Chapter Three
Takun Saka Part 1 Complete Hausa Novel · about 193 min read
...........Hafsat tai azamar ɗago kanta tana dubanta, duk da hawayen da ke sharara a kumatunta na azabar da take ji a ƙafarta, cikin ƙarfin halin ta ce, *_“Muhibbat!_* dan ALLAH karki sakamu a wahala da hatsabibancinki. Kwana huɗu kenan kacal da gama kashe wata wutar da kika kunno, indai dan nice karki damu, dama ALLAH ya ƙaddara sai naji ciwon nan koda bata sanadinsu ba, ina roƙonki kibarsu Ya Abubakar su huta da shegen tsokanarnan taki”.
Harara Muhibbat ta zubama Hafsat da murguɗa baki tana juya idanu, harta buɗe baki zatayi magana sai kuma tayi shiru saboda isowarsu cikin harabar asibitin.
Ko kaɗan jami'in nan baiso Muhibbat tayi shiru ba, amma kasancewar yasan aikinsa sai bai nuna hakanba, sai ma ƙoƙarin taimaka musu da yayi domin ganin an shiga da Hafsat taga likita akan lokaci.
Da taimakon jami'in aka duba ƙafar Hafsat da ta samu tsagewar ƙashi, Zahidah sai godiya take masa saboda ƙoƙarin da yaketa musu, dan sunso su kira gida ya hanasu. Hanawar tasa kuma ta bama Muhibbat haushi, dan a ganinta ya cika shishshigin tsiyane kawai, musamman daya kasance duk wani motsinta sai ta ritsa idanunsa akanta.
Tun tana hararsa a ƙasan ido da masa ƙunƙuni har takai ta fito fili tana dalla masa harara. Ganin dai ba daina kallon nata zaiyi ba a tsiwace ta ce, “Wai malam kallon fa? Dan ALLAH karka cinyeni a tsaye mana”.
Sosai yanda tai maganar ya bashi dariya, dan tsaf ya gama fahimtar itaɗin matsiwaciyace ta gaske. Sannan babu tsoro sam a cikin idanunta kona sisin kwabo. Komai baice mata ba, sai ma ɗauke kansa da yayi kawai gefe tamkar bai jita ba. Taja tsoki tana murguɗa baki da miƙewa tabar wajen.
Can gefe ta koma tana ƙoƙarin sarrafa wayarta cike da ƙwarewa. Cikin ƙanƙanin lokaci kiran da tayi ya shiga, sai da aka ɗaga sannan takai kunne tana faɗin, “Assalamu alaika Yaya”.
Amsa mata akai da ga can, kafinma ya gama rufe baki cikin shagwaɓa taci gaba da magana. “Yah Uthman muna hospital ne”.
A tsananin tsorace muryarsa ta bayyana, “Hospital Auta?! Waye bai da lafiya?”.
“Oh Yaya calm dawn, Hafsat ce taji ciwo a ƙafa amma da sauƙi, dan yanzu haka ma an gama mata gyaran sunce tsagewan ƙashine”.
“Ya ALLAH! Auta wai sai yaushe ne zakuyi hankali ku kam? Yanzu haka a wajen shegen rawan kan nan naku hakan ta faru?”.
“Na rantse Yaya bafa da gangan bane, wasu marasa kirki ne suka kusan turemu a power bike”.
“What?!. Power bike fa? Ku miya kaiku kan titin da masu power bike kebi!!?”.
Yanda yay maganar a tsawace ne ya sata zabura, duk cikin yayun nata yafi kowa sauƙin hali bayan Yah Abubakar. Sai dai kuma idan ya rikice tafi tsoronsa fiye da kowa a cikinsu..... Cikin katse mata tunani yace, “Zan turo muku Ammar yanzun nan danni naje katsina ne..”
Yana gama faɗan hakan ya yanke wayar. Kasaƙe Muhibbat tayi tana kallon wayar, yayinda gefen zuciyarta ke ayyana mata neman mafita. A fili tace, “Tab Yah Ammar! Wlhy bazan bari ya samemu a asibitin nan ba wannan ɗan matsalar”. Da sauri tabar wajen zuwa inda jami'in nan mai amsa sunan driver-n taxi yake da Zahidah.
“Zahidah tunda sunce zasu iya sallamarmu gara mu wuce gida, dan na haɗa gurmi wlhy”.
Zahidah dake mata kallon mamaki tace, “Gurmi kuma! Nami to?”.
“Humm daga kiran Yah Uthman fa na faɗa masa shine wai zai turo mana Yah Ammar shi yana katsina. Ni kuma wlhy banason Yah Ammar yazo asibitin nan ya samemu saboda yafi gidan haya matsala kema kin sani”.
Kafin Zahidah dake dariya tace wani abu jami'in nan yay saurin cewa, “Ai sunma sallemu daman, inaga ku shiga ku fito da ita kawai mana”.
Harararsa Muhibbat tayi tana ɗaure fuska. “Ikon ALLAH sai kallo, wai ni kam bawan ALLAH ca'akai ka kula damu ne kokuwa? Taxi ɗinka muka hau ka kawomu inda muke buƙata, to sai mi kuma ya rage?”.
Murmushi yayi idanunsa a kanta, “Sai ku bani kuɗina ya rage ƙanwata”.
“Ya salam! Dan ALLAH kayi haƙuri bawan ALLAH. Wlhy gaba ɗaya mun shafa'a ne”. Zahidah ta faɗa tana laluben bag ɗinta.
“Karki damu ƴammata babu damuwa. Nasan kuna a rikicene ai. Amma ƙawar nan taki ya kamata ta rage tsiwa”.
Zahidah dake miƙa masa ɗari biyar tai dariya, “Kaga fita batunta ga kuɗinka mun gode sosai”.
“Ai karki damu riƙe kawai sai na kaiku inda zaku yanzu sai na amsa”.
“Malam gara dai ka amshi kudinka kai gaba, dan bazamu sake shiga motarkaba ɗan sarkin shiga sharo ba shanu”. Muhibbat ta faɗa tana hararsa.
Saurin toshe bakinta Zahidah tayi itama tana hararta, “Wai nikam Hibbat kodai wadda tai miki wankan jego bata gasa bakin nan bane da baya barin kowa. Ina laifin bawan ALLAHn nan, kigafa ƙoƙarin da yay mana akan Hafsat”.
Hibbat ta buge hannun Zahidah da haushi, “To dan kuma ya taimakemu sai ya ishemu da shishshigin jaraba. ALLAH ni banason shishshigi da ƙwala kai a faranti irin na wasu mazan”.
Tana gama faɗa tai shigewarta ɗakin da Hafsat take. Duk binta sukai da kallo, kafin Zahidah ta maido kallonta ga jami'in. “Ayya dan ALLAH kai haƙuri. Ita haka take sam ba'a gane kanta tamkar mai aljanu”.
Ƙaramar dariya yayi yana sosa tsakkiyar kansa da key ɗin taxi ɗin. Yace, “Kinga karki damu ni salon natama birgeni yakeyi, irin waɗanan sam ba'a cutarsu a duk inda suka shiga. Je kawai ki fito dasu na kaiku kafin a sake kirana ɗan shishshigi”.
A yanda ya ƙare maganar cikin langaɓe kai kalar tausayi yasa Zahidah ƙyalƙyalewa da dariya tana shiga ɗakin domin su fiddo da Hafsat..
Da ƙyar Muhibbat ta amince jami'in nan mai taxi ya ɗaukesu zai maida gida. Dan ko sai kumbura take a motar tana ƙananun ƙunƙuni alamar bataso hakan ba. Shi dai yakanyi murmushi lokaci-lokaci idan ya ɗago ya dubeta ta mirror yaga yanda take cika baki da iska tana harare-harare........
★.★.★.★.★.★
Kamar yanda aka saba yau ɗinma tuni media ta ɗauka. Gidajen redio dana televisions harma da yanar gizo mutane sai tofa albarkacin bakinsu suke. Dan lamarin wannan gagarumin ɓarawo ya daina bama mutane tsoro sai al'ajabi da mamaki. Kullum ji suke jami'an tsaro na farautarsa, mai makon ya tsorata ya ɓuya sai ƙarama gawurta yake a al'amuransa. Gashi babban abinda zai baka mamaki manya-manyan ƙusoshin ƙasar masu lasisin iya ɗaukar mataki yake bi yana yashewa da saka rayuwansu cikin tarkuna. Dan da wahala ya kafa maka ƙahon zuƙa daga ƙarshe baka koma ƙarƙashin binciken hukumar *EFCC🐦* ba, ko ka ƙare rayuwarka da ciwon paralysis saboda barazanarsa idan yay dirar mikiya aka kaddarorinka da kuɗaɗenka. Yanzu dai yanda ya yashe asusun matar gwamna bawai ya barta bane kenan. Duk da neman da ake masa ruwa a jallo cikin kwanaki ƙanƙani zai sake silalowa ya danƙara mata wani harbin mai zafi har sai ya kai rayuwarta ƙasa kwance zai barta.
Duk yanda ƴan jarida sukaso jin ta bakin jami'an tsaro da gidan gwamnati akan wannan al'amari abin ya gagara. Sun haƙura dole suna bada labarin iya abinda idanunsu suka gani da ɓarnar da wannan mutumi ya tafka a baya kafin wannan ɗin.
Yayinda a gefe kuma jama'ar gari suketa tofa nasu. Wasu najin daɗin abinda yakeyi ɗin dan bawai a satar kuɗin manyan ƙasar kawai ya tsaya ba, har ƴan fashi da suka addabi mutane da ƴan ta'adda yakan kama waɗanda har yanzu babu wanda zai iya cewa ga inda yake kaisu ya ɓoye. duk da kuwa shima ɗin mai laifi ne a bayyane, wasu ko na jifansa da ALLAH wadai saboda suna ganin bashi da maraba da ƴan ta'addar da yake kamawa ai. Yayinda ƴan kanzagi ke zaman rubuta shaci faɗi su yaɗa a kafafen yanar gizo game da shi da ayyukansa..............✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k)
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR
*_ALLAH ka gafartama iyayen mu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_🔮TAKUN SAAƘA!!🔮_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
_ZAFAFA BIYAR 2K22_
_________________________
*_Chapter Four_*
...........Suna baro cikin asibitin Muhibbat ta kashe wayarta dan ma kar Yah Ammar ya sameta.
Tun farkon shigowa anguwar tace a saukesu. Amma sai Zahidah tace sam basu yarda ba a kaisu har ƙofar gida. Zata fara masifa Hafsat ta ce, “Kiyi haƙuri ya kaimu saboda bazan iya taka ƙafarnan ba Hibbah”.
Shiru tayi bata sake tankawa ba har suka iso ƙofar gidan su Hafsat daya kasance a farko, sai nasu Zahidah, Muhibbat ce ƙarshe. Saboda ciwon dake tare da Hafsat ɗin ya sakasu cewa a tsaya ƙofar gidansu. Zahidah ta bama mai taxi kuɗinsa tana godiya. Amma sai yaƙi amsa. Mamaki ƙarara a fuskar Zahidah da Hafsat. Sun buɗe baki zasu magana yay musu alamar suyi shiru.
“Basai kunce komai ba, inhar da wannan mai bakin tsiwar tare da ku anta kaiku waje ƙyauta kenan babu ko sisin ku”. Yay maganar idanunsa akan Muhibbat yana wani sassanyan murmushi.
Hararar da yay tsammani ta watsa masa, cikin takaici tabar wajen batare da tace komai ba. Kira Zahidah da Hafsat suka shiga ƙwala mata suna dariya, amma ko waiwayensu batai ba harta ƙarasa gaban wani gida mai baƙin gate. Sai da ta kama murfin zata shiga ta waigo, ganin har yanzu mai taxi ɗin na tare da su yasata jan tsaki akan laɓɓanta ta ce, “Maye kawai”. Daga haka ta shige ciki.
Gida ne da zamu iya kiransa babba a girma da ginuwa. Dan a ƙalla akwai ɓangarori biyu zuwa uku a cikinsa. Ɓangarori biyu na farkon shiga gidan sunfi haɗuwa da tsaruwa, zakaga hakan tun daga wajema kafin ka kai ga shiga ciki, sai dai kuma ɗayan dake daga ciki ya fisu girma, amma bai kai su ƙyawu ba.
Harara ta zubama sashen guda biyu tana taɓe baki, tana gab da wucesu taja tsaki a zuciyarta wanda batai zaton ya fito har waje ba.
“K!! Dan ubanki wa kikema tsoki!!”.
Wata buɗaɗɗiyar murya mai cike da hargowa ta faɗa. Cak ta tsaya ƙirjinta na bugawar tsoro, tabbas da ace tasan mugun nan ya dawo gidan da bazata shigo ba sai magriba. Jin takun tafiya a bayanta alamar ya taso ya sakata juyowa. Ƙiris ya rage ya iso gareta, babu shiri ta kwasa da gudu zuwa sashen can ciki tana ƙwala kiran sunan Ummi!.
“Ya ilahi! Tanee lafiyarki kuwa? Wai sai yaushe ne hankali zai game jikinki kisan girma ya fara zuwa miki!”.
Ummi dake ƙoƙarin fitowa a kitchen riƙe da ludayin miya a hannu ta faɗa. Dai-dai isowar Hibbah cikin falon itama a guje. Bayan Ummi taje ta maƙale.
“K da wa kuma?”.
Ummi ta faɗa tana juyowa gareta fuska a ɗaure.
“Wannan mugunne fa Junaid Ummi. daga na shigo ina tsaki ya hau zagina kamar nasan da zamansa ma a gidan”.
Baki Ummi ta buge mata, tai saurin ja da baya daga jikinta tana dafewa.
“Wannan bakin naki da kanwa bata jiƙa a cikinsa shi zaisa kiyita shan wahala a wajen mutanen gidan nan Tanee. Mara kunyar banza matsamin a hanya”.
Gefe Hibbah ta matsa gudun kar Ummi ta sake kai mata wani dukan hawaye cike da idanunta. Sai da taga ta koma kitchen ɗin sannan ta nufi ɗakinta zuciyarta na ƙara jin tsanar mutanen gidan nasu. Da ace zata samu wata dama a hannunta koda ta yini guda ce sai ta bisu da bulala hansin-hansin, musamman ma Hajiya Mama da Abba da wannan azzalumin Junaid ɗin. Mukulli ta murza a ƙofar tata dan batason sake magana da kowa.
Tunda Ummi ta jiyo ƙarar rufe ƙofar Hibbah sai tai murmushi, tasan hakan na nufin tayi fushi, ba kuma zata buɗe ba sai Yah Abubakar yazo ya lallasheta ko jarabar danna Computer ɗin tata ta motsa. Watsar da ita tai ta cigaba da aikinta saboda bataso magriba ta sameta. Cikin ranta tana tunanin yaushe Junaid ɗin ya dawo ƙasar? Dan bataji alamun murna da ga yaran gidan ba sam. Rashin mai amsa mata zancen ya sata watsarwa ta cigaba da aikin gabanta.
Harta kammala ta shige babu wanda ya shigo a cikin samarin ƴaƴan nata, fatan dawowa lafiya tai musu sannan ta shiga wanka.
A ɓangaren Hibbah ma wankan tayi, kasancewar tana fashin salla tana kammala kintsawa ta fito, dan ta tabbatar Ummi ta shige. bakuma zata sake leƙo falon ba sai bayan sallar isha'i. Yayunta kuwa bata tsammanin yau zasu kwana a gidan ma. Musamman Yah Abubakar da Yah Usman da yace yana katsina.
Study table ɗinta ta haye dake can gefen falon a wani ɗan lungun. An shirya mata wajen tsaf da kayan karatu na musamman saboda kasancewarta ƴar gata, sannan haziƙa wajen sanin sirrin sarrafa Computer.
Tun ana ɗaukar lamarin nata shashanci har takai yanzu Yayansu Abubakar naci da ga tagomashin ƙwazon nata ta hanyar aikinsa na tsaro. Dan yasha sakata ayyuka masu muhimmancin gaske ana kuma samun nasara tunma bata kai haka shekaru ba. Wannan dalilin ne ya sakashi tsaya mata wajen ganin ta cika burinta akan zurfin nazari game da na'ura mai ƙwaƙwalwa.
Cike da ƙwarewa ta kunna Computer ɗinta saboda aikin data tarkatarma kanta na bibiyar masu power bike. Dan ta ɗauka alwashin kosu ɗin ƴaƴan uban waye sai ta gano su insha ALLAH.
Babu wanda ya shigo gidan sai Ummi data fito bayan sallar isha'i tace ta tashi taje taci abinci tunda babu wanda ya dawo a yayun nata har yanzu. Da to ta amsawa Ummin, tana gani ta koma ciki ta cigaba da aikinta cike da zaƙuwa.
Ummi dake jiyo motsin Hibbah ta shiga ƙwala mata kira ganin dare ya farayi. ta tabbatar kuma inba da gaske tayi mata ba, zata iya kaiwa biyun dare akan Computer ɗin batare da gajiyawa ba.
*_Tanee! Tanee!!_* wai bazaki tashi a gaban Computer ɗin nan kije ki kwanta ba sai na ci ƙaniyarki ko?!”.
Hibbah dake zaune a cikin falon daga can gefen study table ta ƙwaɓe fuska tamkar zatai kuka. A kallo ɗaya zaka fahimci tarin ƙuruciyar dake tattare da ita, dan kwata-kwata bazata gaza shekaru goma sha tara a duniya ba. Jin tahowar mutum ta bayanta ta miƙe da sauri a gaban Computer ɗin tana faɗin, “Wayyo Ummi nafa kusan gamawa wlhy”.
“Ai ba Ummi ɗin bace, mai kunnen ƙashi nine”.. Ƙyaƙyƙyawan saurayi mai tsananin kama da ita da bazai wuce shekaru ashirin da takwas ba ya faɗa a bayanta tare da kai mata ranƙwashi bisa kai. Tsalle tai zuwa gefe tana fasa ƙara duk da kuwa bai sameta ba. Ya balla mata harara yana kai hannu kan mouse ɗin Computer ɗin ya kasheta baki ɗaya. Dai-dai lokacin da yake ɗagowa ya nuna mata hanyar ƙofar ɗakinta yana faɗin, “kama gabanki kafin jikinki yay tsami anan”.
Idanunta dake tara ruwan hawaye ta shiga ƙyaƙyƙyaftawa. Cikin narkewar fuska tace, “Yah Umar dan ALLAH ka barni wlhy zuwa 12 zan shige na kwanta. ALLAH akwai abinda nakeyi mai muhimmanci a ciki”.
Charger ɗinta dake jikin socket ya fizga da nufin kai mata duka. Da sauri ta dirga wani uban tsalle da ihu tare da kwasa a guje zuwa hanyar ɗakin nata.
“Wai wane irin salon iskanci ne haka za'a dinga damun mutane da ihu kamar ƴaƴan rashin ƙwaɓa!”.
Wata murya mai kauri da amo ta faɗa daga bayansu. Basai an sanar musu wanene ba, dan haka Tanee dake gab da shiga ɗakinta ta ida afkawa da sauri tana rufo ƙofar. Umar yaɗan rumtse idanunsa yana cije lip ɗinsa na ƙasa da ƙarfi alamar son saisaita kansa dan jin zafin furucin mutumin da aƙalla zai iya kai shekaru Hamsin da huɗu zuwa da biyar
“Wai dan iskanci ba magana nakeba akaimin banza saboda rashin tarbiyya!. To dan uban mutum dai duk yanda yake kallona nine uban ubansa ma bama shi ba. Sannan kuma mijin uwarsa ne ni!!”.
Murmushi mai ɗaci Umar yayi yana haɗiye abinda ya tsaya masa a maƙoshi saboda kallon da Ummi dake fitowa tai masa. Yaja numfashi a sarƙe da faɗin, “Kayi haƙuri Abba ba wani abu bane ba. Nine da Tanee”.
“Eh lallai ai basai ka faɗaba na gani kai da taɓararriya ne, to ubanmi kale mata da har takema mutane ihu kamar wadda ake lalub....”
Cikin ɓacin rai Ummi ta katsesa da faɗin, “Kai Umar wuce ka tafi sai da safe”.
Zuwa yay ya wuce yana faman taunar lips ɗinsa dan shi kaɗai yasan tuƙuƙin baƙin cikin da yakeji a cikin ransa game da ƙanin mahaifin nasu da a yanzu suke kira da Abba saboda maye gurbin mahaifinsu da yayi dalilin ƙaddarar mutuwa, tabbas badan mahaifiyarsu ba da ko kallon hanyar da sukabi tuni kawun nasu bazai ringayi ba. Amma dasun yun ƙuro itace mai taka musu burki.
Umar na ficewa Abba ya saki wani shegen tsaki da nufar hanyar ɗakin Ummi. Itama bayansa tabi a fusace. Suna shiga cikin ɗakin a zafafe tace, “Halilu ina rabaka da jifarmin ƴaƴa da mugayen furuci amma baka kiyayewa. Ka sani idan ada ni dasu mun ɗauka wulaƙancinka da tozarci wlhy yanzu bazamu ɗauka ba. Dan badan ina takama yaran nan birki ba a kanka bisa dalilin mahaifinsu da tuni sun tabbatar maka da suma sunkai girma. Idan kuma bazaka bariba to lallai zan buɗe musu ƙofar dana rufe domin maka hijjabi akan hakan.....”
Wata wawuyar dariya ya saki yana faɗawa saman gadonta. Cikin salon iskanci da izgilanci yakai ƙafa ya taɗota sai gata ta faɗo kansa. Yunƙurawa tai zata tashi ya birkiceta zuwa ƙasa ya koma samanta. Dogon gashin da ALLAH ya azurtata da shi duk da tsufa yasa ya fara sirkawa da furfura ya damƙe cikin hannunsa tare da ɗan kwalin kanta ya fisga da ƙarfi, tare da sak ɗayan hannunsa ya danne mata baki............✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
Duka gamayyar biyar din(1k)
1,000
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_🔮TAKUN SAAƘA!!🔮_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
_ZAFAFA BIYAR 2K22_
🔥🔥🔥🔥🔥
*_LAST BONANZA_*
*KARO NA QARSHE!*
*_farincinku shine namu,ZAFAFAN DAI,sun sake amsa kokenku,sun sake rage muku kaso 20 cikin 100_*
*_Daga yau 29 ga wata,har zuwa 31 ga watan nan,xaku iya biyan 800 a amadadin 1000 na kudin litattafai biyar_*
*_za'a fara posting in sha Allah 3st January da yardar Allah_*
*HANZARTA KI BIYA NAKI KAFIN RANAKUN SU QARE*
*XAKI BIYA TA WANNAN ACCOUNT NUMBER DIN*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
SAIKU TURA SHAIDAR BIYA
08184017082
GA MASU TURA KATIN WAYA KO KUMA VTU,SAIKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYANKU
09134848107
_________________________
*_Chapter Five_*
............Wani irin rawa jikin Ummi ya fara saboda azaba. Ya ƙyalƙyale da dariya yana wani fici-fici da ƙananun idanunsa jajaye. “Asiya idan kin manta bara na tuna miki. Daga ke har ƴaƴanki da kikeji girmansu ya kai yanzu a tafin hannuna kuke wlhy. Zan kuma iya binku ɗaya bayan ɗaya na salwantar da rayuwarku batare da wani mahaluki ya iya gane hakan ba ko zargina. Kamar yanda na gagareki a baya da kikeji da ƙuruciya a yanzunma hakan take. Dan haka ki cigaba da buɗemin ido da tsagerancin nan naki kiga idan ban kai rayukanku ƙasa ba cikin ƙanƙanin lokaci”.
Ya ƙare mganar da hankaɗa kanta ta bigi fuskar gadon. Wata siririyar ƙara ta saki ta zaba. Cike da juriyar zaluncin data saba sha daga garesa ta dubesa da idanunta da suka kaɗa zuwa ja tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallar dake taruwa a cikinsu. “Insha ALLAHU Haƙilu bazaka taɓa cin nasara akan zuri'ata ba bayan nasarar aure na da kayi a baya, bazan gaji da faɗa makaba ko yanzu kana samun nasarane a kaina saboda wasu dalilai na lizzamin zaren ƙaddara, amma ka jira lokaci, dan kaɗan ya rage azo dai-dai wajen da zakasha mamaki.......”
Sake buga kanta yay a fusace kafin takai ƙarshen zancenta saboda sukar zuciyarsa da kalamanta sukeyi a duk sanda ta maimaita masa su, ya saka hannunsa ya danne mata baki yana ƙyalƙyalewa da dariya. “Iyakarki kauɗin banza da cika baki Asiya, amma ki sani ni Haƙilu nafi ƙarfinki, dan baki da maraba da wulaƙantacciyar dabba a gareni, amfaninki a wajena kawai samun abinda nai kwaɗayi a gareki tun farko kika hanani, yanda kika wulaƙantani a kansa a baya haka zan cigaba da samunsa a gareki cikin wulaƙantarwa da ƙasƙantar dake a ƙasan takalmana.”
Da iya ƙarfinta tai yunƙurin turesa amma ta gaza hakan, sai ma ƙara jigata da wahaluwa da takeyi a hannunsa. Yayinda shikuma yake ƙyalƙyala dariyar shaƙiyanci a gareta da izgili, cikin tsantsar zalunci da wulaƙantarwa ya shiga ƙoƙarin yin tarayya da ita kamar wanda ke tare da ƙasƙantacciyar karuwarsa. Yanayi yana kai mata mari saboda ƙoƙarin ƙwatar kanta da takeyi a garesa.
Kamar kullum sai da ya galabaitar da Ummi son ransa sannan ya barta yana faman tuntsurar dariyar rashin imani. Yaja kayansa ya saka bayan ya goge ƙazantar jikinsa da gashin kanta tare da tofa mata yawu ya fice yana cigaba da ƙyalƙyala dariyar.
Wani irin siririn kuka Ummi ta saki mai cin rai a wajen. Takai kusan awa ɗaya tanayinsa kafin ta miƙe zuwa toilet da ƙyar saboda azaba. Dukkan dabarun data sabayi domin gyara jikinta a duk lokacin da hakan ta faru tsakaninsu su ta gudanar, koda ta fito doguwar riga ta saka tahau saman abin salla ta fara gayama ALLAH kukanta akan zaluncin Alhaji Haƙilu ƙanin mijinta ada, sannan kuma mijinta a yanzu.
Bayan tayi nafilfilinta tai zaman karatun AL-QUR'ANI. Sai da taji zuciyarta tayi mata sanyi, nutsuwarta ta dawo jikinta sannan tai addu'a ta ɗan kwanta, cikin lokaci ƙanƙani barci mai daɗi yay gaba da ita tamkar bata da wata damuwa.
★
Kamar yanda ta horar da yaranta tun suna ƙanana yau ma tun kiran sallar farko na asuba suka tashi. Sai da duk sukai alwala sanann suka firfito daga ɗakunansu su biyar abin sha'awa, dan a daren duk suka dawo ba kamar yanda ta tsammaci zasu kwana a wajen ba, a tunaninsu tayi barci ita da auta shiyyasa basu shigo ba. Ammar ne ya nufi ƙofar ɗakin Hibbah ya shiga mata knocking da kiran sunanta har sai da yaji ta amsa. “Tashi kiyi salla, saura kuma idan kin idar ki sake kwanciya tunda kinsan dai yau kinada text ɗin safe”.
Bai jira amsartaba yabar wajen dan yayunsa na jiransa. Basu damu da tada Ummi ba, dan sunsan ita bata makara saboda mace ce mai tsantseni da yawan kula da ibada, bata da wasa sam akan bautar ALLAH. Hakama koda suka fito daga sashen nasu basuyi gigin tada sauran jama'ar gidan ba suka fice abinsu zuwa massallacin anguwar.
Daƙyar Hibbah ta tashi zuwa toilet saboda barcin dake cikin idonta. Cikin layi da rangaji irin na wadda ta tashi a barci ta shige bayin. Kusan mintuna ashirin sai gata ta fito ɗaure da towel tana tsane gashinta da wani alamun ta samu tsarki. Zani ta ɗaura ta saka hijjab har ƙasa ta tada salla.
*_7:34am_*
A gurguje take shiri tana yawan kallon agogon ɗakin nata saboda kiran da Ummi keta faman ƙwalamata daga falo.
Cikin kumbura fuska da ƙunƙuni take faɗin, ‘Kai Ummi wannan kira kamar makauniya, ai ba kowa ne ya jamin wannan makararba sai Yah Ammar, duk da yasan zanje makaranta harda min gargaɗin karna koma barci sai gashi bayan dawowarsu massallaci ya tsareni sai na haɗa masa indomie wai nafi kowa iya dafawa........’
“Tanee! Tanee!!”.
Ummi ta sake ƙwalama Hibbah kira again. Ƙoƙari amsawa take cikin zazzaƙar muryata tana tattare tarkacen abinda zata buƙata a cikin bag ɗinta mai zubin school bag. Daga can ta sake faɗin, “Auta kina kallon agogo kuwa?!”.
Saurin ɗaukar bag ɗin tayi da gyalenta tayo waje da hanzari. Tun kafin ta ƙaraso tsakkiyar falon Yah Umar ya wullomata harara cikin faɗa. “Wai ke kullum sai kin makara kin makarar da mutane hankalinki ke kwanciya a gidan nan ko? Tun kina zuwa secondary halinki kenan, yanzu kin fara jami'ar ma baki canjaba”.
Fuska ta kumbura tana tura baki, ta ajiye bag ɗinta da gyalen a saman kujera tana ƙarasawa dining ɗin inda duk suke zaune har Ummi, dan haka suke cin abinci a tare duk safiya da dare. Cikin shagwaɓar data saba da tsiwar da bata barin bakinta tace, “Kai Yaya Umar naga dai Yah Ammar ne ya sakani makara, sakanifa yayi na dafa masa noodles”.
Yah Ammar dake kujerar gefenta yana ƙoƙarin fara cin indomie ɗin data dafa masan ya zubomata uwar harara shima yana faɗin, “Dama can kin saba makararki yarinya zaki wani jingina dani”.
Baki ta sake buɗewa zatayi magana Yah Usman dake duba wasu takardu dake gabansa a dining ɗin shima ya watso musu harara ita da Ammar ɗin, “Dalla malamai karku cika mana kunne kuma ko”.
Ummi dake turama Hibbah kofin kunu data zuba mata tace, “Ai inda sabo sun saba, Ammar da Tanee basa taɓa zama waje guda basu isheka ba, sai kace suna ganin hanjin junansu. Nikam babu mai barina da ciwon kai kowa yayi ya gama ya kama gabansa”.
Baki Hibbah ta kuma cikawa da iska tana duban Yah Muhammad da Yah Abubakar masu kareta. Yaya Abubakar dake hidimar haɗama kansa shayi yayi murmushi, “Auta yada kallona kuma? Nimafa yau gashi kina neman makarar dani bayan nace da wuri zan fita”.
Cikin shagwaɓar da takema yayun nata saboda so da ƙaunarta da sukeyi ta ce, “Yaya kaima ko?” ta faɗa tana maida dubanta ga Yah Muhammad da ke ta faman latsa wayarsa. Ƙaramar dariya yayi tunkan tace komai, ya ajiye wayar tasa yana amsar kunun da shima Ummi ta zuba masa dan kusan halinsu ɗaya da Muhibba shima bai cika son tea ba. “Kinga autan Ummi manta da kowa ki karya, yau da kaina ma zan kaiki makaranta bazakibi Ammar ba, maza lokaci na sake ja”.
Jin Yah Muhammad yace da kansa zai kaita makaranta yau ya saka bakinta washewa. Ta kalli Yah Ammar abokin tsamartata tana masa gwalo. Kusan duk sai da sukai murmushi kowa na girgiza kansa cike da mata kallon so da ƙauna.
Basai an faɗa ba, yanda ƴan uwata da Ummin su kema Hibba a gidan zaisa kowa fahimtar ita ɗin ƴar gata ce kuma shalele. A kullum kowa burinsa yaga farin cikinta. Koda laifi tayi suka zaneta ko mata faɗa daga baya sai su koma mata nasiha da lallashinta har sai sunga ta koma rayuwata ta ƙiriniya da rashin ji suke samun nutsuwa. Sai dai kuma a ɓangaren Abba da sauran matansa sam ba haka bane. Sun tsani Muhibbat tamkar ita kaɗaice ƴa a gidan. Hakama sauran ƴaƴan gidan duk basa sonta. Kafin Hibbah takai haka kullum tambayata mi sukai musu? Amma babu mai bata amsa a tsakanin Ummi da yayunta guda biyar. Sai da tayi hankali ne zuwa yanzu take ɗan fahimtar wasu abubuwan duk da dai ba wani ya taɓa zama ya sanar da ita gaskiyar dalilinba har zuwa yanzun.
Itace farkon kammalawa, ta miƙe tana faɗin, “Alhmdllh”.
Yaya Abubakar ya dubeta da kulawa cikin lallashi yace, “Auta ki dingacin abinci ko zaki ƙara girma fiye da haka dan ALLAH, ke kowa na girma yayi ƙiba banda ke, makarantar nan kamar ƙara tsiyayar dake take ma”.
Murmushi tayi cike daso da ƙaunar Yayun nata masu sonta. Tace, “Yah Abubakar duk wannan ƙatuwan dana zama, da kaɗan fa Yah Ammar ya fini tsaho”.
Harara Yah Ammar ya galla mata da faɗin, “Tunda nine marainin wayonki ko? bar ganin Ummi a wajen, na tashi ɓarar dake zanyi ALLAH”.
Dariya duk suka sanya masa, dan da alama da haushi yake maganar. Hibbah tai masa gwalo da ɗaukar bag da gyalenta ta fice da gudu saboda ganin zai miƙe, tasan kuma kanta zaiyo.
A ƙofar fita falon taci karo da Abba. Tai saurin komawa baya jikinta naɗan rawar kaɗuwa. Dan duk da rashin tsoro na Muhibbah a rayuwarta tana matuƙar jin tsoron Abba tun tana ƴar ƙarama. Hararar da yake wulla mata ya sata sake sata duƙar da kanta idanunta na tara ƙwalla.
“Wane kalar shashanci ne kuma haka? Da girmanki amma kullum lalacewa al'amuranki ke ƙarayi saboda ke ƴar ido ce!!”.
Sam Hibbah bata son tsawa, shiyyasa da zaran Abban ya mata ita take rikicewa, yanzu ɗinma duk sai jikinta ya hau ɓari, muryarta na rawa alamar tahowar kuka tai saurin faɗin, “Kayi haƙuri Abba bansan ka tahoba ALLAH. Ina kwana”.
Ciki yay batare daya amsa mataba yana jan tsaki. Hibbah ta bisa da kallo wasu hawaye masu zafi na sakko mata bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Ido suka haɗa da Yah Usman. Ya girgiza mata kansa alamar kar tai kuka. Dan tun tsawar da Abban yay mata duk hankalinsu ya dawo kansu.
Suma koda suka gaishesa bai amsa musu ba. Sai faman mazurai yakeyi. Basu sakebi takansaba duk suka kwashi kayayyakinsu sunama Ummi sai sun dawo. Itako amsa musu take da fara'a tamkar batasan da zaman Abban a wajenba ma.
Yah Muhammad ne ya kama hannun Hibbah da ko motsi ta kasayi har yanzun. Sai da sukazo har wajen motarsa yasa handkerchief ya share mata hawayenta batare daya ce komaiba. Sauran ƴan uwansa ma kuma bai basu damar cewa komai ɗin ba. Sai umarnin yin addu'ar fita gida kamar yanda suka saba yay musu.
Suna kammalawa kowa ya hau abin hawansa. Yah Muhammad da Hibbah. Abubakar ya ɗauka Usman da Umar a motarsa dansu basu da mota har yanzu sai mashina. Ammar ma ya hau mashin ɗinsa lifan shi kaɗai tunda yau Hibbah tabi babban yaya...........✍
_BONANZA, BONANZA, BONANZA 20% OFF ZAFAFA PAID BOOKS, OFFER ENDS ON 31st DEC 12AM INSHA ALLAH!_
_ASSALAMU ALAIKUM!!_
_ZUWAGA MASOYA, KUMA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR._
_KORAFI YA KARBU, DAGA YAU LARABA 29 GA WATAN DECEMBER IN SHAA ALLAH, ZUWA 31 GA DECEMBER RANAR JUMU’AH KENAN. BISAGA KORAFI DA NEMAN RAGE KUDIN ZAFAFA NA DUBU DAYA KAN LITTAFAN BIYAR, IN SHAA ALLAHU, KORAFIN KU YA ISA GARE MU. KUMA MUN AMINCE. ZAMU KARBI 800 GA LITTAFAI BIYAR DIN DA KUKE BUKATA, A MAIMAKON DUBU DAYA NA BOOKS BIYAR. YAU LARABA ZUWA JUMU’AH KARSHEN WATAN DECEMBER KENAN. ZAMU RUFE KARBAR 800 KUDIN ZAI KOMA DUBU DAYA KARFE 12 NA DAREN RANAR JUMU’AH INSHA ALLAH._
_GA WATAN JANAIRU (3st JANUARY, ZAMU CIGABA DA KARBAR DUBU DAYA KAN LITTAFAN BIYAR._
_A KUMA 1 JANUARY DINNE IDAN ALLAH YA KAI MU, ZAMU FARA SAKIN PAGES DIN LITTAFAN NA KUDI, WATO PAID PAGES👏🏼👏🏼NA BOOKS DIN._
_LITTATTAFAN SUNE: *DABI’AR ZUCIYA (FALL IN LOVE)* NA SAFIYYAH HUGUMA_
_*HALIN GIRMA (GLAMOROUS LOVE)* NA HAFSAT RANO_
_*DEEN MARSHALL: (INTENSE LOVE)* NA MAMUH GEE_
_*SO DA ZUCIYA (A LOVE SO BEAUTIFUL)* NA: NANA HAFSAT MSS XOXO_
_*TAKUN SAAKA(LOVE IN TIME)* NA: BILLYN ABDULL._
_KAI DAGA JIN SUNAYEN KASAN ZA’A SHA GWAGWARMAYA A KUMA KARU DA DARUSSAN DA ZASU KOYAR, NA FADAKARWA DA NISHADANTAR WA HADI DA TACACCIYAR KAUNA MARAR GAURAYE_
_DOMIN KASANCEWA CIKIN MABIYA LITTAFAN ZAFAFAN SAI A TUNTUBE MU TA.👇🏾_
*_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*
*ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*
*_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*
*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*
*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*
*_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_*
*_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_*
*_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_*
*_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_*
*_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_*
*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*
2👉🏾400
3👉🏾500
4👉🏾700
5👉🏾1000
*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*
09134848107
*_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
#team zafafa biyar
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
__________________
*_ASSALAMU ALAIKUM BEAUTIFUL PEOPLE!! ZAFAFA BIYAR FAMILY💯💯🙌🏽❤️_*
_MUNGODE DA ZABIN LITTAFAN ZAFAFA BIYAR. ALLAH YA KARA BUDI YA KUMA BAR ZUMUNCI_
*_KAMAR KO DA YAUSHE, WANNAN KARON MA MUNZO DA KOKON BARAR YOUTUBE CHANNEL DIN YARON MU, SUDEIS MASOYI KUMA MAKARANCI, MAHADDACIN ALKUR’ANI MA GIRMA_*
_WANNAN KARON MA DAN ALLAH A TEMAKA ADANNA WA CHANNEL DINSA KARARRWA DOMIN KASANCEWA DA MU A DUK SANDA MUKA DORA FEFAN BIDIYON SA, A TALLAFA A KALLA A KUMA DANNA MASA SUBSCRIPTION. HAKAN NA KARAWA SUDEIS KWARIN GWIWAR SAKE DAGEWA YA KUMA KARA KAIMI WAJEN YIN KARATUN SOSAI. MUNGODE KWARAI💯🙌🏽❤️_
*_GA CHANNEL DIN DAKE YOUTUBE NAN👇🏾_*
https://youtube.com/c/sudaiskura
_Sudais is a young boy who has passion in recitation of the Holy Qur'an at a very young age._
_Please help him grow his YouTube channel by subscribing and liking his videos to encourage the little boy. Jazakumullahu khairan🙏🏻_
_________________________
*_Chapter Six_*
..............Ƙoƙarin kauda fuskarta taketa faman yi saboda kar Yah Muhammad ya ga hawayen dake guje-gujen sakko mata akan fuska tun bayan barowarsu gida. Sai dai kuma abinda bata sani ba tuni ya fahimci kuka takeyi, yadai mata shiru ne domin bata damar rage nauyin zuciyarta.
Sai da ya ɗauka titin da zai kaisu har makarantar tasu sannan yay gyaran murya batare da ya kalleta ba. Shiru Hibbah bata motsa ba saboda zurfi da tai a tunani....
“Auta!”
Ya kira sunanta cike da kulawa. Nanma shiru babu alamar ta jisa. Leɓensa yaɗan ciza na ƙasa yana gangarawa gefen titi. Harya kashe motar gaba ɗaya ya juya yana kallonta batasan mi yakeyi ba. Cikin damuwar data bayyana sosai akan fuskarsa ya ce, “Muhibbat!!”.
A firgice ta juyo garesa tana sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya. Sai kuma tai saurin kai hannunta akan fuskarta ta shiga share hawayenta tana ƙaƙalo murmushi. “Lah Yaya banjikaba ALLAH. Ina can wajen kallon hanya har idanuna na hawaye dan ƙauyanci”.
Murmushin da bai niyyar yi baneba ya suɓuce masa. A ransa yanajin ƙaunar ƴar ƙanwar tasu da yaba halinta na manya. Duk da rawan kanta da tsiwa ita ɗin yarinyace data san yakamata. Tana da wasu nagartattun halaye da sai ka nutsu gareta kake iya ganosu. Amma a kallo ɗaya zaka iya dangantata da yarinya mai rawar kai da shirme. Ya ɗanja numfashi yana furzarwa a hankali tare da kafeta da idanunsa irin nata.
“Mi kike tunani Muhibbat!?”.
A yanda yay maganar babu wasa a cikinta ne ya sata ɗago idanunta dake ƙoƙarin tara ƙwalla ta dubesa. Sai kuma tai saurin girgiza kanta tana ƙoƙarin maida kukan dake son ƙwace mata.
“Ba bu komai Yayah”.
Ta faɗa muryarta na rawa.
Sosai ya sake kafeta da idanunsa dake canja kala zuwa ɓacin rai. Sai dai kuma cikin tausasa murya ya ce, “Kin dai san banason ƙarya ko?”.
Kanta ta jinjina masa hawayen da taketa ƙoƙarin makalewa suka gangaro a hankali bisa fuskarta.... “Yaya! Abba ne, miyasa baya sonmu? Musamman ma ni ya tsaneni bayason ganina”.
Takai ƙarshen maganar tata da fashewa da wani irin kuka mai cin rai ga ma'abocin saurare. Idanunsa ya lumshe a hankali tare da cije leɓensa na ƙasa da ƙarfi. Addu'a ya fara karantowa a zuciyarsa domin samun dai-daito daga fushi da fusatar damuwar ƴar uwar tasa. Ya kamo hannunta cikin nashi ya rumtse da ƙarfi.
Kamar jira take ta sake fashewa da wani kukan, fuskarta ta kwantar akan hannayen nasu dake cikin na juna, hawayenta suka shiga gangarowa har akan fatar hannunsa data ɗora kanta a kai. Cikin kuka ta cigaba da faɗin “Yaya miyasa Ummi ta yarda ta auresa? Bayan kuma tasan shi ɗin mugu ne. Miyasa bata haƙura ta zauna damu mu kaɗai ba bayan rasuwar Abbanmu?. Wlhy Yaya banason Abba na tsanes.......”
“Muhibbat!”. Yay saurin katseta da ƴar tsawa.
Ɗago kanta tai tana kalonsa, ganin yanda ya ɗaure fuska ne ya sake sakata fashewa da kukan.
Yaya miyasa bakwaso nace banason Abba bayan shima baya son mu. Kullum shike gusar da farin ciki a kan fuskokinku. Duk randa yazo sashenmu sai Ummi tayi kuka a ɓoye. Sannan fuskarta tana kumbura kamar wadda aka daka Yayanmu”.
A matuƙar razane yake kallonta a yanzun. Dan tabbas tun basukai hakaba suke tambayar Ummi mike samunta a fuska a maban-banta lokaci, amma sai takan ce musu wani ciwo ne yake mata haka akan fuska lokaci-lokaci, amma tana shan magani. Sunsha damunta suje asibiti amma sai taƙi yarda. Sai dai kuma yau gashi ƙaramar ƙanwarsu tazo da wani batu mai girma. Shin kodai da gaske ne da ake cewa duk ƙanƙantar ɗiya mace tafi ɗa namiji lura da maida hankali akan abu.......
“Yayanmu dan ALLAH kasa mubar musu gidansu mu koma can wani gari da zama mu daina ganinsu suma su daina ganinmu.”
Hibbah ta katse masa tunani ta hanyar girgizasa tana kuka da roƙonsa.
“Tanee! kinga nutsu muyi magana. Maza share hawayenki na tambayeki”.
Da sauri ta shiga share hawayenta da handkerchief ɗinsa. Duk da wasu nabin wasu hakan bai hanata faɗin, “Yaya na goge”.
“Auta kin taɓa ganin wani ya daki Ummi ne?”.
Kanta ta girgiza masa.
“To miyasa kikace kamar ana dukanta?”.
“Yaya nidai haka kawai nake ganin kamar shatin yatsu a fuskarta a duk randa fuskan yay kumburi. Sai kuma ranar da Abba ya kwana a sashenmu na taɓa jin kamar tana kuka na fito ɗaukar ruwa dana manta ban ɗauka ba da dare. Tana kuka sosai, ina kumajin muryan Abba yana mata kamar magana cikin faɗansan nan”.
Kallonta kawai yake ko ƙyaftawa babu, acan ƙasan ransa kuma yanama kalamanta fashin baƙi dalla-dalla. Ganin yaƙi cewa komai yasata kai hannunta akan masa ta girgiza shi.
Ajiyar zuciya ya sauke da haɗiye damuwar dake neman kufcewa akan kamilalliyar fuskarsa.
“Yaya baka yarda ba ko?”.
“A'a Auta, taya zan ƙaryataki bayan nasan ke ɗin baki da ƙarya. Kawai dai ina nazari ne akan maganar taki. Amma inaga yanzu ba shine lokacin yinsa ba. Bara na kaiki makaranta karki makara. Idan mun koma gida zamuyi magana. Amma na roƙeki bayan ni karki faɗama kowa zancen nan har cikin su Usman kinji ko”.
“Insha ALLAH Yaya bazan faɗa musu ba. Amma dan ALLAH ka tambayi Ummi kaji ko Abba yake dukanta ne?”.
Ɗan murmushi yayi a ƙasan ransa yana jinjina wautarta. “Karki damu insha ALLAH bazan manta ba.
Koba komai ta ɗanji sanyi a ranta. Dan haka ta ƙarasa share hawayenta nauyin da zuciyarta yay mata yana sauka a hankali.
Tunda ya tada motar suka cigaba da tafiya sai shi ya koma cikin yanayin shiru ɗin. Dan gaba ɗaya tunaninsa da hankalinsa sun koma akan zantukan Hibbah.
Koda suka isa makarantar sai da ya sakata tai addu'a kafin ta fita a motar, ya miƙa mata 1k tare da mata gargaɗin ta dage akan text din da yaji Ammar ya faɗa zatayi. Inba hakaba bazai kaita chaina ɗin da take burin zuwa ƙaro ilimin kimiya da fasaha ba”.
Cike da son cikar burinta ta tabbatar masa insha ALLAH zata dage wajen cinye text ɗin da maki mai yawa. Daga haka ta shiga ɗaga masa hannu har yay reverse yabar wajen. Ƙoƙarin nufar department ɗinsu tayi ranta fal saƙe-saƙe itama. Ta duba department ɗin su Zahidah a ranta tana tunanin suma sunzo tuni, dan suma sunce mata suna da text yau tun 8am.
★★★★
Koda su Hibbah suka fita a class bata nema su Hafsat ba. Dan tanason samun nutsuwar ƙarasa aikinta na jiya. Kai tsaye ɗakin dake ajiye da na'urori mai ƙwaƙwalwa na department ɗin nasu ta nufa. Dan tana ɗaya daga zaƙaƙuran yara mata matasa dake baje kolin basira da ƙwazon da ALLAH ya basu akan ilimin kimiya da fasa.
Ta samu ɗalibai irinta masu naci da ƙulafuci ɗai-ɗai a ɗakin. Bataima kowa magana ba ta zauna a table guda ɗaya
dake daga can lungu tana sauke ajiyar zuciya, tsabar yanda take nacema Computer ɗin wajen saboda daɗin da take mata har security ta ƙirƙira ta saka dan tanada ajiye-ajiye da yawa a ciki. Akwai wani yaro da suke ƴar tsama da shi, shima yanada ƙwazo matuƙa akan fannin, ya taɓa mata manaƙisar lalata mata securitys ɗin data saka domin binciken abinda take ɓoyewa a Computer daba tata ita kaɗai ba. Aiko data tashi ita sai da tai masa ɓarnar daya gwammaci da bai aikata mata ba, dan babbar ma'ajiyarsa ta Computer ɗinsa dake gida taima kutse, tare da aikata ɓarna da har iyayensa sai da suka saka police zuwa har gida domin kamata. Sai dai kasancewar tana da Yah Abubakar hakan bata faruba, sukai ƙoƙarin ganin sun rufe case ɗin.
Flash ta ciro a bag ɗinta tai connecting da Computer ɗin ta shiga abinda ya kawota cike da ƙwarewa da fatan nasara. Kusan mintuna goma sha uku tana abu ɗaya, sai faman sauke ajiyar zuciya take akai-akai. Harma ta fidda rai da nasara sai gashi cikin amincin ALLAH ta kuma dace. Wani lallausan murmushi ta saki da ambaton kalmar “Alhmdllhi” tana rungume Computer ɗin dan farin ciki. Tuno da bata sanarma Yah Abubakar bane ya sata saurin ɗauka wayarta. Batare da tunanin komai ba ta dailing number ɗinsa. Sai dai harta tsinke bai ɗaga ba. Ta tura baki gaba alamar jin haushi tana ƙoƙarin sake kiransa. Nanma ɗin dai babu amsa. Cikin takaici ta ƙara ƙoƙarin sake kira a karo na uku sai ga nashi kiran ya shigo.
Ɗagawa tai da sauri tare da kwaɗa sallama cikin karaɗinta da shagwaɓa. Daga can Yaya Abubakar ya amsa yana faɗin, “Autar Ummi lafiya dai ko? Ina cikin aiki ne fa”.
“Lafiya lau Yaya dama fa wani abu zan sanar maka. Jiya baka dawo da wuri bane har nayi barci, ɗazun kuma na manta ne saboda Abba”.
“Okay to ina jinki”.
“Uhm yauwa Yayana. Kasan wani abu? Jiya muna fitowa a school wasu masu power bike suka kusan turemu, sanadin hakan ma har Hafsat ɗin gidan aunty Kulu ta samu rauni a ƙafarta sai da akai mata gyara a asibiti. To ni kuma tun a jiyan na jefa musu agogon nan nawa, yanzu haka na gano inda suk.......”
Kafin takai ƙarshen maganar tata ma Yaya Abubakar ya miƙe a zabure da ga can yana faɗin, “Masu power bike?!”.
“Yes! Yaya. Kasansu ne?”.
“Kinga auta kina ina? Wannan maganar bata waya bace zanzo yanzu na sameki, karfa ki faɗama kowa bayan ni”.
Kafin ta samu damar cewa wani abu ya yanke wayar.
“Oh Yaya kama tsaya na gama maganata mana zaka wani yanke. To nama fasa faɗa maka sai nan da awa uku”. Tai maganar tana haɗa kayanta da fushi ita a dole taji haushi. Tana ƙoƙarin rataya bag ɗinta a baya kira ya shigo wayar tata. Ganin Zahidah ya sata ɗagawa tana kai wayar kunnenta da nufar ƙofar fita daga wajen.
Tana cikin sauraren Zahidah dake faɗa mata inda take taje ta sameta taga ansha gabanta. Takaici ya sakata janye wayar daga kunnenta ta ɗago domin ganin wane shege ne ya tare mata hanya.
Turus ta ɗanyi tana kallon zaratan mazajen dake a gabanta riƙe da manyan bindugu tamkar wasu mala'ikun ɗaukar rai. Duk da rashin tsoronta sai da taji wani abu mai kama da firgici ya gitta mata. Ta motsa bakinta a hankali idanunta na wani mar-mar.
“Bayin ALLAH lafiya kuwa?”.
Ta tambaya tana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya.
Ɗaya da ga cikinsu ne ya nuna mata i'd card ɗinsa da faɗin, “Mu jami'an tsaro ne da ga hukumar ƴan sanda ta farin kaya. Munzo nan ne kuma dominki Muhibbat Aliyu Hamza”.
“Wurina kuma? To ni miya haɗani da ku? Wama ya faɗa muku sunana?”.
“Duk zaki sami amsoshinki idan munje office”.
A tsiwace tace, “Hu'um ai wlhy bazan biku ba, barama na kira Yayan.....”
Zare wayar da ɗaya daga cikinsu yayi ne ya saka sauran maganar tata maƙalewa. Ya katse kiran da taima Yaya Abubakar yana kashe wayarma baki ɗaya.
Wani yawu Muhibbat ta haɗiye da ƙyar tana binsu da kallo tare da ɗalibai ƴan uwanta da hankalinsu ya fara kaiwa garesu suka ɗan fara taruwa domin kallon mike faruwa. Mota suka nuna mata. Da farko batai niyyar shigaba. Amma tuna tana dasu Yaya Abubakar aduniya ya sata shanye dukkan wata fargabarta ta shiga motar tana ƙunƙunin amshe mata waya da sukayi.
Dai-dai lokacin da suke shigewa motar suma Zahidah da aka kai mata labarin anga ƴan sanda na neman ƙawarta ta iso wajen. Hankalinta tashe ta shiga ƙwala kiran sunan Hibbah da sam batama jita ba. A firgice ta lalubo wayarta domin san kiran Ummi ta sanar mata ko zata sanarma cikin su Yaya Umar, dan ruɗewar da tayi tasa tama manta da cewar Yaya Ammar shima anan makarantar yake nasa karatun, yana a shekarar ƙarshe ne ta kammalawa..
★♣♠♣♠♣♠♣★♣♠♣♠♣♠♣★
Ummi na zaune a can inuwar mangwaro dake backyard ita kaɗai tun barin Abba sashen nata bayan ya gama shuka mata shika-shikan rashin mutuncinsa da ya saba. Lalle take sakama yatsun hannunta dan ita mace ce mai son jan lalle sosai. Har takai ta koyama Hibbah kasancewar tun tana ƴar ƙaramarta take mata itama.
Kallon wayarta da kira ya shigo tayi duk zatonta ma Hibbah ce. Batai mamakin ganin Zahidah ba, dan tasan Hibbah zata iya amfani da wayar tata wajen kiranta idan tata wayar babu kuɗi. Ɗayan hannunta tasa ta ɗauka wayar fuskarta da Murmushin tuna a yanda Autar tata ta fita cike da tsoron Abba a tare da ita.
“Autan Umminta yaya dai?”.
Ta faɗa dai-dai lokacin da take ɗora wayar akan kunnenta.
“Ummi ba ita bace nice Zahidah”.
Jin yanda muryan Zahidah ke rawa kuma a firgice ya saka Ummi ruɗewa ta shiga jera mata tambayoyi..
“Ummi akwai matsala ne wlhy, yanzu ina capteria muna waya da Hibbah ina faɗa mata ta fito class ina jiranta muci abinci sai wayan ya katse. Ina ƙoƙarin sake kiranta a zatona network ne sai ga wani course mate ɗina yazo yake sanar min ga jami'an tsaro can suna neman sister ɗina. Na tafi domin tabbatarwa kawai na iske harta shiga motarsu sun wuce da ita Ummi. Ni kuma gashi bani da no ɗin su Yaya Abubakar balle na sanar musu shine na kiraki dan ki sanar musu”.
_(Hasbinallahu wa-ni'imal wakil)_ Ummi ta shiga mai-maitawa da sauri-sauri dan jin wani irin yuuu cikin idanunta da kanta. Cikin ƙoƙarin haɗiye tashin hankalin da take ciki ta ce, “Wani laifin ta aikata ne Zahidah?”.
“Ni dai Ummi a sanina bata aikata komaiba wlhy.”
“Shikenan bara na kira Abubakar naji idan yana kusa ko Muhammad”.
“To Ummi”. Zahidah ta faɗa tana share hawayen da suka gangaro mata akan kumatu. A kallo ɗaya zaka fahimci a matuƙar firgice take. Gashi ita kaɗai ce yau dan Hafsat batazo ba saboda ƙafarta.
Hango Yaya Ammar da ke nufota da sassarfa ya sakata tunawa da yana a cikin makarantar shima. A zabure itama ta nufosa.
“Zahidah! Ina Muhibbah?”.
Ya faɗa cikin furzar da hucin hakkin gudun da yayi dai-dai isowarsa gabanta.
Bayanin abinda ta sani da wanda taji a bakin mutane tai masa tana share hawaye. Hankalinsa ya ƙara tashi matuƙa shima. Dan duk tsokanarta bata taɓa kaiwa matakin hakaba, a yanda yaji wai ƴan sanda da manyan bindugu ya matuƙar harmutsa tunaninsa.
Babu shiri ya shiga neman no ɗin Yaya Abubakar, sai dai kuma number busy take nuna masa alamar yana waya da wani kenan ko makamancin hakan. Maida akalar kiransa yayi akan Yaya Muhammad. Bugu biyu ya ɗaga. Ko sallama bai masa ba ya shiga masa bayanin abinda ke faruwa.
Ko tari kasa yi Yaya Muhammad yay. Sai numfashinsa ne dake tafiya a sarƙe tamkar mai ciwon Asthma. Batare da ya iya furta komai ba ya yanke wayar. Kamar jira sai ga kiran Ummi ya shigo masa.
Sam baiyi tunanin taji mike faruwa ba itama. Dan haka yay ƙoƙarin saita kansa dan ganin bai tada mata hankali ba. Sai dai a yanda yaji muryarta tun a sallama ya matuƙar tada masa hankalin. A hautsine ya shiga tambayarta lafiya? Dan ko kaɗan basason tashin hankalinta.
Duk yanda Ummi taso danne damuwar dake a cikin muryarta ta kasa hakan. Cikin gwamewar numfashi ta shiga yimasa bayanin duk yanda sukayi da Zahidah.
Da sauri ya ce, “Ummi dan ALLAH ki kwantar da hankalinki, insha ALLAH zamu nemi idan take bara na nema Abubakar yanzun nan”.
Bai jira cewarta ba ya yanke wayar dan bayason shima ta fahimci rauninsa kai tsaye..............✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Chapter Seven_*
..........Lokaci da aka basu da ga gidan gwamnati na kamo wannan gagarumin ɓarawo da babu wanda yasan ainahin kamanninsa na zahiri yay matuƙar tada hankalin kowacce hukuma ta ƴan sanda dake a jihar. A ɓangaren jami'an ƴan sanda na farin kaya tuni sun duƙufa wajen bincike suma. Musamman da ya kasance jami'ansu ne suka sami nasarar samo wheelchair da sauran kayan da ɓarawon yay amfani da su a waccan ranar.
Tabbas wannan ɓarawo yana da matuƙar wayo da dabaru kala-kala da ganosa ke bama duk wasu jami'ai wahala kai tsaye. A duk ɓarnar da zai aikata yana aikatata ne da maban-banta fuskoki da salo daban-daban kuma. A kusan shekara biyu kenan da fitowarsa a bayyane babu wanda zai iya cewa ga fuskarsa ta ainahi ko samun wani labari nasa koda ƙanƙani ne.
Duk da dai wasu a cikin jami'ai da suka ƙware sosai wajen aiki da binciko mai laifi sun taka rawar gani sosai wajen kafa masa tarkuna na musamman amma yana tsallakesu saboda duk tsiyar da zai shuka ba gaba gaɗi yake aikata ta ba sai ya shirya da shiri na gaske.
Bayan zama na musamman da sukayi jiya game da binciken da sukeyi akansa furucin matashiyar budurwa ya shigo cikin jerin abubuwan da suka zauna domin tattaunawa. Lokaci ne da bai kamata suyi sakaci da duk wata dama da zatazo musu ba komin ƙanƙantarta. Dan haka basu tsaya sanya ba wajen bibiyar matashiyar budurwa mai cikakken suna *_MUHIBBAT ALIYU HAMZA_* da jami'insu ya kawo musu labarin alwashinta akan abin farautarsu. Dan haka suka kasance biye da ita tun a safiyar yau, tun daga ƙofar gidansu har zuwa cikin makaranta, shigarta class da fitowarta zuwa Computers room. Dukkan binciken data gudanar har zuwa kiran da taima Yaya Abubakar duk akan idon wanda ke biye da ita ne batare data sani ba...
Sosai tashin hankali ke tattare da Muhibbah ganin inda aka kawota. Duk da Yayanta jami'in tsaro ne na ƴan sanda mai muƙamin d.p.o bata taɓa zuwa police station ba. Amma a yau sai gata a cikin headquarters na ƴan sandan farin kaya tsumu-tsumu batare da tasan laifin data aikata ba.
Wani lafiyayyen office aka kaita da yaji kayan more rayuwa tamkar ba'a hukumar ƴan sanda ba. Ta saci kallon dattijon mutumin dake zaune kansa duƙe yana aiki kan takardun dake a gabansa. Cikin girmamawa wanda ya shigo da ita office ɗin ya ƙame yana salute ɗinsa.
Sai a lokacin ya ɗago fuskarsa ɗauke da murmushi ya dubesu ita da shi. Kansa ya jinjinama wanda ya kawota ɗin idanunsa a kanta. Gurin zama ya nuna mata da faɗin, “Ɗiyata bismilla zauna ko?”.
Ajiyar zuciya ta saki dan har cikin ranta ta ɗanji sanyi. Gaishesa tayi da girmamawa zuciyarta na sake samun nutsuwa da shi. Ko ba'a faɗa mataba a yanayin shigarsa da shekarunsa ya isa tabbatar mata shi ɗin mai faɗa aji ne a hukumar.
Ɗan kafeta yay da idanusa na kusan sakan ashirin ko ƙyaftawa bayayi. A take tsigar jikinta ta fara tashi tsoro na sake faɗaɗa a zuciyarta. _Hasbinallahu wa-ni'imar wakil_ ta shiga maimaitawa tare da sunayen ALLAH.
Murmushi ya sakar mata da yin ƙaramar gyaran murya yana ɗauke idanun nasa a kanta. Cikin taushin murya yace, *“Muhibbat Aliyu Hamza ko?”.*
Hibbah ta jinjina masa kanta cikin dakiya da dauriyar hana bayyanar gazawarta tana faɗin, “Eh yallaɓai”.
“Ɗalibar koyon kimiya da fasaha a babbar jami'a ta jihar nan?”.
Nanma kanta ta jinjina masa da faɗin, “Eh yallaɓai”.
“Uhm masha ALLAH. ALLAH yay riƙo da hannayenki ki zama abar alfahin ƙasarki baki ɗaya. Ina matuƙar son naga ƙananun yara musamman ma mata masu himma da ƙwazo akan abinda yay mana ƙaranci irinki”.
A karon farko Hibbah ta saki murmushin jin daɗin yabon data samu da ga garesa tana faɗin, “Thanks you Uncle”.
Murmushi ya sakar mata har haƙoransa na bayyana. “Kinsan miyasa aka kawoki nan?”.
“A'a Uncle”. Ta faɗa cike da marairaicewarta da taso bashi dariya amma sai ya danne. Cikin ƙwarewar aiki ya ce, “Taimakonki muke nema akan masu power bike ɗin jiya da suka kusan tureku, harma sister ɗinku taji ciwo a ƙafarta”.
Kallonsa Hibbah tayi cike da tsarguwa. Fahimtar hakan da yayi ya sashi saurin faɗin, “Muna son gano kosu ɗin ƴaƴan waye? a garin nan, mu kuma kamasu mu hukuntasu. Dan bai kamata ba ace dan kawai suna ƴaƴan masu arziƙi ba su dinga shatar tituna suna zabga gudu tamkar nasu su kaɗai. Zasu iya amfani da wannan damar suyita kashe al'umma saboda ƙarfin ikon iyayensu kuma talaka bazai iya kai ƙara a ƙwatar masa haƙƙinsa ba. Yanzu bayan ALLAH ya taƙaita muku wahala jiya da bamusan halin da kuke ciki ba zuwa yanzu ai ko. Kalla nan kiga”.
Ya ƙare maganar yana ɗaukar remote ɗin da ke gabansa tare da janye idanunsa a kanta ya maidawa ga ƙatuwar tv dake mamake da kusan rabin bangon office ɗin. “Kinsan wannan mutumin?”.
Fuskar dattijo mai cike da ƙasumba a cikin shigar manyan kaya ta bayyana. Kallon kusan minti ɗaya tai masa kafin ta girgiza kanta. “A'a yallaɓai ban sanshiba. Bamma taɓa ganinsa ba”.
Wani ya kuma nunowa da faɗin, “Wannan fa?”.
“Shima haka ban sanshi ba”. Hibbah ta faɗa idonta akan hoton matashin saurayi mai saida rake a Wheelbarrow.
Cigaba yay da latso mata hotuna kala-kala na mabanbanta mutane tana cewa bata sansu ba. Sai wani guda biyu na kusan ƙarshe data taɓa gani an nuna a labarai kwanaki.
“Yallaɓai wannan dai na taɓa ganinsa a tv, dan an taɓa nunasa kwanaki a labarai, kuma hoton yata yawo a social media akan cewar shi ɗin babban ɓarawo ne ɗan yahoo da ya yashe manyan kuɗaɗen wani attajiri. Yayana ma yace suma suna nemansa ruwa a jallo. Kuma nemansa kukeyi halan?”.
Sosai ma kuwa nemansa muke muma tare da waɗancan na farkon dana nuna miki. Amma rashin mai taimaka mana irinki yasa mun gagara hakan. Amma shiɗin wanene yayan naki?”
Kanta tsaye batare da tunanin komai ba ta ce, “Uncle shima ɗan sanda ne”.
“Woow masha ALLAH. Lallai naji daɗin hakan sosai. Kuma zanso ganinsa shima harma nai masa ƙarin girma saboda samun ƙanwa irinki mai ƙwazon da ya kamata ƙasa gaba ɗaya tai alfahari dake”.
Murmushi tayi cike da jin daɗin jin za'a ƙarama Yaya Abubakar ɗinta girma ta sanadinta. Shima ganin ta hau yanda yake buƙata saboda ƙuruciya sai ya ƙara faɗaɗa murmushinsa da faɗin, “Idan har kikai mana wanann taimakon da zan miki bayani akansa yanzun to lallai yayanki zai ƙara zama babban mutum, kema kuma zaki rama jin ciwon da aka saka ƙawarki tayi jiya. Da ga ƙarshe zaki samu ƙyauta mai tsokar gaske”.
Batare da tunanin komaiba ta ce, “Insha ALLAH zan taimakeku Uncle, indai Yaya Abubakar zai ƙara samun girma”.
Cike da jinjina wautarta fara'ar fuskarsa ta sake bayyana. “Yauwa ɗiya ta. Aikin da zaki mana shine gano mana inda masu power bike ɗin jiya suke.”
“Lah Uncle ai nama g.....”
Sai kuma tai shiru tare da dafe bakinta saboda tunowa da gargaɗin Yaya Abubakar na ɗazun akan karta sake ta sanarma kowa.
“Miya faru ki kai shiru ɗiyata?”.
Da sauri ta girgiza masa kanta. “Babu komai Uncle, inason kai musu magana su fara bani wayata nayi magana da Yaya Abubakar”.
Shiru yayi cike da nazarinta, a zuciyarsa. Yace (Yarinya mai wayo). A fili kam ganin ta kafesa da ido yay saurin sakin murmushi. “Okay okay babu damuwa zan musu magana su baki. Amma kafin hakan zaki cika mana alƙawarin mu. Idan ba hakaba kuma zamu cigaba da riƙeki anan, tare da sakawa a kamo mana Mamanki dasu yaya Abubakar ɗin naki mu faɗama duniya cewar sunada alaƙa da wancan hotunan mutanen da muke nema kin amince?”.
A take dukkan fara'ar dake kan fuskar Hibbah ta ɓace ɓat. Shima tuni saɓanin murmushi ya maye gurbin tasa fuskar. Ya kuma tsatstsare ta da idanunsa cike da tsoratarwa. “Yanzun nan zan bada umarnin zuwa a ɗakko min Umminki. Tare da Yayanku Muhammad har wajen aikinsa. Sai Umar da Usman. Aliyu (Ammar) kuwa yanzu haka akwai jami'anmu dake zagaye da shi a makarantarku. Kalla nan”.
Ya ƙare maganar da juya mata lap-top ɗinsa. Wani irin firgici da ruɗani ne suka bayyana a fuskar Muhibbat ganin hotunan Yayunta tare da hotunan ɗazun daya nuna mata na waɗanda ake nema. Kowanne da taƙaitaccen bayanin dangantashi da waɗan can masu laifin. A ƙarshe aka bayyana Ummi matsayin mahaifiyarsu tare da ita mai taimaka musu kasancewarta masaniya akan ilimin sarrafa Computer.
Saurin ɗora hannunta tayi akan baki saboda kukan dake neman kufce mata. Ta shiga girgiza masa kanta a kiɗime. “Please yallaɓai kar kai haka dan ALLAH. Ni ƴan uwana ba ƴan ta'adda bane. Basu taɓa aikata laifin komai ba sai alkairi. Karka zaluncesu ta dalilina....”
“Inhar baki so ganinsu a cikin wani hali sai kiyi mana abinda muka sakaki ki zama sanadin alkairinsu. Bawai ina lallaɓaki bane dan bazamu iya sarrafaki kimana dole ba. Inda naso tursasaki da tun a daren jiya zamu ɗakkoki har gida kiyi mana aikin akan dole.” yay maganar a matuƙar kausashe yana bugar desk ɗinsa.
Ɗan zabura baya Hibbah tai jikinta na rawa. Yayinda shi kuma ya shiga ƙwala kiran sunan jami'in su Nura.
Da sauri Nura ya shigo yana ƙamewa da faɗin, “Yes sir!”.
“Maza a shirya jami'an da zasu fita operation yanzun nan.”
“Okay sir”. Ya sake faɗa da girmamawa yana ficewa.
Miƙewa yay shima yana nuna Hibbah da faɗin, “Oya miƙe”.
“Yallaɓ.....”
Hannu yasa yay zipping bakinsa alamar karta sake cewa komai.
Ɗakin da ke ajiye da na'urori masu ƙwaƙwalwa aka kai Hibbah. Inda suka sami mutane kusan goma sha uku a ciki. Kai tsaye wajen zama aka nuna mata alamar dama ita ake jira. Zama tai tana haɗiyar zuciya. Batason yin aikin saboda gargaɗin Yaya Abubakar. A gefe kuma batason a cutar mata da ahali akan abinda basu ji ba basu gani ba. A wani gefe na zuciyarta kuma nason yi kodan abinda mutanen suka nema yi musu jiya har ga Hafsat da ciwo.
Waya irin ta jami'an tsaro aka ajiye a gabanta. Tare da kunna ƙaton tv irin na office ɗin data baro da shima ke a jikin bango. Hoton yayunta da rahotannin da aka shirya na karya dan tsoratar da ita suka bayyana.
Ta sauke idanunta dake cike da ƙwalla a hankali bisa computer ɗin gabanta.
“Ki nutsu wajen yin aikin da zai ƙuɓutar da ƴan uwanki zama criminals zuwa taurari ta sanadinki, ko kiyi sakacin yin aikin da zai dusashe haskensu da ga taurari zuwa criminals ta sanadinki.”
Mutumin ɗazu ya faɗa cikin tabbatarwa da murya mai kaushi.
Kai kawai ta jinjina masa tana maijin wani ɗaci a zuciyarta da taurin zuciya. Sai da tayi addu'a a cikin zuciyarta kafin ta fara aikin cike da ƙwarewa. Kasancewar ɗazun dama ta binciko a inda suke sai yanzu batasha wahala ba duk da wannan Computer ɗin nada matuƙar tsaro fiye da tasu ta makaranta.
Da wayar gabanta ta dinga amfani wajen yin magana da jami'an da suka fita operation ɗin tana sanar musu hanyoyin da zasu bi har zuwa location ɗin da agogon data jefama masu power bike jiya yake. Hakan shike nufin tabbacin samun su inhar agogon na tare da su basu farga sun yadda ba.......
\★/★\★/★\★/★\★/★\★/★\
Anguwar *_jahje street_*, anguwace mai ƙarancin rashin hayaniyar jama'a kasancewar ta ɗauke da manyan gidaje na masu hannu da shuni. Ko da rana ka shigo wannan anguwa zaka sameta tsit tamkar halittun da ke a cikinta basa numfashi. Akan samu ƙarancin gittawar ababen hawa da na mutane masu tafiya a ƙafa sai dai jefi-jefi. Shima hakan tafi kasancewa a ranakun hutun ƙarshen mako ko hutun ranakun ma'aikata da kan gitta.
Sabo da rashin sakewarsu da juna yasa bazasu iya tantance kansu ba dan rayuwa ake ta babu ruwan wani da wani. Idan kaga magana ta shiga tsakaninsu sai idan ALLAH yasa ka fito maƙwafcinka ma ya fito ai gaisuwar hello hi shikenan kowa ya shige sabgar gabansa.
A cikin gida mai lamba 110 matasan samari ne da shekarunsu zai iya kaiwa ashirin da biyar zuwa da shida, harma mai da bakwai za'a iya samu. Gaba ɗayansu bakwai zaune suke a ƙayataccen falon gidan mai matuƙar girma da ƙawa ga mai kallo. Su dukansu kowa harkar gabansa ya ke yi. Wasu na kallon ƙwallo, wasu na daga gefe suna sarrafa wayoyin hannunsu.
Ɗaya da ga cikinsu ya nutsu wajen sarrafa waya. Sai dai a hakan hira kan shiga a tsakaninsu musam akan kallon ƙwallon da mutum huɗu suka fi maida hankali a kansa.
Wani mahaukacin horn daya nema harmutsa kwaƙwalensu da ga gate ya sakasu miƙewa a rikice gaba ɗayansu suna ambaton *_Master!!_*. Biyu da ga ciki suka shiga tattare ledojin dattin da sukai ciye-ciye tare da gwangwanen maltina da coc.. Ɗaya ya fita a guje domin zuwa ya buɗe masa ƙofar falon da ke rufe da security.
Buɗe ƙofar yayi dai-dai da isowarsa cikin takun ƙasaita da tabbatar da shiɗin fa ya isa. Sanye yake cikin baƙin wando jeans da baƙar t-shirt. Sai dai ya ɗora jacket baka itama a samanta batare da ya ja zip ɗinta ba. Sam ba'a ganin fuskarsa, sakamakon hular jacket ɗin dake har saman kansa, ga norse mask da baƙin google toshe da idanunsa. Ƙafarsa ma sanye take cikin baƙin takalmi.
Cikin zafin nama da ALLAH yay masa yasa hannunsa da ke sanye cikin safar hannu ya matsar da wanda ya buɗe masa ƙofar ya shigo cikin falon.
Hakan ya kara tabbatar musu da babu lafiya, dan kowa bai kalla a cikinsu ba ya nufi wata ƙofa a hargitse.
Kallon juna sukayi cike da tsoro, cike da ƙarfin hali ɗaya da ga cikinsu yace, “Brothers babu lafiya fa”.
“Tabbas babu lafiya Khalid. Akwai abinda ya saka Master a wannan yanayi.....”
Maganar tasa ta kakare a maƙoshi saboda fitowar wanda suke kira Master. Cikin wata irin murya mai amo da nutsuwa ya fara magana da faɗa. “Ina kayan da kuka fita aiki da su jiya?”.
A tare sukai rige-rigen nufar ɗakunan barcinsu. Babu jimawa sai gasu suna dawowa ɗaya bayan ɗaya da kayan a hannu. Na'urar bincike da ke a hannunsa ya shiga kangawa jikin kayan. Akan jakkar Habib ta tabbatar da zarginsa. Ya fisgi bag ɗin da sauri yana zazzage dukkan abubuwan da ke a ciki, sannan ya ɗaura na'urar akan kayan. Saurin daukewa yay ya sake maidawa akan jakar. ƙaramin fuskar agogo mai kama da flower dake manne a jiki ta fara kawo jar danja tana ɗaukewa. Yay saurin fisge agogon da dudu-du girmansa bai wuce girman ficika ba. Numfashi ya fusga da ƙarfi, hakama sauran yaran nasa duk sai da sukai ajiyar zuciya. Dan abinda sukaga ya cire ɗin ya tabbatar musu wani ya kafa musu tarko ne ba tare da sun farga ba.
Batare da yace dasu komai ba ya nufi na'urorin dake acan gefen falon an katangesu da glass na ƙawa daya zamewa falon baki ɗaya ado. Cikin wata na'ura ya saka agogon, bayan kamar sakan biyar ya cire ya fito ya nufi waje. Yana fita suka shiga kakkauda duk wani kaya suna maida shi a salon da zai basu kariya dan da alama yau ta ƙwaɓe.
Baifi mintuna uku da fitarba sai gashi ya dawo. Hanyar ƙofar da ya nufa ya sakasu binsa da sauri suma dan sun kammala kauda dukkan abinda ya kamata su kauda ɗin. A kuma dai-dai lokacin sukejin ƙarar buɗe gate ɗin gidan alamar wanda suka sami nasarar bibiyar tasu sun iso. Sun kumafi ƙyautata zaton ƴan sanda ne abokan *_TAKUN SAAƘAr_* su.............✍
*_Hum, wannan fa shine ana dara ga dare yayi🐒🚶🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_MG's SKINCARE_*
*_Ina manyan Mata, da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau?_*💃🏻
*_To maza kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki_*
*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*💃🏻💃🏻
*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne a gareku💃🏻_*
*_Sai kuma beauty kit gbdy na gyaran jiki, su cream da komai ne acikin shi💃🏻_*
*_Then akwai bridal kit shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*
_Duk zaku tabbatar da hakanne ta hanyar nemansu ku gwada kuma har sai kun bama wasu labari💃🏻😍🥰_.
Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift
_*Sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks, juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_
*___________________________*
*_Chapter Eight_*
...........Wani wawan tsaki ya ja tare da kai hannu kan Wadrobe ɗin dake a jikin bangon ɗakin ya danna wani maɓalli. A take ta zuge kanta, ɓoyayyar ƙofar sirri da ke a jikin bangon ta bayyana.
Cikin sauri suka shiga shigewa mamaki fal ransu, dan ko su da ke tare da shi tsahon shekaru basu taɓa sanin da ƙofar ba. Bama batun ƙofa kawai ba, ko fuskarsa ta ainahi har yanzun basu sani ba. Yanda yake zuwama duniya da mabanbanta fuskoki suma haka yake zuwa musu, duk da kuwa akwai alaƙa tsakaninsa da wasu a cikinsu ta zuminci.
Shi mutum ne mai aiki da matuƙar taka tsan-tsan a kowane ɓangare, shiyyasa yay dogon zangon da har yanzu an kasa cimmasa a duk tarkuna da ake ɗana masa, dan kota ina idanunsa a buɗe suke, hakama kunnuwansa. Sai da duk suka gama fita yana kallon jami'an tsaron da ke shigowa cikin gidan da sanɗa ta cikin tab ɗin dake a hannunsa. “Humm” ya faɗa yana rufe tab ɗin, shima yabi bayan yaran nasa tare da maida ƙofar a yanda take kamar babu.
Koda ya fito bai tankasu ba, sai wasu ƙananun fitilu masu azabar haske daya fiddo a aljihun wandonsa ya shiga kunnasu yana mika musu, A take ko ina ya gauraye da haske har suna iya ganin gabansu. Sam babu ruwa ko datti a ciki, hanyace ɗoɗar da basusan iyakarta ba, domin dama can ba'a yisa dan ruwa ya wuce ba. Sukam dai ɗunbin tsoro da mamakin Master ɗin nasu tuni ya gama kashesu a tsaye. Tun fitowarsu a ɗakin da suka tsinci kansu a cikin doguwar hanyar ruwa komai ya kuma kwance musu game da shi. Sagade sukai suna kallon ikon ALLAH da sake tsorata da al'amarinsa. Lallai sun sake yarda da gaskiyar zantukan mutane da ke kiransa *Hatsabibi shu'umi*.
“Zakuje ne ko zaku tsaya kallo na?”.
Sautin furicinsa ya maido da hankalinsu jikinsu kusan a tare lokaci guda.
Da sauri suka haɗa baki wajen faɗin, “Sorry Master!”.
★★★
Jami'an tsaron da suka iso anguwar bisa jagorancin Hibbah da ke basu haske ta hanyar waya kuwa tun kafin su iso gidan suka ajiye motocinsu can farkon layin suka ƙaraso da ƙafa. Mai-gadi da dama yake zaman jiran tsammani kamar yanda Master yay masa bayani ana yin knocking gate ɗin ya tashi ya buɗe bayan ya ƙara ƙarar redio ɗinsa da yake ji.
Jami'in da ya fara isowa wajen cikin son nuna basaja ya bama mai-gadi hannu yana murmushi. Babu musu shima mai gadin ya bashi hannu sukai musabaha cikin nuna ƙaulanin rashin sani.
“Sai dai gashi ban waye kaba bawan ALLAH. Kuma su alhaji basu sanarmin wani baƙo zaizo nan ba”. Mai-gadi ya faɗa lokacin da yake sakin hannun jami'i da yazo a suffar basaja.
Jami'in da furucin mai-gadi ya ɗan tsaya masa a rai ya ce, “Kana nufin masu gidan basa nan kenan?”.
“Tabbas basa nan mai-gida. Yau kwanansu tara kenan da komawa can ƙasar da suke zaune ai”.
Wani kallon kama rainamin hankali jami'in yay masa, amma sai ya saki murmushi da maida hannayensa baya yanama ƴan uwansa alamar su taho ba tare da yasan mai-gadin na lure da shi ba.
Baki mai-gadi ya buɗe zai sake magana sauran jami'an suka iso suma. Bindiga wanda ya fara zuwa ya nuna masa tare da turasa cikin gidan duk suma suka shishshigo. Duk rarrabuwa sukai a kowace kusurwa ta gidan suka fara shiga da sanɗa, wanda ya fara zuwan kuma na tare da mai-gadi da zuciyarsa ke cike da tsoron kar dai ƙaryarsu ta ƙare yau, dan shi duk tunaninsa su Master na'a cikin gidan suma tunda bai sanar masa shirinsa ba bayan aikin da zaiyi kawai. Duk da ya yarda da hatsabibancin uban gidan nasu amma dolene akwai ɓacin rana. Da alama kuma idan har ta ƙwaɓe yau da shi zata fara ruftawa. To amma insha ALLAH zaiyi ƙoƙarin ganin ya bi duk abinda Master ya faɗa masa yanda ya kamata.
Sai da jami'in nan ya tabbatar abokan aikinsa sun gama zagaye gidan sannan ya tasa ƙeyar mai-gadi shima suka nufi ciki. Ƙofar shiga da suka fahimci a rufe take suka bashi umarnin buɗewa. Amma sai ya nuna musu sam bai san password ɗin ba shi.
Jikinsa jami'in ya fara laluba, ya ciro waya nokia da tasha ɗaurin ƙyauraye da salataf. Wayar ya jujjuya a hannunsa yana ƙare mata kallo fuska a yatsine, kafin ya maida dubansa garesa yana sake gyara zaman bindigar da ya ɗora masa a saman kai.
“Nasan dai kanada number ɗin mai-gidan, maza ka kirashi yanzun nan ya faɗa maka password ɗin komu ɓalla ƙofar a yanda muka gadama.”
Babu wani nuna damuwa ko ɗar mai-gadi ya amsa wayar ya shiga laluben Number. Dailing yayi kansa tsaye, sai dai harta tsinke ba'a ɗaga ba. Ya sake kira a karo na biyu, sai da taje gab da tsinkewa aka ɗaga cikin muryar isa. Cikin girmamawa mai-gadi yay gaisuwa, sannan ya ɗara da bayanin cewar jami'an tsaro ne sukazo gidan suna buƙatar password na ƙofa wai zasuyi bincike, bai san mi suke nema ba. Carab jami'in ya amshe wayar yasa a kunnensa bayan ya kalla no. Ɗin da mai-gadin ya kira ya tabbatar da ta ƙetare ce.
“Jami'an tsaro kuma? Rabi'u!. To mu miya haɗa gidanmu da jami'an tsaro?”.
“Bincikenmu ne ya nuna mana wannan gidan na masu laifine Alhaji. Bazamu tabbatar da ba haka bane ba sai mun shiga mun duba kuma. Dan haka muna jiran mabuɗin sirrin ƙofar da ga gareka kawai, kafin muyi magana ta gaba da kai idan har ya kama”.
“Okay to babu damuwa yallaɓai”. Daga can aka faɗa tare da zayyano masa password ɗin.
A sakawa ɗaya kuwa ƙofar ta buɗe. kusan rabi a cikinsu suka shiga ciki akabar wasu a waje. Akan idon mai-gadi suka shiga hargitsa gidan tako ina. Sai dai abin mamaki babu wani alamun abun rashin gaskiya da sukayi gamo da shi. Cikin glass ɗin nan da computers ke ciki ɗazun yanzu babu shi, sai wasu ƙayatattun flowers masu ɗaukar hankali da ƙamshinsu ya cika falon.
“Tabbas yarinyar nan ƙarya take mana. Ko tana ɗaya da ga cikinsu ne yawo da hankalinmu kawai take son yi”. Ɗaya daga cikin jami'an ya faɗa a hasale.
“Sam banajin hakan a raina, akwai dai wani ɓoyayyen abunda bamu sani ba. Karku manta shiɗin mutum ne mai matuƙar wayo da dabaru kala-kala. Tabbas ya fahimci ana bibiyarsa ne ya bada ƙafa. Kokuma yayi amfani da wanann location ɗin domin sakamu zargi.”
“Nima zuciyata tafi rayamin hakan yallaɓai”. Wani ma ya sake faɗa cikin jin zafi.
“Karku samu damuwa. ai rana 99 da tara na ɓarawo, ɗaya tak na mai kaya. Inhar kere na yawo, zabo na yawo watarana dole a gamu. Tunda yace shi hatsabibi ne ya samu dai-dai da shi kuwa. Zamu bar wasu a gidan nan har sai mun tabbatar da gaskiyar babu wani abun zargi a cikinsa”.
Duk sun amsa da girmamawa. Shi dai mai-gadi kallonsu kawai yake yana kwasar dariya a zuciyarsa. Koda suka fito harabar gidan sun tsara wanɗanda za'a bari, wanda zasu koma kuma suka nufi hanyar barin gidan. Karaf idon ɗaya ya sauka akan bag dake rataye acan ƙarshen gate ɗin gidan ta waje. Saurin zuwa yay ya ɗakko yana nuna musu. Commander ɗin operation ɗin nasu ya amsa yana zazzage jakkar cikin kulawa gudun kar a saka musu bom a ciki.
Agogon Hibbah ne ya fara faɗowa tare da takarda mai ɗauke da sunansa akoda yaushe da facemark. Sai ɗan gajeren rubutu a bayan takardar.
*_“Bibiyata na nufin ƙare rayuwarku a wahala. Inhar bani naso kusan niɗin wanene ba, bazaku taɓa ganoni da kanku ba har abada insha ALLAHU rabbi. Dan haka ku daina azabtar da kanku wajen bibiyata komai yana da lokacinsa”_*
_Master👌🏼_
Wani wawan tsaki jami'in daya gama karanta takardar yaja. Ya cije leɓensa na ƙasa da ƙarfi, cikin alwashi yace, “Ni kuma na maka alƙawarin da wannan hannun nawa zan kamaka, sannan na maka horo mai tsananin gaske wanda sai ka gwammaci mutuwarka da rayuwarka shaiɗani”.
Suma sauran zukatansu na matukar ƙuna suka ɗauki nasu alwashin.....
___________★★★__________
Yaya Abubakar ya shiga tashin hankali matuƙa lokacin da yake isowa cikin makarantar su Hibbah yaji abinda ya faru a bakin Ammar da Zahidah. Tare da samun ƙarin bayani a bakunan wasu ɗaliban.
Da taimakon wani malamin su Hibbah ya shiga Computers room nasu yay bincike a computer ɗin da ta gudanar da binciken. Sai dai kuma ta saka security, shiga yay gwada passwords kala-kala yayi wanda yasan tana amfani da su a gida ko zata iya amfani da su. Sai dai sam babu wanda ya buɗe. Cike da ɓacin rai ya mike yana bugar desk ɗin cikin ƙunar zuciya. Lalubo wayarsa da ke ring a aljihu yayi. Yaya Muhammad ne, ɗagawa yay sukai yar magana ya yanke. Wani abokinsa ya kira kasancewar shi jami'i ne a hukumar ƴan sandan ta farin kaya. Ya tabbatar shine kawai zai iya bincika masa idan Hibbah na hukumar tasu. Bayan ya ɗaga ko gaisuwar kirki ba suyi ba ya sanar masa bukatarsa. A take jami'in ya tabbatar masa lallai Hibbah na'a headquarters ɗin tasu dan yaji ƙishin-ƙishin ɗin zancen yanzu a bakin wani ogansu cewar akwai yarinya da ke da alƙa da case ɗin na jiya.
Yanke wayar kawai yayi batare da sun ƙarasa maganar tasu ba, ya kira Yaya Muhammad yana sanar masa a inda zasu haɗu yanzun nan......
__________________________
Master da yaransa kam bayan ƴar tafiyar da sukayi ta cikin hanyar kwata sai gasu sun ɓilla ta wani ƙaramin gida. Gidane ginanne mai ƙyau na dai-dai mai matsakaicin ƙarfi. Yanda yake bin ko ina cike da nazari haka suma suke kallon gidan. Bayan kamar mintuna biyu ya gyara tsaiwarsa sosai yana fuskantarsu. Binsu ya gamayi da kallo ɗaya bayan ɗaya batare da su suna kallon ko ƙwayar idonsa ba. Tabbas sun jima suna kwaɗayin ganin fuskarsa, amma sam yaƙi basu damar hakan koda da kuskure..
_Gyaran muryar da yay ne ya katse tunaninsu. Ya sake gyara tsaiwarsa yana tura hannayensa duka cikin aljihun wandonsa. Muryarsa a kausashe da tabbatar musu da fushinsa ya fara magana cike da nutsuwa da ƙasaitar sa,
“Yau mun tsallake rijiya da baya, amma wataran saboda sakacinku tabbas bazamu tsallake ba. A kullum ina faɗa muku duk sanda zakuyi aiki, ku ringa yinsa da *_ƘWAƘWALWA DA ZUCIYA_* a haɗe. Dan duk lokacin da ɗan adam yay amfani da ƙwaƙwalwa kawai wajenin aikata muhimman abubuwa to ya tabbatar zai kasance mai yawan shiga ruɗani da tafiya yana dawowa baya saboda wani ya fika kaifin basirar. Idan ko da zuciya kaɗai ka dogara wajen ginin muhimman abubuwa, kasani nasararka ragaggiyace saboda zuciya abinda ke mata daɗi kawai take ayyanawa da buƙatar ya kasance mata. Bai kuma zama lallai ka kasance cikin jin daɗi da farin ciki ba a kowanne daƙiƙa na rayuwarka. Dan wani lokacin hanyar jin daɗi wahala ce, wata hanyar wahalar kuma jin daɗi ce. Wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe, idan ba hakaba ni ɗin nan da kaina zan bada ƙafar da za'a kama duk wanda ya cigaba da sakaci a cikinku. Ba kuma zan taɓa kuɓutar da shi ba har sai ya jigata yasan muhimmancin bama kasan kariyar yin aiki cikin tsantseni. Duk wanda ya haremu ya sokemu akan dai-dai kuma na jinjinama ƙwaƙwalwarsa da kaifin tunani. Sai dai na baku awa goma kacal ku ganomin koshi ɗin ɗan gidan uban wanene. Dan sai ya amshi hukunci dai-dai da iyawarsa!”_.
“Insha ALLAHU zamu kiyaye sir. Muna kuma neman afuwa daga gareka”. Suka faɗa a tare cike da girmamawa a garesa. Yayinda Habib da yasan komai ya farune ta sanadinsa yay ƙasa da kansa bayan ya sake matsowa gabansa. “Ka gafarceni Master, dan wannan tabbas sakaci na ne. Amma wlhy sam bansan ta yaya akai hakan ta kasance ba. Sannan koda muka dawo kuma ban fargaba.”
Hannu kawai ya ɗaga masa batare da yayi magana ba. Sai kuma ya nufi ƙofar fita da ga gidan baki ɗaya. Da kallo duk suka bisa har ya isa ƙofar ya buɗe sannan ya juyo yana kallonsu shima.
“Zan sake maimaita muku awa goma kacal, na samu cikakken labarin akan ko shiɗin wanene!......” Daga haka ya ida ficewa baki ɗaya.
A tare suka sauke ajiyar zuciya. Sun tabbatar a salon da yay maganar babu wasa a cikinta, dama can kuma ba wasan ya ke musu ba ballema su ɗauketa wasa. Suma kuma har cikin ransu suna bukatar sanin wanene wanda yay musu wannan tarkon da suka tsallake rijiya da baya?..........✍
*_Gadai jami'an tsaro basu sami nasarar aikin Hibbah ba, ga kuma Master ya bada awanni goma domin binciko wanda ya haresu, hibbah dai kuma itace ta kai harin da babu niyyar dalilin da su suke kallo. To yaya zata kasance kenan tsakanin Muhibbat Aliyu Hamza da Jami'an ƴan sanda da Master kenan?🤔. TAKUN SAAƘA wasa farin girki👎🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_MG's SKINCARE_*
*_Ina manyan Mata, da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau?_*💃🏻
*_To maza kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki_*
*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*💃🏻💃🏻
*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne a gareku💃🏻_*
*_Sai kuma beauty kit gbdy na gyaran jiki, su cream da komai ne acikin shi💃🏻_*
*_Then akwai bridal kit shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*
_Duk zaku tabbatar da hakanne ta hanyar nemansu ku gwada kuma har sai kun bama wasu labari💃🏻😍🥰_.
Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift
_*Sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks, juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_
____________________
*_Chapter Nine_*
.............Tunda jami'an suka dawo da labarin rashin nasara zukatan manyansu yay matuƙar ƙunci. Awanni ƙalilan suka rage musu da ga umarnin gidan gwamnati. Cikarsu babu Master a hannunsu kuwa yana nufin sun gaza a idanun al'ummar jiharsu da ƙasa baki ɗaya. Hakama ga gwamna da muƙarrabansa.
A gefe ga gidajen jaridu da duk wata kafar yaɗa labarai sun baza kunnuwa da idanun domin ganin yanda awanni ashirin da huɗu zasu cika tare da wannan ɓarawo a hannunsu ko saɓanin hakan.
Waɗan nan tunane-tunanen nasu yasa su shirya zaman meeting na gaggawa.
Dukkan wani babba mai alhakin faɗa aji ya hallara a ɗakin da meeting ɗin zai gudana. Sai wanda ya jagoranci jami'an da suka dawo yanzun nan da shirin kamo Master da yaransa..
Kowa ka kalla a ɗakin meeting ɗin kasan yaci ya ƙoshi, dan babu wasu kamannin wahala tare da su. Da'ace ƙasace mai ƙyaƙyƙyawan tsari sun cancanci yin ritaya duk su koma gefe a kawo matasa masu jini a jika da basirarsu ke aiki da kaifin ƙwaƙwalwa a zuba a madadinsu. Su kuma su zama dattijai masu bada shawara wa ƙasa ta bayan fage matsayinsu na iyayen ƙasa. Sai dai sam a wannan ƙasar tamu ba haka bane ba. Anyi sakacin barin matasan da ke da basirar zuwa da salonsu na ƙuruciya wajen kawoma ƙasa cigaba zama ƴan ta'adda, dukkan tarin basirarnan tasu da ƙuruciya ta koma aiki ne ƙarƙashin aikata laifuka. Iyayenmu da gwagwarmayar rayuwa da raunin shekaru sukaima yawa sun zama sune masu riƙe da madafun iko wajen zartarwa da hukuntarwa. A duk lokacin da ƙasa tai sakacin rashin amfani da basirar matasa da ƙuruciyarsu wajen aikata alkairi, to lallai shaiɗanu zasuyi amfani da basira da ƙuruciyar waɗanan matasan wajen kafa tantin ta'addancin da zai ruguza ƙasa.
A ƙasarmu ta gado iyayenmu sune ƴan siyasarmu, sune masu riƙe da madafun iko na mulkin gargajiya da na siyasa, sune riƙe da hukumomin ladabtar da masu laifi, sune riƙe da manyan kuɗaɗe na kasuwanci, sune riƙe da makarantun da ake bamu ilimi, sune.. Sune... Sune komai.
Babu wata hanya ko ƙofa da suka barma matasan wajen nuna bajintarsu da ƙwazon da ALLAH ya haliccesu da shi. Kallonmu suke masu yawan wauta, masu shashanci, masu ƙuruciya, masu rashin kunya da rashin ganin girman na gaba da su. Masu... Masu... Ta ko ina. Amfaninmu kawai mu cigaba da zama a ƙasa har sai lokacinmu yayi. To yaushene lokacin namu zaiyi? Shin sai muma mun kai irin shekarunsu mu danne na ƙasa da mu kenan?. indai har a haka za'a cigaba da tafiya lallai da alamar ƙasar tamu bazata taɓa zama mai sauyawa ba ko samun ci gaba. Domin anyi sakacin ajiye lokaci an ɗauki rauni.
Shi kuma lokaci a duk sanda aka gaza amfani da shi ta hanyar da ya dace wucewa yakeyi yabar mai shi da cizon yatsa da dana sani. A lokacin kuma daka buƙaci gyarawa sai ya kufce maka dan kayi sakaci wajen sarrafashi a sanda ya dace. To ya kamata manyan ƙasarmu su fahimci MATASANMU sune LOKACINMU. Cigaba da sakacin ƙinyin amfani da baiwarsu akan lokaci na nufin baragurbi amsarsu su su amfana da wannan damar wajen maidasu masu ruguza ƙasar da ku kuke ganin kunata ginawa. Sanda zakuyi ƙoƙarin son tarosu kuma sunyi nisan da bazasuji kiranku ba sam.
Bawai munason fiddo da gazawarku bane ma duniya ko goyon bayan laifukan matasa. Muna buƙatar ku duba ku kuma fahimci sai da matasa ƙasa ke iya samun ci gaba. Basu dama kuma shike nufin daƙile dama a hannun masu ɗorasu bisa bigiren ta'addanci. Kun cancanci kuma muyi alfahari da ku, dan kun bamu gudunmawa ta musamman bayan kasancewarku iyaye a garemu.
Bayan ƙarin bayani da suka samu a bakin jami'in da suka fita bibiyar Master zukatansu sun ƙara ɗaci. Ɗakin yayi shiru kowa na nazari da tunani a cikin zuciyarsa. Ɗaya da ga cikinsu da zuciyarsa ke raya masa wani abu ya nema izinin yin magana.
“Bismillah, an baka dama. Ya kamata kowa ya faɗi abinda ke bakinsa ko hakan zai bamu wani haske da ga kullewar da kawunanmu sukayi.” Ogan nasu ya faɗa cike da taraddadi.
Kansa ya jinjina da faɗin, “Thanks you sir. Dama wani tunanine yakemin yawo a zuciya game da ita wannan yarinyar datai mana aikin. Shin baƙwa tunanin shine ya tsara duk hakan kasancewarsa shu'umin mutum kuwa?. Al'amarin da matuƙar mamaki ta yanda ta bibiyesa cikin sauƙi. Idan har dama ba shirinsa bane ta yaya akai ta jefa masa abunda ta samu damar bibiyarsa?”.
Da sauri wanda ke a kusa da shi ya ashe da faɗin, “Ashe bani kaɗai nake wannan tunanin ba. Tabbas da alamar akwai lauje cikin naɗi game da wannan al'amarin. Nasan za'a iya samun mai ƙwazo da kaifin basirarta, amma yanda al'amarin ya faru da ƙanƙantar shekarunta sai nake ganin kawai shiri ne na musamman akai. Dan bana hangen tana da wani ƙyaƙyƙyawan tunanin da har zuciyarta zata bata damar aikata hakan. Banda shirme da shiririta mi yaran yanzun suka iya? musamman ma ita da ta kasance MACE”. Ya ƙare maganar cikin jin zafi sosai.
Wanda ya gana da Hibbah dake ta faman buga pen a kan laɓɓansa yana kallonsu da nazarin maganganunsu yay murmushi. “Wannan tunanin namu na ganin yaranmu bazasu iya komai ba wajen taka rawar gani ke maida ƙasarmu da mu baya a koda yaushe. Da hakan kuma suke samun damar yin amfani da basirar tasu a gurɓatacciyar hanya. Tabbas ita ɗin MACE ce kuma ƙaramar yarinya, amma kallonta da rauni na *ɗiya mace* shine babban kuskuren mu. Banace inada tabbacin bata da alaƙa da shi ba, dan shi shu'umin mutum ne hatsabibi da zai iya aikata duk ma abinda bamuyi tunaninsa ba ko munyi. Sai dai banason mu kasa fahimtar cewar itama duk da kasancewar tata MACE zata iya taka wata rawar gani a harkar tsaro da duk wani sha'ani na rayuwa duk da raunin da ALLAH yay mata. Shawarata anan itace mizai hana mu jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya”.
Sake maida hankalinsu sukai garesa domin sonjin ƙarshen zancen.
Ya gyara abin maganar gabansa yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya. “Ma'anar mu jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya shine muyi amfani da wannan yarinyar ta hanyar riƙeta a jikinmu ta zame mana ma'aikaciyar sirri. Ta wannan hanyar zamu amfanu da alkairinta da kaifin basirarta. Mu kuma saka mata ido wajen gano shin akwai alaƙar da zuciyarmu take zargin tsakaninta da shi ko babu?”.
“Yes! Wannan shawarar taka tayi matuƙa *A.G*”. Ogansu ya faɗa yana tafa masa. Hakanne yasa suma sauran tafa masa duk da wasunsu batai musu ba sam. Dansu babu abinda zukatansu ke ayyana musu sai ganin babu abinda Hibbah zata iya matsayinta na ɗiya MACE mai kuma ƙarancin shekaru.
Sun cigaba da tattaunawa har zuwa wani lokaci, kafin ogan nasu ya bada damar shigo da Hibbah.
Hibbah da damuwar ahalinta kecin ranta ta shigo fuskarta a cinkushe babu ko ɗigon walwala. Babu abinda zuciyarta tafi bukata a yanzu kamar tozali da Ummi da yayunta dan tabbatar da babu abinda ya faru da su. Zama tai a kujerar da aka nuna mata bayan ta gaishesu ranta fal jin haushinsu, musamman mutumin ɗazun da tun shigowarta da shi ta fara haɗa ido yana mata murmushi.
Bayan sun gama nazartarta da ƙare mata kallo ogan nasu yay gyaran muryar da ta saka Hibbah ɗago manyan idanun ta kallesa. Ganin yanda ya kafeta da nasane ya sata sake maida kanta ta duƙar tana wasa da yatsun hannunta.
“Muhibbat Aliyu Hamza!”.
Ya kirayi sunanta murya babu alamar wasa. Hakanne ya saka gabanta faɗuwa, ta sake ɗagowa tana amsa masa da rawar murya. “Na'am yallaɓai”.
“Miye alaƙarki da Master!?”.
“Master kuma yallaɓai? Ni ban sanshi ba”.
“Kin tabbatar?”.
Kanta ta jinjina masa.
“Taya za'ai mu yarda baki da alaƙa da shi?. Bayan tsahon shekaru biyu kenan kowace hukuma ta jami'an tsaro farautarsa suke, amma sun gaza koda ganin farcen yatsansa. Sai gashi ke a cikin kwana ɗaya rak kin haresa akan dai-dai?”.
“Ni wlhy yallaɓai bansanshi ba, bakuma ni da wata alaƙa da shi ko sanin wanene shi. Na aikata duk abinda kukaga nayi ne saboda wasa da rayukan mutane da sukeyi ta hanyar power rider amma badan wani dalili ba”.
“Okay, mu ɗauka hakanne kamar yanda kika faɗa ɗin. Yanzu wane tunani kikeyi game da makomar ahalinki?”.
Saurin ɗagowa tai tana kallonsa idanunta cike da ƙwalla. Muryarta na rawa tace, “Amma yallaɓai naga na muku aikin da kuka buƙata dan na tabbata kun kamasa. Kuma kun tabbatar min hakan shine fansar ahalina ai”.
“Eh tabbas haka muka faɗa, sai dai kuma ba'a samu nasara ba kamar yanda mukai tunanin za'a samu. Rashin samun nasarar kuma na nufin shigar ahalinki a haɗari ta fuska biyu. Na farko mu jami'an tsaro ba zamu barsu ba har sai wancan hatsabibin yazo hannunmu. Hakan shine zai wankeki a garemu mu tabbatar baki da alaƙa da shi, ahalinki kuma su kuɓuta. Na biyu dole ne mu baki kariya yanzun dan tabbas zaki zama abin farautarsa kema dan bazai barki ba tunda kin karya masa tarihi. Dolene kowane motsinki dana ahalinki su kasance a tare damu. Idan kin amince ki cike wannan. Kokuma kiyi tafiyarki amma babu ruwanmu da abinda zai samu ahalinki. Zakuma mu fitar da bayanan sune ke aikata laifukan da muka nuna miki ɗazun da mabanbanta fuskoki. Kinga za'a kamasu a kaisu kotu, da ga ƙarshe a yanke musu hukuncin kisa bayan duniya ta sansu matsayin ƴan ta'adda”
Sosai tashin hankali ya bayyana a fuskar Hibbah. Idanunta suka ciko da hawaye ta shiga girgiza musu kai laɓɓanta na rawa. “Dan ALLAH yallaɓai karkuyimin haka. Wlhy bani da alaƙa da mutumin nan sam, iya gaskiyata na sanar muku.”
“Ta hanyar shigowa kiyi aikin sirri da mu ne kawai zai tabbatar mana da hakan, ahalinki kuma su kuɓuta da ga garesa da mu kammu. Gashi ki cike waɗan nan takardun idan har kin amince”.
Da ƙarfi Hibbah ta rumtse idanunta. Wani irin zafi da ɗaci na sauka mata cikin zuciya. Karan farko na rayuwarta da taji tsiwa batai mata rana ba. Tanajin tsana mai yawan gaske akan mutumin da batasan wanene shi ba. Yayinda gefe na zuciyar tata ke jin haushin waɗan nan jami'ai da ke son yin amfani da damar da ALLAH ya basu ta hanyar amfani da ita. Wani gefen kuma na haske mata ahalinta cikin bala'i mai muni da idan har ta zama sanadin shigarsu cikinsa har gaban abada bazata taɓa yafema kanta ba. A take wani irin kangarewa da bushewar zuciya suka saukar mata. Batare da yin wani dogon nazari ba wautar ƙuruciya ta fisgeta da zuciya wajen ɗaukar pen ta hau cike takardun da ɓarin jiki, batare data duba mi suka ƙunsa ba..
Fusatar tata ta basu matuƙar mamaki da al'ajabi. Sai dai zukatansu na ayyana musu tanayin komai ne domin ahalinta. Dan fahimtar sune rauninta ya sakasu yin amfani da su wajen tursasata. Aiko sunci nasara, dan ta cike takardun kamar yanda suka buƙata. Ta kuma saka hannu bisa takardar contract ɗin zatai musu aikin sirri har sai sun kama Master. Su kuma bazasu saki wancan bayanan ƙaryar da suka shirya ba domin mata ɗaurin talala saboda ƙarancin shekarunta.
Sun mata bayanai sosai da zata iya fahimta. Tare da bata date ɗin da zata fara amsar horo na musamman a ɓoye. Da ga ƙarshe sukai mata dogon gargaɗi akan riƙe dukkan abinda suka tattauna matsayin sirri. Dan inhar ta fitar tamkar ta bayyana ƴan uwanta ma duniya ne matsayin ƴan ta'adda. Daga haka suka sallameta.
Fitowar Hibbah da aka haɗa da jami'ai biyu zasu mata rakkiya zuwa gida yayi dai-dai da isowar Yaya Abubakar da Yaya Muhammad station ɗin. Tana ƙyalla ido a kansu ta kwasa da gudu garesu. Jikin Yaya Abubakar dake gaba ta faɗa tare da fashewa da kuka.
Shima rungumeta yay yana mai rintse idanunsa da suka kaɗa sukai jajur. Yaya Muhammad ya ƙaraso garesu da sassarfa shima. Dafa kanta da yayine ya sata barin jikin Yaya Abubakar ta rungumeshi shima. Cikin son danne nasa ɓacin ran ya saki murmushi yana ɗagota da shafa kanta. Hannu yasa ya shiga share mata hawaye. “Kukan ya isa haka nan, ba gamu tare da ke ba”. Ya ƙare maganar da sake sakar mata murmushi mai kwantar da hankali.
Yaya Abubakar da shima ke ƙoƙarin ganin ya shanye tasa da muwar ya ce, “Bara naje zanyi magana da su”.
Da sauri Hibbah ta riƙo hannunsa tana girgiza kanta. Cikin sanyin da basu santa da shi ba ta ce, “Yaya karka je. Ka barsu kawai babu abinda sukai min”.
“Karki damu, ba wani abu bane yanzu zan fito”. Yay maganar da zare hannunsa cikin nata yana shafa kanta. Kama hannunta Yaya Muhammad yay shima ya buɗe mota ya sakata, tare da ɗaukar goran ruwa ya miƙa mata. “Sha ruwa ki wanke fuskarki ina zuwa”.
Hibbah na ƙoƙarin dakatar da shi bai jira cewarta ba ya nufi cikin station ɗin shima. Jitai kamar ta fasa ihu, dan gani take kamar shigar tasu na nufi jami'an zasu riƙesu su sanarma duniyar ƴan ta'adda ɗinne su.
Ganin an shafe kusan mintuna a shirin tai yunƙurin bin bayansu, sai dai tana buɗe motar suna fitowa kowannensu ransa a ɓace. Ta sauke ajiyar zuciya da yin sagade tai tana kallonsu har suka ƙaraso. Yaya Muhammad ya sake kama hannunta ya sata a motar sannan ya zagaya ya shiga shima. Yayinda Yaya Abubakar ya zauna mazaunin driver.
Suna fara tafiya kiran Ammar ya shigo wayar Yaya Muhammad. Kamar bazai ɗaga ba sai kuma ya ɗaga ɗin. Da ga can Ammar ya fara magana cikin ɗacin murya. “Yaya kazo gida dan ALLAH akwai matsala. Hajiya mama da Abba na nan sun taru akan Ummi harda Junaid. Nayi magana kuma ta dakatar dani. Wlhy zanma Haƙilu (Abba) dukan mutuwa sai dai Ummi ta tsinemin. Har wannan shegiyar tsohuwar ba raga mata zanba dan mahaifina ta haifa ba ni ba.”
“Ammar!!”
Yaya Muhammad ya kirayi sunansa a tsawace jin zai yanke kiran shima jikinsa na matuƙar rawar ɓacin rai.
Tuni Ammar ya riga ya katse kiran baima jisa ba. Yaya Abubakar da duk yaji komai ya ƙara ƙarfin gudun motar, cikin ƙanƙanin lokaci sai gasu a ƙofar gidan. Tun a waje yay fakin, gaba ɗayansu suka fita da sauri zuwa ciki. Dan tun da ga waje suna jiyo kururuwa da ihun Hajiya Mama da Momy.
A harmutse suka iske gidan. Ammar da Junaid na kwasar uban dambe. Sai dai duk da kasancewar Junaid yaya ga Ammar hakan bai hana Ammar hayewa saman ruwan cikinsa yana duka ba tamkar ALLAH ya aikosa. Mahaifiyar Ammar ɗin da suke kira Momy taje ceton ɗanta Ammar ya bata mahangurɓa a muƙamuƙi. Tuni ta koma gefe jikinta na matuƙar rawa.
Abba da hajiya mama kuwa tuni suna a wani lungu maƙale dan su ne Ammar ya fara fafara Junaid ɗin ya maresa. Shine faɗan ya juye a tsakaninsu. Da ga cikin lungun Hajiya Mama keta fama kwaɗa ihu da kururuwar Ammar zai kashe mata jika. Yayinda Abba ke a rikice ga tsoro, yana son zuwa ɗakko waya ya kira ƴan sanda yana tsoron fita Ammar da ya juye musu kamar wani mayunwacin zaki ya gansa ya dawo kansa.
Ummi ce kawai akan Ammar tana ƙoƙarin janyesa tana kuka amma ta kasa, dan gaba ɗaya ya juye mata tamkar ba Ammar ɗinta ba. Ya koma ainahin sunansa na ALIYU ZAKI.
Kuka Hibba ta fashe da shi ganin yanda Yaya Ammar kema Junaid dukan mutuwa. Sai jini ke fita ta hancinsa da baki amma yaƙi sakinsa. Da ƙyar Yaya Muhammad da Yaya Abubakar suka iya haɗuwa wajen ɗagasa da ga kan Junaid ɗin. A hakanma sai famar turjewa yake yana nuna Junaid cikin gargaɗi.
“Duk iskanci da kukejin kun iya da rashin mutunci muma mun iyasa. Ba tsoronku bane yasa muke barinku kuna taka mana mahaifiya yanda kuka gadama. Son yin biyayya a gareta da ga taka mana birkin da take na barinku kawai ke dakatar damu. Amma idan har kun isa wani ya sake nuna nata ɗan yatsa a gidan nan ya gani in ban karya shi ba na tauna ƙashin. Wlhy hatta waccan annamimiyar tsohuwar bazan bari ba, sai na ida ƙille ƙafafun nata ta koma gurguwa ta gaske.......”
Kuka sosai Ummi keyi tana kiran sunan Ammar amma yaƙi yin shiru. Su Yaya Muhammad suka turashi sashen nasu da ƙyar suma rayukansu duk a jagule.
A dai-dai wannan lokacin ɗaya da ga cikin ƴammatan gidan ta dawo. Horn tayi mai ƙarfi kamar yanda suka saba. Da sauri mai-gadi dake maƙale yana kallon duk abinda ke faruwa da ga windown ɗakinsa shima ya fito domin buɗe mata gate ɗin. Sai dai shima har cikin ransa yaji matuƙar daɗin dukan nan da Ammar yayma Junaid. Dan duk wani cin zarfi da akema mahaifiyar su Ammar ɗin a gidan akan idonsu ne tun da ƙuruciya.
A guje Ameera ta danno motarta cikin gidan kamar yanda ta saba. Sai dai hango su Abba akan Junaid da ke kwance kamar ya mutu ya sata saurin taka birki tamkar ba'a cikin gida ta ke ba. Fitowa tai da sauri. Ta zaro idanu sosai cikin ƙaraji na rashin tarbiyya take tambayar miya samu Junaid ɗin?.
Abba yay saurin ɗago Junaid ɗin da numfashinsa ke fita da ƙyar yana faɗin, “Kinga maza buɗe mana motarki mu kaisa asibiti shine mafi muhimmanci yanzu. Sauran bayani ƙyaji da ga baya dan anzo gabar da yaƙin duniya na uku zai fara tashi a gidan nan.”
Zata ƙara magana Hajiya mama ta katseta a tsawace. Baki ta murguɗa mata da yin fari da idanu sannan ta nufi motar tata Abba da mai-gadi biye da ita ɗauke da Junaid da gaba ɗaya jini yayma fuskarsa faca-faca...........✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_Ina miƙa sakon ta'aziyya ga ɗaukacin musulmi musamman hausawa na rashin uba kuma jigo, Haziƙi, gwarzo, abin alfaharinmu Sheikh Dr Ahmad bamba. Ya rabbi ka gafarta masa. Ka yafe masa kurakuransa da iyayenmu baki ɗaya. Munyi rashi irin wanda cike gurbinsa abune mai matuƙar wahala a duniyar musulinci. ALLAH ka yafema wannan jarumin dattijan ƙwarai😭🙏🏻_*
__________________________
*_MG's SKINCARE_*
*_Ina manyan Mata, da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau?_*💃🏻
*_To maza kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki_*
*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*💃🏻💃🏻
*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne a gareku💃🏻_*
*_Sai kuma beauty kit gbdy na gyaran jiki, su cream da komai ne acikin shi💃🏻_*
*_Then akwai bridal kit shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*
_Duk zaku tabbatar da hakanne ta hanyar nemansu ku gwada kuma har sai kun bama wasu labari💃🏻😍🥰_.
Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift
_*Sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks, juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_
________________________
*_Chapter Ten_*
...........Ummi na shigowa falon ta wankama Ammar mari. Lokaci guda falon ya ɗauki tsitt. Hibbah ta zazzaro manyan idanunta waje, jikinta na rawa, dan abinda bai taɓa faruwa ba a tsawon sanin da taima Umminsu. Duk iya ɓacin ran da zata nuna idan sukai mata laifi iyakarta da su faɗa da nasiha tun basu kai haka ba.
Ba Hibbah kawai ba, hatta Yaya Muhammad da Yaya Abubakar sai da wutar kansu ta ɗauke. Hakama Yaya Umar da Yaya Usman da ke ƙoƙarin shigowa falon saboda kiransu da mai-gadi yayi ya sanar musu abinda ke faruwa tun sanda Ammar ke jibgar Junaid. Sai dai suna shigowa gidan motar Ameera na fita zuwa asibiti kai Junaid. Tare kuma suka tafi gaba ɗaya gidan, har da Hajiya mama dake fama da ƙafarta.
Ƙananun duka Ummi ta cigaba da kaima Ammar, hawaye masu zafi suna gangaro mata a kumatu. Ammar dake tsaye ƙiƙam tun marinsa da tai kallonta kawai yakeyi shima hawayen na sakko masa na tausayinta. Yayinda wani murmushi mai ɗaci ke bayyana saman fuskarsa. Ummi ta jawosa ta rungume jikinta tana magana cikin rawar murya, “Miyasa zakai haka Aliyu? Miyasa? Ba nace duk abinda zaku gani ba kuyi kamar baku gani ba.”
Da gudu Hibbah ta zo ta rungume Ummin da Yaya Ammar itama. Gefe Yaya Muhammad ya kauda kansa yana ƙoƙarin ɗauke hawayen da suka ciko idanunsa. Yaya Abubakar ma idanunsa sun kaɗa sunyi jajur. Yaya Umar yafi kowa zuciya a cikinsu, yayinda Yaya Usman duk ya fisu sanyi shi da Yaya Muhammad. A wani irin fusace ya juya zai fita a falon Yaya Usman da yasan halin kayansa yay azamar riƙo hannunsa.
“Sake ni!”
Ya faɗa cikin kaushin muryar da ya maido hankalin kowa kansu. Girgiza masa kai Usman ya shiga yi alamar bazai barsa ba. Dan yasan dama badan Ummi da ke dakatar da su ba babu shakka da tuni Umar yayma Abba dukan mutuwa a gidan harma da Hajiya mamar kanta... Da ƙarfi Yaya Umar ya fisgi hannunsa da ga cikin na Usman. Hakan yasa Ummi azamar sakin Ammar tasha gabansa.
Cikin idonsa ta kalla batare da tace masa komai ba. A take yay ƙasa da kansa yana lumshe idanu da cije leɓensa da ƙarfi tamkar zai huda shi. Murmushi tayi tana kamo hannunsa cikin nata. Gaba ɗaya ƴaƴanta tasan lagonsu da hanyar sauke fushinsu. Shiyyasa a kowane lokaci take samun nasarar ladabtar da kowa cikin salon da ya dace. Babu wanda ta sake yima magana a cikinsu, sai kamo hannun Hibbah dake sharar hawaye har yanzu tai tana bin jikinta da kallo tamkar mai neman wani abu.
Da sauri Hibbah ta ce, “Ummi basuyimin komaiba fa, babu abinda ya faru ki kwantar da hankalinki”.
“Ai sun sakaki a tarkon da za'ayi miki ne!”.
Yaya Abubakar ya faɗa a tsawace cikin faɗan da kowa baisan yana da shi ba. Dan shima bai cika hayaniya ba sosai, amma yafi Usman da Muhammad zafi a wasu lokutan.
Ya riƙe ƙugunsa da hanunsa ɗaya, ɗayan yana murza goshinsa cike da damuwa. Yanda ya ke ɗan kaikawo yasa su fahintar akwai matsala kenan. Ummi da dama yin komai ta ke cike da ƙarfin hali ta kafesa da ido.
Zaune Yaya Abubakar ya kai saboda jin zai faɗi, dan shi kaɗai yasan a wane irin damuwa ya ke game da halin da Hibbah ta ke ciki. Gaba ɗaya ƙuruciya ta hanata fahimtar ramin da ta jefa kanta a ciki mai haɗari ne.........
“Abubakar mike faruwa?”
Ummi ta katsesa tana takowa gabansa. Idanunsa da ke jajir ya ɗago yana kallonta, ya ɗan furzar da zazzafar iska yana girgiza kansa. “Ummi tabbas akwai matsala, rawar kanta ta kaita ga jefamu cikin ramin da sam ita bazata fahimci haɗarinsa ba....”
Duk da hibbah a tsorace take da yanayin Yaya Abubakar ɗin, tai saurin katsesa ta hanyar faɗin, “Yayanmu wlhy babu abinda ya faru fa. Kawai dai sun sakani na bibiyar musu masu power bike ɗin nan dana sanar maka ne. Amma da ga haka basuyi min koma.........”
Tsawar da ta sakata kasa ƙarasa zancen ya daka mata. Ta maƙale a jikin bango jikinta na rawa saboda bata taɓa gamo da fushinsa irin haka ba. Shima tsaye ya miƙe yana nunata jikinsa har rawa yake ga idanunsa sunyi jajur. “Idan bakimin shiru ba wlhy sai na ɓallaki a gidan nan yau. Bance miki ki jirani a inda kike nazo na sameki ba? Su masu power rider ɗin da kike tunanin ba komai ba to sune tawagar ɓarawon nan da ake nema ruwa a jallo mai suna *Master!*, shine ya wawashi maƙudan kuɗaɗe jiya a asusun matar gwamna. Kowace hukuma ta jami'an tsaron jiharnan an basu awa ashirin da huɗu ne domin kawosa a mace ko a raye. Ba jihar nan da ƙasarnan kawai ba, hatta duniya baki ɗaya idonsu akan wannan mutumin yake. Amma shine k kika jefa kanki cikin abinda bakisan mafarinsa ba. Su waɗan nan jami'an da suka ɗaukeki zasuyi amfani da ke ne kawai su sami cikar burinsu, sunansu ya sake fiwowa a idon duniya. Kece zakiyi aikin amma sune zasu fito matsayin masu aikin. A tunaninki shi ɗin mahaukaci ne, kosu suna son matsalar tasa ta ƙare ne da wuri? Kuɗaɗen shigar da suke samu su dakata. Kafin yau an sha yimasa tarkuna da sukafi wannan haɗari amma bai kamu ba. Da ga ƙarshe kuma duk wanda yay masa tarkon ana nemansa ne a rasa ma baki ɗaya, ya ɓatar da shi. Wannan yasa a duk lokacin da ya aikata laifin manyan ke makalewa su saka ƙananun ma'aikata yin aikin, da ga ƙarshe suke nuna sunyi aikin ma duniya, wanda yay aikin kuma rayuwarsa ta faɗa a haɗarin da babu wanda zai sakejin yanda akayi, kuma basa wani ɗaukar matakin bashi kariya ko cetosa. Shekarunki goma sha takwas kacal da wasu wattani a duniya Muhibbat! Bama ki gama karatun gina rayuwar taki ba amma kika jefa kanki a wannan haɗarin saboda kunnen ƙashinki. Wannn kunnen babu wanda ya isa ya faɗa masa yaji sa”.
Ya ƙare maganar da takawa inda take maƙure a bango jikinta na rawa ya damƙi kunnenta da ƙarfi yana murzawa cikin yatsun hannunsa. Rawa jikinta ya farayi tana girgiza masa kanta saboda zafi.
Sakin kunnen nata yay yana dungure mata kai, yayinda sauran yayun nata da Ummi keta faman ambaton (innalillahi wa-inna ilaihirraji'un) a zukatansu. Yaya Abubakar ya cigaba da faɗin, “Ba wanann kaɗai bace damuwar Ummi, tunda har basu sami nasarar kamashi ba zargi zasu ɗarsa akanta itama. Dan zasu raba hankalinsu ne yanzu akan tunanin ko shine ya shirya komai wajen yin amfani da ita. Dan duk harin da jami'an tsaro ke kai masa ba'a taɓa cin nasara kamar nata ba da ya gudana cikin kanƙanin lokaci. Yanzu da zarar sun fitar da bayanai wa media cewar sun haresa, harin da kuma aka samu ci gaba a cikinsa fiye da na baya, to kowacce hukumar jami'an tsaro sai sun bibiyi yanda hakan ta kasance ta karƙashin ƙasa, walau jami'anmu nan gida kona ƙetare da ke nanuke cikin case ɗin kamar yanda suka saba mana kutse a cikin ayyukan daya shafi ƙasashenmu. Mu kuma bamu isa muyi koda tari akan nasu ba. A ƙarshe kowa ya bincika ita zai gano. Duk kuma zasu kasance wajen bibiyarta da mu kammu ba tsira zamuyi ba. Shima da ta aikata komai dominsa ba barinta zaiyi ba na sani.
“Ya ALLAH!”.
Ummi da ke neman faɗuwa ta faɗa tana fashewa da kuka. Da sauri sukai kanta gaba ɗaya suna ƙwala mata kira. A wani irin sarƙe numfashinta ya fara fita, ta fara tari.
Rikicewa suka sakeyi, yayinda kukan Hibbah ke ci musu zukata matuƙa. Cikin bada umarni Yaya Muhammad ya ce su dagata a kaita asibiti. Yanda ya faɗa ɗin haka sukai, sai dai suna fitowa harabar gidan ƴan sanda na shigowa. Basuyi yunkurin bi takansu ba. Sai dai muryar Abba da sukaji yana nuna Ammar da cewar shine ya kashe masa yaro ya saka hankalinsu rabuwa biyu.
A ɗan firgice Yaya Usman ya furta, “Kisa?”.
“Eh mara mutunci, ko ƙarya zan masa ne? Tun ɗazun likitoci suke akan Junaid amma babu alamar numfashi tare da shi, dan haka ku kamasa, inhar na rasa ɗana shima sai an kashesa.”
Tarin Ummi ne ya ƙara ƙarfi, sai ga jini na fitowa ta hancinta. Hankalinsu ne ya sake tashi. Sai a lokacinne Abba ya lura da halin da Ummi take a ciki. Maimakon ya saki batun ƴan sanda ya shiga sahun masu kula da ita, sai hakan ta gagara. A kausashe ya bama ƴan sandan damar kama Ammar yana tabbatar musu pretending Ummi keyi kawai.
Ganin duk sun shiga mota ƴan sanda kuma sun cukuykuye Ammar dake turjewa dan hankalinsa nakan halin da mahaifiyarsu ke ciki bata tasu yake ba. Yaya Muhammad ya cema Yaya Usman ya fita yabi ƴan sandan dan susan inda za'a kai Ammar ɗin. Su kuma zasu kai Ummin asibitin.
Badan yaso ba ya fita domin bin umarninsa. Dan duk da an haifesu babu wani yawan tazara a tsakaninsu hakan baya hanasu respecting junansu saboda ƙyaƙyƙyawan training da suka samu da ga mahaifiyarsu.......
★★★★★★★★★★★
A lokacin da wancan tashin hankali ke baibaye da ahalin Hibbah, anan headquarters ɗin ƴan sanda ƙoƙarin fitar da bayanan harin da Hibbah ta kaima master sukeyi. Sai dai kamar yanda Yaya Abubakar yay hasashe sunansu ne ya fito matsayin waɗanda sukai aikin. Sun kuma tabbatar nan da lokaci ƙanƙani zasu gurfanar da Master a saman gwiwoyinsa gaban duniya.
Babban abinda ya ɗauki hankalin jama'a da media baki ɗaya shine. Rahoton ƴan sanda na fita da mintuna uku kacal. Sai ga wani babban labari kuma da ga wannan shahararren ɓarawo mai suna *(MASTER)*. Ya fitar da jerin sunayen wasu manyan kaddarori na matar gwamna da mutane basu taɓa kawoma ransu hasashen tana da alaƙa da su ba a wani shafi nasa. Sannan ya rabasu a manyan gidajen redio da television ta hanyar tura musu saƙwanni kai tsaye a shafukansu na sada zumunta masu matuƙar muhimmanci da yawan mabiya.
Sosai ƙura ta tashi cikin lokaci ƙanƙani, manyan ƴan siyasa abokan takarar wannan jami'iyya suka samu damar baje kolin nasu faɗar albarkacin bakin dan dama tamkar kaɗan ake jira. Yayinda a gefe kuma da yawansu suke goyon bayan shi wanann master da ƙoƙarin wanke laifukansa a idanun mutane.
Fitar wannan kace nace keda wuya takardar gayyata ta bayyana da ga hukumar *(Yaƙi da ta'annatin kayan gwamnati)* zuwa ga matar gwamna. Acewarsu, suna gayyatarta zuwa ofishinsu da ga nan zuwa awanni ashirin da huɗu domin amsa musu wasu tambayoyi. Idan bataje da kanta ba, zasuje har gida su su ɗakkota.
Cikin ƙanƙanin lokaci sai ga ɓangaren gidan gwamnati suma sun yunƙuro wajen maida murtani ta hanyar jifar abokan hamayyar TAKUN SAƘAAr nasu da dangantaka da Master. Suna mai tabbatar ma duniya lallai akwai lauje cikin naɗi. Sannan akwai ayar tambaya dangane da wanzuwar Master. Shin kodai? Kodai......😂🤐.
Ta kowanne fanni gari ya ɗauka zafi, babu wani babban labari sai na wannan badaƙala ta TAKUN SAƘAA tsakanin Master da ya haɗa gurmin zuwa jami'an tsaro da na gwamnati. tare da ƴan siyasa da masu radin faɗin albarkacin baki. A gefe kuma ga talakawa ƴan bani na iya nata faman sharhi akan komai, kai kace agabansu aka ƙulla al'amarin..........
(😖Wai, sunan wata karya. Sharaton. Bily aɗan dinga sassautawa dai🚶🏻😌😒😏😣😝)
*________________________________*
Wani ƙayataccen murmushin da ya saka yaransa shagala a kallonsa ya saki lokacin da yake faman duba wasu da ga cikin Comments na mutane da ke wanzuwa a yanar gizo. Cikin salon ƙasaitarsa da izza ya wani juya kujerar da yake zaune cike da ƙwarewa yana lafewa a cikinta hankali kwance. Tare da wani salon da su kaɗai suke gane mi yake nufi idan yayi sa.
Dariya suka sanya cike da jin daɗin. Dan kobai faɗaba sunsan yana cikin farin ciki matuƙa. A duk sanda ya tada irin wannan ƙurar ya ga taja hankalin ƴan ƙasa da waɗanda yayi dominsu su kansu yakan yafe musu laifuka da sukai masa. Ko ya bisu da ƙyauta mai tsoka da ke sakasu farin ciki. Zai kuma kasance tare da su cike da nishaɗi duk da shiɗin ba mutum bane mai yawan magana akoda yaushe.
Da wannan damar Habib yay amfani wajen gabatar masa da rahoton binciken da ya gudanar akan aikin da ya basu ɗazun. Dan sun wuce adadin awannin da ya basu sosai. Kuma sunsan bawai ya manta bane, ya sharesu ne kawai bisa wani dalili nasa daban. Zatama iya yuwuwa shi tuni ya gama aikin binciken, suma ɗin ya sakasu yi ne kawai domin hukuntasu bisa laifin sakacinsu.
Komai baice akan takardun ba. Hasalima baiko buɗesu ba ya cigaba da duba sakwannin. Yayinda murmushi ke cike da ɓoyayyar fuskarsa da har ake ganin bayyanarsa bisa ta bogin da ke a kanta, wadda idan ba faɗa maka akaiba bazaka taɓa cewa ba fuskarsa bace ba. Su kansu yaransa inda ace da ita kawai yake amfani baya canjawa tabbas zasu ce itace ainahin fuskarsa. Sai dai zuwa da mabanbanta da yakeyi ya sakasu fidda wanann hasashen a cikin ransu.
Ya kai tsahon lokaci tare da su yana bibiyar kowacce kafar yanar gizo da ta yaɗa labarai. Kafin ya miƙe yana faɗin, *“7:30am* zamu koma *L.E street.* Jahje na buƙatar bada ƙafa”.
Wani ihun farin ciki suka saka. Dan a gaba ɗaya gidajen da suke zama gidan *_L.E STREET_* yafi kowanne girma da ababen more rayuwa. Suna matukar mamakin yanda yake sama musu manyan gidajen da suke zama, a kuma manyan anguwanni batare da an farga shiɗin baneba. Tsabar hatsabibancinsa kuma a wasu lokutan sukan koma anguwannin talakawa su zauna har na tsahon wani lokaci. Haka suke tamkar fulanin tashi. Da wahala suyi zaman wata uku a gida batare da sun koma wani ba.
Kansa ya ɗan girgiza da kai kofin coffee ɗinsa saman baki yana barin wajen nasu zuwa jikin windown ƙaramin falon da suke ciki na gidan da ya kawosu ɗazun. Wanda har yanzu basu san taka-maimai a cikin wace anguwa yake ba, dan basu fita ko soro ba har yanzu. Shi kadai ne ya fita bayan awanni takwas ya kuma dawo.
Wani hatsabibin murmushi ya sake saki idonsa kyam akan ƙwan wutar lantarki da ke a tsakar gidan. Haka ya cigaba da tsaiwa a jikin window ɗin yana cigaba da shan coffee ɗinsa da sauraren iya shegen yaransa akan Comments ɗin mutane da suka koma bibiya suma suna kwasar dariya.
Kofin da ya sake kaiwa baki yaji babu komai a ciki ya sakashi ɗago kofin ya kalla. Ba komai ciki ya shanye, hakan sai ya bashi dariya. Amma sai ya gintse kayansa baiyiba sai a zuciya. Juyowa yay da baya ya ajiye cup ɗin ya ɗauka file ɗin da Habib ya ajiye. Cikin muryarsa da sautinta ke fita da nutsuwa da amo yace, “Ayi addu'a kafin a kwanta. Goodnight”.
Kusan a tare suka haɗa baki wajen faɗin, “ALLAH ya tashemu lafiya boss. Sweet dream tare da ƙarin ƙyaƙyƙyawar idea akan ƴan ruda”.
Daƙƙuwa yay musu batare da ya juyoba. Sai dai ya saki murmushi dai-dai yana shigewa. Duk da basuga murmushin nasa ba kasancewar ya juya musu baya hakan bai hanasu yin kananun dariyar farin ciki ba gaba dayansu.
Yana shigewa suka farma gasassun kajin da ya kawo musu tun shigowarsa da ci. Dama sun ɗan ɗaga kafa ne ganin yazo a cikin yanayin babu wasa. Yanzu ko sunsan komai normal ne, sai abinda ba'a rasaba saboda rikita-rikitar Master ɗinsu bata taɓa karewa. Daya toshe waccan matsalar zai ɓallo wata da kansa kafinma ƙurar wadda ya tayar ta lafa.
Shima ko da ya shiga ɗakin zazzafan numfashi ya furzar. Ko'ina fes dan tun bayan barinsu da yayi suka gyara komai. Ya jefa file ɗin hannunsa saman madai-daicin gadon. Kayansa ya shiga zamewa alamar son watsa ruwa. Ya rage da ga shi sai singlet da boxer. A haka ya nufi toilet ɗin.
Tsahon mintuna ashirin ya ɗauka a ciki kafin ya kammala, tun kafin ya fito da ga bayin ya ziro hannu ya kashe wutar ɗakin baki ɗaya. Batare da damuwa da duhun da ya mamaye ko ina ba ya fito a haka. Ta cikin duhun ya iso bakin gadon, ya kai zaune cikin lalube ya ɗakko wayarsa ƙarama. Fitilarta ya kunna, tare da ɗaukar file ɗin da Habib ya bashi. Sam ba'a ganin fuskarsa. Sai dai shi yana ganin rubutun file ɗin kasancewar shi ya haska kai tsaye. Sai alamun bathrobe ɗin dake a jikinsa wadda iya inda hasken ya haska kawai ake gani.
“What?!”.
Ya faɗa cikin subucewar baki ganin bayanan na nuna cewar da taimakon mace aka kai musu harin ɗazun. Macen ma ƴar 18 years kacal. Cikin wani irin rawar jiki yay wurgi da file ɗin yana faɗin, “Impossible! Ni! Ni! Ni ne yarinya ƙarama kamar wannan zata hara. Hari irin wanda wani mahaluki bai taɓa samun galabar yimin shi ba. Kuturun ubacan kayyasa😳............✍
*_HHHH anayi muna ɓallar rake na funtuwa mai zaƙi. Alaji Master yaya take ne😉😝🐒?. In baka saniba ma yanzu ne wasan zai fara😂👎🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_Chapter Eleven_*
..........Cikin gaggawa aka amshi Ummi a asibiti. Dan da ƙyar take fitar da numfashi, ga jinin da yake fita mata ta hanci da tayo tari da ya harmutsa dukkan zukatan su Yaya Muhammad. Hibbah kam ai tama koma musu tamkar zararriya. Dan koda za'a shige da Ummi sai da Yaya Umar ya riƙota shima hawaye masu ɗaci na cika masa idanu.
Yaya Muhammad kam da baida wahalar zubda hawaye gefe kawai ya maida kansa yana sharewa. Umminsu itace duniyarsu. Itace farin cikinsu. Itace ta maye musu dukkan gurbi na dangin mahaifinsu da giɓin mahaifin nasu da suka rasa tsahon shekaru goma sha tara. Tayi haƙuri da damuwoyi kala-kala domin taga sunyi farin ciki. A kullum ƙoƙarin ta su zama mutanen kirki. Su zama masu haƙuri, su zama masu juriya. Su zama.... Su zama... Da yawa. To sukam idan akace sun rasata ina zasu saka kansu da rayuwarsu. Idan suna a gabanta sam basa tuna sun girma. Ganin kansu suke tamkar ƴan shekaru goma-goma. Bazasu so Ummi ta tafi ta barsu batare da sun cika mata burinta na ganin sunyi aure ba. Kamar yanda take addu'ar ganin zuri'arsu suma hakan shine fatansu a yanzun. Suna son yawan ganin dariya a saman fuskarta kamar yanda mahaifinsu yay sanda yana raye. Amma hakan duk bazata tabbataba sai tana a kusa da su........
“Ya ALLAH ka bama Ummi lafiya ka tashi kafaɗunta. ALLAH yasa ni na mutu a madadinta”.
Furucin Muhibbat da ke kuka ya katsema Yaya Muhammad da su Yaya Abubakar tunaninsu. Gaba ɗayansu suka zuba mata idanu na ɗunbin tausayinta da ƙaunarta. Yarinya ce ita mai yawan walwala, kazarkazar, wauta, tsiwa, rawan kai, surutu duk a dalilin gata da kulawar da take samu da ga garesu. Tana matuƙar son Ummi, suma haka. Batasan mahaifinsu ba, shiyyasa suketa ƙoƙarin ganin sun cike mata gurbinsa.
A hankali Yaya Abubakar ya taka inda take durƙushe gaban Yaya Umar da rauni ya cika zuciyarsa na tausayin kansu da autar ta su. Hannu biyu yasa ya kamota ya ɗaga tsaye. “Haba Muhibbat, maimakon kima Ummi addu'ar samun lafiya sai ki dinga ma kanki addu'ar mutuwa a madadinta?. Insha ALLAH Umminmu zata tashi da lafiyarta kinji. Ki mata addu'a da fatan alkairi, ALLAH ya na tare da ita kinji”.
Kanta ta jinjina masa wasu zafafan hawayen na rige-rigen sakko mata. Yasa hannu ya share mata yana murmushin ƙarfin hali.
“Ƙyaƙyƙyawa mai kama da Umminta a komai, sai dai raguwa ce bata kai Ummi jarumta ba”.
Yaya Abubakar ya faɗa cikin ƙarfin hali yana ɗan ja mata kumatu. Maimakon tai dariya da tsalle kamar yanda ta saba idan ya faɗa mata hakan, sai ta faɗa jikinsa ta fashe da kuka. Kusan atare duk suka rumtse idanunsu, dan kukanta na matuƙar sake tada musu hankali.
Kusan mintoci arba'in da biyu likitoci suka ɗauka tare da Ummi. Kafin ALLAH ya basu ikon fitowa. A kusan tare su Yaya Umar suka miƙe a zabure harda Hibbah dake jingine jikin Yaya Umar barcin wahala ya ɗauketa.
Kusan a tare suka furta “Doctor ya jikin Ummin mu?”.
Kallonsu yayi cikin furzar da numfashi yana cire norsemask ɗin fuskarsa. “Inason yin magana da ku a office”. Ya faɗa yana ƙoƙarin wucesu. A take suka rufa masa baya har Muhhibat da Yaya Umar ke riƙe da hannunta. Kusan tare suka shiga da doctor cikin office ɗin. Hakan da sukai sai tausayinsu ya sake kamashi. Dan a kallo ɗaya zakai musu ka hango ɗunbin so da ƙaunar da sukema mahaifiyar tasu. Bai wani tsaya ja musu rai ba yay musu bayani akan matsalar da ke tare da Ummi a ƙasan zuciya da hanjinta. Bincikensu ya nuna kuma ta jima da ciwon yana ta cinta a hankali, sai dai yafi nuna kansane a duk lokacin da wani ɓacin rai ko tashin hankali ya sameta. Amma zasu mata aiki insha ALLAH suna mata fatan samun lafiya.
Duk da maganarsa ta ƙarshe taɗan sakasu jin sanyi hakan bai hana zukatansu shiga cikin matuƙar rauni ba. Ya ɗan ƙara faɗaɗa musu bayanai akan abinda za'a iya buƙata akan aikin da magungunanta. Tare da basu tabbacin inhar sun shirya a yau ɗin nan ma za'a iya mata aikin. A take sukace sun amince, duk da kuwa kuɗaɗen da ya ambata da wuya a iya samunsu kai tsaye da ga garesu. Badan suna da yawa bane sosai, kawai dai suɗin masu tasowa ne ba wasu ɗumbin kuɗaɗe suka tara ba. Amma dai tunda ya ce zasu iya bada rabi idan an kammala aikin su cika zasuyi ƙoƙarin su insha ALLAH.
Take ya basu takarda Yaya Muhammad ya saka hannu. Daga haka suka fito domin tattaunawa akan zancen kuɗin. Dan doctor yace sai sun tura zaiyi ƙoƙarin haɗa wasu da ga kayan aikin insha ALLAH.
Su dukansu suna aiki, Ammar ne kawai da Hibbah ƴan makaranta a cikinsu. Sai Yaya Umar da ke ɗan harkar kasuwanci saboda matsalar rashin samun aiki da matasa ke fama da shi a ƙasar nan. Sai ma yazam a yanzu yafi nutsuwa da kasuwancin sama da aikin da yay karatu akansa. Dama kuma su Yaya Muhammad ɗin nata son ganin sun ƙara masa ƙarfin jari tunda ALLAH yayma kasuwar tasa nasibi.
Sun ɗan tattauna wajen ganin sun haɗa kuɗaɗen, cikin amincin ALLAH ma sai gashi an samu kusan rabin a hannunsu su uku. Idan Yaya Usman yazo shima zasuji mi za'a samu daga garesa. Abba dai basa saka rai game da shi sam.
Basuyi zaman ɓata lokaci ba wajen fita su tattaro kuɗaɗaɗen har Yaya Usman da ya iso asibitin a yanzu shima, dan ya kasa jure zama acan saboda ya gwada ƙoƙarinsa na ganin an bashi Ammar amma hakan ya gagara saboda mugun ƙulli da Abba yaje yayi a station ɗin. Ya tahone kawai dan yasan insha ALLAH Yaya Abubakar zai fiddosa da zaran hankali ya kwanta. Kafin su dawo kuwa an gama shirya komai na shiga theater ɗin. Cikin amincin ALLAH zuwa ƙarfe takwas na dare aka shiga da Ummi. Sun bita da ƙyaƙyƙyawar addu'a da fatan dacewa a zahiri da baɗini.
Yaya Muhammad ne ya fara fahimtar akwai yunwa tattare da Hibbah. Dan gaba ɗaya jikinta ya saki tamkar mara laka. Yana lura da ita ko salla a zaune ta dinga yinta. Hannu yasa ya kamo nata cike da kulawa yana faɗin, “Auta yaushe rabonki da abinci”.
“Tun breakfast ɗin safe Yayanmu, amma kuma banajin yunwa”. Ta faɗa cikin sanyin da basu santa da shi ba.
Su dukansu sai da suka dubeta cike da tausayi. Yaya Usman yay saurin barin wajen batare da yayi magana ba. Cikin lokaci ƙanƙani sai gashi ya dawo da teakaway.
Zama yay da kansa zai bata amma sai tace ta ƙoshi. Dukansu babu wanda bai lallasheta ba amma tace ta ƙoshi. Sai da taga duk sun ɓata rai sanann ta amsa ta ci wanda ya saka mata a baki. Amsar cokali tayi ta ɗiba da kanta shima ta bashi. Ta sake ɗebowa ta bama Yaya Umar. Shima Yaya Abubakar haka. Sannan ta bama Yaya Muhammad shima. Dukansu murmushi suke mata a karon farko tun bayan shigowarsu asibitin da duk rayukansu suke a jagule. Amsa Yaya Usman ɗin yay ya cigaba da bata. Kusan lauma uku ta kauda kanta idanunta na cikowa da ƙwalla.
“Miya faru kuma?”. Yaya Abubakar dake miƙa mata ruwa ya faɗa. Hawayen data matso suka silalo saman kumatunta. Muryarta na rawa tace, “Yayanmu Yaya Ammar fa?”.
Shiru suka ɗanyi duk suna kallonta. Kafin Yaya Abubakar ya shafa kanta fuskarsa ɗauke da murmushin ƙarfin hali. “Karki damu shima zai dawo, insha ALLAH bazai kwana acan ba. Ƙarasa cin abincinki ina zuwa”. Ya ƙare maganar yana mikewa. Tashi Yaya Usman yay yabi bayansa.
Police station ɗin da aka kai Ammar suka nufa. Tun shigowar su Yaya Abubakar wasu a cikin ƴan sanda suka shaidashi saboda aiki ya taɓa haɗashi da wasu a cikinsu. Amma duk da haka sai ya nuna musu i'd card ɗinsa. A zabure sauran ma suka shiga gaishesa. Aka kuma masa iso ofishin ogan wajan.
Tun a shigowarsu ya shaida Yaya Abubakar ɗin. Amma sai ya maze abinsa. Yaya Abubakar ya cije lip ɗinsa dan akwai ƴar tsama a tsakani. Sai dai yana sama da shi. Cikin nuna bai damu da basarwar tasa ba yay masa bayanin kansa. Tare da buƙatar a bashi Ammar.
Cikin yatsine fuska ɗan sandan yace, “To yallaɓai idan ku matsayinku na manya kuna haka su kuma wanda basu da dangi ƴan sanda kuma fa? Laifi ƙaninka yay aka kawosa nan, sai kuyi haƙuri mu gama tattara bayanai akansa mukai maganar kotu kamar zaifi”.
Sosai Yaya Abubakar ya kafesa da ido. Sai kuma ya saki wani lalataccen murmushi yana miƙewa dan yasan wannan tsarin da ga Abba yake. “Wanann basirar ba taka bace. Amma ga saƙo ka bama wanda ya tsara maka ya kuma biyaka. Ya kiyayi ranar maida murtani dan zata kasance mai ɗaci da tsauri. Ya kuma bar raina allura dan itama ƙarfe ce. Duk randa zuri'ar Aliyu Hamza gwarzo sukaji a ransu zasu maida murtani TAKUN SAAƘAR bazai masa ƙyau ba. Wannan hanunka mai sanda ne”. Yaya Abubakar ya ƙare maganar cike da gargaɗi.
Murmushi Yaya Usman yayi. Dan bai taɓa zato da tunanin yaya Abubakar ɗin nasu ya iya zaro zance haka na. Koda suka fito da kansa yasa a kaisa cell ɗin da Ammar yake. Shine ya amshi key tun daga kanta ya buɗesa da kansa.
Wani irin kallo ya tsaya yanama Ammar da yaci uban duka. Da alama ma ba'a jima da dukan nasa ba, dan duk sabbin raunuka ne a jikinsa dake fidda jini. Komai baiceba a lokacin sai kama hannun Ammar ɗin daya taso da sauri yana tambayarsa “Ina Ummi take?” yayi. Bai amsa masa tambayarsa ba sai da suka iso kantar. Ya duba ƴan sandan wajen da sukai tsuru-tsuru cikin kaushin murya yace, “Su waye sukai wannan aikin?”.
Kallon kallo aka shigayi. A matuƙar tsawace yace, “Ba magana nake ba ne?!!”.
Zabura duk sukayi har tsirarun mutane da sukazo belin ƴan uwansu da masu kawo abinci. Cikin rawar murya wani ɗan sanda yace, “Yallabai wlhy ba laifinmu bane sakamu akayi”. Ya ƙare maganar a hankali cike da raɗa saboda fitowar ogansu da ga office dan jin tsawar da Yaya Abubakar yayi.
Takarda Yaya Abubakar ya fisga ya jefama ɗan sandan da yay maganar. “Ina son duka sunayen members na ƴan sandan dake a station ɗin nan. Wanda sukai wannan dukan kuma sunayensu su kasance a ware”.
Wani busashshen yawu ya haɗiye da ƙyar yana ɗaukar takardar. Jikinsa sai tsuma yake ya shiga zano sunayensu ɗaya bayan ɗaya. Bayan ya kammala cikin girmamawa ya mikama Yaya Abubakar ɗin. Uffan baice masaba ya amsa tare da jan hannun Ammar da Yaya Usman ya riƙe ta ɗayan gefen suka fice da ga station ɗin.
Ko a mota ma babu wanda yay magana dan zuciyar Yaya Abubakar takai ƙololuwar ɓaci game da lamarin Abba. Asibitin suka wuce da Ammar shima. Ba ƙaramin tashi hankalin su Yaya Muhammad yay ba ganin dukan da akaima Ammar. Hibbah kuwa kuka ta fashe musu da shi tare da zuwa ta rungume Ammar ɗin.
“Wash ALLAH auta zafi”.
Ya faɗa cike da shagwaɓa saboda jin ta ƙankame masa hannunsa da yake da tabbacin ƴan sandan sun ji masa ciwo. Saurin sakin hanun nasa tai tana sake fashewa da kuka. Ya kai hannu bisa kanta ya dafa yana murmushin ƙarfin hali. “K karki maidani kamar ba namijiba mana. Bakisan dukan ƙarfi ya ƙara min ba ma”.
A yanda yay maganar ya saka su Yaya Umar yin murmushi suna girgiza kansu. Hibbah kuwa kukan ne ya sake kufce mata.
Yaya Umar ne ya kaisa akai treatment ɗinsa da bashi magunguna. Sauran abincin da Hibbah taki ci suka matsa masa yaci da ƙyar shima. Dan sai da Hibbah ta dinga basa a baki yau babu faɗa. Bayan ya kammala yasha magungunan da aka bashi. Duk yanda sukaso yaje gida ya huta yaƙi, yace shima sai yaga fitowar Ummi.
Sha'awa yanda suke ƙaunar junansu ya bama doctor Bilal. dan haka ya bama Ammar ɗin shawarar yazo office ɗinsa ya kwanta to har komai ya kammala sai a tashe sa. Nanma da ƙyar ya amince bisa umarnin yaya Muhammad. Haka dai ya miƙe yana tura baki Hibbah na masa gwalo.
_____________★★★_____________
Duk yanda yaso yin shirin barci ya kwanta hakan ya gagara. Sai fama kai kawo yake a cikin ɗakin, abubuwa da yawa zuciyarsa ke raya masa game da matakin da ya kamata ya ɗauka a kanta. Inhar zata iya kai masa hari ta samesa a ƙanƙanin lokaci. To wane irin shiri kenan zatai a gaba dominsa? Lallai dole ne yasan ita ɗin wacece? Mi kuma ta taka ne haka?. Shin sakata akai? Kokuwa yin kanta ne?.
Waɗanan jerin tambayoyi suketa faman masa kai kawo a zuciya da hanashi nutsuwa. Shiri ya canja saɓanin pyjamas da ya kamata ya saka sai yasa wasu kayan daban.
Yaransa na falon zaune har yanzu suna sha'aninsu sai ganinsa sukai ya fito. Mamakine ya kamasu dan duk zatonsu ya kwanta.
“Boss da matsala ne?”.
Salisu ya faɗa cike da girmamawa.
Kansa ya girgiza masa yana ƙoƙarin ɗaura agogonsa. Sai da yaje gab da fita a falon yace, “Zanje wani waje ne, wani yazo ya rufe gidan”.
Saurin miƙewa Khalid yayi duk da tambayoyine fal bakunansu amma babu damar yi, dan ya nuna baya buƙatarsu. Su ko saboda trianing da suka samu da ga garesa da kowanne irin yare yay magana ko yay nuni suna fahimtar kayansu.
Koda ya wuce Khalid ya dawo zaman tattaunawa sukai, amma sai basu gano komaiba, dan haka sukai jigum-jigum......
________________________________
Alhmdllhi ƙarfe goma aka fiddo Ummi da ga ɗakin theatre cike da nasara. Bayyana muku irin farin cikin da su Yaya Muhammad suke ciki ɓata lokaci ne. Basu sami damar ganinta ba dan an miƙata ɗakin hutu ne. Sai dai bayanin da Dr Sageer yay musu na narar aikin ya saka zukatansu nutsuwa. Har suka amince da shawararsa ta tafiya gida dan ba'a bukatar kowa tare da Ummin sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu.
Basuyi wani zaman ɓata lokaci ba suka tattara suka wuce bayan an tado Ammar da zazzaɓi mai zafi yayma ligif saboda dukan da yaci. Sosai tausayinsa ya bayyana bisa fiskokinsu. Sai dai komai basuce ba bayan Hibbah da ke ta jera masa sannu kamar zatai kuka. Kaɗan-kaɗan ta ɗaura hannunta a goshinsa.
Suna gab da zuwa gida ya bige hannunta data ɗora masa a karo na babu adadi. “K dalla kin isheni, ga hannunki da sanyi”.
Baki Hibbah ta tura gaba. Cike da tsiwa ta murguɗa masa baki da faɗin, “Oh dama ka samu na damu da kai zaka min wani iyayi”.
“To waya aikeki? Uwar iya mai cinikin iya”. Ya faɗa yana gyara kwanciyarsa jikin kujera.
Murmushi Yaya Usman da ke kusa da su yayi yana girgiza kansa kawai. Dan inda sabo sun saba gani. Anjima kaɗan kuma kaga sun koma hirar arziƙi. Kafin awa ɗaya ta rufa sunyi faɗa sau biyu.
Cikin jin haushi Hibbah tace, “Idanma kaga na sake kulaka dan ALLAH ka tsine min Yaya Ammar”.
Baki Ammar ya taɓe da faɗin “ALLAH na gode maka na jefar da ƙwallon mangwaro na huta da ƙuda”.
“Yaya Usman ka ganshi ko?”. Ta faɗa kamar zatai kuka.
“Ya isa manta da lamarinsa auta. Ko sannu karki sake masa har ya warke”.
“Ai baran masa ba ko Yayanmu”. Tai maganar da dungurin wajen ciwon da ke a hannunsa. Ƙaramar ƙara ya saki yana bige mata hannu dan yaji zafi. Ta ƙyalƙyale da dariyar mugunta. Ranƙwashi mai shegen zafi ya bata wanda ya saka bakinta rufewa ruf, sai kuma ta fashe da kuka.
Yaya Abubakar da duk yake jinsu da ga gaba ko kallo basu ishesa ba. Sai ma waya da ya ɗauka yay kiran maigadi ya buɗe musu gate. Koda suka shiga cikin gidan tsitt yake alamar jama'ar cikinsa harsun ƙwanta. Kusa da inda Yaya Muhammad yay parking shima yayi gab da sashensu.
Hibbah da ke kukan ranƙwashin da Ammar yay mata ta fara fita domin kaima Yaya Muhammad ƙara tunda Yaya Abubakar bai bada fuska ba.
“K zoki wuce ciki ki kwanta”. Yaya Abubakar ya dakatar da ita dan bayasan wani dogon magana a yanzu. Yasan kuma indai Hibbah ce bataƙi su kwana ana shashanci ba. Baki ta tura gaba sim-sim ta nufi sashensu.
Yaya Muhammad yay ɗan murmushi yana kallon Yaya Abubakar ɗin. “Siddiq yau fa gaba ɗaya ka zama masifaffe. Kasa duk auta ta firgita da kai”.
“Tana da cika ciki ne wani lokacin”. Yaya Abubakar ya bashi amsa yana kashe motar. Yaya Ammar yace, “Dama hakan kowa ke mata da mun huta da shegen ƙiriniyarta tamkar ƴar mage”.
Kusan duk sai da sukai ƙaramar dariya. Da ga haka suka shige makwancinsu kowa ya nufi ɗakin barcinsa.
Hibbah ma da ta shiga tanata zunɓure-zunɓure shirin barcin tai tana kunkunin wai dan anga Ummi bata nan kowa ya tsaneta. Gobe a asibiti zata kwana bazata biyosu su cinye ta ba.
Da ƙunkunin dai harta kammala shirin barcin ta kwanta bayan tayi addu'a. Sai kuma a lokacin tunanin duk abinda ya faru a wannan yini ya shiga dawo mata. ALLAH dai ya taimaketa barci barawo yaci galaba akanta batare data shirya hakan ba.
*_WASHE GARI_*.
Yau Yaya Umar ne ya shigo yama Hibbah knocking. Sai da yaji ta tashi sanann ya juya ya fita bayan ya mata gargaɗin karta koma barci ta shiga kitchen idan sun dawo salla zaizo ya tayata haɗa breakfast. Da to kawai ta amsa masa dan harga ALLAH barcin bai isheta ba. Sai dai sanin halin masifarsa yasata bin umarninsa bayan ta idar da sallar tai azkar ta fita kitchen ɗin. Bata jima da fara aikin ba suka dawo. Su dukansu babu wanda bai iya girki ba dan Ummi babu abinda bata sakasu na aikin gida. Shiyyasa bata taɓa damuwa da zama da ƴar aiki ba tun da suka fara tasawa.
Yaya Umar ne ya tayata sukai breakfast ɗin. Yaya Usman kuma yanata ƙoƙarin gyara gidan shi da Ammar da ya tayasa dan jikin nasa da sauƙi bakamar jiya ba. Magungunan da aka basa sun taimaka masa matuƙa. Cikin kankanin lokaci suka kammala komai tsaf kowa ya tafi dan watsa ruwa. Sabo da fita aiki yasa duk suka hallara akan lokaci bisa dining. Sai uwar latti ce ko motsinta babu sai da Yaya Muhammad ya je da kansa yay mata knocking.
Koda ta fito masifa Yaya Umar da Usman suka hauta da shi na sakasu yin latti kamar kullum. Cikin son a kareta ta kalla Yaya Abubakar da Muhammad. Duk murmushi sukai mata da nuna mata kujera alamar ta zauna ta rabu da su Umar ɗin. Fuska a kumbure taja kujera ta zauna kuwa. Da ga haka suka fara karyawa.
Sunyi nisa sosai acin abincin Abba ya shigo fagan-fagan Hajiya Mama biye da shi. A tare duk suka ɗago suka zuba musu ido. Sai wani irin tsoronsu da shakkarsu ya shigi su Abban lokaci guda. Yaya Muhammad ne ya fara ɗaule kansa ya maida ga abincin gabansa. Suma sauran duk sai suka yi kamar yanda yay ko gaishesu basuyi ba.
Cikin masifa Hajiya mama tace, Kunci ubanku marasa mutunci. mu zaku kalla ku watsar tamkar wasu kashi?”.
A mamakinsu ko motsi babu wanda yayi, sai ma cigaba da cin abincinsu sukeyi hankali kwance. Hajiya Mama da Abba sukai galala a tsaye kamar gunkuna suna kallon sabon salon iskanci. Suko sunyi tamkarma basusan da zamansu a wajenba.
Wani irin baƙin cikine ya lulluɓe Abba ya shiga zazzaga tujara musamman akan fiddo Ammar, dan dama tun jiya ɗan sandan ya kirasa ya sanar masa. Ya kuma tabbatar masa da Abubakar yana tare da manyansu sosai, idan ya matsa akan Ammar ɗin tofa wata da tafi wadda suka shirya zata taso. Hakan yasa Abbana ɓam da bakinsa. Ya dai ɗauka alwashin zubarma da Ummi tujara tare da sauke duk fushinsa a kanta. Shiyyasa yana kammala sallar safensa da ya keyi a gida kullum bayan rana ta fito ya nufi sashen hajiya Mama ya sanar mata. Shine fa suka taho yima Ummi taron dangi basu san ma bata gidan ba. A zatonsu kuma su Yaya Abubakar ɗin sun fita.
Duk iya tujarar da sukeyi babu wanda yay koda motsi balle nuna yasan da zamansu a wajen har suka kammala breakfast ɗinsu Ammar da Hibbah suka kwashe kayan zuwa kitchen. A gurguje suka wanke kwanikan ita da shi su ka fito dauke da basket ɗin abincin da suka shiryama Ummi irin wanda doctor da suka kira ya tabbatar musu zata iya ci tunda ta farfado tun daren jiyan.
Har yanzu Abba da Hajiya Mama na a sashen suna zubda ruwan tujara. Yayinda kuma babu wanda yay musu koda tari. Hakanne ya sake harzuƙa musu zukata da wanann sabon salon rainin wayon su Yaya Muhammad ɗin. A gabansu kuma suka kulle kowanne ƙofar ɗaki da ke a sashen har kitchen sukai ficewarsu suka barsu a falo. Wannan al'amari yayi matuƙar bakanta ran Abba da Hajiya mama. Kai har ma Momy da ƴaƴanta mata huɗu da duk suka fito saboda hargowar su Abban.
Motar Yaya Muhammad da Yaya Abubakar duk suka shiga yau ma suka fice batare da kowannensu ya hau mashin ba.
Bayan fitarsu tujara ta gidan duniya babu irin wadda Abba da hajiya mama basuyiba a gidan. Ummi ta sha gori da tonon sililin asalinta. Sai da sukayi mai isarsu sukaga babu mai taya musu Sannan sukai shiru. Abba ya shirya fagan-fagan yabar gidan zuwa inda zuciyarsa ke raya masa domin yin maganinsu Yaya Muhammad ɗin baki ɗaya.............✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_Chapter Twelve_*
..............Oho su bama su san sunai ba. Dan koda suka fice a gidan babu wanda yay koda ambatar sunansu Abba ne balle su nuna sun damu da al'amarinsu. Asibiti suka nufa kansu tsaye. Inda sukai tozali da sanyin idaniyarsu da ke zaman jiran isowarsu.
Cike da ɗunbin farin ciki duk suka baibayeta kowa na jera mata tambayoyi game da jikinta da yanda takeji kuma. Komai bata iya ce musuba. Sai murmushi da take musu hannun Hibbah da Ammar a cikin nata tana kallon ciwukan jikin Ammar din. Da sauri ya ce,
“Karki damu Ummi naji sauƙi. Kema ALLAH ya baki lafiya ki cigaba da mana tuwon dawarnan naki da bama son ci”.
A tare suka kyaƙyale da dariya, Murmushin Ummi ma ya sake faɗaɗa ta kai hannu ta shafa fuskarsa. Hannun Hibbah ta kamo ta maida saman tata fuskar. “Ummi nice auta ni zaki shafama fuska ba wannan garjejen mutumin ba”.
Ranƙwashi Ammar ya bata akai. Ta dafe kan da sauri tana sakin karamar ƙara. Ammar ya mike da ga inda yake zaune yana mata gwalo.
“Yaya Umar ka ganshi ko?”.
Harar Ammar Yaya Umar yayi. “Kai wai miyasa baka rabo da zalunci ne. Ko wannan rankwashin da kake mata ma ya hana girma ai taita zama kamar ƴar cilikowa tana addabar mutane da ɗaukar magana”.
Dariya duk suka tuntsure da shi baki ɗaya. Ransu fes da farin cikin tashin Umminsu. gashi doctor ma ya sanar musu nan da kwana uku zasu sallameta taje gida ta cigaba da shan magunguna. Dan dama irin aikin nata mai sauƙi ne inhar an dace da yinsa bisa nasara.
Su suka taimakawa Ummin ta tashi suka jingina mata filo. a tare suka haɗu su duka suka ringa bata abinci duk da Hibbah na isarsu da rigima da rinto. Dan a layi aka dinga bi har Ummi tai musu nuni data ƙoshi. Sai da tasha maganinta sannan sukai mata sallama domin tafiya wajen aiki aka bar mata Hibba da Ammar. Dan su sai ƙura ta lafa zasu koma school musamman ma Hibbah.
Kafin su wuce sun biya office ɗin doctor daya bukaci ganinsu. Bayan sun sake gaisuwa da shi da nuna jin daɗinsu akan nasarar jikin na Ummi ya shiga musu bayani akan wani bawan ALLAH yazo ya biya kuɗin aikin Ummi ɗin duka. Dan haka zai dawo musu da nasu kuɗaɗen insha ALLAH.
Cikin mamaki suke tambyarsa wanene hakan?. Ya sanar musu shima dai bai sani ba kai tsaye. Dan ansha irin wannan taimakon batare da sunsan ainahin wanene ba. Amma kuma bayan hakan ma wani ma ya sake bada kaso ɗaya bisa uku na kuɗin aikin harma ya shiga ya duba Ummi. shima kuma dama yakanyi hakan a wasu lokutan. Yasan kuma zasu gansa suma kafin a sallami Ummi ɗin dan ya fahimci a yau kawai kamar har sabo ya shiga tsakaninsa da Ummi ɗin.
Sosai abubuwan suka basu mamaki, amma sai suka watsar da mamakin sukacema doctor a maida musu kuɗin su da kansu insha ALLAH zasu biya kuɗin aikin mahaifiyar tasu basa buƙatar kowa. Cikin nasiha ya nuna musu hakan ba daidai bane. Sam babu ƙyau maida alkairi baya musamman irin wannan. Suma bawai sun biya bane domin sunga sun gaza.
Dole suka hakura suka amsa tare da yin addu'a ga masu biyan. Da ga haka suka fito domin nufar wajen aikinsu........
_________________________________
A ɓangaren yaran master kam, tun suna zuba idon zaman jiran dawowarsa har suka fidda rai. Dan sun fahimci dai yayi nisan kiwo. Badan sun so ba dole suka tashi sukai shirin barci duk suka kwanta kowa ransa da addu'ar ALLAH ya dawo musu da shi lafiya.
Sukan damu idan yay fitar dare. Saboda sunsan shi sam bayasan yawon dare. Ko su duk aikin da zai sakasu inhar magrib tayi ya haƙura kenan. Sai ko idan ya zama dolen dole. Amma da anyi sallar isha'i basa ƙara fita sai ta lalura.
Koda suka tashi sallar asuba ma basuji motsinsa ba, haka sukai alwala suka fita, dan sunsan duk inda massallacin da ya tadasu yake zasu ganosa a layin insha ALLAH. Sai ga shi fitowar tasu ma ta sakasu fahimtar a ina suke. Ashe bayan layin gidan da suka baro jiya ne. Har cikin ransu suna jinjinama boss ɗinsu, saboda matuƙar wayonsa da basirar iya takun rayuwa. Komai babu wanda ya faɗa suka adana a zukatansu har sukaje salla suka dawo. Sanin yace ƙarfe bakwai da rabi zasu bar gidan yasa basu kwanta ba suka tattare abinda suka ɓata.
Suna tsaka da kimtsawar ne kusan 6:43 sai gashi ya dawo. Kallon mamakin ta inda ya shigo suka shiga masa. Dan sudai basuji alamar buɗe ƙofar gidan ba. Hasalima sakata suka saka mata ta ciki, dole ne sai yayi musu knocking sunzo sun buɗe masa.
Sarai ya fahimci ma'anar kallon da suke masa, amma sai ya basar abinsa. Hakan yasa suka shiga gaishesa da masa barka da dawowa bayan Musbahu ya tashi ya amshi bag ɗin hannunsa.
Hannu kawai ya ɗaga musu, kafin ya fara magana a taƙaice yana nuna bag ɗin da ya shigo da ita, “Gaba ɗayanku zakuyi amfani da kayan cikinta ne, dan a wannan gaɓar magana ake ta kuɗin baƙine ango ya kawo ku kwana anan”.
Cikin girmamawa suka shiga amsa masa suna murmushi. Yayinda shi kuma yay shigewarsa ciki. Zaidu ne ya fara kwashewa da dariya yana faɗin, “Abokan ango waye angon to a cikinku?”.
Salis ya nuna kansa yana wani buɗe hannaye irin eh😉😂. Hararsa Habib yay da taɓe baki. “Banza. Kana ɗan yahoo ubanwa zai baka ƴarsa, wataran shima ka yashe masa asusunsa”.
Sanin boss na gidan ya sakasu fara dariya suna tarewa da hannu. Salis da ke harar Habib ya ce, “Da yake ma talle bataima audi gori duk tafiyar ɗaya ce. Ta wani fanninma gwara ni. Kuma tunda kace haka kwanan nan zakaji na zama ango ɗan baƙin ciki yahoo boy”.
Duka Habib ya kaima Salis ɗin ya kauce yana masa gwalo. Rabi'u yace, “Kai kai ku tsaya kuji. Ni fa da boss yay maganar ɗaurin auren nan sai naji inama irin shine za'a ɗaurama auren. ALLAH na ƙagu naga mai tsaurin idon da zatai wuff da master”.
Dungure masa ƙeya Musbahu yayi da saurin cewa, “Wanan saɓon naka banajin zai tabbata a gidan nan. Inko ya tabbata to lallai sai mun yashe asusun tsohonta tas inaga abiya sadaki da kuɗin auren nata”.
Duk yanda sukaso matse dariyarsu hakan ta gagara, tuni suka shiga ƙyalƙyalewa harda masu faɗowa ƙasa da ga kujera. Khalid ne ya fara farga da Master da tun dariyarsu ta farko ya fito. Tsaye yake a jikin ƙofar ya harɗe ƙafafu da hannayensa a ƙirji kawai ya zuba musu idanu. Da sauri Khalid ya zunguri Rabi'u da ke kusa da shi, babu shiri shima ya gimtse tasa dariya yana zungurin Zaid. Shima Zaid da sauri ya haɗiye tasa yana mintsinin kafar Idris da ke kusa da shi. Musbahu da shima idonsa ya kai yay azamar haɗiye tasa yana rarrafawa zai ɓoye bayan kujera. Habib da Salis da basusan anayi ba kam sai ƙara tuntsurawa suke. Salis yace, “Ni why bana tunanin boss zai wani iya soyayya, dan ita tayi yamma shi yayi gabas. Inagama sai munyi karo-karo wajen badashi sadak......”
Da sauri Musbahu ya rufe masa baki. Hannu Salis ya shiga bige masa yana ƙoƙarin yin magana idonsa ya sauka akan Master da har yanzun yake tsaye yana jinsu. Dan ya wani lumshe idanu tamkar wani mai yin barci a wajen.
Babu shiri Salis ya ture Musbahu gefe ya miƙe da gudu ya afka bedroom. Ganin haka suma duk sai suka shiga rufa masa baya. Wani silent numfashi master yaja yana buɗe idanunsa akan ƙofar ɗakin da suka shigan harda rufo ƙofa. Uffan bai ceba ya juya ya koma cikin ɗakinsa.
Koda suka kammala shirin cikin ɗanyun shaddoji iri ɗaya kalar sararin samaniya suka fito, kasa haɗa ido da shi sukayi. Sai satar kallonsa sukeyi ta ƙasan ido, yayinda dariya ke cin ransu a ƙasan zuciya dan shi tashi shigar ta irin marasa jin direbobin nan ce yayi. Da alama da kansa zai tukasu a mota kenan tsabar iya taku. Gaba yay batare da yayi magana ba duk suka rufa masa baya suna ƙoƙarin gimtse dariyarsu.
Motar bus da zata iya kwashesu ce a waje a fake master nata faman gogewa kai kace driver ɗinne na gaskiya irin wanda suke zuba iya shege a tafa zuwa agege da maraban jos. Dan facemark ɗin dake fuskarsa bata da maraba da ta direbobin da ke tsaka da cin duniya da allura.
Da kansa ya buɗe musu motar yana harararsu dan ganin kallon da suke masa a munafunce suna murmushi. Sai da suka gama shiga ya rufe yana zagayawa mazaunin driver bayan ya dagama matasan dake zaune a wajen mai shayi anata fira akan abinda ya faru jiya na mayar gwamna hannu. Sai zabga gaddama suke kowa na kare abin son sa. Wasu Master, wasu jami'an tsaro, wasu matar gwamna ɗin. Yayinda wasu ke faman zuba ashariya kai kace faɗa ne ya tashi.
Murmushi ya saki yana shigewa a motar saboda jin furicin wani da ke faɗin, “Suma jami'an tsaron lusarai ne da zasu zauna mutum ɗaya ya gagaresu. Kawai dai sunyi niyyar barin shegenne kafin suyi ma rayuwarsa walmakalifatu”
“To ka sani ko aljanine?”.
Wani ya bashi amsa dai-dai master na reverse da motar. Hannu suka ɗago musu wasu na faɗin ALLAH ya sanya alkairi. Dan sun yarda su ɗaurin auren za'aje😂😝.
Lallai maganar yaran master gaskiya ne. Wannan gida yaji kayan ƙawa da more rayuwa. Shi kansa yana matuƙar son gidan. Dan a cikinsa ne kawai yafi sakewa sosai. Sanann anan ne kawai yake zama da yaransa. Amma duk sauran gidajen ba kullum yake kwana tare da su ba sai yaso.
*_BAYAN KWANAKI UKU_*
Alhamdulillahi jikin Ummi yayi ƙyau sosai, dan tattali iya tattali take samu da ga iyalanta sanyin idaniyarta. Yayinda wasu a cikin ƴan uwa ke tururwar zuwa dubata da jiki.
Hibba ce take kwana tare da ita, su kuma su yaya Muhammad da sun taso aiki anan suke tarewa har sai 11 suke wucewa gida. Har zuwa yanzun Abba bai dawo ba da ga tafiyar da yay randa akaima Ummi ai. Itama hajiya mama taɗan lafa da fitinarta saboda ƙafarta data motsa, duk da dai su su yaya Abubakar ɗin sunsan wani abun suke ƙullawa basu nuna sun damu ba.
Junaid ma ya dawo gida bayan kwana biyu da yayi a asibiti. Sai dai kuma tunda ya dawo ɗin ko ƙeyarsa basu gani ba, sai sauran ƴammatan gidan marasa kunya. Su kuma ko kallo basu ishesu ba. Dan a cikinsu wai sonsu su Yaya Abubakar ɗin sukeyi.
Tuni shaƙuwa ta shiga tsakanin Ummi da mutum nan da ya biya kuɗin aikinta kaso ɗaya bisa uku. Dan kamar yanda yaranta ke jurar zuwa kullum safiya dubata haka shima yake zuwa dubata duk safiya. Da rana kuma ya aiko da abinci a kawo mata. Da dare idan ya tashi kasuwa ya shigo da fruits ya sake gaisheta sannan ya wuce. Haka zataita saka masa albarka da masa fatan alkairi akan kasuwancinsa da ya sanar mata yanayi, tare da ma mahaifiyarsa da yace ta rasu addu'a, da mahaifinsa da ke raye.
Addu'ar da take masa ke sakashi jin daɗi. Da kuma yanda su Yaya Umar suka sake da shi sosai tamkar shima ɗan uwansu ne. Hibbah ce dai da ga gaisuwa bata sake kulashi dan dama ita haka take tana da wahalar sabo duk da rawar kanta. Idan kaga ta sake to tare take da Umminta ko yayunta. Su kaɗaine takema yanda taso.
Yau ma suna tsaka da tattare kaya dan an sallamesu Ummi zataje ta cigaba da shan magani a gida yay sallama. Sai da Ummi ta amsa da bashi izinin shigowa sanann ya shigo. Hibbah da ke haɗa kayan ko ɗagowa batai ba balle ta nuna tasan da zamansa. Shima kallo ɗaya yay mata ya dauke kansa. Dan har cikin ransa kallon miskila yake mata tunda ba yarda take tai magana a gabansa ba. Ko surutu take da ya shigo take gimtse bakinta.
Cike da girmamawa ya gaida Ummi da tambayar ta yaya jikinta?. Fuskarta faɗaɗe da murmushi tace, “Alhmdllh yaro na. Ykk ya Abban naka shima?”.
“Lafiya lau ya ke Ummi, yana ma gaisheki da baki haƙurin rashin zuwansa saboda shima yana ɗan fama da ƙafa ne”.
“ALLAH sarki babu damuwa ai. ALLAH shima ya bashi lafiya yasa kaffara ne. Yaya iyali ko babu kaima kamar ƴan uwan naka?”.
Murmushi yayi yana duƙar da kansa ƙasa da kai hannu ya shafi wuyansa zuwa ƙeya. “Ku mana addu'a dai Ummi, ALLAH ya bamu nagari”.
“To amin. Amma ni bansan mi kukema hange-hangen ba sam. Mutum bazai yi aure da ƙuruciyarsa ba kamar yanda iyayenmu sukai mana sai ya gama tsofewa. Ni ban sani ba ko tsoron matan kuke ji ne wai?”.
Murmushin sa ne ya sake faɗaɗa sosai yana faɗin, “Ummi tsoro kuma? Kawai dai matan ne sai a hankali, sai ka dage wajen zaƙulo mai tarbiyya gudun dana sani”.
“Da kuma wanan dan wanan. ALLAH ya baku na gari to”.
“Amin Ummi mun gode”.
Yay maganar yana duban Hibbah. Da sauri tace, “Ina yini”. Yanda tai ɗin ma harya so bashi dariya. Fuskarsa ɗauke da murmushi yace, “Autar mu ykk ya ƙoƙarin kula mana da Ummi?”.
A ranta tace, (Kaji ɗan iya). A fili kam sai tace, “Alhmdllhi Yaya Isma'il. Ya Abba?”.
“Abba yana lafiya, yana ma gaishe ki”.
Murmushi kawai tai batare da ta sake cewa komai ba. Shima sai ya mike kawai yana faɗin, “Ummi bara naje waje idan kun gama shiryawa sai mu wuce”.
Zaram Hibbah tace, “Ai ga Yaya Ammar nan zaizo ya maidamu gida a motar Yaya Muhammad. Dama kaje abinka mun gode”.
Ɗan kallonta yayi na wasu sakanni. “Oh auta, kodai bakison naima Ummi rakkiya na samu lada ne?”.
Baki ta tura gaba ta dauke kanta batare data amsashi ba.
Ummi tai murmushi da faɗin, “Kaga manta da ita Isma'il. Tunda kazo ka kaimu kawai shi Ammar ɗin bara na kirasa basai ya amso motarba ma”.
Godiya yay mata yana ficewa. Hibbah kuma ta hau ƙunkunin ita batason motarsa ya cika shishshigi. Ummi na jinta amma tai mata banza. Sai ma ƙoƙarin kiran Ammar da takeyi a waya akan ya dawo basai ya amso motar ba ga Isma'il yazo.
Badan Hibbah taso ba Isma'il ya kaisu har gida. Sai dai bai shigaba iyakarsa waje ya juya duk da Ummi tace ya shiga. Haƙuri ya bata akan yana sauri ne zai koma kasuwa.
Albarka sosai Ummi ta saka masa. Hakama Ammar yayta masa godiya. Hibbah kam dama tuni ta shigewarta cikin gida. Sai Ammar ne ya kama Ummi suka shiga cikin suma. Babu motsin kowa a gidan da alama yaran duk sun fice. Hajiya mama kuma maybe tana barci ko kallon nata na masifa dan bata gajiya da sanya ido a television, shiyyasa jikokin nata har tsiya suke mata akan hakan.
Ko mintuna ashirin basuyi da shigowa ba maƙwafta suka fara shigowa ƙara yima Ummi sannu. Ciki harda Zahidah da Hafsat tare da iyayensu. Sune suka taimakawa Hibbah wajen gyara gidan tsaf. Suka kuma daura girki. A kitchen ɗinne suka sami damar mata tambayar abinda ya faru ranar game da tafiya da ita da ƴan sanda sukayi.
Duk da aminanta ne tun ƙuruciya sai bata faɗa musu komai ba yanda ya faru saboda tuno gargaɗi da akai mata akan idan ta fitar da zancen za'a saka mata ƴan uwa a tarko. Ta dai basu labarin iya abinda zata iya. Sosai sukaji takaici har cikin ransu. Nan fa suka shiga labarin rauni da hukumomin tsaron ƙasar nan suke da shi.
Zahidah tace, “A kullum ca ake ana aiki amma babu alamar hakan a ƙasa. Shin laifin gwamnati ne ko na jami'an tsaron?.”
Cikin taɓe baki Hibbah ta amshe da faɗin, “Kema dai ƙya faɗa Zahidah. Ita kullum gwamnati tana faɗar kuɗaɗe da take warewa domin harkar tsaro. Amma su jami'an tsaron kullum ca suke basu da kayan aiki isassu. To wai kuɗinne ba'a warewa? Kokuwa jami'anne basa saye? kasa kuɗin suke a tebir kowa ya dauka kasonsa?”.
Da tsantsar takaici Hafsat tace, “Duk ma yanda sukeyi ɗin ai akwai ranar tonon asiri. Ranar da babu wani gacci ko mayafi da ya isa lulluɓe tsiyar da aka shuka aka binne. Ranar da za'ai walƙiya muga kowa da ayyukansa”.
A tare Zahidah da Hibbah sukace, (Insha allahu kuwa).
Haka dai suka cigaba da tattauna abubuwa da dama har suka kammala girkin suka sake gyara Kitchen ɗin. Koda suka fito ɗakin Hibbah suka wuce dan har yanzu ƴan dubiya nata shigowa. Sai dai bayan maigadi ko karen da ke a cikin gidan har yanzu bai leƙo ba. Dama kuma basuje asibitinba. A cewarsu ai ba'a sanar musu bata da lafiya ba.
Sai dare samarin na Ummi suka dawo. zuwa lokacin sashen tsit da ga Ummi sai Hibbah kawai. Hibbah ma tayi barci a kujera dan akwai gajiyar asibiti tare da ita. Sai sautin kiɗa dake tashi da ga sashen momynsu Junaid da hayaniyar ƴammatanta. Da alama wani fati sukeyi, duk da dai shan kiɗa a gidan ba sabon abu bane ba dama.
Sannu Ummi tai musu. Yayinda suka zagayeta kowa nason jin yaya karfin jikinta?. Cike da jin daɗi da fara'a take amsa musu. Kafin tace suje suci abinci kar yayi sanyi. Ammar zai tada Hibbah Ummi ta hanashi.
“ALLAH ka tada ita sai naci gidanku, ka barmin yarinya ta huta ta gaji wlhy, dan tamace kanta ke ciwo”.
“ALLAH yasa gaskiya ne Ummi. Ni naga a kwanaki ukun nan wani sabon hankali take ji da shi. Ko ciwonki ne ya sata nutsuwa oho”. Ammar ya faɗa yana dariya.
Suma su Yaya Muhammad duk murmushi sukayi suna nufar dining.
★★★
Har washe gari babu wanda yazo ya duba Ummi a cikinsu hajiya Mama. Abba dama bai dawoba har yanzun. Ummi ko a fuska bata nuna ta damuba. Haka suma su Yaya Abubakar babu wanda yace uffan akan hakan. Sai ma tarkata Hibbah sukai ta wuce islamiyya tun safe kasancewar yau ɗin weekend ce akwai tahfiz da take zuwa dama har suma kansu.
Badan taso zuwan ba ta tafi harda ƙwallanta dan taga abokin hamayyarta Ammar yau bazai je ba. Da yake a kafane babu nisa ita kaɗai ta fita. Sai da ta fitane taci karo da Hafsat da Zahidah sun taho biyo mata dama. Gaisawa sukai da tambayar jikin Ummi sannan suka wuce islamiyyar.
Islamiyya ce babba matuƙa. Dan tun da ga ƴan shekara uku har zuwa saba'in duk zasu iya karatu a cikinta. sai dai su yara da ga shekara uku zuwa ashirin da biyar suna zuwa ne tun safe har yamma. Daga ashin da shidda zuwa har tsoffi suna zuwa bayan sallar azhar har magriba, kuma iya weekend ne kawai. Dan haka su su Yaya Muhammad sai karfe biyu zasuje. Itace dai da Ammar dama ke tafiya tun safe. Ammar kuma yau akwai abinda zaiyi shiyyasa bazai je ba.
Kamar kowanne sati yau ma sun ɗauki darasi daban-daban har zuwa ƙarfe biyar na yamma da aka tashe su. A ƙafa suka taho Zahidah da Hafsat nata hira banda Hibbah. A yanda suka lura gaba ɗaya ta zama wata shiru-shiru. Kafin faruwar wannan al'amarin a kowane sati sukaje islamiyya sai ta addabi kowa a ajin ko ta takalo faɗa. Su kansu malam sun buga har sun bari, dan mafi yawancin lokaci ƙoƙarin ta ne ke cetonta akan wani tsiyar idan ta tafka.
Cike da jin haushi Hibbah ta ja tsoki tana tsayawa cak da ga tafiyar da sukeyi. Kallonta Zahidah da Hafsat sukai cikin alamun sonjin lafiya?. Bata tanka musu ba, sai kallonta da ta maida kan motar da ke bin bayansu ta gefen titi tunda suka fito Islamiyyar. Suma su Hafsar ɗin sun lura tun ɗazun, sai dai basu kawo a ransu mai motar su yake bi ba. Musamman da ya kasance ya ɗan basu tazara.
Domin tabbatar da su ɗin yake bi a bayyane yay fakin dai-dai inda Hibbah da ta cika tai fam da takaicinsa take.
Cikin takun nutsuwa da cikar haiba ga ma'abocin kallo ƙyaƙyƙyawan saurayi mai tarin kamala ya sanyo kafarsa ƙasa dai-dai yana buɗe ƙofar motar mai baƙin gilashi (tinted glass). Wani shegen ƙamshin turarensa ne ya daki hancunansu tare da sallamar da ke fita cikin ƙasaitacciyar muryarsa mai tarin nutsuwa da sanyi.................✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻
*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*
_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawa nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki._
*_Muna da haɗin_*
_Turaren wutane_
_Humrh_
_Kulacham_
_Turaren wanka_
_Turaren Kaya_
_Gyaran jiki_
_Na amare_
_Da masu jego_
_Da sabulai masu gyara fata_
*_Da magungun nan mata_*
_Irin su kaza_
_Tantabara_
_Tsumi_
_Gumba_
_Zuma_
*_Duka akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*
Wushishi road KADUNA
08067807620
09057713999
_________________________
*_Chapter Thirteen_*
............Gaba ɗaya jin su Hibba ya ɗauke ɗaf a cikin kunnuwansu lokaci guda. Dukansu sun zuba masa ido tamkar waɗanda sukai gamo da wata baƙuwar hallita. Namiji ne tsayayye da za'a iya kiransa namijin gaske a kowacce irin nahiya ko ƙabila. Sanye yake cikin shadda oxblood da ta fidda ainahin kalar fatarsa mai sheƙi. Fuskarsa cike take da ƙasunba da wani madaidaicin gemu mai kama da na gayu irin na ustazan wanan ƙarnin (😳Bily🤐).
A kallo ɗaya zaka fahimci rashin son hayaniya daga garesa. Da alama kuma ba mutum bane mai yawan sakewar fuska a mu'amula ko a yanayi.
Ganin sun shagala wajen kalon sa ya saki wani shegen murmushi yana ƙarasa takowa gaban Hibbah gab. Haka kawai takaici ya kama Hibbah da kallo guda tai masa ta ɗauke kanta tun ɗazun. Cikin ɓata fuska da yatsineta ta ce, “Malam lafiya? Tun ɗazun ka ke ta binmu sai kace wani mai gadin mu”.
Murmushi ya kuma saki, jerarrun haƙoransa farare na bayyana. Ƙoƙarin saka ƙwayar idanunsa cikin nata yake, amma sai taƙi. Sai ma harara da ta sake zuba masa ta ɗauke kai. A hankali taja siririn tsakin da yasa Hafsat da Zahidah shurin ƙafarta da galla mata tagwayen mintsini.
“ALLAH ya isa”. Ta faɗi tana hararsu bayan ta saki ƴar siririyar ƙarar data saka baƙon nasu ƙyalƙyalewa da wata dariyarsa da ke fita a nutse. Harara ta sake zuba masa zata bar wajen yay saurin shan gabanta.
Haushi ya sake kama Hibba. A tsiwace tace, “Malam kana shigarmin hanci fa”
“Ba malam ɗin bane ai. *_Muhammad Shuraim Aliyu_* ne. Idan kina son nabar shiga hancinki address da number kawai nake buƙata”.
“Baka da man kai” ta faɗa tana raɓawa ta gefensa ta wuce batare da ya samu koda harar ba yanzun. Badan Zahidah da Hafsat sun so ba sukace masa (bye) suna bin bayanta. Motarsa yay azamar komawa ya cigaba da binsu duk da uban sauri da Hibbah ke zabgawa tamkar zataci da ka. Jitake a ranta da da akwai lungunan da zatabi ya kaita gidansu da shi zatabi dan taga ƙarshen naci. Sai dai kash, tun daga islamiyyar har zuwa gidansu layine ɗoɗar.
Itace ta fara shigewa gidansu, dan ata wannan hannun itace farko kafin su Hafsat. Dan haka mai mota Shuraim ya tsayar da su Zahidah. Dole suka tsaya dan baiyi kama da wanda za'a cigaba da yarfatawa ba.
“Kuyi haƙuri fa na takura muku, naga mahaɗi nane babu damar yin sakaci. Dan ALLAH miye sunan ƙawarku?.”
Kallon juna Hafsat da Zahidah sukayi. Roƙonsu da ya sake yi ne ya saka Hafsat cewa, “Muhibbat! Aliyu Hamza”.
“Masha ALLAH, nice name. Nan ne gidansu?”.
A taƙaice suka bashi amsa da eh. Shima sai bai sake jan zancen ba yay musu godiya ya koma motarsa ya wuce.
“Gaskiya Hibbah ƴar yawa ce, amma fa guy ɗin nan ya haɗu ALLAH. Yaci sunansa Muhammad Shuraim”. Zahidah ta faɗa tana lumshe ido.
Hafsat tace, “Shiyyasa ai na faɗa masa sunanta. Waya gaya mata ana sakaci da irin waɗan nan gayun a wanan ƙarnin.”
“Barta ai zamuyi maganinta. ALLAH dai yasa har a hallaya haka yake, da kuma zancen aure yazo mu raƙwashe. Dan zanso Hibbah ta auri guy ɗin nan kodan ta kere sa'a a cikin shaggun su Amlah ɗin gidansun can. Masu shegen kakkafi da son asani. Su adole suna hawa motoci. ALLAH idan suka ga guy ɗin nan sai sun haukace. Sai dai kuma ya musu nisa da na Hibbarmu ne”.
“Insha ALLAH”. Cewar Hafsat tana ƙyalƙyala dariyar mugunta. dan harta hango idon ƴan gidan su Hibbah da kullum suke mata iyayi akan su sun waye, sun girmeta. Suna hawa motocin da Abbansu ya saya musu su ƴaƴan so banda Hibbah.
★_____________★____________★
A ɓangaren Master kam tunda suka koma L.E street shida yaransa sukai luf abinsu tamkar basa ƙasar. Da wannan damar jami'an tsaro suka sami na barazanar cewar ya tsorata da harin da suka kai masa ne, ƙilama sun sami nasarar kashesa dan sun harbesa.
A lokacin da yaga wannan rahoto ba ƙaramin dariya abin ya bashi ba ƙwarai da gaske, ya saki wani malalacin mmurmushi mai ƙunshe da ma'anoni masu yawan gaske da shi ya barma kansa saninsu. Har cikin ransa yana mamakin sai yaushe ne ƙasarmu ta gado zata canja ne? Ji dai shareriyar ƙarya da wanɗan da suke amsa sunan iyaye manyan ƙasa suka karkace suka gilla dan kawai su burge su kuma kankaro ma kansu girma.
Yaransa kansu abin ya basu dariya. Har cikin ransu suna tausayin ranar da Master ɗinsu zai maida murtani ga waɗan nan mutanen. Inhar bai kaisu kwance ba tabbas sai ya sakasu kuka da hawayensu ko su ajiye aikin koda lokacin ritaya ɗinsu baiyi ba.
Shi ba'a sakashi yin abu dole, dan haka baice uffanba sai ma sake lafewa da yay domin tabbatar da zancen nasu. Yayinda a gefe kuma idanunsa ƙur akan batun matar gwamna da hukumar sa'ido akan ta'annati da kayan gwamnati take bin cika har yanzun. Jira suke suyi wani sakaci ko kaɗanne ya sake bankaɗo wasu surukan nata ma duniya harma da su kansu...
____________★__★__★___________
“K kuma lafiya kika shigo kina cikama mutane baki da iska?”. Ummi ta faɗa tana kallon Hibbah da dawowarta kenan da ga islamiyya.
“Babu komai Ummi. ALLAH yunwa nake ji ne”.
“Shi abincin da kika tafi da shi fa?”.
“Ummi naci fa. Kawai wata yunwar dai nake sake ji”.
“To ALLAH ya ƙyauta, sai kije ki fara yin wanka kiyi salla sannan kizo kici”.
“Ummi dan ALLAH ki barni in fara ci ni dai”.
Komai Ummi bata sake ce mataba. Sai ma miƙewa tai ta shiga takawa a hankali domin zuwa ɗakinta tai salla. Dan har yanzu jikin nata bawai yayi ƙarfi yanda ya kamata bane. Abincin ma Yaya Usman ne ya yisa kafin su wuce tasu Islamiyyar.
Sai da Hibbah taci tai nak da abinci sannan ta shige ɗakinta. Bata fito ba sai wajen 8:30 da tajiyo hayaniyar yayunta. Cike da ɗokin dawowar tasu ta fito. sai dai ganin harda Isma'il ya sata yin turus.
Komai babu wanda ya ce mata a akan yanayin nata. Sai ma tsokanarta faɗa da Ammar ya shigayi. Amma sai bata tayashi sunyi ba. Masifa ma taketa faman yi a ranta na yanda yayun nata suka sakema Isma'il ɗin kai kace ɗan gidan ne. Shi kansa yanda yake komai kansa tsaye sai ka rantse gidansu ne.
Bata wani jimaba tai musu sai da safe ta shige, ta barsu a falon suna kallon ball suna hira da cin abinci. Ummi ma tunda ta leƙo suka gaisa da Isma'il ɗin ta koma ciki abinta. Dan haka Hibbah bata san sanda Isma'il yabar gidan ba.
Washe gari dai an tafi islamiyya babu fushi. Sai dai kuma damuwar ƴan sandan can da ke damunta har yanzu ya sakata komawa wata silent kwana biyun nan. Ko magana ma bata cika sakin jiki tayi ba. Sannan har yanzu bata sake hawa computer ba. Dama wayarta tunda ta dawo take a kashe taƙi ta kunna.
Yau ma suna fara tafiya a kan hanyarsu ta zuwa islamiyya ta fahimci ana binsu a baya. Wani takaici ne ya turnuƙe ta dan tsaf ta gane guy ɗin jiya ne da tun a ƙofar gate ta watsar da lamarinsa. Ba kuma ta sake tunawa da shi ba sai yanzu da taga motarsa. Sam Zahidah da Hafsat su basu lura da shi ba. Hakan yasa Hibbah fuskewa batace komai ba har suka shige cikin islamiyya.
Ƙarfe biyar suka ta shi yau ma tamkar kowane weekend. Da ga nan kuma sai wani satin. Gaba ɗaya ta sake watsar da lamarin wani Shuraim. Amma a mamakinta sai gashi ta sake ganin yana biye da su har gida. Kamar da safe yanzu ma bai yunƙurin fitowa ba. A yanzu kam su Zahidah sun ganshi. Koda sukaima Hibbah magana sai tai musu tsaki ma.
Ƙyaleta sukai ganin shima bai fito a motar ba.
★★
Duk yanda Hibbah taso watsar da lamarin Shuraim sai hakan bai yuwu ba yau. Dan lokaci-lokaci yakan faɗo mata a rai. Sai dai takan ja tsaki da murguɗa baki tamkar tana a gabansa. Har takai abinda takeyi ɗin ya bama Ummi haushi ta balbaleta da faɗa har su Yaya Muhammad suka shigo.
Sune suka bama Ummin haƙuri da fara tambayar Hibbah cikin lallashi ko wani abu ke damunta ne?. Sam batasan wani boye-ɓoye ba. Musamman ma awajen yayunta da suke da matukar shaƙuwa da juna. Kanta tsaye ta shiga basu labarin abinda takema tsakin.
“Woow, ƴar Tanee ɗin Ummi anyi saurayi Congratulations. Yau ɗaya a tarihi dole na rubuta na ajiye na haɗa da shagalin barbaje kolin fati na musamman a gidan nan nayi suriki a matsayina na yaya mai lasisin cin gadon Muhibbat Aliyu Hamza (Tanee)”. Ammar ya faɗa yana tafa hannaye cike da tsokana. Filo Yaya Abubakar ya ɗauka ya jefe sa da shi. Dariya gaba ɗayansu suka kwashe da shi saboda yanda Ammar ya baje a ƙasa da bata fuska alamar yaji zafi..
Hibbah kam dariya sosai take masa harda faɗowa saman kujera. Ta saka yatsun hannunta a kunne tana masa gwalo kamar yanda yara keyi. Filon da aka jefesa da shi ya ɗauka zai jefo mata ta tashi da gudu tai hanyar ɗakinta.
“Ummi kanta sai da tai dariya. Cikin dariyar ne ta ce, “ALLAH dai ya shirye ku, kai da Tanee ɗin bansan wanda yafi wani shashanci ba. Ni tashi ka ɗakkomin magunguna na a ɗaki tunda ita ta gudu nasan ba sake dawowa zatai ba kuma”.
Amsawa Ammar yayi da to yana mikewa ya nufi ɗakin Ummin. A dai-dai kuma wanann lokacin Abba da hajiya mama da wasu tsoffin maza biyu suka shigo falon da sallama.
Da ga Ummi har yaranta da mamaki suke kallonsu, musamman ma Abba da basusan ya dawo gidan ba. Tsoffin kuma Ummi ce kawai ta sansu. Da ƙyar ta iya buɗe baki cikin ƙarfin hali ta ce, “Kawu sannunku da zuwa”.
Farin ne kawai yace, “Uhumm”. Ɗaya kam bai tanka ba. Sai dai bin su Yaya Muhammad da yake da kallo tamkar idanunsa zasu faɗo ƙasa.
Yaya Muhammad da ya lura da kallon ƙurullar da kuma yanayin da Ummi ta shiga tamkar na ruɗani ya saka shi fara gaishesu. Haka yasa suma sauran ƙannensa fara gaisuwar.
Amsa musu sukai suna cigaba da kallonsu. Yayinda hajiya mama keta faman ƙyaɓe baki. Abba kam sai wani harare-harare yakeyi.
Ummi tai ƙasa da kai cike da ladabi ta hau gaishesu itama. Basu wani amsa mata da ƙyau ba. Sai ma baƙin tsohon ne a kausashe ya ce, “Uh lallai Asiya an samu guri kam tabbas. Ga manyan sojoji kuma a gefe masu tare miki faɗa. Dama irin wanan ai ake gudu akan auren masu asali irin naki. Saboda shi hali naso yakeyi har jikokin bayan-baya. Gashi ko mun gani yau da idanun mu”.
Idanu Ummi ta lumshe a hankali kanta a ƙasa. Wasu zafafan hawaye suka silalo saman kumatunta. Sai dai cikin dabara ta kai hannu ta share dan kar ƴaƴanta su gani. Cikin dauriya da juriyar da kowa ya santa da shi ta ɗago murmushi a saman fuskarta. “Kawu ina fatan kunzo lafiya?”. Ta faɗa domin son kauda wancam zancen da ya fara.
Sai dai sam bataci nasara ba. Dan kuwa hajiya mama ce ta amshe da faɗin, “Ni ko zan faɗa maka hali naso yake Hannafi, dan kuwa gashi nan a zuri'a ta. Wlhy badan jinin ɗan inna (babansu Hibbah) na yawo jikin waɗan man yaran ba da tuni na daɗe da sallama su, babu wanda ya cuceni sai malam da ya ƙarrafa wannan auren da har na mutu bazan taɓa daina kuka da ALLAH wadai a kansa ba. Wai fa kuga waɗan nan sanƙama-sanƙaman yaran ne babu mai ko neman aure. Kuma uwarsu ta zuba musu ido saboda ita ɗin bata hanyar.......”
“Waɗan nan kuma fa? Da ga ina?”. Cewar Ammar da ya fito da ga ɗakin Ummi yaci karo da abinda bai bari ba. Furucinsa kuma ne ya katse zancen da Hajiya mama ta ɗakko tiryan-tiryan.
Babu wanda ya bashi amsa. Sai zuba masa ido da tsoffin sukai tare da Abba. Baki ya buɗe zai sake magana Ummi ta girgiza masa kanta. Kansa ya ɗauke kawai tare da durƙusawa gabanta ya na ajiye ɗan basket ɗin da magungunan nata ke a ciki. Ɓalla mata ya shigayi yana miƙa mata tare da saka mata ruwa akan baki.
Wani uban salllami farin tsohon nan ya shiga jerawa yana tafa hannaye. “Kai mizan gani haka ni Ballo (Bello😂). Wannan wane irin kafurcine kuma haka Hasiya?. Wannan ƙurmisheshen gardin ɗan ke baki ruwa a baki kuma?. A to lallai zancen Hannafi gaskiya ne. Da alama ma ke kinfi uwar taki iya shege”.
A fusace Yaya Umar ya miƙe zai bar falon. Abba ya katsesa a gadarance da faɗin, “To mara mutunci da baiyi gadon arziki ba sai ka tsaya dan zuwan nakune ai”.
Ido Yaya Umar ya rimtse da ƙarfi yana dunƙule hannunsa.
“Kai fitsararre, idan shi ka rainashi ai mu ka ɗaga mana ƙafa kodan rashin saninmu da kai ko.”
Ƙafa Yaya Umar ya ɗaga zai cigaba da tafiya wasu hawaye masu zafin gaske na gangaroma kumatunsa.
“Dawo ka zauna”. Umarni da ga Ummi ya hanashi ajiye kafar da ya ɗaga ɗin.
“Iyeee! A lallai Haƙilu kuna ganin jalalar rayuwa. Wato itace kawai mai sawa da hanawa akan ƴaƴan, bayan wahalar da kaci na kula da su tsahon shekaru. Tabbas Hasiya kinyi asara kekam.
Da sauri Ammar ya ɗago ya kallesa. Ya miƙe tare da nuna Kawu Bello da ɗan yatsa cikin kaushi da ɗaci yace, “Kai kaine kai asara tsohon banza ɗan tasha”.
A tare Hajiya mama da Abba da kawu Bello da kawu Hannafi suka zazzaro ido suna zabura. Ummi tai saurin fisgo hannun Ammar tare da daka masa tsawa. “Aliyu!!”.
Cikin ficewar hayyaci ya fisge hannunta a cikin nasa da faɗin, “Haba Ummi, wai sai yau she ne zaki daina zama anacin kashi akanki a gidannan ne? Babu ruwana da alaƙarsu gareki. Na rantse da ALLAH idan tsoho bai gyara kalaman harshensa ba to kafin ya fita a falon nan zan datse harshen kuwa na jefar ƙasa”.
Ɗimmm
Ummi ta sauke ma Ammar dundu. “Ammar kanada hankali kuwa? Miyasa kai bana faɗa maka kaji ne wai?. Kasan waɗan nan ɗin su wanene a wajena? To iyayena ne, ƙannen mahaifiyata ne, tamakar yanda Hajiya mama ta ke uwa a gareni itama. Ka shiga hankalinka kona saɓa maka kaji ko”.
“Amma Umm.....”
Wani kallo da ta masa ya sakashi yin shiru ya haɗiye sauran maganar.
Wata ƴar dariya Abba yayi da faɗin, “Kun gani ko? Hakafa gidan yake kullum kamar na ƴan tasha. Sun rainani basa ganin mutunci na bale na mama, bayan ma yaƙi nai da zuciyata wajen rufa mata asiri. To uwar tasu ma ba wai raga mata sukeyi ba. Dan haka na ɗakko ku nan dan ayita ta ƙare. Bazan iya cigaba da ciyar da ƙattan banza ba. Dan haka na yanke shawarar aura musu su Amlah, inba hakaba wataran yankan rago za'a samu sunmin a gidan nan. Ita kuma waccan fitsararriyar uwar ƴan janye-janyen jidalin da suke ɗaurama ƙugu a gidan tana zuba taɓara saboda ita ƴar ido ce Junaid zan aurawa. kunga shikenan anyi tuwona maina ko ba komai sun huta da gori ma asalin uwarsu.”
“Wannan gaskiya ne Haƙilu. Ai kama taimaki rayuwarsu. Dan a zamanin nan kowa yaji tushen zancen ta ina zai basu ƴarsa. Balle ma ita da take ƴa mace. Bayan ma ka riga ka bata Junaidu ɗin ai wlhy da nayima Musa kamu ma”.
Da sauri Abba ya ce, “Shi Musan sai yay haƙuri tunda na riga naima Junaid ɗin alƙawari dai. ALLAH ya bashi ta shi”.
Yaya Muhammad da ya ƙule matuƙa da takaicinsu ya buɗe baki zai yi magana. Amma sai Ummi tai saurin girgiza masa kanta cikin gargaɗi. Kawai sai gani tai hawaye suna sakko masa tsabar zuciyarsa ta kai ƙololuwa a ɓaci.
Ummi itace ke katange dukkan yunƙurinsu, sun rasa miyasa take hakan a gare su game da dangin mahaifin nasu. Abinda ma basu gane ba shine a yau. Shin ta amshi ballagazayen ƴaƴan gidan da ake iƙirarin an basu kenan matsayin matansu ko mi? Koda ace zasuyi haƙuri suyi mata biyayya bazasu taɓa amincewa a aurama Junaid Hibbah ba. Sai dai komi zai faru ya faru wlhy...........✍
*_Tofa masu karatu, yaya kenan? Wanene zai ci nasara tsakanin su Abba da su Yaya Muhammad? Ni kaina inason jin wace ƙaddarace baibaye da Ummi da ta fi bukatar haƙuri da cin kashin waɗan nan mutane haka?. Kumuje zuwa. muna gab da tsunduma cikin wasan gadan-gadan😉👎🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________
*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻
*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*
_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawa nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki._
*_Muna da haɗin_*
_Turaren wutane_
_Humrh_
_Kulacham_
_Turaren wanka_
_Turaren Kaya_
_Gyaran jiki_
_Na amare_
_Da masu jego_
_Da sabulai masu gyara fata_
*_Da magungun nan mata_*
_Irin su kaza_
_Tantabara_
_Tsumi_
_Gumba_
_Zuma_
*_Duka akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*
Wushishi road KADUNA
08067807620
09057713999
_________________________
*_Chapter Fourteen_*
.............A gidan Ummi komai ya canja. Gaba ɗaya ya ranta sun bar walwala. Sun daina fara'a. Sun daina zaman hira, abinci ma kaɗan suke tsakura. Idan tai magana suce sun ƙoshi. Ta ko ina ta gaza gane kansu.
Da farko tayi biris da su, duk da kuwa ta fahimcesu tsaf. Sai dai ganin abin nasu bana ƙare bane sai itama lamarin ya fara damunta. Dan ita kanta sun jefata a cikin kaɗaici. Hatta da Hibbah ƴar karamarsu itama ta ɗauke mata wuta. Saboda wannan abun daya faru ma ta tattara ta koma makaranta duk da Yaya Abubakar ya hanata zuwa da.
Duk da ta ɗan fuskanci ƙalubale a wajen mutane a ranar data koma saboda tafiya da itan da ƴan sanda sukazo sukayi ranar haka ta daurema zuciyarta ta cigaba da zuwa. Bakuma ta sanarma kowa ba. Dan a ganinta da zaman gidan su tana cigaba da ganin Abba da baƙinsa gara kallon da ƴan makarantar zasu mata.
Tunfa Ummi na ɗaukar lamarin nasu wasa sai ƙara girmama ya keyi. Dan kwanakin nan biyu ma basa dawowa gidan sai sun dai-daici tayi barci sannan. Hankalinta sosai ya kuma tashi. Ga damuwar yaranta, ga damuwar auren da aketa ƙulle-ƙullen nana musu na son zuciya. Wanda tsaf ta gama fahimta da gane ina hakan ya dosa. Sarai ta gane manufar Abbah akan son ƙulla auren ƴaƴanta da nashi, manufar kuma duk ɗaya ce tsakaninsa da hajiya mama.
Gaba ɗaya ta rasa ina zata saka kanta taji sanyi, babu uwa babu uba, babu abokin shawara a cikin ƴan uwa, babu wanda zata kaima ƙara ya duba matsalarta ya share kukanta. Gudun abinda zaije ya dawo kuma ke sakata kwaɓar ƴaƴanta akowane lokaci. Bata son abinda zai rabata da su. Bata son a cutar mata da su. Dan sune hope ɗinta, sune murmushin fuskarta. Sune masu share hawayenta da tun tana ƴar ƙanƙanuwarta suke kwaranya a bisa kumatunta. Tasan nuna ƙarfinsu ya kawo kuma zai iya zama sanadin da komai Abba zai iya aikatawa a garesu domin samun cikar burinsa, kuma kamar yanda yasha faɗa koda ya salwantar da rayukansu babu mai yarda shine ya aikata. Wasu hawaye ne masu zafi suka silalo mata saman fuska.
Wata banzar dariya Abba da ke shigowa cikin sashen ya shiga tuntsurawa yana tafa hannaye. Cike da izgili ya dubeta sheƙeƙe yana faɗin, “Kuka kuka kuka! Ai kuwa yanzu kika fara kuka Asiya. Yo ina jarumtar taki ne yau? Shin har kin fara zuwa ƙasa ne tunkan ma a ɗaura auran manufarsa kuma ta tabbata?. Tunda har kikace ni ban isaba Asiya, to wlhy kema bazaki taɓa isa ba. Yau ina wanda kike gadar da shi? Ya tafi tamkarma ba'ayisa ba. Abinda kika hanashi yay mana ta hanyar zagon ƙasa ya dawo hannunmu a lokacin da ko ido baki isa ɗagawa akai ba. To suma ƴaƴa mazan da kike ɗagawar kin haifa masa zasu mamaye komai tafin hannunmu zasu cigaba da zama ballagaza kawai. Zaki iya tashi kuma mu shige ciki dan ina bukatar haƙƙina. Inba hakaba kuma zan ƙwata anan cikin falon babu ruwana....”
Hanyar bedroom ɗinta ya nufa yana gama faɗa alamar ta biyosa. Ummi da ke jin wani ƙullutun abu yazo ya tokare maƙoshinta ta shiga karanto duk addu'ar da tazo mata a saman harshe saboda jin numfashinta na fita a gwagwgwame. A hankali sanyi ya rinƙa shiga cikin ƙashinta, yayin da jikinta ya fara wani irin rawa, har haƙwaranta na haɗuwa waje guda. Hannu takai domin lalubo wayarta da ke saman centre table. Sai dai hakan ya gagara sakamakon gushewar gani da ta risketa a lokaci ƙanƙani. Hannunta ya goce da ga lalube wayar, sai gata ƙasa wanwar da ga saman kujera.....
A dai-dai wannan lokacin Hibbah ta shigo tana masifar bibiyarta da kullum Shuraim keyi babu fashi balle nuna gajiyawa duk da yarfatashin da take yi a kulum. Data fita da ga gida zuwa makaranta yana biye da ita. Hakama idan ta dawo sai ya rakota har gida ta hanyar bibiyarta. Zuwa yanzun tun lamarin nasa na bata mamaki har ya koma takaici da al-ajab. Har tabbayar kanta take shin baida aikinyi ne ko mi?. Wannan takaicin nasane ya sata yau ana saukesu a napep taje tai masa knocking glass. Yana saukewa ta balbalesa da masifa batare data yarda sun haɗa ido ba dan karma yay mata kwarjini. Sai dai abin ALLAH wadai da takaici, harta gama masifar tata ma bai nuna yaji haushi ba. Sai ma murmushin da ya nema rikita mata lissafi ya sakar mata yana wani narkewa a cikin kujera.
Wani uban kara ta ƙwalla tana isa inda Ummi ke kwance wanwar tana wani irin tari dake fita da ƙyar. Kiran sunanta ta shigayi tana girgizata hankali tashe. Sai dai ina Ummi ta fita hayyacinta. Dabarar rarumar wayar Ummin ce tazo mata a rai. Batare data nutsu wajen ganin wanda ta kira ba kawai tai dailing numbern farko, dan tasan su ne dai kawai suke yawan kiran no din Ummin tasu a koda yaushe.
“Yaya dan ALLAH kazo gida, Ummi...Umminmu. Na shiga ukuna. Ummi dan ALLAH ki tashi. Wlhy kika mutu nima mutuwa zanyi. Dan ALLAH Ummi na roƙeki karki mutu. wlhy bazamu sake yin fushi da ke ba. Mun tuba Ummi, mun daina. Mun yarda zamu auresu Ummi.......”
Sambatu taketa faman yi tama manta da waya a kunnenta. Kukanta ya fiddo Abba da ga ɗakin Ummi ɗin wando a hannu. dan harya cire kaya ya baje a gado yana jiran jakarsa ta shigo ya murza a wulaƙance. Ido huɗu sukai da Hibbah da ke sake ƙwala kuka tana kiran Ummi da girgizata. Ai sai ta sake fasa wata ƙarar ganin a yanda ya fito, saboda bai saka wandon dai-dai ba an samu mishkila wajen bayyanar jikinsa.
Sakin Ummi tai ta fita a guje da ga sashen baki ɗaya jikinta na rawa. Tana da yayu maza manya. Amma tunda take da su ko zama da singlet da boxers basu taɓa yi a gabanta ba balle a yanayin da Abban ya fito wanda bata taɓa ganin wani mahaluki a yanayin ba.
Jikinsa ta faɗa dai-dai maigadi ya buɗe masa gate ya shigo, dan Hibbah wayarsa ta kira saboda shine na ƙarahe da ya kira Ummi yaji yaya jikinta? Dan ya kwana biyu baizo gidan ba. Duk yanda yaso ganin ya janyeta a jikin nasa hakan ya gagara, sai sake ruƙunƙumesa takeyi jikinta na rawa, yayinda taketa faman son ɓoye fuskarta a ƙirjinsa duk da tsahon nata gaba ɗaya iya ƙirjin nasa ta tsaya.
Cikin zafi-zafi ya shiga tureta yana girgizata. “K Muhibbat nutsu, muje inga Ummin gani nazo”.
Jin muryar da bata yayunta ba ya sata saurin ja da baya tabar jikinsa. Isma'il da ya samu ta rabu da jikin nasa da sassarfa yay gaba abinsa zuwa sashensu har yana haɗawa da ɗan gudu-gudu. kusan cin karo sukai da Abbah da ya koma ya ɗakko kayansa saboda ihun da Hibbah tayi ya farga da halin da yake a ciki. Duk da ya kuma ga Ummi a yashe a ƙasa sai kawai firgici biyu ya kamashi. Na farko kar wani yazo ya gansa a yanda yake sakamakon ihun Hibbah a zata wani abu yaso mata har Ummi ta shiga halin da take ciki a yanzu. Dan haka ya fito dan ya gudu salin alin, idan Hibbah ta sako sunansa a ciki kuwa yasan ta yanda zai kare kansa ai.
Haka kawai zuciyar Isma'il ta raya masa irin abinda Abban ke gudu. Dan haka yasa ƙafa ya taɗesa sai gashi a ƙasa tim. Takan kafafun Abba yabi da shaggun takalman ƙafarsa, ji kake ƙasss ƙashi na bada sautin karyewa ko tsagewa. Wata iriyar wahalalliyar ƙara Abba ya saki tare da ɗaukewar numfashi na wucin gadi. Ko waiwayensa Isma'il baiyiba ya ida afkawa cikin falon inda ya hango Ummi a ƙasa itama babu alamar rai tattare da ita.
“Ummi!... Ummi! Ummi!!” ya shiga ƙwala mata kira da kama hannunta yana girgizawa. Sai dai babu alamar motsi tare da ita sam. Mikewa yay da sauri ya ciro wayarsa yay kiran Yaya Umar da yasan shine mafi kusanci da gida. Sai dai bai ɗaga ba. Tunawa ana sallar la'asar yanzu haka ya sakashi cije lip ɗinsa na ƙasa ya cusa wayar a aljihu. Batare da tunanin komai ba ya ciccibi Ummi gaba ɗayanta yay waje. Sai lokacin Hibbah ta nufo falon sabida hango abinda Isma'il ɗin yay ma Abba.
“Muje asibiti” yace mata kawai yana nufar hanyar gate. Babu musu ta bisa tana kuka da riƙe hannun Ummi ɗin da ya ɗakko. Sai lokacin kuma Hajiya mama ke fitowa da ga sashensu itama. Ta bisu da wani irin kallo mai ma'anoni da yawa saboda ganin baƙon fuska ɗauke da Ummi ɗin. Dan duk zuwan da Isma'il ɗin keyi gidan ba taɓa haɗuwa sukai ba. Wahalallen ihun da Abba ya saki ne ya fargar da ita halin da yake a ciki, babu shiri ta runtuma a guje kansa tana ƙwala kiran sunansa.......
★★★★_____★_____★★★
Tun kan su ƙarasa asibitin Isma'il yay ƙoƙarin kiran doctor Bilal. Cikin sa'a kuwa ya ɗaga dan mutuminsa ne. Bayani yay masa cewar gasu a hanya tare da mara lafiya su zam cikin shiri. Dr bilal yace babu damuwa sai sunzo.
Cikin mintuna kalilan kuwa suka iso asibitin saboda uban gudu da yake zugawa a hanya. Kamar yanda yay fata sun sami su Dr Bilal na dakon isowarsu. Babu ɓata lokaci aka shiga da Ummi ciki.
Kuka sosai Hibbah keyi da son binsu, badan yaso ba ya riƙo hannunta yana ƙoƙarin dakatar da ita. Sai dai taƙi ta nutsu, dole yay mata yanda yasan zata nutsun, ya jawota jikinsa ya rungume. Da ƙarfi ya rumtse idanunsa zuciyarsa na wani irin bahagon gudu.
Itako Hibbah tuni ta ƙara lafewa tana wani irin kuka mai ban tausayi, dan gaba ɗaya ma ta mance a jikin wa take. Sai da ƴar nutsuwa ta fara zo mata ne sakamakon kiran wayarsa da akayi tai azamar janye jikinta. Komai baiceba shima. Sai ƙoƙarin ciro wayarsa da yay a aljihun wandonsa. Ita kuma ta koma kan kujera ta zauna tana cigaba da kukanta da add'ur ALLAH ya bama Umminsu lafiya.
Yaya Umar da yaga miss call ɗinsa bayan fitowarsu massallaci ne ya kirasa. Dan haka yay masa bayanin da bazai ruɗar da shi ba. Koda ya yanke kiran sai ya shiga kiran sauran suma.
★★
Cikin mintuna kalilan yaran Ummi suka gama hallara a asibitin. Gaba ɗaya hankalinsu a tashe yake. Sai dai sunata ƙoƙarin lallashin Hibbah da ke kuka sosai har yanzu. Harda su amai. Ga zazzaɓi mai zafi ya gama lulluɓeta matuƙa.
Fitowar Dr bilal ya sasu maida hankalinau garesa. Cikin son kawar da damuwarsu yace, “Ku kwantar da hankalinku babu wata matsala mai yawa insha ALLAH. Dan yayi ƙoƙarin kawota asibiti akan lokaci. Sai dai ku kiyaye dan ALLAH kar yazam muna tufƙa ana warwarewa.”
A take nutsuwa ta saukar musu. suka shiga jerama Isma'il godiya tamkar zasu ɗaukesa su goya. Shi dai ransa a dagule yake da takaicin Abbansu, dan shi baisan ba mahaifinsu bane.
Sun cigaba da dakon jiran farkawar Ummi da aka sakama ƙarin ruwa a asibitin har wajen sha biyu na dare da aka basu sallama saboda Alhmdllhi komai normal, amma sai Dr Bilal yace su barta anan ta ƙara hutawa har sai gobe idan ALLAH ya kaimu da yamma. Duk sun gamsu da bayanin nasa. Dan haka sukai masa godiya da fitowa dan su tafi gida Hibbah da zata kwana da ita tare da Nurse tayo musu rakkiya.
Har sannan Isma'il na tare da su. Karan farko a tarihi da Hibbah ta dubesa cike da girmamawa da idanunta kumburarru. “Yaya Isma'il mun gode sosai. ALLAH ya bada ladan zuminci. Yanda ka jikan Ummin mu, kaima ALLAH ya baka ƴaƴa da zasu jiƙanka. Ya ƙarama Abbanka lafiya da tsahon rai mai amfani, ya jiƙan Umma”.
Ba karamin ratsa zuciyarsa addu'ar tata tayi ba. Ya kafeta da ido har sai da Yaya Umar ya zunguresa sannan ya sauke ajiyar numfashi da sakin murmushi. “Nagode sosai auta. ALLAH ya karama Ummi lafiya ya albarkaci rayuwarki. ALLAH ya baki miji na gari”.
Cikin jin daɗi yayunta suka amsa masa da amin. Itama tattausan murmushi da bata taɓa masaba a yanzu ta saki tana juya baya alamar taji kunya da addu'arsa ta ƙarshe. Su Yaya Usman suka ƙyalƙyale da dariya Ammar na tsokanarta. Bata kulashi ba dan yau batajin yin faɗa Ummi bata da lafiya.
Tun a asibitin suka rabu da Isma'il. Shi yay gida suma suka wuce gida. Inda tunkan su shiga sukaji labari a bakin maigadi cewar Abba ma na asibiti. Ya fadi ne a bakin ƙofa da alama yaji ciwo a kafafunsa. Hakama goshinsa da bakinsa sun fashe yanata zubar da jini ma.
Kasancewar da ga Hibbah har Isma'il basuyi musu bayani ba sai basu kawo komai a ransu ba suka ɗauka tsautsyine kawai. Addau'ar samun lafiya sukai masa suka shige. Dan ba'ai musu tarbiyyar son ganin lalacewar wani ba koda ace maƙiyinsu ne.
*________________________________*
A ɓangaren Abba kam da ƙyar aka iya ɗagasa da ga inda Isma'il ya taɗesa. Bakinsa duk ya fashe da goshinsa daya daushi kwalliyar tsitstsigen baranda. Hakama kafafunsa da alamar yayi karaya ko targaɗe. Dan ko takasu baya iyayi ma. Hasalima a sume aka ɗaukesa da ga gidan zuwa asibiti saboda jinin da yayta kwararwa kafin Junaid yazo da mota su fita da shi zuwa asibiti.
Su hajiya mama babu wanda yasan ainahin abinda ya faru da Abban suma. sai dai kansu ya ɗaure matuƙa ganin da ga shi sai boxer kayan da ya fito da su a hannu sabida ihun Hibbah yashe a gefe. Sunma rasa yaya zasu fasalta al'amarin musamman da likita ya tabbatar musu kafarsa ɗaya ta samu karaya da hannunsa. Ɗayar kuma tsagewar ƙashi ce ga ciwon goshinsa dana bakinsa da yay wanu zundun-dun uwa an saki shantu.
Hajiya mama ta hana ai masa gyaran karayar wai sunada mai gyaran gargajiya zaizo da ga kauye. Sai a jirasa yana hanyar tahowa. Tun yamma ake jiran mai gyara har dare ya tsala bai iso ba. Haushin abinda Hajiya mama tai musu su kuma likitocin sunce bazasu taɓa ƙafar ba har sai wanda tace ɗin yazo ya gyara masan. Duk roƙon da Momy taita musu sunce bazasuyiba wlhy.
*_WASHE GARI_*
Da safe acikin su Yaya Abubakar babu wanda yabi takan zancen duba wani Abba. Da dai su Ammar suka kammala yin breakfast suka gyara gida sai suka runguɗa asibiti wajen mahaifiyarsu. Sun isketa zaune Hibbah na shafa mata mai saboda wanka da tayo.
Ta dubesu cike da tausayi da begen ƙishirwar murmushinsu. Duk wanda ya gaidata sai ta kamo hannunsa ta shafa kansa tana ƙoƙarin haɗiye hawayenta.
“Ku daina fushi da Umminku kunji”.
Ta faɗa cikin damuwa da ƙunar da takeji a cikin zuciyarta. Komai basu iya cewa ba sai dai dukansu sunyi ƙasa da kawuna ransu fal tausayinta. Musamman Yaya Muhammad da yasan wani yanki na labarinta batare da itama ta sani ba, shima Abbansu ne ya sanar masa kafin ya rasu. Ya kuma tabbatar masa ya faɗa masane saboda wataran yasan kunnensa zaiji gorin da za'aima mahaifiyarsa kar zuciyarsa ta ɗauki wani abun daban. Shine ya fara jan numfashi da ƙyar da dubanta yana ƙoƙari haɗiye hawayen da suka ciko masa ido.
“Ummi baki mana laifin komai ba. Amma dan ALLAH a wanan gaɓar munason jin wani abu game da ke. badan bamu yarda dake bane. Sai don son sanin minene dalilin da yasa duk basa ƙaunarki?. Mi kikayi musu haka da zafi? Miyasa kika yarda kika auresa bayan shiɗin kanin Abbanmu ne? Mai fuska biyu ga mutane”.
Murmushi ta saki mai kuna da kai hannu ta shafo kan Yaya Muhammad. “Muhammadu Aminullahi zan faɗa muku insha ALLAH. Da zaran munje gida yau zakuji komai”.
A take fuskokinsu suka nuna jin daɗin zancenta. Dan danan suka ɓalle mata hira kamar yanda suka saba a baya. Itako sai murmushi take zuciyarya na kara sanyaya da ɗunbin sonsu da kaunarsu.
Dr bilal ne ya shigo, bayan sun gaisa yace suje waje zasu ɗan ƙara duba Ummin suga ya ya komai na tafiya normal. Sun masa godiya tare da fitowa su duka. Duk anan ƙofar ɗakin suke zaune Hibbah nacin abincin da sukazo da shi. Kamar ance ta ɗaga kai sai idanunta karaf akan Zahidah da Hafsat, Muhammad Shuraim biye da su.
Babu shiri ta miƙe zaram tana rarraba idanuwa. Tunkan su ƙaraso tace, “Lallai ma! Miya kawoka nan?”.
Furucin natane yaja hankalin yayun nata gaba ɗaya. A tare suka sauke idanunsu bisa kan Muhammad Shuraim da ke sanye cikin ado da kamshi na shadda da keta maiƙo, ga hular zanna da ya murza wadda ta kara masa cikar kamala da kwar jini.
A fusace Hibba ta sake buɗe baki zatai magana Yaya Umar ya harareta. Dole tai shiru tana wani mar-mar da idanu akaikaice tana ballama Shuraim harara.
Shiko murmushi ya saki yana matuƙar jin mamakin tsaurin ido irin na Hibbah. Ya cigaba da takowa a hankali zuwa gaban su Yaya Muhammad da duk hankalinsu a kansa yake suna kallonsa cike da nazari. Duk da zasu iya yin sa'anni da Yaya Umar cikin girmamawa ya shiga gaishesu su duka. Gashi yaki yarda ya haɗa idanu da su shi a dole yana gaban surukai.
Hakan ba karamin dariya da burgesu yay ba. Ammar sai wani ƙara buɗe ƙwanji ake su a dole yayu. Yaya Muhammad ya ce, “To sai dai bamu gane baƙon namu ba?”.
Murmushi Shuraim yay cike da ladabi yana ɗan shafar ƙeya yace, “Yayanmu bazaka sanni ba. Dama ina jiran lokaci ne nazo gareku. Sai dai jin Momy babu lafiya yasa nazo dubata kafin hakan. Sunana Muhammad Shuraim Aliyu. Mai fata da addu'ar samun nutsatstsiyar yarinya mai tarbiyya kamar Muhibbat....”
Wata malalaciyar harara Hibba ta zuba masa tamkar zata fashe dan takaici da haushinsa. Yayinda Ammar dake guntse dariya a kaikaice yace, “Dama dai a tarbiyyar ka tsaya dana yadda. Amma ba Nutsuw.....”
Gwiwar hannu Yaya Umar dake gefensa yasa ya bugesa. Yay azamar rumtse ido da ɗaura hannunsa a wajen yana faɗin, “Wayyo Ya Umar zaka kashe ni”.
Yaya Abubakar kam murmushi ya sakarma Shuraim shi da Yaya Muhammad. Haka kawai su dai Shuraim ɗin ya birgesu matuƙa. Dan haka Yaya Abubakar yace, “Masha ALLAH mun gode matuƙa. Bara doctor ta fito sai mu shiga ka dubata”.
Sosai daɗi ya kama Shuraim, ya shiga jera musu godiya da addu'ar samun lafiya ga Ummi. Su ma su Zahidah suka shiga gaishesu da tambayar jikin Ummi ɗin. Hibbah kam taƙi kulasu suma wai haushinsu takeji sun faɗama Shuraim sirrinta.
Suma basu kulata ba dan sun gane manufarta sarai. Haka ta ringa antaya musu harara suna ramawa har Doctor ya fito suka shiga su duka.
Tunda suka shigo Ummi take kallon Shuraim da ya durƙusa har ƙasa ya gaisheta da tambayar jikinta. Fahimtar ƙarin bayani take buƙata yasa Ammar fara rattafo zance. Sosai murmushin fuskar Ummi ya sake faɗaɗa. Dan har cikin ranta taji ƙaunar Shuraim da samun nutsuwa da shi. Tana kuma fata da addu'ar ya zame musu mafita akan haɗa Junaid aure da Hibbah da ake ƙoƙarin ƙullawa.
Basu wani jima sosai ba yace zai wuce, bayan ya ajiyema Ummi ledan dubiya. Godiya suka sake masa Ammar ya tafi rakasa. Yana ƙoƙarin ficewa Isma'il ke ƙoƙarin shigowa. Baya ya koma ya bashi hanya. Batare da tunanin komai ba Ammar ya gabatar da Shuraim ga Isma'il ɗin. Shima Shuraim Ammar ya gabatar masa da Isma'il matsayin ɗan uwansu. Hakan ya basu damar yima juna kallon ido ciikin ido. Da alama kallon da Isma'il yayma Shuraim ɗin na tsantsar kishi ne da shima kansa baisan yayi ba. Haka shima Shuraim kallon alamar tambaya da tsoron sakkiyar da babu ruwa yayma Isma'il ɗin kai tsaye. Cike da basarwa kuma sai suka saki hannun juna kowa na ƙoƙarin haɗiye abinda ke ransa da cikin idanunsa, kafin su kalli Hibbah a tare Shuraim ya ida ficewa, Isma'il ya karasa shigowa............✍
*_Tofa mazaje ya take ne?😂😂💃🏻, kodai Hibbahr mu ta mutunci ta haɗa karo ne😹😹😝. To muje zuwa muga wane mai rabon zai ɗauka a ciki, dan har yanzu itaɗin allura ce a cikin ruwa mai rabo ka ɗauka. zamuga yaya TAKUN SAƘAAR zai kasance a filin dagar dan ga Junaidu ma bin Halilu a gehe yana jiran waman dakala bati siddan. Ga kuma oga master da tabbas sai ya binciko hibban tunda ya ɗau alwashin hakan🐒😉😂._*
_Please kuyi manage da ga nan har Monday na ƙara samun sauƙi😭🙏🏻_
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________
*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻
_GYARAN MA NA KAMFANIN TURAREN:_
*YERWA INCENSE AND MORE*
*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*
_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawatattu kuma nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki. hadin bornu/chadian na kamfanin turaren YERWA INCENSE AND MORE_
*_Muna da haɗin_*
_Turaren wuta kala kala na gidah_
_khumrahs_
_Kullaccham_
_Turaren wanka_
_Turaren Kaya_
_Turaren wanki_
_turaren mopping_
_Dukkanil al’ajab (Turaren tsugunno na Matan aure kad’ai)_
_khumratul al’ajab (khumrah ta jiki ta matan aure_
_Muna Gyaran jiki_
_Na amare_
_Da masu jego_
_Da sabulai masu gyara fata_
_Turaren tsugunno_
_zumar goran tula_
_Scented hair cream and spray (man kamshin gashi da gyara gashi_
_Akwaisu kujeran tsugunno
_Dilke and halwa set_
_Burners da igniters da tong_
_turaren fesawa dana ruwa._
_wardrobe balls_
_scented pebbles_
_cotton wooly oudi incense_
_kabbasas_
_Da sauran kayayyaki da yawa da bamu ambata ba_
_Akwai ragi na musanman ga yan zafafa fans❤️_
_Muna bada sari, Ko sayi ‘dai ‘dai akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*
_EMAIL:[email protected] ko INSTAGRAM PAGE d’inmu:yerwaincense_and_more dama nambR mu:08095215215_
_MUNA TURAWA KAYAN MU KO’INA A FADIN NIJERIYA DAMA KASASHEN KETARE.
100% TESTED AND TRUSTED_
••••••••••••••••••••••••••••••••
*_Chapter Fifteen_*
.........Kamar yanda doctor Bilal ya faɗa a ranar suka sallami Ummi tare da sharuɗan da za'a kiyaye game da lafiyarta. Su Yaya Abubakar sun amsa masa tare da tabbatarwa. Wannan ɗin ma akasi aka samu kawai. Da ga haka sukai masa godiya suka tafi da sanyin idaniyarsu gida.
Koda suka isa gidan babu wanda yayma Ummi zancen Abbah, hasalima su sun manta ma. Hidimarsu suka cigaba da yi hankali kwance har dare. Sai da zasu kwanta ne Ummi taji shirun gidan yayi yawa take tambayar Hibbah data maƙale a ɗakinta zata kwana. Bargo Hibbah taja har saman kanta tana sake bajewa a gadon na Ummi. “Ummi nima ban saniba. Ƙila sunje ƙauye ne”.
Shiru Ummi tai tana nazari, tasan Momy ko kowa zaije ƙauye ita dai bazataje ba. Hakama ƴammatan ƴaƴanta. Hajiya Mama da Abban ne kawai suke zuwa, suma idan aikin sharrinsu ya tsikaresu, kuma Abba ma ai bai jima da dawowa ba. Ajiyar zuciya ta sauke da kauda zancen a ranta itama ta kwanta tare da kai hannu ta janye bargon da Hibbah tasa har saman kai.
Duk yanda Ummi taso yin barci gagararta yayi, sai ma dulmiyawa da tai a ƙololuwar duniyar tunani da neman mafita. Taja tsahon lokaci tana ƙullawa da kwancewa kafin ta sami mafitar da take addu'a da fatan ta zame musu alkairi ita da zuri'arta.
Da asuba bayan sun idar da salla Ummi ta dakatar da Hibbah da ga barcin da take ƙoƙarin komawa gado tayi. Cike da shagwaɓa ta lafe a jikin Ummin tana faɗin, “Wayyo Ummi ALLAH barci nakeji, kinga yau weekend ne babu makaranta sai islamiyya, su Yaya bazasuje aiki ba na san suma barcin zasuyi”.
Murmushi kawai Ummin tayi, zuciyarta najin tausayin autar ta bisa hukuncin data yanke akan lamarin duk ƴaƴanta a daren jiya. “Muhibbat!”.
Ta kirayi sunan Hibbah dake lumshe idanu babu wasa. Idanu Hibbah ta buɗe tana kallon Ummin, dan yanda ta kirata da cikakken sunanta babu wasa tasan ƙwarai magana ce mai muhimmanci.
“Na'am Ummi”.
“Tambayarki zanyi?”.
“To Ummi, ALLAH yasa na sani”.
Numfashi Ummi taja da kafe Hibbah da ido. “Duka yayunki babu mai neman aure ne dama?”.
Ɗan jimm Hibbah tai alamar nazari. Kafin tace, “Ummi wai kina nufin sunada ƴammata?”.
Kai Ummi ta jinjina mata kawai.
Hibbah ta ƙyalƙyale da dariya tana kwantawa ta ɗaura kanta a cinyar Ummi. “Uhm ai Ummi fa dama tun kwanaki nakeson na baki labari Yaya Umar ya gargaɗeni. Wai so suke suyi miki surprise ne. Kinga Yaya Muhammad yana da budurwa, Maimunatu (Kausar) ɗin gidan Sheikh Aliyu Abdul-Ra'uff Maina abokin Daddyn mu, mai islamiyyarmu kuma ɗiyar kawarki.......”
Wani irin farin ciki da sanyi ne ya lulluɓe zuciyar Ummi lokaci guda. Ta katse Hibba cike da zumuɗi. “Da gaske Tanee?”.
“Wlhy kuwa Ummi. Kin dai santa babu ruwanta ga hankali, kina zuwa gidansu, suna zuwa nan gidan kinsan tarbiyyarsu. Gata malama a Islamiyyar tamu. Akwai wani dabino da zam-zam da zuma da Yaya Muhammad ya kawo miki kwanaki na rantse itace ta bada a baki. Amma yace idan na faɗa sai ya fasan baki.”
Yanda Hibbah ta ƙare maganarne ya saka Ummi ƙyalƙyalewa da dariya. “Kai Mamana har yanzu dai ke sakara ce ALLAH, basai ki gayamin a sirri ba. Sam baki biyo mai sunanki ba. To Abubakar fa?”.
Cikin dariyar zancen Ummi Hibbah tace, “Tab na Zahidah kenan.”
“Wannan Zahidah ta gidan Auntyn ku Kulu dai dana sani?”.
“Eh wlhy Ummi. Amma yace karsu faɗama kowa sai ta gama makaranta. Nima basusan na ganeba a ɓoye sukeyi”.
Nanma dariyar farin ciki ce ta bayyana akan fuskar Ummi. Har ranta zaɓin Yaya Abubakar da na Yaya Muhammad sun mata hundred percent. Hibbah ta cigaba da faɗin, “Shi kuma Yaya Umar Nafisa ce nasan kin sani dama. Yaya Usman kuma Hafsat itama kin sani. Zakin ki kuma babu kasuwa har yanzun”.
Sosai Ummi taji matuƙar daɗi, dukkan damuwarta sai ta gushe a lokaci guda. Taji ƙwarin gwiwa bisa ga abinda take shiryawa. Dukkan fargabarta ta gushe. A ɓangaren muhalli bata da matsala da yaranta, duk gine-ginensu sai dai ƙarashe. Dan suna fara aiki suka haɗa hannu wajen fara ginin filin da taketa tattali da kaffa-kaffa domin su. Burinta ita da mahaifinsu yanda suka tashi kansu a haɗe su cigaba da rayuwa a waje guda. Shiyyasa koda ya sai filin sai ya damƙashi hannun amininsa kuma malaminsa har sai da suka fara aiki ya basu. Shiyyasa har yanzu Abba da Hajiya Mama basusan da zancen ginin ba........
“Ummi inje in kwanta?”.
Hibbah ta katse mata tunani. Shafa kanta Ummi tai tana murmushi. “A'a ban gama da ke ba. Dan banji ita autata tana da saurayi ba ko a'a?”.
Da sauri Hibbah ta ɓoye kanta tana dariya. “Kai Ummi ni banda wani saurayi. Nifa bazanyi aure ba muna tare mutu karaba”.
“Tab, to auta an taɓa haka kuwa. Muma ai munason zaman gidanmu aka ɗakkomu aka kawo mu naku gidan muka haifeku.” Ummi ta faɗa tana dariya.
“Ni dai bazanyiba ALLAH Ummi. Banason nesa da ke da su Yaya. Indai zanyi aure sai dai mutafi tare ko mijin yazo ya zauna a gidanmu to”.
Dariya sosai Ummi keyi, irin wadda ta jima batayi ba a rayuwarta. Tanee ɗinta kayan shirme da wauta kenan. Da ana haka da ƴaƴa da yawa na tare da iyayensu ai.
Tashi Hibbah tai da gudu ta haye gadon Ummi ta kudundune a bargo ita a dole kunya ta kama ta. Ummi da ke dariya tace, “To shikenan ai ke baki da matsala tunda Junaid ɗan gidan nan ne sai kiyi zamanki tare dam......”
“ALLAH Ummi bana sonsa. Da na auri mugun nan gara na mutu”. Hibbah tai saurin yaye bargon idanunta na cikowa da hawaye. Yayinda fuskarta ke nuna tsananin tsoro da tsanar Junaid ɗin da Ummi ta ambata.
“To shikenan naji. Amma ai kina son Isma'il ko?”.
Idanu Hibbah ta zaro waje a firgice. “Wane Isma'il ɗin Ummi?”.
“Mai zuwa nan gidan mana”.
“Ni dai wlhy a'a Ummi. Shi yayana ne dan ALLAH kibar faɗa.”
“Oh ALLAH, ke kuwa Tanee wa kike so a rayuwarki? To ko wanda yazo dubani a asibiti jiya? Muhammad Shuraim ko?”.
Baki Hibbah ta turo amma batace komai ba. Ummi ta cigaba da faɗin, “Tanee kinga shima alamunsa sun nuna mutumin kirki ne nutsatstse. Ina ƙyautata masa zaton alkairi insha ALLAH. Amma zansa ai bincike a kansa inhar kina son nasa”.
Kwanciya Hibbah tai ta juyama Ummi baya. “Ni Ummi ALLAH ya cika iyayi. Gashi baida fara'a. ga shishshigi ”.
“Duk shi kaɗai?. To lallai tunda kika iya gano waɗan nan kina sonsa kenan, zaki kuma auresa”.
Da sauri Hibbah taja bargo da cewa, “Nifa Ummi a'a baiminba. Sai naje China na dawo zanyi aure”.
“Tanee wannan mafarkinki ne. Amma ban fidda miki ran zaki cikashi ba idan kinyi aure mijinki ya kaiki da kansa”.
Shiru Hibbah tayi dan an taɓo mata inda kuma bata son. Itama Ummi sai bata sake tankawa ba ta cigaba da hidimarta da lissafin ƙullawa da kwancewa.
Zuwa takwas Ammar ya shigo ya tada Hibbah dansu haɗa breakfast su wuce islamiyya duk da sunyi latti. Hibbah kamar zatai kuka ta bisa. koda sukaje kitchen ɗin suna aikin suna faɗa har sai da Yaya Abubakar ya shigo ya tsawatar musu saboda kuka da Ammar ya saka Hibbah.
Suna kammalawa sukai shirin islamiyya. karyawar ma a tsaitsaye sukayita suka fice.
★★★
A yinin ranar su Yaya Muhammad duk a gida sukayisa. Suna tare da Umminsu suna shan hira. Basu sake mata maganar tarinta ba, itama batai musu ba. Sai bayan sallar zuhur suma suka wuce islamiyya. Ganin dai har zuwa yamma babu motsin Abbah da su Hajiya Mama yasa Ummi fita wajen maigadi ta tambayesa ko sunyi tafiya ne.
Baiyi mamaki ba. Dan yasan kaf yaranta a fusace suke da Abban. Bayanin faɗuwar Abban ya bata da kaisa asibiti da akai. Kuma har yau babu wanda ya shigo gidan tun jiyan. Duk da abinda suke mata bataji tayi farin ciki da tsautsayin daya afkawa Abban ba. Sai ma komawa tai falonta ta faɗa duniyar tunani........
_________________________________
A ɓangaren Abba ba ƙaramar jigata yay ba kafin safiya. Ƙafafu sun kumbura suntum. hakama fuskarsa tamkar ƙwaɓun fulawar sabon burodi. Sauƙinsa ma allurar barci da likitocin sukai masa ganin yanda yake rusar kuka ƙafarsa na masa zogi.
Sai kusan huɗu na maraice mai gyaran yazo, a cewarsa sun sami lalacewar motane a hanya. Sai dai kuma a zahirin gaskiya ƙaryama yake bai taho ba sai da safen. Komai likitocin basu ce ba. Sai ma damar yaje yay aikinsa da suka bashi, dan haka suka basu sallama.
Ummi na tsaka da tunaninta taji shigowar motoci, mikewa tai ta leƙa ta windown falonta sai ta hango ana fita da Abbah da ga motar Junaid tamkar gawa. Wani irin faɗuwa gabanta yay. Babu shiri ta fito zuwa tsakar gidan itama. Kusan tare suka shiga sashen Momy da su Hajiya mama da ke biye da mai-gyara da Junaid da suka ɗakko Abba ranga-ranga.
A tsakkiyar falon momy aka shimfiɗe Abba. Sai dai ganin yana numfashi yasa Ummi batace komaiba tabi layin ƴan kallo. Mai-gyara ya fito da kayan aikinsa. sanin abinda zaije ya dawo ya sashi faɗama Junaid cewar ya samo wanda zasu tayasa riƙe Abba dan shi kaɗai bazai iyaba. Badan Junaid yaso ba ya mike ya fita. Babu jimawa sai gashi tare da mai-gadinsu da na maƙwafta. Sai wasu yaran makwaftansu su biyu sa'annin Ammar.
“Yauwa kayi farar dabara da kukazo da yawan”. Cewar mai gyara yana gyara zamansa sosai a gaban kafafun Abba da sukai suntum har ƙyalli sukeyi.
Junaid da mutanen daya gayyato baki ɗaya suka zagaye Abba mai-gyara ya fara aikinsa. Sai dai abin mamaki duk da barcin da Abba keyi ana taɓa ƙafar yay wata iriyar mahaukaciyar zabura da ballara ihu. “Wayyyyyyyoooooo!!!!!! ALLAH na zasu kasheni na shiga uku ni Halilu!!!”.
Babu wanda ihun Abba bai gigita ba a falon. amma ahaka mai-gyara ya cigaba da aikinsa ko tausayi babu. Ihu Abbah yake da iya ƙarfin iko. Tun yana zufa har takai ga sakin fitsari. Can fa abin mamaki da kunya sai ga kashi.
Hanci su Ameerah suka shiga toshewa. Su kansu masu riƙon nashi ji suke kamar su sakesa su gudu dan azabar warin kashin. Suma kuwa yayi ya farfaɗo yafi sau uku. Tun yana ihu da murya mai kauri har ya koma siririya. Daga baya ma akabar jinta gaba ɗaya.
Duk yanda Ummi taso daurewa sai da taji hawaye sun ciko mata idanu. Tai ƙasa da kanta saboda tausayi.
A cikin wannan halin su Hibbah suka fara dawowa gidan. Ihun Abba ne ya ringa jan hankalinsu suka dinga nufo sashen duk da sun manta shekarar karshe da suka shiga sashen. Su kansu tsoro ya kamasu ganin yanda Abban ya koma. Badan sun so ba dole suka dinga toshe hancuna suma saboda wari.
Mai gyara ya ɗora kafa da hannun Abba. Sauran raunikan ma aka gyara. Ya shafa magani ya bada wanda za'a cigaba da masa amfani da shi. Kafin a cake masa ƴan kuɗaɗensa masu nauyi. Aka kuma kaisa masauki dan yace sai da safe zai wuce yamma tayi.
Sai lokacin Hajiya Mama ta farga da su Ummi da yaranta. Ido ɗaya ta kanne ta shiga zazzaga bala'i wai sunzo ganin ƙwaƙwaf. Cikin subutar baki Hibbah taja wani wawan tsaki da faɗin, “Kaɗan ma ya gani. Ummin mu yaso gani a wanann kwatankwacin bala'in sai shi ALLAH ya tsundumasa. In takamarsa zalunci wataran ƙafar za'a guntule.....”
Wata muguwar cafka Hajiya mama ta kaima Hibbah ta ko kwasa a guje tabar sashen. Zata bita Junaid ya riƙota cikin masifa. “Barta kakus. Nine nan zanci uban uwarta, wancan bakin nata mai kama da na reza yau sai na ɓaɓɓarkasa wlhy. Shegiyar yarinya mai bakin akku. Idanma an sakata tazo ta faɗa ne to ina dai-dai da kowane shege a gidan nan. Wama ya sani ko kada mana shi akaiyi. Kai bama zan yardaba ALLAH sai munje kotu”.
Tsaki Ammar yaja tare da kama hannun Ummi suka fice. Su Yaya Muhammad ma kai kawai suka girgiza sukai gaba abinsu da barin su Hajiya mama da takaici. Dan so sukai su tanka su kwashe komai sukai wajen ƴan sanda. Daga nan a wuce kotu har ALLAH yasa sukai gaɓar da suke fata. To sai akai rashin sa'a yaran Ummi masu lurane suka manna musu hauka.
Koda suka koma sashensu basuga Hibbah ba. Sun san ta boye kanta a daki ne saboda tasan tayo laifi, tunda suma suna hanata rashin kunyar. Alwala ma duk sukayi suka fice masallaci. Ummi ma ta nufi ɗakinta gabatar da tata duk da tana jiyo hayaniyar su hajiya mama daketa zage-zage har yanzun.
Koda suka dawo bayan sallar isha'i Hibbah bata yarda ta fitoba har suka ci abinci sukai hira kowa ya tafi makwanci. Babu kuma wanda ya nemeta dan a tabbatar mata batai dai-daiba.
Tun a daren maƙwafta ke shigowa duba Abba dan sunji ihun da yayta zugawa. Duk wanda ya shigo sai su hajiya mama suce yaran Ummi ne suka jima Abban ciwo. Da yawa ba yarda suke ba, saboda sunsan halin matsi da Ummi ke fuskanta a gidan da yaranta tun suna kanana. Dan tunkan ma Hajiya mama ta dawo gidan da zama idan tazo da ga ƙauye haka zataita zubda tujara wa Ummi kala-kala, tunda kuwa mijinta ya rasu ta dawo da zama baki ɗaya sai Ummi ta shiga uku ta lalace itada ƴaƴan ta, gashi nan har yanzu basu huta ba.
*_______________________________*
Shiru kakejin Master da yaransa tamkar basa ƙasar. Babu kalar takalar da jami'an tsaro basu masa ba a kafafen ƴaɗa labarai yay kunnen uwar shegu da kowa. Ko randa zancen kai matar gwamna koto ya fito da ga hukumar yaƙi da ta'annatin kayan gwamnati babu wanda yaji ko tarin master. Shi dama ba sanin taka mai-mai accaunt na duka handles nashi akai ba. Dan kullum cikin canja salo yake.
Sun cigaba da saka idon ganin kozai tanka amma shiru, dan haka suka cigaba da shirya masa tarkuna ta ƙarƙashin ƙasa dan sunsan tabbas zaije kotun.
★★
Yau da yamma Hibbah na makaranta ta fito class cike da gajiya da yunwa. Fatanta kawai ta samu motar komawa gida da wuri dan su Hafsat tuni sun wuce saboda ba department nasu ɗaya ba. Su kuma yau duk lecture ɗin safe sukayi. Ita kaɗaice tayi na yamma.
Ta samu da yawan ɗalibai dake ta tutsutsun shiga motar da duk tazo wucewa. Dan haka tai gaba saboda kanta dake ciwo. Cikin sa'a kuwa tana matsawa gaban sai ga wata taxi ta faka gabanta. Batare da tunanin komaiba ta afka ciki bayan ta sanarma direban inda zai kaita, shi kuma ya faɗa mata kuɗin. Ko ragi bata nema ba dan buƙatarta kawai taje gidan da wuri. Saboda tana tsoron abinda zaije ya dawo ne musamman akan dangin Abbansu dake cike da gidan nasu dubiyar Abba. Dan zuwa yau da yake cika kwana uku jikin nasa da sauƙi.
Ƴan can asalin kauyensu ne sukazo mota guda duba shi. Sai dai hakan ya bama Ummi mamaki da su kansu, dan sam da ga Abba har hajiya mama bason mu'amula da ƴan ƙauyen sukeba yanzun. Shiyyasa har ƙasan ranta takejin akwai wata a ƙasa da suke ƙullawa.
Wasu hawayen tausayin Ummi da su kansu ya cika mata ido. bayan hannu tasa ta share tare da kwantar da kanta jikin sit ɗin ta lumshe idanu ko kanta zai sassauta sara mata.......
Ummi nacan na dakon jiran dawowar Hibbah itama, dan yau da kanta ta soyama Hibbar wainar filawa da tasan tana matuƙar so. Yayinda can ƙasan ranta ke cike da fargabar taruwar dangin mijin nata da nata a gidan. Dan tasan akwai abinda suke ƙullawar da gaske. Sai dai kuma ta saka a ranta komi zasu ƙulla insha ALLAHU ta gama shirya musu a wannan karon. dan itama tun a jiya data fita ta gama tsara komai akan makomar ƴaƴanta. Nasu kawai take jira yanzu ta ɗora da ga inda ta tsaya.
Ilai kuwa hasashen Ummi yayi dai-dai, dan tana tsaka da wannan tunanin akai kiranta sashen Abba ɗin. Hijjab ta saka har ƙasa ta tafi. Tun a falo Maomy ta sakar mata wani habaicin da ya tsaya mata a rai. Sai dai batace komai ba ta ƙarasa falon Abba.
Su kawu Bello ta samu da wasu a dangin Abban. Sai hajiya mama. Bayan ta gaishesu ta nema waje ta zauna duk da ba dukansu suka amsa ba.
A gadarance Kawu Ayuba ya fara bayani. “Hasiya basai mun sake ɓata lokacin tisa magana ba. Nasan kema tunda kika ganmu anan kinsan zancen. Kamar yanda su Yaya Ballo sukazo kwanaki akan maganar auren ƴaƴanki da yaran wajen Alhaji Halilu yanzu batun saka rana ne ya tashi. Saboda tsabar halacci da hangen nesa irin nasa yace kawai tunda munzo dubasa a saka. Shi baya wani bukatar ƴan kunji-kunji tunda batun tuwona maina akeyi. To a yanzu haka dai ga kayan saka rana nan ma duk ya saya dan yace shine uban anguna shine na amare, kuma koma bai faɗa ba dama shine, tunda tun suna kananunsu shiketa wahala akansu. Koda kuwa mahaifinsu na raye shine mai bada auren nasu ai dama. Basai na jaki da nisa ba. Yanzu haka dai an yanke ranar aure wata biyu kacal. Batun kayan aure na akwati da kukeyi anan binni duk yace zaiyi baya buƙatar komai da ga yaran nan. Ita kuma Muhibbatu tunda kun saka yarinya ta nuna bata bukatar wannan haɗin, da azo ta bijire bayan auren kota illata yaro kawai za'a fasa. Za'a bata shi wanda ta kawo ɗin ALLAH ya basu zaman lafiya.....”
A firgice Ummi ta dago ta dubi Abba. Wani shegen murmushi ya sakar mata tare da kashe mata ido ɗaya. Zatai magana yay saurin katseta cikin marairaicewa. “Hakan ai shine yafi kwanciyar hankali Kawu Ayuba. Kaga da alalata zuminci gara dai abi komai a sannu zaifi. Kuma ita mace ce. Banason a cuta mata akan abinda bataso. Dan yarinyace mai hankali da nutsuwa. Duk da damuwar da Junaid ɗin ya shiga nace ya haƙura kawai tunda tana da zaɓinta. Kuma zaɓin nata ma naga mutumin kirkine sunansa Muhammad Shuraim. Ɗan gidan Alhaji Aliyu ne mutumin kirki. Inajin kunyar ma nace bazan bashi jinina ba”.
Harga ALLAH Ummi ta shiga ruɗani, ta kuma ji ɗan sanyi ta wani fannin. Dan tana mamakin ta yaya shi Abban yasan da zancen zuwan Iyayen Muhammad Shuraim ɗin? Kodai su masu kawo kuɗinne sukai mistake ɗin zuwa nan kawo kuɗin maimakon gidan Sheikh Aliyu Abdul-ra'uff Maina? Lallai akwai abinda bata sani ba. Dan akwai manufa da dalilin yin hakan ga Abba, saboda halin makircinsa da ta sani. Hakanan salin alin bazai hana ɗansa ba ya bama wani.........
“Wannan shaiɗancin dai nasan ita ta kitsashi. Duka yarinyar nawa take da tasan wani bijirema zaɓin iyaye. Ni wlhy dan Halilun yace a barta ne da baza'a bari ba. Sai dai idan an aura mata Junaidun ta mutu”. Sababin Kawu Bello ya katse ma Ummi tunaninta.
Cikin makirci Abba ya amshe da faɗin, “A'a kawu bello ba'ayi hakaba ai. shima wnanan ɗin mutumin kirki ne wlhy. Dan yamafi Junaid nagarta. Muyi fatan ALLAH yasa haka shine yafi alkairi”.
A take duk ƴan falon suka shiga yabon Abbah da jinjinama ƙoƙarin sa, Ummi kam anata zaginta wai bata da godiyar ALLAH akan ƙoƙarin da Abban keyi tun bayan rasuwar mahaifin su Ammar. Tare da yi mata gugar zana na habaicin asalinta.
Ita dai uffan batace da su ba. Hasalima hankalinta ya rabune gida biyu. Duk sauran bayanan da suka cigaba dayi sai tama koma bata fahimtar komai. Jinsu kawai dai take da kunne da binsu da ido har aka tashi a taron ko nace suka sallameta.
Koda ta fito a sashen taso zuwa gidan malam sai dai gudun abinda zaije ya dawo da fitar tata yasa ta haƙura. Dan haka tai kiran numbar wayar matarsa da yake ƙawarta ce suna zuminci sosai duka biyun. Sai dai tasan uwargidan Maimunatu yanzu haka tana Oman da autan gidan dake karatu acan.
Bugu biyu Malama Jiddah ta ɗauka. Bayan sun gaisa da ɗan barkwancin ƙawaye Ummi take tambayarta ko Malam na nan kuwa?.
Malama Jiddah tace, “Eh yana nan, sai dai yana tare da kamar baƙin da naji kunyi magana ranar zasuzo yau ɗin. Lafiya dai ko?”.
“Tofa, kaji wani kuma ruɗanin. Umm Muhammad! Lafiya dai ba lafiya ba. Akan baƙin dama na kirasa ban samu ba......” (Komai Ummi ta zayyane mata da ya faru yanzun anan gidansu).
“Bara muga baƙin su wuce to sai na sanar masa. Duk da dai inaji a raina ko duk shine ya tsara hakan dan mijin nan naki sai da siyasa ake iya kamasa a hannu. Ya riga ya zama mai fuska biyu inba ka saniba babu mai cewa zai iya sheɗancin da yake zubawa shi da uwarsa Umm Abubakar. Amma ki kwantar da hankalinki dan ALLAH, ALLAH yana tare damu”.
“Shikenan Umm Muhammad ALLAH yay mana jagora. A gaishe da yaran sai na jiki”.
Sallama sukai da ga haka zuciyar Ummi fal waswasi da saƙe-saƙe.
*__________________*
Ido Hibbah ta buɗe a ɗan yanayin razana saboda barcin da ya figeta. Gabanta ya faɗi lokacin da idanunta ke kaiwa waje ta windown motar da aka sauke gilashi baki ɗaya. Mazaunin direban ta kalla tana haɗiyar yawu da ƙarfi saboda bushewar da maƙoshinta yayi lokaci guda. Tai saurin ɓalle murfin motar ta fito domin tabbatar ma kanta inda ya kawotan fa ba anguwarsu bane...............✍
*_Tofa. Ina mai taxi ya kai Hibbah?. Wane ruɗanine ya shiga kan Ummi game da kawo kuɗin auren Hibbah da ga gidan su Shuraim? da alama ta nuna tasan da zancen. Shin malam Aliyu Abdul-Ra'uff Maina ne ya fara aika iyayen Shuraim ga Abba kokuwa yaya abin yake ne? Wane shiri Ummi keyi akan yaranta da takejin ƙarfin gwiwar nasarar kubutar dasu ne haka? Minene shirin Abba shima game da fasa bama Junaid ɗansa auren Hibbah ya yarda ya bama Muhammad Shuraim? Shin kodai dama shine ya turosa batare da ita Ummin ta farga ba?. 🤔tambayoyinfa da yawa. Yayinda ni kaina amsarsu nake nema🚶🏻😩._*
________________________
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________
*_Chapter Sixteen_*
.........Da sauri ta dafe kanta da ya sara mata da ƙarfi. Cikin ɗacin murya da zafin da takeji a zuciyarta tace, “Wai nikam mina muku ne na laifi? Dan ALLAH kubar rayuwata ta cigaba da tafiya a yanda take karku sakamin ahali a masifa. Wancan karon kunce dan na bibiyi wanine. Wannan karon kuma mina aikata zaku kawoni nan?”.
“Duk bani da amsoshin tambayoyin nan naki. Aikina kawai shine ɗakkoki na kawoki nan wajen. Gashi kuma na cika. Amma idan muka shiga da ga ciki harma abinda baki tambaya ba za'a baki amsarsa na sani”.
A fusace Hibbah ta dubesa zatai magana aka katseta......
“Gaskiya ya faɗa miki, bashi da amsar da zai baki. Dan haka bismilla ɗiya ta”. Dattijon wancan karon da aka kaita office ɗinsa ya faɗa dai-dai yana ƙarasowa inda suke. Dan tun shigowar taxi ɗin cikin station ɗin yake kallonsu ta window. A fahimtar da yay mata na tsiwa da rashin tsoro da kafiya ya sashi yanke shawarar sakkowa da kansa ƙila tafi jin shakkarsa ta shiga.
Sai dai kuma ina. Shima a fusace ta kallesa wasu hawaye masu zafi suna sakko mata. Ganin tana motsa laɓɓanta alamar sonyin magana ya girgiza mata kansa. “Nan ba muhallin da ya dace ki cigaba da cewa komai bane ɗiyata. Ina mai tabbatar miki wannan kiran yasha ban-ban dana farko. Dan kai tsaye ke zai taimaka bamuba Muhibbat. Bakomai yasa nace hakaba sai ƴan uwanki dake gab da shiga haɗari”.
“Ƴan uwa na?!”.
Hibbah ta faɗa ƙirjinta na wani harbawa. Uffan jami'in dattijo A.G baice ba ya juya zuwa office ɗinsa. Da sauri tabi bayansa har tana haɗawa da ɗan gudu. Dan ba ƙaramin hargitsa tunaninta maganarsa ta ƙarshe tayi ba. Duk da yanajin tana binsa da gudu bai tsaya ba sai da ya isa har office ɗinsa. Kusan a tare suka shiga da Hibbah. Tai saurin zuwa gabansa ta durƙusa.
“Uncle dan ALLAH karku cutarmin da ƴan uwa. Ku daina tursasani yi muku abu ta hanyar yimin barazana da su. Kunsan kuwa mi kuka nema haddasama rayuwata a wancan karon? Saura kaɗan na rasa Ummi na, gatana ni da yayuna. Farin cikinmu madubin rayuwarmu. Miyasa kuke son saka alkairi da sharri? Miyasa kuke son yin amfani da ni saboda ku haskaka kanku ma duniya? Miyasa ku ke........”
“Ya isa ɗiyata. Duk yanda kike tunani ba haka abin yake ba a wannan gaɓar. Yanda kiɗan ya sauya itama rawar zata sauya ne dole. Inason ki nutsu ki bani dukkan hankalinki nan, domin haɗa hannu wajen tabbatar ma mutanenmu abinda suke ganin bazai yuwu ba saboda rauni da ƙarancin shekaru da suke kallo kai tsaye”.
“Ni bazan nutsu ba, bazan taɓa nutsuwa ba dan ku taurarine masu wutsiya. Dan ALLAH ku daina saka rayuwata data ahalina cikin *_TAKUN SAƘAR KU_* da bawan ALLAHn nan. Bani da alaƙa da komai nasa kamar yanda kuma bani da alaƙa da ku. Indai harkar computer ce na barta har abada duk da kuwa itace burina, itace mafarki na, itace zummata, itace kaifina. Amma saboda cigaba da rayuwar ahalina cikin salama na tattarata na ajiye. Na manta kaina cikin waɗanda suka iya koda kunnata. Please na roƙeku ku barmin rayuwa data ahali su huta. Ku barni naji da damuwar cikin gidanmu ita kaɗai ta isheni”.
Yanda ta haɗe hannaye tana roƙonsa hawaye na kwarara a kumatunta duk sai tausayinta mai tsanani ya kamashi. Idanunsa suka kaɗa sukai jajur. Kansa ya shiga girgiza mata yana ƙoƙarin kamo hannayenta dake haɗe har yanzu waje guda alamar rokonsa🙏🏻. Sai dai yana kawo hannu ita tai azamar jan nata baya.
Da sauri yace, “Shike nan naji zan barki ki tafi. Amma ki tabbatar Tabbas kinada alaƙa da Master Muhibbat, saboda wannnan ɗin kasarki ce, kuma a ƙasar taki yake aikata dukkan ɓarnarsa. Sannan rayuwar yayunki da mamanki na cikin haɗari a hannun ƙanin mahaifinku da shi wanda kike ganin baki da alaƙar komi da shi. 1Mu kaɗai ne kawai kuma zamu iya cetosu tare da ke kanki. Zakuma muyi hakanne kawai idan kin amince kin yarda zaki cigaba da mana aiki akan mutumin nan Master. Idan kuma bazakiyi ba zaki iya tafiya kawai”.
Shiru Hibbah tai tana kallonsa. Kallo mai cike da ma'anoni da yawa da ita kanta ko ca'akai ta fassarasu bazata iya ba. Kansa ya jinjina mata alamar tabbatarwa.
Sosai zuciyar Hibbah ke ƙara wani irin lugude, babu abinda ke mata kai kawo a zuciya sai batun auren yayunta da ƴaƴan Abba. Dama har cikin ranta tanaji akwai manufa, amma batasan miyasa Ummi ta amince ba bayan kuma ta sanar mata yayun nata nada waɗanda suke so. Wani tunani da yazo mata daban a cikin rai ya sakata kai hannu kawai taja kujera ta zauna tana share hawayenta da suka kasa tsayawa. Shima sai ya sauke ajiyar zuciya da takawa wajen kujerar zamansa ta office ɗin ya zauna yana fiskantarta.
“Miyasa sai ni kaɗai ce zan muku aikin? Bayan nasan akwai mutane da yawa masana kuma jajirtattu akan wannan harkar, waɗanda idan a gabansu nake ni ɗin bakomai bace, bansan kuma komaiba?”.
“Tunani mai ƙyau Muhibbat. Tambayarki na da matuƙar muhummanci kuma ta birgeni. Har cikin raina na sake yarda zaki iya domin kina da kaifin ƙwaƙwalwa. Kafin kiyi mana wancan aikin tunanina irin nasune, ina kallon raunin mace matuƙa nima. Ko a cikin hukumar nan aka bama mace aiki raina kan ɓaci naga babu abinda zata iya. Amma sai ke kika ruguza dukan wannan tunanin nawa a waccan ranar, dan kinyi abinda ƙwararru da yawa suka kasa matsayinki na mace mai ƙarancin shekaru kuma ɗaliba da iya ƙasarta kawai ta samu ilimin kimiya da fasaha. Na zauna nayi dogon nazarin da yasa na fahimci irinku ba'a sakaci da al'amarinku, dan da irinku ƙasashen turawa suka cigaba a nasu ƙasashen da suke birgemu a yau. Muhibbat na miki alƙawarin wannan aikin ƙashin kanki zakiyi. wanda dole duniya tasan da zamanki bayan kammaluwar komai insha ALLAHU. Inason barinma bayana alkairi bayan na ajiye aiki, kuma kece wanan alkairin da nake fatan bari insha ALLAH. Da kuma wanan damar zakiyi amfani kema wajen ceto ahalinki da sake darajasu cikinƴan uwanku, ki wanke baƙin fentin da ƙanin mahaifinku da kakarku sukai muku wanka da shi. Da wanan damar zaki canja masu irin tunanina game da ɗiya mace”
Murmushi Hibbah ta saki wanda ita kaɗai tasan ma'anar kayanta. Ta ɗan muskuta zamanta da faɗin, “Na amince zan muku aiki, sai dai ku sani hakan ba yana nufin idan baku sami nasarar kamashi ba zan cigaba da dawowa nan wajen. Zan muku abinda kuke buƙata ko ba'a sami nasara ba nima zaku kuɓutarmin da ahalina”.
“Tabbas mun amince, harma da wata gagarumar ƙyauta da zaki samu inhar yazo hannun namu.”
“Yallaɓai na bar muku ƙyautar basai kun bani ba. abinda kawai nakeso shine ranar auren yayuna ana gab da halartar ɗaurin aure ku kama Abba ku ɓoye min har sai an kammala ɗaura auren yayuna da matan da suke so da kwanaki biyu. Abu na ƙarshe kuma inason amin cikakken bincike akan Muhammad Shuraim da Abba ya iya hana ɗansa ya yarda na auresa duk da zaɓin Ummi na ne shi”.
“Duk mun amince da sharaɗinki”.
Murmushi Hibbah ta saki a karo na biyu. “Inhar ya kasance Muhammad Shuraim bashi da wani aibu a rayuwarsa zan auresa na rayu da shi matsayin miji kodan son da Ummi na da Yayuna ke masa. Zanbi duk hanyar da zanbi na ganin ya ɗaukeni zuwa ƙasar China yin karatuna akan ilimin kimiya da fasaha. Ni kuma a wannan lokacin zan muku aiki. Ko wanene wanan master ɗin nayi alkawarin insha ALLAH sai na zama sanadin da zaku kamashi a tafin hannunku. Dan haka na baku dama kafin kwanakin aurenmu 60 da aka saka nasan wanene Muhammad Shuraim ciki da bai. A samama ahalina waje na musamman da zasu rayu a lokacin da zan fara farautar MASTER. Dan ko ƙwarzane bana son ya samu koda farcinan hannunsu”.
Wani irin tattausan murmushi dattijo A.G ya saki, yayma Hibbah jinjina. “Tun a ranar farko da kikazo nan na tabbatar zaki iya a cikin idanunki, tabbas zaki iya. Kuma insha ALLAH dukkanin bukatunki zasu biya Muhibbat, daga ƙarshe ƙyautar dana ambata zata kasance biya miki kuɗaɗen tafiya ƙasar China ko wata ƙasa daban yin karatunki. Abinda kawai zakiyi shine neman yardar mijinki”.
A take wani irin farin ciki ya baibaye Hibbah. Ta ɗaga hannu tana addu'ar godiya ga UBANGIJI da fatan nasara akan alƙawarinta.
Shiko dattijo A.G na tayata da amin. Sai da ta sauke hannayenta sannan ya tura mata takarda da pen.
Ki rubutamin dukkan sunayen ƴan gidanku da duk wanda kike tunanin kawo tangarɗa akan auren yayunki anan”.
Takardar ta jawo gabanta tana wani irin dariyar ƙeta. Dan babu wanda take hangowa a idanunta sai Hajiya Mama da su Kawu Hannafi. Bayan ta gama zana masa ya bata wata bag dake ɗauke da tarin files da suka shafi Master. Ya ɗora da gargaɗinta akan muhimmancin riƙe musu sirrinsu.
“Dukkan abinda zaki buƙata da ya shafesa na tanadar miki anan, dole ne sai kin fara shiga kansa, kinyi irin tunaninsa. Ke mace ce, kuma ƙaramar yarinya. Inaji a jikina kafin ya ganoki ko ya farga da ke kin kammala aikin nan insha ALLAH. Kisa a ranki ALLAH na tare da ke, kuma duk inda kika shiga akwai jami'an dana tanada zasu dinga bibiyarki ke da ƴan uwanki domin baku kariya.”
Kai kawai Hibbah ta jinjina masa. Da ga haka ta fito mai taxi ɗin da ya kawota station ɗin ya sake ɗaukarta domin maidata gida.
★★
Kamar yanda Hibbah tai fata koda ta shigo gidan nasu bata sami kowa a falo ba, yayunta babu wanda ya shigo, Ummi kuma tana ɗakinta. Ɗaki ta wuce ta adana bag ɗin da tazo da ita sannan ta fito ta sanarma Ummi ta dawo.
Sosai Ummi ke binta da kallon mamaki ganin tanata washe haƙora kamar ba itace ta fita da ɓacin ran zancen aurensu ba. Komai Ummi batace mata ba akan walwalar tata. Sai ma ce mata da tai idan ta gama taje tai mata list na kayan kwalliya da kayan underwears.
Cike da zumuɗi Hibbah ta fice dan tasan na kayan lefen yayunta ne da za'a haɗa a gidan Sheikh Aliyu Abdul-Ra'uff Maina. A gurgije tai wanka ta kimtsa kanta. Ko abinci bata nema ba duk da yunwa da ciwon kan da ke damunta har yanzun, tai zaman rubuta list ɗin bayan ta kunna wayarta ta shiga WhatsApp ɗinta tana bugar cikin Hafsat da Zahidah akan kalo da sayis ɗinsu.
Cikin awa ɗaya ta kammala komai ta fito ɗauke da takardar. Kai tsaye ɗakin Ummi takai ta ajiye sannan ta fito wajen yayunta suka cigaba da hira. Su kansu sunyi mamakin ganin yanda taketa faman walwala tamkar yanda suka santa tun fil'azal. Sai dai komai basuce mata ba suma.
*________________________*
Kwana uku da faruwar haka Muhammad Shuraim yazo gidan su Hibbah a karon farko. Ya sami ƙyaƙyƙyawar tarba da ga wajen su Yaya Umar, inda aka saukesa ƙaramin falonsu da Dadynsu kan sauke baƙi kafin rasuwarsa.
Da farko Hibbah catai ita bata gayyatarsa, dan haka bazataje ba. Sai da Ummi tai mata jan ido sanann ta zumbula hijjab ta fita ɗauke da karamin tire da aka ɗora ruwa.
Tunda ta shigo da sallama ya kafeta da idanunsa manya da ke neman rikitata. Tiren ta ajiye saman Centre table ɗin falon tana harararsa da kumbura fuska.
“Malam lafiya?”.
Ta faɗa cike da tsiwa.
Kansa ya ɗan girgiza kawai yana lumshe idanunsa dake a kanta ya sake buɗewa. “Ina tausayin bakin nan naki saboda tsiwansa, amma babu komai lokaci kaɗan ya rage ya daina”.
Baki ta taɓe da kaiwa zaune cikin kujera tana faɗin, “Karka ɗauka maganin da kaima iyayena suka yarda da kai lokaci guda nima ya cini. Wasu dalilai ne kawai sukasa na yarda da aurenka badan kayi dai-dai da ra'ayin mijin da naima kaina buri ba”.
“A hakanma na gode. Na kuma sake tabbatar da cewa nazo inda ya dace neman aure. Dan biyayyar da kikai ga iyayenki kawai cikakkiyar amsace akan nagartaciyar tarbiyyar da kika samu da ga garesu mai inganci.”
“Humm” kawai Hibbah ta faɗa batare da tace komai ba.
Shuraim ya murmusa batare da ya nuna damuwa da yanayin nata ba. “Kamar yanda na faɗa miki sunana Muhammad Shuraim Aliyu. A garin nan aka haifeni, anan na tashi, anan na girma, anan nai karatun addini dana boko har zuwa secondary. Kafin na ƙetare wajen ƙasar nayo karatun jami'a har zuwa matakin degree na biyu. A yanzu haka ina akan haɗa degree na na uku tare da harkar kasuwanci tamkar yanda na taso na gani anayi a gidan mu. Abinda ban faɗa miki ba bayan wannan kuma na baki damar yin bincike a kaina dan ki sani. Ƙwarai da gaske naji daɗi matuƙa na samunki musamman da ya kasance ban zaci hakan ba. Abinda zance kawai kiyi haƙuri banyi kamar yanda samarin wannan zamanin keyiba na fara shimfiɗa soyayya kafin aure. Ni sam hakan ba ra'ayina bane ba, shiyyasa tun farko ban taɓa zuwa ƙofar gidanku ba kai tsaye sai dai bibiyarki kawai. A randa kuma iyayena sukazo domin neman izinin zuwa zance gunki sai akace anma bani ke, dan ƙa'idarku ku ba'a barinku dama yin zance. Nagode ƙwarai da gaske Muhibbat. Ina fatan zaki amsheni da hannu biyu batare da tunanin nayi miki kutse cikin rayuwarki ba?”.
Har ga ALLAH kalamansa sun sanyaya ranta. Taji matuƙar kinarsa da girmansa. Sai dai maganarsa ta kusan ƙarshe-ƙarshe akan ba'a barinsu zance ta tsaya mata arai. ta kuma sake tabbatar mata akwai abinda Abba ke ƙullawa game da auren nata da Shuraim, wanda shima da alama baida masaniya akai.
Numfashi taja tare da duƙar da kanta ƙasa, dan a karon farko taji kunyarsa da nauyinsa ta lulluɓe ta. Cikin sanyin muryar da batasan tana da ita ba tace, “ALLAH ya tabbatar mana da alkairi”.
“Amin ya ALLAH” ya faɗa yana murmushi dan ya fahimci dukkan abin cewar data shigo da shi falon ya gudu.
Ba wata hira mai tsayi sukai ba, sai ɗan guntun tarihinta itama data bashi sukai sallama ya tafi itama ta shige ciki. Dama ALLAH-ALLAH take ya wuce ta tafi ga aikin da ke gabanta akan files ɗin da dattijon jami'i ya bata (kamar yanda ta raɗa masa suna😂). Dan tun randa ya bata washe gari ta kwashe Computer ɗinta da ga falo ta maida cikin bedroom. Koda Ummi ta tambayeta dalili sai tace babu komai zata ajiyesu ne dan ta daina amfani da su sai nan gaba.
Ummi ta gamsu da bayaninta ɗari bisa ɗari. Sai dai abinda bata sani ba tuni Hibbah ta haɗa kayan a ɗakinta harma ta fara aiki akan abinda aka sakata. Ta samu bayanai na laifukan da Master ya aikata kashi-kashi, sai flash drive guda uku dake ɗauke da wasu rubuce-rubucensa na yanar gozo, da fuskokin da yake amfani da su. Abinda ta yanke na farko shine zaman yin nazari da kutse na musamman akan facemasks da yake amfani da su. Haka kawai taji a ranta tana son samo ainahin fuskarsa ta ainahi da take kallo a matakin farko na aikinta. Zatayi hakanne ta wasu hanyoyi da take ganin zasu taimaketa duk da ko farcensa baya bari a gani rufesa yake. Sai duka handles ɗinsa na yanar gizo da ya taɓa amfani da su ta hanyar tura saƙo. Da nambobin waya da yay kira dasu masu tsananin tsaro.
Yanzu gaba ɗaya lokacinta da hankalinta duk sun koma akan binciken Master da ayyukansa. Ta matuƙar maida kanta busy batare da kowa ya sani ba. Sai da safe ne idan Yayunta suka ga idanunta duk a kumbure suyita tambayarta miya hanata barci?. Takance karatune na exam da zasu fara. Tanason ta dage ne saboda shirye-shiryen exam ɗin zai haɗe mata da hidimar biki.
Duk sun gamsu da bayanin nata, dan haka sukai mata nasiha kawai akan ta ringa sassautawa tana barci dan karta saka kanta a matsala. Insha ALLAH zataci.
★★★★★
A lokacin da Hibbah keta kaikawo akan ƙoƙarin yin kutse cikin lamarin Master a gidansu shirye-shiryen biki ake tuƙuru ta fanin su Hajiya Mama da Abba da ke faman jiyyar ƙafarsa da hannu. Shiri suke na bikin ƴaƴan gata ta kowanne fanni. Dan hatta da gidajen da su Yaya Muhammad zasu zauna da amare Abba duk ya saka abokinsa ya nema musu haya, ya kuma biya kuɗin hayar da kudinsa acewarsa zai biya na farko daga haka su cigaba da biya.
Komai dake faruwa Ummi na kallo. Sai dai ta maida kanta makauniyar ƙarfi da yaji bata taɓa nuna alamar tana fahimta ba. Sai ma faman nata shirye-shiryen da takeyi ita da Sheikh Aliyu Maina da iyalansa itama. Dan a yanzu haka ma anata shirin miƙa akwatunan lefen auren su Yaya Muhammad da suka haɗama kansu da kansu zuwa gidan amarensu. Gidansu kuma na gab da kammaluwa sai sam barka da fatan alkairi.
*______________________________*
Kwanakin biki sun cigaba da turawa, shirye-shiye na ƙara faɗaɗa a kowanne ɓangare. Sai dai kuma a ɓangaren Hibbah ita hankalinta a tashe yake matuƙa bisa dalilai biyu. Na farko shine har yanzu bata sake ji da ga jami'an tsaro ba, musamman akan binciken da sukace zasu mata game da Muhammad Shuraim da zuwa yanzu shaƙuwa mai ƙarfi ta ƙara shiga tsakaninsu. Dan tun daga waccan ranar duk bayan kwana biyu sai yazo gidansu. Bawata hira sukeba mai yawa, mafi yawanci ma akan karatu ne dan tafi sakin jiki da shi.
Na biyu ganin yanda su Abba ke shirye-shiryen auren duk da yana kwance har yanzu yana fama da ƙafa sai yake ɗaga mata hankali take ganin tamkar tarkon data ɗana musu domin kuɓutar da yayunta bamai yuwuwa bane a garesu. Cikin ɓacin rai yau ta tattara dukanin kayan da A.G ya bata ta maida a bag ɗin. Dama addu'a taketa faman yi ALLAH yasa Ummi ta fita zuwa gidan malam da taji tana faɗa zata.
Tana samu yayunta suka fita, Ummi ma ta fita gidan malam ɗin tare da su sai itama ta samu ta siɗaɗa ta fice da addu'ar ALLAH yasa har taje ta dawo Ummi bata dawo gidan ba.
Tana shirin shiga napep aka dakatar da ita. Tai saurin juyowa a rikice jin an ambaci sunanta. Kallon sama zuwa ƙasa taima matashin saurayin da batasan daga ina ya fito ba. Shima batare da wani damuwar kallon da take masanba ya miƙa mata ƙaramar jakkar hannunsa.
“Babu buƙatar ki sake komawa can. Zaki sami dukkan bayanan da kike buƙata anan. Akwai waya yace zai kiraki tanan zakuyi magana. Kiyi komai da kula”.
Batare da ya jira cewarta ba ya juya ya barta tsaye galala da jikka a hannu tana binsa da kallo. Takaici da haushi yasa mai napep jan napep ɗinsa yabar wajen yana masifar an bata masa lokaci.
Itama Hibbah juyawa tai ta koma gida jiki da sauri..............✍
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________
Harara Muhibbat ta zubama Hafsat da murguɗa baki tana juya idanu, harta buɗe baki zatayi magana sai kuma tayi shiru saboda isowarsu cikin harabar asibitin.
Ko kaɗan jami'in nan baiso Muhibbat tayi shiru ba, amma kasancewar yasan aikinsa sai bai nuna hakanba, sai ma ƙoƙarin taimaka musu da yayi domin ganin an shiga da Hafsat taga likita akan lokaci.
Da taimakon jami'in aka duba ƙafar Hafsat da ta samu tsagewar ƙashi, Zahidah sai godiya take masa saboda ƙoƙarin da yaketa musu, dan sunso su kira gida ya hanasu. Hanawar tasa kuma ta bama Muhibbat haushi, dan a ganinta ya cika shishshigin tsiyane kawai, musamman daya kasance duk wani motsinta sai ta ritsa idanunsa akanta.
Tun tana hararsa a ƙasan ido da masa ƙunƙuni har takai ta fito fili tana dalla masa harara. Ganin dai ba daina kallon nata zaiyi ba a tsiwace ta ce, “Wai malam kallon fa? Dan ALLAH karka cinyeni a tsaye mana”.
Sosai yanda tai maganar ya bashi dariya, dan tsaf ya gama fahimtar itaɗin matsiwaciyace ta gaske. Sannan babu tsoro sam a cikin idanunta kona sisin kwabo. Komai baice mata ba, sai ma ɗauke kansa da yayi kawai gefe tamkar bai jita ba. Taja tsoki tana murguɗa baki da miƙewa tabar wajen.
Can gefe ta koma tana ƙoƙarin sarrafa wayarta cike da ƙwarewa. Cikin ƙanƙanin lokaci kiran da tayi ya shiga, sai da aka ɗaga sannan takai kunne tana faɗin, “Assalamu alaika Yaya”.
Amsa mata akai da ga can, kafinma ya gama rufe baki cikin shagwaɓa taci gaba da magana. “Yah Uthman muna hospital ne”.
A tsananin tsorace muryarsa ta bayyana, “Hospital Auta?! Waye bai da lafiya?”.
“Oh Yaya calm dawn, Hafsat ce taji ciwo a ƙafa amma da sauƙi, dan yanzu haka ma an gama mata gyaran sunce tsagewan ƙashine”.
“Ya ALLAH! Auta wai sai yaushe ne zakuyi hankali ku kam? Yanzu haka a wajen shegen rawan kan nan naku hakan ta faru?”.
“Na rantse Yaya bafa da gangan bane, wasu marasa kirki ne suka kusan turemu a power bike”.
“What?!. Power bike fa? Ku miya kaiku kan titin da masu power bike kebi!!?”.
Yanda yay maganar a tsawace ne ya sata zabura, duk cikin yayun nata yafi kowa sauƙin hali bayan Yah Abubakar. Sai dai kuma idan ya rikice tafi tsoronsa fiye da kowa a cikinsu..... Cikin katse mata tunani yace, “Zan turo muku Ammar yanzun nan danni naje katsina ne..”
Yana gama faɗan hakan ya yanke wayar. Kasaƙe Muhibbat tayi tana kallon wayar, yayinda gefen zuciyarta ke ayyana mata neman mafita. A fili tace, “Tab Yah Ammar! Wlhy bazan bari ya samemu a asibitin nan ba wannan ɗan matsalar”. Da sauri tabar wajen zuwa inda jami'in nan mai amsa sunan driver-n taxi yake da Zahidah.
“Zahidah tunda sunce zasu iya sallamarmu gara mu wuce gida, dan na haɗa gurmi wlhy”.
Zahidah dake mata kallon mamaki tace, “Gurmi kuma! Nami to?”.
“Humm daga kiran Yah Uthman fa na faɗa masa shine wai zai turo mana Yah Ammar shi yana katsina. Ni kuma wlhy banason Yah Ammar yazo asibitin nan ya samemu saboda yafi gidan haya matsala kema kin sani”.
Kafin Zahidah dake dariya tace wani abu jami'in nan yay saurin cewa, “Ai sunma sallemu daman, inaga ku shiga ku fito da ita kawai mana”.
Harararsa Muhibbat tayi tana ɗaure fuska. “Ikon ALLAH sai kallo, wai ni kam bawan ALLAH ca'akai ka kula damu ne kokuwa? Taxi ɗinka muka hau ka kawomu inda muke buƙata, to sai mi kuma ya rage?”.
Murmushi yayi idanunsa a kanta, “Sai ku bani kuɗina ya rage ƙanwata”.
“Ya salam! Dan ALLAH kayi haƙuri bawan ALLAH. Wlhy gaba ɗaya mun shafa'a ne”. Zahidah ta faɗa tana laluben bag ɗinta.
“Karki damu ƴammata babu damuwa. Nasan kuna a rikicene ai. Amma ƙawar nan taki ya kamata ta rage tsiwa”.
Zahidah dake miƙa masa ɗari biyar tai dariya, “Kaga fita batunta ga kuɗinka mun gode sosai”.
“Ai karki damu riƙe kawai sai na kaiku inda zaku yanzu sai na amsa”.
“Malam gara dai ka amshi kudinka kai gaba, dan bazamu sake shiga motarkaba ɗan sarkin shiga sharo ba shanu”. Muhibbat ta faɗa tana hararsa.
Saurin toshe bakinta Zahidah tayi itama tana hararta, “Wai nikam Hibbat kodai wadda tai miki wankan jego bata gasa bakin nan bane da baya barin kowa. Ina laifin bawan ALLAHn nan, kigafa ƙoƙarin da yay mana akan Hafsat”.
Hibbat ta buge hannun Zahidah da haushi, “To dan kuma ya taimakemu sai ya ishemu da shishshigin jaraba. ALLAH ni banason shishshigi da ƙwala kai a faranti irin na wasu mazan”.
Tana gama faɗa tai shigewarta ɗakin da Hafsat take. Duk binta sukai da kallo, kafin Zahidah ta maido kallonta ga jami'in. “Ayya dan ALLAH kai haƙuri. Ita haka take sam ba'a gane kanta tamkar mai aljanu”.
Ƙaramar dariya yayi yana sosa tsakkiyar kansa da key ɗin taxi ɗin. Yace, “Kinga karki damu ni salon natama birgeni yakeyi, irin waɗanan sam ba'a cutarsu a duk inda suka shiga. Je kawai ki fito dasu na kaiku kafin a sake kirana ɗan shishshigi”.
A yanda ya ƙare maganar cikin langaɓe kai kalar tausayi yasa Zahidah ƙyalƙyalewa da dariya tana shiga ɗakin domin su fiddo da Hafsat..
Da ƙyar Muhibbat ta amince jami'in nan mai taxi ya ɗaukesu zai maida gida. Dan ko sai kumbura take a motar tana ƙananun ƙunƙuni alamar bataso hakan ba. Shi dai yakanyi murmushi lokaci-lokaci idan ya ɗago ya dubeta ta mirror yaga yanda take cika baki da iska tana harare-harare........
★.★.★.★.★.★
Kamar yanda aka saba yau ɗinma tuni media ta ɗauka. Gidajen redio dana televisions harma da yanar gizo mutane sai tofa albarkacin bakinsu suke. Dan lamarin wannan gagarumin ɓarawo ya daina bama mutane tsoro sai al'ajabi da mamaki. Kullum ji suke jami'an tsaro na farautarsa, mai makon ya tsorata ya ɓuya sai ƙarama gawurta yake a al'amuransa. Gashi babban abinda zai baka mamaki manya-manyan ƙusoshin ƙasar masu lasisin iya ɗaukar mataki yake bi yana yashewa da saka rayuwansu cikin tarkuna. Dan da wahala ya kafa maka ƙahon zuƙa daga ƙarshe baka koma ƙarƙashin binciken hukumar *EFCC🐦* ba, ko ka ƙare rayuwarka da ciwon paralysis saboda barazanarsa idan yay dirar mikiya aka kaddarorinka da kuɗaɗenka. Yanzu dai yanda ya yashe asusun matar gwamna bawai ya barta bane kenan. Duk da neman da ake masa ruwa a jallo cikin kwanaki ƙanƙani zai sake silalowa ya danƙara mata wani harbin mai zafi har sai ya kai rayuwarta ƙasa kwance zai barta.
Duk yanda ƴan jarida sukaso jin ta bakin jami'an tsaro da gidan gwamnati akan wannan al'amari abin ya gagara. Sun haƙura dole suna bada labarin iya abinda idanunsu suka gani da ɓarnar da wannan mutumi ya tafka a baya kafin wannan ɗin.
Yayinda a gefe kuma jama'ar gari suketa tofa nasu. Wasu najin daɗin abinda yakeyi ɗin dan bawai a satar kuɗin manyan ƙasar kawai ya tsaya ba, har ƴan fashi da suka addabi mutane da ƴan ta'adda yakan kama waɗanda har yanzu babu wanda zai iya cewa ga inda yake kaisu ya ɓoye. duk da kuwa shima ɗin mai laifi ne a bayyane, wasu ko na jifansa da ALLAH wadai saboda suna ganin bashi da maraba da ƴan ta'addar da yake kamawa ai. Yayinda ƴan kanzagi ke zaman rubuta shaci faɗi su yaɗa a kafafen yanar gizo game da shi da ayyukansa..............✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k)
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR
*_ALLAH ka gafartama iyayen mu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_🔮TAKUN SAAƘA!!🔮_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
_ZAFAFA BIYAR 2K22_
_________________________
*_Chapter Four_*
...........Suna baro cikin asibitin Muhibbat ta kashe wayarta dan ma kar Yah Ammar ya sameta.
Tun farkon shigowa anguwar tace a saukesu. Amma sai Zahidah tace sam basu yarda ba a kaisu har ƙofar gida. Zata fara masifa Hafsat ta ce, “Kiyi haƙuri ya kaimu saboda bazan iya taka ƙafarnan ba Hibbah”.
Shiru tayi bata sake tankawa ba har suka iso ƙofar gidan su Hafsat daya kasance a farko, sai nasu Zahidah, Muhibbat ce ƙarshe. Saboda ciwon dake tare da Hafsat ɗin ya sakasu cewa a tsaya ƙofar gidansu. Zahidah ta bama mai taxi kuɗinsa tana godiya. Amma sai yaƙi amsa. Mamaki ƙarara a fuskar Zahidah da Hafsat. Sun buɗe baki zasu magana yay musu alamar suyi shiru.
“Basai kunce komai ba, inhar da wannan mai bakin tsiwar tare da ku anta kaiku waje ƙyauta kenan babu ko sisin ku”. Yay maganar idanunsa akan Muhibbat yana wani sassanyan murmushi.
Hararar da yay tsammani ta watsa masa, cikin takaici tabar wajen batare da tace komai ba. Kira Zahidah da Hafsat suka shiga ƙwala mata suna dariya, amma ko waiwayensu batai ba harta ƙarasa gaban wani gida mai baƙin gate. Sai da ta kama murfin zata shiga ta waigo, ganin har yanzu mai taxi ɗin na tare da su yasata jan tsaki akan laɓɓanta ta ce, “Maye kawai”. Daga haka ta shige ciki.
Gida ne da zamu iya kiransa babba a girma da ginuwa. Dan a ƙalla akwai ɓangarori biyu zuwa uku a cikinsa. Ɓangarori biyu na farkon shiga gidan sunfi haɗuwa da tsaruwa, zakaga hakan tun daga wajema kafin ka kai ga shiga ciki, sai dai kuma ɗayan dake daga ciki ya fisu girma, amma bai kai su ƙyawu ba.
Harara ta zubama sashen guda biyu tana taɓe baki, tana gab da wucesu taja tsaki a zuciyarta wanda batai zaton ya fito har waje ba.
“K!! Dan ubanki wa kikema tsoki!!”.
Wata buɗaɗɗiyar murya mai cike da hargowa ta faɗa. Cak ta tsaya ƙirjinta na bugawar tsoro, tabbas da ace tasan mugun nan ya dawo gidan da bazata shigo ba sai magriba. Jin takun tafiya a bayanta alamar ya taso ya sakata juyowa. Ƙiris ya rage ya iso gareta, babu shiri ta kwasa da gudu zuwa sashen can ciki tana ƙwala kiran sunan Ummi!.
“Ya ilahi! Tanee lafiyarki kuwa? Wai sai yaushe ne hankali zai game jikinki kisan girma ya fara zuwa miki!”.
Ummi dake ƙoƙarin fitowa a kitchen riƙe da ludayin miya a hannu ta faɗa. Dai-dai isowar Hibbah cikin falon itama a guje. Bayan Ummi taje ta maƙale.
“K da wa kuma?”.
Ummi ta faɗa tana juyowa gareta fuska a ɗaure.
“Wannan mugunne fa Junaid Ummi. daga na shigo ina tsaki ya hau zagina kamar nasan da zamansa ma a gidan”.
Baki Ummi ta buge mata, tai saurin ja da baya daga jikinta tana dafewa.
“Wannan bakin naki da kanwa bata jiƙa a cikinsa shi zaisa kiyita shan wahala a wajen mutanen gidan nan Tanee. Mara kunyar banza matsamin a hanya”.
Gefe Hibbah ta matsa gudun kar Ummi ta sake kai mata wani dukan hawaye cike da idanunta. Sai da taga ta koma kitchen ɗin sannan ta nufi ɗakinta zuciyarta na ƙara jin tsanar mutanen gidan nasu. Da ace zata samu wata dama a hannunta koda ta yini guda ce sai ta bisu da bulala hansin-hansin, musamman ma Hajiya Mama da Abba da wannan azzalumin Junaid ɗin. Mukulli ta murza a ƙofar tata dan batason sake magana da kowa.
Tunda Ummi ta jiyo ƙarar rufe ƙofar Hibbah sai tai murmushi, tasan hakan na nufin tayi fushi, ba kuma zata buɗe ba sai Yah Abubakar yazo ya lallasheta ko jarabar danna Computer ɗin tata ta motsa. Watsar da ita tai ta cigaba da aikinta saboda bataso magriba ta sameta. Cikin ranta tana tunanin yaushe Junaid ɗin ya dawo ƙasar? Dan bataji alamun murna da ga yaran gidan ba sam. Rashin mai amsa mata zancen ya sata watsarwa ta cigaba da aikin gabanta.
Harta kammala ta shige babu wanda ya shigo a cikin samarin ƴaƴan nata, fatan dawowa lafiya tai musu sannan ta shiga wanka.
A ɓangaren Hibbah ma wankan tayi, kasancewar tana fashin salla tana kammala kintsawa ta fito, dan ta tabbatar Ummi ta shige. bakuma zata sake leƙo falon ba sai bayan sallar isha'i. Yayunta kuwa bata tsammanin yau zasu kwana a gidan ma. Musamman Yah Abubakar da Yah Usman da yace yana katsina.
Study table ɗinta ta haye dake can gefen falon a wani ɗan lungun. An shirya mata wajen tsaf da kayan karatu na musamman saboda kasancewarta ƴar gata, sannan haziƙa wajen sanin sirrin sarrafa Computer.
Tun ana ɗaukar lamarin nata shashanci har takai yanzu Yayansu Abubakar naci da ga tagomashin ƙwazon nata ta hanyar aikinsa na tsaro. Dan yasha sakata ayyuka masu muhimmancin gaske ana kuma samun nasara tunma bata kai haka shekaru ba. Wannan dalilin ne ya sakashi tsaya mata wajen ganin ta cika burinta akan zurfin nazari game da na'ura mai ƙwaƙwalwa.
Cike da ƙwarewa ta kunna Computer ɗinta saboda aikin data tarkatarma kanta na bibiyar masu power bike. Dan ta ɗauka alwashin kosu ɗin ƴaƴan uban waye sai ta gano su insha ALLAH.
Babu wanda ya shigo gidan sai Ummi data fito bayan sallar isha'i tace ta tashi taje taci abinci tunda babu wanda ya dawo a yayun nata har yanzu. Da to ta amsawa Ummin, tana gani ta koma ciki ta cigaba da aikinta cike da zaƙuwa.
Ummi dake jiyo motsin Hibbah ta shiga ƙwala mata kira ganin dare ya farayi. ta tabbatar kuma inba da gaske tayi mata ba, zata iya kaiwa biyun dare akan Computer ɗin batare da gajiyawa ba.
*_Tanee! Tanee!!_* wai bazaki tashi a gaban Computer ɗin nan kije ki kwanta ba sai na ci ƙaniyarki ko?!”.
Hibbah dake zaune a cikin falon daga can gefen study table ta ƙwaɓe fuska tamkar zatai kuka. A kallo ɗaya zaka fahimci tarin ƙuruciyar dake tattare da ita, dan kwata-kwata bazata gaza shekaru goma sha tara a duniya ba. Jin tahowar mutum ta bayanta ta miƙe da sauri a gaban Computer ɗin tana faɗin, “Wayyo Ummi nafa kusan gamawa wlhy”.
“Ai ba Ummi ɗin bace, mai kunnen ƙashi nine”.. Ƙyaƙyƙyawan saurayi mai tsananin kama da ita da bazai wuce shekaru ashirin da takwas ba ya faɗa a bayanta tare da kai mata ranƙwashi bisa kai. Tsalle tai zuwa gefe tana fasa ƙara duk da kuwa bai sameta ba. Ya balla mata harara yana kai hannu kan mouse ɗin Computer ɗin ya kasheta baki ɗaya. Dai-dai lokacin da yake ɗagowa ya nuna mata hanyar ƙofar ɗakinta yana faɗin, “kama gabanki kafin jikinki yay tsami anan”.
Idanunta dake tara ruwan hawaye ta shiga ƙyaƙyƙyaftawa. Cikin narkewar fuska tace, “Yah Umar dan ALLAH ka barni wlhy zuwa 12 zan shige na kwanta. ALLAH akwai abinda nakeyi mai muhimmanci a ciki”.
Charger ɗinta dake jikin socket ya fizga da nufin kai mata duka. Da sauri ta dirga wani uban tsalle da ihu tare da kwasa a guje zuwa hanyar ɗakin nata.
“Wai wane irin salon iskanci ne haka za'a dinga damun mutane da ihu kamar ƴaƴan rashin ƙwaɓa!”.
Wata murya mai kauri da amo ta faɗa daga bayansu. Basai an sanar musu wanene ba, dan haka Tanee dake gab da shiga ɗakinta ta ida afkawa da sauri tana rufo ƙofar. Umar yaɗan rumtse idanunsa yana cije lip ɗinsa na ƙasa da ƙarfi alamar son saisaita kansa dan jin zafin furucin mutumin da aƙalla zai iya kai shekaru Hamsin da huɗu zuwa da biyar
“Wai dan iskanci ba magana nakeba akaimin banza saboda rashin tarbiyya!. To dan uban mutum dai duk yanda yake kallona nine uban ubansa ma bama shi ba. Sannan kuma mijin uwarsa ne ni!!”.
Murmushi mai ɗaci Umar yayi yana haɗiye abinda ya tsaya masa a maƙoshi saboda kallon da Ummi dake fitowa tai masa. Yaja numfashi a sarƙe da faɗin, “Kayi haƙuri Abba ba wani abu bane ba. Nine da Tanee”.
“Eh lallai ai basai ka faɗaba na gani kai da taɓararriya ne, to ubanmi kale mata da har takema mutane ihu kamar wadda ake lalub....”
Cikin ɓacin rai Ummi ta katsesa da faɗin, “Kai Umar wuce ka tafi sai da safe”.
Zuwa yay ya wuce yana faman taunar lips ɗinsa dan shi kaɗai yasan tuƙuƙin baƙin cikin da yakeji a cikin ransa game da ƙanin mahaifin nasu da a yanzu suke kira da Abba saboda maye gurbin mahaifinsu da yayi dalilin ƙaddarar mutuwa, tabbas badan mahaifiyarsu ba da ko kallon hanyar da sukabi tuni kawun nasu bazai ringayi ba. Amma dasun yun ƙuro itace mai taka musu burki.
Umar na ficewa Abba ya saki wani shegen tsaki da nufar hanyar ɗakin Ummi. Itama bayansa tabi a fusace. Suna shiga cikin ɗakin a zafafe tace, “Halilu ina rabaka da jifarmin ƴaƴa da mugayen furuci amma baka kiyayewa. Ka sani idan ada ni dasu mun ɗauka wulaƙancinka da tozarci wlhy yanzu bazamu ɗauka ba. Dan badan ina takama yaran nan birki ba a kanka bisa dalilin mahaifinsu da tuni sun tabbatar maka da suma sunkai girma. Idan kuma bazaka bariba to lallai zan buɗe musu ƙofar dana rufe domin maka hijjabi akan hakan.....”
Wata wawuyar dariya ya saki yana faɗawa saman gadonta. Cikin salon iskanci da izgilanci yakai ƙafa ya taɗota sai gata ta faɗo kansa. Yunƙurawa tai zata tashi ya birkiceta zuwa ƙasa ya koma samanta. Dogon gashin da ALLAH ya azurtata da shi duk da tsufa yasa ya fara sirkawa da furfura ya damƙe cikin hannunsa tare da ɗan kwalin kanta ya fisga da ƙarfi, tare da sak ɗayan hannunsa ya danne mata baki............✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
Duka gamayyar biyar din(1k)
1,000
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_🔮TAKUN SAAƘA!!🔮_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
_ZAFAFA BIYAR 2K22_
🔥🔥🔥🔥🔥
*_LAST BONANZA_*
*KARO NA QARSHE!*
*_farincinku shine namu,ZAFAFAN DAI,sun sake amsa kokenku,sun sake rage muku kaso 20 cikin 100_*
*_Daga yau 29 ga wata,har zuwa 31 ga watan nan,xaku iya biyan 800 a amadadin 1000 na kudin litattafai biyar_*
*_za'a fara posting in sha Allah 3st January da yardar Allah_*
*HANZARTA KI BIYA NAKI KAFIN RANAKUN SU QARE*
*XAKI BIYA TA WANNAN ACCOUNT NUMBER DIN*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
SAIKU TURA SHAIDAR BIYA
08184017082
GA MASU TURA KATIN WAYA KO KUMA VTU,SAIKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYANKU
09134848107
_________________________
*_Chapter Five_*
............Wani irin rawa jikin Ummi ya fara saboda azaba. Ya ƙyalƙyale da dariya yana wani fici-fici da ƙananun idanunsa jajaye. “Asiya idan kin manta bara na tuna miki. Daga ke har ƴaƴanki da kikeji girmansu ya kai yanzu a tafin hannuna kuke wlhy. Zan kuma iya binku ɗaya bayan ɗaya na salwantar da rayuwarku batare da wani mahaluki ya iya gane hakan ba ko zargina. Kamar yanda na gagareki a baya da kikeji da ƙuruciya a yanzunma hakan take. Dan haka ki cigaba da buɗemin ido da tsagerancin nan naki kiga idan ban kai rayukanku ƙasa ba cikin ƙanƙanin lokaci”.
Ya ƙare mganar da hankaɗa kanta ta bigi fuskar gadon. Wata siririyar ƙara ta saki ta zaba. Cike da juriyar zaluncin data saba sha daga garesa ta dubesa da idanunta da suka kaɗa zuwa ja tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallar dake taruwa a cikinsu. “Insha ALLAHU Haƙilu bazaka taɓa cin nasara akan zuri'ata ba bayan nasarar aure na da kayi a baya, bazan gaji da faɗa makaba ko yanzu kana samun nasarane a kaina saboda wasu dalilai na lizzamin zaren ƙaddara, amma ka jira lokaci, dan kaɗan ya rage azo dai-dai wajen da zakasha mamaki.......”
Sake buga kanta yay a fusace kafin takai ƙarshen zancenta saboda sukar zuciyarsa da kalamanta sukeyi a duk sanda ta maimaita masa su, ya saka hannunsa ya danne mata baki yana ƙyalƙyalewa da dariya. “Iyakarki kauɗin banza da cika baki Asiya, amma ki sani ni Haƙilu nafi ƙarfinki, dan baki da maraba da wulaƙantacciyar dabba a gareni, amfaninki a wajena kawai samun abinda nai kwaɗayi a gareki tun farko kika hanani, yanda kika wulaƙantani a kansa a baya haka zan cigaba da samunsa a gareki cikin wulaƙantarwa da ƙasƙantar dake a ƙasan takalmana.”
Da iya ƙarfinta tai yunƙurin turesa amma ta gaza hakan, sai ma ƙara jigata da wahaluwa da takeyi a hannunsa. Yayinda shikuma yake ƙyalƙyala dariyar shaƙiyanci a gareta da izgili, cikin tsantsar zalunci da wulaƙantarwa ya shiga ƙoƙarin yin tarayya da ita kamar wanda ke tare da ƙasƙantacciyar karuwarsa. Yanayi yana kai mata mari saboda ƙoƙarin ƙwatar kanta da takeyi a garesa.
Kamar kullum sai da ya galabaitar da Ummi son ransa sannan ya barta yana faman tuntsurar dariyar rashin imani. Yaja kayansa ya saka bayan ya goge ƙazantar jikinsa da gashin kanta tare da tofa mata yawu ya fice yana cigaba da ƙyalƙyala dariyar.
Wani irin siririn kuka Ummi ta saki mai cin rai a wajen. Takai kusan awa ɗaya tanayinsa kafin ta miƙe zuwa toilet da ƙyar saboda azaba. Dukkan dabarun data sabayi domin gyara jikinta a duk lokacin da hakan ta faru tsakaninsu su ta gudanar, koda ta fito doguwar riga ta saka tahau saman abin salla ta fara gayama ALLAH kukanta akan zaluncin Alhaji Haƙilu ƙanin mijinta ada, sannan kuma mijinta a yanzu.
Bayan tayi nafilfilinta tai zaman karatun AL-QUR'ANI. Sai da taji zuciyarta tayi mata sanyi, nutsuwarta ta dawo jikinta sannan tai addu'a ta ɗan kwanta, cikin lokaci ƙanƙani barci mai daɗi yay gaba da ita tamkar bata da wata damuwa.
★
Kamar yanda ta horar da yaranta tun suna ƙanana yau ma tun kiran sallar farko na asuba suka tashi. Sai da duk sukai alwala sanann suka firfito daga ɗakunansu su biyar abin sha'awa, dan a daren duk suka dawo ba kamar yanda ta tsammaci zasu kwana a wajen ba, a tunaninsu tayi barci ita da auta shiyyasa basu shigo ba. Ammar ne ya nufi ƙofar ɗakin Hibbah ya shiga mata knocking da kiran sunanta har sai da yaji ta amsa. “Tashi kiyi salla, saura kuma idan kin idar ki sake kwanciya tunda kinsan dai yau kinada text ɗin safe”.
Bai jira amsartaba yabar wajen dan yayunsa na jiransa. Basu damu da tada Ummi ba, dan sunsan ita bata makara saboda mace ce mai tsantseni da yawan kula da ibada, bata da wasa sam akan bautar ALLAH. Hakama koda suka fito daga sashen nasu basuyi gigin tada sauran jama'ar gidan ba suka fice abinsu zuwa massallacin anguwar.
Daƙyar Hibbah ta tashi zuwa toilet saboda barcin dake cikin idonta. Cikin layi da rangaji irin na wadda ta tashi a barci ta shige bayin. Kusan mintuna ashirin sai gata ta fito ɗaure da towel tana tsane gashinta da wani alamun ta samu tsarki. Zani ta ɗaura ta saka hijjab har ƙasa ta tada salla.
*_7:34am_*
A gurguje take shiri tana yawan kallon agogon ɗakin nata saboda kiran da Ummi keta faman ƙwalamata daga falo.
Cikin kumbura fuska da ƙunƙuni take faɗin, ‘Kai Ummi wannan kira kamar makauniya, ai ba kowa ne ya jamin wannan makararba sai Yah Ammar, duk da yasan zanje makaranta harda min gargaɗin karna koma barci sai gashi bayan dawowarsu massallaci ya tsareni sai na haɗa masa indomie wai nafi kowa iya dafawa........’
“Tanee! Tanee!!”.
Ummi ta sake ƙwalama Hibbah kira again. Ƙoƙari amsawa take cikin zazzaƙar muryata tana tattare tarkacen abinda zata buƙata a cikin bag ɗinta mai zubin school bag. Daga can ta sake faɗin, “Auta kina kallon agogo kuwa?!”.
Saurin ɗaukar bag ɗin tayi da gyalenta tayo waje da hanzari. Tun kafin ta ƙaraso tsakkiyar falon Yah Umar ya wullomata harara cikin faɗa. “Wai ke kullum sai kin makara kin makarar da mutane hankalinki ke kwanciya a gidan nan ko? Tun kina zuwa secondary halinki kenan, yanzu kin fara jami'ar ma baki canjaba”.
Fuska ta kumbura tana tura baki, ta ajiye bag ɗinta da gyalen a saman kujera tana ƙarasawa dining ɗin inda duk suke zaune har Ummi, dan haka suke cin abinci a tare duk safiya da dare. Cikin shagwaɓar data saba da tsiwar da bata barin bakinta tace, “Kai Yaya Umar naga dai Yah Ammar ne ya sakani makara, sakanifa yayi na dafa masa noodles”.
Yah Ammar dake kujerar gefenta yana ƙoƙarin fara cin indomie ɗin data dafa masan ya zubomata uwar harara shima yana faɗin, “Dama can kin saba makararki yarinya zaki wani jingina dani”.
Baki ta sake buɗewa zatayi magana Yah Usman dake duba wasu takardu dake gabansa a dining ɗin shima ya watso musu harara ita da Ammar ɗin, “Dalla malamai karku cika mana kunne kuma ko”.
Ummi dake turama Hibbah kofin kunu data zuba mata tace, “Ai inda sabo sun saba, Ammar da Tanee basa taɓa zama waje guda basu isheka ba, sai kace suna ganin hanjin junansu. Nikam babu mai barina da ciwon kai kowa yayi ya gama ya kama gabansa”.
Baki Hibbah ta kuma cikawa da iska tana duban Yah Muhammad da Yah Abubakar masu kareta. Yaya Abubakar dake hidimar haɗama kansa shayi yayi murmushi, “Auta yada kallona kuma? Nimafa yau gashi kina neman makarar dani bayan nace da wuri zan fita”.
Cikin shagwaɓar da takema yayun nata saboda so da ƙaunarta da sukeyi ta ce, “Yaya kaima ko?” ta faɗa tana maida dubanta ga Yah Muhammad da ke ta faman latsa wayarsa. Ƙaramar dariya yayi tunkan tace komai, ya ajiye wayar tasa yana amsar kunun da shima Ummi ta zuba masa dan kusan halinsu ɗaya da Muhibba shima bai cika son tea ba. “Kinga autan Ummi manta da kowa ki karya, yau da kaina ma zan kaiki makaranta bazakibi Ammar ba, maza lokaci na sake ja”.
Jin Yah Muhammad yace da kansa zai kaita makaranta yau ya saka bakinta washewa. Ta kalli Yah Ammar abokin tsamartata tana masa gwalo. Kusan duk sai da sukai murmushi kowa na girgiza kansa cike da mata kallon so da ƙauna.
Basai an faɗa ba, yanda ƴan uwata da Ummin su kema Hibba a gidan zaisa kowa fahimtar ita ɗin ƴar gata ce kuma shalele. A kullum kowa burinsa yaga farin cikinta. Koda laifi tayi suka zaneta ko mata faɗa daga baya sai su koma mata nasiha da lallashinta har sai sunga ta koma rayuwata ta ƙiriniya da rashin ji suke samun nutsuwa. Sai dai kuma a ɓangaren Abba da sauran matansa sam ba haka bane. Sun tsani Muhibbat tamkar ita kaɗaice ƴa a gidan. Hakama sauran ƴaƴan gidan duk basa sonta. Kafin Hibbah takai haka kullum tambayata mi sukai musu? Amma babu mai bata amsa a tsakanin Ummi da yayunta guda biyar. Sai da tayi hankali ne zuwa yanzu take ɗan fahimtar wasu abubuwan duk da dai ba wani ya taɓa zama ya sanar da ita gaskiyar dalilinba har zuwa yanzun.
Itace farkon kammalawa, ta miƙe tana faɗin, “Alhmdllh”.
Yaya Abubakar ya dubeta da kulawa cikin lallashi yace, “Auta ki dingacin abinci ko zaki ƙara girma fiye da haka dan ALLAH, ke kowa na girma yayi ƙiba banda ke, makarantar nan kamar ƙara tsiyayar dake take ma”.
Murmushi tayi cike daso da ƙaunar Yayun nata masu sonta. Tace, “Yah Abubakar duk wannan ƙatuwan dana zama, da kaɗan fa Yah Ammar ya fini tsaho”.
Harara Yah Ammar ya galla mata da faɗin, “Tunda nine marainin wayonki ko? bar ganin Ummi a wajen, na tashi ɓarar dake zanyi ALLAH”.
Dariya duk suka sanya masa, dan da alama da haushi yake maganar. Hibbah tai masa gwalo da ɗaukar bag da gyalenta ta fice da gudu saboda ganin zai miƙe, tasan kuma kanta zaiyo.
A ƙofar fita falon taci karo da Abba. Tai saurin komawa baya jikinta naɗan rawar kaɗuwa. Dan duk da rashin tsoro na Muhibbah a rayuwarta tana matuƙar jin tsoron Abba tun tana ƴar ƙarama. Hararar da yake wulla mata ya sata sake sata duƙar da kanta idanunta na tara ƙwalla.
“Wane kalar shashanci ne kuma haka? Da girmanki amma kullum lalacewa al'amuranki ke ƙarayi saboda ke ƴar ido ce!!”.
Sam Hibbah bata son tsawa, shiyyasa da zaran Abban ya mata ita take rikicewa, yanzu ɗinma duk sai jikinta ya hau ɓari, muryarta na rawa alamar tahowar kuka tai saurin faɗin, “Kayi haƙuri Abba bansan ka tahoba ALLAH. Ina kwana”.
Ciki yay batare daya amsa mataba yana jan tsaki. Hibbah ta bisa da kallo wasu hawaye masu zafi na sakko mata bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Ido suka haɗa da Yah Usman. Ya girgiza mata kansa alamar kar tai kuka. Dan tun tsawar da Abban yay mata duk hankalinsu ya dawo kansu.
Suma koda suka gaishesa bai amsa musu ba. Sai faman mazurai yakeyi. Basu sakebi takansaba duk suka kwashi kayayyakinsu sunama Ummi sai sun dawo. Itako amsa musu take da fara'a tamkar batasan da zaman Abban a wajenba ma.
Yah Muhammad ne ya kama hannun Hibbah da ko motsi ta kasayi har yanzun. Sai da sukazo har wajen motarsa yasa handkerchief ya share mata hawayenta batare daya ce komaiba. Sauran ƴan uwansa ma kuma bai basu damar cewa komai ɗin ba. Sai umarnin yin addu'ar fita gida kamar yanda suka saba yay musu.
Suna kammalawa kowa ya hau abin hawansa. Yah Muhammad da Hibbah. Abubakar ya ɗauka Usman da Umar a motarsa dansu basu da mota har yanzu sai mashina. Ammar ma ya hau mashin ɗinsa lifan shi kaɗai tunda yau Hibbah tabi babban yaya...........✍
_BONANZA, BONANZA, BONANZA 20% OFF ZAFAFA PAID BOOKS, OFFER ENDS ON 31st DEC 12AM INSHA ALLAH!_
_ASSALAMU ALAIKUM!!_
_ZUWAGA MASOYA, KUMA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR._
_KORAFI YA KARBU, DAGA YAU LARABA 29 GA WATAN DECEMBER IN SHAA ALLAH, ZUWA 31 GA DECEMBER RANAR JUMU’AH KENAN. BISAGA KORAFI DA NEMAN RAGE KUDIN ZAFAFA NA DUBU DAYA KAN LITTAFAN BIYAR, IN SHAA ALLAHU, KORAFIN KU YA ISA GARE MU. KUMA MUN AMINCE. ZAMU KARBI 800 GA LITTAFAI BIYAR DIN DA KUKE BUKATA, A MAIMAKON DUBU DAYA NA BOOKS BIYAR. YAU LARABA ZUWA JUMU’AH KARSHEN WATAN DECEMBER KENAN. ZAMU RUFE KARBAR 800 KUDIN ZAI KOMA DUBU DAYA KARFE 12 NA DAREN RANAR JUMU’AH INSHA ALLAH._
_GA WATAN JANAIRU (3st JANUARY, ZAMU CIGABA DA KARBAR DUBU DAYA KAN LITTAFAN BIYAR._
_A KUMA 1 JANUARY DINNE IDAN ALLAH YA KAI MU, ZAMU FARA SAKIN PAGES DIN LITTAFAN NA KUDI, WATO PAID PAGES👏🏼👏🏼NA BOOKS DIN._
_LITTATTAFAN SUNE: *DABI’AR ZUCIYA (FALL IN LOVE)* NA SAFIYYAH HUGUMA_
_*HALIN GIRMA (GLAMOROUS LOVE)* NA HAFSAT RANO_
_*DEEN MARSHALL: (INTENSE LOVE)* NA MAMUH GEE_
_*SO DA ZUCIYA (A LOVE SO BEAUTIFUL)* NA: NANA HAFSAT MSS XOXO_
_*TAKUN SAAKA(LOVE IN TIME)* NA: BILLYN ABDULL._
_KAI DAGA JIN SUNAYEN KASAN ZA’A SHA GWAGWARMAYA A KUMA KARU DA DARUSSAN DA ZASU KOYAR, NA FADAKARWA DA NISHADANTAR WA HADI DA TACACCIYAR KAUNA MARAR GAURAYE_
_DOMIN KASANCEWA CIKIN MABIYA LITTAFAN ZAFAFAN SAI A TUNTUBE MU TA.👇🏾_
*_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*
*ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*
*_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*
*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*
*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*
*_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_*
*_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_*
*_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_*
*_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_*
*_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_*
*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*
2👉🏾400
3👉🏾500
4👉🏾700
5👉🏾1000
*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*
09134848107
*_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
#team zafafa biyar
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
__________________
*_ASSALAMU ALAIKUM BEAUTIFUL PEOPLE!! ZAFAFA BIYAR FAMILY💯💯🙌🏽❤️_*
_MUNGODE DA ZABIN LITTAFAN ZAFAFA BIYAR. ALLAH YA KARA BUDI YA KUMA BAR ZUMUNCI_
*_KAMAR KO DA YAUSHE, WANNAN KARON MA MUNZO DA KOKON BARAR YOUTUBE CHANNEL DIN YARON MU, SUDEIS MASOYI KUMA MAKARANCI, MAHADDACIN ALKUR’ANI MA GIRMA_*
_WANNAN KARON MA DAN ALLAH A TEMAKA ADANNA WA CHANNEL DINSA KARARRWA DOMIN KASANCEWA DA MU A DUK SANDA MUKA DORA FEFAN BIDIYON SA, A TALLAFA A KALLA A KUMA DANNA MASA SUBSCRIPTION. HAKAN NA KARAWA SUDEIS KWARIN GWIWAR SAKE DAGEWA YA KUMA KARA KAIMI WAJEN YIN KARATUN SOSAI. MUNGODE KWARAI💯🙌🏽❤️_
*_GA CHANNEL DIN DAKE YOUTUBE NAN👇🏾_*
https://youtube.com/c/sudaiskura
_Sudais is a young boy who has passion in recitation of the Holy Qur'an at a very young age._
_Please help him grow his YouTube channel by subscribing and liking his videos to encourage the little boy. Jazakumullahu khairan🙏🏻_
_________________________
*_Chapter Six_*
..............Ƙoƙarin kauda fuskarta taketa faman yi saboda kar Yah Muhammad ya ga hawayen dake guje-gujen sakko mata akan fuska tun bayan barowarsu gida. Sai dai kuma abinda bata sani ba tuni ya fahimci kuka takeyi, yadai mata shiru ne domin bata damar rage nauyin zuciyarta.
Sai da ya ɗauka titin da zai kaisu har makarantar tasu sannan yay gyaran murya batare da ya kalleta ba. Shiru Hibbah bata motsa ba saboda zurfi da tai a tunani....
“Auta!”
Ya kira sunanta cike da kulawa. Nanma shiru babu alamar ta jisa. Leɓensa yaɗan ciza na ƙasa yana gangarawa gefen titi. Harya kashe motar gaba ɗaya ya juya yana kallonta batasan mi yakeyi ba. Cikin damuwar data bayyana sosai akan fuskarsa ya ce, “Muhibbat!!”.
A firgice ta juyo garesa tana sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya. Sai kuma tai saurin kai hannunta akan fuskarta ta shiga share hawayenta tana ƙaƙalo murmushi. “Lah Yaya banjikaba ALLAH. Ina can wajen kallon hanya har idanuna na hawaye dan ƙauyanci”.
Murmushin da bai niyyar yi baneba ya suɓuce masa. A ransa yanajin ƙaunar ƴar ƙanwar tasu da yaba halinta na manya. Duk da rawan kanta da tsiwa ita ɗin yarinyace data san yakamata. Tana da wasu nagartattun halaye da sai ka nutsu gareta kake iya ganosu. Amma a kallo ɗaya zaka iya dangantata da yarinya mai rawar kai da shirme. Ya ɗanja numfashi yana furzarwa a hankali tare da kafeta da idanunsa irin nata.
“Mi kike tunani Muhibbat!?”.
A yanda yay maganar babu wasa a cikinta ne ya sata ɗago idanunta dake ƙoƙarin tara ƙwalla ta dubesa. Sai kuma tai saurin girgiza kanta tana ƙoƙarin maida kukan dake son ƙwace mata.
“Ba bu komai Yayah”.
Ta faɗa muryarta na rawa.
Sosai ya sake kafeta da idanunsa dake canja kala zuwa ɓacin rai. Sai dai kuma cikin tausasa murya ya ce, “Kin dai san banason ƙarya ko?”.
Kanta ta jinjina masa hawayen da taketa ƙoƙarin makalewa suka gangaro a hankali bisa fuskarta.... “Yaya! Abba ne, miyasa baya sonmu? Musamman ma ni ya tsaneni bayason ganina”.
Takai ƙarshen maganar tata da fashewa da wani irin kuka mai cin rai ga ma'abocin saurare. Idanunsa ya lumshe a hankali tare da cije leɓensa na ƙasa da ƙarfi. Addu'a ya fara karantowa a zuciyarsa domin samun dai-daito daga fushi da fusatar damuwar ƴar uwar tasa. Ya kamo hannunta cikin nashi ya rumtse da ƙarfi.
Kamar jira take ta sake fashewa da wani kukan, fuskarta ta kwantar akan hannayen nasu dake cikin na juna, hawayenta suka shiga gangarowa har akan fatar hannunsa data ɗora kanta a kai. Cikin kuka ta cigaba da faɗin “Yaya miyasa Ummi ta yarda ta auresa? Bayan kuma tasan shi ɗin mugu ne. Miyasa bata haƙura ta zauna damu mu kaɗai ba bayan rasuwar Abbanmu?. Wlhy Yaya banason Abba na tsanes.......”
“Muhibbat!”. Yay saurin katseta da ƴar tsawa.
Ɗago kanta tai tana kalonsa, ganin yanda ya ɗaure fuska ne ya sake sakata fashewa da kukan.
Yaya miyasa bakwaso nace banason Abba bayan shima baya son mu. Kullum shike gusar da farin ciki a kan fuskokinku. Duk randa yazo sashenmu sai Ummi tayi kuka a ɓoye. Sannan fuskarta tana kumbura kamar wadda aka daka Yayanmu”.
A matuƙar razane yake kallonta a yanzun. Dan tabbas tun basukai hakaba suke tambayar Ummi mike samunta a fuska a maban-banta lokaci, amma sai takan ce musu wani ciwo ne yake mata haka akan fuska lokaci-lokaci, amma tana shan magani. Sunsha damunta suje asibiti amma sai taƙi yarda. Sai dai kuma yau gashi ƙaramar ƙanwarsu tazo da wani batu mai girma. Shin kodai da gaske ne da ake cewa duk ƙanƙantar ɗiya mace tafi ɗa namiji lura da maida hankali akan abu.......
“Yayanmu dan ALLAH kasa mubar musu gidansu mu koma can wani gari da zama mu daina ganinsu suma su daina ganinmu.”
Hibbah ta katse masa tunani ta hanyar girgizasa tana kuka da roƙonsa.
“Tanee! kinga nutsu muyi magana. Maza share hawayenki na tambayeki”.
Da sauri ta shiga share hawayenta da handkerchief ɗinsa. Duk da wasu nabin wasu hakan bai hanata faɗin, “Yaya na goge”.
“Auta kin taɓa ganin wani ya daki Ummi ne?”.
Kanta ta girgiza masa.
“To miyasa kikace kamar ana dukanta?”.
“Yaya nidai haka kawai nake ganin kamar shatin yatsu a fuskarta a duk randa fuskan yay kumburi. Sai kuma ranar da Abba ya kwana a sashenmu na taɓa jin kamar tana kuka na fito ɗaukar ruwa dana manta ban ɗauka ba da dare. Tana kuka sosai, ina kumajin muryan Abba yana mata kamar magana cikin faɗansan nan”.
Kallonta kawai yake ko ƙyaftawa babu, acan ƙasan ransa kuma yanama kalamanta fashin baƙi dalla-dalla. Ganin yaƙi cewa komai yasata kai hannunta akan masa ta girgiza shi.
Ajiyar zuciya ya sauke da haɗiye damuwar dake neman kufcewa akan kamilalliyar fuskarsa.
“Yaya baka yarda ba ko?”.
“A'a Auta, taya zan ƙaryataki bayan nasan ke ɗin baki da ƙarya. Kawai dai ina nazari ne akan maganar taki. Amma inaga yanzu ba shine lokacin yinsa ba. Bara na kaiki makaranta karki makara. Idan mun koma gida zamuyi magana. Amma na roƙeki bayan ni karki faɗama kowa zancen nan har cikin su Usman kinji ko”.
“Insha ALLAH Yaya bazan faɗa musu ba. Amma dan ALLAH ka tambayi Ummi kaji ko Abba yake dukanta ne?”.
Ɗan murmushi yayi a ƙasan ransa yana jinjina wautarta. “Karki damu insha ALLAH bazan manta ba.
Koba komai ta ɗanji sanyi a ranta. Dan haka ta ƙarasa share hawayenta nauyin da zuciyarta yay mata yana sauka a hankali.
Tunda ya tada motar suka cigaba da tafiya sai shi ya koma cikin yanayin shiru ɗin. Dan gaba ɗaya tunaninsa da hankalinsa sun koma akan zantukan Hibbah.
Koda suka isa makarantar sai da ya sakata tai addu'a kafin ta fita a motar, ya miƙa mata 1k tare da mata gargaɗin ta dage akan text din da yaji Ammar ya faɗa zatayi. Inba hakaba bazai kaita chaina ɗin da take burin zuwa ƙaro ilimin kimiya da fasaha ba”.
Cike da son cikar burinta ta tabbatar masa insha ALLAH zata dage wajen cinye text ɗin da maki mai yawa. Daga haka ta shiga ɗaga masa hannu har yay reverse yabar wajen. Ƙoƙarin nufar department ɗinsu tayi ranta fal saƙe-saƙe itama. Ta duba department ɗin su Zahidah a ranta tana tunanin suma sunzo tuni, dan suma sunce mata suna da text yau tun 8am.
★★★★
Koda su Hibbah suka fita a class bata nema su Hafsat ba. Dan tanason samun nutsuwar ƙarasa aikinta na jiya. Kai tsaye ɗakin dake ajiye da na'urori mai ƙwaƙwalwa na department ɗin nasu ta nufa. Dan tana ɗaya daga zaƙaƙuran yara mata matasa dake baje kolin basira da ƙwazon da ALLAH ya basu akan ilimin kimiya da fasa.
Ta samu ɗalibai irinta masu naci da ƙulafuci ɗai-ɗai a ɗakin. Bataima kowa magana ba ta zauna a table guda ɗaya
dake daga can lungu tana sauke ajiyar zuciya, tsabar yanda take nacema Computer ɗin wajen saboda daɗin da take mata har security ta ƙirƙira ta saka dan tanada ajiye-ajiye da yawa a ciki. Akwai wani yaro da suke ƴar tsama da shi, shima yanada ƙwazo matuƙa akan fannin, ya taɓa mata manaƙisar lalata mata securitys ɗin data saka domin binciken abinda take ɓoyewa a Computer daba tata ita kaɗai ba. Aiko data tashi ita sai da tai masa ɓarnar daya gwammaci da bai aikata mata ba, dan babbar ma'ajiyarsa ta Computer ɗinsa dake gida taima kutse, tare da aikata ɓarna da har iyayensa sai da suka saka police zuwa har gida domin kamata. Sai dai kasancewar tana da Yah Abubakar hakan bata faruba, sukai ƙoƙarin ganin sun rufe case ɗin.
Flash ta ciro a bag ɗinta tai connecting da Computer ɗin ta shiga abinda ya kawota cike da ƙwarewa da fatan nasara. Kusan mintuna goma sha uku tana abu ɗaya, sai faman sauke ajiyar zuciya take akai-akai. Harma ta fidda rai da nasara sai gashi cikin amincin ALLAH ta kuma dace. Wani lallausan murmushi ta saki da ambaton kalmar “Alhmdllhi” tana rungume Computer ɗin dan farin ciki. Tuno da bata sanarma Yah Abubakar bane ya sata saurin ɗauka wayarta. Batare da tunanin komai ba ta dailing number ɗinsa. Sai dai harta tsinke bai ɗaga ba. Ta tura baki gaba alamar jin haushi tana ƙoƙarin sake kiransa. Nanma ɗin dai babu amsa. Cikin takaici ta ƙara ƙoƙarin sake kira a karo na uku sai ga nashi kiran ya shigo.
Ɗagawa tai da sauri tare da kwaɗa sallama cikin karaɗinta da shagwaɓa. Daga can Yaya Abubakar ya amsa yana faɗin, “Autar Ummi lafiya dai ko? Ina cikin aiki ne fa”.
“Lafiya lau Yaya dama fa wani abu zan sanar maka. Jiya baka dawo da wuri bane har nayi barci, ɗazun kuma na manta ne saboda Abba”.
“Okay to ina jinki”.
“Uhm yauwa Yayana. Kasan wani abu? Jiya muna fitowa a school wasu masu power bike suka kusan turemu, sanadin hakan ma har Hafsat ɗin gidan aunty Kulu ta samu rauni a ƙafarta sai da akai mata gyara a asibiti. To ni kuma tun a jiyan na jefa musu agogon nan nawa, yanzu haka na gano inda suk.......”
Kafin takai ƙarshen maganar tata ma Yaya Abubakar ya miƙe a zabure da ga can yana faɗin, “Masu power bike?!”.
“Yes! Yaya. Kasansu ne?”.
“Kinga auta kina ina? Wannan maganar bata waya bace zanzo yanzu na sameki, karfa ki faɗama kowa bayan ni”.
Kafin ta samu damar cewa wani abu ya yanke wayar.
“Oh Yaya kama tsaya na gama maganata mana zaka wani yanke. To nama fasa faɗa maka sai nan da awa uku”. Tai maganar tana haɗa kayanta da fushi ita a dole taji haushi. Tana ƙoƙarin rataya bag ɗinta a baya kira ya shigo wayar tata. Ganin Zahidah ya sata ɗagawa tana kai wayar kunnenta da nufar ƙofar fita daga wajen.
Tana cikin sauraren Zahidah dake faɗa mata inda take taje ta sameta taga ansha gabanta. Takaici ya sakata janye wayar daga kunnenta ta ɗago domin ganin wane shege ne ya tare mata hanya.
Turus ta ɗanyi tana kallon zaratan mazajen dake a gabanta riƙe da manyan bindugu tamkar wasu mala'ikun ɗaukar rai. Duk da rashin tsoronta sai da taji wani abu mai kama da firgici ya gitta mata. Ta motsa bakinta a hankali idanunta na wani mar-mar.
“Bayin ALLAH lafiya kuwa?”.
Ta tambaya tana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya.
Ɗaya da ga cikinsu ne ya nuna mata i'd card ɗinsa da faɗin, “Mu jami'an tsaro ne da ga hukumar ƴan sanda ta farin kaya. Munzo nan ne kuma dominki Muhibbat Aliyu Hamza”.
“Wurina kuma? To ni miya haɗani da ku? Wama ya faɗa muku sunana?”.
“Duk zaki sami amsoshinki idan munje office”.
A tsiwace tace, “Hu'um ai wlhy bazan biku ba, barama na kira Yayan.....”
Zare wayar da ɗaya daga cikinsu yayi ne ya saka sauran maganar tata maƙalewa. Ya katse kiran da taima Yaya Abubakar yana kashe wayarma baki ɗaya.
Wani yawu Muhibbat ta haɗiye da ƙyar tana binsu da kallo tare da ɗalibai ƴan uwanta da hankalinsu ya fara kaiwa garesu suka ɗan fara taruwa domin kallon mike faruwa. Mota suka nuna mata. Da farko batai niyyar shigaba. Amma tuna tana dasu Yaya Abubakar aduniya ya sata shanye dukkan wata fargabarta ta shiga motar tana ƙunƙunin amshe mata waya da sukayi.
Dai-dai lokacin da suke shigewa motar suma Zahidah da aka kai mata labarin anga ƴan sanda na neman ƙawarta ta iso wajen. Hankalinta tashe ta shiga ƙwala kiran sunan Hibbah da sam batama jita ba. A firgice ta lalubo wayarta domin san kiran Ummi ta sanar mata ko zata sanarma cikin su Yaya Umar, dan ruɗewar da tayi tasa tama manta da cewar Yaya Ammar shima anan makarantar yake nasa karatun, yana a shekarar ƙarshe ne ta kammalawa..
★♣♠♣♠♣♠♣★♣♠♣♠♣♠♣★
Ummi na zaune a can inuwar mangwaro dake backyard ita kaɗai tun barin Abba sashen nata bayan ya gama shuka mata shika-shikan rashin mutuncinsa da ya saba. Lalle take sakama yatsun hannunta dan ita mace ce mai son jan lalle sosai. Har takai ta koyama Hibbah kasancewar tun tana ƴar ƙaramarta take mata itama.
Kallon wayarta da kira ya shigo tayi duk zatonta ma Hibbah ce. Batai mamakin ganin Zahidah ba, dan tasan Hibbah zata iya amfani da wayar tata wajen kiranta idan tata wayar babu kuɗi. Ɗayan hannunta tasa ta ɗauka wayar fuskarta da Murmushin tuna a yanda Autar tata ta fita cike da tsoron Abba a tare da ita.
“Autan Umminta yaya dai?”.
Ta faɗa dai-dai lokacin da take ɗora wayar akan kunnenta.
“Ummi ba ita bace nice Zahidah”.
Jin yanda muryan Zahidah ke rawa kuma a firgice ya saka Ummi ruɗewa ta shiga jera mata tambayoyi..
“Ummi akwai matsala ne wlhy, yanzu ina capteria muna waya da Hibbah ina faɗa mata ta fito class ina jiranta muci abinci sai wayan ya katse. Ina ƙoƙarin sake kiranta a zatona network ne sai ga wani course mate ɗina yazo yake sanar min ga jami'an tsaro can suna neman sister ɗina. Na tafi domin tabbatarwa kawai na iske harta shiga motarsu sun wuce da ita Ummi. Ni kuma gashi bani da no ɗin su Yaya Abubakar balle na sanar musu shine na kiraki dan ki sanar musu”.
_(Hasbinallahu wa-ni'imal wakil)_ Ummi ta shiga mai-maitawa da sauri-sauri dan jin wani irin yuuu cikin idanunta da kanta. Cikin ƙoƙarin haɗiye tashin hankalin da take ciki ta ce, “Wani laifin ta aikata ne Zahidah?”.
“Ni dai Ummi a sanina bata aikata komaiba wlhy.”
“Shikenan bara na kira Abubakar naji idan yana kusa ko Muhammad”.
“To Ummi”. Zahidah ta faɗa tana share hawayen da suka gangaro mata akan kumatu. A kallo ɗaya zaka fahimci a matuƙar firgice take. Gashi ita kaɗai ce yau dan Hafsat batazo ba saboda ƙafarta.
Hango Yaya Ammar da ke nufota da sassarfa ya sakata tunawa da yana a cikin makarantar shima. A zabure itama ta nufosa.
“Zahidah! Ina Muhibbah?”.
Ya faɗa cikin furzar da hucin hakkin gudun da yayi dai-dai isowarsa gabanta.
Bayanin abinda ta sani da wanda taji a bakin mutane tai masa tana share hawaye. Hankalinsa ya ƙara tashi matuƙa shima. Dan duk tsokanarta bata taɓa kaiwa matakin hakaba, a yanda yaji wai ƴan sanda da manyan bindugu ya matuƙar harmutsa tunaninsa.
Babu shiri ya shiga neman no ɗin Yaya Abubakar, sai dai kuma number busy take nuna masa alamar yana waya da wani kenan ko makamancin hakan. Maida akalar kiransa yayi akan Yaya Muhammad. Bugu biyu ya ɗaga. Ko sallama bai masa ba ya shiga masa bayanin abinda ke faruwa.
Ko tari kasa yi Yaya Muhammad yay. Sai numfashinsa ne dake tafiya a sarƙe tamkar mai ciwon Asthma. Batare da ya iya furta komai ba ya yanke wayar. Kamar jira sai ga kiran Ummi ya shigo masa.
Sam baiyi tunanin taji mike faruwa ba itama. Dan haka yay ƙoƙarin saita kansa dan ganin bai tada mata hankali ba. Sai dai a yanda yaji muryarta tun a sallama ya matuƙar tada masa hankalin. A hautsine ya shiga tambayarta lafiya? Dan ko kaɗan basason tashin hankalinta.
Duk yanda Ummi taso danne damuwar dake a cikin muryarta ta kasa hakan. Cikin gwamewar numfashi ta shiga yimasa bayanin duk yanda sukayi da Zahidah.
Da sauri ya ce, “Ummi dan ALLAH ki kwantar da hankalinki, insha ALLAH zamu nemi idan take bara na nema Abubakar yanzun nan”.
Bai jira cewarta ba ya yanke wayar dan bayason shima ta fahimci rauninsa kai tsaye..............✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Chapter Seven_*
..........Lokaci da aka basu da ga gidan gwamnati na kamo wannan gagarumin ɓarawo da babu wanda yasan ainahin kamanninsa na zahiri yay matuƙar tada hankalin kowacce hukuma ta ƴan sanda dake a jihar. A ɓangaren jami'an ƴan sanda na farin kaya tuni sun duƙufa wajen bincike suma. Musamman da ya kasance jami'ansu ne suka sami nasarar samo wheelchair da sauran kayan da ɓarawon yay amfani da su a waccan ranar.
Tabbas wannan ɓarawo yana da matuƙar wayo da dabaru kala-kala da ganosa ke bama duk wasu jami'ai wahala kai tsaye. A duk ɓarnar da zai aikata yana aikatata ne da maban-banta fuskoki da salo daban-daban kuma. A kusan shekara biyu kenan da fitowarsa a bayyane babu wanda zai iya cewa ga fuskarsa ta ainahi ko samun wani labari nasa koda ƙanƙani ne.
Duk da dai wasu a cikin jami'ai da suka ƙware sosai wajen aiki da binciko mai laifi sun taka rawar gani sosai wajen kafa masa tarkuna na musamman amma yana tsallakesu saboda duk tsiyar da zai shuka ba gaba gaɗi yake aikata ta ba sai ya shirya da shiri na gaske.
Bayan zama na musamman da sukayi jiya game da binciken da sukeyi akansa furucin matashiyar budurwa ya shigo cikin jerin abubuwan da suka zauna domin tattaunawa. Lokaci ne da bai kamata suyi sakaci da duk wata dama da zatazo musu ba komin ƙanƙantarta. Dan haka basu tsaya sanya ba wajen bibiyar matashiyar budurwa mai cikakken suna *_MUHIBBAT ALIYU HAMZA_* da jami'insu ya kawo musu labarin alwashinta akan abin farautarsu. Dan haka suka kasance biye da ita tun a safiyar yau, tun daga ƙofar gidansu har zuwa cikin makaranta, shigarta class da fitowarta zuwa Computers room. Dukkan binciken data gudanar har zuwa kiran da taima Yaya Abubakar duk akan idon wanda ke biye da ita ne batare data sani ba...
Sosai tashin hankali ke tattare da Muhibbah ganin inda aka kawota. Duk da Yayanta jami'in tsaro ne na ƴan sanda mai muƙamin d.p.o bata taɓa zuwa police station ba. Amma a yau sai gata a cikin headquarters na ƴan sandan farin kaya tsumu-tsumu batare da tasan laifin data aikata ba.
Wani lafiyayyen office aka kaita da yaji kayan more rayuwa tamkar ba'a hukumar ƴan sanda ba. Ta saci kallon dattijon mutumin dake zaune kansa duƙe yana aiki kan takardun dake a gabansa. Cikin girmamawa wanda ya shigo da ita office ɗin ya ƙame yana salute ɗinsa.
Sai a lokacin ya ɗago fuskarsa ɗauke da murmushi ya dubesu ita da shi. Kansa ya jinjinama wanda ya kawota ɗin idanunsa a kanta. Gurin zama ya nuna mata da faɗin, “Ɗiyata bismilla zauna ko?”.
Ajiyar zuciya ta saki dan har cikin ranta ta ɗanji sanyi. Gaishesa tayi da girmamawa zuciyarta na sake samun nutsuwa da shi. Ko ba'a faɗa mataba a yanayin shigarsa da shekarunsa ya isa tabbatar mata shi ɗin mai faɗa aji ne a hukumar.
Ɗan kafeta yay da idanusa na kusan sakan ashirin ko ƙyaftawa bayayi. A take tsigar jikinta ta fara tashi tsoro na sake faɗaɗa a zuciyarta. _Hasbinallahu wa-ni'imar wakil_ ta shiga maimaitawa tare da sunayen ALLAH.
Murmushi ya sakar mata da yin ƙaramar gyaran murya yana ɗauke idanun nasa a kanta. Cikin taushin murya yace, *“Muhibbat Aliyu Hamza ko?”.*
Hibbah ta jinjina masa kanta cikin dakiya da dauriyar hana bayyanar gazawarta tana faɗin, “Eh yallaɓai”.
“Ɗalibar koyon kimiya da fasaha a babbar jami'a ta jihar nan?”.
Nanma kanta ta jinjina masa da faɗin, “Eh yallaɓai”.
“Uhm masha ALLAH. ALLAH yay riƙo da hannayenki ki zama abar alfahin ƙasarki baki ɗaya. Ina matuƙar son naga ƙananun yara musamman ma mata masu himma da ƙwazo akan abinda yay mana ƙaranci irinki”.
A karon farko Hibbah ta saki murmushin jin daɗin yabon data samu da ga garesa tana faɗin, “Thanks you Uncle”.
Murmushi ya sakar mata har haƙoransa na bayyana. “Kinsan miyasa aka kawoki nan?”.
“A'a Uncle”. Ta faɗa cike da marairaicewarta da taso bashi dariya amma sai ya danne. Cikin ƙwarewar aiki ya ce, “Taimakonki muke nema akan masu power bike ɗin jiya da suka kusan tureku, harma sister ɗinku taji ciwo a ƙafarta”.
Kallonsa Hibbah tayi cike da tsarguwa. Fahimtar hakan da yayi ya sashi saurin faɗin, “Muna son gano kosu ɗin ƴaƴan waye? a garin nan, mu kuma kamasu mu hukuntasu. Dan bai kamata ba ace dan kawai suna ƴaƴan masu arziƙi ba su dinga shatar tituna suna zabga gudu tamkar nasu su kaɗai. Zasu iya amfani da wannan damar suyita kashe al'umma saboda ƙarfin ikon iyayensu kuma talaka bazai iya kai ƙara a ƙwatar masa haƙƙinsa ba. Yanzu bayan ALLAH ya taƙaita muku wahala jiya da bamusan halin da kuke ciki ba zuwa yanzu ai ko. Kalla nan kiga”.
Ya ƙare maganar yana ɗaukar remote ɗin da ke gabansa tare da janye idanunsa a kanta ya maidawa ga ƙatuwar tv dake mamake da kusan rabin bangon office ɗin. “Kinsan wannan mutumin?”.
Fuskar dattijo mai cike da ƙasumba a cikin shigar manyan kaya ta bayyana. Kallon kusan minti ɗaya tai masa kafin ta girgiza kanta. “A'a yallaɓai ban sanshiba. Bamma taɓa ganinsa ba”.
Wani ya kuma nunowa da faɗin, “Wannan fa?”.
“Shima haka ban sanshi ba”. Hibbah ta faɗa idonta akan hoton matashin saurayi mai saida rake a Wheelbarrow.
Cigaba yay da latso mata hotuna kala-kala na mabanbanta mutane tana cewa bata sansu ba. Sai wani guda biyu na kusan ƙarshe data taɓa gani an nuna a labarai kwanaki.
“Yallaɓai wannan dai na taɓa ganinsa a tv, dan an taɓa nunasa kwanaki a labarai, kuma hoton yata yawo a social media akan cewar shi ɗin babban ɓarawo ne ɗan yahoo da ya yashe manyan kuɗaɗen wani attajiri. Yayana ma yace suma suna nemansa ruwa a jallo. Kuma nemansa kukeyi halan?”.
Sosai ma kuwa nemansa muke muma tare da waɗancan na farkon dana nuna miki. Amma rashin mai taimaka mana irinki yasa mun gagara hakan. Amma shiɗin wanene yayan naki?”
Kanta tsaye batare da tunanin komai ba ta ce, “Uncle shima ɗan sanda ne”.
“Woow masha ALLAH. Lallai naji daɗin hakan sosai. Kuma zanso ganinsa shima harma nai masa ƙarin girma saboda samun ƙanwa irinki mai ƙwazon da ya kamata ƙasa gaba ɗaya tai alfahari dake”.
Murmushi tayi cike da jin daɗin jin za'a ƙarama Yaya Abubakar ɗinta girma ta sanadinta. Shima ganin ta hau yanda yake buƙata saboda ƙuruciya sai ya ƙara faɗaɗa murmushinsa da faɗin, “Idan har kikai mana wanann taimakon da zan miki bayani akansa yanzun to lallai yayanki zai ƙara zama babban mutum, kema kuma zaki rama jin ciwon da aka saka ƙawarki tayi jiya. Da ga ƙarshe zaki samu ƙyauta mai tsokar gaske”.
Batare da tunanin komaiba ta ce, “Insha ALLAH zan taimakeku Uncle, indai Yaya Abubakar zai ƙara samun girma”.
Cike da jinjina wautarta fara'ar fuskarsa ta sake bayyana. “Yauwa ɗiya ta. Aikin da zaki mana shine gano mana inda masu power bike ɗin jiya suke.”
“Lah Uncle ai nama g.....”
Sai kuma tai shiru tare da dafe bakinta saboda tunowa da gargaɗin Yaya Abubakar na ɗazun akan karta sake ta sanarma kowa.
“Miya faru ki kai shiru ɗiyata?”.
Da sauri ta girgiza masa kanta. “Babu komai Uncle, inason kai musu magana su fara bani wayata nayi magana da Yaya Abubakar”.
Shiru yayi cike da nazarinta, a zuciyarsa. Yace (Yarinya mai wayo). A fili kam ganin ta kafesa da ido yay saurin sakin murmushi. “Okay okay babu damuwa zan musu magana su baki. Amma kafin hakan zaki cika mana alƙawarin mu. Idan ba hakaba kuma zamu cigaba da riƙeki anan, tare da sakawa a kamo mana Mamanki dasu yaya Abubakar ɗin naki mu faɗama duniya cewar sunada alaƙa da wancan hotunan mutanen da muke nema kin amince?”.
A take dukkan fara'ar dake kan fuskar Hibbah ta ɓace ɓat. Shima tuni saɓanin murmushi ya maye gurbin tasa fuskar. Ya kuma tsatstsare ta da idanunsa cike da tsoratarwa. “Yanzun nan zan bada umarnin zuwa a ɗakko min Umminki. Tare da Yayanku Muhammad har wajen aikinsa. Sai Umar da Usman. Aliyu (Ammar) kuwa yanzu haka akwai jami'anmu dake zagaye da shi a makarantarku. Kalla nan”.
Ya ƙare maganar da juya mata lap-top ɗinsa. Wani irin firgici da ruɗani ne suka bayyana a fuskar Muhibbat ganin hotunan Yayunta tare da hotunan ɗazun daya nuna mata na waɗanda ake nema. Kowanne da taƙaitaccen bayanin dangantashi da waɗan can masu laifin. A ƙarshe aka bayyana Ummi matsayin mahaifiyarsu tare da ita mai taimaka musu kasancewarta masaniya akan ilimin sarrafa Computer.
Saurin ɗora hannunta tayi akan baki saboda kukan dake neman kufce mata. Ta shiga girgiza masa kanta a kiɗime. “Please yallaɓai kar kai haka dan ALLAH. Ni ƴan uwana ba ƴan ta'adda bane. Basu taɓa aikata laifin komai ba sai alkairi. Karka zaluncesu ta dalilina....”
“Inhar baki so ganinsu a cikin wani hali sai kiyi mana abinda muka sakaki ki zama sanadin alkairinsu. Bawai ina lallaɓaki bane dan bazamu iya sarrafaki kimana dole ba. Inda naso tursasaki da tun a daren jiya zamu ɗakkoki har gida kiyi mana aikin akan dole.” yay maganar a matuƙar kausashe yana bugar desk ɗinsa.
Ɗan zabura baya Hibbah tai jikinta na rawa. Yayinda shi kuma ya shiga ƙwala kiran sunan jami'in su Nura.
Da sauri Nura ya shigo yana ƙamewa da faɗin, “Yes sir!”.
“Maza a shirya jami'an da zasu fita operation yanzun nan.”
“Okay sir”. Ya sake faɗa da girmamawa yana ficewa.
Miƙewa yay shima yana nuna Hibbah da faɗin, “Oya miƙe”.
“Yallaɓ.....”
Hannu yasa yay zipping bakinsa alamar karta sake cewa komai.
Ɗakin da ke ajiye da na'urori masu ƙwaƙwalwa aka kai Hibbah. Inda suka sami mutane kusan goma sha uku a ciki. Kai tsaye wajen zama aka nuna mata alamar dama ita ake jira. Zama tai tana haɗiyar zuciya. Batason yin aikin saboda gargaɗin Yaya Abubakar. A gefe kuma batason a cutar mata da ahali akan abinda basu ji ba basu gani ba. A wani gefe na zuciyarta kuma nason yi kodan abinda mutanen suka nema yi musu jiya har ga Hafsat da ciwo.
Waya irin ta jami'an tsaro aka ajiye a gabanta. Tare da kunna ƙaton tv irin na office ɗin data baro da shima ke a jikin bango. Hoton yayunta da rahotannin da aka shirya na karya dan tsoratar da ita suka bayyana.
Ta sauke idanunta dake cike da ƙwalla a hankali bisa computer ɗin gabanta.
“Ki nutsu wajen yin aikin da zai ƙuɓutar da ƴan uwanki zama criminals zuwa taurari ta sanadinki, ko kiyi sakacin yin aikin da zai dusashe haskensu da ga taurari zuwa criminals ta sanadinki.”
Mutumin ɗazu ya faɗa cikin tabbatarwa da murya mai kaushi.
Kai kawai ta jinjina masa tana maijin wani ɗaci a zuciyarta da taurin zuciya. Sai da tayi addu'a a cikin zuciyarta kafin ta fara aikin cike da ƙwarewa. Kasancewar ɗazun dama ta binciko a inda suke sai yanzu batasha wahala ba duk da wannan Computer ɗin nada matuƙar tsaro fiye da tasu ta makaranta.
Da wayar gabanta ta dinga amfani wajen yin magana da jami'an da suka fita operation ɗin tana sanar musu hanyoyin da zasu bi har zuwa location ɗin da agogon data jefama masu power bike jiya yake. Hakan shike nufin tabbacin samun su inhar agogon na tare da su basu farga sun yadda ba.......
\★/★\★/★\★/★\★/★\★/★\
Anguwar *_jahje street_*, anguwace mai ƙarancin rashin hayaniyar jama'a kasancewar ta ɗauke da manyan gidaje na masu hannu da shuni. Ko da rana ka shigo wannan anguwa zaka sameta tsit tamkar halittun da ke a cikinta basa numfashi. Akan samu ƙarancin gittawar ababen hawa da na mutane masu tafiya a ƙafa sai dai jefi-jefi. Shima hakan tafi kasancewa a ranakun hutun ƙarshen mako ko hutun ranakun ma'aikata da kan gitta.
Sabo da rashin sakewarsu da juna yasa bazasu iya tantance kansu ba dan rayuwa ake ta babu ruwan wani da wani. Idan kaga magana ta shiga tsakaninsu sai idan ALLAH yasa ka fito maƙwafcinka ma ya fito ai gaisuwar hello hi shikenan kowa ya shige sabgar gabansa.
A cikin gida mai lamba 110 matasan samari ne da shekarunsu zai iya kaiwa ashirin da biyar zuwa da shida, harma mai da bakwai za'a iya samu. Gaba ɗayansu bakwai zaune suke a ƙayataccen falon gidan mai matuƙar girma da ƙawa ga mai kallo. Su dukansu kowa harkar gabansa ya ke yi. Wasu na kallon ƙwallo, wasu na daga gefe suna sarrafa wayoyin hannunsu.
Ɗaya da ga cikinsu ya nutsu wajen sarrafa waya. Sai dai a hakan hira kan shiga a tsakaninsu musam akan kallon ƙwallon da mutum huɗu suka fi maida hankali a kansa.
Wani mahaukacin horn daya nema harmutsa kwaƙwalensu da ga gate ya sakasu miƙewa a rikice gaba ɗayansu suna ambaton *_Master!!_*. Biyu da ga ciki suka shiga tattare ledojin dattin da sukai ciye-ciye tare da gwangwanen maltina da coc.. Ɗaya ya fita a guje domin zuwa ya buɗe masa ƙofar falon da ke rufe da security.
Buɗe ƙofar yayi dai-dai da isowarsa cikin takun ƙasaita da tabbatar da shiɗin fa ya isa. Sanye yake cikin baƙin wando jeans da baƙar t-shirt. Sai dai ya ɗora jacket baka itama a samanta batare da ya ja zip ɗinta ba. Sam ba'a ganin fuskarsa, sakamakon hular jacket ɗin dake har saman kansa, ga norse mask da baƙin google toshe da idanunsa. Ƙafarsa ma sanye take cikin baƙin takalmi.
Cikin zafin nama da ALLAH yay masa yasa hannunsa da ke sanye cikin safar hannu ya matsar da wanda ya buɗe masa ƙofar ya shigo cikin falon.
Hakan ya kara tabbatar musu da babu lafiya, dan kowa bai kalla a cikinsu ba ya nufi wata ƙofa a hargitse.
Kallon juna sukayi cike da tsoro, cike da ƙarfin hali ɗaya da ga cikinsu yace, “Brothers babu lafiya fa”.
“Tabbas babu lafiya Khalid. Akwai abinda ya saka Master a wannan yanayi.....”
Maganar tasa ta kakare a maƙoshi saboda fitowar wanda suke kira Master. Cikin wata irin murya mai amo da nutsuwa ya fara magana da faɗa. “Ina kayan da kuka fita aiki da su jiya?”.
A tare sukai rige-rigen nufar ɗakunan barcinsu. Babu jimawa sai gasu suna dawowa ɗaya bayan ɗaya da kayan a hannu. Na'urar bincike da ke a hannunsa ya shiga kangawa jikin kayan. Akan jakkar Habib ta tabbatar da zarginsa. Ya fisgi bag ɗin da sauri yana zazzage dukkan abubuwan da ke a ciki, sannan ya ɗaura na'urar akan kayan. Saurin daukewa yay ya sake maidawa akan jakar. ƙaramin fuskar agogo mai kama da flower dake manne a jiki ta fara kawo jar danja tana ɗaukewa. Yay saurin fisge agogon da dudu-du girmansa bai wuce girman ficika ba. Numfashi ya fusga da ƙarfi, hakama sauran yaran nasa duk sai da sukai ajiyar zuciya. Dan abinda sukaga ya cire ɗin ya tabbatar musu wani ya kafa musu tarko ne ba tare da sun farga ba.
Batare da yace dasu komai ba ya nufi na'urorin dake acan gefen falon an katangesu da glass na ƙawa daya zamewa falon baki ɗaya ado. Cikin wata na'ura ya saka agogon, bayan kamar sakan biyar ya cire ya fito ya nufi waje. Yana fita suka shiga kakkauda duk wani kaya suna maida shi a salon da zai basu kariya dan da alama yau ta ƙwaɓe.
Baifi mintuna uku da fitarba sai gashi ya dawo. Hanyar ƙofar da ya nufa ya sakasu binsa da sauri suma dan sun kammala kauda dukkan abinda ya kamata su kauda ɗin. A kuma dai-dai lokacin sukejin ƙarar buɗe gate ɗin gidan alamar wanda suka sami nasarar bibiyar tasu sun iso. Sun kumafi ƙyautata zaton ƴan sanda ne abokan *_TAKUN SAAƘAr_* su.............✍
*_Hum, wannan fa shine ana dara ga dare yayi🐒🚶🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_MG's SKINCARE_*
*_Ina manyan Mata, da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau?_*💃🏻
*_To maza kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki_*
*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*💃🏻💃🏻
*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne a gareku💃🏻_*
*_Sai kuma beauty kit gbdy na gyaran jiki, su cream da komai ne acikin shi💃🏻_*
*_Then akwai bridal kit shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*
_Duk zaku tabbatar da hakanne ta hanyar nemansu ku gwada kuma har sai kun bama wasu labari💃🏻😍🥰_.
Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift
_*Sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks, juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_
*___________________________*
*_Chapter Eight_*
...........Wani wawan tsaki ya ja tare da kai hannu kan Wadrobe ɗin dake a jikin bangon ɗakin ya danna wani maɓalli. A take ta zuge kanta, ɓoyayyar ƙofar sirri da ke a jikin bangon ta bayyana.
Cikin sauri suka shiga shigewa mamaki fal ransu, dan ko su da ke tare da shi tsahon shekaru basu taɓa sanin da ƙofar ba. Bama batun ƙofa kawai ba, ko fuskarsa ta ainahi har yanzun basu sani ba. Yanda yake zuwama duniya da mabanbanta fuskoki suma haka yake zuwa musu, duk da kuwa akwai alaƙa tsakaninsa da wasu a cikinsu ta zuminci.
Shi mutum ne mai aiki da matuƙar taka tsan-tsan a kowane ɓangare, shiyyasa yay dogon zangon da har yanzu an kasa cimmasa a duk tarkuna da ake ɗana masa, dan kota ina idanunsa a buɗe suke, hakama kunnuwansa. Sai da duk suka gama fita yana kallon jami'an tsaron da ke shigowa cikin gidan da sanɗa ta cikin tab ɗin dake a hannunsa. “Humm” ya faɗa yana rufe tab ɗin, shima yabi bayan yaran nasa tare da maida ƙofar a yanda take kamar babu.
Koda ya fito bai tankasu ba, sai wasu ƙananun fitilu masu azabar haske daya fiddo a aljihun wandonsa ya shiga kunnasu yana mika musu, A take ko ina ya gauraye da haske har suna iya ganin gabansu. Sam babu ruwa ko datti a ciki, hanyace ɗoɗar da basusan iyakarta ba, domin dama can ba'a yisa dan ruwa ya wuce ba. Sukam dai ɗunbin tsoro da mamakin Master ɗin nasu tuni ya gama kashesu a tsaye. Tun fitowarsu a ɗakin da suka tsinci kansu a cikin doguwar hanyar ruwa komai ya kuma kwance musu game da shi. Sagade sukai suna kallon ikon ALLAH da sake tsorata da al'amarinsa. Lallai sun sake yarda da gaskiyar zantukan mutane da ke kiransa *Hatsabibi shu'umi*.
“Zakuje ne ko zaku tsaya kallo na?”.
Sautin furicinsa ya maido da hankalinsu jikinsu kusan a tare lokaci guda.
Da sauri suka haɗa baki wajen faɗin, “Sorry Master!”.
★★★
Jami'an tsaron da suka iso anguwar bisa jagorancin Hibbah da ke basu haske ta hanyar waya kuwa tun kafin su iso gidan suka ajiye motocinsu can farkon layin suka ƙaraso da ƙafa. Mai-gadi da dama yake zaman jiran tsammani kamar yanda Master yay masa bayani ana yin knocking gate ɗin ya tashi ya buɗe bayan ya ƙara ƙarar redio ɗinsa da yake ji.
Jami'in da ya fara isowa wajen cikin son nuna basaja ya bama mai-gadi hannu yana murmushi. Babu musu shima mai gadin ya bashi hannu sukai musabaha cikin nuna ƙaulanin rashin sani.
“Sai dai gashi ban waye kaba bawan ALLAH. Kuma su alhaji basu sanarmin wani baƙo zaizo nan ba”. Mai-gadi ya faɗa lokacin da yake sakin hannun jami'i da yazo a suffar basaja.
Jami'in da furucin mai-gadi ya ɗan tsaya masa a rai ya ce, “Kana nufin masu gidan basa nan kenan?”.
“Tabbas basa nan mai-gida. Yau kwanansu tara kenan da komawa can ƙasar da suke zaune ai”.
Wani kallon kama rainamin hankali jami'in yay masa, amma sai ya saki murmushi da maida hannayensa baya yanama ƴan uwansa alamar su taho ba tare da yasan mai-gadin na lure da shi ba.
Baki mai-gadi ya buɗe zai sake magana sauran jami'an suka iso suma. Bindiga wanda ya fara zuwa ya nuna masa tare da turasa cikin gidan duk suma suka shishshigo. Duk rarrabuwa sukai a kowace kusurwa ta gidan suka fara shiga da sanɗa, wanda ya fara zuwan kuma na tare da mai-gadi da zuciyarsa ke cike da tsoron kar dai ƙaryarsu ta ƙare yau, dan shi duk tunaninsa su Master na'a cikin gidan suma tunda bai sanar masa shirinsa ba bayan aikin da zaiyi kawai. Duk da ya yarda da hatsabibancin uban gidan nasu amma dolene akwai ɓacin rana. Da alama kuma idan har ta ƙwaɓe yau da shi zata fara ruftawa. To amma insha ALLAH zaiyi ƙoƙarin ganin ya bi duk abinda Master ya faɗa masa yanda ya kamata.
Sai da jami'in nan ya tabbatar abokan aikinsa sun gama zagaye gidan sannan ya tasa ƙeyar mai-gadi shima suka nufi ciki. Ƙofar shiga da suka fahimci a rufe take suka bashi umarnin buɗewa. Amma sai ya nuna musu sam bai san password ɗin ba shi.
Jikinsa jami'in ya fara laluba, ya ciro waya nokia da tasha ɗaurin ƙyauraye da salataf. Wayar ya jujjuya a hannunsa yana ƙare mata kallo fuska a yatsine, kafin ya maida dubansa garesa yana sake gyara zaman bindigar da ya ɗora masa a saman kai.
“Nasan dai kanada number ɗin mai-gidan, maza ka kirashi yanzun nan ya faɗa maka password ɗin komu ɓalla ƙofar a yanda muka gadama.”
Babu wani nuna damuwa ko ɗar mai-gadi ya amsa wayar ya shiga laluben Number. Dailing yayi kansa tsaye, sai dai harta tsinke ba'a ɗaga ba. Ya sake kira a karo na biyu, sai da taje gab da tsinkewa aka ɗaga cikin muryar isa. Cikin girmamawa mai-gadi yay gaisuwa, sannan ya ɗara da bayanin cewar jami'an tsaro ne sukazo gidan suna buƙatar password na ƙofa wai zasuyi bincike, bai san mi suke nema ba. Carab jami'in ya amshe wayar yasa a kunnensa bayan ya kalla no. Ɗin da mai-gadin ya kira ya tabbatar da ta ƙetare ce.
“Jami'an tsaro kuma? Rabi'u!. To mu miya haɗa gidanmu da jami'an tsaro?”.
“Bincikenmu ne ya nuna mana wannan gidan na masu laifine Alhaji. Bazamu tabbatar da ba haka bane ba sai mun shiga mun duba kuma. Dan haka muna jiran mabuɗin sirrin ƙofar da ga gareka kawai, kafin muyi magana ta gaba da kai idan har ya kama”.
“Okay to babu damuwa yallaɓai”. Daga can aka faɗa tare da zayyano masa password ɗin.
A sakawa ɗaya kuwa ƙofar ta buɗe. kusan rabi a cikinsu suka shiga ciki akabar wasu a waje. Akan idon mai-gadi suka shiga hargitsa gidan tako ina. Sai dai abin mamaki babu wani alamun abun rashin gaskiya da sukayi gamo da shi. Cikin glass ɗin nan da computers ke ciki ɗazun yanzu babu shi, sai wasu ƙayatattun flowers masu ɗaukar hankali da ƙamshinsu ya cika falon.
“Tabbas yarinyar nan ƙarya take mana. Ko tana ɗaya da ga cikinsu ne yawo da hankalinmu kawai take son yi”. Ɗaya daga cikin jami'an ya faɗa a hasale.
“Sam banajin hakan a raina, akwai dai wani ɓoyayyen abunda bamu sani ba. Karku manta shiɗin mutum ne mai matuƙar wayo da dabaru kala-kala. Tabbas ya fahimci ana bibiyarsa ne ya bada ƙafa. Kokuma yayi amfani da wanann location ɗin domin sakamu zargi.”
“Nima zuciyata tafi rayamin hakan yallaɓai”. Wani ma ya sake faɗa cikin jin zafi.
“Karku samu damuwa. ai rana 99 da tara na ɓarawo, ɗaya tak na mai kaya. Inhar kere na yawo, zabo na yawo watarana dole a gamu. Tunda yace shi hatsabibi ne ya samu dai-dai da shi kuwa. Zamu bar wasu a gidan nan har sai mun tabbatar da gaskiyar babu wani abun zargi a cikinsa”.
Duk sun amsa da girmamawa. Shi dai mai-gadi kallonsu kawai yake yana kwasar dariya a zuciyarsa. Koda suka fito harabar gidan sun tsara wanɗanda za'a bari, wanda zasu koma kuma suka nufi hanyar barin gidan. Karaf idon ɗaya ya sauka akan bag dake rataye acan ƙarshen gate ɗin gidan ta waje. Saurin zuwa yay ya ɗakko yana nuna musu. Commander ɗin operation ɗin nasu ya amsa yana zazzage jakkar cikin kulawa gudun kar a saka musu bom a ciki.
Agogon Hibbah ne ya fara faɗowa tare da takarda mai ɗauke da sunansa akoda yaushe da facemark. Sai ɗan gajeren rubutu a bayan takardar.
*_“Bibiyata na nufin ƙare rayuwarku a wahala. Inhar bani naso kusan niɗin wanene ba, bazaku taɓa ganoni da kanku ba har abada insha ALLAHU rabbi. Dan haka ku daina azabtar da kanku wajen bibiyata komai yana da lokacinsa”_*
_Master👌🏼_
Wani wawan tsaki jami'in daya gama karanta takardar yaja. Ya cije leɓensa na ƙasa da ƙarfi, cikin alwashi yace, “Ni kuma na maka alƙawarin da wannan hannun nawa zan kamaka, sannan na maka horo mai tsananin gaske wanda sai ka gwammaci mutuwarka da rayuwarka shaiɗani”.
Suma sauran zukatansu na matukar ƙuna suka ɗauki nasu alwashin.....
___________★★★__________
Yaya Abubakar ya shiga tashin hankali matuƙa lokacin da yake isowa cikin makarantar su Hibbah yaji abinda ya faru a bakin Ammar da Zahidah. Tare da samun ƙarin bayani a bakunan wasu ɗaliban.
Da taimakon wani malamin su Hibbah ya shiga Computers room nasu yay bincike a computer ɗin da ta gudanar da binciken. Sai dai kuma ta saka security, shiga yay gwada passwords kala-kala yayi wanda yasan tana amfani da su a gida ko zata iya amfani da su. Sai dai sam babu wanda ya buɗe. Cike da ɓacin rai ya mike yana bugar desk ɗin cikin ƙunar zuciya. Lalubo wayarsa da ke ring a aljihu yayi. Yaya Muhammad ne, ɗagawa yay sukai yar magana ya yanke. Wani abokinsa ya kira kasancewar shi jami'i ne a hukumar ƴan sandan ta farin kaya. Ya tabbatar shine kawai zai iya bincika masa idan Hibbah na hukumar tasu. Bayan ya ɗaga ko gaisuwar kirki ba suyi ba ya sanar masa bukatarsa. A take jami'in ya tabbatar masa lallai Hibbah na'a headquarters ɗin tasu dan yaji ƙishin-ƙishin ɗin zancen yanzu a bakin wani ogansu cewar akwai yarinya da ke da alƙa da case ɗin na jiya.
Yanke wayar kawai yayi batare da sun ƙarasa maganar tasu ba, ya kira Yaya Muhammad yana sanar masa a inda zasu haɗu yanzun nan......
__________________________
Master da yaransa kam bayan ƴar tafiyar da sukayi ta cikin hanyar kwata sai gasu sun ɓilla ta wani ƙaramin gida. Gidane ginanne mai ƙyau na dai-dai mai matsakaicin ƙarfi. Yanda yake bin ko ina cike da nazari haka suma suke kallon gidan. Bayan kamar mintuna biyu ya gyara tsaiwarsa sosai yana fuskantarsu. Binsu ya gamayi da kallo ɗaya bayan ɗaya batare da su suna kallon ko ƙwayar idonsa ba. Tabbas sun jima suna kwaɗayin ganin fuskarsa, amma sam yaƙi basu damar hakan koda da kuskure..
_Gyaran muryar da yay ne ya katse tunaninsu. Ya sake gyara tsaiwarsa yana tura hannayensa duka cikin aljihun wandonsa. Muryarsa a kausashe da tabbatar musu da fushinsa ya fara magana cike da nutsuwa da ƙasaitar sa,
“Yau mun tsallake rijiya da baya, amma wataran saboda sakacinku tabbas bazamu tsallake ba. A kullum ina faɗa muku duk sanda zakuyi aiki, ku ringa yinsa da *_ƘWAƘWALWA DA ZUCIYA_* a haɗe. Dan duk lokacin da ɗan adam yay amfani da ƙwaƙwalwa kawai wajenin aikata muhimman abubuwa to ya tabbatar zai kasance mai yawan shiga ruɗani da tafiya yana dawowa baya saboda wani ya fika kaifin basirar. Idan ko da zuciya kaɗai ka dogara wajen ginin muhimman abubuwa, kasani nasararka ragaggiyace saboda zuciya abinda ke mata daɗi kawai take ayyanawa da buƙatar ya kasance mata. Bai kuma zama lallai ka kasance cikin jin daɗi da farin ciki ba a kowanne daƙiƙa na rayuwarka. Dan wani lokacin hanyar jin daɗi wahala ce, wata hanyar wahalar kuma jin daɗi ce. Wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe, idan ba hakaba ni ɗin nan da kaina zan bada ƙafar da za'a kama duk wanda ya cigaba da sakaci a cikinku. Ba kuma zan taɓa kuɓutar da shi ba har sai ya jigata yasan muhimmancin bama kasan kariyar yin aiki cikin tsantseni. Duk wanda ya haremu ya sokemu akan dai-dai kuma na jinjinama ƙwaƙwalwarsa da kaifin tunani. Sai dai na baku awa goma kacal ku ganomin koshi ɗin ɗan gidan uban wanene. Dan sai ya amshi hukunci dai-dai da iyawarsa!”_.
“Insha ALLAHU zamu kiyaye sir. Muna kuma neman afuwa daga gareka”. Suka faɗa a tare cike da girmamawa a garesa. Yayinda Habib da yasan komai ya farune ta sanadinsa yay ƙasa da kansa bayan ya sake matsowa gabansa. “Ka gafarceni Master, dan wannan tabbas sakaci na ne. Amma wlhy sam bansan ta yaya akai hakan ta kasance ba. Sannan koda muka dawo kuma ban fargaba.”
Hannu kawai ya ɗaga masa batare da yayi magana ba. Sai kuma ya nufi ƙofar fita da ga gidan baki ɗaya. Da kallo duk suka bisa har ya isa ƙofar ya buɗe sannan ya juyo yana kallonsu shima.
“Zan sake maimaita muku awa goma kacal, na samu cikakken labarin akan ko shiɗin wanene!......” Daga haka ya ida ficewa baki ɗaya.
A tare suka sauke ajiyar zuciya. Sun tabbatar a salon da yay maganar babu wasa a cikinta, dama can kuma ba wasan ya ke musu ba ballema su ɗauketa wasa. Suma kuma har cikin ransu suna bukatar sanin wanene wanda yay musu wannan tarkon da suka tsallake rijiya da baya?..........✍
*_Gadai jami'an tsaro basu sami nasarar aikin Hibbah ba, ga kuma Master ya bada awanni goma domin binciko wanda ya haresu, hibbah dai kuma itace ta kai harin da babu niyyar dalilin da su suke kallo. To yaya zata kasance kenan tsakanin Muhibbat Aliyu Hamza da Jami'an ƴan sanda da Master kenan?🤔. TAKUN SAAƘA wasa farin girki👎🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_MG's SKINCARE_*
*_Ina manyan Mata, da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau?_*💃🏻
*_To maza kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki_*
*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*💃🏻💃🏻
*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne a gareku💃🏻_*
*_Sai kuma beauty kit gbdy na gyaran jiki, su cream da komai ne acikin shi💃🏻_*
*_Then akwai bridal kit shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*
_Duk zaku tabbatar da hakanne ta hanyar nemansu ku gwada kuma har sai kun bama wasu labari💃🏻😍🥰_.
Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift
_*Sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks, juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_
____________________
*_Chapter Nine_*
.............Tunda jami'an suka dawo da labarin rashin nasara zukatan manyansu yay matuƙar ƙunci. Awanni ƙalilan suka rage musu da ga umarnin gidan gwamnati. Cikarsu babu Master a hannunsu kuwa yana nufin sun gaza a idanun al'ummar jiharsu da ƙasa baki ɗaya. Hakama ga gwamna da muƙarrabansa.
A gefe ga gidajen jaridu da duk wata kafar yaɗa labarai sun baza kunnuwa da idanun domin ganin yanda awanni ashirin da huɗu zasu cika tare da wannan ɓarawo a hannunsu ko saɓanin hakan.
Waɗan nan tunane-tunanen nasu yasa su shirya zaman meeting na gaggawa.
Dukkan wani babba mai alhakin faɗa aji ya hallara a ɗakin da meeting ɗin zai gudana. Sai wanda ya jagoranci jami'an da suka dawo yanzun nan da shirin kamo Master da yaransa..
Kowa ka kalla a ɗakin meeting ɗin kasan yaci ya ƙoshi, dan babu wasu kamannin wahala tare da su. Da'ace ƙasace mai ƙyaƙyƙyawan tsari sun cancanci yin ritaya duk su koma gefe a kawo matasa masu jini a jika da basirarsu ke aiki da kaifin ƙwaƙwalwa a zuba a madadinsu. Su kuma su zama dattijai masu bada shawara wa ƙasa ta bayan fage matsayinsu na iyayen ƙasa. Sai dai sam a wannan ƙasar tamu ba haka bane ba. Anyi sakacin barin matasan da ke da basirar zuwa da salonsu na ƙuruciya wajen kawoma ƙasa cigaba zama ƴan ta'adda, dukkan tarin basirarnan tasu da ƙuruciya ta koma aiki ne ƙarƙashin aikata laifuka. Iyayenmu da gwagwarmayar rayuwa da raunin shekaru sukaima yawa sun zama sune masu riƙe da madafun iko wajen zartarwa da hukuntarwa. A duk lokacin da ƙasa tai sakacin rashin amfani da basirar matasa da ƙuruciyarsu wajen aikata alkairi, to lallai shaiɗanu zasuyi amfani da basira da ƙuruciyar waɗanan matasan wajen kafa tantin ta'addancin da zai ruguza ƙasa.
A ƙasarmu ta gado iyayenmu sune ƴan siyasarmu, sune masu riƙe da madafun iko na mulkin gargajiya da na siyasa, sune riƙe da hukumomin ladabtar da masu laifi, sune riƙe da manyan kuɗaɗe na kasuwanci, sune riƙe da makarantun da ake bamu ilimi, sune.. Sune... Sune komai.
Babu wata hanya ko ƙofa da suka barma matasan wajen nuna bajintarsu da ƙwazon da ALLAH ya haliccesu da shi. Kallonmu suke masu yawan wauta, masu shashanci, masu ƙuruciya, masu rashin kunya da rashin ganin girman na gaba da su. Masu... Masu... Ta ko ina. Amfaninmu kawai mu cigaba da zama a ƙasa har sai lokacinmu yayi. To yaushene lokacin namu zaiyi? Shin sai muma mun kai irin shekarunsu mu danne na ƙasa da mu kenan?. indai har a haka za'a cigaba da tafiya lallai da alamar ƙasar tamu bazata taɓa zama mai sauyawa ba ko samun ci gaba. Domin anyi sakacin ajiye lokaci an ɗauki rauni.
Shi kuma lokaci a duk sanda aka gaza amfani da shi ta hanyar da ya dace wucewa yakeyi yabar mai shi da cizon yatsa da dana sani. A lokacin kuma daka buƙaci gyarawa sai ya kufce maka dan kayi sakaci wajen sarrafashi a sanda ya dace. To ya kamata manyan ƙasarmu su fahimci MATASANMU sune LOKACINMU. Cigaba da sakacin ƙinyin amfani da baiwarsu akan lokaci na nufin baragurbi amsarsu su su amfana da wannan damar wajen maidasu masu ruguza ƙasar da ku kuke ganin kunata ginawa. Sanda zakuyi ƙoƙarin son tarosu kuma sunyi nisan da bazasuji kiranku ba sam.
Bawai munason fiddo da gazawarku bane ma duniya ko goyon bayan laifukan matasa. Muna buƙatar ku duba ku kuma fahimci sai da matasa ƙasa ke iya samun ci gaba. Basu dama kuma shike nufin daƙile dama a hannun masu ɗorasu bisa bigiren ta'addanci. Kun cancanci kuma muyi alfahari da ku, dan kun bamu gudunmawa ta musamman bayan kasancewarku iyaye a garemu.
Bayan ƙarin bayani da suka samu a bakin jami'in da suka fita bibiyar Master zukatansu sun ƙara ɗaci. Ɗakin yayi shiru kowa na nazari da tunani a cikin zuciyarsa. Ɗaya da ga cikinsu da zuciyarsa ke raya masa wani abu ya nema izinin yin magana.
“Bismillah, an baka dama. Ya kamata kowa ya faɗi abinda ke bakinsa ko hakan zai bamu wani haske da ga kullewar da kawunanmu sukayi.” Ogan nasu ya faɗa cike da taraddadi.
Kansa ya jinjina da faɗin, “Thanks you sir. Dama wani tunanine yakemin yawo a zuciya game da ita wannan yarinyar datai mana aikin. Shin baƙwa tunanin shine ya tsara duk hakan kasancewarsa shu'umin mutum kuwa?. Al'amarin da matuƙar mamaki ta yanda ta bibiyesa cikin sauƙi. Idan har dama ba shirinsa bane ta yaya akai ta jefa masa abunda ta samu damar bibiyarsa?”.
Da sauri wanda ke a kusa da shi ya ashe da faɗin, “Ashe bani kaɗai nake wannan tunanin ba. Tabbas da alamar akwai lauje cikin naɗi game da wannan al'amarin. Nasan za'a iya samun mai ƙwazo da kaifin basirarta, amma yanda al'amarin ya faru da ƙanƙantar shekarunta sai nake ganin kawai shiri ne na musamman akai. Dan bana hangen tana da wani ƙyaƙyƙyawan tunanin da har zuciyarta zata bata damar aikata hakan. Banda shirme da shiririta mi yaran yanzun suka iya? musamman ma ita da ta kasance MACE”. Ya ƙare maganar cikin jin zafi sosai.
Wanda ya gana da Hibbah dake ta faman buga pen a kan laɓɓansa yana kallonsu da nazarin maganganunsu yay murmushi. “Wannan tunanin namu na ganin yaranmu bazasu iya komai ba wajen taka rawar gani ke maida ƙasarmu da mu baya a koda yaushe. Da hakan kuma suke samun damar yin amfani da basirar tasu a gurɓatacciyar hanya. Tabbas ita ɗin MACE ce kuma ƙaramar yarinya, amma kallonta da rauni na *ɗiya mace* shine babban kuskuren mu. Banace inada tabbacin bata da alaƙa da shi ba, dan shi shu'umin mutum ne hatsabibi da zai iya aikata duk ma abinda bamuyi tunaninsa ba ko munyi. Sai dai banason mu kasa fahimtar cewar itama duk da kasancewar tata MACE zata iya taka wata rawar gani a harkar tsaro da duk wani sha'ani na rayuwa duk da raunin da ALLAH yay mata. Shawarata anan itace mizai hana mu jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya”.
Sake maida hankalinsu sukai garesa domin sonjin ƙarshen zancen.
Ya gyara abin maganar gabansa yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya. “Ma'anar mu jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya shine muyi amfani da wannan yarinyar ta hanyar riƙeta a jikinmu ta zame mana ma'aikaciyar sirri. Ta wannan hanyar zamu amfanu da alkairinta da kaifin basirarta. Mu kuma saka mata ido wajen gano shin akwai alaƙar da zuciyarmu take zargin tsakaninta da shi ko babu?”.
“Yes! Wannan shawarar taka tayi matuƙa *A.G*”. Ogansu ya faɗa yana tafa masa. Hakanne yasa suma sauran tafa masa duk da wasunsu batai musu ba sam. Dansu babu abinda zukatansu ke ayyana musu sai ganin babu abinda Hibbah zata iya matsayinta na ɗiya MACE mai kuma ƙarancin shekaru.
Sun cigaba da tattaunawa har zuwa wani lokaci, kafin ogan nasu ya bada damar shigo da Hibbah.
Hibbah da damuwar ahalinta kecin ranta ta shigo fuskarta a cinkushe babu ko ɗigon walwala. Babu abinda zuciyarta tafi bukata a yanzu kamar tozali da Ummi da yayunta dan tabbatar da babu abinda ya faru da su. Zama tai a kujerar da aka nuna mata bayan ta gaishesu ranta fal jin haushinsu, musamman mutumin ɗazun da tun shigowarta da shi ta fara haɗa ido yana mata murmushi.
Bayan sun gama nazartarta da ƙare mata kallo ogan nasu yay gyaran muryar da ta saka Hibbah ɗago manyan idanun ta kallesa. Ganin yanda ya kafeta da nasane ya sata sake maida kanta ta duƙar tana wasa da yatsun hannunta.
“Muhibbat Aliyu Hamza!”.
Ya kirayi sunanta murya babu alamar wasa. Hakanne ya saka gabanta faɗuwa, ta sake ɗagowa tana amsa masa da rawar murya. “Na'am yallaɓai”.
“Miye alaƙarki da Master!?”.
“Master kuma yallaɓai? Ni ban sanshi ba”.
“Kin tabbatar?”.
Kanta ta jinjina masa.
“Taya za'ai mu yarda baki da alaƙa da shi?. Bayan tsahon shekaru biyu kenan kowace hukuma ta jami'an tsaro farautarsa suke, amma sun gaza koda ganin farcen yatsansa. Sai gashi ke a cikin kwana ɗaya rak kin haresa akan dai-dai?”.
“Ni wlhy yallaɓai bansanshi ba, bakuma ni da wata alaƙa da shi ko sanin wanene shi. Na aikata duk abinda kukaga nayi ne saboda wasa da rayukan mutane da sukeyi ta hanyar power rider amma badan wani dalili ba”.
“Okay, mu ɗauka hakanne kamar yanda kika faɗa ɗin. Yanzu wane tunani kikeyi game da makomar ahalinki?”.
Saurin ɗagowa tai tana kallonsa idanunta cike da ƙwalla. Muryarta na rawa tace, “Amma yallaɓai naga na muku aikin da kuka buƙata dan na tabbata kun kamasa. Kuma kun tabbatar min hakan shine fansar ahalina ai”.
“Eh tabbas haka muka faɗa, sai dai kuma ba'a samu nasara ba kamar yanda mukai tunanin za'a samu. Rashin samun nasarar kuma na nufin shigar ahalinki a haɗari ta fuska biyu. Na farko mu jami'an tsaro ba zamu barsu ba har sai wancan hatsabibin yazo hannunmu. Hakan shine zai wankeki a garemu mu tabbatar baki da alaƙa da shi, ahalinki kuma su kuɓuta. Na biyu dole ne mu baki kariya yanzun dan tabbas zaki zama abin farautarsa kema dan bazai barki ba tunda kin karya masa tarihi. Dolene kowane motsinki dana ahalinki su kasance a tare damu. Idan kin amince ki cike wannan. Kokuma kiyi tafiyarki amma babu ruwanmu da abinda zai samu ahalinki. Zakuma mu fitar da bayanan sune ke aikata laifukan da muka nuna miki ɗazun da mabanbanta fuskoki. Kinga za'a kamasu a kaisu kotu, da ga ƙarshe a yanke musu hukuncin kisa bayan duniya ta sansu matsayin ƴan ta'adda”
Sosai tashin hankali ya bayyana a fuskar Hibbah. Idanunta suka ciko da hawaye ta shiga girgiza musu kai laɓɓanta na rawa. “Dan ALLAH yallaɓai karkuyimin haka. Wlhy bani da alaƙa da mutumin nan sam, iya gaskiyata na sanar muku.”
“Ta hanyar shigowa kiyi aikin sirri da mu ne kawai zai tabbatar mana da hakan, ahalinki kuma su kuɓuta da ga garesa da mu kammu. Gashi ki cike waɗan nan takardun idan har kin amince”.
Da ƙarfi Hibbah ta rumtse idanunta. Wani irin zafi da ɗaci na sauka mata cikin zuciya. Karan farko na rayuwarta da taji tsiwa batai mata rana ba. Tanajin tsana mai yawan gaske akan mutumin da batasan wanene shi ba. Yayinda gefe na zuciyar tata ke jin haushin waɗan nan jami'ai da ke son yin amfani da damar da ALLAH ya basu ta hanyar amfani da ita. Wani gefen kuma na haske mata ahalinta cikin bala'i mai muni da idan har ta zama sanadin shigarsu cikinsa har gaban abada bazata taɓa yafema kanta ba. A take wani irin kangarewa da bushewar zuciya suka saukar mata. Batare da yin wani dogon nazari ba wautar ƙuruciya ta fisgeta da zuciya wajen ɗaukar pen ta hau cike takardun da ɓarin jiki, batare data duba mi suka ƙunsa ba..
Fusatar tata ta basu matuƙar mamaki da al'ajabi. Sai dai zukatansu na ayyana musu tanayin komai ne domin ahalinta. Dan fahimtar sune rauninta ya sakasu yin amfani da su wajen tursasata. Aiko sunci nasara, dan ta cike takardun kamar yanda suka buƙata. Ta kuma saka hannu bisa takardar contract ɗin zatai musu aikin sirri har sai sun kama Master. Su kuma bazasu saki wancan bayanan ƙaryar da suka shirya ba domin mata ɗaurin talala saboda ƙarancin shekarunta.
Sun mata bayanai sosai da zata iya fahimta. Tare da bata date ɗin da zata fara amsar horo na musamman a ɓoye. Da ga ƙarshe sukai mata dogon gargaɗi akan riƙe dukkan abinda suka tattauna matsayin sirri. Dan inhar ta fitar tamkar ta bayyana ƴan uwanta ma duniya ne matsayin ƴan ta'adda. Daga haka suka sallameta.
Fitowar Hibbah da aka haɗa da jami'ai biyu zasu mata rakkiya zuwa gida yayi dai-dai da isowar Yaya Abubakar da Yaya Muhammad station ɗin. Tana ƙyalla ido a kansu ta kwasa da gudu garesu. Jikin Yaya Abubakar dake gaba ta faɗa tare da fashewa da kuka.
Shima rungumeta yay yana mai rintse idanunsa da suka kaɗa sukai jajur. Yaya Muhammad ya ƙaraso garesu da sassarfa shima. Dafa kanta da yayine ya sata barin jikin Yaya Abubakar ta rungumeshi shima. Cikin son danne nasa ɓacin ran ya saki murmushi yana ɗagota da shafa kanta. Hannu yasa ya shiga share mata hawaye. “Kukan ya isa haka nan, ba gamu tare da ke ba”. Ya ƙare maganar da sake sakar mata murmushi mai kwantar da hankali.
Yaya Abubakar da shima ke ƙoƙarin ganin ya shanye tasa da muwar ya ce, “Bara naje zanyi magana da su”.
Da sauri Hibbah ta riƙo hannunsa tana girgiza kanta. Cikin sanyin da basu santa da shi ba ta ce, “Yaya karka je. Ka barsu kawai babu abinda sukai min”.
“Karki damu, ba wani abu bane yanzu zan fito”. Yay maganar da zare hannunsa cikin nata yana shafa kanta. Kama hannunta Yaya Muhammad yay shima ya buɗe mota ya sakata, tare da ɗaukar goran ruwa ya miƙa mata. “Sha ruwa ki wanke fuskarki ina zuwa”.
Hibbah na ƙoƙarin dakatar da shi bai jira cewarta ba ya nufi cikin station ɗin shima. Jitai kamar ta fasa ihu, dan gani take kamar shigar tasu na nufi jami'an zasu riƙesu su sanarma duniyar ƴan ta'adda ɗinne su.
Ganin an shafe kusan mintuna a shirin tai yunƙurin bin bayansu, sai dai tana buɗe motar suna fitowa kowannensu ransa a ɓace. Ta sauke ajiyar zuciya da yin sagade tai tana kallonsu har suka ƙaraso. Yaya Muhammad ya sake kama hannunta ya sata a motar sannan ya zagaya ya shiga shima. Yayinda Yaya Abubakar ya zauna mazaunin driver.
Suna fara tafiya kiran Ammar ya shigo wayar Yaya Muhammad. Kamar bazai ɗaga ba sai kuma ya ɗaga ɗin. Da ga can Ammar ya fara magana cikin ɗacin murya. “Yaya kazo gida dan ALLAH akwai matsala. Hajiya mama da Abba na nan sun taru akan Ummi harda Junaid. Nayi magana kuma ta dakatar dani. Wlhy zanma Haƙilu (Abba) dukan mutuwa sai dai Ummi ta tsinemin. Har wannan shegiyar tsohuwar ba raga mata zanba dan mahaifina ta haifa ba ni ba.”
“Ammar!!”
Yaya Muhammad ya kirayi sunansa a tsawace jin zai yanke kiran shima jikinsa na matuƙar rawar ɓacin rai.
Tuni Ammar ya riga ya katse kiran baima jisa ba. Yaya Abubakar da duk yaji komai ya ƙara ƙarfin gudun motar, cikin ƙanƙanin lokaci sai gasu a ƙofar gidan. Tun a waje yay fakin, gaba ɗayansu suka fita da sauri zuwa ciki. Dan tun da ga waje suna jiyo kururuwa da ihun Hajiya Mama da Momy.
A harmutse suka iske gidan. Ammar da Junaid na kwasar uban dambe. Sai dai duk da kasancewar Junaid yaya ga Ammar hakan bai hana Ammar hayewa saman ruwan cikinsa yana duka ba tamkar ALLAH ya aikosa. Mahaifiyar Ammar ɗin da suke kira Momy taje ceton ɗanta Ammar ya bata mahangurɓa a muƙamuƙi. Tuni ta koma gefe jikinta na matuƙar rawa.
Abba da hajiya mama kuwa tuni suna a wani lungu maƙale dan su ne Ammar ya fara fafara Junaid ɗin ya maresa. Shine faɗan ya juye a tsakaninsu. Da ga cikin lungun Hajiya Mama keta fama kwaɗa ihu da kururuwar Ammar zai kashe mata jika. Yayinda Abba ke a rikice ga tsoro, yana son zuwa ɗakko waya ya kira ƴan sanda yana tsoron fita Ammar da ya juye musu kamar wani mayunwacin zaki ya gansa ya dawo kansa.
Ummi ce kawai akan Ammar tana ƙoƙarin janyesa tana kuka amma ta kasa, dan gaba ɗaya ya juye mata tamkar ba Ammar ɗinta ba. Ya koma ainahin sunansa na ALIYU ZAKI.
Kuka Hibba ta fashe da shi ganin yanda Yaya Ammar kema Junaid dukan mutuwa. Sai jini ke fita ta hancinsa da baki amma yaƙi sakinsa. Da ƙyar Yaya Muhammad da Yaya Abubakar suka iya haɗuwa wajen ɗagasa da ga kan Junaid ɗin. A hakanma sai famar turjewa yake yana nuna Junaid cikin gargaɗi.
“Duk iskanci da kukejin kun iya da rashin mutunci muma mun iyasa. Ba tsoronku bane yasa muke barinku kuna taka mana mahaifiya yanda kuka gadama. Son yin biyayya a gareta da ga taka mana birkin da take na barinku kawai ke dakatar damu. Amma idan har kun isa wani ya sake nuna nata ɗan yatsa a gidan nan ya gani in ban karya shi ba na tauna ƙashin. Wlhy hatta waccan annamimiyar tsohuwar bazan bari ba, sai na ida ƙille ƙafafun nata ta koma gurguwa ta gaske.......”
Kuka sosai Ummi keyi tana kiran sunan Ammar amma yaƙi yin shiru. Su Yaya Muhammad suka turashi sashen nasu da ƙyar suma rayukansu duk a jagule.
A dai-dai wannan lokacin ɗaya da ga cikin ƴammatan gidan ta dawo. Horn tayi mai ƙarfi kamar yanda suka saba. Da sauri mai-gadi dake maƙale yana kallon duk abinda ke faruwa da ga windown ɗakinsa shima ya fito domin buɗe mata gate ɗin. Sai dai shima har cikin ransa yaji matuƙar daɗin dukan nan da Ammar yayma Junaid. Dan duk wani cin zarfi da akema mahaifiyar su Ammar ɗin a gidan akan idonsu ne tun da ƙuruciya.
A guje Ameera ta danno motarta cikin gidan kamar yanda ta saba. Sai dai hango su Abba akan Junaid da ke kwance kamar ya mutu ya sata saurin taka birki tamkar ba'a cikin gida ta ke ba. Fitowa tai da sauri. Ta zaro idanu sosai cikin ƙaraji na rashin tarbiyya take tambayar miya samu Junaid ɗin?.
Abba yay saurin ɗago Junaid ɗin da numfashinsa ke fita da ƙyar yana faɗin, “Kinga maza buɗe mana motarki mu kaisa asibiti shine mafi muhimmanci yanzu. Sauran bayani ƙyaji da ga baya dan anzo gabar da yaƙin duniya na uku zai fara tashi a gidan nan.”
Zata ƙara magana Hajiya mama ta katseta a tsawace. Baki ta murguɗa mata da yin fari da idanu sannan ta nufi motar tata Abba da mai-gadi biye da ita ɗauke da Junaid da gaba ɗaya jini yayma fuskarsa faca-faca...........✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_Ina miƙa sakon ta'aziyya ga ɗaukacin musulmi musamman hausawa na rashin uba kuma jigo, Haziƙi, gwarzo, abin alfaharinmu Sheikh Dr Ahmad bamba. Ya rabbi ka gafarta masa. Ka yafe masa kurakuransa da iyayenmu baki ɗaya. Munyi rashi irin wanda cike gurbinsa abune mai matuƙar wahala a duniyar musulinci. ALLAH ka yafema wannan jarumin dattijan ƙwarai😭🙏🏻_*
__________________________
*_MG's SKINCARE_*
*_Ina manyan Mata, da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau?_*💃🏻
*_To maza kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki_*
*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*💃🏻💃🏻
*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne a gareku💃🏻_*
*_Sai kuma beauty kit gbdy na gyaran jiki, su cream da komai ne acikin shi💃🏻_*
*_Then akwai bridal kit shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*
_Duk zaku tabbatar da hakanne ta hanyar nemansu ku gwada kuma har sai kun bama wasu labari💃🏻😍🥰_.
Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift
_*Sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks, juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_
________________________
*_Chapter Ten_*
...........Ummi na shigowa falon ta wankama Ammar mari. Lokaci guda falon ya ɗauki tsitt. Hibbah ta zazzaro manyan idanunta waje, jikinta na rawa, dan abinda bai taɓa faruwa ba a tsawon sanin da taima Umminsu. Duk iya ɓacin ran da zata nuna idan sukai mata laifi iyakarta da su faɗa da nasiha tun basu kai haka ba.
Ba Hibbah kawai ba, hatta Yaya Muhammad da Yaya Abubakar sai da wutar kansu ta ɗauke. Hakama Yaya Umar da Yaya Usman da ke ƙoƙarin shigowa falon saboda kiransu da mai-gadi yayi ya sanar musu abinda ke faruwa tun sanda Ammar ke jibgar Junaid. Sai dai suna shigowa gidan motar Ameera na fita zuwa asibiti kai Junaid. Tare kuma suka tafi gaba ɗaya gidan, har da Hajiya mama dake fama da ƙafarta.
Ƙananun duka Ummi ta cigaba da kaima Ammar, hawaye masu zafi suna gangaro mata a kumatu. Ammar dake tsaye ƙiƙam tun marinsa da tai kallonta kawai yakeyi shima hawayen na sakko masa na tausayinta. Yayinda wani murmushi mai ɗaci ke bayyana saman fuskarsa. Ummi ta jawosa ta rungume jikinta tana magana cikin rawar murya, “Miyasa zakai haka Aliyu? Miyasa? Ba nace duk abinda zaku gani ba kuyi kamar baku gani ba.”
Da gudu Hibbah ta zo ta rungume Ummin da Yaya Ammar itama. Gefe Yaya Muhammad ya kauda kansa yana ƙoƙarin ɗauke hawayen da suka ciko idanunsa. Yaya Abubakar ma idanunsa sun kaɗa sunyi jajur. Yaya Umar yafi kowa zuciya a cikinsu, yayinda Yaya Usman duk ya fisu sanyi shi da Yaya Muhammad. A wani irin fusace ya juya zai fita a falon Yaya Usman da yasan halin kayansa yay azamar riƙo hannunsa.
“Sake ni!”
Ya faɗa cikin kaushin muryar da ya maido hankalin kowa kansu. Girgiza masa kai Usman ya shiga yi alamar bazai barsa ba. Dan yasan dama badan Ummi da ke dakatar da su ba babu shakka da tuni Umar yayma Abba dukan mutuwa a gidan harma da Hajiya mamar kanta... Da ƙarfi Yaya Umar ya fisgi hannunsa da ga cikin na Usman. Hakan yasa Ummi azamar sakin Ammar tasha gabansa.
Cikin idonsa ta kalla batare da tace masa komai ba. A take yay ƙasa da kansa yana lumshe idanu da cije leɓensa da ƙarfi tamkar zai huda shi. Murmushi tayi tana kamo hannunsa cikin nata. Gaba ɗaya ƴaƴanta tasan lagonsu da hanyar sauke fushinsu. Shiyyasa a kowane lokaci take samun nasarar ladabtar da kowa cikin salon da ya dace. Babu wanda ta sake yima magana a cikinsu, sai kamo hannun Hibbah dake sharar hawaye har yanzu tai tana bin jikinta da kallo tamkar mai neman wani abu.
Da sauri Hibbah ta ce, “Ummi basuyimin komaiba fa, babu abinda ya faru ki kwantar da hankalinki”.
“Ai sun sakaki a tarkon da za'ayi miki ne!”.
Yaya Abubakar ya faɗa a tsawace cikin faɗan da kowa baisan yana da shi ba. Dan shima bai cika hayaniya ba sosai, amma yafi Usman da Muhammad zafi a wasu lokutan.
Ya riƙe ƙugunsa da hanunsa ɗaya, ɗayan yana murza goshinsa cike da damuwa. Yanda ya ke ɗan kaikawo yasa su fahintar akwai matsala kenan. Ummi da dama yin komai ta ke cike da ƙarfin hali ta kafesa da ido.
Zaune Yaya Abubakar ya kai saboda jin zai faɗi, dan shi kaɗai yasan a wane irin damuwa ya ke game da halin da Hibbah ta ke ciki. Gaba ɗaya ƙuruciya ta hanata fahimtar ramin da ta jefa kanta a ciki mai haɗari ne.........
“Abubakar mike faruwa?”
Ummi ta katsesa tana takowa gabansa. Idanunsa da ke jajir ya ɗago yana kallonta, ya ɗan furzar da zazzafar iska yana girgiza kansa. “Ummi tabbas akwai matsala, rawar kanta ta kaita ga jefamu cikin ramin da sam ita bazata fahimci haɗarinsa ba....”
Duk da hibbah a tsorace take da yanayin Yaya Abubakar ɗin, tai saurin katsesa ta hanyar faɗin, “Yayanmu wlhy babu abinda ya faru fa. Kawai dai sun sakani na bibiyar musu masu power bike ɗin nan dana sanar maka ne. Amma da ga haka basuyi min koma.........”
Tsawar da ta sakata kasa ƙarasa zancen ya daka mata. Ta maƙale a jikin bango jikinta na rawa saboda bata taɓa gamo da fushinsa irin haka ba. Shima tsaye ya miƙe yana nunata jikinsa har rawa yake ga idanunsa sunyi jajur. “Idan bakimin shiru ba wlhy sai na ɓallaki a gidan nan yau. Bance miki ki jirani a inda kike nazo na sameki ba? Su masu power rider ɗin da kike tunanin ba komai ba to sune tawagar ɓarawon nan da ake nema ruwa a jallo mai suna *Master!*, shine ya wawashi maƙudan kuɗaɗe jiya a asusun matar gwamna. Kowace hukuma ta jami'an tsaron jiharnan an basu awa ashirin da huɗu ne domin kawosa a mace ko a raye. Ba jihar nan da ƙasarnan kawai ba, hatta duniya baki ɗaya idonsu akan wannan mutumin yake. Amma shine k kika jefa kanki cikin abinda bakisan mafarinsa ba. Su waɗan nan jami'an da suka ɗaukeki zasuyi amfani da ke ne kawai su sami cikar burinsu, sunansu ya sake fiwowa a idon duniya. Kece zakiyi aikin amma sune zasu fito matsayin masu aikin. A tunaninki shi ɗin mahaukaci ne, kosu suna son matsalar tasa ta ƙare ne da wuri? Kuɗaɗen shigar da suke samu su dakata. Kafin yau an sha yimasa tarkuna da sukafi wannan haɗari amma bai kamu ba. Da ga ƙarshe kuma duk wanda yay masa tarkon ana nemansa ne a rasa ma baki ɗaya, ya ɓatar da shi. Wannan yasa a duk lokacin da ya aikata laifin manyan ke makalewa su saka ƙananun ma'aikata yin aikin, da ga ƙarshe suke nuna sunyi aikin ma duniya, wanda yay aikin kuma rayuwarsa ta faɗa a haɗarin da babu wanda zai sakejin yanda akayi, kuma basa wani ɗaukar matakin bashi kariya ko cetosa. Shekarunki goma sha takwas kacal da wasu wattani a duniya Muhibbat! Bama ki gama karatun gina rayuwar taki ba amma kika jefa kanki a wannan haɗarin saboda kunnen ƙashinki. Wannn kunnen babu wanda ya isa ya faɗa masa yaji sa”.
Ya ƙare maganar da takawa inda take maƙure a bango jikinta na rawa ya damƙi kunnenta da ƙarfi yana murzawa cikin yatsun hannunsa. Rawa jikinta ya farayi tana girgiza masa kanta saboda zafi.
Sakin kunnen nata yay yana dungure mata kai, yayinda sauran yayun nata da Ummi keta faman ambaton (innalillahi wa-inna ilaihirraji'un) a zukatansu. Yaya Abubakar ya cigaba da faɗin, “Ba wanann kaɗai bace damuwar Ummi, tunda har basu sami nasarar kamashi ba zargi zasu ɗarsa akanta itama. Dan zasu raba hankalinsu ne yanzu akan tunanin ko shine ya shirya komai wajen yin amfani da ita. Dan duk harin da jami'an tsaro ke kai masa ba'a taɓa cin nasara kamar nata ba da ya gudana cikin kanƙanin lokaci. Yanzu da zarar sun fitar da bayanai wa media cewar sun haresa, harin da kuma aka samu ci gaba a cikinsa fiye da na baya, to kowacce hukumar jami'an tsaro sai sun bibiyi yanda hakan ta kasance ta karƙashin ƙasa, walau jami'anmu nan gida kona ƙetare da ke nanuke cikin case ɗin kamar yanda suka saba mana kutse a cikin ayyukan daya shafi ƙasashenmu. Mu kuma bamu isa muyi koda tari akan nasu ba. A ƙarshe kowa ya bincika ita zai gano. Duk kuma zasu kasance wajen bibiyarta da mu kammu ba tsira zamuyi ba. Shima da ta aikata komai dominsa ba barinta zaiyi ba na sani.
“Ya ALLAH!”.
Ummi da ke neman faɗuwa ta faɗa tana fashewa da kuka. Da sauri sukai kanta gaba ɗaya suna ƙwala mata kira. A wani irin sarƙe numfashinta ya fara fita, ta fara tari.
Rikicewa suka sakeyi, yayinda kukan Hibbah ke ci musu zukata matuƙa. Cikin bada umarni Yaya Muhammad ya ce su dagata a kaita asibiti. Yanda ya faɗa ɗin haka sukai, sai dai suna fitowa harabar gidan ƴan sanda na shigowa. Basuyi yunkurin bi takansu ba. Sai dai muryar Abba da sukaji yana nuna Ammar da cewar shine ya kashe masa yaro ya saka hankalinsu rabuwa biyu.
A ɗan firgice Yaya Usman ya furta, “Kisa?”.
“Eh mara mutunci, ko ƙarya zan masa ne? Tun ɗazun likitoci suke akan Junaid amma babu alamar numfashi tare da shi, dan haka ku kamasa, inhar na rasa ɗana shima sai an kashesa.”
Tarin Ummi ne ya ƙara ƙarfi, sai ga jini na fitowa ta hancinta. Hankalinsu ne ya sake tashi. Sai a lokacinne Abba ya lura da halin da Ummi take a ciki. Maimakon ya saki batun ƴan sanda ya shiga sahun masu kula da ita, sai hakan ta gagara. A kausashe ya bama ƴan sandan damar kama Ammar yana tabbatar musu pretending Ummi keyi kawai.
Ganin duk sun shiga mota ƴan sanda kuma sun cukuykuye Ammar dake turjewa dan hankalinsa nakan halin da mahaifiyarsu ke ciki bata tasu yake ba. Yaya Muhammad ya cema Yaya Usman ya fita yabi ƴan sandan dan susan inda za'a kai Ammar ɗin. Su kuma zasu kai Ummin asibitin.
Badan yaso ba ya fita domin bin umarninsa. Dan duk da an haifesu babu wani yawan tazara a tsakaninsu hakan baya hanasu respecting junansu saboda ƙyaƙyƙyawan training da suka samu da ga mahaifiyarsu.......
★★★★★★★★★★★
A lokacin da wancan tashin hankali ke baibaye da ahalin Hibbah, anan headquarters ɗin ƴan sanda ƙoƙarin fitar da bayanan harin da Hibbah ta kaima master sukeyi. Sai dai kamar yanda Yaya Abubakar yay hasashe sunansu ne ya fito matsayin waɗanda sukai aikin. Sun kuma tabbatar nan da lokaci ƙanƙani zasu gurfanar da Master a saman gwiwoyinsa gaban duniya.
Babban abinda ya ɗauki hankalin jama'a da media baki ɗaya shine. Rahoton ƴan sanda na fita da mintuna uku kacal. Sai ga wani babban labari kuma da ga wannan shahararren ɓarawo mai suna *(MASTER)*. Ya fitar da jerin sunayen wasu manyan kaddarori na matar gwamna da mutane basu taɓa kawoma ransu hasashen tana da alaƙa da su ba a wani shafi nasa. Sannan ya rabasu a manyan gidajen redio da television ta hanyar tura musu saƙwanni kai tsaye a shafukansu na sada zumunta masu matuƙar muhimmanci da yawan mabiya.
Sosai ƙura ta tashi cikin lokaci ƙanƙani, manyan ƴan siyasa abokan takarar wannan jami'iyya suka samu damar baje kolin nasu faɗar albarkacin bakin dan dama tamkar kaɗan ake jira. Yayinda a gefe kuma da yawansu suke goyon bayan shi wanann master da ƙoƙarin wanke laifukansa a idanun mutane.
Fitar wannan kace nace keda wuya takardar gayyata ta bayyana da ga hukumar *(Yaƙi da ta'annatin kayan gwamnati)* zuwa ga matar gwamna. Acewarsu, suna gayyatarta zuwa ofishinsu da ga nan zuwa awanni ashirin da huɗu domin amsa musu wasu tambayoyi. Idan bataje da kanta ba, zasuje har gida su su ɗakkota.
Cikin ƙanƙanin lokaci sai ga ɓangaren gidan gwamnati suma sun yunƙuro wajen maida murtani ta hanyar jifar abokan hamayyar TAKUN SAƘAAr nasu da dangantaka da Master. Suna mai tabbatar ma duniya lallai akwai lauje cikin naɗi. Sannan akwai ayar tambaya dangane da wanzuwar Master. Shin kodai? Kodai......😂🤐.
Ta kowanne fanni gari ya ɗauka zafi, babu wani babban labari sai na wannan badaƙala ta TAKUN SAƘAA tsakanin Master da ya haɗa gurmin zuwa jami'an tsaro da na gwamnati. tare da ƴan siyasa da masu radin faɗin albarkacin baki. A gefe kuma ga talakawa ƴan bani na iya nata faman sharhi akan komai, kai kace agabansu aka ƙulla al'amarin..........
(😖Wai, sunan wata karya. Sharaton. Bily aɗan dinga sassautawa dai🚶🏻😌😒😏😣😝)
*________________________________*
Wani ƙayataccen murmushin da ya saka yaransa shagala a kallonsa ya saki lokacin da yake faman duba wasu da ga cikin Comments na mutane da ke wanzuwa a yanar gizo. Cikin salon ƙasaitarsa da izza ya wani juya kujerar da yake zaune cike da ƙwarewa yana lafewa a cikinta hankali kwance. Tare da wani salon da su kaɗai suke gane mi yake nufi idan yayi sa.
Dariya suka sanya cike da jin daɗin. Dan kobai faɗaba sunsan yana cikin farin ciki matuƙa. A duk sanda ya tada irin wannan ƙurar ya ga taja hankalin ƴan ƙasa da waɗanda yayi dominsu su kansu yakan yafe musu laifuka da sukai masa. Ko ya bisu da ƙyauta mai tsoka da ke sakasu farin ciki. Zai kuma kasance tare da su cike da nishaɗi duk da shiɗin ba mutum bane mai yawan magana akoda yaushe.
Da wannan damar Habib yay amfani wajen gabatar masa da rahoton binciken da ya gudanar akan aikin da ya basu ɗazun. Dan sun wuce adadin awannin da ya basu sosai. Kuma sunsan bawai ya manta bane, ya sharesu ne kawai bisa wani dalili nasa daban. Zatama iya yuwuwa shi tuni ya gama aikin binciken, suma ɗin ya sakasu yi ne kawai domin hukuntasu bisa laifin sakacinsu.
Komai baice akan takardun ba. Hasalima baiko buɗesu ba ya cigaba da duba sakwannin. Yayinda murmushi ke cike da ɓoyayyar fuskarsa da har ake ganin bayyanarsa bisa ta bogin da ke a kanta, wadda idan ba faɗa maka akaiba bazaka taɓa cewa ba fuskarsa bace ba. Su kansu yaransa inda ace da ita kawai yake amfani baya canjawa tabbas zasu ce itace ainahin fuskarsa. Sai dai zuwa da mabanbanta da yakeyi ya sakasu fidda wanann hasashen a cikin ransu.
Ya kai tsahon lokaci tare da su yana bibiyar kowacce kafar yanar gizo da ta yaɗa labarai. Kafin ya miƙe yana faɗin, *“7:30am* zamu koma *L.E street.* Jahje na buƙatar bada ƙafa”.
Wani ihun farin ciki suka saka. Dan a gaba ɗaya gidajen da suke zama gidan *_L.E STREET_* yafi kowanne girma da ababen more rayuwa. Suna matukar mamakin yanda yake sama musu manyan gidajen da suke zama, a kuma manyan anguwanni batare da an farga shiɗin baneba. Tsabar hatsabibancinsa kuma a wasu lokutan sukan koma anguwannin talakawa su zauna har na tsahon wani lokaci. Haka suke tamkar fulanin tashi. Da wahala suyi zaman wata uku a gida batare da sun koma wani ba.
Kansa ya ɗan girgiza da kai kofin coffee ɗinsa saman baki yana barin wajen nasu zuwa jikin windown ƙaramin falon da suke ciki na gidan da ya kawosu ɗazun. Wanda har yanzu basu san taka-maimai a cikin wace anguwa yake ba, dan basu fita ko soro ba har yanzu. Shi kadai ne ya fita bayan awanni takwas ya kuma dawo.
Wani hatsabibin murmushi ya sake saki idonsa kyam akan ƙwan wutar lantarki da ke a tsakar gidan. Haka ya cigaba da tsaiwa a jikin window ɗin yana cigaba da shan coffee ɗinsa da sauraren iya shegen yaransa akan Comments ɗin mutane da suka koma bibiya suma suna kwasar dariya.
Kofin da ya sake kaiwa baki yaji babu komai a ciki ya sakashi ɗago kofin ya kalla. Ba komai ciki ya shanye, hakan sai ya bashi dariya. Amma sai ya gintse kayansa baiyiba sai a zuciya. Juyowa yay da baya ya ajiye cup ɗin ya ɗauka file ɗin da Habib ya ajiye. Cikin muryarsa da sautinta ke fita da nutsuwa da amo yace, “Ayi addu'a kafin a kwanta. Goodnight”.
Kusan a tare suka haɗa baki wajen faɗin, “ALLAH ya tashemu lafiya boss. Sweet dream tare da ƙarin ƙyaƙyƙyawar idea akan ƴan ruda”.
Daƙƙuwa yay musu batare da ya juyoba. Sai dai ya saki murmushi dai-dai yana shigewa. Duk da basuga murmushin nasa ba kasancewar ya juya musu baya hakan bai hanasu yin kananun dariyar farin ciki ba gaba dayansu.
Yana shigewa suka farma gasassun kajin da ya kawo musu tun shigowarsa da ci. Dama sun ɗan ɗaga kafa ne ganin yazo a cikin yanayin babu wasa. Yanzu ko sunsan komai normal ne, sai abinda ba'a rasaba saboda rikita-rikitar Master ɗinsu bata taɓa karewa. Daya toshe waccan matsalar zai ɓallo wata da kansa kafinma ƙurar wadda ya tayar ta lafa.
Shima ko da ya shiga ɗakin zazzafan numfashi ya furzar. Ko'ina fes dan tun bayan barinsu da yayi suka gyara komai. Ya jefa file ɗin hannunsa saman madai-daicin gadon. Kayansa ya shiga zamewa alamar son watsa ruwa. Ya rage da ga shi sai singlet da boxer. A haka ya nufi toilet ɗin.
Tsahon mintuna ashirin ya ɗauka a ciki kafin ya kammala, tun kafin ya fito da ga bayin ya ziro hannu ya kashe wutar ɗakin baki ɗaya. Batare da damuwa da duhun da ya mamaye ko ina ba ya fito a haka. Ta cikin duhun ya iso bakin gadon, ya kai zaune cikin lalube ya ɗakko wayarsa ƙarama. Fitilarta ya kunna, tare da ɗaukar file ɗin da Habib ya bashi. Sam ba'a ganin fuskarsa. Sai dai shi yana ganin rubutun file ɗin kasancewar shi ya haska kai tsaye. Sai alamun bathrobe ɗin dake a jikinsa wadda iya inda hasken ya haska kawai ake gani.
“What?!”.
Ya faɗa cikin subucewar baki ganin bayanan na nuna cewar da taimakon mace aka kai musu harin ɗazun. Macen ma ƴar 18 years kacal. Cikin wani irin rawar jiki yay wurgi da file ɗin yana faɗin, “Impossible! Ni! Ni! Ni ne yarinya ƙarama kamar wannan zata hara. Hari irin wanda wani mahaluki bai taɓa samun galabar yimin shi ba. Kuturun ubacan kayyasa😳............✍
*_HHHH anayi muna ɓallar rake na funtuwa mai zaƙi. Alaji Master yaya take ne😉😝🐒?. In baka saniba ma yanzu ne wasan zai fara😂👎🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_Chapter Eleven_*
..........Cikin gaggawa aka amshi Ummi a asibiti. Dan da ƙyar take fitar da numfashi, ga jinin da yake fita mata ta hanci da tayo tari da ya harmutsa dukkan zukatan su Yaya Muhammad. Hibbah kam ai tama koma musu tamkar zararriya. Dan koda za'a shige da Ummi sai da Yaya Umar ya riƙota shima hawaye masu ɗaci na cika masa idanu.
Yaya Muhammad kam da baida wahalar zubda hawaye gefe kawai ya maida kansa yana sharewa. Umminsu itace duniyarsu. Itace farin cikinsu. Itace ta maye musu dukkan gurbi na dangin mahaifinsu da giɓin mahaifin nasu da suka rasa tsahon shekaru goma sha tara. Tayi haƙuri da damuwoyi kala-kala domin taga sunyi farin ciki. A kullum ƙoƙarin ta su zama mutanen kirki. Su zama masu haƙuri, su zama masu juriya. Su zama.... Su zama... Da yawa. To sukam idan akace sun rasata ina zasu saka kansu da rayuwarsu. Idan suna a gabanta sam basa tuna sun girma. Ganin kansu suke tamkar ƴan shekaru goma-goma. Bazasu so Ummi ta tafi ta barsu batare da sun cika mata burinta na ganin sunyi aure ba. Kamar yanda take addu'ar ganin zuri'arsu suma hakan shine fatansu a yanzun. Suna son yawan ganin dariya a saman fuskarta kamar yanda mahaifinsu yay sanda yana raye. Amma hakan duk bazata tabbataba sai tana a kusa da su........
“Ya ALLAH ka bama Ummi lafiya ka tashi kafaɗunta. ALLAH yasa ni na mutu a madadinta”.
Furucin Muhibbat da ke kuka ya katsema Yaya Muhammad da su Yaya Abubakar tunaninsu. Gaba ɗayansu suka zuba mata idanu na ɗunbin tausayinta da ƙaunarta. Yarinya ce ita mai yawan walwala, kazarkazar, wauta, tsiwa, rawan kai, surutu duk a dalilin gata da kulawar da take samu da ga garesu. Tana matuƙar son Ummi, suma haka. Batasan mahaifinsu ba, shiyyasa suketa ƙoƙarin ganin sun cike mata gurbinsa.
A hankali Yaya Abubakar ya taka inda take durƙushe gaban Yaya Umar da rauni ya cika zuciyarsa na tausayin kansu da autar ta su. Hannu biyu yasa ya kamota ya ɗaga tsaye. “Haba Muhibbat, maimakon kima Ummi addu'ar samun lafiya sai ki dinga ma kanki addu'ar mutuwa a madadinta?. Insha ALLAH Umminmu zata tashi da lafiyarta kinji. Ki mata addu'a da fatan alkairi, ALLAH ya na tare da ita kinji”.
Kanta ta jinjina masa wasu zafafan hawayen na rige-rigen sakko mata. Yasa hannu ya share mata yana murmushin ƙarfin hali.
“Ƙyaƙyƙyawa mai kama da Umminta a komai, sai dai raguwa ce bata kai Ummi jarumta ba”.
Yaya Abubakar ya faɗa cikin ƙarfin hali yana ɗan ja mata kumatu. Maimakon tai dariya da tsalle kamar yanda ta saba idan ya faɗa mata hakan, sai ta faɗa jikinsa ta fashe da kuka. Kusan atare duk suka rumtse idanunsu, dan kukanta na matuƙar sake tada musu hankali.
Kusan mintoci arba'in da biyu likitoci suka ɗauka tare da Ummi. Kafin ALLAH ya basu ikon fitowa. A kusan tare su Yaya Umar suka miƙe a zabure harda Hibbah dake jingine jikin Yaya Umar barcin wahala ya ɗauketa.
Kusan a tare suka furta “Doctor ya jikin Ummin mu?”.
Kallonsu yayi cikin furzar da numfashi yana cire norsemask ɗin fuskarsa. “Inason yin magana da ku a office”. Ya faɗa yana ƙoƙarin wucesu. A take suka rufa masa baya har Muhhibat da Yaya Umar ke riƙe da hannunta. Kusan tare suka shiga da doctor cikin office ɗin. Hakan da sukai sai tausayinsu ya sake kamashi. Dan a kallo ɗaya zakai musu ka hango ɗunbin so da ƙaunar da sukema mahaifiyar tasu. Bai wani tsaya ja musu rai ba yay musu bayani akan matsalar da ke tare da Ummi a ƙasan zuciya da hanjinta. Bincikensu ya nuna kuma ta jima da ciwon yana ta cinta a hankali, sai dai yafi nuna kansane a duk lokacin da wani ɓacin rai ko tashin hankali ya sameta. Amma zasu mata aiki insha ALLAH suna mata fatan samun lafiya.
Duk da maganarsa ta ƙarshe taɗan sakasu jin sanyi hakan bai hana zukatansu shiga cikin matuƙar rauni ba. Ya ɗan ƙara faɗaɗa musu bayanai akan abinda za'a iya buƙata akan aikin da magungunanta. Tare da basu tabbacin inhar sun shirya a yau ɗin nan ma za'a iya mata aikin. A take sukace sun amince, duk da kuwa kuɗaɗen da ya ambata da wuya a iya samunsu kai tsaye da ga garesu. Badan suna da yawa bane sosai, kawai dai suɗin masu tasowa ne ba wasu ɗumbin kuɗaɗe suka tara ba. Amma dai tunda ya ce zasu iya bada rabi idan an kammala aikin su cika zasuyi ƙoƙarin su insha ALLAH.
Take ya basu takarda Yaya Muhammad ya saka hannu. Daga haka suka fito domin tattaunawa akan zancen kuɗin. Dan doctor yace sai sun tura zaiyi ƙoƙarin haɗa wasu da ga kayan aikin insha ALLAH.
Su dukansu suna aiki, Ammar ne kawai da Hibbah ƴan makaranta a cikinsu. Sai Yaya Umar da ke ɗan harkar kasuwanci saboda matsalar rashin samun aiki da matasa ke fama da shi a ƙasar nan. Sai ma yazam a yanzu yafi nutsuwa da kasuwancin sama da aikin da yay karatu akansa. Dama kuma su Yaya Muhammad ɗin nata son ganin sun ƙara masa ƙarfin jari tunda ALLAH yayma kasuwar tasa nasibi.
Sun ɗan tattauna wajen ganin sun haɗa kuɗaɗen, cikin amincin ALLAH ma sai gashi an samu kusan rabin a hannunsu su uku. Idan Yaya Usman yazo shima zasuji mi za'a samu daga garesa. Abba dai basa saka rai game da shi sam.
Basuyi zaman ɓata lokaci ba wajen fita su tattaro kuɗaɗaɗen har Yaya Usman da ya iso asibitin a yanzu shima, dan ya kasa jure zama acan saboda ya gwada ƙoƙarinsa na ganin an bashi Ammar amma hakan ya gagara saboda mugun ƙulli da Abba yaje yayi a station ɗin. Ya tahone kawai dan yasan insha ALLAH Yaya Abubakar zai fiddosa da zaran hankali ya kwanta. Kafin su dawo kuwa an gama shirya komai na shiga theater ɗin. Cikin amincin ALLAH zuwa ƙarfe takwas na dare aka shiga da Ummi. Sun bita da ƙyaƙyƙyawar addu'a da fatan dacewa a zahiri da baɗini.
Yaya Muhammad ne ya fara fahimtar akwai yunwa tattare da Hibbah. Dan gaba ɗaya jikinta ya saki tamkar mara laka. Yana lura da ita ko salla a zaune ta dinga yinta. Hannu yasa ya kamo nata cike da kulawa yana faɗin, “Auta yaushe rabonki da abinci”.
“Tun breakfast ɗin safe Yayanmu, amma kuma banajin yunwa”. Ta faɗa cikin sanyin da basu santa da shi ba.
Su dukansu sai da suka dubeta cike da tausayi. Yaya Usman yay saurin barin wajen batare da yayi magana ba. Cikin lokaci ƙanƙani sai gashi ya dawo da teakaway.
Zama yay da kansa zai bata amma sai tace ta ƙoshi. Dukansu babu wanda bai lallasheta ba amma tace ta ƙoshi. Sai da taga duk sun ɓata rai sanann ta amsa ta ci wanda ya saka mata a baki. Amsar cokali tayi ta ɗiba da kanta shima ta bashi. Ta sake ɗebowa ta bama Yaya Umar. Shima Yaya Abubakar haka. Sannan ta bama Yaya Muhammad shima. Dukansu murmushi suke mata a karon farko tun bayan shigowarsu asibitin da duk rayukansu suke a jagule. Amsa Yaya Usman ɗin yay ya cigaba da bata. Kusan lauma uku ta kauda kanta idanunta na cikowa da ƙwalla.
“Miya faru kuma?”. Yaya Abubakar dake miƙa mata ruwa ya faɗa. Hawayen data matso suka silalo saman kumatunta. Muryarta na rawa tace, “Yayanmu Yaya Ammar fa?”.
Shiru suka ɗanyi duk suna kallonta. Kafin Yaya Abubakar ya shafa kanta fuskarsa ɗauke da murmushin ƙarfin hali. “Karki damu shima zai dawo, insha ALLAH bazai kwana acan ba. Ƙarasa cin abincinki ina zuwa”. Ya ƙare maganar yana mikewa. Tashi Yaya Usman yay yabi bayansa.
Police station ɗin da aka kai Ammar suka nufa. Tun shigowar su Yaya Abubakar wasu a cikin ƴan sanda suka shaidashi saboda aiki ya taɓa haɗashi da wasu a cikinsu. Amma duk da haka sai ya nuna musu i'd card ɗinsa. A zabure sauran ma suka shiga gaishesa. Aka kuma masa iso ofishin ogan wajan.
Tun a shigowarsu ya shaida Yaya Abubakar ɗin. Amma sai ya maze abinsa. Yaya Abubakar ya cije lip ɗinsa dan akwai ƴar tsama a tsakani. Sai dai yana sama da shi. Cikin nuna bai damu da basarwar tasa ba yay masa bayanin kansa. Tare da buƙatar a bashi Ammar.
Cikin yatsine fuska ɗan sandan yace, “To yallaɓai idan ku matsayinku na manya kuna haka su kuma wanda basu da dangi ƴan sanda kuma fa? Laifi ƙaninka yay aka kawosa nan, sai kuyi haƙuri mu gama tattara bayanai akansa mukai maganar kotu kamar zaifi”.
Sosai Yaya Abubakar ya kafesa da ido. Sai kuma ya saki wani lalataccen murmushi yana miƙewa dan yasan wannan tsarin da ga Abba yake. “Wanann basirar ba taka bace. Amma ga saƙo ka bama wanda ya tsara maka ya kuma biyaka. Ya kiyayi ranar maida murtani dan zata kasance mai ɗaci da tsauri. Ya kuma bar raina allura dan itama ƙarfe ce. Duk randa zuri'ar Aliyu Hamza gwarzo sukaji a ransu zasu maida murtani TAKUN SAAƘAR bazai masa ƙyau ba. Wannan hanunka mai sanda ne”. Yaya Abubakar ya ƙare maganar cike da gargaɗi.
Murmushi Yaya Usman yayi. Dan bai taɓa zato da tunanin yaya Abubakar ɗin nasu ya iya zaro zance haka na. Koda suka fito da kansa yasa a kaisa cell ɗin da Ammar yake. Shine ya amshi key tun daga kanta ya buɗesa da kansa.
Wani irin kallo ya tsaya yanama Ammar da yaci uban duka. Da alama ma ba'a jima da dukan nasa ba, dan duk sabbin raunuka ne a jikinsa dake fidda jini. Komai baiceba a lokacin sai kama hannun Ammar ɗin daya taso da sauri yana tambayarsa “Ina Ummi take?” yayi. Bai amsa masa tambayarsa ba sai da suka iso kantar. Ya duba ƴan sandan wajen da sukai tsuru-tsuru cikin kaushin murya yace, “Su waye sukai wannan aikin?”.
Kallon kallo aka shigayi. A matuƙar tsawace yace, “Ba magana nake ba ne?!!”.
Zabura duk sukayi har tsirarun mutane da sukazo belin ƴan uwansu da masu kawo abinci. Cikin rawar murya wani ɗan sanda yace, “Yallabai wlhy ba laifinmu bane sakamu akayi”. Ya ƙare maganar a hankali cike da raɗa saboda fitowar ogansu da ga office dan jin tsawar da Yaya Abubakar yayi.
Takarda Yaya Abubakar ya fisga ya jefama ɗan sandan da yay maganar. “Ina son duka sunayen members na ƴan sandan dake a station ɗin nan. Wanda sukai wannan dukan kuma sunayensu su kasance a ware”.
Wani busashshen yawu ya haɗiye da ƙyar yana ɗaukar takardar. Jikinsa sai tsuma yake ya shiga zano sunayensu ɗaya bayan ɗaya. Bayan ya kammala cikin girmamawa ya mikama Yaya Abubakar ɗin. Uffan baice masaba ya amsa tare da jan hannun Ammar da Yaya Usman ya riƙe ta ɗayan gefen suka fice da ga station ɗin.
Ko a mota ma babu wanda yay magana dan zuciyar Yaya Abubakar takai ƙololuwar ɓaci game da lamarin Abba. Asibitin suka wuce da Ammar shima. Ba ƙaramin tashi hankalin su Yaya Muhammad yay ba ganin dukan da akaima Ammar. Hibbah kuwa kuka ta fashe musu da shi tare da zuwa ta rungume Ammar ɗin.
“Wash ALLAH auta zafi”.
Ya faɗa cike da shagwaɓa saboda jin ta ƙankame masa hannunsa da yake da tabbacin ƴan sandan sun ji masa ciwo. Saurin sakin hanun nasa tai tana sake fashewa da kuka. Ya kai hannu bisa kanta ya dafa yana murmushin ƙarfin hali. “K karki maidani kamar ba namijiba mana. Bakisan dukan ƙarfi ya ƙara min ba ma”.
A yanda yay maganar ya saka su Yaya Umar yin murmushi suna girgiza kansu. Hibbah kuwa kukan ne ya sake kufce mata.
Yaya Umar ne ya kaisa akai treatment ɗinsa da bashi magunguna. Sauran abincin da Hibbah taki ci suka matsa masa yaci da ƙyar shima. Dan sai da Hibbah ta dinga basa a baki yau babu faɗa. Bayan ya kammala yasha magungunan da aka bashi. Duk yanda sukaso yaje gida ya huta yaƙi, yace shima sai yaga fitowar Ummi.
Sha'awa yanda suke ƙaunar junansu ya bama doctor Bilal. dan haka ya bama Ammar ɗin shawarar yazo office ɗinsa ya kwanta to har komai ya kammala sai a tashe sa. Nanma da ƙyar ya amince bisa umarnin yaya Muhammad. Haka dai ya miƙe yana tura baki Hibbah na masa gwalo.
_____________★★★_____________
Duk yanda yaso yin shirin barci ya kwanta hakan ya gagara. Sai fama kai kawo yake a cikin ɗakin, abubuwa da yawa zuciyarsa ke raya masa game da matakin da ya kamata ya ɗauka a kanta. Inhar zata iya kai masa hari ta samesa a ƙanƙanin lokaci. To wane irin shiri kenan zatai a gaba dominsa? Lallai dole ne yasan ita ɗin wacece? Mi kuma ta taka ne haka?. Shin sakata akai? Kokuwa yin kanta ne?.
Waɗanan jerin tambayoyi suketa faman masa kai kawo a zuciya da hanashi nutsuwa. Shiri ya canja saɓanin pyjamas da ya kamata ya saka sai yasa wasu kayan daban.
Yaransa na falon zaune har yanzu suna sha'aninsu sai ganinsa sukai ya fito. Mamakine ya kamasu dan duk zatonsu ya kwanta.
“Boss da matsala ne?”.
Salisu ya faɗa cike da girmamawa.
Kansa ya girgiza masa yana ƙoƙarin ɗaura agogonsa. Sai da yaje gab da fita a falon yace, “Zanje wani waje ne, wani yazo ya rufe gidan”.
Saurin miƙewa Khalid yayi duk da tambayoyine fal bakunansu amma babu damar yi, dan ya nuna baya buƙatarsu. Su ko saboda trianing da suka samu da ga garesa da kowanne irin yare yay magana ko yay nuni suna fahimtar kayansu.
Koda ya wuce Khalid ya dawo zaman tattaunawa sukai, amma sai basu gano komaiba, dan haka sukai jigum-jigum......
________________________________
Alhmdllhi ƙarfe goma aka fiddo Ummi da ga ɗakin theatre cike da nasara. Bayyana muku irin farin cikin da su Yaya Muhammad suke ciki ɓata lokaci ne. Basu sami damar ganinta ba dan an miƙata ɗakin hutu ne. Sai dai bayanin da Dr Sageer yay musu na narar aikin ya saka zukatansu nutsuwa. Har suka amince da shawararsa ta tafiya gida dan ba'a bukatar kowa tare da Ummin sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu.
Basuyi wani zaman ɓata lokaci ba suka tattara suka wuce bayan an tado Ammar da zazzaɓi mai zafi yayma ligif saboda dukan da yaci. Sosai tausayinsa ya bayyana bisa fiskokinsu. Sai dai komai basuce ba bayan Hibbah da ke ta jera masa sannu kamar zatai kuka. Kaɗan-kaɗan ta ɗaura hannunta a goshinsa.
Suna gab da zuwa gida ya bige hannunta data ɗora masa a karo na babu adadi. “K dalla kin isheni, ga hannunki da sanyi”.
Baki Hibbah ta tura gaba. Cike da tsiwa ta murguɗa masa baki da faɗin, “Oh dama ka samu na damu da kai zaka min wani iyayi”.
“To waya aikeki? Uwar iya mai cinikin iya”. Ya faɗa yana gyara kwanciyarsa jikin kujera.
Murmushi Yaya Usman da ke kusa da su yayi yana girgiza kansa kawai. Dan inda sabo sun saba gani. Anjima kaɗan kuma kaga sun koma hirar arziƙi. Kafin awa ɗaya ta rufa sunyi faɗa sau biyu.
Cikin jin haushi Hibbah tace, “Idanma kaga na sake kulaka dan ALLAH ka tsine min Yaya Ammar”.
Baki Ammar ya taɓe da faɗin “ALLAH na gode maka na jefar da ƙwallon mangwaro na huta da ƙuda”.
“Yaya Usman ka ganshi ko?”. Ta faɗa kamar zatai kuka.
“Ya isa manta da lamarinsa auta. Ko sannu karki sake masa har ya warke”.
“Ai baran masa ba ko Yayanmu”. Tai maganar da dungurin wajen ciwon da ke a hannunsa. Ƙaramar ƙara ya saki yana bige mata hannu dan yaji zafi. Ta ƙyalƙyale da dariyar mugunta. Ranƙwashi mai shegen zafi ya bata wanda ya saka bakinta rufewa ruf, sai kuma ta fashe da kuka.
Yaya Abubakar da duk yake jinsu da ga gaba ko kallo basu ishesa ba. Sai ma waya da ya ɗauka yay kiran maigadi ya buɗe musu gate. Koda suka shiga cikin gidan tsitt yake alamar jama'ar cikinsa harsun ƙwanta. Kusa da inda Yaya Muhammad yay parking shima yayi gab da sashensu.
Hibbah da ke kukan ranƙwashin da Ammar yay mata ta fara fita domin kaima Yaya Muhammad ƙara tunda Yaya Abubakar bai bada fuska ba.
“K zoki wuce ciki ki kwanta”. Yaya Abubakar ya dakatar da ita dan bayasan wani dogon magana a yanzu. Yasan kuma indai Hibbah ce bataƙi su kwana ana shashanci ba. Baki ta tura gaba sim-sim ta nufi sashensu.
Yaya Muhammad yay ɗan murmushi yana kallon Yaya Abubakar ɗin. “Siddiq yau fa gaba ɗaya ka zama masifaffe. Kasa duk auta ta firgita da kai”.
“Tana da cika ciki ne wani lokacin”. Yaya Abubakar ya bashi amsa yana kashe motar. Yaya Ammar yace, “Dama hakan kowa ke mata da mun huta da shegen ƙiriniyarta tamkar ƴar mage”.
Kusan duk sai da sukai ƙaramar dariya. Da ga haka suka shige makwancinsu kowa ya nufi ɗakin barcinsa.
Hibbah ma da ta shiga tanata zunɓure-zunɓure shirin barcin tai tana kunkunin wai dan anga Ummi bata nan kowa ya tsaneta. Gobe a asibiti zata kwana bazata biyosu su cinye ta ba.
Da ƙunkunin dai harta kammala shirin barcin ta kwanta bayan tayi addu'a. Sai kuma a lokacin tunanin duk abinda ya faru a wannan yini ya shiga dawo mata. ALLAH dai ya taimaketa barci barawo yaci galaba akanta batare data shirya hakan ba.
*_WASHE GARI_*.
Yau Yaya Umar ne ya shigo yama Hibbah knocking. Sai da yaji ta tashi sanann ya juya ya fita bayan ya mata gargaɗin karta koma barci ta shiga kitchen idan sun dawo salla zaizo ya tayata haɗa breakfast. Da to kawai ta amsa masa dan harga ALLAH barcin bai isheta ba. Sai dai sanin halin masifarsa yasata bin umarninsa bayan ta idar da sallar tai azkar ta fita kitchen ɗin. Bata jima da fara aikin ba suka dawo. Su dukansu babu wanda bai iya girki ba dan Ummi babu abinda bata sakasu na aikin gida. Shiyyasa bata taɓa damuwa da zama da ƴar aiki ba tun da suka fara tasawa.
Yaya Umar ne ya tayata sukai breakfast ɗin. Yaya Usman kuma yanata ƙoƙarin gyara gidan shi da Ammar da ya tayasa dan jikin nasa da sauƙi bakamar jiya ba. Magungunan da aka basa sun taimaka masa matuƙa. Cikin kankanin lokaci suka kammala komai tsaf kowa ya tafi dan watsa ruwa. Sabo da fita aiki yasa duk suka hallara akan lokaci bisa dining. Sai uwar latti ce ko motsinta babu sai da Yaya Muhammad ya je da kansa yay mata knocking.
Koda ta fito masifa Yaya Umar da Usman suka hauta da shi na sakasu yin latti kamar kullum. Cikin son a kareta ta kalla Yaya Abubakar da Muhammad. Duk murmushi sukai mata da nuna mata kujera alamar ta zauna ta rabu da su Umar ɗin. Fuska a kumbure taja kujera ta zauna kuwa. Da ga haka suka fara karyawa.
Sunyi nisa sosai acin abincin Abba ya shigo fagan-fagan Hajiya Mama biye da shi. A tare duk suka ɗago suka zuba musu ido. Sai wani irin tsoronsu da shakkarsu ya shigi su Abban lokaci guda. Yaya Muhammad ne ya fara ɗaule kansa ya maida ga abincin gabansa. Suma sauran duk sai suka yi kamar yanda yay ko gaishesu basuyi ba.
Cikin masifa Hajiya mama tace, Kunci ubanku marasa mutunci. mu zaku kalla ku watsar tamkar wasu kashi?”.
A mamakinsu ko motsi babu wanda yayi, sai ma cigaba da cin abincinsu sukeyi hankali kwance. Hajiya Mama da Abba sukai galala a tsaye kamar gunkuna suna kallon sabon salon iskanci. Suko sunyi tamkarma basusan da zamansu a wajenba.
Wani irin baƙin cikine ya lulluɓe Abba ya shiga zazzaga tujara musamman akan fiddo Ammar, dan dama tun jiya ɗan sandan ya kirasa ya sanar masa. Ya kuma tabbatar masa da Abubakar yana tare da manyansu sosai, idan ya matsa akan Ammar ɗin tofa wata da tafi wadda suka shirya zata taso. Hakan yasa Abbana ɓam da bakinsa. Ya dai ɗauka alwashin zubarma da Ummi tujara tare da sauke duk fushinsa a kanta. Shiyyasa yana kammala sallar safensa da ya keyi a gida kullum bayan rana ta fito ya nufi sashen hajiya Mama ya sanar mata. Shine fa suka taho yima Ummi taron dangi basu san ma bata gidan ba. A zatonsu kuma su Yaya Abubakar ɗin sun fita.
Duk iya tujarar da sukeyi babu wanda yay koda motsi balle nuna yasan da zamansu a wajen har suka kammala breakfast ɗinsu Ammar da Hibbah suka kwashe kayan zuwa kitchen. A gurguje suka wanke kwanikan ita da shi su ka fito dauke da basket ɗin abincin da suka shiryama Ummi irin wanda doctor da suka kira ya tabbatar musu zata iya ci tunda ta farfado tun daren jiyan.
Har yanzu Abba da Hajiya Mama na a sashen suna zubda ruwan tujara. Yayinda kuma babu wanda yay musu koda tari. Hakanne ya sake harzuƙa musu zukata da wanann sabon salon rainin wayon su Yaya Muhammad ɗin. A gabansu kuma suka kulle kowanne ƙofar ɗaki da ke a sashen har kitchen sukai ficewarsu suka barsu a falo. Wannan al'amari yayi matuƙar bakanta ran Abba da Hajiya mama. Kai har ma Momy da ƴaƴanta mata huɗu da duk suka fito saboda hargowar su Abban.
Motar Yaya Muhammad da Yaya Abubakar duk suka shiga yau ma suka fice batare da kowannensu ya hau mashin ba.
Bayan fitarsu tujara ta gidan duniya babu irin wadda Abba da hajiya mama basuyiba a gidan. Ummi ta sha gori da tonon sililin asalinta. Sai da sukayi mai isarsu sukaga babu mai taya musu Sannan sukai shiru. Abba ya shirya fagan-fagan yabar gidan zuwa inda zuciyarsa ke raya masa domin yin maganinsu Yaya Muhammad ɗin baki ɗaya.............✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_Chapter Twelve_*
..............Oho su bama su san sunai ba. Dan koda suka fice a gidan babu wanda yay koda ambatar sunansu Abba ne balle su nuna sun damu da al'amarinsu. Asibiti suka nufa kansu tsaye. Inda sukai tozali da sanyin idaniyarsu da ke zaman jiran isowarsu.
Cike da ɗunbin farin ciki duk suka baibayeta kowa na jera mata tambayoyi game da jikinta da yanda takeji kuma. Komai bata iya ce musuba. Sai murmushi da take musu hannun Hibbah da Ammar a cikin nata tana kallon ciwukan jikin Ammar din. Da sauri ya ce,
“Karki damu Ummi naji sauƙi. Kema ALLAH ya baki lafiya ki cigaba da mana tuwon dawarnan naki da bama son ci”.
A tare suka kyaƙyale da dariya, Murmushin Ummi ma ya sake faɗaɗa ta kai hannu ta shafa fuskarsa. Hannun Hibbah ta kamo ta maida saman tata fuskar. “Ummi nice auta ni zaki shafama fuska ba wannan garjejen mutumin ba”.
Ranƙwashi Ammar ya bata akai. Ta dafe kan da sauri tana sakin karamar ƙara. Ammar ya mike da ga inda yake zaune yana mata gwalo.
“Yaya Umar ka ganshi ko?”.
Harar Ammar Yaya Umar yayi. “Kai wai miyasa baka rabo da zalunci ne. Ko wannan rankwashin da kake mata ma ya hana girma ai taita zama kamar ƴar cilikowa tana addabar mutane da ɗaukar magana”.
Dariya duk suka tuntsure da shi baki ɗaya. Ransu fes da farin cikin tashin Umminsu. gashi doctor ma ya sanar musu nan da kwana uku zasu sallameta taje gida ta cigaba da shan magunguna. Dan dama irin aikin nata mai sauƙi ne inhar an dace da yinsa bisa nasara.
Su suka taimakawa Ummin ta tashi suka jingina mata filo. a tare suka haɗu su duka suka ringa bata abinci duk da Hibbah na isarsu da rigima da rinto. Dan a layi aka dinga bi har Ummi tai musu nuni data ƙoshi. Sai da tasha maganinta sannan sukai mata sallama domin tafiya wajen aiki aka bar mata Hibba da Ammar. Dan su sai ƙura ta lafa zasu koma school musamman ma Hibbah.
Kafin su wuce sun biya office ɗin doctor daya bukaci ganinsu. Bayan sun sake gaisuwa da shi da nuna jin daɗinsu akan nasarar jikin na Ummi ya shiga musu bayani akan wani bawan ALLAH yazo ya biya kuɗin aikin Ummi ɗin duka. Dan haka zai dawo musu da nasu kuɗaɗen insha ALLAH.
Cikin mamaki suke tambyarsa wanene hakan?. Ya sanar musu shima dai bai sani ba kai tsaye. Dan ansha irin wannan taimakon batare da sunsan ainahin wanene ba. Amma kuma bayan hakan ma wani ma ya sake bada kaso ɗaya bisa uku na kuɗin aikin harma ya shiga ya duba Ummi. shima kuma dama yakanyi hakan a wasu lokutan. Yasan kuma zasu gansa suma kafin a sallami Ummi ɗin dan ya fahimci a yau kawai kamar har sabo ya shiga tsakaninsa da Ummi ɗin.
Sosai abubuwan suka basu mamaki, amma sai suka watsar da mamakin sukacema doctor a maida musu kuɗin su da kansu insha ALLAH zasu biya kuɗin aikin mahaifiyar tasu basa buƙatar kowa. Cikin nasiha ya nuna musu hakan ba daidai bane. Sam babu ƙyau maida alkairi baya musamman irin wannan. Suma bawai sun biya bane domin sunga sun gaza.
Dole suka hakura suka amsa tare da yin addu'a ga masu biyan. Da ga haka suka fito domin nufar wajen aikinsu........
_________________________________
A ɓangaren yaran master kam, tun suna zuba idon zaman jiran dawowarsa har suka fidda rai. Dan sun fahimci dai yayi nisan kiwo. Badan sun so ba dole suka tashi sukai shirin barci duk suka kwanta kowa ransa da addu'ar ALLAH ya dawo musu da shi lafiya.
Sukan damu idan yay fitar dare. Saboda sunsan shi sam bayasan yawon dare. Ko su duk aikin da zai sakasu inhar magrib tayi ya haƙura kenan. Sai ko idan ya zama dolen dole. Amma da anyi sallar isha'i basa ƙara fita sai ta lalura.
Koda suka tashi sallar asuba ma basuji motsinsa ba, haka sukai alwala suka fita, dan sunsan duk inda massallacin da ya tadasu yake zasu ganosa a layin insha ALLAH. Sai ga shi fitowar tasu ma ta sakasu fahimtar a ina suke. Ashe bayan layin gidan da suka baro jiya ne. Har cikin ransu suna jinjinama boss ɗinsu, saboda matuƙar wayonsa da basirar iya takun rayuwa. Komai babu wanda ya faɗa suka adana a zukatansu har sukaje salla suka dawo. Sanin yace ƙarfe bakwai da rabi zasu bar gidan yasa basu kwanta ba suka tattare abinda suka ɓata.
Suna tsaka da kimtsawar ne kusan 6:43 sai gashi ya dawo. Kallon mamakin ta inda ya shigo suka shiga masa. Dan sudai basuji alamar buɗe ƙofar gidan ba. Hasalima sakata suka saka mata ta ciki, dole ne sai yayi musu knocking sunzo sun buɗe masa.
Sarai ya fahimci ma'anar kallon da suke masa, amma sai ya basar abinsa. Hakan yasa suka shiga gaishesa da masa barka da dawowa bayan Musbahu ya tashi ya amshi bag ɗin hannunsa.
Hannu kawai ya ɗaga musu, kafin ya fara magana a taƙaice yana nuna bag ɗin da ya shigo da ita, “Gaba ɗayanku zakuyi amfani da kayan cikinta ne, dan a wannan gaɓar magana ake ta kuɗin baƙine ango ya kawo ku kwana anan”.
Cikin girmamawa suka shiga amsa masa suna murmushi. Yayinda shi kuma yay shigewarsa ciki. Zaidu ne ya fara kwashewa da dariya yana faɗin, “Abokan ango waye angon to a cikinku?”.
Salis ya nuna kansa yana wani buɗe hannaye irin eh😉😂. Hararsa Habib yay da taɓe baki. “Banza. Kana ɗan yahoo ubanwa zai baka ƴarsa, wataran shima ka yashe masa asusunsa”.
Sanin boss na gidan ya sakasu fara dariya suna tarewa da hannu. Salis da ke harar Habib ya ce, “Da yake ma talle bataima audi gori duk tafiyar ɗaya ce. Ta wani fanninma gwara ni. Kuma tunda kace haka kwanan nan zakaji na zama ango ɗan baƙin ciki yahoo boy”.
Duka Habib ya kaima Salis ɗin ya kauce yana masa gwalo. Rabi'u yace, “Kai kai ku tsaya kuji. Ni fa da boss yay maganar ɗaurin auren nan sai naji inama irin shine za'a ɗaurama auren. ALLAH na ƙagu naga mai tsaurin idon da zatai wuff da master”.
Dungure masa ƙeya Musbahu yayi da saurin cewa, “Wanan saɓon naka banajin zai tabbata a gidan nan. Inko ya tabbata to lallai sai mun yashe asusun tsohonta tas inaga abiya sadaki da kuɗin auren nata”.
Duk yanda sukaso matse dariyarsu hakan ta gagara, tuni suka shiga ƙyalƙyalewa harda masu faɗowa ƙasa da ga kujera. Khalid ne ya fara farga da Master da tun dariyarsu ta farko ya fito. Tsaye yake a jikin ƙofar ya harɗe ƙafafu da hannayensa a ƙirji kawai ya zuba musu idanu. Da sauri Khalid ya zunguri Rabi'u da ke kusa da shi, babu shiri shima ya gimtse tasa dariya yana zungurin Zaid. Shima Zaid da sauri ya haɗiye tasa yana mintsinin kafar Idris da ke kusa da shi. Musbahu da shima idonsa ya kai yay azamar haɗiye tasa yana rarrafawa zai ɓoye bayan kujera. Habib da Salis da basusan anayi ba kam sai ƙara tuntsurawa suke. Salis yace, “Ni why bana tunanin boss zai wani iya soyayya, dan ita tayi yamma shi yayi gabas. Inagama sai munyi karo-karo wajen badashi sadak......”
Da sauri Musbahu ya rufe masa baki. Hannu Salis ya shiga bige masa yana ƙoƙarin yin magana idonsa ya sauka akan Master da har yanzun yake tsaye yana jinsu. Dan ya wani lumshe idanu tamkar wani mai yin barci a wajen.
Babu shiri Salis ya ture Musbahu gefe ya miƙe da gudu ya afka bedroom. Ganin haka suma duk sai suka shiga rufa masa baya. Wani silent numfashi master yaja yana buɗe idanunsa akan ƙofar ɗakin da suka shigan harda rufo ƙofa. Uffan bai ceba ya juya ya koma cikin ɗakinsa.
Koda suka kammala shirin cikin ɗanyun shaddoji iri ɗaya kalar sararin samaniya suka fito, kasa haɗa ido da shi sukayi. Sai satar kallonsa sukeyi ta ƙasan ido, yayinda dariya ke cin ransu a ƙasan zuciya dan shi tashi shigar ta irin marasa jin direbobin nan ce yayi. Da alama da kansa zai tukasu a mota kenan tsabar iya taku. Gaba yay batare da yayi magana ba duk suka rufa masa baya suna ƙoƙarin gimtse dariyarsu.
Motar bus da zata iya kwashesu ce a waje a fake master nata faman gogewa kai kace driver ɗinne na gaskiya irin wanda suke zuba iya shege a tafa zuwa agege da maraban jos. Dan facemark ɗin dake fuskarsa bata da maraba da ta direbobin da ke tsaka da cin duniya da allura.
Da kansa ya buɗe musu motar yana harararsu dan ganin kallon da suke masa a munafunce suna murmushi. Sai da suka gama shiga ya rufe yana zagayawa mazaunin driver bayan ya dagama matasan dake zaune a wajen mai shayi anata fira akan abinda ya faru jiya na mayar gwamna hannu. Sai zabga gaddama suke kowa na kare abin son sa. Wasu Master, wasu jami'an tsaro, wasu matar gwamna ɗin. Yayinda wasu ke faman zuba ashariya kai kace faɗa ne ya tashi.
Murmushi ya saki yana shigewa a motar saboda jin furicin wani da ke faɗin, “Suma jami'an tsaron lusarai ne da zasu zauna mutum ɗaya ya gagaresu. Kawai dai sunyi niyyar barin shegenne kafin suyi ma rayuwarsa walmakalifatu”
“To ka sani ko aljanine?”.
Wani ya bashi amsa dai-dai master na reverse da motar. Hannu suka ɗago musu wasu na faɗin ALLAH ya sanya alkairi. Dan sun yarda su ɗaurin auren za'aje😂😝.
Lallai maganar yaran master gaskiya ne. Wannan gida yaji kayan ƙawa da more rayuwa. Shi kansa yana matuƙar son gidan. Dan a cikinsa ne kawai yafi sakewa sosai. Sanann anan ne kawai yake zama da yaransa. Amma duk sauran gidajen ba kullum yake kwana tare da su ba sai yaso.
*_BAYAN KWANAKI UKU_*
Alhamdulillahi jikin Ummi yayi ƙyau sosai, dan tattali iya tattali take samu da ga iyalanta sanyin idaniyarta. Yayinda wasu a cikin ƴan uwa ke tururwar zuwa dubata da jiki.
Hibba ce take kwana tare da ita, su kuma su yaya Muhammad da sun taso aiki anan suke tarewa har sai 11 suke wucewa gida. Har zuwa yanzun Abba bai dawo ba da ga tafiyar da yay randa akaima Ummi ai. Itama hajiya mama taɗan lafa da fitinarta saboda ƙafarta data motsa, duk da dai su su yaya Abubakar ɗin sunsan wani abun suke ƙullawa basu nuna sun damu ba.
Junaid ma ya dawo gida bayan kwana biyu da yayi a asibiti. Sai dai kuma tunda ya dawo ɗin ko ƙeyarsa basu gani ba, sai sauran ƴammatan gidan marasa kunya. Su kuma ko kallo basu ishesu ba. Dan a cikinsu wai sonsu su Yaya Abubakar ɗin sukeyi.
Tuni shaƙuwa ta shiga tsakanin Ummi da mutum nan da ya biya kuɗin aikinta kaso ɗaya bisa uku. Dan kamar yanda yaranta ke jurar zuwa kullum safiya dubata haka shima yake zuwa dubata duk safiya. Da rana kuma ya aiko da abinci a kawo mata. Da dare idan ya tashi kasuwa ya shigo da fruits ya sake gaisheta sannan ya wuce. Haka zataita saka masa albarka da masa fatan alkairi akan kasuwancinsa da ya sanar mata yanayi, tare da ma mahaifiyarsa da yace ta rasu addu'a, da mahaifinsa da ke raye.
Addu'ar da take masa ke sakashi jin daɗi. Da kuma yanda su Yaya Umar suka sake da shi sosai tamkar shima ɗan uwansu ne. Hibbah ce dai da ga gaisuwa bata sake kulashi dan dama ita haka take tana da wahalar sabo duk da rawar kanta. Idan kaga ta sake to tare take da Umminta ko yayunta. Su kaɗaine takema yanda taso.
Yau ma suna tsaka da tattare kaya dan an sallamesu Ummi zataje ta cigaba da shan magani a gida yay sallama. Sai da Ummi ta amsa da bashi izinin shigowa sanann ya shigo. Hibbah da ke haɗa kayan ko ɗagowa batai ba balle ta nuna tasan da zamansa. Shima kallo ɗaya yay mata ya dauke kansa. Dan har cikin ransa kallon miskila yake mata tunda ba yarda take tai magana a gabansa ba. Ko surutu take da ya shigo take gimtse bakinta.
Cike da girmamawa ya gaida Ummi da tambayar ta yaya jikinta?. Fuskarta faɗaɗe da murmushi tace, “Alhmdllh yaro na. Ykk ya Abban naka shima?”.
“Lafiya lau ya ke Ummi, yana ma gaisheki da baki haƙurin rashin zuwansa saboda shima yana ɗan fama da ƙafa ne”.
“ALLAH sarki babu damuwa ai. ALLAH shima ya bashi lafiya yasa kaffara ne. Yaya iyali ko babu kaima kamar ƴan uwan naka?”.
Murmushi yayi yana duƙar da kansa ƙasa da kai hannu ya shafi wuyansa zuwa ƙeya. “Ku mana addu'a dai Ummi, ALLAH ya bamu nagari”.
“To amin. Amma ni bansan mi kukema hange-hangen ba sam. Mutum bazai yi aure da ƙuruciyarsa ba kamar yanda iyayenmu sukai mana sai ya gama tsofewa. Ni ban sani ba ko tsoron matan kuke ji ne wai?”.
Murmushin sa ne ya sake faɗaɗa sosai yana faɗin, “Ummi tsoro kuma? Kawai dai matan ne sai a hankali, sai ka dage wajen zaƙulo mai tarbiyya gudun dana sani”.
“Da kuma wanan dan wanan. ALLAH ya baku na gari to”.
“Amin Ummi mun gode”.
Yay maganar yana duban Hibbah. Da sauri tace, “Ina yini”. Yanda tai ɗin ma harya so bashi dariya. Fuskarsa ɗauke da murmushi yace, “Autar mu ykk ya ƙoƙarin kula mana da Ummi?”.
A ranta tace, (Kaji ɗan iya). A fili kam sai tace, “Alhmdllhi Yaya Isma'il. Ya Abba?”.
“Abba yana lafiya, yana ma gaishe ki”.
Murmushi kawai tai batare da ta sake cewa komai ba. Shima sai ya mike kawai yana faɗin, “Ummi bara naje waje idan kun gama shiryawa sai mu wuce”.
Zaram Hibbah tace, “Ai ga Yaya Ammar nan zaizo ya maidamu gida a motar Yaya Muhammad. Dama kaje abinka mun gode”.
Ɗan kallonta yayi na wasu sakanni. “Oh auta, kodai bakison naima Ummi rakkiya na samu lada ne?”.
Baki ta tura gaba ta dauke kanta batare data amsashi ba.
Ummi tai murmushi da faɗin, “Kaga manta da ita Isma'il. Tunda kazo ka kaimu kawai shi Ammar ɗin bara na kirasa basai ya amso motarba ma”.
Godiya yay mata yana ficewa. Hibbah kuma ta hau ƙunkunin ita batason motarsa ya cika shishshigi. Ummi na jinta amma tai mata banza. Sai ma ƙoƙarin kiran Ammar da takeyi a waya akan ya dawo basai ya amso motar ba ga Isma'il yazo.
Badan Hibbah taso ba Isma'il ya kaisu har gida. Sai dai bai shigaba iyakarsa waje ya juya duk da Ummi tace ya shiga. Haƙuri ya bata akan yana sauri ne zai koma kasuwa.
Albarka sosai Ummi ta saka masa. Hakama Ammar yayta masa godiya. Hibbah kam dama tuni ta shigewarta cikin gida. Sai Ammar ne ya kama Ummi suka shiga cikin suma. Babu motsin kowa a gidan da alama yaran duk sun fice. Hajiya mama kuma maybe tana barci ko kallon nata na masifa dan bata gajiya da sanya ido a television, shiyyasa jikokin nata har tsiya suke mata akan hakan.
Ko mintuna ashirin basuyi da shigowa ba maƙwafta suka fara shigowa ƙara yima Ummi sannu. Ciki harda Zahidah da Hafsat tare da iyayensu. Sune suka taimakawa Hibbah wajen gyara gidan tsaf. Suka kuma daura girki. A kitchen ɗinne suka sami damar mata tambayar abinda ya faru ranar game da tafiya da ita da ƴan sanda sukayi.
Duk da aminanta ne tun ƙuruciya sai bata faɗa musu komai ba yanda ya faru saboda tuno gargaɗi da akai mata akan idan ta fitar da zancen za'a saka mata ƴan uwa a tarko. Ta dai basu labarin iya abinda zata iya. Sosai sukaji takaici har cikin ransu. Nan fa suka shiga labarin rauni da hukumomin tsaron ƙasar nan suke da shi.
Zahidah tace, “A kullum ca ake ana aiki amma babu alamar hakan a ƙasa. Shin laifin gwamnati ne ko na jami'an tsaron?.”
Cikin taɓe baki Hibbah ta amshe da faɗin, “Kema dai ƙya faɗa Zahidah. Ita kullum gwamnati tana faɗar kuɗaɗe da take warewa domin harkar tsaro. Amma su jami'an tsaron kullum ca suke basu da kayan aiki isassu. To wai kuɗinne ba'a warewa? Kokuwa jami'anne basa saye? kasa kuɗin suke a tebir kowa ya dauka kasonsa?”.
Da tsantsar takaici Hafsat tace, “Duk ma yanda sukeyi ɗin ai akwai ranar tonon asiri. Ranar da babu wani gacci ko mayafi da ya isa lulluɓe tsiyar da aka shuka aka binne. Ranar da za'ai walƙiya muga kowa da ayyukansa”.
A tare Zahidah da Hibbah sukace, (Insha allahu kuwa).
Haka dai suka cigaba da tattauna abubuwa da dama har suka kammala girkin suka sake gyara Kitchen ɗin. Koda suka fito ɗakin Hibbah suka wuce dan har yanzu ƴan dubiya nata shigowa. Sai dai bayan maigadi ko karen da ke a cikin gidan har yanzu bai leƙo ba. Dama kuma basuje asibitinba. A cewarsu ai ba'a sanar musu bata da lafiya ba.
Sai dare samarin na Ummi suka dawo. zuwa lokacin sashen tsit da ga Ummi sai Hibbah kawai. Hibbah ma tayi barci a kujera dan akwai gajiyar asibiti tare da ita. Sai sautin kiɗa dake tashi da ga sashen momynsu Junaid da hayaniyar ƴammatanta. Da alama wani fati sukeyi, duk da dai shan kiɗa a gidan ba sabon abu bane ba dama.
Sannu Ummi tai musu. Yayinda suka zagayeta kowa nason jin yaya karfin jikinta?. Cike da jin daɗi da fara'a take amsa musu. Kafin tace suje suci abinci kar yayi sanyi. Ammar zai tada Hibbah Ummi ta hanashi.
“ALLAH ka tada ita sai naci gidanku, ka barmin yarinya ta huta ta gaji wlhy, dan tamace kanta ke ciwo”.
“ALLAH yasa gaskiya ne Ummi. Ni naga a kwanaki ukun nan wani sabon hankali take ji da shi. Ko ciwonki ne ya sata nutsuwa oho”. Ammar ya faɗa yana dariya.
Suma su Yaya Muhammad duk murmushi sukayi suna nufar dining.
★★★
Har washe gari babu wanda yazo ya duba Ummi a cikinsu hajiya Mama. Abba dama bai dawoba har yanzun. Ummi ko a fuska bata nuna ta damuba. Haka suma su Yaya Abubakar babu wanda yace uffan akan hakan. Sai ma tarkata Hibbah sukai ta wuce islamiyya tun safe kasancewar yau ɗin weekend ce akwai tahfiz da take zuwa dama har suma kansu.
Badan taso zuwan ba ta tafi harda ƙwallanta dan taga abokin hamayyarta Ammar yau bazai je ba. Da yake a kafane babu nisa ita kaɗai ta fita. Sai da ta fitane taci karo da Hafsat da Zahidah sun taho biyo mata dama. Gaisawa sukai da tambayar jikin Ummi sannan suka wuce islamiyyar.
Islamiyya ce babba matuƙa. Dan tun da ga ƴan shekara uku har zuwa saba'in duk zasu iya karatu a cikinta. sai dai su yara da ga shekara uku zuwa ashirin da biyar suna zuwa ne tun safe har yamma. Daga ashin da shidda zuwa har tsoffi suna zuwa bayan sallar azhar har magriba, kuma iya weekend ne kawai. Dan haka su su Yaya Muhammad sai karfe biyu zasuje. Itace dai da Ammar dama ke tafiya tun safe. Ammar kuma yau akwai abinda zaiyi shiyyasa bazai je ba.
Kamar kowanne sati yau ma sun ɗauki darasi daban-daban har zuwa ƙarfe biyar na yamma da aka tashe su. A ƙafa suka taho Zahidah da Hafsat nata hira banda Hibbah. A yanda suka lura gaba ɗaya ta zama wata shiru-shiru. Kafin faruwar wannan al'amarin a kowane sati sukaje islamiyya sai ta addabi kowa a ajin ko ta takalo faɗa. Su kansu malam sun buga har sun bari, dan mafi yawancin lokaci ƙoƙarin ta ne ke cetonta akan wani tsiyar idan ta tafka.
Cike da jin haushi Hibbah ta ja tsoki tana tsayawa cak da ga tafiyar da sukeyi. Kallonta Zahidah da Hafsat sukai cikin alamun sonjin lafiya?. Bata tanka musu ba, sai kallonta da ta maida kan motar da ke bin bayansu ta gefen titi tunda suka fito Islamiyyar. Suma su Hafsar ɗin sun lura tun ɗazun, sai dai basu kawo a ransu mai motar su yake bi ba. Musamman da ya kasance ya ɗan basu tazara.
Domin tabbatar da su ɗin yake bi a bayyane yay fakin dai-dai inda Hibbah da ta cika tai fam da takaicinsa take.
Cikin takun nutsuwa da cikar haiba ga ma'abocin kallo ƙyaƙyƙyawan saurayi mai tarin kamala ya sanyo kafarsa ƙasa dai-dai yana buɗe ƙofar motar mai baƙin gilashi (tinted glass). Wani shegen ƙamshin turarensa ne ya daki hancunansu tare da sallamar da ke fita cikin ƙasaitacciyar muryarsa mai tarin nutsuwa da sanyi.................✍
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
_________________________
*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻
*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*
_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawa nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki._
*_Muna da haɗin_*
_Turaren wutane_
_Humrh_
_Kulacham_
_Turaren wanka_
_Turaren Kaya_
_Gyaran jiki_
_Na amare_
_Da masu jego_
_Da sabulai masu gyara fata_
*_Da magungun nan mata_*
_Irin su kaza_
_Tantabara_
_Tsumi_
_Gumba_
_Zuma_
*_Duka akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*
Wushishi road KADUNA
08067807620
09057713999
_________________________
*_Chapter Thirteen_*
............Gaba ɗaya jin su Hibba ya ɗauke ɗaf a cikin kunnuwansu lokaci guda. Dukansu sun zuba masa ido tamkar waɗanda sukai gamo da wata baƙuwar hallita. Namiji ne tsayayye da za'a iya kiransa namijin gaske a kowacce irin nahiya ko ƙabila. Sanye yake cikin shadda oxblood da ta fidda ainahin kalar fatarsa mai sheƙi. Fuskarsa cike take da ƙasunba da wani madaidaicin gemu mai kama da na gayu irin na ustazan wanan ƙarnin (😳Bily🤐).
A kallo ɗaya zaka fahimci rashin son hayaniya daga garesa. Da alama kuma ba mutum bane mai yawan sakewar fuska a mu'amula ko a yanayi.
Ganin sun shagala wajen kalon sa ya saki wani shegen murmushi yana ƙarasa takowa gaban Hibbah gab. Haka kawai takaici ya kama Hibbah da kallo guda tai masa ta ɗauke kanta tun ɗazun. Cikin ɓata fuska da yatsineta ta ce, “Malam lafiya? Tun ɗazun ka ke ta binmu sai kace wani mai gadin mu”.
Murmushi ya kuma saki, jerarrun haƙoransa farare na bayyana. Ƙoƙarin saka ƙwayar idanunsa cikin nata yake, amma sai taƙi. Sai ma harara da ta sake zuba masa ta ɗauke kai. A hankali taja siririn tsakin da yasa Hafsat da Zahidah shurin ƙafarta da galla mata tagwayen mintsini.
“ALLAH ya isa”. Ta faɗi tana hararsu bayan ta saki ƴar siririyar ƙarar data saka baƙon nasu ƙyalƙyalewa da wata dariyarsa da ke fita a nutse. Harara ta sake zuba masa zata bar wajen yay saurin shan gabanta.
Haushi ya sake kama Hibba. A tsiwace tace, “Malam kana shigarmin hanci fa”
“Ba malam ɗin bane ai. *_Muhammad Shuraim Aliyu_* ne. Idan kina son nabar shiga hancinki address da number kawai nake buƙata”.
“Baka da man kai” ta faɗa tana raɓawa ta gefensa ta wuce batare da ya samu koda harar ba yanzun. Badan Zahidah da Hafsat sun so ba sukace masa (bye) suna bin bayanta. Motarsa yay azamar komawa ya cigaba da binsu duk da uban sauri da Hibbah ke zabgawa tamkar zataci da ka. Jitake a ranta da da akwai lungunan da zatabi ya kaita gidansu da shi zatabi dan taga ƙarshen naci. Sai dai kash, tun daga islamiyyar har zuwa gidansu layine ɗoɗar.
Itace ta fara shigewa gidansu, dan ata wannan hannun itace farko kafin su Hafsat. Dan haka mai mota Shuraim ya tsayar da su Zahidah. Dole suka tsaya dan baiyi kama da wanda za'a cigaba da yarfatawa ba.
“Kuyi haƙuri fa na takura muku, naga mahaɗi nane babu damar yin sakaci. Dan ALLAH miye sunan ƙawarku?.”
Kallon juna Hafsat da Zahidah sukayi. Roƙonsu da ya sake yi ne ya saka Hafsat cewa, “Muhibbat! Aliyu Hamza”.
“Masha ALLAH, nice name. Nan ne gidansu?”.
A taƙaice suka bashi amsa da eh. Shima sai bai sake jan zancen ba yay musu godiya ya koma motarsa ya wuce.
“Gaskiya Hibbah ƴar yawa ce, amma fa guy ɗin nan ya haɗu ALLAH. Yaci sunansa Muhammad Shuraim”. Zahidah ta faɗa tana lumshe ido.
Hafsat tace, “Shiyyasa ai na faɗa masa sunanta. Waya gaya mata ana sakaci da irin waɗan nan gayun a wanan ƙarnin.”
“Barta ai zamuyi maganinta. ALLAH dai yasa har a hallaya haka yake, da kuma zancen aure yazo mu raƙwashe. Dan zanso Hibbah ta auri guy ɗin nan kodan ta kere sa'a a cikin shaggun su Amlah ɗin gidansun can. Masu shegen kakkafi da son asani. Su adole suna hawa motoci. ALLAH idan suka ga guy ɗin nan sai sun haukace. Sai dai kuma ya musu nisa da na Hibbarmu ne”.
“Insha ALLAH”. Cewar Hafsat tana ƙyalƙyala dariyar mugunta. dan harta hango idon ƴan gidan su Hibbah da kullum suke mata iyayi akan su sun waye, sun girmeta. Suna hawa motocin da Abbansu ya saya musu su ƴaƴan so banda Hibbah.
★_____________★____________★
A ɓangaren Master kam tunda suka koma L.E street shida yaransa sukai luf abinsu tamkar basa ƙasar. Da wannan damar jami'an tsaro suka sami na barazanar cewar ya tsorata da harin da suka kai masa ne, ƙilama sun sami nasarar kashesa dan sun harbesa.
A lokacin da yaga wannan rahoto ba ƙaramin dariya abin ya bashi ba ƙwarai da gaske, ya saki wani malalacin mmurmushi mai ƙunshe da ma'anoni masu yawan gaske da shi ya barma kansa saninsu. Har cikin ransa yana mamakin sai yaushe ne ƙasarmu ta gado zata canja ne? Ji dai shareriyar ƙarya da wanɗan da suke amsa sunan iyaye manyan ƙasa suka karkace suka gilla dan kawai su burge su kuma kankaro ma kansu girma.
Yaransa kansu abin ya basu dariya. Har cikin ransu suna tausayin ranar da Master ɗinsu zai maida murtani ga waɗan nan mutanen. Inhar bai kaisu kwance ba tabbas sai ya sakasu kuka da hawayensu ko su ajiye aikin koda lokacin ritaya ɗinsu baiyi ba.
Shi ba'a sakashi yin abu dole, dan haka baice uffanba sai ma sake lafewa da yay domin tabbatar da zancen nasu. Yayinda a gefe kuma idanunsa ƙur akan batun matar gwamna da hukumar sa'ido akan ta'annati da kayan gwamnati take bin cika har yanzun. Jira suke suyi wani sakaci ko kaɗanne ya sake bankaɗo wasu surukan nata ma duniya harma da su kansu...
____________★__★__★___________
“K kuma lafiya kika shigo kina cikama mutane baki da iska?”. Ummi ta faɗa tana kallon Hibbah da dawowarta kenan da ga islamiyya.
“Babu komai Ummi. ALLAH yunwa nake ji ne”.
“Shi abincin da kika tafi da shi fa?”.
“Ummi naci fa. Kawai wata yunwar dai nake sake ji”.
“To ALLAH ya ƙyauta, sai kije ki fara yin wanka kiyi salla sannan kizo kici”.
“Ummi dan ALLAH ki barni in fara ci ni dai”.
Komai Ummi bata sake ce mataba. Sai ma miƙewa tai ta shiga takawa a hankali domin zuwa ɗakinta tai salla. Dan har yanzu jikin nata bawai yayi ƙarfi yanda ya kamata bane. Abincin ma Yaya Usman ne ya yisa kafin su wuce tasu Islamiyyar.
Sai da Hibbah taci tai nak da abinci sannan ta shige ɗakinta. Bata fito ba sai wajen 8:30 da tajiyo hayaniyar yayunta. Cike da ɗokin dawowar tasu ta fito. sai dai ganin harda Isma'il ya sata yin turus.
Komai babu wanda ya ce mata a akan yanayin nata. Sai ma tsokanarta faɗa da Ammar ya shigayi. Amma sai bata tayashi sunyi ba. Masifa ma taketa faman yi a ranta na yanda yayun nata suka sakema Isma'il ɗin kai kace ɗan gidan ne. Shi kansa yanda yake komai kansa tsaye sai ka rantse gidansu ne.
Bata wani jimaba tai musu sai da safe ta shige, ta barsu a falon suna kallon ball suna hira da cin abinci. Ummi ma tunda ta leƙo suka gaisa da Isma'il ɗin ta koma ciki abinta. Dan haka Hibbah bata san sanda Isma'il yabar gidan ba.
Washe gari dai an tafi islamiyya babu fushi. Sai dai kuma damuwar ƴan sandan can da ke damunta har yanzu ya sakata komawa wata silent kwana biyun nan. Ko magana ma bata cika sakin jiki tayi ba. Sannan har yanzu bata sake hawa computer ba. Dama wayarta tunda ta dawo take a kashe taƙi ta kunna.
Yau ma suna fara tafiya a kan hanyarsu ta zuwa islamiyya ta fahimci ana binsu a baya. Wani takaici ne ya turnuƙe ta dan tsaf ta gane guy ɗin jiya ne da tun a ƙofar gate ta watsar da lamarinsa. Ba kuma ta sake tunawa da shi ba sai yanzu da taga motarsa. Sam Zahidah da Hafsat su basu lura da shi ba. Hakan yasa Hibbah fuskewa batace komai ba har suka shige cikin islamiyya.
Ƙarfe biyar suka ta shi yau ma tamkar kowane weekend. Da ga nan kuma sai wani satin. Gaba ɗaya ta sake watsar da lamarin wani Shuraim. Amma a mamakinta sai gashi ta sake ganin yana biye da su har gida. Kamar da safe yanzu ma bai yunƙurin fitowa ba. A yanzu kam su Zahidah sun ganshi. Koda sukaima Hibbah magana sai tai musu tsaki ma.
Ƙyaleta sukai ganin shima bai fito a motar ba.
★★
Duk yanda Hibbah taso watsar da lamarin Shuraim sai hakan bai yuwu ba yau. Dan lokaci-lokaci yakan faɗo mata a rai. Sai dai takan ja tsaki da murguɗa baki tamkar tana a gabansa. Har takai abinda takeyi ɗin ya bama Ummi haushi ta balbaleta da faɗa har su Yaya Muhammad suka shigo.
Sune suka bama Ummin haƙuri da fara tambayar Hibbah cikin lallashi ko wani abu ke damunta ne?. Sam batasan wani boye-ɓoye ba. Musamman ma awajen yayunta da suke da matukar shaƙuwa da juna. Kanta tsaye ta shiga basu labarin abinda takema tsakin.
“Woow, ƴar Tanee ɗin Ummi anyi saurayi Congratulations. Yau ɗaya a tarihi dole na rubuta na ajiye na haɗa da shagalin barbaje kolin fati na musamman a gidan nan nayi suriki a matsayina na yaya mai lasisin cin gadon Muhibbat Aliyu Hamza (Tanee)”. Ammar ya faɗa yana tafa hannaye cike da tsokana. Filo Yaya Abubakar ya ɗauka ya jefe sa da shi. Dariya gaba ɗayansu suka kwashe da shi saboda yanda Ammar ya baje a ƙasa da bata fuska alamar yaji zafi..
Hibbah kam dariya sosai take masa harda faɗowa saman kujera. Ta saka yatsun hannunta a kunne tana masa gwalo kamar yanda yara keyi. Filon da aka jefesa da shi ya ɗauka zai jefo mata ta tashi da gudu tai hanyar ɗakinta.
“Ummi kanta sai da tai dariya. Cikin dariyar ne ta ce, “ALLAH dai ya shirye ku, kai da Tanee ɗin bansan wanda yafi wani shashanci ba. Ni tashi ka ɗakkomin magunguna na a ɗaki tunda ita ta gudu nasan ba sake dawowa zatai ba kuma”.
Amsawa Ammar yayi da to yana mikewa ya nufi ɗakin Ummin. A dai-dai kuma wanann lokacin Abba da hajiya mama da wasu tsoffin maza biyu suka shigo falon da sallama.
Da ga Ummi har yaranta da mamaki suke kallonsu, musamman ma Abba da basusan ya dawo gidan ba. Tsoffin kuma Ummi ce kawai ta sansu. Da ƙyar ta iya buɗe baki cikin ƙarfin hali ta ce, “Kawu sannunku da zuwa”.
Farin ne kawai yace, “Uhumm”. Ɗaya kam bai tanka ba. Sai dai bin su Yaya Muhammad da yake da kallo tamkar idanunsa zasu faɗo ƙasa.
Yaya Muhammad da ya lura da kallon ƙurullar da kuma yanayin da Ummi ta shiga tamkar na ruɗani ya saka shi fara gaishesu. Haka yasa suma sauran ƙannensa fara gaisuwar.
Amsa musu sukai suna cigaba da kallonsu. Yayinda hajiya mama keta faman ƙyaɓe baki. Abba kam sai wani harare-harare yakeyi.
Ummi tai ƙasa da kai cike da ladabi ta hau gaishesu itama. Basu wani amsa mata da ƙyau ba. Sai ma baƙin tsohon ne a kausashe ya ce, “Uh lallai Asiya an samu guri kam tabbas. Ga manyan sojoji kuma a gefe masu tare miki faɗa. Dama irin wanan ai ake gudu akan auren masu asali irin naki. Saboda shi hali naso yakeyi har jikokin bayan-baya. Gashi ko mun gani yau da idanun mu”.
Idanu Ummi ta lumshe a hankali kanta a ƙasa. Wasu zafafan hawaye suka silalo saman kumatunta. Sai dai cikin dabara ta kai hannu ta share dan kar ƴaƴanta su gani. Cikin dauriya da juriyar da kowa ya santa da shi ta ɗago murmushi a saman fuskarta. “Kawu ina fatan kunzo lafiya?”. Ta faɗa domin son kauda wancam zancen da ya fara.
Sai dai sam bataci nasara ba. Dan kuwa hajiya mama ce ta amshe da faɗin, “Ni ko zan faɗa maka hali naso yake Hannafi, dan kuwa gashi nan a zuri'a ta. Wlhy badan jinin ɗan inna (babansu Hibbah) na yawo jikin waɗan man yaran ba da tuni na daɗe da sallama su, babu wanda ya cuceni sai malam da ya ƙarrafa wannan auren da har na mutu bazan taɓa daina kuka da ALLAH wadai a kansa ba. Wai fa kuga waɗan nan sanƙama-sanƙaman yaran ne babu mai ko neman aure. Kuma uwarsu ta zuba musu ido saboda ita ɗin bata hanyar.......”
“Waɗan nan kuma fa? Da ga ina?”. Cewar Ammar da ya fito da ga ɗakin Ummi yaci karo da abinda bai bari ba. Furucinsa kuma ne ya katse zancen da Hajiya mama ta ɗakko tiryan-tiryan.
Babu wanda ya bashi amsa. Sai zuba masa ido da tsoffin sukai tare da Abba. Baki ya buɗe zai sake magana Ummi ta girgiza masa kanta. Kansa ya ɗauke kawai tare da durƙusawa gabanta ya na ajiye ɗan basket ɗin da magungunan nata ke a ciki. Ɓalla mata ya shigayi yana miƙa mata tare da saka mata ruwa akan baki.
Wani uban salllami farin tsohon nan ya shiga jerawa yana tafa hannaye. “Kai mizan gani haka ni Ballo (Bello😂). Wannan wane irin kafurcine kuma haka Hasiya?. Wannan ƙurmisheshen gardin ɗan ke baki ruwa a baki kuma?. A to lallai zancen Hannafi gaskiya ne. Da alama ma ke kinfi uwar taki iya shege”.
A fusace Yaya Umar ya miƙe zai bar falon. Abba ya katsesa a gadarance da faɗin, “To mara mutunci da baiyi gadon arziki ba sai ka tsaya dan zuwan nakune ai”.
Ido Yaya Umar ya rimtse da ƙarfi yana dunƙule hannunsa.
“Kai fitsararre, idan shi ka rainashi ai mu ka ɗaga mana ƙafa kodan rashin saninmu da kai ko.”
Ƙafa Yaya Umar ya ɗaga zai cigaba da tafiya wasu hawaye masu zafin gaske na gangaroma kumatunsa.
“Dawo ka zauna”. Umarni da ga Ummi ya hanashi ajiye kafar da ya ɗaga ɗin.
“Iyeee! A lallai Haƙilu kuna ganin jalalar rayuwa. Wato itace kawai mai sawa da hanawa akan ƴaƴan, bayan wahalar da kaci na kula da su tsahon shekaru. Tabbas Hasiya kinyi asara kekam.
Da sauri Ammar ya ɗago ya kallesa. Ya miƙe tare da nuna Kawu Bello da ɗan yatsa cikin kaushi da ɗaci yace, “Kai kaine kai asara tsohon banza ɗan tasha”.
A tare Hajiya mama da Abba da kawu Bello da kawu Hannafi suka zazzaro ido suna zabura. Ummi tai saurin fisgo hannun Ammar tare da daka masa tsawa. “Aliyu!!”.
Cikin ficewar hayyaci ya fisge hannunta a cikin nasa da faɗin, “Haba Ummi, wai sai yau she ne zaki daina zama anacin kashi akanki a gidannan ne? Babu ruwana da alaƙarsu gareki. Na rantse da ALLAH idan tsoho bai gyara kalaman harshensa ba to kafin ya fita a falon nan zan datse harshen kuwa na jefar ƙasa”.
Ɗimmm
Ummi ta sauke ma Ammar dundu. “Ammar kanada hankali kuwa? Miyasa kai bana faɗa maka kaji ne wai?. Kasan waɗan nan ɗin su wanene a wajena? To iyayena ne, ƙannen mahaifiyata ne, tamakar yanda Hajiya mama ta ke uwa a gareni itama. Ka shiga hankalinka kona saɓa maka kaji ko”.
“Amma Umm.....”
Wani kallo da ta masa ya sakashi yin shiru ya haɗiye sauran maganar.
Wata ƴar dariya Abba yayi da faɗin, “Kun gani ko? Hakafa gidan yake kullum kamar na ƴan tasha. Sun rainani basa ganin mutunci na bale na mama, bayan ma yaƙi nai da zuciyata wajen rufa mata asiri. To uwar tasu ma ba wai raga mata sukeyi ba. Dan haka na ɗakko ku nan dan ayita ta ƙare. Bazan iya cigaba da ciyar da ƙattan banza ba. Dan haka na yanke shawarar aura musu su Amlah, inba hakaba wataran yankan rago za'a samu sunmin a gidan nan. Ita kuma waccan fitsararriyar uwar ƴan janye-janyen jidalin da suke ɗaurama ƙugu a gidan tana zuba taɓara saboda ita ƴar ido ce Junaid zan aurawa. kunga shikenan anyi tuwona maina ko ba komai sun huta da gori ma asalin uwarsu.”
“Wannan gaskiya ne Haƙilu. Ai kama taimaki rayuwarsu. Dan a zamanin nan kowa yaji tushen zancen ta ina zai basu ƴarsa. Balle ma ita da take ƴa mace. Bayan ma ka riga ka bata Junaidu ɗin ai wlhy da nayima Musa kamu ma”.
Da sauri Abba ya ce, “Shi Musan sai yay haƙuri tunda na riga naima Junaid ɗin alƙawari dai. ALLAH ya bashi ta shi”.
Yaya Muhammad da ya ƙule matuƙa da takaicinsu ya buɗe baki zai yi magana. Amma sai Ummi tai saurin girgiza masa kanta cikin gargaɗi. Kawai sai gani tai hawaye suna sakko masa tsabar zuciyarsa ta kai ƙololuwa a ɓaci.
Ummi itace ke katange dukkan yunƙurinsu, sun rasa miyasa take hakan a gare su game da dangin mahaifin nasu. Abinda ma basu gane ba shine a yau. Shin ta amshi ballagazayen ƴaƴan gidan da ake iƙirarin an basu kenan matsayin matansu ko mi? Koda ace zasuyi haƙuri suyi mata biyayya bazasu taɓa amincewa a aurama Junaid Hibbah ba. Sai dai komi zai faru ya faru wlhy...........✍
*_Tofa masu karatu, yaya kenan? Wanene zai ci nasara tsakanin su Abba da su Yaya Muhammad? Ni kaina inason jin wace ƙaddarace baibaye da Ummi da ta fi bukatar haƙuri da cin kashin waɗan nan mutane haka?. Kumuje zuwa. muna gab da tsunduma cikin wasan gadan-gadan😉👎🏻_*
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________
*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻
*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*
_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawa nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki._
*_Muna da haɗin_*
_Turaren wutane_
_Humrh_
_Kulacham_
_Turaren wanka_
_Turaren Kaya_
_Gyaran jiki_
_Na amare_
_Da masu jego_
_Da sabulai masu gyara fata_
*_Da magungun nan mata_*
_Irin su kaza_
_Tantabara_
_Tsumi_
_Gumba_
_Zuma_
*_Duka akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*
Wushishi road KADUNA
08067807620
09057713999
_________________________
*_Chapter Fourteen_*
.............A gidan Ummi komai ya canja. Gaba ɗaya ya ranta sun bar walwala. Sun daina fara'a. Sun daina zaman hira, abinci ma kaɗan suke tsakura. Idan tai magana suce sun ƙoshi. Ta ko ina ta gaza gane kansu.
Da farko tayi biris da su, duk da kuwa ta fahimcesu tsaf. Sai dai ganin abin nasu bana ƙare bane sai itama lamarin ya fara damunta. Dan ita kanta sun jefata a cikin kaɗaici. Hatta da Hibbah ƴar karamarsu itama ta ɗauke mata wuta. Saboda wannan abun daya faru ma ta tattara ta koma makaranta duk da Yaya Abubakar ya hanata zuwa da.
Duk da ta ɗan fuskanci ƙalubale a wajen mutane a ranar data koma saboda tafiya da itan da ƴan sanda sukazo sukayi ranar haka ta daurema zuciyarta ta cigaba da zuwa. Bakuma ta sanarma kowa ba. Dan a ganinta da zaman gidan su tana cigaba da ganin Abba da baƙinsa gara kallon da ƴan makarantar zasu mata.
Tunfa Ummi na ɗaukar lamarin nasu wasa sai ƙara girmama ya keyi. Dan kwanakin nan biyu ma basa dawowa gidan sai sun dai-daici tayi barci sannan. Hankalinta sosai ya kuma tashi. Ga damuwar yaranta, ga damuwar auren da aketa ƙulle-ƙullen nana musu na son zuciya. Wanda tsaf ta gama fahimta da gane ina hakan ya dosa. Sarai ta gane manufar Abbah akan son ƙulla auren ƴaƴanta da nashi, manufar kuma duk ɗaya ce tsakaninsa da hajiya mama.
Gaba ɗaya ta rasa ina zata saka kanta taji sanyi, babu uwa babu uba, babu abokin shawara a cikin ƴan uwa, babu wanda zata kaima ƙara ya duba matsalarta ya share kukanta. Gudun abinda zaije ya dawo kuma ke sakata kwaɓar ƴaƴanta akowane lokaci. Bata son abinda zai rabata da su. Bata son a cutar mata da su. Dan sune hope ɗinta, sune murmushin fuskarta. Sune masu share hawayenta da tun tana ƴar ƙanƙanuwarta suke kwaranya a bisa kumatunta. Tasan nuna ƙarfinsu ya kawo kuma zai iya zama sanadin da komai Abba zai iya aikatawa a garesu domin samun cikar burinsa, kuma kamar yanda yasha faɗa koda ya salwantar da rayukansu babu mai yarda shine ya aikata. Wasu hawaye ne masu zafi suka silalo mata saman fuska.
Wata banzar dariya Abba da ke shigowa cikin sashen ya shiga tuntsurawa yana tafa hannaye. Cike da izgili ya dubeta sheƙeƙe yana faɗin, “Kuka kuka kuka! Ai kuwa yanzu kika fara kuka Asiya. Yo ina jarumtar taki ne yau? Shin har kin fara zuwa ƙasa ne tunkan ma a ɗaura auran manufarsa kuma ta tabbata?. Tunda har kikace ni ban isaba Asiya, to wlhy kema bazaki taɓa isa ba. Yau ina wanda kike gadar da shi? Ya tafi tamkarma ba'ayisa ba. Abinda kika hanashi yay mana ta hanyar zagon ƙasa ya dawo hannunmu a lokacin da ko ido baki isa ɗagawa akai ba. To suma ƴaƴa mazan da kike ɗagawar kin haifa masa zasu mamaye komai tafin hannunmu zasu cigaba da zama ballagaza kawai. Zaki iya tashi kuma mu shige ciki dan ina bukatar haƙƙina. Inba hakaba kuma zan ƙwata anan cikin falon babu ruwana....”
Hanyar bedroom ɗinta ya nufa yana gama faɗa alamar ta biyosa. Ummi da ke jin wani ƙullutun abu yazo ya tokare maƙoshinta ta shiga karanto duk addu'ar da tazo mata a saman harshe saboda jin numfashinta na fita a gwagwgwame. A hankali sanyi ya rinƙa shiga cikin ƙashinta, yayin da jikinta ya fara wani irin rawa, har haƙwaranta na haɗuwa waje guda. Hannu takai domin lalubo wayarta da ke saman centre table. Sai dai hakan ya gagara sakamakon gushewar gani da ta risketa a lokaci ƙanƙani. Hannunta ya goce da ga lalube wayar, sai gata ƙasa wanwar da ga saman kujera.....
A dai-dai wannan lokacin Hibbah ta shigo tana masifar bibiyarta da kullum Shuraim keyi babu fashi balle nuna gajiyawa duk da yarfatashin da take yi a kulum. Data fita da ga gida zuwa makaranta yana biye da ita. Hakama idan ta dawo sai ya rakota har gida ta hanyar bibiyarta. Zuwa yanzun tun lamarin nasa na bata mamaki har ya koma takaici da al-ajab. Har tabbayar kanta take shin baida aikinyi ne ko mi?. Wannan takaicin nasane ya sata yau ana saukesu a napep taje tai masa knocking glass. Yana saukewa ta balbalesa da masifa batare data yarda sun haɗa ido ba dan karma yay mata kwarjini. Sai dai abin ALLAH wadai da takaici, harta gama masifar tata ma bai nuna yaji haushi ba. Sai ma murmushin da ya nema rikita mata lissafi ya sakar mata yana wani narkewa a cikin kujera.
Wani uban kara ta ƙwalla tana isa inda Ummi ke kwance wanwar tana wani irin tari dake fita da ƙyar. Kiran sunanta ta shigayi tana girgizata hankali tashe. Sai dai ina Ummi ta fita hayyacinta. Dabarar rarumar wayar Ummin ce tazo mata a rai. Batare data nutsu wajen ganin wanda ta kira ba kawai tai dailing numbern farko, dan tasan su ne dai kawai suke yawan kiran no din Ummin tasu a koda yaushe.
“Yaya dan ALLAH kazo gida, Ummi...Umminmu. Na shiga ukuna. Ummi dan ALLAH ki tashi. Wlhy kika mutu nima mutuwa zanyi. Dan ALLAH Ummi na roƙeki karki mutu. wlhy bazamu sake yin fushi da ke ba. Mun tuba Ummi, mun daina. Mun yarda zamu auresu Ummi.......”
Sambatu taketa faman yi tama manta da waya a kunnenta. Kukanta ya fiddo Abba da ga ɗakin Ummi ɗin wando a hannu. dan harya cire kaya ya baje a gado yana jiran jakarsa ta shigo ya murza a wulaƙance. Ido huɗu sukai da Hibbah da ke sake ƙwala kuka tana kiran Ummi da girgizata. Ai sai ta sake fasa wata ƙarar ganin a yanda ya fito, saboda bai saka wandon dai-dai ba an samu mishkila wajen bayyanar jikinsa.
Sakin Ummi tai ta fita a guje da ga sashen baki ɗaya jikinta na rawa. Tana da yayu maza manya. Amma tunda take da su ko zama da singlet da boxers basu taɓa yi a gabanta ba balle a yanayin da Abban ya fito wanda bata taɓa ganin wani mahaluki a yanayin ba.
Jikinsa ta faɗa dai-dai maigadi ya buɗe masa gate ya shigo, dan Hibbah wayarsa ta kira saboda shine na ƙarahe da ya kira Ummi yaji yaya jikinta? Dan ya kwana biyu baizo gidan ba. Duk yanda yaso ganin ya janyeta a jikin nasa hakan ya gagara, sai sake ruƙunƙumesa takeyi jikinta na rawa, yayinda taketa faman son ɓoye fuskarta a ƙirjinsa duk da tsahon nata gaba ɗaya iya ƙirjin nasa ta tsaya.
Cikin zafi-zafi ya shiga tureta yana girgizata. “K Muhibbat nutsu, muje inga Ummin gani nazo”.
Jin muryar da bata yayunta ba ya sata saurin ja da baya tabar jikinsa. Isma'il da ya samu ta rabu da jikin nasa da sassarfa yay gaba abinsa zuwa sashensu har yana haɗawa da ɗan gudu-gudu. kusan cin karo sukai da Abbah da ya koma ya ɗakko kayansa saboda ihun da Hibbah tayi ya farga da halin da yake a ciki. Duk da ya kuma ga Ummi a yashe a ƙasa sai kawai firgici biyu ya kamashi. Na farko kar wani yazo ya gansa a yanda yake sakamakon ihun Hibbah a zata wani abu yaso mata har Ummi ta shiga halin da take ciki a yanzu. Dan haka ya fito dan ya gudu salin alin, idan Hibbah ta sako sunansa a ciki kuwa yasan ta yanda zai kare kansa ai.
Haka kawai zuciyar Isma'il ta raya masa irin abinda Abban ke gudu. Dan haka yasa ƙafa ya taɗesa sai gashi a ƙasa tim. Takan kafafun Abba yabi da shaggun takalman ƙafarsa, ji kake ƙasss ƙashi na bada sautin karyewa ko tsagewa. Wata iriyar wahalalliyar ƙara Abba ya saki tare da ɗaukewar numfashi na wucin gadi. Ko waiwayensa Isma'il baiyiba ya ida afkawa cikin falon inda ya hango Ummi a ƙasa itama babu alamar rai tattare da ita.
“Ummi!... Ummi! Ummi!!” ya shiga ƙwala mata kira da kama hannunta yana girgizawa. Sai dai babu alamar motsi tare da ita sam. Mikewa yay da sauri ya ciro wayarsa yay kiran Yaya Umar da yasan shine mafi kusanci da gida. Sai dai bai ɗaga ba. Tunawa ana sallar la'asar yanzu haka ya sakashi cije lip ɗinsa na ƙasa ya cusa wayar a aljihu. Batare da tunanin komai ba ya ciccibi Ummi gaba ɗayanta yay waje. Sai lokacin Hibbah ta nufo falon sabida hango abinda Isma'il ɗin yay ma Abba.
“Muje asibiti” yace mata kawai yana nufar hanyar gate. Babu musu ta bisa tana kuka da riƙe hannun Ummi ɗin da ya ɗakko. Sai lokacin kuma Hajiya mama ke fitowa da ga sashensu itama. Ta bisu da wani irin kallo mai ma'anoni da yawa saboda ganin baƙon fuska ɗauke da Ummi ɗin. Dan duk zuwan da Isma'il ɗin keyi gidan ba taɓa haɗuwa sukai ba. Wahalallen ihun da Abba ya saki ne ya fargar da ita halin da yake a ciki, babu shiri ta runtuma a guje kansa tana ƙwala kiran sunansa.......
★★★★_____★_____★★★
Tun kan su ƙarasa asibitin Isma'il yay ƙoƙarin kiran doctor Bilal. Cikin sa'a kuwa ya ɗaga dan mutuminsa ne. Bayani yay masa cewar gasu a hanya tare da mara lafiya su zam cikin shiri. Dr bilal yace babu damuwa sai sunzo.
Cikin mintuna kalilan kuwa suka iso asibitin saboda uban gudu da yake zugawa a hanya. Kamar yanda yay fata sun sami su Dr Bilal na dakon isowarsu. Babu ɓata lokaci aka shiga da Ummi ciki.
Kuka sosai Hibbah keyi da son binsu, badan yaso ba ya riƙo hannunta yana ƙoƙarin dakatar da ita. Sai dai taƙi ta nutsu, dole yay mata yanda yasan zata nutsun, ya jawota jikinsa ya rungume. Da ƙarfi ya rumtse idanunsa zuciyarsa na wani irin bahagon gudu.
Itako Hibbah tuni ta ƙara lafewa tana wani irin kuka mai ban tausayi, dan gaba ɗaya ma ta mance a jikin wa take. Sai da ƴar nutsuwa ta fara zo mata ne sakamakon kiran wayarsa da akayi tai azamar janye jikinta. Komai baiceba shima. Sai ƙoƙarin ciro wayarsa da yay a aljihun wandonsa. Ita kuma ta koma kan kujera ta zauna tana cigaba da kukanta da add'ur ALLAH ya bama Umminsu lafiya.
Yaya Umar da yaga miss call ɗinsa bayan fitowarsu massallaci ne ya kirasa. Dan haka yay masa bayanin da bazai ruɗar da shi ba. Koda ya yanke kiran sai ya shiga kiran sauran suma.
★★
Cikin mintuna kalilan yaran Ummi suka gama hallara a asibitin. Gaba ɗaya hankalinsu a tashe yake. Sai dai sunata ƙoƙarin lallashin Hibbah da ke kuka sosai har yanzu. Harda su amai. Ga zazzaɓi mai zafi ya gama lulluɓeta matuƙa.
Fitowar Dr bilal ya sasu maida hankalinau garesa. Cikin son kawar da damuwarsu yace, “Ku kwantar da hankalinku babu wata matsala mai yawa insha ALLAH. Dan yayi ƙoƙarin kawota asibiti akan lokaci. Sai dai ku kiyaye dan ALLAH kar yazam muna tufƙa ana warwarewa.”
A take nutsuwa ta saukar musu. suka shiga jerama Isma'il godiya tamkar zasu ɗaukesa su goya. Shi dai ransa a dagule yake da takaicin Abbansu, dan shi baisan ba mahaifinsu bane.
Sun cigaba da dakon jiran farkawar Ummi da aka sakama ƙarin ruwa a asibitin har wajen sha biyu na dare da aka basu sallama saboda Alhmdllhi komai normal, amma sai Dr Bilal yace su barta anan ta ƙara hutawa har sai gobe idan ALLAH ya kaimu da yamma. Duk sun gamsu da bayanin nasa. Dan haka sukai masa godiya da fitowa dan su tafi gida Hibbah da zata kwana da ita tare da Nurse tayo musu rakkiya.
Har sannan Isma'il na tare da su. Karan farko a tarihi da Hibbah ta dubesa cike da girmamawa da idanunta kumburarru. “Yaya Isma'il mun gode sosai. ALLAH ya bada ladan zuminci. Yanda ka jikan Ummin mu, kaima ALLAH ya baka ƴaƴa da zasu jiƙanka. Ya ƙarama Abbanka lafiya da tsahon rai mai amfani, ya jiƙan Umma”.
Ba karamin ratsa zuciyarsa addu'ar tata tayi ba. Ya kafeta da ido har sai da Yaya Umar ya zunguresa sannan ya sauke ajiyar numfashi da sakin murmushi. “Nagode sosai auta. ALLAH ya karama Ummi lafiya ya albarkaci rayuwarki. ALLAH ya baki miji na gari”.
Cikin jin daɗi yayunta suka amsa masa da amin. Itama tattausan murmushi da bata taɓa masaba a yanzu ta saki tana juya baya alamar taji kunya da addu'arsa ta ƙarshe. Su Yaya Usman suka ƙyalƙyale da dariya Ammar na tsokanarta. Bata kulashi ba dan yau batajin yin faɗa Ummi bata da lafiya.
Tun a asibitin suka rabu da Isma'il. Shi yay gida suma suka wuce gida. Inda tunkan su shiga sukaji labari a bakin maigadi cewar Abba ma na asibiti. Ya fadi ne a bakin ƙofa da alama yaji ciwo a kafafunsa. Hakama goshinsa da bakinsa sun fashe yanata zubar da jini ma.
Kasancewar da ga Hibbah har Isma'il basuyi musu bayani ba sai basu kawo komai a ransu ba suka ɗauka tsautsyine kawai. Addau'ar samun lafiya sukai masa suka shige. Dan ba'ai musu tarbiyyar son ganin lalacewar wani ba koda ace maƙiyinsu ne.
*________________________________*
A ɓangaren Abba kam da ƙyar aka iya ɗagasa da ga inda Isma'il ya taɗesa. Bakinsa duk ya fashe da goshinsa daya daushi kwalliyar tsitstsigen baranda. Hakama kafafunsa da alamar yayi karaya ko targaɗe. Dan ko takasu baya iyayi ma. Hasalima a sume aka ɗaukesa da ga gidan zuwa asibiti saboda jinin da yayta kwararwa kafin Junaid yazo da mota su fita da shi zuwa asibiti.
Su hajiya mama babu wanda yasan ainahin abinda ya faru da Abban suma. sai dai kansu ya ɗaure matuƙa ganin da ga shi sai boxer kayan da ya fito da su a hannu sabida ihun Hibbah yashe a gefe. Sunma rasa yaya zasu fasalta al'amarin musamman da likita ya tabbatar musu kafarsa ɗaya ta samu karaya da hannunsa. Ɗayar kuma tsagewar ƙashi ce ga ciwon goshinsa dana bakinsa da yay wanu zundun-dun uwa an saki shantu.
Hajiya mama ta hana ai masa gyaran karayar wai sunada mai gyaran gargajiya zaizo da ga kauye. Sai a jirasa yana hanyar tahowa. Tun yamma ake jiran mai gyara har dare ya tsala bai iso ba. Haushin abinda Hajiya mama tai musu su kuma likitocin sunce bazasu taɓa ƙafar ba har sai wanda tace ɗin yazo ya gyara masan. Duk roƙon da Momy taita musu sunce bazasuyiba wlhy.
*_WASHE GARI_*
Da safe acikin su Yaya Abubakar babu wanda yabi takan zancen duba wani Abba. Da dai su Ammar suka kammala yin breakfast suka gyara gida sai suka runguɗa asibiti wajen mahaifiyarsu. Sun isketa zaune Hibbah na shafa mata mai saboda wanka da tayo.
Ta dubesu cike da tausayi da begen ƙishirwar murmushinsu. Duk wanda ya gaidata sai ta kamo hannunsa ta shafa kansa tana ƙoƙarin haɗiye hawayenta.
“Ku daina fushi da Umminku kunji”.
Ta faɗa cikin damuwa da ƙunar da takeji a cikin zuciyarta. Komai basu iya cewa ba sai dai dukansu sunyi ƙasa da kawuna ransu fal tausayinta. Musamman Yaya Muhammad da yasan wani yanki na labarinta batare da itama ta sani ba, shima Abbansu ne ya sanar masa kafin ya rasu. Ya kuma tabbatar masa ya faɗa masane saboda wataran yasan kunnensa zaiji gorin da za'aima mahaifiyarsa kar zuciyarsa ta ɗauki wani abun daban. Shine ya fara jan numfashi da ƙyar da dubanta yana ƙoƙari haɗiye hawayen da suka ciko masa ido.
“Ummi baki mana laifin komai ba. Amma dan ALLAH a wanan gaɓar munason jin wani abu game da ke. badan bamu yarda dake bane. Sai don son sanin minene dalilin da yasa duk basa ƙaunarki?. Mi kikayi musu haka da zafi? Miyasa kika yarda kika auresa bayan shiɗin kanin Abbanmu ne? Mai fuska biyu ga mutane”.
Murmushi ta saki mai kuna da kai hannu ta shafo kan Yaya Muhammad. “Muhammadu Aminullahi zan faɗa muku insha ALLAH. Da zaran munje gida yau zakuji komai”.
A take fuskokinsu suka nuna jin daɗin zancenta. Dan danan suka ɓalle mata hira kamar yanda suka saba a baya. Itako sai murmushi take zuciyarya na kara sanyaya da ɗunbin sonsu da kaunarsu.
Dr bilal ne ya shigo, bayan sun gaisa yace suje waje zasu ɗan ƙara duba Ummin suga ya ya komai na tafiya normal. Sun masa godiya tare da fitowa su duka. Duk anan ƙofar ɗakin suke zaune Hibbah nacin abincin da sukazo da shi. Kamar ance ta ɗaga kai sai idanunta karaf akan Zahidah da Hafsat, Muhammad Shuraim biye da su.
Babu shiri ta miƙe zaram tana rarraba idanuwa. Tunkan su ƙaraso tace, “Lallai ma! Miya kawoka nan?”.
Furucin natane yaja hankalin yayun nata gaba ɗaya. A tare suka sauke idanunsu bisa kan Muhammad Shuraim da ke sanye cikin ado da kamshi na shadda da keta maiƙo, ga hular zanna da ya murza wadda ta kara masa cikar kamala da kwar jini.
A fusace Hibba ta sake buɗe baki zatai magana Yaya Umar ya harareta. Dole tai shiru tana wani mar-mar da idanu akaikaice tana ballama Shuraim harara.
Shiko murmushi ya saki yana matuƙar jin mamakin tsaurin ido irin na Hibbah. Ya cigaba da takowa a hankali zuwa gaban su Yaya Muhammad da duk hankalinsu a kansa yake suna kallonsa cike da nazari. Duk da zasu iya yin sa'anni da Yaya Umar cikin girmamawa ya shiga gaishesu su duka. Gashi yaki yarda ya haɗa idanu da su shi a dole yana gaban surukai.
Hakan ba karamin dariya da burgesu yay ba. Ammar sai wani ƙara buɗe ƙwanji ake su a dole yayu. Yaya Muhammad ya ce, “To sai dai bamu gane baƙon namu ba?”.
Murmushi Shuraim yay cike da ladabi yana ɗan shafar ƙeya yace, “Yayanmu bazaka sanni ba. Dama ina jiran lokaci ne nazo gareku. Sai dai jin Momy babu lafiya yasa nazo dubata kafin hakan. Sunana Muhammad Shuraim Aliyu. Mai fata da addu'ar samun nutsatstsiyar yarinya mai tarbiyya kamar Muhibbat....”
Wata malalaciyar harara Hibba ta zuba masa tamkar zata fashe dan takaici da haushinsa. Yayinda Ammar dake guntse dariya a kaikaice yace, “Dama dai a tarbiyyar ka tsaya dana yadda. Amma ba Nutsuw.....”
Gwiwar hannu Yaya Umar dake gefensa yasa ya bugesa. Yay azamar rumtse ido da ɗaura hannunsa a wajen yana faɗin, “Wayyo Ya Umar zaka kashe ni”.
Yaya Abubakar kam murmushi ya sakarma Shuraim shi da Yaya Muhammad. Haka kawai su dai Shuraim ɗin ya birgesu matuƙa. Dan haka Yaya Abubakar yace, “Masha ALLAH mun gode matuƙa. Bara doctor ta fito sai mu shiga ka dubata”.
Sosai daɗi ya kama Shuraim, ya shiga jera musu godiya da addu'ar samun lafiya ga Ummi. Su ma su Zahidah suka shiga gaishesu da tambayar jikin Ummi ɗin. Hibbah kam taƙi kulasu suma wai haushinsu takeji sun faɗama Shuraim sirrinta.
Suma basu kulata ba dan sun gane manufarta sarai. Haka ta ringa antaya musu harara suna ramawa har Doctor ya fito suka shiga su duka.
Tunda suka shigo Ummi take kallon Shuraim da ya durƙusa har ƙasa ya gaisheta da tambayar jikinta. Fahimtar ƙarin bayani take buƙata yasa Ammar fara rattafo zance. Sosai murmushin fuskar Ummi ya sake faɗaɗa. Dan har cikin ranta taji ƙaunar Shuraim da samun nutsuwa da shi. Tana kuma fata da addu'ar ya zame musu mafita akan haɗa Junaid aure da Hibbah da ake ƙoƙarin ƙullawa.
Basu wani jima sosai ba yace zai wuce, bayan ya ajiyema Ummi ledan dubiya. Godiya suka sake masa Ammar ya tafi rakasa. Yana ƙoƙarin ficewa Isma'il ke ƙoƙarin shigowa. Baya ya koma ya bashi hanya. Batare da tunanin komai ba Ammar ya gabatar da Shuraim ga Isma'il ɗin. Shima Shuraim Ammar ya gabatar masa da Isma'il matsayin ɗan uwansu. Hakan ya basu damar yima juna kallon ido ciikin ido. Da alama kallon da Isma'il yayma Shuraim ɗin na tsantsar kishi ne da shima kansa baisan yayi ba. Haka shima Shuraim kallon alamar tambaya da tsoron sakkiyar da babu ruwa yayma Isma'il ɗin kai tsaye. Cike da basarwa kuma sai suka saki hannun juna kowa na ƙoƙarin haɗiye abinda ke ransa da cikin idanunsa, kafin su kalli Hibbah a tare Shuraim ya ida ficewa, Isma'il ya karasa shigowa............✍
*_Tofa mazaje ya take ne?😂😂💃🏻, kodai Hibbahr mu ta mutunci ta haɗa karo ne😹😹😝. To muje zuwa muga wane mai rabon zai ɗauka a ciki, dan har yanzu itaɗin allura ce a cikin ruwa mai rabo ka ɗauka. zamuga yaya TAKUN SAƘAAR zai kasance a filin dagar dan ga Junaidu ma bin Halilu a gehe yana jiran waman dakala bati siddan. Ga kuma oga master da tabbas sai ya binciko hibban tunda ya ɗau alwashin hakan🐒😉😂._*
_Please kuyi manage da ga nan har Monday na ƙara samun sauƙi😭🙏🏻_
*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________
*_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻
_GYARAN MA NA KAMFANIN TURAREN:_
*YERWA INCENSE AND MORE*
*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*
_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawatattu kuma nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki. hadin bornu/chadian na kamfanin turaren YERWA INCENSE AND MORE_
*_Muna da haɗin_*
_Turaren wuta kala kala na gidah_
_khumrahs_
_Kullaccham_
_Turaren wanka_
_Turaren Kaya_
_Turaren wanki_
_turaren mopping_
_Dukkanil al’ajab (Turaren tsugunno na Matan aure kad’ai)_
_khumratul al’ajab (khumrah ta jiki ta matan aure_
_Muna Gyaran jiki_
_Na amare_
_Da masu jego_
_Da sabulai masu gyara fata_
_Turaren tsugunno_
_zumar goran tula_
_Scented hair cream and spray (man kamshin gashi da gyara gashi_
_Akwaisu kujeran tsugunno
_Dilke and halwa set_
_Burners da igniters da tong_
_turaren fesawa dana ruwa._
_wardrobe balls_
_scented pebbles_
_cotton wooly oudi incense_
_kabbasas_
_Da sauran kayayyaki da yawa da bamu ambata ba_
_Akwai ragi na musanman ga yan zafafa fans❤️_
_Muna bada sari, Ko sayi ‘dai ‘dai akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_*
_EMAIL:[email protected] ko INSTAGRAM PAGE d’inmu:yerwaincense_and_more dama nambR mu:08095215215_
_MUNA TURAWA KAYAN MU KO’INA A FADIN NIJERIYA DAMA KASASHEN KETARE.
100% TESTED AND TRUSTED_
••••••••••••••••••••••••••••••••
*_Chapter Fifteen_*
.........Kamar yanda doctor Bilal ya faɗa a ranar suka sallami Ummi tare da sharuɗan da za'a kiyaye game da lafiyarta. Su Yaya Abubakar sun amsa masa tare da tabbatarwa. Wannan ɗin ma akasi aka samu kawai. Da ga haka sukai masa godiya suka tafi da sanyin idaniyarsu gida.
Koda suka isa gidan babu wanda yayma Ummi zancen Abbah, hasalima su sun manta ma. Hidimarsu suka cigaba da yi hankali kwance har dare. Sai da zasu kwanta ne Ummi taji shirun gidan yayi yawa take tambayar Hibbah data maƙale a ɗakinta zata kwana. Bargo Hibbah taja har saman kanta tana sake bajewa a gadon na Ummi. “Ummi nima ban saniba. Ƙila sunje ƙauye ne”.
Shiru Ummi tai tana nazari, tasan Momy ko kowa zaije ƙauye ita dai bazataje ba. Hakama ƴammatan ƴaƴanta. Hajiya Mama da Abban ne kawai suke zuwa, suma idan aikin sharrinsu ya tsikaresu, kuma Abba ma ai bai jima da dawowa ba. Ajiyar zuciya ta sauke da kauda zancen a ranta itama ta kwanta tare da kai hannu ta janye bargon da Hibbah tasa har saman kai.
Duk yanda Ummi taso yin barci gagararta yayi, sai ma dulmiyawa da tai a ƙololuwar duniyar tunani da neman mafita. Taja tsahon lokaci tana ƙullawa da kwancewa kafin ta sami mafitar da take addu'a da fatan ta zame musu alkairi ita da zuri'arta.
Da asuba bayan sun idar da salla Ummi ta dakatar da Hibbah da ga barcin da take ƙoƙarin komawa gado tayi. Cike da shagwaɓa ta lafe a jikin Ummin tana faɗin, “Wayyo Ummi ALLAH barci nakeji, kinga yau weekend ne babu makaranta sai islamiyya, su Yaya bazasuje aiki ba na san suma barcin zasuyi”.
Murmushi kawai Ummin tayi, zuciyarta najin tausayin autar ta bisa hukuncin data yanke akan lamarin duk ƴaƴanta a daren jiya. “Muhibbat!”.
Ta kirayi sunan Hibbah dake lumshe idanu babu wasa. Idanu Hibbah ta buɗe tana kallon Ummin, dan yanda ta kirata da cikakken sunanta babu wasa tasan ƙwarai magana ce mai muhimmanci.
“Na'am Ummi”.
“Tambayarki zanyi?”.
“To Ummi, ALLAH yasa na sani”.
Numfashi Ummi taja da kafe Hibbah da ido. “Duka yayunki babu mai neman aure ne dama?”.
Ɗan jimm Hibbah tai alamar nazari. Kafin tace, “Ummi wai kina nufin sunada ƴammata?”.
Kai Ummi ta jinjina mata kawai.
Hibbah ta ƙyalƙyale da dariya tana kwantawa ta ɗaura kanta a cinyar Ummi. “Uhm ai Ummi fa dama tun kwanaki nakeson na baki labari Yaya Umar ya gargaɗeni. Wai so suke suyi miki surprise ne. Kinga Yaya Muhammad yana da budurwa, Maimunatu (Kausar) ɗin gidan Sheikh Aliyu Abdul-Ra'uff Maina abokin Daddyn mu, mai islamiyyarmu kuma ɗiyar kawarki.......”
Wani irin farin ciki da sanyi ne ya lulluɓe zuciyar Ummi lokaci guda. Ta katse Hibba cike da zumuɗi. “Da gaske Tanee?”.
“Wlhy kuwa Ummi. Kin dai santa babu ruwanta ga hankali, kina zuwa gidansu, suna zuwa nan gidan kinsan tarbiyyarsu. Gata malama a Islamiyyar tamu. Akwai wani dabino da zam-zam da zuma da Yaya Muhammad ya kawo miki kwanaki na rantse itace ta bada a baki. Amma yace idan na faɗa sai ya fasan baki.”
Yanda Hibbah ta ƙare maganarne ya saka Ummi ƙyalƙyalewa da dariya. “Kai Mamana har yanzu dai ke sakara ce ALLAH, basai ki gayamin a sirri ba. Sam baki biyo mai sunanki ba. To Abubakar fa?”.
Cikin dariyar zancen Ummi Hibbah tace, “Tab na Zahidah kenan.”
“Wannan Zahidah ta gidan Auntyn ku Kulu dai dana sani?”.
“Eh wlhy Ummi. Amma yace karsu faɗama kowa sai ta gama makaranta. Nima basusan na ganeba a ɓoye sukeyi”.
Nanma dariyar farin ciki ce ta bayyana akan fuskar Ummi. Har ranta zaɓin Yaya Abubakar da na Yaya Muhammad sun mata hundred percent. Hibbah ta cigaba da faɗin, “Shi kuma Yaya Umar Nafisa ce nasan kin sani dama. Yaya Usman kuma Hafsat itama kin sani. Zakin ki kuma babu kasuwa har yanzun”.
Sosai Ummi taji matuƙar daɗi, dukkan damuwarta sai ta gushe a lokaci guda. Taji ƙwarin gwiwa bisa ga abinda take shiryawa. Dukkan fargabarta ta gushe. A ɓangaren muhalli bata da matsala da yaranta, duk gine-ginensu sai dai ƙarashe. Dan suna fara aiki suka haɗa hannu wajen fara ginin filin da taketa tattali da kaffa-kaffa domin su. Burinta ita da mahaifinsu yanda suka tashi kansu a haɗe su cigaba da rayuwa a waje guda. Shiyyasa koda ya sai filin sai ya damƙashi hannun amininsa kuma malaminsa har sai da suka fara aiki ya basu. Shiyyasa har yanzu Abba da Hajiya Mama basusan da zancen ginin ba........
“Ummi inje in kwanta?”.
Hibbah ta katse mata tunani. Shafa kanta Ummi tai tana murmushi. “A'a ban gama da ke ba. Dan banji ita autata tana da saurayi ba ko a'a?”.
Da sauri Hibbah ta ɓoye kanta tana dariya. “Kai Ummi ni banda wani saurayi. Nifa bazanyi aure ba muna tare mutu karaba”.
“Tab, to auta an taɓa haka kuwa. Muma ai munason zaman gidanmu aka ɗakkomu aka kawo mu naku gidan muka haifeku.” Ummi ta faɗa tana dariya.
“Ni dai bazanyiba ALLAH Ummi. Banason nesa da ke da su Yaya. Indai zanyi aure sai dai mutafi tare ko mijin yazo ya zauna a gidanmu to”.
Dariya sosai Ummi keyi, irin wadda ta jima batayi ba a rayuwarta. Tanee ɗinta kayan shirme da wauta kenan. Da ana haka da ƴaƴa da yawa na tare da iyayensu ai.
Tashi Hibbah tai da gudu ta haye gadon Ummi ta kudundune a bargo ita a dole kunya ta kama ta. Ummi da ke dariya tace, “To shikenan ai ke baki da matsala tunda Junaid ɗan gidan nan ne sai kiyi zamanki tare dam......”
“ALLAH Ummi bana sonsa. Da na auri mugun nan gara na mutu”. Hibbah tai saurin yaye bargon idanunta na cikowa da hawaye. Yayinda fuskarta ke nuna tsananin tsoro da tsanar Junaid ɗin da Ummi ta ambata.
“To shikenan naji. Amma ai kina son Isma'il ko?”.
Idanu Hibbah ta zaro waje a firgice. “Wane Isma'il ɗin Ummi?”.
“Mai zuwa nan gidan mana”.
“Ni dai wlhy a'a Ummi. Shi yayana ne dan ALLAH kibar faɗa.”
“Oh ALLAH, ke kuwa Tanee wa kike so a rayuwarki? To ko wanda yazo dubani a asibiti jiya? Muhammad Shuraim ko?”.
Baki Hibbah ta turo amma batace komai ba. Ummi ta cigaba da faɗin, “Tanee kinga shima alamunsa sun nuna mutumin kirki ne nutsatstse. Ina ƙyautata masa zaton alkairi insha ALLAH. Amma zansa ai bincike a kansa inhar kina son nasa”.
Kwanciya Hibbah tai ta juyama Ummi baya. “Ni Ummi ALLAH ya cika iyayi. Gashi baida fara'a. ga shishshigi ”.
“Duk shi kaɗai?. To lallai tunda kika iya gano waɗan nan kina sonsa kenan, zaki kuma auresa”.
Da sauri Hibbah taja bargo da cewa, “Nifa Ummi a'a baiminba. Sai naje China na dawo zanyi aure”.
“Tanee wannan mafarkinki ne. Amma ban fidda miki ran zaki cikashi ba idan kinyi aure mijinki ya kaiki da kansa”.
Shiru Hibbah tayi dan an taɓo mata inda kuma bata son. Itama Ummi sai bata sake tankawa ba ta cigaba da hidimarta da lissafin ƙullawa da kwancewa.
Zuwa takwas Ammar ya shigo ya tada Hibbah dansu haɗa breakfast su wuce islamiyya duk da sunyi latti. Hibbah kamar zatai kuka ta bisa. koda sukaje kitchen ɗin suna aikin suna faɗa har sai da Yaya Abubakar ya shigo ya tsawatar musu saboda kuka da Ammar ya saka Hibbah.
Suna kammalawa sukai shirin islamiyya. karyawar ma a tsaitsaye sukayita suka fice.
★★★
A yinin ranar su Yaya Muhammad duk a gida sukayisa. Suna tare da Umminsu suna shan hira. Basu sake mata maganar tarinta ba, itama batai musu ba. Sai bayan sallar zuhur suma suka wuce islamiyya. Ganin dai har zuwa yamma babu motsin Abbah da su Hajiya Mama yasa Ummi fita wajen maigadi ta tambayesa ko sunyi tafiya ne.
Baiyi mamaki ba. Dan yasan kaf yaranta a fusace suke da Abban. Bayanin faɗuwar Abban ya bata da kaisa asibiti da akai. Kuma har yau babu wanda ya shigo gidan tun jiyan. Duk da abinda suke mata bataji tayi farin ciki da tsautsayin daya afkawa Abban ba. Sai ma komawa tai falonta ta faɗa duniyar tunani........
_________________________________
A ɓangaren Abba ba ƙaramar jigata yay ba kafin safiya. Ƙafafu sun kumbura suntum. hakama fuskarsa tamkar ƙwaɓun fulawar sabon burodi. Sauƙinsa ma allurar barci da likitocin sukai masa ganin yanda yake rusar kuka ƙafarsa na masa zogi.
Sai kusan huɗu na maraice mai gyaran yazo, a cewarsa sun sami lalacewar motane a hanya. Sai dai kuma a zahirin gaskiya ƙaryama yake bai taho ba sai da safen. Komai likitocin basu ce ba. Sai ma damar yaje yay aikinsa da suka bashi, dan haka suka basu sallama.
Ummi na tsaka da tunaninta taji shigowar motoci, mikewa tai ta leƙa ta windown falonta sai ta hango ana fita da Abbah da ga motar Junaid tamkar gawa. Wani irin faɗuwa gabanta yay. Babu shiri ta fito zuwa tsakar gidan itama. Kusan tare suka shiga sashen Momy da su Hajiya mama da ke biye da mai-gyara da Junaid da suka ɗakko Abba ranga-ranga.
A tsakkiyar falon momy aka shimfiɗe Abba. Sai dai ganin yana numfashi yasa Ummi batace komaiba tabi layin ƴan kallo. Mai-gyara ya fito da kayan aikinsa. sanin abinda zaije ya dawo ya sashi faɗama Junaid cewar ya samo wanda zasu tayasa riƙe Abba dan shi kaɗai bazai iyaba. Badan Junaid yaso ba ya mike ya fita. Babu jimawa sai gashi tare da mai-gadinsu da na maƙwafta. Sai wasu yaran makwaftansu su biyu sa'annin Ammar.
“Yauwa kayi farar dabara da kukazo da yawan”. Cewar mai gyara yana gyara zamansa sosai a gaban kafafun Abba da sukai suntum har ƙyalli sukeyi.
Junaid da mutanen daya gayyato baki ɗaya suka zagaye Abba mai-gyara ya fara aikinsa. Sai dai abin mamaki duk da barcin da Abba keyi ana taɓa ƙafar yay wata iriyar mahaukaciyar zabura da ballara ihu. “Wayyyyyyyoooooo!!!!!! ALLAH na zasu kasheni na shiga uku ni Halilu!!!”.
Babu wanda ihun Abba bai gigita ba a falon. amma ahaka mai-gyara ya cigaba da aikinsa ko tausayi babu. Ihu Abbah yake da iya ƙarfin iko. Tun yana zufa har takai ga sakin fitsari. Can fa abin mamaki da kunya sai ga kashi.
Hanci su Ameerah suka shiga toshewa. Su kansu masu riƙon nashi ji suke kamar su sakesa su gudu dan azabar warin kashin. Suma kuwa yayi ya farfaɗo yafi sau uku. Tun yana ihu da murya mai kauri har ya koma siririya. Daga baya ma akabar jinta gaba ɗaya.
Duk yanda Ummi taso daurewa sai da taji hawaye sun ciko mata idanu. Tai ƙasa da kanta saboda tausayi.
A cikin wannan halin su Hibbah suka fara dawowa gidan. Ihun Abba ne ya ringa jan hankalinsu suka dinga nufo sashen duk da sun manta shekarar karshe da suka shiga sashen. Su kansu tsoro ya kamasu ganin yanda Abban ya koma. Badan sun so ba dole suka dinga toshe hancuna suma saboda wari.
Mai gyara ya ɗora kafa da hannun Abba. Sauran raunikan ma aka gyara. Ya shafa magani ya bada wanda za'a cigaba da masa amfani da shi. Kafin a cake masa ƴan kuɗaɗensa masu nauyi. Aka kuma kaisa masauki dan yace sai da safe zai wuce yamma tayi.
Sai lokacin Hajiya Mama ta farga da su Ummi da yaranta. Ido ɗaya ta kanne ta shiga zazzaga bala'i wai sunzo ganin ƙwaƙwaf. Cikin subutar baki Hibbah taja wani wawan tsaki da faɗin, “Kaɗan ma ya gani. Ummin mu yaso gani a wanann kwatankwacin bala'in sai shi ALLAH ya tsundumasa. In takamarsa zalunci wataran ƙafar za'a guntule.....”
Wata muguwar cafka Hajiya mama ta kaima Hibbah ta ko kwasa a guje tabar sashen. Zata bita Junaid ya riƙota cikin masifa. “Barta kakus. Nine nan zanci uban uwarta, wancan bakin nata mai kama da na reza yau sai na ɓaɓɓarkasa wlhy. Shegiyar yarinya mai bakin akku. Idanma an sakata tazo ta faɗa ne to ina dai-dai da kowane shege a gidan nan. Wama ya sani ko kada mana shi akaiyi. Kai bama zan yardaba ALLAH sai munje kotu”.
Tsaki Ammar yaja tare da kama hannun Ummi suka fice. Su Yaya Muhammad ma kai kawai suka girgiza sukai gaba abinsu da barin su Hajiya mama da takaici. Dan so sukai su tanka su kwashe komai sukai wajen ƴan sanda. Daga nan a wuce kotu har ALLAH yasa sukai gaɓar da suke fata. To sai akai rashin sa'a yaran Ummi masu lurane suka manna musu hauka.
Koda suka koma sashensu basuga Hibbah ba. Sun san ta boye kanta a daki ne saboda tasan tayo laifi, tunda suma suna hanata rashin kunyar. Alwala ma duk sukayi suka fice masallaci. Ummi ma ta nufi ɗakinta gabatar da tata duk da tana jiyo hayaniyar su hajiya mama daketa zage-zage har yanzun.
Koda suka dawo bayan sallar isha'i Hibbah bata yarda ta fitoba har suka ci abinci sukai hira kowa ya tafi makwanci. Babu kuma wanda ya nemeta dan a tabbatar mata batai dai-daiba.
Tun a daren maƙwafta ke shigowa duba Abba dan sunji ihun da yayta zugawa. Duk wanda ya shigo sai su hajiya mama suce yaran Ummi ne suka jima Abban ciwo. Da yawa ba yarda suke ba, saboda sunsan halin matsi da Ummi ke fuskanta a gidan da yaranta tun suna kanana. Dan tunkan ma Hajiya mama ta dawo gidan da zama idan tazo da ga ƙauye haka zataita zubda tujara wa Ummi kala-kala, tunda kuwa mijinta ya rasu ta dawo da zama baki ɗaya sai Ummi ta shiga uku ta lalace itada ƴaƴan ta, gashi nan har yanzu basu huta ba.
*_______________________________*
Shiru kakejin Master da yaransa tamkar basa ƙasar. Babu kalar takalar da jami'an tsaro basu masa ba a kafafen ƴaɗa labarai yay kunnen uwar shegu da kowa. Ko randa zancen kai matar gwamna koto ya fito da ga hukumar yaƙi da ta'annatin kayan gwamnati babu wanda yaji ko tarin master. Shi dama ba sanin taka mai-mai accaunt na duka handles nashi akai ba. Dan kullum cikin canja salo yake.
Sun cigaba da saka idon ganin kozai tanka amma shiru, dan haka suka cigaba da shirya masa tarkuna ta ƙarƙashin ƙasa dan sunsan tabbas zaije kotun.
★★
Yau da yamma Hibbah na makaranta ta fito class cike da gajiya da yunwa. Fatanta kawai ta samu motar komawa gida da wuri dan su Hafsat tuni sun wuce saboda ba department nasu ɗaya ba. Su kuma yau duk lecture ɗin safe sukayi. Ita kaɗaice tayi na yamma.
Ta samu da yawan ɗalibai dake ta tutsutsun shiga motar da duk tazo wucewa. Dan haka tai gaba saboda kanta dake ciwo. Cikin sa'a kuwa tana matsawa gaban sai ga wata taxi ta faka gabanta. Batare da tunanin komaiba ta afka ciki bayan ta sanarma direban inda zai kaita, shi kuma ya faɗa mata kuɗin. Ko ragi bata nema ba dan buƙatarta kawai taje gidan da wuri. Saboda tana tsoron abinda zaije ya dawo ne musamman akan dangin Abbansu dake cike da gidan nasu dubiyar Abba. Dan zuwa yau da yake cika kwana uku jikin nasa da sauƙi.
Ƴan can asalin kauyensu ne sukazo mota guda duba shi. Sai dai hakan ya bama Ummi mamaki da su kansu, dan sam da ga Abba har hajiya mama bason mu'amula da ƴan ƙauyen sukeba yanzun. Shiyyasa har ƙasan ranta takejin akwai wata a ƙasa da suke ƙullawa.
Wasu hawayen tausayin Ummi da su kansu ya cika mata ido. bayan hannu tasa ta share tare da kwantar da kanta jikin sit ɗin ta lumshe idanu ko kanta zai sassauta sara mata.......
Ummi nacan na dakon jiran dawowar Hibbah itama, dan yau da kanta ta soyama Hibbar wainar filawa da tasan tana matuƙar so. Yayinda can ƙasan ranta ke cike da fargabar taruwar dangin mijin nata da nata a gidan. Dan tasan akwai abinda suke ƙullawar da gaske. Sai dai kuma ta saka a ranta komi zasu ƙulla insha ALLAHU ta gama shirya musu a wannan karon. dan itama tun a jiya data fita ta gama tsara komai akan makomar ƴaƴanta. Nasu kawai take jira yanzu ta ɗora da ga inda ta tsaya.
Ilai kuwa hasashen Ummi yayi dai-dai, dan tana tsaka da wannan tunanin akai kiranta sashen Abba ɗin. Hijjab ta saka har ƙasa ta tafi. Tun a falo Maomy ta sakar mata wani habaicin da ya tsaya mata a rai. Sai dai batace komai ba ta ƙarasa falon Abba.
Su kawu Bello ta samu da wasu a dangin Abban. Sai hajiya mama. Bayan ta gaishesu ta nema waje ta zauna duk da ba dukansu suka amsa ba.
A gadarance Kawu Ayuba ya fara bayani. “Hasiya basai mun sake ɓata lokacin tisa magana ba. Nasan kema tunda kika ganmu anan kinsan zancen. Kamar yanda su Yaya Ballo sukazo kwanaki akan maganar auren ƴaƴanki da yaran wajen Alhaji Halilu yanzu batun saka rana ne ya tashi. Saboda tsabar halacci da hangen nesa irin nasa yace kawai tunda munzo dubasa a saka. Shi baya wani bukatar ƴan kunji-kunji tunda batun tuwona maina akeyi. To a yanzu haka dai ga kayan saka rana nan ma duk ya saya dan yace shine uban anguna shine na amare, kuma koma bai faɗa ba dama shine, tunda tun suna kananunsu shiketa wahala akansu. Koda kuwa mahaifinsu na raye shine mai bada auren nasu ai dama. Basai na jaki da nisa ba. Yanzu haka dai an yanke ranar aure wata biyu kacal. Batun kayan aure na akwati da kukeyi anan binni duk yace zaiyi baya buƙatar komai da ga yaran nan. Ita kuma Muhibbatu tunda kun saka yarinya ta nuna bata bukatar wannan haɗin, da azo ta bijire bayan auren kota illata yaro kawai za'a fasa. Za'a bata shi wanda ta kawo ɗin ALLAH ya basu zaman lafiya.....”
A firgice Ummi ta dago ta dubi Abba. Wani shegen murmushi ya sakar mata tare da kashe mata ido ɗaya. Zatai magana yay saurin katseta cikin marairaicewa. “Hakan ai shine yafi kwanciyar hankali Kawu Ayuba. Kaga da alalata zuminci gara dai abi komai a sannu zaifi. Kuma ita mace ce. Banason a cuta mata akan abinda bataso. Dan yarinyace mai hankali da nutsuwa. Duk da damuwar da Junaid ɗin ya shiga nace ya haƙura kawai tunda tana da zaɓinta. Kuma zaɓin nata ma naga mutumin kirkine sunansa Muhammad Shuraim. Ɗan gidan Alhaji Aliyu ne mutumin kirki. Inajin kunyar ma nace bazan bashi jinina ba”.
Harga ALLAH Ummi ta shiga ruɗani, ta kuma ji ɗan sanyi ta wani fannin. Dan tana mamakin ta yaya shi Abban yasan da zancen zuwan Iyayen Muhammad Shuraim ɗin? Kodai su masu kawo kuɗinne sukai mistake ɗin zuwa nan kawo kuɗin maimakon gidan Sheikh Aliyu Abdul-ra'uff Maina? Lallai akwai abinda bata sani ba. Dan akwai manufa da dalilin yin hakan ga Abba, saboda halin makircinsa da ta sani. Hakanan salin alin bazai hana ɗansa ba ya bama wani.........
“Wannan shaiɗancin dai nasan ita ta kitsashi. Duka yarinyar nawa take da tasan wani bijirema zaɓin iyaye. Ni wlhy dan Halilun yace a barta ne da baza'a bari ba. Sai dai idan an aura mata Junaidun ta mutu”. Sababin Kawu Bello ya katse ma Ummi tunaninta.
Cikin makirci Abba ya amshe da faɗin, “A'a kawu bello ba'ayi hakaba ai. shima wnanan ɗin mutumin kirki ne wlhy. Dan yamafi Junaid nagarta. Muyi fatan ALLAH yasa haka shine yafi alkairi”.
A take duk ƴan falon suka shiga yabon Abbah da jinjinama ƙoƙarin sa, Ummi kam anata zaginta wai bata da godiyar ALLAH akan ƙoƙarin da Abban keyi tun bayan rasuwar mahaifin su Ammar. Tare da yi mata gugar zana na habaicin asalinta.
Ita dai uffan batace da su ba. Hasalima hankalinta ya rabune gida biyu. Duk sauran bayanan da suka cigaba dayi sai tama koma bata fahimtar komai. Jinsu kawai dai take da kunne da binsu da ido har aka tashi a taron ko nace suka sallameta.
Koda ta fito a sashen taso zuwa gidan malam sai dai gudun abinda zaije ya dawo da fitar tata yasa ta haƙura. Dan haka tai kiran numbar wayar matarsa da yake ƙawarta ce suna zuminci sosai duka biyun. Sai dai tasan uwargidan Maimunatu yanzu haka tana Oman da autan gidan dake karatu acan.
Bugu biyu Malama Jiddah ta ɗauka. Bayan sun gaisa da ɗan barkwancin ƙawaye Ummi take tambayarta ko Malam na nan kuwa?.
Malama Jiddah tace, “Eh yana nan, sai dai yana tare da kamar baƙin da naji kunyi magana ranar zasuzo yau ɗin. Lafiya dai ko?”.
“Tofa, kaji wani kuma ruɗanin. Umm Muhammad! Lafiya dai ba lafiya ba. Akan baƙin dama na kirasa ban samu ba......” (Komai Ummi ta zayyane mata da ya faru yanzun anan gidansu).
“Bara muga baƙin su wuce to sai na sanar masa. Duk da dai inaji a raina ko duk shine ya tsara hakan dan mijin nan naki sai da siyasa ake iya kamasa a hannu. Ya riga ya zama mai fuska biyu inba ka saniba babu mai cewa zai iya sheɗancin da yake zubawa shi da uwarsa Umm Abubakar. Amma ki kwantar da hankalinki dan ALLAH, ALLAH yana tare damu”.
“Shikenan Umm Muhammad ALLAH yay mana jagora. A gaishe da yaran sai na jiki”.
Sallama sukai da ga haka zuciyar Ummi fal waswasi da saƙe-saƙe.
*__________________*
Ido Hibbah ta buɗe a ɗan yanayin razana saboda barcin da ya figeta. Gabanta ya faɗi lokacin da idanunta ke kaiwa waje ta windown motar da aka sauke gilashi baki ɗaya. Mazaunin direban ta kalla tana haɗiyar yawu da ƙarfi saboda bushewar da maƙoshinta yayi lokaci guda. Tai saurin ɓalle murfin motar ta fito domin tabbatar ma kanta inda ya kawotan fa ba anguwarsu bane...............✍
*_Tofa. Ina mai taxi ya kai Hibbah?. Wane ruɗanine ya shiga kan Ummi game da kawo kuɗin auren Hibbah da ga gidan su Shuraim? da alama ta nuna tasan da zancen. Shin malam Aliyu Abdul-Ra'uff Maina ne ya fara aika iyayen Shuraim ga Abba kokuwa yaya abin yake ne? Wane shiri Ummi keyi akan yaranta da takejin ƙarfin gwiwar nasarar kubutar dasu ne haka? Minene shirin Abba shima game da fasa bama Junaid ɗansa auren Hibbah ya yarda ya bama Muhammad Shuraim? Shin kodai dama shine ya turosa batare da ita Ummin ta farga ba?. 🤔tambayoyinfa da yawa. Yayinda ni kaina amsarsu nake nema🚶🏻😩._*
________________________
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________
*_Chapter Sixteen_*
.........Da sauri ta dafe kanta da ya sara mata da ƙarfi. Cikin ɗacin murya da zafin da takeji a zuciyarta tace, “Wai nikam mina muku ne na laifi? Dan ALLAH kubar rayuwata ta cigaba da tafiya a yanda take karku sakamin ahali a masifa. Wancan karon kunce dan na bibiyi wanine. Wannan karon kuma mina aikata zaku kawoni nan?”.
“Duk bani da amsoshin tambayoyin nan naki. Aikina kawai shine ɗakkoki na kawoki nan wajen. Gashi kuma na cika. Amma idan muka shiga da ga ciki harma abinda baki tambaya ba za'a baki amsarsa na sani”.
A fusace Hibbah ta dubesa zatai magana aka katseta......
“Gaskiya ya faɗa miki, bashi da amsar da zai baki. Dan haka bismilla ɗiya ta”. Dattijon wancan karon da aka kaita office ɗinsa ya faɗa dai-dai yana ƙarasowa inda suke. Dan tun shigowar taxi ɗin cikin station ɗin yake kallonsu ta window. A fahimtar da yay mata na tsiwa da rashin tsoro da kafiya ya sashi yanke shawarar sakkowa da kansa ƙila tafi jin shakkarsa ta shiga.
Sai dai kuma ina. Shima a fusace ta kallesa wasu hawaye masu zafi suna sakko mata. Ganin tana motsa laɓɓanta alamar sonyin magana ya girgiza mata kansa. “Nan ba muhallin da ya dace ki cigaba da cewa komai bane ɗiyata. Ina mai tabbatar miki wannan kiran yasha ban-ban dana farko. Dan kai tsaye ke zai taimaka bamuba Muhibbat. Bakomai yasa nace hakaba sai ƴan uwanki dake gab da shiga haɗari”.
“Ƴan uwa na?!”.
Hibbah ta faɗa ƙirjinta na wani harbawa. Uffan jami'in dattijo A.G baice ba ya juya zuwa office ɗinsa. Da sauri tabi bayansa har tana haɗawa da ɗan gudu. Dan ba ƙaramin hargitsa tunaninta maganarsa ta ƙarshe tayi ba. Duk da yanajin tana binsa da gudu bai tsaya ba sai da ya isa har office ɗinsa. Kusan a tare suka shiga da Hibbah. Tai saurin zuwa gabansa ta durƙusa.
“Uncle dan ALLAH karku cutarmin da ƴan uwa. Ku daina tursasani yi muku abu ta hanyar yimin barazana da su. Kunsan kuwa mi kuka nema haddasama rayuwata a wancan karon? Saura kaɗan na rasa Ummi na, gatana ni da yayuna. Farin cikinmu madubin rayuwarmu. Miyasa kuke son saka alkairi da sharri? Miyasa kuke son yin amfani da ni saboda ku haskaka kanku ma duniya? Miyasa ku ke........”
“Ya isa ɗiyata. Duk yanda kike tunani ba haka abin yake ba a wannan gaɓar. Yanda kiɗan ya sauya itama rawar zata sauya ne dole. Inason ki nutsu ki bani dukkan hankalinki nan, domin haɗa hannu wajen tabbatar ma mutanenmu abinda suke ganin bazai yuwu ba saboda rauni da ƙarancin shekaru da suke kallo kai tsaye”.
“Ni bazan nutsu ba, bazan taɓa nutsuwa ba dan ku taurarine masu wutsiya. Dan ALLAH ku daina saka rayuwata data ahalina cikin *_TAKUN SAƘAR KU_* da bawan ALLAHn nan. Bani da alaƙa da komai nasa kamar yanda kuma bani da alaƙa da ku. Indai harkar computer ce na barta har abada duk da kuwa itace burina, itace mafarki na, itace zummata, itace kaifina. Amma saboda cigaba da rayuwar ahalina cikin salama na tattarata na ajiye. Na manta kaina cikin waɗanda suka iya koda kunnata. Please na roƙeku ku barmin rayuwa data ahali su huta. Ku barni naji da damuwar cikin gidanmu ita kaɗai ta isheni”.
Yanda ta haɗe hannaye tana roƙonsa hawaye na kwarara a kumatunta duk sai tausayinta mai tsanani ya kamashi. Idanunsa suka kaɗa sukai jajur. Kansa ya shiga girgiza mata yana ƙoƙarin kamo hannayenta dake haɗe har yanzu waje guda alamar rokonsa🙏🏻. Sai dai yana kawo hannu ita tai azamar jan nata baya.
Da sauri yace, “Shike nan naji zan barki ki tafi. Amma ki tabbatar Tabbas kinada alaƙa da Master Muhibbat, saboda wannnan ɗin kasarki ce, kuma a ƙasar taki yake aikata dukkan ɓarnarsa. Sannan rayuwar yayunki da mamanki na cikin haɗari a hannun ƙanin mahaifinku da shi wanda kike ganin baki da alaƙar komi da shi. 1Mu kaɗai ne kawai kuma zamu iya cetosu tare da ke kanki. Zakuma muyi hakanne kawai idan kin amince kin yarda zaki cigaba da mana aiki akan mutumin nan Master. Idan kuma bazakiyi ba zaki iya tafiya kawai”.
Shiru Hibbah tai tana kallonsa. Kallo mai cike da ma'anoni da yawa da ita kanta ko ca'akai ta fassarasu bazata iya ba. Kansa ya jinjina mata alamar tabbatarwa.
Sosai zuciyar Hibbah ke ƙara wani irin lugude, babu abinda ke mata kai kawo a zuciya sai batun auren yayunta da ƴaƴan Abba. Dama har cikin ranta tanaji akwai manufa, amma batasan miyasa Ummi ta amince ba bayan kuma ta sanar mata yayun nata nada waɗanda suke so. Wani tunani da yazo mata daban a cikin rai ya sakata kai hannu kawai taja kujera ta zauna tana share hawayenta da suka kasa tsayawa. Shima sai ya sauke ajiyar zuciya da takawa wajen kujerar zamansa ta office ɗin ya zauna yana fiskantarta.
“Miyasa sai ni kaɗai ce zan muku aikin? Bayan nasan akwai mutane da yawa masana kuma jajirtattu akan wannan harkar, waɗanda idan a gabansu nake ni ɗin bakomai bace, bansan kuma komaiba?”.
“Tunani mai ƙyau Muhibbat. Tambayarki na da matuƙar muhummanci kuma ta birgeni. Har cikin raina na sake yarda zaki iya domin kina da kaifin ƙwaƙwalwa. Kafin kiyi mana wancan aikin tunanina irin nasune, ina kallon raunin mace matuƙa nima. Ko a cikin hukumar nan aka bama mace aiki raina kan ɓaci naga babu abinda zata iya. Amma sai ke kika ruguza dukan wannan tunanin nawa a waccan ranar, dan kinyi abinda ƙwararru da yawa suka kasa matsayinki na mace mai ƙarancin shekaru kuma ɗaliba da iya ƙasarta kawai ta samu ilimin kimiya da fasaha. Na zauna nayi dogon nazarin da yasa na fahimci irinku ba'a sakaci da al'amarinku, dan da irinku ƙasashen turawa suka cigaba a nasu ƙasashen da suke birgemu a yau. Muhibbat na miki alƙawarin wannan aikin ƙashin kanki zakiyi. wanda dole duniya tasan da zamanki bayan kammaluwar komai insha ALLAHU. Inason barinma bayana alkairi bayan na ajiye aiki, kuma kece wanan alkairin da nake fatan bari insha ALLAH. Da kuma wanan damar zakiyi amfani kema wajen ceto ahalinki da sake darajasu cikinƴan uwanku, ki wanke baƙin fentin da ƙanin mahaifinku da kakarku sukai muku wanka da shi. Da wanan damar zaki canja masu irin tunanina game da ɗiya mace”
Murmushi Hibbah ta saki wanda ita kaɗai tasan ma'anar kayanta. Ta ɗan muskuta zamanta da faɗin, “Na amince zan muku aiki, sai dai ku sani hakan ba yana nufin idan baku sami nasarar kamashi ba zan cigaba da dawowa nan wajen. Zan muku abinda kuke buƙata ko ba'a sami nasara ba nima zaku kuɓutarmin da ahalina”.
“Tabbas mun amince, harma da wata gagarumar ƙyauta da zaki samu inhar yazo hannun namu.”
“Yallaɓai na bar muku ƙyautar basai kun bani ba. abinda kawai nakeso shine ranar auren yayuna ana gab da halartar ɗaurin aure ku kama Abba ku ɓoye min har sai an kammala ɗaura auren yayuna da matan da suke so da kwanaki biyu. Abu na ƙarshe kuma inason amin cikakken bincike akan Muhammad Shuraim da Abba ya iya hana ɗansa ya yarda na auresa duk da zaɓin Ummi na ne shi”.
“Duk mun amince da sharaɗinki”.
Murmushi Hibbah ta saki a karo na biyu. “Inhar ya kasance Muhammad Shuraim bashi da wani aibu a rayuwarsa zan auresa na rayu da shi matsayin miji kodan son da Ummi na da Yayuna ke masa. Zanbi duk hanyar da zanbi na ganin ya ɗaukeni zuwa ƙasar China yin karatuna akan ilimin kimiya da fasaha. Ni kuma a wannan lokacin zan muku aiki. Ko wanene wanan master ɗin nayi alkawarin insha ALLAH sai na zama sanadin da zaku kamashi a tafin hannunku. Dan haka na baku dama kafin kwanakin aurenmu 60 da aka saka nasan wanene Muhammad Shuraim ciki da bai. A samama ahalina waje na musamman da zasu rayu a lokacin da zan fara farautar MASTER. Dan ko ƙwarzane bana son ya samu koda farcinan hannunsu”.
Wani irin tattausan murmushi dattijo A.G ya saki, yayma Hibbah jinjina. “Tun a ranar farko da kikazo nan na tabbatar zaki iya a cikin idanunki, tabbas zaki iya. Kuma insha ALLAH dukkanin bukatunki zasu biya Muhibbat, daga ƙarshe ƙyautar dana ambata zata kasance biya miki kuɗaɗen tafiya ƙasar China ko wata ƙasa daban yin karatunki. Abinda kawai zakiyi shine neman yardar mijinki”.
A take wani irin farin ciki ya baibaye Hibbah. Ta ɗaga hannu tana addu'ar godiya ga UBANGIJI da fatan nasara akan alƙawarinta.
Shiko dattijo A.G na tayata da amin. Sai da ta sauke hannayenta sannan ya tura mata takarda da pen.
Ki rubutamin dukkan sunayen ƴan gidanku da duk wanda kike tunanin kawo tangarɗa akan auren yayunki anan”.
Takardar ta jawo gabanta tana wani irin dariyar ƙeta. Dan babu wanda take hangowa a idanunta sai Hajiya Mama da su Kawu Hannafi. Bayan ta gama zana masa ya bata wata bag dake ɗauke da tarin files da suka shafi Master. Ya ɗora da gargaɗinta akan muhimmancin riƙe musu sirrinsu.
“Dukkan abinda zaki buƙata da ya shafesa na tanadar miki anan, dole ne sai kin fara shiga kansa, kinyi irin tunaninsa. Ke mace ce, kuma ƙaramar yarinya. Inaji a jikina kafin ya ganoki ko ya farga da ke kin kammala aikin nan insha ALLAH. Kisa a ranki ALLAH na tare da ke, kuma duk inda kika shiga akwai jami'an dana tanada zasu dinga bibiyarki ke da ƴan uwanki domin baku kariya.”
Kai kawai Hibbah ta jinjina masa. Da ga haka ta fito mai taxi ɗin da ya kawota station ɗin ya sake ɗaukarta domin maidata gida.
★★
Kamar yanda Hibbah tai fata koda ta shigo gidan nasu bata sami kowa a falo ba, yayunta babu wanda ya shigo, Ummi kuma tana ɗakinta. Ɗaki ta wuce ta adana bag ɗin da tazo da ita sannan ta fito ta sanarma Ummi ta dawo.
Sosai Ummi ke binta da kallon mamaki ganin tanata washe haƙora kamar ba itace ta fita da ɓacin ran zancen aurensu ba. Komai Ummi batace mata ba akan walwalar tata. Sai ma ce mata da tai idan ta gama taje tai mata list na kayan kwalliya da kayan underwears.
Cike da zumuɗi Hibbah ta fice dan tasan na kayan lefen yayunta ne da za'a haɗa a gidan Sheikh Aliyu Abdul-Ra'uff Maina. A gurgije tai wanka ta kimtsa kanta. Ko abinci bata nema ba duk da yunwa da ciwon kan da ke damunta har yanzun, tai zaman rubuta list ɗin bayan ta kunna wayarta ta shiga WhatsApp ɗinta tana bugar cikin Hafsat da Zahidah akan kalo da sayis ɗinsu.
Cikin awa ɗaya ta kammala komai ta fito ɗauke da takardar. Kai tsaye ɗakin Ummi takai ta ajiye sannan ta fito wajen yayunta suka cigaba da hira. Su kansu sunyi mamakin ganin yanda taketa faman walwala tamkar yanda suka santa tun fil'azal. Sai dai komai basuce mata ba suma.
*________________________*
Kwana uku da faruwar haka Muhammad Shuraim yazo gidan su Hibbah a karon farko. Ya sami ƙyaƙyƙyawar tarba da ga wajen su Yaya Umar, inda aka saukesa ƙaramin falonsu da Dadynsu kan sauke baƙi kafin rasuwarsa.
Da farko Hibbah catai ita bata gayyatarsa, dan haka bazataje ba. Sai da Ummi tai mata jan ido sanann ta zumbula hijjab ta fita ɗauke da karamin tire da aka ɗora ruwa.
Tunda ta shigo da sallama ya kafeta da idanunsa manya da ke neman rikitata. Tiren ta ajiye saman Centre table ɗin falon tana harararsa da kumbura fuska.
“Malam lafiya?”.
Ta faɗa cike da tsiwa.
Kansa ya ɗan girgiza kawai yana lumshe idanunsa dake a kanta ya sake buɗewa. “Ina tausayin bakin nan naki saboda tsiwansa, amma babu komai lokaci kaɗan ya rage ya daina”.
Baki ta taɓe da kaiwa zaune cikin kujera tana faɗin, “Karka ɗauka maganin da kaima iyayena suka yarda da kai lokaci guda nima ya cini. Wasu dalilai ne kawai sukasa na yarda da aurenka badan kayi dai-dai da ra'ayin mijin da naima kaina buri ba”.
“A hakanma na gode. Na kuma sake tabbatar da cewa nazo inda ya dace neman aure. Dan biyayyar da kikai ga iyayenki kawai cikakkiyar amsace akan nagartaciyar tarbiyyar da kika samu da ga garesu mai inganci.”
“Humm” kawai Hibbah ta faɗa batare da tace komai ba.
Shuraim ya murmusa batare da ya nuna damuwa da yanayin nata ba. “Kamar yanda na faɗa miki sunana Muhammad Shuraim Aliyu. A garin nan aka haifeni, anan na tashi, anan na girma, anan nai karatun addini dana boko har zuwa secondary. Kafin na ƙetare wajen ƙasar nayo karatun jami'a har zuwa matakin degree na biyu. A yanzu haka ina akan haɗa degree na na uku tare da harkar kasuwanci tamkar yanda na taso na gani anayi a gidan mu. Abinda ban faɗa miki ba bayan wannan kuma na baki damar yin bincike a kaina dan ki sani. Ƙwarai da gaske naji daɗi matuƙa na samunki musamman da ya kasance ban zaci hakan ba. Abinda zance kawai kiyi haƙuri banyi kamar yanda samarin wannan zamanin keyiba na fara shimfiɗa soyayya kafin aure. Ni sam hakan ba ra'ayina bane ba, shiyyasa tun farko ban taɓa zuwa ƙofar gidanku ba kai tsaye sai dai bibiyarki kawai. A randa kuma iyayena sukazo domin neman izinin zuwa zance gunki sai akace anma bani ke, dan ƙa'idarku ku ba'a barinku dama yin zance. Nagode ƙwarai da gaske Muhibbat. Ina fatan zaki amsheni da hannu biyu batare da tunanin nayi miki kutse cikin rayuwarki ba?”.
Har ga ALLAH kalamansa sun sanyaya ranta. Taji matuƙar kinarsa da girmansa. Sai dai maganarsa ta kusan ƙarshe-ƙarshe akan ba'a barinsu zance ta tsaya mata arai. ta kuma sake tabbatar mata akwai abinda Abba ke ƙullawa game da auren nata da Shuraim, wanda shima da alama baida masaniya akai.
Numfashi taja tare da duƙar da kanta ƙasa, dan a karon farko taji kunyarsa da nauyinsa ta lulluɓe ta. Cikin sanyin muryar da batasan tana da ita ba tace, “ALLAH ya tabbatar mana da alkairi”.
“Amin ya ALLAH” ya faɗa yana murmushi dan ya fahimci dukkan abin cewar data shigo da shi falon ya gudu.
Ba wata hira mai tsayi sukai ba, sai ɗan guntun tarihinta itama data bashi sukai sallama ya tafi itama ta shige ciki. Dama ALLAH-ALLAH take ya wuce ta tafi ga aikin da ke gabanta akan files ɗin da dattijon jami'i ya bata (kamar yanda ta raɗa masa suna😂). Dan tun randa ya bata washe gari ta kwashe Computer ɗinta da ga falo ta maida cikin bedroom. Koda Ummi ta tambayeta dalili sai tace babu komai zata ajiyesu ne dan ta daina amfani da su sai nan gaba.
Ummi ta gamsu da bayaninta ɗari bisa ɗari. Sai dai abinda bata sani ba tuni Hibbah ta haɗa kayan a ɗakinta harma ta fara aiki akan abinda aka sakata. Ta samu bayanai na laifukan da Master ya aikata kashi-kashi, sai flash drive guda uku dake ɗauke da wasu rubuce-rubucensa na yanar gozo, da fuskokin da yake amfani da su. Abinda ta yanke na farko shine zaman yin nazari da kutse na musamman akan facemasks da yake amfani da su. Haka kawai taji a ranta tana son samo ainahin fuskarsa ta ainahi da take kallo a matakin farko na aikinta. Zatayi hakanne ta wasu hanyoyi da take ganin zasu taimaketa duk da ko farcensa baya bari a gani rufesa yake. Sai duka handles ɗinsa na yanar gizo da ya taɓa amfani da su ta hanyar tura saƙo. Da nambobin waya da yay kira dasu masu tsananin tsaro.
Yanzu gaba ɗaya lokacinta da hankalinta duk sun koma akan binciken Master da ayyukansa. Ta matuƙar maida kanta busy batare da kowa ya sani ba. Sai da safe ne idan Yayunta suka ga idanunta duk a kumbure suyita tambayarta miya hanata barci?. Takance karatune na exam da zasu fara. Tanason ta dage ne saboda shirye-shiryen exam ɗin zai haɗe mata da hidimar biki.
Duk sun gamsu da bayanin nata, dan haka sukai mata nasiha kawai akan ta ringa sassautawa tana barci dan karta saka kanta a matsala. Insha ALLAH zataci.
★★★★★
A lokacin da Hibbah keta kaikawo akan ƙoƙarin yin kutse cikin lamarin Master a gidansu shirye-shiryen biki ake tuƙuru ta fanin su Hajiya Mama da Abba da ke faman jiyyar ƙafarsa da hannu. Shiri suke na bikin ƴaƴan gata ta kowanne fanni. Dan hatta da gidajen da su Yaya Muhammad zasu zauna da amare Abba duk ya saka abokinsa ya nema musu haya, ya kuma biya kuɗin hayar da kudinsa acewarsa zai biya na farko daga haka su cigaba da biya.
Komai dake faruwa Ummi na kallo. Sai dai ta maida kanta makauniyar ƙarfi da yaji bata taɓa nuna alamar tana fahimta ba. Sai ma faman nata shirye-shiryen da takeyi ita da Sheikh Aliyu Maina da iyalansa itama. Dan a yanzu haka ma anata shirin miƙa akwatunan lefen auren su Yaya Muhammad da suka haɗama kansu da kansu zuwa gidan amarensu. Gidansu kuma na gab da kammaluwa sai sam barka da fatan alkairi.
*______________________________*
Kwanakin biki sun cigaba da turawa, shirye-shiye na ƙara faɗaɗa a kowanne ɓangare. Sai dai kuma a ɓangaren Hibbah ita hankalinta a tashe yake matuƙa bisa dalilai biyu. Na farko shine har yanzu bata sake ji da ga jami'an tsaro ba, musamman akan binciken da sukace zasu mata game da Muhammad Shuraim da zuwa yanzu shaƙuwa mai ƙarfi ta ƙara shiga tsakaninsu. Dan tun daga waccan ranar duk bayan kwana biyu sai yazo gidansu. Bawata hira sukeba mai yawa, mafi yawanci ma akan karatu ne dan tafi sakin jiki da shi.
Na biyu ganin yanda su Abba ke shirye-shiryen auren duk da yana kwance har yanzu yana fama da ƙafa sai yake ɗaga mata hankali take ganin tamkar tarkon data ɗana musu domin kuɓutar da yayunta bamai yuwuwa bane a garesu. Cikin ɓacin rai yau ta tattara dukanin kayan da A.G ya bata ta maida a bag ɗin. Dama addu'a taketa faman yi ALLAH yasa Ummi ta fita zuwa gidan malam da taji tana faɗa zata.
Tana samu yayunta suka fita, Ummi ma ta fita gidan malam ɗin tare da su sai itama ta samu ta siɗaɗa ta fice da addu'ar ALLAH yasa har taje ta dawo Ummi bata dawo gidan ba.
Tana shirin shiga napep aka dakatar da ita. Tai saurin juyowa a rikice jin an ambaci sunanta. Kallon sama zuwa ƙasa taima matashin saurayin da batasan daga ina ya fito ba. Shima batare da wani damuwar kallon da take masanba ya miƙa mata ƙaramar jakkar hannunsa.
“Babu buƙatar ki sake komawa can. Zaki sami dukkan bayanan da kike buƙata anan. Akwai waya yace zai kiraki tanan zakuyi magana. Kiyi komai da kula”.
Batare da ya jira cewarta ba ya juya ya barta tsaye galala da jikka a hannu tana binsa da kallo. Takaici da haushi yasa mai napep jan napep ɗinsa yabar wajen yana masifar an bata masa lokaci.
Itama Hibbah juyawa tai ta koma gida jiki da sauri..............✍
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*
*_NAJI DADI SHINE GARI......_*
*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*
_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_
*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*NA SABUWAR SHEKARAR 2022*
*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*
*SABBIN LABARAI*
*SABUWAR SHEKARA*
*SABON NISHADI*
*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*
*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*
*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.
*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_
*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_
*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_
*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_
*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number
08184017082
*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*
09134848107
Littafi daya
1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).
*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽
#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
_________________________