← Book details Anti Romance Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 7

Sashe 5

Anti Romance Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hajjo tasha zuwa Katsina kai masa ziyara ba a logging ba No a dakinsa zasu kwana ,sosai ya maida besty dinsa farkansa ,cikine kadai bai taba yin mata ba shima saboda da sun gama sex zai dirka mata meso a drinks ,that is that.... A yawon zuwa dubiyansa ne ta hadu da mijinta wanda ya kasance abokin aikin faruk ,abun takaicin wai faruk ne yake ma abokinsa kamfain akan ta soshi ,ashe haukan banza takeyi take yaudarar kanta take kore samarinta a tunanin ta faruk mugun sonta yake ashe sha'awa ce kawai da shakuwar jini ba so na aure ba ,Da da fari ta nuna masa ɓacin ransa da kin saurayin daya kawo mata ,amma katsaham ya gabatar mata da zarah matsayin yarinyar da zai aura , yarinya mai aji shuwa Arab ga boko ga ta mahaddaciyar Kur'ani gata ƴar jarida ga babanta Babban ɗan kasuwa kundai san en Maiduguri da makafin dukiya ,uwa uba ita ce ƴar fari a wajen iyayenta kuma siya mace tilo cikin zaratan maza ,to ta Ina zata hada kanta da zarah? Wacce bata buɗe ma faruk gindi ya kwasa ganima ba?

Wani abun ban haushin,tunda faruk ya hadu da Zarah duk mugun sha'awarsa na don cin mace sai ya salance ,ynz attention ɗinsa ya koma kan zarah baya jin sha'awar ko wace mace sai ita.

Batayi masu bakin ciki ba ,kuma lokaci daya taji tana son zarah Albarkacin son da take yiwa faruk ,tayi supporting dinsu emotionally akasha biki amarya ta tare a gidan mijin ta da ke Alkali road kaduna.

Sosai suke ƙawance tsakanin zarah da Hajjo ,kuma da taimakon zarah hajjo ta amince ta auri baban Afrah ,amma in ta tuna yanda faruk ya dinga dirka mata meso a drinks sai taji ma ita ko tayi aure bazata taɓa haihuwa ba ,faruk ya kone mata kwayayen haihuwa.

Rayuwa mai albarka ya cigaba da gudana ƙaruwar arziki albarka yara ,kowannensu na kula da mijinsa basa zuwa aiki Amma interprenuers ne sun yarda da kasuwanci kuma yana basu duk abunda mace ke burin samu a rayuwa ,saidai barazanar hajjo daya ne ,rashin yardan da bata dashi tsakanin ita da mijinta ,Gani yake duk Mazan duniya ta gama saninsu kafin tayi aure ,bai san cewa sharrin sha'awa ne ba da kuma sharrin besty ba.

Wawuyar ajiyar numfashi taja gamida goge ƙwalla a sarari Hajjo ta magantu da “Ubangiji kasa kuskuren da na aikata da babanki Afreen sakamakon soyayya bazai tasiri a soyayyar ku da ƴata Afrah ba ,don so daya ne so na jini kuma shine nake gani a tsakanin ku....”

Oum Aphnan
09065990265
[2/10, 11:15 PM] Chuchu👻: ANTI ROMANTIC
Pg F

________
“Ɗan lami?!!! ” dije ta ƙwalla kiran sunan shi cikin muryar mamaki gami da dafe ƙirji.
A kaikaice ya kalle ta, kawai ya dauke kai, ya bi bayan matarsa sajida wacce tayi shigewar ta cikin gida da gudu, tun sanda taji yarinyar nan ta kirasa da ‘baba’

“Saj Listen to me”
“Bana son jin komai a wajenka Sugar, a,ina ka samo wa'innan trash en? Ehy eh? Just answer me where have you got those trashes? ” ta cakumo kwalar rigarsa tana girgiza sa

Sauke muryarsa yayi a nitse “Ki saurare ni Saj. It have been Too long in sa dije a cikin idanuwa na, talkless of that nasty looking kid... ”
A zafafe ta katse shi

“Shine har take kiranka da baba”?

“Yes I just heard from her, means Dije ne ta haihu”

“owhoo dama ka san ta amma kake ƙoƙarin basarwa? ”

“Ina son ki, kin ga bazan iya maki karya ba, but the fact is that shekaru kusan 7 kenan bansa dije a ido na ba tun muna kauye”

“Now choose! Ka zaba ko ni ko dije!!! ”

“Wa'iyazubillah ina zaki hada kanki da ƴar ƙauye, da iliminki da wayewanki”

“Yoo na sani? Tunda ku maza munafukai ne, gashi ka kwatanto mata gidan ta taho zata gallazi rayukanmu”

“Saj Trust me, bansan wa ya nuna mata gidan nan ba. ”
“Hmm amma tell me, kenan wannan dijen matarka ce? Plz Sugar blum kar ka fadamun wancan mummunar yarinyar ƴar ka ce 🥲”

Ya kasa bata amsa da bakinsa saboda yanda yaga madarar tashin hankali a tattare da ita sai faman gyada mata kai da yakeyi kamar kutu, wanda hakan ta tabbatar mata da eh hakan ne su ɗin iyalansa ne, he can't deny.

***
A compound kuwa, Wai wuce sun da ɗan lami yayi,ba tare da ya kula su ko ya damu dasu ba, ko a jikinsu wai an tsikari kakkausa. Alamu ya nuna basu san Me ake kira wulakanci ba.
Dije katar katar taja hannun erta can ƙarƙashin inuwar dogayen bishiyoyin furannin da suka ƙawata jikin katangar gidan. Ta janyo jikkar Ghana must go dinsu ta zuge ta fiddo dankwalinta ta shimfida masu a wajen
“oya oya zauna”

Make kafada naja tayi “Um um ni yunwa nike ji”

Daddagewa dije tayi ta buga mata tsawa gami da zare mata ido kamar saukar aradu
“Don uban ki me kika ga ina kokarin yi? Bana son cin kahurci”

Tsit naja tayi ta samu waje ta tankwashe kafa, shikuma copr bimbo yana daga can wajen Gate yana hango su cikin tsammanin jiran warabbuka.

Sandara sandaran tuwayenta na dawa ta karyo daga cikin roban hanji waje,wanda duk ta hautsina a cikin kayan sawansu ta dauko leda a cikin roban tuwon shake da miyar kuka baka wuluk, ba manja tayi ko na man ƙuli ne Allah ne masani.

Ta dauko wata baƙar tukunya kamar anyi gobara a ciki ta zuba karyayyun tuwon, ta an taka miya a kai ta sa murfin kwanan sha ta rufe tukunyar dashi, don tukunyar bata da murfi, ta waigo ta kalli Naja da keta kwarara hamma kamar zata ci babu.

“Ke Naju ɗan yi mun yaye yaye in ta da wuta kinji in ɗumama mana abinci ”

Zumɓuro baki naja tayi “Ummana baki ga gidan an gayu bane, basu zubar da shara ni ina zan samo ledojin hura wuta”

Dunƙula hannu tayi ta wurgo mata daƙuwa “ungo nan, ni kike gayawa gidan en gayu,? Aah ƴan wuta ne ba ƴan gayu ba, kaji mun ƴar ƙashin Bura uwa... Kinje kin samo mun ledoji ko ƙaƙa, ga kwandon zuwa shara can”

Ta nuna mata kwandon sharar copr bimbo da yatsa.
Ba musu naja ta Mike ta nufi wajen.

Ita kuma dije ta dauko mungula mungulan duwarwatsun murhunta guda uku a cikin jaka ta samu karkashin inuwar fulawa ta jera duwatsun girkin nan a saman interlocks din gidan, ta fiddo diddigar itace da Naju ke mata roro a gidan da ake saida iccen garinsu, idan me iccen ya kira ayi masa faskaren itacce sai su bi su kwashe kananun da ya ragu ki ganshi kusa himiiii.

Landanan danan ta banka masu kalanxir ta kyatta ashana ta kara sa ledoji, nan da nan gida ya gurnuke da hayaki da kaurin dumamen tuwon dawa miyar baƙar kuka.

Tun daga nesa copr bimbo ya fara masu ihu, wai zasu kona masu interlocks, ina suka taɓa gani....

Oum aphnan
[2/10, 11:15 PM] Chuchu👻: ANTI-ROMANTIC
Oum Aphnan
Page E

1.Akan Dadirona
2.Auren Sha'awa
3.Abu Uku
4.Bagidajiya
5.Bariki Gadona
6.Bad biya
7.Banana Island
8.Gwauro
9.Gidan Daɗi
10.Hariji
11.Indo Maƙata
12.Jarababben Namiji
13.Jinin Sarauta
14.Laylerh
15.Namiji kishi
16.Qasaitattun Mata
17.Ramuwar gayya
18.Rayuwar Afredarh
19.Sugar Mummies
20.Sinadarin Ma'aurata
21.Yaron Gidana
22.Ƴan Lesbians
Chat or call via
09065990265

________.
Littafin Kudine
Regular ₦500
Special /Email ₦1000

Katin MTN ko tanan Bank din

7782217014.
Mohammed Hassana
Fcmb

Shaidar biya ta nan Number
09065990265
_________
Dije kam dukan ƙofar ta cigaba da yi ,a firgice Copr Bimbo ya wangale Gate din ya leko da kansa hannunsa rike da sandan sa irin na ƴan sanda .
Jan ido yayi mata yana turo mata timbinsa gaba kamar zai hankaɗe ta .
“Who Are You?”
Tafdi! Anzo wajen ,Dije fa ba turanci , murguɗa masa baki tayi
“Dallah malam kauda mun da shirgegen cikin ka in wuce”

Tsawa ya daka mata ,saboda yana jin Hausan kadan kadan “Baka wucewa nace ,Gidan ubanka ne?”

“Aah fa ,mace nake kabar mai dani namiji”

Hurar da iskar bakinsa yayi ,ya lura wannan fa za ayi bura uba da ita.
“Kai wa kikai nema?”

“Wajen mai gidan nazo”

“Mai gidan? Wa kenan?”
“Ɗan lami birkila ,inkiya makil jaksin”

“Kinyi ɓatan kai ba nan gidan bane ba,kautar da jikinki in rufe kofa”

“Kai malam bani son iskanci ,bar ganinka da kakin ƴan sanda wallahi bazanji tsoronka ba ,nan ne gidan Ɗan lami, Baga adireshinsa nan ba komai iri ɗaya”

Tana magana tana Kwanto takardan a haɓar zani kamar kudi

Miƙa hannu yayi ya amsa cikin mamaki ,tabbas shine ,amma waye shikuwa ya ba wannan mahaukaciyar kwatancen gidan nan?

“Haka ne amma nan ba gidan Ɗan lami birkila bane ,unguwar masu kudine ,kiyi hakuri ki koma gida kuskure aka samu...” tsalle tayi ta dire a kan ƙafarta ta kama ƙugu.

“In ka isa Allah ya kona Ni ,kasan wuyan da mukasha kafin muzo nan? Rankatakaf kudin hannuna ya kare sai ynz ka wani cemun ba nan ba ,to ban yarda ba...to waima tsaya in na bar nan inje ina a daren nan ,so kake mu fada mugun hannu a yanke kanmu?”

Hajia Sajida Fitowar ta kenan daga BQ ta gama zazzage ma Baba mai shara kwandon bala'i ,ta jiyo hayaniyar Copr Bimbo da mutane daga waje.
Wani tsawa ta daka masa
“BIMBOOO!!”

Dararramm! Ya bugo gate din dasu Dije a waje ya amsa a firgice yana kallon Sajida dake can wajen gaban premises dinta

“Kai da wanene anan?”
“Wai wasu bakine suke son shigowa nayi ,nayi dasu su tafi sun ki,wai nan ne address din su”

“For how long it will take you ? Kwana zakayi kuna gardaman kafin su yarda?”

Girgiza mata kai yayi kansa a duke
“Open the gate jooorhh” ta daka masa tsawa ,tana mai bashi umurnin ya buɗe gate din.

Ai cikin rawar jiki ya buɗe ma su Dije gate ai kuwa suka shigo ɗuuuu,kamar su ɗari ne zasu shigo gidan ba su biyu ba.

Wani ƙaskantaccen kallo Sajida ta bi su dashi tana ƙare ma buhunan kayansu kallo
A gatsale tace “Daga ina?”

Da sauri Dije ta ɗago ta kalle ta ,kawai sai ta bude baki tana nunata da yatsa “Dama kece?”
Chapter 5 · 0% Book details