Chapter 2:flight or fight .
Shade Of Rufaida Part 1 Complete Hausa Novel · about 42 min read
*Bayan kwana biyu*
Mata ne makil a babban tsakar gidan dayasha bugun cement duk sun sanya ankon su ta rubber rubber milk colour da ja dukan su dinkunan su iri daya..
Babba da yaro tsoffi da matan anguwa sai hayaniya ake anata cin shinkafa kamar Allah ne ya aiko su,ga wasu a can gefe sun baza faranti suna famar shan kwate,wasu na warban zazzafar masa da miyan taushe wacca taji dage dagen Kan naman rago,wasu nacin dafa duka ta rice, ga zobo drink ga kunun zaki ga uwar gayya wato taliya jollof da kuma tuwon shinkafa,...
daga can gefe kuma wasu tsofaffi ne a shinfede akan tabarmai suna famar rera wakokin zube suna buga kirari irinna zalamammun makwaidatan maroka wanda sukayi degree a harkan barace barace da kwaram agidajen biki.
At same time Kidan wakar hausa mai dauke da kalaman soyayya ta mawakin nan hamisu breaker na tashi sosai sautin kida ta cikke iskan wajen
wasu matan na rawa ana shewa ana manna musu kudade,wasu kuwa banda gulma da tsugudidi ba abunda sukeyi wani irin gudan nishadi akeyi daga gani kasan gidan biki ne daya amsa sunan sa gidan biki.
Gidan Babban gidane mai fadin gaske wanda saika wuce inda ake shagalin bikin sannan kabi wata sashe dasuke kira da sashen YAA MALAM.
Kasancewar sashen yaa malam yafi kowani sashi girma agidan daga nan ma yake sauke Manyan baqin da sukazo bikin musamman domin shi
Mutane ne akoina saidai duk da haka ko ina agidan fess yake,duk dama biki ake a gidan amma basa barin koda cokali akasa, anshare cementin kasan tasss an shimfida tabarmai ko ina dai sai kyalli yake tsabagen tsaftar su.
ginin flat daya ne a sashen YAA MALAM self contain ce mai dauke da wani babban fankacecen falo da akalla zai iya daukan mutane talatin, falon na dauke da wasu irin hadaddun kujeru brown color asalin design din da can mai tumtum dan ko pilow ba ayi musu ba,sai ledan tsakar dakinsa mai shegen kyau shima bown colour da yar sallayar sa agefe sai wayansu jimammun jakunan littafai da kwalaben tawadar sa,da kwaryaye da Alluna da ake jerawa ajikin bango sak irin shigen kwalliyar da mutanen da can sukeyi ma muhallin su.
kana ganin dakin kaga dakin babban magidanci kuma MALAMIN addini zaune yake a babban kujerar tsakiya tare da baqinsa yan birnin kudu da surukunan sa wanda suka shigo ba da jimawa ba,yau yaa MALAM ya fito ras yasha fararen shadda inda akamai dinkin malum malum yy kyau kwarai kamar bashii ba.
Agefen sa wata tsohuwa ce wacce a shekaru akalla bazata wuce 68 ba taci uwar atampar ta super holland gold daketa sheqa gyalli kaman an shafa mai mangyda ajikinsa, an mata dinkin buba da zanin sa data daura akan rigan dake ma kyam take dan ita tsufar bai lalata mata jikinta sosai ba,motsatsen kafanta da gabaki dayanshi yasha jan lallai tayi irin lallen nan ne da akafi sani da dungulmin tsohuwa.
fara sol ce tsohuwar,gashin kanta dana giranta duk sunyi furfura sabida tsabar tsufa, sai goshinta d kan hancin ta daketa fidda uban zufa
Kuma dudda tsufan nata siffarta bai hana nuna kamannin ta da magidancin dake zaune kusa da itan ba,hakan ya kara bayyana cewa mahaifiyarshi ce.
A cikin muryanta na tsofaffi mai tafe da dan masifa ta kira sunan sa a hankli tace..."Bukar,bukar,bukar wai sau nawa na kira sunanka?Shiru yay dan baison ya amsa ta agaban baqinsan ya sauke kai ya maida hanklinsa kanta dan baiso tabashi kunya agaban su duk dama jin kunya ba wata aba bace data damesa.
Murya kasa kasa Tace kaga dai sau uku nakiraka ko toh wlh nagaji da zaman nan kodai ka tsawatar wa yarka ta dawo kona tattara yinawa yinawa nabarma gidanka nakoma chan cikin gari Gidan dan uwanka zaidu ai dama saida yace in huta kafafuna nayi fafur naki bin nashi,yo mai zan gani anan?abunda aka saba dai shi akayi shi nikuma an ajiye ni kamar bazaurar gawa..tsaki taja mtswww,tace aikin banza aikin wofi kawai..ni ka gayamin abunda zaka fada min kawai in kama gaba na
Dan rangwofowa yayi,baqar fuskan nan nasa a balain turmushe yana kallon ta sanin cewa yanda take masifan ne kawai yasa zai sassauto da muryan sa qasa ya kulata dan yatsani a rinka aibata shi ko akira sunan kanin sa zaidu acikin lamarin sa yace "kiyakuri
Hajiya Mama yi hakuri"..bata kulashi ba can ta yaface hakwararta da dan tsinke kasar wuyarta tace
,"bawani zancen na yakuri" ta watsa mai harara atsakar idoh tana nunashi da dan yatsa tace yau kuma wani iskanci RUFAIDA ta samo ku kuma kuka daure mata gindi?Baice komi ba,ta kuma Jan tsaki yo inba hakaba Aljanu ne mutanen datake jin tsoron su?koko mudinne Mayu da ta guje mu?Ai Cha nayi yau duk yan uwane da abokan arziki suka cika gidan nan,yau ake bikin yayarta SUHANE amma wai ace tun safe ba'aga yarinyar nan ba tasaci hanya ta sabe silihu tafice? yo kajimin yar banzan yarinya marar kan gado,nide ba waje na ta debo yawon banza ba,sai dai awajenka,ko awajen uwarta hadiza.."
Tana gama sumbatun ta taja tayi shiru sabida rashin amsa mitar ta da yaa MALAM din yayi, sallaman da akayi ne daga bakin kofa ya dada Jan hanklin su,wata kyaykyawan mace mai dan jiki yar doguwa tasaka madaidaicin Atampa an mata dinkin riga da zani doguwan riga plain
ta shigo dakin fuskarta ba yabo ba fallasa ta karaso ciki ta gaida tsohuwar a ladabce
Tace sannu da hutawa hjiya mamah"Kallo ta kare mata saf sannan ta harareta batare data amsaba hakan yasa matar sunkyar dakai ta dubi yaa malam dake kallonta tace "gani Mai gida naji ka aiko akirani" cikin fushi yana girgiza kafa yace shin wai ina RUFAIDAR taje ne?"
shiru tadanyi tana kallonshi kafin ta sauke ajiyan zuciya a hankli mai cike da damuwa tace "malam nima bansan inda take ba" ..
"karya takeyi, na rantse maka Bukar, kunma isa?wlh, wlh kajini dakyau na rantse maka na sake rantsewa in baku nemo min jikata rufaida ba yau saina tsine muku Albarkan dake kanku tas kaida matarka kafun intafiyata Gidan zaidu inda kwanciyan hankali yake achan".. ta karashe maganan tana uban huci kaman dagaske.
kallonta kawai yaa malam yayi cike da takaicinta dan ya gama fahimtar meyasa take son tada rikici,da alama so kawai take baqin sa susan me ake ciki nacewa rufaida batason auren koda ma zasuce sun fasa,sosai ya gano salon mahaifiyar san kuma yasan babu yadda za'ayi ta juya ma rufaida baya.
Dada daure fuskan sa yayi. yace "haba mamah, to kibari nai magana mana kawai ai basai rufaidar tazo bama dama akan batun auren ta ne,zata budi baki yayi sauri yamike tsaye yace nace kiyakuri ko?babu kuma inda zakije sai an gama maganar, kiyakuri wayannan baqin domin mu sukazo rufaidar dama kawai ake jira dan karkuce na zalunceta
kwafa tayi tawani rau rau da idanunta tana binsa da kallon mamakin furta mata hakan dayayi dan karkada kafafunta tyi tace toh da ba aga rufaidan ba ai sai ka yi maganan ka ai dama hakan kasaba yi".
Kasa cewa komi yayi sabida yafison sai yarshin tana cikinsu sannan yay bayanin sa a tsanake domin ya jadadda qudirin sa a zuciyar duk wnda yake shakkar yiyuwar lamarin auren rufaida acikin gidan
,lura da hakan yasa tsohuwar ta miqe tayi waje tabarsu dan sosai takejin zafin abunda dantan yakeyi ma yayansa
Na musu aure batare da son ransu ba
kallon matar sa yayi datai shiru tana jinsu jikinta a matukar sanyaye,a dake ya juyo kanta yace KE hadiza wai ina RUFAIDAR taje ne? Ki fadi tsakaninki da Allah" a sanyayei ta dago tace "wlh mai gida nima bansani ba. bansan inda tayiba, ina fama da jama'an biki ban masan bata gidan ba saida su Jadwa sukazo ta fadamin wai yau kwata kwata bataga rufai ba"
cikin fushi da tsananin takaicinsu ita da yartan yace "to kije koma ina take ki nemota kin daisan sabida ita na aje manyan mutanen dake nan ko?yaune ranar da zasu ganta kuma yau nakeso na jadadda maganan ranar auren ta agaban kowa yaji
Inhar rufaida guduwa tayi dan ta tozartani duniya da lahira bazan yafe miki ba hadiza..
Umma tace...a'a dama fa tace da ita za'akai yayarta chan anguwar gidan mijinta inaga rufaida ba guduwa tayi ba... atake ya tsareta dacewa ohon miki nidai na fadamiki kinemota ta dawo gidan nan yanzun nan"...
dan ajiyan zuciya ta sauke tana kallonshi kafin ta miqe tsaye tana girgiza kai cike da takaicin sa ta juya zata fice tabar dakin can saikuma sai ta juyo ta kalleshi da idanunta da sukadan chanza kala tace "amma malam kasan matsalan yarinyar nan rufaida ko? batun yau mukasan bata son auren nan ba tanada muguwar tsor...o..n aur..e itafa karatu take son yi
cikin wata muguwar harara ya katseta da sauri ta hanyar cewa karatun yaci ubansa Nace miki..."yanzu rufaida yarinya ce da zakice min tana tsoron aure?KE meye amfanin ki amatsayinki na mahaifiyanta?MIJI gashinan ni na samar mata kuma WALLAHI shi zata aura.Ya karashe maganan yana nuni da daya daga cikin dattijan mazan da suke zaune a falon wanda da alama hirar su sukeyi bama jinsu sukeyi ba.
Da sauri umma Hadiza tayi saurin dauke idanunta akan su musamn akan shi Wanda akace za'abawa rufaida,gashi nan dai Wani tsohon tsoho dan ko a shekaru tasan ya haife rufaidan ta,runtse idanun ta tayi jin wani qullutun baqin cikin daya tokare ta akirji ganin ko a fuska ma bai dace da yarta ba
" .. Kinga kisan yanda zakiyi kinemo ta kindaiga raina a abace yake kina kara bata lokaci karfe biyar za'a zo daukan Suhane kuma tare zasu tafi yanzu karfe hudu ne harda kwata"juyawa tayi ahankali tafita daga dakin batare datace mishi uffan ba, da kyar ma ta iya saita fuskanta ta amsa gaisuwan mutanen dake tsakar gida ke mata amatsayin ta na uwar Gidan kuma uwar amarya
Nan ta wuce ta shiga bangaren su inda falontan ma ke cike da jama'an ta dana anguwa ana zaune anyi makil
Gefe tayi tabude wani dan daki ta shiga ciki,wata babbar mace ce a zaune a dakin tana hada kayan akwatin Amarya da za'a tafi dasu kana ganin matar kaga kamanin manyan hajiyoyi maida kofar umma hadiza tayi ta rufe ta shigo ta zauna kan gadon sun dabas jikinta sam babu kwari da sauri tasa hannu tana goge kwallan dayake shirin zubo mata,cikin sauri matar dake hada kaya a akwatin ta saki kayan hanunta tazagayo tazo ta gabanta tace
"meye haka kuma hadiza!menene kike kuka Maman rufaidah?"
Duk dama hawayen sunki dena zubowa share idanuntan tayi tanadan nishi nishi da alamun kukan ne ke cinta sosai aranta tace "Hajiya jasmine,wallahi narasa yanda zanyi da yaa malam, kullum, kullum dakika sani saiya jamin rashin mutunci daga wurin mutane,zanji da baqin cikin ya aurar da suhane ga wanda bazabinta ba ne ko wayannan mugayen mutanen daya rariko wai zai nuna musu rufaida? yanzu laifinane dan rufaida Tace batason auren wurin makaranta zatayi?duka duka rufaidan nawa take? Itafa ko secondary schl bata kammala ba, Yau koni na hallice ta ai ba zan tursasa ta ta aure namijin daba ta ma san dashi ba ...ni kawai nasan rufaida dagan gan ta gudu tabar Gidan nan tun safe..inba haka ba Munanan dake ai inata kwada lamber wayarta ta baya shiga,natura yan uwanta duk sunje makota da Gidan kawayen ta kiramin ita wai ba'a ganta ba,kuma malam yaki yabar maganan, dan Allah ya zanyi? Narasa yanda zanyi na
chanza ra'ayin malam ko ita kanta rufaidar, narasa wace irin yarinya ce ita da batada haqurin yin biyayya ma iyayenta kamar sauran yan uwanta.
Amma har Ace yau bikin yar uwarta na jini sabida fitina wai ta gudu tabar gidan nan? ni yanzu a ina zanje in ganta,dan Allah ya zanyi da raina?" takarashe maganan cikin dagon murya sosai hawaye na gangarowa daga idanunta gwanin tausayi, da sauri matar ta rungumeta ta daura kanta ajikinta tana shafa bayanta sigar lallashi,tace "haba umma hadiza ya isa, ya isa haka kidena kukan nan dan Allah,ki bari na gwada kiranta kozai shiga, is okay."
Ta fadi hakan tana rarumar wayarta kirar iphone x newest version takai kunnen ta bayan ta dialing number rufaidar
,ringing yake tayi har saida ya kusa yankewa sannan aka daga...
Batama jira jin sautin muryanta taba cikin tsigar fada tace"..ke rufaida?koma daga ina kike toh kiyi maza kitaho gida yanzun nan..
Ko gama sauke wayar a kunnenta batayi ba sukaji motsin mutum ta bayan su atake dukkanin su suka juyo suna kallon ta inda ta fito da matukar mamaki a fuskokin su.
Bayan ta diro ciki A hankali ta juya cikin sanyin jiki ta karashe rufe windows din dakin sann ta juyo tana kallonsu ganin yadda suka tattaso tsaye suma suna kallonta
Karasawa gefen gadon tayi jiki babu kwari ta xauna a qasa murya can kasa tace ina yini Ammi jasmine?
Dagowa hjy jasmine tayi tunkan ma ta amsa umma hadiza ta katse ta a tsawace cikin bacin rai.. Tace..."ke Rufaida ashe bakida hankali?..Daga ina kike?nice tun safe daga ina kike?...sauri kiris ta gwada mata mari hajya jasmine ta janye ta baya tana huci..
A hankli jikin rufaida ya shiga rawa tuni koinanta ya dau kyarma tsaban takaicin dake cinta har cikin ranta wasu maquson hawayene suka shiga gangaro mata akan fuskarta wanda daga ganin su kasan bata shirya musu ba,yanayin ta mai cike da jin haushi da kuma tsananin so da tausayin mahaifiyartan.
Itama umman Ji take inama tana da ikon cikama rufaida burinta kamar yadda kowacce uwa take muradin cika ma yarta nata burin,sai dai kash Koda shike ba yau akasaba ba,yayun ta hudu an aurar dasu ahaka da wuya ne in ita ta kufce ma wannan mummunar aqida na mahaifinsu.
Tabbas itakanta da zataso tabaiwa yarta rufaida damar yin rayuwarta mai cike da haske da buri amma tasan hakan ba abu mai yuwa bane har abada auren nan dai shine qaddarar su.
Nan Ta fusato cikin sake maimaita mata tambayar ta"..Nace daga ina kika fito rufaida?ko bazaki bude bakin ki amsa ni bane?mahaifinki cewa yake har abada bazai yafeni ba sabida nice nake koya maki wayannan dabiun
Rufaida...
...cikin sauri Rufaidar ta dago kanta ta kalle mahaifiyartan jin alamar bakin ciki da kukan dake tafe a muryan ta,atake itama nata idanun suka gwaranyo da zafafan hawaye masu matukar karya gabobin jiki.
Rawa sosai jikinta ya shigayi muryan ta a disashe kallo daya zaka mata kasan tana cikin damuwa da tashin hankli,cikin wata tokararrayiyar muryan ta data kasa fita ta furta sunan mahaifiyar tan tace
"Umma dan Allah..
Dan Allah umma kiyi haquri ki yafeni,badan na quntata miki na fita a Gidan nan ba..
Kukan ne ya subuce mata mai tsuma "umma kinsan bana son bacin ranki
Jimin afuwa dana kasa danne zuciyata..umma dan Allah ki fahimce ni..umma dan All..ah..karkice na saba maki,sabida ke kawai na dawo gidan nan yanzu ,amma wallhy bana son auren nan umma..nikam mutuwa zanyi..
Ta karashe cikin sautin kuka mai qarfi da tsuma zuciya duka jikinta sai rawa yakeyi a durqushe agaban su.
Wani irin kukan fitar rai takeyi idanun ta a rufe kyammm bata ma iya budesu.
..shiru ne ya ratsa tsakanin sau dan hanklin su gaba daya a tashe yake na ganin yanayin rufaida, hjiya jasmine ta bi tarasa wazata fara tarba acikin su dukan su hawaye ne masu rauni yake sauka daga idanun su..kukan zuci sosai umma hadiza takeyi dan duk cikin yayan ta sun fi shaquwa da samun fahimtar juna da rufaida
Saidai Wani ciwon tabbas baida maganin daya wuce addua,hakan yasa Ta rufe idanun ta tsam cikin masifa
Tace rufaida ashe Kema mutuncin nawa xaki kwabar?meye na fada maki jiya da safe bance dake kiyi haquri ba rufaida?inkinyi masa biyayya mutuwa zakiyi?wato rufaida kin gwammaci kiga na fadi na mutu agidan nan sannan xaki haqura da shegen taurin kan naki ko...toh inkikayi masa taurin kan auren sai afasa yinshi dake?sanin kanki ne koda birnin sin kika tafi kika dawo sai anmiki auren nan,kidai duba dai tun daga kan babban dadarku murja har ita wacce kikebi suhane da ake shirin kaita yau ba'ayi auren fashe agidan nan ba,kisani, akanki kuma baza a fasa ba..
Wani sabon Kukan rufaida ta barke dashi durqushe a kasa agaban su ganin yaddaa hjya jasmine ta rirriiko mahaifiyartan dake a zuciye takeyi mata fadar looking both confused nd frustrated,"..
Ji take kamar ranta da zuciyarta duka zasu bar jikinta tsaban radadin azaban kuncin asaran burikan ta da tarwatsewar da rayuwarta yake shirin yi a lokaci guda..
Duk dama ta taso cikin ganin yayunta duka sunai ma mahaifinsu biyayya wa auren dolen da yake musu amma ita aranta jitake sam bazata taba iyawa ba...For what sake? Ita da ko secondryn ma bai bari ta kammala ba...?Inama ace yaa malam yadan kyale maganan auren nan har sai tayi ss3 dinta tukuna tunda dai ss2 take aynzu..
Saidai ayadda taga yasa ranshi da dukkan imaninshi akan zancen auren tan nan da wuyane ya fuskance damuwarta har ma ya saurare umman ta bare kuma ita..
Itadai tasan ance wajen karban auren yayarta suhane ya nemar mata miji kuma da alamun bayaso sukufce masa ne shiyasa yakeso ayi aure nan da wuri,dan cewa akayi suna da kudi sosai daga kasar waje ma suka taho..
Kukan fitar rai rufaida takeyi cikin tunanin yadda zatai asarar rayuwarta tun umma hadiza tana mata fada har ta gaji ta biyewa hjya jasmine suka suka dawo rarashin ta amma haka fir taki ta amshi batun auren nan aranta cewa take bazata taba iyawa ba..
Daga bisani da umma taga abun babu sauki kawai tayi waje ta barsu
"tana ficewa Rufaida ta durqusa kasa gaban hjya jasmine da idanunta da sukayi lufu lufu tace Ammi jasmine dan Allah ki kira kawu zaidu ya samin baki Wallahy zanyi duka abunda akace inyi muddin yaa MALAM zai kyaleni nayi karatuna,Ammi kirisss ya rage in kammala secndry
...Ammi bana son a aurar dani..Dan Allah kitaimaka min Ammy..Sosai take kuka ko inanta sanda ya sauya kamani daga na mutum tsabn kaduwa da tashin hanklin datake ciki..
Kasa cewa komi hjy jasmine tayi dan ita kanta tasan waye yaaa malam din
Uwarsa ma data tsuguna ta haifesa bata fiye lanqwasa shi ba bare ita datake a matsayin matar kanin shi?jikinta a sanyaye ta dago idanun ta da s sukayi sanyi a natse take kallon yanayin rufaidar dan sosai tausayin yarinyar ya shigeta,sabida tana burgeta sosai,a kaf cikin yaran yaaa malam itace kawai ta gwada borancewa dan ta karba ma kanta yanci na kokrin cimma burikan rayuwanta masu kyau Amma yayunta kam hannu bibbiyu ma suke biye masa akan lamarin sa na musu auren dolen dayakeyi..
Yatsun Hannunta ta kama sannan ta jawota har saman gadon sun,ajiyeta tayi kusa da ita ta rungumeta ajikinta sosai Babu abunda rufaida takeyi sai hawaye da kuka mai taba zuciya dan har cikin kasan ranta ta tsani abunda ke shirin afkuwa da ita..
Haquri da nasiha
Hjya jasmine ta rika bata amma ina kamar ma tunxirata akeyi,da kyar ta lallabeta ta yi alwala da niyyar haka intayi salla raka'a biyu zuciyarta zaiyi sanyi,shigarta bayi keda wuya saiga sallamar umman ta wacce ta kasa dago idanunta sama ta kalle su bare ta zauna a dakin
Daga gnin yanayin ta kasan dauriya kawai takeyi,cike da karfin hali".Tace
Hjya saiki fito masu daukar suhan din sun yi himma,ina ita RUFAIDAR? Ko itace a bayi?..dan miqewa tsaye hjy tayi tana dada gyara zaman mayafinta tace" "eh rufaida tana cikin bayi"..Ni nace mata tayi alwala tayi dan nafila naga tun dzu kukan kawai takeyi..kada kai kawai umma tayi batace uffan ba sukayi tsayuwar jiran fitowar tan Atare,dan shiru ne ya gifta tsakanin su,dukan su bakin su dauke da magana amma anrasa wanda zai fara cewa dan uwansa komi.
"Koya ake ciki da tsayuwar maganan ranan auren rufaidar oho?hjy jasmine ta shiga raya maganganu aranta itadai tasan tun shekaran jiya hajy mama take mitar cewa yaaa malam yaki jinta akan maganan auren rufaida shikuma dan uwan sa zaidu yace bazai taba saka bakinsa akan maganan ba,hjy tayi tayi akan koda ya barta ta kammala secndry schl nan da watanni amma sam yaki yace ya riga ya bada ita.
Akan wannan magana ta auren rufaida Gaba daya saida kansu ya daure,kowa tausayin ta yakeyi sabida duk sauran yan uwanta ba haka aka musu ba dan kowacce sanda yabarta tayi candy sannan ya aurar da ita,shin komaiyasa ya canza tsarin sa akan rufaidar oho?
Muryan umma ne ya katse ma hjy jasmine nazarinta,kallon kofar bayin take tana cewa
"Rufaida kiyi sauri kifito mana dan Allah,sai kuma tadanyi shiru,can Tace toh mahaifinki ne ya aiko ni in fitto dake aiko sallama kwayi da yar uwankin ko..
...hjy jasmine najinsu bata motsa ba bayan minti uku saiga rufaidar ta fito..sauke kanta kasa tayi ganin
Kallo daya suka bibbita dashi,umma Tace hjya muje ko?..Tace ok bismilla sannan ta ruko hannun rufaidar sukayo waje Umma ta saka kai wajen musu jagora har sasshen yaaa malam Inda yake acike makil da sauran yan uwanta mata da kakan su hjya mama da babbar yar Hajiya jasmine din wato barister fareesa zayd matazu.
Gaba daya hanklin rufaida baiya jikin ta,hasalima batasan awani yanayi take ciki ba,tafiya takeyi a xauce tare da hjy jasmine tamkar anajan rakumi da akala dan batama jin sautin komi face na zuciyarta dayake bugun shirin tarwatsewa dan kanshi
Tun daga bakin kofar dakinsan zaka soma jiyo sautin nasihohi da kalamai na zaman aure dake tashi ataciki,hawaye ne masu tsananin zafisuka kara ciko mata idanun ta jin Muryan yaa malam ayayin dayake bada fatawarsa har suka shigo suka zauna baima kalle su ba.
Yace:
"Aure babbar ni'ima ce wacce take kange mutum daga afkawa sharrin shaidan,aure yakan karawa mace da namiji kima acikin sauran jama a
Allah yakan sanyawa auren da akayi dominsa yardan sa da albarka acikin sa
Irin albarkar da ma'abotansa zasuji dadin rayuwar auren su ba tare da dauwamammen bacin rai ba"
Ni na sauke haqqin hakan akanku,domin In nema maku wannan kima da darajar na nema maku mazaje dakaiina wayanda zasu ji kaina kuma suji kanku.
Yau Ga mahaifiyata nan ita shaida ce duniya wa lahira".na neman wa duka yayana mazaje nagari batare da taimakon kowa ba
,"..toh wallahy, na rantse muku da Allahn daya halicceni, na rantse da kabarin baba na,
Duk wacce tayi asarar auranta duniya da lahira ban yafe mata ba.
Ke murja ke ruqayyya,atake first nd send born dinsa suka kalle sa jikinsu a matukar sanyaye
,Wani irin bushe fuskan sa yyi yace naji wasu kananan magangun banza da wofi na tasowa daga wajenku,wai bakwa jin dadin zama da majazenku ko?,toh wallhy inkuka biye ma uwayen ku suka zuga ku aka sake ku kuka fito daga gidan aurenku toh fa saidai ku koma zama akarkashin su can su ciyardaku su shayardaku
Dan Daga ranar da aka sake ku kusa aranku..."babuni babu ku"..Ni kuma ban tsine muku ba, amma kusani har abada na Haramce ku da taka kafafunku a kofar gidana.
Sabida haka duk wacce ta kashe aurenta sai ta san Inda dare ya mata amma ba a gidana ba.
Ya juyo a fusace ya kalle jadwa suhan da rufaida..
Yace Fatan maganata ya shiga kunnen kowacce acikin ku?
Atare Suka amsa shi da eh suna masu gyada kansu cikin gaggawa.
Yace Allah ne kawai zai sanya albarka acikin rayuwarku idan yaga manufarku na zaman aure saima ya sanya muku zuria dayyaba,yana kaiwa nan yace toh
"Ai saiku tashi ku kai ita suhan din yanzun..
Ba musu adda murja da adda rukayya da adda Jadwa suka miqe cikin shirinsu"
..anan kuma Hjya mama ta miqe da kyar cikin sauri tayi fafur a hanya Tace sam bazasu wuce ba...A rikice Tace kai bukar,da sauri ya shareta yyy gaba kamar ma baiji ta ba amma bata fasa ba,Nace ka dakata min,sai yaja dai ya tsaya can gefe batare dayama juyo danya kalle tan ba, "kamar ya Zakace akaita gidan miji Mu bamuyi namu maganan ba?kai waye da zaka wanice akaita?akan mubamu da abunda zamuce ma yarinyar kenan?Wani irin daure fuskar sa yy tamau,da kamar ma bazai amsaba saiya juyo ya haura mata da wa'azi, yana cewa ba a jinkirta aure da mutuwa dan haka kawai akai suhane gidan mijinta duk wanda zai mata nasiha saiya bita can yayi mata,Hajiy ta Inda take shiga bata nan take fita ba amma ko ajikinsa..baima san anayi ba..InTa fada shima saiya fada,dama can dabiar sa ne girman kai,yafiso in yayi nasiha kar wanima yace zaiyi,har yaushe akayi ilimin addini da za a nuna masa? Shi ko kunyar idon yayan cikinsa sa bayaji bare sauran nunawa yake kamar basu da haqqin yin magana bayan nashi,yanaji hjya tasa mai ihu tana cewa baiya saka adalci a al'amarun sa saidai shi ganin rakin ta yake a matsayin shirme irin na tsoffi da tsatsube tsatsube irin na mata,gaba daya saida suka tada hanklin kowa a dakin,ga mutane awaje makil ana jiran fitowar amarya
Miqewar da rufaida tayi zata fice ne ya jawo hanklinsa kanta,da alaman shirin fita take yi dake surutun sun ya soma haura mata kai Wani irin ciwo kantan ya soma mata bazata,cikin sanyin jiki ta miqe ta jikin ummanta kamar wanda zata rabe ta gefenta ta wuce,Wani wuff yaa malam yaa cakumo ta kamar zai figeta
,"shin ina zakije?idanun ta atake suka firfito a mugun tsorace ta dago kanta sama zata amsashi baima jira tace cass ba sai tssssss taji ya watsa mata Wani makohon mari akan fiskarta sanda ta sabule daga hannunn shi ta kife kasa a gigice
"...duka wayanda suka taso zasuzo kanta a tsawace yay kara cikin dakatar dasu,,Cikin tsawa da fada yace "Shasha sha kawai..Allah wadar naka ya lalace.
Ke wai Harni ne zaki nemi ki kunyartar?babu yarinyar danace zan mata aure ta gudu tun safe ba aganta ba waidon bata son aure,To kiji da kyau na riga dana Amshi sadakin Alaji BATURE akanki GOBE asabar da karfe 9 na safe daurin AUREN Ku
.
Hannu ya turmusa acikin aljihun sa ya fiddo wasu makudan kudi ya watso su kam fuskarta yabi ya kwashe ya maidasu aljihunsa A lokacin mutuwa ne kawai yaki zuwa na rufaida amma takai kololowa wajen zaucewa da baqin ciki
"Inkin ga dama saiki kashe kanki kafin goben..Auren ki kamar anyi angama,koda mutuwa kkyi
Bi'izinillah sai an daura auren nan da gawarki,domin in nuna miki cewa nine mai nasara akanki,nine gaba dake,sabida nine ubanki bake kika haifeni ba..ni ne nan mai iko da rayuwarki.
Har ke kin isa ince zanmiki aure ki bijire min?toh ga sakamakon silar taurin kainki nafasa jiran zagowar sati gobe gobe zaki barmin gidana
Makarnatar na hana,Na kuma haramta duk wata hidiman biki domin ki,daga an daura aurenki gobe zaki bi mijinki duk wanda ya daga kafarsa wai zai kaiki gidan miji Allah ya isa..Allah ya rufamin asiri babu wata yar iskan yarinyar da zata tona min
.....Wani irin birgima akasa rufaida takeyi tana kuka sanda tayi fayau tana rokon sa gafara amma ina baiya najin ta dan dabiar sa ne ya hawra can sama yana bunkasa musamman idan ana bashi haquri
Anan ya hada harda sauran borin fushinsa ya borance ya kore masu fidda amarya waje yana cewa rufaida tayi ma yan uwantan duka kallon karshe dan daga yau bazata kara ganinsu ba.
Kuka kawai rufaida take yi kanta akan kafar kakarsu da ke matse kwalla itama tana ta kwararo bambami duka abanza Umma kuwa tunda ta kife kanta akasa tana hawaye bata kara dagowa ba danji take kamar kirjinta zai fashe yy aman wuta tsaban radadi.
,"hjy jasmine da yarta faressa su suka jagorance murja ruqayya da jadwa sukayi waje da amarya suhan a cikin yaran kaf babu wanda xuciyarta baiya cike da jimamin tuna mumumunan kalaman mahaifin su akansu saukin abun daya dake su sun masa biyayya
Hasalima duka ganin laifin rufaidar sukeyi datazo da wannan sabon salo na neman wa kanta yancin yin karatu wanda aganin su hakan bata makai lokacine da neman karawa wakai takaici,dan tun bayauba kowa yasan halin mahaifinsu Yaaa malam, da rikakken ra'ayinsa na babu mai saka shi bare kuma mai kuma hanashi.
Surayyahms contact 08060712446
Part 1 IS FREE,TUKUICI NE GAREKU MASOYA NA U CAN READ IT HAR ZUWA INDA ZAMU TSAYA,SAIDAI CIGABAN SHI NA KUDI NE,PLS SHOW SOME LOVE AND SUBCRIBE the ACCESS FEE IS 300 NAIRA ONLY
VIA 0152983148
MOH'D SULE SURAYYA GTB.
OR katin MTN vtu tran via 08060712446
Screenshot ur evidence to SURAYYAHMS 08060712446
OR MAMAN MUBENA
08036651119.
11/18/21, 5:34 PM - Buhainat: *™✓SHADE OF RUFAIDAH*
_BY_
_SURAYYAHMS_
_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_
BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.
Part1:chapter 3
*Too fast,too soon*
Yamma ya rufa sosai dan haka yan kai amarya suna fitowa aka dau himmar kaita gidan mijinta dake can ta bayan babban airport din gari ,Alaji omar okene babban dan kasuwa ne kuma yana da kudi sosai dan haka shi aka bawa suhan din a matsayin mijin aure,saidai shi asalin sa inyamuri ne ta uwa ta uba,cikaken haihuwar Abia state ne girman cikin garin kano,shiyasa ma a Fuska da dabiar sa bazakayi saurin cewa shi inyamuri bane dake acikin hausawar ya taso tun yanada shekara hudu na haihuwa,.
Toh Wayanda suka san asalinsa since neman kudi ne ya fara tarkatosu shida iyayen sa sukazo garin kano suka yada zango a bayan gari,ande san inyamuri da shegen son neman kudi dan haka sunyi sana'oi kala kala suyi wannan suyi wannn saidai da lokaci ya dan karaja Alaji omar ya girma iyayen sa suka rasu, sana'ar da ya dawo yi was unknown ba a Kara gane masa ba.
Kaf makwabta da abokan harka babu wanda ya isa yace yasan takamammen sana'ar alaji omar okene except for d little little business investment wanda basufi cikin cokali ba,gashi a kullum sai habbaka yakeyi,arzikin gobe saiya ci uban na yau haka na jibi he is just flourishing day by day babu kakkautawa,tunda yaje kasar waje ya dawo ya yaxo ya siya wata mahaukaciyar gidan bene mai hawa takwas mutane suka fara saka mai kahon zuka,this man became centr of attraction dan kowa so yake yasan kalar sana'ar da yakeyi wanda ba a gani saidai agansa da miliyoyin kudi yana facaka yadda ransa yake so,hakan yasa ya rinka shiga kwama cala kala kala da yan anguwan su, wasu akan gaskiyar su ne,wasu kuma akan hassada ne da mugun nufi irin na dan adam musamman in yaga dan uwansa yasamu arzikin daya zarce nashi a bugu daya
But none of them eva defeated him,Allah bai taba bada kowa sa'a akan Alaji okene ba dan sau tari akanyi surkulle har kotu an jejje da shi anma ba aci galaba akansa ba.
Duk wani Zato da mummunan baqi babu wanda ba ayi akan dukiyar san Nan ba, wasu sunce blood money ne dama can matsafi ne wasu kuma sunce mugun barawo ne.
Ahaka Anshafi akalla shekaru shida ana kana nan magana ana ta wannan rigungimu daga baya har aka gaji aka kyalesa da dukiyar sa yana kuma yadda yakeso bai fasa ba..
A tsarin sa a duk macen daya gani ta masa kyau to saiya aureta,sannan baya auren mummunan mace,shi asalin zangwadaddiya mai diri da kyaun fuska yake tayawa,shiyasa yakan murqushe naira wa yan mata,ya kuma narka kudade da kayan alatu ma iyayenta har sai ya cimma burinsa na aurota.
Duk dama bawani sabuwar zance bane yawancin
Matan dayake aura basu wuce watanni biyu uku agidan sa suke ficewa,but hakan baiya hana zalamammun yan mata,zaurawa da kwadayayun iyayen su bashi hadin kai wajen kara Wani auren shi kansa ayau bazai iya tantance matan daya aura ya sake ba..
Bayan matsalar sa nacewa ba'asan silar arzikin sa,problem din zaman gidansa shine duk wacce aka kawota a matsayin mata toh tabbas sai ya dawo da ita walkantaciyar baiwa.
Amma ahakan mutane basu taba yadda da wannan maganan sabida ko anyi auren baya dena kashewa
Iyayen matansa kudi da musu alheri,da siyan niqi niqin kayan duniya da kuma mugun girmama su
Out of 100 baifi 2% ne kawai zasu yadda cewa cikin gidansa shi mugun gaske bane sai a wanda ya gani da idonsa dan bakaramin azaba da baqar kunci yake cusa ma matan sa ba
Cikin haka ne Har Allah ya hadashi da suhan yar gidan malam bukar wanda aka fisani da yaa malam,wanda bugu daya ya same shiga wajensa dake dama tsohon dabiar Yaa malam din ne aurar da yayansa domin samun kudi da abun duniya.
Kwata kwata da haduwar su da shirin auren baifi wata biyu
zunzurutun kudi da abinci Alaji okene ya rinka bawa yaa malam kyautansu har ya cimma burinsa na samun yarsa suhan.
Toh a Wajen karban auren tan ne dayazo da Wani abokin sa mai Suna Alaji BATURE dan America, anan shima yaga rufaida yace lallai abasa shima ya aura,yaa malam kuma daya riga yaga kudi idanunsa sun kife sai bai iya ce musu a'a ba.
Yana sane da cewa alkwari yy ma mahaifiyar sa na cewa zai bar yayansa mata kaf su same koda sec cerficate,amma jin ance Alaji BATURE zai iya kufce musu ya koma kasar waje yasa ya turje y bijire yace sam sai anyi auren rufaida da gaggawa.
Shi Alaji BATURE babu wanda yasan asalinsa sai babban abokinsa Alaji okene,ko yanayin arzikin su ma iri daya ne which of course babu wanda yake gane boyayyen sirrin su..
Shima ance yanada mata biyu kuma dukan su yan nigeria ne sabida shi a United state yake da zama shikam ma babu wanda ya taba sanin gidansa,time to time haka business meeting dinsu yake kawosa wajen Alaji okene
Kudi sosai Alaji bature ya narka wajen kwato yardan Yaa malam cikin gaggawa akan auren sa da rufaid
Yace nan da kwana uku yakeso ya tafi america can gidan sa dan haka zaifi kyau ayi biki ya wuce can da sabuwar matarsa rufaida.
Bangaren gidan ya malam*****
Kafun ace wani abu har waje ya washe tasss yan kodon biki duk kowa ya koma gidansa.
Daga cikin gidan ma babu kowa ata daki,Hajiya Mama da umma hadiza ne suka firfito tsakar gidan agigice da rufaida a hannu a hannu dan babu abunda takeyi sai suma..hjy maman ne akanta tanai mata fifita da mayafin ta,Wani uban shessheka rufaida takeja atake numfashin ta saiya dauke,"rufaida?rufai?"Hadeiza maza jeki ki kawo min ruwa..cikin hanzari umman ta miqe ta wuce kitchen ta dawo da modan ruwa a hannu ta miqa ma hjy mama wanda bata yi wata wata ba tahau yayyafa mata a fuska,tafi minti biyar tana hakan da kyar ta sake dan nishi sann suka san ma tana raye,Gaba daya hanklin su baya jikin su kaf idanun su yy jaaa,sun rasa yadda zasuyi Da lamarin
hjy tayi hawaye harta gaji umma hadiza kam bata iya cewa komi sai yawan sauke ajiyan zuciya datakeyi itama,sosai zuciyarta yake mata ciwo da radadi saidai ayanzu bata ma jin kodan ciwon tan damuwar da yarta yakeciki shiyafi komi daga mata hankli .
Ganin rufaida ahaka yasa take tunanin in har aka rabasu gobe hala itakam tasamu silar mutuwarta kenan
A Yau data fi kowa mugunjin radadin zafin rabuwa da yarta suhane da sauran yayanta, da kuma cewa da mijinta yayi ya yafesu ko an sako su har abada kar su dawo masa gida,inta tuna hakan takanji kamar wuta ne yake ci ata cikin jikinta,ga kuma rufaida wacce tasan tabbas ba sauya ra'ayinsa xaiyi akanta ba
Da kyar suka rinka jinyarta harta samu tayi bacci,dukan su jira sukeyi har wajen misalin 1 saura ma dare amma yaa malam bai dawo ba.
Babu yadda umma ta iya haka ta danne nata damuwar ta rinka lallaba hjy mama dan ta samu ta runtsa,da kyar ta cimma hakan dan cewa take baza a daura auren nan ba
zata kira danta zaidu sassafe zaizo ya tsaya mata tunda shi bukar din bai dauketa abakin komi ba..
*****
MAFARI.....
(Tushen su)
Asalin sunan mahaifin rufaida wato yaa malam shine Abubakar Ahmad salahudeen.
ya taso ya kuma girma ne a can wata kauye dake ake kira bazarkowa,a can jahar maiduguri yankin daya hadasu sosai da ynkunan kasar chadi.
mahaifiyarsa hajiya mama wacce asalin sunanta ne Hasiya Abdullahi,ita asalin shuwa arab ce ta uwa ta uba shiyasa a bugu daya kaganta zaka iya ce mata barabiya dan duk Wani siffar su na kyan jiki da kyan tsari tana dashi gashin kanta baki wuluk gata da diri da hasken fata da fararen idanu,gidan su gidan malamai ne dan haka anan ma garin maidugurin ta soma aure,auren wuri irin na al'adan mutanen da wanda tun yarinya tana da shekara 12 itama akayi mata,dake hasiya tataso ne a gidan mutunci hakan yasa ta auri wani babban makiyayin malamin zaure wanda asalin shi ba dan nigeria bane dan kasar eritrea ne Sunan sa Ahamadu salahudeen al'adab ana iya cemasa malami.
Wanda akace Daga kasar sa yy hijra yaje egypt ya kuma je ethiopia da qasar mali da sudan ya koyo karatun qur'ani,zallan karatun Allo na asalin fasalin warash ya kwarance,ahaka ya shafe kusan shekaru ashirin yanayi toh bayan ya gama ne yay hijra ta kasar chad har ya dawo kasar nigeria da zama Inda ya sauka a jahar maiduguri Amma bai shigo asalin cikin gari ba
Anan ma bai zauna ba ya kafa babban makarntar addini na zallan bada ilimin warash,duka Wani sirri da alhidaya dake dauke acikin ayoyin qur'ani ya nemi ilimin sanin su kuma sosai yake iya amfani dasu
Akan haka Ya shahara ya daukaka yay arxikin rufawa kai asiri,mutane daga kasashen da suka sanshi sosai suke zuwa zauren sa neman taimakon sa akan lamarin daya shafe rayuwar su kona lapyar su kona cigaban arzikin su koma akan maqiyansu.
A farko tsakanin sa da Allah yake aikin sa na taimako da ilimantarwa Inda yake amfani da ayoyin Allah ya warkan ya kuma saukaka,amma daga baya sai girman kai da jiji da kai ya bala'in kama zuciyar shi musamman dayaga yadda dumbin mutane suke yaba qarfin ilminshi da kaifin aikin sa,suke daukaka sa ake jin maganan sa ana mugun girmama Inda yasa kafarsa ya taka,sai ya zamto yay kaurin suna da daraja a lokaci guda.
Ana haka a hankli saiya shiga cusa ma almajiran sa ra'ayi wanda baishafe addini da tarbiya ba,ashe a boye yakanyi aiki irin na sihiri ma yan siyasa da masu arzikin kasar nigeria with time har hakan ya fito filli duniya suka San yana hada lamarinsa da aljanu da tsafi duk dama yaki sam ya amince musu cewa gaskiya ne yana hada al amuransa da sihiri
A duk halina duniya babu wanda ya isa yaja da malam Ahamadu a girman kai da son musunta abunda baizo daidai danashi ra'ayin ba.
hakan yasa wasu tsirarrun malamai a maidugurin suka fara kalubalantar sa akan yaji tsoron Allah,inyaji waa'zin saiyayi musu yace kuma hassada ake mishi akan ilimin da Allah ya riga ya bashi..
Gashi Allah ya dora masa girman kan da koyayi bata kuma yasan ya batan bazai taba amincewa ba muddin ace Wani ne yamasa gyaran,a rayuwan sa da lamarin xuciyar sa ya riga ya tsara cewa shi yayi ilimin da ya zarce Wani dan adam galibi yay masa gyara ko shi ya amshe gyaran domin in yy Hakan ji yake kamar an rage masa Wani abu daga kimarsa.
Haka yake rayuwarsa yanajin cewa Shi sarkin ilimi ne da kima da daraja,hakan ya jawo wasu almajiran sa suka bijirre masa saidai mafi yawansun sunan tare dashi.
Sosai yake adawa da sauran malaman addini da suke gaya masa gaskiya,saiya juya abun yace ai sudin kafurai ne, turawa ne duk suka batasu,daga haka ya fara cusa ma mabiyansa ra'ayin kin neman ilimin kimiyyya da fasaha,ya kuma ce musu wannan ilimin shi zai batar dasu zai rabasu da Allah .
Shekaran sa uku da auren hasiya(hjy mamah) suka haihu suka haifi dansu mai suna Abbakar
Wanda akafi sani da
yaa malam..
Yaah malam shine babban dansu kwalli daya wanda ya gado ubansa sosai tako ta ina da kamanni da komi,asalin akan harkan gardancin mahaifinsa ya rainesa,ya girma ya zamto cikakke kuma rikakken gardi wanda baisan komi game da duniya ba sai karatun qur'ani da aka rainosa dashi.
yaa malam yana da shekara biyar babansan yazo ya rasu,bayan nan da kyar ma mahaifiyar sa hasiyar (hjiy mama) ta rabasa da kauyen da suke sukazo cikin gari ahakan ma wata da watanni yyi yana fushi da dacin rai da ita, baya cin abincinta waidan ta rabasa da gidan gadon ubansa ta kawosa cikin gari cikin arna.
Duk da hakan Rayuwar gardancin sa yakeyi abunsa,duk Wani abu dazai hadasa da neman ilimi irinna bature to ya tsaneshi,Wani bin har aga kamar yafi karfin mahaifiyar san ne.
Saidai kuma hjy Hasiyar asalin ta mai raki ce duk tsiyarsa haka yake dawowa dan dolensa ya mata biyayya dan sosai yake kaunarta aransa.
A xamanta dashi Babu yadda batayi dashi yay koda primary school ba amma haka yaki sam,inma ta damesa saiya fara mata barazanar cewa zai barta zaije kawai ya shiga uwa duniya yay rayuwar sa yadda yake so,itakuwa intaji ya furta hakan saita hqra kawai ta kyaleshi shiyasa ma tun yana yaron ya barke da gararin gari yana sana'an rimi da koyarwa har yayita kokri dan ya tara almajiran sa..
When he reached 7 kafin nan hjy mama tayi Wani auren ta auri Wani babban mutum dan asalin garin katsinan dikko mai kudin gaske anace dashi Alhji dikko matazu.
Shi Matarsa ce ta rasu saiya auri hajya mamah,toh Tunda ya auretan suka bar maiduguri suka koma zama a babban gidan sa dake garin kano.
shima babu yadda baiyi da yaa malam akan yaje makaranta yy karatu ba amma haka yakimusu fir, karshen ta ma guje musu yayi agidan ya nemi gidan haya ata bayan gari yana rayuwar gardancin sa,akan haka saida yasha wahala matuka kafun ya saba da mutanen anguwa,sabida shi yarone amma jahili ne mai tsananin girman kai da nuna isa,hjy mama itake ci dashi ta shayar dashi but shi jahilin mutum daga anmasa gyara ko fada sai yace an masa gori..
Wani bin ya gwammaci ya kwana da baqar yunwa da amasa gyara,saiya zamto Zaman haquri kawai kowa yakeyi da yaa malam musamman ma mijin mahaifiyarsan wato alhaj dikko matazu wanda bakasafai ma yake girmama shi ba.
Ana haka ko shekara basuyi da dawowarsu kano ba Hjiy hasiya ta haifi kaninshi aka samasa Suna Zaid dikko matazu,an haife zaid da shekara bakwai a duniya shima mahaifin nasa alhj dikko ya rasu,cikin ikon Allah haka zayd din ya girma yayi ilimi ya kuma gaji dukiya mai tarin yawa irin na ubansa,sai ya dawo shahararren babban hamshakin dan kasuwa a garin kano,kuma yyi karatu sosai ya zamto babban lawya a fannin shariar musulunci kaf garin ana kiransa da suna YAA SHEIKH sabida tsabar kwarencewar sa wajen iya aiki da ilimin da Allah ya basa.
"Toh kasancewar su yan uba da yaa Malam sai basu cika wani shiri sosai ba,dake tun yana dan karami a kullum yaa malam yazo gidan yagansa da uniform din boko yakance masa .. "kai tafican ARNE kawai"..shikuwa kalman matukar haushi yake basa,Shekara goma ne a tsakanin su amma hakan bai hana su kaurewa wajen cece kuce musamman inya furta ma zayd din hakan ba.
sai dai duk batawar da zasuyi a tsakanin su bada dadewa zakaga sun shirya domin kuwa akwai wannan soyayyar jinin dake cikin xuciyar su wanda hjy mamar ce take dada karfafawa Duk dama Sun kasance mutane biyu ne masu mabanbatan ra'ayi game da rayuwa.
As time goes on zayd sai yayi qarfin ilimi da arxiki shikuma yaa malam ya tara almajirai yana koyar dasu
Da haka ya sanu yasamu mabiya dayawa har yyi gidan kansa ata bayan gari.
Tun yana da shekara sha bakwai yayi aure matar sa na farko mai suna Tani bata iya jure halayen sa ba tafice dan ko haihuwa batayi agidan sa ba
Bai daddara ba ya auro wata bazaura mai suna Shafa'atu itace ta haifa masa yarsa ta farko wato murja..
Itakam baqar azaban yunwa ne ya fiddata.
Sai ya auro wata dillaliya anace mata gambo,itama tazo ta haifar masa ya mace mai suna ruqayya da bori da hauka itama ta fice a gidansa
Can sannan ya auro hadeiza wacce tsabar haqurin iya zama dashi datakeyi yasa mutane suke ganin kamar ma itace ya auro a farko
Hadieza marainiyar Allah ce ba uwa ba uba tsohuwar data raineta ne ta bada ita aure wa yaa malam sakamakon maganin daya mata na ciwon zuciya wanda bata da kudin biyanshi saita biyashi da auren yar rikonta kwalli daya hadieza..
Hakan yasa bai taba daraja Matarsa hadiza ba,gani yake
Kamar sadaqa aka bashi ita,shiyasa tunda ta auresa bata tabajin dadin rayuwarta a hannun sa ba,wulkancin yau daban na gobe da daban harta haifa masa yaya uku,wato Jadwa,suhan da yar autarsu rufaida.
A fadi tashi da kame kame suke tafiyar da rayuwar su,tsakanin ta da Allah ta rike yayan kishiyoyin ta Duk dama basu taba gode mata ba.
Yaa malam haka yaki sam yabar dan uwansan yaa sheik ya taimake sa koda da sana'a ne sabida wannan tsinannen girman kan jahilcin jin cewa fa shine ma agabansa a shekaru.
A Kullum cikin ikirari yake na cewa zai iya rayuwar sa kuma baya bukatr taimakon kowa bare azo anamasa gori.
Har suka girma sosai suka manyanta hankli ya dan daidaita kansu ba kamar da can ba
Ayanzu dai kowa nayin rayuwar sa ne ayadda halayen sa suke bi dashi.
Tsananin Girman kai yasa Yaa malam yyi ta wahalar gina rayuwar sa acikin baqar talauci.
shiyasa da yayansa mata suka girma sai kawai ya fara aurar dasu ga masu kudi yana caskar kudin abunshi,dama can Shida iyalansan suna zama ne a kaskantacen anguwa dan shi bayason hada kafa da masu ilimin boko ya tsane su har ransa baison muamala dasu,kawai ya bar yayan san suyi karatu ne sabida bin umarnin uwar san duk da hakama dakyar suke wuce secndry schull maza saiya kawo namiji yace ya badasu
Shikuma Yaa sheik sanda ya kammala service dinsa ya auri matar sa hajiya jasmine khalid matori,ita yar gidan wani tsohon govenor ne tana da kaninta kwalli daya wanda akece masa IMAD,...tunda mahaifin ta ya rasu yaa sheik yake kyaywar dawainiya da dukan lamuran mahaifiyarta mai suna Hajiya saddika fulani
Hakan yasa suke matukar son junan su, suna gudanar da rayuwarsu ne cikin tsananin girmama juna da baiwa iyayen su haqqin su sosai..
Yadda mijinta zayd yake qirmama mahaifiyarta haka Itama take mugun girmama nashi mahaifiyar...
Shiyasa a Duk yadda hajya mama taso ta raba muhallin ta dasu hakan baiyuba saboda hjya jasmine taki sam haryau su rabu kuma suna zaman su atare cikin lumana da kwanciyar hanklu
Hjy jasmine Bata wani dade da auren zayd ba ta haifar masa yaya har guda biyar,..
Babban yarta mace wanda tayi karatun law a kasar london anace mata barister FAREESAH zayd matazu ko anty reesa,sai babban dansu namiji capt MUFRAD zayd matazu shikuma navy aka turasa a kasar south korea,Inda ya fito da babban matsayin sa na captain ana yawan cemai capt. muffy,..sai mabiyinsa mai suna KEEYAN zayd matazu ana yawan ce masa maska cos he is an enginering student in saudi arabian petroleum engineering stands.
Sai kuma NAZLI zayd matazu
Ita kuma medical student ce tana 2nd year dinta a medical school in india
daga ita sai yar autarsu SHUKRA(khadija zayd matazu) dake karanta fannin international law anan university of nigeria nsukka.
sunada eldest step sis wacce ake cewa Anty Anu,ita kuma asalin sunanta laila zayd matazu,saidai ita ba yar sunna bace,qaddara ya fada wa yaa sheik aka sameta,so her mum is from sokoto state, who uses magic to seduce zayd matazu dan ta cika Wani burinta na rabashi da matarsa jasmine tun farkon auren su amma bataci nasara akansa ba,ta haifi Anu and then she died immidietly batare da auren san akanta ba,,
So a hannun iyayen mahaifiyarr Anu ta girma,Anu kusan sa'ar Anty fareesa ne, dake ma ita ba yar sunna bace so bata cika son zama da su ba hutu kawai take xuwa shima da kkyar in su hajya mama sun tursasa ta
..hakan yasa kusan rabin yan uwanta basa kaunarta thy dont like her much to be around them musamman ma nazli da shukra wayanda sukadau kishi da tsanar duniya suka daura mata..
..tsawon lokaci rayuwar su a hakan yake tafiya yau shiri shiri gobe a araba gari,evn thou iyayen su basu taba nuna bambamci akan yayan su ba .
At times Anu takanzo gidan ne kawai dan hjy jasmine da kuma kakarsu hajya mama amma badon tahada kai da yan uwantan ba
She actually prefer to live her life respectfully gudun kar wata rana a cakka mata baqar magana ko ace mata shegiya..
Anty fareesa kuwa yar ba ruwanta ne last 5years tayi aure daga aikinta sai biyayya wa iyayenta kuma ita kowa nata ne batajin ko daukar gulma,kowa na bata respect cos tana da dattako da halin manya not long ta haifi yaranta biyu wato Iman da,jawad.
shikuma capt muffy shine ake daukar sa kamar magajin baban su zayd matazu,every body loves him sabida halayensa da suka matukar banbanta dana kowa,shi Wani irin murdaden mutum ne,just last year ya daure ya auro wata office girl ana cemata Aina'u Abbakar makarfi,wanda ake cewa Ayn makarfi.
So Keeyan is just a friendly normal guy shidai baya iya fada da kowa Kuma ta Wani fannin Suna masifafiyar kama da yayan sa mufrad
Nazli kuwa yar high standard of living ce tana da mugun ji da kanta duk dama ilimin addini ya shigeta sosai so tana dan sa tunani aharkan rayuwarta badai jijii da kaina jahilci ba,she is high temperd and sumtimes very vulnerable tanada saurin karaya.
"Shukra?she is worst of all she hate evryone nd suspect evryone kullum itake spreading hateful news nd malicess acikin gidan alhaj zayd matazu.....
Rashin samun kyakkwar hadin kai tsakanin yaa malam da kanin sa yaa sheik yasa yayansu ma basa zumunta da juna.
For the fact dat level dinsu ma ya bambamta sai kowa yake jajjan baya da kowa,they are close cousins amma babu bai iya saurin cewa hakan,cos compare to familyn matazu yaran yaaa malam suna rayuwar kaskanci ne da talauci,sannan kowa yasan ba'a basu kwararren ilimin kimiyya ba..
Shiyasa suma yaran nasa suka kama kansu sosai,da wuya zakaga su rufaida da adda murja ko su suhan sunzo bakonta gdan uncle dinsu zaidu matazu.
Dake ko sunzo ziyara ma kallon kauyawa ko marasa ilimi yaransa suke musu Haka yasa Sai suke yawan kama girman su basa son shiga hidamar su ko hira akeyi bakasafai suke tsoma bakin su ba
Dama kuma daga sunzo gidan saidai sugama bulayin su a sashen kakarsu Hajiya mama in sun gama sai su shigo main mansion din suyi ma hjy jasmine sallama sukama gaban su...
Nazli da shukra sunfi kowa tsanar su aransu sabida ko babu komi yayan yaaa malam kaffff Allah ya axurta su da masiffafiyar kyaun jiki da kuma kyaun fuska nagani na fada.
Sukuwa Gudun raini yasa Baifi a kirga zuwan su gidanba ma..they are well acquiented with each other amma zumuncin dake tsakanin su sama sama suke gudanar dashi dan ko kadan bai samu daman yin qarfi ba...
08060712446
Surayyahms
*BUSINESS PROMOTION AND ADVERTS♨️📢*
SHAHARARRIYAR MARUBUCIYAR LITTAFIN NAN KUDI KUMBAR SUSA Da AHUMAGGAH TANA
FARINCIKIN SANAR DA MASOYANTA MUSAMMAN MA YAN KASUWA DA MASU KANANAN BUSINESS DA SUKE BUKATAN BUSINESS PROMOTION KO ADVERTS,A SAMAN LITTAFI KO STATUS IN DA ZA'A TALLATA KUMA BAYYANA SANA'OIN SU GA DUNIYA LUNGU DA SAQO MUTANE SU GANI DOMIN ASANDA SU DA ABUBUWAN DA SUKE SAYARWA CIKIN FARASHI MAI SAUKI,AM GOING TO MAKE IT CHEAP SABIDA MASU KANANAN SANA'OI SUNFI MU BUKATAR SAMUN WANNAN DAMA.
Game bukata sai ya tuntubeta kai tsaye 👉🏿@08060712446
Sa'a tafi sammako yar uwa ur customers might be in our timeline💋👌🏿
Part 1 IS FREE,TUKUICI NE GAREKU MASOYA NA U CAN READ IT HAR ZUWA INDA ZAMU TSAYA,SAIDAI CIGABAN SHI NA KUDI NE,PLS SHOW SOME LOVE AND SUBCRIBE the ACCESS FEE IS 300 NAIRA ONLY
VIA 0152983148
MOH'D SULE SURAYYA GTB.
OR katin MTN vtu tran via 08060712446
Screenshot ur evidence to SURAYYAHMS 08060712446
OR MAMAN MUBENA
08036651119.
11/18/21, 5:36 PM - Buhainat: *™✓SHADE OF RUFAIDAH*
_BY_
_SURAYYAHMS_
_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_
BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.
Part1:chapter 5
*Aina'u makarfi*
_*F1 expresso:emirate street, new extension.kano state,Nigeria.*_
Anguwa ne na manyan mutane wanda shaharar sa bai tsaya ga kyafaffun ginan ginan gidajen zamanin dake nan ba harda kasancewar muhallai na muhimman mutane masu tsantsar daraja,kudi,ilimi,mukami,suna,kai harma da masu mulki da sarauta a kasar.
Anguwa ne wanda aka tsara shi ata can gefe da cikin gari ta Inda kokadan ba a samun yawan cunkuso ko hayaniyar jama'a.
Anyi tsarin anguwar ne street by street kuma kowani street yana da lanes dinsa,so gaba daya anguwar yanada mashiga da mafita guda biyar ne kacal,snn akowani mashigar street akwai manya kuma dogayen dirarrun kofunar karfe wanda zai tabbatr maka da cewa ana rufe kowata gabar shiganta musammn in dare yayi..
A kofar Kowani gaban shiga wata yar tenti ne na jamian tsaro wanda aka musu horo na musanman domin lura da masu shige da fice a anguwar.
Emirate street kusan mafarkin kowani dan adam ne, dan acikin masu kudin ma bakowa yake samun daman zama anan ba,Wa duka anguwar ake cewa "emirate street"saidai lane din ne kawai yake banbanta su Inda zakaga dark golden signal board a manne a jikin kofar kowani mashiga
Gate na farko shine f1 expresso, na biyu f2 expresso...har zuwa f5..sannan acikin ko Wanne gate not less dan 1000 buildings zakagani a jere,a takaice za'ayi iya cewa Duka Duka anguwar emirate street na dauke ne da 5,000 exclusive buildings including malls,restaurant,masjids nd churches hospitals and trade fairs..
Saidai kasuwannin su da asibitan su tamkar masu kawai akayi,dan duka mutanen dake zama awajen are born with silver spoons wanda kullum zakana ganin su cikin swags na high standard of living styles,talaka ko mai karamin karfi bazai taba iya jure expenses din zama anan ba.
A first street wato f1 expresso,Anyi Wani kyafaffen gida wanda yake daura da Gidan Wani shahararren 7starred Army general wanda akai ce masa general murtala kosoko
Wannan gida ya shahara ne sabida tsantsar kyaunsa da yadda aka kawata gaban sa da shuke shuken fulawowi masu ratsa hasken idanu,sai kuma uban tashen kima da mutunci damai gidan yakeyi musamman a idon jama'a....
A jikin babban golden gate din shiga ciki aka manna silver bell plate mai bala'in dauke ido anrubuta 4321 Attor.Zaid D matazu residence.
Yadda tawaje yake a kawace da shuke shuke hakama cikin gidan yake,koina an tsarasa ne cikin tsafta da kwarewat so One single lane ne zai kaika har cikin harabar gidan dake dauke da wata madaidaiciyar parking space da dan karamin cool down na zama ko shakatawa.
So the main mansion stays in d middle,dan sosai ake iya zagaye gidan harta bayansa batare da kakai bangon sa ba,sai ya kasance filin daketa bayan gidan yafi na gaban gidan yawa alaman su mutane ne da basason a gifta musu a bazata bare a shiga cikin harkan personal life dinsu
so Swimming pools dinsu,relaxation outdoor palors da main garage da Duk Wani abu na shakatawa Duk anan abaya suke bata gaba ba..
Cikin gidan kuwa bangare hudu kacal yake dashi
bangaren farko na dauke da sashen iyayen ne sai na biyu na kakar su hjya hasiya,na ukun sashen yaran su ne wanda yake da dakuna masu kyau fadi da yelwa guda takwas dukanin su ajere hudu na kallon hudu,anan nazli da keeyan da shukra suke zama kowada personal room dinsa,sai sauran rooms din da suka rage aka barsu kamar quest room musammn ma in baqon na jini ne ko na kusa da su sosai.
Mata ne makil a babban tsakar gidan dayasha bugun cement duk sun sanya ankon su ta rubber rubber milk colour da ja dukan su dinkunan su iri daya..
Babba da yaro tsoffi da matan anguwa sai hayaniya ake anata cin shinkafa kamar Allah ne ya aiko su,ga wasu a can gefe sun baza faranti suna famar shan kwate,wasu na warban zazzafar masa da miyan taushe wacca taji dage dagen Kan naman rago,wasu nacin dafa duka ta rice, ga zobo drink ga kunun zaki ga uwar gayya wato taliya jollof da kuma tuwon shinkafa,...
daga can gefe kuma wasu tsofaffi ne a shinfede akan tabarmai suna famar rera wakokin zube suna buga kirari irinna zalamammun makwaidatan maroka wanda sukayi degree a harkan barace barace da kwaram agidajen biki.
At same time Kidan wakar hausa mai dauke da kalaman soyayya ta mawakin nan hamisu breaker na tashi sosai sautin kida ta cikke iskan wajen
wasu matan na rawa ana shewa ana manna musu kudade,wasu kuwa banda gulma da tsugudidi ba abunda sukeyi wani irin gudan nishadi akeyi daga gani kasan gidan biki ne daya amsa sunan sa gidan biki.
Gidan Babban gidane mai fadin gaske wanda saika wuce inda ake shagalin bikin sannan kabi wata sashe dasuke kira da sashen YAA MALAM.
Kasancewar sashen yaa malam yafi kowani sashi girma agidan daga nan ma yake sauke Manyan baqin da sukazo bikin musamman domin shi
Mutane ne akoina saidai duk da haka ko ina agidan fess yake,duk dama biki ake a gidan amma basa barin koda cokali akasa, anshare cementin kasan tasss an shimfida tabarmai ko ina dai sai kyalli yake tsabagen tsaftar su.
ginin flat daya ne a sashen YAA MALAM self contain ce mai dauke da wani babban fankacecen falo da akalla zai iya daukan mutane talatin, falon na dauke da wasu irin hadaddun kujeru brown color asalin design din da can mai tumtum dan ko pilow ba ayi musu ba,sai ledan tsakar dakinsa mai shegen kyau shima bown colour da yar sallayar sa agefe sai wayansu jimammun jakunan littafai da kwalaben tawadar sa,da kwaryaye da Alluna da ake jerawa ajikin bango sak irin shigen kwalliyar da mutanen da can sukeyi ma muhallin su.
kana ganin dakin kaga dakin babban magidanci kuma MALAMIN addini zaune yake a babban kujerar tsakiya tare da baqinsa yan birnin kudu da surukunan sa wanda suka shigo ba da jimawa ba,yau yaa MALAM ya fito ras yasha fararen shadda inda akamai dinkin malum malum yy kyau kwarai kamar bashii ba.
Agefen sa wata tsohuwa ce wacce a shekaru akalla bazata wuce 68 ba taci uwar atampar ta super holland gold daketa sheqa gyalli kaman an shafa mai mangyda ajikinsa, an mata dinkin buba da zanin sa data daura akan rigan dake ma kyam take dan ita tsufar bai lalata mata jikinta sosai ba,motsatsen kafanta da gabaki dayanshi yasha jan lallai tayi irin lallen nan ne da akafi sani da dungulmin tsohuwa.
fara sol ce tsohuwar,gashin kanta dana giranta duk sunyi furfura sabida tsabar tsufa, sai goshinta d kan hancin ta daketa fidda uban zufa
Kuma dudda tsufan nata siffarta bai hana nuna kamannin ta da magidancin dake zaune kusa da itan ba,hakan ya kara bayyana cewa mahaifiyarshi ce.
A cikin muryanta na tsofaffi mai tafe da dan masifa ta kira sunan sa a hankli tace..."Bukar,bukar,bukar wai sau nawa na kira sunanka?Shiru yay dan baison ya amsa ta agaban baqinsan ya sauke kai ya maida hanklinsa kanta dan baiso tabashi kunya agaban su duk dama jin kunya ba wata aba bace data damesa.
Murya kasa kasa Tace kaga dai sau uku nakiraka ko toh wlh nagaji da zaman nan kodai ka tsawatar wa yarka ta dawo kona tattara yinawa yinawa nabarma gidanka nakoma chan cikin gari Gidan dan uwanka zaidu ai dama saida yace in huta kafafuna nayi fafur naki bin nashi,yo mai zan gani anan?abunda aka saba dai shi akayi shi nikuma an ajiye ni kamar bazaurar gawa..tsaki taja mtswww,tace aikin banza aikin wofi kawai..ni ka gayamin abunda zaka fada min kawai in kama gaba na
Dan rangwofowa yayi,baqar fuskan nan nasa a balain turmushe yana kallon ta sanin cewa yanda take masifan ne kawai yasa zai sassauto da muryan sa qasa ya kulata dan yatsani a rinka aibata shi ko akira sunan kanin sa zaidu acikin lamarin sa yace "kiyakuri
Hajiya Mama yi hakuri"..bata kulashi ba can ta yaface hakwararta da dan tsinke kasar wuyarta tace
,"bawani zancen na yakuri" ta watsa mai harara atsakar idoh tana nunashi da dan yatsa tace yau kuma wani iskanci RUFAIDA ta samo ku kuma kuka daure mata gindi?Baice komi ba,ta kuma Jan tsaki yo inba hakaba Aljanu ne mutanen datake jin tsoron su?koko mudinne Mayu da ta guje mu?Ai Cha nayi yau duk yan uwane da abokan arziki suka cika gidan nan,yau ake bikin yayarta SUHANE amma wai ace tun safe ba'aga yarinyar nan ba tasaci hanya ta sabe silihu tafice? yo kajimin yar banzan yarinya marar kan gado,nide ba waje na ta debo yawon banza ba,sai dai awajenka,ko awajen uwarta hadiza.."
Tana gama sumbatun ta taja tayi shiru sabida rashin amsa mitar ta da yaa MALAM din yayi, sallaman da akayi ne daga bakin kofa ya dada Jan hanklin su,wata kyaykyawan mace mai dan jiki yar doguwa tasaka madaidaicin Atampa an mata dinkin riga da zani doguwan riga plain
ta shigo dakin fuskarta ba yabo ba fallasa ta karaso ciki ta gaida tsohuwar a ladabce
Tace sannu da hutawa hjiya mamah"Kallo ta kare mata saf sannan ta harareta batare data amsaba hakan yasa matar sunkyar dakai ta dubi yaa malam dake kallonta tace "gani Mai gida naji ka aiko akirani" cikin fushi yana girgiza kafa yace shin wai ina RUFAIDAR taje ne?"
shiru tadanyi tana kallonshi kafin ta sauke ajiyan zuciya a hankli mai cike da damuwa tace "malam nima bansan inda take ba" ..
"karya takeyi, na rantse maka Bukar, kunma isa?wlh, wlh kajini dakyau na rantse maka na sake rantsewa in baku nemo min jikata rufaida ba yau saina tsine muku Albarkan dake kanku tas kaida matarka kafun intafiyata Gidan zaidu inda kwanciyan hankali yake achan".. ta karashe maganan tana uban huci kaman dagaske.
kallonta kawai yaa malam yayi cike da takaicinta dan ya gama fahimtar meyasa take son tada rikici,da alama so kawai take baqin sa susan me ake ciki nacewa rufaida batason auren koda ma zasuce sun fasa,sosai ya gano salon mahaifiyar san kuma yasan babu yadda za'ayi ta juya ma rufaida baya.
Dada daure fuskan sa yayi. yace "haba mamah, to kibari nai magana mana kawai ai basai rufaidar tazo bama dama akan batun auren ta ne,zata budi baki yayi sauri yamike tsaye yace nace kiyakuri ko?babu kuma inda zakije sai an gama maganar, kiyakuri wayannan baqin domin mu sukazo rufaidar dama kawai ake jira dan karkuce na zalunceta
kwafa tayi tawani rau rau da idanunta tana binsa da kallon mamakin furta mata hakan dayayi dan karkada kafafunta tyi tace toh da ba aga rufaidan ba ai sai ka yi maganan ka ai dama hakan kasaba yi".
Kasa cewa komi yayi sabida yafison sai yarshin tana cikinsu sannan yay bayanin sa a tsanake domin ya jadadda qudirin sa a zuciyar duk wnda yake shakkar yiyuwar lamarin auren rufaida acikin gidan
,lura da hakan yasa tsohuwar ta miqe tayi waje tabarsu dan sosai takejin zafin abunda dantan yakeyi ma yayansa
Na musu aure batare da son ransu ba
kallon matar sa yayi datai shiru tana jinsu jikinta a matukar sanyaye,a dake ya juyo kanta yace KE hadiza wai ina RUFAIDAR taje ne? Ki fadi tsakaninki da Allah" a sanyayei ta dago tace "wlh mai gida nima bansani ba. bansan inda tayiba, ina fama da jama'an biki ban masan bata gidan ba saida su Jadwa sukazo ta fadamin wai yau kwata kwata bataga rufai ba"
cikin fushi da tsananin takaicinsu ita da yartan yace "to kije koma ina take ki nemota kin daisan sabida ita na aje manyan mutanen dake nan ko?yaune ranar da zasu ganta kuma yau nakeso na jadadda maganan ranar auren ta agaban kowa yaji
Inhar rufaida guduwa tayi dan ta tozartani duniya da lahira bazan yafe miki ba hadiza..
Umma tace...a'a dama fa tace da ita za'akai yayarta chan anguwar gidan mijinta inaga rufaida ba guduwa tayi ba... atake ya tsareta dacewa ohon miki nidai na fadamiki kinemota ta dawo gidan nan yanzun nan"...
dan ajiyan zuciya ta sauke tana kallonshi kafin ta miqe tsaye tana girgiza kai cike da takaicin sa ta juya zata fice tabar dakin can saikuma sai ta juyo ta kalleshi da idanunta da sukadan chanza kala tace "amma malam kasan matsalan yarinyar nan rufaida ko? batun yau mukasan bata son auren nan ba tanada muguwar tsor...o..n aur..e itafa karatu take son yi
cikin wata muguwar harara ya katseta da sauri ta hanyar cewa karatun yaci ubansa Nace miki..."yanzu rufaida yarinya ce da zakice min tana tsoron aure?KE meye amfanin ki amatsayinki na mahaifiyanta?MIJI gashinan ni na samar mata kuma WALLAHI shi zata aura.Ya karashe maganan yana nuni da daya daga cikin dattijan mazan da suke zaune a falon wanda da alama hirar su sukeyi bama jinsu sukeyi ba.
Da sauri umma Hadiza tayi saurin dauke idanunta akan su musamn akan shi Wanda akace za'abawa rufaida,gashi nan dai Wani tsohon tsoho dan ko a shekaru tasan ya haife rufaidan ta,runtse idanun ta tayi jin wani qullutun baqin cikin daya tokare ta akirji ganin ko a fuska ma bai dace da yarta ba
" .. Kinga kisan yanda zakiyi kinemo ta kindaiga raina a abace yake kina kara bata lokaci karfe biyar za'a zo daukan Suhane kuma tare zasu tafi yanzu karfe hudu ne harda kwata"juyawa tayi ahankali tafita daga dakin batare datace mishi uffan ba, da kyar ma ta iya saita fuskanta ta amsa gaisuwan mutanen dake tsakar gida ke mata amatsayin ta na uwar Gidan kuma uwar amarya
Nan ta wuce ta shiga bangaren su inda falontan ma ke cike da jama'an ta dana anguwa ana zaune anyi makil
Gefe tayi tabude wani dan daki ta shiga ciki,wata babbar mace ce a zaune a dakin tana hada kayan akwatin Amarya da za'a tafi dasu kana ganin matar kaga kamanin manyan hajiyoyi maida kofar umma hadiza tayi ta rufe ta shigo ta zauna kan gadon sun dabas jikinta sam babu kwari da sauri tasa hannu tana goge kwallan dayake shirin zubo mata,cikin sauri matar dake hada kaya a akwatin ta saki kayan hanunta tazagayo tazo ta gabanta tace
"meye haka kuma hadiza!menene kike kuka Maman rufaidah?"
Duk dama hawayen sunki dena zubowa share idanuntan tayi tanadan nishi nishi da alamun kukan ne ke cinta sosai aranta tace "Hajiya jasmine,wallahi narasa yanda zanyi da yaa malam, kullum, kullum dakika sani saiya jamin rashin mutunci daga wurin mutane,zanji da baqin cikin ya aurar da suhane ga wanda bazabinta ba ne ko wayannan mugayen mutanen daya rariko wai zai nuna musu rufaida? yanzu laifinane dan rufaida Tace batason auren wurin makaranta zatayi?duka duka rufaidan nawa take? Itafa ko secondary schl bata kammala ba, Yau koni na hallice ta ai ba zan tursasa ta ta aure namijin daba ta ma san dashi ba ...ni kawai nasan rufaida dagan gan ta gudu tabar Gidan nan tun safe..inba haka ba Munanan dake ai inata kwada lamber wayarta ta baya shiga,natura yan uwanta duk sunje makota da Gidan kawayen ta kiramin ita wai ba'a ganta ba,kuma malam yaki yabar maganan, dan Allah ya zanyi? Narasa yanda zanyi na
chanza ra'ayin malam ko ita kanta rufaidar, narasa wace irin yarinya ce ita da batada haqurin yin biyayya ma iyayenta kamar sauran yan uwanta.
Amma har Ace yau bikin yar uwarta na jini sabida fitina wai ta gudu tabar gidan nan? ni yanzu a ina zanje in ganta,dan Allah ya zanyi da raina?" takarashe maganan cikin dagon murya sosai hawaye na gangarowa daga idanunta gwanin tausayi, da sauri matar ta rungumeta ta daura kanta ajikinta tana shafa bayanta sigar lallashi,tace "haba umma hadiza ya isa, ya isa haka kidena kukan nan dan Allah,ki bari na gwada kiranta kozai shiga, is okay."
Ta fadi hakan tana rarumar wayarta kirar iphone x newest version takai kunnen ta bayan ta dialing number rufaidar
,ringing yake tayi har saida ya kusa yankewa sannan aka daga...
Batama jira jin sautin muryanta taba cikin tsigar fada tace"..ke rufaida?koma daga ina kike toh kiyi maza kitaho gida yanzun nan..
Ko gama sauke wayar a kunnenta batayi ba sukaji motsin mutum ta bayan su atake dukkanin su suka juyo suna kallon ta inda ta fito da matukar mamaki a fuskokin su.
Bayan ta diro ciki A hankali ta juya cikin sanyin jiki ta karashe rufe windows din dakin sann ta juyo tana kallonsu ganin yadda suka tattaso tsaye suma suna kallonta
Karasawa gefen gadon tayi jiki babu kwari ta xauna a qasa murya can kasa tace ina yini Ammi jasmine?
Dagowa hjy jasmine tayi tunkan ma ta amsa umma hadiza ta katse ta a tsawace cikin bacin rai.. Tace..."ke Rufaida ashe bakida hankali?..Daga ina kike?nice tun safe daga ina kike?...sauri kiris ta gwada mata mari hajya jasmine ta janye ta baya tana huci..
A hankli jikin rufaida ya shiga rawa tuni koinanta ya dau kyarma tsaban takaicin dake cinta har cikin ranta wasu maquson hawayene suka shiga gangaro mata akan fuskarta wanda daga ganin su kasan bata shirya musu ba,yanayin ta mai cike da jin haushi da kuma tsananin so da tausayin mahaifiyartan.
Itama umman Ji take inama tana da ikon cikama rufaida burinta kamar yadda kowacce uwa take muradin cika ma yarta nata burin,sai dai kash Koda shike ba yau akasaba ba,yayun ta hudu an aurar dasu ahaka da wuya ne in ita ta kufce ma wannan mummunar aqida na mahaifinsu.
Tabbas itakanta da zataso tabaiwa yarta rufaida damar yin rayuwarta mai cike da haske da buri amma tasan hakan ba abu mai yuwa bane har abada auren nan dai shine qaddarar su.
Nan Ta fusato cikin sake maimaita mata tambayar ta"..Nace daga ina kika fito rufaida?ko bazaki bude bakin ki amsa ni bane?mahaifinki cewa yake har abada bazai yafeni ba sabida nice nake koya maki wayannan dabiun
Rufaida...
...cikin sauri Rufaidar ta dago kanta ta kalle mahaifiyartan jin alamar bakin ciki da kukan dake tafe a muryan ta,atake itama nata idanun suka gwaranyo da zafafan hawaye masu matukar karya gabobin jiki.
Rawa sosai jikinta ya shigayi muryan ta a disashe kallo daya zaka mata kasan tana cikin damuwa da tashin hankli,cikin wata tokararrayiyar muryan ta data kasa fita ta furta sunan mahaifiyar tan tace
"Umma dan Allah..
Dan Allah umma kiyi haquri ki yafeni,badan na quntata miki na fita a Gidan nan ba..
Kukan ne ya subuce mata mai tsuma "umma kinsan bana son bacin ranki
Jimin afuwa dana kasa danne zuciyata..umma dan Allah ki fahimce ni..umma dan All..ah..karkice na saba maki,sabida ke kawai na dawo gidan nan yanzu ,amma wallhy bana son auren nan umma..nikam mutuwa zanyi..
Ta karashe cikin sautin kuka mai qarfi da tsuma zuciya duka jikinta sai rawa yakeyi a durqushe agaban su.
Wani irin kukan fitar rai takeyi idanun ta a rufe kyammm bata ma iya budesu.
..shiru ne ya ratsa tsakanin sau dan hanklin su gaba daya a tashe yake na ganin yanayin rufaida, hjiya jasmine ta bi tarasa wazata fara tarba acikin su dukan su hawaye ne masu rauni yake sauka daga idanun su..kukan zuci sosai umma hadiza takeyi dan duk cikin yayan ta sun fi shaquwa da samun fahimtar juna da rufaida
Saidai Wani ciwon tabbas baida maganin daya wuce addua,hakan yasa Ta rufe idanun ta tsam cikin masifa
Tace rufaida ashe Kema mutuncin nawa xaki kwabar?meye na fada maki jiya da safe bance dake kiyi haquri ba rufaida?inkinyi masa biyayya mutuwa zakiyi?wato rufaida kin gwammaci kiga na fadi na mutu agidan nan sannan xaki haqura da shegen taurin kan naki ko...toh inkikayi masa taurin kan auren sai afasa yinshi dake?sanin kanki ne koda birnin sin kika tafi kika dawo sai anmiki auren nan,kidai duba dai tun daga kan babban dadarku murja har ita wacce kikebi suhane da ake shirin kaita yau ba'ayi auren fashe agidan nan ba,kisani, akanki kuma baza a fasa ba..
Wani sabon Kukan rufaida ta barke dashi durqushe a kasa agaban su ganin yaddaa hjya jasmine ta rirriiko mahaifiyartan dake a zuciye takeyi mata fadar looking both confused nd frustrated,"..
Ji take kamar ranta da zuciyarta duka zasu bar jikinta tsaban radadin azaban kuncin asaran burikan ta da tarwatsewar da rayuwarta yake shirin yi a lokaci guda..
Duk dama ta taso cikin ganin yayunta duka sunai ma mahaifinsu biyayya wa auren dolen da yake musu amma ita aranta jitake sam bazata taba iyawa ba...For what sake? Ita da ko secondryn ma bai bari ta kammala ba...?Inama ace yaa malam yadan kyale maganan auren nan har sai tayi ss3 dinta tukuna tunda dai ss2 take aynzu..
Saidai ayadda taga yasa ranshi da dukkan imaninshi akan zancen auren tan nan da wuyane ya fuskance damuwarta har ma ya saurare umman ta bare kuma ita..
Itadai tasan ance wajen karban auren yayarta suhane ya nemar mata miji kuma da alamun bayaso sukufce masa ne shiyasa yakeso ayi aure nan da wuri,dan cewa akayi suna da kudi sosai daga kasar waje ma suka taho..
Kukan fitar rai rufaida takeyi cikin tunanin yadda zatai asarar rayuwarta tun umma hadiza tana mata fada har ta gaji ta biyewa hjya jasmine suka suka dawo rarashin ta amma haka fir taki ta amshi batun auren nan aranta cewa take bazata taba iyawa ba..
Daga bisani da umma taga abun babu sauki kawai tayi waje ta barsu
"tana ficewa Rufaida ta durqusa kasa gaban hjya jasmine da idanunta da sukayi lufu lufu tace Ammi jasmine dan Allah ki kira kawu zaidu ya samin baki Wallahy zanyi duka abunda akace inyi muddin yaa MALAM zai kyaleni nayi karatuna,Ammi kirisss ya rage in kammala secndry
...Ammi bana son a aurar dani..Dan Allah kitaimaka min Ammy..Sosai take kuka ko inanta sanda ya sauya kamani daga na mutum tsabn kaduwa da tashin hanklin datake ciki..
Kasa cewa komi hjy jasmine tayi dan ita kanta tasan waye yaaa malam din
Uwarsa ma data tsuguna ta haifesa bata fiye lanqwasa shi ba bare ita datake a matsayin matar kanin shi?jikinta a sanyaye ta dago idanun ta da s sukayi sanyi a natse take kallon yanayin rufaidar dan sosai tausayin yarinyar ya shigeta,sabida tana burgeta sosai,a kaf cikin yaran yaaa malam itace kawai ta gwada borancewa dan ta karba ma kanta yanci na kokrin cimma burikan rayuwanta masu kyau Amma yayunta kam hannu bibbiyu ma suke biye masa akan lamarin sa na musu auren dolen dayakeyi..
Yatsun Hannunta ta kama sannan ta jawota har saman gadon sun,ajiyeta tayi kusa da ita ta rungumeta ajikinta sosai Babu abunda rufaida takeyi sai hawaye da kuka mai taba zuciya dan har cikin kasan ranta ta tsani abunda ke shirin afkuwa da ita..
Haquri da nasiha
Hjya jasmine ta rika bata amma ina kamar ma tunxirata akeyi,da kyar ta lallabeta ta yi alwala da niyyar haka intayi salla raka'a biyu zuciyarta zaiyi sanyi,shigarta bayi keda wuya saiga sallamar umman ta wacce ta kasa dago idanunta sama ta kalle su bare ta zauna a dakin
Daga gnin yanayin ta kasan dauriya kawai takeyi,cike da karfin hali".Tace
Hjya saiki fito masu daukar suhan din sun yi himma,ina ita RUFAIDAR? Ko itace a bayi?..dan miqewa tsaye hjy tayi tana dada gyara zaman mayafinta tace" "eh rufaida tana cikin bayi"..Ni nace mata tayi alwala tayi dan nafila naga tun dzu kukan kawai takeyi..kada kai kawai umma tayi batace uffan ba sukayi tsayuwar jiran fitowar tan Atare,dan shiru ne ya gifta tsakanin su,dukan su bakin su dauke da magana amma anrasa wanda zai fara cewa dan uwansa komi.
"Koya ake ciki da tsayuwar maganan ranan auren rufaidar oho?hjy jasmine ta shiga raya maganganu aranta itadai tasan tun shekaran jiya hajy mama take mitar cewa yaaa malam yaki jinta akan maganan auren rufaida shikuma dan uwan sa zaidu yace bazai taba saka bakinsa akan maganan ba,hjy tayi tayi akan koda ya barta ta kammala secndry schl nan da watanni amma sam yaki yace ya riga ya bada ita.
Akan wannan magana ta auren rufaida Gaba daya saida kansu ya daure,kowa tausayin ta yakeyi sabida duk sauran yan uwanta ba haka aka musu ba dan kowacce sanda yabarta tayi candy sannan ya aurar da ita,shin komaiyasa ya canza tsarin sa akan rufaidar oho?
Muryan umma ne ya katse ma hjy jasmine nazarinta,kallon kofar bayin take tana cewa
"Rufaida kiyi sauri kifito mana dan Allah,sai kuma tadanyi shiru,can Tace toh mahaifinki ne ya aiko ni in fitto dake aiko sallama kwayi da yar uwankin ko..
...hjy jasmine najinsu bata motsa ba bayan minti uku saiga rufaidar ta fito..sauke kanta kasa tayi ganin
Kallo daya suka bibbita dashi,umma Tace hjya muje ko?..Tace ok bismilla sannan ta ruko hannun rufaidar sukayo waje Umma ta saka kai wajen musu jagora har sasshen yaaa malam Inda yake acike makil da sauran yan uwanta mata da kakan su hjya mama da babbar yar Hajiya jasmine din wato barister fareesa zayd matazu.
Gaba daya hanklin rufaida baiya jikin ta,hasalima batasan awani yanayi take ciki ba,tafiya takeyi a xauce tare da hjy jasmine tamkar anajan rakumi da akala dan batama jin sautin komi face na zuciyarta dayake bugun shirin tarwatsewa dan kanshi
Tun daga bakin kofar dakinsan zaka soma jiyo sautin nasihohi da kalamai na zaman aure dake tashi ataciki,hawaye ne masu tsananin zafisuka kara ciko mata idanun ta jin Muryan yaa malam ayayin dayake bada fatawarsa har suka shigo suka zauna baima kalle su ba.
Yace:
"Aure babbar ni'ima ce wacce take kange mutum daga afkawa sharrin shaidan,aure yakan karawa mace da namiji kima acikin sauran jama a
Allah yakan sanyawa auren da akayi dominsa yardan sa da albarka acikin sa
Irin albarkar da ma'abotansa zasuji dadin rayuwar auren su ba tare da dauwamammen bacin rai ba"
Ni na sauke haqqin hakan akanku,domin In nema maku wannan kima da darajar na nema maku mazaje dakaiina wayanda zasu ji kaina kuma suji kanku.
Yau Ga mahaifiyata nan ita shaida ce duniya wa lahira".na neman wa duka yayana mazaje nagari batare da taimakon kowa ba
,"..toh wallahy, na rantse muku da Allahn daya halicceni, na rantse da kabarin baba na,
Duk wacce tayi asarar auranta duniya da lahira ban yafe mata ba.
Ke murja ke ruqayyya,atake first nd send born dinsa suka kalle sa jikinsu a matukar sanyaye
,Wani irin bushe fuskan sa yyi yace naji wasu kananan magangun banza da wofi na tasowa daga wajenku,wai bakwa jin dadin zama da majazenku ko?,toh wallhy inkuka biye ma uwayen ku suka zuga ku aka sake ku kuka fito daga gidan aurenku toh fa saidai ku koma zama akarkashin su can su ciyardaku su shayardaku
Dan Daga ranar da aka sake ku kusa aranku..."babuni babu ku"..Ni kuma ban tsine muku ba, amma kusani har abada na Haramce ku da taka kafafunku a kofar gidana.
Sabida haka duk wacce ta kashe aurenta sai ta san Inda dare ya mata amma ba a gidana ba.
Ya juyo a fusace ya kalle jadwa suhan da rufaida..
Yace Fatan maganata ya shiga kunnen kowacce acikin ku?
Atare Suka amsa shi da eh suna masu gyada kansu cikin gaggawa.
Yace Allah ne kawai zai sanya albarka acikin rayuwarku idan yaga manufarku na zaman aure saima ya sanya muku zuria dayyaba,yana kaiwa nan yace toh
"Ai saiku tashi ku kai ita suhan din yanzun..
Ba musu adda murja da adda rukayya da adda Jadwa suka miqe cikin shirinsu"
..anan kuma Hjya mama ta miqe da kyar cikin sauri tayi fafur a hanya Tace sam bazasu wuce ba...A rikice Tace kai bukar,da sauri ya shareta yyy gaba kamar ma baiji ta ba amma bata fasa ba,Nace ka dakata min,sai yaja dai ya tsaya can gefe batare dayama juyo danya kalle tan ba, "kamar ya Zakace akaita gidan miji Mu bamuyi namu maganan ba?kai waye da zaka wanice akaita?akan mubamu da abunda zamuce ma yarinyar kenan?Wani irin daure fuskar sa yy tamau,da kamar ma bazai amsaba saiya juyo ya haura mata da wa'azi, yana cewa ba a jinkirta aure da mutuwa dan haka kawai akai suhane gidan mijinta duk wanda zai mata nasiha saiya bita can yayi mata,Hajiy ta Inda take shiga bata nan take fita ba amma ko ajikinsa..baima san anayi ba..InTa fada shima saiya fada,dama can dabiar sa ne girman kai,yafiso in yayi nasiha kar wanima yace zaiyi,har yaushe akayi ilimin addini da za a nuna masa? Shi ko kunyar idon yayan cikinsa sa bayaji bare sauran nunawa yake kamar basu da haqqin yin magana bayan nashi,yanaji hjya tasa mai ihu tana cewa baiya saka adalci a al'amarun sa saidai shi ganin rakin ta yake a matsayin shirme irin na tsoffi da tsatsube tsatsube irin na mata,gaba daya saida suka tada hanklin kowa a dakin,ga mutane awaje makil ana jiran fitowar amarya
Miqewar da rufaida tayi zata fice ne ya jawo hanklinsa kanta,da alaman shirin fita take yi dake surutun sun ya soma haura mata kai Wani irin ciwo kantan ya soma mata bazata,cikin sanyin jiki ta miqe ta jikin ummanta kamar wanda zata rabe ta gefenta ta wuce,Wani wuff yaa malam yaa cakumo ta kamar zai figeta
,"shin ina zakije?idanun ta atake suka firfito a mugun tsorace ta dago kanta sama zata amsashi baima jira tace cass ba sai tssssss taji ya watsa mata Wani makohon mari akan fiskarta sanda ta sabule daga hannunn shi ta kife kasa a gigice
"...duka wayanda suka taso zasuzo kanta a tsawace yay kara cikin dakatar dasu,,Cikin tsawa da fada yace "Shasha sha kawai..Allah wadar naka ya lalace.
Ke wai Harni ne zaki nemi ki kunyartar?babu yarinyar danace zan mata aure ta gudu tun safe ba aganta ba waidon bata son aure,To kiji da kyau na riga dana Amshi sadakin Alaji BATURE akanki GOBE asabar da karfe 9 na safe daurin AUREN Ku
.
Hannu ya turmusa acikin aljihun sa ya fiddo wasu makudan kudi ya watso su kam fuskarta yabi ya kwashe ya maidasu aljihunsa A lokacin mutuwa ne kawai yaki zuwa na rufaida amma takai kololowa wajen zaucewa da baqin ciki
"Inkin ga dama saiki kashe kanki kafin goben..Auren ki kamar anyi angama,koda mutuwa kkyi
Bi'izinillah sai an daura auren nan da gawarki,domin in nuna miki cewa nine mai nasara akanki,nine gaba dake,sabida nine ubanki bake kika haifeni ba..ni ne nan mai iko da rayuwarki.
Har ke kin isa ince zanmiki aure ki bijire min?toh ga sakamakon silar taurin kainki nafasa jiran zagowar sati gobe gobe zaki barmin gidana
Makarnatar na hana,Na kuma haramta duk wata hidiman biki domin ki,daga an daura aurenki gobe zaki bi mijinki duk wanda ya daga kafarsa wai zai kaiki gidan miji Allah ya isa..Allah ya rufamin asiri babu wata yar iskan yarinyar da zata tona min
.....Wani irin birgima akasa rufaida takeyi tana kuka sanda tayi fayau tana rokon sa gafara amma ina baiya najin ta dan dabiar sa ne ya hawra can sama yana bunkasa musamman idan ana bashi haquri
Anan ya hada harda sauran borin fushinsa ya borance ya kore masu fidda amarya waje yana cewa rufaida tayi ma yan uwantan duka kallon karshe dan daga yau bazata kara ganinsu ba.
Kuka kawai rufaida take yi kanta akan kafar kakarsu da ke matse kwalla itama tana ta kwararo bambami duka abanza Umma kuwa tunda ta kife kanta akasa tana hawaye bata kara dagowa ba danji take kamar kirjinta zai fashe yy aman wuta tsaban radadi.
,"hjy jasmine da yarta faressa su suka jagorance murja ruqayya da jadwa sukayi waje da amarya suhan a cikin yaran kaf babu wanda xuciyarta baiya cike da jimamin tuna mumumunan kalaman mahaifin su akansu saukin abun daya dake su sun masa biyayya
Hasalima duka ganin laifin rufaidar sukeyi datazo da wannan sabon salo na neman wa kanta yancin yin karatu wanda aganin su hakan bata makai lokacine da neman karawa wakai takaici,dan tun bayauba kowa yasan halin mahaifinsu Yaaa malam, da rikakken ra'ayinsa na babu mai saka shi bare kuma mai kuma hanashi.
Surayyahms contact 08060712446
Part 1 IS FREE,TUKUICI NE GAREKU MASOYA NA U CAN READ IT HAR ZUWA INDA ZAMU TSAYA,SAIDAI CIGABAN SHI NA KUDI NE,PLS SHOW SOME LOVE AND SUBCRIBE the ACCESS FEE IS 300 NAIRA ONLY
VIA 0152983148
MOH'D SULE SURAYYA GTB.
OR katin MTN vtu tran via 08060712446
Screenshot ur evidence to SURAYYAHMS 08060712446
OR MAMAN MUBENA
08036651119.
11/18/21, 5:34 PM - Buhainat: *™✓SHADE OF RUFAIDAH*
_BY_
_SURAYYAHMS_
_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_
BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.
Part1:chapter 3
*Too fast,too soon*
Yamma ya rufa sosai dan haka yan kai amarya suna fitowa aka dau himmar kaita gidan mijinta dake can ta bayan babban airport din gari ,Alaji omar okene babban dan kasuwa ne kuma yana da kudi sosai dan haka shi aka bawa suhan din a matsayin mijin aure,saidai shi asalin sa inyamuri ne ta uwa ta uba,cikaken haihuwar Abia state ne girman cikin garin kano,shiyasa ma a Fuska da dabiar sa bazakayi saurin cewa shi inyamuri bane dake acikin hausawar ya taso tun yanada shekara hudu na haihuwa,.
Toh Wayanda suka san asalinsa since neman kudi ne ya fara tarkatosu shida iyayen sa sukazo garin kano suka yada zango a bayan gari,ande san inyamuri da shegen son neman kudi dan haka sunyi sana'oi kala kala suyi wannan suyi wannn saidai da lokaci ya dan karaja Alaji omar ya girma iyayen sa suka rasu, sana'ar da ya dawo yi was unknown ba a Kara gane masa ba.
Kaf makwabta da abokan harka babu wanda ya isa yace yasan takamammen sana'ar alaji omar okene except for d little little business investment wanda basufi cikin cokali ba,gashi a kullum sai habbaka yakeyi,arzikin gobe saiya ci uban na yau haka na jibi he is just flourishing day by day babu kakkautawa,tunda yaje kasar waje ya dawo ya yaxo ya siya wata mahaukaciyar gidan bene mai hawa takwas mutane suka fara saka mai kahon zuka,this man became centr of attraction dan kowa so yake yasan kalar sana'ar da yakeyi wanda ba a gani saidai agansa da miliyoyin kudi yana facaka yadda ransa yake so,hakan yasa ya rinka shiga kwama cala kala kala da yan anguwan su, wasu akan gaskiyar su ne,wasu kuma akan hassada ne da mugun nufi irin na dan adam musamman in yaga dan uwansa yasamu arzikin daya zarce nashi a bugu daya
But none of them eva defeated him,Allah bai taba bada kowa sa'a akan Alaji okene ba dan sau tari akanyi surkulle har kotu an jejje da shi anma ba aci galaba akansa ba.
Duk wani Zato da mummunan baqi babu wanda ba ayi akan dukiyar san Nan ba, wasu sunce blood money ne dama can matsafi ne wasu kuma sunce mugun barawo ne.
Ahaka Anshafi akalla shekaru shida ana kana nan magana ana ta wannan rigungimu daga baya har aka gaji aka kyalesa da dukiyar sa yana kuma yadda yakeso bai fasa ba..
A tsarin sa a duk macen daya gani ta masa kyau to saiya aureta,sannan baya auren mummunan mace,shi asalin zangwadaddiya mai diri da kyaun fuska yake tayawa,shiyasa yakan murqushe naira wa yan mata,ya kuma narka kudade da kayan alatu ma iyayenta har sai ya cimma burinsa na aurota.
Duk dama bawani sabuwar zance bane yawancin
Matan dayake aura basu wuce watanni biyu uku agidan sa suke ficewa,but hakan baiya hana zalamammun yan mata,zaurawa da kwadayayun iyayen su bashi hadin kai wajen kara Wani auren shi kansa ayau bazai iya tantance matan daya aura ya sake ba..
Bayan matsalar sa nacewa ba'asan silar arzikin sa,problem din zaman gidansa shine duk wacce aka kawota a matsayin mata toh tabbas sai ya dawo da ita walkantaciyar baiwa.
Amma ahakan mutane basu taba yadda da wannan maganan sabida ko anyi auren baya dena kashewa
Iyayen matansa kudi da musu alheri,da siyan niqi niqin kayan duniya da kuma mugun girmama su
Out of 100 baifi 2% ne kawai zasu yadda cewa cikin gidansa shi mugun gaske bane sai a wanda ya gani da idonsa dan bakaramin azaba da baqar kunci yake cusa ma matan sa ba
Cikin haka ne Har Allah ya hadashi da suhan yar gidan malam bukar wanda aka fisani da yaa malam,wanda bugu daya ya same shiga wajensa dake dama tsohon dabiar Yaa malam din ne aurar da yayansa domin samun kudi da abun duniya.
Kwata kwata da haduwar su da shirin auren baifi wata biyu
zunzurutun kudi da abinci Alaji okene ya rinka bawa yaa malam kyautansu har ya cimma burinsa na samun yarsa suhan.
Toh a Wajen karban auren tan ne dayazo da Wani abokin sa mai Suna Alaji BATURE dan America, anan shima yaga rufaida yace lallai abasa shima ya aura,yaa malam kuma daya riga yaga kudi idanunsa sun kife sai bai iya ce musu a'a ba.
Yana sane da cewa alkwari yy ma mahaifiyar sa na cewa zai bar yayansa mata kaf su same koda sec cerficate,amma jin ance Alaji BATURE zai iya kufce musu ya koma kasar waje yasa ya turje y bijire yace sam sai anyi auren rufaida da gaggawa.
Shi Alaji BATURE babu wanda yasan asalinsa sai babban abokinsa Alaji okene,ko yanayin arzikin su ma iri daya ne which of course babu wanda yake gane boyayyen sirrin su..
Shima ance yanada mata biyu kuma dukan su yan nigeria ne sabida shi a United state yake da zama shikam ma babu wanda ya taba sanin gidansa,time to time haka business meeting dinsu yake kawosa wajen Alaji okene
Kudi sosai Alaji bature ya narka wajen kwato yardan Yaa malam cikin gaggawa akan auren sa da rufaid
Yace nan da kwana uku yakeso ya tafi america can gidan sa dan haka zaifi kyau ayi biki ya wuce can da sabuwar matarsa rufaida.
Bangaren gidan ya malam*****
Kafun ace wani abu har waje ya washe tasss yan kodon biki duk kowa ya koma gidansa.
Daga cikin gidan ma babu kowa ata daki,Hajiya Mama da umma hadiza ne suka firfito tsakar gidan agigice da rufaida a hannu a hannu dan babu abunda takeyi sai suma..hjy maman ne akanta tanai mata fifita da mayafin ta,Wani uban shessheka rufaida takeja atake numfashin ta saiya dauke,"rufaida?rufai?"Hadeiza maza jeki ki kawo min ruwa..cikin hanzari umman ta miqe ta wuce kitchen ta dawo da modan ruwa a hannu ta miqa ma hjy mama wanda bata yi wata wata ba tahau yayyafa mata a fuska,tafi minti biyar tana hakan da kyar ta sake dan nishi sann suka san ma tana raye,Gaba daya hanklin su baya jikin su kaf idanun su yy jaaa,sun rasa yadda zasuyi Da lamarin
hjy tayi hawaye harta gaji umma hadiza kam bata iya cewa komi sai yawan sauke ajiyan zuciya datakeyi itama,sosai zuciyarta yake mata ciwo da radadi saidai ayanzu bata ma jin kodan ciwon tan damuwar da yarta yakeciki shiyafi komi daga mata hankli .
Ganin rufaida ahaka yasa take tunanin in har aka rabasu gobe hala itakam tasamu silar mutuwarta kenan
A Yau data fi kowa mugunjin radadin zafin rabuwa da yarta suhane da sauran yayanta, da kuma cewa da mijinta yayi ya yafesu ko an sako su har abada kar su dawo masa gida,inta tuna hakan takanji kamar wuta ne yake ci ata cikin jikinta,ga kuma rufaida wacce tasan tabbas ba sauya ra'ayinsa xaiyi akanta ba
Da kyar suka rinka jinyarta harta samu tayi bacci,dukan su jira sukeyi har wajen misalin 1 saura ma dare amma yaa malam bai dawo ba.
Babu yadda umma ta iya haka ta danne nata damuwar ta rinka lallaba hjy mama dan ta samu ta runtsa,da kyar ta cimma hakan dan cewa take baza a daura auren nan ba
zata kira danta zaidu sassafe zaizo ya tsaya mata tunda shi bukar din bai dauketa abakin komi ba..
*****
MAFARI.....
(Tushen su)
Asalin sunan mahaifin rufaida wato yaa malam shine Abubakar Ahmad salahudeen.
ya taso ya kuma girma ne a can wata kauye dake ake kira bazarkowa,a can jahar maiduguri yankin daya hadasu sosai da ynkunan kasar chadi.
mahaifiyarsa hajiya mama wacce asalin sunanta ne Hasiya Abdullahi,ita asalin shuwa arab ce ta uwa ta uba shiyasa a bugu daya kaganta zaka iya ce mata barabiya dan duk Wani siffar su na kyan jiki da kyan tsari tana dashi gashin kanta baki wuluk gata da diri da hasken fata da fararen idanu,gidan su gidan malamai ne dan haka anan ma garin maidugurin ta soma aure,auren wuri irin na al'adan mutanen da wanda tun yarinya tana da shekara 12 itama akayi mata,dake hasiya tataso ne a gidan mutunci hakan yasa ta auri wani babban makiyayin malamin zaure wanda asalin shi ba dan nigeria bane dan kasar eritrea ne Sunan sa Ahamadu salahudeen al'adab ana iya cemasa malami.
Wanda akace Daga kasar sa yy hijra yaje egypt ya kuma je ethiopia da qasar mali da sudan ya koyo karatun qur'ani,zallan karatun Allo na asalin fasalin warash ya kwarance,ahaka ya shafe kusan shekaru ashirin yanayi toh bayan ya gama ne yay hijra ta kasar chad har ya dawo kasar nigeria da zama Inda ya sauka a jahar maiduguri Amma bai shigo asalin cikin gari ba
Anan ma bai zauna ba ya kafa babban makarntar addini na zallan bada ilimin warash,duka Wani sirri da alhidaya dake dauke acikin ayoyin qur'ani ya nemi ilimin sanin su kuma sosai yake iya amfani dasu
Akan haka Ya shahara ya daukaka yay arxikin rufawa kai asiri,mutane daga kasashen da suka sanshi sosai suke zuwa zauren sa neman taimakon sa akan lamarin daya shafe rayuwar su kona lapyar su kona cigaban arzikin su koma akan maqiyansu.
A farko tsakanin sa da Allah yake aikin sa na taimako da ilimantarwa Inda yake amfani da ayoyin Allah ya warkan ya kuma saukaka,amma daga baya sai girman kai da jiji da kai ya bala'in kama zuciyar shi musamman dayaga yadda dumbin mutane suke yaba qarfin ilminshi da kaifin aikin sa,suke daukaka sa ake jin maganan sa ana mugun girmama Inda yasa kafarsa ya taka,sai ya zamto yay kaurin suna da daraja a lokaci guda.
Ana haka a hankli saiya shiga cusa ma almajiran sa ra'ayi wanda baishafe addini da tarbiya ba,ashe a boye yakanyi aiki irin na sihiri ma yan siyasa da masu arzikin kasar nigeria with time har hakan ya fito filli duniya suka San yana hada lamarinsa da aljanu da tsafi duk dama yaki sam ya amince musu cewa gaskiya ne yana hada al amuransa da sihiri
A duk halina duniya babu wanda ya isa yaja da malam Ahamadu a girman kai da son musunta abunda baizo daidai danashi ra'ayin ba.
hakan yasa wasu tsirarrun malamai a maidugurin suka fara kalubalantar sa akan yaji tsoron Allah,inyaji waa'zin saiyayi musu yace kuma hassada ake mishi akan ilimin da Allah ya riga ya bashi..
Gashi Allah ya dora masa girman kan da koyayi bata kuma yasan ya batan bazai taba amincewa ba muddin ace Wani ne yamasa gyaran,a rayuwan sa da lamarin xuciyar sa ya riga ya tsara cewa shi yayi ilimin da ya zarce Wani dan adam galibi yay masa gyara ko shi ya amshe gyaran domin in yy Hakan ji yake kamar an rage masa Wani abu daga kimarsa.
Haka yake rayuwarsa yanajin cewa Shi sarkin ilimi ne da kima da daraja,hakan ya jawo wasu almajiran sa suka bijirre masa saidai mafi yawansun sunan tare dashi.
Sosai yake adawa da sauran malaman addini da suke gaya masa gaskiya,saiya juya abun yace ai sudin kafurai ne, turawa ne duk suka batasu,daga haka ya fara cusa ma mabiyansa ra'ayin kin neman ilimin kimiyyya da fasaha,ya kuma ce musu wannan ilimin shi zai batar dasu zai rabasu da Allah .
Shekaran sa uku da auren hasiya(hjy mamah) suka haihu suka haifi dansu mai suna Abbakar
Wanda akafi sani da
yaa malam..
Yaah malam shine babban dansu kwalli daya wanda ya gado ubansa sosai tako ta ina da kamanni da komi,asalin akan harkan gardancin mahaifinsa ya rainesa,ya girma ya zamto cikakke kuma rikakken gardi wanda baisan komi game da duniya ba sai karatun qur'ani da aka rainosa dashi.
yaa malam yana da shekara biyar babansan yazo ya rasu,bayan nan da kyar ma mahaifiyar sa hasiyar (hjiy mama) ta rabasa da kauyen da suke sukazo cikin gari ahakan ma wata da watanni yyi yana fushi da dacin rai da ita, baya cin abincinta waidan ta rabasa da gidan gadon ubansa ta kawosa cikin gari cikin arna.
Duk da hakan Rayuwar gardancin sa yakeyi abunsa,duk Wani abu dazai hadasa da neman ilimi irinna bature to ya tsaneshi,Wani bin har aga kamar yafi karfin mahaifiyar san ne.
Saidai kuma hjy Hasiyar asalin ta mai raki ce duk tsiyarsa haka yake dawowa dan dolensa ya mata biyayya dan sosai yake kaunarta aransa.
A xamanta dashi Babu yadda batayi dashi yay koda primary school ba amma haka yaki sam,inma ta damesa saiya fara mata barazanar cewa zai barta zaije kawai ya shiga uwa duniya yay rayuwar sa yadda yake so,itakuwa intaji ya furta hakan saita hqra kawai ta kyaleshi shiyasa ma tun yana yaron ya barke da gararin gari yana sana'an rimi da koyarwa har yayita kokri dan ya tara almajiran sa..
When he reached 7 kafin nan hjy mama tayi Wani auren ta auri Wani babban mutum dan asalin garin katsinan dikko mai kudin gaske anace dashi Alhji dikko matazu.
Shi Matarsa ce ta rasu saiya auri hajya mamah,toh Tunda ya auretan suka bar maiduguri suka koma zama a babban gidan sa dake garin kano.
shima babu yadda baiyi da yaa malam akan yaje makaranta yy karatu ba amma haka yakimusu fir, karshen ta ma guje musu yayi agidan ya nemi gidan haya ata bayan gari yana rayuwar gardancin sa,akan haka saida yasha wahala matuka kafun ya saba da mutanen anguwa,sabida shi yarone amma jahili ne mai tsananin girman kai da nuna isa,hjy mama itake ci dashi ta shayar dashi but shi jahilin mutum daga anmasa gyara ko fada sai yace an masa gori..
Wani bin ya gwammaci ya kwana da baqar yunwa da amasa gyara,saiya zamto Zaman haquri kawai kowa yakeyi da yaa malam musamman ma mijin mahaifiyarsan wato alhaj dikko matazu wanda bakasafai ma yake girmama shi ba.
Ana haka ko shekara basuyi da dawowarsu kano ba Hjiy hasiya ta haifi kaninshi aka samasa Suna Zaid dikko matazu,an haife zaid da shekara bakwai a duniya shima mahaifin nasa alhj dikko ya rasu,cikin ikon Allah haka zayd din ya girma yayi ilimi ya kuma gaji dukiya mai tarin yawa irin na ubansa,sai ya dawo shahararren babban hamshakin dan kasuwa a garin kano,kuma yyi karatu sosai ya zamto babban lawya a fannin shariar musulunci kaf garin ana kiransa da suna YAA SHEIKH sabida tsabar kwarencewar sa wajen iya aiki da ilimin da Allah ya basa.
"Toh kasancewar su yan uba da yaa Malam sai basu cika wani shiri sosai ba,dake tun yana dan karami a kullum yaa malam yazo gidan yagansa da uniform din boko yakance masa .. "kai tafican ARNE kawai"..shikuwa kalman matukar haushi yake basa,Shekara goma ne a tsakanin su amma hakan bai hana su kaurewa wajen cece kuce musamman inya furta ma zayd din hakan ba.
sai dai duk batawar da zasuyi a tsakanin su bada dadewa zakaga sun shirya domin kuwa akwai wannan soyayyar jinin dake cikin xuciyar su wanda hjy mamar ce take dada karfafawa Duk dama Sun kasance mutane biyu ne masu mabanbatan ra'ayi game da rayuwa.
As time goes on zayd sai yayi qarfin ilimi da arxiki shikuma yaa malam ya tara almajirai yana koyar dasu
Da haka ya sanu yasamu mabiya dayawa har yyi gidan kansa ata bayan gari.
Tun yana da shekara sha bakwai yayi aure matar sa na farko mai suna Tani bata iya jure halayen sa ba tafice dan ko haihuwa batayi agidan sa ba
Bai daddara ba ya auro wata bazaura mai suna Shafa'atu itace ta haifa masa yarsa ta farko wato murja..
Itakam baqar azaban yunwa ne ya fiddata.
Sai ya auro wata dillaliya anace mata gambo,itama tazo ta haifar masa ya mace mai suna ruqayya da bori da hauka itama ta fice a gidansa
Can sannan ya auro hadeiza wacce tsabar haqurin iya zama dashi datakeyi yasa mutane suke ganin kamar ma itace ya auro a farko
Hadieza marainiyar Allah ce ba uwa ba uba tsohuwar data raineta ne ta bada ita aure wa yaa malam sakamakon maganin daya mata na ciwon zuciya wanda bata da kudin biyanshi saita biyashi da auren yar rikonta kwalli daya hadieza..
Hakan yasa bai taba daraja Matarsa hadiza ba,gani yake
Kamar sadaqa aka bashi ita,shiyasa tunda ta auresa bata tabajin dadin rayuwarta a hannun sa ba,wulkancin yau daban na gobe da daban harta haifa masa yaya uku,wato Jadwa,suhan da yar autarsu rufaida.
A fadi tashi da kame kame suke tafiyar da rayuwar su,tsakanin ta da Allah ta rike yayan kishiyoyin ta Duk dama basu taba gode mata ba.
Yaa malam haka yaki sam yabar dan uwansan yaa sheik ya taimake sa koda da sana'a ne sabida wannan tsinannen girman kan jahilcin jin cewa fa shine ma agabansa a shekaru.
A Kullum cikin ikirari yake na cewa zai iya rayuwar sa kuma baya bukatr taimakon kowa bare azo anamasa gori.
Har suka girma sosai suka manyanta hankli ya dan daidaita kansu ba kamar da can ba
Ayanzu dai kowa nayin rayuwar sa ne ayadda halayen sa suke bi dashi.
Tsananin Girman kai yasa Yaa malam yyi ta wahalar gina rayuwar sa acikin baqar talauci.
shiyasa da yayansa mata suka girma sai kawai ya fara aurar dasu ga masu kudi yana caskar kudin abunshi,dama can Shida iyalansan suna zama ne a kaskantacen anguwa dan shi bayason hada kafa da masu ilimin boko ya tsane su har ransa baison muamala dasu,kawai ya bar yayan san suyi karatu ne sabida bin umarnin uwar san duk da hakama dakyar suke wuce secndry schull maza saiya kawo namiji yace ya badasu
Shikuma Yaa sheik sanda ya kammala service dinsa ya auri matar sa hajiya jasmine khalid matori,ita yar gidan wani tsohon govenor ne tana da kaninta kwalli daya wanda akece masa IMAD,...tunda mahaifin ta ya rasu yaa sheik yake kyaywar dawainiya da dukan lamuran mahaifiyarta mai suna Hajiya saddika fulani
Hakan yasa suke matukar son junan su, suna gudanar da rayuwarsu ne cikin tsananin girmama juna da baiwa iyayen su haqqin su sosai..
Yadda mijinta zayd yake qirmama mahaifiyarta haka Itama take mugun girmama nashi mahaifiyar...
Shiyasa a Duk yadda hajya mama taso ta raba muhallin ta dasu hakan baiyuba saboda hjya jasmine taki sam haryau su rabu kuma suna zaman su atare cikin lumana da kwanciyar hanklu
Hjy jasmine Bata wani dade da auren zayd ba ta haifar masa yaya har guda biyar,..
Babban yarta mace wanda tayi karatun law a kasar london anace mata barister FAREESAH zayd matazu ko anty reesa,sai babban dansu namiji capt MUFRAD zayd matazu shikuma navy aka turasa a kasar south korea,Inda ya fito da babban matsayin sa na captain ana yawan cemai capt. muffy,..sai mabiyinsa mai suna KEEYAN zayd matazu ana yawan ce masa maska cos he is an enginering student in saudi arabian petroleum engineering stands.
Sai kuma NAZLI zayd matazu
Ita kuma medical student ce tana 2nd year dinta a medical school in india
daga ita sai yar autarsu SHUKRA(khadija zayd matazu) dake karanta fannin international law anan university of nigeria nsukka.
sunada eldest step sis wacce ake cewa Anty Anu,ita kuma asalin sunanta laila zayd matazu,saidai ita ba yar sunna bace,qaddara ya fada wa yaa sheik aka sameta,so her mum is from sokoto state, who uses magic to seduce zayd matazu dan ta cika Wani burinta na rabashi da matarsa jasmine tun farkon auren su amma bataci nasara akansa ba,ta haifi Anu and then she died immidietly batare da auren san akanta ba,,
So a hannun iyayen mahaifiyarr Anu ta girma,Anu kusan sa'ar Anty fareesa ne, dake ma ita ba yar sunna bace so bata cika son zama da su ba hutu kawai take xuwa shima da kkyar in su hajya mama sun tursasa ta
..hakan yasa kusan rabin yan uwanta basa kaunarta thy dont like her much to be around them musamman ma nazli da shukra wayanda sukadau kishi da tsanar duniya suka daura mata..
..tsawon lokaci rayuwar su a hakan yake tafiya yau shiri shiri gobe a araba gari,evn thou iyayen su basu taba nuna bambamci akan yayan su ba .
At times Anu takanzo gidan ne kawai dan hjy jasmine da kuma kakarsu hajya mama amma badon tahada kai da yan uwantan ba
She actually prefer to live her life respectfully gudun kar wata rana a cakka mata baqar magana ko ace mata shegiya..
Anty fareesa kuwa yar ba ruwanta ne last 5years tayi aure daga aikinta sai biyayya wa iyayenta kuma ita kowa nata ne batajin ko daukar gulma,kowa na bata respect cos tana da dattako da halin manya not long ta haifi yaranta biyu wato Iman da,jawad.
shikuma capt muffy shine ake daukar sa kamar magajin baban su zayd matazu,every body loves him sabida halayensa da suka matukar banbanta dana kowa,shi Wani irin murdaden mutum ne,just last year ya daure ya auro wata office girl ana cemata Aina'u Abbakar makarfi,wanda ake cewa Ayn makarfi.
So Keeyan is just a friendly normal guy shidai baya iya fada da kowa Kuma ta Wani fannin Suna masifafiyar kama da yayan sa mufrad
Nazli kuwa yar high standard of living ce tana da mugun ji da kanta duk dama ilimin addini ya shigeta sosai so tana dan sa tunani aharkan rayuwarta badai jijii da kaina jahilci ba,she is high temperd and sumtimes very vulnerable tanada saurin karaya.
"Shukra?she is worst of all she hate evryone nd suspect evryone kullum itake spreading hateful news nd malicess acikin gidan alhaj zayd matazu.....
Rashin samun kyakkwar hadin kai tsakanin yaa malam da kanin sa yaa sheik yasa yayansu ma basa zumunta da juna.
For the fact dat level dinsu ma ya bambamta sai kowa yake jajjan baya da kowa,they are close cousins amma babu bai iya saurin cewa hakan,cos compare to familyn matazu yaran yaaa malam suna rayuwar kaskanci ne da talauci,sannan kowa yasan ba'a basu kwararren ilimin kimiyya ba..
Shiyasa suma yaran nasa suka kama kansu sosai,da wuya zakaga su rufaida da adda murja ko su suhan sunzo bakonta gdan uncle dinsu zaidu matazu.
Dake ko sunzo ziyara ma kallon kauyawa ko marasa ilimi yaransa suke musu Haka yasa Sai suke yawan kama girman su basa son shiga hidamar su ko hira akeyi bakasafai suke tsoma bakin su ba
Dama kuma daga sunzo gidan saidai sugama bulayin su a sashen kakarsu Hajiya mama in sun gama sai su shigo main mansion din suyi ma hjy jasmine sallama sukama gaban su...
Nazli da shukra sunfi kowa tsanar su aransu sabida ko babu komi yayan yaaa malam kaffff Allah ya axurta su da masiffafiyar kyaun jiki da kuma kyaun fuska nagani na fada.
Sukuwa Gudun raini yasa Baifi a kirga zuwan su gidanba ma..they are well acquiented with each other amma zumuncin dake tsakanin su sama sama suke gudanar dashi dan ko kadan bai samu daman yin qarfi ba...
08060712446
Surayyahms
*BUSINESS PROMOTION AND ADVERTS♨️📢*
SHAHARARRIYAR MARUBUCIYAR LITTAFIN NAN KUDI KUMBAR SUSA Da AHUMAGGAH TANA
FARINCIKIN SANAR DA MASOYANTA MUSAMMAN MA YAN KASUWA DA MASU KANANAN BUSINESS DA SUKE BUKATAN BUSINESS PROMOTION KO ADVERTS,A SAMAN LITTAFI KO STATUS IN DA ZA'A TALLATA KUMA BAYYANA SANA'OIN SU GA DUNIYA LUNGU DA SAQO MUTANE SU GANI DOMIN ASANDA SU DA ABUBUWAN DA SUKE SAYARWA CIKIN FARASHI MAI SAUKI,AM GOING TO MAKE IT CHEAP SABIDA MASU KANANAN SANA'OI SUNFI MU BUKATAR SAMUN WANNAN DAMA.
Game bukata sai ya tuntubeta kai tsaye 👉🏿@08060712446
Sa'a tafi sammako yar uwa ur customers might be in our timeline💋👌🏿
Part 1 IS FREE,TUKUICI NE GAREKU MASOYA NA U CAN READ IT HAR ZUWA INDA ZAMU TSAYA,SAIDAI CIGABAN SHI NA KUDI NE,PLS SHOW SOME LOVE AND SUBCRIBE the ACCESS FEE IS 300 NAIRA ONLY
VIA 0152983148
MOH'D SULE SURAYYA GTB.
OR katin MTN vtu tran via 08060712446
Screenshot ur evidence to SURAYYAHMS 08060712446
OR MAMAN MUBENA
08036651119.
11/18/21, 5:36 PM - Buhainat: *™✓SHADE OF RUFAIDAH*
_BY_
_SURAYYAHMS_
_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_
BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.
Part1:chapter 5
*Aina'u makarfi*
_*F1 expresso:emirate street, new extension.kano state,Nigeria.*_
Anguwa ne na manyan mutane wanda shaharar sa bai tsaya ga kyafaffun ginan ginan gidajen zamanin dake nan ba harda kasancewar muhallai na muhimman mutane masu tsantsar daraja,kudi,ilimi,mukami,suna,kai harma da masu mulki da sarauta a kasar.
Anguwa ne wanda aka tsara shi ata can gefe da cikin gari ta Inda kokadan ba a samun yawan cunkuso ko hayaniyar jama'a.
Anyi tsarin anguwar ne street by street kuma kowani street yana da lanes dinsa,so gaba daya anguwar yanada mashiga da mafita guda biyar ne kacal,snn akowani mashigar street akwai manya kuma dogayen dirarrun kofunar karfe wanda zai tabbatr maka da cewa ana rufe kowata gabar shiganta musammn in dare yayi..
A kofar Kowani gaban shiga wata yar tenti ne na jamian tsaro wanda aka musu horo na musanman domin lura da masu shige da fice a anguwar.
Emirate street kusan mafarkin kowani dan adam ne, dan acikin masu kudin ma bakowa yake samun daman zama anan ba,Wa duka anguwar ake cewa "emirate street"saidai lane din ne kawai yake banbanta su Inda zakaga dark golden signal board a manne a jikin kofar kowani mashiga
Gate na farko shine f1 expresso, na biyu f2 expresso...har zuwa f5..sannan acikin ko Wanne gate not less dan 1000 buildings zakagani a jere,a takaice za'ayi iya cewa Duka Duka anguwar emirate street na dauke ne da 5,000 exclusive buildings including malls,restaurant,masjids nd churches hospitals and trade fairs..
Saidai kasuwannin su da asibitan su tamkar masu kawai akayi,dan duka mutanen dake zama awajen are born with silver spoons wanda kullum zakana ganin su cikin swags na high standard of living styles,talaka ko mai karamin karfi bazai taba iya jure expenses din zama anan ba.
A first street wato f1 expresso,Anyi Wani kyafaffen gida wanda yake daura da Gidan Wani shahararren 7starred Army general wanda akai ce masa general murtala kosoko
Wannan gida ya shahara ne sabida tsantsar kyaunsa da yadda aka kawata gaban sa da shuke shuken fulawowi masu ratsa hasken idanu,sai kuma uban tashen kima da mutunci damai gidan yakeyi musamman a idon jama'a....
A jikin babban golden gate din shiga ciki aka manna silver bell plate mai bala'in dauke ido anrubuta 4321 Attor.Zaid D matazu residence.
Yadda tawaje yake a kawace da shuke shuke hakama cikin gidan yake,koina an tsarasa ne cikin tsafta da kwarewat so One single lane ne zai kaika har cikin harabar gidan dake dauke da wata madaidaiciyar parking space da dan karamin cool down na zama ko shakatawa.
So the main mansion stays in d middle,dan sosai ake iya zagaye gidan harta bayansa batare da kakai bangon sa ba,sai ya kasance filin daketa bayan gidan yafi na gaban gidan yawa alaman su mutane ne da basason a gifta musu a bazata bare a shiga cikin harkan personal life dinsu
so Swimming pools dinsu,relaxation outdoor palors da main garage da Duk Wani abu na shakatawa Duk anan abaya suke bata gaba ba..
Cikin gidan kuwa bangare hudu kacal yake dashi
bangaren farko na dauke da sashen iyayen ne sai na biyu na kakar su hjya hasiya,na ukun sashen yaran su ne wanda yake da dakuna masu kyau fadi da yelwa guda takwas dukanin su ajere hudu na kallon hudu,anan nazli da keeyan da shukra suke zama kowada personal room dinsa,sai sauran rooms din da suka rage aka barsu kamar quest room musammn ma in baqon na jini ne ko na kusa da su sosai.