Gabatarwa
Doctor Shazim Part 1 Complete Hausa Novel · about 95 min read
âœ
👨â€âš•ï¸ Doctor Shazim👨â€âš•ï¸
  Â
Daga alƙalamin
KHADIJA ( M ) ABDULWAHAB
KAINAAT... âœÂ
*_KING AND QUEEN WRITING CHAMBER_*
Proud to my first novel
Ina alfahari da kasan cewar wannan littafi na farko agareni 📚Â
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ma É—aukakin sarki mai kowa mai komi da ya bani ikwan rubuta wannan littafi.
Ya ubangiji al'arshe kabani ikwan rubuta abin da zai amfani muslinci da muslmai, ka bani ikwan rubuta abun da zai amfaneni duniya da lahira ðŸ™
âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸
Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na littafin  nan ba ta kowace hanya, ba tare da an nemi izni a wurina ba.
idan kunne ya ji jiki ya tsira!
Wannan labari Æ™agegen ne ,sannan ban rubuta shi ba da niyyar muzanta wani ko cin mutuncin wani ba, duk  wanda ya ga wani abu yayi shige da halayyar shi arashi ne.Â
Season one
Free
Episode 1_2
🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥
_Ø¨ÙØ³Ù’م٠اللَّه٠الرَّØÙ’مَٰن٠الرَّØÙيمÙ_
12 June 2003
_Ƙarfe 12:30 Am
Yanayin sanyin da gari yayi, da iskar da ke kaÉ—awa wanda ya haddasa ganyayyakin bishiyu yin rangaji, tare da ba da wata sassanyar iska.
Yadda sauran ruwan saman da ƙasa bata gama shanyewa ba, da wanda yake gudu acikin kwalbatoci zai tabattar maka da lallai damuna ta kama.
Shiru anguwar take sai kace ba kowa a cikin ta saboda yanayi na dare haɗi da damuna, duk da daman ba'a cika samun mutane na kai kawo a cikin irin waɗannan anguwannin ba ko da kuwa da rana ne, sai hasken bulbs daya haske anguwar haɗe dana street lamps kaɗai ake gani.
Anguwace irin ta masu faɗa aji a cikin ƙasa, domin kuwa daga shahararrun yan kasuwa sai manya a gwamnati ke a cikin ta.
Motace ta shararo da gudu daga kwanar dake hannun dama a cikin anguwar, yayin da wasu ba ƙaƙen motoci guda huɗu ke biye da ita.
Gudu motar take sosai har ta fita daga cikin anguwar ta hau babban titi, still wa É—annan moticin na biye da ita a baya
Daga irin gudun da mamallakin motar ke yi zaka san cewa yana gudu ne tsakanin rayuwa da mutuwa.
ta mirror É—in motar yake hangen fitilar motocin da ke binsa,
yana gudu motocin na bin sa har suka hau kan titin da zai fitar da kai daga garin, gudu suke har suka fita daga garin,
in ban da salati da neman É—auki daga ubangiji babu abun da mai motar nan ke yi.
domun shi a yau ya san tashi taƙare, saboda ya galabaita a dalilin dukan daya sha, tukin neman ga garar sa yake, ƙarfinsa ya kusa ƙarewa, dubawa yayi ta cikin mirror motar amma bai ga alamun waɗannan motocin ba, tunani ya fara to ko ya tsre masu ne, amma duk da haka bai fasa gudun da yake ba, wani mummunan Bugun da yaji an kaima ma motar shi ne yasa shi fahimtar ce wa kenan wata hanyar suka bi amma suna biye da shi mirror ɗin motar ya kalla, amma sai yaga ba waɗan cen motocin ba ne, wata ƙatuwa truck ce ke binsa yanzu saɓanin waɗancen motocin, ba shiri ya karya kwana ya faɗa cikin daji, gudu kawai yake amma ba wai ya san inda yake dosa ba ne, tsintar kansa kawai yayi a bakin wani ƙaton rami mai zurfin gaske, dole tasa shi taka birki ba dan ya shirya ma hakan ba sai dan baya da wani zaɓi, kawai ya sadakat kwanan shi a yau sun ƙare.
bai gama wannan tunanin ba yaji me truck É—in ya kaima motar shi wani mumunan bugu wanda ya haddasa mashi buguwar kai nan take ya suma.
Sake ja da baya me truck É—in yayi ya kaima motar wani bugun wanda yafi na É—azun, nan take motar tayi cikin ramin, ko karar faÉ—awar ta ba'a ji saboda tsananin zurfi irin na ramin .
parking me truck ɗin yayi a bakin ramin tare da leƙa ramin ta hanyar hasken motarshi daya bari a kunne.
wani irin ramine me zurfin gaske, wanda tsananin zurfin shi zai sa ka kasa ganin abunda ke ƙasan ramin.
dariya yayi me sauti da amo tare da cewa yanzu kam nasan zan samu cikwan kuÉ—ina domin wannan sai dai uwar shi ta haifi wani amma ba dai shi ba.
komawa yayi cikin motar shi, anan yasamu wayar shi na ringing ɗaukar wayar yayi
boss shine sunan daya bayyana a jikin screen ɗin wayar, picking call ɗin yayi tare da sa wayar a handspree tun kafin yace wani abu me kiran nashi yace " Ina fatan kagama dashi? "
answer ya bama boss ɗin da cewa " ai wannan tashi ta ƙare sai dai uwar shi ta haifi wani amma ba dai shi ba, dan a yanzu yana can ya gana da magabatan sa"
"amma naji daɗin jin haka" boss  ɗin ya faɗa .
"amma boss ya kake ganin za'ayi da matar shi da yaran shi ?" me truck É—in ya tambaya.
"Kar ka damu da wannan big boss.  zaiji da komai , yanzu dai katuraman da account number ka domin natura maka Sauran kuɗin aikin ka "
"thank you so much boss" me truck É—in ya faÉ—a. boss É—in ya ce
"don mind" Kit ya kashe wayar
account number ya turama boss tare da yima motar key ya bar wajen
WANNAN KENNAN.
🌹~ _Kainaat_ ~ 🌹
Gida ne matsa kaici shi ba ƙarami ba shi kuma ba babba ba chan sosai ɗan dai dai.
gida ne namasu rufin a siri kuma yan boko naji da faÉ—a.
Painting É—in gidan ya kasance white and blue color ne, haka ma get É—in gidan blue and white ne.
daka shiga compound ɗin gidan zaka fara cin karo da ɗakin mai gadi daga hannun hagu Sai parking lot daga hannun dama wanda ke ɗauke da rides masu kyen gaske da tsada na fashion a ƙallah za su kai guda 5 a parking lot ɗin.
Sai garden mai kyen gaske ga suke suke masu É—aukar hankali.
Sai boys quarters dake bayan part É—in masu gidan.
Masha Allah na furta a ya yin da nayi arba da parlorn gidan wanda aka ƙawata shi da furniture's masu kyen gaske da tsada, komai na cikin parlor onion and pitch color ne, daga gefen daman parlor twin up stairs ne me kyau
Sai kitchen dake gefan hagu wanda yake haÉ—e da store kusa da shi kuma dining area ne mai É—auke da chairs guda 7,Sai wani É—an corridor daga gabas É—in parlor mai É—auke da 4 bedrooms, daga chan kuma up stairs É—in ya kasu kashi 3,part É—in matar gidan dake haÉ—e dana yaranta ke hannun hagu Sai na me gidan dake hannun dama sai chan gaba na yaron gidan ne namiji. daga part É—in dake hannun hagu naji anata kwala Kiran Aaimah! Aairah!! Aairah!!!.
Wata kyakyawar mace ce tafito daga ɗaya daga cikin bedroom ɗin ta nufi wanda ke kallon nata ta na cigaba da Kiran
" Aaimah " da "Aairah".
Fara ce sosai tana da jiki ba sosai ba ita ba rammama ba Ita ba mai ƙiba ba a kalla zata kai kimanin shekara 50 . jikin ta sanye yake da sleeping dress riga da wando masu santsi yana yi da Pakistan dress pink color. ba ƙaramin kyau suka yima surar jikinta ba.
"Kun kuwa san ƙarfe nawa" ta faɗa yayin da take tura ƙufar bedroom ɗin ta shiga.
Masha Allah na faÉ—a domin kuwa bedroom ne me kyan gaske, komai na cikin sa ya kasan ce pink and white color ne , yaji kaya masu kyan gaske bawai cike yake da kaya ba.
bed ne sai bed side drawers, sai dressing mirror gefen shi kuwa wardrobe ne wanda clothes set ne ciki sai jikin ƙofar shigowa kuma jere suke da ƙofar bathroom sai wani ɗan corridor inda ya kasan ce laundry basket ne da shoe rag ne sai bag hanger , bags ne masu kyau na gayu dana school kowace bag set biyu ce kuma color ɗaya.
turus ta tsaya ganin ta kwance har yanzu akan bed, " Aairah lafiya kike kuwa da baki tashi ba ina Aaimah take Ita ma, ko yau baku zuwah school ne iye. "
Ƙarar buɗe ƙofar bathroom taji juyawa tayi, wata kyakyawar budurwa ce ke tsaye jikinta ɗaure da towel iya gwiwarta jikin ta sai raɓar ruwa yake, alamar wanka tayi, fara ce Ita ma kamar mahaifiyar ta tana da dogon gashi har ƙugunta, ga matsakai tan idanu masu ɗauke da brown eyeball da zara zaran eyelashes, hancinta ma ɗan dai dai dogon bamai yawa ba sosai, ga small mouth me ɗauke da pink lips, tana da shape mai ɗaukar hankali sannan tana da tsayi amma ba sosai ba chan. masha Allah kawai zamuce, akalla zatai kimanin shekara 18 a duniya.
"Ok kintashi kenan Aaimah ce kenan bata tashiba."
"Wallahi mom tunɗazu nake tashin ta amma taki tashi wai Ita batagaji da bacci ba."
"Tafi ke ki shirya, rabu da Ita yanzu ai zata tashi ba dan halinta ba " mom ta faɗa a lokacin da ta ƙarasa jikin bed ɗin , "Aaimah! Aaimah!! wake up, its time for school , ko kina sone kuyi late ne iye autar mom . "
"Uhm uhm uhm haba mom wai miyasa kike cema Aaimah auta nifa" Aairah tafaɗa yayin da take buga ƙafa tan turo baki haɗe da rike ƙugu.
ai kuwa nan Aaimah ta tashi tana ma Aairah dariya harda gwalo, dama duk abunda mom ke faÉ—a tana ji, tashi ne kawai bata yi ba
"mom kinganta ko dariya take man harda gwalo"Aairah ta faɗa sai wani turo baki take da hura hanci. "Ke da'alla rabu da Ita, ai kema autah ce"
mom ta faɗa tana dariya ganin yarda Aairah kema Aaimah dariya harda tsalle, "oho dai ai ni aka fara cemawa" mom ta katse ta da cewa
" To ya isa haka maza kushirya
ABIE na nan yayi shirin tafiya , kunsan dai yau zai koma wurin aiki abuja."
"to shikenan mom gamu nan zuwa" har suna haÉ—a baki wurin faÉ—in haka.
fita Mom tayi daga bedroom ɗin haɗe da jawo masu ƙofa, ta shi Aaimah ta yi ta nufi bathroom tana faɗin my twin sister dan Allah kifito man da uniform ɗina kafin na fito"Aairah ta ce " to sannu mom kinji koh"
"haba twin sister dan Allah fa nace" Aaimah ta faÉ—a tana lan gwabar da kai , Aairah ta ce " hmmm sai shegen daÉ—in baki kamar ta Allah"
" Pls twinee" Aaimah tasake faÉ—a
"shikenan ba dan halinki ba"Aairah ta faɗa tana ya tsine fuska,murmushi Aaimah tayi tana faɗin "yawwa twenny Ni na san nafi kowa Sa'ar Yar uwa a duniya shiyyasa nake alfahari dake baki sani ba fah irin daɗin da nake ji Idan naganki kusa dani ba" , baki kawai Aairah ta saki tana sauraron ƙar yar da Aaimah ke shirga mata. "wallahi Aaimah kin bani ki rinƙa jin tsoron Allah , ko kunyar ƙarya ba kyaji " gwalo Aaimah tayi hadi da jawo ƙofar bathroom ta shige, dariya kawai Aairah tayi haɗi da girgiza kai tana faɗin " Allah ya shirya ki Aaimah da karya"
wurin dressing mirror ta wuce Vaseline É—in dove ta shafa tare da farar powder kaÉ—an ta shafa a fuskar ta sai kwalli da tasa ma eye's É—in ta, wurin wardrobe É—in su ta wuce buÉ—ewa tayi , kaya ne masu yawan gaske komai set biyune, wurinda hijaban su suke daban haka ma sleeping dress É—insu da ban suma dogayen riguna da atamfofi wurinsu suma da ban haka ma uniform É—in su na school dana Islamiyya,
uniform É—in school ta É—ako masu set biyu itada Aaimah wurin bed É—in su ta koma da kayan a hannun ta domin ta shirya.
shaf shaf ta shirya cikin uniform É—in ta masu É—an karan kyau, riga ce da skirt, rigar white color ce, skirt É—in wanda ya kasance iyakarsa gwiwarta pink color sai sock's fara me ratsin pink daga sama sai top wacce itama ta kasan ce pink color sai Yar baby hijab it kuma white color ce, wurin corridor É—in su ta nufa shoe da school bags É—in su ta É—auko masu, white color ne takalman snikers sai school bag pink color.
"Sis kin É—auko man nima uniform É—in" Aaimah ta faÉ—a wacce fitowar ta kenan daga bathroom. amsa Aairah ta bata da "Eh Amma fa kiyi sauri ki shirya kona tafi wurin Abie na barki" wurin dressing mirror Aaimah ta nufa tana faÉ—in" sorry karki damu yanzu zan shirya ki bani 5 minute insha Allah " shaf shaf itama ta shirya cikin nata uniform É—in Masha Allah
Itama ba ƙaramin kyau tayi ba saboda itama Aaimah kykyawa ce sosai a bun da kawai Aairah zata nuna mata tsayine shima ba wani finta tayi ba sosai ka mannin su ɗaya da Aairah tsayinne dai kawai banbancin su shima sai insun jera zaka fahimci hakan.
Snickers É—in ta itama ta saka tare da amsar bag É—inta dake hannun Aairah
a tare suka fita daga bedroom ɗin direct part ɗin Abie suka nufa, hannun su cikin na juna suka shiga parlor ne mai matuƙar kyau, dan yafi na down stairs kyau da haɗuwa domin ya ƙawatu da expensive furniture's, komai na cikin parlorn sky blue ne da fari.
wani kykyawan matshin tsohone wanda Akallah zaikai ki manin shekara 60 a duniya, yana da haske shima sosai, zaune yake akan 2 siter
" abie " kenan
tea yake sha wanda mom ta haɗa mashi, sallama sukayi tare da ƙarasawa ciki suna faɗin "abie ina Kwana antashi Lafiya "suka faɗa yayin da suke samun wuri kusa da abie suka zauna,
"lafiya lau alhmdllh my daughters ina fatan kuma kuntashi lafiya" "Alhmdllh abie " suka faÉ—a, Abie ya ce
"to Masha Allah haka ake so"
"amma Abie zaka tafi yau shine baza ka yi breakfast damu ba" Aaimah ta faÉ—a tana turo baki
"Sorry my daughters duk da ma laifin kune tunda tun É—azu ya kama ta ace kuntashi amma kuka yita bacci gashi ni kuma sauri nake, ai daya ke bajima wa zanyiba wannan time É—in, zandawo very soon kunji koh."
"shikenan abie Allah ya dawo da kai lafiya"da ameen abie ya amsa tare da kai cup É—in tea bakin sa.
"to uwayen surutu atashi aje ayi breakfast time na kurewa, abar shima abie ya samu ya gama nashi breakfast ɗin karya makara "mom ce ke magana wacce fitowar ta kenan daga bedroom ɗin abie hannun ta riƙe da jakar kayan shi da zaiyi tafiya da Ita
"Uhmmmmm haba mom dan Allah kibari muƙara sa yin ban kwana mana" Aairah ta faɗa tana turo baki, dariya kawai Abie ke masu
"Kinci gidan ku nace kutashi kuyi breakfast yana chan baba larai tashirya maku, nima abarni nayi ban kwana da mijina"
"ah mom sai kice mutashi soyayya ta motsa, to bari muyi ta kanmu," Aairah ta faÉ—a tareda yin dariya
"Kunci gidan ku jairan banza marasa kunya kawai "abie ne ya faɗa tare da yi masu daƙƙu wa
dariya suka kwashe da Ita, " abari muga soyayya tukunnan sai mu tafi" Aaimah ta faɗa hadi da gyara zaman ta, wurin su mom ta nufo ai bashiri suka mike da gudu suka fita daga part ɗin suna dariya.......
"Kaga man jairan yara marasa kunya"mom ta faɗa yayin da take zama kan hannun sofa da abie ke zaune, dariya abie yayi tare da cewa "Allah ya shirya, dan inkika biye ma su Aairah sai su samaki ciwan kai" "wallahi kuwa ai abdallah ne kawai maganin su, yama shigo kuwa" mom ta faɗa.
Aa ina jin baigama shirin zuwa hospital nasan daya gama zai shigo muyi sallama, haka ne kuma mom ta faɗa tare da cewa" yanzu dai ba wannan ba yaushe zaka dawo? "
"2 week's kawai fa zanyi "
"ashe kuwa kashirya zuwa dani abuja kenan Indai 2 week's zakayi ƙafata ƙafarka, murmushi abie yayi haɗi dacewa "to su fa yaran ki kibarma wa su iye"
" dan Allah kabar ma maganr yara Sai kace wasu yan goye saunawa Nake zuwa abujar batare da su ba"
Assalamu Alaikum sukaji an faɗa katse labarin dasuke sukayi haɗi da amsa sallamar, wani matashin saurayi ne kyakyawan gaske wanda ko ba'a faɗa maka waye shi ba kamanin sa da abie zaitabbatar maka da cewa ɗan sane, DR. ABDALLAH MUHAMMAD HASHIM kenan matashi maiji da waye wa ga ilimi both side boko da Islama, farine shi ma sosai yana da tsayi dai dai misali gashi irin mazannan ne masu motsajiki dan yana da kirar jiki mai kyan gaske ga ƙasumba irin ta yan gayu domin kuwa daga ganin ta kasan tana shan gyara, jikin sa sanye yake da uniform ɗin sa na aiki hannun sa riƙe da briefcase ɗin shi, ƙarasawa ciki yayi wuri ya samu ya zauna,yana faɗin " inakwana abie mom ina kwana", lafiya lau alhmdllh suka amsa mashi abie ya ɗaura da cewa "har anyi shirin fita aiki kenan? "
" eh abie dayake ina da shiga thearter  ƙarfe 10:00,"Â
"masha Allah , Allah ya taimaka," "ameen ya rabbi , abie dawuri zaka wuce ne yau? "
"eh dawuri zan wuce saboda gobe tunda safe ina da shiga court â€, amma insha Allah bazan jima ba zan dawo ina ma tuna nin two days zanyi na dawo"
"to shikenan abie Allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya" da ameen suka amsa mom na faɗin
"breakfast É—inka nachan dining, sannan su Aairah na nan kawuce dasu school in baza kayi late ba,Â
"amma mom mi ya hanasu bin school bus yau? "
" uhm kai dai bari, shegiyar shiririta ce irin tasu , kasan halin su yanzu haka idan akace maka suna can basu kammala breakfast ɗin su ba ba'a gardama, narasa gane shiririta irin tasu Aaimah wallahi yara sai kace ba masu jini ba ajiki suyita abu kamar basu sanyi, Allah dai ya shirya su, ameen abdallah ya faɗa tare da cewa "bari naje nayi breakfast ɗin sai na dubasu"
"ok muma ga mu nan sakkowa"tashi yayi ya fice ya nufi dining, tunkafin ya isa yake jin hayaniyar Aaimah da Aairah sunata zagaye dining Aairah ta ɓatama Aaimah baby jiba da tea itakuma Aaimar nacewa saita rama shine fa suke ta zagaye dining baaba larai sai cewa take su bari amma ina kamar ƙara zugasu take.
Tsawa abdallah ya daka masu tare da cewa "ashe ku shasha shune ban sani ba, zaku dawo ku zauna ko sai ranku ya baci sakarkarun banza da wofi, wallahi kushiga hankalin ku kullum girma kuke amma ɗabi'un ku sak na yara. bashiri kowace cikin su ta nemi wurin zama, baaba larai ce ta matso zatayi serving ɗin ya abdallah tana faɗin " abdallah an tashi lafiya"
"lafiya lau baaba, ina kwana," Alhmdllh tace "mizan zuba maka"
"a'a kibarshi kawai baaba Aairah ta zuba man,"
"to shikenan ni bari nawuce kitchen"
Aairah yace ma tayi serving ɗin sa ita kuma Aaimah tayi sauri ta chanzo hijab ɗin ta tunda sungama breakfast ɗin su , to tace haɗi da tashi ta nufi bedroom ɗin su.
Abie ne ke saukowa shi da mom hannun ta riƙe da jakar kayan sa , "abie kafito " ya abdallah ya faɗa ayayin da yake kar ɓar jakar kayan a hannun mom,yana faɗin "abie muje koh" yayin da yake fita daga parlorn , bayansa suka bi har da Aaimah wacce sakowarta kenan daga bedroom ɗin su dataje chanzo hijab,"adawo lafiya, alhaji Allah ya kiyaye hanya yakai ka lafiya ya dawo da kai lafiya" "ameen ya rabbi baaba larai" abie ya bata amsa, fita sukayi compound ɗin gidan wurin motar abie suka wuce wacce baka driver ya daɗe da fito da ita dan har ya abdallah ya saka ma abie kayan shi a booth ɗin motar bankwana suka shigayi su Aairah har da hawaye abie sai lallashin su yake.
abdallah ne yace" dan Allah abie ka kyale yarannan sai sun sa kayi late", "kuyi hakuri bazan jimaba zan dawo may be na dawo nan da 2 days kunji" "to abie Allah yatsare hanya"
ameen abie yace
abdallah ne yace "to kuwuce ciki ku ɗauko school bag ɗin ku na ajiye ku a school, abie Allah ya tsare" ya faɗa  haɗi da tasa keyar su Aaimah zuwa ciki, mom ce ta matso kusa da abie tana cewa "wallahi barrister kamar kar ka tafi nake ji"
" tofah yara shagwaɓa uwa shagwaɓa toni wazan kama" ya faɗa yana dariya "uhmm kaima kasan wanda zaka Kama" ta faɗa tana ɓata rai, "yau naji shiyyasa kenan kika ƙi magana sai da yaran ki suka shige ciki zakiyi man adawo lafiya , ashe shagwaɓa za'ayiman ban sani ba ", mom tace "ok hakama zakace "ta faɗa haɗi da juyawa zata nufi ciki , hannun ta abie ya riƙo yana faɗin "Sorry kubrah, kema kinsan wasa nake , karki damu bazan jima ba zan dawo insha Allah"
"to shikenan Allah ya dawo man da kai lafiya" ameen abie ya faÉ—a yayin da yake shiga cikin mota sit É—in baya ya zauna bala driver na gaba key yayima motar, hanu mom ke É—aga ma abie shima yana É—aga mata,suka nufi gate,buÉ—e masu gate baba mai gadi yayi yana faÉ—in a dawo lafiya " mom na nan tsaye har sai da motar tafita daga gidan sannan ta juya tashiga ciki , dasu Aairah tacikaro suma sun fito a dawo lafiya tayi masu tawuce ciki abdallah ne ya sauko daga upstairs part din sa Â
Yana ce masu ku wuce mu Tafi.
 🌹~KAINAAT~🌹
Fita sukayi wajen mota suka shiga abdallah ya jasu gate suka nufa wanda tun fitar abie baba megadi yabar masu shi buɗe gaishe dashi suka yi ya amsa yana masu adawo lafiya da ameen abdallah ya amsa yayin da suke fita daga gidan,
abdallah ne yace" dama ana duka school ɗin ku wallahi dasai nasa yau anmaku dukan tsiya. "
"dan Allah ya abdallah kayi hakuri bazamu ƙara ba"
"kundai ci sa'a kawai ba'a duka da kungane kuranku yau da daga yau bazaku sake baccin safe ba, ace wai kuna bacci har school bus tatafi kuga yan hutu koh"
Kayi hakuri dan Allah wallahi baza mu ƙara ba"
, "ni da'allah kuyi man shiru sai bada hakuri sai kace masu tuban gagaskiya bayan nasan ƙarawa zakuyi" ya faɗa yayin da yake hawa kan titin ring road in da nan ne school ɗin su take bakin gate ɗin school ɗin yayi parking tare da cewa "kufito kuwuce ciki, fita sukayi suna yi mashi adawo lafiya Allah yasa yace motar yayi ma key yabar wajen tare da Kama hanyar hospital ɗin da ya
Episode 3_4
 Â
 .
LITTLE ANGELS PRIMARY AND SECONDARY SCHOOL. shine sunan school É—inÂ
Kamar yanda school uniform ɗin suka kasance pink and white color haka paint ɗin school ɗin shima pink and white color ne.
Cikin school ɗin suka shiga Masha Allah school ce mekyan gaske ta yayan masu arziki Upstairs ce makarantar wanda ya kasan ce down na yara up kuma na manya ne, up stairs suka nufa domin an daɗe da gama ASSEMBLY shiyyasa suka nufa class, S. S. 3 shine class ɗin su , shiga sukayi ciki for master ɗin su suka samu yana ma shirin fita domin ya gama abunda ya kaishi.
"Aairah And Aaimah  Muhammad hashim , why are you coming late" for mastern ya faɗa, Sorry sir we have wake up too late that the reason why we came to school late and it will never Happen again Aaimah ta faɗa yayin da Aairah ke ta bata fuska irin tafi ƙarfin ta bashi amma sa.
this should be the last, get sitet for mastern ya faɗa hadi da fita daga class ɗin .
Kallan juna sukayi haɗi da kwashewa da dariya, Aairah tace Why are you coming late tana kwai kwa yona maganar for master ɗin , dariya suka sake kwashe wa da Ita,
Aaimah tace this should be the last. wannan karan duka yan class ɗin ke dariya.
Sit ɗin su suka zauna suna cigaba da dariya,
Allah ya shirya ku twins domin yanzu abun naku sai adu'a mu samma make Aairah da uncle Hamza na magana sai wani harar sa kike," bazaki gane bane "Aeesha" Aairah ta faɗa wacce akakira da Aeesha tace to ganar dani.
"Ke wallahi haushi uncle hamza ke bani dafa Ina masa kallon mutumin arziki ashe dan banza ne, baki ji munce ya dai na zuwa gida yi mana lesson ba, Ai korar sa ya abdallah yay, saboda abun da ke kai shi bashi yake yiba, Ko kunya baijiba yace wai yana son Aaimah sai kuma yana lesson kiga yana kokarin taɓa ma mutun hannun ai kuwa rannan ashe duk abun da yake faɗa a kunnan ya abdallah, shine fa ya kore shi yace karya Kara ganin sa, to Wallahi inta kaice maki komu dukan da mukasha wurin ya abdallah sai kin tausaya mana dan Wallahi buguwa mukayi kamar gangar church kuma mom tace ba ruwan ta gashi abie baya gari, shiyyasa innagan shi Nake jin kamar na shaƙe sa"Aairah ta faɗa  tana hura hanci, Allah ya shirya sa to Aeesha ta faɗa , Ameen dai.
be silent biology teachern su ne yace haka wanda shigowar sa kenan yasame su sunata surutu, natsuwa suka yi suna sauraron lesson ɗin dayake masu.
_F. M. CÂ MEDICAL CENTER_
zaune a office É—in shi da ke Amenity, waya ce a kunnan sa da alama waya yake.
"haba dude ai dole nace haka tsawan shekarar mu nawa muna tare ace baka taba ziyarta taba su mom ma a suna ka ɗai suka sanka sai waya, ai tare bata ce haka ba amma nasan maganin ka zan haɗa ka kawai da ammy ne nasan ita zata saka kazo ba dan kashirya ba konasa mom takiraka may be kazo ya abdallah ne ya faɗi haka,, On the other hand nacikin wayar yace,, sorry my man ba haka bane nima ina san zuwa to ayyuka ne suka min yawa shiyyasa amma insha Allah ina nan zuwa very soon,, ai nima ina da tarin ayyuka amma Nake ajiye su na ziyarceka,, inkuma Sai zanyi aure zaka zo inji to, duk da in zanyi sai tare da kai don ina samun mata zan haɗa ka da ammy kaima ka fito da taka ko aba da kai sadaka" abdallah ya faɗa yana dariya.
"haba kaima kasan wa za'a ba da sadaka Indai aure zakayi bisimillah ban hanaka ba amma ni ba yanzu ba.
"shikenan tun da kai bazaka chanza ba kullum ace mutum amsar sa ɗaya, ina gaishe da su ammy "ya abdallah ya faɗa .
"zasuji insha Allah nima ka gaishe man dasu mom kace mata ina nan zuwa very soon "
"Allah yasa domin kuwa na san halinka,"
Karka damu dude zan zo insha Allah, to shikenan sai anjima , abdallah ya faɗa , ok nagode sai anjima kashe wayar yayi shiri yayi haɗi da fita daga office ɗin dakin tiyatar yanu fa.
 10:00 am
LAGOS.
_EKO HOSPITAL._
Patient ne zazaune wanda da alama sun zo ganin likita ne.
wata Nurse ce tafito daga Office aƙalla zatayi kimanin shekara 25 jikin ta sanye da fararen kaya riga da wando hulace kawai akan ta saɓanin wasu nurses ɗin da ke sanye da baby hijab, baka ce amma ba baki sosai ba wurin patient din tanufo, hadi dacewa DR. Is on the way, yayin da take amsar Katin patient ɗin wani dattijo ne zaune bai bada card ɗin shi ba da alama ma baiji mi nurse ɗin tace ba,"hey bring your card"
nurse ɗin ta faɗa ganin bai ba da nashi Katin ba," ƴata ni bana da Kati yau nafara zuwa".dattijon ya faɗa dakyar alamar ba karamin kamu ciwan yayi masa ba ,cikin harshen hausa tafara mgn duk da batayi Kama da hausawa ba kuma bawani iya hausar tayiba sosai " to ya kake so ayi Katin ka keso nabaka ne komi"
"a'a naji ance ana bada magani kyauta shiyyasa nazo" dattijon yafada, wani kallon rainin wayau take ma dattijon har ya gama magana, cikin karaji tace "hey hausa people nabani mamaki, to bari kiji nan ba charity hospital bane dan hk kitashi kiba mutane wurin, in ban da abunki ta ina wannan hospital ɗin tayi Kama da charity hospital koh ance maki irin hospital ɗiin kune na arewa" nurse din ta faɗa hadi da nuna masa hanyar fita. " haba Victoria kin man ta me doctor yace duk time ɗin da marasa ƙarfi suka zo ne " wata kyakyawar nurse ke faɗin haka chocolate color ce a ƙalla zatayi kima nin shekara 23 itama sanye take da fararen kaya rigada wando sai farar baby hijab, zuwan ta ke nan tasamu victoria nayima dattijo masifa Ita bahaushiya ce sabanin victoria, "ina ruwana ai yan zu ba ya nan sai dai inkece zaki faɗa masa
Kasa tashi dattijon yayi jikinsa sai rawa yake, tsawa ta dakama dattijo, haɗi dacewa "I said get out from this hospppppp, kasa karasawa tayi adalilin saukar wani mahaukacin mari dataji a kuncinta batai aune ba tasake jin wani marin a dayan kunchinta bashiri ta kife ƙasa, gaba ɗaya hankalin patient dana nurses ya dawo kan wanda yayi marin.
Tsaye yake jikinsa sanye da blue uniform ɗin sa na aiki, kafarsa na sanye da black din takalmi sai hannunsa dake riƙe da briefcase da lab coat ɗin  sa, dogone yana da tsayi, farine sosai kyakyawan gaske ya nada dogon hanci sai eyes masu black ɗin eyeball, small mouth me ɗauke da red lips, sumar kan sa wacce tasha gyara koma take kan shan gyara black color ta sauko saman neak ɗin shi ya sha rawani irin na larabawa, dama da ka ganshi kai tsaye zaka ce balarabe ne kukuma half cast  , akallah zai yi kima nin shekara 29 zuwa 30.
Good morning sir, nurses É—in suka shiga gaishe da shi hannu kawai yake É—aga masu yayin yake kiran security
ƙara sowa security ɗin sukayi suna gaishe da shi cikin girmamawa, amsa masu yayi yana nuna masu dattijon haɗi da cewa kushigar min dashi office yayin da yake ba daya daga cikin securityn key din office ɗin shi, kamashi sukayi suka ɗaurashi akan keken daukar marasa lpy wannan nurse ɗince wacce tayima victoria mgn ta matso kusa da shi hannu ta mika zata anshi briefcase ɗin dake hannun shi dakatar da Ita yayi, magana ya fara cikin harshen turanci nurse "hidaya me nace ne gameda masu zuwa neman tai mako? "
" kace duk wanda yazo neman tai mako ah EKO aturashi ABNOOR, kuma itama nurse Victoria tasani kuma sai da nasake faɗa mata da tana ma datijjon faɗa"
"shikenan koma dai miye Wannan yazama nakarshe ina ba haka ba dukkan ku sai ranku ya ɓaci "ya fada haɗi da nufar office ɗin shi
  🌹~ KAINAAT ~ 🌹
Tasowa victoria tayi daga duÆ™ewar datayi domin ta maru, haryanzu bata dawo dai dai ba, masifa tafara yima nurse Hidaya akan Ita ta haÉ—a ta da dr haryayi mata wannan marin, "to bari kiji Victoria garama tun wuri kifita daga harkata basai da na gar gaÉ—e kiba amma mikika ce ke kina ganin dr shazim bazai iya yimaki komai ba ke yar gaban goshi, kedai kawai za fin mari ne yasa zaki sauke a kaina mizai hana shi dr bazaki bishi office kiyi mashi masifar ba "hidaya ta faÉ—a  tana dariya sauran nurses É—in ma dariya suke saboda sun san magana ce hidaya ta faÉ—a ma victoria saboda ba Æ™aramin so take ma DR. SHAZIM ba, mutsww victoria taja tsaki saboda haushin dariyar dasuke mata ta kuma gane miyasa su dariya wuce wa tayi office É—in dr saboda itace ke tura mashi da patient,Â
Shiga tayi cikin office ɗin haɗi dacewa, good morning sir zaune yake yana rubutu ajikin file wanda da alama na wannan dattijon ne yayin da shikuma dattijon yake kwance bisa gadon marasa lafiya a office ɗin , ko kallon inda take bai yiba sake gaishe da shi tayi, call nurse hidaya for me abun da kawai ya ce mata kenan, hakuri ta shiga bashi dan bazata iya daina aiki dashi ba domin in har chanzata zaiyi da nurse hidaya to sai dai tabar hospital ɗin saboda bazata juri ganin shi tare da wata ba,  tsawa yada kamata domin yaga bata da niyyar fita daga office ɗin yace " get out from my office" haɗi da nuna mata hanya, fita tayi daga office ɗin zuwa office ɗinsu na nurses fashe wa tayi da kuka, tana faɗin bazai yuwu ba wlh dr shazim nawa ne ni ka ɗai babu wacce ta isa ta raɓesa sai ni taƙara fashewa dawani kukan, wata nurse ce tashi go office ɗin wacce itama daga ganin ta ba muslma bace tana cewa , "ai yanzu kika fara kuka victoria,  dama ba sai da na faɗa maki ba kitashi tsaye amma kika kiji to wallahi Idan bakiyi wasa ba kina nan sake dabaki hidaya zata kwace shi, sai dai kizama ƴar kallo"
"haba destiny yaza ki man wannan mumu nan maganar,  kisan kuwa yanda nake son dr shazim kuwa da kinsan yanda nake son shi da baki ce haka ba"
" victoria kenan inaga bakisan halin hausa peoples bane zaki sha mamaki inkika tsaya wasa domin kuwa Ita hidaya yarensu ɗaya bayan nan religion ɗin suma ɗaya kina ganin zai kula ki ne yana ganin hidaya, kawai kitashi tsaye"
"to ya zanyi ki bani shawara pls"wani munafukin murmushi destiny tayi haɗi da cewa yanzu dai kifara kiramashi hidaya tukkun nan zuwa anjima sai muyi magana "
" haba destiny yazakice nakirata sai dai yaji haushi amma ni bazan kira taba wlh" "kaji sakarya in ban da kina sakarci in baki kira mashi ita ba taya zai gane kintuba kuma itama hidayan ki roketa akan ta tayaki bashi hakuri nasan zatayi," "uhmmm shi kenan ta faɗa haɗi da barin office ɗin domin kiran hidayar, dariya destiny ta kwashe da Ita haɗi da cewa "zaki gane baki da hankali Victoria zakisan cewa ni ba kanwar lasa bace yanda kika ki brother samuel to haka zaki rasa shazim shima sakarya kawai" .
wurin su hidaya Victoria tanufa,ta zuwa ta tsaya hannunta riƙe da ƙugu tace" kizo dr . nakira tana faɗa ta juya kai gefe, "wakenan acikin mu?" watace cikin nurses ɗin dake zaune ta faɗa , "tasan kanta ai acewar Victoria , sarai sungane hidaya take nufi sbd sun San tana yar tsama da Ita amma sai suka nuna basu gane ba "hidaya kinsanfa ke nake nufi amma kinyi kamar baki ganeba zanje na faɗa masa bazaki zoba"
" kejiman Victoria da karfin halin, kin faɗi sunan tane daza kice ta ƙizuwa"
"ah to gane mana hanya sister maryam" acewar wata daga cikin nurses ɗin "haba Victoria nina rasa me hidaya ta tare maki a hospital ɗinnan,ai ko bakomi ƴar uwarki ce tawurin aiki, amma ace kullum baki da abokiyar faɗa sai Ita"
karka faÉ—a man mgnr banza mana Joseph ina ruwanka"
 "sorry shawara ce" barin wurin yayi wanda akakira da Joseph
"mike faruwa ne anan cewar destiny wacce isowarta kenan, a'a hidaya Victoria bata faɗa maki dr nakira ba nagan ki zaune ko har kin dawo daga wurin shi
"A'a destiny yanzu zanje, ok destiny ta faɗa haɗi dacewa kefa Victoria naga kinyi tsaye kutafi mana bin bayan hidaya destiny da Victoria sukayi suna ɗan yin nisa da sauran nurse's ɗin destiny ta ɗan taba Victoria alamar ta roki hidaya akan ta taya ta ba dr haƙuri ganin baza tayi ba yasa destiny dakatar da hidaya haɗi da cewa "kiyi hakuri hidaya akan abun da Victoria tayi maki haushin dariyar da kuka yi matane ɗazu, amma kiyi hakuri" "shikenan bakomi, ni da man bawani riƙe taba" "shikenan amma ki taya ta ba ma dr hakuri pls karya cireta daga cikin nurses ɗin dake tura mashi patient pls, a ranta take faɗan"ok shiyyasa kenan tazo ta ciman mutun ci"amma a zahiri sai tace "bkm yawuce insha Allah zan taya ta" thanks Victoria ta faɗa yayin da suka kawo office ɗin shiga ciki sukayi sallama hidaya tayi yayin da Victoria ke bayan ta, dr gani hidaya ta faɗa, ok a saka patient a layi amma mutum 15 kawai zan duba sauran kiturasu office ɗin DR KABIR, sorry sir ni ina iya tura su a cewar Victoria data ga yayi kamar bai san tana wurin ba, as from today this is the last time dazaki Kara zuwa office ɗin na I hope you understand, a fuwan sir kayi mata haƙuri bazata ƙara ba hidaya ta faɗa gaban ta na faɗuwa tsoron kar itama ya koreta, nagama magana get out
ƙasa Victoria tayi akan gwiwo winta tana ci gaba da bashi haƙuri harda kuka, I said get out from my office ya faɗa da tsawa yana nuna mata hanyar fita, fita tayi tana kuka kamar ranta zai fita ,kema zaki iya tafiya" Ok sir hidaya ta faɗa fita itama tayi " wajen office ɗin ta samu Victoria da destiny suna ganin ta suka nufe ta rokonta suka shigayi a kan ta taya victoria ba ma dr haƙuri " shikenan insha Allah zan taya ta kar ku damu hidaya ta faɗa hadi da sharema Victoria hawayen dake fuskarta ta cigaba da kwantar mata da hankali godiya sukayi mata sannan suka koma office ɗin da suke zama ita kuma ta wuce wurin patient domin tura ma dr su .
haka ya cigaba da ganin patient shikuma wannan dattijon ruwan da aka sa mashi na ƙarewa yasa driver ya mai dashi ABNOOR aka bashi gado , bashi ne ya bar EKO ba sai wurin 12:30 sannan ya wuce ABNOOR nan ma yaga patient dayawa saboda da nan yafi jimawa a nan a kan eko , abnoor hospital ɗin sane halak malak Ita kuma eko aiki yake a chan, sau biyu  yake zuwa eko a sati idan yana lagos saboda yana visiting wasu Hospital ɗin , kuma in yaje 2 to 3 hours yake yi yaje abnoor   , amma standard in da yafi zama abnoor ne saboda chan har ranar Saturday yana zuwa in yana lagos ,sai wurin 6:00 ya tashi daga aiki dan har an fara kiraye kirayen sallar magrib masallacin hospital ɗin ya nufa domin gabatar da sallah sai bayan angama tukkun nan yanu fi gida,
horn yayi a bakin wani katafaren gida naji da faɗa dake Victorian Ice land , gida ne har gida wanda daga gani ba sai an faɗa maka ba kasan cewa an narkar da kuɗi, me gadine ya bude masa gate, ciki ya shiga  ya nufi parking lot da ke chan cikin gidan,ɗakin mai gadine farko daka shigo gidan sai boys quarters daga chan gaba sai kayi ƴar tafiya sannan zaka iso part ɗin masu gidan sai parking lot dake gefe  sai wani katon garden dake bayan part ɗin masu gidan hade da Wani katon swimming pool me kyen gaske,ride's ne gasunan kala kala a kallah zasu kai 6 a parking lot ɗin , parking yayi cikin gidan ya nufa tura ƙofar shiga part ɗin yayi bakinsa ɗauke da sallama,parlor ne me kyan gaske komai na cikin sa ya kasan ce golden and white color ne royal sofas ne masu kyan gaske set biyu sai wani ƙaton dining table mai chairs kusan guda 10 , sai wasu bedroom guda 3 dake hannun dama sai kitchen da store atare, wani corridor ya nufa inda yana shiga nan ma wani madaidaicin parlorn me dauke da sofa a set 1 komai na cikin sa golden color ne sai dining mai dauke da chairs guda 5 sai two bedroom, daya daga cikin su ya nufa bakinsa ɗauke da sallama, wata kyakyawar mace ce zaune a kan sallaya itama farace sosai suna Kama da dr banbanchi Ita mace ce shikuma namiji zata yi kimanin shekara 50 , sanye take da hijab hannun ta reke da chasbaha tana ja , da a lama sallah ta gama, sallamar da yayi ta amsa mashi yayin da yake ƙarasa wa inda take zaune wuri ya nema ya zauna "an wuni lafiya ammy, ya gida"ya faɗa , amsa mashi tayi da" lafiya qlu Alhmdllh ya aiki ya fama da patient, alhmdllh ammy, Masha Allah ta faɗa haɗi da cewa katashi ka shiga ciki domin kasamu ka huta zansa fatima ta kawo maka dinner ɗinka , dama shi ba ma'a bocin cin abinci a dinning bane, to shikenan ammy bari na wuce ciki, fito wa yayi daga bedroom ɗin yanu stairs dake parlor wani part ya shiga wanda da alama nasa ne tura ƙofar yayi haɗi dayin sallama, ya kutsa kai ciki parlor ne shima ma dai dai ci me kyan gaske komai nacikin sa ash and black ne bedroom ya nufa wanda shima bedroom ɗin kayan cikin sa ash ne hattada furnitures ɗin ciki ash ne ɗan corridor ya nufa cloth set ne sai gefe laundry basket, kayan jikin sa ya shiga ragewa ya koma daga shi sai boxer bathroom yanu fa domin watsa ruwa after 15 minutes ya fito jikin sa sanye da bathrobe wurin clothes set ɗinsa ya nufa jallabiya ya saka ajikin sa bathroom yakoma domin ɗauro alwallah sbd time ɗin sallah isha yayi  masallachin gidan ya nufa dan gabatarda sallah anagama sallah part ɗin sa ya koma a parlor ya zauna kan sofa bai jima da zama ba yaji ana nocking tambaya yayi waye ne " fatima " ce Yaya ok shigo ya faɗa , turo ƙofar tayi tashigo bakinta ɗauke da sallama kyakyawar matashiya ce akalla zatayi kima nin shekara 18_19 fara ce itama tana kamada ammyn su amma ba sosaiba dr dai shine ke kama da Ita sosai " ina wuni Yaya andawo lafiya, lafiya qlu , dama ammy ce tace nakawo maka dinner ɗin ka, ok ajiye kan table, ajiye mashi tayi haɗi dafita jawo table din yayi , serving ɗin kanshi yashiga yi, yana kammala cin abincin bedroom ɗinsa ya koma laptop dinsa ya jawo dake kan bedside aiki yashiga yi.....
KATSINA....Â
Su Aaimah ne zaune a falon mom suna kallo, sanye suke da pajamas sky blue,  mom ce tafito daga bedroom ɗin ta, ita ma sanye take da pajamas purple color, waya ce a kunnan ta  da alama waya take wuri tasamu kan sofa ta zauna tana cigaba da wayar " mom abie ne Aaimah ta faɗa yayin da take matsowa kusa da mom, daga mata kai mom tayi alamar eh" mom dan Allah kice muna gaishe shi munkira shi bai ɗauka ba, to kaji Wai twins ɗinka nagaishe da kai wai sunkiraka baka ɗauka ba mom ta faɗa , mika ma Aaimah wayar tayi da a lama cewa yayi a basu wayar, amsa tayi haɗi da cewa" inawuni abie ya Abuja, ya kuma aiki " on the other hand abie yace" lafiya qlu Alhmdllh ya gida ya kuma school " Alhmdllh abie ta bashi amsa, abie ko kace ina nake Aaimah ka ɗai kasani" Aairah ce ke mgn wacce ƙara sowarta kenan "afuwan yanzu zance kina ina sai kuma gaki ya gida ya schll" Alhmdllh abie yaushe zaka dawo, jibi insha Allah zan dawo " to Allah ya kaimu abie , ameen ya faɗa  sun jima suna waya sannan suka yi sallam, bedroom ɗinsu suka nufa domin bacci dan mom ta daɗe dashige wa nata bedroom ɗin ....
Episode 5_6
_FRIDAY......._
sauko wa yake daga stairs jikin sa sanye da baƙaƙen coat hannun sa riƙe da briefcase , ammy ce zaune kan sofa ƙaraso wa yayi kusa da ita " Ina kwana Ammy ina fatan kintashi lafiya " ya fada yayin da yake samu wuri kusa da Ammy ya zauna " lafiya lau Shazim har kafito," eh ammy ya bata amsa," ga breakfast din ka nan kan dinning" "to,ammy kinkuwa yi waya da NORAIZ "( kanin sa mai bimasa yayan fatima dayake baya nan yana kasar portland yana masters akan business ) ya fada yayin da yake nufar dinning "eh naji yace yana nan zuwa ranar sunday ( lahadi ) , ammy ta fada " eh ammy haka yake fada man jiya, "to Allah ya kaimu lafiya" Jiya uncle ɗin ku ya kirani, yace kai ka ɗai suke jira" shiru yayi baice komai ba sai da ammy ta sake cewa "da kai fa nake magana, ni ban san mikake nufi ba , da anyi magana sai kayi shiru, tun yaushe ake abu ɗaya sai yawo kake ma mutane da hankali"
"kiyi haƙuri ammy, wlh ban gama abun da nake ba, kuma nifa bani da wata wacce zance ina so, nafi son su barin harsai na samu wacce nake so"
"to bari kaji na faɗa maka ni ba ruwana daga yanzu bazan sake shiga maganar ba duk hukuncin da suka yanke akan ka babu ruwana "shazim yace "dan Allah ammy karkice haka idan kika zare hannunki innah zata iya zuga su su yanke man hukuncin da duk sukaga dama"
"to idan har baka son haka tafaru to dole sai ka nema ma kanka masalaha" "insha Allah ammy"
"to Allah ya yarda, ameen ammy ".
fatima ce ta fito daga bedroom dinta dake kusa da na Ammy jikinta sanye da uniform , dinning ta nufo Ita ma domin breakfast
" Ina kwana Yaya dafatan antashi lafiya " lafiya qlu ya bata Amsa, yana gama breakfast ya mike hadi da daukar briefcase din shi " Ammy ni zan wuce, to a dawo lafiya Allah ya bada sa'a, ameen Ammy fita yayi zuwa parking lot, gaisawa ya tsaya yi da masu aikin gidan tun daga kan maibama flower ruwa Har izuwa kan maigadi sannan ya fuce daga gidan, ABNOOR ya nufa domin yau baya zuwa EKO.
ABDULƘADIR  ABUBAKAR NURADDEEN PRIVATE HOSPITAL ( ABNOOR ).
Direct office din sa ya nufa briefcase din sa ya aje akan table zama yayi hadi da bude laptop dinsa Aiki yafara kafin time din daya ke duba patient yayi. sallama a kayi hadi da turo kofar wani matashin saurayi ne wanda zasu yi sa'anni da shazim din.
Amsa mashi sallama yayi, shigowa yayi daga ciki hadi da mikama shazim din hannu suka yi musa baha , sannan ya zauna kan kujerar dake gaban table din " shazim amma yanzu ka shigo ko dan nazo baka nan, eh shigowata kenan nakama aiki , ai ku manya ne agogo sarkin aiki, haka dai kake gani majeed karfin haline kawai, wlh kuwa ai kana kokari, to ya za'ayi, dole a nema"
"hakane dama maganar kayan da suka kusa ƙarewa ne"
"kai ai kuwa gara daka tuna man dan har na manta, zanyi magana da su yau insha Allah "
"to shikenan  nibari nakoma office"
"to shikenan nima yanzu zanje duba patient insha Allah sbd da time din sallah nayi zan tashi sai kuma gobe Idan Allah ya kaimu, ameen majeed ya fada hadi da barin office din shima baijima ba ya fita dakin marasa lafiya nufa sai 12:10 sannan ya dawo office yana shiga bawani jimawa yayi ba ya hada kan kayansa ya fito direct gida ya nufa bedroom din ammy ya fara zuwa gaisawa kawai sukayi ya nufi part din sa bedroom din sa ya nufa kayan jikin sa ya shiga ragewa ya nufi bathroom after 10 minutes ya fito kugunsa daure da towel dressin mirror ya nufa mai ya shafa mai dankaran kamshi, comb yasa ya shiga combing din kansa sannan ya shafesa da man aloe da hair spray clothes set dinsa ya nufa shaf shaf ya shirya cikin wata shadda ƴar ubansu milk color ba karamin b
kyau yayi ba sannan ya dauko hula ya daura brown color, feshe jikin sa yayi da turare mai ƙamshi,sannan ya nufi shoe rag dinsa takalmi ya dauko me kyan gaske shima brown color. masha ALLAH kawai zamuce dan ba karamin kyau yayi ba wayoyin sa dake bedside ya dauka fita yayi daga bedroom din yana zuba kamshi, ya nufi down stairs parlorn ammy zaune ya sameta tana karatun Al'qur'an tana kai aya tace " sai masallaci kenan, eh ammy ya bata amsa , to shikenan a dawo lpy nima zanje gida domin na ƙasa duba jikin baba , to saikin dawo Allah ya bashi lfy nima insha Allah yanzu daga masallachi zan biya na gaishe shi saina dawo ya fada hadi da kama hanyar fita Ammy nacewa a dawo lpy , da innah asabe ya cikaro ( mai Aikin su) zata shiga wurin Ammy, gaishe da Ita yayi ta amsa mashi da " Lafiya lau Shazim har za'a tafi masallachi kenan, eh ya bata amsa hadida fice wa daga falon ya nufi parking lot mota yashiga mai gadi ya bude masa gate ya fuce.........
_KATSINA......._
AIRAH
Zaune take bakin gado jikinta daure da towel da alama wanka zatayi .
"sister gaskiya kiyi sauri kifito nima nayi wanka kinsan yau abie zai dawo kuma mom tace muje gidan granny mu gaishe ta har so nake muje gidan aunty safiya ( kanwar MOm wacce suke uwa daya uba daya) mun kwana biyu ba muje ba "Aairah ta fada.
fitowa Aaimah tayi daga bathroom jikinta daure da towel " bawani sis zaki ziyara ne kodai zakije ganin ya MUS'AF dan nasan halinki sarai, Amma wlh Aaimah kin bani da sharri yau she nace maki saboda shi zanje gidan ni dai ziyara zani bawai saboda ya mus'af , dan wlh ki bari karki jaman ya usman yaji wannan maganar , ai kuwa saina fada masa ince bakiji gargadin da yayi maki ba, ni wlh har mamaki kike bani kirasa dawa zakiyi soyayya sai ya mus'af harka duk ta yarin ta, eh naji matar babban mutum sai mi koda ace na girmi ya mus'af ina ruwan ki Aairah ta fada tana huro hanchi, Allah ya baki hakuri Aairah ni nayi nan Aaimah ta fada hadi da nufar dressing mirror bathroom Aairah ta nufa shaf shaf Aaimah ta shirya cikin atamfa super Red color ɗinkin riga da skirt tana nan tsaye tana fesa turare Aairah ta fito sai bata rai take shiryawa itama tayi cikin atamfa color daya data Aaimah tana gamawa ba tai ma Aaimah magana ba taka ma hanyar fita daga bedroom din, murmushi Aaimah tayi hadi dacewa " ki nafa iya cewa kinji haushi, bata bata amsa ba sai tsaki data ja, haba twin sis kiyi hakuri bazan sake ba kinji ta ya mus'af sorry pls Aaimah tafada hadi da matsowa kusa da Aairah sake bata hakuri tayi tare da cewa haba abun gidan ya mus'af kiyi dariya mana dan Allah tafa da yayin da take langwabar da kai, murmushi kawai tayi hadi da cewa wallahi Aaimah ki daina kushe man ya mus'af Indai kina so mu zauna lafiya da ke, kaina bisa wuya na daina insha Allah Aaimah ta fada hadi dajan hannun Aairah suka fita bedroom din mom suka nufa samun ta sukayi zaune gaban dressing mirror tana saka sarka a wuyan ta sanye take da wani hadaden less brown color ta sha daurin ture kaga tsiya hannunta ya sha dan hannu da zobe na gold kalar sarkarta, har suna hada baki wurin fadin masha Allah  , Aaimah ce ta ce "kice yau an tashi rikita mana abie kenan , wannan kwaliyya haka mom ai sai ya ka sa gane ki yayi tuna nin sabuwar amarya aka kawo masa, Aairah tayi charab tace ba kiga harda ture kaga tsiya ba, lallai duk wanda ya ture ya taro match ba yan ball, murmushi kawai mom tayi hadi da cewa kun rainani ko, na lura ni kuka maida granny da dadi, Aa wane mu kawai dai munga kin hadu kar abie ya riki ce, ALLAH ya shirya ku mom ta fada ameen suka amsa, Aairah tace daman mom daga gidan granny zamu wuce gidan aunty safiya dan Allah, shikenan Idan kunje kuce ina gaishe ta , to shikenan mom zataji Insha Allah amma sai abie ya shigo sannan zamu tafi , to shikenan mom ta fada..
Ya usman ne ya shigo bedroom din jikinsa sanye da shadda maroon color sallama yayi hadi da shigo wa gaishe da shi su Aairah su kayi hadi da ficewa falo zama sukayi kan sofa suna kallo.
a chan kuma bedroom din mom gaishe sa Ita usman yayi, amsa mashi tayi hadi da cewa har ka dawo daga masallachin, eh mom ya bata amsa, abinci fa, a kai maka part dinka ko zaka sauko kachi a dinning, a'a a barshi nan zan sauko Idan abie ya shigo sai muci tare da ku , dan nayi waya da shi da ina kan hanya wai ashe ya dawo yana gidan dadi (kakar su ta wurin uba mahaifiyar Abee) amma yanzu zai taho, to shikenan bari nasa ajera abinci kan dinning sai muci tare da dashi dama nayi tuna nin basu kusa isowa ba, to shikenan mom ni na wuce part dina kafin ya kai da shigowa ya fada hadi da ficewa itama mom fita tayi direct kitchen tawuce a chan tasa mu baba larai na zuba abinci cikin warmers "yawwa baba kice harkin kwashe kafin nazo, halan kinga najima ban dawo ba sallah nayi sai nace bari kawai nayi har da wanka tun da nasan san da zan dawo nasan a bincin ya nuna kuma barrister na hanya shiyyasa, A'a nima sai da nayi wankan da naga baki sauko bane kuma ya nuna sai nace bari kawai na kwashe, to shikenan bari na jerasu a dinning mom ta fada hadi da daukar warmers din ta nufi dinning bala driver ne ya shigo hannun sa dauke da kaya suna cikin gaisawa mom sukaji sallamar abie daga bayan su sauko wa su Aairah sukayi da gudu jin sallamar abie, nufar sa su kayi da gudu hugging din su yayi yana murmushi sun bi sun makalkale shi mom ce ta matso tana cewa ku sake sa man, kunbi kun makalkalesa , haba mom kwana biyu fa baya nan, to ko baya nan fa , ya kwaso gajiya shine zaku kara masa wata, ku sake sa mana , sakin sa su kayi kan sofa suka zauna, shi kuma up stairs ya hau shi da mom , bala ne ya sake shigowa da wasu kayan na abie,  jakar kayan abie ka dai bala ya kai sama sauran kayan kuma kitchen ya nufa dasu .
AFTER 25 minutes........
abie ne da mom ke sauko wa daga up stairs abie har ya chanza kayan jikin shi da alama wanka yayi dinning suka nufa ta sowa su Aairah sukayi suma suka nufo dinning din " Aairah maza kije ki kira yayan ku mom ta fada, tashi Aairah tayi direct part din ya abdallah ta nufa tsit parlorn shi, ba kowa sai kamshi kawai dake tashi ya hadu parlorn golding color ne komai na ciki , bedroom din sa ta nufa nocking tayi tambaya yayi waye, Aairah ce, yaya mom tace ka sauko abie ya dawo ta bashi amsa, gani nan zuwa yace, fita tayi daga part din ta koma wurin su mom , yace ga shinan zuwa ta fada yayin da take samun wurin zama serving din su Aaimah ta shiga yi sai ga ya abdallah shima ya sauko jikin sa sanye da jallabiya karaso wa yayi yana gaishe da abie da gajiyar tafiya, amsa mashi abie yayi tare da tambayar shi ya aiki,amsa ya bama abie da alhmdllh shima serving din sa Aaimah tayi , abinci suka shiga ci ba magana sai dai karar spoon dake tashi, su Aairah suka fara tashi, ba dai har kun ta shi ba, abie ya tambaya yana binsu da idanu, eh abie zamuje gidan granny ne shiyyasa kuma fa mun koshi, Aairah ta bashi amsa, to shikenan sai kun dawo kar dai ayi dare , a dawo dawuri kunji, Insha Allah abie baza mu kai ba, Allah yasa, ameen suka fada hadi da nufar up stairs , abie suna gama cin abinci kan sofa suka koma suna fira shi da ya abdallah ,mom kuma tattare dishes din da su kayi amfani dasu tayi ta nufi kitchen, baaba larai ce ta fito daga corridor din da da kinta yake wurin su abie ta nufo hadi da gaishe da abie tana tambayar shi ya gajiyar hanya amsa mata yayi da, "lafiya lau alhmdllh, ya gida ya kuma muka same ku, alhmdllh muke naga sako nagode Allah ya saka da alkairi, ameen nagode bakomi abie ya bata amsa ( nasan masu karatu zasu ce godiyar mi baaba larai keyi ma abie , kudi ya ba ma mom ta ba ma dukan hadiman gidan dama ya kan yi haka duk In zaiyi tafiya.) Kitchen ta nufa anan ya samu mom na wanke dishes din da suka ci abinci " ah hajiya dakin bari nazo na wanke ai, A'a bakomi baaba kema ki huta mom ta bata amsa, to shikenan bari muyi tare" inji baaba larai, A'a dakin bar shi Allah kinga na kusa gamawa ai, to shikenan , su Aairah ne suka sauko sun sha jalbab har kasa sai bag kalar ta kalmin dake ka farsu kara sowa su kayi wurin su abie hadi da cewa sai mun dawo,abdallah ne ya ce" mudi na nan waje shi zai kaiku" to suka ce hadi da nufar wurin mom sun cewa sai mun dawo a dawo lafiya tayi masu , ficewa su kayi harabar gidan, a nan suka samu mudi na jiran su , motar suka nufa, shiga su kayi, key yayi ma motar suka fice da ga gidan dama me gadi ya bude masu gate labari kawai Aaimah da Aairah keyi shi dai mudi nashi saurare har suka isu gidan granny horn mudi yayi a bakin gate din gidan bude masa gate din a kayi ya shiga daga ciki ya na parking suka fito gidane dan dai dai me kyau cikin gidan suka nufa wata kyakyawar tsohowa ce suka samu zaune a parlor tana kallon SUNNAH TV ( granny kenan mahaifiyar mom ce) sallama su kayi da gudu suka nufi yar tsohuwar, granny tace " karku kuskura ku fado man , salon ku ida kara sa man yan kafafun da nake fama dasu" Aaimah tace "haba granny daga munyi murnar ganin ki sai kice zamu ida karasa maki yan kafafun"ta fada tana turo baki, Aairah ce tace " shiyyasa yau zan zuga tsoho yayi maki kishiya tun da baki da kafafu" granny tace " sai dai ke ayi maki kishiya, amma ba dai ni ba, saboda ni ba wacce zata iya kishi dani, in kuma kece kishiyar inji tunwuri" dariya suka kwashe da Ita su duka Aairah tace " wah wai ni , ai kuwa da kin sha kwar kwasa da kisi si na, murmushi kawai granny tayi hadi da fadin Allah ya shiryeki yan biyu ( dayake haka take ce masu kokuma Hassana da hussainah) gaishe da Ita sukayi suna tambayar tsoho na nan, ( wato mijin granny) granny ce ta basu amsa da "yana parlor da yake ganin dalibn sa, inajin ma karatu suke saboda yau juma'ah ( malamin addini ne shi duk da ya tsufa hakan bai hana shi koyar da daliban sa ba) Aaimah tace" to shikenan granny bari muje gidan aunty safiya mu dawo, kilan time din ya gama, to sai kun dawo ku gaishe man da ita granny ta fada Aairah ce tace zataji insha Allah fita sukayi harabar gidan nan suka samu mudi zaune kan benchi suna fira da me gadin gidan, gannin sun fito yasa shi ta sowa Aairah ce tace "kabar shi kawai ba nisa za muyi ba gidan aunty safiya za muje, to ya fada hadi da koma wa kan benchi ya zauna su kuma fita su kayi daga gidan, tafiya su kayi a kafa ba mai nisa ba suka iso gidan tura yar kofar dake gefen gate su kayi hadi da shiga gidan, gida ne mai girma ba laifi dan har ya kusa girman gidan su, part din masu gidan suka nufa da sallama a bakin su suka shiga parlorn, yan yara suka samu na wasa a parlorn mace da na miji a kalla za suyi kimanin shekara 10, suna jin sallamar su suka nufo su da gudu suna masu "oyoyo aunties ya gida ya mom" su Aaimah suka ce"lafiya lau hisham sai ku ka dai a parlor kai da hibba, wata matashiya ce ta leko daga up stairs jin haya niyar yaran zata yi sa'anni dasu Aaimah tana ganin su Ita ma da gudu ta sauko tana fadi "oyoyo lovely sister da kuka ce kun fasa zuwa" Aairah tace "kedai bari najma, dafa har mun fasa saboda abie zai dawo yau, to da muka koma gida daga school mom take ce ma ai yama kusa isowa, to shine fa muka shirya tana dawo wa muka taho, najma tace "gaskiya naji dadi, da Allah har nayi fushi, Aaimah tace "yanzu dai ba wannan ba naji banji mutsin Ummah ba ( Aunty SAFIYA suke cema Ummah sbd su najma ) ko bata nan ne , tana dakin abba najma ta bata amsa hadi da jan hannun su tana cewa kumu tafi part din abban daga nan sai ku gaisa dashi ko , ok muje, part din abban suka nufa, sallama su kayi yayin da suke shiga cikin parlorn zaune suka same su kan sofa, amsa masu sallamar suk ayi aunty safiya tace "ah lallai yau ina da mn yan baki" abba yace " lallai kam yau muna da man yan baki, ya mom din ku da abie ya kuma school, alhmdllh abba suka amsa mashi, to masha Allah abba ya fada najma ce tace " to ku tashi mutafi daki, da to suka amsa mata hadi da mikewa suka fice direct bedroom din najma suka nufa suna shiga suka yada zango akan bed din ta Aairah ce tace " wai nikam ina Yaya mus'af ne najma,Aaimah ta ce " uhmm dama nasan hali har ni zakiyi ma bariki wai ziyara za muzo bayan nasan karyane, eh din naji komi za kice kice Aairah ta fada tana murguda ma Aaimah baki ,najma ce tace" ya Isa haka inkuka fara sai kuba mutun haushi wlh , ya mus'af ne deko to yana part dinsa bari nakira maki shi a waya koke kikira shi ba shi kenan ba, Aaimah tace aikin san wasa nake maki ko rabin rai , niban wani sani ba Aairah ta fada, to yanzu kinsan shikenan ko ta wuce, bari ni na kira maki shi da kaina a cewar Aaimah hadi da ciro wayarta tayi dealing number sa kiran na shiga ta mikama Aairah wayar picking call din yayi hadi da ce " Aslm, wslm ta bashi amsa, sai cewa yayi" Aaimah ya kike ya gida yasu mom da ya abdallah, ina kuma sweetie nah take, bubbuga kafafu ta shiga yi tana turo baki hadi dacewa" haba Qalbei nice kenan baka gane ba , su najma miza suyi inba dariya ba suna cewa a she soyayyar bata kaiba da har ake kasa gane muryar juna , fa shewa da kukan shagwaba Aairah tayi hadi da cewa ka gani koh Aaimah da najma nayi man dariya, on the other hand yace " sorry sweet heart nayi tuna nin Aaimah ce, kinga ai numberta ce amma kiyi hakuri kinji my, najma na gidan kune, Aa fa kai da nazo nayi surprise dinka, amma sai ka bata komai baka gane ni ba Aairah ta fada, sorry kinji tawan fada man kina ina kinji, turo baki gaba tayi hadi da cewa " Ina bedroom din najma , am coming sweet heart ya fada hadi da kashe wayar,ajiye wayar tayi Ita ma hadi da yima su najma gwalo "oho dai ke da ba'agane ba najma ta fada hadi da tafawa ita da Aaimah" nocking sukaji ana yi da sauri Aairah ta nufi kofar tana bu dewa wani matashin saurayi ne tsaye jikin sa sanye da jeans da T-shirt na kamfanin Gucci farine kyakyawan karshe a kalla zai yi kimanin shekara 20 murmushi Aairah ta sakar mashi shima martanin murmushi ya mayar mata, gaishe da shi Aaimah tayi, ficewa su kayi daga bedroom din, su Aaimah kuwa fira kawai suke har aka kira sallar asr, sallah suka tashi su kayi a lokacin Aairah itama ta shigo domin yin sallar Aaimah ce tace ma Aairah ai nayi tunanin nisa ku kayi da naga kun fita ashe kuna kusa, banza Aairah tayi da ita ta nufi bathroom domin yin alwala, basu ne suka bar gidan ba sai wajen 5:00 sannan suka koma gidan granny najma da Aaimah na gaba yayin da Aairah da mus'af ke bayan su , suna shi ga granny tace a she zaku dawo harna yi tuna nin kun wuce gida a she kuna nan, kallon mus'af tayi tana fadin" kai kuma lafiya kayi man tseye a kai , aure ne dai banyi ehe" dariya mus'af yayi hadi da cewa sai mi, dama ni yarinya nake so me jini a jika ba tsohuwa ba, dariya suka kwashe da Ita su duka, haba kai dai kawai dan ba zaka samu bane , ya safiyar take ina su Hibbatu da hisham ,
lafiya lau suke granny, fira suka shiga yi da granny tana tsokanar su a nan tsoho ya same su, gaishe da shi suka yi , dashi suka taru suna ta firar ba sune suka bar gidan ba sai kusan 5:50 sannan mudi ya mayar da su gida duk da mus'af ya so mai da su, amma suka ce ya barshi tun da da driver suka zo ,da shigar su gida bedroom suka nufa domin time din sallar magrib ya kusa kayan jikin su suka cire suka sanya ma rasa nauyi, sau kowa su kayi down stairs direct kitchen suka nufa wurin mom da baaba larai dake shirya dinner , kama masu aikin su kayi har suka kammala kowa ya nufi bedroom dinsa domin gabatar da sallar magrib wacce ake kira.
KAINAAT
_Lagos....._
Innah asabe ce a kitchen ita da fatima suna girki kiran sallar da a ke yine yasa fatima cewa "Innah kije kiyi sallah zan karasa aikin, to amma kefa, karki damu Innah kitafi kawai ( da yake tana fashin sallah ne) To shikenan, fita tayi daga kitchen din ta nufi dakin ta, shazim ne ya shigo cikin gidan jikin sa sanye da farar jallabiya da alama daga masallachi yake par Ammy ya nufa bai isketa ba sai yawuce bedroom din ta nan ma bata nan fitowa yayi daga part din ya nufi main parlor fatima ya gani ta fito daga kitchen hannun ta rike da food flask " Ammy bata dawo bane, eh bata dawo ba , ok ya fada hadi da Komawa part din sa, sanda Innah a sabe zata koma kitchen har fatima ta gama komai da yake sai da ta jira aka kira sallah isha tayi, kama mata kawai tayi suka gyara kitchen din, falo fatima tafita kiran daya daga cikin ma aikatan gidan tayi a waya domin yazo ya daukar masu a binchin su, sallama a kayi daga kofar falon hadi da turo ta, fateemah ce tace yawwa ilya hadi da shiga kitchen fitowa tayi hannun ta dauke da food flask din masu aikin mika mashi tayi , part dinsu ita da Ammy ta nufa bedroom din ta ta shige kayan jikinta tacire towel ta daura bathroom ta wuce domin yin wanka 10 minutes ta fito daga bathroom din dressing mirror ta nufa mai kawai ta shafa ta nufi clothes set dinta dama ta sanya pad tun a toilet shiryawa tayi cikin pajamas lemon green ta yafa mayafi white mai dan girma feshe jikin ta tayi da turare mai dadin kamshi fita tayi daga bedroom din a falon Ammy ta zauna kan sofa wayar ta dake charge tacire ta shiga chatting wurin 9:00 sai ga Ammy wacce shazim ya dauko falo ta tsaya shi kuwa up stairs ya haura sai 9:30 fatima da Ammy su kayi dinner dan shi shazim cewa yayi takai masa part din sa suna kammala wa fatima ta kwashe kayan da suka yi amfani dasu ta kai kitchen nan falo ta zauna suna fira da Ammy sai wuri 10:00 su katashi kowa ya shige bedroom dinsa
, zaune yake kan sofa dake bakin bed dinsa yana aiki a laptop dinsa sai wurin 12:00 ya rufe laptop din toilet ya nufa bayan 5 minutes yafi to jikin sa da danshin ruwa da alama alwala yayi, wardrobe dinsa ya nufa sallaya ya fito da Ita ya shim fida shafa'i da wutiri yayi ya jima kan sallayar yana adu'oi sannan ya niketa ya maida ta cikin wardrobe, bed dinsa ya nufa hadi da kashe bulbs din dakin bedside ya kunna, zama yayi daga bakin bed din adu'a yayi ya sha fa a fuskar sa sannan ya ida hawa kan bed din kwanciya yayi hadi da jan blanket yarufe iya kugunsa.
To nace Asuba tagari doctor nima bari naje na nemi nawa makwanchi.😴
Washe gari.......
Zaune Ammy da fatima suke kan dinning suna breakfast, shazim ne ya shigo jikin sa sanye da jogging suit black color sai p-cap white hannun sa rike da water bottle wurin su Ammy ya nufa " ina kwana Ammy fatan kin tashi lafiya ya fada Ammy tace "lafiya lau alhmdllh, yau baka zuwa abnoor ne, amsa ya bata da " A'a Ammy zanje, ok naga har 10:30 tayi Ammy ta fada , shazim yace " eh wlh nayi late wurin tashi daga bacci amma yanzu zan shiga ciki nashirya Insha Allah, to shikenan sai ka shirya ga breakfast dinka nan na jiran ka a dinning, to Ammy ya fada hadi da nufar part din sa.............
✨ _Victoria_ . ✨
Anguwace ta christianity irin ta masu kara min Karfi, destiny naga ni ta fito da ga wani gida ta nufi wan da ke opposite din inda ta fito jikin ta sanye da gown iya gwiwarta purple color kanta da kitson kalaba na attachment ka farta sanye da flat shoe, gidan dan karami ne, ko ina ya sha cement dakuna biyu ne a gidan nufar daya daga cikin kofofin tayi knocking hadi dacewa" excuse" daga cikin dakin naji ance "come in" tura kofar tayi hadi da shiga Victoria ce acikin
dakin tana ta faman jan straight gown taki shigar ta destiny ce tace " lallai Victoria a she bakima shirya ba kin kuwa san nisan da wurin ya ke da shi sai fa munfita Lagos kuma fa kinsan yau ana zuwa church da yamma, sorry destiny yanzu zan shirya mu tafi, abun da yasa ma nayi late bari nayi sai momy ( mahaifiyar ta ) ta tafi market sannan domin in tasan inda zamu ba zata bari mu tafi, Victoria naga ma shiryawa suka fita gidan tafiya sukayi sai da suka hau kan titi tukun suka tsai da mai mashin suka hau, tafiya su kayi mai dan nisa sannan suka kawo wani dan karamin kyauye duk duwatsu suna kawowa inda mashin bai wuce wa suka sauka, kudin sa suka bashi su kuma suka cigaba da tafiya nanma sai da su kayi tafiya ba laifi tukun suka kawo wata yar bukka ita kadai a wurin sai mutane jere a bakin bukkar suna karaso wa suma suka bi layi, sun jima a tsaye layi bai zo kansu ba, victoria harta gaji da tsayuwa ta duƙa, lokacin da layi ya zo kansu shiga sukayi tare cikin bukkar, wani mutum ne zaune gaban sa wasu kahuna ne sai kawunnan mutane kwaran gwal jikin sa sanye yake da jajayen kaya fuskar sa duk ta sha digedige fari sai idanun sa kewaye da bakin fenti gaishe dashi sukayi dawani irin yare mara dadin ji shi kuwa kwashewa yayi dawata irin dariya sannan ya tambaye su meke tafe dasu, destiny ce ta kora masa bayani a kan abun da yake tafe dasu, dariya ya sake kwashe wa da Ita sannan yayi yan surkullen shi wani magani ya dauko cikin wani bakin tulu ya basu destiny tasa hannu ta karba ita kuwa Victoria sai zare idanu take kudi suka dauka masu yawan gaske suka ajiye a gaban bokan sannan suka fice daga bukkar ta hanyar da suka biyo ta nan suka bi sai da suka kawo cikin kyauyen tukun suka samu wani mashindin ya dawo dasu gida,  gidan su destiny suka wuce dan lokacin kafe 4:15 dakin destiny suka nufa zama sukayi suna huce gajiyar tafiya destiny ce tace" ina zuwa" tana fada ta fice daga dakin batafi 1 minute ba ta dawo da kwano a hannun ajiye shi tayi gaban Victoria fita ta sake yi sai gata ta sake shigowa hannun ta rike da pure water guda biyu zama tayi hadi da bude kwanon sakwara ce da miyar okra ( kubewa) suna cikin ci saiga wani namiji ya shigo dakin sanye ya ke da crazy jeans sai singlet gashin kansa kuwa yasha dada ( yanda yan iska keyima gashin su ya koma kamar lagwani )da kaga yana yin sa zaka san a buge yake, ya na ganin Victoria ya kama washe baki  daure fuska Victoria tayi tana ganinsa , kusa da Ita ya matso kamar zai yi hugging din ta ba shiri ta mike tsaye hadi da daka mashi tsawa tana cewa" which kind of this nonsense samuel " bangane wulakanci ba Victoria you are my wife ya fada yana washe baki, destiny dai na gefe tana kallon su bata ce masu kala ba sai da taga Victoria na niyyar fita da ga dakin sannan taba Victorian hakuri shi kuma Samuel ce mashi tayi "ya fita ya basu wuri tun da shi ba shi da hankali , Victoria tace bata son shi to mi yasa zai ta kura ma rayuwar ta, Komawa Victoria tayi ta zauna sai wani cika take tana batsewa, suna kammala cin a binci fita su kayi bakin wani fanfu suka wanke hannu Victoria ce tace "destiny zan tafi gida domin nayi shirin zuwa church din kuma kin ga momy bata san nafita ba kar ta dawo bata ganni ba, kawai dai kinson zuwane amma aikin san bata dawo ba, da ta dawo da mun iske momy ( mahaifiyar destiny ) a gida itama ta dawo tun da wurin business din su daya, kuma tare suke fita su dawo tare, to kawai Victoria tace, komawa su kayi dakin, destiny tace " kinsan fatan da nake kuwa Victoria, Aa sai kin fada Victoria ta fada tana sauraron mi destiny zata ce, so nake wannan wawuyar hidaya ta taya ki bama dr hakuri kamar yarda da tace, a samu sa'a shi kuma ya maida ki uhmmm zata sha mamakin abun da zamuyi mata dan sai munrabata da eko ma gaba daya yan da ba zata sake ganin dr ba, nima haka nake so zata sha mamaki In dai ya mai da ni wuri na, dariya sukayi harda ta fawa suna nan suna shirya yan da za su yima hidaya sai ga mahaifiyar destiny tashi go , suna jin shigo warta suka fito daga dakin gaishe da Ita su kayi yayin da destiny ke amsar kayan da momyn ta ta shigo dasu, Victoria ce tace "ni na tafi" to saina shigo destiny ta fada tana fita gida ta shiga momynta ta samu a dakin zaune cewa tayi" good afternoon momy , afternoon daga ina kike na shigo baki nan momyn tafa da , ina gidan su destiny ne momy, ok kawai momyn tace, wurin 5:00 suka shirya domin zuwa church ( suna zuwa church su duk ranar Asabar domin gyaregyre sbd lahadi ) gidan su destiny , Victoria taje daga chan suka wuce church din.........
_Katsina......_
Mom ce zaune a main falo suna fira da baaba larai abdallah ne ke saukowa daga stairs case jikinsa sanye da jallabiya wurin su mom ya zu hadi da cewa fira kuke ne nagan ku zaune, wlh kuwa sai ina haka naga kasha jallabiya mom tafada amsa ya bata da cewa zan danje wani wuri ne daga nan zan tsaya sai angama sallah sannan zan dawo, mom tace" ah kace wurin diyata za'a amma sai kaje mata da jallabiya sai kace wani limami, murmushi kawai yayi hadi da cewa " mi za kiyi da wata diya keda kike da yan biyu duk mata a gaban ki, mom ce tace " duk da ina dasu kari ai bai kin dadi koh baaba larai" haka ne kuwa hajiya baaba larai ta bata amsa, Mom ce ta kuma cewa" ni dai yau she zaka kawo man surukata gidan nan" abdallah ne yace " ki bari mom dana samu wacce ta dace dani zan kawo maki Ita har gida, uhmmm Allah ya shirye ka abdallah wata kan har yanzu baka samu wacce tada ce da kai ba ko, nasan maganinka ai sawa xanyi abie dinku ya zabo maka mata tun da kai ka kasa Mom ta fada, abdallah yace" haba mom kamar ni za'a za boma mata, ai kuwa dana bani , yo ai sai abokaina suyi man dariya, mom tace" to In dai baka son auren dole to ka fito da mata kayi aure, kai ko kunya bakaji shekara 30 fa amma ace baka da mata haba ina amfani ' dan Allah mom kibar batun auren, dolenan , In dai aure ne very soon zanyi in Allah ya yarda, Allah ya yarda mom ta fada, ni na wuce sai na dawo ya fada hadi da nufar kofar fita, a dawo lafiya mom ta fada , fira mom suka cigaba Ita baaba larai suna nan zaune sai gasu Aaimah sun shigo da'a lama daga Islamiyya suke dan jikin su sanye suke da hijabi blue color gaishe da su su kayi sannan suka nufi bedroom din su wanka su kayi hadi da alwallar magrib sannan suka sanya kaya marasa nauyi a daki suka zauna har sai da su kayi sallah isha tukunnan suka fita falo fira sukeyi a kan Islamiyya anan mom tasa me su har da abie wanda baijima da dawowa ba daga masallachi nan sukai ta fira har 9:00 sannan su kayi dinner kowa ya wuce dakin sa suna shiga daki wayar Aairah na ringing dauko wayar tayi dake ajiye kan bedside murmushi tayi data dauki wayar taga mai kiran Aaimah ce tace " halan ya mus'af  ne, daga mata kai Aairah tayi to sai da safe domin nasan ke ba yanzu ba Aaimah ta fada hadi da hayewa kan bed taja blanket Ita kuwa Aairah zama tayi bakin bed ta cigaba da waya ba Ita bace ta gama wayar nan ba sai wurin 10:55 sannan ta haye bed adu'a tayi ta shafa hadi da shafa ma Aaimah sannan taja blanket Ita ma bayan ta kashe bulbs da bedside lamp.....
Asuba ta gari yan biyu 😴
Episode 7_8
Mom ce zaune a main parlor suna fira da baaba larai ya abdallah ne ke saukowa daga stairs case jikinsa sanye da jallabiya wurin su mom ya nufo hadi da cewa "fira kuke ne nagan ku zaune? "
"eh , sai ina haka nagan kasha jallabiya" mom ta fada amsa ya bata da cewa zan danje wani wuri ne daga nan zan tsaya sai angama sallah sannan zan dawo, mom tace" ah kace wurin ɗiyata za'a, amma Sai ka je mata da jallabiya Sai kace wani limami," murmushi kawai yayi hadi da cewa " mizakiyi da wata diya ke da kike da yan biyu duk mata a gaban ki, mom ce tace " duk da ina dasu ƙari ai bai ƙin daɗi koh baaba larai? " haka ne kuwa hajiya baaba larai ta bata amsa, Mom ta kuma cewa" ni dai yaushe zaka kawo man surukata gidannan? " abdallah ne yace " karki damu mom, dana samu wacce ta dace dani zan kawo maki ita har gida, uhmmm Allah ya shirye ka abdallah wata kan har yanzu baka samu wacce tada ce da kai ba ko, na san maganin ka ai, sawa zanyi abie dinku ya zabo maka mata tun da kai ka kasa Mom ta fada, ya abdallah yace" haba mom kamar ni za'a zaɓo ma mata , ai kuwa dana ji kunya, yo ai sai abokaina suyi man dariya, mom tace" to In dai baka son auren dole to kafito da mata kayi aure kai ko kunya bakaji shekara 30 fa amma ace baka da mata, haba ina amfani ' dan Allah mom kibar batun auren dolen nan In dai aure ne very soon zanyi in Allah ya yarda, Allah ya yarda mom ta fada, ni nawuce sai na dawo ya fada hadi da nufar kofar fita, a dawo lafiya Mom ta fada , fira mom suka cigaba Ita baaba larai sai gasu Aaimah sun shigo daga Islamiyya jikin su sanye da hijabi blue color, gaishe dasu su kayi sannan suka nufi bedroom din su , wanka sukayi hadi da al'walar magrib sannan suka sanya kaya ma rasa nauyi a daki suka zauna har sai da sukayi sallah isha tukunnan suka fita parlor,kan sofa suka zauna suna  fira islamiyya a nan mom ta same su harda abie wanda baijima da da wowa ba daga masallachi nan suka zauna suna  fira har 9:00, sannan sukayi dinner kowa ya wuce dakin sa , suna shiga daki wayar Aairah na ringing dauko wayar tayi dake ajiye kan bedside tana murmushi ganin mai kiranta, Aaimah ce tace " halan ya mus'af ne, daga mata kai Aairah tayi, to sai da safe domin nasan ke ba yanzu ba Aaimah ta fada, bed ta nufa ta kwanta taja blanket , Ita kuwa Aairah zama tayi bakin bed ta cigaba da waya, ba ita bace ta gama wayar nan ba sai wurin 10:55 sannan ta haye bed, adu'a tayi ta shafa ta shafa ma Aaimah sannan taja blanket Ita ma bayan ta kashe bulbs da bedside lamp.....
_Washe gari........_
Zaune suke kan sallaya suna adu'a da tasbihi, tashi Aaimah tayi daga kan sallayar ta nufi inda suke Ajiye Alqur'ani , guda ɗaya ta ɗauko, kusa da Aairah ta dawo ta zauna hadi da mika mata tana cewa" sister amsa in karanto maki haddar da nayi, inda nayi kuskure saiki gyara man,"
to in dan na gama maki nima sai ki amsar man"to Aaimah " karatu ta fara cikin ƙira'a mai daɗi ,Aairah na sauraron ta  inda tayi kukure sai ta gyara mata, sai da suka gama amsar ma junan su hadda tukunnan suka mai da qur'anan wurin da suke a jiye su , fita suka yi daga bedroom saboda gari ya waye Ƙarfe 7:00 na safe,  main parlor suka nufa a kitchen suka samu mom da baaba larai suna hada breakfast gaishe dasu sukayi , amsa masu su kayi cikin kulawa Mom tace " ina fatan dai kungama hardar ku ta yau, eh mom , to masha Allah, baaba larai tace " kace muna da bikin hadda dana kammala makarantar gagarumi gidan nan, to Allah ya taimaka ya nuna mana lokacin lpy" har hada baki suke wurin cewa ameen, kama masu aikin su kayi harsuka gama sannan su Aairah suka jera kan dinning, bedroom din su suka koma domin shirin zuwa Islamiyya ( Islamiyyar harda suke, in suka tafi tun safe sai yamma duk ranar weekend, Idan kuma ba weekend bane karfe 2:30 suke zuwa sutaso da yamma, amma ban da ranar Friday in kuma an yi hutun school to kullum ne ban da friday .)
Aaimah ce ta fara shiga toilet domin yin wanka ita kuma Aairah uniform dinsu na Islamiyya ta dauko masu tare da bags dinsu , Aaimah na fitowa itama ta shiga shaf shaf Aaimah ta shirya cikin uniform din san da Aairah ta fito har Aaimah ta gama shirin ta ita ma cikin kankanin lokaci tashirya suna gamawa suka fice zuwa main parlor dinning suka nufa domin yin breakfast suna gamawa part din abie da na mom suka nufa domin ce masu zasu tafi , a dawo lpy suka yi masu , fita su kayi harabar gidan anan suka samu mudi na jiran su dan shine ke kaisu, sai wurin 10:00 su mom su kayi nasu breakfast din saboda weekend........
✨ _SHAZIM_ ✨
Yau sunday baya zuwa aiki , kwance yake kan sofa a bedroom din sa ya baje papers da laptop din sa yana,  tun da ya gama sallar asuba ya ke nan wurin yana aiki har bacci yayi awan gaba da shi, jikin sa sanye yake da jallabiya, wayarsa ajiye saman cikin sa yayin da ya sa ɗayan hannun sa ya rufe fuskar sa, wayar sa dake saman cikin sa ce ta fara ringing, hannun sa dake kan fuskar sa ya janye yana ya tsina fuska alamar an katse mashi baccin sa , daukar wayar yayi "Brother" shine sunan daya bayyana akan screen din wayar picking call din yayi hadi da Kara wayar a kunne " hello Yaya na cikin wayar ya fada, "ba zaka chanza ba ko noraiz , ina amfanin wani hello kana muslim "
  " a fuwan big bro noraiz ya fada, Allah ya shirye ka, ameen Yaya ka tashi lpy yasu Ammy da fatima? , lafiya lau suke kaifa, Ina fatan kai ma kana lafiya? , ina lpy Yaya, oka Masha Allah shazim ya fada hadi da cewa ya maganar da wowar ka yau, domin da naga kiranka nayi tuna nin kace man ka iso dan nasan halin ka da chanza lokaci idan zaka dawo , A'a ba haka bane Yaya ina nan zuwa yau din Insha Allah , kawai dai ban samu biyo jirgin safe bane shiyyasa nakira ka na fada maka sai dai da yamma insha Allah, ok Allah ya kawo ku lpy, ameen Yaya sai an jima, ok kawai shazim ya faɗa hadi da kashe wayar ya ajiyeta kan center table, sai da yayi 5 minutes a kan sofar  sannan ya mike, papers din da ya baza ya kwashe da laptop ya saka cikin din briefcase, cire jallabiyar dake jikin sa yayi ya koma da gashi sai shorts toilet ya nufa ya jima a toilet din sannan ya fito ya nufi dressing mirror anan ma ya jima yana yan shafe shafe sai kace mace sannan ya nufi clothes dinsa shiryawa yayi cikin jeans and T_ shirt fita yayi daga bedroom din part din Ammy ya nufa a parlor ya same ta Ita ka dai, fatima na Islamiyya, gaishe da Ita yayi , amsa mashi tayi wuri ya samu ya zauna kusa da ita, Ammy tace " ga breakfast dinka chan kan dinning tun dazu har nayi tuna nin yau baka fitowa a daki za kayi weekend , wane ni Ammy , kina a gida na zauna daki, ai dole na fito na tayaki fira, tun da auta na Islamiyya kuma rigimenmen ki baya nan duk da yau zai dawo , murmushi kawai Ammy hadi da cewa kunyi waya da shine naji yace da safe jirginsu zai taso, kin dai san halin ka yanki Ammy da chanza lokaci inzai dawo, wai kuma yanzu sai yamma tukun, Allah ka shirya mai babban suna kai dai, ameen Ammy ya fada hadi da tashi ya nufi dinning, warmer din dake kan dinning din ya shiga bu dewa yana duba abun da ke cikin su. cup ya dauka ya hada tea sannan ya zu ba arish, wurin Ammy ya dawo ya zauna suna fira shi da Ammy yayin da shi kuma yake cin abincin sunjima suna fira har aka fara kiran sallar zuhur sannan su ka tashi Ammy ta nufi dakinta shi kuma ya nufi part din sa domin yin alwala.....
✨ _HIDAYA_ ✨
 Flat house ne me kyan gaske Masha Allah na masu rufin asiri kutsa kai nayi cikin parlorn gidan wanda komai na cikin sa brown color ne, hidaya naga ni zaune kan dinning ta lunch ita da mahaifiyar ta kamanin su ɗaya, tashi hidaya tayi mahaifiyar ta tace " mi ki ke nufi, naga kin tashi ? "
" na ƙoshi ne mama" wai ni kam hidaya mike da munki ne, a ce kwata kwata mutum baya son cin abinci, ko baki da lafiya ne,"
" lpy ta kalau mama,  dan nayi breakfast a makare ne , amma lafiya ta qalau, to shikenan, bedroom din ta ta nufa, kayan jikin ta ta cire ta shiga  toilet ta dan jima sannan ta fito jikinta daure da da towel, dressing mirror din dake dakin ta nufa simple make-up tayi sannan ta nufi wardrobe din dake kusa da dressing mirror din, gwon ta dauko ta atamfa da mayafi, shiryawa tayi cikin kayan Masha Allah dan bakaramin kyau kayan sukai ma fatar taba, da yake hidaya chocolate ce ita ba faraba sannan ita ba baka ba,  wayarta dake kan bed ta dauka da jaka wurin da takalmanta suke ta nufa É—an flat shoe ta dauko tasa , fice wa tayi daga dakin bedroom din ta nufi na mamar ta zaune ta same ta kan gado sallama tayi hadi da cewa" mama zan tafi gidan su maryam" mama tace " to shikenan sai kin dawo ina gaishe da hajiya lubabatu, sannan karfa kiyi yamma kinsan dai Baban ku yana gari, insha Allah mama bazan jima ba zan dawo, to saikin dawo fita tayi daga bedroom din hadi da ficewa , a bakin gate ta tsaya tana neman abun hawa bata jima ba ta samu napep shiga tayi sannan ta yima mai napep din kwatancen anguwar da zai kaita, tafiya sukayi mai dan nisa balaifi sannan suka iso wata anguwa  bakin gate din wani gida yayi parking me napep din fita tayi hadi da bashi kudinsa ya wuci ita kuma ta nufi gidan, mai gadi ta samu zaune akan É—an benchi, gaishe da shi tayi, ya amsa mata yana faÉ—in "yasu mama ku, suna lafiya da alama ya santa shiga tayi cikin gidan, part biyu ne gidan daya daga ciki part din ta nufa shiga tayi tai parlor gidan yake kamar ba kowa wani dan corridor ta nufa É—akuna ne kusan guda hudu ƙofofin su na kallon juna wanda, ke farko ta shiga bedroom ne mai kyau , bed ne sai wardrobe da toilet da dressing mirror, ba kowa dakin sai karar ruwa daga cikin bathroom alamar a kwai mutum a ciki wuri tasamu gefen bed din ta zauna batajima da zama ba sai ga maryam ta fito daga bathroom daure da towel " a she dai zaki zo maryam din ta fada , wlh kuwa , zan zo mana, ykk ya gida ya su mama, lpy qlu suke maryam ta fada hidaya tace " bakowa ne gidan sai ke kadai? "Â
" A'a suna nan , kawai dai suna É—aki ne, ok, naji shiru ne da na shigo , A'a suna nan bari dai nasa kaya dai" maryam ta fada haÉ—i da nufar wardrobe, kaya ta dauko riga da skirt na martial , shaf shaf ta shirya sannan ta dawo wurin hidaya ta zauna tana fadin " wai ni kam sister ya kuka kare da Victoria kinsan tun ranar da ku kayi fada da ita, bamu sake wata magana ba, ya kuka kare naga dr ya mai da ki wurin ta, kin kuwa san dadin da naji, domin nasan insha Allah burinki ya kusa cika" hidaya tace " bakomi , bamu sake wata magana da ita ba da sunan sa in sa ba, dan har roÆ™una su kayi ita da destiny akan na taya ta bama dr hakuri ya maida ta wurin ta, to ke saikika ce mata mi? Maryam ta fada ta na tsare ta da idanu , hidaya tace " mazan ce kuwa maryam, tun da ta roÆ™e ni mi zai hana, amma wallahi hidaya baki da hankali sai kawai kije kice ma dr dan Allah yayi ma Victoria hakuri koh, uhmmm ko dai yanzu kin haÆ™ura da shi ne baki son sa yanzu? Maryam ta jefa mata tambaya hidaya tace " wlh maryam bazan boye maki ba ina son dr har zuciyata, to amma shine zaki taya ta kuma kinsan cewa son shi take, dama kawai take jira ta raba shi da kowa , to ya zanyi maryam, komi tayi dan kanta tun da har ta roÆ™eni zan taya ta mana,maryam tace " uhmm sannu uwar masu tausayi tun da ta rokeki ai sai ki bashi haÆ™urin, wlh ke ba kisan wacece Victoria da destiny ba, su kan su muna funtar junan su suke yi inma baki sani ba to kisani ita kanta destiny din son dr take muna funtar Victoria kawai take, shiyyasa kike fadan haka ni da na daÉ—e dasu ni zan baki labarin ko su su waye garama tun wuri ki mai da hankalin ki a kan dr ki kyale wata Victoria da destiny chan , amma fa inkinji shawarata, dan wallahi kika tai make su, sai kinyi dana sannin haka, amma fa inkinji, shikenan ngd sosai da shawarar ki , amma sister sai nake ganin kamar dr bazai soni ba, kina ganin in ya shigo hospital duk matan dake hospital din bamu isheshi kallo ba, amma zan ciga ba da rokwan Allah in har shi alkairi ne a rayuwa ta Allah ya tabbatar man, to ameen, amma ya ka mata kisanar dashi cewa kina son sa, ko ba komai zai san ke masoyiyar sa ce, koya kike gani, zanyi kokarin haka insha Allah, amma gaskiya  ina tsoron abun da zai biyo baya karma ya zo ya da katar dani kamar yan da yayi ma Victoria , abun da bazan soba kenanÂ
Maryam c tace " to idan baki fada masa ba taya zai gane kina son shi , ki fada masa kawai insha Allah ba abun da zai biyo baya sai Alkairi kuma insha Allah zan taya ki da adu'a, smeen sister nagode sosai Allah ya barmu tare, ameen karki damu maryam ta fada chanza firar su kayi zuwa wata suna nan zaune har a kayi sallar asr , sallah suka tashi su kayi sannan suka fita daga dakin suka nufi parlorn gidan
Wannan kenan..........
✨ _Ammy_ ✨
Zaune take kan sallaya a bedroom dinta bata jima da gama yin sallah ba wayar ta da ke kan dressing mirror ce tayi ringing hannu tasa ta dauko wayar murmushi tayi hadi dacewa "Allah sarki mai babban suna ina jin ya kara so, daga wayar tayi hadi da Kara wayar a kunne sallama tayi da murmushi a fuskar ta, on the other hand na cikin wayar yace wa'alaikumus salam my Ammy ya gida, lafiya lau mai babban suna ya hanya, alhmdllh ammy  mun kusa sauka insha Allah , nan da Karfe 5:30 shiyyasa na kira ki fada ma ilya yazo ya dauke ni na kira Yaya bai dauka, may be baya kusane Ammy ta fada" to Ammy ki fada ma ilyan, yanzu kuwa Allah dai ya kawo ku lpy, ameen Ammy wlh harna ƙosa na ganni kusa da ke, Allah dai ya dawo da kai lafiya, ameen ya fada, kashe wayar tayi , mike wa tayi daga kan sallayar parlor ta fita kan sofa ta zauna , number ilya ta shiga nema cikin wayar ta sai ga fatima ta dawo daga Islamiyya wurin Ammyn ta nufo hadi da cewa " barka da gida Ammy, mikike yi zaune ke kadai s parlor? , ta fada yayin da take samun wuri kusa da Ammy ta zauna, amsa Ammy ta bata da "number ilya nake nema saboda zai dauko mai babban suna , ya noor ya dawo ne ta fada hadi da mikewa harzata nufi upstair Ammy tace " dawo uwar zumuɗi cewa nayi zai dauko shi bawai ya dawo ba" da wowa tayi tana turo baki gaba hadi da cewa "to Ammy ƙarfe nawa zai dawo , Ammy tace" ƙarfe 5:00 insha Allah jirgin su zai sauka, shiyyasa yace a kira mashi ilya yaje ya dauko sa;; Ammy dan Allah zanbi ilya inzai tafi, cewa Ammy tayi" to shikenan maza kije " bata ma tsaya sauraron mi Ammy zata ce ba ta nufi dakin ta da sauri, wanka ta fara shiga bata jima ba ta fito sanye da bathrobe shaf shaf tashirya cikin doguwar riga abaya tayi rolling da gyelen a kanta, wayar ta kawai da jaka ta dauka ta fice daga dakin inda tabar Ammy nan ta sa meta,  ƙara sowa fatima tayi wurin ta tana fadi" yawwa Ammy na shirya kinyi ma ilyan magana " A'a bari nayi sai kin shirya tukunnan , ai a kwai sauran lokaci, duka yanzu ƙarfe 4:00 kuma kinga cewa yayi sai 5:30 jirgin zai sauka
Ammy ai da kinyi mashi magana, kinsan fa a kwai nisa Airport din zamu yi kusan 20 to 30 minutes bamu kai ba fah kuma ga go slow" Ammy tace "haka  ne nasha'afa ne shiyyasa amma bari na kira ilyan ya fitar da mota sai ku tafi ta fada yayin da take kiran ilya a waya yana picking tace " ilya ka fitar da mota zakuje Airport kai da fatima domin dauko mai babban suna yana hanya, to Ammy insha Allah yanzu kuwa zan fito da ita ilya ya fada da yake shima Ammy yake cewa, to shikenan ga fatimar nan fito wa Ammy ta fada hadi da rejecting din kiran, mike wa Fatima tayi hadi da cema Ammy sai sun dawo a dawo lafiya Ammy tayi mata sannan ta tashi ta nufi , kitchen innah Asabe ta samu a kitchen din tana gyarashi domin fara shirye shiryen dinner , Innah asabe na ganin ammy tace " barka da fitowa hajiya, da yawwa Ammy ta amsa mata" kina bukatar wani abune ? Innah asabe ta fada saboda ganin Ammyn datayi a kitchen a wannan lokaci " eh kinsan mai babban suna na hanya to shine nake son a daura dinner tun yanzu , kuma shima shazim bai ci komai ba ya fita ga fatima ita ma kuma, kinga in aka gama da wuri zai fi ai, innah asabe tace"ah yaufa muna da babban bako,shiyyasa naga fatima ta wuce da gudu dan bata ma lura da niba Ammy tace" kinsan halin Fatima da zumuɗin, ai ina ce mata yana hanya duk tabi ta rude tana chan tabi ilya Airport, dariya Innah Asabe tayi hadi dacewa" Allah dai ya kawo shi lafiya, ameen Ammy tace shirye shiryen daura dinner suka shiga yi..
✨ _SHAZIM_ ✨
 shigowa yayi main parlor bakinsa dauke da sallama, da alama daga waje yake baya cikin gidan, su Ammy dake kitchen suka amsa mashi sallamar, fitowa Ammy tayi daga kitchen din tana cewa" kai ashe baka gidan, ka kuwa yi waya da ƙanin ka? ya ce man ya kira wayarka baka dauka ba "
" Eh na ɗan fita ne tun dazu har bedroom din ki nazo na same ki kina bacci, wayar na silent ne sai daga baya naga kiran sa, yace man ai kunyi waya akan kitura mashi ilya ya dauko shi, eh Ammy ta fada hadi da Komawa kitchen din shikuma part dinsa ya nufa,  bedroom dinsa ya wuce kayan jikin sa ya rage ya nufi toilet bayan kamar 15 minutes sai gashi ya fito sanye da bathrobe dressing mirror dinsa ya nufa hadi da zama kan stool din dake gaban mirror din, ya jima yana yan shafe shafensa sannan ya nufi wardrobe , shiryawa yayi cikin kana nun kaya riga da wando, wandon baki iyakar sa gwiwarsa sai rigar fara mara nauyi mai gajeran hannu, wurin dressing mirror ya koma feshe jikin sa yayi da turare sannan ya fita daga bedroom din ya nufi down stairs parlorn Ammy, dinning ya nufa yaga bakomi, fita yayi daga parlorn ya nufi kitchen wurin su Ammy yana shiga yace " Ammy akwai abinci, yunwa nake ji, gashi nan ana girkawa saura ka dan mukarsa Ammy tafada, gaskiya Ammy bazan iya jiraba sosai nake jin yunwar babu wani abu koda mara nauyi ne? Ya tambaya, Ammy ta ce" bari na yanka maka fruit ta fada hadi da bude fridge ta dauko fruit ta wanke yanka mashi tayi ƙanana ta zuba mashi a ɗan bowl ta mika mashi amsa yayi hadi da cewa " nagode sosai Ammy sannan ya fice daga kitchen din, main parlor ya koma TV ya kunna hadi da daukar remote yana chanza channel zuwa TVC news, zaman shi yayi kan sofa yana shan fruit tana kallo
Wannan kenan............
🌹~ _KAINAAT_ ~ 🌹
_MURTALA MUHAMMAD INTERNATIONALÂ AIRPORT
Mutane ne iri iri wasu najiran time din da zasu hau jirgi, wasu kuma sun zo daukar yan uwan sune, wasu na cikin mota wasu na zaune akan chairs din da aka ta nada domin masu zama.
Motar su fatima ce ta kara so cikin airport din parking lot din dake wurin ilya ya nufa parking yayi, fatima ce tabfara fitowa sannan shima ya fito, cikin airport din suka nufa inda mutane ke zaune fatima ta nufa, wuri ta samu ta zauna , wayar ta da ke cikin bag ce ta fara ringing fito da ita tayi "YA DR" shine sunnan daya bayyana akan screen din wayar, picking call din tayi hadi da sallama, on the other hand nacikin wayar ya amsa mata sallamar " ina wuni ya dr , ya gida ya kwana biyu, lafiya lau Alhmdllh Bintalo, turo baki Fatima tayi cikin shagwaba tace" haba Yaya nace fa bana son sunnan amma baka dai na ceman ba, ta fada tana dan bubuga kafafu, dariya na cikin wayar yayi, ai kuwa nan tashiga yi mashi kukan shagwaba tana cewa " dariya ma na baka koh"
"sorry fatimaaaaaa" ya fada hadi da jan sunan,
Uhmmm kawai tace,
sake mgn nacikin wayar yayi "bana ce kiyi hakuri ba, ai duk laifin kine kinsan fa nace kibar ceman ya dr nan da kika kware wurin kirana dashi, shiyyasa nima nace maki haka kinga nima na rama kenan, amma kiyi hakuri bazan sake ba kinji" "shikenan Yaya ya wuce"
"Yawwah koke fa, yasu Ammy kina ina ne haka naji hayaniyar mutane?
amsa ta bashi da " Ina airport , munzo daukar ya noor ne "
" ok yau zai dawo kenan, kice ina gaishe dashi ina mashi ya gajiyar tafiya "
" to zai ji Insha Allah yaya "
" ok take care of your self for me pls, bye" ya fada, itama " bye" tace masa hadi da rejecting call din, game ta shiga bugawa a wayar tana nan zaune aka fara sanar war iso war jirgin 5:30 tashi tayi ta koma inda mutane ke tsai tsaye domin tarbar yan uwan su passengers ne suka fara biyo wata kofa da aka rubuta EXIST da manya harafi wacce domin su aka tana de ta fatima dai na nan tsaye, mutane kuwa wanda suga yan uwan su nata rugawa da gudu suna tarbarsu, ita dai sai zare idanu take sokawai take taga ta ina ya noor din ta zai bullo. Wani matashin saurayi ne ya bullo jikin sa sanye da ƙananun kaya jeans and T -shirt na company gucci, jaka rataye a kafadar sa baka jikinta an rubuta ADIDAS da farin paint da manyan haruffa, hannun sa rike da trolley yana ja P-cap ce a kansa sai face mask akallah zai yi kimanin shekara 25 a duniya.
Fatima ce ta rugo da gudu tana fadin ya NOORRR tana nufar wannan saurayin, sakin trolley din dake hannun sa yayi fa dawa tayi jikinsa tana dariya hadi dacewa " shine kawani boye face dan nasha wahala wurin gane ka koh " janye ta yayi daga jikinsa yana cewa " Autar Ammy kedai haryau Allah baisa kinsan cewa kingirma ba koh, fatima tace " haba ya Noor haka ma za kace koh, shikenan tunda baka yi farin ciki da ganina ba " ta fada hadi da juyawa zata bar wurin, hannun ta ya riko yana cewa " sorry my yar qanwerh, wasa fa nake maki, kema kinsan nayi farin ciki da ganin ki autar mu " ya fada hadi da jan kumatunta tana dariya " koke fah " ya fada hadi da cire facemask din da yasa MASHA ALLAH nafada daganin wannan kyakyawar fuskar ta Noraiz kamannin sa daya da fatima , dan dai shi namijine ita kuma mace.
ilya ne yakaraso inda suke yana washe baki Noraiz yace " kice tare kike da ilya Ammy " ya fada yana mikama ilya hannu domin suyi musabaha.
ilya  yace " ina wuni, ya hanya, ya aka baro mutane turai " dariya fatima da Noraiz sukayi jin ilya yace wai ya aka baro mutanen turai, amsa mashi Noraiz yayi da " alhmdllh ilya ya gida " amsawa ilya yayi da " lafiya qlu " ilya yace hadi da daukar trolley din Noraiz suka bar wurin, parking lot suka nufa booth ilya ya bude ya saka trolley da jakar Noraiz, shiga sukayi cikin motar Noraiz da ilya naga ita kuma fatima na baya, key ilya yayi ma motar suka bar airport din, hanyar gida suka nufa suna tafe suna fira Noraiz ne yace " wai ina ya shazim fatima " amsa ta bashi da "may be yana gida , danni banjima da dawowa daga Islamiyya ba na biyo ilya"  "ok " kawai Noraiz yace yayin da suka iso anguwar su horn ilya yayi time dinda suka iso bakin gate din gidan, megadi ne ya bude masu gate din, ilya ya danna kan hancin motar ciki, parking lot ya nu fa parking yayi, fitowa su kayi daga motar suka nufi cikin gidan, ilya na biye da su a baya hannun sa dauke da trolley da bag din Noraiz.
Shiga sukayi cikin gidan bakin su dauke da sallama
Da sauri Noraiz ya nufi shazim dake zaune kan sofa, hugging din sa yayi hadi da cewa nayi missing din ka yy sosai
shafa kansa shazim yayi kamar wani karamin yaro yana cewa " to ai yanzu komai ya wuce tun da gaka nan ka dawo"
" haka ne kuwa yaya " Noraiz ya fada
Ammy ce ta fito daga kitchen ita da Innah Asabe wurin su suka nufa Ammy nace wa" oyoyo mai babban suna " tashi Noraiz yayi ya nufi Ammy hugging dinta yayi yana cewa " nayi kewar ki sosai Ammynah " nima nayi kewar ka mai babban suna " Ammy ta fada, Innah Asabe ce ta matso tana cewa " marhabun lale mai babban mutum, ya hanya, ya kuma karatu " Amsa ya bata da " alhmdllh " nan suka shiga firar yau she gamo, ilya haurawa yayi upstairs domin kaima Noraiz kayan sa part din sa, baijima ba ya sauko yana cema kayan na part dinka nakaima maka.
godiya Noraiz yayi mashi, ficewa ilya yayi ya koma bakin gate wurin mai gadi dama nan take zama.
Noraiz ne yatashi yana cewa " zanshiga na watsa ruwa na fito naga time din sallah magrib yakusa" ya fada yayi da yake haurawa upstairs.
Ammy c tace " shazim  abincin fa koba yanzu ba "
"A'a Ammy sai an jima in mun dawo sallar magrib sannan" to shikenan " Ammy ta fada , tashi yayi ya nufi upstairs shima
Ammy ma da Innah Asabe nasu bedroom din suka nufa aka bar fatima ta gyara kitchen da jera abinchi kan dinning (Â sbd bata sallah )Â tana gama wa itama ta nufi nata bedroom din wanka tashiga (Â dama tana yin wanka kusan sau hudu arana intana period )
✨ _NORAIZ_ ✨
Fitowa yayi daga bathroom sanye da bathrobe  ( part din sa shima ya hadu sai dai bai kai na shazim girma ba, amma dai masha Allah yayi kyau ) dressing mirror yanufa mai kawai yashafa ma jikin sa yanufi clothes set dinsa jallabiya ya dauko black color yasa wurin kayan sa da ilya ya kawo masa ya nufa, turare ya dauko cikin jakar sa ya fesa gadi da mai dashi
Ficewa yayi daga part din dama yayi alwala tun a toilet , part din shazim ya nufa dake kusa da nashi
yana shiga shazim din na fitowa daga bedroom din shima sanye ya keda jallabiya
Ficewa kawai sukayi suka nufi masallachin dake chan main gate din gdn basune suka dawo cikin gidan ba sai da su kayi har isha tukun suka dawo cikin gdn
parlorn Ammy suka yada zango fatima kadai suka samu zaune a parlorn suna zama sai ga Ammy ta fito wuri ta samu ta zauna tana cewa " to a tashi ga abinci chana najira " to suka cemata hadi da nufar dinning din Fatima ce tayi serving din su.......
✨ _KATSINA_ ✨
Zaune suke kan dinning suna dinner su duka gidan baka jin komai sai karar plate da spoon
Suna gamawa abie da abdallah da Mom suka koma kan sofa yayin da su Aairah ke gyara dinning din, suna gamawa wurin su abie suka dawo suka zauna fira suka shiga yi abie na tambayar su yaushe zasu fara exam din SSCE " saura 3 weeks abie " suka bashi amsa " to Allah ya bada sa'a, da Ameen suka amsa " abie wace school zaka kaimu in mungama " Aaimah ta tambaye shi" ban gane inda zan kai kuba , kuda kuke da school a cikin grinku, a i ba sai kunje wani gari ba " abie ya fada yana tsare su da idanu " A'a gaskiya abie Muyi primary school da secondary school a nan sannan kuma ace munyi high school a nan gaskiya abie s chanza mana " to sai dai kunga ma exam din tukunnan, to shikenan abei " chanza firar sukayi zuwa wata, sai kusan 9:30 sannan su Aairah suka nufi dakinsu sbd sun fara karatun exam gakuma zuwa school gobe
Suna shiga bedroom din su wanka sukayi hadi da sanya pajamas dinsu sannan suka dauki books dinsu suna dubawa sai wurin 12:00 sannan sukayi bacci.......
Episode 9_10
Sanye suke da uniform din su na school, ko wacce rataye da school bag din ta, ficewa su kayi daga bedroom din suka nufi main parlor su Mom suka samu kan dinning suma basu jima da zuwa dinning area ba, gaishe dasu su kayi hadi da samun wuri kan dinning din suka zauna, abie ne yace " yau yan biyu an shirya dawuri kenan " amsa suka bashi da " eh abie "
"to Allah ya taimaka ya ba da sa'a"
da ameen suka amsa, mom ta miko masu tea da ta hada masu " thanks Mom" suka fada hadi da sa hannu suka Karba, basu fi minti 10 ba suka tashi suna goge bakin su da tissue paper suna fadin sai mun dawo , a dawo lpy su mom suka yi masu fice wa su kayi suna fadin Allah yasa.
Suna fita daga gidan sai ga school bus dinsu ta shigo anguwar, sai da ta kawo dai dai inda suke tayi parking, kofar bus dince ta bude shiga su kayi daga ciki suka nemi wuri suka zauna kusa da wannan friend din ta su Aeesha
Aeesha tace "twin friends yau wace rana kun fito da wuri kun hau bus first round " ta fada da murmushi a fuskar ta " kedai bari kawai Aeesha sa'a ce kawi yau " Aairah tafada yayin da Aaimah ke cewa " sai kace kema kullum da wuri kike zuwa Aeesha " dariya Aeeshar tayi hadi da cewa " ai wlh duk da haka gara ni dai "
"bawani nan, wlh kema muguwar let comer ce " Aaimah tafa da yayin da bus din keshiga cikin School
bus stop, bus din tanu fa parking tayi aka bude kofar student nata fita suna nufar assembly ground
Inda ss 3 ke tsayawa nan su Aairah suka nufa annan suka samu sauran yan class din su wanda suka zo dawuri, gaisawa suka shiga yi.
bayan 30 minutes aka gama assembly kowa ya nufi class din su
✨SHAZIM✨
Saukowa suke daga upstairs shi da Noraiz parlor Ammy suka nufa, kan dinning suka same ta , gaishe da ita su kayi Noraiz yace " ammy ina fatima nagan ki ke kadai kan dinning? " amsa ta bashi da " Fatima ai ta wuce school"
" kai na manta fah, amma Ammy yau she take gama wa ne "
" tace man dai next month zasu fara exam, daga wannan week din ma ta gama zuwa school sai kuma exam "
" Allah ya taimaka ya bada sa'a, yaya " Noraiz ya kira Shazim dake zaune yana sauraron su, da na'am ya amsa mashi , Noraiz yace " amma dai yaya fatima a abuja zatayi  university kamar yanda take bukata intagama secondary school "sai da yayi kusan 5 seconds sannan yace "A'a nan za tayi school din ta gata ga ammy, " ya fada fuskar sa babu a lamun wasa, hankan yasa dole Noraiz ya kama bakin sa yayi shiru amma baiji dadin shawarar da yayan nasu ya yanke ba, saboda fatima ta ƙwallafa rai akan zuwa abuja saboda sa'ada , " Allah ya taimaka " kawai yace yaci gaba da breakfast din sa, Ammy duk da ta fison fatimar tayi karatu kusa da ita.amma sai tace "wai shazim mi yasa kake haka ne, tun da kai ka janye jiki da abuja, mi yasa suma zaka sa dole sai sun janye jiki da abuja ne wai, miye ai bun dan tayi karatu a can, duk ni ma nafi son tayi kusa da ni" ɗan nisawa yayi sannan yace "ammy ni ba haka nake nufi ba, kwai naga zaki yi kaɗai ci ne, ke kaɗai a gida "katse shi ammy tayi da cewa "in dai dan ta nine karka hanata zuwa abuja, idan bata nan baga ku nan ba kai da noraiz "
"ammy mu ba zama muke ba, idan muka fita tun safe sai dare fa muke da wowa"
"to naji sai dare kuke da wowa, itama idan ta je makaranta ba sai da yamma zata riƙa dawowa ba? " ta ƙarasa faɗa da sigar tambaya tana tsare shi da idanu
"ammy dan Allah kiyi haƙuri tayi karatun ta nan, itama sai ta fi jin daɗi karatun, chan haya niyar innah kawai ta ishe ta " uhmm kawai ammay tace ba tare da ta sake cewa komi ba ,
Ba wanda ya sake magana cikin su har suka kammala breakfast din , shazim ne ya fara ajiye fork din da yake cin arish hannu ya mika ya yagi tissue din dake kan dinning ya goge bakinsa sannan ya dauki robar ruwa ya sha, ya mike ya nufi sofar da ya ajiye briefcase dinsa ya na fadin "Ammy nizan wuce" cup din tea din da ta kai baki ta janye tana fadin " a dawo lafiya , Allah ya ba da sa'a, an jima ka dan zanje gidan baba may be baza ka same ni sanda zaka dawo, dan zanjima kilama sai dare ma zan dawo "
" ameen, ina gaishe da malam, sai na dawo" ya fada yayin da yake shirin barin parlorn, Noraiz yace " a dawo lafiya Yaya, Idan na ajiye ammy gidan malam zan biyu ta wurin ka insha Allah "
" Allah ya kawo ka lafiya " kawai ya fada hadi da ficewa, parking lot ya nufa motarsa wacce yasa aka wanke masa ya nufa, bude kofar motar yayi briefcase din sa ya aje da lab coat, sannan ya zagaya driver seat ya zauna , key yayima motar ya nufi main gate , gaisawa yayi da ma'aikatan gidan sannan ya fice daman mai gadi yariga da ya bude masa gate,eko ya nufa yana tafiya yana sauraron karatun alqur'ani a motar....
✨HIDAYA✨
Tsaye take gefen titin anguwar su tana jiran abun hawa, kusan 5 minutes tana nan bata samu abun hawa bata samu ba, wata bakar motace ta shigo anguwar tasu, tunda motar ta shigo anguwar tasu take ma motar kallon kamar tasan mamalakinta, motar na ƙarasowa kusa da ita tana rage gudu, kallon motar kawai take sai da ta kawo dab da ita sannan aranta tace" wannan ai kamar motar dr kabir " parking motar a kayi hadi da sauke glass din motar, kyakyawan saurayine fari amma ba sosai chan ba, akallah zai yi kima nin shekara 28 zuwa 30, sanye yake da blue din kaya complete riga da wando sannan fuskar sa sanye take da glass, hidaya tace" ina kwana dr" amsa mata yayi da " lafiya lau , mikike yi tsaye anan " hidaya tace " ina jiran abun hawa ne dr" ok yace sannan kuma ysake cewa " to shigo ciki mu wuce "
" A'a dr katafi kawai zan samu abun hawa insha Allah " hidaya ta fada, glass din dake fuskar shi ya cire hadi da cewa " to fah, hidaya ko dai kina tsoron na sayar dake ne iye " murmushi tayi hadi da cewa " A'a ba haka bane "
ajiyar zuciya ya sauke hadi da cewa " to inhar ba haka bane, to kishiga mu wuce " to kawai tace hadi da zagayawa ta shiga ciki, key yayima motar yana cewa " wlh kina bani mamaki hidaya, sai kace wata ƙara mar yarinya in ki ka yi wani abun " murmushi kawai tayi masa ba tare da tace komai ba, haka sukai ta tafiya yana janta da fira har suka iso eko , parking lot din asibitin ya nufa hadi dayin parking, har tasa hannu zata bude kofa ya da katar da ita yana cewa " wai hidaya tsorona ki keji ne, naga har wani sauri kike ki fita"
"A'a " kawai tace hadi da duƙar da kanta ƙasa, " shikenan bakomi kina iya tafiya "ya fada ficewa tayi daga motar shikuma ya tsaya tatara kayan sa dake back seat, tana fitowa motar shazim na parking, dr kabir ne ya fito hannun sa riƙe da tarkacen sa yana cema hidaya su tafi , tafiya suke sunkusa kawo inda motar shazim take sai gashi ya fito,miƙa masa hannu dr kabir yayi sukayi musabaha,  hidaya ta gaishe da shi, da lpy kawai ya amsa mata , wuce wa tayi tabar su shi da dr kabir tayi cikin asibitin, office din su da nurses kezama ta nufa, ba kowa ciki sai friend ɗin ta maryam da alama wadan da suka zo duk sun fita.
" lafiya yau ki ka yi late ? " maryam ta tambaya , ƙarasowa inda take hidaya tayi tana cewa "ke dai bari, banyi bacci bane jiya dawuri shiyyasa nayi late" dafa kafadar ta maryam tayi tana cewa " kingama yanke shawara yan da zaki tunkari dr da maganar koh "
" a'a gaskiya, maryam ina jin tsoro ne, ban san ya dr zai dauki maganar tawa ba " hannun hidaya maryam taja suka zauna sannan tace " ki kwantar da hankalin ki hidaya Insha Allah alkairi ne zai biyo baya, kinji" ajiyar zuciya hidaya ta sauke tana cewa " to Allah yasa haka maryam " da ameen maryam ta amsa mata hadi da cewa " tashi mufita" ta fada tana jan hannun hidaya, fice wa su kayi suka nufi inda yan uwansu nurses suke, gaishe da junan su suka shigayi , office din dr Shazim hidaya ta nufa tana cema maryam " sister bari naje office din dr na dawo"
"ok sai kin dawo " maryam ta fada, office din hidaya ta nufa hadi da tura kufar ta shiga bakinta ɗauke da sallama.
amsa mata sallamar yayi, sannan tace "dr asa patient a layi " amsa ya bata da" eh " har zata fice sai kuma ta dawo sai da tayi 2_3 seconds sannan dai ta daure tace" afuwan dr dama ina so ne Muyi wata mgn " ɗago kansa yayi daga aikin da yake ya tsare ta da idanu alamar ina sauraronki, magana ta fara " dama dr maganar Victoria ce " daga mata hannu yayi alamar ya isa haka " ya zama na ƙarshe da zaki ƙara man maganar ta  a nan, in ba haka ba kema zaki bita , fatan kingane "
" ok sir insha bazan sake ba " ta fada hadi da ficewa daga   office din , direct wurin patient ta wuce, ta shiga aikin ta , a haka Victoria da destiny suka same ta, wuri suka samu suka zauna kusa da ita , gaisawa su kayi sannan Victoria tace " hidaya ya maganar mu ne" ajiyar zuciya hidaya tayi sannan tace " gsky kiyi haÆ™uri Victoria, ko yanzu daga wurin dr nake nayi nayi ya haÆ™uri amma yaki, dan har cewa yayi kona daina masa magnar ki ko nima ya koreni " wani kallon banza Victoria tayi mata sannan ta ce " munafukar banza, wannan nasan duk shirin kine, to kisani kamar yanda kika rabani da dr nima sai na rabaki dashi " mikewa hidaya tayi tana cewa" kije kiyi duk abun da za kiyi Victoria, tun da ke baki da mutunci " fada sosai ya kaure tsakanin su har Victoria na neman kaima hidaya duka, destiny na jenye ta,  su maryam ne suka zo wurin saboda hayaniyar Victoria data jawo hankalin su, nan suka shiga cewa gsky baki da mutunci Victoria, komawa Victoria tayi kansu tana ce masu munafukai tasan ai da hadin bakin su, ai kuwa abun yayi masu zafi nan suka shiga maida mata da martani,Â
Hayaniya ce ta damesa harta na neman haddasa masa ciwan kai hakan tasa shi dole ajiye abun da yake yi, telephone ï¸ din dake office din ya dauka, dialing numbers yayi ana picking call din yace kasa meni a office dina yana gama fada yayi rejecting kiran bayan 30 seconds sai gashi anturo kofar, wani security ne ya shigo gaishe da shazim yayi hadi da cewa dr gani " wai hayaniyar mi nake ji ne" afuwan dr bari naje na duba " ok kawai yace masa, fita security yayi inda su Victoria suke ya nufa nan ya same su har lokacin basu dai na fadan da suke, hidaya sai kuka take saboda a rayuwarta ta tsani fitina, su maryam ne ke maida ma Victoria martanin, É—aya daga cikin nurses É—in mata security ya tambaya  mike faruwa amsa ta bashi " zuwana kenan na same su suna hayaniya sai dai ban san miye maÆ™asudun faÉ—an na su ba "
" to shikenan " shine kawai abun da security ya faɗa ya komawa office ɗin shazim ya sanar dashi cewa " sir su nurse Victoria ne ke hayaniya, ina jin dai wani abun ne ya ha dasu "
"Mutsww"shazim yaja tsaki a ranshi yace "nonsense kawai dasu, zasu wani tada ma mutane hankali , sakarkaru banza "
achan kuwa waje dr kabir ne ya fito daga office ɗinsa ya nufi inda su Victoria suke shima hayaniyar su ce ta dame shi, yana isowa wurin dukan su su kayi shiru tsaki yaja hadi da cewa" wlh kunbani mamaki matuƙa , ashe bakuda hankali " ya fada hadi danuna hidaya ya nace wa " wacece nan , mi kuma akayi mata take kuka" da yake duƙe take shiyyasa bai gane ko wacece ba, maryam tace "dr hidaya ce" matsowa yayi kusa da ita yana fadi "mike da munta ne " amsa maryam ta bashi da cewa " Victoria ce ke ci mata mutunci ita kuma bata iya ramawa shine take kuka, mukuma " hannu ya daga ma maryam hadi da cewa "ya isa haka, oya tashi " yace ma hidaya, mikewa tayi fuskar nan duk tayi sharkaf da hawaye "wuce muje" yace, binsa tayi a baya har office ɗinsa , toilet ya nuna mata " shiga ki wanke fuskar ki " shiga tayi ta wanke fuskarta sannan ta fito
wuri ya nuna mata kan sofa da ke cikin office din
 zama tayi tana  sauke ajiyar zuciya
ita bakomai yafi bata haushi ba wai a ce daga taimako Victoria zatayi mata haka, gyaran murya dr kabir yayi haɗi da zama kan sofar yana fuskantar hidaya yace " hidaya nasan wannan ba halinki bane miyasa kike biye ma mutane irin waɗanna, ke da ita bafa ɗaya bane al'adar ku ba ɗaya ba kwata kwata ita batasan kunya ba saboda ba'a koya mata ba amma ke duk wanda ya ganki zai yimaki kallon wacce bata san mutuncin kanta ba, pls hidaya karki sake"
" insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba nagode "
" bakomai karki damu tashi ki tafi kicigaba da abun da kike yi "
" ok" ta faɗa hadi da mikewa ta fice, wurin patient ta koma ta cigaba da turama dr su.
✨noraiz✨
Parlorn ammy ya shigo jikinsa sanye da kananu kaya farar riga da bakin wando, yana shigowa Ammy na fitowa daga bedroom dinta sanye take da hijab har kasa, Noraiz yace " yawwa Ammy harkin shirya kenan " "eh" Ammy ta fada, ficewa su kayi, parking lot suka nufa wurin wata bakar mota rang rover suka nufa Noraiz ne ya bude mata kofa sannan ya zagaya driver seat ya zauna hadi da yima motar key ya nufi main gate, megadi ne ya tashi ya bude masu gate gaishe da Ammy mai gadin yayi amsa mashi tayi cikin kulawa sannan Noraiz yayima motar key suka fice
tafiya su kayi sosai sannan suka sha kwanar wani road mikewa suyi sosai sannan suka tsaya abakin wani gida horn Noraiz yayi abakin gate din gidan.
ƙofar dake jikin gate din gidan aka bude wani mutum ne ya leko yana ganin motar Noraiz ya koma da sauri
gate din gidan aka bude ciki Noraiz ya danna hancin motar ciki, parking lot din dake gidan Noraiz ya nufa hadi da yin parking, fitowa su kayi shi da Ammy suka wuce cikin gidan
👨â€âš•ï¸ Doctor Shazim👨â€âš•ï¸
  Â
Daga alƙalamin
KHADIJA ( M ) ABDULWAHAB
KAINAAT... âœÂ
*_KING AND QUEEN WRITING CHAMBER_*
Proud to my first novel
Ina alfahari da kasan cewar wannan littafi na farko agareni 📚Â
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ma É—aukakin sarki mai kowa mai komi da ya bani ikwan rubuta wannan littafi.
Ya ubangiji al'arshe kabani ikwan rubuta abin da zai amfani muslinci da muslmai, ka bani ikwan rubuta abun da zai amfaneni duniya da lahira ðŸ™
âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸ âœ–ï¸
Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na littafin  nan ba ta kowace hanya, ba tare da an nemi izni a wurina ba.
idan kunne ya ji jiki ya tsira!
Wannan labari Æ™agegen ne ,sannan ban rubuta shi ba da niyyar muzanta wani ko cin mutuncin wani ba, duk  wanda ya ga wani abu yayi shige da halayyar shi arashi ne.Â
Season one
Free
Episode 1_2
🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥
_Ø¨ÙØ³Ù’م٠اللَّه٠الرَّØÙ’مَٰن٠الرَّØÙيمÙ_
12 June 2003
_Ƙarfe 12:30 Am
Yanayin sanyin da gari yayi, da iskar da ke kaÉ—awa wanda ya haddasa ganyayyakin bishiyu yin rangaji, tare da ba da wata sassanyar iska.
Yadda sauran ruwan saman da ƙasa bata gama shanyewa ba, da wanda yake gudu acikin kwalbatoci zai tabattar maka da lallai damuna ta kama.
Shiru anguwar take sai kace ba kowa a cikin ta saboda yanayi na dare haɗi da damuna, duk da daman ba'a cika samun mutane na kai kawo a cikin irin waɗannan anguwannin ba ko da kuwa da rana ne, sai hasken bulbs daya haske anguwar haɗe dana street lamps kaɗai ake gani.
Anguwace irin ta masu faɗa aji a cikin ƙasa, domin kuwa daga shahararrun yan kasuwa sai manya a gwamnati ke a cikin ta.
Motace ta shararo da gudu daga kwanar dake hannun dama a cikin anguwar, yayin da wasu ba ƙaƙen motoci guda huɗu ke biye da ita.
Gudu motar take sosai har ta fita daga cikin anguwar ta hau babban titi, still wa É—annan moticin na biye da ita a baya
Daga irin gudun da mamallakin motar ke yi zaka san cewa yana gudu ne tsakanin rayuwa da mutuwa.
ta mirror É—in motar yake hangen fitilar motocin da ke binsa,
yana gudu motocin na bin sa har suka hau kan titin da zai fitar da kai daga garin, gudu suke har suka fita daga garin,
in ban da salati da neman É—auki daga ubangiji babu abun da mai motar nan ke yi.
domun shi a yau ya san tashi taƙare, saboda ya galabaita a dalilin dukan daya sha, tukin neman ga garar sa yake, ƙarfinsa ya kusa ƙarewa, dubawa yayi ta cikin mirror motar amma bai ga alamun waɗannan motocin ba, tunani ya fara to ko ya tsre masu ne, amma duk da haka bai fasa gudun da yake ba, wani mummunan Bugun da yaji an kaima ma motar shi ne yasa shi fahimtar ce wa kenan wata hanyar suka bi amma suna biye da shi mirror ɗin motar ya kalla, amma sai yaga ba waɗan cen motocin ba ne, wata ƙatuwa truck ce ke binsa yanzu saɓanin waɗancen motocin, ba shiri ya karya kwana ya faɗa cikin daji, gudu kawai yake amma ba wai ya san inda yake dosa ba ne, tsintar kansa kawai yayi a bakin wani ƙaton rami mai zurfin gaske, dole tasa shi taka birki ba dan ya shirya ma hakan ba sai dan baya da wani zaɓi, kawai ya sadakat kwanan shi a yau sun ƙare.
bai gama wannan tunanin ba yaji me truck É—in ya kaima motar shi wani mumunan bugu wanda ya haddasa mashi buguwar kai nan take ya suma.
Sake ja da baya me truck É—in yayi ya kaima motar wani bugun wanda yafi na É—azun, nan take motar tayi cikin ramin, ko karar faÉ—awar ta ba'a ji saboda tsananin zurfi irin na ramin .
parking me truck ɗin yayi a bakin ramin tare da leƙa ramin ta hanyar hasken motarshi daya bari a kunne.
wani irin ramine me zurfin gaske, wanda tsananin zurfin shi zai sa ka kasa ganin abunda ke ƙasan ramin.
dariya yayi me sauti da amo tare da cewa yanzu kam nasan zan samu cikwan kuÉ—ina domin wannan sai dai uwar shi ta haifi wani amma ba dai shi ba.
komawa yayi cikin motar shi, anan yasamu wayar shi na ringing ɗaukar wayar yayi
boss shine sunan daya bayyana a jikin screen ɗin wayar, picking call ɗin yayi tare da sa wayar a handspree tun kafin yace wani abu me kiran nashi yace " Ina fatan kagama dashi? "
answer ya bama boss ɗin da cewa " ai wannan tashi ta ƙare sai dai uwar shi ta haifi wani amma ba dai shi ba, dan a yanzu yana can ya gana da magabatan sa"
"amma naji daɗin jin haka" boss  ɗin ya faɗa .
"amma boss ya kake ganin za'ayi da matar shi da yaran shi ?" me truck É—in ya tambaya.
"Kar ka damu da wannan big boss.  zaiji da komai , yanzu dai katuraman da account number ka domin natura maka Sauran kuɗin aikin ka "
"thank you so much boss" me truck É—in ya faÉ—a. boss É—in ya ce
"don mind" Kit ya kashe wayar
account number ya turama boss tare da yima motar key ya bar wajen
WANNAN KENNAN.
🌹~ _Kainaat_ ~ 🌹
Gida ne matsa kaici shi ba ƙarami ba shi kuma ba babba ba chan sosai ɗan dai dai.
gida ne namasu rufin a siri kuma yan boko naji da faÉ—a.
Painting É—in gidan ya kasance white and blue color ne, haka ma get É—in gidan blue and white ne.
daka shiga compound ɗin gidan zaka fara cin karo da ɗakin mai gadi daga hannun hagu Sai parking lot daga hannun dama wanda ke ɗauke da rides masu kyen gaske da tsada na fashion a ƙallah za su kai guda 5 a parking lot ɗin.
Sai garden mai kyen gaske ga suke suke masu É—aukar hankali.
Sai boys quarters dake bayan part É—in masu gidan.
Masha Allah na furta a ya yin da nayi arba da parlorn gidan wanda aka ƙawata shi da furniture's masu kyen gaske da tsada, komai na cikin parlor onion and pitch color ne, daga gefen daman parlor twin up stairs ne me kyau
Sai kitchen dake gefan hagu wanda yake haÉ—e da store kusa da shi kuma dining area ne mai É—auke da chairs guda 7,Sai wani É—an corridor daga gabas É—in parlor mai É—auke da 4 bedrooms, daga chan kuma up stairs É—in ya kasu kashi 3,part É—in matar gidan dake haÉ—e dana yaranta ke hannun hagu Sai na me gidan dake hannun dama sai chan gaba na yaron gidan ne namiji. daga part É—in dake hannun hagu naji anata kwala Kiran Aaimah! Aairah!! Aairah!!!.
Wata kyakyawar mace ce tafito daga ɗaya daga cikin bedroom ɗin ta nufi wanda ke kallon nata ta na cigaba da Kiran
" Aaimah " da "Aairah".
Fara ce sosai tana da jiki ba sosai ba ita ba rammama ba Ita ba mai ƙiba ba a kalla zata kai kimanin shekara 50 . jikin ta sanye yake da sleeping dress riga da wando masu santsi yana yi da Pakistan dress pink color. ba ƙaramin kyau suka yima surar jikinta ba.
"Kun kuwa san ƙarfe nawa" ta faɗa yayin da take tura ƙufar bedroom ɗin ta shiga.
Masha Allah na faÉ—a domin kuwa bedroom ne me kyan gaske, komai na cikin sa ya kasan ce pink and white color ne , yaji kaya masu kyan gaske bawai cike yake da kaya ba.
bed ne sai bed side drawers, sai dressing mirror gefen shi kuwa wardrobe ne wanda clothes set ne ciki sai jikin ƙofar shigowa kuma jere suke da ƙofar bathroom sai wani ɗan corridor inda ya kasan ce laundry basket ne da shoe rag ne sai bag hanger , bags ne masu kyau na gayu dana school kowace bag set biyu ce kuma color ɗaya.
turus ta tsaya ganin ta kwance har yanzu akan bed, " Aairah lafiya kike kuwa da baki tashi ba ina Aaimah take Ita ma, ko yau baku zuwah school ne iye. "
Ƙarar buɗe ƙofar bathroom taji juyawa tayi, wata kyakyawar budurwa ce ke tsaye jikinta ɗaure da towel iya gwiwarta jikin ta sai raɓar ruwa yake, alamar wanka tayi, fara ce Ita ma kamar mahaifiyar ta tana da dogon gashi har ƙugunta, ga matsakai tan idanu masu ɗauke da brown eyeball da zara zaran eyelashes, hancinta ma ɗan dai dai dogon bamai yawa ba sosai, ga small mouth me ɗauke da pink lips, tana da shape mai ɗaukar hankali sannan tana da tsayi amma ba sosai ba chan. masha Allah kawai zamuce, akalla zatai kimanin shekara 18 a duniya.
"Ok kintashi kenan Aaimah ce kenan bata tashiba."
"Wallahi mom tunɗazu nake tashin ta amma taki tashi wai Ita batagaji da bacci ba."
"Tafi ke ki shirya, rabu da Ita yanzu ai zata tashi ba dan halinta ba " mom ta faɗa a lokacin da ta ƙarasa jikin bed ɗin , "Aaimah! Aaimah!! wake up, its time for school , ko kina sone kuyi late ne iye autar mom . "
"Uhm uhm uhm haba mom wai miyasa kike cema Aaimah auta nifa" Aairah tafaɗa yayin da take buga ƙafa tan turo baki haɗe da rike ƙugu.
ai kuwa nan Aaimah ta tashi tana ma Aairah dariya harda gwalo, dama duk abunda mom ke faÉ—a tana ji, tashi ne kawai bata yi ba
"mom kinganta ko dariya take man harda gwalo"Aairah ta faɗa sai wani turo baki take da hura hanci. "Ke da'alla rabu da Ita, ai kema autah ce"
mom ta faɗa tana dariya ganin yarda Aairah kema Aaimah dariya harda tsalle, "oho dai ai ni aka fara cemawa" mom ta katse ta da cewa
" To ya isa haka maza kushirya
ABIE na nan yayi shirin tafiya , kunsan dai yau zai koma wurin aiki abuja."
"to shikenan mom gamu nan zuwa" har suna haÉ—a baki wurin faÉ—in haka.
fita Mom tayi daga bedroom ɗin haɗe da jawo masu ƙofa, ta shi Aaimah ta yi ta nufi bathroom tana faɗin my twin sister dan Allah kifito man da uniform ɗina kafin na fito"Aairah ta ce " to sannu mom kinji koh"
"haba twin sister dan Allah fa nace" Aaimah ta faÉ—a tana lan gwabar da kai , Aairah ta ce " hmmm sai shegen daÉ—in baki kamar ta Allah"
" Pls twinee" Aaimah tasake faÉ—a
"shikenan ba dan halinki ba"Aairah ta faɗa tana ya tsine fuska,murmushi Aaimah tayi tana faɗin "yawwa twenny Ni na san nafi kowa Sa'ar Yar uwa a duniya shiyyasa nake alfahari dake baki sani ba fah irin daɗin da nake ji Idan naganki kusa dani ba" , baki kawai Aairah ta saki tana sauraron ƙar yar da Aaimah ke shirga mata. "wallahi Aaimah kin bani ki rinƙa jin tsoron Allah , ko kunyar ƙarya ba kyaji " gwalo Aaimah tayi hadi da jawo ƙofar bathroom ta shige, dariya kawai Aairah tayi haɗi da girgiza kai tana faɗin " Allah ya shirya ki Aaimah da karya"
wurin dressing mirror ta wuce Vaseline É—in dove ta shafa tare da farar powder kaÉ—an ta shafa a fuskar ta sai kwalli da tasa ma eye's É—in ta, wurin wardrobe É—in su ta wuce buÉ—ewa tayi , kaya ne masu yawan gaske komai set biyune, wurinda hijaban su suke daban haka ma sleeping dress É—insu da ban suma dogayen riguna da atamfofi wurinsu suma da ban haka ma uniform É—in su na school dana Islamiyya,
uniform É—in school ta É—ako masu set biyu itada Aaimah wurin bed É—in su ta koma da kayan a hannun ta domin ta shirya.
shaf shaf ta shirya cikin uniform É—in ta masu É—an karan kyau, riga ce da skirt, rigar white color ce, skirt É—in wanda ya kasance iyakarsa gwiwarta pink color sai sock's fara me ratsin pink daga sama sai top wacce itama ta kasan ce pink color sai Yar baby hijab it kuma white color ce, wurin corridor É—in su ta nufa shoe da school bags É—in su ta É—auko masu, white color ne takalman snikers sai school bag pink color.
"Sis kin É—auko man nima uniform É—in" Aaimah ta faÉ—a wacce fitowar ta kenan daga bathroom. amsa Aairah ta bata da "Eh Amma fa kiyi sauri ki shirya kona tafi wurin Abie na barki" wurin dressing mirror Aaimah ta nufa tana faÉ—in" sorry karki damu yanzu zan shirya ki bani 5 minute insha Allah " shaf shaf itama ta shirya cikin nata uniform É—in Masha Allah
Itama ba ƙaramin kyau tayi ba saboda itama Aaimah kykyawa ce sosai a bun da kawai Aairah zata nuna mata tsayine shima ba wani finta tayi ba sosai ka mannin su ɗaya da Aairah tsayinne dai kawai banbancin su shima sai insun jera zaka fahimci hakan.
Snickers É—in ta itama ta saka tare da amsar bag É—inta dake hannun Aairah
a tare suka fita daga bedroom ɗin direct part ɗin Abie suka nufa, hannun su cikin na juna suka shiga parlor ne mai matuƙar kyau, dan yafi na down stairs kyau da haɗuwa domin ya ƙawatu da expensive furniture's, komai na cikin parlorn sky blue ne da fari.
wani kykyawan matshin tsohone wanda Akallah zaikai ki manin shekara 60 a duniya, yana da haske shima sosai, zaune yake akan 2 siter
" abie " kenan
tea yake sha wanda mom ta haɗa mashi, sallama sukayi tare da ƙarasawa ciki suna faɗin "abie ina Kwana antashi Lafiya "suka faɗa yayin da suke samun wuri kusa da abie suka zauna,
"lafiya lau alhmdllh my daughters ina fatan kuma kuntashi lafiya" "Alhmdllh abie " suka faÉ—a, Abie ya ce
"to Masha Allah haka ake so"
"amma Abie zaka tafi yau shine baza ka yi breakfast damu ba" Aaimah ta faÉ—a tana turo baki
"Sorry my daughters duk da ma laifin kune tunda tun É—azu ya kama ta ace kuntashi amma kuka yita bacci gashi ni kuma sauri nake, ai daya ke bajima wa zanyiba wannan time É—in, zandawo very soon kunji koh."
"shikenan abie Allah ya dawo da kai lafiya"da ameen abie ya amsa tare da kai cup É—in tea bakin sa.
"to uwayen surutu atashi aje ayi breakfast time na kurewa, abar shima abie ya samu ya gama nashi breakfast ɗin karya makara "mom ce ke magana wacce fitowar ta kenan daga bedroom ɗin abie hannun ta riƙe da jakar kayan shi da zaiyi tafiya da Ita
"Uhmmmmm haba mom dan Allah kibari muƙara sa yin ban kwana mana" Aairah ta faɗa tana turo baki, dariya kawai Abie ke masu
"Kinci gidan ku nace kutashi kuyi breakfast yana chan baba larai tashirya maku, nima abarni nayi ban kwana da mijina"
"ah mom sai kice mutashi soyayya ta motsa, to bari muyi ta kanmu," Aairah ta faÉ—a tareda yin dariya
"Kunci gidan ku jairan banza marasa kunya kawai "abie ne ya faɗa tare da yi masu daƙƙu wa
dariya suka kwashe da Ita, " abari muga soyayya tukunnan sai mu tafi" Aaimah ta faɗa hadi da gyara zaman ta, wurin su mom ta nufo ai bashiri suka mike da gudu suka fita daga part ɗin suna dariya.......
"Kaga man jairan yara marasa kunya"mom ta faɗa yayin da take zama kan hannun sofa da abie ke zaune, dariya abie yayi tare da cewa "Allah ya shirya, dan inkika biye ma su Aairah sai su samaki ciwan kai" "wallahi kuwa ai abdallah ne kawai maganin su, yama shigo kuwa" mom ta faɗa.
Aa ina jin baigama shirin zuwa hospital nasan daya gama zai shigo muyi sallama, haka ne kuma mom ta faɗa tare da cewa" yanzu dai ba wannan ba yaushe zaka dawo? "
"2 week's kawai fa zanyi "
"ashe kuwa kashirya zuwa dani abuja kenan Indai 2 week's zakayi ƙafata ƙafarka, murmushi abie yayi haɗi dacewa "to su fa yaran ki kibarma wa su iye"
" dan Allah kabar ma maganr yara Sai kace wasu yan goye saunawa Nake zuwa abujar batare da su ba"
Assalamu Alaikum sukaji an faɗa katse labarin dasuke sukayi haɗi da amsa sallamar, wani matashin saurayi ne kyakyawan gaske wanda ko ba'a faɗa maka waye shi ba kamanin sa da abie zaitabbatar maka da cewa ɗan sane, DR. ABDALLAH MUHAMMAD HASHIM kenan matashi maiji da waye wa ga ilimi both side boko da Islama, farine shi ma sosai yana da tsayi dai dai misali gashi irin mazannan ne masu motsajiki dan yana da kirar jiki mai kyan gaske ga ƙasumba irin ta yan gayu domin kuwa daga ganin ta kasan tana shan gyara, jikin sa sanye yake da uniform ɗin sa na aiki hannun sa riƙe da briefcase ɗin shi, ƙarasawa ciki yayi wuri ya samu ya zauna,yana faɗin " inakwana abie mom ina kwana", lafiya lau alhmdllh suka amsa mashi abie ya ɗaura da cewa "har anyi shirin fita aiki kenan? "
" eh abie dayake ina da shiga thearter  ƙarfe 10:00,"Â
"masha Allah , Allah ya taimaka," "ameen ya rabbi , abie dawuri zaka wuce ne yau? "
"eh dawuri zan wuce saboda gobe tunda safe ina da shiga court â€, amma insha Allah bazan jima ba zan dawo ina ma tuna nin two days zanyi na dawo"
"to shikenan abie Allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya" da ameen suka amsa mom na faɗin
"breakfast É—inka nachan dining, sannan su Aairah na nan kawuce dasu school in baza kayi late ba,Â
"amma mom mi ya hanasu bin school bus yau? "
" uhm kai dai bari, shegiyar shiririta ce irin tasu , kasan halin su yanzu haka idan akace maka suna can basu kammala breakfast ɗin su ba ba'a gardama, narasa gane shiririta irin tasu Aaimah wallahi yara sai kace ba masu jini ba ajiki suyita abu kamar basu sanyi, Allah dai ya shirya su, ameen abdallah ya faɗa tare da cewa "bari naje nayi breakfast ɗin sai na dubasu"
"ok muma ga mu nan sakkowa"tashi yayi ya fice ya nufi dining, tunkafin ya isa yake jin hayaniyar Aaimah da Aairah sunata zagaye dining Aairah ta ɓatama Aaimah baby jiba da tea itakuma Aaimar nacewa saita rama shine fa suke ta zagaye dining baaba larai sai cewa take su bari amma ina kamar ƙara zugasu take.
Tsawa abdallah ya daka masu tare da cewa "ashe ku shasha shune ban sani ba, zaku dawo ku zauna ko sai ranku ya baci sakarkarun banza da wofi, wallahi kushiga hankalin ku kullum girma kuke amma ɗabi'un ku sak na yara. bashiri kowace cikin su ta nemi wurin zama, baaba larai ce ta matso zatayi serving ɗin ya abdallah tana faɗin " abdallah an tashi lafiya"
"lafiya lau baaba, ina kwana," Alhmdllh tace "mizan zuba maka"
"a'a kibarshi kawai baaba Aairah ta zuba man,"
"to shikenan ni bari nawuce kitchen"
Aairah yace ma tayi serving ɗin sa ita kuma Aaimah tayi sauri ta chanzo hijab ɗin ta tunda sungama breakfast ɗin su , to tace haɗi da tashi ta nufi bedroom ɗin su.
Abie ne ke saukowa shi da mom hannun ta riƙe da jakar kayan sa , "abie kafito " ya abdallah ya faɗa ayayin da yake kar ɓar jakar kayan a hannun mom,yana faɗin "abie muje koh" yayin da yake fita daga parlorn , bayansa suka bi har da Aaimah wacce sakowarta kenan daga bedroom ɗin su dataje chanzo hijab,"adawo lafiya, alhaji Allah ya kiyaye hanya yakai ka lafiya ya dawo da kai lafiya" "ameen ya rabbi baaba larai" abie ya bata amsa, fita sukayi compound ɗin gidan wurin motar abie suka wuce wacce baka driver ya daɗe da fito da ita dan har ya abdallah ya saka ma abie kayan shi a booth ɗin motar bankwana suka shigayi su Aairah har da hawaye abie sai lallashin su yake.
abdallah ne yace" dan Allah abie ka kyale yarannan sai sun sa kayi late", "kuyi hakuri bazan jimaba zan dawo may be na dawo nan da 2 days kunji" "to abie Allah yatsare hanya"
ameen abie yace
abdallah ne yace "to kuwuce ciki ku ɗauko school bag ɗin ku na ajiye ku a school, abie Allah ya tsare" ya faɗa  haɗi da tasa keyar su Aaimah zuwa ciki, mom ce ta matso kusa da abie tana cewa "wallahi barrister kamar kar ka tafi nake ji"
" tofah yara shagwaɓa uwa shagwaɓa toni wazan kama" ya faɗa yana dariya "uhmm kaima kasan wanda zaka Kama" ta faɗa tana ɓata rai, "yau naji shiyyasa kenan kika ƙi magana sai da yaran ki suka shige ciki zakiyi man adawo lafiya , ashe shagwaɓa za'ayiman ban sani ba ", mom tace "ok hakama zakace "ta faɗa haɗi da juyawa zata nufi ciki , hannun ta abie ya riƙo yana faɗin "Sorry kubrah, kema kinsan wasa nake , karki damu bazan jima ba zan dawo insha Allah"
"to shikenan Allah ya dawo man da kai lafiya" ameen abie ya faÉ—a yayin da yake shiga cikin mota sit É—in baya ya zauna bala driver na gaba key yayima motar, hanu mom ke É—aga ma abie shima yana É—aga mata,suka nufi gate,buÉ—e masu gate baba mai gadi yayi yana faÉ—in a dawo lafiya " mom na nan tsaye har sai da motar tafita daga gidan sannan ta juya tashiga ciki , dasu Aairah tacikaro suma sun fito a dawo lafiya tayi masu tawuce ciki abdallah ne ya sauko daga upstairs part din sa Â
Yana ce masu ku wuce mu Tafi.
 🌹~KAINAAT~🌹
Fita sukayi wajen mota suka shiga abdallah ya jasu gate suka nufa wanda tun fitar abie baba megadi yabar masu shi buɗe gaishe dashi suka yi ya amsa yana masu adawo lafiya da ameen abdallah ya amsa yayin da suke fita daga gidan,
abdallah ne yace" dama ana duka school ɗin ku wallahi dasai nasa yau anmaku dukan tsiya. "
"dan Allah ya abdallah kayi hakuri bazamu ƙara ba"
"kundai ci sa'a kawai ba'a duka da kungane kuranku yau da daga yau bazaku sake baccin safe ba, ace wai kuna bacci har school bus tatafi kuga yan hutu koh"
Kayi hakuri dan Allah wallahi baza mu ƙara ba"
, "ni da'allah kuyi man shiru sai bada hakuri sai kace masu tuban gagaskiya bayan nasan ƙarawa zakuyi" ya faɗa yayin da yake hawa kan titin ring road in da nan ne school ɗin su take bakin gate ɗin school ɗin yayi parking tare da cewa "kufito kuwuce ciki, fita sukayi suna yi mashi adawo lafiya Allah yasa yace motar yayi ma key yabar wajen tare da Kama hanyar hospital ɗin da ya
Episode 3_4
 Â
 .
LITTLE ANGELS PRIMARY AND SECONDARY SCHOOL. shine sunan school É—inÂ
Kamar yanda school uniform ɗin suka kasance pink and white color haka paint ɗin school ɗin shima pink and white color ne.
Cikin school ɗin suka shiga Masha Allah school ce mekyan gaske ta yayan masu arziki Upstairs ce makarantar wanda ya kasan ce down na yara up kuma na manya ne, up stairs suka nufa domin an daɗe da gama ASSEMBLY shiyyasa suka nufa class, S. S. 3 shine class ɗin su , shiga sukayi ciki for master ɗin su suka samu yana ma shirin fita domin ya gama abunda ya kaishi.
"Aairah And Aaimah  Muhammad hashim , why are you coming late" for mastern ya faɗa, Sorry sir we have wake up too late that the reason why we came to school late and it will never Happen again Aaimah ta faɗa yayin da Aairah ke ta bata fuska irin tafi ƙarfin ta bashi amma sa.
this should be the last, get sitet for mastern ya faɗa hadi da fita daga class ɗin .
Kallan juna sukayi haɗi da kwashewa da dariya, Aairah tace Why are you coming late tana kwai kwa yona maganar for master ɗin , dariya suka sake kwashe wa da Ita,
Aaimah tace this should be the last. wannan karan duka yan class ɗin ke dariya.
Sit ɗin su suka zauna suna cigaba da dariya,
Allah ya shirya ku twins domin yanzu abun naku sai adu'a mu samma make Aairah da uncle Hamza na magana sai wani harar sa kike," bazaki gane bane "Aeesha" Aairah ta faɗa wacce akakira da Aeesha tace to ganar dani.
"Ke wallahi haushi uncle hamza ke bani dafa Ina masa kallon mutumin arziki ashe dan banza ne, baki ji munce ya dai na zuwa gida yi mana lesson ba, Ai korar sa ya abdallah yay, saboda abun da ke kai shi bashi yake yiba, Ko kunya baijiba yace wai yana son Aaimah sai kuma yana lesson kiga yana kokarin taɓa ma mutun hannun ai kuwa rannan ashe duk abun da yake faɗa a kunnan ya abdallah, shine fa ya kore shi yace karya Kara ganin sa, to Wallahi inta kaice maki komu dukan da mukasha wurin ya abdallah sai kin tausaya mana dan Wallahi buguwa mukayi kamar gangar church kuma mom tace ba ruwan ta gashi abie baya gari, shiyyasa innagan shi Nake jin kamar na shaƙe sa"Aairah ta faɗa  tana hura hanci, Allah ya shirya sa to Aeesha ta faɗa , Ameen dai.
be silent biology teachern su ne yace haka wanda shigowar sa kenan yasame su sunata surutu, natsuwa suka yi suna sauraron lesson ɗin dayake masu.
_F. M. CÂ MEDICAL CENTER_
zaune a office É—in shi da ke Amenity, waya ce a kunnan sa da alama waya yake.
"haba dude ai dole nace haka tsawan shekarar mu nawa muna tare ace baka taba ziyarta taba su mom ma a suna ka ɗai suka sanka sai waya, ai tare bata ce haka ba amma nasan maganin ka zan haɗa ka kawai da ammy ne nasan ita zata saka kazo ba dan kashirya ba konasa mom takiraka may be kazo ya abdallah ne ya faɗi haka,, On the other hand nacikin wayar yace,, sorry my man ba haka bane nima ina san zuwa to ayyuka ne suka min yawa shiyyasa amma insha Allah ina nan zuwa very soon,, ai nima ina da tarin ayyuka amma Nake ajiye su na ziyarceka,, inkuma Sai zanyi aure zaka zo inji to, duk da in zanyi sai tare da kai don ina samun mata zan haɗa ka da ammy kaima ka fito da taka ko aba da kai sadaka" abdallah ya faɗa yana dariya.
"haba kaima kasan wa za'a ba da sadaka Indai aure zakayi bisimillah ban hanaka ba amma ni ba yanzu ba.
"shikenan tun da kai bazaka chanza ba kullum ace mutum amsar sa ɗaya, ina gaishe da su ammy "ya abdallah ya faɗa .
"zasuji insha Allah nima ka gaishe man dasu mom kace mata ina nan zuwa very soon "
"Allah yasa domin kuwa na san halinka,"
Karka damu dude zan zo insha Allah, to shikenan sai anjima , abdallah ya faɗa , ok nagode sai anjima kashe wayar yayi shiri yayi haɗi da fita daga office ɗin dakin tiyatar yanu fa.
 10:00 am
LAGOS.
_EKO HOSPITAL._
Patient ne zazaune wanda da alama sun zo ganin likita ne.
wata Nurse ce tafito daga Office aƙalla zatayi kimanin shekara 25 jikin ta sanye da fararen kaya riga da wando hulace kawai akan ta saɓanin wasu nurses ɗin da ke sanye da baby hijab, baka ce amma ba baki sosai ba wurin patient din tanufo, hadi dacewa DR. Is on the way, yayin da take amsar Katin patient ɗin wani dattijo ne zaune bai bada card ɗin shi ba da alama ma baiji mi nurse ɗin tace ba,"hey bring your card"
nurse ɗin ta faɗa ganin bai ba da nashi Katin ba," ƴata ni bana da Kati yau nafara zuwa".dattijon ya faɗa dakyar alamar ba karamin kamu ciwan yayi masa ba ,cikin harshen hausa tafara mgn duk da batayi Kama da hausawa ba kuma bawani iya hausar tayiba sosai " to ya kake so ayi Katin ka keso nabaka ne komi"
"a'a naji ance ana bada magani kyauta shiyyasa nazo" dattijon yafada, wani kallon rainin wayau take ma dattijon har ya gama magana, cikin karaji tace "hey hausa people nabani mamaki, to bari kiji nan ba charity hospital bane dan hk kitashi kiba mutane wurin, in ban da abunki ta ina wannan hospital ɗin tayi Kama da charity hospital koh ance maki irin hospital ɗiin kune na arewa" nurse din ta faɗa hadi da nuna masa hanyar fita. " haba Victoria kin man ta me doctor yace duk time ɗin da marasa ƙarfi suka zo ne " wata kyakyawar nurse ke faɗin haka chocolate color ce a ƙalla zatayi kima nin shekara 23 itama sanye take da fararen kaya rigada wando sai farar baby hijab, zuwan ta ke nan tasamu victoria nayima dattijo masifa Ita bahaushiya ce sabanin victoria, "ina ruwana ai yan zu ba ya nan sai dai inkece zaki faɗa masa
Kasa tashi dattijon yayi jikinsa sai rawa yake, tsawa ta dakama dattijo, haɗi dacewa "I said get out from this hospppppp, kasa karasawa tayi adalilin saukar wani mahaukacin mari dataji a kuncinta batai aune ba tasake jin wani marin a dayan kunchinta bashiri ta kife ƙasa, gaba ɗaya hankalin patient dana nurses ya dawo kan wanda yayi marin.
Tsaye yake jikinsa sanye da blue uniform ɗin sa na aiki, kafarsa na sanye da black din takalmi sai hannunsa dake riƙe da briefcase da lab coat ɗin  sa, dogone yana da tsayi, farine sosai kyakyawan gaske ya nada dogon hanci sai eyes masu black ɗin eyeball, small mouth me ɗauke da red lips, sumar kan sa wacce tasha gyara koma take kan shan gyara black color ta sauko saman neak ɗin shi ya sha rawani irin na larabawa, dama da ka ganshi kai tsaye zaka ce balarabe ne kukuma half cast  , akallah zai yi kima nin shekara 29 zuwa 30.
Good morning sir, nurses É—in suka shiga gaishe da shi hannu kawai yake É—aga masu yayin yake kiran security
ƙara sowa security ɗin sukayi suna gaishe da shi cikin girmamawa, amsa masu yayi yana nuna masu dattijon haɗi da cewa kushigar min dashi office yayin da yake ba daya daga cikin securityn key din office ɗin shi, kamashi sukayi suka ɗaurashi akan keken daukar marasa lpy wannan nurse ɗince wacce tayima victoria mgn ta matso kusa da shi hannu ta mika zata anshi briefcase ɗin dake hannun shi dakatar da Ita yayi, magana ya fara cikin harshen turanci nurse "hidaya me nace ne gameda masu zuwa neman tai mako? "
" kace duk wanda yazo neman tai mako ah EKO aturashi ABNOOR, kuma itama nurse Victoria tasani kuma sai da nasake faɗa mata da tana ma datijjon faɗa"
"shikenan koma dai miye Wannan yazama nakarshe ina ba haka ba dukkan ku sai ranku ya ɓaci "ya fada haɗi da nufar office ɗin shi
  🌹~ KAINAAT ~ 🌹
Tasowa victoria tayi daga duÆ™ewar datayi domin ta maru, haryanzu bata dawo dai dai ba, masifa tafara yima nurse Hidaya akan Ita ta haÉ—a ta da dr haryayi mata wannan marin, "to bari kiji Victoria garama tun wuri kifita daga harkata basai da na gar gaÉ—e kiba amma mikika ce ke kina ganin dr shazim bazai iya yimaki komai ba ke yar gaban goshi, kedai kawai za fin mari ne yasa zaki sauke a kaina mizai hana shi dr bazaki bishi office kiyi mashi masifar ba "hidaya ta faÉ—a  tana dariya sauran nurses É—in ma dariya suke saboda sun san magana ce hidaya ta faÉ—a ma victoria saboda ba Æ™aramin so take ma DR. SHAZIM ba, mutsww victoria taja tsaki saboda haushin dariyar dasuke mata ta kuma gane miyasa su dariya wuce wa tayi office É—in dr saboda itace ke tura mashi da patient,Â
Shiga tayi cikin office ɗin haɗi dacewa, good morning sir zaune yake yana rubutu ajikin file wanda da alama na wannan dattijon ne yayin da shikuma dattijon yake kwance bisa gadon marasa lafiya a office ɗin , ko kallon inda take bai yiba sake gaishe da shi tayi, call nurse hidaya for me abun da kawai ya ce mata kenan, hakuri ta shiga bashi dan bazata iya daina aiki dashi ba domin in har chanzata zaiyi da nurse hidaya to sai dai tabar hospital ɗin saboda bazata juri ganin shi tare da wata ba,  tsawa yada kamata domin yaga bata da niyyar fita daga office ɗin yace " get out from my office" haɗi da nuna mata hanya, fita tayi daga office ɗin zuwa office ɗinsu na nurses fashe wa tayi da kuka, tana faɗin bazai yuwu ba wlh dr shazim nawa ne ni ka ɗai babu wacce ta isa ta raɓesa sai ni taƙara fashewa dawani kukan, wata nurse ce tashi go office ɗin wacce itama daga ganin ta ba muslma bace tana cewa , "ai yanzu kika fara kuka victoria,  dama ba sai da na faɗa maki ba kitashi tsaye amma kika kiji to wallahi Idan bakiyi wasa ba kina nan sake dabaki hidaya zata kwace shi, sai dai kizama ƴar kallo"
"haba destiny yaza ki man wannan mumu nan maganar,  kisan kuwa yanda nake son dr shazim kuwa da kinsan yanda nake son shi da baki ce haka ba"
" victoria kenan inaga bakisan halin hausa peoples bane zaki sha mamaki inkika tsaya wasa domin kuwa Ita hidaya yarensu ɗaya bayan nan religion ɗin suma ɗaya kina ganin zai kula ki ne yana ganin hidaya, kawai kitashi tsaye"
"to ya zanyi ki bani shawara pls"wani munafukin murmushi destiny tayi haɗi da cewa yanzu dai kifara kiramashi hidaya tukkun nan zuwa anjima sai muyi magana "
" haba destiny yazakice nakirata sai dai yaji haushi amma ni bazan kira taba wlh" "kaji sakarya in ban da kina sakarci in baki kira mashi ita ba taya zai gane kintuba kuma itama hidayan ki roketa akan ta tayaki bashi hakuri nasan zatayi," "uhmmm shi kenan ta faɗa haɗi da barin office ɗin domin kiran hidayar, dariya destiny ta kwashe da Ita haɗi da cewa "zaki gane baki da hankali Victoria zakisan cewa ni ba kanwar lasa bace yanda kika ki brother samuel to haka zaki rasa shazim shima sakarya kawai" .
wurin su hidaya Victoria tanufa,ta zuwa ta tsaya hannunta riƙe da ƙugu tace" kizo dr . nakira tana faɗa ta juya kai gefe, "wakenan acikin mu?" watace cikin nurses ɗin dake zaune ta faɗa , "tasan kanta ai acewar Victoria , sarai sungane hidaya take nufi sbd sun San tana yar tsama da Ita amma sai suka nuna basu gane ba "hidaya kinsanfa ke nake nufi amma kinyi kamar baki ganeba zanje na faɗa masa bazaki zoba"
" kejiman Victoria da karfin halin, kin faɗi sunan tane daza kice ta ƙizuwa"
"ah to gane mana hanya sister maryam" acewar wata daga cikin nurses ɗin "haba Victoria nina rasa me hidaya ta tare maki a hospital ɗinnan,ai ko bakomi ƴar uwarki ce tawurin aiki, amma ace kullum baki da abokiyar faɗa sai Ita"
karka faÉ—a man mgnr banza mana Joseph ina ruwanka"
 "sorry shawara ce" barin wurin yayi wanda akakira da Joseph
"mike faruwa ne anan cewar destiny wacce isowarta kenan, a'a hidaya Victoria bata faɗa maki dr nakira ba nagan ki zaune ko har kin dawo daga wurin shi
"A'a destiny yanzu zanje, ok destiny ta faɗa haɗi dacewa kefa Victoria naga kinyi tsaye kutafi mana bin bayan hidaya destiny da Victoria sukayi suna ɗan yin nisa da sauran nurse's ɗin destiny ta ɗan taba Victoria alamar ta roki hidaya akan ta taya ta ba dr haƙuri ganin baza tayi ba yasa destiny dakatar da hidaya haɗi da cewa "kiyi hakuri hidaya akan abun da Victoria tayi maki haushin dariyar da kuka yi matane ɗazu, amma kiyi hakuri" "shikenan bakomi, ni da man bawani riƙe taba" "shikenan amma ki taya ta ba ma dr hakuri pls karya cireta daga cikin nurses ɗin dake tura mashi patient pls, a ranta take faɗan"ok shiyyasa kenan tazo ta ciman mutun ci"amma a zahiri sai tace "bkm yawuce insha Allah zan taya ta" thanks Victoria ta faɗa yayin da suka kawo office ɗin shiga ciki sukayi sallama hidaya tayi yayin da Victoria ke bayan ta, dr gani hidaya ta faɗa, ok a saka patient a layi amma mutum 15 kawai zan duba sauran kiturasu office ɗin DR KABIR, sorry sir ni ina iya tura su a cewar Victoria data ga yayi kamar bai san tana wurin ba, as from today this is the last time dazaki Kara zuwa office ɗin na I hope you understand, a fuwan sir kayi mata haƙuri bazata ƙara ba hidaya ta faɗa gaban ta na faɗuwa tsoron kar itama ya koreta, nagama magana get out
ƙasa Victoria tayi akan gwiwo winta tana ci gaba da bashi haƙuri harda kuka, I said get out from my office ya faɗa da tsawa yana nuna mata hanyar fita, fita tayi tana kuka kamar ranta zai fita ,kema zaki iya tafiya" Ok sir hidaya ta faɗa fita itama tayi " wajen office ɗin ta samu Victoria da destiny suna ganin ta suka nufe ta rokonta suka shigayi a kan ta taya victoria ba ma dr haƙuri " shikenan insha Allah zan taya ta kar ku damu hidaya ta faɗa hadi da sharema Victoria hawayen dake fuskarta ta cigaba da kwantar mata da hankali godiya sukayi mata sannan suka koma office ɗin da suke zama ita kuma ta wuce wurin patient domin tura ma dr su .
haka ya cigaba da ganin patient shikuma wannan dattijon ruwan da aka sa mashi na ƙarewa yasa driver ya mai dashi ABNOOR aka bashi gado , bashi ne ya bar EKO ba sai wurin 12:30 sannan ya wuce ABNOOR nan ma yaga patient dayawa saboda da nan yafi jimawa a nan a kan eko , abnoor hospital ɗin sane halak malak Ita kuma eko aiki yake a chan, sau biyu  yake zuwa eko a sati idan yana lagos saboda yana visiting wasu Hospital ɗin , kuma in yaje 2 to 3 hours yake yi yaje abnoor   , amma standard in da yafi zama abnoor ne saboda chan har ranar Saturday yana zuwa in yana lagos ,sai wurin 6:00 ya tashi daga aiki dan har an fara kiraye kirayen sallar magrib masallacin hospital ɗin ya nufa domin gabatar da sallah sai bayan angama tukkun nan yanu fi gida,
horn yayi a bakin wani katafaren gida naji da faɗa dake Victorian Ice land , gida ne har gida wanda daga gani ba sai an faɗa maka ba kasan cewa an narkar da kuɗi, me gadine ya bude masa gate, ciki ya shiga  ya nufi parking lot da ke chan cikin gidan,ɗakin mai gadine farko daka shigo gidan sai boys quarters daga chan gaba sai kayi ƴar tafiya sannan zaka iso part ɗin masu gidan sai parking lot dake gefe  sai wani katon garden dake bayan part ɗin masu gidan hade da Wani katon swimming pool me kyen gaske,ride's ne gasunan kala kala a kallah zasu kai 6 a parking lot ɗin , parking yayi cikin gidan ya nufa tura ƙofar shiga part ɗin yayi bakinsa ɗauke da sallama,parlor ne me kyan gaske komai na cikin sa ya kasan ce golden and white color ne royal sofas ne masu kyan gaske set biyu sai wani ƙaton dining table mai chairs kusan guda 10 , sai wasu bedroom guda 3 dake hannun dama sai kitchen da store atare, wani corridor ya nufa inda yana shiga nan ma wani madaidaicin parlorn me dauke da sofa a set 1 komai na cikin sa golden color ne sai dining mai dauke da chairs guda 5 sai two bedroom, daya daga cikin su ya nufa bakinsa ɗauke da sallama, wata kyakyawar mace ce zaune a kan sallaya itama farace sosai suna Kama da dr banbanchi Ita mace ce shikuma namiji zata yi kimanin shekara 50 , sanye take da hijab hannun ta reke da chasbaha tana ja , da a lama sallah ta gama, sallamar da yayi ta amsa mashi yayin da yake ƙarasa wa inda take zaune wuri ya nema ya zauna "an wuni lafiya ammy, ya gida"ya faɗa , amsa mashi tayi da" lafiya qlu Alhmdllh ya aiki ya fama da patient, alhmdllh ammy, Masha Allah ta faɗa haɗi da cewa katashi ka shiga ciki domin kasamu ka huta zansa fatima ta kawo maka dinner ɗinka , dama shi ba ma'a bocin cin abinci a dinning bane, to shikenan ammy bari na wuce ciki, fito wa yayi daga bedroom ɗin yanu stairs dake parlor wani part ya shiga wanda da alama nasa ne tura ƙofar yayi haɗi dayin sallama, ya kutsa kai ciki parlor ne shima ma dai dai ci me kyan gaske komai nacikin sa ash and black ne bedroom ya nufa wanda shima bedroom ɗin kayan cikin sa ash ne hattada furnitures ɗin ciki ash ne ɗan corridor ya nufa cloth set ne sai gefe laundry basket, kayan jikin sa ya shiga ragewa ya koma daga shi sai boxer bathroom yanu fa domin watsa ruwa after 15 minutes ya fito jikin sa sanye da bathrobe wurin clothes set ɗinsa ya nufa jallabiya ya saka ajikin sa bathroom yakoma domin ɗauro alwallah sbd time ɗin sallah isha yayi  masallachin gidan ya nufa dan gabatarda sallah anagama sallah part ɗin sa ya koma a parlor ya zauna kan sofa bai jima da zama ba yaji ana nocking tambaya yayi waye ne " fatima " ce Yaya ok shigo ya faɗa , turo ƙofar tayi tashigo bakinta ɗauke da sallama kyakyawar matashiya ce akalla zatayi kima nin shekara 18_19 fara ce itama tana kamada ammyn su amma ba sosaiba dr dai shine ke kama da Ita sosai " ina wuni Yaya andawo lafiya, lafiya qlu , dama ammy ce tace nakawo maka dinner ɗin ka, ok ajiye kan table, ajiye mashi tayi haɗi dafita jawo table din yayi , serving ɗin kanshi yashiga yi, yana kammala cin abincin bedroom ɗinsa ya koma laptop dinsa ya jawo dake kan bedside aiki yashiga yi.....
KATSINA....Â
Su Aaimah ne zaune a falon mom suna kallo, sanye suke da pajamas sky blue,  mom ce tafito daga bedroom ɗin ta, ita ma sanye take da pajamas purple color, waya ce a kunnan ta  da alama waya take wuri tasamu kan sofa ta zauna tana cigaba da wayar " mom abie ne Aaimah ta faɗa yayin da take matsowa kusa da mom, daga mata kai mom tayi alamar eh" mom dan Allah kice muna gaishe shi munkira shi bai ɗauka ba, to kaji Wai twins ɗinka nagaishe da kai wai sunkiraka baka ɗauka ba mom ta faɗa , mika ma Aaimah wayar tayi da a lama cewa yayi a basu wayar, amsa tayi haɗi da cewa" inawuni abie ya Abuja, ya kuma aiki " on the other hand abie yace" lafiya qlu Alhmdllh ya gida ya kuma school " Alhmdllh abie ta bashi amsa, abie ko kace ina nake Aaimah ka ɗai kasani" Aairah ce ke mgn wacce ƙara sowarta kenan "afuwan yanzu zance kina ina sai kuma gaki ya gida ya schll" Alhmdllh abie yaushe zaka dawo, jibi insha Allah zan dawo " to Allah ya kaimu abie , ameen ya faɗa  sun jima suna waya sannan suka yi sallam, bedroom ɗinsu suka nufa domin bacci dan mom ta daɗe dashige wa nata bedroom ɗin ....
Episode 5_6
_FRIDAY......._
sauko wa yake daga stairs jikin sa sanye da baƙaƙen coat hannun sa riƙe da briefcase , ammy ce zaune kan sofa ƙaraso wa yayi kusa da ita " Ina kwana Ammy ina fatan kintashi lafiya " ya fada yayin da yake samu wuri kusa da Ammy ya zauna " lafiya lau Shazim har kafito," eh ammy ya bata amsa," ga breakfast din ka nan kan dinning" "to,ammy kinkuwa yi waya da NORAIZ "( kanin sa mai bimasa yayan fatima dayake baya nan yana kasar portland yana masters akan business ) ya fada yayin da yake nufar dinning "eh naji yace yana nan zuwa ranar sunday ( lahadi ) , ammy ta fada " eh ammy haka yake fada man jiya, "to Allah ya kaimu lafiya" Jiya uncle ɗin ku ya kirani, yace kai ka ɗai suke jira" shiru yayi baice komai ba sai da ammy ta sake cewa "da kai fa nake magana, ni ban san mikake nufi ba , da anyi magana sai kayi shiru, tun yaushe ake abu ɗaya sai yawo kake ma mutane da hankali"
"kiyi haƙuri ammy, wlh ban gama abun da nake ba, kuma nifa bani da wata wacce zance ina so, nafi son su barin harsai na samu wacce nake so"
"to bari kaji na faɗa maka ni ba ruwana daga yanzu bazan sake shiga maganar ba duk hukuncin da suka yanke akan ka babu ruwana "shazim yace "dan Allah ammy karkice haka idan kika zare hannunki innah zata iya zuga su su yanke man hukuncin da duk sukaga dama"
"to idan har baka son haka tafaru to dole sai ka nema ma kanka masalaha" "insha Allah ammy"
"to Allah ya yarda, ameen ammy ".
fatima ce ta fito daga bedroom dinta dake kusa da na Ammy jikinta sanye da uniform , dinning ta nufo Ita ma domin breakfast
" Ina kwana Yaya dafatan antashi lafiya " lafiya qlu ya bata Amsa, yana gama breakfast ya mike hadi da daukar briefcase din shi " Ammy ni zan wuce, to a dawo lafiya Allah ya bada sa'a, ameen Ammy fita yayi zuwa parking lot, gaisawa ya tsaya yi da masu aikin gidan tun daga kan maibama flower ruwa Har izuwa kan maigadi sannan ya fuce daga gidan, ABNOOR ya nufa domin yau baya zuwa EKO.
ABDULƘADIR  ABUBAKAR NURADDEEN PRIVATE HOSPITAL ( ABNOOR ).
Direct office din sa ya nufa briefcase din sa ya aje akan table zama yayi hadi da bude laptop dinsa Aiki yafara kafin time din daya ke duba patient yayi. sallama a kayi hadi da turo kofar wani matashin saurayi ne wanda zasu yi sa'anni da shazim din.
Amsa mashi sallama yayi, shigowa yayi daga ciki hadi da mikama shazim din hannu suka yi musa baha , sannan ya zauna kan kujerar dake gaban table din " shazim amma yanzu ka shigo ko dan nazo baka nan, eh shigowata kenan nakama aiki , ai ku manya ne agogo sarkin aiki, haka dai kake gani majeed karfin haline kawai, wlh kuwa ai kana kokari, to ya za'ayi, dole a nema"
"hakane dama maganar kayan da suka kusa ƙarewa ne"
"kai ai kuwa gara daka tuna man dan har na manta, zanyi magana da su yau insha Allah "
"to shikenan  nibari nakoma office"
"to shikenan nima yanzu zanje duba patient insha Allah sbd da time din sallah nayi zan tashi sai kuma gobe Idan Allah ya kaimu, ameen majeed ya fada hadi da barin office din shima baijima ba ya fita dakin marasa lafiya nufa sai 12:10 sannan ya dawo office yana shiga bawani jimawa yayi ba ya hada kan kayansa ya fito direct gida ya nufa bedroom din ammy ya fara zuwa gaisawa kawai sukayi ya nufi part din sa bedroom din sa ya nufa kayan jikin sa ya shiga ragewa ya nufi bathroom after 10 minutes ya fito kugunsa daure da towel dressin mirror ya nufa mai ya shafa mai dankaran kamshi, comb yasa ya shiga combing din kansa sannan ya shafesa da man aloe da hair spray clothes set dinsa ya nufa shaf shaf ya shirya cikin wata shadda ƴar ubansu milk color ba karamin b
kyau yayi ba sannan ya dauko hula ya daura brown color, feshe jikin sa yayi da turare mai ƙamshi,sannan ya nufi shoe rag dinsa takalmi ya dauko me kyan gaske shima brown color. masha ALLAH kawai zamuce dan ba karamin kyau yayi ba wayoyin sa dake bedside ya dauka fita yayi daga bedroom din yana zuba kamshi, ya nufi down stairs parlorn ammy zaune ya sameta tana karatun Al'qur'an tana kai aya tace " sai masallaci kenan, eh ammy ya bata amsa , to shikenan a dawo lpy nima zanje gida domin na ƙasa duba jikin baba , to saikin dawo Allah ya bashi lfy nima insha Allah yanzu daga masallachi zan biya na gaishe shi saina dawo ya fada hadi da kama hanyar fita Ammy nacewa a dawo lpy , da innah asabe ya cikaro ( mai Aikin su) zata shiga wurin Ammy, gaishe da Ita yayi ta amsa mashi da " Lafiya lau Shazim har za'a tafi masallachi kenan, eh ya bata amsa hadida fice wa daga falon ya nufi parking lot mota yashiga mai gadi ya bude masa gate ya fuce.........
_KATSINA......._
AIRAH
Zaune take bakin gado jikinta daure da towel da alama wanka zatayi .
"sister gaskiya kiyi sauri kifito nima nayi wanka kinsan yau abie zai dawo kuma mom tace muje gidan granny mu gaishe ta har so nake muje gidan aunty safiya ( kanwar MOm wacce suke uwa daya uba daya) mun kwana biyu ba muje ba "Aairah ta fada.
fitowa Aaimah tayi daga bathroom jikinta daure da towel " bawani sis zaki ziyara ne kodai zakije ganin ya MUS'AF dan nasan halinki sarai, Amma wlh Aaimah kin bani da sharri yau she nace maki saboda shi zanje gidan ni dai ziyara zani bawai saboda ya mus'af , dan wlh ki bari karki jaman ya usman yaji wannan maganar , ai kuwa saina fada masa ince bakiji gargadin da yayi maki ba, ni wlh har mamaki kike bani kirasa dawa zakiyi soyayya sai ya mus'af harka duk ta yarin ta, eh naji matar babban mutum sai mi koda ace na girmi ya mus'af ina ruwan ki Aairah ta fada tana huro hanchi, Allah ya baki hakuri Aairah ni nayi nan Aaimah ta fada hadi da nufar dressing mirror bathroom Aairah ta nufa shaf shaf Aaimah ta shirya cikin atamfa super Red color ɗinkin riga da skirt tana nan tsaye tana fesa turare Aairah ta fito sai bata rai take shiryawa itama tayi cikin atamfa color daya data Aaimah tana gamawa ba tai ma Aaimah magana ba taka ma hanyar fita daga bedroom din, murmushi Aaimah tayi hadi dacewa " ki nafa iya cewa kinji haushi, bata bata amsa ba sai tsaki data ja, haba twin sis kiyi hakuri bazan sake ba kinji ta ya mus'af sorry pls Aaimah tafada hadi da matsowa kusa da Aairah sake bata hakuri tayi tare da cewa haba abun gidan ya mus'af kiyi dariya mana dan Allah tafa da yayin da take langwabar da kai, murmushi kawai tayi hadi da cewa wallahi Aaimah ki daina kushe man ya mus'af Indai kina so mu zauna lafiya da ke, kaina bisa wuya na daina insha Allah Aaimah ta fada hadi dajan hannun Aairah suka fita bedroom din mom suka nufa samun ta sukayi zaune gaban dressing mirror tana saka sarka a wuyan ta sanye take da wani hadaden less brown color ta sha daurin ture kaga tsiya hannunta ya sha dan hannu da zobe na gold kalar sarkarta, har suna hada baki wurin fadin masha Allah  , Aaimah ce ta ce "kice yau an tashi rikita mana abie kenan , wannan kwaliyya haka mom ai sai ya ka sa gane ki yayi tuna nin sabuwar amarya aka kawo masa, Aairah tayi charab tace ba kiga harda ture kaga tsiya ba, lallai duk wanda ya ture ya taro match ba yan ball, murmushi kawai mom tayi hadi da cewa kun rainani ko, na lura ni kuka maida granny da dadi, Aa wane mu kawai dai munga kin hadu kar abie ya riki ce, ALLAH ya shirya ku mom ta fada ameen suka amsa, Aairah tace daman mom daga gidan granny zamu wuce gidan aunty safiya dan Allah, shikenan Idan kunje kuce ina gaishe ta , to shikenan mom zataji Insha Allah amma sai abie ya shigo sannan zamu tafi , to shikenan mom ta fada..
Ya usman ne ya shigo bedroom din jikinsa sanye da shadda maroon color sallama yayi hadi da shigo wa gaishe da shi su Aairah su kayi hadi da ficewa falo zama sukayi kan sofa suna kallo.
a chan kuma bedroom din mom gaishe sa Ita usman yayi, amsa mashi tayi hadi da cewa har ka dawo daga masallachin, eh mom ya bata amsa, abinci fa, a kai maka part dinka ko zaka sauko kachi a dinning, a'a a barshi nan zan sauko Idan abie ya shigo sai muci tare da ku , dan nayi waya da shi da ina kan hanya wai ashe ya dawo yana gidan dadi (kakar su ta wurin uba mahaifiyar Abee) amma yanzu zai taho, to shikenan bari nasa ajera abinci kan dinning sai muci tare da dashi dama nayi tuna nin basu kusa isowa ba, to shikenan mom ni na wuce part dina kafin ya kai da shigowa ya fada hadi da ficewa itama mom fita tayi direct kitchen tawuce a chan tasa mu baba larai na zuba abinci cikin warmers "yawwa baba kice harkin kwashe kafin nazo, halan kinga najima ban dawo ba sallah nayi sai nace bari kawai nayi har da wanka tun da nasan san da zan dawo nasan a bincin ya nuna kuma barrister na hanya shiyyasa, A'a nima sai da nayi wankan da naga baki sauko bane kuma ya nuna sai nace bari kawai na kwashe, to shikenan bari na jerasu a dinning mom ta fada hadi da daukar warmers din ta nufi dinning bala driver ne ya shigo hannun sa dauke da kaya suna cikin gaisawa mom sukaji sallamar abie daga bayan su sauko wa su Aairah sukayi da gudu jin sallamar abie, nufar sa su kayi da gudu hugging din su yayi yana murmushi sun bi sun makalkale shi mom ce ta matso tana cewa ku sake sa man, kunbi kun makalkalesa , haba mom kwana biyu fa baya nan, to ko baya nan fa , ya kwaso gajiya shine zaku kara masa wata, ku sake sa mana , sakin sa su kayi kan sofa suka zauna, shi kuma up stairs ya hau shi da mom , bala ne ya sake shigowa da wasu kayan na abie,  jakar kayan abie ka dai bala ya kai sama sauran kayan kuma kitchen ya nufa dasu .
AFTER 25 minutes........
abie ne da mom ke sauko wa daga up stairs abie har ya chanza kayan jikin shi da alama wanka yayi dinning suka nufa ta sowa su Aairah sukayi suma suka nufo dinning din " Aairah maza kije ki kira yayan ku mom ta fada, tashi Aairah tayi direct part din ya abdallah ta nufa tsit parlorn shi, ba kowa sai kamshi kawai dake tashi ya hadu parlorn golding color ne komai na ciki , bedroom din sa ta nufa nocking tayi tambaya yayi waye, Aairah ce, yaya mom tace ka sauko abie ya dawo ta bashi amsa, gani nan zuwa yace, fita tayi daga part din ta koma wurin su mom , yace ga shinan zuwa ta fada yayin da take samun wurin zama serving din su Aaimah ta shiga yi sai ga ya abdallah shima ya sauko jikin sa sanye da jallabiya karaso wa yayi yana gaishe da abie da gajiyar tafiya, amsa mashi abie yayi tare da tambayar shi ya aiki,amsa ya bama abie da alhmdllh shima serving din sa Aaimah tayi , abinci suka shiga ci ba magana sai dai karar spoon dake tashi, su Aairah suka fara tashi, ba dai har kun ta shi ba, abie ya tambaya yana binsu da idanu, eh abie zamuje gidan granny ne shiyyasa kuma fa mun koshi, Aairah ta bashi amsa, to shikenan sai kun dawo kar dai ayi dare , a dawo dawuri kunji, Insha Allah abie baza mu kai ba, Allah yasa, ameen suka fada hadi da nufar up stairs , abie suna gama cin abinci kan sofa suka koma suna fira shi da ya abdallah ,mom kuma tattare dishes din da su kayi amfani dasu tayi ta nufi kitchen, baaba larai ce ta fito daga corridor din da da kinta yake wurin su abie ta nufo hadi da gaishe da abie tana tambayar shi ya gajiyar hanya amsa mata yayi da, "lafiya lau alhmdllh, ya gida ya kuma muka same ku, alhmdllh muke naga sako nagode Allah ya saka da alkairi, ameen nagode bakomi abie ya bata amsa ( nasan masu karatu zasu ce godiyar mi baaba larai keyi ma abie , kudi ya ba ma mom ta ba ma dukan hadiman gidan dama ya kan yi haka duk In zaiyi tafiya.) Kitchen ta nufa anan ya samu mom na wanke dishes din da suka ci abinci " ah hajiya dakin bari nazo na wanke ai, A'a bakomi baaba kema ki huta mom ta bata amsa, to shikenan bari muyi tare" inji baaba larai, A'a dakin bar shi Allah kinga na kusa gamawa ai, to shikenan , su Aairah ne suka sauko sun sha jalbab har kasa sai bag kalar ta kalmin dake ka farsu kara sowa su kayi wurin su abie hadi da cewa sai mun dawo,abdallah ne ya ce" mudi na nan waje shi zai kaiku" to suka ce hadi da nufar wurin mom sun cewa sai mun dawo a dawo lafiya tayi masu , ficewa su kayi harabar gidan, a nan suka samu mudi na jiran su , motar suka nufa, shiga su kayi, key yayi ma motar suka fice da ga gidan dama me gadi ya bude masu gate labari kawai Aaimah da Aairah keyi shi dai mudi nashi saurare har suka isu gidan granny horn mudi yayi a bakin gate din gidan bude masa gate din a kayi ya shiga daga ciki ya na parking suka fito gidane dan dai dai me kyau cikin gidan suka nufa wata kyakyawar tsohowa ce suka samu zaune a parlor tana kallon SUNNAH TV ( granny kenan mahaifiyar mom ce) sallama su kayi da gudu suka nufi yar tsohuwar, granny tace " karku kuskura ku fado man , salon ku ida kara sa man yan kafafun da nake fama dasu" Aaimah tace "haba granny daga munyi murnar ganin ki sai kice zamu ida karasa maki yan kafafun"ta fada tana turo baki, Aairah ce tace " shiyyasa yau zan zuga tsoho yayi maki kishiya tun da baki da kafafu" granny tace " sai dai ke ayi maki kishiya, amma ba dai ni ba, saboda ni ba wacce zata iya kishi dani, in kuma kece kishiyar inji tunwuri" dariya suka kwashe da Ita su duka Aairah tace " wah wai ni , ai kuwa da kin sha kwar kwasa da kisi si na, murmushi kawai granny tayi hadi da fadin Allah ya shiryeki yan biyu ( dayake haka take ce masu kokuma Hassana da hussainah) gaishe da Ita sukayi suna tambayar tsoho na nan, ( wato mijin granny) granny ce ta basu amsa da "yana parlor da yake ganin dalibn sa, inajin ma karatu suke saboda yau juma'ah ( malamin addini ne shi duk da ya tsufa hakan bai hana shi koyar da daliban sa ba) Aaimah tace" to shikenan granny bari muje gidan aunty safiya mu dawo, kilan time din ya gama, to sai kun dawo ku gaishe man da ita granny ta fada Aairah ce tace zataji insha Allah fita sukayi harabar gidan nan suka samu mudi zaune kan benchi suna fira da me gadin gidan, gannin sun fito yasa shi ta sowa Aairah ce tace "kabar shi kawai ba nisa za muyi ba gidan aunty safiya za muje, to ya fada hadi da koma wa kan benchi ya zauna su kuma fita su kayi daga gidan, tafiya su kayi a kafa ba mai nisa ba suka iso gidan tura yar kofar dake gefen gate su kayi hadi da shiga gidan, gida ne mai girma ba laifi dan har ya kusa girman gidan su, part din masu gidan suka nufa da sallama a bakin su suka shiga parlorn, yan yara suka samu na wasa a parlorn mace da na miji a kalla za suyi kimanin shekara 10, suna jin sallamar su suka nufo su da gudu suna masu "oyoyo aunties ya gida ya mom" su Aaimah suka ce"lafiya lau hisham sai ku ka dai a parlor kai da hibba, wata matashiya ce ta leko daga up stairs jin haya niyar yaran zata yi sa'anni dasu Aaimah tana ganin su Ita ma da gudu ta sauko tana fadi "oyoyo lovely sister da kuka ce kun fasa zuwa" Aairah tace "kedai bari najma, dafa har mun fasa saboda abie zai dawo yau, to da muka koma gida daga school mom take ce ma ai yama kusa isowa, to shine fa muka shirya tana dawo wa muka taho, najma tace "gaskiya naji dadi, da Allah har nayi fushi, Aaimah tace "yanzu dai ba wannan ba naji banji mutsin Ummah ba ( Aunty SAFIYA suke cema Ummah sbd su najma ) ko bata nan ne , tana dakin abba najma ta bata amsa hadi da jan hannun su tana cewa kumu tafi part din abban daga nan sai ku gaisa dashi ko , ok muje, part din abban suka nufa, sallama su kayi yayin da suke shiga cikin parlorn zaune suka same su kan sofa, amsa masu sallamar suk ayi aunty safiya tace "ah lallai yau ina da mn yan baki" abba yace " lallai kam yau muna da man yan baki, ya mom din ku da abie ya kuma school, alhmdllh abba suka amsa mashi, to masha Allah abba ya fada najma ce tace " to ku tashi mutafi daki, da to suka amsa mata hadi da mikewa suka fice direct bedroom din najma suka nufa suna shiga suka yada zango akan bed din ta Aairah ce tace " wai nikam ina Yaya mus'af ne najma,Aaimah ta ce " uhmm dama nasan hali har ni zakiyi ma bariki wai ziyara za muzo bayan nasan karyane, eh din naji komi za kice kice Aairah ta fada tana murguda ma Aaimah baki ,najma ce tace" ya Isa haka inkuka fara sai kuba mutun haushi wlh , ya mus'af ne deko to yana part dinsa bari nakira maki shi a waya koke kikira shi ba shi kenan ba, Aaimah tace aikin san wasa nake maki ko rabin rai , niban wani sani ba Aairah ta fada, to yanzu kinsan shikenan ko ta wuce, bari ni na kira maki shi da kaina a cewar Aaimah hadi da ciro wayarta tayi dealing number sa kiran na shiga ta mikama Aairah wayar picking call din yayi hadi da ce " Aslm, wslm ta bashi amsa, sai cewa yayi" Aaimah ya kike ya gida yasu mom da ya abdallah, ina kuma sweetie nah take, bubbuga kafafu ta shiga yi tana turo baki hadi dacewa" haba Qalbei nice kenan baka gane ba , su najma miza suyi inba dariya ba suna cewa a she soyayyar bata kaiba da har ake kasa gane muryar juna , fa shewa da kukan shagwaba Aairah tayi hadi da cewa ka gani koh Aaimah da najma nayi man dariya, on the other hand yace " sorry sweet heart nayi tuna nin Aaimah ce, kinga ai numberta ce amma kiyi hakuri kinji my, najma na gidan kune, Aa fa kai da nazo nayi surprise dinka, amma sai ka bata komai baka gane ni ba Aairah ta fada, sorry kinji tawan fada man kina ina kinji, turo baki gaba tayi hadi da cewa " Ina bedroom din najma , am coming sweet heart ya fada hadi da kashe wayar,ajiye wayar tayi Ita ma hadi da yima su najma gwalo "oho dai ke da ba'agane ba najma ta fada hadi da tafawa ita da Aaimah" nocking sukaji ana yi da sauri Aairah ta nufi kofar tana bu dewa wani matashin saurayi ne tsaye jikin sa sanye da jeans da T-shirt na kamfanin Gucci farine kyakyawan karshe a kalla zai yi kimanin shekara 20 murmushi Aairah ta sakar mashi shima martanin murmushi ya mayar mata, gaishe da shi Aaimah tayi, ficewa su kayi daga bedroom din, su Aaimah kuwa fira kawai suke har aka kira sallar asr, sallah suka tashi su kayi a lokacin Aairah itama ta shigo domin yin sallar Aaimah ce tace ma Aairah ai nayi tunanin nisa ku kayi da naga kun fita ashe kuna kusa, banza Aairah tayi da ita ta nufi bathroom domin yin alwala, basu ne suka bar gidan ba sai wajen 5:00 sannan suka koma gidan granny najma da Aaimah na gaba yayin da Aairah da mus'af ke bayan su , suna shi ga granny tace a she zaku dawo harna yi tuna nin kun wuce gida a she kuna nan, kallon mus'af tayi tana fadin" kai kuma lafiya kayi man tseye a kai , aure ne dai banyi ehe" dariya mus'af yayi hadi da cewa sai mi, dama ni yarinya nake so me jini a jika ba tsohuwa ba, dariya suka kwashe da Ita su duka, haba kai dai kawai dan ba zaka samu bane , ya safiyar take ina su Hibbatu da hisham ,
lafiya lau suke granny, fira suka shiga yi da granny tana tsokanar su a nan tsoho ya same su, gaishe da shi suka yi , dashi suka taru suna ta firar ba sune suka bar gidan ba sai kusan 5:50 sannan mudi ya mayar da su gida duk da mus'af ya so mai da su, amma suka ce ya barshi tun da da driver suka zo ,da shigar su gida bedroom suka nufa domin time din sallar magrib ya kusa kayan jikin su suka cire suka sanya ma rasa nauyi, sau kowa su kayi down stairs direct kitchen suka nufa wurin mom da baaba larai dake shirya dinner , kama masu aikin su kayi har suka kammala kowa ya nufi bedroom dinsa domin gabatar da sallar magrib wacce ake kira.
KAINAAT
_Lagos....._
Innah asabe ce a kitchen ita da fatima suna girki kiran sallar da a ke yine yasa fatima cewa "Innah kije kiyi sallah zan karasa aikin, to amma kefa, karki damu Innah kitafi kawai ( da yake tana fashin sallah ne) To shikenan, fita tayi daga kitchen din ta nufi dakin ta, shazim ne ya shigo cikin gidan jikin sa sanye da farar jallabiya da alama daga masallachi yake par Ammy ya nufa bai isketa ba sai yawuce bedroom din ta nan ma bata nan fitowa yayi daga part din ya nufi main parlor fatima ya gani ta fito daga kitchen hannun ta rike da food flask " Ammy bata dawo bane, eh bata dawo ba , ok ya fada hadi da Komawa part din sa, sanda Innah a sabe zata koma kitchen har fatima ta gama komai da yake sai da ta jira aka kira sallah isha tayi, kama mata kawai tayi suka gyara kitchen din, falo fatima tafita kiran daya daga cikin ma aikatan gidan tayi a waya domin yazo ya daukar masu a binchin su, sallama a kayi daga kofar falon hadi da turo ta, fateemah ce tace yawwa ilya hadi da shiga kitchen fitowa tayi hannun ta dauke da food flask din masu aikin mika mashi tayi , part dinsu ita da Ammy ta nufa bedroom din ta ta shige kayan jikinta tacire towel ta daura bathroom ta wuce domin yin wanka 10 minutes ta fito daga bathroom din dressing mirror ta nufa mai kawai ta shafa ta nufi clothes set dinta dama ta sanya pad tun a toilet shiryawa tayi cikin pajamas lemon green ta yafa mayafi white mai dan girma feshe jikin ta tayi da turare mai dadin kamshi fita tayi daga bedroom din a falon Ammy ta zauna kan sofa wayar ta dake charge tacire ta shiga chatting wurin 9:00 sai ga Ammy wacce shazim ya dauko falo ta tsaya shi kuwa up stairs ya haura sai 9:30 fatima da Ammy su kayi dinner dan shi shazim cewa yayi takai masa part din sa suna kammala wa fatima ta kwashe kayan da suka yi amfani dasu ta kai kitchen nan falo ta zauna suna fira da Ammy sai wuri 10:00 su katashi kowa ya shige bedroom dinsa
, zaune yake kan sofa dake bakin bed dinsa yana aiki a laptop dinsa sai wurin 12:00 ya rufe laptop din toilet ya nufa bayan 5 minutes yafi to jikin sa da danshin ruwa da alama alwala yayi, wardrobe dinsa ya nufa sallaya ya fito da Ita ya shim fida shafa'i da wutiri yayi ya jima kan sallayar yana adu'oi sannan ya niketa ya maida ta cikin wardrobe, bed dinsa ya nufa hadi da kashe bulbs din dakin bedside ya kunna, zama yayi daga bakin bed din adu'a yayi ya sha fa a fuskar sa sannan ya ida hawa kan bed din kwanciya yayi hadi da jan blanket yarufe iya kugunsa.
To nace Asuba tagari doctor nima bari naje na nemi nawa makwanchi.😴
Washe gari.......
Zaune Ammy da fatima suke kan dinning suna breakfast, shazim ne ya shigo jikin sa sanye da jogging suit black color sai p-cap white hannun sa rike da water bottle wurin su Ammy ya nufa " ina kwana Ammy fatan kin tashi lafiya ya fada Ammy tace "lafiya lau alhmdllh, yau baka zuwa abnoor ne, amsa ya bata da " A'a Ammy zanje, ok naga har 10:30 tayi Ammy ta fada , shazim yace " eh wlh nayi late wurin tashi daga bacci amma yanzu zan shiga ciki nashirya Insha Allah, to shikenan sai ka shirya ga breakfast dinka nan na jiran ka a dinning, to Ammy ya fada hadi da nufar part din sa.............
✨ _Victoria_ . ✨
Anguwace ta christianity irin ta masu kara min Karfi, destiny naga ni ta fito da ga wani gida ta nufi wan da ke opposite din inda ta fito jikin ta sanye da gown iya gwiwarta purple color kanta da kitson kalaba na attachment ka farta sanye da flat shoe, gidan dan karami ne, ko ina ya sha cement dakuna biyu ne a gidan nufar daya daga cikin kofofin tayi knocking hadi dacewa" excuse" daga cikin dakin naji ance "come in" tura kofar tayi hadi da shiga Victoria ce acikin
dakin tana ta faman jan straight gown taki shigar ta destiny ce tace " lallai Victoria a she bakima shirya ba kin kuwa san nisan da wurin ya ke da shi sai fa munfita Lagos kuma fa kinsan yau ana zuwa church da yamma, sorry destiny yanzu zan shirya mu tafi, abun da yasa ma nayi late bari nayi sai momy ( mahaifiyar ta ) ta tafi market sannan domin in tasan inda zamu ba zata bari mu tafi, Victoria naga ma shiryawa suka fita gidan tafiya sukayi sai da suka hau kan titi tukun suka tsai da mai mashin suka hau, tafiya su kayi mai dan nisa sannan suka kawo wani dan karamin kyauye duk duwatsu suna kawowa inda mashin bai wuce wa suka sauka, kudin sa suka bashi su kuma suka cigaba da tafiya nanma sai da su kayi tafiya ba laifi tukun suka kawo wata yar bukka ita kadai a wurin sai mutane jere a bakin bukkar suna karaso wa suma suka bi layi, sun jima a tsaye layi bai zo kansu ba, victoria harta gaji da tsayuwa ta duƙa, lokacin da layi ya zo kansu shiga sukayi tare cikin bukkar, wani mutum ne zaune gaban sa wasu kahuna ne sai kawunnan mutane kwaran gwal jikin sa sanye yake da jajayen kaya fuskar sa duk ta sha digedige fari sai idanun sa kewaye da bakin fenti gaishe dashi sukayi dawani irin yare mara dadin ji shi kuwa kwashewa yayi dawata irin dariya sannan ya tambaye su meke tafe dasu, destiny ce ta kora masa bayani a kan abun da yake tafe dasu, dariya ya sake kwashe wa da Ita sannan yayi yan surkullen shi wani magani ya dauko cikin wani bakin tulu ya basu destiny tasa hannu ta karba ita kuwa Victoria sai zare idanu take kudi suka dauka masu yawan gaske suka ajiye a gaban bokan sannan suka fice daga bukkar ta hanyar da suka biyo ta nan suka bi sai da suka kawo cikin kyauyen tukun suka samu wani mashindin ya dawo dasu gida,  gidan su destiny suka wuce dan lokacin kafe 4:15 dakin destiny suka nufa zama sukayi suna huce gajiyar tafiya destiny ce tace" ina zuwa" tana fada ta fice daga dakin batafi 1 minute ba ta dawo da kwano a hannun ajiye shi tayi gaban Victoria fita ta sake yi sai gata ta sake shigowa hannun ta rike da pure water guda biyu zama tayi hadi da bude kwanon sakwara ce da miyar okra ( kubewa) suna cikin ci saiga wani namiji ya shigo dakin sanye ya ke da crazy jeans sai singlet gashin kansa kuwa yasha dada ( yanda yan iska keyima gashin su ya koma kamar lagwani )da kaga yana yin sa zaka san a buge yake, ya na ganin Victoria ya kama washe baki  daure fuska Victoria tayi tana ganinsa , kusa da Ita ya matso kamar zai yi hugging din ta ba shiri ta mike tsaye hadi da daka mashi tsawa tana cewa" which kind of this nonsense samuel " bangane wulakanci ba Victoria you are my wife ya fada yana washe baki, destiny dai na gefe tana kallon su bata ce masu kala ba sai da taga Victoria na niyyar fita da ga dakin sannan taba Victorian hakuri shi kuma Samuel ce mashi tayi "ya fita ya basu wuri tun da shi ba shi da hankali , Victoria tace bata son shi to mi yasa zai ta kura ma rayuwar ta, Komawa Victoria tayi ta zauna sai wani cika take tana batsewa, suna kammala cin a binci fita su kayi bakin wani fanfu suka wanke hannu Victoria ce tace "destiny zan tafi gida domin nayi shirin zuwa church din kuma kin ga momy bata san nafita ba kar ta dawo bata ganni ba, kawai dai kinson zuwane amma aikin san bata dawo ba, da ta dawo da mun iske momy ( mahaifiyar destiny ) a gida itama ta dawo tun da wurin business din su daya, kuma tare suke fita su dawo tare, to kawai Victoria tace, komawa su kayi dakin, destiny tace " kinsan fatan da nake kuwa Victoria, Aa sai kin fada Victoria ta fada tana sauraron mi destiny zata ce, so nake wannan wawuyar hidaya ta taya ki bama dr hakuri kamar yarda da tace, a samu sa'a shi kuma ya maida ki uhmmm zata sha mamakin abun da zamuyi mata dan sai munrabata da eko ma gaba daya yan da ba zata sake ganin dr ba, nima haka nake so zata sha mamaki In dai ya mai da ni wuri na, dariya sukayi harda ta fawa suna nan suna shirya yan da za su yima hidaya sai ga mahaifiyar destiny tashi go , suna jin shigo warta suka fito daga dakin gaishe da Ita su kayi yayin da destiny ke amsar kayan da momyn ta ta shigo dasu, Victoria ce tace "ni na tafi" to saina shigo destiny ta fada tana fita gida ta shiga momynta ta samu a dakin zaune cewa tayi" good afternoon momy , afternoon daga ina kike na shigo baki nan momyn tafa da , ina gidan su destiny ne momy, ok kawai momyn tace, wurin 5:00 suka shirya domin zuwa church ( suna zuwa church su duk ranar Asabar domin gyaregyre sbd lahadi ) gidan su destiny , Victoria taje daga chan suka wuce church din.........
_Katsina......_
Mom ce zaune a main falo suna fira da baaba larai abdallah ne ke saukowa daga stairs case jikinsa sanye da jallabiya wurin su mom ya zu hadi da cewa fira kuke ne nagan ku zaune, wlh kuwa sai ina haka naga kasha jallabiya mom tafada amsa ya bata da cewa zan danje wani wuri ne daga nan zan tsaya sai angama sallah sannan zan dawo, mom tace" ah kace wurin diyata za'a amma sai kaje mata da jallabiya sai kace wani limami, murmushi kawai yayi hadi da cewa " mi za kiyi da wata diya keda kike da yan biyu duk mata a gaban ki, mom ce tace " duk da ina dasu kari ai bai kin dadi koh baaba larai" haka ne kuwa hajiya baaba larai ta bata amsa, Mom ce ta kuma cewa" ni dai yau she zaka kawo man surukata gidan nan" abdallah ne yace " ki bari mom dana samu wacce ta dace dani zan kawo maki Ita har gida, uhmmm Allah ya shirye ka abdallah wata kan har yanzu baka samu wacce tada ce da kai ba ko, nasan maganinka ai sawa xanyi abie dinku ya zabo maka mata tun da kai ka kasa Mom ta fada, abdallah yace" haba mom kamar ni za'a za boma mata, ai kuwa dana bani , yo ai sai abokaina suyi man dariya, mom tace" to In dai baka son auren dole to ka fito da mata kayi aure, kai ko kunya bakaji shekara 30 fa amma ace baka da mata haba ina amfani ' dan Allah mom kibar batun auren, dolenan , In dai aure ne very soon zanyi in Allah ya yarda, Allah ya yarda mom ta fada, ni na wuce sai na dawo ya fada hadi da nufar kofar fita, a dawo lafiya mom ta fada , fira mom suka cigaba Ita baaba larai suna nan zaune sai gasu Aaimah sun shigo da'a lama daga Islamiyya suke dan jikin su sanye suke da hijabi blue color gaishe da su su kayi sannan suka nufi bedroom din su wanka su kayi hadi da alwallar magrib sannan suka sanya kaya marasa nauyi a daki suka zauna har sai da su kayi sallah isha tukunnan suka fita falo fira sukeyi a kan Islamiyya anan mom tasa me su har da abie wanda baijima da dawowa ba daga masallachi nan sukai ta fira har 9:00 sannan su kayi dinner kowa ya wuce dakin sa suna shiga daki wayar Aairah na ringing dauko wayar tayi dake ajiye kan bedside murmushi tayi data dauki wayar taga mai kiran Aaimah ce tace " halan ya mus'af  ne, daga mata kai Aairah tayi to sai da safe domin nasan ke ba yanzu ba Aaimah ta fada hadi da hayewa kan bed taja blanket Ita kuwa Aairah zama tayi bakin bed ta cigaba da waya ba Ita bace ta gama wayar nan ba sai wurin 10:55 sannan ta haye bed adu'a tayi ta shafa hadi da shafa ma Aaimah sannan taja blanket Ita ma bayan ta kashe bulbs da bedside lamp.....
Asuba ta gari yan biyu 😴
Episode 7_8
Mom ce zaune a main parlor suna fira da baaba larai ya abdallah ne ke saukowa daga stairs case jikinsa sanye da jallabiya wurin su mom ya nufo hadi da cewa "fira kuke ne nagan ku zaune? "
"eh , sai ina haka nagan kasha jallabiya" mom ta fada amsa ya bata da cewa zan danje wani wuri ne daga nan zan tsaya sai angama sallah sannan zan dawo, mom tace" ah kace wurin ɗiyata za'a, amma Sai ka je mata da jallabiya Sai kace wani limami," murmushi kawai yayi hadi da cewa " mizakiyi da wata diya ke da kike da yan biyu duk mata a gaban ki, mom ce tace " duk da ina dasu ƙari ai bai ƙin daɗi koh baaba larai? " haka ne kuwa hajiya baaba larai ta bata amsa, Mom ta kuma cewa" ni dai yaushe zaka kawo man surukata gidannan? " abdallah ne yace " karki damu mom, dana samu wacce ta dace dani zan kawo maki ita har gida, uhmmm Allah ya shirye ka abdallah wata kan har yanzu baka samu wacce tada ce da kai ba ko, na san maganin ka ai, sawa zanyi abie dinku ya zabo maka mata tun da kai ka kasa Mom ta fada, ya abdallah yace" haba mom kamar ni za'a zaɓo ma mata , ai kuwa dana ji kunya, yo ai sai abokaina suyi man dariya, mom tace" to In dai baka son auren dole to kafito da mata kayi aure kai ko kunya bakaji shekara 30 fa amma ace baka da mata, haba ina amfani ' dan Allah mom kibar batun auren dolen nan In dai aure ne very soon zanyi in Allah ya yarda, Allah ya yarda mom ta fada, ni nawuce sai na dawo ya fada hadi da nufar kofar fita, a dawo lafiya Mom ta fada , fira mom suka cigaba Ita baaba larai sai gasu Aaimah sun shigo daga Islamiyya jikin su sanye da hijabi blue color, gaishe dasu su kayi sannan suka nufi bedroom din su , wanka sukayi hadi da al'walar magrib sannan suka sanya kaya ma rasa nauyi a daki suka zauna har sai da sukayi sallah isha tukunnan suka fita parlor,kan sofa suka zauna suna  fira islamiyya a nan mom ta same su harda abie wanda baijima da da wowa ba daga masallachi nan suka zauna suna  fira har 9:00, sannan sukayi dinner kowa ya wuce dakin sa , suna shiga daki wayar Aairah na ringing dauko wayar tayi dake ajiye kan bedside tana murmushi ganin mai kiranta, Aaimah ce tace " halan ya mus'af ne, daga mata kai Aairah tayi, to sai da safe domin nasan ke ba yanzu ba Aaimah ta fada, bed ta nufa ta kwanta taja blanket , Ita kuwa Aairah zama tayi bakin bed ta cigaba da waya, ba ita bace ta gama wayar nan ba sai wurin 10:55 sannan ta haye bed, adu'a tayi ta shafa ta shafa ma Aaimah sannan taja blanket Ita ma bayan ta kashe bulbs da bedside lamp.....
_Washe gari........_
Zaune suke kan sallaya suna adu'a da tasbihi, tashi Aaimah tayi daga kan sallayar ta nufi inda suke Ajiye Alqur'ani , guda ɗaya ta ɗauko, kusa da Aairah ta dawo ta zauna hadi da mika mata tana cewa" sister amsa in karanto maki haddar da nayi, inda nayi kuskure saiki gyara man,"
to in dan na gama maki nima sai ki amsar man"to Aaimah " karatu ta fara cikin ƙira'a mai daɗi ,Aairah na sauraron ta  inda tayi kukure sai ta gyara mata, sai da suka gama amsar ma junan su hadda tukunnan suka mai da qur'anan wurin da suke a jiye su , fita suka yi daga bedroom saboda gari ya waye Ƙarfe 7:00 na safe,  main parlor suka nufa a kitchen suka samu mom da baaba larai suna hada breakfast gaishe dasu sukayi , amsa masu su kayi cikin kulawa Mom tace " ina fatan dai kungama hardar ku ta yau, eh mom , to masha Allah, baaba larai tace " kace muna da bikin hadda dana kammala makarantar gagarumi gidan nan, to Allah ya taimaka ya nuna mana lokacin lpy" har hada baki suke wurin cewa ameen, kama masu aikin su kayi harsuka gama sannan su Aairah suka jera kan dinning, bedroom din su suka koma domin shirin zuwa Islamiyya ( Islamiyyar harda suke, in suka tafi tun safe sai yamma duk ranar weekend, Idan kuma ba weekend bane karfe 2:30 suke zuwa sutaso da yamma, amma ban da ranar Friday in kuma an yi hutun school to kullum ne ban da friday .)
Aaimah ce ta fara shiga toilet domin yin wanka ita kuma Aairah uniform dinsu na Islamiyya ta dauko masu tare da bags dinsu , Aaimah na fitowa itama ta shiga shaf shaf Aaimah ta shirya cikin uniform din san da Aairah ta fito har Aaimah ta gama shirin ta ita ma cikin kankanin lokaci tashirya suna gamawa suka fice zuwa main parlor dinning suka nufa domin yin breakfast suna gamawa part din abie da na mom suka nufa domin ce masu zasu tafi , a dawo lpy suka yi masu , fita su kayi harabar gidan anan suka samu mudi na jiran su dan shine ke kaisu, sai wurin 10:00 su mom su kayi nasu breakfast din saboda weekend........
✨ _SHAZIM_ ✨
Yau sunday baya zuwa aiki , kwance yake kan sofa a bedroom din sa ya baje papers da laptop din sa yana,  tun da ya gama sallar asuba ya ke nan wurin yana aiki har bacci yayi awan gaba da shi, jikin sa sanye yake da jallabiya, wayarsa ajiye saman cikin sa yayin da ya sa ɗayan hannun sa ya rufe fuskar sa, wayar sa dake saman cikin sa ce ta fara ringing, hannun sa dake kan fuskar sa ya janye yana ya tsina fuska alamar an katse mashi baccin sa , daukar wayar yayi "Brother" shine sunan daya bayyana akan screen din wayar picking call din yayi hadi da Kara wayar a kunne " hello Yaya na cikin wayar ya fada, "ba zaka chanza ba ko noraiz , ina amfanin wani hello kana muslim "
  " a fuwan big bro noraiz ya fada, Allah ya shirye ka, ameen Yaya ka tashi lpy yasu Ammy da fatima? , lafiya lau suke kaifa, Ina fatan kai ma kana lafiya? , ina lpy Yaya, oka Masha Allah shazim ya fada hadi da cewa ya maganar da wowar ka yau, domin da naga kiranka nayi tuna nin kace man ka iso dan nasan halin ka da chanza lokaci idan zaka dawo , A'a ba haka bane Yaya ina nan zuwa yau din Insha Allah , kawai dai ban samu biyo jirgin safe bane shiyyasa nakira ka na fada maka sai dai da yamma insha Allah, ok Allah ya kawo ku lpy, ameen Yaya sai an jima, ok kawai shazim ya faɗa hadi da kashe wayar ya ajiyeta kan center table, sai da yayi 5 minutes a kan sofar  sannan ya mike, papers din da ya baza ya kwashe da laptop ya saka cikin din briefcase, cire jallabiyar dake jikin sa yayi ya koma da gashi sai shorts toilet ya nufa ya jima a toilet din sannan ya fito ya nufi dressing mirror anan ma ya jima yana yan shafe shafe sai kace mace sannan ya nufi clothes dinsa shiryawa yayi cikin jeans and T_ shirt fita yayi daga bedroom din part din Ammy ya nufa a parlor ya same ta Ita ka dai, fatima na Islamiyya, gaishe da Ita yayi , amsa mashi tayi wuri ya samu ya zauna kusa da ita, Ammy tace " ga breakfast dinka chan kan dinning tun dazu har nayi tuna nin yau baka fitowa a daki za kayi weekend , wane ni Ammy , kina a gida na zauna daki, ai dole na fito na tayaki fira, tun da auta na Islamiyya kuma rigimenmen ki baya nan duk da yau zai dawo , murmushi kawai Ammy hadi da cewa kunyi waya da shine naji yace da safe jirginsu zai taso, kin dai san halin ka yanki Ammy da chanza lokaci inzai dawo, wai kuma yanzu sai yamma tukun, Allah ka shirya mai babban suna kai dai, ameen Ammy ya fada hadi da tashi ya nufi dinning, warmer din dake kan dinning din ya shiga bu dewa yana duba abun da ke cikin su. cup ya dauka ya hada tea sannan ya zu ba arish, wurin Ammy ya dawo ya zauna suna fira shi da Ammy yayin da shi kuma yake cin abincin sunjima suna fira har aka fara kiran sallar zuhur sannan su ka tashi Ammy ta nufi dakinta shi kuma ya nufi part din sa domin yin alwala.....
✨ _HIDAYA_ ✨
 Flat house ne me kyan gaske Masha Allah na masu rufin asiri kutsa kai nayi cikin parlorn gidan wanda komai na cikin sa brown color ne, hidaya naga ni zaune kan dinning ta lunch ita da mahaifiyar ta kamanin su ɗaya, tashi hidaya tayi mahaifiyar ta tace " mi ki ke nufi, naga kin tashi ? "
" na ƙoshi ne mama" wai ni kam hidaya mike da munki ne, a ce kwata kwata mutum baya son cin abinci, ko baki da lafiya ne,"
" lpy ta kalau mama,  dan nayi breakfast a makare ne , amma lafiya ta qalau, to shikenan, bedroom din ta ta nufa, kayan jikin ta ta cire ta shiga  toilet ta dan jima sannan ta fito jikinta daure da da towel, dressing mirror din dake dakin ta nufa simple make-up tayi sannan ta nufi wardrobe din dake kusa da dressing mirror din, gwon ta dauko ta atamfa da mayafi, shiryawa tayi cikin kayan Masha Allah dan bakaramin kyau kayan sukai ma fatar taba, da yake hidaya chocolate ce ita ba faraba sannan ita ba baka ba,  wayarta dake kan bed ta dauka da jaka wurin da takalmanta suke ta nufa É—an flat shoe ta dauko tasa , fice wa tayi daga dakin bedroom din ta nufi na mamar ta zaune ta same ta kan gado sallama tayi hadi da cewa" mama zan tafi gidan su maryam" mama tace " to shikenan sai kin dawo ina gaishe da hajiya lubabatu, sannan karfa kiyi yamma kinsan dai Baban ku yana gari, insha Allah mama bazan jima ba zan dawo, to saikin dawo fita tayi daga bedroom din hadi da ficewa , a bakin gate ta tsaya tana neman abun hawa bata jima ba ta samu napep shiga tayi sannan ta yima mai napep din kwatancen anguwar da zai kaita, tafiya sukayi mai dan nisa balaifi sannan suka iso wata anguwa  bakin gate din wani gida yayi parking me napep din fita tayi hadi da bashi kudinsa ya wuci ita kuma ta nufi gidan, mai gadi ta samu zaune akan É—an benchi, gaishe da shi tayi, ya amsa mata yana faÉ—in "yasu mama ku, suna lafiya da alama ya santa shiga tayi cikin gidan, part biyu ne gidan daya daga ciki part din ta nufa shiga tayi tai parlor gidan yake kamar ba kowa wani dan corridor ta nufa É—akuna ne kusan guda hudu ƙofofin su na kallon juna wanda, ke farko ta shiga bedroom ne mai kyau , bed ne sai wardrobe da toilet da dressing mirror, ba kowa dakin sai karar ruwa daga cikin bathroom alamar a kwai mutum a ciki wuri tasamu gefen bed din ta zauna batajima da zama ba sai ga maryam ta fito daga bathroom daure da towel " a she dai zaki zo maryam din ta fada , wlh kuwa , zan zo mana, ykk ya gida ya su mama, lpy qlu suke maryam ta fada hidaya tace " bakowa ne gidan sai ke kadai? "Â
" A'a suna nan , kawai dai suna É—aki ne, ok, naji shiru ne da na shigo , A'a suna nan bari dai nasa kaya dai" maryam ta fada haÉ—i da nufar wardrobe, kaya ta dauko riga da skirt na martial , shaf shaf ta shirya sannan ta dawo wurin hidaya ta zauna tana fadin " wai ni kam sister ya kuka kare da Victoria kinsan tun ranar da ku kayi fada da ita, bamu sake wata magana ba, ya kuka kare naga dr ya mai da ki wurin ta, kin kuwa san dadin da naji, domin nasan insha Allah burinki ya kusa cika" hidaya tace " bakomi , bamu sake wata magana da ita ba da sunan sa in sa ba, dan har roÆ™una su kayi ita da destiny akan na taya ta bama dr hakuri ya maida ta wurin ta, to ke saikika ce mata mi? Maryam ta fada ta na tsare ta da idanu , hidaya tace " mazan ce kuwa maryam, tun da ta roÆ™e ni mi zai hana, amma wallahi hidaya baki da hankali sai kawai kije kice ma dr dan Allah yayi ma Victoria hakuri koh, uhmmm ko dai yanzu kin haÆ™ura da shi ne baki son sa yanzu? Maryam ta jefa mata tambaya hidaya tace " wlh maryam bazan boye maki ba ina son dr har zuciyata, to amma shine zaki taya ta kuma kinsan cewa son shi take, dama kawai take jira ta raba shi da kowa , to ya zanyi maryam, komi tayi dan kanta tun da har ta roÆ™eni zan taya ta mana,maryam tace " uhmm sannu uwar masu tausayi tun da ta rokeki ai sai ki bashi haÆ™urin, wlh ke ba kisan wacece Victoria da destiny ba, su kan su muna funtar junan su suke yi inma baki sani ba to kisani ita kanta destiny din son dr take muna funtar Victoria kawai take, shiyyasa kike fadan haka ni da na daÉ—e dasu ni zan baki labarin ko su su waye garama tun wuri ki mai da hankalin ki a kan dr ki kyale wata Victoria da destiny chan , amma fa inkinji shawarata, dan wallahi kika tai make su, sai kinyi dana sannin haka, amma fa inkinji, shikenan ngd sosai da shawarar ki , amma sister sai nake ganin kamar dr bazai soni ba, kina ganin in ya shigo hospital duk matan dake hospital din bamu isheshi kallo ba, amma zan ciga ba da rokwan Allah in har shi alkairi ne a rayuwa ta Allah ya tabbatar man, to ameen, amma ya ka mata kisanar dashi cewa kina son sa, ko ba komai zai san ke masoyiyar sa ce, koya kike gani, zanyi kokarin haka insha Allah, amma gaskiya  ina tsoron abun da zai biyo baya karma ya zo ya da katar dani kamar yan da yayi ma Victoria , abun da bazan soba kenanÂ
Maryam c tace " to idan baki fada masa ba taya zai gane kina son shi , ki fada masa kawai insha Allah ba abun da zai biyo baya sai Alkairi kuma insha Allah zan taya ki da adu'a, smeen sister nagode sosai Allah ya barmu tare, ameen karki damu maryam ta fada chanza firar su kayi zuwa wata suna nan zaune har a kayi sallar asr , sallah suka tashi su kayi sannan suka fita daga dakin suka nufi parlorn gidan
Wannan kenan..........
✨ _Ammy_ ✨
Zaune take kan sallaya a bedroom dinta bata jima da gama yin sallah ba wayar ta da ke kan dressing mirror ce tayi ringing hannu tasa ta dauko wayar murmushi tayi hadi dacewa "Allah sarki mai babban suna ina jin ya kara so, daga wayar tayi hadi da Kara wayar a kunne sallama tayi da murmushi a fuskar ta, on the other hand na cikin wayar yace wa'alaikumus salam my Ammy ya gida, lafiya lau mai babban suna ya hanya, alhmdllh ammy  mun kusa sauka insha Allah , nan da Karfe 5:30 shiyyasa na kira ki fada ma ilya yazo ya dauke ni na kira Yaya bai dauka, may be baya kusane Ammy ta fada" to Ammy ki fada ma ilyan, yanzu kuwa Allah dai ya kawo ku lpy, ameen Ammy wlh harna ƙosa na ganni kusa da ke, Allah dai ya dawo da kai lafiya, ameen ya fada, kashe wayar tayi , mike wa tayi daga kan sallayar parlor ta fita kan sofa ta zauna , number ilya ta shiga nema cikin wayar ta sai ga fatima ta dawo daga Islamiyya wurin Ammyn ta nufo hadi da cewa " barka da gida Ammy, mikike yi zaune ke kadai s parlor? , ta fada yayin da take samun wuri kusa da Ammy ta zauna, amsa Ammy ta bata da "number ilya nake nema saboda zai dauko mai babban suna , ya noor ya dawo ne ta fada hadi da mikewa harzata nufi upstair Ammy tace " dawo uwar zumuɗi cewa nayi zai dauko shi bawai ya dawo ba" da wowa tayi tana turo baki gaba hadi da cewa "to Ammy ƙarfe nawa zai dawo , Ammy tace" ƙarfe 5:00 insha Allah jirgin su zai sauka, shiyyasa yace a kira mashi ilya yaje ya dauko sa;; Ammy dan Allah zanbi ilya inzai tafi, cewa Ammy tayi" to shikenan maza kije " bata ma tsaya sauraron mi Ammy zata ce ba ta nufi dakin ta da sauri, wanka ta fara shiga bata jima ba ta fito sanye da bathrobe shaf shaf tashirya cikin doguwar riga abaya tayi rolling da gyelen a kanta, wayar ta kawai da jaka ta dauka ta fice daga dakin inda tabar Ammy nan ta sa meta,  ƙara sowa fatima tayi wurin ta tana fadi" yawwa Ammy na shirya kinyi ma ilyan magana " A'a bari nayi sai kin shirya tukunnan , ai a kwai sauran lokaci, duka yanzu ƙarfe 4:00 kuma kinga cewa yayi sai 5:30 jirgin zai sauka
Ammy ai da kinyi mashi magana, kinsan fa a kwai nisa Airport din zamu yi kusan 20 to 30 minutes bamu kai ba fah kuma ga go slow" Ammy tace "haka  ne nasha'afa ne shiyyasa amma bari na kira ilyan ya fitar da mota sai ku tafi ta fada yayin da take kiran ilya a waya yana picking tace " ilya ka fitar da mota zakuje Airport kai da fatima domin dauko mai babban suna yana hanya, to Ammy insha Allah yanzu kuwa zan fito da ita ilya ya fada da yake shima Ammy yake cewa, to shikenan ga fatimar nan fito wa Ammy ta fada hadi da rejecting din kiran, mike wa Fatima tayi hadi da cema Ammy sai sun dawo a dawo lafiya Ammy tayi mata sannan ta tashi ta nufi , kitchen innah Asabe ta samu a kitchen din tana gyarashi domin fara shirye shiryen dinner , Innah asabe na ganin ammy tace " barka da fitowa hajiya, da yawwa Ammy ta amsa mata" kina bukatar wani abune ? Innah asabe ta fada saboda ganin Ammyn datayi a kitchen a wannan lokaci " eh kinsan mai babban suna na hanya to shine nake son a daura dinner tun yanzu , kuma shima shazim bai ci komai ba ya fita ga fatima ita ma kuma, kinga in aka gama da wuri zai fi ai, innah asabe tace"ah yaufa muna da babban bako,shiyyasa naga fatima ta wuce da gudu dan bata ma lura da niba Ammy tace" kinsan halin Fatima da zumuɗin, ai ina ce mata yana hanya duk tabi ta rude tana chan tabi ilya Airport, dariya Innah Asabe tayi hadi dacewa" Allah dai ya kawo shi lafiya, ameen Ammy tace shirye shiryen daura dinner suka shiga yi..
✨ _SHAZIM_ ✨
 shigowa yayi main parlor bakinsa dauke da sallama, da alama daga waje yake baya cikin gidan, su Ammy dake kitchen suka amsa mashi sallamar, fitowa Ammy tayi daga kitchen din tana cewa" kai ashe baka gidan, ka kuwa yi waya da ƙanin ka? ya ce man ya kira wayarka baka dauka ba "
" Eh na ɗan fita ne tun dazu har bedroom din ki nazo na same ki kina bacci, wayar na silent ne sai daga baya naga kiran sa, yace man ai kunyi waya akan kitura mashi ilya ya dauko shi, eh Ammy ta fada hadi da Komawa kitchen din shikuma part dinsa ya nufa,  bedroom dinsa ya wuce kayan jikin sa ya rage ya nufi toilet bayan kamar 15 minutes sai gashi ya fito sanye da bathrobe dressing mirror dinsa ya nufa hadi da zama kan stool din dake gaban mirror din, ya jima yana yan shafe shafensa sannan ya nufi wardrobe , shiryawa yayi cikin kana nun kaya riga da wando, wandon baki iyakar sa gwiwarsa sai rigar fara mara nauyi mai gajeran hannu, wurin dressing mirror ya koma feshe jikin sa yayi da turare sannan ya fita daga bedroom din ya nufi down stairs parlorn Ammy, dinning ya nufa yaga bakomi, fita yayi daga parlorn ya nufi kitchen wurin su Ammy yana shiga yace " Ammy akwai abinci, yunwa nake ji, gashi nan ana girkawa saura ka dan mukarsa Ammy tafada, gaskiya Ammy bazan iya jiraba sosai nake jin yunwar babu wani abu koda mara nauyi ne? Ya tambaya, Ammy ta ce" bari na yanka maka fruit ta fada hadi da bude fridge ta dauko fruit ta wanke yanka mashi tayi ƙanana ta zuba mashi a ɗan bowl ta mika mashi amsa yayi hadi da cewa " nagode sosai Ammy sannan ya fice daga kitchen din, main parlor ya koma TV ya kunna hadi da daukar remote yana chanza channel zuwa TVC news, zaman shi yayi kan sofa yana shan fruit tana kallo
Wannan kenan............
🌹~ _KAINAAT_ ~ 🌹
_MURTALA MUHAMMAD INTERNATIONALÂ AIRPORT
Mutane ne iri iri wasu najiran time din da zasu hau jirgi, wasu kuma sun zo daukar yan uwan sune, wasu na cikin mota wasu na zaune akan chairs din da aka ta nada domin masu zama.
Motar su fatima ce ta kara so cikin airport din parking lot din dake wurin ilya ya nufa parking yayi, fatima ce tabfara fitowa sannan shima ya fito, cikin airport din suka nufa inda mutane ke zaune fatima ta nufa, wuri ta samu ta zauna , wayar ta da ke cikin bag ce ta fara ringing fito da ita tayi "YA DR" shine sunnan daya bayyana akan screen din wayar, picking call din tayi hadi da sallama, on the other hand nacikin wayar ya amsa mata sallamar " ina wuni ya dr , ya gida ya kwana biyu, lafiya lau Alhmdllh Bintalo, turo baki Fatima tayi cikin shagwaba tace" haba Yaya nace fa bana son sunnan amma baka dai na ceman ba, ta fada tana dan bubuga kafafu, dariya na cikin wayar yayi, ai kuwa nan tashiga yi mashi kukan shagwaba tana cewa " dariya ma na baka koh"
"sorry fatimaaaaaa" ya fada hadi da jan sunan,
Uhmmm kawai tace,
sake mgn nacikin wayar yayi "bana ce kiyi hakuri ba, ai duk laifin kine kinsan fa nace kibar ceman ya dr nan da kika kware wurin kirana dashi, shiyyasa nima nace maki haka kinga nima na rama kenan, amma kiyi hakuri bazan sake ba kinji" "shikenan Yaya ya wuce"
"Yawwah koke fa, yasu Ammy kina ina ne haka naji hayaniyar mutane?
amsa ta bashi da " Ina airport , munzo daukar ya noor ne "
" ok yau zai dawo kenan, kice ina gaishe dashi ina mashi ya gajiyar tafiya "
" to zai ji Insha Allah yaya "
" ok take care of your self for me pls, bye" ya fada, itama " bye" tace masa hadi da rejecting call din, game ta shiga bugawa a wayar tana nan zaune aka fara sanar war iso war jirgin 5:30 tashi tayi ta koma inda mutane ke tsai tsaye domin tarbar yan uwan su passengers ne suka fara biyo wata kofa da aka rubuta EXIST da manya harafi wacce domin su aka tana de ta fatima dai na nan tsaye, mutane kuwa wanda suga yan uwan su nata rugawa da gudu suna tarbarsu, ita dai sai zare idanu take sokawai take taga ta ina ya noor din ta zai bullo. Wani matashin saurayi ne ya bullo jikin sa sanye da ƙananun kaya jeans and T -shirt na company gucci, jaka rataye a kafadar sa baka jikinta an rubuta ADIDAS da farin paint da manyan haruffa, hannun sa rike da trolley yana ja P-cap ce a kansa sai face mask akallah zai yi kimanin shekara 25 a duniya.
Fatima ce ta rugo da gudu tana fadin ya NOORRR tana nufar wannan saurayin, sakin trolley din dake hannun sa yayi fa dawa tayi jikinsa tana dariya hadi dacewa " shine kawani boye face dan nasha wahala wurin gane ka koh " janye ta yayi daga jikinsa yana cewa " Autar Ammy kedai haryau Allah baisa kinsan cewa kingirma ba koh, fatima tace " haba ya Noor haka ma za kace koh, shikenan tunda baka yi farin ciki da ganina ba " ta fada hadi da juyawa zata bar wurin, hannun ta ya riko yana cewa " sorry my yar qanwerh, wasa fa nake maki, kema kinsan nayi farin ciki da ganin ki autar mu " ya fada hadi da jan kumatunta tana dariya " koke fah " ya fada hadi da cire facemask din da yasa MASHA ALLAH nafada daganin wannan kyakyawar fuskar ta Noraiz kamannin sa daya da fatima , dan dai shi namijine ita kuma mace.
ilya ne yakaraso inda suke yana washe baki Noraiz yace " kice tare kike da ilya Ammy " ya fada yana mikama ilya hannu domin suyi musabaha.
ilya  yace " ina wuni, ya hanya, ya aka baro mutane turai " dariya fatima da Noraiz sukayi jin ilya yace wai ya aka baro mutanen turai, amsa mashi Noraiz yayi da " alhmdllh ilya ya gida " amsawa ilya yayi da " lafiya qlu " ilya yace hadi da daukar trolley din Noraiz suka bar wurin, parking lot suka nufa booth ilya ya bude ya saka trolley da jakar Noraiz, shiga sukayi cikin motar Noraiz da ilya naga ita kuma fatima na baya, key ilya yayi ma motar suka bar airport din, hanyar gida suka nufa suna tafe suna fira Noraiz ne yace " wai ina ya shazim fatima " amsa ta bashi da "may be yana gida , danni banjima da dawowa daga Islamiyya ba na biyo ilya"  "ok " kawai Noraiz yace yayin da suka iso anguwar su horn ilya yayi time dinda suka iso bakin gate din gidan, megadi ne ya bude masu gate din, ilya ya danna kan hancin motar ciki, parking lot ya nu fa parking yayi, fitowa su kayi daga motar suka nufi cikin gidan, ilya na biye da su a baya hannun sa dauke da trolley da bag din Noraiz.
Shiga sukayi cikin gidan bakin su dauke da sallama
Da sauri Noraiz ya nufi shazim dake zaune kan sofa, hugging din sa yayi hadi da cewa nayi missing din ka yy sosai
shafa kansa shazim yayi kamar wani karamin yaro yana cewa " to ai yanzu komai ya wuce tun da gaka nan ka dawo"
" haka ne kuwa yaya " Noraiz ya fada
Ammy ce ta fito daga kitchen ita da Innah Asabe wurin su suka nufa Ammy nace wa" oyoyo mai babban suna " tashi Noraiz yayi ya nufi Ammy hugging dinta yayi yana cewa " nayi kewar ki sosai Ammynah " nima nayi kewar ka mai babban suna " Ammy ta fada, Innah Asabe ce ta matso tana cewa " marhabun lale mai babban mutum, ya hanya, ya kuma karatu " Amsa ya bata da " alhmdllh " nan suka shiga firar yau she gamo, ilya haurawa yayi upstairs domin kaima Noraiz kayan sa part din sa, baijima ba ya sauko yana cema kayan na part dinka nakaima maka.
godiya Noraiz yayi mashi, ficewa ilya yayi ya koma bakin gate wurin mai gadi dama nan take zama.
Noraiz ne yatashi yana cewa " zanshiga na watsa ruwa na fito naga time din sallah magrib yakusa" ya fada yayi da yake haurawa upstairs.
Ammy c tace " shazim  abincin fa koba yanzu ba "
"A'a Ammy sai an jima in mun dawo sallar magrib sannan" to shikenan " Ammy ta fada , tashi yayi ya nufi upstairs shima
Ammy ma da Innah Asabe nasu bedroom din suka nufa aka bar fatima ta gyara kitchen da jera abinchi kan dinning (Â sbd bata sallah )Â tana gama wa itama ta nufi nata bedroom din wanka tashiga (Â dama tana yin wanka kusan sau hudu arana intana period )
✨ _NORAIZ_ ✨
Fitowa yayi daga bathroom sanye da bathrobe  ( part din sa shima ya hadu sai dai bai kai na shazim girma ba, amma dai masha Allah yayi kyau ) dressing mirror yanufa mai kawai yashafa ma jikin sa yanufi clothes set dinsa jallabiya ya dauko black color yasa wurin kayan sa da ilya ya kawo masa ya nufa, turare ya dauko cikin jakar sa ya fesa gadi da mai dashi
Ficewa yayi daga part din dama yayi alwala tun a toilet , part din shazim ya nufa dake kusa da nashi
yana shiga shazim din na fitowa daga bedroom din shima sanye ya keda jallabiya
Ficewa kawai sukayi suka nufi masallachin dake chan main gate din gdn basune suka dawo cikin gidan ba sai da su kayi har isha tukun suka dawo cikin gdn
parlorn Ammy suka yada zango fatima kadai suka samu zaune a parlorn suna zama sai ga Ammy ta fito wuri ta samu ta zauna tana cewa " to a tashi ga abinci chana najira " to suka cemata hadi da nufar dinning din Fatima ce tayi serving din su.......
✨ _KATSINA_ ✨
Zaune suke kan dinning suna dinner su duka gidan baka jin komai sai karar plate da spoon
Suna gamawa abie da abdallah da Mom suka koma kan sofa yayin da su Aairah ke gyara dinning din, suna gamawa wurin su abie suka dawo suka zauna fira suka shiga yi abie na tambayar su yaushe zasu fara exam din SSCE " saura 3 weeks abie " suka bashi amsa " to Allah ya bada sa'a, da Ameen suka amsa " abie wace school zaka kaimu in mungama " Aaimah ta tambaye shi" ban gane inda zan kai kuba , kuda kuke da school a cikin grinku, a i ba sai kunje wani gari ba " abie ya fada yana tsare su da idanu " A'a gaskiya abie Muyi primary school da secondary school a nan sannan kuma ace munyi high school a nan gaskiya abie s chanza mana " to sai dai kunga ma exam din tukunnan, to shikenan abei " chanza firar sukayi zuwa wata, sai kusan 9:30 sannan su Aairah suka nufi dakinsu sbd sun fara karatun exam gakuma zuwa school gobe
Suna shiga bedroom din su wanka sukayi hadi da sanya pajamas dinsu sannan suka dauki books dinsu suna dubawa sai wurin 12:00 sannan sukayi bacci.......
Episode 9_10
Sanye suke da uniform din su na school, ko wacce rataye da school bag din ta, ficewa su kayi daga bedroom din suka nufi main parlor su Mom suka samu kan dinning suma basu jima da zuwa dinning area ba, gaishe dasu su kayi hadi da samun wuri kan dinning din suka zauna, abie ne yace " yau yan biyu an shirya dawuri kenan " amsa suka bashi da " eh abie "
"to Allah ya taimaka ya ba da sa'a"
da ameen suka amsa, mom ta miko masu tea da ta hada masu " thanks Mom" suka fada hadi da sa hannu suka Karba, basu fi minti 10 ba suka tashi suna goge bakin su da tissue paper suna fadin sai mun dawo , a dawo lpy su mom suka yi masu fice wa su kayi suna fadin Allah yasa.
Suna fita daga gidan sai ga school bus dinsu ta shigo anguwar, sai da ta kawo dai dai inda suke tayi parking, kofar bus dince ta bude shiga su kayi daga ciki suka nemi wuri suka zauna kusa da wannan friend din ta su Aeesha
Aeesha tace "twin friends yau wace rana kun fito da wuri kun hau bus first round " ta fada da murmushi a fuskar ta " kedai bari kawai Aeesha sa'a ce kawi yau " Aairah tafada yayin da Aaimah ke cewa " sai kace kema kullum da wuri kike zuwa Aeesha " dariya Aeeshar tayi hadi da cewa " ai wlh duk da haka gara ni dai "
"bawani nan, wlh kema muguwar let comer ce " Aaimah tafa da yayin da bus din keshiga cikin School
bus stop, bus din tanu fa parking tayi aka bude kofar student nata fita suna nufar assembly ground
Inda ss 3 ke tsayawa nan su Aairah suka nufa annan suka samu sauran yan class din su wanda suka zo dawuri, gaisawa suka shiga yi.
bayan 30 minutes aka gama assembly kowa ya nufi class din su
✨SHAZIM✨
Saukowa suke daga upstairs shi da Noraiz parlor Ammy suka nufa, kan dinning suka same ta , gaishe da ita su kayi Noraiz yace " ammy ina fatima nagan ki ke kadai kan dinning? " amsa ta bashi da " Fatima ai ta wuce school"
" kai na manta fah, amma Ammy yau she take gama wa ne "
" tace man dai next month zasu fara exam, daga wannan week din ma ta gama zuwa school sai kuma exam "
" Allah ya taimaka ya bada sa'a, yaya " Noraiz ya kira Shazim dake zaune yana sauraron su, da na'am ya amsa mashi , Noraiz yace " amma dai yaya fatima a abuja zatayi  university kamar yanda take bukata intagama secondary school "sai da yayi kusan 5 seconds sannan yace "A'a nan za tayi school din ta gata ga ammy, " ya fada fuskar sa babu a lamun wasa, hankan yasa dole Noraiz ya kama bakin sa yayi shiru amma baiji dadin shawarar da yayan nasu ya yanke ba, saboda fatima ta ƙwallafa rai akan zuwa abuja saboda sa'ada , " Allah ya taimaka " kawai yace yaci gaba da breakfast din sa, Ammy duk da ta fison fatimar tayi karatu kusa da ita.amma sai tace "wai shazim mi yasa kake haka ne, tun da kai ka janye jiki da abuja, mi yasa suma zaka sa dole sai sun janye jiki da abuja ne wai, miye ai bun dan tayi karatu a can, duk ni ma nafi son tayi kusa da ni" ɗan nisawa yayi sannan yace "ammy ni ba haka nake nufi ba, kwai naga zaki yi kaɗai ci ne, ke kaɗai a gida "katse shi ammy tayi da cewa "in dai dan ta nine karka hanata zuwa abuja, idan bata nan baga ku nan ba kai da noraiz "
"ammy mu ba zama muke ba, idan muka fita tun safe sai dare fa muke da wowa"
"to naji sai dare kuke da wowa, itama idan ta je makaranta ba sai da yamma zata riƙa dawowa ba? " ta ƙarasa faɗa da sigar tambaya tana tsare shi da idanu
"ammy dan Allah kiyi haƙuri tayi karatun ta nan, itama sai ta fi jin daɗi karatun, chan haya niyar innah kawai ta ishe ta " uhmm kawai ammay tace ba tare da ta sake cewa komi ba ,
Ba wanda ya sake magana cikin su har suka kammala breakfast din , shazim ne ya fara ajiye fork din da yake cin arish hannu ya mika ya yagi tissue din dake kan dinning ya goge bakinsa sannan ya dauki robar ruwa ya sha, ya mike ya nufi sofar da ya ajiye briefcase dinsa ya na fadin "Ammy nizan wuce" cup din tea din da ta kai baki ta janye tana fadin " a dawo lafiya , Allah ya ba da sa'a, an jima ka dan zanje gidan baba may be baza ka same ni sanda zaka dawo, dan zanjima kilama sai dare ma zan dawo "
" ameen, ina gaishe da malam, sai na dawo" ya fada yayin da yake shirin barin parlorn, Noraiz yace " a dawo lafiya Yaya, Idan na ajiye ammy gidan malam zan biyu ta wurin ka insha Allah "
" Allah ya kawo ka lafiya " kawai ya fada hadi da ficewa, parking lot ya nufa motarsa wacce yasa aka wanke masa ya nufa, bude kofar motar yayi briefcase din sa ya aje da lab coat, sannan ya zagaya driver seat ya zauna , key yayima motar ya nufi main gate , gaisawa yayi da ma'aikatan gidan sannan ya fice daman mai gadi yariga da ya bude masa gate,eko ya nufa yana tafiya yana sauraron karatun alqur'ani a motar....
✨HIDAYA✨
Tsaye take gefen titin anguwar su tana jiran abun hawa, kusan 5 minutes tana nan bata samu abun hawa bata samu ba, wata bakar motace ta shigo anguwar tasu, tunda motar ta shigo anguwar tasu take ma motar kallon kamar tasan mamalakinta, motar na ƙarasowa kusa da ita tana rage gudu, kallon motar kawai take sai da ta kawo dab da ita sannan aranta tace" wannan ai kamar motar dr kabir " parking motar a kayi hadi da sauke glass din motar, kyakyawan saurayine fari amma ba sosai chan ba, akallah zai yi kima nin shekara 28 zuwa 30, sanye yake da blue din kaya complete riga da wando sannan fuskar sa sanye take da glass, hidaya tace" ina kwana dr" amsa mata yayi da " lafiya lau , mikike yi tsaye anan " hidaya tace " ina jiran abun hawa ne dr" ok yace sannan kuma ysake cewa " to shigo ciki mu wuce "
" A'a dr katafi kawai zan samu abun hawa insha Allah " hidaya ta fada, glass din dake fuskar shi ya cire hadi da cewa " to fah, hidaya ko dai kina tsoron na sayar dake ne iye " murmushi tayi hadi da cewa " A'a ba haka bane "
ajiyar zuciya ya sauke hadi da cewa " to inhar ba haka bane, to kishiga mu wuce " to kawai tace hadi da zagayawa ta shiga ciki, key yayima motar yana cewa " wlh kina bani mamaki hidaya, sai kace wata ƙara mar yarinya in ki ka yi wani abun " murmushi kawai tayi masa ba tare da tace komai ba, haka sukai ta tafiya yana janta da fira har suka iso eko , parking lot din asibitin ya nufa hadi dayin parking, har tasa hannu zata bude kofa ya da katar da ita yana cewa " wai hidaya tsorona ki keji ne, naga har wani sauri kike ki fita"
"A'a " kawai tace hadi da duƙar da kanta ƙasa, " shikenan bakomi kina iya tafiya "ya fada ficewa tayi daga motar shikuma ya tsaya tatara kayan sa dake back seat, tana fitowa motar shazim na parking, dr kabir ne ya fito hannun sa riƙe da tarkacen sa yana cema hidaya su tafi , tafiya suke sunkusa kawo inda motar shazim take sai gashi ya fito,miƙa masa hannu dr kabir yayi sukayi musabaha,  hidaya ta gaishe da shi, da lpy kawai ya amsa mata , wuce wa tayi tabar su shi da dr kabir tayi cikin asibitin, office din su da nurses kezama ta nufa, ba kowa ciki sai friend ɗin ta maryam da alama wadan da suka zo duk sun fita.
" lafiya yau ki ka yi late ? " maryam ta tambaya , ƙarasowa inda take hidaya tayi tana cewa "ke dai bari, banyi bacci bane jiya dawuri shiyyasa nayi late" dafa kafadar ta maryam tayi tana cewa " kingama yanke shawara yan da zaki tunkari dr da maganar koh "
" a'a gaskiya, maryam ina jin tsoro ne, ban san ya dr zai dauki maganar tawa ba " hannun hidaya maryam taja suka zauna sannan tace " ki kwantar da hankalin ki hidaya Insha Allah alkairi ne zai biyo baya, kinji" ajiyar zuciya hidaya ta sauke tana cewa " to Allah yasa haka maryam " da ameen maryam ta amsa mata hadi da cewa " tashi mufita" ta fada tana jan hannun hidaya, fice wa su kayi suka nufi inda yan uwansu nurses suke, gaishe da junan su suka shigayi , office din dr Shazim hidaya ta nufa tana cema maryam " sister bari naje office din dr na dawo"
"ok sai kin dawo " maryam ta fada, office din hidaya ta nufa hadi da tura kufar ta shiga bakinta ɗauke da sallama.
amsa mata sallamar yayi, sannan tace "dr asa patient a layi " amsa ya bata da" eh " har zata fice sai kuma ta dawo sai da tayi 2_3 seconds sannan dai ta daure tace" afuwan dr dama ina so ne Muyi wata mgn " ɗago kansa yayi daga aikin da yake ya tsare ta da idanu alamar ina sauraronki, magana ta fara " dama dr maganar Victoria ce " daga mata hannu yayi alamar ya isa haka " ya zama na ƙarshe da zaki ƙara man maganar ta  a nan, in ba haka ba kema zaki bita , fatan kingane "
" ok sir insha bazan sake ba " ta fada hadi da ficewa daga   office din , direct wurin patient ta wuce, ta shiga aikin ta , a haka Victoria da destiny suka same ta, wuri suka samu suka zauna kusa da ita , gaisawa su kayi sannan Victoria tace " hidaya ya maganar mu ne" ajiyar zuciya hidaya tayi sannan tace " gsky kiyi haÆ™uri Victoria, ko yanzu daga wurin dr nake nayi nayi ya haÆ™uri amma yaki, dan har cewa yayi kona daina masa magnar ki ko nima ya koreni " wani kallon banza Victoria tayi mata sannan ta ce " munafukar banza, wannan nasan duk shirin kine, to kisani kamar yanda kika rabani da dr nima sai na rabaki dashi " mikewa hidaya tayi tana cewa" kije kiyi duk abun da za kiyi Victoria, tun da ke baki da mutunci " fada sosai ya kaure tsakanin su har Victoria na neman kaima hidaya duka, destiny na jenye ta,  su maryam ne suka zo wurin saboda hayaniyar Victoria data jawo hankalin su, nan suka shiga cewa gsky baki da mutunci Victoria, komawa Victoria tayi kansu tana ce masu munafukai tasan ai da hadin bakin su, ai kuwa abun yayi masu zafi nan suka shiga maida mata da martani,Â
Hayaniya ce ta damesa harta na neman haddasa masa ciwan kai hakan tasa shi dole ajiye abun da yake yi, telephone ï¸ din dake office din ya dauka, dialing numbers yayi ana picking call din yace kasa meni a office dina yana gama fada yayi rejecting kiran bayan 30 seconds sai gashi anturo kofar, wani security ne ya shigo gaishe da shazim yayi hadi da cewa dr gani " wai hayaniyar mi nake ji ne" afuwan dr bari naje na duba " ok kawai yace masa, fita security yayi inda su Victoria suke ya nufa nan ya same su har lokacin basu dai na fadan da suke, hidaya sai kuka take saboda a rayuwarta ta tsani fitina, su maryam ne ke maida ma Victoria martanin, É—aya daga cikin nurses É—in mata security ya tambaya  mike faruwa amsa ta bashi " zuwana kenan na same su suna hayaniya sai dai ban san miye maÆ™asudun faÉ—an na su ba "
" to shikenan " shine kawai abun da security ya faɗa ya komawa office ɗin shazim ya sanar dashi cewa " sir su nurse Victoria ne ke hayaniya, ina jin dai wani abun ne ya ha dasu "
"Mutsww"shazim yaja tsaki a ranshi yace "nonsense kawai dasu, zasu wani tada ma mutane hankali , sakarkaru banza "
achan kuwa waje dr kabir ne ya fito daga office ɗinsa ya nufi inda su Victoria suke shima hayaniyar su ce ta dame shi, yana isowa wurin dukan su su kayi shiru tsaki yaja hadi da cewa" wlh kunbani mamaki matuƙa , ashe bakuda hankali " ya fada hadi danuna hidaya ya nace wa " wacece nan , mi kuma akayi mata take kuka" da yake duƙe take shiyyasa bai gane ko wacece ba, maryam tace "dr hidaya ce" matsowa yayi kusa da ita yana fadi "mike da munta ne " amsa maryam ta bashi da cewa " Victoria ce ke ci mata mutunci ita kuma bata iya ramawa shine take kuka, mukuma " hannu ya daga ma maryam hadi da cewa "ya isa haka, oya tashi " yace ma hidaya, mikewa tayi fuskar nan duk tayi sharkaf da hawaye "wuce muje" yace, binsa tayi a baya har office ɗinsa , toilet ya nuna mata " shiga ki wanke fuskar ki " shiga tayi ta wanke fuskarta sannan ta fito
wuri ya nuna mata kan sofa da ke cikin office din
 zama tayi tana  sauke ajiyar zuciya
ita bakomai yafi bata haushi ba wai a ce daga taimako Victoria zatayi mata haka, gyaran murya dr kabir yayi haɗi da zama kan sofar yana fuskantar hidaya yace " hidaya nasan wannan ba halinki bane miyasa kike biye ma mutane irin waɗanna, ke da ita bafa ɗaya bane al'adar ku ba ɗaya ba kwata kwata ita batasan kunya ba saboda ba'a koya mata ba amma ke duk wanda ya ganki zai yimaki kallon wacce bata san mutuncin kanta ba, pls hidaya karki sake"
" insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba nagode "
" bakomai karki damu tashi ki tafi kicigaba da abun da kike yi "
" ok" ta faɗa hadi da mikewa ta fice, wurin patient ta koma ta cigaba da turama dr su.
✨noraiz✨
Parlorn ammy ya shigo jikinsa sanye da kananu kaya farar riga da bakin wando, yana shigowa Ammy na fitowa daga bedroom dinta sanye take da hijab har kasa, Noraiz yace " yawwa Ammy harkin shirya kenan " "eh" Ammy ta fada, ficewa su kayi, parking lot suka nufa wurin wata bakar mota rang rover suka nufa Noraiz ne ya bude mata kofa sannan ya zagaya driver seat ya zauna hadi da yima motar key ya nufi main gate, megadi ne ya tashi ya bude masu gate gaishe da Ammy mai gadin yayi amsa mashi tayi cikin kulawa sannan Noraiz yayima motar key suka fice
tafiya su kayi sosai sannan suka sha kwanar wani road mikewa suyi sosai sannan suka tsaya abakin wani gida horn Noraiz yayi abakin gate din gidan.
ƙofar dake jikin gate din gidan aka bude wani mutum ne ya leko yana ganin motar Noraiz ya koma da sauri
gate din gidan aka bude ciki Noraiz ya danna hancin motar ciki, parking lot din dake gidan Noraiz ya nufa hadi da yin parking, fitowa su kayi shi da Ammy suka wuce cikin gidan