tana aikin daddanawa.
Nocking ƙofar bedroom ɗin a kayi,yamutse fuska tayi cike da izza tace “waye?”
ɗan ɗaga murya munirat dake tsaye bakin ƙofar tayi “munirat ce mamy”
“ke da waye ne?” mamy ta faɗa
“ba kowa ni kaɗai ce”
“ok shigo”mamyn ta faɗa.
a hankali munirat ta turo ƙofar ta shigo bakinta ɗauke da sallama,ƙaremata kallon mamy ta shiga yi tun daga sama har ƙasa, a bakin bed ɗin ta tsaya,cike da girmamawa ta durƙusa har ƙasa ta gaishe da mamy.
ƙin amsa mata mamy tayi sai ma cewa tayi “ina sauraronki mi ya kawoki ɗakina?”ta faɗa tana wani yamutse fuska.
“dama zuwa nayi na sanar dake hajiya maimunatu matar yallaɓai hashim ta zo ita da ƴaƴanta suna part ɗin madam zulaihart”
“mi su ka zo yi”mamy ta faɗa tana wani tsuke fuska
“nima ban sani ba amma ina tunanin sun zo yima madam jaje ne”
jinjina kai mamy tayi“naji daɗin jin wannan labari da ki ka zo man dashi, abunda nake so dake ki sa man ido akan kowa dake part ɗin komai ki ka gani ki sanar dani, komai ƙanƙantar abu ki sanar da ni”
“in sha Allah madam” jinjina kai mamy tayi“yawwa haka nake son ji, tashi ki tafi bana son janar ya shigo ya sameki, zan tura maki saƙon ki ta waya” miƙewa munirat ɗin tayi “nagode sosai Allah ya ƙara girma”ta faɗa tana nufar ƙofar fita ta fice.
tsaki mamy taja tana faɗin“munafuncin banza ko miye abun zuwa jaje in ba tsabar tsugudidi ba” mamyn ta faɗa tana sake jan wani tsakin.
wayarta ta ɗauka tayi dialing wata number, bugu biyu a ka yi picking, murmushi ta saki yayin da take kara wayar a kunenta.
“Allah ya taimaki first lady,hutawar ki lafiya hajiyar yallaɓi Ahmad”mamy ta faɗa ta na sakin dariya,on the other hand ta cikin wayar itama dariya ta saki.
“kullum da kalar tsokanar da ki ke zuwa MABARUKA, yau kuma ni ki ke ma wannan kirarin?”
“ai kin can canta ne, ya ki ke ya kwana biyu?”
“Alhmdllh, fatan kema kina lafiya, ina madam ɗinki take?”
taɓe baki mamy tayi “tana nan kamar yanda ki ka santa,ban ma baki labari ba”
“ina jinki mi ya faru?”
“uhmm ina wannan shari'ar da suke akan ƙawarta wannan munafukar hajiya Asma'un?”
“eh na gane ,ɗazu naji WASEEF na mata jaje wai an yankema hajiya Asma'u hukuncin ɗaurin rai da rai”
“eh ashe kinji?”
“naji waseef na mata jaje kin san ni ba ma'abociyar bibiyar labarai bace”
“ai kuwa kamar yanda ki ka ji an yanke mata hukuncin ɗaurin rai da rai”
“tab! Allah ya kyauta gaba,ki ce yau ku baku ba walwala”
“bata ba walwala dai, kema kin san babu abun da zai hanani walwala dama abun da na daɗe ina jira kenan dan wallahi ba ƙaramin jin haushin Asma'un nan nake ba”
dariya mai ɗan sauti ta cikin wayar ta saki “duk da haka da kinyi mata kara ai zaman tare baice haka ba”
“wa ni? Allah ya ki ya ye dama ta dawo magana na samu na nannausa mata na san sai ta da ɗe tana damunta”
dariya ta cikin wayar ta sake saki “gaskiya mabaruka baki da kir ki, mai makon ki taya ta ja je shine zaki ɓige da gaya mata magana”
“Allah ya ki ya ye ai ga abokan cin mushenta can ɗayar har ta zo wai ja je ɗayar munafukar ma na san tana nan zuwa anjima”
“baki da dama mabaruka, nima anjima ko gobe zan shigo nayi mata ja jen”
taɓe baki mamy tayi“ai da yake ke akwai kara a tsakanin ku”
“to ya zanyi tunda Allah ya haɗa Auratayya a tsakanin ƴaƴan mu dole ne zumunci ko bama so”
“Allah ya kawo ki lafiya” da Ameen ta cikin wayar ta amsa, sallama su kayi.
wata number mamy ta sake dialing, ringing wayar ta shiga yi, sai da kiran ya kusa katsewa sanann a kayi picking, murmushi mamy ta saki tana faɗin
“kaga abun gidan janar, halama bacci ki ke nake kira ba'a picking in time”
on the other hand ta cikin wayar tace “ina fa na shiga kitchen ne wurin masu aiki, kin san idan baka sa masu ido sai suyi maka shirme”
murmushi mamy ta saki“ kice kina can kina gasa masu aya a tafin hannu dan na san halinki ba sauƙi ne dake ba”
“duk rashin sauƙina na kai ki ne?”
“ai wallahi masu aikin ne sai da jan ido, idan kayi sanya sai su kawo maka raini”
“haka ne kam,to ya gidan, ya kwana biyu fatan kina lafiya??”
“lafiya lau Alhmdllh, ya naki gidan”
taɓe baki mamy tayi“ yana nan yanda ki ka san shi sai ma abunda ya ci gaba” murmushi ta cikin wayar ta saki
“ki ce kina nan kin hana dangin nasara masu jan kunne sakat”
“mi za'a fasa, ai in dai ina raye ta shiga uku”
“Allah ya shirya man ke ƙawata, ki zo ki samu mata a har gidan mijinta ki hanata rawar gaban hantsi”
“tama isa, wanda yace tayi sakacin da mijinta yayi mata kishiya”
“kina sha'aninki ta wajena, wai ni kam ɗazu nake gani a TV an yanke ma ƙawarta hukuncin ɗaurin rai da rai”
“eh Allah yayi maganin ɗayar munafukar saura manyan, kin san kuwa ɗayar harta kwaso ƙafa ta zo jaje??”
“wa ki ke nufi?”
“wacece kuwa ban da uwar ƴan tausayi maimunatu” tsaki ta cikin wayar taja
“munafukan banza kawai, na san ɗayar munafukar ma tana nan zuwa”
“wannan a rubuce take sai ta zo”
“wallahi haushi hajiya maryam ke bani, sai girman kan masifa”
“ai wallahi bake kaɗai take ba haushi ba, wani lokacin idan tana hura hanci tanama mutane kallon banza ji nake kamar na rufeta da duka”
“ke dai ki bari mai abun duniyar ma batayi ji da kai ba sai ita”
“za ki shigo anjima?” mamy ta faɗa
“mi zan zo nayi”
“ai nayi tunanin ko zaki zo mata ja je”
“wa ni? Allah ya ki ya ye, lokacin da hajiya Asma'un zata kashe mijinta shawara tayi dani da zan zo mata ja je, ai in kin ganni lahira to kaini a kayi”
dariya mamy ta saki “shiyyasa nake sonki ƙawata, yanzu na gama waya da hajiya SALIMA ta ce zata zo”
“ita ki ka ce ji tayi zata iya”
“ai kin san so akwai alaƙa mai ƙarfi a tsakanin su”
“wace alaƙa?, daga ɗanta na Auren ɗiyarta shikenan ko dan IRFAN na hannun mijinta, ni ba NAEEM bane ke Auren NAFISAT, ke ni bazan iya ba alaƙar Aure ma dake tsakanin nafisat da naeem dan bani da yanda zanyi ne amma wallahi da ba'ayi Auren ba”
“nima dai haka na gani”
“rabu da ita kawai sai mun haɗu ranar juma'a a part ɗin Abba”
“ok Allah ya kaimu” da Ameen matar ta amsa sallama su kayi.
𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫
Mom da momy ne kawai babu a parlorn, Yumah na kusa da laatifa sai zuba mata zance take yayin da balqis da fa'iza ke zaune saman sofa suna firar yaushe gamo.
tashi Nainarh tayi ta nufi bedroom ɗin Yumnah,da sannu su laatifa su ka bita balqis kuwa banda binta da kallon tsana babu abunda take, haka nan taji bata son Nainarh ita kanta bata san dalili ba amma taji ta tsaneta.
Sallama su ka ji daga bayan su da sauri su ka kai duban su ga matar dake shigowa, ta ɗau wanka baƙar Abaya tayi rolling da gyalenta,da gudu Yumnah ta nufeta hugging ɗinta tayi tana faɗin“momy kema ashe kina hanya” murmushi matar ta saki tana raba jikin su
“wani ya zo kenan da har ki ke tunanin nima ina hanya” murmushi Yumah ta saki “momy ma ta zo tare da su Aunty laatifa” ta faɗa yayin da su ke ƙarasowa cikin parlorn, cike da girmamawa su laatifa su ka shiga gaishe da matar tana amsa masu cikin kulawa yayinda take hugging ɗin su ɗaya bayan ɗaya.
“su mom na garden ita da momy” Yumnah ta faɗa
“ok bari na ƙarasa wajen su” ta faɗa yayinda take nufar sliding door dake parlor wacce daga nan kana iya hangen cikin garden ɗin da kusan zagaye yake da gidan.
shuke shuke ne a cikin a garden ɗin masu matuƙar ɗaukar hankali da ban sha'awa,ga grass carpet dake malale a cikin garden ɗin,ƙaton swimming pool ne a cikin garden yayinda aka ƙawata gafe da gefenshi da lounger chairs da deck chair masu kyan gashe domin zama,ducks ne ke shawagi a cikin swimming pool ɗin farare tas da su,daga can gefen swimming pool ɗin wasu rukunin bishiyu ne masu matuƙar ɗaukar hankali sunyi rukuni,peacocks ne masu kyan gaske ke yawo tsakanin bishiyun,babu kalar tsuntsun da babu a cikin garden ɗin.
A tsakiyar bishiyun mom Maryam ta hango mom da momy kishingiɗe saman rug sun yi matashi da tum tum yayin da aka cika masu gaban su da fresh fruit cikin kwandon kaba haɗe da snacks da soft drinks masu sanyi.
Momy ka ɗaice ta ɗan gatsi Apply yayin da mom ta zuba ma ducks ɗin dake shawagi cikin ruwa ido,damuwar halinda Aminyarta take ciki ce duk ta isheta ,bata so duniya ta juya mata baya lokaci guda ba.
“ki kwantar da hankalin ki barisster in sha Allah babu abun da zai faru da Asma'u,ina sha Allah zata kuɓuta su kuma wanda su kayi silar jefata cikin wannan halin da izinin Allah asirin su zai tonu”
Ajiyar zuciya mom tayi
“babu abunda yafi ɗaga man hankali sama da yanda jami'an tsaro da mutanen gidan su ka kafe akan ita ta kashe shi, ni na san wacece Asma'u ko dabba bazata iya kashewa ba bare ɗan Adam”
“nima a iya sani na da ita bazata iya aikata wannan babban laifin ba amma in Sha Allah gaskiya za tayi halinta”
“ina fatan haka”
fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙaraso in da suke, sallamarta su ka ji daga bayan su ,da sauri su ka kai duban su gareta, murmushi su ka sakar ma juna yayinda su ka miƙewa, hugging ɗin juna su ka shiga yi cike da kulawa suke gaishe da junan su,kalar ta su gaisuwar kenan a duk lokacin da su ka haɗu da juna.
saman rug ɗin su ka koma su ka zauna,sake gaisawa su kayi
“ya kuma mu ka ji da abun da ya faru da Asma'u” mom Maryam ta faɗa
“sai godiyar Ubangiji” momy ta faɗa
“Allah ya kuɓutar da ita”
“Ameen ya Allah” mom ta faɗa yayin da take ɗaukar sherry glass cup ta zuba ma mom maryam drink mai sanyi, miƙa mata tayi , murmushi mom Maryam ta saki ya yinda take amsar cup ɗin.
shiru ne ya gitta a tsakanin su,kowa da abunda yake saƙawa a ranshi ba kamar mom da kwata kwata bata cikin walwala,mom maryam ce ta katse shirun na su.
“amma barisster kin ɗauki wani mataki a kan shari'ar nan?” ta faɗa ya yinda take ajiye cup ɗin dake hannunta.
“ban fahimci ya ki ke nufi ba ,wane mataki zan ɗauka??”
mom ta faɗa cikin rashin fahimtar Abun da mom maryam ɗin take nufi.
“ai nayi tunanin zaki sa ayi maki bincike na daban akan case ɗin,idan Allah yasa aka dace kinga ba sai a tada shari'ar ba tunda hukuncin ɗaurin rai da rai ne”
“wane bincike zan sa ayi bayan wanda barisster Hashim yayi”
yana yin fuskar mom maryam me ya canza “uhmm barisster hashim fa ki ka ce?”
“eh shine lawyer dangin marigayi ,duk wani bincike da ya kamata ayi yayi”
“kenan kin yarda ita ta kashe mijinata?”
“A'a sai dai na san barisster ba zai faɗi abunda ba shikenan ba, kuma bana zargin zai haɗa kai da kowa dan kawai yayi nasara a kaina”
girgiza kai mom maryam tayi,mom Maimunatu na kallon su ƙala ba tace ba
“am sorry hajiya Maimunatu ba wai ina zargin barisster ba ne” murmushi kawai mom Maimunatu tayi ko zargin barisster su ke ya za tayi halin mijin nata ne dole a zargeshi.
“mu duka mun san cewa barisster baya ƙaunar zulaihart tun fil'azal, ni bana zargin zai iya haɗa kai da wasu dan dai kawai ya cika burin shi akan barisster,amma ƙara binciken da za kiyi yanada matuƙar amfani ni a nawa tunanin amma ya ku ka gani”
shiru mom tayi tana tsunduma duniyar tunani ta wani ɓan garen hajiya maryam na da gaskiya sai dai bata son ta binciko ma kanta abunda zai hanata zaman lafiya duk da har zuciyarta bata zargin Aminyarta zata aikata laifi makamancin haka.
“maganarki gaskiya ce hajiya maryam,ƙara binciken yanada amfani,sai dai waye zaiyi binciken?” mom Maimunatu ta faɗa
“haka ne ƙara binciken yanada amfani, Allah yasa ya zama sanadiyyar tonuwar asirin duk wanda ke da sa hannu,sai dai ta maganar Maimunatu wa zan sa yayi man binciken?” mom ta faɗa
“yawwa burina dama ku fahimce ni, maganar kuma wanda zaiyi binciken ba matsala bace karku manta gidan nan cike yake da jami'an tsaro kala kala samun wanda zaiyi bincike ba abun bane mai wahala NAEEM ma zai iya tunda dama aikin shi ne”
jinjina kai su kayi da alama sun aminta da maganar mom maryam
“shikenan zan samu lokaci mu zauna da shi,zanyi mashi bayanin yanda case ɗin yake” mom ta faɗa
“yawwa hakan yayi ,sai dai fa ya zamana cikin sirri zaiyi shi, kuma kar ya sanar a wajen aikin su yayi shi parsonal,duk da na san aikin su dama na sirri ne sai dai wannan ya ɗauke shi a matsayin na gida bana aiki ba” mom maryam ta faɗa
“in dai wannan ne ba matsala”a cewar mom , murmushi mom Maimunatu ta saki
“shiyyasa nake sonki hajiya maryam akwai kawo shawara mai ɓullewa” murmushi su ka saki gaba ɗayan su
“abun ne wallahi ya taɓa zuciyata,baiwar Allah nan babu ruwanta amma ace lokaci guda wani ya dabaibayeta da sharri,su barta mana taji da zaluncin kashe mata miji da su kayi mana ba sai sun manna mata kisan a kanta ba”
“gaskiya ko waye ba ƙaramin cutar da ita yayi ba” firar su suka shigayi suna alhinin abunda ya faru da ƙawar mom.
𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫
A tsaye take a gaba motar ta ƙirar honda Black color, blue black ɗin Abaya ce a jikinta ta yafa gyalen saman kanta,hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta,cikin faɗa faɗa take faɗin
“Enaaya wai zaki fito ne ko sai nayi tafiyata?”
daga cikin motar naji Muryar yar ƙaramar yarinya tana faɗin “momy gani nan fitowa hand bag ɗina zan ɗauka”
tsaki matar taja “ko uwar mi za kiyi da hand bag,ni kinga tafiyata idan kin gama kilibibin naki kya shigo” matar ta faɗa tana nufar entrance ɗin gidan.
da sauri wata ƴar ƙaramar yarinyar ta fito, Black ɗin abaya ce a jikinta tayi rolling da gyalen, simple make_up ne a fuskarta yayin da kyawawan idanunta ke manne da ɗan sunglasses dai dai idonta mai butterfly,ƴar hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta,highills ne a ƙafarta ba ƙaramin kyau tayi ba.
bayan mahaifiyarta ta tabi tana wani tako ɗai ɗai kamar wata uwar mata,a main parlor part ɗin ta samu mahaifiyarta tana jiranta,glass elevator dake part ɗin mom yarinyar ta nufa da sauri mahaifiyarta ta tace.
“ENAAYA ina kuma za kije?” ya mutse fuska yarinyar tayi tana faɗin “part ɗin mom mana”ta faɗa cike da yanga
“muje mu fara gaishe da mamy tukun” mahaifiyar ta faɗa tana nufar part ɗin mamy,juyawa yarinyar tayi tana faɗin
“ni gaskiya bazanje part ɗin mamy ba,haka nan kawai ta rufe mutum da faɗa ba abunda yayi mata,kuma Ni dady nake son nunama wannan kwalliyar dan karma sister ta rigani,sai kin dawo kawai momy ”
yarinyar ta faɗa tana nufar elevator part ɗin mom.
girgiza kai kawai mahaifiyarta ta tayi tana faɗin “Allah ya shirya ki Enaaya”
A parlor ta samu mamy zaune saman sofa kayan ɗazu ne a jikinta,bakinta ɗauke da sallama ta ƙarasa ciki.
fuskar mamy da fara'a ta amsa mata sallamar tana sannu da zuwa,wuri ta samu saman sofa ta zauna.
“in wuni mamy, ya gida”
“lafiya lau NADIYA, ya gida?”
“lafiya lau”
“masha Allah,Ina uwayen sanabe ko ana islamiyya?”
murmushi nadiya ta saki tana faɗin“A'a ta shiga part ɗin mom ne” jinjina kai mamy tayi tana maimaita kalmar part ɗin mom.
“watau ni tafi ƙarfin ta zo ta gaishe ni,shine ta wuce wajen ƙanwar uwarta, tunda ban haifi mahaifinta ba ai ba tazo ta gaishe ni ba,zata zo ta sameni ne” murmushi kawai Aunty nadiya tayi dafa gaskiyar enaaya mamy ba dai faɗa ba.
“tana nan zata shigo,na san duk saurin ta haɗu da dady ne”
“A'a tayi zamanta kawai ba sai ta zo ba”
“kiyi haƙuri mamy idan ranki ya ɓaci”
uhmm kawai mamy tace mata ba tare da ta sake cewa komai ba.
sallama su ka ji daga bayan su ,Aunty nadiya ce kawai ta kai dubanta ga mai shigowa,riga da skirt na atamafa ne a jikinta ta yafa mayafi tun daga kanta fuskarta tasha make_up,manyan idanunta sun sha eyelashes na company, hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta yayinda yaranta ke biye a bayanta mace da namiji ,namijin ya ɗau wankan jeans and t_shirt,hannuwan shi zube su ke cikin aljihun wandon shi kamar wani babban mutum, fuskar nan tashi a ɗaure take, ƴar macen ce ke sanye da Pakistan dress riga da wando ta yafa mayafin kayan saman kafaɗar ta, anyi mata parking gashinta a tsakiyar kai,light make_up ne a fuskarta,ƙafarta sanye take cikin wedge shoe masu kyan gaske, itama sunglasses ne a fuskarta mai butterfly kamar Enaaya.
da sauri Aunty nadiya ta miƙe fuskarta ɗauke da murmushi ta nufi matar dake shigowa, hugging ɗin juna su kayi,gaba ɗayan su suna sakin murmushi.
“sister NAFISAT shine baki faɗa man kuna tafe ba ai dana jira ku” Aunty nadiya ta faɗa yayinda su ke raba jikinsu daga na juna.
“uhmm ki bari kawai nima ban san da fitar ba, ina zaune ya NAEEM yace wai mu zo,Ni ban ma san mi ke faruwa ba” ta faɗa tana ɗan ya mutse fuska.
“tare ku ke dashi ne?”
“eh ajiye mu yayi yaje ya dawo”
zuba masu ido mamy dake zaune tayi tana kallon su,wurin mamy Aunty nafisat ta nufa, gaishe da ita tayi cikin girmamawa,mamy da fara'ar ta ta amsa mata,suma yaran gaishe da mamy da Aunty nadiya su kayi,taɓe baki mamy tayi
“miskili kafi mahaukaci ban haushi,yau kuma aljanun sun bari a zo a gaishe ni kenan?”
ɗan taɓe baki Aunty nafisat tayi tana dallama yaron harara da duk ya wani ɓata fuska shi dole an sa shi abunda baiyi niyya ba,da sauri ya kalli gefe ganin kallon da mahaifiyar tashi tayi mashi,tsaki taja.
“momy nadiya wai ina Enaaya ne?” ƴar macen ta faɗa
“tana part ɗin mom” ko gama faɗa nadiya ba tayi ba ta juya da sauri ta nufi ƙofar fita,bin bayanta namijin yayi, da sauri Aunty nafisat ta daka mashi tsawa
“ina za ka ,ko kaima Enaayar ƙawarka ce?”
“ai wajen Aunty Yumnah zan je” ya faɗa yana ficewa daga parlor ba tare da ya tsaya jin mi Aunty nafisat ɗin za tace,jinjina kai Aunty nafisat tayi.
“wai shi mi a kayi mashi yake wannan kumbura fuskar?” mamy ta tambaya
“saboda nace sai mun fara shigowa nan shi baiyi niyyaba shine yake wannan cin ɗacin”
“kaga ƴan bantan uban yara sun raina ni,sai kace wata uwar nake masu da ba sa son zuwa in da nake”
“iskanci ne kawai irin na su” a cewar Aunty nadiya
“zanyi maganin su ɗaya bayan ɗaya ne”mamy ta faɗa.
canza fira su kayi,su Aunty nafisat Nama mamy jajen abunda ya faru da mom,taɓe baki kawai mamy tayi ba tare da ta ce masu komai ba.
𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫
ƙarar takun takalminta ne ya cika masu kunne,da sauri su ka kai duban su gaba bakin ƙofa,mamaki ne gaba ɗaya ya cika su,dariya fa'iza ta saki tana faɗin
“ƙamshi duk ya cika mana hanci kace uwayen mata ne a hanya” tsayawa Enaaya tayi tana wani tsuke baki
“kar wanda yasa ran zanyi mashi oyoyo,saboda wannan kwalliyar ta dady ce” ta faɗa tana wani yi masu fari da ido ta cikin glass, murmushi su saki
“yanzu baby Enaaya ko ni baza kiyi ma oyoyo ba” Yumnah ta faɗa tana wani marairaice fuska.
“gaskiya yau sai dai kiyi haƙuri Aunty Yumnah kwalliyar nan ta dady ce,ki bari idan na dawo daga wurin shi nayi maki oyoyo”
tsuke fuska yumnah tayi tana riƙe ƙugu“ai kuwa bana so”
“shikenan tunda so ki ke su Aunty balqis suyi mana dariya” Enaaya ta faɗa tana nufar stairs case dake hannun daman parlor,tana tafiya tana wani jujjuya jiki.
murmushi kawai balqis tayi tana faɗin “manyan mata sun hallara kowa yayi ta kansa” dariya su ka kwashe gaba ɗayan su.
*KITCHEN*
Gaba ɗaya masu aikin gidan suna kitchen domin lokacin fara aikin dinner yayi,a hankali take tafiya dan karma taji ƙarar takalminta
alama tayi ma masu aikin dake ciki da kar suyi magana,da gudu ta nufi Eishrat dake tsaye gaban fridge tana jera drinks,kamar daga sama taji mutum ya faɗa saman bayanta, ƙara ta saki tana jefar da lemun dake hannunta,dariya ta fashe da ita.
“gaskiya chef Ishrat kin cika tsoro” ajiyar zuciya Ishrat ta sauke dan ba ƙaramin tsorata tayi ba saboda bata san da shigowar ta ba sai dai kawai tajita a jikinta.
tsuke fuska Eishrat tayi tana
“amma baby Aneesah kin raina ni da yawa” dariya Aneesah ta kwashe da ita
“ba wani kin dai cika tsoro ne”
“to naji,saukar yaushe?”
yamutse fuska Aneesah tayi “yanzu muka zo da momy fatan kin ajiye man Alƙawari na?”
yana yin fuskar Eishrat ne ya sauya “Ayyah! baby Aneesah ban san za kizo yau ba”
ɓata fuska Aneesah tayi “chef Eishrat na fa sanar dake jiya, ko kin manta na kiraki da landline ɗin kitchen?” Aneesah ta faɗa tana tsuke baki
“sorry baby Aneesah mantawa na yi,amma yanzu zan haɗa maki”
ɓata fuska Aneesah tayi “har dady ya fita baki kammala haɗa man ba”
murmushi Ishrat ta saki
“wasa nake maki baby, tunda ki ka sanar da ni zuwan ku na haɗa maki”
da sauri Aneesah ta dafe saitin zuciyarta tana wani lumshe ido
“wai Allah! har kin sa hankali na ya kwanta,da yau kin sa sister Enaaya tayi man dariya, duk wannan saurin da nake dan kar ta rigani ba dady wani abu”
“Ayyah sorry,na san ta rigaki dan tun ɗazu tana part ɗin shi”
yamutse fuska Aneesah tayi “ita komai nata cikin sauri take yin shi,ai na san duk abun da zata bashi bazai kai wanda zan kai mashi ba”
“nima ina fatan haka, bari na shirya maki komai” Ishrat ta faɗa.
ƙaton wooden tray Ishrat ta ɗauka, fridge ta buɗe fruit salad ta ɗauko a cikin bowl sannan ta ɗauko yogurt daga gani haɗin gida ne mara zaƙi da lemun wanda shima haɗashi tayi da kanta sai chocolate cake.
Murmushi Aneesah ta saki ganin abun da tafi buƙata,dish rag ta nufa cups ta ɗauko da fork guda biyu ta ɗaura saman tray,ficewa su kayi daga KITCHEN ɗin Aneesah na gaba yayin da Ishrat ɗin ke biye da ita.
bakin su ɗauke da sallama su ka shiga cikin parlor,su Yumnah na nan zaune kamar yanda Enaaya ta barsu,Jamal na kwance saman sofa yayi pillow da laps ɗin Yumnah.
murmushi su ka saki yayin da su ke amsa sallamar da su kayi,sama Aneesah ta nufa ba tare da tace ma kowa ƙala ba suma binta su kayi da ido dan sun san ba lallai ta tanka masu ba tana sauri taje wurin dady.
bin bayanta Ishrat tayi ,dariya fa'iza ta saki tana faɗin “yan bantan uban yara kowa zai haƙura ya barma wani dadyn a cikin su?”
“rabu da ƴan ƙwal uba sun gama iskancin su su barma su mom majin su,yara sai kilibibin masifa”
a cewar Balqis, murmushi laatifa ta saki
“kar kuga laifin su,kuma da kune a matsayin su na san sai kunyi abun da yafi nasu”
“haba Aunty laatifa mu mi yasa ba mu yima Abbah haka”
“babu face ne shiyyasa” murmushi kawai su kayi ba tare da sun ce komai ba.
A kishingiɗe yake saman rug carpet dake katafaren parlon shi, ya ɗaura kanshi saman tum tum yayin da Enaaya ke gefenshi ,cike da salo da kisisina take bashi labarin school ɗin su,ya ƙafeta da ido sai sakin murmushi yake.
sallamar Aneesah da Ishrat ce ta katse masu firar da su ke, waro ido waje Enaaya tayi yayinda take miƙewa tsaye
“wayyo Allah nah!, sister Aneesah dama za ki zo” Enaaya ta faɗa tana yarfe hannu
murmushi Aneesah ta saki tana ƙarasowa ciki, da sauri Enaaya ta nufeta, hugging ɗin juna su kayi sai sakin murmushi su ke,raba jikin su su kayi.
gaishe da junansu su ka shiga yi kamar wasu manyan mutane, Ishrat da dady ban da sakin murmushi babu abun da su ke.
cikin parlor Ishrat ta ƙarasa a gaban dady ta ajiye tray
“barka da hutawa dady” murmushi dadyn ya saki
“lafiya lau Ishrat,sannu da ƙoƙari” murmushi kawai Ishrat ɗin ta saki tana nufar ƙofar fita
“thank u” Aneesah ta faɗa, alamar jinjina Ishrat ɗin tayi mata tana ficewa daga parlorn.
wurin dady Aneesah ta ƙaraso tana sakar mashi murmushi haɗi da fari da idanu, murmushi kawai dadyn ya saki yana girgiza kai lamarin su Aneesah na matuƙar bashi mamaki.
a saman rug ɗin su ka zauna, gaishe da dady Aneesah tayi yayinda take zuba mashi lemu a cup,cikin kulawa dady ya amsa gaisuwar yayin da yake ƙarɓar cup ɗin lemun da take miƙa mashi.
a tare su ka shiga cin chocolate cake ɗin banda dady saboda ciwan sugar
fira su ka shiga zuba mashi yan sauraron su.
Aunty nafisat sun jima a part ɗin mamy kafin su ka shigo part ɗin mom lokacin har su mom Maryam sun tafi ya rage saura fa'iza da Yumnah kawai, nainarh har time ɗin tana kwance a bedroom ɗin Yumnah.
bedroom ɗin mom su ka shiga a zaune su ka sameta bakin bed ɗinta tunda su mom Maryam su ka tafi take a nan zaune.
cike da girmamawa su ka shiga gaishe da ita tana amsa masu cikin kulawa,sosai su ka nuna alhinin su kan abunda ya faru da ƙawar mom ɗin.
tambayar su Aneesah mom tayi dan tun ɗazu suna part ɗin dady ba su fito ba, murmushi kawai tayi ko da su ka sanar da ita suna can.
fira su ka shiga taɓawa sama sama har aka fara kiran sallar magrib, bedroom ɗin Yumnah su ka nufa domin yin sallah,sunyi mamakin ganin nainarh dan basu san da zamanta a gidan ba,kasa haƙuri Aunty nafisat tayi har sai da ta tambayi Yumnah wacece,faɗa mata ko wacece Yumnah tayi.
taɓe baki kawai Aunty nafisat ɗin tayi Aunty Nadiya kuwa ko kallon in da su ke ba tayi ba tana sallame sallah ta fice daga ɗakin zuwa na mom, anan ta samu Aneesah da Enaaya sai zubama mom fira su ke Jamal na gafen su zaune.
Aunty nafisat ma data gama sallah bedroom ɗin mom ta koma,ko da lokacin sallar isha yayi a nan su kayi ta,suna zaune saman carpet sallame sallar su kenan a kayi nocking ƙofar bedroom ɗin.
da sauri Enaaya taje ta buɗe, a tsaye suke su biyu ɗaya suit ne a jikinshi yayin da ɗayan ke sanye da Army trouser da white ɗin shirt.
Kamannin fuskar su ka ɗai zai tabbatar maka da su ɗin jinin dady da mom ne ba kamar mai Army trouser ɗin.
Da gudu Enaaya ta faɗa saman jikin mai Army trouser ɗin wando tana faɗin “oyoyo dady NAEEM ashe da rabon mu gana yau”
dariya su ka saki gaba ɗayan su
“ai kuwa da rabon mu gana, ya school?” ya faɗa yayinda yake raba jikinsu
“Alhmdllh dady NAEEM,wai ina ka shige kwana biyu bana ganin ka?”
“aiki ne ya yi man yawa baby Enaaya,kuma ma ai idan kina son gani na kin san in da zaki same ni”
ɗan zaro ido tayi tana kallon wanda ke kusa dashi “wannan maganar tafi karfina dady NAEEM,ga dady nah nan ka tambaye shi” ta faɗa tana komawa cikin ɗakin da gudu.
murmushi kawai su ka saki ya NAEEM na faɗin “kenan dai ADNAN kai ke hanata zuwa gida na?” ya faɗa yana ɗan tsuke fuska.
“haba SECOND FATHER sai ka ce baka san sharrin Enaaya ba,ni ƙarya take man”
cikin ɗakin su ka ƙarasa ya NAEEM na faɗin “yanzu dai maganar wa zan kama tsakanin ku?”
“tawa mana dady NAEEM” Enaaya ta faɗa tana wani marmar da ido.
da sauri ya NAEEM yasa hannu yana toshe bakin shi haɗi da ɗan zaro ido kamar yanda Enaaya tayi ɗazu, girgiza mashi kai ta shiga yi alamar kar ya faɗa tana zare ido.
dariya gaba ɗayan su suka sa dan sun san saboda mi ya NAEEM yayi mata haka watau dadyn ta ƙarya yake.
da gudu Aneesah ta faɗa jikin ya ADNAN tana mashi oyoyo, Jamal ma nufo su yayi,Barka da zuwa yayi masu yana koma bakin bed daya ta so.
gaishe da ya NAEEM Aunty Nadiya tayi tanama ya ADNAN sannu da dawowa,hakama Aunty nafisat gaishe da su tayi.
ta shi su kayi su ka fice daga ɗakin ya zama daga mom sai su ya NAEEM ɗin,a gabanta su ka zo su ka zauna ƙasa suna tanƙwashe gwiwowin su kamar masu neman gafara.
cikin girmamawa su ka shiga gaishe da ita tana amsa masu cike da kulawa.
“ya aiki” ta tambaye su da Alhmdllh su ka amsa mata haɗi da jajanta mata abun da ya faru.
“in sha Allah gaskiya za tayi halinta” ya Adnan ya faɗa, da Ameen su ka amsa.
sun ɗan jima suna fira kafin su ka tashi zuwa part ɗin dady dan su gaishe da shi,har sun kai bakin ƙofa mom tace ma ya NAEEM tana son magana dashi gobe idan ya dawo aiki ya zo ya sameta,da to ya amsa mata, ficewa su kayi zuwa part ɗin dady.
su Aunty Nadiya na zaune parlorn Ishrat ta shigo ta sanar da su an kammala dinner.
“sannunki da ƙoƙari Ishrat” fa'iza ta faɗa, murmushi Ishrat ɗin ta saki tana barin parlorn.
a dinning room su ka hallara saman makeken dinning table mai mazaunin mutum shabiyu, Aneesah da Enaaya sun sa dady a tsakiya, Nainarh ka ɗaice babu, itama ba bu yanda Yumnah ba tayi da ita ba a kan ta fito suyi dinner amma taƙi sai dai aka kai mata nata can,tsit ka ke ji sai ƙarar spoon da plate dake tashi kowa na ba ciki haƙƙin sa.
hakan ya ba dady damar kafe su da ido yana kallon su cike da Alfaharin yanzu duk shi ke da wannan danma wasu basa nan,yana yin fuskarshi ne ya canza da alama ya tuna da wani abun,hawaye ne su ka taru a idanuwan shi saurin goge su yayi yana kawar da tunanin a ranshi.
sai wurin ƙarfe goma na dare su ya NAEEM su ka bar gidan,har part ɗin mamy Aunty Nadiya da Aunty nafisat su ka shiga yi mata bankwana harda su ya NAEEM amma ban da su Enaaya dan cewa su kayi basa zuwa da iyayen su ka matsa masu sai ficewa su kayi daga gidan da gudu.
murmushi kawai fa'iza da Yumnah su ka saki suna bin bayan su Aneesarh.
cikin girmamawa su ya NAEEM su ka gaishe da ita amma sai ta amsa masu tana wani ya mutse fuska,hakan bai dame su ba idan da sabo ai sun saba.
ba su zauna ba su ka fice a parking space su ka samu su Enaaya tare da su fa'iza,sallama su kayi ma junan su su ka nufi motocin su yayin da fa'iza da yumnah su ka koma ciki, barin gidan su kayi zuwa na su gidajen dake cikin Estate ɗin...
_*Ep11_12*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
_____________________________
A main parlor fa'iza da Yumnah su kayi sallama fa'iza ta nufi part ɗin mamy yayin da Yumnah ta nufi na su part ɗin.
direct ɗakinta ta nufa, a hankali ta tura ƙofar bakinta ɗauke da sallama, a tsaye ta hango Nainarh bakin sliding door ɗin dake cikin ɗakin ta zubama cikin estate ɗin da yake ƙwanyar da haske kamar rana ido, jefi jefi take hange motoci na kai kawo a cikin Estate ɗin.
A zahiri kallon cikin Estate ɗin take a ɓaɗi kuwa hankalinta na can prison wajen mahaifiyarta, ko a wane hali take, wasu irin zafafan hawayen su ka wanke fuskarta lokacin data tuna irin kisan wulaƙancin da a kayi ma mahaifinta.
Sosai take zubar da ƙwalla kwata kwata ko sallamar Yumnah ba taji ba, bakin door ɗin Yumnah ta ƙaraso, a hankali ta kira sunan Nainarh amma bata amsa mata ba saboda hankalinta da baya tare da ita, dafa kafaɗarta Yumnah tayi, da sauri ta kai dubanta ga Yumnah.
“nainarh dan Allah ki daina sa damuwa a ranki, komai zai wuce”
da sauri Nainarh ta faɗa jikin Yumnah tana sakin kuka mai sauti,jikin Yumnah ne yayi sanyi, wani irin tausayin Nainarh ne ya rufeta musamman yanda taji jikin Nainarh ya ɗauki zafi.
ɗan bubbuga bayanta ta shiga yi tana lallashin ta.
“nainarh dan Allah ki daina sa damuwa a ranki, komai zai wuce, ki daina kuka dan Allah,naji ma jikin naki ya ɗau zafi gashi ya Irfan ɗin baizo ba,amma bari naje medical room na samo maki maganin zazzaɓi kafin zuwa gobe”
Yumnah ta faɗa yayin da take raba jikin su,jan hannun Nainarh tayi zuwa ottoman chair dake bakin bed.
“ki zauna bari na kawo maki magani, naga ma ko dinner ɗinki ba ki ci ba” Yumnah ta faɗa tana kallon dinner ɗin da Ishrat ta kawo mata.
cikin dasashiyar muryarta tace
“bana jin yunwa ne”
girgiza kai Yumnah tayi “bazai yuwu ba, idan baki son wannan ne na kawo maki wani, amma zama da yunwa ba masalaha bace”
“na ƙoshi ne Yumnah, bazan iya cin komai ba”
“dole kisa wani abu a cikin ki” Yumnah ta faɗa tana kwashe kayan abincin da aka kawo mata tana nufar ƙofar fita ta fice daga ɗakin, kitchen ta fara nufa ta ajiye trayn kafin ta fice.
Ƙaton medical room ɗin su ta shiga babu abun da babu a cikin shi,komai da mara lafiya zai buƙata a kwashi a ciki,girmanshi zai kai clinic.
glass drawer dake ɗauke da nau'in magunguna ta nufa,side ɗin da magungunan zazzaɓi dana ciwan kai ta buɗi maganin zazzaɓi dana ciwan kai ta ɗauko mata, mai da ƙofar tayi ta rufe, ƙofar fita ta nufa light ɗin ɗakin ta kashe haɗi da ficewa.
da mom taci karo zata part ɗin dady hannunta riƙe da tea cup wanda ta haɗa ma dady herbal tea.
“ke kuma daga ina?” mom ta faɗa, in da take ta ƙaraso.
“magani na ɗauko ma Nainarh”
“ya Allah!, kinga shaf namanta IRFAN ɗin bai zo ba, gashi yanzu dare yayi da na sa dr lelah ya dubata, jikin nata yayi zafi ne sosai?”
“A'a da sauƙi, damuwace tayi mata yawa”
“dole damuwa tayi mata yawa, yanzu tafi da maganin ki bata” mom ta faɗa tana nufar part ɗin dady.
Kitchen Yumnah ta nufa,hot milk da coffee ta haɗa mata,saman ɗan madaidaicin tray ta ɗaura da maganin,ruwa ta ɗauko mata cikin fridge, ɗaukar trayn tayi ta ficewa zuwa bedroom ɗinta.
kamar yanda ta barta haka ta same ta zaune,ku sa da ita ta zo ta ajiye mata tryan, ɗaya daga cikin chairs ɗin dake ajiye bakin sliding door dake ɗakin ta jawo,zama tayi tana tasa Nainarh gaba.
“gashinan ki sha ko ɗaya daga cikin su ne sai kisha magani”ruwa ta ɗauka da nufin su zata sha,da sauri Yumnah ta girgiza mata kai.
“kar muyi haka dake Nainarh,ki daure kisha hot milk ɗin nan ko da baki sha coffee ba” jinjina mata kai tayi tana ajiye ruwan data ɗauka ta ɗauki milk ɗin ta kafa a baki,da kyar tasha rabin cup ɗin shima Nainarh ta tursasata har ta sha kamar haka.
yumnah da kanta ta shiga miƙa mata maganin tana sha,bayan data kammala tashi tayi ta kai kayan kitchen.
Toilet Nainarh ta shiga,ruwa ta watsa dan taji daɗin jikinta,tana fitowa Yumnah na shiga,wata ƙofa ta nufa,tanƙamemiyar glass drawer ce gari guda,daga waje kana hangen cikinta shaƙe take da sutura kala kala,kowace sutura wajenta daban.
ɓangaren pajamas ta buɗe tsaye tayi tana kallon kayan har Yumnah ta shigo, girgiza kai tayi yayinda take ƙarasowa ciki.
“please Nainarh ki riƙa abu da hanzari,yanzu ɗauko kayan ne ki ka ɗauki lokaci haka”
da kallo kawai Nainarh ta bita har ta ɗauko ma su kayan da zasu sa,riga da wando na saƙa farare ta miƙa mata saboda zazzaɓin da take ne yasa ta ɗauko mata su.
fita Nainarh tayi daga ɗakin,ƴar gown ɗin data ɗauko ta zura a jikinta,baby bant tasa ta ɗauke kanta,ficewa tayi daga ɗakin,samun Nainarh tayi har ta kwanta,itama bed ɗin ta nufa, laptop ɗinta dake ajiye saman night stand ta ɗauka,opreting ɗinta ta shiga yi, video call ne ya shigo ta laptop ɗin.
murmushi ta saki tana faɗin “yanzu nake shirin kiran ka saiga kiran naka” picking call ɗin tayi, a shagwaɓe tace “hey” tana yarfa yatsun hannunta irin na gayu.
Yana daga zaune saman Leather chair,da alama a office yake, Army shirt ce a jikinshi haɗe da trouser ɗinta,sosai rigar tabi shape ɗin broad chest ɗinsa ta bayyanar da strong arms ɗinsa,kallo ɗaya za kayi mashi ka tabbatar da jinshi turawa ne,kyakkyawa ne na gaske,hancinshi a tsaye yake ƙem, blue eyes ɗin shi sai ɗaukar ido su ke, kwantaccen sajenshi baƙi wul sai sheƙi yake,sumar kanshi ta sauka har saman neck ɗinshi,daga yanayin zanen tattoo ɗin dake saman neck ɗin shi da ear ring mai alamar Cross ɗin dake a ƙunnanshi zai tabbatar maka da Addinin shi.
ƙayataccen murmushi ya sakar mata wanda ya ƙara bayyanar da kyawun fuskarshi yana maida mata martanin sallamar da tayi mashi, a shagwaɓe cikin harshen nasara tace “mi yasa baka kirani ba duk yau?”
in a cool voice yace“Am sorry, yayan ki ne yau duk yabi ya takura man” murmushi ta saki
“ko dai ka takura mashi,kai ma fa na san..” murmushi ta saki ba tare data ƙarasa ba,wani irin killer smile ya sakar mata,shagwaɓe mashi fuska tayi kamar za tayi kuka.
cikin shauƙin soyayya su ke waya Nainarh na daga kwance tana sauraronta sama sama kafin bacci yayi awan gaba da ita.
Yumnah ba itace ta gama waya ba sai wajen ƙarfe uku na dare, kusan kullum haka take ɓata lokaci suna waya saboda shi lokacin ne ya ke samun sararin kiranta saboda banbancin lokaci dake tsakanin ƙasashen guda biyu.
*WASHE GARI*
Alhmdllh jikin Nainarh zazzaɓin ya sauka sai ciwan kai da take fama dashi har lokacin gashi har time ɗin Irfan bai zo ba.
kwance take saman bed ita ka ɗai a ɗakin,babu yanda Yumnah ba tayi da ita ba ta zo su fita tayi breakfast tare da su amma taƙi sai dai a kawo mata a ɗaki.
turo ƙofar ɗakin a kayi aka shigo, Yumnah ce ta shigo jikinta sanye da riga da wando masu taushi peach color ta yafa farin mayafin a saman kanta.
cikin ɗakin ta ƙaraso “ki tashi ki shirya mom tace mu tafi hospital Dr Faawar ya dubaki tunda ya Irfan bai zo ba”
yumnah ta faɗa yayinda take nufar toilet,tashi Nainarh tayi tana bin bayanta da ido,bata motsa daga inda take ba har Yumnah ta fito sanye da bathrobe.
“tashi ki shiga” Yumnah ta faɗa,sauka Nainarh tayi daga saman bed ɗin toilet ɗin ta nufa
“ki fa yi sauri kar mom tace tare da wani za ku tafi ko ya Irfan ya shigo”
Dressing room ta nufa,shaf shaf ta shiga shiryawa duk tana wannan saurin ne dan kar wani abu yasa a fasa fitar ko Irfan ɗin ya shigo dan da ƙyar ta samu mom ta amince akan za su je hospital ɗin dan cewa tayi kawai su tafi clinic ɗin dake cikin Estate ɗin ko ta kira dr Faawar ɗin ya zo har gida ya duba Nainarh.
Nocking taji anyi,da sauri ta ƙarasa zura rigar data fara sawa,ficewa tayi zuwa cikin bedroom ɗin har time ɗin Nainarh bata fito ba,ƙofar ta nufa tana faɗin waye.
shiru taji wanda ke Nocking bai Bata amsa ba ba'a kuma fasa Nocking ɗin ba,buɗe ƙofar tayi da ɗan faɗa faɗa tace “wai waye ke neman fasa ma mutane kunne da noc.......”
bata ƙarasa ba ganin wanda ke tsaye,wani kyakkyawan matashi saurayi ne tsaye yana sanye da wandon suit a jikinshi tare da shirt long sleeve mai maɓallai gaba,hannunshi riƙe da briefcase ɗin shi tare da rigar suit ɗin da bai sa ba.
tun daga ƙafafunshi dake sanye cikin leather shoes masu masifar kyau ta shiga kallo ,dogo ne ɗan dai dai fatan jikinshi fara ce tas,yanada broad chest tana iya hangen six pack ɗin shi saboda maɓallan rigar da bai sa duka ba ,hancinshi a tsaye yake ƙem ga wasu idanuwa masu jan hankali farare tas da su,launin ƙwayar idonshi ash color ce, pink lips ɗin shi ba ƙaramin ɗaukar ido su ke ba,yanada ɗan tsayin fuska ga wani kalar kwantaccen saje sai sheƙi yake,kwantacciyar sumar kanshi har saman neck ɗin shi ta sauka, fuskar shi a ɗaure take kamar wanda aka aiko ma saƙon mutuwa.
Tsuke fuska yayi ganin irin kallon da take mashi
“ya Irfan kai ne!!?” Yumnah ta faɗa
“ban sani ba,zaki ban hanya na wuce ko sai kin gama kallon nawa?” da sauri ta matsa mashi,wani wawan tsaki yaja yana kunna kai zuwa ciki.
A tsakiyar ɗakin ya tsaya
“ina yarinyar take?”
“tana toilet” ta bashi amsa,tsaki yaja yana juyawa ya nufi ƙofa
“idan ta fito ina parlorn mom ku same ni a can”
har ya kai bakin ƙofa, Nainarh ta turo ƙofar toilet ta fito jikinta ɗaure da towel iya gwiwarta ta saki sumar kanta har gadon bayanta.
“yawwa gata nan ma ta fito” Yumnah ta faɗa,sai a lokacin Nainarh ta lura da mutum a tsaye,juyowa yayi karab idanunsu suka shiga cikin na juna,tun daga kan shantala shantalan ƙafafunta farare ya fara kallo har izuwa kan pro khaki eyes ɗinta,kafe juna da ido su kayi kamar sun samu TV Yumnah na daga tsaye tana kallon ikon Allah.
Nainarh ce ta fara janye ido ta gabanta na wani irin mummunan faɗuwa,ƙaton namiji a gabanta gashi daga ita sai towel,da sauri ta nufi dressing room ɗin har tana tuntuɓe,da kallo kawai ya bita har ta shige cikin ɗakin,wani irin yanayi yake ji a tattare da shi wanda bai san minene ba.
Tsaki yaja,duk sai yaji haushin kanshi ya rufeshi ko miye a jikin yarinyar da ya tsaya yana kallo shi da kullum cikin ganin ƴan mata yake daban daban wanda su ka fita komai nesa ba kusa ba,duk sai yaji ya tsani kanshi,a zafafe ya juya ya fice yana sake jan wani tsaki.
da kallon mamaki Yumnah ta bishi har ya ɓace ma ganinta, dariya ta kwashe da ita tana nufar dressing room ɗin da sauri, a tsaye ta samu Nainarh gaban clothset ta kasa taɓuka komai jikinta har wani rawa rawa yake.
“wai da baki sa kayan ba,ya Irfan fa baya son jira yana iya tafiyar shi”
shiru Nainarh tayi, girgiza kai Yumnah tayi “na lura ba ƙaramar wahala zan sha ba wajen dawo dake dai dai”
Yumnah ta ɗauko mata kayan da zata sa,ficewa tayi ta bata wuri,shaf shaf ta shirya ta fito,ficewa su kayi daga ɗakin.
parlorn mom su ka je,wayam su ka samu parlorn ba kowa,hakan yasa su ka ƙarasa bedroom ɗin mom ita ka ɗai su ka samu.
“mom ina ya Irfan ɗin?”
“ya fice,ga magani nan ya bata,zo Nainarh,ya jikin naki?” ƙarasawa tayi gaban mom ɗin
“da sauƙi”
“Allah ya ƙara sauki,mi Irfan ɗin yace yana damunki?”
“mom ya Irfan fa bai dubata ba cewa yayi mu same shi a parlorn ki”
“amma yace ya dubata,ɗauko mata ruwa tasha maganin to”
da to Yumnah ta amsa tana ficewa daga ɗakin,dawowa tayi hannunta riƙe da glass cup na ruwa, Nainarh ta miƙamawa,mom ta Bata maganin tasha.
“kwanta ki huta kinji” mom ta faɗa, a saman bed ɗinta Nainarh ta kwanta Yumnah sai complain take ma mom akan Nainarh ta cika sa damuwa a ranta.
*UNITED STATE*
_*Las Vegas (Nevada)*_
*10:00 pm*
A hankali ta zuro ƙafarta dake sanye da flip-flops masu gashi gashi, bathrobe ce a jikinta yayin da kanta ke naɗe cikin short towel da alama daga wanka take.
masu aikinta ne su ka shigo su biyu,juyawa tayi ta nufi ƙofar HOME BEAUTY bin bayanta masu aikin su kayi.
Ɗakin ya haɗu sosai,yana da girma ba laifi,komai na cikin shi unique ne,beauty shelf ne manne jikin bangon ɗakin an jera kayan gyaran jiki kala kala dana gyaran gashi harda foot care product da skin care product masu tsadar gaske,ga wani faskeken mirror a jikin bango tun daga sama har ƙasa ,daga gabanshi tulip chairs ne guda biyu, daga can ɓangaren da skin and foot product su ke lounger chair ce.
nufar lounger chair tayi ta zauna miƙar da ƙafafuwanta tayi tana kwantar da kanta saman head ɗin chair ɗin haɗe da lumshe ido.
ɗaya daga cikin matan ce ta matso ɓangaren skin product ta buɗe, mayuka masu matuƙar tsada ta shiga fito da su,gyaran jiki ta shiga yi mata,cikin ƙanƙanin lokaci fatar jikinta ta riƙa wani glowing tana fitar da wani daddaɗan ƙamshi.
A hankali ta buɗe idon ta,sauka tayi daga saman kujerar ta nufi mirror dake ɗakin,ƙarema kanta kallo ta shiga,ta ɗan ɗauki tsawan mintoci tana kallon kanta a mirror kafin ta nufi ɗaya daga cikin kujerun dake gaban mirror ta zauna.
ɗayar matarce ta nufo inda take,warware mata short towel ɗin dake saman kanta tayi ,nan take sumar kanta ta zubo har saman bayanta,hairdryer ta jawo, busar mata da kan ta shiga yi,bayan data kammala ne ta ɗauko smoothing serum haɗe wide tooth comb,shafa mata ta shigayi tana taje mata kan,saidata tabbatar ya shartu tukun ta shiga kwarara mata hair oils masu daɗin ƙamshi tana cuɗa kan yanda oil ɗin zai shiga ko ina.
Nan take color ɗin kanta light gloden brown ya ciza sai ƙyalli yake da ɗaukar ido ga wani daddaɗan ƙamshi dake fita daga cikin shi.
Straightener ta ɗauka ta shiga miƙar mata da gashi,bayan data ta gama miƙar da gashin,half up half down style tayi mata a kan, ba ita da ake yima gyaran ba hatta su kansu masu gyaran ba ƙaramin tafiya da su kan yayi ba.
Kallon kanta tayi a mirror,ita kanta ta san baƙaramin kyau tayi ba,side smile ta saki, simple make_up su kayi mata,baƙaramin kyau tayi ba.
miƙewa tayi ta nufi wata ƙofa a cikin ɗakin wacce za ta sadaka da dressing room ɗin ta.
Masha Allah na furta a yayin da nayi arba da dressing room ɗin wanda idan ba an faɗa maka a gida ne ba zaka yi tunanin boutique ne,duk wani nau'i na sutura a kwaishi a cikin, hatta jakunkuna da takalma babu abun da babu.
Ƙatuwar wall drawer ce mai ɗauke da sliding door zagaye da ɗakin,daga waje kana iya hangen tarin suturun dake ciki,ɓangaren pajamas da ban,ɓangaren gwon da ban skirts, shorts, underwears, trousers,shirt, sweaters komai da ku ka sani nadaga ɓangaren sutura an ware mashi wajen shi,idan muka koma ɓangaren takalma da jakunkuna abun sai ya baka tsoro,takalma ne da jakunkuna iri iri ga su na.
daga tsakiyar ɗakin half drawer ce ajiye ƙasa doguwa wacce itama marfinta ya kasance na glass, tsawanta ya kusa tsawan ɗakin ta kwance,an kakkasata kashi kashi wanda bakomai ne a cikinta ba sai gold jeweleries,wristwatch, watch chain, watch glass, sunglasses,links,neak chain,rings,babu abun da babu na adon ƴa mace,komai na ciki daga gold sai zinari.
bango ɗaya na ɗakin mirror ne,daga gaban shi stool ne guda biyu masu kyan gaske,zama tayi kan ɗaya daga cikin stool ɗin,masu aikin ne su ka shiga zaɓo mata kayan da za su dace da fitar da za tayi,sun jima wajen ganin sun ɗauko mata kayan da su ka dace,kafin su ka dawo in da take zaune hannunsu riƙe da sexy summer bodycon dress masu matuƙar jan hankali.
gwada kayan su ka shiga yi a jikinta,duk wacce su ka ɗaura saita girgiza kai alamar ba tayi mata ba,haka su ka shiga gwada kayan,aƙalla sun gwada yafi kala ashirin har sun fara gajiya da gwada mata kayan sai da ƙyar su kaci sa'a ta zaɓi wata White color mai one shoulder tana da baza daga ƙasa,bazar taji adon sparkling stones masu matuƙar ɗaukar ido.
A jiyar zuciya su ka sauke ganin sunyi nasarar samarta wacce ta dace don baƙaramar wahala su ka sha ba wajen ɗaukowa da maidawa, ɓangare takalma su ka koma nan ma jido mata su suka shiga yi,duk wanda su ka nuna sai ta nuna baiyi mata ba sai da ƙyar su ka samu ta ɗauki wani high hill Pump black color masu shegen tsini.
Ɓangaren da jeweleries su ke su ka nufa,basu sha wata wahala ba wajen zaɓo mata ɗan kunne da sarƙa sai Agogo da chain ɗin ƙafa.
Turo ƙofar ɗakin a kayi aka shigo tun kafin ta ƙaraso ta san ko wacece ita ka ɗai ce a cikin ma'aikatan gidan ke da lasisin shigowa part ɗin ta ba tare da ta nemi izinin ba, su kansu na'urorin dake sarrafa part ɗin sun san da zamanta.
kyakkyawar matashiyar dattijiwa ce ta shigo,baturiya ce, sai dai duk da manyantar ta hakan bai nuna a fatarta ba,fatarta kamar ba ta tsohuwa ba, kyakkyawa ce ajin farko ,hancinta tsaye yake babu lanƙawasa bakinta ɗan dai dai, launin idonta sak irin na Nailar Acme white grey.
long sleeve shirt ce a jikinta tare da A_line skirt wanda ya wuce gwiwarta,sumar kanta dake da jefi jefi na furfura sai sheƙi take tana ɗaukar ido, simple make_up ne a fuskarta ba ƙaramin kyau yayi mata ba jikinta sai fitar da wani ni'imtaccen ƙamshi yake.
Aunty Sophia kenan ƴar ƙwalisar tsuhuwa ko budurwa bazata gwada mata iya ɗaukar wanka ba wasu abubuwan duk a wurinta masu Aikin Nailar ke koya,ta san ta kan fashion.
In da Nailar take ta ƙarasa fuskarta ɗauke da murmushi wanda yaba dimples ɗin ta damar lotsawa,ta cikin mirror Nailar ke hangenta, Murmushi itama ta sakar mata.
cikin girmamawa masu Aikin su ka shiga gaishe da Aunty Sophia,harara ta ɗan watsa masu da sauri su ka sadda kai saboda sanin laifin su na ƙin faɗa mata Nailar zata fita, hugging ɗin ta tayi ta baya.
“i miss U so much Aunty sopi,jiya shi ne kwata kwata baki nemi ni ba?” Nailar ta faɗa a shagwaɓe kamar ba ita ba, murmushi Aunty Sophia tayi tana miƙewa tsaye haɗi da juyo da stool ɗin da Nailar ke zaune.
“my baby na shigo fa kina bacci,bana son na takuraki ne shiyyasa na fice”
ɓata fuska Nailar tayi “dama na san babu wanda zai kashe man ear phone sai ke”
“nayi laifi kenan?” taɓe baki Nailar tayi“ dan kin san baki laifi a wajena shiyyasa ki ke yanda ki ka ga dama”
ƴar dariya Aunty Sophia ta saki wacce ta bayyanar da kyawawan haƙoranta.
juya mata baya Nailar tayi tana turo baki,kallon masu Aikin tayi da ido tayi masu alamar su fice,kayan dake hannunsu su ka ajiye saman table su ka fice.
cikin ɗakin Aunty Sophia ta nufa, ɓangaren underwears ta nufa,bandeau style top ta ɗauko mata haɗe boyshorts masu matuƙar jan hankali white color.
dawowa tayi wurin Nailar,miƙa mata tayi “am sorry idan na ɓata ran Queen,ga wannan kisa sai na idasa shirya gimbiyata da kaina” turo baki Nailar tayi
“ni bazan iya sawa ba” ɗan zaro ido Aunty Sophia tayi
“ƴata fa yanzu budurwa ce dole ta koyi wasu abubuwan da kanta ba sai masu aiki sunyi mata ba”
tashi Nailar tayi sai ɓata fuska take ta amshi kayan dake hannun Aunty Sophia, murmushi Aunty Sophia ta saki,cikin ɗakin ta nufa sai turo baki take.
saman ɗaya daga cikin stool ɗin Aunty Sophia ta zauna tana sakin murmushi ita ka ɗai ke kema Nailar haka a zauna lafiya,tana da matuƙar ƙima a idanun Nailar a kwai soyayya mai ƙarfi a tsakanin su, Nailar ta ɗauketa tamkar mahaifiyarta tun tana ƴar ƙaramarta Aunty Sophia ke kula da ita Nanny ɗinta ce hakan yasa su ka shaƙu,wani lokacin har cewa masu Aikin gidan keyi suna kama.
Dawowa Nailar tayi in da Aunty Sophia take ta cire bathrobe ɗin pant da bra ɗin ne kawai a jikinta, a gaban Aunty Sophia tazo ta tsaya,da sauri Aunty Sophia tasa hannu ta rufe fuskanta hakan da tayi ba ƙaramin dariya yaba Nailar ba.
“baby ya kamata ki riƙa jin kunya ta fa, yanzu ke ko a jikinki ki tsaya haka a gabana”
“dan mi zanji kunyarki,ni bana jin kunyar kowa”
“dama taya za kiji kunya bayan wannan tsinannun na maki wanka har yanzu” ta faɗa yayin da take zame hannunta daga saman idanunta
ƴar dariya Nailar ta saki “Aunty sopi wai har yanzu baki daina jin haushin Lara da Lolah ba”
“taya zan daina jin haushin su,wasu ƙatti da su kamar ƴan dambe kullum suna gane man jikin baby” ta faɗa tana tsuke fuska
tsawan shekaru abun na cimata tuwo a ƙwarya dan dai kawai bata da yanda za tayi,da tana iya hana Nailar wankan da aike mata da tuni ta hana hatta masu aikinta haushin yanda Nailar ta sakar masu komai na rayuwarta take ji ,ace comon sutura su za su cire su sa mata.
“zaki fara ƴan tunane tunanen naki ko,su fa basa da laifi,nice mai laifi sai dai idan ni zaki hukunta”
“zan hukuntaki ne mana idan har baki daina wannan san jikin hanzarce ba”
“shikenan yanzu tunda kin korar mansu sai ki ƙarasa aikin na su”
dungure mata kai Aunty Sophia tayi tana ɗaukar rigar da zata sa,ɗan sosa in da ta dungureta tayi “ karfa garin wannan fushin naki ki ɓata man gyaran kai na”
zura mata rigar Aunty Sophia tayi,ta zage mata zip,kallon yanda rigar tayi mata tayi a mirror
“yanzu haka zaki je maza suyi ta kallon jikin ki”
“iya kar su kallon,kuma ma Ni da nake zaune a office ina ruwana da su”
“kafin ki shiga office ɗin maza nawa zasu kalle ki musamman wannan ƴan iskan security guard ɗin naki masu fuskar sheɗanu”
“to yanzu wane kaya ki ke so na sa?”
Na jikinta ta nuna mata dariya Nailar ta saki “ kina so ajina ya zuba ko,ace na zama tsohuwa”
“zaki zama tsohuwar ne mara kunya” murmushi kawai Nailar ta saki,idan har kaji dariyar Nailar to tana tare da Aunty Sophia ko momyn ta,Aunty Sophia baturiya ce amma ɗabi'unta sun banbanta dana turawa.
sun ɗan ɗauki tsawan lokacin wajen shiryawa,ba ƙaramin kyau Nailar tayi ba kamar ka saceta ka guda,sosai rigar tabi shape ɗin jikinta,ƴar pose Aunty Sophia ta ɗauko mata tare da sunglasses mai shegen kyau pose ɗin taji adon stones multicolors sai ɗaukar ido take,wata ƴar locker Nailar ta nufa,ɗan duƙawa tayi saitin wata ƴar na'ura dake jikin locker ɗin,idanunta ta saita a jikin na'urar da alama Eye ID ne a jikin ƙofar,nan take ƙofar ta buɗe,ƙananan bindigu ne a ciki nau'i daban daban tare da bullet ɗin su,watama idan ka ganta zaka ɗauka lipstick ne,ɗaya daga cikin su ta ciro.
bullet ta ɗauka guda biyar ta zuba a ciki kafin ta ɗaga rigar dake jikinta,wani ɗan belt dake jikin boyshorts ɗin dake jikinta ta saka bindigar da alama anyi shi ne saboda haka.
maida locker tayi ta rufe,juyowa tayi tana kallon Aunty Sophia da tunda ta buɗe locker ta kauda kai,bata ma san ganin abunda ke ciki, murmushi Nailar ta saki tana ƙarasowa inda take.
A tare su ka fice daga ɗakin Aunty Sophia na faɗin ji take kamar kar Nailar ta fita Ita kuwa sai sakar mata murmushi take.
A parlor su ka samu masu aikinta su biyu na jiran su kowacce su ta ɗauki wankan suit black color,tunda su ka fito Aunty Sophia ke banka masu harara sai kace sune za fita da Nailar ba ita bace zata fita da su ba.
Elevator su ka shiga ta kai su a salin main parlor gidan wanda in ka shigo dashi zaka fara cin karo.
main entrance ɗin gidan su ka nufa,yanzu ma sai da ƙofar tayi scanning fuskar Nailar kafin su ka fice harda Aunty Sophia.
Harabar gidan ƙwanyar take da haske kamar da rana,motocin ne guda biyar a bakin ƙofar fitowa,huɗu baƙaƙe ne ƙirar HYUNDAI yayin da ɗayar ta kasance fara ƙirar Mercedes benz s class a tsakiyar su.
rissinawa security guard da masu aikin dake yawo jefi jefi su kayi suna gaishe da Nailar da Aunty Sophia,cikin kulawa Aunty Sophia ke amsa masu.
har gaban Mercedes benz ɗin Aunty Sophia ta raka Nailar,da kanta ta buɗe mata door ɗin ta shiga tana mata fatan dawowa lafiya,kissing hannunta Nailar tayi tana faɗin saina dawo,a dawo lafiya Aunty Sophia ta faɗa tana rufe mata marfin motar.
Motocin security guard ɗin su ka shiga tare da masu Aikin Nailar,Aunty Sophia na nan tsaye har su ka nufi gate ɗin gidan,sai da taga bata ganinsu tukunna ta koma ciki,ranta duk a jagule, ji take inama zata iya hana Nailar fita.
_*HEART OF VEGAS CLUB AND CASINO*_
Tun daga nesa zaka fara hangen hasken sparkling bulbs na haska saman building ɗin in da aka rubuta _* heart of Vegas club and casino*_ da wani irin style.
Tsarin ginin building ɗin ma kawai abun kallo ne,
A katafaren parking lot na club ɗin da ya ciki da tarin rides masu shegen kyau da tsada su kayi parking a wajen parking ɗin motocinta wanda ya kasance nata ne ita kaɗai su ka nufa.
Dai dai ta parking ɗin su su kayi, security guard ɗinta ne su ka fara fitowa tare da masu aikinta,ɗaya daga cikin su ne yazo ya buɗe mata marfin motar.
A hankali ta zuro ƙafafunta,kafin ta ƙarasa fitowa,gaba tayi suna biye da ita a baya,da wasu jibga jibgan security guard dake sanye cikin baƙaƙen kaya ƙugunsu soke da bindigu su ka ci karo a bakin entrance ɗin shiga,tun kafin ta ƙaraso su ka bata hanya suna ɗan rissanar da kansu Alamar gaisuwa,ko kallon in da suke ba tayi ba ta nufi security door ɗin shiga.
Wata irin katafariyar ƙofa ce wacce kai daga ganinta kasan ba ƙaramin waje bane,ƙofarce ta fara magana cikin harshen turanci
“welcome to Heart of Vegas,ur Access card please” da sauri ɗaya daga cikin masu aikin ta ciro wani ɗan card a pose ɗin Nailar dake hannunta ta mannashi a jikin ƙofar.
dan da nan ƙofar tayi acknowledging card ɗin tana faɗin“welcome miss Nailar”
nan take ƙofar ta shiga zugewa,ciki ta kunna kai suna biye da ita.
wani irin katafaren club ne su ka shigo,yaji kayan alatu kamar baza'a mutu ba,yana yin tsarinshi yasha ban ban da sauran clubs.
mata ne a tsaye a stage strippers cikin wata irin shaiɗaniyar sutura suna poll dance sauti na tashi,ga mata ga maza wasu a zaune wasu a tsaye suna taka rawa ana spraying dollars,wasu na shan giya,wasu na shaƙar cocaine,ga customize azul na yawo ta ko’ina ana kaiwa wayanda sukai order, gawasu kalan shisha da a irin wannan club ɗin kaɗai ake samun su, ga vape anasha suma,idan kashigo club din nan kai kanka kasan ana barin kuɗi, ga wasu irin security guards dake a different corner tsaitsaye da communicative devices a kunnensu kai kace gumaka ne yanda suka tsaya kiƙam ko alamar breath babu.
Kiɗan dake tashi ne ya tsaya,Dj ne ya shiga sanar da zuwan Nailar hakan yasa mutanen dake ciki kai duban su gareta,ihu da sowa ne ya fara tashi wasu na ambatar Queen wasu President,ƙayataccen murmushi ta saki tana ɗaga masu hannu,gun gun wasu maza ne su ka nufo in da take sai tangaɗi suke alamar sun sha sun sha sunyi tatul,da sauri security guard ɗinta su ka dakatar da su, murmushi gefen fuska ta saki tana yarfa masu ƴan yatsunta haɗi da ɗan cizon ƙasan lips ɗinta so sexy,ba ƙaramin jan hankalin mazan dake wurin tayi ba harda ma mata,ca su ka yi mata da idanu kamar tsaffin mayu ga nama suna kallo amma ba halin tunkara.
fly kiss ta sakar masu tana nufar glass elevator dake cikin wurin, security guard ɗin ta na biye da ita.
Wani irin ƙato casino su ka shigo,yaji kayan alatu a cikin uwar dukiya a ka narkar wajen gidana shi ba kaɗan ba ,da kaɗan ne bai ƙarasa girman club ɗin da su ka fara shigowa ba.
Wani irin casino Aesthetic ne mai matuƙar ɗaukar ido,ga wasu matsiyatan poker tables and gaming table haɗe da chairs ɗin su,casino cards ne a kowane table,a ƙalla ko wane table na ɗauke da chairs guda biyar.
Mata da maza ne zazzaune saman chairs ɗin, casino cards ne a gabansu suna buga caca ga tarin dollers da kowane a cikin ya ajiye a matsayin kuɗin wasan shi, nau'in beers ne masu tsadar gaske haɗe cigarettes wanda tsadar su ta kai mutum ya sayi gida da mota na mutunci a gaban su,wasu na shan giya wasu na zuƙar taba ana buga wasa kiɗa na tashi ƙasa ƙasa.
nan ma security guard ne a kowane corner tsaye ƙiƙam.
murmushi Nailar ta saki ganin yanda ake buga wasan,fito tayi wanda ya jawo hankalin mutanen dake wurin,ihu mazan dake wurin su ka saka suna faɗin QUEEN!!!!
dariya Nailar ta saki tana ɗaga masu hannu,wani ɗan corridor ta nufa,shuffle machines ne haɗe da slot machines, video poker and video lottery terminals a wajen, ma'aikata ne zaune saman poker chairs suna opreting ɗin su.
cikin girmamawa su ka shiga gaishe da ita kamar za su russuna mata,jin jina masu kai ta shiga yi, office ɗin ta ta nufa dake can floor ɗin ƙarshe,a bakin ƙofar shiga office ɗin security guard ɗinta suka tsaya masu aikin su ka bi bayanta.
wasu numbobi ta danna a jikin ƙofar nan take ƙofar ta buɗe,kutsa kai tayi ciki jelarta na biye da ita,wani irin katafaren office su ka shigo kamar na shugaban ƙasa,ga sanyin AC dake busowa kamar ƙanƙara,ƙaton transparent glass office table ne a ciki haɗe leather chair mai shegen kyau,laptop ce ajiye saman table ɗin haɗe office lamp,daga gefe 50gm ne na cocaine anyi packaging ɗin su sai Cuba Aliados cigarettes dake a cikin ƙana nan kwalayenta itama anyi packaging ɗinta sai kwalaben shisha nau'i daban daban masu tsadar gaske,ga ɗan madaidaicin bottle keeper wanda aka jera kwalabanan beers kala daban daban.
daga can gefe poker table ne wanda ke ɗauke da casino cards,sai faskekiyar glass computer dake ajiye anyi connecting ɗin ta da gaba ɗaya CCTV CAMERAS dake heart of Vegas.
Cikin office ɗin su ka ƙarasa,chair ɗinta ta nufa ta zauna yayin da masu aikin suka nufi wasu sofas guda biyu su ka zauna, laptop ɗin dake ajiye saman table ɗin ta buɗe,opreting ɗinta ta shiga yi a hankali.
Muryar na'urace ta karaɗe office ɗin tana sanar da zuwan MDs na gaba ɗaya club da casino ɗin, izinin shigowa ta ba da ta hanyar danna wani maddani a jikin table ɗin,a hankali ƙofar ta shiga zugewa,wasu murɗa murɗan ƙatti ne majiya ƙarfi su ka shigo cikin shigar baƙaƙen suit,gaban table ɗin Nailar su ka ƙara so.
gaishe da ita su kayi suna russunawa,amsa masu tayi tana nuna masu kujerun dake facing ɗinta,zama su kayi saman kujerun.
“is there any problem?”
“no ma,but kayan da Boss ta turo suna hanya,muna sa ran isowar su next tommorow around 2:00Am”
jinjina kai Nailair tayi“good,bayan nan babu komai?”
“yes”
“ok,take this” ta faɗa tana nuna masu packeg ɗin cocaine da cigarettes,miƙewa tsaye su kayi,ɗaukar kayan su kayi suna mata sallama haɗi da ficewa.
tura kujeran da take zaune tayi,ƙafafunta ta ɗaura saman table ɗin tana jinginar da kanta saman head ɗin kujerar,ɗaya daga cikin masu aikin ce ta miƙe,can cikin office ɗin ta nufa,bata jima a sai gata ta fito hannunta ɗauke da ƙatuwar kwalbar champagne haɗe da champagne tulip glass sai ice a cikin bowl,har gaban table ɗin Nailar ta ƙaraso,ajiyewa tayi,ice ɗin ta fara zubawa a cikin cup kafin ta buɗe kwalbar, tsiyaya mata tayi cikin cup ɗin ta miƙa mata,amsa tayi tana wani lumshe ido.
barin wajen tayi,komawa tayi ta ɗauko masu milkshakes guda biyu,duk yanda su ke son shan kayan shaye shaye Nailar ta hana sai dai su sha lemu ko milkshake.
wayarta ce ta fara ringing,kallon screen ɗin tayi love shine sunan daya bayyana, murmushi ne ya bayyana a fuskarta, picking call ɗin tayi tana kara wayar a kunne.
“sweetheart” shine sunan da Nailar ta furta,on the other hand murmushi ta cikin wayar ta saki
“baby nah ya ki ke,ya gidan” ɓata fuska Nailar tayi “babu daɗi,yaushe zaki dawo?"
“kinyi kewata ne?”
“i really miss u, please come back home” Nailar ta faɗa kamar zata sa kuka
murmushi ta saki
“i think next week,fatan kina office?”
“momy mai makon ki tambayi lafiyata amma ta office ki ke,wai tsaya dani da wannan business ɗin ma wa ki ka fi so ne?”
“nafi sonki sama da komai, sorry fatan kina lafiya”
“lafiya lau,fatan kema haka”
“ina lafiya kamar yanda ki ke,kina office ɗin?”
ɓata fuska Nailar tayi
“yes,su Joseph sun sanar dani kayan da ki kayi order suna hanya?”
“yes, Please my baby ki kasance a wurin lokacin da shipment ɗin zai ƙaraso bana son any problem ya faru, kaya ne masu tsadar gaske, munada tarin customers a ƙasa wanda zuwan kayan kawai su ke jira”
“please momy,su Joseph za su iya ji da komai ba sai naje ba”
“no kije dai zaifi,zan turo maki komai ta email,ki tabbatar ba wani kuskure”
turo baki Nailar tayi ba tare da tace komai ba da alama ba taji daɗi ba,sallama su kayi, ajiye wayar tayi saman desk tana lumshe ido haɗe da sakin ɗan ƙaramin tsaki.
Sai Around 5:00Am ta koma gida a gajiye,ko kayan dake
jikinta bata cire ba ta faɗa saman bed,ficewa masu aikin su kayi bayan sun ajiye mata bag ɗin ta haɗe da wayarta.
Aunty Sophia da saurinta ta zo amma sai ta tarar tana bacci, murmushi kawai tayi taja mata blanket,kissing forehead ɗinta tayi ta fice daga ɗakin...
_Ep 13_14_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
______________________________
*ABUJA NIGERIA*
Turus ta tsaya ganin ko kallon dinner ɗin da aka kawo mata ba tayi ba, kallonta ta kai zuwa bed ɗin dake ɗakin, a zaune take ta jingina da head bord ɗin gadon,photon mahaifiyarta tare da mahaifinta ne riƙe a hannunta sai aikin shafawa take yayin da hawaye ke sintiri a fuskarta.
girgiza kai Yumnah tayi yayin da take ƙarasawa bakin bed ɗin, zama tayi kusa da ita tana dafa kafaɗarta,cikin sigar lallashi ta fara magana.
“sister Nainarh na san abun da ciwo, nasan zai ɗauki lokaci kafin zuciyarki ta dake, sai dai ki sani yawan ku ka da sa damuwa a rai bashi ke maganin matsala ba Adu'a itace maganin duk wata matsala, a halin yanzu Adu'arki su ke buƙata sama da komai, in sha Allah komai daran daɗewa gaskiya za tayi halinta, in dai da rai wata rana a gabanki duk wani mai sa hannu a al'amarin zai zo a ƙasƙance dan neman yafiyarki,dan haka ina so ki daina yawan kukan nan da sa damuwa a ranki”
shiru Nainarh tayi tana sauraron Yumnah, hannu Yumnah tasa ta shiga goge mata hawayen dake zuba daga fuskarta tana sake kwantar mata da zuciya.
“kiyi haƙuri kinji,komai zai wuce in sha Allah”
“na kasa mantawa da irin kisan wulaƙancin da a kayi ma mahaifana,a gaban su ka kashe shi amma Court ta ɗaura laifin a kan mahaifiyata ba tare da tausayin halin rasa mijinta da take ciki ba”
“Allah ya fisu Nainarh,duk wani mai sa hannu asirin shi zai tonu,ki kwantar da hankalinki komai zai wuce mahaifiyarki zata dawo gare da izinin Ubangiji,ki daina kuka kinji” jinjina mata kai Nainarh tayi,sosai Yumnah ta shiga kwantar mata da hankali,har ta samu ta ɗan saki jikinta.
*ASO VILLA*
Kyakkyawar matashiyar matace kwance saman makeken gadon ta,daga yanayin yanda numfashinta ke fita zaka fahimci ba ta cikin kwanciyar hankali.
Wani mahaukacin Nocking a kayi ma ƙofar ɗakin wanda yayi sanadiyyar farkawar ta,a firgice ta farka tana ambaton Innalillahi wa Inna Ilaihi rajiun,sake nocking ɗin a kayi kamar za'a ɓalla ƙofar.
Waro kyawawan idonta tayi tana kallon ƙofar gabanta na wani irin lugudan duka, Adu'a ta shiga yi Allah yasa ba shi bane duk da ta san babu wanda zaiyi mata wannan Nocking ɗin a irin wannan lokacin bayan shi.
Wata irin kakkausar murya wacce kenuna mamallakinta a buge yake taji daga bakin ƙofar ɗakin
“KAINART wai uwar mi kike a ciki ne da bazaki zo ki buɗe man ba, wallahi ki ka bari na shigo da kaina sai kin yaba ma aya zaƙinta” ya faɗa yana sake kaima ƙofar wani mahaukacin duka.
hawaye ne su ka wanke fuskarta dama ta san zaiyi wuya ace ba shi bane,ita kam yau ta shiga uku dan daga yanayin muryar shi baya a cikin hayyacinshi,banko ƙofar yayi kamar zai karyata, da gudu ta duro daga saman gado jiki na rawa ta kama handle ɗin ƙofar ta buɗe mashi.
matashin magidanci da aƙalla zai kai kimanin shekaru 32 zuwa da 3 a duniya,baƙaƙen suit ne a jikinshi yayinda hannunshi ke riƙe da ƙatuwar Whiskey , kyakyawane sai dai munanan ɗabi'un shi sun boye kyawun fuskarshi.
cikin ɗakin ya ƙaraso yana huci kamar wani mawuyacin zaki, jifa yayi da kwalbar dake hannunshi ƙasa ta tarwatse sauran ruwan dake ciki ya malale a ƙasa,ja da baya tayi ganin irin kallon ƙasƙancin da yake mata, cikin rawa murya tace
“dan Allah ya Zaabith kayi....” bata ƙarasa ba ya wanketa da lafiyayyun maruka har sau biyu,dan da nan jinta da ganinta su ka ɗauke na wucin gadi taurari ta fara gani suna mata shawagi a cikin idanunta, bata dawo daga hutun marin da yayi mata ba taji saukar belt, dukanta ya shiga yi kamar ya samu jaka.
kuka take tana ambaton “dan Allah ya zaabith kayi haƙuri, na tuba bazan sake ba” ko saurarenta baya yi dukanta kawai yake kamar an aiko shi,bai ƙyaleta ba sai da ya tabbar ya sauya mata kammani tukun ya jefar da belta ɗin ƙasa,wuyan rigarta ya cakumo yana manne bakinshi da nata,kamar zai cire mata baki haka ya shiga kissing ɗinta,cikin rashin imani ya shiga yayyaga suturar dake jikinta, doguwar sumar kanta ya jawo kamar zai cire mata ita yayi jefa da ita saman gadon babu tausayi ko imani ya shiga biyan buƙatar shi da ita, sai da ya tabbar ya kusa kasheta tukun ya ƙyaleta ya miƙe,yana tangaɗi ya nufi wata ƙofa wacce nake kyautata zaton toilet ne.
wani sabon kuka ta saki ta rasa wannan wace irin rayuwa take, ko baiwar da aka siyo ba'a wulaƙantata kamar yanda Zaabith ke mata kuma a haka wai ita ɗin matarshi ce ta sunnah wacce su kayi Auren soyayya bana ƙiyayya ba,wasu zafafan hawayen ne suka sake wanke mata fuska.
da jan jiki ta sauko daga saman bed ɗin,blanket ɗin dake shimfiɗe taja ta rufe jikinta,a daddafe ta nufi ƙofar fita, ficewa tayi daga ɗakin, a hankali take tafiya tana ƴan waige waige gudun karta haɗu da wani ko masu aikin gidan su ganta a irin wannan yanayin, Allah ya taimaketa har ta kawo bakin ƙofar wani ɗaki bata haɗu da kowa a hanyar ba, tura ƙofar ɗakin tayi ta shige,mai da ƙofar tayi ta rufe da key,a jikin ƙofar tabar key ɗin,yara ne ƴan maza guda biyu kwance saman makeken bed ɗin dake ɗakin cikin shigar PJ white color, sai sharar baccin su suke hankali kwance.
Ƙofar toilet ta nufa, tsarkake jikinta tayi,sannan ta gasa jikinta da yayi mata tsami, bathrobe ta zura a jikinta ta fito,zuwa tayi tsakiyar yaran ta kwanta bayan ta kashe light ɗin ɗakin,hugging ɗin yaran tayi ajikinta yayinda hawaye ke sintiri zuba daga idanunta, tsawan shekara goma kenan da yin Auren su,shekara ɗaya kawai su kayi suna shan soyayya amma tun daga nan komai ya lalace kullum cikin fuskantar azaba take daga Zaabith duk wasu munanan halayenshi babu wanda bai nuna mata ba, ya fita gida sai sanda yaga dama zai dawo,idan ya koma wajen Aiki Lagos sai yayi wata da watanni bai dawo ba duk ranar da zai dawo a buge yake dawo mata kuma a ranar ta shiga uku, iyayenshi sunyi faɗa sunyi faɗan sunyin jan hankalin amma a banza,duk da fara tara iyali da su kayi bai sa ya canza halayen shi ba.
tayi tunanin zaman su a gidan gomnati zai sa ya canza ɗabi'un shi kodan gudun zubar mutuncin mahaifin shi da siyasarshi a idon duniya,amma a banza saima abun da yaci gaba gashi duk wannan uƙubar da take ciki ta kasa sanar da iyayenta duk dan gudun lalacewar zumunci dake tsakanin su saboda mahaifin Zaabith yaya ne ga mahaifinta uban su ɗaya.
ta jima tana saƙawa da kwancewa har baccin wahala yayi awan gaba da ita rungume da ƴaƴanta, lokacin da ya fito daga toilet ɗin ƙugunshi ɗure da towel, kallon gadon daya barta a kwance yayi, ganin wayam bata nan me yasa shi jan wani mahaukacin tsaki yana faɗin “zan kamaki ne yarinya”.
ƙofar fita shima ya nufa, ficewa yayi daga ɗakin zuwa master bedroom ɗin shi, yana shiga ɗakin a saman gadon shi ya faɗa rub da ciki babu Adu'a babu komai,cikin ƙanƙanin lokaci bacci yayi awan gaba dashi.
*WASHE GARI*
Tunda Asussu ba ta koma ɗakinta ta gyara gudun masu aiki su ganshi haka bata son su zargi wani Abu,duk da irin azabar da take sha a wajen shi har kawo wannan lokaci tana son shi tana kuma yi mashi kallon uban ƴaƴanta, Adu'arta a kullum Allah yasa ya gane kuskuren da yake aikatawa.
shaf shaf ta gama kauda komai,toilet ta shiga wanka tayi haɗe da Alwala,fitowa tayi ta nufi cloth set ɗin ta,doguwar rigar Abaya ta ɗauko ta zura a jikinta,da ƙyar ta zura rigar a jikinta saboda ciwukan da taji a dalilin dukan da yayi mata duk ya faffasa mata baya,sawun duka har saman wuyanta ga marin da yayi mata, ta san dole sawun hannunshi ya fito.
a saman kai ta ɗaura mayafin Abayar tukun ta ɗauko hijab,ficewa tayi daga ɗakin dan ta san a kowane lokaci zai iya dawowa.
Bedroom ɗin yaranta ta koma,a kwance ta same su kamar yanda ta barsu, tashin su ta shiga yi domin lokacin sallah yayi,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga toilet su ka ɗauro Alwala,jallabiya ta ɗauko masu cikin kayan su, cire PJ ɗin dake jikin su suka yi suka zura jallabiya.
“momy Dady ya dawo ko??”faɗuwa gabanta yayi dalilin tambayar da yaron yayi mata.
“Eh ya dawo tare ma za ku tafi masallaci,yana ɗakin shi kuje ku same shi”
“momy shine ya dake ki ko” faɗuwa gabanta ya sake yi
“shine ko momy??” yaran su ka sake jefa mata tambayar
saurin ƙaƙalo murmushi tayi tana girgiza masu kai alamar A'a
“shi ne mana momy,ga sawun duka nan a fuskar ki”
“faɗuwa nayi Ammar ba duka bane”
“duka ne mana,gashi nan sawun hannunshi ne a saman fuskar ki”
“momy mun gaji da dukan ki da dady yake,sai mun rama maki dukan da yake maki yaji shima idan da daɗi,kuma sai mun sanar da grandfa har yanzu bai daina dukanki ba”
duk yanda take daurewa kasawa tayi hawaye ne su ka wanke fuskarta,tun tana ɓoye masu yanzu yaran babu abunda ba su sani ba game da irin zaman iyayen na su.
hanyar fita su ka nufa suna sai sun faɗama grandfa Aman har ya fara zubar da hawaye,da sauri tabi bayan su,jawo su tayi zuwa jikinta, hugging ɗin su tayi.
“kuyi haƙuri Aman kar ku sanar da dady Ahmad,dadyn ku bada gangan ya mareni ba ya bani haƙuri bazai sake ba”
“momy kullum haka yake faɗa,amma har yau bai daina ba,kinga da gangan yake dukan ki”
“duk da haka Ammar shi ɗin fa mahaifin ku ne,idan baku rufa mashi asiri ba waye zai rufa mashi,kuyi haƙuri kunji ko,ku yafe mashi nima na yafe mashi”
sake shigewa su kayi jikinta suna sakin kuka,wasu hawaye ne itama su ka wanke fuskarta,ɗan bubbuga bayan su ta shiga yi
“ya isa haka ku daina kuka kun ji,zai daina wata rana” raba jikin su ta yi,hannu tasa ta shiga goge masu hawayen fuskar su.
“kuje yana ɗaki ku same shi” maƙe mata kafaɗa su kayi
“mu dai tare da grandfa zamu tafi da su uncle Waseef”
“ki bar mu kawai momy muje tare da grandfa”
“shikenan sai kun dawo,Allah yayi maku Albarka”
da Ameen su ka amsa suna nufar ƙofar fita,turo ƙofar ɗakin da a kayi ne ya dakatar da su,gaba ɗayan su suka kai dubansu gare shi.
farar jallabiya ce a jikinshi,jikin shi da alamar danshin ruwan da yayi alwala,cikin ɗakin ya ƙaraso,hannuwan shi biyu ya buɗe ma yaran alamar su zo gareshi fuskar shi a sake.
tsuke fuska su kayi suna bin shi da wani irin kallon tsana,lamarin yayi matuƙar ɗaure mashi,da sauri ya kai duban shi ga kainart dake tsaye tana kallon su,saurin kauda kai tayi kamar ma bata ga abun da su Ammar ɗin su kayi mashi ba.
ta gefen shi su ka zo za su wuce,saurin kamo hannun su yayi,wayancewa yayi irin kamar ma bai fahimci mi yaran su ke nufi ba “ fushi ku ke da dady saboda bai dawo da wuri ba,kuyi.....” bai ƙarasa ba saboda fisgewa da su kayi daga riƙon da yayi masu,ƙofar fita su ka nufa ba tare da ko sun kalli inda yake ba,baki ya saki kamar saka rai wai yau shine su Aman su kayi ma haka,mi hakan ke nufi mahaifiyar su ta fara hure masu kunne ke nan.
yana nan tsaye har su ka ɓacce ma ganin shi,jinjina kai yayi yana nufo in da take,da sauri ta ɗauki hijab ɗin ta zata zura a jikinta,a zafafe ya fisge hijab ɗin yayi jifa da ita,damƙara sumar kanta yayi,rintse ido tayi saboda zafin daya ziyarci kanta.
“wato raini ya fara shiga tsakanin mu ko,har kin fara tara yara kina gaya masu ina dukan ki ko,a tunaninki dan kin sanar da su hakan zai canza wani Abu ne,ki sani a duk faɗin duniyar nan babu wani wanda ya isa ya hanani abun da nayi niyya ko da kuwa mahaifina ne,dan na san shi ki ke tunanin zai iya hanani??”
cikin ƙunar rai tace “a tunanin ka ya Zaabith su Ammar ba su san abun da ka ke aikatawa ba ne?,ko a tunaninka ba su da wayan sanin abun da kake aikatawa ,karka manta kasha dukana a gaban su dan mi baza su ji haushin ka ba,nifa mahaifiyar su ce”
fisgar kanta yayi kamar zai cire shi gaba ɗaya “to sai mi dan sun sani,ke baki isa ki shiga tsakani na da su ba saboda ni ɗin mahaifin su ne ko suna so ko basa so”
fashewa tayi da kuka
“kaji tsoron Allah ya Zaabith,ka sani alhakin mu bazai barka ba,Allah zai saka m...” tsawa ya daka mata
“ya isa haka” ya faɗa yana sakin gashin kanta,idan da abun da ke tada hankalinshi ta furta Allah zai saka mata baya son tana barin shi da Allah, yana tsoron ranar da Allah zai tashi saka mata.
ƙofar fita ya nufa,da kallo ta bishi har ya fice hawaye sai sintiri suke a fuskarta.
hijab ɗinta ta zura, prayer mat ta shinfiɗa,gabatar da sallah ta shiga yi,ta jima zaune tana kai ku kanta ga Ubangiji sammai da ƙassai.
Tana a nan kwance a kayi Nocking ɗin ɗakin, tambayar waye tayi ba tare da ta tashi ba.
“saraj ce dama madam Salima ce tace ki fito time ɗin breakfast yayi,takuma ce anjima za ku je can family house ɗin ku”
“bana jin daɗi sarah,ki kawo man nawa breakfast ɗin nan kawai”
“to shikenan,ya zance ma Madam ɗin?”
“ki faɗa mata bana lafiya”
“to shikenan” mai aikin ta faɗa tana barin wajen,bayan kamar minti biyar mai aikin ta dawo.
iznin shiga Kainart ɗin ta bata,a hankali ta turo ƙofar ɗakin ta shigo hannunta ɗauke da tryan data haɗa mata breakfast ,saman ɗan table ɗin dake ɗakin ta ajiye mata.
“sannu madam,Allah ya baki lafiya”
“Ameen sarah,su Ammar na wajen dady ne?”
“eh suna can harda yallaɓai Zaabith”
“ok shikenan zaki iya tafiya”
“ok Allah ya ƙaro sauƙi” da Ameen kainart ɗin ta amsa,ficewa mai aikin tayi.
* Big Daddy's house*
Mom da ya Naeem ne zaune a saman gondola chairs dake cikin garden ɗin gidan,ɗan madaidaicin glass table ne a gaban su an cika masu shi da fresh fruit haɗe da snacks, yayin da mom ke riƙe da wasu takardu a hannunta sai jujjuyasu take,
kallonta ya Naeem yayi “mom kinyi shiru ba kice komai ba?”
ɗan sauke ajiyar zuciya tayi tana kallon ya naeem ɗin daya kafeta da idanu,takardun dake hannunta ta miƙa mashi
“ban san ta in da zan fara maka bayani ba ne naeem”
“koma ta yayane ki fara mom Zan fahimce ki in sha Allah”
jinjina kai mom tayi “wani taimako nake so kayi mana game da case ɗin Asma'u”
“umarni za kice mom,Dan kinfi ƙarfin neman taimako a gare mu,mi kike buƙata nayi maki a kan case ɗin?”
“yawwa,ina so ka sake wani sabon bincike a kan case ɗin bayan wanda jami'an tsaro su kayi”
“amma mom saboda mi?”
“naeem zuciyata ta kasa yarda cewa Aminiyata zata iya aikata wannan laifin ,duk da ɗan Adam yana canzawa akan yanda ka san shi amma ita ina kyautata mata zato”
“shikenan mom in Sha Allah zanyi yanda ki ke so ,amma dole sai na samu wasu ƙarin bayanan sama da wannan da ki ka bani”
“wanann ba damuwa bace,ko a wajen yarinyar ta zaka iya samun wasu baya nan,sannan akwai masu aikin gidan da masu gadi duk da sun bada bayanan su a court da wurin ƴan sanda sai dai bayanan na su ban gamsu da su ba, ina ji a raina kamar sun ɓoye wani ko wanda su ke da alhaki a kan kisan su suka hansu faɗar gaskiya”
“shikenan ba damuwa mom ko da sun ɓoye wani Abu nayi maki alƙawarin sai sun magantu dole za su faɗi gaskiya”
“yawwa haka nake son ji,amma ina so ya zama sirri kai ka ɗai nake so kayi aikin sai wanda ka yarda da dashi daga cikin yaran ka wanda kasan bazai yaudareka ba”
“karki damu da wannan mom,komai zai tafi yanda ki ke so in sha Allah”
jinjina kai mom ɗin tayi “bayanan komai yana a cikin takardun nan”
“zaka samu komai a ciki,tun daga tarihin rayuwar su, sunayen mutanen da suke mu'amula da CP lokacin da yana raye da ita kanta Asma'u da duk wani ma'aikacin su,hatta ƙasashen da su ke yawan zuwa da garuruwa da wurare da su ka fi yawan zuwa a faɗin ƙasar nan zaka samu, Naeem kar kayi sakace da su duk da na san ba halinka bane amma ka kula da su sosai akwai baya nan da ko Court bata san da zaman su ba naƙi bayyanar da su ne a gabanta saboda wasu dalilai nawa, dan Allah ka maida hankali a kan su Naeem”
ɗan dariya ya Naeem yayi “dama na daɗe ina zargin tsakanin ke da dady wa SAM ya gado naci da bin ƙwaƙwafi case Ashe ke ce?”
murmushi mom ta saki “bana son shashanci Naeem,wannan case ɗin karka manta Aminiyata ce a ciki kaga kuwa dole na nace akan shi”
“haka ne in sha zan baje gaba ɗaya ilimina akan wannan case ɗin,zanyi ƙoƙarin ganin munyi nasarar fitar da momy in sha Allah”
“haka nake son ji,ka ko yi waya da SAM?”
“A'a,mun kwana biyu ba muyi waya ba,kin san ɗan naki sarki ne sai ya sha iska yake neman mutane gashi ko ka kira shi a banza idan ba yana free ba shine zai ɗaga ko idan yaga missed call ya kira”
“nima kwana biyu bai kirani ba,amma Alyar da James sun kira ni kuma sun shaida man yana lafiya,aiki ne yayi mashi yawa”
“nima Alyar ya kirani harma ya ke sanar dani suna nan zuwa ƙarshen shekarar nan shi da James,na dai ce su lallaɓa SAM ɗin nima zan gwada sa'ata ko za'a samu wannan karan ya biyo su”
“duk lokacin da mu kayi waya dashi sai na roƙi Alfarmar ya taimaka ko kiran dadyn ku ne yayi a waya ko ya tura mashi message ko da bai zo ba amma ina,baƙar zuciyar dana rasa awajen wa ya gadota taƙi barinshi,harda momy da Uncle Jonas nasha haɗashi saboda yafi jin maganar su sama da tawa amma a banza sunyi sunyi yaƙi, ko da picking call ɗin dadyn ku ne yayi idan ya kirashi amma ina”
“in sha Allah mom wata rana da ƙafarshi zai tako ya zo har ƙasar nan saboda dady,komai zai wuce”
“bana tunanin SAM zai yafe ma dadyn ku,ya riƙeshi sosai a zuciyar shi,tsawan shekara 18 fa kenan”
“mom ki daina wannan tunanin in sha Allah zai yafe mashi wata rana,koda shekara 50 ne,ke da ma yayi ma laifin ki ka yi haƙuri bare shi SAM ɗin,zai dawo da kanshi saboda dadyn in sha Allah”
“Allah yasa haka Naeem”
“in sha Allah mom,wata rana komai zai wuce har jikokin SAM ɗinki za ki gani a gabanki dan na san burinku kenan ke da Dady”
murmushi ta saki “Allah yasa haka,da kuwa nayi farin ciki mara misaltuwa”
“Ameen mom,ni zan wuce gida”
“ok muje nima zan koma ciki” tashi su kayi, jerawa su kayi a tare su ka nufi ƙofar cikin gidan.
part ɗin dady su ka nufa,a kishingiɗe su ka same shi saman rug carpet yana duba wani littafin addini,bakin su ɗauke da sallama su ka ƙara da ciki,ɗagowa dady yayi yana amsa masu sallamar.
kusa da shi ya Naeem ya zauna mom kuma ta zauna saman kujera
kallon su dady yayi fuskarshi a sake yace “uwa da ɗa daga ina haka,wani abun daɗin ya faru ne”
murmushi ya Naeem yayi “barka da hutawa dady”
“barka dai Naeem,ya Aiki yau ba ku shigo tare da Adnan ɗin ba?”
“Eh kila sai anjima zai shigo”
“Allah ya kaimu anjimar lafiya,na shiga wurin Abbah ɗazu yace kwana biyu bai saka a idon ba ina fatan dai lafiya?”
“Ayyuka ne su ka ɗan yi man yawa kwana biyu shiyyasa ban shiga ba na bari sai ranar juma'a”
“duk da haka Naeem tunda har kana samun lokacin shigowa nan ai ka ɗan leƙa ku gaisha ko da da dare ne”
“in sha Allah daga nan zan shiga”
“yawwa hakan yayi,Allah yayi maku Albarka”
“Ameen dady” ya Naeem ɗin ya faɗa yana miƙewa,sallama yayi masu ya fice.
*Main Parlor*
da sauri yaja baya saboda karon da yayi da mutum,duban shi ya kai ga matashin saurayin dake tsaye a gaban shi sai layi yake kamar zai faɗon mashi,da tsantsar mamaki yake bin saurayin dake neman ya raɓa ta gefenshi ya wuce,a wani zafafe ya fisgoshi baya,saukar maruka matashin saurayin yaji a saman fuskar shi wanda su kayi sanadiyyar dawowar shi cikin hayyacin shi,da sauri yasa hannuwanshi ya dafe kumatunshi.
ɗan uwan shi dake bayan shi ganin irin marin da ya Naeem ya sauke ma ɗan uwan nashi ne yasa shi komawa baya cikin sanɗa ya koma parking space ya shige motar da su ka zo,mai da ƙofar yayi ya rufe a hankali,shiru yayi yana baza ido a hanya ko zaiga wucewar ya naeem.
tun daga kan crazy short ɗin dake jikin shi da ƴar iskar shirt ɗin dake jikinshi mai kama da rariya zuwa ɗan iskan askin dake kanshi ya Naeem ke kallo,ga wani chain dake manne a wuyan shi kunnenshi ɗaya a huje yake ya saka ear ring.
wani marin ya Naeem ya sake kifa mashi,dafe kuncinshi yayi sai ga hawaye shar da alama marin ya shige shi sosai
“dan Allah second father kayi haƙuri,wallahi bangaka bane shiyyasa na bigeka” saurayin ya faɗa yana watso ido kamar tsohun kwarto a kan ya Naeem.
“daga gidan ubanwa kake haka?” ya naeem ya faɗa yana cakumo wuyan rigar shi
cikin rawar murya yace “wallahi daga islamiyya muke Ni da YAZDAN,yazdan dan Allah ba daga can muke ba” ya faɗa yana waigawa bayan shi wayam ya gani babu yazdan
“wallahi daga can muke” ya sake faɗa yana kallon ya naeem,dariya ma maganar tashi ta so ba ya naeem in ba ya ɗauke shi ɗan iska kamar shi ba taya zaice mashi daga islamiyya yake da irin wannan shigar ya yarda,ta ina ma yayi kama da mai zuwa islamiyya.
“saboda ka ɗauke ni shashasha kamar kai ko”
“wallahi ka tambayi yazdan daga can muke mun shiga gida ne muka canza kaya”
“in tambayi abokin cin
mushenka ko,zan kamashi ne shima”
“Allah ba ƙarya muke ba”
“to naji, karanta man abun da aka koya maku yau ko ka kwana kana frog jump”
da ƙyar ya haɗe yawu jin abunda ya naeem ɗin yace,raba ido ya shiga yi kamar wanda yayi ma sarki ƙarya
“oya kai nake saurare” ya naeem ɗin ya faɗa fuska a tsuke yana harɗe hannuwanshi a ƙirji
nan fa ido ya raina fata,ƴan kame kame ya fara,ran ya naeem ne ya fara ɓaci,cakumo kwalar rigar shi yayi yaja shi ƙiiii zuwa waje,yazdan na ganin haka yayi saurin kwanciya cikin motar sai zare ido yake.
ɗaya daga cikin sojojin dake shawagi cikin Estate ɗin ya Naeem ya kira,da sauri sojan ya ƙaraso,ƙato ne bana wasa ba,daga bakin parking space zuwa bakin main entrance ɗin shiga gidan ya Naeem ya nuna ma sojan
“ka sashi frog jump ko sau ɗaya ya tsaya ka kirani”
“ok sir” sojan ya faɗan yana sakin murmushi dama rana irin wanann yake jira saboda yaron ya raina su kwata kwata baya ganin su da ƙima ya raina su.
barin wurin ya Naeem yayi ya nufi motar shi,shiga yayi,key yayi ma motar ya bar wurin.
“amma wallahi second father ya gama dakai FA'IZ,ya rasa wa zai sa ya hukunta ka sai waɗannan ƴan iskan sojojin, tir wallahi” yazdan ya faɗa yana buɗe marfin motar ya fito
“oya start,ko yanzu na kira shi” sojan ya faɗa yana kallon Fa'iz ɗin dake tsaye yana binshi da kallon ƙasƙanci
“an gaya maka tsoron shi nake ji ne?”
“wannan kuma matsalar kace,zaka fara ko sai na kira shi?” sojan ya faɗa yana zaro wayar shi daga Aljihu
“kai dallah malam dakata,ce maka a kayi bazan yi ba ne?”
“to fara idan ba so kake na kira shi ba”
tsaye Fa'iz yayi sai ƴan kalle kalle yake,yana tsoron ya Naeem amma bai son ajinshi ya zuba a gaban securitys ɗin gidan.
yazdan ne ya ƙaraso wajen shima sai layi yake kamar zai faɗi ƙasa,kayan jikinshi iri ɗaya ne dana Fa'iz sai dai shi kanshi kitso ne saɓanin Fa'iz dake da aski
“malam ai sai ka tafi ko” yazdan ɗin ya faɗa yana ma sojan kallon rainin wayau.
“na tafi saboda kai ka sani ko?”sojan ya faɗa ,kallon fa'iz yazdan yayi su ka kwashe da wata ƴar iskar dariya “cewa za kayi na shan fura kake so,ai da kayi magana”
Fa'iz ne ya zura hannu cikin Aljihu ya ciro bandir ɗin dollers ya watsama sojan yana jan hannun yazdan “zo mu tafi kaji”
ran sojan ne yayi matuƙar ɓaci hakan yasa ya fisgo rigar Fa'iz ɗin “kai har ni zaka wulaƙanta?” sojan ya faɗa
“an wulaƙanta ka,dama can kai ba wulaƙantaccen bane,maza ka sauke hannunka saman jiki na ko ranka yayi mummunan ɓaci yanzu” Fa'iz ya faɗa dai dai jiniyar motocin sojoji na tunkaro gidan,da sauri Yazdan ya duƙa ya kwashe kuɗin.
mota biyu ce ta security guard ta nufo parking space ɗin yayin da su ka sako wata baƙar Nissan a tsakiyar su, parking motocin su kayi,da gudu security guard ɗin su ka shiga fitowa suna nufar baƙar Nissan ɗin dake tsakiyar su, ɓack seat ɗin motar ɗaya daga cikin security ya buɗe.
Wata kaykyawar mata ce ta fito cikin shigar lafaya fara mai adon flowers ja,tasha adon zobba da sarƙa na gold, high hills ne a ƙafarta,cikin takun izza ta nufo in da su Fa'iz ɗin su ke ,sojan na ganinta ya saki Fa'iz ɗin yana ɗan rissanawa ya gaisheta,taɓe baki Fa'iz yayi yana faɗin matsiyaci kawai.
murmushi su saki shida yazdan suna ƙarasawa in da matar take, hugging ɗin su tayi itama fuskarta ɗauke da murmushi,raba jikinta tayi da nasu tana faɗin “ 5 and 6 lafiya na ganku tsaye nan,mike faruwa??”
kallon sojan dake tsaye yazdan yayi “wannan matsiycin ne ya Naeem wai yasa yasa Fa'iz tsallan kwaɗo” kallon sojan matar tayi “wai haka ne?”
“eh ranki ya daɗe” sojan ya bata amsa,dubanta ta kai ga Fa'iz
“laifin mi kayi mashi yasa a hukuntaka?”
“momy babu abunda nayi mashi,kawai kin san ya tsaneni ne” girgiza kai matar tayi
“babu yanda za'ayi Naeem yasa a hukuntaka haka nan Fa'iz dole a kwai abun da kayi mashi,jeka kawai wajen aikin ka” ta faɗa tana kallon sojan
“to ranki ya daɗe” sojan ya faɗa yana barin wajen,bai so Hajiya ta zo ba yaso yau ya koyama Fa'iz hankali amma idan ba yau ai akwai gobe.
cikin gidan su ka nufa ita da su Fa'iz ɗin securitys ɗin ta da PA ɗin ta har sun biyo su ta dakatar dasu,ciki su ka shiga su yazdan sai zuba mata ƙarya su ke wai sunyi broke gashi kwana biyu dady bai basu ko sisi ga motar su babu mai a ƙasa suke takawa zuwa school,murmushi kawai tayi tana girgiza kai ta san ƙarya su ke mata,hannu ta zura a jakar ta ciro bandir ɗin ƴan dubu dubu har guda shidda ta basu kowa uku uku,godiya su ka shiga zuba mata kamar tsaffin maroƙa.
A main Parlor su ka rabu ta nufi part ɗin mom su kuma su ka nufi part ɗin mamy.
tun daga first parlorn mamy Fa'iz ya shiga ƙwala mata kira
“mamy! mamy!! mamy!!!,wai ba kowa ne a gidan nake magana anyi man banza??” masu aikin gidan najin maganar shi su ka nemi wajen ɓuya dan sun san muddin ya gansu sun shiga uku baijin kunyar taɓa jikin su a gaban kowa ko da kuwa mahaifiyar shi ce .
kitchen ɗin part ɗin ya fara leƙawa ganin babu kowa ne yasa shi jinjina kai yana faɗin “ƙana nan ƴan iska basa nan kenan” ya faɗa yana nufar ƙofar bedroom ɗin mamy.
A bakin ƙofa yaci karo da mamy doguwar rigar less ce a jikinta kanta babu ɗan kwali gashin Attachment ɗin ta har gadon bayanta kamar dai kullum,daga sama har ƙasa ta shiga ƙare mashi kallon kafin ta sauke idonta kan fuskarshi da sawun hannun ya Naeem ya fito raɗau.
“mamy wai ina ki ka shige ne sai ƙwala maki kira nake?” ya faɗa yana layi kamar zai faɗo mata,saboda tsaɓar shaye shaye ko bai sha komai ba baya iya tsayuwa dai dai sai ka ganshi yana layi
“kai Ni da Allah karka faɗo man a ka,daga ina kake haka?”
“daga yawo”ya bata amsa a gadarance
“yawon iskanci ko, a can ma ka samu wani ya ɗauke ka da mari ko?,wallahi Fa'iz ka shiga hankalinka dani,kai kullum burinka kaja man abun zagi ko dan ubanka”
shafa kumatun shi yayi “nifa ba abun zagin da nake ja maki,kuma wannan sawun marin da ki ka gani Naeem ne ya mare ni dan kawai na bigeshi ban gani ba”
“mari fa kace, wai tsayama wane Naeem ɗin??”
“akwai wani Naeem ɗin ne banda wanda ki ka sani”
“ya mareka dan kawai ka buge shi?”
“eh” ya bata amsa
“yana cikin gidan ko ya fita”
“ya fita” ya bata amsa
“idan ya fita ai uwar shi na nan” mamy ta faɗa tana damƙar hannun Fa'iz ɗin ta ja shi zuwa part ɗin mom,dan suyi saurin isa ta corridor da zai sadaka da duk wani part dake second floor tabi,cikin ƙan ƙanin lokaci su ka iso part ɗin mom Fa'iz sai faɗi yake ta sake shi amma ina...
_*Ep 15_16*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
______________________________
A saman sofa suka samu mom da matar data shigo,fizge hannunshi Fa'iz yayi, babu sallama babu Nocking mamy ta hau surfa masifa
“wallahi bazata saɓu ba bindiga a ruwa,bazai yiwu ko wane ɗan iska yariƙa dakar man yaro ba ehe” kusan a tare mom da matar data shigo su ka kai duban su ga mamy dake fama sirfa masifa, Yumnah da gudu ta fito daga ɗakin mom.
“naga dai iskanci babu wanda baiyin shi,Allah na tuba akwai wanda akafi sani da iskanci sama da soja,wane irin iskanci ne nasu Bama gani a gidanan, ko kuwa wanda ke matse ƴaƴan mutane a office da sunan aiki ne ba ɗan iska ba, ko wanda ya haiƙe ma tsarar haihuwar shi da ƙananun shekaru ya kuma wanke ƙafa ya koma can cikin nasara masu jan kunne dangi sheɗan ne ba ɗan iska ba, ko mai yawan mashaya duk daren Allah ne ba ɗan iska ba!!???”
daga mom har matar data shigo zuba mata ido su kayi kawai suna kallonta kamar wata mai taɓin hankali.
“to wallahi bazan yarda ba tunda ba wani yasha man wahalar haihuwa ba ehe” clapping hand taji anyi daga bayanta.
Da sauri gaba ɗayan su ka kai duban su ga dady dake tsaye can sama tun ɗazu ya dafa handrail,tunda mamy ta shigo yake tsaye yana kallonta,wani irin mummunan faɗuwa gaban mamy ya shiga yi duk a tunaninta baya gidan.
parlorn dady ya nufo yana faɗin “da kyau uwar ɗa,da kyau wacce ta iya haihuwar ɗan kirki” ya faɗa yana ƙarasowa in da suke.
Fa'iz shan jinin jikinshi yayi ganin irin kallon da dady ke mashi,yana ƙarasowa in da yake ya ɗauke shi da lafiyayyun maruka har sau biyu,da sauri ya dafe kuncin shi.
Mamy gabanta ne ya faɗi,nan ta shiga ƴan kame kame da nufin ba dadyn haƙuri,wata mahaukaciyar tsawa ya daka mata wacce ba ita da yayi mawa ba hatta su mom sai da ƴan hanjin cikin su suka kaɗa “yanzu ni na mareshi ko zaki rama mashi??”
Ya faɗa yana sake saukema Fa'iz ɗin wani lafiyayyan marin “haba janar taya za kaita dukan yaron haka,ba fa shi yayi maka laifi ba”
“na sake marin shi dan na gwada maki iskancin soja kamar yanda ki ka faɗa”
dadyn ya faɗa a karo na uku yana sake ɗauke fa'iz ɗin da wani marin har sai da ya saki fitsari a wando, yumnah bata san sanda ta fashe da dariya ba, da sauri tasa hannu ta toshe bakinta gudun kar wani yajita.
“dan Allah janar kayi haƙuri, wallahi ba haka nake nufi ba”
“haka ki ke nufi mana,ai gwara na gwada maki iskancin sojan”
“dan Allah dady kayi haƙuri ba dan ni ba” fa'iz ɗin ya faɗa hawaye na zobo mashi shar
“yiman shiru ko nayi ƙasa ƙasa da kai a wurin nan shashasha” da sauri fa'iz ɗin yasa hannu yan kama bakin shi, kallo mamy dady yayi
“Mabaruka!!!” dady ya kira sunanta da kakkausar murya,jiki na ɓari tace
“Na'am”
“wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe da ƙafarki zata sake takowa zuwa ɓangaren zulaihart da sunan tujara ko rashin mutunci, Naeem yaya yake ga Fa'iz ya isa ya hukuntashi akan kowane laifi da yayi,daga yau idan ki ka sake tada jijiyoyin wuya akan Naeem ko wani a cikin ƴaƴana ya hukunta ɗanki, ina mai tabbatar maki zaki gamu da fushina wanda hakan bazai taɓa maki daɗi ba kinji na faɗa maki”
“naji in sha Allah hakan bazata sake faruwa ba” mamy ta faɗa kamar da gaske,hanyar fita dady ya nuna mata ita da Fa'iz ɗin
“maza kija ɗanki ki ba mutane wuri”
kama hannun fa'iz ɗin tayi sumi sumi su ka fice
kallon dady matar data shigo tayi “ina wuni ya Tahir, na sameku lafiya?”
“lafiya lau Salima ya mutanen gidan, ina ki ka baro man ƙanina” murmushi matar ta saki tana faɗin “ yana can yana fama da jama'a”
“ai dole ne, Allah dai yasa a gama lafiya” dady ya faɗa
“Ameen ya Allah”
“ki gaishe man da shi” dadyn ya faɗa yana nufar part ɗinshi
“zaiji in sha Allah” matar ta faɗa tana kai dubanta ga mom
“ba mu gisaba, na same ku lafiya?”
“lafiya lau hajiya salima, ya kuma fama da jama'a”
“lafiya lau Alhmdllh,ashe kuma abunda ya faru da Asma'u kenan, to Allah ya kyauta gaba”
“Ameen ya Allah” mom ta faɗa
“da tare zamu zo da Kainart bata jin daɗi ne shiyyasa bamu zo tare ba amma tana maki jaje”
“Ayya Allah sarki, ina amsawa Allah ya bata lafiya”
“Ameen summa Ameen”
ƙarasowa yumnah tayi cikin parlor
“momy shine baki zo man da su Ammar ba?”
“suna school ne yumnah”
“ke ki ka ma biye mata idan tana son ganin su ai ta san in da zata same su”
“ai kuwa dai, dan tunda yallaɓai yaci zaɓe ina jin zuwan yumnah Villa sau ɗaya shima bata wani jimaba ta dawo”
ɓata fuska yumnah tayi “school bata bari na saketa, kuma dokokin gidan gwamnatin ne momy sunyi yawa”
“kaji ja'ira banza lokacin da ku kuna gidan gwamnatin ai ba suyi maki yawa dokokin ba sai yanzu ko, kawai baki son zumunci”
“ba haka bane momy”
“to yaya ne?”
“ina nan zan zo kafin muyi resuming school”
“ina nan ina saurare Allah ya kawo ki lafiya”
“Ameen” tashi matar tayi tana faɗin
“bari na shiga ɓangaren mabaruka mu gaisa”
“to nagode Allah ya bar zumunci, a gaishe man da Kainart ɗin”
“za taji in sha Allah”
“momy sai na zo” yumnah ta faɗa
“Allah ya kawo ki lafiya” da Ameen ta amsa, har main parlor mom ta rakata, part ɗin mamy hajiya salima ta nufa.
Mamy a lokacin da su ka fito daga part ɗin mom, fiszge hannunshi yayi daga riƙon da tayi mashi
“mamy ai ga irinta nan sai da nace ki ƙyale ni gashi nan yanzu kin ja man shan maruka, na san yanzu hankalin ki ya kwanta?”
“wallahi Allah ne ya ceceta da ace janar baya gida yau data gane kurenta”
taɓe fa'iz yayi “ kullum haka ki ke cewa,kin taɓa ɗaukar mataki a kan mom ɗin ne ko da sau ɗaya, wallahi mamy ina guje maki randa dady zai shuka maki rashin mutunci saboda matarshi”
“wane shi, ya dai shuka mata rashin mutunci”
“ai yanzu naga faɗan da yayi maki ita yayi mawa,wallahi mamy ki rage shige mata wallahi ko ƴaƴanta ba raga maki za suyi ba, ki bar ganin kowa ya zuba maki ido a gidanan kamar ana tsoronki, wallahi lokacin biye maki ne basu dashi amma duk randa ki ka kaisu bango abun bazaiyi kyauba”
“faɗa mata gaskiya fa'iz kullum abunda nake so ta gane kenan amma taƙi, wallahi mamy wannan abun da ki ke ida sirema dady ki ke, dan zubarma kanki da mutunci ki ke a gaban kowa muma kina ja mana” Fa'iza ta faɗa wacce fitowarta kenan daga bedroom ɗin ta
baki mamy ta saki ta rasa har yaushe tayi lalacewar da Fa'iz da Fa'iza su ka rainata irin haka “ni ku ke faɗa ma haka dan uwarku?”
“gaskiya ce kuma daga ƙinta sai ɓata, kai yazdan zo mu tafi muje kawai restaurant muci abincin a can” Fa'iz ya faɗa yana jan hannun yazdan su ka fice, Fa'iza ma shigewa tayi ɗakin ta da kallo kawai mamy ta bisu.
duk wannan hargagin da take tana yi ne saboda su amma basa gani
“Allah ya wadaran naka ya lalace” ta faɗa tana nufar ɗaya daga cikin sofas ɗin parlorn ta zauna, masu Aiki dake laɓe suna sauraron abun da ke faruwa ban da Allah ya ƙara babu abun da su ke.
hajiya salima ta shigo parlorn bakinta ɗuke da sallama, da sauri mamy ta kai dubanta gareta,tashi tayi ta nufeta fuskarta ɗauke da murmushi, hugging ɗin juna su kayi.
“saukar yushe?” mamy ta faɗa tana jan hannunta su ka nufi sofa su ka zauna
“dama yaushe zaki ganni kinje kina tsula tsiyarki” mom salima ta faɗa
“wai da ke ce a parlorn, ni inama na lura da wacece ido a rufe suke ne raina ya ɓaci”
“ai naga alama, wai dama mabaruka har yanzu baki daina hargagi da zulaihart irin wannan ba?”
“yaushe kuwa zan daina, ai idan kinga na daina to na sake sender ta ƙasar su kamar shekarun baya” kallon baki da hankali matar ta shiga binta dashi.
“ke har yanzu kina tunanin zaki iya raba Tahir da zulaihart ne, to wallahi idan ma bacci ki ke tun wuri ki farka kar kije garin tsige igiyar Aurenta ke ki tsige taki a banza”
“ban gane ba, mi kike nufi”
“ko wannan matakin daya ɗauka yau akan fa'iz a gabanki saboda zagin ƴaƴanta da ki ka yi ya isa yasa kiyi hankali kisan cewa da da yanzu ba ɗaya bane”
“ni wallahi Hajiya salima kin barni a cikin duhu,dan ban gane inda maganar ki ta dosa ba”
“ kin manta bala'in da ki ka shiga lokacin baya?, da ba dan mama Ameena ba da yanzu kina wani gidan ba wannan ba, idan zaki canza salon kishin ki ki canza idan kuma haka ki ke ganin ya fiye maki tam, shi dai yaƙi ɗan zamba ne”
jinjina kai mamy ta shiga yi alamar gamsuwa da maganar hajiya salima “shikenan naji zanyi ƙoƙarin ganin na sauya”
“hakan dai shi ya fi, ni na shigo ko gaisawa ba muyi ba,kin wuni lafiya?”
“lafiya lau, ya yau ban ganki da tawagarki ba?”
“ki bari kawai ni na hana su biyo ni nace suyi zaman su jaje zanje ba ɗabbaka siyasa ba, ko security cewa nayi su jira ni a waje”
“kina sha'aninki ta wajen Ahmad, ai wallahi ni lokacin da janar na kan kujerar shugaban ƙasa duk in da zani da tawagata nake zuwa ai shine girman”
“ban manta ba” matar ta faɗa, mai aiki mamy ta ƙwalama kira dan ta kawo ma hajiya salima ruwa da lemu.
“ai barshi kawai mabaruka nasha a part ɗin zulaihart tafiya ma zanyi”
“nifa kinga abun da ke haɗani dake kenan,dan mi zaki sha ruwa a wajenta”
“ni dai yanzu idan na sake dawowa na sha, amma yanzu kam gaba nayi”
“shikenan Allah ya nu na man lokacin da zaki sake dawowar” da Ameen hajiya salima ta amsa, a tare su ka miƙe ita da mamy.
har parking space mamy ta rakata, sai da taga tashin motocin ta tukun ta koma ciki.
*ASO VILLA*
Kusan a tare motocinta da motar da aka ɗauko su Ammar daga school ta shigo.
A bakin main entrance ɗin shiga part ɗin su motocin su kayi parking, drivern da yayi driving ɗin su ne ya fito ya buɗe masu,da gudu su ka fito suna nufar motar kakar tasu,suna isowa security na buɗe mata ƙofa ta fito.
da gudu suka faɗa jikinta “oyoyo granny,shine ki ka fita bama nan ko” murmushi ta saki tana shafa fuskokin su
“ayi man afuwa gidan big daddy naje”
shagwaɓe fuska su kayi “amma granny kin san cewa muma muna son zuwa shine ki ka tafi bama nan”
“ayi man Afuwa,ai gobe za ku haɗu dashi a gidan Abbah” ta faɗa tana jan hannunsu suka nufi cikin gidan
“ai gidan Abbah ba gidan shi bane,mu gidan shi muke son zuwa”
“karku damu idan kuna son zuwa sai nasa dadyn ku ya kaiku gobe da kun dawo daga school,kunga sai kuyi ma Aunty Yumnah weekend ko” tsallan murna su kayi
“yeee har gidan papa ma sai muje”
“na san Aunty Yumnah zata kai ku ko ina,amma fa sai dady da momynku sun amince”
ɓata fuska su kayi “dady bazai amince ba mu dai kawai kice ya kaimu”
“to naji muje na duba jikin momyn ku” ɗan zaro ido su kayi suna kallonta
“mi ya samu momy?”
“bata jin daɗi ne” Hajiya Salima ta faɗa dai dai tana tura ƙofar ɗakin kainart ɗin,wayam su ka gani bata ciki har ƙofar toilet sai da Aman yayi nocking amma bata ciki, Ammar ne yace kila tana bedroom ɗin su ,ficewa su kayi zuwa bedroom ɗin na su.
A kwance su ka sameta saman bed ɗin su Aman, idanunta a rufe kamar mai bacci,gaba ɗaya ta rasa mike mata daɗi a duniyar nan,har ta ƙagara ya tattara kayan shi ya koma Lagos.
da gudu su ka ƙarasa in da take,faɗawa su kayi saman jikinta
“momy mun dawo” a firgice ta miƙe zaune dan ba ƙaramin tsoro su ka bata ba, ajiyar zuciya ta sauke ganin su.
“amma yaran nan anyi ja'iran yara,ba kuga bata jin daɗi ba shine zaku faɗa mata haka” Hajiya Salima ta faɗa yayin da ta ƙarasowa bakin bed ɗin.
da sauri kainart ɗin taja gyalen abayarta ta rufe gefe da gafen fuskarta tana kai dubanta ga Hajiya Salima
“momy har kin dawo?”
“na dawo kainart,ya jikin naki?”
“Alhmdllh,ya su mom ɗin?”
“suna lafiya,tana ma gaishe dake”
“ina amsawa”
“mi Dr yace yana damunki?”
“zazzaɓi ne kawai”
“to Allah ya sawaƙa” da Ameen kainart ɗin ta amsa,tashi hajiya Salima tayi
“ku kuzo ko muje can sarah ta shirya ku,kunga momy ba lafiya”
da gudu su ka sauka daga saman bed ɗin suna nufar ƙofar fita,bin bayan su hajiya salima tayi tana sakin murmushi, murmushi itama kainart ɗin ke saki har su ka fice daga ɗakin.
*Uncle Hashim's House*😡
A zaune su ke saman dinning chairs a katafaren dinning room ɗin gidan,baka jin ƙarar komai sai na spoon da plate ɗin da su ke cin abincin.
gaba ɗaya a takure take saboda kafetan da ido da dadynta yayi,hakan ya hanata sukuni,momy da balqis sai cin abincin su suke hankali kwance dan basu san abun da ke faruwa ba.
a hankali ta ajiye spoon ɗin hannunta tana miƙewa da nufin barin wajen,table ɗin ya buga da ƙarfi wanda yayi sanadiyar dawo da hankalin momy da balqis kan su.
“koma ki zauna” ya faɗa da kakkausar murya yana nuna mata chair ɗin data tashi,da ɗan rawa rawar jiki ta nufi chair ɗin ta zauna,duƙar da kanta tayi ƙasa gabanta na faɗuwa.
“barrister lafiya?” momy ta faɗa tana ajiye spoon ɗin dake hannunta,maida kanshi yayi kan abincin da yake ci ba tare da ya tanka mata ba kamar ma ba dashi take magana ba.
sanin bazai tanka mata bane ya sata kallon laatifa,da ido tayi mata alama da lafiya, girgiza mata kai laatifa tayi alamar itama bata sani ba hawaye na taruwa a idonta.
“Allah ya kyauta” shine kawai abun da momy tace tana cigaba da cin abincinta,sun kai tsawan 20 mins kafin kamar daga sama su kaji ya kira suna balqis murya a kausashe.
da sauri balqis ɗin ta ajiye spoon ɗin dake hannunta
“na'am dady”
“last day mi ya kai ki court??” ya faɗa babu alamun wasa a fuskar shi,kamar saukar ardu haka laatifa taji tambayar duk da ba ita yayi mawa ba,tayi tunanin ya bar maganar tun lokacin ashe ba haka ba.
gabanta na faɗuwa ta kai dubanta ga balqis tana mata alama da ido data rufa mata asiri.
“naje saboda Aunty laatifa ne”
wani mugun kallo yayima laatifa
“saboda mi?”
“bata jin daɗi ne shine nace ta zauna gida ni na wakilceta” jinjina kai barrister yayi.
“mi na faɗa maki laatifa??” ya faɗa yana tsareta da idanu
“dady ba fa ita ta tura ni ba, da kaina nace zanje”
“tambayar ki nayi?” girgiza mashi kai balqis tayi
“dan Allah kayi haƙuri dady wallahi bani nace taje ba”laatifa ta faɗa a hankali
“laatifa kin raina maganata ko,bance maki idan za kiyi yawan iskancinki ki daina sa ƴata a ciki ba”
kamar zata fashe da kuka tace “kace dady”
“wato saboda ban isa ba shine ki ka turata cikin ƙattin da ki ka saba yawo da su ko?”
“kayi haƙuri dady bazan sake ba”
rai a ɓace momy tace“wai lafiyar ka kuwa barrister,itama ba ƴar ka bace ,mi yasa k..?” bata ƙarasa ba yayi saurin daka mata tsawa yana ɗaga mata hannu,hakan yasa tayi shiru tana kallon shi cike da mamaki.
“wannan ya zama rana ta ƙarshe da zan sake maki warning akan ƴata,duk yawan banzan da za kiyi kiyishi ke kaɗai amma banda ƴata kinji na faɗa maki”
“in sha Allah hakan bazata sake faruwa” laatifa ta faɗa hawayen da su ka taru a idonta na zubowa.
tashi yayi ya nufi bedroom ɗin shi,da wani kallo momy ta rakashi,tashi laatifa tayi ta nufi bedroom ɗinta yayin da take fashewa da wani matsanancin kuka, balqis ma kuka ta fashe da shi sun rasa yaushe dadyn su zai rage wannan ƙiyayyar da yake ma laatifa.
bayan laatifa momy tabi hakama balqis,a kwance su ka sameta ta kifa kanta saman matress tana fitar da wani kalar kuka mai ban tausayi,zama momy tayi kusa da ita hannunta ta ɗaura saman bayan laatifa,a hankali take shafa bayanta.
“momy wai mi yasa dady ya tsaneni,mi yasa baya sona kamar yanda yake son balqis, nima ba ƴarshi bace ko ina da wani uban wanda ni ban san shi,momy dan Allah idan ba shine mahaifina ba ki faɗa man???”
saurin toshe mata baki momy tayi da tafin hannunta “kul laatifa kar na sake jin bakin ki ya furta wannan kalaman,ki daina tunanin baya sonki ne, mahaifinki na sonki fiye ma da yanda yake son balqis,yana yi maki haka ne saboda ya kasa mantawa da abun da ya faru shekarun baya,ki dage da Adu'a wata rana sai labari”
“momy mi yasa dady har yanzu ya kasa gane cewa ba abun da yake zargi ba ne,momy har sau nawa zan faɗa mashi babu abunda ya faru dani kawai taimako na SAM yayi”
“saboda shi mahaifinki ne abun na damun shi shiyyasa ya kasa mantawa,kiyi haƙuri kinji in sha Allah wata rana gaskiya za tayi halin ta dadyn ki zai gane baki da laifi”
“momy amma ke mi yasa ki ka fahimce ni,dady baya sona ne kawai”
ta kai ƙarshen maganar tana sake fashewa da wani matsanancin kukan.
momy bata san lokacin da itama hawaye su ka wanke fuskarta ba, balqis ma ƙarfin kukan da take ne ya ƙaru,gaba ɗayan su rasa me lallashin wani a kayi,sai da su kayi mai isar su tukun momy ta shiga lallashin su,da ƙyar ta samu su kayi shiru,tashi laatifa tayi ta nufi toilet.
tashi momy tayi ta fice zuwa ɗakin barrister, a tsaye ta sameshi gaban wardrobe ɗin shi fitowarshi kenan daga wanka ƙugunshi ɗaure da towel.
“kaji tsoron Allah barrister,ka sani wannan aibatatan da kake ba shine mafita ba,itama ƴace a wurin ka kamar balqis,kuma ka sani ɗan Adam bai isa ya tsallake jarabawar da Allah yayi mashi ba,ko da ace abunda kake zargi gaskiya ne, kai ba mahaifinta bane dan mi bazaka ɗauki ƙaddararta hannu bibbiyu ba,amma ace tsawan shekaru ka kasa mantawa da abu,kullum cikin aibatata da nuna mata tsana kake, Allah ma munayi mashi laifi ya haƙura sai kai ne bazaka yafe ma ƴarka ba kan laifin da zargi kawai kake baka da tabbaci, haba barrister ka zama mahaifin ƙwarai mana”
“kin gama?” shine kawai abun da yace,wani ƙululun baƙi ciki ne ya tokare mata maƙoshi wato ma ta gama
“get out from my room” ya faɗa yana nuna mata hanyar fita,rai a ɓace ta juya ta nufi ƙofar fita har ta kama handle ɗin ƙofar sai kuma ta tsaya,rai a ɓace ta juyo tana kallonshi.
“ka sani balqis da laatifa Amana ce Allah ya baka,kuma zai tambayeka akan yanda ka tafiyar da rayuwar su,ka sani muddin baka gyara alaƙarka da ƴarka ba za kayi daka sani ne mara amfani” tana gama faɗa haka ta fice daga ɗakin baki ɗaya,tsaki yaja kawai yana cigaba da abunda ke gaban sa.
shaf shaf ya shirya cikin pajamas ɗin shi white color masu fatsi fatsin baƙi,feshe jikin shi yayi da perfume ɗin shi masu ƙamshi,bed ɗin shi ya haye yayi kwanciyar shi bayan ya kashe light ɗin ɗakin.
wayar dake kan nightstand ya ɗauka,dialing wata number yayi,bugu biyu a kayi picking call ɗin,kara wayar yayi a kunne,in low voice yake waya yanda ko kusa dashi ka tsaya bazaka iya jin abunda yake cewa ba,idan ka shigo ɗakin sai ka rantse da Allah bacci yake.
barrister kenan ko matashin saurayi bazai gwada mashi iya kashe murya idan yana waya ba.
*Big daddy's House*
“ko fa mi za kice sai dai kice amma yau sai kin fita dinning kinyin dinner tare da kowa na gidan nan,na gaji da wanna ƙunshi kan naki da ki ke”
“please Yumnah ki fahimta mana,bana jin yunwa ne ba wai ban son fita ba”
“to naji,muje ni ki raka ni koda ba kici komai ba ai za ki gaisa da mom da dady,kuma zaki rage wanann yawan tunane tunanen da kike”
duk yanda ta so zille ma Yumnah akan ta ƙyaleta Yumnah taƙi bata dama dan dole ta miƙe,hijab ɗinta dake saman bed ɗin ta ɗauka,zurawa tayi a jikinta
“muje to” ta faɗa tana kallon Yumnah
“ko ke fa,amma wannan hijab ɗin da ki ka sa saikace wacce zataje gaban sirikai, dinning fa zamu je ba wani waje ba”
“ni dai haka zanje”
“ai saiki ta tafiya haka”yumnah ta faɗa tana jan hannunta su ka fice.
Mom da dady ka ɗai su ka samu a dinning ɗin, Ishrat na daga tsaye tana serving ɗin su,bakin su ɗauke da sallama su ka ƙarasa cikin dinning room ɗin,zama su kayi saman chairs yayinda su ke gaishe da dady da mom.
murmushi dady yayi yana kai duban shi ga Nainarh,cikin kulawa su ka amsa masu gaisuwar da su kayi dady na faɗin
“ɗiyata kinyi wuyar gani,tun ranar da muka dawo daga wajen mahaifiyar ki ban sake saki a idona ba,ina fatan dai lafiya?”
“lafiya lau dady” Nainarh ta faɗa tana duƙar da kanta ƙasa
“yanzu ma fa da ƙyar na samu ta fito,kullum tana ɗaki daga kuka sai tunani” Yumnah ta faɗa tana kallon Nainarh data sadda kai ƙasa.
“wai haka ɗiyata?” shiru Nainarh tayi tana wasa da gefen hijab ɗinta
“ki dai na sa damuwa a ranki kinji, mahaifiyar ki zata dawo gareki,in sha Allah asirin wanda su ka kashe mahaifinki zai tonu”
“in sha Allah” Nainarh ta faɗa
“bana son kina sa damuwa a ranki kinji ko,ke da ma ki ke da wata mahaifiyar a kusa dake miye na sa damuwa a ranki” dady ya faɗa yana nuna mom da tunda su ka shigo dinning ɗin ta kafe Nainarh da ido ko ƙyaftawa ba tayi dan duk maganar da dady ke yi bata sani ba hankalin ta baya wajen.
“zulaihart!” dady ya kira sunanta,ɗan saurin kallon dadyn tayi
“lafiya ki ka kafe ƴar taki da kallo” murmushi mom ta saki
“wani lokaci sai nake ganin tana man kama da ƴar uwata,sai dai ita bata kai ta kazar kazar ba Nainarh ta cika sanyi” mom ta faɗa tana sake kai dubanta ga Nainarh data sadda kai ta sauraron su.
“nima na jima ina ganin kamaninta da Carol, da ace ban san mahaifiyar ta ba kuma a ce Carol ta taɓa Aure da babu abunda zai hana nace ƴarta ce”
murmushi mom ta saki “nima ina yawan faɗama mahaifiyar ta haka,wani lokacin idan nace haka sai tace dan kawai ina son Nainarh ne yasa nake ganin kamanin su”
“ta iya yiwuwa” dadyn ya faɗa, Yumnah da Nainarh dai na jin su,fa'iza ce ta shigo dinning room ɗin,tsaye tayi tana riƙe ƙugu fuskarta a turɓune
“shine yau aka rasa wanda zai kirani ko?” ta faɗa tana sake tsuke fuska.
“sorry Aunty Fa'iza nayi tunanin a part ɗin mamy za kiyi dinner shiyyasa ban kira ki ba” Yumnah ta faɗa tana ɗan kama kunnenta alamar sorry
“nima ayi man Afuwa na rashin faɗa maki da banyi ba” Ishrat ta faɗa wacce ke serving ɗin Yumnah da Nainarh,ɗaya daga cikin kujerun Fa'iza ta nufa ta zauna.
“ni dama na san ai kun rigada kun gama rainani gidan nan” murmushi kawai dady da mom su ka saki.
gaishe da su dady fa'iza tayi, murmushi dady yayi yana faɗin
“ai da nayi tunanin baki gannu ba”
ɗan murmushi tayi tana sosa ƙeyar ta.
serving ɗin ta itama Ishrat tayi kafin ta bar dinning ɗin,tsit wurin yayi ba wanda ya sake magana.
mom ta fara tashi kafin dady ya miƙe yana kallon Yumnah yace “Autar mom ina fatan baki manta gobe juma'a ba?”
“ban manta da gyaran part ɗin shalelen dady ba,gobe tunda safe zansa a gyara shi”
“good,haka ne son ji,sai da safe ku”
har haɗa baki suke wajen furta good night,jinjina masu kai dadyn yayi yana fice daga dinning room ɗin.
suma basu wani jimaba su ka tashi, Ishrat ta zo tare da su munirat su ka kwashe kayan da su kaci abinci su ka gyara wajen tsaf.
🎀
_*🔥🔥SHIRYAYYIYAR ƘADDARA 🔥🔥💫*_
_*Season one*_
_*FREE*_🔥
*_KING AND QUEEN WRITING CHAMBER_*🤴 👸
𝑄𝑢𝑒𝑒𝑛 𝐾𝑎𝑖𝑛𝑒𝑟𝑡..... ✍💫
𝑇ℎ𝑒 𝑤𝑟𝑖𝑡𝑒𝑟 𝑜𝑓 𝐷𝑜𝑐𝑡𝑜𝑟 𝑆ℎ𝑎𝑧𝑖𝑚 𝑎𝑛𝑑 𝑛𝑜𝑤 𝑠ℎ𝑖𝑟𝑦𝑎𝑦𝑦𝑎𝑟 𝑘𝑎𝑑𝑑𝑎𝑟𝑎
_*Episode 1_2*_
_*Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ma ɗaukakin sarki mai kowa mai komi da ya bani ikwan rubuta wannan littafi.*_
_*Ya ubangiji al'arshe kabani ikwan rubuta abin da zai amfani muslinci da muslmai, ka bani ikwan rubuta abun da zai amfaneni duniya da lahira 🙏*_
❌❌❌❌❌❌❌
_*Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na littafin nan ba ta kowace hanya ba tare da an nemi izni a wurina ba.*_
_*idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi min haƙƙina!*_
_*Wannan labari ƙagegen ne ,sannan ban rubuta shi ba da niyyar muzanta wani ko cin zarafin wani ba, duk wanda ya ga wani abu yayi shige da halayyar shi to arashi ne ba da nufi ba*_.
*A big big hug to Khadija Sabi'u yahaya A.k.a Nainarh kd Nkds*
*special thanks to Ameenatu Muhammad Yakasai A.k.a oum Yasmeen the writer of Binta ƴar jagaliya*
_*Dedicated to my family*_
*@Kainaat1733*
*Wattpad*
_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ_
1:30 am
*Sydney,Australia*
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
______________________________
Can cikin bacci taji ana nocking window ɗakin da su ke,a hankali ta buɗe idanuwanta da su kayi mata nauyi.
sake nocking ɗin window a kayi, gabanta ne ya ɗan faɗi dan duk a tunanin ta a mafarki ne taji nocking ɗin ba gaske ba.
jin an dage da nocking ɗin ne yasa tayi saurin kallon gefanta, baccin shi yake shara abun shi hankali kwance, magidanci ne da a ƙalla zai kai kimanin shekaru 60 a duniya,baƙi ne kyakyawan gaske matar dake gefan shi itama zata kai kima nin shekaru 46 zuwa da 8 a duniya.
fara ce kyakyawa ajin farko, kai tsaye idan ka kalleta ba zaka ce zata kai kimanin wannan shekarun ba.
ɗan bubbuga pillow da yake kwance ta shiga yi tana kiran sunan shi cikin muryar raɗa
“ranka ya daɗe! ranka ya daɗe!!” a ƙalla sai da ta kira sunan shi kusan sau uku ba tare da ya farka ba still ba'a fasa nocking ɗin da ake yi ba.
ƙara sautin kiran sunan shi tayi cikin harshen hausa take faɗin“dan Allah ka tashi, inajin fa babu lafiya yau a ɗakin nan” ko gezau baiyi ba gashi wanda yake nocking yanzu ƙoƙarin buɗe window yake ta ƙarfin tsiya ya shigo.
cikin muryar kuka ta fara haɗa shi da Allah akan ya tashi
“dan Allah yallaɓai ka tashi , babu lafiya”
can cikin baccin shi yaji shashekar kukan ta, firgigit ya faraka, jin dai da gaske kukan take ne yasa shi tashi da sauri yana faɗin“lafiya mi yasa ki ku ka??”
window ta nuna mashi cikin yin ƙasa da murya tace“wani ke ƙoƙarin shigowa ta window” duban shi ya kai ga sliding door dake ɗakin,wacce mutum idan yaje gabanta ko ya buɗe zai iya hangen cikin garin sydney da harabar hotel ɗin.
zuro ƙafar shi yayi daga kan bed ɗin ya sauko wurin window ya nufa, ɗan saurarawa yayi,bugun windowa yaji anyi da ƙarfin gaske can yaji sautin kukan mace cikin harshen turanci tana faɗin“please open the door, help please!”
ɗan ja da baya yayi yana mamakin wacece kuma mi ya kawo ta window ɗakin su duk yawan ɗakunan dake cikin hotel ɗin tarasa in da zata zo sai na su, banda zare ido babu abunda matar dake zaune kan bed take.
ƙara ƙarfin kukan tayi da dukan window tana cigaba da faɗin“please help me,open the door please”
shahada kawai yayi ya nufi window, hannu yasa ya yaye curtain ɗin dake jikin window,matashiyar baturiya ce ya gani tsaye da uban ciki haihuwa yanzu ko anjima,da ƴar madaidaiciyar jaka rataye a kafaɗar ta, a ƙalla zata kai kima nin shekaru 25 a duniya.
fuskar ta sharkaf da hawaye idanunta sunyi jawur hakama hancinta da kumatunta, kyakyawa ce ajin farko tana da manyan idanuwa da tsayayyen hanci har baka sai ɗan ƙaramin baki mai ɗauke da red lips tana da tsayi dai dai misali.
baƙar duguwar riga ce a jikinta, har ƙasa rigar ta kai mata, ta rufe kanta da mayafin rigar.
ganin yayi shiru ya zuba mata idano ne yasa ta sake fashewa da wani kukan tana sake roƙon shi da ya taimake ta.
tasowa matar dake zaune kan bed tayi ta nufo bakin window, kallon baturiyar dake tsaye tayi daga sama har ƙasa.
“yallaɓai mu taimake ta” ta faɗa tana kallon mijin nata dake tsaye.
hannu yasa ya buɗe door, kamar jira take ya buɗe da mugun sauri ta shigo cikin ɗakin kamar zata faɗin,sakin jakar dake rataye a kafaɗar ta tayi, da sauri matar ta taro ta tana faɗin ki kula cikin harshen turanci.
kamata tayi har zuwa cikin ɗakin, jakar data yarda mutumin ya ɗauka yana bin bayan su,sofa da ke ɗakin su ka nufa, zaunar da ita tayi, a gefanta ya ajiye mata jakar, nufar wani ɗan table dake ɗauke da robar ruwa da cup matar tayi, ɗaukowa tayi ta dawo wurin sofar.
tsiyaya mata ruwan tayi a cup ta miƙa mata, hannunta har rawa yake wurin amsar cup ɗin, kallon mijinta dake tsaye matar tayi wani irin tausayin baturiya ne ya kamasu daga gani ba ƙaramar wahala tasha ba.
da sauri ta dafe ƙaton cikinta tana ɗan rintse ido da fatin “Auch, oh my god”
ƙoƙarin miƙewa take saboda wani ciwan mara daya taso mata lokaci guda, da sauri matar ta ajiye cup ɗin hannunta sannu ta shiga yi mata tana sa hannu ta taro ta.
ƙara baturiya ta fasa tana faɗin matar ta kaita toilet,matar kamar zata fashe da ku ka ta kalli mijinta tana faɗin“haihuwa ce za tayi”ɗan zaro ido yayi
“ya za muyi kenan?”
“nima ban sani ba, da ace a gida muke ina da komai da zamu buƙata”
“haka ne, yanzu babu wani taimako da za ki iya yi mata?”
“akwai sai dai su kasan basa son haihuwa a gida sai a hospital”
“yanzu tana a wannan halin ina ruwanta da inda zata haihu, tunda dai Allah yasa ke dr ce kawai kiyi mata abun da ya dace”
“shikenan”matar ta faɗa,barin wurin mijin matar yayi ya koma can nesa da su sosai.
tai makon gaggawa matar ta shiga bata, banda kuka da kiran sunan mahaifiyar ta babu abun da baturiyar nan ke yi.
sannu matar ke mata tana bata haƙuri, ba ƙaramar azaba baturiyar ke sha ba matar na iya bakin ƙoƙarin ta ganin ta taimake ta.
mijinta ma dake can nesa da su adu'a yake tayi Allah ya sauƙeta lafiya.
wahala sosai take sha gashi har yanzu haihuwar sai a hankali, barin wurinta matar tayi ta nufi mijinta fuskarta duk tayi jagajaga da hawaye
“yallaɓai ina tunanin dole fa sai mun kaita hospital”
“saboda mi?”
“nayi iya yanda zanyi amma haihuwar sai tazo sai ta koma”
“dr yanzu ya zamuyi?, kinga nan ba ƙasarmu bace fita da ita daga cikin hotel ɗin nan haɗari ne, gashi daga gani yana yin data shigo wani ne ya biyota, kuma na san wanda ke binta duk in da yake yana nan cikin hotel ɗin”
“to yanzu ya za'ayi kenan?”
“shine nima ban sani ba”
“ko zaka nemi alfarma wurin dr mark sai yazo da nurses su dubata”
“anya dr kina ganin barin wani ya san halin da ake ciki ba zai jaza matsala ba kinga nan ba ƙasar mu bace kada daga timako mu jefa rayuwar mu cikin haɗari”
“to yallaɓai ya ka ke so muyi?”
ko rufe baki matar ba tayiba kukan jariri ya cika ɗakin da mugun sauri ta juya ta koma can cikin ɗakin, a durƙushe ta samu baturiyar nan riƙe da jaririya a hannu ga wata sabuwar naƙuda da ta taso mata.
da sauri matar ta nufeta tana amsar jaririyar dake hannunta, towel ta ɗauka ta lulluɓe jikin jaririyar ta kwantar da ita saman sofa a hankali,gaban baturiyar ta dawo tana mata sannu haɗi da bata taimakon daya dace,ko minti ɗaya ba'ayi ba ta sake santolo wata jaririyar fara ƙar da ita kyakyawar gaske kamar wacce ta fara haihuwa sai dai wannan bata numfashi kwata kwata babu alamun rai a tattare da ita.
da sauri matar ta karɓi yarinyar ta shiga jujjuyata,kusa da ƴar uwarta daketa tsala kuka ta matsa ta kwantar da ita,ɗaukar mai ran tayi ta shiga goge mata jikinta bayan ta gama ta gogema ɗayar jikin itama,baturiyar tana daga in da take durƙushe ta kafe kyawawan yaran nata da kallo fahimtar ɗaya bata numfashi ne yasa ta tashi a hankali ta nufi jariran,shafa fuskar yaran ta shigayi can kuma ta fashe da kuka tana tambayar matar bata da rai ne.
jinjina mata kai matar tayi hawaye na bin kumatunta dan ba ƙaramin tausayi baturiyar ta bata ba,kuka sosai baturiyar ta fashe dashi matar na lallashinta har ta samu tayi shiru.
ɗaya bayan ɗaya matar ta shiga da yaran toilet ta wanke su a cikin jakar da mahaifiyar tasu data shigo da ita kayan jarirai ne harda su teddys,wasu riga da wando na saƙa farare ta sama yarinyar,gawar kuwa lulluɓeta tayi da farin towel ta kwantar saman sofa kusa da ƴar uwarta,taimaka ma mahaifiyar tasu tayi zuwa toilet danta gyara jikinta,ruwa ta haɗa mata da duk wani abu da zata buƙata tukun ta fice daga toilet ɗin ta bata wuri,cikin ɗakin ta dawo ta gyara wurin kamar wani abu bai faru ba sannan ta nufi wurin jariran,ɗaukar jaririyar daketa faman kuka tayi ta nufi mijinta ta miƙa mashi, hannun biyu yasa ya amshi jaririyar
“masha Allah, Allah ya rayata” ya faɗa
“Ameen,ƴaƴa biyu ne sai dai ɗayar ba ta zo da rai ba”
“Allahu Akbar, Allah ya raya mata wannan ɗin”
“Ameen”
“mahaifiyar ta su fa?”
“Alhmdllh ta haihu,tana toilet ma yanzu haka”ta bashi amsa
“masha Allah, amma ya ki ke ganin za muyi da ita duba da yanda ta shigo gashi kuma time ɗin tafiyar mu na ƙurewa?”
“yanzu dai mu bari ta fito na sake duba lafiyarta sannan sai mu tambayeta daga ina take”
“shikenan ba damuwa” amsar jaririyar tayi daga hannunshi
Zama su kayi kan sofar dake kusa da su
“yallaɓai yarinyar kyakyawa ce ina ma ace ni na haifeta”
murmushi yayi yana kallon fuskar matar ta shi“da kuwa munyi farin cikin da bamu taɓa irin sa a ruyuwar mu ba”
“da sai mun tara shagali irin wanda ba'a taɓayi ba a duniya ko da a finafinai da littafi”matar ta faɗa tana sakin murmushi da shafa kumatun jaririyar, shima mijin shafa kumatun yarinyar yayi da fara'a a fuskar shi.
“yallaɓai dan ma ba kaga ɗayar ba,kyakyawa ce itama ta ƙarshe da ka ganta kaga ƴar uwarta sai dai tafi kama da mahaifiyar su kamar an tsaga kara”
“zan so kuwa na ganta”
sun jima a nan zaune suna jiran fitowar mahaifiyar jaririyan daga toilet amma su kaji shiru har lokacin bata fito ba
“yallaɓai anya lafiya?, naji shirun nata yayi yawa”
“haka ne gashi time na ƙure ma na, ko za kije ki dubata?” tashi matar tayi ta miƙa masa jaririyar da tayi shiru tayi lamo a hannunta.
tun kafin ta ƙarasa bakin ƙofar toilet ɗin gabanta yayi wani mugun faɗi, fara fahimtar a kwai abun da ke shirin faruwa ko ma ya faru tayi, ba ta sake tabbatar da hakan ba sai da taga babu gawar jaririyar data bari,da ƙarfi ta ƙwala ma mijinta kira
“yallaɓai!yallaɓai!!” ta kira sunan shi har sau biyu, a hanzarce ya iso in da take , sofa ta nuna mashi da sauri ya kai dubansa zuwaga sofa amma sai yaga ba komai
“mi ya faru ne?”
“babu gawar jaririyar” ta faɗa cikin rawar murya tana zare ido
“to ina mahaifiyar tasu?”
“tana toilet”
“to kila ita ta ɗauketa”
“anya kuwa?” ta faɗa tana zaro ido
“fara dubata ki gani tukun” a hankali tayi nocking ƙofar toilet ɗin shiru taji, sake nocking tayi nan ma shiru taji babu almun mutum,deciding tayi ta tura ƙofar toilet ɗin ta shiga kawai, tura ƙofar tayi ta shiga wayam taga toilet ɗin ba kowa kamar ma ba'ayi amfani da shi ba, gabanta ne yayi wani mummunan faɗuwa da sauri ta fice tana ambaton Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.
“lafiya?” mijin ya tambaya da alum ruɗu
“ba kowa,bata ciki” ta bashi amsa bakinta na rawa
“ya salam, to ina ta tafi?”
“nima ban sani ba” dube dube su ka shiga yi cikin ɗakin wai ko ta shiga wani wuri har bakin window data shigo mijin matar ya nufa yana leƙa wajen ko ta nan ta fita amma bai ga alamun ta nan ta fita ba, hankali su ne yayi ƙololuwar tashi.
“yallaɓai anya matar nan ba aljana bace?”
“wane irin aljana ana zaman lafiya”
“idan ba aljana ba, taya za ace ta fita bamu sani ba kuma da yarinya a hannunta”
“koma dai minene zama nan bai kama mu ba,mu haɗa kayan mu kawai mu tafi Airport dama lokacin tafiyar ya gabato dan hankalina bai kwanta da wannan lamarin ba”
mijin ya faɗa yana kwantar da jaririyar dake hannun shi saman sofa sai a sannan ya lura da ƴar guntuwar takarda da wani ɗan madaidaicin teddy bear a jikinshi an rubuta mommy a kan sofa.
da sauri ya ɗauki takardar ya duba rubutu ne a jikin takardar cikin harshen turanci, fara karantawa yayi da sauri matar ta nufo shi ganin pepar a hannunshi kusan a tare su ka gama karanta abun da ke cikin takardar, da sauri su ka kalli juna
“anya yallaɓai wannan lamarin akwai tsoratar wa, taya uwa za tayi kyauta da ƴarta daga haihuwarta ba tare da ta ko san wanda ta ba”
“gaskiya abun akwai ban tsoro sai dai yanzu abun da za'ayi kawai mu tafi Airport ɗin idan ya so ma kirata tunda ga number waya nan ta rubuta”
“to shikenan” matar ta faɗa tana cigaba da haɗa masu kayan su cikin ɗan madaidaicin trolly, tana gama haɗa kayan ta ɗauki teddy ta saka cikin bag ɗinta sannan ta ɗauko mayafi mai ɗan girma cikin kayanta ta lulluɓe jaririyar a kafaɗa ta saɓa jaririyar mijinta kuma yaja trollyn su ka fice daga ɗakin....
*Abuja_Nigeria*
_*COURT*_
Mutanene ta ko ina a harabar court ɗin ƴan jaridu ne ƴan gidan radio da television , ƴan social media gasu nan birjik a harabar kowa burinshi ace shine na farko wurin ɗaukar rahoton yanda shari'ar zata kaya.
mutane dake kai kawo a harabar da wanda suke zaune sai faɗin albarkacin bakin su suke wasu na iƙirarin idan har hukuncin koto baiyi masu yanda suke so ba to babu abun da zai hanasu ɗaukar doka a hannun su sai dai duk abun da zai biyo baya ya biyo.
mutanen dake bakin gate security sun hanasu shigowa kansu abun kallon ne wasu galan galan na fetur ne a hannun su yayin da wasu tayoyi ne a hannun su duk yan ɗaukar doka ne a hannu idan court batayi masu adalci ba.
Wasu danƙara daƙaran motacine na gidan television suka dunfaro court ɗin tun kafin su ƙaraso police ɗin dake wurin suka shiga kora mutane gefe dan su basu hanya.
A ƙalla motocin gidan tv zasu kai guda biyar huɗu baƙaƙe ne ƙirar reng rover yayin da suka sako tv broadcasting van car white color a tsakiyar su da gudun gaske suka nufo court ɗin,ganin irin gudun da suke ne yasa mutane darewa suka basu hanya, tuni security's sun buɗe masu gate suna ƙarasowa ciki suka shige , sai da suka gama dai daita parking tukun suka shiga fitowa kowanen su sanye yake da journalist jacket black color a gaban rigar anyi rubutu da farin paint inda aka rubuta press da mayan haruffa.
ba ɓata lokacin suka shiga fito da kayan aikin su cameras ne yan uban su dan duk yan jaridar dake wurin babu masu nagartatun kayan aiki masu tsada kamar na su.
cikin ƙanƙanin lokaci suka gama dai daita kayan aikin su bayan sun gama daidaitawa ne aka buɗe back seat na motar dake gaban tv broadcasting van car, wata matashiyar budurwa ce tafito sanye take da pant suit white color tayi roling da black ɗin veil,high hills ne a ƙafarta black color,fara ce kyakyawar gaske wurin cameras ɗin ta nufo cikin takun ƙasaita.
Kallo fa ya koma sama gaba ɗaya hankalin mutane ya dawo kan su sai ƙus ƙus ke tashi a wurin.
wannan matashiyar budurwar ce ta fara gabatar da shirin nasu cikin harshen hausa amma saboda zaƙin muryar ta kamar bada hausa take magana ba
“masu kallon mu barkan mu da sake saduwa acikin shirin mu mai farin jini GANI YA KORI JI, a inda muke kawo maku shari'ar hajiya Asma'u wacce ake zargin dasa hannunta a kisan mijinta wato CP ( commissioner of police ) na wannan jaha ,masu kallon mu idan baku manta ba a wancan lokacin koto ta ɗaga sharia'ar zuwa goma ga wanta febrairun shekarar da muke ciki bisa ga wasu dalilai, a yaune adadin kwanakin da koto ta yanke dan zartar da hukunci suka cika , ku biyo mu dan jin yanda shari'ar zata kaya”
tana gama faɗa ma'aikatan suka kashe kemarorin, wani daga cikin ma'aikanta ne yace “good job BALQIS babu wanda zaice ba LAATIFA ba ce” ɗan ya mutse fuska tayi tana faɗin “thanks” tana komawa back seat ɗin motar data fito, jinjina kai kawai yayi,yana sakin murmushi tana shiga cikin motar wayarta dake ringing ta ɗauka picking call ɗin tayi haɗi da kara wayar a kunnenta, muryar mai kiranta ne ya daki dodon kunnan ta
“ hello balƙis ya aikin yake tafiya?”
ya mutse fuska tayi tana faɗin “wallahi bawani abun duk wahala ne, kuma ni banga amfanin bin wannan shari'ar ba”
“haba balqis miye abun wahalar aciki, na kalli live kuma naga kinyi ƙoƙari, ke da yake ba yar jarida bace shiyyasa zaki ce haka”
taɓe baki tayi tana faɗin “ni dai wallahi kin haɗani da Aiki Aunty laatifa”
“kai balƙis miyasa za kice haka bana jin daɗi kina faɗin haka sai naga kamar na takura maki ne ba da son ranki ki kayi ba” jin abun da laatifa tace yasa balqis cewa “ni baki takura man ba, dan nayi niyya ne yasa na zo”
“shikenan sai kin dawo amma dan Allah kar kice ma dady ni na nace kizo please”
“zance mashi ni nayi niyya ba ke ki ka sani ba,amma kin tabbata zaki cika man alƙawari na?”
“nagode ƙanwata sai kin dawo karki damu”
“ok sai na dawo” balƙis ɗin ta faɗa tana rejecting kiran iska ta fesar daga bakinta,wayarta ta shiga shafawa tana kallon wallpaper wayar tana sakin murmushi,sai sakin murmushi take tana aikin shafa wayar, matso da wayar tayi zuwa fuskarta kissing screen ɗin wayar tayi tana faɗin
“am eager to see u my hero,i miss u”
tana cikin wannan shauƙin taji hayaniya tayi yawa ga kuma jiniyar motocin security Army's da yake glass ɗin motar da take ciki na gaba a buɗe yake,tsaki taja tana faɗin
“i hate this sound gaskiya Aunty latifa baki kyauta man ba” ta faɗa tana ɗan jan tsaki, nocking ɗin ƙofar motar taji anyi da sauri ta juya tana kallon mai yin nocking ɗin ranta a haɗe tace “what?”
“sorry dama cewa zanyi ki fito ga BARRISTER ZULAIHAT nan ta ƙaraso” ya mutsa fuska tayi tana faɗin ok
fitowa tayi daga motar sai wani sa hannu take tana kare fuskanta saboda zafin rana.
wasu jibga jibgan motacin sojoji ne ke shigowa cikin court ɗin gaba ɗaya sun cika court ɗin da ƙarar jiniyar su yayin da tsakiyar su wasu expensive bullet proof latest car ne masu nufashi guda biyu fara da baƙa.
Anan compound ɗin court ɗin su kayi parking,security Army's ne suka fara fitowa daga cikin motacin su hannuwan su riƙe da manyan bindigu ga wasu soke a ƙugun su.
farar motar su ka nufa, wani jibgegen security guard ne ya buɗe back seat ɗin motar.
wata kyakyawar baturiyar mata ce ta fito daga back seat ɗin a ƙalla zata kai kimanin shekara 50 a duniya, kyakyawa ce ajin farko ƴar gayu kai tsaye idan ka kalleta ba zaka ce tayi waɗannan shekarun ba a duniya,sanye take da fararen flat pant suit a jikinta ta yafa farin mayafi a kanta,tana da dara daran idanu farare wanda cikin su ya kasacen Ash ne a manne su ke da farin medical glasse,fuskarta ɗauke take da ni'imceccen murmushi.
𝑏𝑎𝑟𝑟𝑖𝑠𝑡𝑒𝑟 𝑧𝑢𝑙𝑎𝑖ℎ𝑎𝑡 𝑘𝑒𝑛𝑎𝑛 𝑓𝑖𝑟𝑠𝑡 𝑤𝑖𝑓𝑒 𝑜𝑓 𝑡ℎ𝑒 𝑓𝑜𝑟𝑚𝑒𝑟 𝑝𝑟𝑒𝑠𝑖𝑑𝑒𝑛𝑡 𝑜𝑓 𝑛𝑖𝑔𝑒𝑟𝑖𝑎,𝑤𝑎𝑐𝑐𝑒 𝑚𝑢𝑡𝑎𝑛𝑒 𝑘𝑒𝑚𝑎 𝑙𝑎𝑘𝑎𝑏𝑖 𝑑𝑎 𝑙𝑎𝑢𝑦𝑎𝑟 𝑎𝑙'𝑢𝑚𝑚𝑎ℎ.
daga front seat na motar security guard ce ta fito hannunta riƙe da black coat da white hand bag sai briefcase rataye a ƙafaɗar ta wanda nake kyautata zaton na barrister ne.
wani daga cikin security guard ɗin ne ya buɗe back seat ɗin baƙar motar dake bayan wacce barrister zulaihat ta fito,ƴan mata ne guda biyu su ka fito, dukan su baƙar abayace a jikinsu anyi mata aiki da golding stones sai sheƙi da ɗaukar ido su ke, sunyi roling da glenta,fuskar ɗaya sanye take da niƙab,ɗayar kuwa sunglasses ne manne a fuskarta dake ɗauke da fara'a,hannunta riƙe da ƴar madaidaiciyar bag ta company Gucci golding color,tana matuƙar kama da barrister zulaihat kamar an tsaga kara.
cikin tafiyar ƙasaita balqis ta ƙaraso wurin su tana sakin murmushi,tana isowa hugging ɗin barrister tayi tana faɗin “good morning mom” raba jikin su barrister tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace
“morning balqis, yau kece da kanki?” murmushi balqis tayi tana faɗin “ayyuka ne su ka yima Aunty laatifa yawa shine tace nazo nayi attending wannan shari'ar dan bata so tayi missing”
“good,laatifa ba dai aiki ba” barrister ta faɗa,ƴan matan nan ne suka ƙaraso wurin su, mai niƙab ɗin ce ta gaishe da balqis yi tayi kamar bata san da ita take ba,saima kyauda kai da tayi tana kallon gefe, yamutse fuska mai kama da barrister tayi tana faɗin “Abun ma yar haka ce ko Aunty balqis” murmushi balqis tayi kamar ba ita ba tana faɗin
“miye kuma yumnah shagwaɓa” bubbuga ƙafa wacce aka kira da yumnah ta shiga yi tana turo baki da faɗin
“mom kina jin Aunty balqis ko, ba zata daina ce man haka ba”
“bana cike da wannan shiritar taki yumnah,balqis nayi ciki”
barrister ta faɗa tana yin gaba, bin bayanta yumnah da wannan budurwar dake sanye da niƙab su kayi yummah na cigaba da shagwaɓarta security guard ɗin na biye da su.
murmushi kawai balqis tayi tana komawa wurin aikinta.
Yan jarida na ta so suyi magana da barrister amma security guard ɗin ta sun ƙi ba su dama,amma saboda ƙwaƙwa irinta ƴan jarida ana ture su amma suna jefoma barrister tambayoyi.
A bakin ƙofar office ɗinta security
su ka tsaya macen dake ɗuke da jakarta da rigarta ce ka ɗai ta shiga ciki sauran securitys ɗin kuma su ka zagaye office ɗin yanda ko ƙuda bai isa ya gitta ba tare da sun ƙwamushe shi ba.
Wani irin haɗaɗen office ne naji da faɗa, yasha expensive desk da leather chair's masu shegen kyau ,barrister zulaihat kujerarta ta nufa ta zauna,akan desk ɗinta securityn ta ajiye mata hand bag ɗinta sannan ta rataya mata coat ɗinta jikin office suit hanger,wasu files ta ciro daga cikin briefcase ɗinta ta shiga dubasu tana ƙarasa haɗa hujjojine kafin lokacin shiga court ɗin yayi.
saman sofa dake cikin office ɗin yumnah su ka nufa su ka zauna sai a lokacin ne ɗayar ta yaye niƙab ɗin dake fuskar ta, masha Allah na furta da ganin kyakyawar fuskar matashiyar budurwar wacce a shekaru bazata wuce sha tara ko ashirin ba kusan sa'anni ne da yumnah.
damuwace ƙarara akan fuskarta, murmushi yumnah tayi tana faɗin
“yanzu dan Allah da ki ka cire wannan abun ba kiji daɗi ba?” kallon yumnah kawai matashiyar tayi ba tare da tace komai ba
“zaki fara wannan shirun naki ko, mom kiyi mata magana mana ta saki jiki da ni ko dan taga na damu da ita” yumnah ta faɗa tana wani ɓata fuska, girgiza kai kawai barrister tayi tana cigaba da aikin dake gabanta ba tare da tace ma yumnah komai ba.
“mom kema shirun zaki man?” ta faɗa tana turo baki kamar zata fashe da kuka
“yumnah wai miyasa ke baki san lokacin da mutum ke son magana da lokacin da bai so ba, baki san halin da take ciki bane zaki dameta?”
a hankali ta kama kunnenta tana faɗin “sorry mom, zama da damuwa bashi ke maganin matsala ba, that's why nake son ta ɗan saki jikinta” kallon matashiyar tayi tace
“sorry NAINARH idan na takura maki, inaso ki saki jiki ne kawai”
murmushi wacce aka kira da nainarh ta saki
“karki damu baki takura man ba, nagode da kulawar ki a gare ni”
martanin murmushi yumnah ta mayar mata tana buɗe hand bag ɗin data shigo da ita, ciro wayarta ƙirar iPhone 14 pro max tayi dialing wata number,waya ta shiga yi cike da shagwaɓa.
miƙewa barrister tayi da sauri security ta matso tana harharɗa files ɗin dake kan desk ɗin tana maidawa cikin briefcase, ganin haka ne yasa su yumnah miƙewa da sauri nainarh na maida niƙab ɗinta tana ɗaurawa, kallon su barrister tayi tace “ina zaku?” yumnah tace “mom ba time yayi ba”
“eh, ku zauna anan duk yanda shari'ar tayi za kuji” duƙar da kai nainarh tayi alamar ba haka taso ba
matsowa barrister tayi ta dafa kafaɗar “sorry nainarh ba dan wani abu yasa nace ku zauna nan ba sai dan tsoron abun da zai biyo baya acikin court, nan sai kin fi samun tsaro”
“shikenan mom,amma ba za'a neme ni ba?” nainarh ta faɗa
“babu mai neman ki, idan yiwuwar hakan ma ta taso za'a zo a tafi dake ne, fatana dai ki kwantar da hankalin ki” gyaɗa mata kai kawai tayi.
Komawa su kayi su ka zauna barrister kuma su ka fice,security tunda su ka ji alamun buɗe ƙofar office ɗin su ka gyara tsayuwar su tana fitowa su ka nufi cikin court ɗin har lokacin yan jarida basu daina binta da jefo mata tambayoyi.
ciki su ka ƙarasa security guard biyu ne suka shiga cikin court room haɗi da macen sauran su ka tsaya a waje, lokacin da su ka shiga court room ɗin a cike take,duk wani mai ruwa tsaki ya hallara suna zaune a mazaunin su yan jarida sun saita kamarorin su jiran a fara kawai su ke, balqis na daga zaune saman chair daga can baya,Attorney tables da aka tanada domin su ta nufa zama tayi security na ajiye mata briefcase ɗinta daga gefenta su ka tsaya,gaishe da ita attorneys ɗin su ka shigayi tana amsa masu cikin kulawa , mutum biyu ne a cikin su ko kallon in da take ba suyi ba,wata macece da wani namiji,fuskar ko wanen su a haɗe take kamar an aiko masu da saƙon mutuwa, namijin ya jingina da head board ɗin chair ɗin da yake zaune hannunshi riƙe da ƙwallon wasan chess yana wasa da ita saman desk,murmushi saki tana faɗin “good morning BARRISTER HASHIM” sai a time ɗin ya juyo masha Allah na faɗa kyakyawa ne na gaske fatar jikinshi chocolate color ce, kallonta yayi da wasu lumsassun idanuwanshi, kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kai yana faɗin “morning” kamar irin anyi mashi dolen nan,girgiza kai kawai tayi tana buɗe briefcase ɗinta ta fito da files da laptop ɗinta dake ciki......
_*Episode 3_4*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
_________________________
Prison officers ne su ka shigo su biyu sai mata guda biyu ma'aikatan prison sun sako wata mata a tsakiyar su yayinda police maza gudu biyar ke a bayan su kowanen su riƙe yake da bindigar sa,uniform ɗin prison ne a jikin matar inda a gaban rigarta aka rubuta number 106 da farin fenti’ black ɗin hulace a kanta,hannunta a sanye yake da handcuff, kanta a duƙe yake har su ka ƙarasa cikin court ɗin, kusa da brisster zulaihat matar ta zauna yayin da police ɗin su ka tsaya a bayan su.
ƙus ƙus ne ya fara tashi a cikin court room ɗin wasu na tausaya ma matar yayin da wasu ke kiranta da munafuka in sha Allah asirinta sai ya tonu.
shiru su kayi sun kafe juna da ido kowa na so yayi ma ɗan uwansa magana amma ya kasa daga brisster har mata,ƙwalla ne ya taru idon matar da sauri brisster ta miƙa mata handkerchief tana faɗin “karki kiyi kuka, in sha Allah yau gaskiya za tayi halinta” jinjina mata kai matar tayi tana goge hawayen dake zuba a idonta, brisster ma dauriya kawai take amma itama kukan take son yi kawai ta daure ne dan karta ƙara karyama matar zuciya.
A hankali matar tace “ina nainarh?”
“suna office ɗina ita da yumnah, na hanata shigowa nan ne dan ban san wani abu ya faru da ita” jinjina kai kawai matar tayi da ka ganta ka san tana cikin matsananciyar damuwa.
ɗaya daga cikin prison offices ɗin ne yace “hajiya za mu iya tafiya?” miƙewa matar tayi su ka nufi in da aka tanada domin zaman su,zama tayi matan su ka sata a tsakiya.
miƙewa su kayi gaba ɗayan su saboda shigowar alƙali,saida alƙali ya zauna tukun suma suka zauna,bayan koto tayi tsit, miƙewa judicial Assister yayi ya gabatar da ƙara bayan ya kammala ne alƙali ya buƙaci da lawyer masu ƙara ya fito.
Cikin ƙwarewar aiki clerk yake typing duk wani abu da ake furtawa a cikin court kama daga sunaye mutane har zuwa yanda shari'ar ke tafiya ga DAR (digital Audio recording ) box a gefenshi tana ɗaukar komai.
miƙewa tsaye brisster hashim yayi wasu files dake gabanshi ya ɗauka yana ajiye chess ball ɗin dake hannunshi, fitowa yayi daga inda yake zaune yana wani gyara zaman coat ɗin dake jikinshi,papers ɗin dake hannunshi ya miƙama judicial Assister, juyawa yayi ya miƙama alƙali.
“my lord wannan rahoton gawar marigayi ne wanda ƙwararon likitoci su ka gudanar tare da horoton cctv camera dake gidan shi, sai bincike da ƴan sanda su ka gudanar akan shatin hannun hajiya Asma'u da aka samu a jikin bindigar da aka kashe marigayi da duk wasu wayoyi daya amsa kafin faruwar abun,sai sunayen witness”
yana gama faɗa ya koma mazauninshi ya zauna yana ɗaukar ball ɗin shi ya cigaba da juyata saman table.
miƙewa mom tayi cikin taƙon kamala ta fito tsakiyar court,ɗan rissinar da kai tayi tana kallon alƙali alamar girmamawa, jinjina mata kai alƙalin yayi,takardar dake hannunta ta miƙama judicial Assister tana faɗin
"my lord wannan sune jadawalin shedo da nayi ma court alƙawarin kawowa"
tashi judicial Assister ɗin yayi ya miƙama alƙali takardar, amsa alƙalin yayi yana ɗaukar glass ɗin shi ya manna a ido, ya ɗan ɗauki tsawan lokaci yana duba duka takardun harda wanda brisster hashim ya bada kafin yace“zaki iya tafiya” godiya tayi mashi tana komawa ta zauna.
“idan malam Aisha tana kusa ta matso gaban koto” Alƙali ya faɗa, a hankali matar ta miƙe daga cikin mutanen dake zaune saman chair, jikinta sai rawa yake daga ganin yana yinta bata cikin natsuwarta,ƙarasowa tayi ta tsaya a cikin witness stand, tashi mom tayi ta nufi in da matar ta tsaya.
ƴan jarida nan su ka fara ɗaukar komai, tasowa balqis tayi ta dawo inda mutane su ke hannunta riƙe da abun magana,juyawa tayi saitin da attorney su ke karab idanunta su ka haɗu da na brisster hashim wani ɗan iskan kallo ya watsa mata wanda yasa ƴan hanjin cikinta kaɗawa ita kaɗai ta san ma'anar wannan kallon daya watsa mata , da sauri ta duƙar da kai tana juyawa ta bar wurin da sauri, gyaɗa kai yayi yana maida hankalinshi ga Alƙali.
Rantsuwa Alƙali ya fara sa Aisha tayi akan zata faɗin gaskiya, kafin ya ɗaura da cewa “court na san sanin cikaken tarihin ki?”
kasa magana tayi saboda wani irin rawa da jikinta yake har sai da Alƙali ya sake magana “kina ɓata ma koto lokaci" da ido mom tayi mata alama data kwantar da hankalin ta, magana ta fara cikin rawa rawar murya dake nuna rashin natsuwarta
“suna na Aisha Usman shekaruna 42 ni ƴar asalin garin faskari ce dake jahara katsina,nazo Abuja ne ta dalilin wata ƙanwar mahaifiyata itace sanadiyyar fara aikina a gidan marigayi”
“malama Aisha tsawan wane lokaci ki ka san marigayi da matar shi hajiya Asma'u?”
“tsawan shekara goma sha biyar”
“ko zaki iya faɗa ma court yanda zamantakewar gidan take tsakaninki da masu gidan?”
“mutanene masu karamci da san al'ummah ko da kuwa ya kasance na ƙasa da su ne, duk tsawan shekarun dana ɗauka tare da su basu taɓa nuna man cewa wai ni ƙasa nake da su ba, hajiya Asma'u ta ɗauke ni tamkar ƙawarta kuma ƴar uwarta,haka marigayi tamkar ƴar uwarshi ta jini haka ya ɗauke ni”
ƴan rubuce rubuce Alƙali yayi kafin ya ɗago yana faɗin “ko zaki iya bama court labarin yanda kisan marigayi ya....” tun kafin Alƙali ya ƙarasa magana tayi saurin ƙatse shi jikinta na rawa tace “wallahi ni ban san komai a game da kisan marigayi....”
desk Alƙali ya buga yana faɗin “nan court ce, ki san yanda zaki riƙa magana, laifi ne Alƙali na magana ka tari numfashin shi, ki kiyaye”
“tuba nake” ta faɗa
tunda Alƙali ya fara magana gaban matar nan ke faɗuwa, tama kasa ɗagowa ta kalli Alƙalin ko mutanen dake cikin court ɗin,brisster hashim kuwa da wannan matar tunda Alƙali ya fara gabatar da ƙara ya mida hankalin shi kan Alƙali ko motsin kirki ba yayi ƙwallon chess ɗin dake hannunshi ma ajiyeta yayi.
tambayar Alƙali ya sake jefa mata, kawai sai gani a kayi tafashe da kuka abun yayi matuƙar ɗaurema brisster kai hajiya Asma'u kuwa jikinta sanyi yayi zuciyarta ta karaya, ta san da wahala ta ƙubuta, Aisha ka ɗaice shedar da take ganin zata iya taimakawa wajen faɗar gaskiya.
wicked side smile brisster hashim ya saki, yana kallon macen dake kusa da shi su ka kashe ma juna ido, da yawan brisster's ɗin dake wurin sun jin daɗin yanda abun ke tafiya ƙalilan ne abun ya taɓa zuciyar su.
sai da ta gama kukan mai isarta tukun Alƙali yace“koto na saurarenki”
“wallahi ni ban san komai ba, hasalima bana garin abun ya far.....”
da sauri brisster zulaihat ta tari numfashin matar tana faɗin
“my lord!, shaidata ta shiga halin ruɗani, tana tsoron magana a gaban court sabo....”
da sauri matar tace “babu ruɗanin da na shiga, kuma ba wai ina jin tsoro ba ne , gaskiya ce nake faɗa, bana nan abun ya faru” matar ta faɗa with full confidence,mamaki kamar ya kashe mom, saboda Aisha tana Abuja komai ya faru amma a gaban koto tace bata nan, brisster hashim har ƙara gyara zama yake abun yana tafiya yanda yake so.
“laifi ne katse shaida yayin bada amsar da Alƙali ya tambaye shi, brisster ki kiye”
“tuba nake” ta faɗa
“ina ki ka je a lokacin da abun ya faru?” Alƙali ya jefa mata tambaya
“naje garin mu domin duba jikin ɗana da ke fama da ciwan daji ( cancer ), kuma hajiya Asma'u da kanta ta bani izinin tafiya ita da mijinta”
“ A ranar yaushe ki kayi tafiyar?”
“na tafi garin mu ranar laraba a washe garin ranar Alhamis nake samun labarin abun da ya faru”
“mi yasa baki dawo ba da ki ka samun labarin abun da ya faru da ubangidan na ki?”
“saboda lalurar ɗana, jikinshi ne yayi tsanani shiyyasa ban samu damar zuwa ba”
ƴan rubuce rubuce Alƙali yayi kafin yace “zaki iya komawa ki zauna, kotu za tayi bincike akan bayanan da ki ka bata, lawyer masu ƙara ko kana da tambayoyin da za kayi ma malam Aisha” miƙewa brisster hashim yayi yana gyara zaman coat ɗin shi, cikin takun ƙasaita ya nufi tsakiyar koton, cikin maganar ƙasaita yake faɗin “my lord, ina so zanyi ma shaida wasu ƴan tambayoyi”
izini Alƙali ya bashi
“godiya nake” ya faɗa yana matsawa in da Aisha take tsaye
“malam Aisha ina so zanyi maki wasu ƴan tambayoyi,ya zamantakewar iyayen gidan naki take, shin kafin mutuwar cp ko a kwai wani saɓani da ya taɓa shiga tsakaninshi da uwar ɗakin ki, ko akwai rashin jituwa tsakaninsu, wasu dai Abubuwa maka mantan haka???”
“babu yallaɓai,a kwai fahimta a tsakaninsu, marigayi yana matuƙar kyautata ma matar shi hatta mu ƴan aiki ya ɗauke mu da matuƙar daraja”
jinjina kai brisster hashim yayi yana faɗin “ita fa uwar ɗakin taki, ya nata halayen su ke, bata da wasu ɗabiu marasa kyau wanda baku jin daɗin su???”
ran brisster zulaihat ne ya fara ɓaci da irin tambayoyin da brisster hashim kema Aisha
“gaskiya babu”
“koda a ɓoye bata da su?” ya sake mata tambayar, miƙewa brisster zulaihat tayi rai a ɓace “objection my lord”
“sustained”Alƙali ya faɗa yana bata izini
“lawyer masu ƙara kamar yana son tursasa witness ɗina akan dole sai ta faɗi abun da bashi ba”
“brisster hashim ka kiyaye” jinjina kai brisster hashim yayi
“malam Aisha a ra'ayin ki ne ki ka tafi gida ko kuwa uwar ɗakin kice ta nuna dacewar tafiyar ki a wannan lokacin?”
“Itace tace ya kamata na tafi na duba jikin shi , da tace man haka sai nace mata zan shirya ranar juma'a ko asabar naje amma sai tace na shirya gobe na tafi da farko naƙi amincewa da tafiyar a washe garin nace kawai zan tura masu kuɗin su fara amfani dashi kafin zuwa ranar juma'ar na tafi, amma sai ta zaunar dani ta nuna man dacewar na tafi a goben shine na amince”
“da tace ki tafi a lokacin ba kiyi wani tunani ba ko akwai dalilin da yasa tace kije?”
Miƙewa brisster tayi tana ɗan dukan table ɗin dake gabanta “objection my lord”
“Overruled”Alƙali ya faɗa
komawa tayi ta zauna tana cizon yatsa na rashin bata dama da Alƙali yayi, side smile brisster hashim ya saki
amsar tambayar da brisster hashim yayi mata ta bashi
“banyi tunanin komai ba, saboda idan ahalina suna cikin matsala ta kan fini shiga damuwa akan halin da nake ciki,shiyyasa banyi zargin komai ba”
jinjina kai brisster yayi “mudi mai gadi ya sanar da koto cewa akwai wani matashin saurayi dake yawan zuwa wurin uwar ɗakin na ki, baki taɓa tunanin mike kawoshi wajenta ba , ko miye alaƙarta da shi ???"
“sunan sa Abid, ɗan ƙanwarta ne dake zaune a ƙasar waje, yana yawan zuwa wurinta duk lokacin da yazo suna samu saɓani da marigayi saboda kwata kwata jinin marigayi bai haɗu dana Abid ba, saboda Abid yaro ne mara tarbiya baya girmama na gaba da shi , gashi duk lokacin da yazo sai ya takura ma yarinyar su , hakan yasa marigayi baya son yana zuwa gidan, ita hajiya sai ta nuna ba taji daɗi ba kan nuna kyara da tsangwama da yake akan yaron, a ranar da mu kayi magana kan tafiyata ya zo gidan har saɓani ya shiga tsakanin shi da marigayi ya dake shi, abun yayi matuƙar ɓata ran hajiya har su ka samu saɓani da marigayi, bayan mungama magana da ita naje ɗakina na wanke kayan da zan tafi da su na zagaya baya zanyi shanya na hangesu ita da Abid suna tattauna wasu maganganu wanda ban san mi su ke tattaunawa ba, nayi ƙoƙarin naji abun da su ke faɗa amma abun ya gagara saboda tazara dake tsakanin mu,bayan na koma ɗakina cikin dare naji Abid ɗin yana waya a bayan ɗakina kamar yana faɗama wanda suke waya saɓanin da su ka samu da marigayi bana jin mi na ciki wayar ke faɗa masa na dai ji yana faɗin a cikin satinnan ya kamata suyi aiki a kanshi ko zai daina mashi shiga hanci da ƙudindine, na tsorata da jin abun daya faɗa har na kasa bacci , washe gari tunda safe na samu hajiya da maganar amma sai ta nuna kar na damu da abokan kasuwancin shi yake waya”
tunda Aisha ta fara jera wannan jawabin gaban hajiya Asma'u ke faɗuwa bata taɓa sanin komai dake faruwa a gidan Aisha na sane ba sai yanzu.
“abokan ka suwanci, ko kin san wane irin ka suwanci yake?, sannan wane saɓani ya shiga tsakanin shi da marigayi?”
“gaskiya ban san kasuwanci da yake ba, amma na taɓa jin labari a wurin mai gadi cewa yaron yana harkar kayan maye , kuma dukiyar da yake juyawa ta hajiya Asma'un ce ”
jinjina kai brisster yayi
“wane saɓani ne ya shiga tsakanin shi da marigayi?” ya sake maimaita mata tambayar
“gaskiya ban sani ba”
juyawa brisster hashim yayi ya kalli Alƙali “my lord , tun ranar da mai gadin gidan ya ba police duk wasu bayanai akan yaro suka tsaurara bincike sai dai kash bayan kwana biyu da fara binciken na su aka samu gawar shi yaron a cikin gidan shi anyi mashi kisa makamancin na marigayi,hakan na nufin hajiya Asma'u ta tura Aisha gida ne dan ta samu damar aiwatar da shirinta ba tare da wani ya ganota ba,sannan ta sallami ma'aikatan gidan dan kar su ga abunda zai faru,Abid ya ƙi bata haɗin kai ne shiyyasa ta tura makasan da su ka kashe cp su ka kashe shi dan kar ya zame mata matsala”
“Objection my lord”
jinjina mata kai Alƙali yayi alamar amincewa
“my lord lawyer masu ƙara na son tabbatar da laifi akan wacce nake karewa ba tare da ƙwararan hujjoji ba”
“brisster hashim ka kiyaye”
“tuba nake”
jinjina kai Alƙali yayi kafin ya ɗauki pen ɗin shi yayi ƴan rubuce rubuce
“lawyer masu ƙara ko kana da sauran wasu tambayoyi da za kayi ma malam Aisha”
“su kenan tambayoyin da nake son yi mata” brisster hashim ya faɗa, tsaki brisster taja a zuciyarta tana faɗin
“ko ina amfanin wannan tambayoyin”
“lauyan wanda ake ƙara ko kina da wasu tambayoyi da za kiyi ma malam Aisha?”
miƙewa brisster tayi “eh my lord” dama Alƙali ya bata, fitowa tayi brisster hashim kuma ya koma mazauninshi.
“malam Aisha a bayanan da hajiya Asma'u ta bada da kuma binciken da muka gudanar ya tabbatar mana da cewa kina a gidan a ranar da abun ya faru , hasalima kece ki ka fara sanar da su zuwa mugayen mutanen da su ka shigo gidan”
“wallahi brisster bana garin ita da kanta tace naje, munyi maganar da ita yau washe gari tunda safe na tafi”
murmushi gefen fuska brisster ta saki tana faɗin “ƴan uwan naki su su ka bada shedar cewa a ranar ba kije garin naku ba sai a washe garin ranar da abun ya faru”
shiru Aisha tayi ba tare da tace komai ba
“malama Aisha ke koto ke saurare?”
“ranar na tafi sai dai ban samu isa garin ba sai cikin dare,hakan yasa basu san da zuwa na ba sai washe gari”jinjina kai brisster tayi tana juyawa ta kalli Alƙali
“my lord malama Aisha ta sanar da koto cewa bata nan abun ya faru, a binciken dana gudanar ya tabbatar man da tana a cikin komai ya faru”
“binciken koto zai tabbatar da hakan, kina da sauran wasu tambayoyi da za kiyi mata”
“babu sauran wasu tambayoyi da zanyi mata”
“malam Aisha zaki iya komawa mazauninki kafin binciken koto ya kammala”
“godiya nake” ta faɗa tana ɗan rissinar da kai,barin witness stand ɗin tayi ta koma mazauninta ba tare da ta bari sun haɗa ido da brisster ba ko hajiya Asma'u.
brisster wurin zamanta ta koma itama,haka shari'ar ta cigaba da tafiya duk wasu jadawalin sunayen witness ( sheda) sai da Alƙali ya kira su gaban koto yana masu tambayoyi bayan ya kammala masu ya ba brisster's dama suma suyi masu nasu tambayoyi, ko wane sheda da kalar amsar da yake ba dawa a kan kisan marigayi CP,hajiya Asma'u tun tana sa ran kuɓuta har ta sadaƙata tasan bazata taɓa kuɓuta ba daga yanayin amsoshin da shedun ke ba court,brisster ma gwiwowinta sun sage bata taɓa shari'a irin wannan ba tana shari'a akan kisa amma kuma bata taɓa rashin nasara ba amma wannan shari'ar na neman tafi ƙarfinta , shedun da take taƙama dasu gaba ɗaya sun juya mata baya,duk wanda aka kira a cikin su abu ɗaya su ke faɗi hajiya Asma'u ta kashe mijinta kuma suna bada ƙwararan hujjoji wanda dole koto ta yarda .
brisster hashim kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha yasan zaiyi wuya yau bai yi nasara akan brisster zulaihat ba abun da ya daɗe yana jira kenan tsawan shekaru.
Magana Alƙali ya fara, tsit kotun tayi kowa na sauraron hukuncin da court zata yanke “binciken kotu ya tabbar da malam Aisha bata nan a ranar ashirin da ɗaya ga watan biyar”
Ajiyar zuciya Aisha ta sauke tana dafe saitin zuciyarta, brisster wani mugun faɗuwa gabanta yayi hajiya Asma'u kuwa tuni hawaye sun taru a cikin idanunta
“bayan kammala haɗa duk wasu hujjoji da binciken koto dana likitocin dake kula da gawar marigayi CP ya tabbatar da hajiya Asma'u itce ta kashe CP” tunda Alƙali ya fara magana brisster hashim ke sakin murmushi, brisster zulaihat kuwa banda faɗuwa babu abun da gabanta ke yi.
“kotu ta yanke ma hajiya Asma'u hukuncin kisa ta hanyar rataya tare da biyan tara ta naira milayan hamsin”
Wani irin murmushin farin ciki barisster Hashim ya saki yana kallon ƴan uwan shi wanda hukuncin yayi masu dai dai,a ɗayan ɓangaren kuwa barisster Zulaihart wani irin tashin hankali mara misaltuwa ta tsinci kanta, da dama mutanen dake Court ɗin abun yayi masu daɗi yayin da wasu ke tausaya ma Hajiya Asma'un.
ana cikin jimamin hukuncin da court ɗin ta yanke sai ga saƙo daga fadar shugaban ƙasa na nemama Hajiya Asma'u sassaucin kotu daga rataya zuwa ɗaurin rai da rai tare da biyan tara ta nera miliyan ɗari saɓanin hamshin.
Ran barisster hashim idan yayi dubu ya ɓaci ba haka yaso ba yaso hukuncin kisa aka yanke mata ta hanyar rataya bai so ɗaurin rai da rai ba amma idan ya tuna ba wai zata fito bane sai hankalishi ya kwanta, mom ta ɗan ji sassauci da ba kisa bane ɗaurin rai da rai ne sai dai idan ta tuna halin da hajiya Asma'u da nainarh za su shiga hankalinta na tashi.
wasu daga cikin mutane kwata kwata ba su so haka ba gani suke kamar wata maƙarƙashiya ce ake ƙullawa.
Miƙewa Alƙali yayi gaba ɗaya su ka miƙe,ƙofar office ɗin shi ya nufa kamar jira a ke Alƙali ya fita koto ta ɗauki haya niya kowa da abunda ke fitowa daga bakin shi,can compound ɗin curt ɗin kamar zai fashe saboda haya niyar mutane, mom tunda Alƙali ya fita ta kifa kanta saman desk ko motsin kirki ta kasa yi,matsowa wannan security guard ɗin tayi tana bata haƙuri, miƙewa brisster hashim yayi yana wani gyara zaman rigar shi fuskarshi ɗauke da murmushin mugunta, ɗaya bayan ɗaya mutane su ka fara fita daga cikin kotun suna tofa albarkacin su.
hanyar fita prison officers suka nufa da hajiya Asma'u, da ƙyar take taka ƙafafuwanta suna zuwa tsakiyar court ɗin ta yanke jiki ta faɗi a sume, salati mutanen da su ka rage a ciki su ka rabka da sauri mom ta miƙe kusan a tare su ka isa inda hajiya Asma'u ke yashe a ƙasa ita da wasu mata guda biyu, amma kafin su ƙaraso ma'aikatan gidan yarin sunyi mata rumfa mom ka ɗai su ka bari ta ƙarasa in da take, jijjigata ta shiga yi tana kiran sunanta amma ko gezau ba tayi ba, ɗaya daga cikin prison officers ne ya miƙoma mom ruwa,a hannu ta zuba ruwan ta shafa mata a fuska, tayi hakan kusan sau ba adadi amma bata farfaɗo ba mom bata san lokacin da ta fashe da wani matsanancin kuka ba,doctors ɗin gidan yari ɗaya daga cikin jami'an gidan yarin ya kira, ba'ayi five minutes ba sai gasu sun ƙaraso, nurses huɗu mata ne su ka kamata su ka ɗaura saman stretcher,ficewa su kayi da ita daga cikin court ɗin bayan su mom tabi tana goge hawayen dake zarya saman kumatunta, a hanzarce security guard ɗinta tabi bayan ta har zuwa in da su kayi parking Ambulance,ganin fitowar mom ne yasa sauran security guard ɗin nufota da sauri saboda mutane da ƴan jarida da suka fara jefa mata tambayoyi harda na hauka, wasu ma a fakaice magana su ke gaya mata,buɗe Ambulance ɗin ɗaya daga cikin officers ɗin yayi ciki su ka saka hajiya Asma'u,maganganu mutane ke jifa ma mom,tana jinsu amma tayi kamar bata jin mi suke cewa tana nan tsaye har sai da taga ficewar Ambulance ɗin daga cikin court ɗin tukun ta juya da nufin ta koma office ɗinta, juwar da za tayi taga brisster hashim tsaye ya harɗe hannuwa saman chest ɗin shi, wani ɗan iskan murmushi ya sakar mata yana tunkaro in da take tsaye, bashi hanya security guard ɗinta su kayi da alama dai shima ba ƙaramin mutum bane.
zuba mashi ido tayi har ya ƙaraso inda take, murmushi ya saki cikin wata irin murya kalar ta ƴan duniya yace
“ya dai lawyer Al'ummah?, yau ina goyan bayan Al'ummar taki yake?”
ɗauke kai mom tayi wani ƙululun baƙin ciki na tokare mata maƙoshi, dariya brisster hashim ya saki
“see u next time” ya faɗa yana kashe mata ido ɗaya, barin wurin mom tayi securitys ɗinta su ka bi bayanta, da kallo brisster hashim ya bita har ta ƙarasa inda su kayi parking motocin su,duk Abun da ke faruwa balqis na tsaye tana kallo,hawaye ne su ka taru a idonta ta rasa dalili rashin jituwar brisster hashim da mom, juyawa tayi ta nufi motocinsu ta shiga barin court ɗin su kayi baki ɗaya.
wannan lawyer ce ta nufo brisster hashim dake tsaye
“brisster na lura so ka ke baƙin ciki ya kashe brisster zulaihat a yau ” ta faɗa tana sakin murmushi, martanin murmushi ya sakar mata yana
faɗin “yanzu ta fara gani in dai ni ne”
“Allah ya shirya ka, gaskiya baka kyautawa matar yayan ka ce fa”
“na tsaneta bana son ganinta” ya faɗa yana barin wajen, bin bayan shi lawyer tayi.
waya brisster ta ɗauka tayi dialing number yumnah bugu ɗaya tayi picking “ku fito ina parking space ku same ni” tana gama faɗa tayi rejecting ba tare da ta tsaya jin mi yumnah za tace.
miƙewa yumnah tayi tana kallon nainarh data zuba uban tagumi, girgiza kai tayi tana nufar ta, dafa kafaɗar tayi firgigit nainarh tayi ta miƙe a tsorace har sai da gaban yumnah ya faɗin
“yumnah an gama shari'ar ne?” nainarh tajefa mata tambaya
“ban sani ba, amma dai mom tace mu sameta waje ban sani ba ko an gam....” tun kafin ta ƙarasa nainarh ta nufi hanyar fita da sauri, bin bayanta yumnah tayi.
tana fitowa ƴan jarida su ka yo mata caaa, sai jefa mata tambayoyi su ke marasa kan gado, ruɗewa tayi ta rasa in da zata dosa hawaye har sun fara zuba daga idanuwanta,ganin halin da take ciki ne yasa securitys ɗin nufarta, zagayeta su kayi suna tutture ƴan jaridar, in da mom ke tsaye tana jiran su suka nufa,maganganun mutane ne su ka fara ɗaukar hankalinta da irin kallon da suke binta da shi
“itace ɗiyarta ko kunya ba tajiba ta kashe ma yarinya ubanta saboda neman duniya kawai”
“ai hukuncin da kotu ta yanke mata bashi ya kamata da ita ba hukuncin kisa ne dai dai da ita”
“saboda brisster zulaihat yasa ba'a yanke mata hukuncin kisa ba, kasan suke da ƙasar sai yanda su kayi da talaka” maganganun dake fitowa daga bakin mutane kenan, tunda ta fara sauraronsu gabanta ke faɗuwa.
bayan su yumnah ta biyo sai turo baki take kamar zata fashe da kuka,da sauri nainarh ta nufi mom hawaye na fita daga idanunta “mom ina ummah?” shine tambayar data jefa ma brisster, juyawa mom tayi ta shige motar ta ba tare da tace mata komai ba, motar da ke bayan wacce brisster ta shiga security guard ɗin ya buɗe ma nainarh da nufin ta shiga, a masifance ta maida marfin ƙofar ta rufe tana juyawa zata nufi cikin court ɗin, da sauri brisster ta fito tana faɗin “kar ku barta ta wuce”
umarnin mom su ka bi, duk yanda nainarh ta so shiga cikin court room ɗin hanata security su kayi ƙarshe data gaji zubewa tayi ƙasa tana fashewa da wani matsanancin kuka,kamata mom tayi ta miƙar da ita tana lallashinta su ka nufi mota, itama daurewa kawai take yumanh da yake saurin kuka ne gareta har ta fara matse ƙwalla abun tausayi, motar da su ka zo ita da nainarh ta shiga nainarh kuma a tare su ka shiga da brisster, kuka take kamar ranta zai fita tun brisster na daurewa har itama ta kaida zubar da ƙwalla, a tamanin security guard ɗin su ka shiga motocin su, da gudun gaske su ka fice daga court ɗin.
tun daga farkon shigowa anguwar zaka tabbatar da anguwa ce ta manyan mutane masu faɗa aji a cikin ƙasa,manyan gine gine ne ta ko ina,tun daga nesa ƙarar jiniyar motocin su ka cika anguwar,da wani irin matsiyacin gudu su ka shigo anguwar, miƙe titin su kayi shantal sai da su ka kusa kai ƙarshen shi tukun suka karya kwana,tun daga farkon street ɗin da su ka shigo check point ne na sojoji,kowanen su ƙatuwar bindigace a hannunshi yayin da wasu ke soke a ƙugunansu, tun kafin motocin su ƙaraso sojojin dake zaune bakin ɗan gate ɗin da su ke sawa su ka buɗe masu, suna isowa babu jira suka wuce,tafiyar kusan minti goma sha biyar su kayi a ƙalla sun wuce check point na sojoji da ƴan sanda kusan guda goma kafin su ka kawo bakin wani ƙatafaran gate,ba sojojin dake gadin gate ɗin ba shi kanshi gate ɗin abun kallo ne, wani irin zungureren gate ne ƙaton gaske.
ga wasu irin manya manyan sojoji dake gadin shi, kwata kwata babu ɗigon imani a fuskar su,sojojin dake zaune saman bench ne suka miƙe da sauri lokacin da motocin su ka ƙaraso bakin gate ɗin,wani mahaukacin horn akayi da motar dake gaba da sauri wani soja ya danna wani abu dake hannunshi mai kama da remote nan take gate ɗin ya shiga zugewa zuwa gefe ɗaya,da gudun gaske suka danna kan hancin motocin zuwa ciki, masha Allah na furta a yayin da nayi arɓa da ƙaton Castle ɗin da su ka shigo,gidajene a cikin shi na alfarma hagu da dama aƙalla za su kai kimanin guda hamsin kusan a jere suke sai dai akwai tazara mai ɗan yawa a tsakanin ko wane gida, security guard ne ke yawo a cikin Castle ɗin ta ko ina,babu abun da babu a ciki kama daga clinic ne sport center, garden babu abun da babu a ciki, duk wani abu na more rayuwa a kwaishi a cikin estate ɗin.
a ƙalla sunyi tafiyar kusan minti biyar kafin su ka kawo bakin wani ƙaton luxury Villa wanda yafi ko wane gida dake cikin estate ɗin girma haɗuwa da tsaruwa, yana yin shi ma da ban yake da gidajen dake ciki shi ba'a jere yake da sauran gidajen ba yana a tsakiyar su yana fuskantar gate ɗin estate ɗin, water falls ne masu matuƙar kyau da ban shawa'a a bakin villa ɗin da a ƙalla ya kai hawa biyar, parking motocin su kayi...
_*Episode 5_6*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
___________________________
A zaune take saman royal sofa mai mazaunin mutum uku dake a katafaren main parlorn dake villa ɗin,faɗa maku tsaruwa da haɗuwar parlorn ɓata lokaci ne,royal sofas ne a cikin shi kusan set shidda, komai na cikin parlorn white and golding color ne,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke tashi a cikin parlorn haɗe da sanyi AC,parlorn iya haɗuwa ya haɗu.
duguwar rigar lace ce a jikinta ɗinkin bubu,wuyanta yasha adon sarƙar gold hakama hannuwanta da ƴan yatsunta da suka sha ƙunshin jan lalle sunsha zobunan gold masu tsadar gaske, fara ce mata ƴar duma duma ba laifi kyakyawa ce,gashin attachment ne a kanta ya zubo har gadon bayanta,wani daddaɗan ƙamshine ke fita daga jikinta wanda ya haɗe da na fresheners ɗin dake parlorn ya bada wani ni'imtaccen sanyin ƙamshi.
tsadaddiyar wayarta ƙirar company Samsung ce kare a kunenta da alama waya take,cikin maganarta ta ƙasaita da isa take faɗin
“nayi matuƙar jin daɗin wannan daddaɗan labarin daga gareka”
bana iya jin mi na cikin wayar ke faɗa, murmushi ta saki tana cigaba da faɗin
“kar ka damu in dai nice zaka samu harda gyara ma, fatana dai sirrin mu ya cigaba da ɓoyiwa”
jin jina kai tayi har ta buɗe baki za tayi magana ƙarar dirar motocin su ya katse ta, da sauri ta miƙe daga saman sofa ta nufi bakin window cikin taƙun izza da ƙasaita, yaye curtains ɗin dake jikin window tayi,a hankali ta sauke idanunta a compound ɗin gidan,kusan a tare aka buɗe motacin dake tsakiyya, brisster zulaihat ce ta fito ɗayan ɓangaren kuma nainarh ce ta fito dafe da kai yayin da yumnah ta fito daga bayan motar dake bayan ta su,daga ganin yanayin fuskarta ba ƙaramin ku ka tasha ba.
main entrance ɗin gidan su ka nufo wannan security guard ɗin ce ta shiga gaban su yayin da mazan su ka rufa masu baya har bakin entrance ɗin villa ɗin,wani ɗan card security guard ɗin ta ciro daga aljihun wandonta ta zura a jikin wata ƴar na'ura dake jikin ƙofar , cikin ƙanƙanin lokaci ƙofar ta shiga zugewa,zare card ɗin tayi, kama Nainarh mom tayi, ciki su ka kunna kai ban da security guard ɗin maza, juyawa su kayi su ka koma in da su ke zama.
Taɓe baki matar tayi tana sakin curtain ɗin ta juya zuwa cikin parlorn, ya mutse fuska tayi
“sorry kaji ni shiru, dangin yahudawan ce ta dawo, matar nan akwai ɗan banzan taurin kan tsiya,babu abun da ta rasa a rayuwa amma saboda tsabar zubar ma da kai aji ina ita ina aikin lawyer dukiya mulki babu wanda Allah bai bata ba, daga gidan mijin har gidan iyaye da ƴaƴa amma ta zaɓi wannan aikin wahalar”
jinjina kai tayi can ta kwashe da dariya tana faɗin
“no ba haka nake nufi ba, kaima ai kafi ƙarfin shi kawai ra'ayi ne irin naku kai da ita”
dariya ta sake saki tana faɗin “ok bye bye, take care of ur self for me sai na sake jinka” tana gama faɗa ta janye wayar daga kunnenta, mazauninta ta koma ta zauna tana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya tana wani jijjiga ƙafarta dake manne da chain na gold, ƙafar sai sheƙin ƙunshin jan lalle take.
tana a nan zaune su ka shigo parlorn bakin su ɗauke da sallama, daga yanyin da su kayi sallamar zaka tabbatar da rashin natsuwar da su ke a ciki, yumnah har time ɗin kuka take,miƙewa matar tayi tana nufar su fuskarta ɗauke da wani shu'umin murmushi, tana ƙarasowa gabansu tace
“Ashe haka shari'a ta kasan ce?” banza mom tayi da ita kamar bada ita take ba
“dama duk wanda yace tukunyar wani bazata tafasa ba to tabbas tashi ko zafi ba za tayi ba,to Allah dai ya kyauta na gaba”
ta faɗa tana sakin murmushi,wucewa mom tayi ba tare da ta tanka mata ba ta nufi elevator,bin bayan ta su yumnah su kayi.
dariya matar ta saki tana faɗin
“ita ƙarya dama ai fure take bata ƴaƴa,salihan bayi kullum a cikin nasara suke, tsinanne kuwa baya taɓa nasara akan masu daraja”
mom na jinta amma tayi kamar bata san tana yi ba, wasu madannai ta dannan a jikin elevator, buɗewa ƙofar tayi su ka shige ciki,wata ƴar iskar dariya mata ta sake saki
“Allah ya la'anci yahudawa da nasarawa, duk wanda ya kasance cikin wa ƴannan da Allah ya la'anta yayi asara, Allah mungode maka da kayo mu cikin jinsi mafi daraja da ɗaukaka kayo mu a muslmai ba sabon tuba ba” dariya ta saki tana bin su mom da kallo har suka yi sama.
juyawa tayi da nufin komawa mazauninta,wata kyakyawar budurwace tsaye a bayanta fara ce sai dai ba irin sosai ɗinnan ba,gown ce a jikinta white color ta ɗan wuce gwiwarta yayinda kanta ke sanye da hular saƙa baƙa,manya idanunta farare ƙar ta zubama matar, tsuke fuskarta matar tayi tana wani yamutse fuska tace “miye ki ka wani tsare ni da idanu uwata?” girgiza kai tayi cikin ƙunar rai da takaici tace
“MAMY gaskiya abun da ki ke baki kyautawa, miyasa kullum ki ke son zubarma kanki da mutunci ne?, yanzu dan Allah abun da ki ka yima mom kin kyauta?, gaskiya mamy ki dai na wannan ba hali bane mai kyau,kina jawo ma kanki abun kunya damu kan mu”
“ehyye!,sannu uwata, nace sannu uwata faɗa za kiyi man?” ta faɗa kamar zata rufeta da duka
“mamy ba faɗa zanyi maki ba, ina faɗa maki gaskiya ne a matsayina na ƴar ki, hakan bai dace ba”
“to bana so” mamy ta faɗa
“mamy dole na faɗa maki gaskiya,idan har DADY ya san baki daina wannan ɗabiun ba bazai taɓa raga maki ba kin dai san halin shi, a kullum mom tana son ku zauna lafiya amma ke baki son haka, kullum burinki ki tada fitina, kuma mamy da ki ke mata gori kema fa ba rawa ki kayi Allah ya hallice ki muslmar ba sai kiga tafiki dacewa ita data shiga muslincin daga baya sama dake da aka haifa a cikin s...”
bata ƙarasa ba mamy ta daka mata tsawa tana faɗin “FA'IZA! ni ki ke faɗama wannan kalaman dan uwarki?”
“kiyi haƙuri mamy gaskiya ce”
riƙe haɓa tayi “ah gaba gaba duka zaki fara kaiman idan banyi wasa ba”
“Allah ya tsare ni da kai maki duka mamy, amma ki sani wallahi sai na sanar da DADY baki dai na cin mutuncin mom ba, kuma ma ai ya hanaki zama main parlor,kin dai san sauran idan har yazo ya sameki”
tana faɗar haka ta nufi elevator da su mom su ka hau da sauri dan ta san zamanta a wurin bazai haifar da ɗa mai ido ba, madannan dake jiki ta danna.
“ina zaki uwar iyayi?” mamy ta faɗa tana ɗan ɗaga murya
“zanje na lallashi mom ne”
baki mamy ta saki har fa'iza ta ɓace ma ganinta, jinjina kai tayi tana faɗin
“zan kama ki ne dan ubanki, sai naji uban dake zugaki kina faɗa man magana san ranki” ta faɗa tana nufar elevator dake ɗayan ɓangaren parlorn ta shiga, dan ta san muddin dady ya shigo ya sameta a main parlorn ranta idan yayi dubu to sai ya ɓaci.
ƙofar elevator ne ya buɗe, zuro ƙafarta tayi ta nufi wani ɗan corridor,wata ƙofa ta shiga,wani haɗaɗen parlor ne ta shigo,ya fi na ƙasan da su ka baro kyau da tsaruwa, komai na cikin shi ya kasance gloding color ne,set ɗin sofa biyu a cikin shi.
Wata ƙofa ta nufa wacce nake kyautata zaton kitchen ne,tura ƙofar tayi ta shiga makeken kitchen ne gari guda babu wani da babu a ciki,ma'aikata ne su shidda gaba ɗayan su mata ne, kowaccen su na sanye da uniform ɗinta riga da wando, rigar fara ce yayin da wandon ya kasance baƙi, kowannen su aikin gaban shi yake, bakinta ɗauke da sallama ta shiga, gaba ɗaya su ka ɗago suna kallonta, amsa mata sallamar su kayi suna ɗan rissinawa su ka gaishe ta, cikin kulawa ta amsa masu tana ƙarasawa cikin kitchen ɗin, ɗaya daga cikin su ce tace
“Aunty Fa'iza mi ki ke buƙata, ai da kin kira waya ba sai kin zo da kanki ba?”
dish rag ta nufa tana faɗin “karki damu ISHRAT zan ɗauka da kaina, kawai dai ina so ku haɗa ma su mom lafiyayyan abinci mai rai da lafiya”
“in sha Allah yanzu za'a kammla” jinjina kai tayi tana ɗaukar plate mai ɗan girma ta nufi fridge,kayan ci da sha ne shaƙe a cikin shi, duk wannan kayan ƙwalam da maƙulashe dake ciki ruwa da lemu kawai ta ɗauka ta ɗaura saman plate ɗin,ƙofar fita ta nufa ɗan dakatawa tayi.
“kina buƙatar wani abun ne?” ishrat ta faɗa
“A'a, wai yaushe ummah za ta dawo ne?”
“tace man yau ko gobe amma ba tabbas” ishrat ɗin ta faɗa, jinjina kai fa'iza tayi tana ficewa daga kitchen ɗin.
parlorn data shigo ta koma wata ƙofa ta nufa nan ma wani madaidaicin parlor ne, anan ta samu yumnah da nainarh,nainarh har lokacin kuka take yumnah kuwa ta dafe kanta da hannunta ɗaya yayin da idanunta ke a lumshe hawaye na fita,wannan security na zaune gefen nainarh tana lallashinta
“Assalamu Alaikum” ta faɗa tana ƙarasawa cikin parlorn,
“good morning ma” security guard ɗin ta faɗa
“morning”fa'iza ta faɗa tana nufar in da suke ,trayn dake hannunta ta ajiye saman table, zama tayi kusa da nainarh, dafa ƙafaɗarta tayi
“ba kuka ya kamata kiyi ba Nainarh, Adu'a ya kamata kiyi in sha Allah komai yayi farko zaiyi ƙarshe, in sha Allah babu abun da zai faru da momyn ki,zata dawo gareki in sha Allah”
lallashinta fa'iza ta shigayi tana faɗa mata kalamai masu daɗi, shiru nainarh tayi tana sauke ajiyar zuciya, kallon yumnah fa'iza tayi
“Autar dady da mom kukan ya isa haka sai kisa zuciyarta ta karaya, ki daina kinji” jin jina mata kai kawai yumnah tayi
“ku shiga ɗaki sai ku kwanata ku huta kunji, ga breakfast can nasa su ishrat su haɗa maku” da to su ka amsa mata, suna tashi itama
miƙewa tayi tana faɗin “mom na ciki ne?” da eh yumnah ta bata amsa.
trayn ta ɗauka,ƙofar dake kallon dama ta nufa, a hankali ta tura ƙofar bakinta ɗauke da sallama,masha Allah na furta a yayin da nayi arba da katafaren bedroom ɗin data shigo,expensive furniture's ne a cikin shi na alfarma,royal bed ɗin dake ciki kawai abun kallo ne,yasha blanket da bedsheet masu tsadar gaske, bed ɗin a cike yake da pillows, bedroom ɗin ba wani cike yake da kaya ba, bed ne kawai sai nightstand dake ɗauke da bedside lamps sai dressing mirror,sai sofas guda biyu dake can bakin sliding window sai ɗan round table dake tsakiyar su.
Cikin ɗakin ta ƙarasa yayin da take yin sallama, a tsaye ta hango brisster zulaihat bakin window hannunta riƙe da curtains,girgiza kai fa'iza tayi cike da tausayawa ta nufi in da brisster take, sallama ta sake yi dan a tunaninta bata jita ba,kafe garden ɗin dake bayan villa ɗin tayi da ido yayin da hawaye ke sauka daga idanunta, a zahiri kallon shuke shuke dake cikin garden ɗin masu ɗaukar hankali take amma a zahirin gaskiya hankalinta kwata kwata ba'a kan su yake ba,babban tashin hankalin ta a wane hali yanzu aminiyarta take ciki sannan ya rayuwar nainarh zata kasance ba tare da mahaifiyarta ba, da sauri ta juyo jin an dafa kafaɗar ta.
kallon fa'iza dake tsaye a bayanta tayi
“Fa'iza yaushe ki ka shigo?”
“mom yanzu na shigo ina ta ƙwala sallama ba kijini ba, mom dan Allah ki daina sa damuwa a ranki kar wani abun ya same ki, in sha Allah momy zata fito”
ajiyar zuciya ta sauke,hannu fa'iza tasa ta shiga guge mata hawayen dake zuba daga idonta tana sake bata haƙuri, jan hannunta tayi su ka nufi sofas ɗin dake wurin.
Zama su kayi suna fuskantar juna
“mom in sha Allah zata fito, mom kinfi kowa sanin yanke mata hukuncin ɗaurin rai da rai ba shike nuna gaskiya baza tayi halinta ba,ba kuma shi ke nuna ba zata iya fitowa wata rana ba, dan Allah ki kwantar da hankalin ki”
“Nagode fa'iza” shine kawai abun da brisster tace
“mom kinfi ƙarfin haka a waje na fatana dai ki rage damuwar a zuciyar ki, sannan nayi maki Alƙawari mom zan tayaki da Adu'a Allah ya bayyanar da gaskiya”
“Ameen fa'iza”
“sannan mom ina mai baki haƙuri akan abun da mamy tayi maki, bata kyauta ba dan Allah kiyi haƙuri”
murmushi brisster ta saki yarinyar akwai shiga rai ta na matuƙar burgeta
“fa'iza kenan idan da sabo ai yaci ace na saba da hakin mamyn ku, karki damu abun da tayi man kwata kwata bai ɓata man rai ba”
“shikenan mom amma duk da haka ina mai baki haƙuri a madadinta” murmushi brisster ta saki
trayn data shigo ta nufa, ruwa ta tsiyaya mata a cup
“mom gashi kisha, na sa chefs su haɗa maku breakfast dan na san haka ku ka fita bakuci komai ba”
”nagode fa'iza Allah ya biyaki da mafificin Alkairi”
“mom dan Allah ki daina gode man”
“ya zama dole ne fa'iza”
“ni dai dan Allah ki daina gode man, nifa ƴarki ce kuma mom kin san cewa babu godiya tsakanin iyaye da ƴaƴansu” murmushi brisster ta sake saki tana zubama fai'za ido, fa'iza badai iya tsara kalamai masu daɗi ba.
Turo ƙofar bedroom ɗin a kayi, da sauri su ka kai duban su ga ƙofar
a tsaye ya ke ya harɗe hannuwan shi a ƙirji,Army green ɗin shirt ce a jikinshi haɗe da Army trouser wanda ya tsaya mashi iya gwiwa , babban mutum ne da a ƙalla zai kai kimanin shekaru 56 zuwa da 8 a duniya, dogo ne sosai yana da jiki, ƙaƙƙarfa ne na gaske kamar ba dattijo ba, a ido idan ka kalleshi baza kace shi ke da waɗannan shekarun ba,fari ne kyakyawa kallo ɗaya za kayi mashi ka hango kamaninshi da fa'iza da yumnah,da gudu fa'iza ta nufe shi, faɗawa tayi jikinshi
“good morning dady”
murmushi ya saki yana jan kumatunta “har yanzu baki san kin girma ba ko fa'iza?, kina abu sai kace yumnah” ɓata fuska tayi kamar ƙaramar yarinya “dady nice ma yumnah” zuba masu ido brisster tayi tana kallon su baƙaramin birgeta suka yi ba, raba jikin su yayi yana faɗin
“ƙwarai ma kuwa”
cikin ɗakin ya ƙarasa, ƙofar fita fa'iza ta nufa tana faɗin
“mom sai na dawo, dady ka barta ta kwanta ta huta ta gaji” ta faɗa tana jan handle ɗin ƙofa
“na lura fa'iza kin raina ni da yawa” dariya tayi tana jan ƙofar ta fice, murmushi kawai mom tayi tana girgiza kai.
bakin bed dady ya nufa,zama yayi yana zuba ma barrister ido, ɓata fuska tayi kamar zata fashe da kuka ta nufeshi, tana ƙarasowa gabanshi faɗawa tayi jikinshi tayi hugging ɗin shi,hannu biyu yasa ya zagaye bayanta,shafa doguwar sumar kanta ya shiga yi
“Barrister lafiya?”
saukar hawayenta yaji a saman chest ɗin shi, da sauri ya ɗago da fuskar ta yana kallo,hawaye ya gani suna zarya a kumatun ta.
hannu yasa ya shiga share mata su “gaskiya ƙarshen wannan aikin naki ya zo,bazaiyu a riƙa sa man mata kuka ba, dole ki ajiye wannan aikin dama ba so nake ba saboda kin dage kina so ne kawai yasa na barki”
“sir kar kace haka,wannan aikin da nake ban san iya adadin ladar da nake samu ba, zaka so ka zama sanadiyyar yankewar wannan ladar?”
“amma kullum sai su riƙa sa man ke kuka, bana jin daɗin hakan?”
“ba laifin su bane kukan ne dole nayi, ina ji ina gani na kasa taimakon Aminiyata kotu ta yanke mata hukunci ba tare da ta aikata laifin ba”
“karki damu,in sha Allah komai zai daidaita yanke mata hukuncin ai ba yana nufin shikenan ba,ki dai na kuka kinji bana so”
wasu hawayen ne su ka sake zubuwa, ɗan bubbuga bayanta ya shigayi “ya isa haka, idan ba nima nawa hawayen ki ke son gani ba”
hannu tasa tana share hawayen “na daina”
“yawwa ko ke fa,ina ita yarinya Asma'un?”
“dama ina so na nemi wata Alfarma a wurin ka”
“Alfarma kuma?”
“Eh,dangin mahaifiyarta sun so tafiya da ita amma nace A'a saboda karatunta zata zauna anan in yaso sai su riƙa tafiya tare da yumnah,kuma dai gaskiya ina son ta zauna a tare da ni sai tafi samun kulawa sama da can, zata iya zama nan ba matsala?” jinjina kai yayi
“dama makarantar su ɗaya da yumnah ne?”
“eh school ɗin su ɗaya”
“shikenan ba damuwa, zata iya zama a nan ɗin ai kema tamkar mahaifiya ki ke a gareta”
“haka ne, nagode sosai Allah yasa da Alkairi”
ɗan ɗaure fuska yayi
“ni ki ke ma godiya zulaihat?”
“eh mana, idan an kyautata maka sai ka gode ai ba wani abu bane”
“to bana so, nan ɗin gidan ki ne kina da ikon ajiye duk wanda ki ke so, idan kuma ki ka sake godeman to ni da ke ne” murmushi tayi tana kwantar da kanta saman shoulder ɗin shi
“zuwa anjima ina so zanje prison dan na duba jikinta,his excellency yanke jiki fa tayi ta faɗi na shiga tashin hankali matuƙa a lokacin”
“Allah ya kaimu anjimar sai mu tafi tare, Allah ya bata lafiya”
“Ameen ya Allah”
𝑄𝑢𝑒𝑒𝑛 𝐾𝑎𝑖𝑛𝑒𝑟𝑡..... ✍💫
Baƙar motar ce ƙirar benz ta tukaro gate ɗin estate ɗin,sanin halin mamallakiyar motar ne yasa tun kafin motar ta ƙaraso sojojin dake gadin gate ɗin su kayi hanzarin buɗe mata ƙofa,babu ɓata lokaci ta danna kan hancin motar zuwa ciki,ɗaya daga cikin gidajen motar ta nufa,a parking space ɗin duplex ɗin data nufa tayi parking,dai daita parking tayi, kafin aka buɗe motar ƙafarta ta zuro kafin ta fito gaba ɗayanta,iska ta shaƙa ta fesar, hannu ta zura ta ɗauko hand bag ɗinta, main entrance ɗin duplex ɗin ta nufa bayan ta rufe motar, sai ya mutse fuska take alamar ta gaji.
Wani madanni ta danna jikin ƙofar, nan take ƙofar ta buɗe, ciki ta kunna kai,mash Allah na furta a yayin da nayi arba da haɗaɗɗen parlorn data shigo, komai na cikin shi ya kasance light brown, faɗa maku haɗuwa da tsaruwar parlorn ɓata lokaci ne,babu kowa a parlorn sai mai aiki dake ƴan goge goge,jin ƙarar buɗe ƙofa ne yasa mai aikin ɗagowa, ganin wacce ta shigo ne yasa ta nufota da sauri,hannu ta miƙa da nufin amsar jakar dake hannunta tana faɗin
“good Afternoon ma” wani ɗan iskan kallo mai haɗe da harara ta watsa ma mai aikin, saurin sadda kai ƙasa mai aikin tayi tana ja da baya,tsaki taja tana nufar stairs case dake parlorn.
da kallo kawai mai aikin ta bita har ta ɓacce ma ganin ta,taɓe baki tayi tana komawa kan aikin dake gabanta, a bakin ƙofar wani ɗaki ta tsaya, tura ƙofar tayi ta shiga,wani haɗaɗeb bedroom ne ta shigo komai na cikin shi ɗan dai dai babu haya niya, ciki ta ƙarasa tana kiran sunan
“Aunty laatifa! am home where are u” matashirya mata ta hango zaune kan study chair yayin da laptop ke a saman desk tana operating.
“Aunty nah sarkin aiki,a gidan ma baki huta ba, gaskiya mijinki ya shiga shiga uku na san a daren ku ma nafarko kwana za kiyi kina aiki, shiyyasa momy ke ce maki agogo sarkin aiki”
juyowa tayi masha Allah na faɗa da ganin wannan madarar kyan, laatifa kyakyawa ce ajin farko,riga da wando ne a jikinta masu taushi, kanta babu ɗan kwali tayi parking gashinta a tsakiyar kai, medical glass ɗin dake idonta ta cire.
“ƙanwata idan ban yi aiki ba mi ki ke so nayi?”
“gaskiya kina aje wa kina hutawa”
“shikenan, ya gajiyar aiki?” ya mutse fuska tayi yayin da take samun wuri bakin bed ta zauna
“aiki babu daɗi” murmushi laatifa ta saki wanda ya ƙarama kyakyawar fuskarta kyau
“gaskiya Balqis kin cika raki, miye abun gajiya a wannan aikin ke da kina bayan mota kina shan iskar Ac”
“haka za kice mana tunda ke kin saba, duk ranar dana sha court za kice haka”
“ba wai zan ce ba haka ne ma, kawai dai kin cika raki”
“shikenan naji ina alƙawari na?”
“yanzun nan na gama tura mashi saƙo ta email kin san baya ɗaukar kira ba tare da ka fara tura mashi saƙo ba”
“haka ne, amma ai ke naga kuna waya”
“wannan ai shi ke kirana, amma duk lokacin da ni nake son magana da shi sai na fara tura mashi saƙo tukun” taɓe baki Balqis tayi
“shi dai komai nashi na daban ne”
“classic boy ake faɗa maki dole komai nashi ya kasance unique,ke dai kawai ki dage da Adu'a dan akwai aiki a gabanki”
“ni kaina na sani Aunty laatifa abun har tsoro yake bani”
“karki damu nima zan tayaki da adu'a ”
“in sha Allah, bari na tafi ɗakin momy bata san na dawo ba, nan na fara shigowa”
“ok anjima zaki bani labarin yanda ƙarar ta kasance”
“kin ma tuna man, wallahi dady ya ganni ba kiga harar da ya watsa man ba kamar ƴan hanjin ciki na su faɗo” dafe ƙirji laatifa tayi
“nashiga uku!! dan Allah da gaske ki ke”laatifa ta faɗa da tsantsar tashin hankali
“wallahi kuwa na san dole yaji ba'asin abun da ya kaini, amma zanyi duk yanda zanyi ganin bai gane ke ki ka tura ni ba”
“yawwa dan Allah kice ra'ayi ki ka yi ba ni nace kije ba”
“in sha Allah karki damu”
“yawwa na gode” ƙofar fita Balqis ɗin ta nufa tana ƙara jaddadamata karta damu.
zama tayi bakin bed dafe kanta“ya Allah” ta furta,da alama hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba jin dadyn su yaga Balqis.
Balqis tana fita daga ɗakin wani ɗan corridor ta nufa, wani ɗan madaidaicin parlor ta shiga,a zaune take saman sofa mai mazaunin mutum biyu les ne a jikinta ɗinkin half bubu da zani, hannunta da wuyanta sun sha adon zinari, wayace kare a kunenta da alama waya take
“lamari ai baiyi daɗi ba, in sha Allah anjima idan Barrister ya dawo zan tambaye shi naje nayi mata jaje ai abun ayi jaje ne” murmushi Balqis ta saki tana ƙarasawa cikin parlor.
faɗawa tayi saman jikinta“momy na dawo” da sauri ta janye wayar daga kunenta “ja'irar banza kin girma amma baki san kin girma ba, ba ki gani waya nake, karya ni ki ke son yi?” tashi tayi zaune tana turo baki“momy daga nayi kewarki zaki rufe ni da faɗa”
“an rufeki da faɗa, dan gidan ku haka ake kewa kina shirin karya ni”
“ke momy haka ki ke daga abun arziƙi sai ki rufe mutum da faɗa na san da dady ne bazai ce man komai ba”
"ai shi ki ka ce ƙashin shi ƙwari ne gare shi” ficewa Balqis ɗin tayi daga parlorn tana gungunai.
Mai da wayar tayi a kunne “kina jina da wannan ja'irar yarinyar tana neman karya ni”bana jin mi na cikin wayar ke faɗa
“to shikenan idan Allah yasa mun haɗu anjimar to shikenan, idan kuma bamu haɗu ba sai ranar friday kenan idan mun haɗu a part ɗin Abbah” jinjina kai tayi kafin daga bisa ni su kayi sallama.
*UNITED STATE*
_*Las Vegas (Nevada)*_
_*Nailarh Racing Track (N.R.T)*_
Ƙaton track ne gari guda wanda girmanshi zai kai girman wani babban ƙauyen,kallo ɗaya zaka ma wurin ka hango tsirarar dukiyar da aka kashe wajen gina shi,
ta ko ina ka duba mutane ne zazzaune a saman chairs gaba ɗaya hankalin su naga wasan da ake gabatarwa,kowa burinshi nashi yayi nasara,duka mutanen dake wurin suna sanye ne da polo shirt white color wacce a gabanta a kayi rubutu da ɓakin fenti in da aka rubuta QUEEN da manya haruffa daga saman shirt ɗin logo ne na sunan center ɗin ( N R T) sai p_cap da hat wanda suma aka rubuta QUEEN a jikinsu kamar na shirt ɗin,maza ke sanye da p_cap yayin da mata ke sanye da hat wacce aka yi mata kwalliya da gashin tsintsaye a samanta, Al'adar wurin wasan ce duk wanda zai shiga sai an bashi wannan shirt da cap ya sa wanda kyauta ce daga mamallakiyar wurin wasan.
dawakai ne kyawawan gaske ke gudu a tsakiyar filin,yayin da mamallakansu ke saman su jikin su sai salƙi yake yana ɗaukar ido,color uku ne dawakan wasu brown yayin da wasu su ka kasance baƙaƙe doki ɗaya ne a wurin ya kasance white color,daga yanayin tsarin dokin zaka san na musamman ne, a jere su ka fara gudun,cikin ƙwarewa da karsashi dawakan ke gudun abun gwanin ban sha'awa,abun dai sai wanda ya gani,rabuwa su ka fara yi da junan su, dawakai uku ne su kayi gaba yayin da su ka bar sauran a baya harda wannan farin dokin yama fisu yin baya sosai sama da sauran dawa kan,sosai su ke gudu dan kaiwa ga matsaya,miƙewa tsaye mutane su ka fara yi da alama dawakan nan gudu uku na daban ne, mutane na da buri a kan su.
Wasa fa ya fara ɗaukar zafi dawakan kansu su ukun sun rabu da juna yanzu biyu ne a gaba ɗayan a baya.
“da alama dai yau tarihin N R T zai canza, ban taɓa ganin wasa irin wannan ba” cewar wani bature dake zaune cikin ƴan kallo, murmushi gefen baki mace dake gefen shi ta saki tana faɗin
“ba abu bane mai yuwuwa canza tarihin N R T cikin sauƙi, a ko wane lokaci da sabon salo take zuwa, kana tunanin wannan baya bayan da tayi babu wata a ƙasa?” taɓe baki yayi yana ɗaga kafaɗa
“i don think,tazarar tayi yawa duba kiga in da su Ryder su ke kalli in da king yake”murmushi matar ta saki
“dear sai kace yau ka fara zuwa kallon wasan N R T”
“ba yau na fara zuwa ba, but wasan yau ne ban taɓa ganin irinshi ba”
“to ka zuba ido za kace na faɗa maka”
“okay” ya faɗa yana mai da glass ɗin shi daya cire.
ran wani magidanci ne daga cikin ƴan kallo ya fara ɓaci,sign matar wannan baturen tayi mashi, duban shi ya kai ga mata da majin
“bazan taɓa ƙyale Anthony ba idan har kuɗina su ka lalace” ya faɗa da alamar ranshi ya ɓaci“but why?” matar shi ta tambaya
“babu alamun zanyi nasara,kin kuma san dama ba da san raina na zuba kuɗi na a wasan nan ba, idan har kuɗina su ka salwanta bazan ƙyale shi ba”
“just bcox of five hundred thousand dollars kake wannan maganar akan brother nah?”
kallonta yayi da mamaki“its not a money?”
“no it's money, but ai kafi ƙarfin su, kuma banyi tunanin zaka iya furta wannan maganar akan Anthony ba”
“it's not my concern,kuɗina kawai na sani”
“sai ka bari idan kaga ba kayi nasara ba sai ka faɗi duk abun da zaka faɗa,ai har yanzu wasan ake”
murmushi takaici mutumin ya saki
“oh wai kina nufin har yanzu kuna da sa rai a wannan wasan,ƙazamin tunani kawai” ya faɗa yana kauda kanshi gefe, haɗa ido su kayi da wannan matar da mijinta, a tare su ka sakar mashi murmushi suna ɗaga mashi hannu, shima hannun ya ɗaga masu yana maida kanshi ga wasan.
Murmushi matar tayi“mi na faɗa maka kowa ya san cewa canza tarihin N R T ba abau bane mai sauƙi, ka dai ji wance magidanci ya saduda ta ƴan kuɗaɗen shi kawai yake” ta faɗa tana sakin murmushi, murmushi shima mijin nata yayi yana jinjina kai da faɗin“na tabbata...
_*Episode 7_8*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
_____________________________
Murmushi matar tayi“mi na faɗa maka kowa ya san cewa canza tarihin N R T ba abau bane mai sauƙi, ka dai ji wance magidanci ya saduda ta ƴan kuɗaɗen shi kawai yake” ta faɗa tana sakin murmushi, murmushi shima mijin nata yayi yana jinjina kai da faɗin“na tabbata”
mai da hankalin su su kayi akan wasan,wasan ne ya fara canza salo kamar walƙiya sai ga dokin dake baya sama da ko wane doki ya zama shine a tsakiyar dawakai biyun dake gaba, kamar a mafarki masu kallon wasan ke kallon ikon Allah,tashi wannan magidanci yayi yana jan tsaki ya kalli matar shi
“kin dai ji abun dana faɗa maki sisi na ban yarda tayi ciwo ba” yana gama faɗa ya bar wurin gaba ɗaya, taɓe baki matar tayi ita har a lokacin ba taga wani alamar rashin nasara ba tunda dai ba'a gama wasan ba.
fita dokin yayi daga cikin jerin dawakai biyun daya shiga ya zama shine ke biye da dokin dake gaba sai dai akwai ƴar tazara a tsakaninsu,sosai dawakan ke gudu cike da karsashi suna tunkarar matsayar wasan in da ya kasance nan ne ƙarshe duk wanda ya riga isa shine ya lashe gasara.
hankalin mutane dake sa ran cin gasar ne yayi matuƙar tashi, tuni zufa ta shiga wanke wasu daga cikin su saboda maƙudan kuɗin da su ka zuba wanda suke ganin suna gab da yin asara,seconds Biyar ya rage a kammala wasan,bai wuci taku kaɗan ya ragema dokin dake gaba ya isa matsayar wasan, kamar walƙiya wannan farin dokin ya gita ta gabanshi ya riga shi isa matsayar, da sauri ma hayin dokin yaci birki rai a ɓace ga ci yana gani amma ya rasa.
Ihu da sowa ne ya fara tashi a wurin wasan haɗe da kiɗe kiɗe, a fusace ɗai ɗai kun mutane su ka fara tashi suna barin wurin wasan,birki dokin yaci cike da kuzari mamallakin dokin ya sauko, da sauri wasu matasan ƴan mata su biyar suna sanye da riga da skirt iya gwiwar su, rigar white color yayin da skirt ɗin ya kasance black color aƙalla kowace a cikin su zata kai kimanin shekara 28 zuwa 30,cikin filed ɗin su ka nufa a gaban wannan dokin su ka tsaya ɗaya na riƙe da water bottle yayin da wata ke riƙe da ɗan ƙaramin towel wacce tafi kowa girma a cikin su ce take goye da backpack sauran biyu babu komai a hannun su sai sakin murmushi su ke, wani matashi sauarayi ne ya amshi dokin, helmet ɗin dake kanta wacce aka rubuta Queen a jikinta ta zame tabarakallahu ahsanul kaliƙin na furta da ganin wannan maƙurara kyan.
fara ce tas doguwa kyakyawar gaske wacce idan akace kyau to fa anazuwa kanta an rufe babin kyau,tana da idanuwa masu matuƙar jan hankali launin Acme white grey sai sheƙi su ke ga zira ziran eye lashes ɗinta da su ka ƙara ƙawata su,tana da siraran laɓɓa launin light pink masu matuƙar taushi tana da ɗan tsayin fuska hancinta a tsaye yake kem,tana da cikar gashin gira sai dai ba sosai ba,kanta ta ɗan girgiza yayin da take zame ɗan ƙaramin ribbon ɗin data ɗaure gashin kanta nan take wavy hair ɗinta launin light golding brown ta tarwatse a gadon bayanta ,tana da shape mai matuƙar ɗaukar hankali skin ɗinta sai sheƙi take tana salƙi kamar hasken rana bai taɓa raɓarta ba.
kissing neck ɗin dokin tayi tana ɗan sakin murmushin gefen baki har sai da dimples ɗinta su ka lotsa sosai murmushin ya ƙarama kyakyawar fuskarta kyau
“madam water”ɗaya daga cikin matan ta faɗa tana miƙa mata water bottle ɗin dake hanunta mai kyan gaske wacce a jikinta aka rubuta Queen, ya mutse fuska tayi ba tare da ta ko kalli in da matar take ba,wacce ke riƙe da towel a hanunta ce ta matsa kusa da ita daddaɗan ƙamshin turaren ta ne ya daki hancin matar har sai da ta lumshe ido duk da zufar da tayi haka bai hana dawwamamman ƙamshinta fita ba, a hankali ta shiga goge mata zufar da tayi,jefi jefi mutane su ka shiga ƙarasowa cikin field ɗin suna mata congrat yayin da take ya mutse masu fuska ba tare da ta amsa masu ba hakan bai dame su ba saboda sanin halinta sunma samu sa'a yau da har ta tsaya harma take yamutse masu fuska.
barin wurin matashi yayi da dokin, ɗaga ma dokin hannu ta shiga yi tana faɗin“ i miss u” murmushi matan su ka saki,fly kiss ta ma dokin tana sakin murmushi,bata bar wurin ba har sai da ta daina ganin dokin tukun ta bar wurin yayin da matan ke biye da ita har gaban wasu motoci guda bakwai,guda shidda rang robbers ne yayinda su ka saka wata farar Rolls Royce tsakiyar su sai ɗaukar ido take,body guards ne tsaye a bakin motocin Aƙalla za su kai su biyar ban da drivers ɗin da da su kayo driving motocin,cikin girmama su ka shiga gaishe da ita suna tayata murnar lashe wasan, babu wanda ya samu arziƙin data amsa mashi sai ma nufar wannan fara rolls royce ɗin dake tsakiyar motocin tayi, da sauri ɗaya daga cikin su ya buɗe mata back seat ta shiga,komawa su kayi cikin motocin harda wannan matan,a jere su ka hau wani dogon titi a cikin wurin wasan.
A kishingiɗe take a cikin motar ta lumshe idanunta yayin da sanyin Ac ke ratsata, tafiya mai ɗan nisa su kayi kafin su ka nufo wani katafaren gate ga wasu irin jibga jibgan security guard a bakin shi, horn driver dake gaba yayi, babu ɓata lokaci security guard ɗin su ka buɗe masu gate,da gudu motocin su ka kunna kai ciki security guard ne ke kai kawo ta ko ina na wurin, titi ne su ka sake miƙewa shantal, wani ɗan ƙaramin gate na ɓakin ƙarfe wanda ya kasance shara shara kana iya hange ciki su ka nufo, wani remote driver dake gaba ya danna nan take gate ɗin ya buɗe ciki su ka kutsa kai ciki.
masha Allah na furta da ganin irin haɗuwar wurin ,ƙatafaren luxury skyscraper ne iya ganinka, ta ko ina ka kallah a jikin ginin gilasai ne masu matuƙar ɗaukar ido A ƙalla yana da sassa guda shidda,harabar gidan kanta abun kallo ce lion water fall ne a tsakiyar gidan yayin da yake fitar da ruwa da styel daban daban, security guard ne ke kai kawo a ko ina na harabar gidan.
A bakin skyscraper ɗin su kayi parking da sauri ɗaya daga cikin security guard ɗin ya fito ya buɗe mata car door,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fitowa,gaba ɗaya matan gaban motar da take ciki su ka zo su ka tsaya, a hankali ta zuro ƙarta kafin ta fito gaba ɗaya, security guard ɗin dake kai kawo ne su ka shiga rissinawa suna gaishe da ita, hannu kawai ta ɗaga masu kafin a hanzarce ta nufi gidan matan nan na take mata baya,a bakin main entrance ɗin gidan suka tsaya,wata irin haɗaɗiyar ƙoface ta glass,sai ta fuskarta tayi a jikin wata na'ura dake manne jikin ƙofar wacce nake kyautata zaton face ID ne magana na'urar ta fara cikin harshen turanci
“welcome back home miss NAILARH”
zugewa ƙofar ta shigayi, kutsa kai su kayi ciki, wani katafaren parlorn ne su ka shigo,painting cikin shi sliver glod ne, an ƙawatashi da manya manyan sofas jigunannun gaske masu matuƙar taushi da daɗin zama set huɗu sai throw pillows dake kan ko wace sofa, daga tsakiyar parlorn round glass table ne an jera flower vase masu matuƙar kyau, daga saman ceiling ɗin ginin crystal chandeliers ne golding color masu girman gaske an ƙawata su da kwalliya, sai faskekiyar flat creen tv mai matuƙar girma ta mamaye kusan rabin bangon da take sai kayan sauti dake gefe da gefen tv, sparkling floor lamps ne ajiye a ƙasa suna bada haske mai launika daban daban, ga dogayen curtains wanda aka ƙawata da zanen furanni kewaye da parlorn an zuge su,idan ka kalli ƙasan parlorn wanda ya kasance na glass wasu irin kifaye ne masu launika a jikin su suke shawagi.
komai na cikin parlorn golding color ne hatta stairs case ɗin dake ciki,A ƙalla floor ɗin na ɗauke da parlor biyar harda wannan wanda ya kasance shine babba a cikin su kuma yake a tsakiyar su, daga cikin parlorn zaka iya hangen sauran falukan dake floor ɗin,masu karatu ba ƙaramar dukiya aka kashe a wajen haɗa wannan parlorn ba idan nace sai na fayyace maku komai dake cikin shi to tabbas anan book one zai ƙare,kawai ku ida ƙissma sauran a zuciyar ku.
ma'aikata ne ke kai komo a cikin parlorn, zubewa su ka shigayi akan gwiwowunsu suna kai gaisuwa gareta, ko kallon in da suke ba tayi ba.
glass elevator su ka nufa,ɗan yatsanta tasa a jikin na'ura dake jikin ƙofar elevator nan take ƙofar ta buɗe, ciki ta shiga tana lumshe idanunta alamar gajiya,mara mata baya ma'aikatan su kayi,ɗaya daga cikin ma'aikatan ce ta danna wasu madanni dake ɗauke da nombobi a jikin su,ƙofarce ta shiga zuge, sama elevator tayi da su, daga ta ciki zaka iya hangen manya manyan parlor kan da suke wuce masu matuƙar kyau wanda tsayawa fayyace su har littafin ya ƙare ba'a gama faɗar kyawu da haɗuwar su ba, tsayawa elevator yayi da alama sun kawo in da za su tsaya, ƙofar ce ta shiga zugewa,sai data gama zugewa tas tukun tasa kai ta fice ma'aikatan na biye da ita kamar wasu jela.
nan ma wani katafaren parlorn ne su ka shigo wanda yafi na farkon haɗuwa sai dai bai kaishi girma ba,ma'aikatan ne nan ma ke kai kawo, take su ka shiga zubewa ƙasa suna gaishe da ita, hannu kawai ta ɗaga masu yayin da take yin gaba, a bakin wata katafariyar ƙofa su ka dakata, ɗaya daga cikin matan ce tayi saurin miƙa mata wayarta dake hannunta, amsa tayi yayin da take ɗaura tafin hanunta saman na'urar dake jikin ƙofar, zanen hannunta ne ya fito a jikin na'urar ,scanning hannunta na'urar ta shigayi na tsawan secon biyar kafin na'urar ta fara magana kamar ta ƙofar da su ka fara shigowa yayin da ƙofar ke zugewa.
sai da ƙofar ta gama zugewa tas tukun ta kunna kai zuwa ciki yayin da matan guda biyu ke biye da ita sauran su ka kama gaban su, wacce ke ɗauke da backpack ce ta bi bayanta sai ɗaya wacce take riƙe da towel ɗin data goge mata jiki.
wani irin katafaren bedroom su ka shigo a ƙalla girman shi ya isa ayi ɗan ƙaramin plat house saboda girma da faɗin shi, bedroom ɗin yana ɗauke da king size bed light golding, gadon na shimfiɗe da tattausan bedsheet da ƙaton blanket mai azabebben taushi ga jerin pillows wanda su ka kusa cinye kwata gadon,
gefe da gefen gadon nightstand ne mai ɗauke bed sides lamps daga gaban gadon ottoman table ne mai ɗauke da drawer chest a jikin shi daga saman shi anyi mashi kwalliya da wasu stones masu sheƙi an mamman a jikin shi.
daga ƙasan gadon wani haɗaɗɗe rug ne mai gashi gashi a jikin shi tsabar taushin shi har bacci mutum zai iya a kanshi ba tare da ya fahimci ba'a katifa yake ba,idan ka kalli saman ɗakin wani irin ƙaton chandeliers ne,daga hannun dama na ɗakin glass sliding door ce wanda nan ma wani bedroom ɗin ne sai dai komai na cikin shi white color ne, daga ɗayan ɓangaren kuma wani haɗaɗen stairs case ne can ma saman wani bedroom ɗin ne sai dai bai kai wannan dana kusa da shi girma ba, daga ɓangaren haggun ɗakin wasu ƙofofi ne guda uku a jere ɗaya bathroom sai spa and saloon wanda yake haɗe massege spa sai ɗaya ƙofar dressing room ne wanda idan ka shiga cikin shi zaka ɗauka boutique ne.
wacce ke goye da back pack ɗin ce ta nufi laundry room,ɗurƙusawa ɗayar tayi a gabanta takalamin ƙafarta ta shiga cire mata, zama tayi saman ɗan stool hakan ya bata dama wurin cire mata takalmin, bayan data gama cire takalmin,sama nailarh ta ɗaga hannunta hakan yaba matar damar cire mata rigar dake jikinta tayi ta barta daga ita sai bra ta ajiye gefe kafin ta koma kan wandon, wandon shima zame mata shi tayi shantala shantalan cinyoyinta ne su ka bayyana farare tas da su sai sheƙi su ke kai kace haske rana bai taɓa ratsasu ba,kwashe kayan matar tayi ta nufi laundry room da su,a tare su ka fito daga laundry room ɗin ita da wacce ta fara shiga sallama su kayi mata su ka fice daga ɗakin.
A kasalance ta shiga taka ƙafafunta tana nufar ƙofar toilet, tafiya take kamar bata son gaka ƙasa tana tafiya ko ina na jikinta na juyawa musamman ƙugunta da zanen rose flower na tattoo ya ƙarama fatar bayanta kyau,tun kafin ta ƙaraso bakin ƙofar ta shiga zugewa kutsa kai tayi ciki,wani irin bathroom mai girman gaske komai na cikin shi expensive ne,harda silver bed mai ɗauke da rober mattress mai haɗe da pillow sai daga jikin bangon toilet ɗin glass drawer ce mai girman gaske an rarrabata gida gida wanda bakomai ne a cikinta ba sai tarin shower gels,soaps,shampoos, towels, bathrobes,sponges da flip flops.
ƙofa biyu ce a toilet ɗin da wadda ta shigo sai wata dake can ɗayan ɓan garen , silver bed ɗin ta nufa kwanciya tayi rub da ciki tana sauke ajiyar zuciya,wasu irin abubuwa ne a jikin ɗayar ƙofar masu kama da bulbs haske su ka shiga kawowa suna fitar da wani irin sauti can kuma su ka daina suna sanar da isowar lolah da larah,a hankali ta furta open ba tare da ta ɗago ba, zugewa ƙofar ta shiga yi, wasu matan turawa ne su ka shigo manya da su kamar ƴan wrestling,baƙin mini skirt ne a jikin su tare da farar shirt ajikin rigunan su an rubata sunayen su da wani irin style, haka shigar ma'aikatan gidan take.
in da take su ka ƙaraso gaishe da ita su kayi suna ɗan rissinawa,bata amsa masu ba hakan bai dame su ba idan da sabo sun saba da halin uwar gidan ta su,lolah ce ta nufi glass drawer ɗin nan, buɗewa tayi ta ɗauko shower gel tare da soap da shampoo da sponge,a saman wani ɗan table mai ƙafafu ta ɗaura, maida ƙofar drawer tayi ta rufe turo table ɗin tayi zuwa gaban bed ɗin, ɗaukar shampoo larah tayi, buɗe marfin tayi ta shiga tsiyayama Nailarh shi a kai, bayan data gama ne tashiga cuɗa mata kan sai data tabbatar ya wanku tukun ta jawo hand shower ta shiga wanke mata kan, bayan data gama ne ta ɗauki shower gel ta shiga zubawa a ko ina na jikin Nailarh,sponge sock lolah ta saka a hannun ta larah na gama zuba shower gel ɗin ta shiga mulka mata mashi a ko ina na jikinta, ko motsi Nailarh ba tayi kamar matatta su ke juyata yanda su ke so dan su wanko ko ina na jikinta.
sangarta da gata ne yasa Nailarh ko wanka bata ma kanta ba wai dan bata iya ba isa ce kawai da lalacewa tasa bata iya yi da kanta musammusam ta ajiye lolah da larah dan su riƙa yi mata wanka wanda aikin su ke nan a gidan, daga wankan ta da yi mata massege sai gyaran jiki babu abun da su ke iya aikin su kenan.
ta ɗauki tsawan lokaci tana cuɗa mata jikinta sai data tabbatar ko ina na jikinta ya wanku tukun larah ta jawo hand shower ta shiga wanke mata jikin bayan data gama ne ta ɗauko hairdryer ta shiga busar mata da gashin kanta bayan data kammala busar mata da kan ta nufi glass drawer ɗin nan ta ɗauko bathrobe da flip flops ta dawo a bakin bed ɗin ta ajiye mata, a kasalance Nailarh ta sauko daga saman bed ɗin,flip flops ɗin ta zura a ƙafarta, miƙa mata bathrobe ɗin tayi , ƙarɓa tayi da kanta ta zura kafin ta cire hook ɗin bra ɗin dake jikinta ta ciro a ƙasa ta yarda ita kafin ta warware igiyar pant ɗin shima nan ƙasa ta sake shi, igiyar bathrobe ɗin ta ɗaure ƙofar fita ta nufa ba tare da ta ko kalli ɗaya daga cikin su ba.
bra da pant ɗin lolah ta kwashe ta nufi dustbin ta saka Nailarh tana da wata ɗabi'a ta rashin maimaita sutura idan har kaga ta maimaita sutura to ba ƙaramin sonta take ba bra da pant dama su daga idan ta cire su to sun zama wasted bata ƙara amfani da su,gyra toilet ɗin su kayi su ka maida komai mazaunin shi sannan su ka wanke toilet ɗin duk da ba datti yayi ba bayan da su ka gama ƙofar da su ka shigo su ka nufa tun kafin su isa ƙofar ta buɗe alamar an basu izinin fita, ficewa su kayi.
Nailarh tana fita daga toilet ɗin wannan sliding glass door ɗin ta nufa tana isowa ƙofar na buɗewa, ciki ta kutsa kai sai wani lumshe ido take, nan ma bedroom ne komai na cikin shi white color ne , babu wata hayaniya a cikin shi bed ne sai nightstand dake ɗauke da bedside lamps sai rug mai taushi dake shimfiɗe a ƙasa sai chaise lounge chair dake bakin wata ƙatuwar glass sliding door wacce da an buɗeta zata sadaka da ƙyataccen swimming pool wand kusan haɗe yake da ɗakin ƙofar ce kawai ta raba su sai ruwan da suke a kewaye daga bakin swimming pool ɗin lounger chairs ne guda biyu suna fuskantar juna sai daga can ɗan nesa da su ball chair ce daga gabanta ɗan madaidaicin glass table ne.
nightstand ɗin ta nufa ear phone ɗin dake ajiye ta ɗauka tare da eye mask,bed ɗin ta dawo a kune ta sa ear phone ɗin kafin ta rufe idonta da mask ɗin, faɗawa tayi saman bed ɗin ta ɗaura kanta saman pillow tana saka ɗaya tsakankanin cinyoyinta yayin da ta rungume ɗaya a haka bacci yayi awan gaba da ita yayin da waƙar data kunna a ear phone take ratsa ƙwaƙwalwarta, Al'adarta ce bacci tana sauraron sauti.
_*ABUJA . NIGERIA*_
_*G J I ESTATE*_
momy da laatifa ne zaune saman sofa da alama fita za su yi,momy ta ɗau wankan swiss lace maroon color ta yafa mayafi saman kanta, wayace kare a kunenta da alama waya take laatifa na daga gefenta zaune saman sofa mai mazaunin mutum ɗaya ta ɗau wankan black abaya tayi rolling da gyalenta simple make_up ne a fuskarta sai medical glass ɗinta dake ƙarama kyakyawar fuskarta kyau,wayar tace riƙe a hanunta tana aikin latsawa, janye wayar momy tayi daga kunenta tana ɗan jan tsaki
“du kace zaka fita tare da Balqis sai ta ɓata maka lokaci,gaskiya tafiya zanyi na barku ni driver ya kaini idan ta gama shiriritar kun ta ho”
momy ta faɗa tana miƙewa tsaye ta ɗauki hand bag ɗinta, tashi laatifa tayi itama tana ɗaukar hand bag ɗin ta “baza ki tafi ki barni ba momy, tare zamu tafi ita driver ya kaita
“gani nan bama sai an tafi an barni ba” Balqis ta faɗa yayin da take taka stairs case tana nufo parlorn, Abaya ce a jikinta tayi rolling gyalen kamar yanda laatifa tayi tana riƙe da hand bag a hannunta fuskarta tasha uban make_up ba ƙaramin kyau tayi ba.
harara momy ta watsa mata tana nufar ƙofar fita daga parlorn, murmushi Balqis ta saki yayin da ta ƙarasowa cikin parlorn, bin bayan momy su kayi,a parking space su ka sameta har ta buɗe back seat na wata ɓakar Acura ta shiga,ƙarasowa su kayi laatifa ta shiga driver seat yayin da Balqis ta buɗe front seat kusa da laatifa ta shiga, babu ɓata lokaci laatifa tayi ma motar key haɗi da reverse, cikin Estate ɗin su ka nufa tafiya su kayi mai ɗan nisa, parking space ɗin gidan dady su ka nufa, parking laatifa tayi haɗi da kashe motar, momy ta fara fitowa sannan sai Balqis, momy bata tsaya jiran su ba ta nufi main entrance ɗin villa ɗin,fitowa laatifa tayi a tare su ka jera zuwa entrance ɗin a lokacin da su ka ƙaraso har ƙofar ta buɗe alamar an basu izinin shiga.
a tare su ka kutsa kai, babu kowa a parlorn sai jefi jefin ma'aikata dake kai kawo, gaishe da su su ka shiga yi cikin kulawa momy da laatifa su ka shiga amasawa yayin da Balqis ko kallon banza ba su isheta ba, glass elevator dake parlorn ta ɓangaren mom su ka nufa,laatifa ta danna nombobin dake jikin elevator ɗin,zugewa ƙofar tayi, momy ta fara shiga kafin su ka bi bayanta rufewa ƙofar tayi elevator tayi sama da su.
ba su samu kowa a main parlorn mom ba hakan yasa su ka nufi ɗayan parlorn,yumnah da fa'iza su ka samu zaune a parlorn kowacce ta tasa waya a gaba sai aikin latsawa take ba su jima da dawowa daga prison ba duba jikin mahaifiyar nainarh, bakin su ɗauke da sallama su ka ƙarasa ciki, ɗagowa su kayi suna amsa masu sallamar da gudu yumnah ta taso ta nufi momy faɗawa tayi jikinta tana faɗin oyoyo, murmushi momy ta saki tana shafa bayanta.
“sannu da zuwa momy, ina wuni , yanzu mom ta shiga ciki”
“lafiya lau Alhmdllh ya hutu” da Alhmdllh yumnah ta amsa yayin da take raba jikin su gaishe da momy fa'iza tayi cikin kulawa momy ta amasa mata tana faɗin
“yan hutu, shine har yau banga ƙafarku ba ko” sunnar dai fa'iza tayi tana sakin murmushi
yumnah da sauri ta nufi laatifa buɗe mata hannuwa laatifa tayi tana sakar mata murmushi da sauri ta ƙarasa gabanta faɗawa tayi jikinta tana faɗin
“nayi missing ɗinki sosai Aunty laatifa” murmushi laatifa tayi tana shafa bayanta
“nima nayi missing ɗinki, ya hutu”
“hutu ya kusa ƙarewa” yumnah ta faɗa yayin da suke raba jikin su, taɓe fuska Balqis tayi tana nufar ƙofar bedroom ɗin mom yayin da take faɗin
“ni bari nayi ciki tunda babu wanda yayi missing ɗin na dama banyi na mutum ba” dariya gaba ɗayan su ka saki saboda sun san bakomai yasa Balqis faɗin haka sai tsabar kishi saboda babu wanda yayi mata oyoyo
“Aunty Balqis ai ni mun haɗu a court shiyyasa ban yi maki oyoyo ba” yumnah ta faɗa, murmushi fa'iza ta tayi tana faɗin “ke nan dai wannan faɗan dani ake, to Allah ya huci zuciyarki ƴar uwa nayi kewarki ya ki ke”
ya mutse fuska Balqis tayi tana faɗin “lafiya” dariya gaba ɗayan su suka saki ganin yanda ta amsa bayan abun da take so kenan, girgiza kai momy tayi tana nufar sofa ta zauna, ƙofar bedroom ɗin mom Balqis ta buɗe ta shiga,zama laatifa da Yumnah su kayi fa'iza itama zama tayi yayin da take gaishe da laatifa, cikin kulawa ta amsa mata, fira su ka shiga taɓawa.
Mom ce ta fito hannunta riƙe dana Balqis dake sakin murmushi, da sauri laatifa ta miƙe sakin hannun Balqis mom tayi tana buɗe ma laatifa hannuwanta alamar ta zo gareta, laatifa ba tayi ƙasa a gwiwa ba ta ƙarasa ga mom ɗin, hugging ɗinta tayi fukarta ɗauke da murmushi
“mom ina wuni, mun same ku lafiya”
“lafiya lau agogo sarkin aiki” mom ta faɗa yayin da take raba jikin su, ɓata fuska laatifa tayi tana faɗin “mom kema haka za ki ce”
dariya Balqis tayi tana faɗin
“wallahi mom gaskiya ki ka faɗa Aunty laatifa bata saurarama aiki” momy na daga zaune,murmushi ta saki a ranta tana faɗin sarakai za ku fara
“ai ba sai kin faɗa ba Balqis na santa ne” mom ta faɗa
“shikenan mom tunda kema haka za kice” laatifa ta faɗa tana komawa mazauninta
“wasa nake maki laatifa ai aiki abu ne mai kyau” murmushi laatifa ta saki jin mom wasa take mata itafa babu abun da ta tsana sama da ace mata ta cika nacema aiki.
sofa da momy take zaune mom ta nufa, tashi momy tayi su kayi hugging ɗin juna kafin su ka raba jikin su fuskokin su ɗauke da murmushi, gaishe da juna su ka shiga yi cikin kulawa yayin da suke samun wurin zama su ka zauna,masu aiki fa'iza ta kira dan su kawo ma su momy abun sha ta hanyar landline ɗin kitchen.
fira sosai su ka shiga yi a tsakaninsu momy na jajanta ma mom abun da ya faru da aminiyarta hajiya Asma'u,tambayar mom momy tayi ina ɗiyar hajiya Asma'u take
“tunda mu ka dawo daga prison wajen mahaifiyarta ta shige ciki bata jin daɗi,yumnah je ki kira man ita” mom ta faɗa, har yumnah ta miƙe fa'iza tayi saurin tashin tana faɗin “bari na kira ta”ta faɗa tana nufar corridor da zai sada ka da bedroom ɗin yumnah, tura ƙofar bedroom ɗin tayi ta shiga bakinta ɗauke da sallama.
bedroom ɗin yana da girma sosai, king size bed ne a cikin shi mai matuƙar kyau gefe da gefen shi nightstand ne mai ɗauke da bedside lamps,daga saman headboard ɗin bed ɗin ƴar rumfa ce mai haɗe da sparkling bulbs,sai ƙaton dressing mirror an cika gaban shi da body lotion da perfume masu dadda ɗan ƙamshi da tsadar gaske, tsakar ɗakin shimfiɗe yake rug carpet.
daga bakin sliding door glass balls chairs ne guda biyu suna kallon juna, daga wajen door ɗin ƴar baranda ce mai ɗauke da chairs guda biyu tsakiyar su round table ne daga nan kana iya hangen cikin estate ɗin da swimming pool dake cikin garden ɗin gidan.
A kwance fa'iza ta hangota saman makeken gadon ta rufe jikinta da duvet, bakin bed ɗin fa'iza ta ƙarasa pillow da take kwance ta ɗan bubbuga tana kiran sunanta, a hankali ta shiga buɗe idanuwanta da su kayi mata ɗauyi ga wani irin azabebben ciwo da kanta yake yi mata
“ki tashi mom na parlor tana kiran ki”pro khaki eyes ɗinta ta sauke akan fuskar fa'iza da tayi maganar,eyes ɗin sun ɗanyi jajja jajja saboda baccin data fara ga ciwan kai.
A hankali ta tashi zaune hanunta dafe da kanta, matsawa fa'iza tayi tana bata hanya dan ta samu damar saukowa, a hankali ta zuro da fararen ƙafafunta ƙasa,rober gown ce a jikinta ,rigar ta kamata ta bayyanar da surar jikinta,kanta babu ɗan kwali, water wave hair ɗinta har gadon bayanta ya sauka, gashin duk ya ɗan yamutse saboda bai samu gyara kwana biyu ba,sannu fa'iza ta shiga yi ma mata yayin da take binta da kallon ba ƙaramin tafiya da ita kyan nainarh yayi ba yarinyar ce Allah ya zuba mata kyau ko mace ƴar uwarta ta kalleta sai ta sake kallon, hijab ɗin ta dake kan bed ɗin ta ɗauka ta zura a jikinta.
“muje”fa'iza ta faɗa, gaba nainarh tayi fa'iza na biye da ita, a hankali take taka ƙasa kamar zata faɗi saboda rashin ƙwarin jikinta,tunda su ka shigo parlor momy da laatifa ke bin nainarh da kallo har su ka ƙaraso ciki, wurin mom nainarh ta nufa tana faɗin mom gani, momy ta nuna mata tana faɗin “ga momyn su laatifa nan kun gaisa” sai a sannan nainarh ta kai dubanta ga momy.
gaishe da ita tayi cikin kulawa momy ta amsa mata tana faɗin“ ya jikin ki naji ance ba ki jin daɗi”
“da sauki Alhmdllh” ta faɗa, gaishe da laatifa tayi cikin kulawa laatifa ta amsa mata Balqis tunda su ka shigo parlorn kallo ɗaya tayi ma nainarh ta ɗauke kai
“amma kin sha magani kuwa?” laatifa ta faɗa cikin nuna kulawa
“A'a” nainarh ta faɗa tana nufar rug carpet zata zauna saboda wani jiri da take ji, da sauri momy ta nuna mata kusa da ita tace ta zauna.
sannu su ka shiga jera mata mom na faɗin“bari idan IRFAN ya shigo ya duba ki, yumnah kira man shi a waya kice nace idan ya taso daga aiki ina son ganin shi”
da to yumnah ta amsa tana ɗaukar wayar ta ta shiga contact, number Irfan ta shiga nema, dialing number tayi ringing ta shiga yi har ta katse bai ɗaga ba, sake kira tayi sai da ta kusa katsewa ta samu sa'a yayi picking,sallama tayi tana gaishe da shi babu wanda ya amsa mata daga ciki sai cewa yayi“ lafiya ki ke man irin wannan kiran?”
shagwaɓe fuska yumnah tayi kamar tana a gaban shi
“dama mom ce tace idan ka ta so daga aiki ka shigo gida tana son ganinka” rejecting kiran yayi kawai ba tare da yace komai ba, taɓe baki yumnah tayi.
masu aiki ne su ka shigo hannun su ɗauke wooden tray, soft drinks ne da ruwa masu sanyi haɗe da glass cups, cikin parlorn su ka ƙaraso bakin su ɗuke da sallama, amsa masu sallama su kayi,ajiye tryas ɗin su kayi saman glass round table ɗin dake parlorn, ficewa su kayi, fa'iza ce ta shiga zuba masu ruwan da lemu ta miƙa masu.
masu aikin suna fita daga parlorn ɗaya kitchen ta nufa yayin da ɗaya ta nufi elevator, da sauri ƴar uwarta tace“munirat ina za kije?”
“part ɗin mamy ”wacce aka kira da munirat ta faɗa, girgiza kai wacce ta kira munirat ɗin tayi tana faɗin
“munirat ina rabaki da kiwan kyalla kina akuya ta haihu, wallahi ki daina shishige ma mamy, dan wallahi za kiyi da kin sani dan ita ba'a mata gwaninta ina guje maki ranar da zata shuka maki rashin mutunci”
“banji bakin ki ba, kuma ni bani ke shishige mata ba itace ke jana a jiki”
“na dai faɗa maki dan idan baki san abun da ya faru da baaba jummai ba gara tun wuri ki sani”
“ni dai naji,yanzu zan dawo” ta faɗa tana daddana madannan dake jikin elevator, girgiza kai kawai ƴar uwar tata tayi tana nufar kitchen...
_*Episode 9_10*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
______________________________
A kishingiɗe take saman makeken king size bed ɗinta ta ɗauki wankan rantsatsiyar shadda white color anyi mata aiki da red color ɗin zare, fuskarta tasha make_up a ko wane lokaci zaka samu hannuwanta da wuyanta da ƙafarta cikin adon gold ko zinari, kanta babu ɗan kwali gashin Attachment ɗin dake kanta ya sauka har gadon bayanta,wayarta ce a hannunta tana aikin daddanawa.
Nocking ƙofar bedroom ɗin a kayi,yamutse fuska tayi cike da izza tace “waye?”
ɗan ɗaga murya munirat dake tsaye bakin ƙofar tayi “munirat ce mamy”
“ke da waye ne?” mamy ta faɗa
“ba kowa ni kaɗai ce”
“ok shigo”mamyn ta faɗa.
a hankali munirat ta turo ƙofar ta shigo bakinta ɗauke da sallama,ƙaremata kallon mamy ta shiga yi tun daga sama har ƙasa, a bakin bed ɗin ta tsaya,cike da girmamawa ta durƙusa har ƙasa ta gaishe da mamy.
ƙin amsa mata mamy tayi sai ma cewa tayi “ina sauraronki mi ya kawoki ɗakina?”ta faɗa tana wani yamutse fuska.
“dama zuwa nayi na sanar dake hajiya maimunatu matar yallaɓai hashim ta zo ita da ƴaƴanta suna part ɗin madam zulaihart”
“mi su ka zo yi”mamy ta faɗa tana wani tsuke fuska
“nima ban sani ba amma ina tunanin sun zo yima madam jaje ne”
jinjina kai mamy tayi“naji daɗin jin wannan labari da ki ka zo man dashi, abunda nake so dake ki sa man ido akan kowa dake part ɗin komai ki ka gani ki sanar dani, komai ƙanƙantar abu ki sanar da ni”
“in sha Allah madam” jinjina kai mamy tayi“yawwa haka nake son ji, tashi ki tafi bana son janar ya shigo ya sameki, zan tura maki saƙon ki ta waya” miƙewa munirat ɗin tayi “nagode sosai Allah ya ƙara girma”ta faɗa tana nufar ƙofar fita ta fice.
tsaki mamy taja tana faɗin“munafuncin banza ko miye abun zuwa jaje in ba tsabar tsugudidi ba” mamyn ta faɗa tana sake jan wani tsakin.
wayarta ta ɗauka tayi dialing wata number, bugu biyu a ka yi picking, murmushi ta saki yayin da take kara wayar a kunenta.
“Allah ya taimaki first lady,hutawar ki lafiya hajiyar yallaɓi Ahmad”mamy ta faɗa ta na sakin dariya,on the other hand ta cikin wayar itama dariya ta saki.
“kullum da kalar tsokanar da ki ke zuwa MABARUKA, yau kuma ni ki ke ma wannan kirarin?”
“ai kin can canta ne, ya ki ke ya kwana biyu?”
“Alhmdllh, fatan kema kina lafiya, ina madam ɗinki take?”
taɓe baki mamy tayi “tana nan kamar yanda ki ka santa,ban ma baki labari ba”
“ina jinki mi ya faru?”
“uhmm ina wannan shari'ar da suke akan ƙawarta wannan munafukar hajiya Asma'un?”
“eh na gane ,ɗazu naji WASEEF na mata jaje wai an yankema hajiya Asma'u hukuncin ɗaurin rai da rai”
“eh ashe kinji?”
“naji waseef na mata jaje kin san ni ba ma'abociyar bibiyar labarai bace”
“ai kuwa kamar yanda ki ka ji an yanke mata hukuncin ɗaurin rai da rai”
“tab! Allah ya kyauta gaba,ki ce yau ku baku ba walwala”
“bata ba walwala dai, kema kin san babu abun da zai hanani walwala dama abun da na daɗe ina jira kenan dan wallahi ba ƙaramin jin haushin Asma'un nan nake ba”
dariya mai ɗan sauti ta cikin wayar ta saki “duk da haka da kinyi mata kara ai zaman tare baice haka ba”
“wa ni? Allah ya ki ya ye dama ta dawo magana na samu na nannausa mata na san sai ta da ɗe tana damunta”
dariya ta cikin wayar ta sake saki “gaskiya mabaruka baki da kir ki, mai makon ki taya ta ja je shine zaki ɓige da gaya mata magana”
“Allah ya ki ya ye ai ga abokan cin mushenta can ɗayar har ta zo wai ja je ɗayar munafukar ma na san tana nan zuwa anjima”
“baki da dama mabaruka, nima anjima ko gobe zan shigo nayi mata ja jen”
taɓe baki mamy tayi“ai da yake ke akwai kara a tsakanin ku”
“to ya zanyi tunda Allah ya haɗa Auratayya a tsakanin ƴaƴan mu dole ne zumunci ko bama so”
“Allah ya kawo ki lafiya” da Ameen ta cikin wayar ta amsa, sallama su kayi.
wata number mamy ta sake dialing, ringing wayar ta shiga yi, sai da kiran ya kusa katsewa sanann a kayi picking, murmushi mamy ta saki tana faɗin
“kaga abun gidan janar, halama bacci ki ke nake kira ba'a picking in time”
on the other hand ta cikin wayar tace “ina fa na shiga kitchen ne wurin masu aiki, kin san idan baka sa masu ido sai suyi maka shirme”
murmushi mamy ta saki“ kice kina can kina gasa masu aya a tafin hannu dan na san halinki ba sauƙi ne dake ba”
“duk rashin sauƙina na kai ki ne?”
“ai wallahi masu aikin ne sai da jan ido, idan kayi sanya sai su kawo maka raini”
“haka ne kam,to ya gidan, ya kwana biyu fatan kina lafiya??”
“lafiya lau Alhmdllh, ya naki gidan”
taɓe baki mamy tayi“ yana nan yanda ki ka san shi sai ma abunda ya ci gaba” murmushi ta cikin wayar ta saki
“ki ce kina nan kin hana dangin nasara masu jan kunne sakat”
“mi za'a fasa, ai in dai ina raye ta shiga uku”
“Allah ya shirya man ke ƙawata, ki zo ki samu mata a har gidan mijinta ki hanata rawar gaban hantsi”
“tama isa, wanda yace tayi sakacin da mijinta yayi mata kishiya”
“kina sha'aninki ta wajena, wai ni kam ɗazu nake gani a TV an yanke ma ƙawarta hukuncin ɗaurin rai da rai”
“eh Allah yayi maganin ɗayar munafukar saura manyan, kin san kuwa ɗayar harta kwaso ƙafa ta zo jaje??”
“wa ki ke nufi?”
“wacece kuwa ban da uwar ƴan tausayi maimunatu” tsaki ta cikin wayar taja
“munafukan banza kawai, na san ɗayar munafukar ma tana nan zuwa”
“wannan a rubuce take sai ta zo”
“wallahi haushi hajiya maryam ke bani, sai girman kan masifa”
“ai wallahi bake kaɗai take ba haushi ba, wani lokacin idan tana hura hanci tanama mutane kallon banza ji nake kamar na rufeta da duka”
“ke dai ki bari mai abun duniyar ma batayi ji da kai ba sai ita”
“za ki shigo anjima?” mamy ta faɗa
“mi zan zo nayi”
“ai nayi tunanin ko zaki zo mata ja je”
“wa ni? Allah ya ki ya ye, lokacin da hajiya Asma'un zata kashe mijinta shawara tayi dani da zan zo mata ja je, ai in kin ganni lahira to kaini a kayi”
dariya mamy ta saki “shiyyasa nake sonki ƙawata, yanzu na gama waya da hajiya SALIMA ta ce zata zo”
“ita ki ka ce ji tayi zata iya”
“ai kin san so akwai alaƙa mai ƙarfi a tsakanin su”
“wace alaƙa?, daga ɗanta na Auren ɗiyarta shikenan ko dan IRFAN na hannun mijinta, ni ba NAEEM bane ke Auren NAFISAT, ke ni bazan iya ba alaƙar Aure ma dake tsakanin nafisat da naeem dan bani da yanda zanyi ne amma wallahi da ba'ayi Auren ba”
“nima dai haka na gani”
“rabu da ita kawai sai mun haɗu ranar juma'a a part ɗin Abba”
“ok Allah ya kaimu” da Ameen matar ta amsa sallama su kayi.
𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫
Mom da momy ne kawai babu a parlorn, Yumah na kusa da laatifa sai zuba mata zance take yayin da balqis da fa'iza ke zaune saman sofa suna firar yaushe gamo.
tashi Nainarh tayi ta nufi bedroom ɗin Yumnah,da sannu su laatifa su ka bita balqis kuwa banda binta da kallon tsana babu abunda take, haka nan taji bata son Nainarh ita kanta bata san dalili ba amma taji ta tsaneta.
Sallama su ka ji daga bayan su da sauri su ka kai duban su ga matar dake shigowa, ta ɗau wanka baƙar Abaya tayi rolling da gyalenta,da gudu Yumnah ta nufeta hugging ɗinta tayi tana faɗin“momy kema ashe kina hanya” murmushi matar ta saki tana raba jikin su
“wani ya zo kenan da har ki ke tunanin nima ina hanya” murmushi Yumah ta saki “momy ma ta zo tare da su Aunty laatifa” ta faɗa yayin da su ke ƙarasowa cikin parlorn, cike da girmamawa su laatifa su ka shiga gaishe da matar tana amsa masu cikin kulawa yayinda take hugging ɗin su ɗaya bayan ɗaya.
“su mom na garden ita da momy” Yumnah ta faɗa
“ok bari na ƙarasa wajen su” ta faɗa yayinda take nufar sliding door dake parlor wacce daga nan kana iya hangen cikin garden ɗin da kusan zagaye yake da gidan.
shuke shuke ne a cikin a garden ɗin masu matuƙar ɗaukar hankali da ban sha'awa,ga grass carpet dake malale a cikin garden ɗin,ƙaton swimming pool ne a cikin garden yayinda aka ƙawata gafe da gefenshi da lounger chairs da deck chair masu kyan gashe domin zama,ducks ne ke shawagi a cikin swimming pool ɗin farare tas da su,daga can gefen swimming pool ɗin wasu rukunin bishiyu ne masu matuƙar ɗaukar hankali sunyi rukuni,peacocks ne masu kyan gaske ke yawo tsakanin bishiyun,babu kalar tsuntsun da babu a cikin garden ɗin.
A tsakiyar bishiyun mom Maryam ta hango mom da momy kishingiɗe saman rug sun yi matashi da tum tum yayin da aka cika masu gaban su da fresh fruit cikin kwandon kaba haɗe da snacks da soft drinks masu sanyi.
Momy ka ɗaice ta ɗan gatsi Apply yayin da mom ta zuba ma ducks ɗin dake shawagi cikin ruwa ido,damuwar halinda Aminyarta take ciki ce duk ta isheta ,bata so duniya ta juya mata baya lokaci guda ba.
“ki kwantar da hankalin ki barisster in sha Allah babu abun da zai faru da Asma'u,ina sha Allah zata kuɓuta su kuma wanda su kayi silar jefata cikin wannan halin da izinin Allah asirin su zai tonu”
Ajiyar zuciya mom tayi
“babu abunda yafi ɗaga man hankali sama da yanda jami'an tsaro da mutanen gidan su ka kafe akan ita ta kashe shi, ni na san wacece Asma'u ko dabba bazata iya kashewa ba bare ɗan Adam”
“nima a iya sani na da ita bazata iya aikata wannan babban laifin ba amma in Sha Allah gaskiya za tayi halinta”
“ina fatan haka”
fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙaraso in da suke, sallamarta su ka ji daga bayan su ,da sauri su ka kai duban su gareta, murmushi su ka sakar ma juna yayinda su ka miƙewa, hugging ɗin juna su ka shiga yi cike da kulawa suke gaishe da junan su,kalar ta su gaisuwar kenan a duk lokacin da su ka haɗu da juna.
saman rug ɗin su ka koma su ka zauna,sake gaisawa su kayi
“ya kuma mu ka ji da abun da ya faru da Asma'u” mom Maryam ta faɗa
“sai godiyar Ubangiji” momy ta faɗa
“Allah ya kuɓutar da ita”
“Ameen ya Allah” mom ta faɗa yayin da take ɗaukar sherry glass cup ta zuba ma mom maryam drink mai sanyi, miƙa mata tayi , murmushi mom Maryam ta saki ya yinda take amsar cup ɗin.
shiru ne ya gitta a tsakanin su,kowa da abunda yake saƙawa a ranshi ba kamar mom da kwata kwata bata cikin walwala,mom maryam ce ta katse shirun na su.
“amma barisster kin ɗauki wani mataki a kan shari'ar nan?” ta faɗa ya yinda take ajiye cup ɗin dake hannunta.
“ban fahimci ya ki ke nufi ba ,wane mataki zan ɗauka??”
mom ta faɗa cikin rashin fahimtar Abun da mom maryam ɗin take nufi.
“ai nayi tunanin zaki sa ayi maki bincike na daban akan case ɗin,idan Allah yasa aka dace kinga ba sai a tada shari'ar ba tunda hukuncin ɗaurin rai da rai ne”
“wane bincike zan sa ayi bayan wanda barisster Hashim yayi”
yana yin fuskar mom maryam me ya canza “uhmm barisster hashim fa ki ka ce?”
“eh shine lawyer dangin marigayi ,duk wani bincike da ya kamata ayi yayi”
“kenan kin yarda ita ta kashe mijinata?”
“A'a sai dai na san barisster ba zai faɗi abunda ba shikenan ba, kuma bana zargin zai haɗa kai da kowa dan kawai yayi nasara a kaina”
girgiza kai mom maryam tayi,mom Maimunatu na kallon su ƙala ba tace ba
“am sorry hajiya Maimunatu ba wai ina zargin barisster ba ne” murmushi kawai mom Maimunatu tayi ko zargin barisster su ke ya za tayi halin mijin nata ne dole a zargeshi.
“mu duka mun san cewa barisster baya ƙaunar zulaihart tun fil'azal, ni bana zargin zai iya haɗa kai da wasu dan dai kawai ya cika burin shi akan barisster,amma ƙara binciken da za kiyi yanada matuƙar amfani ni a nawa tunanin amma ya ku ka gani”
shiru mom tayi tana tsunduma duniyar tunani ta wani ɓan garen hajiya maryam na da gaskiya sai dai bata son ta binciko ma kanta abunda zai hanata zaman lafiya duk da har zuciyarta bata zargin Aminyarta zata aikata laifi makamancin haka.
“maganarki gaskiya ce hajiya maryam,ƙara binciken yanada amfani,sai dai waye zaiyi binciken?” mom Maimunatu ta faɗa
“haka ne ƙara binciken yanada amfani, Allah yasa ya zama sanadiyyar tonuwar asirin duk wanda ke da sa hannu,sai dai ta maganar Maimunatu wa zan sa yayi man binciken?” mom ta faɗa
“yawwa burina dama ku fahimce ni, maganar kuma wanda zaiyi binciken ba matsala bace karku manta gidan nan cike yake da jami'an tsaro kala kala samun wanda zaiyi bincike ba abun bane mai wahala NAEEM ma zai iya tunda dama aikin shi ne”
jinjina kai su kayi da alama sun aminta da maganar mom maryam
“shikenan zan samu lokaci mu zauna da shi,zanyi mashi bayanin yanda case ɗin yake” mom ta faɗa
“yawwa hakan yayi ,sai dai fa ya zamana cikin sirri zaiyi shi, kuma kar ya sanar a wajen aikin su yayi shi parsonal,duk da na san aikin su dama na sirri ne sai dai wannan ya ɗauke shi a matsayin na gida bana aiki ba” mom maryam ta faɗa
“in dai wannan ne ba matsala”a cewar mom , murmushi mom Maimunatu ta saki
“shiyyasa nake sonki hajiya maryam akwai kawo shawara mai ɓullewa” murmushi su ka saki gaba ɗayan su
“abun ne wallahi ya taɓa zuciyata,baiwar Allah nan babu ruwanta amma ace lokaci guda wani ya dabaibayeta da sharri,su barta mana taji da zaluncin kashe mata miji da su kayi mana ba sai sun manna mata kisan a kanta ba”
“gaskiya ko waye ba ƙaramin cutar da ita yayi ba” firar su suka shigayi suna alhinin abunda ya faru da ƙawar mom.
𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫
A tsaye take a gaba motar ta ƙirar honda Black color, blue black ɗin Abaya ce a jikinta ta yafa gyalen saman kanta,hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta,cikin faɗa faɗa take faɗin
“Enaaya wai zaki fito ne ko sai nayi tafiyata?”
daga cikin motar naji Muryar yar ƙaramar yarinya tana faɗin “momy gani nan fitowa hand bag ɗina zan ɗauka”
tsaki matar taja “ko uwar mi za kiyi da hand bag,ni kinga tafiyata idan kin gama kilibibin naki kya shigo” matar ta faɗa tana nufar entrance ɗin gidan.
da sauri wata ƴar ƙaramar yarinyar ta fito, Black ɗin abaya ce a jikinta tayi rolling da gyalen, simple make_up ne a fuskarta yayin da kyawawan idanunta ke manne da ɗan sunglasses dai dai idonta mai butterfly,ƴar hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta,highills ne a ƙafarta ba ƙaramin kyau tayi ba.
bayan mahaifiyarta ta tabi tana wani tako ɗai ɗai kamar wata uwar mata,a main parlor part ɗin ta samu mahaifiyarta tana jiranta,glass elevator dake part ɗin mom yarinyar ta nufa da sauri mahaifiyarta ta tace.
“ENAAYA ina kuma za kije?” ya mutse fuska yarinyar tayi tana faɗin “part ɗin mom mana”ta faɗa cike da yanga
“muje mu fara gaishe da mamy tukun” mahaifiyar ta faɗa tana nufar part ɗin mamy,juyawa yarinyar tayi tana faɗin
“ni gaskiya bazanje part ɗin mamy ba,haka nan kawai ta rufe mutum da faɗa ba abunda yayi mata,kuma Ni dady nake son nunama wannan kwalliyar dan karma sister ta rigani,sai kin dawo kawai momy ”
yarinyar ta faɗa tana nufar elevator part ɗin mom.
girgiza kai kawai mahaifiyarta ta tayi tana faɗin “Allah ya shirya ki Enaaya”
A parlor ta samu mamy zaune saman sofa kayan ɗazu ne a jikinta,bakinta ɗauke da sallama ta ƙarasa ciki.
fuskar mamy da fara'a ta amsa mata sallamar tana sannu da zuwa,wuri ta samu saman sofa ta zauna.
“in wuni mamy, ya gida”
“lafiya lau NADIYA, ya gida?”
“lafiya lau”
“masha Allah,Ina uwayen sanabe ko ana islamiyya?”
murmushi nadiya ta saki tana faɗin“A'a ta shiga part ɗin mom ne” jinjina kai mamy tayi tana maimaita kalmar part ɗin mom.
“watau ni tafi ƙarfin ta zo ta gaishe ni,shine ta wuce wajen ƙanwar uwarta, tunda ban haifi mahaifinta ba ai ba tazo ta gaishe ni ba,zata zo ta sameni ne” murmushi kawai Aunty nadiya tayi dafa gaskiyar enaaya mamy ba dai faɗa ba.
“tana nan zata shigo,na san duk saurin ta haɗu da dady ne”
“A'a tayi zamanta kawai ba sai ta zo ba”
“kiyi haƙuri mamy idan ranki ya ɓaci”
uhmm kawai mamy tace mata ba tare da ta sake cewa komai ba.
sallama su ka ji daga bayan su ,Aunty nadiya ce kawai ta kai dubanta ga mai shigowa,riga da skirt na atamafa ne a jikinta ta yafa mayafi tun daga kanta fuskarta tasha make_up,manyan idanunta sun sha eyelashes na company, hand bag ɗinta ce riƙe a hannunta yayinda yaranta ke biye a bayanta mace da namiji ,namijin ya ɗau wankan jeans and t_shirt,hannuwan shi zube su ke cikin aljihun wandon shi kamar wani babban mutum, fuskar nan tashi a ɗaure take, ƴar macen ce ke sanye da Pakistan dress riga da wando ta yafa mayafin kayan saman kafaɗar ta, anyi mata parking gashinta a tsakiyar kai,light make_up ne a fuskarta,ƙafarta sanye take cikin wedge shoe masu kyan gaske, itama sunglasses ne a fuskarta mai butterfly kamar Enaaya.
da sauri Aunty nadiya ta miƙe fuskarta ɗauke da murmushi ta nufi matar dake shigowa, hugging ɗin juna su kayi,gaba ɗayan su suna sakin murmushi.
“sister NAFISAT shine baki faɗa man kuna tafe ba ai dana jira ku” Aunty nadiya ta faɗa yayinda su ke raba jikinsu daga na juna.
“uhmm ki bari kawai nima ban san da fitar ba, ina zaune ya NAEEM yace wai mu zo,Ni ban ma san mi ke faruwa ba” ta faɗa tana ɗan ya mutse fuska.
“tare ku ke dashi ne?”
“eh ajiye mu yayi yaje ya dawo”
zuba masu ido mamy dake zaune tayi tana kallon su,wurin mamy Aunty nafisat ta nufa, gaishe da ita tayi cikin girmamawa,mamy da fara'ar ta ta amsa mata,suma yaran gaishe da mamy da Aunty nadiya su kayi,taɓe baki mamy tayi
“miskili kafi mahaukaci ban haushi,yau kuma aljanun sun bari a zo a gaishe ni kenan?”
ɗan taɓe baki Aunty nafisat tayi tana dallama yaron harara da duk ya wani ɓata fuska shi dole an sa shi abunda baiyi niyya ba,da sauri ya kalli gefe ganin kallon da mahaifiyar tashi tayi mashi,tsaki taja.
“momy nadiya wai ina Enaaya ne?” ƴar macen ta faɗa
“tana part ɗin mom” ko gama faɗa nadiya ba tayi ba ta juya da sauri ta nufi ƙofar fita,bin bayanta namijin yayi, da sauri Aunty nafisat ta daka mashi tsawa
“ina za ka ,ko kaima Enaayar ƙawarka ce?”
“ai wajen Aunty Yumnah zan je” ya faɗa yana ficewa daga parlor ba tare da ya tsaya jin mi Aunty nafisat ɗin za tace,jinjina kai Aunty nafisat tayi.
“wai shi mi a kayi mashi yake wannan kumbura fuskar?” mamy ta tambaya
“saboda nace sai mun fara shigowa nan shi baiyi niyyaba shine yake wannan cin ɗacin”
“kaga ƴan bantan uban yara sun raina ni,sai kace wata uwar nake masu da ba sa son zuwa in da nake”
“iskanci ne kawai irin na su” a cewar Aunty nadiya
“zanyi maganin su ɗaya bayan ɗaya ne”mamy ta faɗa.
canza fira su kayi,su Aunty nafisat Nama mamy jajen abunda ya faru da mom,taɓe baki kawai mamy tayi ba tare da ta ce masu komai ba.
𝑸𝒖𝒆𝒆𝒏 𝑲𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒕💫
ƙarar takun takalminta ne ya cika masu kunne,da sauri su ka kai duban su gaba bakin ƙofa,mamaki ne gaba ɗaya ya cika su,dariya fa'iza ta saki tana faɗin
“ƙamshi duk ya cika mana hanci kace uwayen mata ne a hanya” tsayawa Enaaya tayi tana wani tsuke baki
“kar wanda yasa ran zanyi mashi oyoyo,saboda wannan kwalliyar ta dady ce” ta faɗa tana wani yi masu fari da ido ta cikin glass, murmushi su saki
“yanzu baby Enaaya ko ni baza kiyi ma oyoyo ba” Yumnah ta faɗa tana wani marairaice fuska.
“gaskiya yau sai dai kiyi haƙuri Aunty Yumnah kwalliyar nan ta dady ce,ki bari idan na dawo daga wurin shi nayi maki oyoyo”
tsuke fuska yumnah tayi tana riƙe ƙugu“ai kuwa bana so”
“shikenan tunda so ki ke su Aunty balqis suyi mana dariya” Enaaya ta faɗa tana nufar stairs case dake hannun daman parlor,tana tafiya tana wani jujjuya jiki.
murmushi kawai balqis tayi tana faɗin “manyan mata sun hallara kowa yayi ta kansa” dariya su ka kwashe gaba ɗayan su.
*KITCHEN*
Gaba ɗaya masu aikin gidan suna kitchen domin lokacin fara aikin dinner yayi,a hankali take tafiya dan karma taji ƙarar takalminta
alama tayi ma masu aikin dake ciki da kar suyi magana,da gudu ta nufi Eishrat dake tsaye gaban fridge tana jera drinks,kamar daga sama taji mutum ya faɗa saman bayanta, ƙara ta saki tana jefar da lemun dake hannunta,dariya ta fashe da ita.
“gaskiya chef Ishrat kin cika tsoro” ajiyar zuciya Ishrat ta sauke dan ba ƙaramin tsorata tayi ba saboda bata san da shigowar ta ba sai dai kawai tajita a jikinta.
tsuke fuska Eishrat tayi tana
“amma baby Aneesah kin raina ni da yawa” dariya Aneesah ta kwashe da ita
“ba wani kin dai cika tsoro ne”
“to naji,saukar yaushe?”
yamutse fuska Aneesah tayi “yanzu muka zo da momy fatan kin ajiye man Alƙawari na?”
yana yin fuskar Eishrat ne ya sauya “Ayyah! baby Aneesah ban san za kizo yau ba”
ɓata fuska Aneesah tayi “chef Eishrat na fa sanar dake jiya, ko kin manta na kiraki da landline ɗin kitchen?” Aneesah ta faɗa tana tsuke baki
“sorry baby Aneesah mantawa na yi,amma yanzu zan haɗa maki”
ɓata fuska Aneesah tayi “har dady ya fita baki kammala haɗa man ba”
murmushi Ishrat ta saki
“wasa nake maki baby, tunda ki ka sanar da ni zuwan ku na haɗa maki”
da sauri Aneesah ta dafe saitin zuciyarta tana wani lumshe ido
“wai Allah! har kin sa hankali na ya kwanta,da yau kin sa sister Enaaya tayi man dariya, duk wannan saurin da nake dan kar ta rigani ba dady wani abu”
“Ayyah sorry,na san ta rigaki dan tun ɗazu tana part ɗin shi”
yamutse fuska Aneesah tayi “ita komai nata cikin sauri take yin shi,ai na san duk abun da zata bashi bazai kai wanda zan kai mashi ba”
“nima ina fatan haka, bari na shirya maki komai” Ishrat ta faɗa.
ƙaton wooden tray Ishrat ta ɗauka, fridge ta buɗe fruit salad ta ɗauko a cikin bowl sannan ta ɗauko yogurt daga gani haɗin gida ne mara zaƙi da lemun wanda shima haɗashi tayi da kanta sai chocolate cake.
Murmushi Aneesah ta saki ganin abun da tafi buƙata,dish rag ta nufa cups ta ɗauko da fork guda biyu ta ɗaura saman tray,ficewa su kayi daga KITCHEN ɗin Aneesah na gaba yayin da Ishrat ɗin ke biye da ita.
bakin su ɗauke da sallama su ka shiga cikin parlor,su Yumnah na nan zaune kamar yanda Enaaya ta barsu,Jamal na kwance saman sofa yayi pillow da laps ɗin Yumnah.
murmushi su ka saki yayin da su ke amsa sallamar da su kayi,sama Aneesah ta nufa ba tare da tace ma kowa ƙala ba suma binta su kayi da ido dan sun san ba lallai ta tanka masu ba tana sauri taje wurin dady.
bin bayanta Ishrat tayi ,dariya fa'iza ta saki tana faɗin “yan bantan uban yara kowa zai haƙura ya barma wani dadyn a cikin su?”
“rabu da ƴan ƙwal uba sun gama iskancin su su barma su mom majin su,yara sai kilibibin masifa”
a cewar Balqis, murmushi laatifa ta saki
“kar kuga laifin su,kuma da kune a matsayin su na san sai kunyi abun da yafi nasu”
“haba Aunty laatifa mu mi yasa ba mu yima Abbah haka”
“babu face ne shiyyasa” murmushi kawai su kayi ba tare da sun ce komai ba.
A kishingiɗe yake saman rug carpet dake katafaren parlon shi, ya ɗaura kanshi saman tum tum yayin da Enaaya ke gefenshi ,cike da salo da kisisina take bashi labarin school ɗin su,ya ƙafeta da ido sai sakin murmushi yake.
sallamar Aneesah da Ishrat ce ta katse masu firar da su ke, waro ido waje Enaaya tayi yayinda take miƙewa tsaye
“wayyo Allah nah!, sister Aneesah dama za ki zo” Enaaya ta faɗa tana yarfe hannu
murmushi Aneesah ta saki tana ƙarasowa ciki, da sauri Enaaya ta nufeta, hugging ɗin juna su kayi sai sakin murmushi su ke,raba jikin su su kayi.
gaishe da junansu su ka shiga yi kamar wasu manyan mutane, Ishrat da dady ban da sakin murmushi babu abun da su ke.
cikin parlor Ishrat ta ƙarasa a gaban dady ta ajiye tray
“barka da hutawa dady” murmushi dadyn ya saki
“lafiya lau Ishrat,sannu da ƙoƙari” murmushi kawai Ishrat ɗin ta saki tana nufar ƙofar fita
“thank u” Aneesah ta faɗa, alamar jinjina Ishrat ɗin tayi mata tana ficewa daga parlorn.
wurin dady Aneesah ta ƙaraso tana sakar mashi murmushi haɗi da fari da idanu, murmushi kawai dadyn ya saki yana girgiza kai lamarin su Aneesah na matuƙar bashi mamaki.
a saman rug ɗin su ka zauna, gaishe da dady Aneesah tayi yayinda take zuba mashi lemu a cup,cikin kulawa dady ya amsa gaisuwar yayin da yake ƙarɓar cup ɗin lemun da take miƙa mashi.
a tare su ka shiga cin chocolate cake ɗin banda dady saboda ciwan sugar
fira su ka shiga zuba mashi yan sauraron su.
Aunty nafisat sun jima a part ɗin mamy kafin su ka shigo part ɗin mom lokacin har su mom Maryam sun tafi ya rage saura fa'iza da Yumnah kawai, nainarh har time ɗin tana kwance a bedroom ɗin Yumnah.
bedroom ɗin mom su ka shiga a zaune su ka sameta bakin bed ɗinta tunda su mom Maryam su ka tafi take a nan zaune.
cike da girmamawa su ka shiga gaishe da ita tana amsa masu cikin kulawa,sosai su ka nuna alhinin su kan abunda ya faru da ƙawar mom ɗin.
tambayar su Aneesah mom tayi dan tun ɗazu suna part ɗin dady ba su fito ba, murmushi kawai tayi ko da su ka sanar da ita suna can.
fira su ka shiga taɓawa sama sama har aka fara kiran sallar magrib, bedroom ɗin Yumnah su ka nufa domin yin sallah,sunyi mamakin ganin nainarh dan basu san da zamanta a gidan ba,kasa haƙuri Aunty nafisat tayi har sai da ta tambayi Yumnah wacece,faɗa mata ko wacece Yumnah tayi.
taɓe baki kawai Aunty nafisat ɗin tayi Aunty Nadiya kuwa ko kallon in da su ke ba tayi ba tana sallame sallah ta fice daga ɗakin zuwa na mom, anan ta samu Aneesah da Enaaya sai zubama mom fira su ke Jamal na gafen su zaune.
Aunty nafisat ma data gama sallah bedroom ɗin mom ta koma,ko da lokacin sallar isha yayi a nan su kayi ta,suna zaune saman carpet sallame sallar su kenan a kayi nocking ƙofar bedroom ɗin.
da sauri Enaaya taje ta buɗe, a tsaye suke su biyu ɗaya suit ne a jikinshi yayin da ɗayan ke sanye da Army trouser da white ɗin shirt.
Kamannin fuskar su ka ɗai zai tabbatar maka da su ɗin jinin dady da mom ne ba kamar mai Army trouser ɗin.
Da gudu Enaaya ta faɗa saman jikin mai Army trouser ɗin wando tana faɗin “oyoyo dady NAEEM ashe da rabon mu gana yau”
dariya su ka saki gaba ɗayan su
“ai kuwa da rabon mu gana, ya school?” ya faɗa yayinda yake raba jikinsu
“Alhmdllh dady NAEEM,wai ina ka shige kwana biyu bana ganin ka?”
“aiki ne ya yi man yawa baby Enaaya,kuma ma ai idan kina son gani na kin san in da zaki same ni”
ɗan zaro ido tayi tana kallon wanda ke kusa dashi “wannan maganar tafi karfina dady NAEEM,ga dady nah nan ka tambaye shi” ta faɗa tana komawa cikin ɗakin da gudu.
murmushi kawai su ka saki ya NAEEM na faɗin “kenan dai ADNAN kai ke hanata zuwa gida na?” ya faɗa yana ɗan tsuke fuska.
“haba SECOND FATHER sai ka ce baka san sharrin Enaaya ba,ni ƙarya take man”
cikin ɗakin su ka ƙarasa ya NAEEM na faɗin “yanzu dai maganar wa zan kama tsakanin ku?”
“tawa mana dady NAEEM” Enaaya ta faɗa tana wani marmar da ido.
da sauri ya NAEEM yasa hannu yana toshe bakin shi haɗi da ɗan zaro ido kamar yanda Enaaya tayi ɗazu, girgiza mashi kai ta shiga yi alamar kar ya faɗa tana zare ido.
dariya gaba ɗayan su suka sa dan sun san saboda mi ya NAEEM yayi mata haka watau dadyn ta ƙarya yake.
da gudu Aneesah ta faɗa jikin ya ADNAN tana mashi oyoyo, Jamal ma nufo su yayi,Barka da zuwa yayi masu yana koma bakin bed daya ta so.
gaishe da ya NAEEM Aunty Nadiya tayi tanama ya ADNAN sannu da dawowa,hakama Aunty nafisat gaishe da su tayi.
ta shi su kayi su ka fice daga ɗakin ya zama daga mom sai su ya NAEEM ɗin,a gabanta su ka zo su ka zauna ƙasa suna tanƙwashe gwiwowin su kamar masu neman gafara.
cikin girmamawa su ka shiga gaishe da ita tana amsa masu cike da kulawa.
“ya aiki” ta tambaye su da Alhmdllh su ka amsa mata haɗi da jajanta mata abun da ya faru.
“in sha Allah gaskiya za tayi halinta” ya Adnan ya faɗa, da Ameen su ka amsa.
sun ɗan jima suna fira kafin su ka tashi zuwa part ɗin dady dan su gaishe da shi,har sun kai bakin ƙofa mom tace ma ya NAEEM tana son magana dashi gobe idan ya dawo aiki ya zo ya sameta,da to ya amsa mata, ficewa su kayi zuwa part ɗin dady.
su Aunty Nadiya na zaune parlorn Ishrat ta shigo ta sanar da su an kammala dinner.
“sannunki da ƙoƙari Ishrat” fa'iza ta faɗa, murmushi Ishrat ɗin ta saki tana barin parlorn.
a dinning room su ka hallara saman makeken dinning table mai mazaunin mutum shabiyu, Aneesah da Enaaya sun sa dady a tsakiya, Nainarh ka ɗaice babu, itama ba bu yanda Yumnah ba tayi da ita ba a kan ta fito suyi dinner amma taƙi sai dai aka kai mata nata can,tsit ka ke ji sai ƙarar spoon da plate dake tashi kowa na ba ciki haƙƙin sa.
hakan ya ba dady damar kafe su da ido yana kallon su cike da Alfaharin yanzu duk shi ke da wannan danma wasu basa nan,yana yin fuskarshi ne ya canza da alama ya tuna da wani abun,hawaye ne su ka taru a idanuwan shi saurin goge su yayi yana kawar da tunanin a ranshi.
sai wurin ƙarfe goma na dare su ya NAEEM su ka bar gidan,har part ɗin mamy Aunty Nadiya da Aunty nafisat su ka shiga yi mata bankwana harda su ya NAEEM amma ban da su Enaaya dan cewa su kayi basa zuwa da iyayen su ka matsa masu sai ficewa su kayi daga gidan da gudu.
murmushi kawai fa'iza da Yumnah su ka saki suna bin bayan su Aneesarh.
cikin girmamawa su ya NAEEM su ka gaishe da ita amma sai ta amsa masu tana wani ya mutse fuska,hakan bai dame su ba idan da sabo ai sun saba.
ba su zauna ba su ka fice a parking space su ka samu su Enaaya tare da su fa'iza,sallama su kayi ma junan su su ka nufi motocin su yayin da fa'iza da yumnah su ka koma ciki, barin gidan su kayi zuwa na su gidajen dake cikin Estate ɗin...
_*Ep11_12*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
_____________________________
A main parlor fa'iza da Yumnah su kayi sallama fa'iza ta nufi part ɗin mamy yayin da Yumnah ta nufi na su part ɗin.
direct ɗakinta ta nufa, a hankali ta tura ƙofar bakinta ɗauke da sallama, a tsaye ta hango Nainarh bakin sliding door ɗin dake cikin ɗakin ta zubama cikin estate ɗin da yake ƙwanyar da haske kamar rana ido, jefi jefi take hange motoci na kai kawo a cikin Estate ɗin.
A zahiri kallon cikin Estate ɗin take a ɓaɗi kuwa hankalinta na can prison wajen mahaifiyarta, ko a wane hali take, wasu irin zafafan hawayen su ka wanke fuskarta lokacin data tuna irin kisan wulaƙancin da a kayi ma mahaifinta.
Sosai take zubar da ƙwalla kwata kwata ko sallamar Yumnah ba taji ba, bakin door ɗin Yumnah ta ƙaraso, a hankali ta kira sunan Nainarh amma bata amsa mata ba saboda hankalinta da baya tare da ita, dafa kafaɗarta Yumnah tayi, da sauri ta kai dubanta ga Yumnah.
“nainarh dan Allah ki daina sa damuwa a ranki, komai zai wuce”
da sauri Nainarh ta faɗa jikin Yumnah tana sakin kuka mai sauti,jikin Yumnah ne yayi sanyi, wani irin tausayin Nainarh ne ya rufeta musamman yanda taji jikin Nainarh ya ɗauki zafi.
ɗan bubbuga bayanta ta shiga yi tana lallashin ta.
“nainarh dan Allah ki daina sa damuwa a ranki, komai zai wuce, ki daina kuka dan Allah,naji ma jikin naki ya ɗau zafi gashi ya Irfan ɗin baizo ba,amma bari naje medical room na samo maki maganin zazzaɓi kafin zuwa gobe”
Yumnah ta faɗa yayin da take raba jikin su,jan hannun Nainarh tayi zuwa ottoman chair dake bakin bed.
“ki zauna bari na kawo maki magani, naga ma ko dinner ɗinki ba ki ci ba” Yumnah ta faɗa tana kallon dinner ɗin da Ishrat ta kawo mata.
cikin dasashiyar muryarta tace
“bana jin yunwa ne”
girgiza kai Yumnah tayi “bazai yuwu ba, idan baki son wannan ne na kawo maki wani, amma zama da yunwa ba masalaha bace”
“na ƙoshi ne Yumnah, bazan iya cin komai ba”
“dole kisa wani abu a cikin ki” Yumnah ta faɗa tana kwashe kayan abincin da aka kawo mata tana nufar ƙofar fita ta fice daga ɗakin, kitchen ta fara nufa ta ajiye trayn kafin ta fice.
Ƙaton medical room ɗin su ta shiga babu abun da babu a cikin shi,komai da mara lafiya zai buƙata a kwashi a ciki,girmanshi zai kai clinic.
glass drawer dake ɗauke da nau'in magunguna ta nufa,side ɗin da magungunan zazzaɓi dana ciwan kai ta buɗi maganin zazzaɓi dana ciwan kai ta ɗauko mata, mai da ƙofar tayi ta rufe, ƙofar fita ta nufa light ɗin ɗakin ta kashe haɗi da ficewa.
da mom taci karo zata part ɗin dady hannunta riƙe da tea cup wanda ta haɗa ma dady herbal tea.
“ke kuma daga ina?” mom ta faɗa, in da take ta ƙaraso.
“magani na ɗauko ma Nainarh”
“ya Allah!, kinga shaf namanta IRFAN ɗin bai zo ba, gashi yanzu dare yayi da na sa dr lelah ya dubata, jikin nata yayi zafi ne sosai?”
“A'a da sauƙi, damuwace tayi mata yawa”
“dole damuwa tayi mata yawa, yanzu tafi da maganin ki bata” mom ta faɗa tana nufar part ɗin dady.
Kitchen Yumnah ta nufa,hot milk da coffee ta haɗa mata,saman ɗan madaidaicin tray ta ɗaura da maganin,ruwa ta ɗauko mata cikin fridge, ɗaukar trayn tayi ta ficewa zuwa bedroom ɗinta.
kamar yanda ta barta haka ta same ta zaune,ku sa da ita ta zo ta ajiye mata tryan, ɗaya daga cikin chairs ɗin dake ajiye bakin sliding door dake ɗakin ta jawo,zama tayi tana tasa Nainarh gaba.
“gashinan ki sha ko ɗaya daga cikin su ne sai kisha magani”ruwa ta ɗauka da nufin su zata sha,da sauri Yumnah ta girgiza mata kai.
“kar muyi haka dake Nainarh,ki daure kisha hot milk ɗin nan ko da baki sha coffee ba” jinjina mata kai tayi tana ajiye ruwan data ɗauka ta ɗauki milk ɗin ta kafa a baki,da kyar tasha rabin cup ɗin shima Nainarh ta tursasata har ta sha kamar haka.
yumnah da kanta ta shiga miƙa mata maganin tana sha,bayan data kammala tashi tayi ta kai kayan kitchen.
Toilet Nainarh ta shiga,ruwa ta watsa dan taji daɗin jikinta,tana fitowa Yumnah na shiga,wata ƙofa ta nufa,tanƙamemiyar glass drawer ce gari guda,daga waje kana hangen cikinta shaƙe take da sutura kala kala,kowace sutura wajenta daban.
ɓangaren pajamas ta buɗe tsaye tayi tana kallon kayan har Yumnah ta shigo, girgiza kai tayi yayinda take ƙarasowa ciki.
“please Nainarh ki riƙa abu da hanzari,yanzu ɗauko kayan ne ki ka ɗauki lokaci haka”
da kallo kawai Nainarh ta bita har ta ɗauko ma su kayan da zasu sa,riga da wando na saƙa farare ta miƙa mata saboda zazzaɓin da take ne yasa ta ɗauko mata su.
fita Nainarh tayi daga ɗakin,ƴar gown ɗin data ɗauko ta zura a jikinta,baby bant tasa ta ɗauke kanta,ficewa tayi daga ɗakin,samun Nainarh tayi har ta kwanta,itama bed ɗin ta nufa, laptop ɗinta dake ajiye saman night stand ta ɗauka,opreting ɗinta ta shiga yi, video call ne ya shigo ta laptop ɗin.
murmushi ta saki tana faɗin “yanzu nake shirin kiran ka saiga kiran naka” picking call ɗin tayi, a shagwaɓe tace “hey” tana yarfa yatsun hannunta irin na gayu.
Yana daga zaune saman Leather chair,da alama a office yake, Army shirt ce a jikinshi haɗe da trouser ɗinta,sosai rigar tabi shape ɗin broad chest ɗinsa ta bayyanar da strong arms ɗinsa,kallo ɗaya za kayi mashi ka tabbatar da jinshi turawa ne,kyakkyawa ne na gaske,hancinshi a tsaye yake ƙem, blue eyes ɗin shi sai ɗaukar ido su ke, kwantaccen sajenshi baƙi wul sai sheƙi yake,sumar kanshi ta sauka har saman neck ɗinshi,daga yanayin zanen tattoo ɗin dake saman neck ɗin shi da ear ring mai alamar Cross ɗin dake a ƙunnanshi zai tabbatar maka da Addinin shi.
ƙayataccen murmushi ya sakar mata wanda ya ƙara bayyanar da kyawun fuskarshi yana maida mata martanin sallamar da tayi mashi, a shagwaɓe cikin harshen nasara tace “mi yasa baka kirani ba duk yau?”
in a cool voice yace“Am sorry, yayan ki ne yau duk yabi ya takura man” murmushi ta saki
“ko dai ka takura mashi,kai ma fa na san..” murmushi ta saki ba tare data ƙarasa ba,wani irin killer smile ya sakar mata,shagwaɓe mashi fuska tayi kamar za tayi kuka.
cikin shauƙin soyayya su ke waya Nainarh na daga kwance tana sauraronta sama sama kafin bacci yayi awan gaba da ita.
Yumnah ba itace ta gama waya ba sai wajen ƙarfe uku na dare, kusan kullum haka take ɓata lokaci suna waya saboda shi lokacin ne ya ke samun sararin kiranta saboda banbancin lokaci dake tsakanin ƙasashen guda biyu.
*WASHE GARI*
Alhmdllh jikin Nainarh zazzaɓin ya sauka sai ciwan kai da take fama dashi har lokacin gashi har time ɗin Irfan bai zo ba.
kwance take saman bed ita ka ɗai a ɗakin,babu yanda Yumnah ba tayi da ita ba ta zo su fita tayi breakfast tare da su amma taƙi sai dai a kawo mata a ɗaki.
turo ƙofar ɗakin a kayi aka shigo, Yumnah ce ta shigo jikinta sanye da riga da wando masu taushi peach color ta yafa farin mayafin a saman kanta.
cikin ɗakin ta ƙaraso “ki tashi ki shirya mom tace mu tafi hospital Dr Faawar ya dubaki tunda ya Irfan bai zo ba”
yumnah ta faɗa yayinda take nufar toilet,tashi Nainarh tayi tana bin bayanta da ido,bata motsa daga inda take ba har Yumnah ta fito sanye da bathrobe.
“tashi ki shiga” Yumnah ta faɗa,sauka Nainarh tayi daga saman bed ɗin toilet ɗin ta nufa
“ki fa yi sauri kar mom tace tare da wani za ku tafi ko ya Irfan ya shigo”
Dressing room ta nufa,shaf shaf ta shiga shiryawa duk tana wannan saurin ne dan kar wani abu yasa a fasa fitar ko Irfan ɗin ya shigo dan da ƙyar ta samu mom ta amince akan za su je hospital ɗin dan cewa tayi kawai su tafi clinic ɗin dake cikin Estate ɗin ko ta kira dr Faawar ɗin ya zo har gida ya duba Nainarh.
Nocking taji anyi,da sauri ta ƙarasa zura rigar data fara sawa,ficewa tayi zuwa cikin bedroom ɗin har time ɗin Nainarh bata fito ba,ƙofar ta nufa tana faɗin waye.
shiru taji wanda ke Nocking bai Bata amsa ba ba'a kuma fasa Nocking ɗin ba,buɗe ƙofar tayi da ɗan faɗa faɗa tace “wai waye ke neman fasa ma mutane kunne da noc.......”
bata ƙarasa ba ganin wanda ke tsaye,wani kyakkyawan matashi saurayi ne tsaye yana sanye da wandon suit a jikinshi tare da shirt long sleeve mai maɓallai gaba,hannunshi riƙe da briefcase ɗin shi tare da rigar suit ɗin da bai sa ba.
tun daga ƙafafunshi dake sanye cikin leather shoes masu masifar kyau ta shiga kallo ,dogo ne ɗan dai dai fatan jikinshi fara ce tas,yanada broad chest tana iya hangen six pack ɗin shi saboda maɓallan rigar da bai sa duka ba ,hancinshi a tsaye yake ƙem ga wasu idanuwa masu jan hankali farare tas da su,launin ƙwayar idonshi ash color ce, pink lips ɗin shi ba ƙaramin ɗaukar ido su ke ba,yanada ɗan tsayin fuska ga wani kalar kwantaccen saje sai sheƙi yake,kwantacciyar sumar kanshi har saman neck ɗin shi ta sauka, fuskar shi a ɗaure take kamar wanda aka aiko ma saƙon mutuwa.
Tsuke fuska yayi ganin irin kallon da take mashi
“ya Irfan kai ne!!?” Yumnah ta faɗa
“ban sani ba,zaki ban hanya na wuce ko sai kin gama kallon nawa?” da sauri ta matsa mashi,wani wawan tsaki yaja yana kunna kai zuwa ciki.
A tsakiyar ɗakin ya tsaya
“ina yarinyar take?”
“tana toilet” ta bashi amsa,tsaki yaja yana juyawa ya nufi ƙofa
“idan ta fito ina parlorn mom ku same ni a can”
har ya kai bakin ƙofa, Nainarh ta turo ƙofar toilet ta fito jikinta ɗaure da towel iya gwiwarta ta saki sumar kanta har gadon bayanta.
“yawwa gata nan ma ta fito” Yumnah ta faɗa,sai a lokacin Nainarh ta lura da mutum a tsaye,juyowa yayi karab idanunsu suka shiga cikin na juna,tun daga kan shantala shantalan ƙafafunta farare ya fara kallo har izuwa kan pro khaki eyes ɗinta,kafe juna da ido su kayi kamar sun samu TV Yumnah na daga tsaye tana kallon ikon Allah.
Nainarh ce ta fara janye ido ta gabanta na wani irin mummunan faɗuwa,ƙaton namiji a gabanta gashi daga ita sai towel,da sauri ta nufi dressing room ɗin har tana tuntuɓe,da kallo kawai ya bita har ta shige cikin ɗakin,wani irin yanayi yake ji a tattare da shi wanda bai san minene ba.
Tsaki yaja,duk sai yaji haushin kanshi ya rufeshi ko miye a jikin yarinyar da ya tsaya yana kallo shi da kullum cikin ganin ƴan mata yake daban daban wanda su ka fita komai nesa ba kusa ba,duk sai yaji ya tsani kanshi,a zafafe ya juya ya fice yana sake jan wani tsaki.
da kallon mamaki Yumnah ta bishi har ya ɓace ma ganinta, dariya ta kwashe da ita tana nufar dressing room ɗin da sauri, a tsaye ta samu Nainarh gaban clothset ta kasa taɓuka komai jikinta har wani rawa rawa yake.
“wai da baki sa kayan ba,ya Irfan fa baya son jira yana iya tafiyar shi”
shiru Nainarh tayi, girgiza kai Yumnah tayi “na lura ba ƙaramar wahala zan sha ba wajen dawo dake dai dai”
Yumnah ta ɗauko mata kayan da zata sa,ficewa tayi ta bata wuri,shaf shaf ta shirya ta fito,ficewa su kayi daga ɗakin.
parlorn mom su ka je,wayam su ka samu parlorn ba kowa,hakan yasa su ka ƙarasa bedroom ɗin mom ita ka ɗai su ka samu.
“mom ina ya Irfan ɗin?”
“ya fice,ga magani nan ya bata,zo Nainarh,ya jikin naki?” ƙarasawa tayi gaban mom ɗin
“da sauƙi”
“Allah ya ƙara sauki,mi Irfan ɗin yace yana damunki?”
“mom ya Irfan fa bai dubata ba cewa yayi mu same shi a parlorn ki”
“amma yace ya dubata,ɗauko mata ruwa tasha maganin to”
da to Yumnah ta amsa tana ficewa daga ɗakin,dawowa tayi hannunta riƙe da glass cup na ruwa, Nainarh ta miƙamawa,mom ta Bata maganin tasha.
“kwanta ki huta kinji” mom ta faɗa, a saman bed ɗinta Nainarh ta kwanta Yumnah sai complain take ma mom akan Nainarh ta cika sa damuwa a ranta.
*UNITED STATE*
_*Las Vegas (Nevada)*_
*10:00 pm*
A hankali ta zuro ƙafarta dake sanye da flip-flops masu gashi gashi, bathrobe ce a jikinta yayin da kanta ke naɗe cikin short towel da alama daga wanka take.
masu aikinta ne su ka shigo su biyu,juyawa tayi ta nufi ƙofar HOME BEAUTY bin bayanta masu aikin su kayi.
Ɗakin ya haɗu sosai,yana da girma ba laifi,komai na cikin shi unique ne,beauty shelf ne manne jikin bangon ɗakin an jera kayan gyaran jiki kala kala dana gyaran gashi harda foot care product da skin care product masu tsadar gaske,ga wani faskeken mirror a jikin bango tun daga sama har ƙasa ,daga gabanshi tulip chairs ne guda biyu, daga can ɓangaren da skin and foot product su ke lounger chair ce.
nufar lounger chair tayi ta zauna miƙar da ƙafafuwanta tayi tana kwantar da kanta saman head ɗin chair ɗin haɗe da lumshe ido.
ɗaya daga cikin matan ce ta matso ɓangaren skin product ta buɗe, mayuka masu matuƙar tsada ta shiga fito da su,gyaran jiki ta shiga yi mata,cikin ƙanƙanin lokaci fatar jikinta ta riƙa wani glowing tana fitar da wani daddaɗan ƙamshi.
A hankali ta buɗe idon ta,sauka tayi daga saman kujerar ta nufi mirror dake ɗakin,ƙarema kanta kallo ta shiga,ta ɗan ɗauki tsawan mintoci tana kallon kanta a mirror kafin ta nufi ɗaya daga cikin kujerun dake gaban mirror ta zauna.
ɗayar matarce ta nufo inda take,warware mata short towel ɗin dake saman kanta tayi ,nan take sumar kanta ta zubo har saman bayanta,hairdryer ta jawo, busar mata da kan ta shiga yi,bayan data kammala ne ta ɗauko smoothing serum haɗe wide tooth comb,shafa mata ta shigayi tana taje mata kan,saidata tabbatar ya shartu tukun ta shiga kwarara mata hair oils masu daɗin ƙamshi tana cuɗa kan yanda oil ɗin zai shiga ko ina.
Nan take color ɗin kanta light gloden brown ya ciza sai ƙyalli yake da ɗaukar ido ga wani daddaɗan ƙamshi dake fita daga cikin shi.
Straightener ta ɗauka ta shiga miƙar mata da gashi,bayan data ta gama miƙar da gashin,half up half down style tayi mata a kan, ba ita da ake yima gyaran ba hatta su kansu masu gyaran ba ƙaramin tafiya da su kan yayi ba.
Kallon kanta tayi a mirror,ita kanta ta san baƙaramin kyau tayi ba,side smile ta saki, simple make_up su kayi mata,baƙaramin kyau tayi ba.
miƙewa tayi ta nufi wata ƙofa a cikin ɗakin wacce za ta sadaka da dressing room ɗin ta.
Masha Allah na furta a yayin da nayi arba da dressing room ɗin wanda idan ba an faɗa maka a gida ne ba zaka yi tunanin boutique ne,duk wani nau'i na sutura a kwaishi a cikin, hatta jakunkuna da takalma babu abun da babu.
Ƙatuwar wall drawer ce mai ɗauke da sliding door zagaye da ɗakin,daga waje kana iya hangen tarin suturun dake ciki,ɓangaren pajamas da ban,ɓangaren gwon da ban skirts, shorts, underwears, trousers,shirt, sweaters komai da ku ka sani nadaga ɓangaren sutura an ware mashi wajen shi,idan muka koma ɓangaren takalma da jakunkuna abun sai ya baka tsoro,takalma ne da jakunkuna iri iri ga su na.
daga tsakiyar ɗakin half drawer ce ajiye ƙasa doguwa wacce itama marfinta ya kasance na glass, tsawanta ya kusa tsawan ɗakin ta kwance,an kakkasata kashi kashi wanda bakomai ne a cikinta ba sai gold jeweleries,wristwatch, watch chain, watch glass, sunglasses,links,neak chain,rings,babu abun da babu na adon ƴa mace,komai na ciki daga gold sai zinari.
bango ɗaya na ɗakin mirror ne,daga gaban shi stool ne guda biyu masu kyan gaske,zama tayi kan ɗaya daga cikin stool ɗin,masu aikin ne su ka shiga zaɓo mata kayan da za su dace da fitar da za tayi,sun jima wajen ganin sun ɗauko mata kayan da su ka dace,kafin su ka dawo in da take zaune hannunsu riƙe da sexy summer bodycon dress masu matuƙar jan hankali.
gwada kayan su ka shiga yi a jikinta,duk wacce su ka ɗaura saita girgiza kai alamar ba tayi mata ba,haka su ka shiga gwada kayan,aƙalla sun gwada yafi kala ashirin har sun fara gajiya da gwada mata kayan sai da ƙyar su kaci sa'a ta zaɓi wata White color mai one shoulder tana da baza daga ƙasa,bazar taji adon sparkling stones masu matuƙar ɗaukar ido.
A jiyar zuciya su ka sauke ganin sunyi nasarar samarta wacce ta dace don baƙaramar wahala su ka sha ba wajen ɗaukowa da maidawa, ɓangare takalma su ka koma nan ma jido mata su suka shiga yi,duk wanda su ka nuna sai ta nuna baiyi mata ba sai da ƙyar su ka samu ta ɗauki wani high hill Pump black color masu shegen tsini.
Ɓangaren da jeweleries su ke su ka nufa,basu sha wata wahala ba wajen zaɓo mata ɗan kunne da sarƙa sai Agogo da chain ɗin ƙafa.
Turo ƙofar ɗakin a kayi aka shigo tun kafin ta ƙaraso ta san ko wacece ita ka ɗai ce a cikin ma'aikatan gidan ke da lasisin shigowa part ɗin ta ba tare da ta nemi izinin ba, su kansu na'urorin dake sarrafa part ɗin sun san da zamanta.
kyakkyawar matashiyar dattijiwa ce ta shigo,baturiya ce, sai dai duk da manyantar ta hakan bai nuna a fatarta ba,fatarta kamar ba ta tsohuwa ba, kyakkyawa ce ajin farko ,hancinta tsaye yake babu lanƙawasa bakinta ɗan dai dai, launin idonta sak irin na Nailar Acme white grey.
long sleeve shirt ce a jikinta tare da A_line skirt wanda ya wuce gwiwarta,sumar kanta dake da jefi jefi na furfura sai sheƙi take tana ɗaukar ido, simple make_up ne a fuskarta ba ƙaramin kyau yayi mata ba jikinta sai fitar da wani ni'imtaccen ƙamshi yake.
Aunty Sophia kenan ƴar ƙwalisar tsuhuwa ko budurwa bazata gwada mata iya ɗaukar wanka ba wasu abubuwan duk a wurinta masu Aikin Nailar ke koya,ta san ta kan fashion.
In da Nailar take ta ƙarasa fuskarta ɗauke da murmushi wanda yaba dimples ɗin ta damar lotsawa,ta cikin mirror Nailar ke hangenta, Murmushi itama ta sakar mata.
cikin girmamawa masu Aikin su ka shiga gaishe da Aunty Sophia,harara ta ɗan watsa masu da sauri su ka sadda kai saboda sanin laifin su na ƙin faɗa mata Nailar zata fita, hugging ɗin ta tayi ta baya.
“i miss U so much Aunty sopi,jiya shi ne kwata kwata baki nemi ni ba?” Nailar ta faɗa a shagwaɓe kamar ba ita ba, murmushi Aunty Sophia tayi tana miƙewa tsaye haɗi da juyo da stool ɗin da Nailar ke zaune.
“my baby na shigo fa kina bacci,bana son na takuraki ne shiyyasa na fice”
ɓata fuska Nailar tayi “dama na san babu wanda zai kashe man ear phone sai ke”
“nayi laifi kenan?” taɓe baki Nailar tayi“ dan kin san baki laifi a wajena shiyyasa ki ke yanda ki ka ga dama”
ƴar dariya Aunty Sophia ta saki wacce ta bayyanar da kyawawan haƙoranta.
juya mata baya Nailar tayi tana turo baki,kallon masu Aikin tayi da ido tayi masu alamar su fice,kayan dake hannunsu su ka ajiye saman table su ka fice.
cikin ɗakin Aunty Sophia ta nufa, ɓangaren underwears ta nufa,bandeau style top ta ɗauko mata haɗe boyshorts masu matuƙar jan hankali white color.
dawowa tayi wurin Nailar,miƙa mata tayi “am sorry idan na ɓata ran Queen,ga wannan kisa sai na idasa shirya gimbiyata da kaina” turo baki Nailar tayi
“ni bazan iya sawa ba” ɗan zaro ido Aunty Sophia tayi
“ƴata fa yanzu budurwa ce dole ta koyi wasu abubuwan da kanta ba sai masu aiki sunyi mata ba”
tashi Nailar tayi sai ɓata fuska take ta amshi kayan dake hannun Aunty Sophia, murmushi Aunty Sophia ta saki,cikin ɗakin ta nufa sai turo baki take.
saman ɗaya daga cikin stool ɗin Aunty Sophia ta zauna tana sakin murmushi ita ka ɗai ke kema Nailar haka a zauna lafiya,tana da matuƙar ƙima a idanun Nailar a kwai soyayya mai ƙarfi a tsakanin su, Nailar ta ɗauketa tamkar mahaifiyarta tun tana ƴar ƙaramarta Aunty Sophia ke kula da ita Nanny ɗinta ce hakan yasa su ka shaƙu,wani lokacin har cewa masu Aikin gidan keyi suna kama.
Dawowa Nailar tayi in da Aunty Sophia take ta cire bathrobe ɗin pant da bra ɗin ne kawai a jikinta, a gaban Aunty Sophia tazo ta tsaya,da sauri Aunty Sophia tasa hannu ta rufe fuskanta hakan da tayi ba ƙaramin dariya yaba Nailar ba.
“baby ya kamata ki riƙa jin kunya ta fa, yanzu ke ko a jikinki ki tsaya haka a gabana”
“dan mi zanji kunyarki,ni bana jin kunyar kowa”
“dama taya za kiji kunya bayan wannan tsinannun na maki wanka har yanzu” ta faɗa yayin da take zame hannunta daga saman idanunta
ƴar dariya Nailar ta saki “Aunty sopi wai har yanzu baki daina jin haushin Lara da Lolah ba”
“taya zan daina jin haushin su,wasu ƙatti da su kamar ƴan dambe kullum suna gane man jikin baby” ta faɗa tana tsuke fuska
tsawan shekaru abun na cimata tuwo a ƙwarya dan dai kawai bata da yanda za tayi,da tana iya hana Nailar wankan da aike mata da tuni ta hana hatta masu aikinta haushin yanda Nailar ta sakar masu komai na rayuwarta take ji ,ace comon sutura su za su cire su sa mata.
“zaki fara ƴan tunane tunanen naki ko,su fa basa da laifi,nice mai laifi sai dai idan ni zaki hukunta”
“zan hukuntaki ne mana idan har baki daina wannan san jikin hanzarce ba”
“shikenan yanzu tunda kin korar mansu sai ki ƙarasa aikin na su”
dungure mata kai Aunty Sophia tayi tana ɗaukar rigar da zata sa,ɗan sosa in da ta dungureta tayi “ karfa garin wannan fushin naki ki ɓata man gyaran kai na”
zura mata rigar Aunty Sophia tayi,ta zage mata zip,kallon yanda rigar tayi mata tayi a mirror
“yanzu haka zaki je maza suyi ta kallon jikin ki”
“iya kar su kallon,kuma ma Ni da nake zaune a office ina ruwana da su”
“kafin ki shiga office ɗin maza nawa zasu kalle ki musamman wannan ƴan iskan security guard ɗin naki masu fuskar sheɗanu”
“to yanzu wane kaya ki ke so na sa?”
Na jikinta ta nuna mata dariya Nailar ta saki “ kina so ajina ya zuba ko,ace na zama tsohuwa”
“zaki zama tsohuwar ne mara kunya” murmushi kawai Nailar ta saki,idan har kaji dariyar Nailar to tana tare da Aunty Sophia ko momyn ta,Aunty Sophia baturiya ce amma ɗabi'unta sun banbanta dana turawa.
sun ɗan ɗauki tsawan lokacin wajen shiryawa,ba ƙaramin kyau Nailar tayi ba kamar ka saceta ka guda,sosai rigar tabi shape ɗin jikinta,ƴar pose Aunty Sophia ta ɗauko mata tare da sunglasses mai shegen kyau pose ɗin taji adon stones multicolors sai ɗaukar ido take,wata ƴar locker Nailar ta nufa,ɗan duƙawa tayi saitin wata ƴar na'ura dake jikin locker ɗin,idanunta ta saita a jikin na'urar da alama Eye ID ne a jikin ƙofar,nan take ƙofar ta buɗe,ƙananan bindigu ne a ciki nau'i daban daban tare da bullet ɗin su,watama idan ka ganta zaka ɗauka lipstick ne,ɗaya daga cikin su ta ciro.
bullet ta ɗauka guda biyar ta zuba a ciki kafin ta ɗaga rigar dake jikinta,wani ɗan belt dake jikin boyshorts ɗin dake jikinta ta saka bindigar da alama anyi shi ne saboda haka.
maida locker tayi ta rufe,juyowa tayi tana kallon Aunty Sophia da tunda ta buɗe locker ta kauda kai,bata ma san ganin abunda ke ciki, murmushi Nailar ta saki tana ƙarasowa inda take.
A tare su ka fice daga ɗakin Aunty Sophia na faɗin ji take kamar kar Nailar ta fita Ita kuwa sai sakar mata murmushi take.
A parlor su ka samu masu aikinta su biyu na jiran su kowacce su ta ɗauki wankan suit black color,tunda su ka fito Aunty Sophia ke banka masu harara sai kace sune za fita da Nailar ba ita bace zata fita da su ba.
Elevator su ka shiga ta kai su a salin main parlor gidan wanda in ka shigo dashi zaka fara cin karo.
main entrance ɗin gidan su ka nufa,yanzu ma sai da ƙofar tayi scanning fuskar Nailar kafin su ka fice harda Aunty Sophia.
Harabar gidan ƙwanyar take da haske kamar da rana,motocin ne guda biyar a bakin ƙofar fitowa,huɗu baƙaƙe ne ƙirar HYUNDAI yayin da ɗayar ta kasance fara ƙirar Mercedes benz s class a tsakiyar su.
rissinawa security guard da masu aikin dake yawo jefi jefi su kayi suna gaishe da Nailar da Aunty Sophia,cikin kulawa Aunty Sophia ke amsa masu.
har gaban Mercedes benz ɗin Aunty Sophia ta raka Nailar,da kanta ta buɗe mata door ɗin ta shiga tana mata fatan dawowa lafiya,kissing hannunta Nailar tayi tana faɗin saina dawo,a dawo lafiya Aunty Sophia ta faɗa tana rufe mata marfin motar.
Motocin security guard ɗin su ka shiga tare da masu Aikin Nailar,Aunty Sophia na nan tsaye har su ka nufi gate ɗin gidan,sai da taga bata ganinsu tukunna ta koma ciki,ranta duk a jagule, ji take inama zata iya hana Nailar fita.
_*HEART OF VEGAS CLUB AND CASINO*_
Tun daga nesa zaka fara hangen hasken sparkling bulbs na haska saman building ɗin in da aka rubuta _* heart of Vegas club and casino*_ da wani irin style.
Tsarin ginin building ɗin ma kawai abun kallo ne,
A katafaren parking lot na club ɗin da ya ciki da tarin rides masu shegen kyau da tsada su kayi parking a wajen parking ɗin motocinta wanda ya kasance nata ne ita kaɗai su ka nufa.
Dai dai ta parking ɗin su su kayi, security guard ɗinta ne su ka fara fitowa tare da masu aikinta,ɗaya daga cikin su ne yazo ya buɗe mata marfin motar.
A hankali ta zuro ƙafafunta,kafin ta ƙarasa fitowa,gaba tayi suna biye da ita a baya,da wasu jibga jibgan security guard dake sanye cikin baƙaƙen kaya ƙugunsu soke da bindigu su ka ci karo a bakin entrance ɗin shiga,tun kafin ta ƙaraso su ka bata hanya suna ɗan rissanar da kansu Alamar gaisuwa,ko kallon in da suke ba tayi ba ta nufi security door ɗin shiga.
Wata irin katafariyar ƙofa ce wacce kai daga ganinta kasan ba ƙaramin waje bane,ƙofarce ta fara magana cikin harshen turanci
“welcome to Heart of Vegas,ur Access card please” da sauri ɗaya daga cikin masu aikin ta ciro wani ɗan card a pose ɗin Nailar dake hannunta ta mannashi a jikin ƙofar.
dan da nan ƙofar tayi acknowledging card ɗin tana faɗin“welcome miss Nailar”
nan take ƙofar ta shiga zugewa,ciki ta kunna kai suna biye da ita.
wani irin katafaren club ne su ka shigo,yaji kayan alatu kamar baza'a mutu ba,yana yin tsarinshi yasha ban ban da sauran clubs.
mata ne a tsaye a stage strippers cikin wata irin shaiɗaniyar sutura suna poll dance sauti na tashi,ga mata ga maza wasu a zaune wasu a tsaye suna taka rawa ana spraying dollars,wasu na shan giya,wasu na shaƙar cocaine,ga customize azul na yawo ta ko’ina ana kaiwa wayanda sukai order, gawasu kalan shisha da a irin wannan club ɗin kaɗai ake samun su, ga vape anasha suma,idan kashigo club din nan kai kanka kasan ana barin kuɗi, ga wasu irin security guards dake a different corner tsaitsaye da communicative devices a kunnensu kai kace gumaka ne yanda suka tsaya kiƙam ko alamar breath babu.
Kiɗan dake tashi ne ya tsaya,Dj ne ya shiga sanar da zuwan Nailar hakan yasa mutanen dake ciki kai duban su gareta,ihu da sowa ne ya fara tashi wasu na ambatar Queen wasu President,ƙayataccen murmushi ta saki tana ɗaga masu hannu,gun gun wasu maza ne su ka nufo in da take sai tangaɗi suke alamar sun sha sun sha sunyi tatul,da sauri security guard ɗinta su ka dakatar da su, murmushi gefen fuska ta saki tana yarfa masu ƴan yatsunta haɗi da ɗan cizon ƙasan lips ɗinta so sexy,ba ƙaramin jan hankalin mazan dake wurin tayi ba harda ma mata,ca su ka yi mata da idanu kamar tsaffin mayu ga nama suna kallo amma ba halin tunkara.
fly kiss ta sakar masu tana nufar glass elevator dake cikin wurin, security guard ɗin ta na biye da ita.
Wani irin ƙato casino su ka shigo,yaji kayan alatu a cikin uwar dukiya a ka narkar wajen gidana shi ba kaɗan ba ,da kaɗan ne bai ƙarasa girman club ɗin da su ka fara shigowa ba.
Wani irin casino Aesthetic ne mai matuƙar ɗaukar ido,ga wasu matsiyatan poker tables and gaming table haɗe da chairs ɗin su,casino cards ne a kowane table,a ƙalla ko wane table na ɗauke da chairs guda biyar.
Mata da maza ne zazzaune saman chairs ɗin, casino cards ne a gabansu suna buga caca ga tarin dollers da kowane a cikin ya ajiye a matsayin kuɗin wasan shi, nau'in beers ne masu tsadar gaske haɗe cigarettes wanda tsadar su ta kai mutum ya sayi gida da mota na mutunci a gaban su,wasu na shan giya wasu na zuƙar taba ana buga wasa kiɗa na tashi ƙasa ƙasa.
nan ma security guard ne a kowane corner tsaye ƙiƙam.
murmushi Nailar ta saki ganin yanda ake buga wasan,fito tayi wanda ya jawo hankalin mutanen dake wurin,ihu mazan dake wurin su ka saka suna faɗin QUEEN!!!!
dariya Nailar ta saki tana ɗaga masu hannu,wani ɗan corridor ta nufa,shuffle machines ne haɗe da slot machines, video poker and video lottery terminals a wajen, ma'aikata ne zaune saman poker chairs suna opreting ɗin su.
cikin girmamawa su ka shiga gaishe da ita kamar za su russuna mata,jin jina masu kai ta shiga yi, office ɗin ta ta nufa dake can floor ɗin ƙarshe,a bakin ƙofar shiga office ɗin security guard ɗinta suka tsaya masu aikin su ka bi bayanta.
wasu numbobi ta danna a jikin ƙofar nan take ƙofar ta buɗe,kutsa kai tayi ciki jelarta na biye da ita,wani irin katafaren office su ka shigo kamar na shugaban ƙasa,ga sanyin AC dake busowa kamar ƙanƙara,ƙaton transparent glass office table ne a ciki haɗe leather chair mai shegen kyau,laptop ce ajiye saman table ɗin haɗe office lamp,daga gefe 50gm ne na cocaine anyi packaging ɗin su sai Cuba Aliados cigarettes dake a cikin ƙana nan kwalayenta itama anyi packaging ɗinta sai kwalaben shisha nau'i daban daban masu tsadar gaske,ga ɗan madaidaicin bottle keeper wanda aka jera kwalabanan beers kala daban daban.
daga can gefe poker table ne wanda ke ɗauke da casino cards,sai faskekiyar glass computer dake ajiye anyi connecting ɗin ta da gaba ɗaya CCTV CAMERAS dake heart of Vegas.
Cikin office ɗin su ka ƙarasa,chair ɗinta ta nufa ta zauna yayin da masu aikin suka nufi wasu sofas guda biyu su ka zauna, laptop ɗin dake ajiye saman table ɗin ta buɗe,opreting ɗinta ta shiga yi a hankali.
Muryar na'urace ta karaɗe office ɗin tana sanar da zuwan MDs na gaba ɗaya club da casino ɗin, izinin shigowa ta ba da ta hanyar danna wani maddani a jikin table ɗin,a hankali ƙofar ta shiga zugewa,wasu murɗa murɗan ƙatti ne majiya ƙarfi su ka shigo cikin shigar baƙaƙen suit,gaban table ɗin Nailar su ka ƙara so.
gaishe da ita su kayi suna russunawa,amsa masu tayi tana nuna masu kujerun dake facing ɗinta,zama su kayi saman kujerun.
“is there any problem?”
“no ma,but kayan da Boss ta turo suna hanya,muna sa ran isowar su next tommorow around 2:00Am”
jinjina kai Nailair tayi“good,bayan nan babu komai?”
“yes”
“ok,take this” ta faɗa tana nuna masu packeg ɗin cocaine da cigarettes,miƙewa tsaye su kayi,ɗaukar kayan su kayi suna mata sallama haɗi da ficewa.
tura kujeran da take zaune tayi,ƙafafunta ta ɗaura saman table ɗin tana jinginar da kanta saman head ɗin kujerar,ɗaya daga cikin masu aikin ce ta miƙe,can cikin office ɗin ta nufa,bata jima a sai gata ta fito hannunta ɗauke da ƙatuwar kwalbar champagne haɗe da champagne tulip glass sai ice a cikin bowl,har gaban table ɗin Nailar ta ƙaraso,ajiyewa tayi,ice ɗin ta fara zubawa a cikin cup kafin ta buɗe kwalbar, tsiyaya mata tayi cikin cup ɗin ta miƙa mata,amsa tayi tana wani lumshe ido.
barin wajen tayi,komawa tayi ta ɗauko masu milkshakes guda biyu,duk yanda su ke son shan kayan shaye shaye Nailar ta hana sai dai su sha lemu ko milkshake.
wayarta ce ta fara ringing,kallon screen ɗin tayi love shine sunan daya bayyana, murmushi ne ya bayyana a fuskarta, picking call ɗin tayi tana kara wayar a kunne.
“sweetheart” shine sunan da Nailar ta furta,on the other hand murmushi ta cikin wayar ta saki
“baby nah ya ki ke,ya gidan” ɓata fuska Nailar tayi “babu daɗi,yaushe zaki dawo?"
“kinyi kewata ne?”
“i really miss u, please come back home” Nailar ta faɗa kamar zata sa kuka
murmushi ta saki
“i think next week,fatan kina office?”
“momy mai makon ki tambayi lafiyata amma ta office ki ke,wai tsaya dani da wannan business ɗin ma wa ki ka fi so ne?”
“nafi sonki sama da komai, sorry fatan kina lafiya”
“lafiya lau,fatan kema haka”
“ina lafiya kamar yanda ki ke,kina office ɗin?”
ɓata fuska Nailar tayi
“yes,su Joseph sun sanar dani kayan da ki kayi order suna hanya?”
“yes, Please my baby ki kasance a wurin lokacin da shipment ɗin zai ƙaraso bana son any problem ya faru, kaya ne masu tsadar gaske, munada tarin customers a ƙasa wanda zuwan kayan kawai su ke jira”
“please momy,su Joseph za su iya ji da komai ba sai naje ba”
“no kije dai zaifi,zan turo maki komai ta email,ki tabbatar ba wani kuskure”
turo baki Nailar tayi ba tare da tace komai ba da alama ba taji daɗi ba,sallama su kayi, ajiye wayar tayi saman desk tana lumshe ido haɗe da sakin ɗan ƙaramin tsaki.
Sai Around 5:00Am ta koma gida a gajiye,ko kayan dake
jikinta bata cire ba ta faɗa saman bed,ficewa masu aikin su kayi bayan sun ajiye mata bag ɗin ta haɗe da wayarta.
Aunty Sophia da saurinta ta zo amma sai ta tarar tana bacci, murmushi kawai tayi taja mata blanket,kissing forehead ɗinta tayi ta fice daga ɗakin...
_Ep 13_14_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
______________________________
*ABUJA NIGERIA*
Turus ta tsaya ganin ko kallon dinner ɗin da aka kawo mata ba tayi ba, kallonta ta kai zuwa bed ɗin dake ɗakin, a zaune take ta jingina da head bord ɗin gadon,photon mahaifiyarta tare da mahaifinta ne riƙe a hannunta sai aikin shafawa take yayin da hawaye ke sintiri a fuskarta.
girgiza kai Yumnah tayi yayin da take ƙarasawa bakin bed ɗin, zama tayi kusa da ita tana dafa kafaɗarta,cikin sigar lallashi ta fara magana.
“sister Nainarh na san abun da ciwo, nasan zai ɗauki lokaci kafin zuciyarki ta dake, sai dai ki sani yawan ku ka da sa damuwa a rai bashi ke maganin matsala ba Adu'a itace maganin duk wata matsala, a halin yanzu Adu'arki su ke buƙata sama da komai, in sha Allah komai daran daɗewa gaskiya za tayi halinta, in dai da rai wata rana a gabanki duk wani mai sa hannu a al'amarin zai zo a ƙasƙance dan neman yafiyarki,dan haka ina so ki daina yawan kukan nan da sa damuwa a ranki”
shiru Nainarh tayi tana sauraron Yumnah, hannu Yumnah tasa ta shiga goge mata hawayen dake zuba daga fuskarta tana sake kwantar mata da zuciya.
“kiyi haƙuri kinji,komai zai wuce in sha Allah”
“na kasa mantawa da irin kisan wulaƙancin da a kayi ma mahaifana,a gaban su ka kashe shi amma Court ta ɗaura laifin a kan mahaifiyata ba tare da tausayin halin rasa mijinta da take ciki ba”
“Allah ya fisu Nainarh,duk wani mai sa hannu asirin shi zai tonu,ki kwantar da hankalinki komai zai wuce mahaifiyarki zata dawo gare da izinin Ubangiji,ki daina kuka kinji” jinjina mata kai Nainarh tayi,sosai Yumnah ta shiga kwantar mata da hankali,har ta samu ta ɗan saki jikinta.
*ASO VILLA*
Kyakkyawar matashiyar matace kwance saman makeken gadon ta,daga yanayin yanda numfashinta ke fita zaka fahimci ba ta cikin kwanciyar hankali.
Wani mahaukacin Nocking a kayi ma ƙofar ɗakin wanda yayi sanadiyyar farkawar ta,a firgice ta farka tana ambaton Innalillahi wa Inna Ilaihi rajiun,sake nocking ɗin a kayi kamar za'a ɓalla ƙofar.
Waro kyawawan idonta tayi tana kallon ƙofar gabanta na wani irin lugudan duka, Adu'a ta shiga yi Allah yasa ba shi bane duk da ta san babu wanda zaiyi mata wannan Nocking ɗin a irin wannan lokacin bayan shi.
Wata irin kakkausar murya wacce kenuna mamallakinta a buge yake taji daga bakin ƙofar ɗakin
“KAINART wai uwar mi kike a ciki ne da bazaki zo ki buɗe man ba, wallahi ki ka bari na shigo da kaina sai kin yaba ma aya zaƙinta” ya faɗa yana sake kaima ƙofar wani mahaukacin duka.
hawaye ne su ka wanke fuskarta dama ta san zaiyi wuya ace ba shi bane,ita kam yau ta shiga uku dan daga yanayin muryar shi baya a cikin hayyacinshi,banko ƙofar yayi kamar zai karyata, da gudu ta duro daga saman gado jiki na rawa ta kama handle ɗin ƙofar ta buɗe mashi.
matashin magidanci da aƙalla zai kai kimanin shekaru 32 zuwa da 3 a duniya,baƙaƙen suit ne a jikinshi yayinda hannunshi ke riƙe da ƙatuwar Whiskey , kyakyawane sai dai munanan ɗabi'un shi sun boye kyawun fuskarshi.
cikin ɗakin ya ƙaraso yana huci kamar wani mawuyacin zaki, jifa yayi da kwalbar dake hannunshi ƙasa ta tarwatse sauran ruwan dake ciki ya malale a ƙasa,ja da baya tayi ganin irin kallon ƙasƙancin da yake mata, cikin rawa murya tace
“dan Allah ya Zaabith kayi....” bata ƙarasa ba ya wanketa da lafiyayyun maruka har sau biyu,dan da nan jinta da ganinta su ka ɗauke na wucin gadi taurari ta fara gani suna mata shawagi a cikin idanunta, bata dawo daga hutun marin da yayi mata ba taji saukar belt, dukanta ya shiga yi kamar ya samu jaka.
kuka take tana ambaton “dan Allah ya zaabith kayi haƙuri, na tuba bazan sake ba” ko saurarenta baya yi dukanta kawai yake kamar an aiko shi,bai ƙyaleta ba sai da ya tabbar ya sauya mata kammani tukun ya jefar da belta ɗin ƙasa,wuyan rigarta ya cakumo yana manne bakinshi da nata,kamar zai cire mata baki haka ya shiga kissing ɗinta,cikin rashin imani ya shiga yayyaga suturar dake jikinta, doguwar sumar kanta ya jawo kamar zai cire mata ita yayi jefa da ita saman gadon babu tausayi ko imani ya shiga biyan buƙatar shi da ita, sai da ya tabbar ya kusa kasheta tukun ya ƙyaleta ya miƙe,yana tangaɗi ya nufi wata ƙofa wacce nake kyautata zaton toilet ne.
wani sabon kuka ta saki ta rasa wannan wace irin rayuwa take, ko baiwar da aka siyo ba'a wulaƙantata kamar yanda Zaabith ke mata kuma a haka wai ita ɗin matarshi ce ta sunnah wacce su kayi Auren soyayya bana ƙiyayya ba,wasu zafafan hawayen ne suka sake wanke mata fuska.
da jan jiki ta sauko daga saman bed ɗin,blanket ɗin dake shimfiɗe taja ta rufe jikinta,a daddafe ta nufi ƙofar fita, ficewa tayi daga ɗakin, a hankali take tafiya tana ƴan waige waige gudun karta haɗu da wani ko masu aikin gidan su ganta a irin wannan yanayin, Allah ya taimaketa har ta kawo bakin ƙofar wani ɗaki bata haɗu da kowa a hanyar ba, tura ƙofar ɗakin tayi ta shige,mai da ƙofar tayi ta rufe da key,a jikin ƙofar tabar key ɗin,yara ne ƴan maza guda biyu kwance saman makeken bed ɗin dake ɗakin cikin shigar PJ white color, sai sharar baccin su suke hankali kwance.
Ƙofar toilet ta nufa, tsarkake jikinta tayi,sannan ta gasa jikinta da yayi mata tsami, bathrobe ta zura a jikinta ta fito,zuwa tayi tsakiyar yaran ta kwanta bayan ta kashe light ɗin ɗakin,hugging ɗin yaran tayi ajikinta yayinda hawaye ke sintiri zuba daga idanunta, tsawan shekara goma kenan da yin Auren su,shekara ɗaya kawai su kayi suna shan soyayya amma tun daga nan komai ya lalace kullum cikin fuskantar azaba take daga Zaabith duk wasu munanan halayenshi babu wanda bai nuna mata ba, ya fita gida sai sanda yaga dama zai dawo,idan ya koma wajen Aiki Lagos sai yayi wata da watanni bai dawo ba duk ranar da zai dawo a buge yake dawo mata kuma a ranar ta shiga uku, iyayenshi sunyi faɗa sunyi faɗan sunyin jan hankalin amma a banza,duk da fara tara iyali da su kayi bai sa ya canza halayen shi ba.
tayi tunanin zaman su a gidan gomnati zai sa ya canza ɗabi'un shi kodan gudun zubar mutuncin mahaifin shi da siyasarshi a idon duniya,amma a banza saima abun da yaci gaba gashi duk wannan uƙubar da take ciki ta kasa sanar da iyayenta duk dan gudun lalacewar zumunci dake tsakanin su saboda mahaifin Zaabith yaya ne ga mahaifinta uban su ɗaya.
ta jima tana saƙawa da kwancewa har baccin wahala yayi awan gaba da ita rungume da ƴaƴanta, lokacin da ya fito daga toilet ɗin ƙugunshi ɗure da towel, kallon gadon daya barta a kwance yayi, ganin wayam bata nan me yasa shi jan wani mahaukacin tsaki yana faɗin “zan kamaki ne yarinya”.
ƙofar fita shima ya nufa, ficewa yayi daga ɗakin zuwa master bedroom ɗin shi, yana shiga ɗakin a saman gadon shi ya faɗa rub da ciki babu Adu'a babu komai,cikin ƙanƙanin lokaci bacci yayi awan gaba dashi.
*WASHE GARI*
Tunda Asussu ba ta koma ɗakinta ta gyara gudun masu aiki su ganshi haka bata son su zargi wani Abu,duk da irin azabar da take sha a wajen shi har kawo wannan lokaci tana son shi tana kuma yi mashi kallon uban ƴaƴanta, Adu'arta a kullum Allah yasa ya gane kuskuren da yake aikatawa.
shaf shaf ta gama kauda komai,toilet ta shiga wanka tayi haɗe da Alwala,fitowa tayi ta nufi cloth set ɗin ta,doguwar rigar Abaya ta ɗauko ta zura a jikinta,da ƙyar ta zura rigar a jikinta saboda ciwukan da taji a dalilin dukan da yayi mata duk ya faffasa mata baya,sawun duka har saman wuyanta ga marin da yayi mata, ta san dole sawun hannunshi ya fito.
a saman kai ta ɗaura mayafin Abayar tukun ta ɗauko hijab,ficewa tayi daga ɗakin dan ta san a kowane lokaci zai iya dawowa.
Bedroom ɗin yaranta ta koma,a kwance ta same su kamar yanda ta barsu, tashin su ta shiga yi domin lokacin sallah yayi,ɗaya bayan ɗaya su ka shiga toilet su ka ɗauro Alwala,jallabiya ta ɗauko masu cikin kayan su, cire PJ ɗin dake jikin su suka yi suka zura jallabiya.
“momy Dady ya dawo ko??”faɗuwa gabanta yayi dalilin tambayar da yaron yayi mata.
“Eh ya dawo tare ma za ku tafi masallaci,yana ɗakin shi kuje ku same shi”
“momy shine ya dake ki ko” faɗuwa gabanta ya sake yi
“shine ko momy??” yaran su ka sake jefa mata tambayar
saurin ƙaƙalo murmushi tayi tana girgiza masu kai alamar A'a
“shi ne mana momy,ga sawun duka nan a fuskar ki”
“faɗuwa nayi Ammar ba duka bane”
“duka ne mana,gashi nan sawun hannunshi ne a saman fuskar ki”
“momy mun gaji da dukan ki da dady yake,sai mun rama maki dukan da yake maki yaji shima idan da daɗi,kuma sai mun sanar da grandfa har yanzu bai daina dukanki ba”
duk yanda take daurewa kasawa tayi hawaye ne su ka wanke fuskarta,tun tana ɓoye masu yanzu yaran babu abunda ba su sani ba game da irin zaman iyayen na su.
hanyar fita su ka nufa suna sai sun faɗama grandfa Aman har ya fara zubar da hawaye,da sauri tabi bayan su,jawo su tayi zuwa jikinta, hugging ɗin su tayi.
“kuyi haƙuri Aman kar ku sanar da dady Ahmad,dadyn ku bada gangan ya mareni ba ya bani haƙuri bazai sake ba”
“momy kullum haka yake faɗa,amma har yau bai daina ba,kinga da gangan yake dukan ki”
“duk da haka Ammar shi ɗin fa mahaifin ku ne,idan baku rufa mashi asiri ba waye zai rufa mashi,kuyi haƙuri kunji ko,ku yafe mashi nima na yafe mashi”
sake shigewa su kayi jikinta suna sakin kuka,wasu hawaye ne itama su ka wanke fuskarta,ɗan bubbuga bayan su ta shiga yi
“ya isa haka ku daina kuka kun ji,zai daina wata rana” raba jikin su ta yi,hannu tasa ta shiga goge masu hawayen fuskar su.
“kuje yana ɗaki ku same shi” maƙe mata kafaɗa su kayi
“mu dai tare da grandfa zamu tafi da su uncle Waseef”
“ki bar mu kawai momy muje tare da grandfa”
“shikenan sai kun dawo,Allah yayi maku Albarka”
da Ameen su ka amsa suna nufar ƙofar fita,turo ƙofar ɗakin da a kayi ne ya dakatar da su,gaba ɗayan su suka kai dubansu gare shi.
farar jallabiya ce a jikinshi,jikin shi da alamar danshin ruwan da yayi alwala,cikin ɗakin ya ƙaraso,hannuwan shi biyu ya buɗe ma yaran alamar su zo gareshi fuskar shi a sake.
tsuke fuska su kayi suna bin shi da wani irin kallon tsana,lamarin yayi matuƙar ɗaure mashi,da sauri ya kai duban shi ga kainart dake tsaye tana kallon su,saurin kauda kai tayi kamar ma bata ga abun da su Ammar ɗin su kayi mashi ba.
ta gefen shi su ka zo za su wuce,saurin kamo hannun su yayi,wayancewa yayi irin kamar ma bai fahimci mi yaran su ke nufi ba “ fushi ku ke da dady saboda bai dawo da wuri ba,kuyi.....” bai ƙarasa ba saboda fisgewa da su kayi daga riƙon da yayi masu,ƙofar fita su ka nufa ba tare da ko sun kalli inda yake ba,baki ya saki kamar saka rai wai yau shine su Aman su kayi ma haka,mi hakan ke nufi mahaifiyar su ta fara hure masu kunne ke nan.
yana nan tsaye har su ka ɓacce ma ganin shi,jinjina kai yayi yana nufo in da take,da sauri ta ɗauki hijab ɗin ta zata zura a jikinta,a zafafe ya fisge hijab ɗin yayi jifa da ita,damƙara sumar kanta yayi,rintse ido tayi saboda zafin daya ziyarci kanta.
“wato raini ya fara shiga tsakanin mu ko,har kin fara tara yara kina gaya masu ina dukan ki ko,a tunaninki dan kin sanar da su hakan zai canza wani Abu ne,ki sani a duk faɗin duniyar nan babu wani wanda ya isa ya hanani abun da nayi niyya ko da kuwa mahaifina ne,dan na san shi ki ke tunanin zai iya hanani??”
cikin ƙunar rai tace “a tunanin ka ya Zaabith su Ammar ba su san abun da ka ke aikatawa ba ne?,ko a tunaninka ba su da wayan sanin abun da kake aikatawa ,karka manta kasha dukana a gaban su dan mi baza su ji haushin ka ba,nifa mahaifiyar su ce”
fisgar kanta yayi kamar zai cire shi gaba ɗaya “to sai mi dan sun sani,ke baki isa ki shiga tsakani na da su ba saboda ni ɗin mahaifin su ne ko suna so ko basa so”
fashewa tayi da kuka
“kaji tsoron Allah ya Zaabith,ka sani alhakin mu bazai barka ba,Allah zai saka m...” tsawa ya daka mata
“ya isa haka” ya faɗa yana sakin gashin kanta,idan da abun da ke tada hankalinshi ta furta Allah zai saka mata baya son tana barin shi da Allah, yana tsoron ranar da Allah zai tashi saka mata.
ƙofar fita ya nufa,da kallo ta bishi har ya fice hawaye sai sintiri suke a fuskarta.
hijab ɗinta ta zura, prayer mat ta shinfiɗa,gabatar da sallah ta shiga yi,ta jima zaune tana kai ku kanta ga Ubangiji sammai da ƙassai.
Tana a nan kwance a kayi Nocking ɗin ɗakin, tambayar waye tayi ba tare da ta tashi ba.
“saraj ce dama madam Salima ce tace ki fito time ɗin breakfast yayi,takuma ce anjima za ku je can family house ɗin ku”
“bana jin daɗi sarah,ki kawo man nawa breakfast ɗin nan kawai”
“to shikenan,ya zance ma Madam ɗin?”
“ki faɗa mata bana lafiya”
“to shikenan” mai aikin ta faɗa tana barin wajen,bayan kamar minti biyar mai aikin ta dawo.
iznin shiga Kainart ɗin ta bata,a hankali ta turo ƙofar ɗakin ta shigo hannunta ɗauke da tryan data haɗa mata breakfast ,saman ɗan table ɗin dake ɗakin ta ajiye mata.
“sannu madam,Allah ya baki lafiya”
“Ameen sarah,su Ammar na wajen dady ne?”
“eh suna can harda yallaɓai Zaabith”
“ok shikenan zaki iya tafiya”
“ok Allah ya ƙaro sauƙi” da Ameen kainart ɗin ta amsa,ficewa mai aikin tayi.
* Big Daddy's house*
Mom da ya Naeem ne zaune a saman gondola chairs dake cikin garden ɗin gidan,ɗan madaidaicin glass table ne a gaban su an cika masu shi da fresh fruit haɗe da snacks, yayin da mom ke riƙe da wasu takardu a hannunta sai jujjuyasu take,
kallonta ya Naeem yayi “mom kinyi shiru ba kice komai ba?”
ɗan sauke ajiyar zuciya tayi tana kallon ya naeem ɗin daya kafeta da idanu,takardun dake hannunta ta miƙa mashi
“ban san ta in da zan fara maka bayani ba ne naeem”
“koma ta yayane ki fara mom Zan fahimce ki in sha Allah”
jinjina kai mom tayi “wani taimako nake so kayi mana game da case ɗin Asma'u”
“umarni za kice mom,Dan kinfi ƙarfin neman taimako a gare mu,mi kike buƙata nayi maki a kan case ɗin?”
“yawwa,ina so ka sake wani sabon bincike a kan case ɗin bayan wanda jami'an tsaro su kayi”
“amma mom saboda mi?”
“naeem zuciyata ta kasa yarda cewa Aminiyata zata iya aikata wannan laifin ,duk da ɗan Adam yana canzawa akan yanda ka san shi amma ita ina kyautata mata zato”
“shikenan mom in Sha Allah zanyi yanda ki ke so ,amma dole sai na samu wasu ƙarin bayanan sama da wannan da ki ka bani”
“wanann ba damuwa bace,ko a wajen yarinyar ta zaka iya samun wasu baya nan,sannan akwai masu aikin gidan da masu gadi duk da sun bada bayanan su a court da wurin ƴan sanda sai dai bayanan na su ban gamsu da su ba, ina ji a raina kamar sun ɓoye wani ko wanda su ke da alhaki a kan kisan su suka hansu faɗar gaskiya”
“shikenan ba damuwa mom ko da sun ɓoye wani Abu nayi maki alƙawarin sai sun magantu dole za su faɗi gaskiya”
“yawwa haka nake son ji,amma ina so ya zama sirri kai ka ɗai nake so kayi aikin sai wanda ka yarda da dashi daga cikin yaran ka wanda kasan bazai yaudareka ba”
“karki damu da wannan mom,komai zai tafi yanda ki ke so in sha Allah”
jinjina kai mom ɗin tayi “bayanan komai yana a cikin takardun nan”
“zaka samu komai a ciki,tun daga tarihin rayuwar su, sunayen mutanen da suke mu'amula da CP lokacin da yana raye da ita kanta Asma'u da duk wani ma'aikacin su,hatta ƙasashen da su ke yawan zuwa da garuruwa da wurare da su ka fi yawan zuwa a faɗin ƙasar nan zaka samu, Naeem kar kayi sakace da su duk da na san ba halinka bane amma ka kula da su sosai akwai baya nan da ko Court bata san da zaman su ba naƙi bayyanar da su ne a gabanta saboda wasu dalilai nawa, dan Allah ka maida hankali a kan su Naeem”
ɗan dariya ya Naeem yayi “dama na daɗe ina zargin tsakanin ke da dady wa SAM ya gado naci da bin ƙwaƙwafi case Ashe ke ce?”
murmushi mom ta saki “bana son shashanci Naeem,wannan case ɗin karka manta Aminiyata ce a ciki kaga kuwa dole na nace akan shi”
“haka ne in sha zan baje gaba ɗaya ilimina akan wannan case ɗin,zanyi ƙoƙarin ganin munyi nasarar fitar da momy in sha Allah”
“haka nake son ji,ka ko yi waya da SAM?”
“A'a,mun kwana biyu ba muyi waya ba,kin san ɗan naki sarki ne sai ya sha iska yake neman mutane gashi ko ka kira shi a banza idan ba yana free ba shine zai ɗaga ko idan yaga missed call ya kira”
“nima kwana biyu bai kirani ba,amma Alyar da James sun kira ni kuma sun shaida man yana lafiya,aiki ne yayi mashi yawa”
“nima Alyar ya kirani harma ya ke sanar dani suna nan zuwa ƙarshen shekarar nan shi da James,na dai ce su lallaɓa SAM ɗin nima zan gwada sa'ata ko za'a samu wannan karan ya biyo su”
“duk lokacin da mu kayi waya dashi sai na roƙi Alfarmar ya taimaka ko kiran dadyn ku ne yayi a waya ko ya tura mashi message ko da bai zo ba amma ina,baƙar zuciyar dana rasa awajen wa ya gadota taƙi barinshi,harda momy da Uncle Jonas nasha haɗashi saboda yafi jin maganar su sama da tawa amma a banza sunyi sunyi yaƙi, ko da picking call ɗin dadyn ku ne yayi idan ya kirashi amma ina”
“in sha Allah mom wata rana da ƙafarshi zai tako ya zo har ƙasar nan saboda dady,komai zai wuce”
“bana tunanin SAM zai yafe ma dadyn ku,ya riƙeshi sosai a zuciyar shi,tsawan shekara 18 fa kenan”
“mom ki daina wannan tunanin in sha Allah zai yafe mashi wata rana,koda shekara 50 ne,ke da ma yayi ma laifin ki ka yi haƙuri bare shi SAM ɗin,zai dawo da kanshi saboda dadyn in sha Allah”
“Allah yasa haka Naeem”
“in sha Allah mom,wata rana komai zai wuce har jikokin SAM ɗinki za ki gani a gabanki dan na san burinku kenan ke da Dady”
murmushi ta saki “Allah yasa haka,da kuwa nayi farin ciki mara misaltuwa”
“Ameen mom,ni zan wuce gida”
“ok muje nima zan koma ciki” tashi su kayi, jerawa su kayi a tare su ka nufi ƙofar cikin gidan.
part ɗin dady su ka nufa,a kishingiɗe su ka same shi saman rug carpet yana duba wani littafin addini,bakin su ɗauke da sallama su ka ƙara da ciki,ɗagowa dady yayi yana amsa masu sallamar.
kusa da shi ya Naeem ya zauna mom kuma ta zauna saman kujera
kallon su dady yayi fuskarshi a sake yace “uwa da ɗa daga ina haka,wani abun daɗin ya faru ne”
murmushi ya Naeem yayi “barka da hutawa dady”
“barka dai Naeem,ya Aiki yau ba ku shigo tare da Adnan ɗin ba?”
“Eh kila sai anjima zai shigo”
“Allah ya kaimu anjimar lafiya,na shiga wurin Abbah ɗazu yace kwana biyu bai saka a idon ba ina fatan dai lafiya?”
“Ayyuka ne su ka ɗan yi man yawa kwana biyu shiyyasa ban shiga ba na bari sai ranar juma'a”
“duk da haka Naeem tunda har kana samun lokacin shigowa nan ai ka ɗan leƙa ku gaisha ko da da dare ne”
“in sha Allah daga nan zan shiga”
“yawwa hakan yayi,Allah yayi maku Albarka”
“Ameen dady” ya Naeem ɗin ya faɗa yana miƙewa,sallama yayi masu ya fice.
*Main Parlor*
da sauri yaja baya saboda karon da yayi da mutum,duban shi ya kai ga matashin saurayin dake tsaye a gaban shi sai layi yake kamar zai faɗon mashi,da tsantsar mamaki yake bin saurayin dake neman ya raɓa ta gefenshi ya wuce,a wani zafafe ya fisgoshi baya,saukar maruka matashin saurayin yaji a saman fuskar shi wanda su kayi sanadiyyar dawowar shi cikin hayyacin shi,da sauri yasa hannuwanshi ya dafe kumatunshi.
ɗan uwan shi dake bayan shi ganin irin marin da ya Naeem ya sauke ma ɗan uwan nashi ne yasa shi komawa baya cikin sanɗa ya koma parking space ya shige motar da su ka zo,mai da ƙofar yayi ya rufe a hankali,shiru yayi yana baza ido a hanya ko zaiga wucewar ya naeem.
tun daga kan crazy short ɗin dake jikin shi da ƴar iskar shirt ɗin dake jikinshi mai kama da rariya zuwa ɗan iskan askin dake kanshi ya Naeem ke kallo,ga wani chain dake manne a wuyan shi kunnenshi ɗaya a huje yake ya saka ear ring.
wani marin ya Naeem ya sake kifa mashi,dafe kuncinshi yayi sai ga hawaye shar da alama marin ya shige shi sosai
“dan Allah second father kayi haƙuri,wallahi bangaka bane shiyyasa na bigeka” saurayin ya faɗa yana watso ido kamar tsohun kwarto a kan ya Naeem.
“daga gidan ubanwa kake haka?” ya naeem ya faɗa yana cakumo wuyan rigar shi
cikin rawar murya yace “wallahi daga islamiyya muke Ni da YAZDAN,yazdan dan Allah ba daga can muke ba” ya faɗa yana waigawa bayan shi wayam ya gani babu yazdan
“wallahi daga can muke” ya sake faɗa yana kallon ya naeem,dariya ma maganar tashi ta so ba ya naeem in ba ya ɗauke shi ɗan iska kamar shi ba taya zaice mashi daga islamiyya yake da irin wannan shigar ya yarda,ta ina ma yayi kama da mai zuwa islamiyya.
“saboda ka ɗauke ni shashasha kamar kai ko”
“wallahi ka tambayi yazdan daga can muke mun shiga gida ne muka canza kaya”
“in tambayi abokin cin
mushenka ko,zan kamashi ne shima”
“Allah ba ƙarya muke ba”
“to naji, karanta man abun da aka koya maku yau ko ka kwana kana frog jump”
da ƙyar ya haɗe yawu jin abunda ya naeem ɗin yace,raba ido ya shiga yi kamar wanda yayi ma sarki ƙarya
“oya kai nake saurare” ya naeem ɗin ya faɗa fuska a tsuke yana harɗe hannuwanshi a ƙirji
nan fa ido ya raina fata,ƴan kame kame ya fara,ran ya naeem ne ya fara ɓaci,cakumo kwalar rigar shi yayi yaja shi ƙiiii zuwa waje,yazdan na ganin haka yayi saurin kwanciya cikin motar sai zare ido yake.
ɗaya daga cikin sojojin dake shawagi cikin Estate ɗin ya Naeem ya kira,da sauri sojan ya ƙaraso,ƙato ne bana wasa ba,daga bakin parking space zuwa bakin main entrance ɗin shiga gidan ya Naeem ya nuna ma sojan
“ka sashi frog jump ko sau ɗaya ya tsaya ka kirani”
“ok sir” sojan ya faɗan yana sakin murmushi dama rana irin wanann yake jira saboda yaron ya raina su kwata kwata baya ganin su da ƙima ya raina su.
barin wurin ya Naeem yayi ya nufi motar shi,shiga yayi,key yayi ma motar ya bar wurin.
“amma wallahi second father ya gama dakai FA'IZ,ya rasa wa zai sa ya hukunta ka sai waɗannan ƴan iskan sojojin, tir wallahi” yazdan ya faɗa yana buɗe marfin motar ya fito
“oya start,ko yanzu na kira shi” sojan ya faɗa yana kallon Fa'iz ɗin dake tsaye yana binshi da kallon ƙasƙanci
“an gaya maka tsoron shi nake ji ne?”
“wannan kuma matsalar kace,zaka fara ko sai na kira shi?” sojan ya faɗa yana zaro wayar shi daga Aljihu
“kai dallah malam dakata,ce maka a kayi bazan yi ba ne?”
“to fara idan ba so kake na kira shi ba”
tsaye Fa'iz yayi sai ƴan kalle kalle yake,yana tsoron ya Naeem amma bai son ajinshi ya zuba a gaban securitys ɗin gidan.
yazdan ne ya ƙaraso wajen shima sai layi yake kamar zai faɗi ƙasa,kayan jikinshi iri ɗaya ne dana Fa'iz sai dai shi kanshi kitso ne saɓanin Fa'iz dake da aski
“malam ai sai ka tafi ko” yazdan ɗin ya faɗa yana ma sojan kallon rainin wayau.
“na tafi saboda kai ka sani ko?”sojan ya faɗa ,kallon fa'iz yazdan yayi su ka kwashe da wata ƴar iskar dariya “cewa za kayi na shan fura kake so,ai da kayi magana”
Fa'iz ne ya zura hannu cikin Aljihu ya ciro bandir ɗin dollers ya watsama sojan yana jan hannun yazdan “zo mu tafi kaji”
ran sojan ne yayi matuƙar ɓaci hakan yasa ya fisgo rigar Fa'iz ɗin “kai har ni zaka wulaƙanta?” sojan ya faɗa
“an wulaƙanta ka,dama can kai ba wulaƙantaccen bane,maza ka sauke hannunka saman jiki na ko ranka yayi mummunan ɓaci yanzu” Fa'iz ya faɗa dai dai jiniyar motocin sojoji na tunkaro gidan,da sauri Yazdan ya duƙa ya kwashe kuɗin.
mota biyu ce ta security guard ta nufo parking space ɗin yayin da su ka sako wata baƙar Nissan a tsakiyar su, parking motocin su kayi,da gudu security guard ɗin su ka shiga fitowa suna nufar baƙar Nissan ɗin dake tsakiyar su, ɓack seat ɗin motar ɗaya daga cikin security ya buɗe.
Wata kaykyawar mata ce ta fito cikin shigar lafaya fara mai adon flowers ja,tasha adon zobba da sarƙa na gold, high hills ne a ƙafarta,cikin takun izza ta nufo in da su Fa'iz ɗin su ke ,sojan na ganinta ya saki Fa'iz ɗin yana ɗan rissanawa ya gaisheta,taɓe baki Fa'iz yayi yana faɗin matsiyaci kawai.
murmushi su saki shida yazdan suna ƙarasawa in da matar take, hugging ɗin su tayi itama fuskarta ɗauke da murmushi,raba jikinta tayi da nasu tana faɗin “ 5 and 6 lafiya na ganku tsaye nan,mike faruwa??”
kallon sojan dake tsaye yazdan yayi “wannan matsiycin ne ya Naeem wai yasa yasa Fa'iz tsallan kwaɗo” kallon sojan matar tayi “wai haka ne?”
“eh ranki ya daɗe” sojan ya bata amsa,dubanta ta kai ga Fa'iz
“laifin mi kayi mashi yasa a hukuntaka?”
“momy babu abunda nayi mashi,kawai kin san ya tsaneni ne” girgiza kai matar tayi
“babu yanda za'ayi Naeem yasa a hukuntaka haka nan Fa'iz dole a kwai abun da kayi mashi,jeka kawai wajen aikin ka” ta faɗa tana kallon sojan
“to ranki ya daɗe” sojan ya faɗa yana barin wajen,bai so Hajiya ta zo ba yaso yau ya koyama Fa'iz hankali amma idan ba yau ai akwai gobe.
cikin gidan su ka nufa ita da su Fa'iz ɗin securitys ɗin ta da PA ɗin ta har sun biyo su ta dakatar dasu,ciki su ka shiga su yazdan sai zuba mata ƙarya su ke wai sunyi broke gashi kwana biyu dady bai basu ko sisi ga motar su babu mai a ƙasa suke takawa zuwa school,murmushi kawai tayi tana girgiza kai ta san ƙarya su ke mata,hannu ta zura a jakar ta ciro bandir ɗin ƴan dubu dubu har guda shidda ta basu kowa uku uku,godiya su ka shiga zuba mata kamar tsaffin maroƙa.
A main Parlor su ka rabu ta nufi part ɗin mom su kuma su ka nufi part ɗin mamy.
tun daga first parlorn mamy Fa'iz ya shiga ƙwala mata kira
“mamy! mamy!! mamy!!!,wai ba kowa ne a gidan nake magana anyi man banza??” masu aikin gidan najin maganar shi su ka nemi wajen ɓuya dan sun san muddin ya gansu sun shiga uku baijin kunyar taɓa jikin su a gaban kowa ko da kuwa mahaifiyar shi ce .
kitchen ɗin part ɗin ya fara leƙawa ganin babu kowa ne yasa shi jinjina kai yana faɗin “ƙana nan ƴan iska basa nan kenan” ya faɗa yana nufar ƙofar bedroom ɗin mamy.
A bakin ƙofa yaci karo da mamy doguwar rigar less ce a jikinta kanta babu ɗan kwali gashin Attachment ɗin ta har gadon bayanta kamar dai kullum,daga sama har ƙasa ta shiga ƙare mashi kallon kafin ta sauke idonta kan fuskarshi da sawun hannun ya Naeem ya fito raɗau.
“mamy wai ina ki ka shige ne sai ƙwala maki kira nake?” ya faɗa yana layi kamar zai faɗo mata,saboda tsaɓar shaye shaye ko bai sha komai ba baya iya tsayuwa dai dai sai ka ganshi yana layi
“kai Ni da Allah karka faɗo man a ka,daga ina kake haka?”
“daga yawo”ya bata amsa a gadarance
“yawon iskanci ko, a can ma ka samu wani ya ɗauke ka da mari ko?,wallahi Fa'iz ka shiga hankalinka dani,kai kullum burinka kaja man abun zagi ko dan ubanka”
shafa kumatun shi yayi “nifa ba abun zagin da nake ja maki,kuma wannan sawun marin da ki ka gani Naeem ne ya mare ni dan kawai na bigeshi ban gani ba”
“mari fa kace, wai tsayama wane Naeem ɗin??”
“akwai wani Naeem ɗin ne banda wanda ki ka sani”
“ya mareka dan kawai ka buge shi?”
“eh” ya bata amsa
“yana cikin gidan ko ya fita”
“ya fita” ya bata amsa
“idan ya fita ai uwar shi na nan” mamy ta faɗa tana damƙar hannun Fa'iz ɗin ta ja shi zuwa part ɗin mom,dan suyi saurin isa ta corridor da zai sadaka da duk wani part dake second floor tabi,cikin ƙan ƙanin lokaci su ka iso part ɗin mom Fa'iz sai faɗi yake ta sake shi amma ina...
_*Ep 15_16*_
*Bound by fate,freed by love, A romantic Odyssey*❤💘💘
______________________________
A saman sofa suka samu mom da matar data shigo,fizge hannunshi Fa'iz yayi, babu sallama babu Nocking mamy ta hau surfa masifa
“wallahi bazata saɓu ba bindiga a ruwa,bazai yiwu ko wane ɗan iska yariƙa dakar man yaro ba ehe” kusan a tare mom da matar data shigo su ka kai duban su ga mamy dake fama sirfa masifa, Yumnah da gudu ta fito daga ɗakin mom.
“naga dai iskanci babu wanda baiyin shi,Allah na tuba akwai wanda akafi sani da iskanci sama da soja,wane irin iskanci ne nasu Bama gani a gidanan, ko kuwa wanda ke matse ƴaƴan mutane a office da sunan aiki ne ba ɗan iska ba, ko wanda ya haiƙe ma tsarar haihuwar shi da ƙananun shekaru ya kuma wanke ƙafa ya koma can cikin nasara masu jan kunne dangi sheɗan ne ba ɗan iska ba, ko mai yawan mashaya duk daren Allah ne ba ɗan iska ba!!???”
daga mom har matar data shigo zuba mata ido su kayi kawai suna kallonta kamar wata mai taɓin hankali.
“to wallahi bazan yarda ba tunda ba wani yasha man wahalar haihuwa ba ehe” clapping hand taji anyi daga bayanta.
Da sauri gaba ɗayan su ka kai duban su ga dady dake tsaye can sama tun ɗazu ya dafa handrail,tunda mamy ta shigo yake tsaye yana kallonta,wani irin mummunan faɗuwa gaban mamy ya shiga yi duk a tunaninta baya gidan.
parlorn dady ya nufo yana faɗin “da kyau uwar ɗa,da kyau wacce ta iya haihuwar ɗan kirki” ya faɗa yana ƙarasowa in da suke.
Fa'iz shan jinin jikinshi yayi ganin irin kallon da dady ke mashi,yana ƙarasowa in da yake ya ɗauke shi da lafiyayyun maruka har sau biyu,da sauri ya dafe kuncin shi.
Mamy gabanta ne ya faɗi,nan ta shiga ƴan kame kame da nufin ba dadyn haƙuri,wata mahaukaciyar tsawa ya daka mata wacce ba ita da yayi mawa ba hatta su mom sai da ƴan hanjin cikin su suka kaɗa “yanzu ni na mareshi ko zaki rama mashi??”
Ya faɗa yana sake saukema Fa'iz ɗin wani lafiyayyan marin “haba janar taya za kaita dukan yaron haka,ba fa shi yayi maka laifi ba”
“na sake marin shi dan na gwada maki iskancin soja kamar yanda ki ka faɗa”
dadyn ya faɗa a karo na uku yana sake ɗauke fa'iz ɗin da wani marin har sai da ya saki fitsari a wando, yumnah bata san sanda ta fashe da dariya ba, da sauri tasa hannu ta toshe bakinta gudun kar wani yajita.
“dan Allah janar kayi haƙuri, wallahi ba haka nake nufi ba”
“haka ki ke nufi mana,ai gwara na gwada maki iskancin sojan”
“dan Allah dady kayi haƙuri ba dan ni ba” fa'iz ɗin ya faɗa hawaye na zobo mashi shar
“yiman shiru ko nayi ƙasa ƙasa da kai a wurin nan shashasha” da sauri fa'iz ɗin yasa hannu yan kama bakin shi, kallo mamy dady yayi
“Mabaruka!!!” dady ya kira sunanta da kakkausar murya,jiki na ɓari tace
“Na'am”
“wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe da ƙafarki zata sake takowa zuwa ɓangaren zulaihart da sunan tujara ko rashin mutunci, Naeem yaya yake ga Fa'iz ya isa ya hukuntashi akan kowane laifi da yayi,daga yau idan ki ka sake tada jijiyoyin wuya akan Naeem ko wani a cikin ƴaƴana ya hukunta ɗanki, ina mai tabbatar maki zaki gamu da fushina wanda hakan bazai taɓa maki daɗi ba kinji na faɗa maki”
“naji in sha Allah hakan bazata sake faruwa ba” mamy ta faɗa kamar da gaske,hanyar fita dady ya nuna mata ita da Fa'iz ɗin
“maza kija ɗanki ki ba mutane wuri”
kama hannun fa'iz ɗin tayi sumi sumi su ka fice
kallon dady matar data shigo tayi “ina wuni ya Tahir, na sameku lafiya?”
“lafiya lau Salima ya mutanen gidan, ina ki ka baro man ƙanina” murmushi matar ta saki tana faɗin “ yana can yana fama da jama'a”
“ai dole ne, Allah dai yasa a gama lafiya” dady ya faɗa
“Ameen ya Allah”
“ki gaishe man da shi” dadyn ya faɗa yana nufar part ɗinshi
“zaiji in sha Allah” matar ta faɗa tana kai dubanta ga mom
“ba mu gisaba, na same ku lafiya?”
“lafiya lau hajiya salima, ya kuma fama da jama'a”
“lafiya lau Alhmdllh,ashe kuma abunda ya faru da Asma'u kenan, to Allah ya kyauta gaba”
“Ameen ya Allah” mom ta faɗa
“da tare zamu zo da Kainart bata jin daɗi ne shiyyasa bamu zo tare ba amma tana maki jaje”
“Ayya Allah sarki, ina amsawa Allah ya bata lafiya”
“Ameen summa Ameen”
ƙarasowa yumnah tayi cikin parlor
“momy shine baki zo man da su Ammar ba?”
“suna school ne yumnah”
“ke ki ka ma biye mata idan tana son ganin su ai ta san in da zata same su”
“ai kuwa dai, dan tunda yallaɓai yaci zaɓe ina jin zuwan yumnah Villa sau ɗaya shima bata wani jimaba ta dawo”
ɓata fuska yumnah tayi “school bata bari na saketa, kuma dokokin gidan gwamnatin ne momy sunyi yawa”
“kaji ja'ira banza lokacin da ku kuna gidan gwamnatin ai ba suyi maki yawa dokokin ba sai yanzu ko, kawai baki son zumunci”
“ba haka bane momy”
“to yaya ne?”
“ina nan zan zo kafin muyi resuming school”
“ina nan ina saurare Allah ya kawo ki lafiya”
“Ameen” tashi matar tayi tana faɗin
“bari na shiga ɓangaren mabaruka mu gaisa”
“to nagode Allah ya bar zumunci, a gaishe man da Kainart ɗin”
“za taji in sha Allah”
“momy sai na zo” yumnah ta faɗa
“Allah ya kawo ki lafiya” da Ameen ta amsa, har main parlor mom ta rakata, part ɗin mamy hajiya salima ta nufa.
Mamy a lokacin da su ka fito daga part ɗin mom, fiszge hannunshi yayi daga riƙon da tayi mashi
“mamy ai ga irinta nan sai da nace ki ƙyale ni gashi nan yanzu kin ja man shan maruka, na san yanzu hankalin ki ya kwanta?”
“wallahi Allah ne ya ceceta da ace janar baya gida yau data gane kurenta”
taɓe fa'iz yayi “ kullum haka ki ke cewa,kin taɓa ɗaukar mataki a kan mom ɗin ne ko da sau ɗaya, wallahi mamy ina guje maki randa dady zai shuka maki rashin mutunci saboda matarshi”
“wane shi, ya dai shuka mata rashin mutunci”
“ai yanzu naga faɗan da yayi maki ita yayi mawa,wallahi mamy ki rage shige mata wallahi ko ƴaƴanta ba raga maki za suyi ba, ki bar ganin kowa ya zuba maki ido a gidanan kamar ana tsoronki, wallahi lokacin biye maki ne basu dashi amma duk randa ki ka kaisu bango abun bazaiyi kyauba”
“faɗa mata gaskiya fa'iz kullum abunda nake so ta gane kenan amma taƙi, wallahi mamy wannan abun da ki ke ida sirema dady ki ke, dan zubarma kanki da mutunci ki ke a gaban kowa muma kina ja mana” Fa'iza ta faɗa wacce fitowarta kenan daga bedroom ɗin ta
baki mamy ta saki ta rasa har yaushe tayi lalacewar da Fa'iz da Fa'iza su ka rainata irin haka “ni ku ke faɗa ma haka dan uwarku?”
“gaskiya ce kuma daga ƙinta sai ɓata, kai yazdan zo mu tafi muje kawai restaurant muci abincin a can” Fa'iz ya faɗa yana jan hannun yazdan su ka fice, Fa'iza ma shigewa tayi ɗakin ta da kallo kawai mamy ta bisu.
duk wannan hargagin da take tana yi ne saboda su amma basa gani
“Allah ya wadaran naka ya lalace” ta faɗa tana nufar ɗaya daga cikin sofas ɗin parlorn ta zauna, masu Aiki dake laɓe suna sauraron abun da ke faruwa ban da Allah ya ƙara babu abun da su ke.
hajiya salima ta shigo parlorn bakinta ɗuke da sallama, da sauri mamy ta kai dubanta gareta,tashi tayi ta nufeta fuskarta ɗauke da murmushi, hugging ɗin juna su kayi.
“saukar yushe?” mamy ta faɗa tana jan hannunta su ka nufi sofa su ka zauna
“dama yaushe zaki ganni kinje kina tsula tsiyarki” mom salima ta faɗa
“wai da ke ce a parlorn, ni inama na lura da wacece ido a rufe suke ne raina ya ɓaci”
“ai naga alama, wai dama mabaruka har yanzu baki daina hargagi da zulaihart irin wannan ba?”
“yaushe kuwa zan daina, ai idan kinga na daina to na sake sender ta ƙasar su kamar shekarun baya” kallon baki da hankali matar ta shiga binta dashi.
“ke har yanzu kina tunanin zaki iya raba Tahir da zulaihart ne, to wallahi idan ma bacci ki ke tun wuri ki farka kar kije garin tsige igiyar Aurenta ke ki tsige taki a banza”
“ban gane ba, mi kike nufi”
“ko wannan matakin daya ɗauka yau akan fa'iz a gabanki saboda zagin ƴaƴanta da ki ka yi ya isa yasa kiyi hankali kisan cewa da da yanzu ba ɗaya bane”
“ni wallahi Hajiya salima kin barni a cikin duhu,dan ban gane inda maganar ki ta dosa ba”
“ kin manta bala'in da ki ka shiga lokacin baya?, da ba dan mama Ameena ba da yanzu kina wani gidan ba wannan ba, idan zaki canza salon kishin ki ki canza idan kuma haka ki ke ganin ya fiye maki tam, shi dai yaƙi ɗan zamba ne”
jinjina kai mamy ta shiga yi alamar gamsuwa da maganar hajiya salima “shikenan naji zanyi ƙoƙarin ganin na sauya”
“hakan dai shi ya fi, ni na shigo ko gaisawa ba muyi ba,kin wuni lafiya?”
“lafiya lau, ya yau ban ganki da tawagarki ba?”
“ki bari kawai ni na hana su biyo ni nace suyi zaman su jaje zanje ba ɗabbaka siyasa ba, ko security cewa nayi su jira ni a waje”
“kina sha'aninki ta wajen Ahmad, ai wallahi ni lokacin da janar na kan kujerar shugaban ƙasa duk in da zani da tawagata nake zuwa ai shine girman”
“ban manta ba” matar ta faɗa, mai aiki mamy ta ƙwalama kira dan ta kawo ma hajiya salima ruwa da lemu.
“ai barshi kawai mabaruka nasha a part ɗin zulaihart tafiya ma zanyi”
“nifa kinga abun da ke haɗani dake kenan,dan mi zaki sha ruwa a wajenta”
“ni dai yanzu idan na sake dawowa na sha, amma yanzu kam gaba nayi”
“shikenan Allah ya nu na man lokacin da zaki sake dawowar” da Ameen hajiya salima ta amsa, a tare su ka miƙe ita da mamy.
har parking space mamy ta rakata, sai da taga tashin motocin ta tukun ta koma ciki.
*ASO VILLA*
Kusan a tare motocinta da motar da aka ɗauko su Ammar daga school ta shigo.
A bakin main entrance ɗin shiga part ɗin su motocin su kayi parking, drivern da yayi driving ɗin su ne ya fito ya buɗe masu,da gudu su ka fito suna nufar motar kakar tasu,suna isowa security na buɗe mata ƙofa ta fito.
da gudu suka faɗa jikinta “oyoyo granny,shine ki ka fita bama nan ko” murmushi ta saki tana shafa fuskokin su
“ayi man afuwa gidan big daddy naje”
shagwaɓe fuska su kayi “amma granny kin san cewa muma muna son zuwa shine ki ka tafi bama nan”
“ayi man Afuwa,ai gobe za ku haɗu dashi a gidan Abbah” ta faɗa tana jan hannunsu suka nufi cikin gidan
“ai gidan Abbah ba gidan shi bane,mu gidan shi muke son zuwa”
“karku damu idan kuna son zuwa sai nasa dadyn ku ya kaiku gobe da kun dawo daga school,kunga sai kuyi ma Aunty Yumnah weekend ko” tsallan murna su kayi
“yeee har gidan papa ma sai muje”
“na san Aunty Yumnah zata kai ku ko ina,amma fa sai dady da momynku sun amince”
ɓata fuska su kayi “dady bazai amince ba mu dai kawai kice ya kaimu”
“to naji muje na duba jikin momyn ku” ɗan zaro ido su kayi suna kallonta
“mi ya samu momy?”
“bata jin daɗi ne” Hajiya Salima ta faɗa dai dai tana tura ƙofar ɗakin kainart ɗin,wayam su ka gani bata ciki har ƙofar toilet sai da Aman yayi nocking amma bata ciki, Ammar ne yace kila tana bedroom ɗin su ,ficewa su kayi zuwa bedroom ɗin na su.
A kwance su ka sameta saman bed ɗin su Aman, idanunta a rufe kamar mai bacci,gaba ɗaya ta rasa mike mata daɗi a duniyar nan,har ta ƙagara ya tattara kayan shi ya koma Lagos.
da gudu su ka ƙarasa in da take,faɗawa su kayi saman jikinta
“momy mun dawo” a firgice ta miƙe zaune dan ba ƙaramin tsoro su ka bata ba, ajiyar zuciya ta sauke ganin su.
“amma yaran nan anyi ja'iran yara,ba kuga bata jin daɗi ba shine zaku faɗa mata haka” Hajiya Salima ta faɗa yayin da ta ƙarasowa bakin bed ɗin.
da sauri kainart ɗin taja gyalen abayarta ta rufe gefe da gafen fuskarta tana kai dubanta ga Hajiya Salima
“momy har kin dawo?”
“na dawo kainart,ya jikin naki?”
“Alhmdllh,ya su mom ɗin?”
“suna lafiya,tana ma gaishe dake”
“ina amsawa”
“mi Dr yace yana damunki?”
“zazzaɓi ne kawai”
“to Allah ya sawaƙa” da Ameen kainart ɗin ta amsa,tashi hajiya Salima tayi
“ku kuzo ko muje can sarah ta shirya ku,kunga momy ba lafiya”
da gudu su ka sauka daga saman bed ɗin suna nufar ƙofar fita,bin bayan su hajiya salima tayi tana sakin murmushi, murmushi itama kainart ɗin ke saki har su ka fice daga ɗakin.
*Uncle Hashim's House*😡
A zaune su ke saman dinning chairs a katafaren dinning room ɗin gidan,baka jin ƙarar komai sai na spoon da plate ɗin da su ke cin abincin.
gaba ɗaya a takure take saboda kafetan da ido da dadynta yayi,hakan ya hanata sukuni,momy da balqis sai cin abincin su suke hankali kwance dan basu san abun da ke faruwa ba.
a hankali ta ajiye spoon ɗin hannunta tana miƙewa da nufin barin wajen,table ɗin ya buga da ƙarfi wanda yayi sanadiyar dawo da hankalin momy da balqis kan su.
“koma ki zauna” ya faɗa da kakkausar murya yana nuna mata chair ɗin data tashi,da ɗan rawa rawar jiki ta nufi chair ɗin ta zauna,duƙar da kanta tayi ƙasa gabanta na faɗuwa.
“barrister lafiya?” momy ta faɗa tana ajiye spoon ɗin dake hannunta,maida kanshi yayi kan abincin da yake ci ba tare da ya tanka mata ba kamar ma ba dashi take magana ba.
sanin bazai tanka mata bane ya sata kallon laatifa,da ido tayi mata alama da lafiya, girgiza mata kai laatifa tayi alamar itama bata sani ba hawaye na taruwa a idonta.
“Allah ya kyauta” shine kawai abun da momy tace tana cigaba da cin abincinta,sun kai tsawan 20 mins kafin kamar daga sama su kaji ya kira suna balqis murya a kausashe.
da sauri balqis ɗin ta ajiye spoon ɗin dake hannunta
“na'am dady”
“last day mi ya kai ki court??” ya faɗa babu alamun wasa a fuskar shi,kamar saukar ardu haka laatifa taji tambayar duk da ba ita yayi mawa ba,tayi tunanin ya bar maganar tun lokacin ashe ba haka ba.
gabanta na faɗuwa ta kai dubanta ga balqis tana mata alama da ido data rufa mata asiri.
“naje saboda Aunty laatifa ne”
wani mugun kallo yayima laatifa
“saboda mi?”
“bata jin daɗi ne shine nace ta zauna gida ni na wakilceta” jinjina kai barrister yayi.
“mi na faɗa maki laatifa??” ya faɗa yana tsareta da idanu
“dady ba fa ita ta tura ni ba, da kaina nace zanje”
“tambayar ki nayi?” girgiza mashi kai balqis tayi
“dan Allah kayi haƙuri dady wallahi bani nace taje ba”laatifa ta faɗa a hankali
“laatifa kin raina maganata ko,bance maki idan za kiyi yawan iskancinki ki daina sa ƴata a ciki ba”
kamar zata fashe da kuka tace “kace dady”
“wato saboda ban isa ba shine ki ka turata cikin ƙattin da ki ka saba yawo da su ko?”
“kayi haƙuri dady bazan sake ba”
rai a ɓace momy tace“wai lafiyar ka kuwa barrister,itama ba ƴar ka bace ,mi yasa k..?” bata ƙarasa ba yayi saurin daka mata tsawa yana ɗaga mata hannu,hakan yasa tayi shiru tana kallon shi cike da mamaki.
“wannan ya zama rana ta ƙarshe da zan sake maki warning akan ƴata,duk yawan banzan da za kiyi kiyishi ke kaɗai amma banda ƴata kinji na faɗa maki”
“in sha Allah hakan bazata sake faruwa” laatifa ta faɗa hawayen da su ka taru a idonta na zubowa.
tashi yayi ya nufi bedroom ɗin shi,da wani kallo momy ta rakashi,tashi laatifa tayi ta nufi bedroom ɗinta yayin da take fashewa da wani matsanancin kuka, balqis ma kuka ta fashe da shi sun rasa yaushe dadyn su zai rage wannan ƙiyayyar da yake ma laatifa.
bayan laatifa momy tabi hakama balqis,a kwance su ka sameta ta kifa kanta saman matress tana fitar da wani kalar kuka mai ban tausayi,zama momy tayi kusa da ita hannunta ta ɗaura saman bayan laatifa,a hankali take shafa bayanta.
“momy wai mi yasa dady ya tsaneni,mi yasa baya sona kamar yanda yake son balqis, nima ba ƴarshi bace ko ina da wani uban wanda ni ban san shi,momy dan Allah idan ba shine mahaifina ba ki faɗa man???”
saurin toshe mata baki momy tayi da tafin hannunta “kul laatifa kar na sake jin bakin ki ya furta wannan kalaman,ki daina tunanin baya sonki ne, mahaifinki na sonki fiye ma da yanda yake son balqis,yana yi maki haka ne saboda ya kasa mantawa da abun da ya faru shekarun baya,ki dage da Adu'a wata rana sai labari”
“momy mi yasa dady har yanzu ya kasa gane cewa ba abun da yake zargi ba ne,momy har sau nawa zan faɗa mashi babu abunda ya faru dani kawai taimako na SAM yayi”
“saboda shi mahaifinki ne abun na damun shi shiyyasa ya kasa mantawa,kiyi haƙuri kinji in sha Allah wata rana gaskiya za tayi halin ta dadyn ki zai gane baki da laifi”
“momy amma ke mi yasa ki ka fahimce ni,dady baya sona ne kawai”
ta kai ƙarshen maganar tana sake fashewa da wani matsanancin kukan.
momy bata san lokacin da itama hawaye su ka wanke fuskarta ba, balqis ma ƙarfin kukan da take ne ya ƙaru,gaba ɗayan su rasa me lallashin wani a kayi,sai da su kayi mai isar su tukun momy ta shiga lallashin su,da ƙyar ta samu su kayi shiru,tashi laatifa tayi ta nufi toilet.
tashi momy tayi ta fice zuwa ɗakin barrister, a tsaye ta sameshi gaban wardrobe ɗin shi fitowarshi kenan daga wanka ƙugunshi ɗaure da towel.
“kaji tsoron Allah barrister,ka sani wannan aibatatan da kake ba shine mafita ba,itama ƴace a wurin ka kamar balqis,kuma ka sani ɗan Adam bai isa ya tsallake jarabawar da Allah yayi mashi ba,ko da ace abunda kake zargi gaskiya ne, kai ba mahaifinta bane dan mi bazaka ɗauki ƙaddararta hannu bibbiyu ba,amma ace tsawan shekaru ka kasa mantawa da abu,kullum cikin aibatata da nuna mata tsana kake, Allah ma munayi mashi laifi ya haƙura sai kai ne bazaka yafe ma ƴarka ba kan laifin da zargi kawai kake baka da tabbaci, haba barrister ka zama mahaifin ƙwarai mana”
“kin gama?” shine kawai abun da yace,wani ƙululun baƙi ciki ne ya tokare mata maƙoshi wato ma ta gama
“get out from my room” ya faɗa yana nuna mata hanyar fita,rai a ɓace ta juya ta nufi ƙofar fita har ta kama handle ɗin ƙofar sai kuma ta tsaya,rai a ɓace ta juyo tana kallonshi.
“ka sani balqis da laatifa Amana ce Allah ya baka,kuma zai tambayeka akan yanda ka tafiyar da rayuwar su,ka sani muddin baka gyara alaƙarka da ƴarka ba za kayi daka sani ne mara amfani” tana gama faɗa haka ta fice daga ɗakin baki ɗaya,tsaki yaja kawai yana cigaba da abunda ke gaban sa.
shaf shaf ya shirya cikin pajamas ɗin shi white color masu fatsi fatsin baƙi,feshe jikin shi yayi da perfume ɗin shi masu ƙamshi,bed ɗin shi ya haye yayi kwanciyar shi bayan ya kashe light ɗin ɗakin.
wayar dake kan nightstand ya ɗauka,dialing wata number yayi,bugu biyu a kayi picking call ɗin,kara wayar yayi a kunne,in low voice yake waya yanda ko kusa dashi ka tsaya bazaka iya jin abunda yake cewa ba,idan ka shigo ɗakin sai ka rantse da Allah bacci yake.
barrister kenan ko matashin saurayi bazai gwada mashi iya kashe murya idan yana waya ba.
*Big daddy's House*
“ko fa mi za kice sai dai kice amma yau sai kin fita dinning kinyin dinner tare da kowa na gidan nan,na gaji da wanna ƙunshi kan naki da ki ke”
“please Yumnah ki fahimta mana,bana jin yunwa ne ba wai ban son fita ba”
“to naji,muje ni ki raka ni koda ba kici komai ba ai za ki gaisa da mom da dady,kuma zaki rage wanann yawan tunane tunanen da kike”
duk yanda ta so zille ma Yumnah akan ta ƙyaleta Yumnah taƙi bata dama dan dole ta miƙe,hijab ɗinta dake saman bed ɗin ta ɗauka,zurawa tayi a jikinta
“muje to” ta faɗa tana kallon Yumnah
“ko ke fa,amma wannan hijab ɗin da ki ka sa saikace wacce zataje gaban sirikai, dinning fa zamu je ba wani waje ba”
“ni dai haka zanje”
“ai saiki ta tafiya haka”yumnah ta faɗa tana jan hannunta su ka fice.
Mom da dady ka ɗai su ka samu a dinning ɗin, Ishrat na daga tsaye tana serving ɗin su,bakin su ɗauke da sallama su ka ƙarasa cikin dinning room ɗin,zama su kayi saman chairs yayinda su ke gaishe da dady da mom.
murmushi dady yayi yana kai duban shi ga Nainarh,cikin kulawa su ka amsa masu gaisuwar da su kayi dady na faɗin
“ɗiyata kinyi wuyar gani,tun ranar da muka dawo daga wajen mahaifiyar ki ban sake saki a idona ba,ina fatan dai lafiya?”
“lafiya lau dady” Nainarh ta faɗa tana duƙar da kanta ƙasa
“yanzu ma fa da ƙyar na samu ta fito,kullum tana ɗaki daga kuka sai tunani” Yumnah ta faɗa tana kallon Nainarh data sadda kai ƙasa.
“wai haka ɗiyata?” shiru Nainarh tayi tana wasa da gefen hijab ɗinta
“ki dai na sa damuwa a ranki kinji, mahaifiyar ki zata dawo gareki,in sha Allah asirin wanda su ka kashe mahaifinki zai tonu”
“in sha Allah” Nainarh ta faɗa
“bana son kina sa damuwa a ranki kinji ko,ke da ma ki ke da wata mahaifiyar a kusa dake miye na sa damuwa a ranki” dady ya faɗa yana nuna mom da tunda su ka shigo dinning ɗin ta kafe Nainarh da ido ko ƙyaftawa ba tayi dan duk maganar da dady ke yi bata sani ba hankalin ta baya wajen.
“zulaihart!” dady ya kira sunanta,ɗan saurin kallon dadyn tayi
“lafiya ki ka kafe ƴar taki da kallo” murmushi mom ta saki
“wani lokaci sai nake ganin tana man kama da ƴar uwata,sai dai ita bata kai ta kazar kazar ba Nainarh ta cika sanyi” mom ta faɗa tana sake kai dubanta ga Nainarh data sadda kai ta sauraron su.
“nima na jima ina ganin kamaninta da Carol, da ace ban san mahaifiyar ta ba kuma a ce Carol ta taɓa Aure da babu abunda zai hana nace ƴarta ce”
murmushi mom ta saki “nima ina yawan faɗama mahaifiyar ta haka,wani lokacin idan nace haka sai tace dan kawai ina son Nainarh ne yasa nake ganin kamanin su”
“ta iya yiwuwa” dadyn ya faɗa, Yumnah da Nainarh dai na jin su,fa'iza ce ta shigo dinning room ɗin,tsaye tayi tana riƙe ƙugu fuskarta a turɓune
“shine yau aka rasa wanda zai kirani ko?” ta faɗa tana sake tsuke fuska.
“sorry Aunty Fa'iza nayi tunanin a part ɗin mamy za kiyi dinner shiyyasa ban kira ki ba” Yumnah ta faɗa tana ɗan kama kunnenta alamar sorry
“nima ayi man Afuwa na rashin faɗa maki da banyi ba” Ishrat ta faɗa wacce ke serving ɗin Yumnah da Nainarh,ɗaya daga cikin kujerun Fa'iza ta nufa ta zauna.
“ni dama na san ai kun rigada kun gama rainani gidan nan” murmushi kawai dady da mom su ka saki.
gaishe da su dady fa'iza tayi, murmushi dady yayi yana faɗin
“ai da nayi tunanin baki gannu ba”
ɗan murmushi tayi tana sosa ƙeyar ta.
serving ɗin ta itama Ishrat tayi kafin ta bar dinning ɗin,tsit wurin yayi ba wanda ya sake magana.
mom ta fara tashi kafin dady ya miƙe yana kallon Yumnah yace “Autar mom ina fatan baki manta gobe juma'a ba?”
“ban manta da gyaran part ɗin shalelen dady ba,gobe tunda safe zansa a gyara shi”
“good,haka ne son ji,sai da safe ku”
har haɗa baki suke wajen furta good night,jinjina masu kai dadyn yayi yana fice daga dinning room ɗin.
suma basu wani jimaba su ka tashi, Ishrat ta zo tare da su munirat su ka kwashe kayan da su kaci abinci su ka gyara wajen tsaf.