← Book details Yar Zaman Daki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 7

Sashe 1

Yar Zaman Daki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*'YAR ZAMAN ƊAKI*

©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️

https://chat.whatsapp.com/HFVRd4aXG6A8v3OngGn29A

1&2

Manyan motoci ne a jere sun yi jerin gwano kala-kala, idan ka ƙare musu kallo kusan kalolin motar launi biyu ne akwai launi farare da baƙaƙe. Abokan ango ne tsaitsaye kusan kowanne yana jiran ƴan matan da ya sauke don mayar da su gida, kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci suna cikin farincikin taya abokinsu murnar aure.

Gidan babba ne amma plat ne cike yake da kayan more rayuwa, ya sha ƙyalƙyali da hasken ƙan lantarki. Kana ƙare wa gidan kallo za ka fahimci dukiya ta samu makwanci a wurin, duba da irin ɗimbin dukiyar da aka narka a ciki.

"To Zarah kin ga dai kin samu gida irin wanda kowacce ƴa mace take fata, ki yi biyayya ga mijinki ku zauna lafiya, shi zaman aure ɗan haƙuri ne yi na yi bari na bari..." Wata Dattijuwa da take kusa da Amarya Zarah ta riƙa yi mata nasihar zaman aure, ƴan matan da ke tsaitsaye sai kalle-kalle suke yi kowacce tana ayyana ina ma gidanta ne. Matan auren cikin su mafi yawa suna raya Allah ya hore wa mazajensu suma daƙara musu kamarsa, wasu daga cikin iyaye kuma na fatan suma Allah ya bawa nasu ƴaƴa irin wannan gida.

Zarah bata furta komai ba kasancewar kanta na cikin mayafi, har mutanen da suke cikin gidan suka watse sakamakon abokan Ango sai zabga horn suke yi. Ɗakin Zarah ya rage daga ita sai ƙawayenta uku, a hankali ta zame mayafinta tana ƙare wa ɗakin kallo. Amma kana ƙare wa fuskarta kallo za ka fahimci akwai ɓacin rai a tattare da ita, Lubna da ke gefe ta ce: "Zarah ya dai na ga har yanzu ba ki da walwala ko dai akan maganar nan ne?"

Dogon tsaki Zarah ta yi ta furta, "Lubna an yi min adalci kenan? Ace daren farkona wai za a kawo min wata ƴar zaman ɗaki?" Aisha ta taɓe baki tana faɗin, "Ni fa ban ga abin damuwa ba, kuna ɗakinku tana nata. Kuma mutumin nan yana tsananin ƙaunarki, ki dangwali arziki ki bar arziki a mazauninsa." Sadiya ta yi gajeren tsaki tana cewa, "Wallahi Zarah abin haushi gare ki, bakya cin uwar yarinya idan ta ji wuya da ƙafarta za ta gudu.Ki zauna wata ƙanƙanuwar yarinya ta ɓata miki farincikinki, ki zo ki yi biyu babu."

Nan take ƙawayen Zarah suka ci gaba da bata shawarwari na kyau da na banza, lokaci ɗaya ta ware tana farinciki don ta fahimci abin da suke ɗorata a kai.

Ba a jima ba Ango ya ƙaraso shi da abokansa, fito wa ya yi daga motar abokinsa Sani. Bayan motar ya buɗe Walida na zaune tana ƴan kalle-kalle, tana ganin ya buɗe mata ta yi masa murmushi. Hannunta ya kama ya ce, "Fito mun zo gida." Wani Abokinsa Yunusa da ke gefe ya ce,

"Mutumina ba ka so cin amarci ba, haka kawai ranar aurenka ka ɗauko yarinya yoo ko ƴar cikinka ce ai ka kaita ajiya." Khalid ango ya yi dariya ya ce, "Ku dai kuka sani kanku ake ji." Cikin raha abokansa suka raka shi, aka yi barkwancin da aka saba tsakanin Angwaye da Amare, daga ƙarshe aka yi sayen baki ƙawayen amarya da abokan ango suka watse.

Zarah ban da yaƙe babu abin da take yi don kar ta nunawa Khalid bata so zuwan Walida ba, Khalida ya ɗauko manyan ledoji biyu duka cike suke da kaji. Gefe ɗaya katan-katan ɗin lemuka ne sai manyan yegot da kayan ƙwalam da maƙwalashe. Khalid da kansa ya ɗauki Walida ya kaita ɗakinta haɗe da ajiye mata ƙaramar ledarta da ya saya mata kazarta guda ɗaya a ciki, sai lemon jarka da alawoyi. A madadin Khalida ya fita sai ya zauna a gefen gadon, shi kaɗai ya yi jim kamar mai nazari sannan ya furta, "Wannan wacce irin rayuwa ce haka ni ban haifa ba, ba dangin iya ba na baba amma na ƙare da dakon wahala."

Walida da ke gefe ta zuba masa ido ta ce, "Uncle magana kake yi?" Khalid ya wayance da dariyar yaƙe ya ce, "A'a Walida. Cewa na yi Walida ƴar Uncle, yanzu dai ga namanki ko sai da safe za ki ci?" Walida ta leƙa ledar tana juyar da kanta gefe tana shinshine-shinshine ta ce, "Amma dai wannan kazar ba gashin inji ba ce?" Khalid ya zuba mata ido wani takaici ya kama shi, a ɗiƙile ya furta, "Idan bakya ci ki bari sai da safe kya ci."

Khalid na gama maganar ya nufi bakin ƙofa tun bai ƙarasa ba Walida yanƙare baki ta fashe da kuka. Riƙe ƙugu Khalid ya yi a ƙagauce ya dawo murya a shaƙe ya ce, "Me ye kuma?"

Ledar kazarta ta nuna masa tana maƙale hannu ta ce, "Kazar nan ce take cizo na a hannu, kuma ni ka zo ka kwanta a nan." Da mamaki Khalid ya furta, "Kaza kuma? Gasasshiyar kazar ce take cizonki..." Khalid bai rufe baki ba ya ji ledar kazar ta bada ƙaraas alamun taunar ƙashi, da sauri Khalid ya sake buɗe wa sai dai ga mamakinsa yana buɗe ledar ya ga sai taunannun ƙashi, wasu ma an yi dugu-dugu da shi. Cinyoyin kazar ne kawai aka cinye tsokokin ba tare da an tauye ƙashin ba.

Yana shirin yin magana ya ji Walida ta saki ƙatuwar gyatsa sannan ta ce, "Uncle zan sha ruwa." Khalid ya ƙwalalo ido waje ya ce, "Ina kazar cikin ledar?" Walida ta ce, "To ai sai na sha ruwa zan ci." Khalid ya sake bankaɗe ledar ya ce, "Ba yanzu na nuna buɗe kazar har kika ce ba gashin inji ba ce?" Walida ta sake sakin gatsa haɗe da ɗaukan tsinken sakace tana kwakwule haƙoranta.

MEYE HARSASHENKU AKAN WALIDA? 😂

LITTAFIN KYAUTA NE AMMA BAN YI ALƘAWARIN YIN TYPING MAI TSAYI BA SABODA LITTAFIN KUƊIN DA NAKE YI, ZAN YI ƘOƘARIN YIN POSTING KULLIN INSHA ALLAH.🥰
*'YAR ZAMAN ÆŠAKI*

©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️

https://chat.whatsapp.com/HFVRd4aXG6A8v3OngGn29A

3&4

Khalid zuru ya yi yana kallon Walida da take sakace tana lumshe ido, sai da ta gama sakace ta ɗago daga kishinɗe ta ce, "Uncle ƙishirwa nake ji." Ba tare da ya kalli wurin da yake tsammanin anan ruwa da yegot ɗin suke ba, ya miƙa hannu har lokacin idonsa na kan Walida, yana taɓa robar yegot ɗaya ya ji ba faɗi garam alamar an shanye abin da yake ciki. Wannan karon sai da cikinsa ya kaɗa amma don kar ya nuna mata ya ɗan tsorata ya hau borin kunya da cewar, "Wai me yake faruwa ne? Kaji tun ba a je ko'ina ba sun ƙare shi ma yegot ɗin an shanye shi duka, wallahi duk uban da yake aikata min haka daidai nake da zamaninsa."

Amarya Zarah tana can zaune tana jiran dawowar Khalid ango, ƙamshin kazar ne ya gama cika mata hanci ban da haɗiyar yawu babu abin da take yi. Jin shirun Khalid ya yi yawa ya sa ta fara jin haushi saboda tana tuna Walida wani takaici yake mamaye birnin zuciyarta, a hankali ta miƙe ta isa bakin ledar kazar. Ta faki ido tana kallon hanyar shigo wa amma jin shirun da ta ji ya sa ta kai hannu da niyyar buɗe ledar, lokaci ɗaya ta ji kamar an ce. "Wayyo ni Amarya Kaza." A ɗan zabure Zarah ta ja da baya tana waige-waige don yadda ta ji kazar na magana raɗau a kunnenta, da sauri ta nufi sashen da ta ga Khalid ya bi.

Tana zuwa ta samu Khalid tsugunne a gaban Walida yana cewa, "Walida ki yi bacci kin ga Auntynki na can tana jirana." Walida ta kwaɓe baki ta ce, "A'a ni dai ka kwana a nan." Ganin yanda Khalid yake lallaɓa Walida ya tunzura zuciyar Zarah, tun daga bakin ƙofa ta saki uban ashar tana faɗin:

"Khalid me kake yi haka? Wai ni ce Amaryar ko yarinyar nan? Tun da ka shigo gidan nan ka taho wurin yarinyar nan ni ina can ina zaman jiranka, wallahi da na san wulaƙancin nan za a min da..." Tun bata ƙarasa ba Walida ta tashi zaune ta ce, "Don Allah ki yi haƙuri Aunty." A zafafe Zarah ta dakatar da ita da cewar, "Rufe min baki munafuka ƙanƙanuwarki da ke sai iyayi." Khalid ya miƙe jiki a sanyaye ya ce, "Don Allah ki yi haƙuri Zarah, ni fa ba wani abu ne ya tsayar da ni ba. Dubi ledar nan." Khalid ya yi maganar yana ɗago wa Zarah ledar kazar. Ganin taunannun ƙashi ya ƙara harzuƙata ta ce, "Eh to tun da kun cinye gani ƴar iska ai dole ka nuna min ƙashi amma gaskiya Khalid ka cuce ni da na san cin kashin da za ka min kenan da..." Khalid ya katse Zarah tare da zayyane mata abin da ya faru. Da farko ta so ƙaryatawa amma da ta tuna abin da ta ji sai tsoro ya sake kamata. Suna nan tsaye Walida ta ɗago ta ce, "Uncle ku je ni fa bacci nake ji."

Khalid ba ƙaramin daɗi ya ji ba, cikin shauƙi, so da ƙauna ta riƙo hannun Zarah suka wuce sashensu. Suna zuwa Khalid ya rungumo Zarah yana kashe mata ido ɗaya ya ce, "Habibity kin ga yadda kika yi kyau kuwa?" Kafin Zarah ta yi magana suka ji magana kamar raɗa an ce, "Duk kyawunta ta kai kaza." A firgice duk suka waiga, Khalid ya fara leƙe ta window ya ce, "Zarah amma dai babu wanda aka bari a ƴan kawo amarya ko?" A daƙile Zarah ta ce, "Sai ƴar zaman ɗaki waya sani ko laɓe take mana." Khalid ya wayance da cewar, "Haba dai Walida ba za ta yi haka ba. Yanzu dai miƙo min ledar kazar nan ki ga."
Chapter 1 · 0% Book details