← Book details Taki Zaman Aure Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 2 OF 3

Chapter 1

Taki Zaman Aure Part 1 Complete Hausa Novel · about 128 min read

بِسْمِ اللّٰهِ الرَّحْمٰنِ الرَّحِيْمِ

Tasss muka ji sautin saukar mari, irin marin da zai iya kurmantar da mutum a take. Na kai hannuna da sauri na dafe kuncina hawaye na sauko min. Hana ta rufe fuskarta ta fashe da kuka, kamar yadda Mama ma take kukan marin da Abbah yayi mata.

“Abun da na ga damar badawa kenan idan kin ga dama ki zubar daman baki taba godewa ba ai baki taba godewa ba idan na yi miki abu, kullum cikin kuka kike kuma a cikinsa zaki kare Hajara...”

Ba a iya fatar baki yake mata fadan ba, sai da ya hada mata da duka yana harbin kafafuwanta har sai da ta fadi. Da gudu na nufi gurin da take ina kuka, sai dai kamin na tabata sai ya fisge ni ya jefar a kasa.

“Abbah dan Allah ka yi hakuri”

Na fada ina kokarin tashi na sake nufa gurin da mahaifiyata take. A madadin yayi hakuri sai ya kara rufeta da dukan kamar ana kara masa karfi, ya saba idan ya fara dukanta sai ya canja mata kamannin sannan yake barinta, dukan mahaifiyarmu a gaban idonmu wani abu ne da Abbah ya saba yi, tun muna kanana har girmanmu, agaban kowa zai iya fada mata magana marar dadi, idan kuma ta yi masa ba daidai ba baya duban mu ko a tsakar gida zai iya rufe ta da duka, mu kuma muka kasa sabawa da halinsa. A kullum idan yana dukanta na kam ji kamar ni yake duka zubar hawayena suka fi nata yawa domin ko bayan abun ya laba na kam kebe na yi kukan abun da Abba yake mata.

“Dan Allah Abbah ka yi hakuri...”

Na sake fada ina kwantawa ta inda yake shurinta domin na tare mata, sai ya hada har da ni yana shurin har sai da yayi mai isarsa sannan ya kyale mu ya fice daga gidan. A nan na samu damar tashi na rika Mama ita ma ta tashi, da taimakon Hana  muka kaita daki, karfi hali irin na Mama muna shiga dakin sai ta yanke kuka da take ta share hawayena ta dubu mu ni da kanwata Hana ta ce.

“Kar na ji wani ya fadawa Yayanku abun da ya faru, musamman ma ke Noor kin fi uban kowa baki”

Ta nuna ni saboda ni suke cewa na fi rawar kai da surutu.

“Wallahi Mama ba zan fada masa ba”

Hana ta fada, ni dai na yi shiru domin Allah ne kadai ya sani ko zan iya rike kaina ban fada ko kuma na fada, ya danganta da yadda abun ya tsikare ni. Waje mu ka fito ni da Hana mu ka cigaba da aikin gidan, ita take wanke wanke ni kuma ina shara sai da muka gyara gidan tsab sannan Hana ta fara shiga ta yi wanka bayan ta fito ni ma na shiga na yi wanka na fito mai kawai na shafa ma zauna a kan katifarmu har sai da ta gama shiryawa ta fita sannan na bude durowarta na dauko doguwar rigarta na saka na dauki bakin dankwali na daura, na san zata yi masifa dan haka na shiryawa komai ma. Ina fitowa waje ta hau da masifa na saka mata gown na je na cire.

“Wallahi ba zan cire ba, tufafina duk sun yi datti haka kike son na zauna sirara a gida ko kuma so kike na saka mai datti ko kuma na Mama zan saka, duk masifar da zaki yi sai dai ki yi amman ba zan cire ba”

“Noor ki cire min tufafi kin ga kullum kin fi son mu yi masifa har ana jin mu makota ko? Mama ta miki magana ki daina taba min kaya ba zaki daina ba ko?”

Na marairaice mata fuska.

“Ki yi hakuri daga wannan ba zan sake ba”

“Kullum ai haka kike cewa daga wannan ba zaki sake ba kuma ba zai hana gobe ki sake din ba”

Ban san lokacin da na watsa mata wani kallon banza ba.

“Wai ke Hannatu baki gajiya da masifa ne kamar tsohuwa kullum cikin bala'i”

“Allah ya raba ni da bala'i ai ke kika ja, kullum sai kin yi abun da za ayi magana”

A raina na yi tsaki na nufi karkashin inuwar mangoro na zauna ina ta hararata, bata dai kula ni ta cigaba da karatun, ni kuwa sai aikin gyara rigar dake zubo min nake daman jikin ba daya ba kayanta sun min yawa ta fini kiba da tsayi idan muka jera wani sa'in ma sai ace ita ce  yaya ni ce kanwa, daman kuma tsakanina da ita wata goma sha uku ne.

“Mtscheeeeeeee bakar masifa tufafi ya mata yawa amman sai ta saka, ko kunya bata ji a ganta da kayan kanwarta”

Daga inda nake zaune nake jiyo ihunta duk da ba ni take kallo ba na san da ni take.

“Ai bala'in neman zuwanki duniya ne ya hana ni kiba, gashi nan Mama tana fadar yadda na sha wahala kamar ba zan rayu ba saboda ke, ko gama shan no-no ban yi ba kika karbe azzaluma”

Kyalkyalewa ta yi da dariya ta kalleni domin ta fahimci a bakin gaskiyata nake maganar.

“Mahaukaciya, daman can ba jikin kibar ne dake ba, ke da aka haifa da wata bakwai ma Allah ne ya so ki Wallahi da yanzu baki duniyar ma”

“Yen yen yen yen... Fuska kamar agwaluma sai baki kamar zunubi”

Na fada ina yamutsa mata fuska, a madadin ta ji haushi sai ta sake kyalkyalwa da dariya tana girgiza kai. A karo na biyu na sake watsa mata harara na dauke kai ina kallo kofa domin na san lokacin dawowar Yaya Nabil ya kusa ko ma nace yayi. Ashe kuwa na canka daidai kamar jiran ake na maida ido a gurin sai gashi ya shigo rike da yar ledarsa kamar na tashi da sauri na tarbo shi, ni ce mai binsa kuma ni ce mai karba duk abin da zai shigo da shi gidan a kullum saboda na san kayan dadi yake kawowa daga restaurant din da yake aiki.

“Sannu da zuwa Yaya Nabil...”

“Yauwa ina Mama?”

Ya nufo gurin da na tashi ya zauna sai na zauna kusa da shi ina fadin.

“Tana daki tana bachi”

“Bachi lafiya?”

“Tun dazun ma take bachin fadan da suka yi da Abbah ne sai ta yi bachi”

Hana ta bude yana kallona.

“Ahhh ke kam kin ji haushin rayuwa Noor kin ji haushi kin shiga uku”

“Toh ai dai ba fada masa na yi nace ya doketa ba, ko kin ji na yi maganar dukan da yayi mata ne? Munafuka me zuwa lahira da kokon dambu”

Ta ja tsaki ta tashi ta nufi dakin Mama, yaya kuma ya jefar da hular ya mike tsaye zuciyarsa na cika.

“Wai Abba yaushe zai daina wannan halin ne? Wai yaushe zai fahimci Mama ta kai matsayin da ya kamata ya daina dukanta, ba zan iya jurar wannan abun ba, gaskiya na gaji, Wallahi ba dan yana ubana ba ba zai saka hannu da doki Mama na bar shi da rai ba, wannan wane irin rayuwa ne...”

Fada yake sosai kana kallonsa zaka san ransa ya bace, daman haka yake hawa idan ya ji abun da ya faru, idan kuma yana gidan tarewa yake baya taba yarda hannun Abba ya kai hannun Mama. Yana cira kafa ya nufi dakin Mama ta fito Hana na bayanta kana gani kasan ta kitsa mata munafurcin abun da na yi, ni kuma ba wai na yi ne dan bana jin maganar Mama kawai dai na fada masa ne saboda mu taru mu yi bakincikin a tare, ai shi ma yana daga cikin iyalan gidan ya kamata komai ya faru ya sani.

“Noor wai ke wane irin kunne ne da ke, me ke motsi a kanki?”

Na sauke kaina kasa domin ban san kalar amsar da zan bawa Mama ba, daman can ko ban yi laifi ba ganin laifina take balle kuma Hana ta kitsa mata munafurci.

“Me na fada miki?”

“Cewa kika yi kar na faada masa”

“To yanzu me kike yi?”

“Fada masa na yi”

“Wane gargadi na yi miki?”

Na dan turo baki gaba na mike tsaye na tsaya bayan Yaya Nabil, domin karamin aikin Mama ne ta riko ni ta fara duka a gurin.

“Cewa kika yi kar na fada, sai kuma na fada”

“Toh ya miki kyau, yau sai kin ci ubanki a gidan nan”

Na yi saurin ba bayan yaya ba tare da na dandana abinci da ya dawo da shi ba, na fito kofar fita gidan na tsaya a nan rai a bace san tun da Mama tace sai na ci ubana sai na ci duka ko wani hukuncin mai tsanani kuwa.

“Ka dawo ya aikin?”

Magana take da Yaya Nabil tana kokarin zauna a gurin da na tashi. Daker ya amsa mata da Alhamdullahi ya nufi dakinsa ni dai ina tsaye a bakin kofar jiran kawai nake na ga ta taso na auna a waje. Ina kallo suka cinye jollof din da Yaya ya zo da ita har da nama Mama bata ba ni ba saboda kawai na fada masa abun daya faru.

“Mama yanzu kuwa cinyewa kuka yi? Ina kallo ku hana min?”

Ina maganar hawaye na silalon min a ido domin abun yayi min bakinciki. A take Mama ta kara min da kalamai masu zafi.

“Ba kin zabi munafurcin, zaki ci ubanki ai kuma karki fasa ki cigaba ko zaman aure sai ya miki wuya Noor saboda wannan halin naki”

Ni dai ban sake cewa komai ba na nufi gurin da Hijab dina yake rataye na dauka na saka talkamina na fice daga gidan. Gida uku na wuce sannan na shiga na hudu da ya kasance gidansu kawata Zee. Sallama na yi aka amsa min na gaishe da Mamanta cikin mutunci sannan na tambayi kawata.

“Umma Zainab na nan?”

“Zainab bata dawo ba, ta tafi gurin bikinsu Salwa na dauka ke ma kina can?”

“Aa ni bana da kudin abun hawa kuma nesa za'ayi event din shi yasa na ce sai dai gobe idan za'ayi kamu sai na tafi”

“Gaskiya ai ya kamata ki tafi kam, Salwa ai kuna mutuncin sosai idan baki je ba ba zata ji dadi ba”

Na zauna a gurin na karbi kayan miyar da take gyara na cigaba da gyara mata ina mata hira. Daman mun saba na kan zauna na yi hira da ita fiye da yadda nake yi da Zainab ma, sai dai duk yawan surutun da suke cewa ina da shi ban taba fada mata labarin gidanmu ba domin na san a inda surutun nawa yake. Sai da gama na nika mata a blender ta sannan na ari wayarta, na shige dakinsu Zee na kira rabin rayuwata Zafeer.

“Hello babyna”

Na yi dariya mai cike da shuki da jindadin yadda ya gane ni dince tun kamin ma na yi magana.

“Ya aka yi ka gane?”

“Da zarar na ga bakuwar number ko an yi min fulashin ko an kira na san Matata ce”

“Toh ka kira kar mu cinye katin wayar Maman Zainab ce”

“Baby Noor me kai ki ga wayar Maman Zainab kuma?”

Na bata fuska kamar yana gaba jin yana kokarin kara min bacin rai bayan wanda aka saka min a gidanmu.

“Zainab bata nan kuma ina son jin muryar ka what do you expect then? Kasan Yaya Nabil ba zai ba ni wayarsa sai idan na sata”

“Calm down Baby is okay bari na kira yanzu”

Na yi murmushi na kashe wayar, haka yake rikicewa idan ya ji raina ya bace ko kadan baya son damuwata. Few seconds da yanke kiran ya kira ni na amsa na kara a kunne na kwanta a kujera ina murmushi.

“Zafeer ka dawo school?”

“Na dawo ina gurin aiki ma”

“Zafeer na so?”

“Me zaki yi a nan”

“Na gan ka kawai”

“Aa nan gurin aikina ne Babe Noor be kamata kina zuwa ba sai da dalili, anjima ai zan shigo sai mu ga juna ni ma na yi missing dinki”

“Okay”

Na amsa shi sai ya dauko wata hirar ta soyayya mun kusa minti talatin muna wayar sannan ya muka yi sallama yana ta tsokana ta da ce min amaryarsa. Bayan mun gama wayar na fito waje na yi alwala na shiga dakin da na fito na yi sallah ban daga daga kan sallayar ba Umma ta kawo min shimkafa da miya a plate har da spoon da ruwa. Aiko na gyara zama ina godiya da Allah yayi min sakamakon da abincin da Mama da hana min gashi na samu shimkafa da miya my favorite. Rabi na ci na sha ruwa na dauko plate din na fito waje na samu murfi na rufe.

“Gida zaki je da shi?”

Sai na juyo na kalleta a kunyace domin ban yi tsammanin tana daga bakin kofarta zaune ba.

“Zauna ki ci, idan zaki tafi sai na zuba miki a cooler ki kai musu”

“Aa daman rufewa zan yi kar na bar abincin a bude saboda na koshi...”

Ta yi dan murmushi domin tasan karya nake, plate biyu ma zan iya zama na cinye balle plate daya, kibar ce kawai babu amman cin abinci nake sosai kamar yar yunwa.

“Ke Nooriya zauna ki cinye abincin, nan ba gidan bakuncinki ba ne, Idan zaki tafi zan zuba miki wani nace, ni kike kunya ko kuma su Zainab da basa gidan?”

A kunyace na zauna waje na cinye abinci tass sannan na aje plate dinta. Sai ta tashi ta shiga kitchen dinta ta zubo min wani abincin a madaidaiciyar cooler ta rufe ta miko min na karba ina godiya kunya na lullube ni, da ma Zainab dince ba zan ji kunya ba amman mahaifiyarta ai da nauyi.

“Na gode Umma”

“Babu komai, ina wayata kin gama da ita?”

“Eh tana dakin su Zainab a can na aje”

“To zan dauka idan kin je ki gaishe da Mamanki”

“Zata ji”

Na juyo na nufi kofar fita har lokacin kunya nake ji, ina fitowa gidan na lullube abincin da Hijab, ko kofar gidanmu ban kalla ba na wuce na mike hanyar har na fita kwararon gidanmu na kama hanyar titi, daga unguwarmu zuwa unguwar da Zafeer yake aiki babu wani tazara mai yawa, dan haka da kafa na taka har gurin aikinsa yana hango ni ya aje karfen dake hannunsa ya taso ya nufo inda nake da mamakinsa a fuska.

“Baby i thought mu yi magana ba zaki zo ba”

Na dan yi fuskar shagwaba kamar zan yi masa kuka.

“Abinci na kawo maka fa...”

Na bude hijab din sai kular da na boye ta bayyana. Ya saka hannu biyu ya karba da sauri yana kallon fuskata da manyan idanuwansa masu tsananin fari da kyau.

“Ban sani ba I'm sorry... Na kusa tashi ma wacan motar kawai zan yi ma faci sai na tafi, zo ki zauna ina gamawa sai mu tafi gida”

Shi ya fara wucewa gaba ni kuma na bi bayansa har muka isa gurin motar ya bani cooler na rike shi kuma ya shiga yi ma motar faci. Ta gilashin motar da ya kasance baki nake kallon kai na ina gyara girata da ta yamutse, ba zato ba tsammani aka fara zuke gilashin motar har aka saukeshi kasa, ban taba zaton akwai mutun a cikin ba har sai da na yi arba da wata kyakkyawar matar da nake kyautata zatin budurwa ce amman ta girme ni nesa ba kusa ba, irin yan matan nan yayan masu kudi masu ji da kamsu.
Murmushi ta yi tana gyara zaman katon gilashin dake idonta.

“Wannan kanwarka ce?”

Matar da tambaya kamshin turarenta na fitowa dake cikin motar da kida yake tashi a hankali. Zafeer ya dago ya kalleni yana mikewa tsaye.

“Aa....”

Ni kuwa na yi karaf na tare numfashinsa na ce.

“Eh ni kanwarsa ce”

Zafeer ya kalleni da sauri sai daga masa gira.

“Yaya zan aje abincin a can”

Shi dai mamaki ya hana shi ce min komai har na juya na nufi gurin da yake zama na aje abincin, juyowar da zan yi sai ganinsa na yi a bayana.

“Me yasa kika ce haka Baby Noor”

“To ka sani ko sonka take yi, baka ga mai kudi ba ce”

“Idan tana so, me hakan zai kare ni da shi”

“Sai ta rika baka kudi”

“And...?”

He asked still confuse.

“Sai ka aure ni..”

Murmushi ne abun da ya biyo bayan mamakinsa sai ya girgiza kai ya juya ya koma gurin motar, ni ma na bi bayansa ina murmushi ina tsaye gefensa yayi mata facin ya gama, sai ta cire gilashin idonta ta miko masa 5k. Tana masa wani kallo kamar wata rikakkiyar karuwa.

“Gashi you can keep the change”

A take na ji ana kirkira wani abu mai kamar wuta kamar garwashi a zuciyata.

“Na gode”

Ya furta sannan ya juyo ya kalleni.

“And wannan matar da zan aura ce In Shaa Allah, so ba kanwata ba ce I'm her fiance an mana engage da ita shekara uku da suka wuce”

“Wow Maa shaa Allah Allah ya sa alheri”

Ta fada sannan ta rufe gilashin motarta ta yi mata key ta kama hanya. Na dube shi

“Me yasa ka fada haka? Gashi har ta baka kudi mai yawa ma tun yanzu”

“Ta saba ai duk lokacin da ta zo kudi mai yawa take badawa, and ni bana jiran kudin wani na kusa kare karatu kuma ina wannan aikin waya san me zan zama nan gaba? Ban ga amfanin yin karya ba saboda na ci kudin wani, and be kamata na boyewa kowa a alakarmu ba i love you so much ban ga dalilin da zai saka na boye alakarmu a guron wani ba, you're my life Noor ke tawa ce har abada”

Cikin tsakiyar idanuwana yake kallo yana kitsa min maganar da ta dade da zaunawa a zuciyata. Na yi murmushi wutar sonsa na kara huruwa a zuciyata.

“Mu tafi gida Zafeer”

“Jira ni a nan zan bawa oga kudinsa sai mu tafi, i love you”

Ya kashe min ido daya tare da yi min blow kiss. A gurin ya bar ni sai da ya bawa ogansa kudinsa ya dauko kayan aikinsa da cooler da na kawo masa abinci muka kamo hanyar gida muna tafe muna hira. Har muka shigo unguwar mu dabam tsakanin gidanmu da gidansu gida biyar ne a tsakani sai dai be shiga gidan na su ba duk da Kasancewar ya fi kusa har sai da ya rakani har kofar na mu gidan sai da na shiga sannan ya juya.


#KhadeejaCandy


https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx


Assalamu Alaikum...
Ina talata muku
KHADEEJA CANDY STORE 🥰🙌
Muna siyar da Atamfa, Laces, Mayafai, Talkami da Jaka, Akwaituna, Kayan Kitchen, Zanen Gado, da kuma kayan kawata gida ko falo.

✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫 -2


Daga bakin zaure na tsaya ina leka ciki sai na hango Hana tana daka a turmi Mama kuma tana zaune gaban murhu tana aikin hura wuta. Yaya Nabil kuma yana daga gafe yana wanke wandonsa da talkami.

“Ina kika je?”

Na kalli Yaya sai na jingina da kofar bana son amsa masa tambayar domin na san fada zai min ni kuma ban iya karya ba komai za ayi min sai na fadi gaskiya.

“Ba magana nake miki ba”

Ya daka min tsawa, na dan matsa baya na saka hannu a baki ina cin akaifata.

“Yaya Mama fa ta cinye abincin da ka kawo kuma tace zata min duka shi ne na bar gidan na tafi gidansu Zee mamanta ta ba ni abinci bayan na ci ta zuba min wani a kula na kaiwa Zafeer”

Yaya ya girgiza kai yana murmushi.

“Yanzu ke gidan ku ana kokuwar yadda za a cefane a girka masara amman kin samu abinci sai ki kaiwa saurayinki? Noor Allah ya shirya ki”

Mama ta tabe baki

“Ai wannan yarinyar abu ne mai wahala ta yi jinkaina, duk abun da ta samu a duniyar nan sai dai ta kai ma saurayi babu ruwanta da ni”

“Toh ni Mama me nake samu? Kullum fa babu ne a gidan, kuma ai kece kika ce dukana zaki yi shiyasa na kai masa”

“Kya ji da shi dai, wuce ki daki kasan gadona ki dauki kudin adashe ki kai ma Assabe ki ce ga zubi na biyar nan”

“Mama yanzu kina da kudin adashe kika hana ni na babur din da zan tafi bikinsu Salwa?”

“Kudin adashen zan baki ki tafi biki? Wa nake ma dashen ba ku ba? Kudin kayan aure nake tara muku ai”

Ina jin haka na san Mama ta sauko kenan dan haka na wuce cikin gidan na shiga dakinta na dauko kudin a gurin da ta saba ajewa na fito ina kallon Yaya Nabil da zai zubar da ruwan kumfa.

“Yaya na kawo kala ɗaya ka wanke min dan Allah?”

Wata uwar harara ya watso min sai na yi saurin barin jikin kofar dakin na nufi hanyar waje.

“Kawo kala daya amman”

Ban yi mamakin jin haka daga gareshi ba, daman Yaya Nabil mutum ne mai sauki kai a gareni. Na juyo cike da kuzari da jindadi na nufi dakinmu na dauko tufafina na sallah babba da mayafin sai kuma na tuna ba lallai ne Hana ta yarda ta min kwaliya ba dan haka na dauko abayata na mika masa ta.

“Gashi Yayana na gode”

Na mika masa cike da ladabi.

“Kuma na fada miki ki daina zuwa gurin aikin Zafeer ko? Ba yau na sha miki magana amman baki ji”

“Abinci kawai na kai mishi idan ba yace na kai mishi abinci ba ko kuma na zo na karbi abu Wallahi bana zuwa, Yaya ni ma fa ina da hankalina”

Be sake ce min komai ba ya jefa abayar a ruwa ya fara wankewa ni kuma na nufi kofar fita ina yi ma Hana gwalo. Domin na san idan ita ce ba zata wanke min ba ko da kuwa zan yi hauka.

“Dan Allah can mai kayan aro”

“Na ji dai na ji dai ba zan cire ba”

Na fice abuna ina tafiya a natse, daman can bana kama da marasa tarbiya ko natsuwa zakewar da nake abu ma idan na san mutum ne ne nake yi, idan ban sake jiki a guri ba ko uffan bana cewa. Cikin natsuwa na isa gidansu Talatu mai adashe na bata kudin kuma na fada mata zubi na shida ne kamar yadda Mama tace ma fada, sannan na juyo na fito, a kokarina na takaitawa kaina wahala na biyo ta kwararo kwararo domin ya fi sauki sama da mike hanya sambal.

Wani abun da ban saka rai da tsammani ba ashe rabon ganin wani abun ne ya biyo da ni ta hanyar, Abbah na gani tsaye kofar gidansu Gambo mai furar yan gayu rike da yar ledarsa baka sai gyaran riga yake. Ban yo mamaki ba domin akwai zaurawa a gidan har biyu da kuma yan matan da ba a taba yi ma aure ba. Rage tafiya na yi saboda na samu damar ganin wadda Abbanmu yake so cikin ƴaƴan gidan, amman hakata bata cin ma ruwa ba, domin har na kawo kusa da Abbah yarinyar bata fito ba.

“Abbah ina wuni”

Na gaishe shi, sai yayi saurin dauke kai kamar be gan ni ya hade rai.

“Abbah gidan dawo (Fura) za a siyo maka kawo na karbo maka”

Na fada cikin ladabi sai dai hikimar ba dan na siyo masa ba ne kawai sai dan na dalilinsa na zuwa gurin.

“Me kike yi a nan?”

Ya daka min tsawa dai da na zabura zuciyata ta buga kamar zata fado.

“Mama ce ta aike ni na siyo mata fura”

Na fada ina kokarin kare kaina, rufe bakina ke da wuya sai ga Bilki ta fito daya daga cikin yan matan da suke gidan ta chaba ado kamar wanda zata je gurin biki. Ganina tsaye ina kallonta ya saka ta juya da sauri ta koma cikin gidan ba tare da ta fito ba.

“Zaki wuce ko sai na ci ubanki?”

Kalamin da Abbah yayi ya dawo da dubana gurinsa sai na matsa baya da sauri na kama hanyar gida ina tafe ina waigensa shi kuma be fasa cika yana min dakuwa ba (Zagin hannu kun san hausar mu da ta ku ba daya ba😁) har sai da na karya kwana a nan na boya cikin wani kwararo ina lekonsa, wayarsa na ga ya ciro yana dannawa sai dai kamin ya kai wayar a kunne wani kamin yaro ya fito yayi magana da shi, sai na ga Abbah ya mika masa ledar hannunsa sannan ya juya ta hanyar da na biyo ya wuce.

‘Wato Balki da Abbah na take soyayya kenan hmmm’

Na fada a raina a zahiri kuma sai na juya na nufi hanyar gida, kamin na isa zuciyata ta cika har ta kusa fashewa tsabar takaici da baki ciki. Ban tsaya sallama ba haka na shiga gidan na zauna kusa da Mama dake tuka tuwon masara na jera mata abun da ya faru sai hakki nake saboda bacin rai.

“Wata kila dai fura zai siya”

Yaya Nabil ya fada kamar wanda be yarda da maganar ta ba.

“Wallahi ba wata fura, ai ba leda aka kawo masa ba shi ya bada ledar aka shiga da ita gidan, kuma har ce masa na yi ya kawo kudi na karbo masa sai ma zagina da yayi”

Ina maganar ina yamutsa fuska.

“Wallahi sai na mata mugun duka”

Mama ta nuna ni da muciyar da take tuka tuwo da alamar dake nuna babu wasa maganarta.

“Wallahi ko yatsa na ji ance kin nunawa Balki sai na ci ubanki sai na miki dukan da zai daukeki lokaci kina jinya, kuma kin san halin Abbanku ko? Bara saboda Amaryarss ya karya miki hannu, idan baki cire idonki akan Balki ba sai zai iya kashe ki ma”

“Amman abun da yake be dace ba, irin wannan ke janyo raini s unguwa, kuma ko aure zai yi me zai yi da Balki Fisabilillahi”

Cewar Yaya Nabil cikin da bakinciki. Mama tace

“To ya zaku yi Mahaifinku ne sai Hakuri, idan ya tashi aikata abu kun san babu wanda ya isa ya hana hakan faruwa, saboda haka bana son na ji bakin kowa a cikinku, musamman ma ke Noor ke ce marar jin magana, duk dukan da za'a miki ba ki ji”

Na turo baki gaba, domin Allah kadai ya san irin rashin mutum da zan yi ma Balki idan ta yarda da auri ubanmu.

“Har da leda baka ya bata”

Na sake fada ina tuna dukan da yayi ma Mama dazun saboda tace ya bada garin masara babu kudin cefane.

“Daman ke kin iya karawa miya gishi ai, idan baki fadi komai ba to ba ke ba ce”

Na juya ba kalli Hana na watsa mata harara. Yaya Nabil ya shafa kansa damuws na bayyana a fuskarsa.

“Wani lokacin sai na ji kamar na tafi na bar garin nan Wallahi, abubuwan da Abbah yake sun yi yawa, muna neman abun da za mu ci amman shi ta aure yake, yaushe ya auro Baaba Maryam yanzu kuma ace har ya fara tunanin auro wata, watan ma karamar yarinya sa'ar yarsa”

“Kuma dazun saboda kudin cefa ne ya doke ki Mama wai bata godewa komai ya kawo Allah kadai ya san meye a ledar nan da zai bawa Balki”

Mama ta rufe tuwon tana fadar.

“Cigaba karki fasa, tun da kin zama yar iska gararariyar gidan nan, ke idan aka ce kar ayi abu sai kin yi, ki cigaba”

Ina jin haka na yi shiru da bakina ban sake cewa komai ba, daga haka maganar ta mutu sai dai kowa da abun da yake sakawa a ransa. Ana hada hadar kiran sallah magariba Abbah ya shigo gidan a lokacin duka hannayenmu suna cikin tuwon masarar da Mama ta girka. Ni da Yaya muna ci a kwano daya daman idan yana gida hade mana abinci nake saboda na bawa Hana haushi.

“Wa'alaikumussalam”

Mama ta amsa mu kuma muka masa sannu da zuwa, sama sama yake kallo kamar wanda yayi arba da abun kyama, more especially ma ni.

“A kawo abincin ko sai ka yi Sallah”

Abbah yayi kamar be ji abun da Mama take fada ba ya nufi wani dutse da ya saba zama yayi alwala ya zauna, ina ganin haka na cire hannuna a abinci na nufi butarsa na dauka na zubo ruwa kamin na karasa gurin da yake zaune sai fada ya biyo baya.

“Wai kamar ni a cikin gidan za a wurgar min da buta a waje, aje ta babu ruwa har sai na taba, saboda an rai min wayo kuma duk laifinki ne Hajara”

Ban yarda na karasa gurin da yake zaune ba, na aje butar daga nesa domin yanayinsa yana nuna alamar ransa a bace yake kuma zai iya kai min duka. A madadin ya dora laifin a gareni sai ya juya ya kalli Mama yana nuna ni da hannu.

“Kin gani ko? Raina nin da kike min yara sun dauka, gashi ta kawo ruwa ta aje nesa da ni wato na taso na dauka”

Mama ta kalleni kamar zata ce wani abu sai kuma ta yi shiru, domin yanayin tsayin da na yi ya nuna alamar tsoron karasa nake kusa da shi. Ko da kuwa ban aikata komai ba Abbah zai iya min duka balle kuma na gan shi a gidansu Balki kuma ya san sai na fada.

“Ba zaki dauki ruwan ki bashi ba sai na ci ubanki”

Yaya Nabil ya daka min tsawa kamar ba shi ba, wata kila laifin da Abbah ya dorawa Mama ne ya fusata shi. Na duka na dauki ruwa, ban kai ga mika ma Abbah ba ya juyo ya kalli Yaya Nabil.

“Tooooo ka ci ubanta, ni kake zagi ba ita ba, daman ai ni na san ba kaunata kake a gidan nan ba, to sai ka ta so gani zaune a nan ki cinye ni, zan baka mai da yaji, daman ai yanzu abun da yara suke yayi kenan su kashe iyayensu, sai a fara saka ka a gidan redio ana hira da kai ka ga ka ci riba...”

“Subhanallahi kar Allah ya kaddara mana wannan ranar ko bana raye, kar Allah ya nuna mana wannan ranar, bana fatan hakan”

Mama ta fada tana cire hannunta a kwanon tuwon da take ci.

“Kina fata kan ai duk tarbiyar da kika koya musu ita suke yi, daga matan har mazan ita dai wannan babu albarka a tare da ita tun da aka haife ta komai ya lalace, gashi nan kuma yanzu tana daukar tarbiyar da kike koya Musu”

Ya karasa yana nuna ni haka yake yawan fada, wai tun da aka haife ni komai ya lalace masa har yau be zama kowa ba.

“Dukan abun da zai samu bawa daga Allah ne Malam ka daina maida laifin a gurin Noor, kuma ni bana koya musu tarbiyar da zai saka su raina ka Allah yana gani ai”

Mama ta fada cikin yanayin dake nuna kukan na son fitowa a idanuwanta da bakinta. Sannan ta kalli Hana ta ce.

“Karbi ruwa ki ba shi wata kila tsoro take ji kar ka doketa kasan halin Noor Malam ba sai an fada maka ba”

Kana ta kalli Nabil

“Tashi ka tafi gurin Sallah”

Ya cire hannunsa a tuwon da tuni ya dakatar da cinsa ya mike tsaye ba tare da ya wanke hannun ba ya fice a haka kamar wanda baya son kara minti daya a gidan. Hana ta karbi ruwan hannuna ta karasa kusa da Abbah ta aje masa, sannan ta Abbah ya kalleni.

“Kuma bari na fada miki Noor, idan na ji yarinyar da fadi wani abu akanki sai na lahira ya fi ki jindadi, kin san sau uku ina neman aure kina lalatawa ko? Allah yasa ki aikata wani na ji”

Na yi shiru ina tsaye a gurin kamar hoto har sai da Mama ta yi min alama da na bar gurin da kai. Sannan na kauce na koma na dauke kayan da muka ci abinci na kai gurin da muka saba ajewa, juyowar da zan yi sai hawaye ya sauko a ido. A cikin kalaman da Abbah yake yawan yi min babu mai bata min rai kamar cewar ni din ba alheri ba ce a tare da shi, kusan ya fi tsanata fiye da Hana da Ya Nabil. Hannuna na saka na share hawayena na nufi wata butar na dauka na zuba ruwa na nufi bandaki, ina fitsari ina hawaye, ban yarda na fito ba har sai da Abbah ya fice daga gidan, ba zan iya fadar cewar ni ce kadai ban san dadin mahaifi ba, kusan dukanmu haka muke tun da muka bude ido mun samu mahaifinmu mutum mai wuyar sha'ani da baya sakewa da iyalansa duka kuma babu kalar wanda be mana, musamman ma ni da na kasance marar jin magana. Abu ne mai wahala wani kalami mai dadi ya fito daga bakin mahaifinmu izuwa garemu, idan ma mun dada masa to zai bar abun a ransa ne ba zai yi magana ba, idan kuma muka bata masa a take zamu gani.
Mahaifina wani kalar mutum ne mai wuyar sha'ani mai wuyar mu'alama ga Iyalinsa, kuma mai son zuciya da zafin hannu abu kadan zai doke mu ko mahaifiyarmu a gaban idonmu. Rayuwar da muke yi a cikin gidan mu izuwa yanxu ya ci ace mun saba da ita amman ni na kasa sabawa da hakan, kullum ganin abun nake kamar sabo.

“Noor ba dai kuka kike ba?”

Na daga kai na kalli Hana dake rike da karamar buta tana dafe da kafadata.

“Hana Abbah yana yawan fadar bani da albarka ko ba ni da sa'a, yana yawan cewa sanadina ya rasa aikinsa sanadina ya fara talauci, idan mutum ya ce miki haka sai kin ji kamar ki kashe kanki, balle kuma mahaifi, kullum kalma sabuwa take zame min”

“Haba Noor ke da kike haske? Hake gidan nan hasken zuciyarmu, idan baki nan babu mai sakewa maganar Abbah ta daina damunki, Abbah ba shi da dadi a gurin kowa ke kin sani Mama ma be raga mata ba balle kuma mu, dan Allah karki bata ranki”

“Toh”

Na amsa ina share hawayena, sannan na cigaba da alwalar. Yaya Nabil be dawo gidan ba sai bayan Sallah Isha'i yana shigowa Mama ta hada mu gaba daya ta yi mana nasiha shi kuma ta ja masa kunne akan zagin da yayi min dazun a gaban Abbah.

“Raina ne ya bace Mama Noor ce ta yi laifin Amman gurinki yake maida laifi, kuma ita ja hakan ya faru, ba wai na zage ta dan yana tsaye a gurin ba ne, Wallahi zuciyata ce ta rufe na yi mata zagin”

“Toh ka rika danne zuciyarka dan Allah ka rika kawar da ido akan komai, ka samu ku rabu lafiya da mahaifinku”

Yaya amsa da In Shaa Allahu sannan ya tashi ya dauko kayan da ya wanke ya shimfida tabarma a waje ya fara gogewa da dutsen karfe na wuta. Sai da ya gama goge na shi sannan na dauko Abayata ya goge min ya nade min ya kawo min har inda nake zaune ya mika min.

“Na gode Yayana”

Murmushi kawai yayi min ya juya ya shige dakinsa na kalli Hana dake sauraren littafi a wayar Mama na ce.

“Kin gani ba irinki ba, ke baki da nasiha ko tufafinki aka taba sai kin fara fada”

Uffan bata ce min ba gaba daya hankalinta ya tattara ya koma gurin wayar dake makale a kunnenta. Sai dai sallamar da Abbah yayi ya saka ta yi saurin cire wayar ta tashi zaune ni kuma na amsa sallamar na masa sannu da zuwa na shige dakinmu, shigata da mintuna kadan Hana ta shigo. Daga ni har ita babu wanda ya sake fita dakin gar garin Allah ya waye.

Kamar yadda muka saba Hana ce take hada mana abun karyawa saboda ita ce mai zuwa makaranta, saboda haka da wuri take tashi ta dumama mana idan an raga abinci idan kuma koko za a siyo ko a dama duk ita ce take yi. Sai dai yau ni dai bana sha'awar cin dumame dan haka ban fito na karbi nawa ba sai da na ji motsin Yaya Nabil yana magana da Mama a tsakar gida. Fitowa na yi na zauna bakin kofar dakinmu a lokacin Hana ta dade da wuce makarantar boko.

“Yaya ina kwana”

“Lafiya Kalau sai yanzu kika tashi”

“Tun dazun ta tashi, wai ita yau bata son dumame shi ne taki fitowa ta karba”

Mama ta fada tana juyowa ta kalleni. Yaya Yayi murmushi ya girgiza kai.

“Ni dai yau ba ni da ko sisi idan zaki ci dumame ki ci, idan ba zaki ci ba cikinki ne”

“Yaya dan Allah ka siya min indomie Wallahi bana son dumeme kullum shi muke ci”

Mama ta saka dariya.

“Wuya bata ci ba yarinya, idan kika ji yunwa da kanki zaki nemi tuwon ma”

Mama ta tashi ta shige dakinta, Yaya kuma yayi fitarsa aka bar ni a gurin zaune, sai da na ga babu sarki sai Allah na dauki kwano na gutsira tuwon kadan na ci na aje sauran, tsintsiya na dauka na share ko'ina na gyara daman wanki da wanke wanke ko girki ba nawa ba ne, a cikin aikin gidan babu abun da na tsana kamar wanke wanke da wanki, girki kuma Mama ta fi sha'awa ta girka da kanta, ba kasafai take bari muna mata girki ba.

Misalin karfe biyu da mintun Hana ta dawo daga makaranta, ita kam bata tsaya neman wani abincin ba ta saka dumamen da na ce ba zan ci ba ta cinye abunta ta bar ni da yunwa a ciki. Ina tsaka da miyar ta cinye min tuwo kawata Zee ta shigo gidan cikin shirinta na ankon kamu, ba karamin burge ni ta yi ba domin ta yi kyau sosai ankon ya karbe ta gashi ni ban yi ba, sai yabon kyauta nake.

“Mama kin gani sai da na ce Yaya yayi min ankon nan ya ki”

“Komai dai Yayanki, ki rika tausaya masa mana Noor abun ai sai ya masa yawa, komai dai shi ne, me yasa baki ce Zafeer yayi miki ba?”

Na kalli Mama dake kare danta.

“Shi ai be da kudi”

“Shi kuma yayanki banki ne ko?”

Na turo baki gabana ina son yi mata kukan shagwaba.

“Yanzu kuma ko sisi ba ni da na tafiya bikin nan fa”

“Daina kallona Wallahi ni ma ba ni da ko naira”

Zee ta saka mana dariya.

“Ashe kuwa ba za aje da ke ba, ni ma ba ni da kudin tafiya, na san dawowa ba zai yi wahala ba saboda samari”

“Bari na tafi gurin Yaya ina binsa kudi 700 ya bani ko 200 na samu na napep”

Na tashi na zuba ruwa a bokita na shiga bandaki na yi wanka na fito na shafa mai na dauki hodar Hana na shafa da jan bakinta na yi kwalliya na yi kyau sosai sannan na saka abayata na dora mayafin, na fito daga dakin na bar Zee tana kara gyara fuskarta sa kayan kwalliyar Hana dake ta yi mana masifa wai sai mun biyata ai kwaliyar kudi take ba kyauta ba.

“Daga nan zaki iya tafiya a kafa har gurin aikinsa? Kuma kika sani ko yana da kudin ko babu, wannan tafiyar kamar ta dole Noor?”

Mama ta fara kokarin hana ni, aiko take na bata fuska.

“Mama komai fa ban tafi ba na Salwa kuma wannan ne event na karshe ni dai ina son zuwa, kuma Yaya ba zai rasa kudin da zai ba ni”

“Allah ya kiyaye ga ki ga hanya, idan be ga dama ba ai ba zai baki ba, ko ma ya hana ki tafiya bikin”

Na saka talkamina na high hill na fice daga gidan, ba a kafa na taka ba titi na isa na tari mai adaidaita sahu na fada masa inda zai kai ni yace na bada 200 naira kasancewar babu wani tazara sosai.

“Kadai san Kareem Restaurant ko?”

“Hajiya tun da ke kin san guri ai babu wata matsala”

Na shiga Napep din ya ina ta rabon ido har muka isa Fancy Restaurant din na fito na shiga ciki domin ba wannan ne zuwana na farko ba, can ciki na wuce na yi magana da wani na fada masa ya kira min Yayana.

“Yana can ciki aiki suke lafiya?”

“Lafiya kalau mai Napep zan sallama kuma zan yi magana da shi”

“Bari na kira shi a waya amman idan suna girki ba a bari su fita”

Ina tsaye a gurin abokinsa yana ta kiransa a waya be amsa ba, hakan ya saka hankali ya dan tashi domin na san halin wasu masu Napep ba su da mutunci. Komawa na yi na leka waje na sake dawowa ganin hankalina ya tashi ya saka Yusuf tambayar nawa ne kudin napep din na fada masa sai ya saka hannunsa aljihu ya ciro 200 ya ba ni na fita da saurina na kaiwa mai Napep din.
Sannan na dawo na tsaya reception din, ina ta kallon mutane da yadda ake ta sake sabunta gurin, a kullum idan ka zo sai ka ga ya sake zama sabo.

“Noor yayi picking yace ki zauna ki jira shi sai sun gama girkin zai fito”

Abokinsa ya fada, na kalli katon agogon dake gurin na ga uku da yan mintuna, na san ya kusan tashi aikin ma gaba daya, saboda haka na nemi guri a teburin da mutane suke zama na zauna ni kadai ina ta jin rashin sakewa saboda akwai mutane da yawa a gurin, duk kuwa da kasancewar kowa sha'anin gabansa yake. Ta dayan bangaren kuma ina jin dadin yadda sanyin Ac ke ratsa jikina, rabon da na ji sanyi ac har na manta.


https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx


Assalamu Alaikum...
Ina talata muku
KHADEEJA CANDY STORE 🥰🙌
Muna siyar da Atamfa, Laces, Mayafai, Talkami da Jaka, Akwaituna, Kayan Kitchen, Zanen Gado, da kuma kayan kawata gida ko falo.

✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫 -3

Ina zaune a gurin wasu iyalai suka shigo, ba zan iya fadar cewar masu kudi ne sosai ko akasin haka ba. Sai dai alama ta nuna suna da rufin asiri. Teburin sake gabana suka kama yan mata hudu ne sai maza uku da kuma magidancin da zan iya shaidar cewar mahaifinsu saboda kama da tsufan da yayi. Wadda ta zauna a gefensa kuma bana bukatar a fada min cewar ita din uwace domin alamu ya nuna haka. Hannu biyu na saka na yi tagumi ina kallon yadda uban yake handling yayansa mazan suka koma a dayan teburin suka zauna matan kuma suka zauna tare shi.

Sai da suka fara daukar littafin dake teburin suka duba kalar abincin da suke so, tukuna daya daga cikin ma'aikatan gurin ya zo yayi taking orders. Ni kam sai kallonsu nake cike da burge, ba kudin ne abun burgewa ba, ba zuwa restaurants ko order abinci, soyayyar ce ta shiga zuciyata yadda uba yake nunawa yayansa soyayya da kauna yana ta hira da matan suna dariya mazan kuma suna jefo na su hirar daga can inda suke zaune. Wani abu ne da ni na rasa tun tashina, ban tana zama da mahaifina ya tambaye damuwata ko dadi ba, wata hirar farincikin bata taba hada ni da shi ba, ban taba aikata wani abu ya nuna jindadinsa.

“Noor....”

Na juyo dama da ni sai na yi arba da Yayana, hannayensa na ji a fuskata yana share min hawayen da ban san sun zubo ba.

“Kuka kike yi? Saboda na dade?”

Ya tambaya saboda ya san ni da kukan shagwaba kamar wata wadda ta tashi cikin gata. Sai na girgiza masa kai na juya na kalli mutanen

“Wani abu da na rasa nake kallon wasu da suke da shi, kalli yadda suke cin abinci tare da Babansu be burge ka ba Yaya?”

Ya daga kai ya kalli gurin kamin ya dube yana sauke ajiyar zuciya.

“Wata rana ina jin kamar hakan zai faru amman na san ba zai taba faruwa ba”

“Kin cika tunani da yawa, a kawo miki wani abu zaki ci?”

Na saka hannuna da kaina na share hawayen da suka sake zubo min na dubi Yaya dake sanye da uniform din gurin sai tausayinsa ya kama ni, na san yayana ba mutum ne mai son zaman banza ba, yana da kokarin nema, saboda dukanmu mun taso a rayuwar talauci mun san babu kuma mun saba da hakan. A aljihunsa ake samun kudin chefane gidanmu a kullum kuma da kudinshi Mama take zuba adashe tana mana tanadin kayan aure.

“Wa zai biya? Ni ba ruwana bana da ko shishi...”

Yayi dariya domin ya san kadan daga halina ne zan iya komai ko bana da ko sisi sai dai duk abun da zai faru ya faru.

“Za a cire salary”

“Toh a kawo, daman Yaya ban ci komai ba tun safe, kuma ban taba cin abinci a Restaurant ba”

“Me kika so?”

“Akawo naman kaza da na kayan ciki da shawarma da pizza da...”

Ban gama zanawa ba ya katsene.

“Ke fa baki da hankali, duk plate daya a nan 5k plate nawa zaki ci?”

Na bude baki na kalli mutanen gabana na kirga si na kirga kudin da za su kashe.

“Tab toh Yaya a kawo kaza”

“Kaza 10k ne ke kuma abun da zaki ci ba zai wuce 2k”

“Toh ai ka ce 5k ne plate”

“Rabi zan kawo miki”

Be jira abun da zan ce ba ya juya ya bar ni a gurin zaune. Babu jimawa ya dawo rike da plate wata yar shimkafa ce kamar na roka sai wani kofin lemu da gorar ruwa mai yawa.

“Yaya wannan ba zai ce min komai ba, iya halshe zai tsaya”

“Masu kudi kadan suke ci ki yi cin masu kudi, ko baki ga yadda Restaurant din yake ba?”

Ya zare min ido sannan ya tafi ya bar ni a gurin. Ba dan kar nutane su kalle ni da ba zan ci wannan abinci ba, wannan ai rowa Yaya yake min a gurin aikinsa. Na daure na kai zuciyata nesa na cinye abincin nan tass ko shimkafa daya ban bari a gurin ba, lemun ma duka na shanye sannan na dauki ruwan na sha. Kamin na mike tsaye sai ga Yaya ya zo yana kokarin dauke kayan har da ruwan aiko na saka hannu na dauke ruwana, gudun siyar da hali yasa be ce min komai ba ya shiga ciki da kayan, babu jimawa ya fito sanye da kayansa na gida ya rika hannuna muka kama hanyar fita.

“Mi zaki yi da gorar ruwa wane irin kauyanci ne wannan Noor dan Allah ki aje”

“Wallahi ba zan jefar ba, ai ba kyau wulakanta ruwa, kuma ai siya muka yi ba sata ba”

Ina jinsa yana jan tsaki amman ban jefar da ruwana ba, ko ba komai kowa ya gani zai san na ci abinci a gurin, masu kudi ma haka nake ganin suna yi ai, suna rike gorar ruwa a hannu idan suna yawa. Sai da muka fita gate din gurin gaba daya sannan yake tambaya me ya kawo ni ma.

“Yaya kudina zaka ba ni, bikin salwa zan je, dari bakwai daka ara zaka ba ni abuna”

Ya daka min tsawa.

“Ba salwa ba kwai, yanxu saboda bikin wata Salwa kika kwaso kafa kika zo har gurin da nake aiki har da aron na Napep, kuma sau nawa zan biyaki bashinki ne Noor shekarab jiya kin karbi dari biyu last week na baki dari uku dari biyu kawai kika biyo ni, kuma yanzu kin hau Napep da ita, gashi nan kin saka ni siyen plate daya 5k sakaryar yarinya kawai”

Ban san lokacin da na tsayar da tafiyar da nake na dube shi.

“Yaya wannan abincin da naman kahirar ne 5k? Kam bala'i Wallahi a ana zalimci duniya, kuma ni kudina 700 ne”

“Da yardar Allah ba zan sake rantar kudinki ba, ke idan an ari kudinki babu zaman lafiya, kuma sai ki rika kari saboda baki tsoron Allah”

Yana masifar yana tare mai adaidaita, yadda fuskarsa ta hade sai ka rantse da Allah ba shi ne yake tarairayata a cikin restaurant din ba.

“Kuma wannan abincin da kika ci bashi ne sai kin biya. Malam Wurno Road”

Ya karasa yana magana da mai adaidaita sahun.

“Yaya ba gida zamu je ba?”

“Ban sani ba, kuma Allah yasa mu je kin zubar min da mutunci mu koma gida ki ga yadda zan miki wulakanci”

“Toh wai ni nace ka kawo min abinci? Ba kai ka ba ni ba dan kanka to miye na masifa kuma”

“Saboda dari bakwai kika zo har gurin aikina, kuma idan ban kawo miki wani abu abokan aikina ai za su min gulma, kuma kin ba ni tausayi da farko”

Ban yarda na sake cewa komai ba, domin abu ne mai sauke ya sauke ni a hanyar ya tafi ya bar ni, na lura ba karamin hawa yayi wannan masifar da yake ta min kamar na ce ya ba ni abinci a dole. Tun da muka shigo unguwar mai adaidaita be tsaya ko'ina ba har sai da Yaya ya bukaci haka. Gaban wani katon gida ya faka Yaya ya fito ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudi ya bawa mai adaidainta.

“Zai wuce da ke gida”

Ina jin haka na yi saurin fita cikin Napep din na fara yi masa magiya ina kuka. Har ga Allah ba zan yarda ya shiga wannan katon gidan ba tare da ni ba, ko ba komai ai zan bawa idanuwana abinci.

“Yaya ka yi hakuri dan Allah karka ce ya wuce da ni gida, tare da kai zan tafi dan Allah Yaya ka yi hakuri, na yafe maka 700 din ka yi hakuri Yaya dan Allah”

“Ba biki zaki ba?”

“Na fasa”

Ya tsaya yana kallona kamar wadda ya rasa ya zai yi da ni. Ni ko sai rokonsa nake ina magiya kamar wadda za a saka a cikin wata ni'ima. Ganin haka ya saka ya sallami mai Napep din ya nufi gate din gidan dake rufe. Kwankwasa yayi aka bude masa farin gate din muka shiga ciki yana gaisawa da masu tsaron kofar.
Galala na yi ina tafiya ina kallon yadda gidan ya tsaru da abubuwa gidan sama har hawa biyu, gashi komai na gidan fari ne tun daga motoci har fentin gidan, wata babbar kofar ya nufa ya danna door bell sannan yaja ya tsaya, kallo daya yayi min na natsu sa kyau na sauke kaina kasa, ba sai ya tuna min ba, ni ma ai ina ganin yadda komai yake tsare na san gidan masu alfarma ne.

Wata yar lukutar yarinya ce ta bude mana kofar, fara ce sosai babu alamar kashi a jikinta tsokoki ne suke ta rawa kamar wata tufa.

“Tine babanki na nan?”

“Eh ku shigo”

Yaya ne ya fara wuce sannan na shiga ina maimaita sunan nata da yayi min kama da ba kafirai. Suuuuuu na fara jin sanyin ac na ratsani irin tsarin nan na musamman, wannan sanyin ya ci uban na wanda na ji a Restaurant. Da katon Tv na fara arba indiawa dake ciki suna magana kai kace fasa tv za su yi su fito, ga wani kamshin turare da ke tashi kamar dakin Amarya. Ban raina kaina ba sai da na zauna a kujerar da Yaya ya zauna, wani kalar laushi na ji da ban taba jin na zauna a makamancin abu na ji haka ba. Idanuwa suka ce me muka zo yi ba kallo ba, a nan na fara tantance komai na katon falon da ya kasance fari kamar yadda curtains din da labulaye suke, wata kalar wuta ce a rufin mai blue sai haskowa take.

A hankali na sauke idona gurin stairs da aka kawata kamar ba za a mutu ba, a nan na lura da kasan ba tile ba ne, ba kuma suminti ba, wani abu ne mai tsantsi da daukar ido aka malaya a gaba daya falon har zuwa inda muke zaune, ga wani zare zare da aka saka a ciki kamar maciji.

“Yaya Yaya Yaya”

Na kira sunansa na taba shi ya nuna masa wutar sama dake blinking na nuna masa tv na nuna masa tile din sannan na matse hannuna ina masa rada.

“Ac ac ac, sanyi dadi, kujera laushi, kamshi ko'ina ko Yaya?”

Da sauri ya kawar da fuskarsa yayi kamar be gan ni, can kuma ban san abun da zuciyarsa ta raya masa ba, sai ganin na yi ya mike tsaye ya kama hannuna na Mike tsaye muka nufi kofa ya bude kofar ya tura ni waje ya rufe. Ba dan ina da zuciya mai kyau ba Wallahi da na nuna masa tijara na koma ciki da karfi, daga zuwa gidan masu arziki sai wulakanci ta biyo baya, miye laifina dan na ga wani abu ya burge ni, ina ce ban taba gani ba sai yau. Kuma gidanmu ai ba ac nake ba fankar dakinmu ma ta lalace kullum a zafi muke bachi.

A raina na yi guntun tsaki, ina jin haushin yadda be bari na ga mutanen gidan ba, wata kila ma su kawo masa wani abu mai dadi ya ci shi kadai ko ma me ya zo yi a gidan oho, ta dayan bangaren kuma ina mamakin Ina Yaya ya san masu arziki haka. Entrance na nufa na tsaya a gurin na rumgume hannayena tare da gorar ruwan sa na yi guzuri, ina kallon kofar falon ko za a bude.

“Who's this?”

Wani mutun ne tsaye a gefena rike da laptop a hannuna yana kallona.

“Noor...”

Na amsa masa ina dauke kai irin dauke kan dake nuna fushi nake.

“Me kike yi a nan? Can i help you?”

“No ina tare da wani ne”

“Wani?”

“Nabil”

“Okay”

Har ya wuce sai kuma ya dawo baya kadan ya kalleni.

“Me sa kika tsaya a waje? Ke budurwarsa ce?”

Kallonsa nake jin yake yake kokarin kure hakurina da tambayoyi kamar wani dan jarida.

“Me yasa kake ta tambaya haka? Kai ne mai gidan nan ne ko kuma me?”

Ya daga kasansa ya Kalli gidan, da alama dai shi ma bako ne domin yanayin kallon da yake ya nuna haka.

“Aa ni yaron mai gidan nan”

“Daman ai baka yi kama da mai gidan ba”

Ya dan bude ido ya daga gira kadan yana kallona.

“Haka ne, ke budurwar Nabil ce?”

“Ni kanwarsa ce, mun fito daga wata Stupid Restaurant ne yace na rakoshi nan”

“Stupid Restaurant?”

Tambayata yake kamar mai mamaki shi ma dai da alama bakauye ne kamar ni.

“Eh mana idan ba Stupid Restaurant ba, ina za a siyar da abinci haka haka ba wai 5k”

Na nuna masa kam akaifata, sai yayi murmushi ya kara juyowa da kyau kamar mai jindadin zancen.

“Abinci akwai tsada ne?”

“Sosai ni zan iya cinye plate goma ma ban koshi ba, sai wani munafukin lemu da ake zubawa a cup, da ruwa ka ga ragowar ruwan nan na zo da shi, wai Yaya na jefar na Jefar ni kuwa na ki, har da wani cewa wai masu kudi ai kadan suke ci su koshi, masu kudi dan ba su san darajar naira ba za su je wannan gurin su ci abinci har na 5k wai kazar ma 10k ji fa? Saboda yan raina yan Nigeria, Mtseee”

Na ja guntun tsaki.

“Amman da gaske ke za ki iya cinye abincin plate goma?”

“Tsab kuwa”

Ya kalleni daga kasa zuwa sama kamar mai auna idan zan iya ko ba zan iya ba.

“Haka nake ba kiba sai ci, hahaha”

Na yi dariyar kunya kamin ya fara kokarin kare kaina.

“Wasa nake na koshi”

Yayi murmushi mai sauti. Sannan ya miko min hannunsa daya.

“Nice to meet you....”

“Noor...”

Na fada masa, sannan na duba ko'ina na ga babu mai ganina na mika masa hannuna, daman can gaisawa da maza na daga cikin abun da yake matukar burgeni.

“Kai me ye sunanka?”

“Kareem, you can call me Kareem”

“Nice, nan gidan kake zama?”

“Ba sosai ba, mai gidan be cika son ina zama ba”

Ya amsa ni, ni kam ban yi mamakin amsar ba.

“Ai dole yayi wulakanci wadanda ba su kai shi kudi ba ma suna wulakanci balle mai wannan gidan, kana gani ka san mai kudi ne sosai”

Na fada, sai ya sake daga kamshi yana kallon gidan.

“Not really yana da rufin asiri dai”

“Ba wani rufin asiri yana da kudi sosai Wallahi, kai dan Allah wannan gidan be burge ka ba?”

Yayi murmushi, a madadin ya amsa ni sai ya jefo min wata tambayar.

“Me yasa kika tsaya a waje? Da kin shiga ciki kin ga yadda cikin yake ai”

“Na shiga fa, amman Yaya ya fito da ni kar na masa kauyanci”

Be sake ce min komai ba ya nufi kofar ya bude, sai ya juyo ya kalleni yayi alama da na zo na shiga da kai. Abun nema ya samu haka na taka na nufi kofar na shige cikin falon, sai dai wani abun da ya daure min kai kuma ya ba ni mamaki shi ne mikewar da Yaya Nabil na yi zaton ko zai sake korani waje ne sai na ga ya risina yana mikawa mutumen dake baya gaisuwa.

“Ranka ya dade barka da yamma”

“Nabil ya gida?”

“Lafiya Kalau Oga, ban samu zuwa tare da Coworkers dina na duba ka dazun saboda ina can ciki gurin girki, shi ne na yanke shawara sai na tashi aiki sai na zo na gaishe ka”

“Ka kyauta have a seat please”

Ya nuna masa kujera sannan shi ma ya zauna, ni dai tsabar mamaki sai na tafi zan zauna a kasa saboda kunya da daurewar kai.

“Karki zauna a kasa mana, ga kujera”

Ya nuna min kujerar da Yaya yake zaune. Sai Yaya ya bugu kafadata.

“Ki gaishe shi mana, oganmu ne, shi ne mai Restaurant din da muke aiki”

Kulololo na ji cikina yayi wani kuka kamar na yunwa, har sai da ya kalleni hakan kuma be hana ni zubewa kasa na sabunta gaisuwata ba.

“Ina wuni”

“Mun gaisa a waje ai, kin tuna? Tashi ki zauna”

Na mike tsaye ina juyawa na kalli Yaya Nabil sai ya watsa min wani mugun kallo. Na yi saurin sauke idona kasa ina jin kamar na tsargi kaina.

“Toh ai Yaya baka fada min oganka ba ne, ao ya za'ayi na sani...”

Na yi zaton a zuciyata nake maganar ashe ta fito ban sani ba, har sai da ogan da ban gama yarda shi ne mai gidan ba ya amsa ni.

“Toh me kika yi? You're just friendly that's”

Da sauri na rufe bakina, wata sabuwar kunya na kara rufeni, kamin na daga kai ina kallon wata mata dake saukowa a stairs, babu wani walwala a tare da ita, shi ma kuma mai gidan na lura da yadda fuskarsa ya sauya daga murmushin da yake min zuwa hade fuska irin na mazan da basa son wasa.

“Nabil”

“Hajiya ina wuni?”

“Lafiya Kalau ya aiki?”

“Alhamdullahi”

Ni ma na gaishe ta sai ta amsa min fuska a sake, sai dai bata yarda ko gefen da mijinta yake ta kalla ba, shi ma kuma sai yayi kamar be san da wanzuwarta a cikin falon ba. Har ta nufi wata hanyar da nake kyautata zaton kitchen ne. Yaya Nabil ya mike tsaye ya kalleni ni ma sai na mike tsaye.

“Zamu wuce oga Allah kara lafiya yasa kaffara ne”

“Ameen na gode”

Ni dai ban ce komai ba, na bi bayan Yaya ina kallon kofar da matar ta shiga.

“Nabil”

Yaya ya juyo da sauri yana kallon ogan nasa da ya kirashi.

“Ranka ya dade”

“Ka koma da ita Restaurant ta zabi duk abun da take so, Noor sai an jima ko?”

Ya karasa yana kallona da Murmushi a fuskarsa kamar ba shi ba, wani kyakkyawan murmushi na aika masa mai kayatarwa sa jan hankali saboda jindadin yace a ba ni duk abun da nake so.

“Amman... Okay Sir mun gode sosai Allah ya kara rufa asiri”

“Thank You”

Na fada in a low voice gudun kar matarsa ta ji ta fito tace zata min duka, domin na lura matan auren yanzu ba su da hankali akan mazanjesu sai su yi ma mace duka. Hannu ya dago min alamar bye bye sannan na juya muka cire tare da Yaya. Rufe kofar falon ke da wuya Yaya ya fara tambayata me na yi.

“Ban yi komai ba, amman Yaya baka lura ba? Kamar baya zaman lafiya da matarsa ko?”

Yaya janyo hannuna da sauri muka sauko daga gurin.

“Wallahi ba dan wani abu ba, da sai na ce masa ina gyaran aure saboda na ci kudi, na ce masa ni mai bada shawarware ni akan aure.... Kuma yana da kyau ko Yaya? Wannan lukutar yarinyar yarsa ce? Matarsa ma kyakkyawa ce ko Yaya?”

Muna tafiya ina fadar abun da ke zuciyata a iyakar gaskiyata.

“Ban sani ba, Noor Ban taba sanin baki da hankali ba, sai yau gidansa fa ko'ina camara ne har da wani fadar kina gyaran auren saboda baki da hankali, shiyasa kika nace sai kin biyo saboda ki zubar min da mutunci”

Be sake hannuna ba sai da muka fito daga cikin gidan gaba daya. A raina ina ta ayyana irin takeaway da zan yi ma rabin raina Zafeer idan mun koma restaurant din...
https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx

✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫 -4


KAREEM POV.

After fitarsu, Yusura ta fito daga kitchen rike da cup din ruwa.

“Me za a girka anjima?”

Daf da zata wuce shi tambaya. Ba tare da ya kalleta ba ya amsa.

“Ba a gida zan ci abincin dare ba”

Ta daga kadunta alamar ko a jikinta sannan ya wuce ta haye sama.

Mike tsaye ya saka hannunsa daya a aljihu dayan kuma rike da wayarsa a hannu ya sake cewa daga falon ya nufi gurin da ya saba zama. Sai da ya isa gurin sannan ya amsa kira na biyu dake shigowa wayarsa.

“Hello”

“Darling na yi missing dinka badly”

“Toh ya muka iya, tun da mijinki ya ki barin gari? Sai hakuri”

“Zamu iya haduwa ko yana gari...”

Yayi murmushi ya shafa sajensa.

“aa kar dai mu shiga hakkinsa da yawa, kar zunubin ya mana yawa, kara idan baya gari wannan kina da Hujja”

“Wata kila baka yi marmarina yadda na yi marmarinka ba ko?”

“Na yi mana, amman dai kar mu wuce gona da iri, kin san ai yadda nake kaunarki”

“Ko kirana baka yi Kareem”

“Be kamata na kira ki idan mijinki yana gari ba, akwai abubuwan da na iyakancewa kaina aikatasu, Safeena dole muna hakuri da wani abun fa”

“Kawai dai baka so na kamar yadda nake son ka shiyasa”

Ya shafa kansa yayi murmushi.

“You're the love of my life, ke kadai kika na aikata wani aiki da zai ba ni zunubi mai yawa Safeena, ke kin sani idan bana sonki ba zan yarda wata mu'alama ta hada mu ba haka ne?”

“Eh amman...”

Sai kuma ta yi shiru kamar wadda ta rasa abin cewa.

“Yau na ga wata yarinya mai yanayi da ke, har ta fiki wauta da sakarci ma”

Yana maganar yana murmushi.

“A ina ka ganta?”

Ta tambaya daga dayan bangaren.

“Wani yarona na gurin aiki ne ya zo duba ni sai ta biyo shi, ina kallonta ke nake ta tunawa”

Shiru ne ya biyo baya har na tsawon lokaci.

“Safeena...”

Ya kira sunanta sai ta amsa masa da muryar dake nuna ta damu.

“No wait ba abun da kike tunani ba ne, ke kin cika kishi fa, ba yadda kike zato ba ne, babu wannan a zuciyata har abada ke kadai ce kwallin kwal...”

Ta sauke ajiyar zuciyata.

“Duk ranar da ka so wata Kareem zan iya mutuwa”

“Ba zaki mutu ba, saboda ba zan so ba, na san yadda kike da tsananin kishi ai, zan kiyaye”

“Ina fatan haka”

“Ina mijikinki yake?”

“Yana daki, ni kuma ina harabar gida ne”

“Ni ma ina harabar gidan, amman yanxu zan fita, je ki samu mijinki zamu yi magana anjima”

“Okay i love you”

“I love you too”

Ya sauke wayar yana murmushi. Kana ya busar da iskar bakinsa ya sake shafa kansa ya sauko zuwa sajensa. Sannan ya juyo ya fito daga garden din ya nufo cikin gidan. Ganin kofar falon bude ya fahimtar da shi bako ya shigo gidan, domin daga shi har matarshi da yaransa biyu basa barin kofa a bude. Be karasa ba ya ji sautin kuka da kara mai razanarwa da muryar da be tantance ba. Hakan ya kasa shi cira kafa ya shiga falon da sauri. Yarinyar da ta fita dazun ya gani tsaye kusa da kofar rike da kai tana ihu, Yusura na tsaye gabanta rike da glass cup.

“Me ke faruwa a nan?”

Yarinyar ta juyo ta kalleshi da sauri sai ta kara rushewa da kuka.

“Wai daga na shigo ina nemanka sai ta buga min cup din ruwa akai kalla har yayi jini”

Ta nuna masa jinin hannunsa. Sai ya juya ya kalli Yusura.

“Why?”

“Rashin kunya ta yi min”

Ta ba shi amsa babu alamar wasa a fuskarka. Yarinyar ta girgiza kai da sauri.

“Wallahi karya take komai ban ce mata ba, kawai na shigo nace dan Allah ina mai gidan nan, mijinta shi ne kawai ta buga min cup a kai”

Kareem ya juya ya kalli Yusura dake tsaye rike da cup din.

“Kishi kike?”

“Kishi?”

Ta maimaita tana ja baya tare da yin dariyar rainin wayo.

“Kishi dai kishi? Na rasa waye zan yi kishi sai kai? Allah ya tsare gatarina da saran shuka mtscheeeeeeee”

Taja dogon tsaki ta juya ya bar musu gurin. Kareem ya kalli yarinyar da jini ke fita a goshinta yace

“Me yasa kika dawo?”

“Yaya ya tafi abun shi, wai ba zai koma restaurant din ba, kuma zai buga waya ya fada musu karya nake kar a bani, yana ta min fada a hanya, kuma yace ba zan bishi gida ba sai dai kowa yayi tafiyarsa, shi ne ya saka a Napep yace ya kai ni gida, ni kuma sai da muka yi nisa sai na cewa mai napep din ya dawo da ni nan gidan amman ya biyo wata hanya da Yaya ba zai gani ba, kuma yana waje ban bashi kudi ba”

“All this long story ban gane me kike nufi ba”

“Ina nufin Yaya so yake na tafi gida ba tare da na karba kyautar da ka ba ni ba, kuma yace ba zai tafi da ni can din ba”

Ya rike kunkurunsa yana murmushin da ya kusa zame masa dariya.

“Ammm ya ma sunanki?”

“Noor sau uku kenan ina fada maka”

“Yanzu ba zan sake mantawa ba, I'm sorry yanzu muje a duba kanki...”

Ta juya tana rike da goshin ta fita daga falon, sai ya bi bayanta har sun saka entrance din sun isa gurin motarsa ya tuna keys dinsa basa aljihunsa.

“Noor jira ni a nan zan dauko keys dina”

“Toh amman ka yi sauri kar ta fito”

Yayi murmushi.

“Ba zata sake fitowa ba”

Ya juya ya koma cikin falon, kai tsaye sama ya nufa ya shiga dakinsa ya dauko keys din, ya nufo curtains dinsa dake dage zai sauke kasa sai ya hango Noor tsaye a inda ya barta sai daga hannu take bakinta na motsi da alama masifa take, hakan ya saka shi saurin saukowa domin yayi tunanin ko Yusura ce tsaye jikin kofar falon, saboda ya hango kofar take kallo. Ga mamakin sai ga ita kadai ce take fadan tana kallon kofar falon. Sai da yaja kofar sannan ya nufi Motar ya bude sai da ya fara shiga sannan Noor ta shiga, yayi reverse ya fice gidan, tuki yake a hankali yana kallon yadda Noor ta natsu sam ba zaka ce tana da yawan magana ko kiriniya ba, babu wannan alamar a fuskarta da jikinta natsassiya ce sosai idan bata bude baki ba.


NOOR POV.

Shiga motar alfarma irin wadda ban taba shiga ba, ga wani sanyi ac mai dadi da laushi yana ratsa fatata ya saka natsu sosai ina jin yadda duniyar masu arziki take da dadi, sam na manta da ciwon da mahaukaciyar matar ogan su Yaya ta ji min a goshi har sai da muka isa wata babbar Asibiti, ni da nake zaton chemist zai kai ni domin ciwon ba wani babba ne ba. Fakawa yayi a gaban kofar emergency baya tsoron ma su masa fada.

“Za su maka fada basa bari a faka a nan ”

Daf da zai fita na fada masa haka sai ya juyo ya kalleni yayi min murmushi, da alama dai murmushi al'adarsa ce, ko ba komai ai yana masa kyau. Wani abun da ya ba ni mamaki shi ne har muka shiga cikin asibitin gaishe shi ake kuma babu wanda yace masa komai a yanayin yadda ya faka motarsa. Wani karamin daki da zan iya kira da office ya shiga da ni, yaja min kujera.

“Zauna”

Ya fada, sai na zauna kamar yadda ya bukata ina rabbata masa yadda komai ya faru.

“Ina yin sallama fa na ga ta sauko sai na ce mata ina wuni tace lafiya kalau, sai na ce dan Allah mai gidanki yana nan, sai tace me kike nemansa, na ce mata ni ce yarinyar da yace na je restaurant na karbi abu ina son magana da shi, kawai sai ta matso kusa da ni ta buga min cup, bata ma tsaya ta ji ko miye ba, ni ai ba soyayya muke ba balle ta yi kishi ko?”

Ya dauke idonsa daga kallon waya da yake ya kalleni.

“Ba kishi take ba, kawai dai kaddara ta hau kanki ne, wata kila ranta ne a bace, kin san daman irinku kaddara ta fi hawa kanku”

“Kishi take mana, ta ga budurwar kyakkyawa ta yi tunanin na zo gurin mijinta ne, ni kam lalacewa ai bata kai na bi saurayana har gidansu ba”

Wannan karon murmushin da ke bayyana hakoransa yayi.

“Ba kishi take ba, bata taba kishina ba, kuma ba zata fara yanzu ba?”

“Ba matarka ba ce?”

“Matata ce”

“Dole ai zata yi kishinka, iskanci kawai yayi mata yawa, ni daman tun zuwana na fahimci baku zaman lafiya, Wallahi da zaka bi shawara kawai ka yi mata kishiya”

Kamin na fadi kalmar karshe sai da na rage muryata gudun kar wani ya ji, ganin nake kamar tana kusa zata iya sake rusa min wani abun akai ne. Gira biyu ya daga yana kallona kamar mai mamaki.

“Wallahi ka kara aure, duk zata daina wannan halin”

“Wani be taba ba ni shawarar nan ba, amman kin kawo shawara mai kyau, sai dai ni bana sha'awar auren mace sama da daya, saboda haka na zabi na mutu a haka”

Na yatsina fuska zan yi magana aka turo kofar office din, wata likita ce ta shigo tana sanye da atamfa ta dora rigar likitoci a sama.

“Doctor gashi, ni kam na ce lafiya ka shigo yanzu”

Murmushi yayi mata ya karbi keken da ta turo masa.

“kin kare kenan thank you”

“Ur Welcome”

Sai da ta fice sannan na kalleshi jin an kira shi da Doctor.

“Kai likita ne ko?”

Ya daga min kai yana saka safar hannu sannan ya rika goshina ya fara gyara min gurin, sai da ya saka min wasu ruwan azaba na gane ashe na ji ciwo sosai kawai dauriya ce da jarumta irin tawa ta saka ban yi hawaye ba sai ihu. Idona ya kai gurin katon hotonsa dake office din yana sanye da suit a kasan hoton an rubuta masa Dr Kareem. Mamaki ya cika ni sai a lokacin hankali ya karkata akan abun da ya kamata na gane tuntuni.

“Kai ne Dr Kareem? Ana yawan fadarka har a redio ana hira da kai laaa ashe kai ne”

“Kina jin labarina kenan?”

Ya saki kaina bayan ya gama rufe min raunin.

“Sosai... Laaa amman Yaya be taba fada min kai ne Dr Kareem ba, kuma be taba fada min kai ne mai Kareem Restaurant ba...”

“Toh ai baki san ni ba, shiyasa be fada miki ba”

“Haka ne”

Na fada ina kallonsa cike da burgewa domin likita ne da yayi kaurin suna a garin nan, sai dai ban taba zaton zan ganshi bagas a arha haka ba.

“Wai mutane suke cewa wai idan mace ta yi cikin shege ko kuna unwanted ciki domin da ta zo gurin Dr Kareem zai zubar mata, haka suke fada wai gaskiya ne?”

Ba da wata manufa na yi tambayar ba, tambayar abun da nake son sani ne akansa a iyakar gaskiyata domin haka mutane suke yawan fada akansa shiyasa ake cewa yana da kudi sosai. Sai dai yanayin yadda na ga ya dago ya kalleni ya razanar da ni, ni ko a ganina tambaya ce kawai na yi domin hausawa sun ce waka a bakin mai ita tafi dadi. Matsowa yayi kusa da ni ya raba hannayensa biyu ya daga kujera da nake zaune yana kallon cikin idona.

“Noor shekararki nawa?”

Na yi saurin sauke idona kasa na kama jikina sosai zuciyata na bugawa.

“Ka ba ni tsoro”

Sai yayi murmushi ya dauke hannayensa ya matsa baya.

“Aa sheri suke min kin san mutane akwai hassada, hassada ce kawai”

Ni dai na yi shiru domin jikina na bani da farko kamar tambayar ta wa bata masa dadi ba, ko kuma ya fahimta a baibaiye ne.

“Kin san me yasa na tambaya shekarun ki?”

Yana tambayar yana kallona, na girgiza kai ina jin kamar duka na zai yi duk kuwa da kasancewar murmushi ne a fuskarsa.

“Saboda my ex kamar ke take, zata yi tambaya any how, zata fadi duk abun da ya zo mata a bakinta, bata tunani irin na mutane ita a komai nata tunanin dabam yake, yanayin surutunki mu'alamarki sakin jiki da kowa duk haka take, ina son ki zama kawata shiyasa na tambaya shekarunki”

Sai a lokacin hankalina ya kwanta, sai na yi dariya na mike tsaye.

“Idan na zama kawarka hakan yana nufin idan na zo asibitin nan, kyauta za a duba ni, kuma a duk lokacin da ba ga dama zan tafi restaurant dinka na ci abin da nake so ko na karba ba zaka ce komai ba”

“Huh?”

Ya furta yana kallona cike da burgewa, sai na daga masa kai.

“Eh shi ne abotai ai”

“Shikenan na yarda”

Ya furta cikin sanyi murya, yana kada kai a hankali. Farinciki ya cika ni har na kasa ce masa komai sai murmushin dake tattare da dariya nake.

“Mu tafi ko?”

“Toh”

Na bi bayansa domin tuni yayi gaba ya bude min kofar.

“Ni daman na san sheri suke maka ai da kana zubar da ciki ba zaka haifi wannan yarinyar ba, matarka zaka fara zubarwa...”

Ban karasa ba na ji hannunsa ya rufe min baki, dayan hannunsa kuma a wuyana ya saka ni gaba yana turani kamar wata akuya, aiko sai na duke na subuce na juyo na kalleshi rai a bace.

“Ya kana min haka sai aje ce an ga Noor wani Kato na taba ta”

Ya nuna kansa.

“Ni ne Katon? Beside neman mata ba halina ba ne, kowa zai iya shaidata da wannan bana neman mata, kuma na rufe bakinki ne saboda karki fadi wata maganar wasu su ji”

“Na gane”

Na amsa a hankali sannan na jera tare da shi muna tafiya, kana gani kasan ni kanwarsa domin ya fi ni tsayi sosai. Da kaina na Bude Motar na shiga shi ma ya shiga bangarensa a yanzu kam na gane dalilin da ya saka ba ayi masa fada ba a lokacin da ya faka mota a kofar emergency. Ban sake cewa komai ba domin na lura kamar surutuna ya fara effecting dinsa.

“Noor ya na ji ki shiru, ko maganar ta kare”

A lokacin da na juyo na kalleshi sai na ga kallona yake da da abun da ya zame masa wajibun wato murmushi a fuska.

“Na ga ai baka son surutu ne?”

“Inji waye? Ni ina son surutu sosai, shiyasa na sake da ke ba, ni mutum mai mai son wasa da dariya mai son nishadi, shiyasa kika burge yau din nan domin ina son mace da ko iska ya wuce sai ta bani labari yadda ya wuce, shiyasa nake son Ex dita amman na lura ke kamar ma kin fita”

“Ex din mutuwa ta yi?”

Ya girgiza kai ba tare da ya kalleni ba.

“Tana nan”

“To ka auro ta mana, ka aje ta a gidan ka, ka ga matarka ma ba zata sake fasawa baki kai ba saboda kishi”

“Ta yi aure ai, ina miki zancen baya ne”

Na yi kwafa.

“Wallahi ba dan haka ba da zai na zugaka ka kara aure, ni Wallahi da ni ce kai aure zan kara matar nan ta bata min rai daga tambaya? Kamar ta ji kowa kishi”

Wannan karon dariya yake min.

“Matata bata kishi, babu wani abu mai alaka da kishi a tsakanina da Matata, kawai dai kin zo a rashin sa'a ne, ko dai kin mata rashin kunyar kamar yadda ta fada, kawai an rubuto jininki zai zuba a yau ne”

Takaici ya hana ni cewa komai, wato bangaren matarsa zai dauka har yana yarda da zancenta ya watsar da nawa. Har muka isa restaurant din ban sake ce masa komai ba.

“Me za a kawo miki?”

Na dan kalleshi ina turo baki gaba.

“Ai da kunya ba komai zan iya fada a nan ba, ni dai zan shiga na karba ka fada musu”

Yayi shiru yana kallona kamar ba zai ce komai ba, sai kuma yayi murmushi ya daga min kai, sannan ya ciro wayarsa ya kira wadda ban san waye ba, ya fada masa wata zata shigo yanzu ya bata duk abun da take so.

“Zaki iya tafiya, amman ba sai kin fadawa kowa tare muke ba, ba a taba ganina da mace ba”

“Zaka iya tafiyarka ai, ni ma ba a ganina da maza, ni ma ba yar iska ba ce ba wai kai ne kadai na kwarai ba”

Ina fada ina yatsina fuska domin na lura so yake ya nuna shi na kwarai ne, ni ce yar iska.

“Ban ce ke yar iska ba ce, kawai ina son na kai ki gida ne cikin mutunci saboda na yi ma iyayenki bayanin yadda kika ji rauni, waya sani idan ban tafi ba za su iya dukanki”

Na kalleshi da sauri na tuni ma na manta da rauni.

“Eh Wallahi musamman ma Baba, bari na je na dawo to”

Na bude motar na fita ina jin kaina kamar wata yar shugaban kasa, ahh a rayuwata fa ban taba shiga mota mai kyau mai tsada irin wannan ba, kuma ina fitowa motar na shiga restaurant na karbo kayan dadi, wayyo Allah ina ma yan unguwar mu za su gan ni a yau. Sai da na kusa shiga reception din sai kuma na tuna da wani abu na dawo baya da sauri na kwankwasa gilashin motarsa sai ya sauke bakin gilashin yana kallona.

“Dan Allah ko zaka min alfarma idan na fito daga sai ka rufe idonka ko kuma ka fita motar har sai na saka abun da na karbo tukuna”

A bakin gaskiyata nake fada masa, domin kar na kwaso kaya da yawa ya ji babu dadi ai da kunya ko, daga kyauta na wuce gona da iri kuma yana gani.

“Ki ce karya min jari zaki yi ko?”

Yanayin yadda yayi maganar da kamar tsoro sai ya saka dariya ta subuce min, na yi bayabaya ina tafiya da baya baya ina dariya, shi ma murmushi yake yana kallona har na juya. Ni dai iyakar abun da na sani ba zan bar wannan banzar ta wuce ni ba, ba zan yarda na fito ba tare da na dauko abun da nake so ba, waya sani ma ko ba zan sake zuwa ba, ai Yaya ba zai bari na sake zuwa ba, kuma hausawa sun ce waman taraka bati sidda fa huwa wawa au sakare, wai duk wadda ya ga bati ya bar shi shi wawa ne ko sakare.

Ina shiga gurin na fada musu abubuwan da nake so, snack kala kala da naman kaza da farfesun kifi da na kayan ciki, har da wata yar tsutsa da na taba ganin turawa suna ci a tv sai da na saka aka hado min da ita yau dai ni ma zan dandana kayan masu kudi na ji me ake ji. Haka na riko leda biyar na fito ina boye ledodin a bayana dan kar ya gani, yace ba ni da hankali na kwashe masa kayan shago. A lokacin da na iso gurin motar sai ya bude min bayan motar na saka komai a ciki na rufe sannan na bude gidan gaba na shiga. Cingan na tarar yana ci yana kokarin juya motar

“Ka ga me na zo da shi?”

“Ba kin ce kar na kalla ba? I respect that”

Ya amsa ba tare da ya kalleni ba. Hakan ba karamin dadi yayi min ba. Sai na saki jiki ina fada masa inda zai bi har muka isa unguwarmu.

“Kwanar gidan mu mota bata shiga, ka aje motarka a nan ka raka ni a kafa”

“Ko dai na kira Yayanki ya zo ya tafi da kai?”

“Aa ko da shi ya yarda Babanmu ba zai yarda ba, kara dai kaje idan aka kira Babana ka masa bayani shi ne zan tsira, dan Allah ka min wannan alfarmar ba zan sake damunka ba daga yau na maka alkawari ba zaka sake ganina ba”

Ya daga min kai, sannan ya kashe motar. Har na bude na fita sai kuma na dawo ya leka shi.

“Amman ka zauna a motar sai na yi nisa sai ka biyo ni”

“Saboda me?”

“Saboda Saurayina idan ya gani zai ji haushi ransa zai bace yana da kishi sosai zai iya maka duka ma”

Yayi murmushin kasaita.

“Ni mai dukana ai sai ya shirya, zai dai yi kishi amman ba zai ina nuna min yatsa ba ma”

“Yana da karfi”

Na fada masa dan ya san Zafeer dina ba rago ba ne.

“Yana da kudi?”

“Aa”

“Toh ba shi da karfi”

“Ba zaka gane ba ai”

“Ke ce dai ba zaki gane ba, saboda ke yarinyar ce baki san yanayin kasar nan ba”

“What ever ni dai karka jera da ni, kuma zan bar maka ledodin a mota sai ka dauko min idan mun isa ka bawa Yayana ya shiga da su?”

“Na dauko kuma?”

“Eh ai ni mutanen unguwa za su iya fadawa Zafeer sun gan ni da ledodi manya, amman kai babu wadda ya san ka ai, ko kuma idan mun tafi ka kira Yaya ka ce ya zo ya dauki ledodin”

“Toh sai dai haka”

“Da nine kai ma cewa Yaya zan yi ya tafi gida yayi kwana biyu”

Ya kalleni.

“Saboda ya wulakanta kanwarsa, ai idan ni yarka ce ba zaka so ayi min haka ba right? Kuma ya bijirewa umarninka be kamata yayi haka ba”

“Haka ne”

Na fita na rufe motar na kama hanya ina fakar idon mutane, sai da na yi nisa sannan na juyo na kalleshi, bawan Allah ashe yana bayana daga can nesa yana bin sawuna. Sai da na isa bakin kofar gidanmu sannan na ja na tsaya har ya iso.

“Ka aika yaro kace kana Sallama da Babanmu”

“Okay”

Tsakanin amsawarsa da okay da yayi da kuma fitowar Baba da ban yi zaton yana gidan a wannan lokacin ba ban san wadda ya riga wani ba. Na ja baya da sauri na koma kusa da ogan kamar zan shige jikinsa.

“Toh Yar iska marar mutunci ina kika dauko wannan kuma?”

Kamar yadda nayi tsammani kalma marar dadi ce ta fito daga bakin mahaifina a izuwa gareni a gaban mutumen da mahaifina be san waye ba.

“Ayi hakuri ranka ya dade, dan akasi aka samu ta bugu a kai shi ne na ce bari na zo na yi muku bayani”

“Ai dama mutuwa ta yi, wannan yarinyar bata da amfani a garemu, wawuyar banza yar iska, ta maka hauka ko?”

Ogan Yaya ya juyo ya kalleni kamar mai mamakin jin furucin mahaifina akaina, ni kuma kunya da bakincikin suka saka na sauke kaina kasa ina taba yatsuna.

“Aa kareta ta na yi ba da gangan ba, ina tare da mota ne bata lura ba ni kuma burkin be tsaya ba sai na ji mata rauni a kai kadan, shiyasa na ce zan so na yi bayani a gidansu kuma na bada kudin magani, amman ayi hakuri dan Allah ba laifinta ba ne”

Baba na jin zancen mota da kudin magani sai fuskarsa ta sauya ya dan saki fuskar kadan.

“Babu komai, ita ce ai bata jin magana”

“Sunana Kareem Ibrahim Kalil, ni ne mai gurin da yaronka Nabil yake aiki”

“Maa Shaa Allahu, ashe ma abun duk gida ne, sannu da zuwa, bari na kira shi shi ma be dade da shigowa gida ba ai”

Kamin mutumen ya sake cewa komai Baba ya juya ya shiga gida. A lokaci ne ya juyo ya kalleni.

“Ki yi hakuri da abun da mahaifinki ya fada, wata kila ransa ne ya bace”

Na kalleshi ina murmushi.

“Na saba ai, Babana yana yawan cewa ba ni da sa'a babu alheri a tare da ni”

Da dare na karasa maganar irin dariyar dake tattare da bakinciki, shi kam kallona kawai yake kamin ya juya daga ni har shi mu kalli Yaya da ya fito daga cikin gidan. Cikin rawar jiki da girmamawa Yaya ya gaishe shi sannan ya kalleni.

“Noor ina kika je? Na iso gida Mama tace baki zo ba, dole na koma nemanki”

Na yi shiru ina turo baki, babu zato balle tsammani na tsinkayi muryar Ogan nasa yana karanta masa cewar ya zauna gida yayi kwana biyu.

“Ranka ya dade laifi na yi? Ko... Ko.. Noor ta yi wani abu ne”

Yana tambaya jikinsa na rawa.

“Kai ne dai ka yi laifi a wane dalili zaka tafi kai dabam ita dabam? Yanzu idan wani abun ya same ta fa? Kuma na baka umarni cewar ka tafi da ita ta dauki abun da kake so baka yi haka ba? Ban isa da kai ba kenan?”

“Dan girman Allah ka yi hakuri oga... Dan Allah ka yi hakuri”

“Ba korarka na yi ba, amman dai ka zauna sai Monday zaka koma aiki”

Wallahi ji na yi kamar na daka tsalle na dire saboda muryar lallai wannan mutumen mai saukin kaine sosai mai jin maganar mata.

“Mu je mota ka karbo mata sako, Noor Allah ya tsare gaba”

Ya karasa yana kallona.

“Ameen”

Na amsa sannan na shige cikin gida ina jin kaina kamar wata sarauniya a yau.
https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx


Assalamu Alaikum...
Ina talata muku
KHADEEJA CANDY STORE 🥰🙌
Muna siyar da Atamfa, Laces, Mayafai, Talkami da Jaka, Akwaituna, Kayan Kitchen, Zanen Gado, da kuma kayan kawata gida ko falo.

✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫 -5


KAREEM POV.

After ya mika masa tsarabar Noor ya bude motar ya shiga sai Nabil ya rage tsawonsa yana bashi hakuri.

“Ranka ya dade dan Allah ka yi hakuri, Wallahi ba zan sake bijirewa umarninka ba, kuma idan wani abun marar dadi Noor ta yi maka da ya saka ya kanye wannan hukuncin dan Allah ka yi hakuri”

Kareem ya kirga 10k ya mike masa.

“Noor bata min komai ba, kuma a yanzu ina jin hakan da na yi yayi daidai domin be kamata na baka umarni ka saba ba, ba wai na koreka ba ne noo zaka zauna ne a gida har Monday”

“Toh ranka ya dade”

Har Kareem yaja gambo zai rufe motar sai kuma ya kalli Nabil

“Shekarar kanwarka nawa?”

“Wannan watan zata yi 15”

‘Fresh one, shiyasa kanta be tsaya ba, tashen balaga take’

Ya fada a ransa a zahiri kuma sai ya sake tambayar Nabil.

“Kai kuma fa?”

“19 ranka ya dade”

“Okay, amman tana karatu?”

“Bata karatu gaskiya, bata son makaranta”

“Why?”

“Haka nan kawai bata son karatun, kanwarta da kusan suke tawaye tana karatu sosai amman ita bata son makaranta”

“Kuma aka zuba mata ido? Baku tsoron future dinta ya lalace?”

“Toh ya za'ayi ranka ya dade ai ka ga yadda take, Baba ne kawai zai iya da ita shi kuma karatun ba damuwarsa yayi ba”

“Allah ya kyauta”

“Ameen mun gode”

Ya rufe motar ya juya, ya fice daga unguwar. Ba gida ya nufa kai tsaye ba restaurant dinsa ya sake komawa a gurin yayi sallah La'asar yana fitowa Masallacin abokinsa Hafiz na fakawa kusa da motarsa, Kareem ya karasa gurinsa ya mika masa hannu suka gaisa.

“Dazun na ga motarka, na so mu yi magana amman ban san fitarka ba”

Kareem yayi murmushi tunawa da Noor.

“Wata bakuwa na yi mai kiriniya ita ta saka ni zuwa nan kuma na kaita gida”

“Bakuwa?”

Hafiz ya tambaya domin be taba jin abokinsa yayi zancen wata mace ba bayan Safeena da matarsa, ko siblings dinsa iyakarsa da su gaisuwa, sai kuma fada idan sun yi ba daidai ba.

“Yeah wani yaro na ne, da yake aiki nan ya zo duba ni sai ya zo da kanwarsa to kanwarsa ce rikitacciya”

Yana maganar yana murmushi maganarsa da ita yake tunawa a lokacin da take fada masa abincin restaurant dinsa yayi tsada.

“Kuma ka kawo ta nan ka kaita gida? Ko dai...”

Kareem yayi hanzarin katse shi yana girgiza kai

“Noo kai yarinya ce irin fresh yaran nan yanzu take girma, kuma ni bayan Safeena babu kowa a raina”

Hafiz yaja tsaki jin ya ambaci sunan matar da ya fi tsana a duniya fiye da kowa, matar da ta sauya dabi'u da mu'amalar amininsa zuwa wani dabam da ba shi ba.

“Ya jikinka?”

“Alhamdullahi na ji sauki sosai”

“Amman baka shiga aiki ba yau, domin na shiga ban same ka ba, na tambaya aka ce baka shigo ba”

“Na shiga da yamman nan na kai Noor na mata treatment”

“Wace Noor me ya faru?”

“Yarinyar da nake baka labari yanzu ita ce Noor, Yusura ce ta buga mata abu akai kan ya fashe jini ya zuba shi ne a kaita asibiti”

Da mamaki Hafiz yake kallon abokin nasa.

“Yusura ta fasa mata kai kace fa? How?”

Kareem ya dan tabe baki yana jingina da motar Hafiz.

“Yusura tace wai ta fada mata magana ne, amman ita yarinyar tace Yusura kishinta take saboda ta ga kyakkyawar budurwa”

Yana maganar yana dariya, Hafiz ma yayi dariya.

“And she got lucky ka kaita asibiti”

“Daman wa zai kaita asibiti ba ni ba, matata fa ta fasa mata kai, a asibitin ma tambayoyi take min har da na banza wai ance ina zubar da ciki”

Hafiz ya tintsire da dariya.

“Kirikiri?”

“Wallahi a gida ma haka ta gama ba ni labari wai restaurant dina yana da tsadar abinci, amman bata san ni ne mai restaurant din ba sai daga baya”

“Zan so ganin yarinyar nan”

“You better not babu ruwanta take zata fara maka maganar da ta zo bakinta, kuma ka san kai ba irina ba ne zaka iya fusata, amman labarin cikin nan ya ba ni mamaki”

“Kareem kenan, ka yi kaurin suna kowa ya san kwarewarka akan iya aiki da daukar komai babu wasa, so dole makiya za su nemi hanyar da za su yada wani abun kyama game da kai”

“Toh ai ni taimako kawai nake, bana cirewa sai wanda na san akwai matsala, amman masu cikin shige ni bana zubarwa”

“Duk yadda zaka yi ba zaka gujewa mutane ba, wata ma cikin banza zata dauko ta zo tace maka mai matsala ne ka burke mata ta zubar”

“Aa sai na yi bincike nake yi ai, ni ba shashasha ba ne irin Noor”

Hafiz da sai a lokacin ya rufe motarsa ya kalli Kareem.

“Muje ka bani labarin yarinyar nan there is something special about her...”

Kareem ya jera da abokinsa suna tafiya ya zuba hannayensa duka biyu aljihu. Har suka isa office labarin abun da Noor ta yi masa yake ma Hafiz, and Hafiz was so excited domin ya dade yana jiran irin wannan labarin daga gurin abokinsa.

“Amman be dace mahaifi ya furtawa yarsa haka ba, ko da daga ita sai shi ne balle kuma har a gaban wani”

Hafiz ya fada bayan ya zauna. Kareem ya daga kafadunsa.

“Ni ma shi na gani, irin haka ke sa yaro ya lalace, ni ma ban jidadi ba balle kuma ita, amman tace min ita ai ta saba, duk sai ta ba ni tausayi Wallahi, gata karamar yarinya she's just 14 no 15 this month”

“Kasan fa wasu iyayen idan talauci ya halbo su ido rufewa yake”

“Baka da kirki Barrister amman fa akwai alamar haka, domin daga ganin gidan nan da unguwar ma ka san suna fama da talauci ko'ina kwata”

Ya fada yana ciro wayarsa dake ringing ya duba, ganin sunan Safeena ya saka shi dan shakkun dagawa a gaban Hafiz domin ya san ba karamin abu ba ne su yi fada saboda kiran, but babu yadda zai yi dole ya daga domin ba zai tana iya rejecting kiran Safeena ba kuma ba zai ga kiranta ya kasa dagawa ba.

“Hello...”

“Kareem guess what?”

Safeena ta fada daga dayan bangaren.

“Ina guest's House dinka”

“Safeena i thought mun yi magana idan mijinki yana nan ba zamu ga juna ba? Dazun nan ma ba mun yi maganar nan ba?”

“Na kasa rike kaina ne, kuma i have surprised for you shiyasa na zo, kawai magana za mu yi”

“Shi ke nan gani nan zuwa”

Ya amsa da kamar yanayin damuwa, sannan ya sauke wayar.

“Yanzu baka ko jin kunya barina zaka yi a nan ka tafi ka gurinta”

Cewar Hafiz cike da takaici. Kareem yayi murmushi.

“Kamar baka san tsakanina da Safeena ba? Tana son ganina and i can't say No”

“Ka ji tsoron Allah Kareem, kana mu'alama da matar aure macen har da yayanta hakkin ai sai ya maka yawa”

“Shiyasa na ce idan mijinta yana gari ba zamu rika ganin juna ba”

“Yanzu idan wani ya kwanta da matarka ya zaka ji? Amman kai kana yi ma matar wani?”

“If wani ya aikata matata haka, kashe shi zan yi, ba zan iya jurar komai ba, ko da kuwa Yusura ce da bana so balle ace wadda nake so”

“Amman kake aikatawa matar wani? Idan kuka mutum a wannan halin kace me? Waya sani ma ko ita ma tana tare da Ex dinta”

“Ex dinta yana can kasar waje, ba dan an cilasta mata aurena ba, da yanzu tana can tare da shi suna rayuwa ni ma da yanzu da Safeena nake rayuwa, amman ya zamu yi kaddarar mu ta zo a haka”

“Ka yi sabon Allah kace kaddararka ce a haka? Kareem ka raina wayon mutane Wallahi”

Kareem ya busar da iskar bakinsa.

“Wai da duk wannan abun why not ta kashe auren ka aureta?”

Kareem ya girgiza kai da sauri saying no to Hafiz question.

“Har abada, ba zan iya aurenta ba, idan ta fito gidan mijinta wa zai rike mata yayanta? Ni dai yadda nake da kishin nan kasan ba zan iya rike yayan wani ba, kuma...”

Yayi shiru.

“Kuma me? Ba zaka aureta ba saboda kana jin ba da kai kadai take tare ba?”

“Da ni kadai take tare a yanzu na sani, amman daga lokacin da zan aureta ba ni da wannan tabbacin, what after na aureta ta koma tana mu'amala da tsohon mijinta kuma? Ko wani? Daga lokacin da na fara kaiwa jikin Safeena sai aka tsinke igiyar aminci a tsakanina da ita, for now na san ni kadai ne, amman idan na aureta ba zan samu aminci ba”

“Kenan haka zamu yi ta zama har bada?”

“Not har a bada, ina fatar canjin”

“A hakan?”

Hafiz ya tambaya yana masa wani kallo. Kareem yayi dariya grabbing his phone ya mike tsaye ya fice daga office din.

“Allah ka tsare mana imaninmu ka tsare mu da auren mata irin Safeena”

Ya fada yana juyawa ya bi kofar office din da kallo. Kareem na shiga motarsa ya dauki hanyar gidansa da ya gina da kansa saboda Safeena da kuma irin tsarin da take so, sai dai kaddarar rayuwa bata ba su damar zama ma'aurata ba, sai suka zama ma'aikatan aikata zunubi. Yana yin horn mai gadi ya bude masa gate sai ya shiga ya faka motarsa, yana ganin motarta ya tabbatar tana gidan kamar yadda ta fada masa. Ya bude motar ya fito ya nufi kofar falon ya saka key ya murda ta bude ya shiga. Yanayin arba da ita sai murmushi ya baibaiye fuskarsa ta taso da sauri tana kamshi turare mai karfi ta rumgume shi.

“I miss you so much”

Ta fada tana shafa fuskarsa, bakinta ya sumbanta ya rike bayanta.

“I miss you too, kwana biyun nan da baki kusa kamar na yi hauka”

Ta yi dariyar jindadi.

“Ba ga matarka ba?”

“Matata ai kin san once in a month ne, amman ke kullum ne, kin san yadda nake sonki ai”

Ta sake yin murmushi ya kai bakinsa cikin nata, sun dauki lokaci a haka kamin ya cire bakinsa.

“Yau kam ba zamu wuce nan ba, Safeena ina son ki rika jin maganata, na fada miki idan mijinki yana nan ba zamu rika haduwa ba”

“Na sani, yanzu kawai na zo maka da abun mamaki ne kuma abun Farinciki”

“Surprised din me ne?”

Ya tambaya yana kokarin raba jikinsa da nata, sai ta yi baya ta nufi jakarta ta bude ta dauko abu sannan ta boye a bayanta.

“Rufe idonka”

Ya rufe idon yana murmushi har sai da ya ji matsowarta kusa da shi ta ce ya bude sannan ya bude. Yana yin arba da surprised din sai murmushin dake fuskarsa ya gushe, mamaki ya koma masa tashin hankali.

“Innalilillahi Wa'inna Ilaihirraji'un”

Ya furta har sau biyu sannan ya karbi PT scrip din yana dubawa.

“Me hakan yake nufi?”

“Ciki mana Kareem, kai fa likita ne”

Ta fada cikin tsananin farinciki, da tsammanin shi ma farincikin zai yi. A take ya ji gaba daya tsigar jikinsa tana tashi.

“Cikin waye Safeena?”

“Cikin Kareem, mijina shekaranjiya ya dawo ai ba za ace na yi cikin tsakanin jiya zuwa yau ba, kuma tun da liyin ya nuna sosai that's mean cikin ya dade, kasan for the whole 3 months muna tare, I'm happy Kareem zan haifi ďanka...”

Ta kai hannunsa ta taba fuskarsa tana murmushin jindadi sai ya buge mata hannaye ya fadi zaune ya shafa kansa ya mike tsaye ya sake komawa ya zauna.

“Me ya faru? Wannan abun Farinciki ne a tsakaninmu Kareem”

Ta nufeshi ta rika shi sai ya kauce daga rikon.

“Baki da hankali Safeena baki da hankali, miye abun farinciki a nan? Kina da aure ki yi ciki da wani a waje kuma ki ce abun farinciki?”

“Saboda naka ne Kareem, duka yara uku da na haifa na Abdull be, ina son na haihu da kai, ka san yadda nake sonka...”

Ya aje PT din trying to calm himself down.

“Na sani, amman ban da ciki, wannan kuma mun wuce gona da iri ba zamu iya rumgumar abun da ya biyo baya ba”

Ta kalli cikin idonsa hawaye na cika idonta.

“Me kake nufi?”

“Zamu zubar Safeena ba zamu taba haihuwa a tsakaninmu ba har abada, babu wannan”

Ya matsa zai taba ta sai ta matsa baya tana kallonsa.

“Me kake nufi kenan?”

“Zubar zamu yi, ba zam iya wannan ba Safeena ba mu wuce gona da iri ba”

“Na yi mamakin jin wannan kalamar daga bakinka, ban yi zaton haka ba, ni ina son cikin idan kai baka so ni ban daina kaunarka”

“Ni ma ban daina kaunarki ba, amman ba zamu yi cikin banza ba, kuma da igiyar aure akanki”

“Ba zan iya zubarwa ba Kareem, ba zan iya ba”

“Safeena na san muna son juna amman...”

“Ba zan zubar ba Kareem ka daina magiya...”

Ya tsaya yana kallonta da mamaki.

“Shi ke nan ki aje cikin, ni kuma zan tsinke duk wata alaka tsakanina da ke”

Yana furta haka ya nufi kofar fita falon ransa a bace.

“Kana wasa da mace Kareem”

Ta fada masa cikin fushi sai ya juyo ya kalleta.

“Ke kuma kina wasa da rayuwarki...”

Ya juya Fuuu ya fice daga falon ya barta tsaye cike da mamaki.


NOOR POV.

Sai da Yaya ya fara aje ledodi sannan ya ciro dubu goma cif ya mikawa Baba.

“Gashi yace a siya mata magana”

Baba ya karbi kudin da sauri ya kirga sannan ya saka aljihu ya mike tsaye be kula abun da ke cikin ledodin ba yayi ficewarsa ba tare da ya ba ni ko sisi ba, balle kuma Mama. Da kadan yake jira tace yayi rufeta da masifa, ni kam ban yi hanzarin tana komai ba har sai da na dan jira na ji ko Yaya zai yi fada amman ga dukan alamu damuwa ta hana shi cewa komai. Hana ta janyo ledodin da fara budewa daman tuni kamshi ya kara cika mana hanci.

“Nidai bari na bude idan ba za ku bude ba”

Na kai hannu na taba leda daya sai Mama ta buge min hannu, ina kokarin juyowa na kalleta ta dauke ni da mari har sai da yatsanta ya fada min ido, zan yi ihu ta rufe ni da duka iyakar karfinta.

“Shiyasa ubanki kullum yake kuka dake, halinki ya fara isata, na gaji da ke Noor na gaji da halinki sakaryar yarinya dakikiya marar hankali da bata san ciwon kanta ba, yar iska gantalalliya, kullum haka kike ke babu ranar da za ki gayu”

Daker Yaya ya kawace a hannun Mama ina kuka sosai. Ba zan iya fadar dalilinta na duka ba, iyakar abun da zan iya shaida shi ne ranta a bace yake tun shigowata har zamana, wata kila Baba ne yayi mata ba daidai ba, dalilina ko kuma wani abun ne ya faru kamin dawowata.

“Babu abun da zaki ci a cikin nan, wannan Mugun kwadayin da rawar kai sai ya zama ajalinki matukar baki daina ba, yar iskar yarinya da bata gudun abun magana”

Na mike tsaye ina kuka har bada iya gani saboda hawayen da suka min zuba. Ji nayi an kwashe min kafafuwa na fadi kasa ribbbb gurin da na ji rauni a dazun ya sake buguwa har na yanzu ya fi na dazun radadi da zurfi.

“Mama dan Allah ki yi hakuri, ki yi hakuri Mama dan Allah ki yafe mata”

Shi ne abun da na ji Hana na fada Yaya kuma yana rikon Mama.


Follow the KHADEEJA CANDY channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01

*Duk mai son ya rika samun Littafin TA KI ZAMAN AURE yayi following wannan Channel din mai suna KHADEEJA CANDY a nan zaku rika samu duka littafaina in Sha Allah*


✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫 -6


Duka sosai Mama tayi min tun tana dukana tana zagina har ta kai tana dukana tana kuka kamar yadda nake kuka. Hana ma kuka take saboda ta ga ina kuka daman haka take duk fitinarmu da ita idan wani abu ya bata min rai ko ya saka ni kuka ita tana shiga damuwa sosai, wani lokacin har ta kan fi ni ma saboda Mama tana cewa ni ban san ciwon kaina ba, sai dai wani ya sanin min. Na rarrafa na tashi zaune ina jin tsiyayar ruwan da na tabbatar na jini ne a kaina.

“Mama yanzu me ye amfanin haka? Gashi yanzu kin ji mata rauni a raunin da ta ji, yanzu kuma a koma jinya ana neman na magani Baba kuma ba badawa zai yi ba kin san tun da kudin nan suka kai hannunsa ba zai bada su ba, kuma halin nan ba dainawa zata yi miye amfanin dukan?”

Bana ganin fuskar kowa saboda kuka, sai dai zan iya shaidar muryar Yaya Nabil ne mai maganar cikin yanayin damuwa.

“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”

Shi ne abun da nake ta jin Mama na maimaita cikin kuka, na dai na samu na isa bakin kofar dakinmu da rarrafe, na shige ciki na kwanta. Daga lokacin da na kwanta sai kukan ya tsaya min daman can Allah be yi da son kuka ba, ba komai ke saka ni kuka na dade ba, sai dai na bar abu a cikin zuciyata idan na tuna ya kuna min rai, shi ma kuma da zarar na samu wani abu da zai dauke min hankali a take zan manta sai idan an bude sabon shafi kuma.

“Jinin ya tsaya?”

Na ji muryar Yaya Nabil sai na tashi zaune na kai hannu na taba gurin har lokacin zafi yake min sosai, kuma jinin yana zuba sai dai ba kamar dazun ba.

“Rashin jin magana ke ja miki shiga matsala Noor, ke babu ranar da zaki yi hankali? Kuma kin san idan kika aikata wani abu laifin a gurin Mama yake komawa, fitar nan da kika yi babu kalar fadan da Baba be yi ma Mama ba saboda ta barki kin fita, na dawo gida na tarar baki gidan sai wani sabon fada ya tashi”

“Ka ce Mama ta yi hakuri ba zan sake ba”

Shi ne akwai abun da na ji zan iya fada, domin ni na janyowa kaina matsala da kaina, kuma Mama ta yi gaskiya kwadayina ne sila. Yaya Nabil ya fita daga dakin be jimawa ya dawo rike da maganin ciwon kai ya mika min.

“Ki Sha biyu idan jinin be tsaya ba anjima sai mu tafi gurin Saminu ya sake gyara miki gurin, ni ma gashi kina son ki zama silar korata daga aiki, Allah kadai ya san me kika masa da yace na zauna gida na kwana biyu”

Na san fadar gaskiyar zai sake jefani a matsala ne, dan haka na zabi shiru daman hausawa sun ce shiru ya fi yawan magana alheri. Ina cikin dakin ban fito ba sai da aka yi sallah magariba, a lokacin jinin ya daina min zuba, dan haka na nemi tsumma na gyara gaban kaina na goge jinin na saka wani kyalle na daure gurin sannan na fito na nufi gurin da buta take na dauka na zuba ruwa na yi alwala. Ina ganin ledodin Kareem Restaurant a tsakar gidan na san Mama sun cinye komai, hakan kuma ba karamin koma min rai yayi ba, ashe wahalar banza na sha ba zan ci komai a ciki ba. Da hawaye na gama alwala na mike tsaye kenan Hana ta fito daga bandaki rike da buta, Mama kuma tana dakinta tana sallah.

“Mama ta rantse ba zaki ci ba, shiyasa ban shiga da shi dakinmu na ci a dakin Mama”

Na kalleta cikin yanayi na rashin jindadi dake bayyana har a muryata na ce.

“Kun cinye duka kuma?”

Ta daga min kai.

“Mama ta miki haka ne saboda karki sake aikatawa gobe, dan Allah ki daina abun da kike Noor, dan Allah ki daina”

“Ba roka na yi ba, shi ya ba ni ku tambayi Yaya idan ba ku yarda ba, Hana har da yar tsutsar kun cinye?”

“Aa zubarwa aka yi, waye zai ci tsutsa idan ba ke da abinki ba Noor, abun kyama”

Ban sake ce mata komai ba na nufi dakinmu na shimfida dankwalina na saka hijab na fara sallah idan na yi sujuda sai na kai gefen goshina a kasa saboda rabin ciwon yake min. Ina gama sallah yaro ya shigo yana sallama, ina jin Mama ta amsa masa.

“Wai Zafeer yana sallama da Noor”

“Ka ce gata nan zuwa”

Yaron ya juya ya fita, shiru ban ji Mama tace na tashi na tafi ba, na san kuma Zafeer ba tafiya zai yi ba sai ya gan ni, ko kuma idan an fada masa ba zan samu fitowa ba. Dan haka na mike tsaye na fice daga dakin na isa bakin kofar dakin Mama na tsaya daga bakin kofa na fara da bata hakuri.

“Mama ki yi hakuri, ba zan sake ba”

Ta yi kamar bata ji ba.

“Na tafi gurin kiran da Zafeer yake min?”

Na tambaya a kokarin na zama yarinyar kirki.

“Idan kika tashin fitsararki umarnina kike nema? Yar iskar yarinya marar mutunci”

Daga jin wannan kalama na san Mama bata gama sauka daga fushin nan ba. Sululu na fice daga gidan kamar macijiya, ina fita waje na samu Zafeer tsaye yana danna wayarsa, kamin na karasa gurin da yake tsaye na fashe masa da kuka a take ya dago kai da sauri ya kalleni hankalinsa a tashe.

“Me ya faru Baby Noor waya taba ki?”

Ya kunna fitilar wayarsa ya haska fuskata.

“Subhanallahi me ya same ki waya fasa miki kai? Me kika yi Noor who did this to you? Who touch my Babeee”

Tambayata yake hankalinsa a tashe zuciyarsa na cika, ban yi mamaki ba domin ya saba fusata a duk lokacin da aka taba ni.

“Waya miki wannan duka Noor fada min mana...”

Cikin kuka na fada masa abun da ya faru tun daga irin karyar da Kareem yayi ma su Mama cewar mota ce ta buge ni, har zuwa dukan da Mama ta yi min.

“Kuma sun cinye duka naman ba su ba ni komai ba, ko yar tsutsar nan da na so na ci ba su ba ni sun zubar”

Juya baya yayi yanayin fuskarsa ya sauya kamar zai fashe da kuka, ya jingina da ginin gidanmu ya kife kansa. Kamin ya dago ya kalleni.

“Iyeyenki kadai suka kai su yi miki haka Noor, su kadai ne suka da ikon dukanki su fitar miki da jini haka kuma na kyale su, Allah ya daran talauci Noor, ba dan shi ba da yanzu na aureki da yanzu karkashina kike rayuwa, wani abu duk ba zai faru ba”

“Sun cinye komai har tsutsar nan irin wadda masu kudi suke ci, na so na ci na ji me ake ji”

“Ana zancen rauninki kina zancen tsutsa, idan kin ci me zaki ji?”

“Na ji abun da suke ci mana, har kai na dauko maka naka fa, ai kasan komai na samu sai na kawo maka”

Na fada cikin kuka.

“Ni dai dan Allah ki daina daukar komai kike gani ki saka a bakin nan Noor, wani abun da kike ganin masu kudi suna ci, masu kudin nan ba dukansu ne suka da hankali ba, komai kika samu ki ta kaiwa bakin nan na ki kuma idan mun yi aure....”

Na share hawayena na kalleshi.

“Me? Kawai ba ina son na ji yadda ake ji ba ne, yanzu ai ba zan sake samu ba”

“Yanzu dai shiga cikin gida ki fadawa Mama zan kaiki a duba raunin nan”

Na juya sai ya kira ni na dawo. Ya haska fuskata ya saka rigarsa ya goge min hawayen da kyau.

“Kar ki shiga kuma tace kin min kuka ta miki fada”

Na dauke kai na koma cikin gidan na tsaya daga jikin kofar dakinta na sanar mata.

“A dawo lafiya”

Ita ce amsar da ta ba ni, sai na juyo ya dawo na fada masa muka kama hanyar titi ni da shi. Muna tafiya yana kallona har muka isa na zauna a kujera mai shagon ya bude ciwon ya sake wanke min ya sake rufewa ina kuka saboda zafi, Zafeer kuma yana rarrashina kamar wata jaririya.

“Ya isa ya isa shikenan an gama daga wannan, ka yi mata a hankali, da zafi fa”

Bayan ya gama ya bani maganin ciwon kai da na rage radadi. Sannan Zafeer ya biya shi muka taso muka kamo hanyar gida.

“Me kike son na siya miki?”

“Kana da kudi?”

“Ina da dubu uku fada min abun da kike so na siya miki, kin ce Mama bata baki komai ba ko?”

Na daga kai.

“Eh amman ka aje kudin ba kudin aure muke tarawa ba?”

“Idan ana tara kudin aure sai aki cin dadi? Jira ni a nan zan je na dawo”

“Toh”

Duk maganar da nake masa cikin shagwaba nake masa, daman can haka al'adarta take magana cikin shagwaba kamar wata wadda ta tashi a cikin gata, balle kuma na kai ga wadda ke shagwaba ni. Ta inda ya bar ni akwai hudu kasancewar unguwar babu wuta yau, babu wadda zai shaidi ni ce har ya je yayi siyayyar da zai yi ya dawo. Nama ya siyo min saboda ya san halina da son nama kamar kura, sai kayan marmari a dayar ledar dayar wadanda suka hada da Apple biyu sai ayaba da lemu da kankana, dayar ledar kuma cake ne irin kananan da ake saidawa 150 guda daya, ya siyo min guda hudu da kunun aya.

“Na gode sosai Zafeer”

Na fada ina jindadi sosai gaba daya ya wanke min kwadayi da bacin ran dake tare da ni.

“Anything for my Baby Noor, idan Mama tace fada min kika yi abun da ya faru, ki ce aa daman na zo da siyayyar tun kamin mu tafi”

“Toh”

Na amsa sannan na jera da shi muka kama hanya, muna tafe muna hira har muka iso gida.

“Ni zan tafi, yau babu hira saboda baki da lafiya, sai dai gobe idan na dawo, amman Noor ki daina bijirewa maganar iyayenki, duk abin da kika san zai saka Mama ta dukeki ko Baba ki daina kin ci? Kuma ki yi ta mana Addu'A Allah ya bude mana kofofi na samu karasa gidan da nake na hada komai a bani ke ki huta nima na huta”

“Okay, toh... Zafeer ina sonka sosai sosai sosai”

Yayi murmushi yana kallona cikin hasken farin wata.

“Ina sonki ninki yadda kike so na Noor, ke tawa ce har abada, we mean to be akwai wani bend a tsakaninmu da babu wadda zai iya karya shi i love you so much”

Magana yake min a hankali cikin sanyin murya da kwantar da kai kamar mai son na fahimta ko na haddace. Kamin ya juya ya duba ya ga babu mai ganinmu ya sumbanci goshina sannan yayi baya da sauri ya daga min hannu yana min bye bye. Ni ma na mayar masa sannan na shiga gida raina fess har na manta da komai, dakin Mama na fara shiga da murna ta sai kuwa na yi sa'a ina taka kafata wutar nepa na kawowa. Ba zube ledodin a gabanta da far'ata.

“Mama gashi Zafeer ya siyo min”

Wani banzan kallo da Mama ta watsa min ya saka annurin dake fuskata gushewa.

“Fada masa kike yi abun da ya faru yaje yayi miki siyayya?”

“Aa ban fada masa ba, na fada masa dai na ji ciwo ne saboda mota ta buge ni, daman ya zo da siyayyar kamin mu tafi na aje a zaure ne”

“Je ki ci ni wadda na ci dazun ya wadatar da ni”

Ta fada tana cigaba da jan carbinta, fadar hakan kuma sai ya saka na ji wani iri na ji komai ya fita a raina.

“Mama dan Allah ki ci”

Ta juyo ta kalleni sannan ta kai hannu ta bude ledodin ta bude ayaba ta dauki daya ta bude ta ci.

“Allah ya shirya ki, Allah ya yaye min wannan bakinciki na ki”

Ta fada idonta na cika da hawaye, ban san me zance dan haka na dauke ledodin na fice daga dakin. Hana ma kadan ta dauka saboda ta ci na dazu, na cire leda daya na ajewa Yaya nashi, daman shi Baba be cika maida hankali a irin wannan ba ko ba shi aka yi zai iya cewa baya ci ma.
Na ci komai sannan na dauki na yaya na kai masa dakinsa na dawo na yi sallah Isha'i na kwanta. Ban farka ba sai washe gari ana kiran sallah Asuba.

Kamar kullum Hana ta hada abun karyawa sannan ta wuce makaranta, ni kuma na fita na fara dibar ruwa daga fanfo ina kawowa cikin gida, Yaya ne yake yi sai dai a duk ranar da yake da makaranta baya diban ruwan ni nake yi saboda ni ce mai zaman banza. Bayan na gama na dauki tsintsiya na share ko'ina na shiga na yi wanka na dauki tufafin Hana na saka, ina fitowa Mama ta rufe ni da fada.

“A haka zaki kare saboda baki san ciwon kanki ba, wuce ki cire mata kaya”

“Nawa sun yi datti Mama”

“Ki saka haka, ko kuma ki daura zane ki dauko tufafin ki wanke, har na islamiyarku ki wanke dan yau sai kin je makaranta”

Na juya na koma cikin rashin jindadi na cire tufafi na dauki zane na daura na ciro uniform din da kala biyu na fito waje na wanke na shanya. Na koma daki na zauna, ina jin lokacin da yaro ya shigo yace Zafeer yana sallama da ni. Katon Hijab na nema na saka saboda zane ne a jikina nan ma ban tsira ba ina fitowa Mama ta fara halbina da kalamai marasa dadi.

“Ai dole ki zuba katon hijab saboda baki da tufafi, ke kan kin ji haushin rayuwa, wannan Zafeer din zai daukarwa kansa aiki, Allah yasa ma zai iya zama da ke, domin dai babu namijin da zai iya zama da mace irinki, matukar baki sauya hali ba zaman aure sai ya miki wuya Nooriyya”

Ni dai ban ce komai ba na fice daga gidan, sai na same shi a waje tsaye yana jiran fitowa.

“Baby Noor ya jikin?”

Na masa dariya a yayinda yake min murmushi.

“Na ji sauki, har na yi wanki na yi diban ruwa”

Ya kalleni kamar zai ce wani abu sai kuma yayi shiru.

“Mama ta miki fada jiya?”

“Aa ban fada mata gaskiya ba, yadda ka fada haka na ce mata”

“Shikenan ki shiga ciki ni zan wuce makaranta yanzu, yau zamu zana jarabarmu ta karshe ki min addu'a Allah ya ba ni sa'a”

“Allah ya baka sa'a Allah yasa ka fito da results mai kyau”

“Ameen i love you”

“I love you too”

Yayi min bye bye Ni ma na masa sannan ya wuce, ni kuma na koma cikin gidan. Kamar yadda Mama ta fada sai na tafi makaranta lokaci na yi na shirya cikin uniform dina kuka ne kawai ban yi ba amman bana son zuwa makaranta ko kadan, ina saka uniform Hana na tsokanata wai yau ni nice zan tafi makaranta za'ayi ruwa bla bla ne dai ban kulata ba, Mama ta zuba mana kwadon kanzo muka ci, Hana ya raga na hade da nata na cinye sannan na sha ruwa muka kama hanya.

“Ni da zaki taimaka min ma ba zan tafi ba, sai na tafi bikin Salwa yau ne za'ayi na karshe fa, kuma jiya ban tafi ba, na san idan na yi ma mama magana zata min fada shiyasa ban yi ba”

“Da rauni a kai zaki tafi biki kamar Bikin dole? Yanzu duk fadan da aka miki jiya be shige ki ba, sai wani zancen bikin kike Noor kin shiga uku”

“Ni ban shiga uku ba, ke kika shiga uku”

Na rama, sannan muka cigaba da tafiyar, cikin rashin jidadi na isa Islamiyar, kowa mamakin ganina yake kusan tun da na yi sauka sai dai na leko makarantar na koma bana wani zuwa. Har Malaminsu sai da tsokani ne wai ya ga ana hada hadari a gari ashe ni ce zan shigo makarantar. Ni dai ban kula su ba, na bude littafaina aka fara zuba min karatu kamar ba gobe, shiyasa malamaina suke yawan yabani suna cewa da zan natsu na yi karatu ba karamin amfanina za aci ba, kuma ni ma zan ci amfamin ilimina domin ina da fahimta sosai ina da basirar haddace abu, kuma komai aka fada min bana mantawa, natsuwa ce kawai da jin magana suke ganin kamar bani da ita, nikam ina ganin natsuwata suke dai suke ganin haka. Kowa ya tambaya me ya same ni a kai cewa nake mota ta kade ni.
Misalin karfe biyar aka fara haramar tafiya duba Malam Sule mai bin babban malaminsu kusan komai da ya shafi makaranta shi yake yi, ashe ba shi da lafiya wai kariya ya samu sati biyu, ni ban sani ba sai yanzu, saboda bana zuwa karanta duk wani abu da ya shafi makaranta bani da labarinsa.

Malam Babba ne ya dauki nauyin duka Napep din da muka hau, mu biyar muka matse a Napep daya zuwa unguwar da Malamin yake, muna isa muka shiga cikin gidan muka gaishe shi, muna waje wata Hajiya ta shigo da manyan ledodi Kareem Restaurant ta aje sannan ta rage tsawo ta gaisa da Malamin. Ni kuma na kira Hana dake can gefe na nuna mata Ledodin.

Ta kalla sai ta yi dariya ni ma na yi dariya, sai dai kamar hakan be yi ma Matar dadi ba, ko kuma dai tana cikin fushi ne take son hausakewa a kanmu oho a take ta hau fada.

“Ledodin Kareem kun san abun da ke ciki? Ko kuma kun raina abun da na kawo ne? Wane irin abu ne wannan?”

Malam Babba ya kalleta.

“Hajiya Lafiya?”

“Ga yarinyar da ta kira dayar can ta nuna mata ledodin da ba kawo, ban san manufarta na yin haka ba”

Malam Babba ya juyo ya kalleni.

“Nooriyya me ya faru”

“Jiya ne mai Restaurant din ya zo da kanshi ba aike ba, har gida ya kawo mana kayan dadi, shi ne na kira Hana na nuna mata ledar ina nufin ta kalli wannan daga can ya fito shi ne wai ta fara bala'i ita masifaffiya, Wallahi na fiki bala'i ni har na siyarwa ina da, daga magana zaki fara fada kamar an miki wani laifi”

Na mayar amsa ina murguda mata baki, kuma na fada mata shi ya zo da kansa saboda ta san muna da matsayi muma.

“Oh ai ban dauka haka ne ba, na dauka wata maganar ce ya dabam, yi hakuri”

Na yi zaton haushi zata ji sai na ga ta maida abun na dariya ta saki fuska ta sauko wata ta fahimci ni ma muna da matsayi, ba dan ma muna cikin yan makarantar mu kuma kowa ya san Zafeer zan aura da sai na yi mata karya na ce saurayina ne. Sai dai wani abun da ban gane kansa ba shi ne kallona take har ta gama gaisawa da Malam Sule ta mike tsaye idonta a kaina yake. Gabatar da ita da Malam Sule yayi a gurin Malam Babba ne muka ji cewar ita ce silar ciwonsa saboda kade shi da ta yi da mota.

“Malam dan Allah ba ni aron dalibar ka zan yi magana da ita”

Ta nuna ni, ni kam abun nema ya samu daman so nake na nuna mata karyar arziki take da kurin banza na ga mai arzikin da be dauki kansa wata tsiya ba, ba kamar ita ba daga magana ta fara ruwan masifa. Malam ya juyo ya kalleni.

“Allah yasa dai ba wata matsala ba ce?”

“Babu wata matsala Wallahi tambayarta kawai zan yi”

Ta amsa fuska a sake. Malam yayi min izini da na tafi sai na mike tsaye na isa gurinta, sai ji na yi ta dafa kafadata muka fita tare bata min magana ba sai da muka isa waje, gaban motar da nake kyautata zaton ta, ta ce muka tsaya tana murmushi ta ce

“Ya sunanki?”

“Noor”

Na amsa a takaice.

“Shi Kareem din mai Kareem Restaurant Saurayinki ne? Ko dan'uwanki”

Jimmmm na dan yi ina tunanin na zaba sakanin saurayi da dan'uwa, idan na ce mata dan'uwa zata san ina da muhimmanci amman Saurayi zai fi karamin kwarjini a idonta dan haka na amsa da.

“Saurayina ne, me yasa kika tambaya?”

Ya sauke ajiyar zuciya da alama jin haka be mata dadi ba.

“Kawai na tambaya ne, saboda ina yawam siyen abinci a restaurant din, kuma a yadda na ji shi Kareem din kwararen likita ne mai duba mutane, na so na samu maganinshi tun da dadewa amman ban samu haka ba, saboda masu aikinsa basa bari na ganshi kuma asibitin idan naje bana samun na duba ni, shiyasa yanzu da na ji kin ce kin san shi na ji dadi kuma har na nemi magana dake private”

“To me zan yi miki?”

Gabana ya fara faduwa karta roki na yi mata alfarmar da ba ni da halin yinta.

“So nake ki hada ni da shi dan Allah”

“Aa gaskiya shi baya son haka”

“Taimaka min zaki yi ina cikin matsala ne, ina fama da wani ciwo ne na kansa a ciki, kuma ance idan har na samu ganinsa ya rubuta min magani zan samu lafiya, dan Allah ki taimaka min kinji kanwata, ni zan ma iya biyanki”

“Aa gaskiya, ni yanzu ganin Malaminmu muka zo, gidanmu idan aka ji za'ayi min fada”

“To karya kike yi ba saurayinki ba ne kenan?”

Na fara saurin kare kaina.

“Aa da gaske ne mana”

“To ki nuna min, indai har da gaske ne, ki kai ni gurinsa”

“Toh ai yanzu baya gida”

“Eh yana restaurant dinsa, daman ance idan Yamma ta yi restaurant dinsa yake zama, idan kin yarda ga mota nan mu tafi yanzu, ga mota nan sai mu shiga, ni zan ma biyaki zan baki ko nawa kike so, ni dai ke hada ni da shi kawai na yi magana ne burina”

Na yi shiru ina nazari na bita ko kuma dai na ki tafiyar, idan kuma na ki tafiyar zata karyata ni, idan kuma na tafi ba lallai ne nima su bar ni na ganshi ba.

“Mu tafi? Dan Allah ki taimaka min, sai magiya nake miki kamar ba musulma ba? Ke baki da tausayi ne a zuciyarki?”

Na kalleta, bata yi kama da mayaudara ba balle na ce karya take, kuma yadda ta marairaice murya nan sai na dan ji tausayinta.

“Ba zamu dade ba?”

“Ba zamu dade ba, kina hada mu zan baki kudin Napep ki dawo sai ki bar mu a can”

“Toh”

Ta bude min mota na shiga sannan ta shiga, ni dai zan taimaka mata ne saboda ta nuna tana cikin damuwa, ba wai dan kar na karyata kaina kawai ba. Har muka isa Restaurant din wata kalma bata shiga tsakanina da ita ba. Na bude motar na fita ita ma ta fito bayan ta saka mask kuma ta maida mayafin dake wuyanta zuwa saman kanta. Gabana na faduwa muka doshi reception din ina ta sake saken kar na ga Yaya duk da na san by this time ya wuce gida domin karfe shida ta yi. Me zan fadawa ma'aikatan su bar ni na shiga ciki shi ne abun da ya tsaya min a rai, idan ma sun bar ni ban san a ina Office dinsa yake ba.

Ta inda na yi sa'a na samu abokin Yaya da duty a gurin kuma ya san ni farin sani, hakan ya taimaka min gurin fada masa ya shiga ciki ya fadawa Dr Kareem Noor ce take son magana da shi.. Babu jimawa ya dawo sai ya ce Dr Kareem din ya ce a shigo da ni ciki, dadin dake cikin raina baya misaltuwa haka na wuce gaba matar da ban san sunanta ba tana bayana abokin Yaya kuma yana gaba har muka isa office din sannan ya nuna min kofar ya juya ya koma. Na juyo na kalli matar dake jan numfashi da karfi tana fitarta wata kila saboda ciwo ne oho dai, na yi murmushi na juya na kai hannu na murda kofar na bude na shiga ciki.

“Noor... Lafi...”

Be karasa ba yayi shiru yana kallon gefena, matar dake bayana tana shigowa wani mutum dake zaune tare da Kareem din da ban san waye ba ya kalleni yana murmushi ya ce.

“Noor Amaryarmu!!!”

Na kalleshi da sauri ina mamakin jin furucinsa kamar wadda ya san karyar da na shiryo. Kareem din ma kallonsa yayi tare dake bayana kuma na ji ta sauke numfashi da karfi ta juya. Ni kuwa na kai hannu na taba ta wai na fada mata ga Dr Kareem din nan, sai jin na yi ta kama hannun ta murde tana kokarin karyawa.

“Safeena...”

Na ji Dr Kareem ya kira sunan da karfi sannan ya nufo inda muke yana kokarin kwace ni a hannunta...


__________________________

Domin samun littafaina akan kari, ku yi following din Channel dina mai suna KHADEEJA CANDY za su samu TA KI ZAMAN AURE daga farko har zuwa inda ake, kuma a can zan rika posting duka littafaina In Sha Allah.


Amman kamin nan ku fada min wane Team kuke.

Team Kareem
Ko
Team Zafeer

Anya kuna ganin Kareem yayi ma kansa adalci kuwa? Mu'alama da matar aure mai yaya har uku?
Shin kuna ganin akwai Uba irin Baba kuwa? Babu dadi gurin matar gidan haka kuma babu gurin yayan gida?
Anya abun da Mama take yi ma Noor tana kyautawa kuwa?


Ku aje min ra'ayinku ni kuma na aje muku dogon shafi gobe idan Allah ya amince.


#KhadeejaCandy

Follow the KHADEEJA CANDY channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01

*Duk mai son ya rika samun Littafin TA KI ZAMAN AURE yayi following wannan Channel din mai suna KHADEEJA CANDY a nan zaku rika samu duka littafaina in Sha Allah*


✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫 -7


KAREEM POV.


Kareem yayi kanta da sauri ya rike Safeena yana kokarin kwatar hannun Noor da ihunta ya cika dakinta tana fadin hannunta.

“Safeena karki karya mata hannu”

Daker ya kwaci hannun Noor a hannunta ta murgude hannun har yayi yaushi, gaba daya Noor ta rude kamar wadda ta fita hayyacinta ta fadi kasa ido a zare tana haki.

“Kin fita daga hayyacinki ne? Me ke damunki?”

Kareem ya tambaya cikin tsawa kamin ya juya ya rika ya kai hannu zai taba hannun Noor sai ta juyar da shi dayan gefe.

“Ya karye Azzaluma yar masan wuta ta karyashi”

Noor ta fada cikin kuka. Kareem ya shiga mata magana a hankali cikin rarrashi yana kokarin rika hannun ya duba.

“Be karye ba, kawo na gani”

Wani hawaye mai zafi ya saukowa Safeena, zafin da take ji a zuciyarta ya fi wadda Noor take ji a hannunta. Duk abun da ake Hafiz na zaune yana kallo be ce kuma be yi yunkurin yin wani abu ba, sai a lokacin da ya ga hawaye ya sauko a idon Safeena.

“Tirr da ke, tirr da uwa irinki... Tir da mata irinki... Tir da haihuwar ya irinki, tir da auren mace irinki, indai har sabon Allah ya kai ya rufe miki ido ki kama hannun wata ki murde saboda kishi, A gaban idona to kin yi hasara kuma kin cika tantiriyar yar iska, kuma haka da kika yi ba zai hana Kareem auren yarinyar nan, albashi sai ki hade zuciya ki mutu”

Ta dauke idonta daga barin kallon Noor ta kalli Hafiz, kamin ta kai hannu ta taba hawayen da bata san da saukarsu ba sai a lokacin, ta yi murmushi ta dubi Kareem dake fadin.

“Babu komai tsakanina da Noor, wace magana kake haka? And ka cire bakinka daga magana da ita, babu ruwanka idan zaka yi magana ka yi da ni ba da ita ba, ba ka da wannan hurumin”

Dauke kai Safeena ta yi ta juya ta fice daga office din. Kareem ya kalleshi cikin damuwa ya ce.

“Akan me zaka fadi wannan maganar? Zata dauka da gaske ne, Safeena tana da mugu mugun kishi, baka san abun da zai je ya dawo ba”

Hafiz ya wulga masa wani wulakantaccen kallo. Har zai yi magana sai kuma ya juya ya kalli Noor da ta cire hijabi saboda wani azabar zafi da take jin ya game jikinta gaba daya sai kuka, Kareem ya ci albakarcin Noor tana gurin ba dan haka ba, Hafiz zai fada masa magana ne marar dadi, sai dai baya son Noor ta san komai dan haka yayi shiru. Kareem ya juya ya kalli Noor sannan ya nufi gurin da keys dinsa suke ya dauka, ya nufi inda take.

“Taso mu tafi asibiti zan duba miki a can”

Noor ta girgiza kai tana jin wani irin azaba a hannu.

“Aa a barshi haka, gyaran akwai zafi ni taimakonta kawai na yi, me yasa zata min haka? Miye laifina ni?”

Kareem din take tambaya tana kuka sai gumi take. Kareem yayi shiru yana kallonta cike da tausayawa ya rasa me zai ce.

“Mamana bata san na zo nan ba, jiya sai da ta yi min duka sai da kaina ya fashe saboda kai, bata bar ni na ci komai da na tafi da shi ba, yau kuma wata ta karya min hannu saboda kai, kuma na san Mama sai ta min duka ko Baba, na san haka zata min ba zan biyota na zo ba”

Tausayinta ya kama shi. Ya sake mika hannu ya rika hannun ta kauce tana kokarin mikewa tsaye.

“Be karye ba Noor, duba kawai zan yi sai na baki magani, idan akwai zafi ba zan taba ba na miki alkwari”

Ta kalleshi.

“Rantse”

Ya daga hannunsa.

“Na rantse”

“Ce ka rantse ba zaka taba min ba idan akwai zafi”

“Na rantse ba zan taba miki ba idan akwai zafi”

“Ce Wallahi Wallahi ba zaka taba ba idan akwai zafi”

“Wallahi Wallahi ba zan taba ba idan akwai zafi”

Ya rantse kamar yadda ta bukata sannan ta yarda, ya dauki Hijabinta zai saka, sannan ya nufi kofa ya bude mata, ta fita tana kuka, a yar fahimtar da yayi mata daga jiya zuwa yau ya san ba lallai ne yace ta yi shiru ta yarda ta yi shirun ba, balle yace ta hakura da kuka saboda hankalin mutane dake karkatowa izuwa garesu a duk inda suka wuce. Ya riga isa gurin motar ya bude motar ta shiga ya rufe sannan ya zagaya ya shiga bangarensa ya tashi motar.
Har suka isa asibitin kuka Noor take domin a tunaninta hannunta ya samu kariya ne. Wannan karon be shiga da ita office dinsa ba ya tsaya da ita a gurin da ake duba marasa lafiya kamar kowa. Ya nade hijabin ya kalli hannu yana son ya taba yana tsoron tsare da ido da ta yi.

“Har yanzu akwai zafi?”

“Eh mana, kana ganin hannun ya karkace ba”

“Kashin ne ya bar gurinsa, amman ba kariya ba ce”

“Wallahi Wallahi da ace ni mai gata ce sai na yi shari'a da matar nan, amman na barta da Allah Allah ya isar min, Allah yasa ciwon jikinta kar ya warke har abada”

Kareem dai be ce mata komai ba sai kallonta yake kamin ya mike tsaye ya bar gurin. Be yi minti goma da tafi ba wata likitar ta zo ta duka tana duba hannun Noor.

“Ta so muje”

Noor ta mike tsaye ta bi bayanta suka shiga bani dakin jinya, a nan suka samu Dr Kareem ya sanya safar hannu yana aje wasu kwalabe a saman karamin teburi. Da kai Dr Kareem yayi ma likitar da ta shigo da ita magana da ma wadda ta shigo bayanta. Sai da ta bari Noor ta zauna sannan dayar ta kama hannun ta rike gam, Noor ta kalli Kareem da sauri.

“Kace ba zaka taba ba”

Ya daga hannunsa sama ya cire safar ya juya yayi ficewarsa daga dakin. Be dawo ba sai da aka gama komai, Noor ta yi kuka har ta galabaita.

“Sannu...”

Ta kalleshi kurun tana hawaye, shi kuma ya kalli bandajen dake kanta sai a lokacin ya lura da ba wadda ya saka mata ba ne a jiya.

“Waya canja miki wannan?”

Ta yi shiru tana haye yawu kamin ta fara kokarin sauka kam gadon.

“Ina saki je?”

“Gida”

Ta amsa tare da fara takawa tana rike da hannun da aka daure mata.

“Okay zan kaiki gida, amman me zamu je ce? Ko dai mu kira Yayanki ya zo asibitin nan?”

Ta girgiza kai da sauri.

“To me zan fadawa Iyayenki?”

Ta girgiza kai.

“Kira min Zafeer”

“Waye Zafeer?”

“Shi ne wadda zan aura”

“To zo ki zauna”

“Bana son asibitin nan bana sonta”

Ta fashe da kuka.

“Shi kenan, muje na kira shi a mota sai ya same mu a restaurant haka ya miki?”

Ta daga kai, sai ya nufi kofar ya bude mata ta fita sannan ya fita. Har suka isa gurin motar tana rike da hannunta kamar wadda ke dauke da jariri. Sai da ya fara tukin sannan ya kalleta a hankali cike da tausayawa ya ce.

“Noor ina kika hadu da wannan matar?”

Ta bashi labari cikin kuka. Sai yayi mata wata tambaya da ya saka ta watsa masa harara.

“So na kike yi?”

Ta hada masa da kwafa.

“Toh why do you lie me yasa kika mata karya?”

“Kaddara da rabon sha wahala, ashe ma ta sanka ita din budurwar ka ce?”

Yayi shiru be amsa mata ba ya dauke kai ya cigaba da tukinsa.

“Ina ta sanka?”

“Ba kin ba ni shawara kara aure ba?”

Ya fada yana kokarin kawar da maganarta.

“Wallahi karka aureta, zata hadu da wacan matar ta ka su yi ta maka hauka”

Yayi murmushi sannan ya dauki wayarsa ya mika mata.

“Saka number saurayin”
Ta karba tana kallon yadda wayar ta cika mata ido.

“Me yasa Mama ta dake ki? Gaskiya kika fada mata?”

“Aa bata fada min laifina ba, wata kila ta dauka ko na roke ka ne”

Ya kalleta.

“Duk abun da kika zaba jiya baki ci komai ba?”

Ta daga masa kai tana kokarin kai wayar a kunnenta.

“Ni zan yi magana da shi”

Ya karba ya kara wayar a kunnesa.

“Wa'alaikusalam ina magana da Zafeer ne”

“Eh wake magana?”

“Sunana Kareem, kuma ina tare da Noor yanzu haka, sai dai ba wata matsala ba ce ta ji ciwo ne a hannu shi ma ba sosai ba, tace a kiraka ka zo ka tafi da ita gida”

A take hankalin Zafeer ya tashi.

“Subhanallahi garin yaya? Ina take tana lafita me ya same ta?”

“Ka kwantar da hankalinka da sauki ba sosai ba ne, gata ka yi magana da ita”

Ya mika mata wayar sai ta karba ta fara zuba masa shagwaba.

“Wata ce fa daga na taimake ta sai ya rike min hannu ta murde, sai da aka daure min aka gyara”

“Kina ina?”

“Ina cikin motar Kareem din, shi ne wadda ya kade ni jiya, gamu mun iso Restaurant dinsa ka zo ka tafi da ni gida, bana son ya kai ni kar Mama ta sake yin fada”

“Noor me ya kai ki gurinsa? Me yasa baki jin magana ke? Taya ma kika tafi gurin? Why Noor why?”

Ta yi shiru bata ce masa komai ba. Kareem na ganin yanayin fuskarta ya sauya ya mika hannu ya karbi wayar ba dan ya san me Zafeer din ya tambaye ta ba.

“Ka zo Kareem Restaurant ka dauke ta, idan ka zo kace a kawo ka office dina kai tsaye”

Ya kashe wayar.

“Jiya na so na kira Yayanki na ce ya jikinki, amman wata damuwa ta saka ni a gaba, na manta da komai”

Bayan ya karbe wayar yake fadar haka a daidai lokacin da ya faka a harabar.

“Kasan wannan matar ko?”

Ta aiko masa da tambayar da be san yadda zai sarrafa halshe ya amsa mata ita ba.

“Na ji ka fadi sunanta, ni ban ma san sunanta ba, budurwarka ce?”

Yayi shiru na tsawon lokaci yana kallon waje ta cikin gilashin motar.

“Aa”

“Tace min tana son ta ganka, mesa ta yi karya?”

“Ke me yasa kika yi karya? Already kina da wadda zaki aura akan wace hujja zaki yi karya?”

Ta yi shiru, sai ya bude motar ya fita ya rufe ya bar Noor a ciki, ya busar da iskar bakinsa ya rufe ido ya bude ya girgiza kai. Sai kuma ya bude motar ya dauko wayarsa ya rufe. Number Safeena yayi dialing ya kai a kunnensa. Wayar ta yi ringing har ta gaji bata daga ba. Ya sake cika bakinsa da iska ya koma cikin motar ya zauna.

“Noor karki sake yi ma wani karyar kin san ni, kuma ki daina bin motane any how ko kin san su ko baki san su ba”

Ta daga mishi kai a hankali cike da natsuwa.

“Kuma ki rika jin maganar iyayenki kin ji?”

Nan ma ta daga mishi kai.

“Ka yi hakuri, ba zan sake ba daga yau ba zaka sake ganina ba”

Ta fada tana hawaye sai kuma ya ji babu dadi.

“No ba wai bana son zuwanki ba ne, kawai bana son ki saka kanki a matsala ne, kin ga iyayenki suna miki duka da fada, kuma kin ga yanzu kin samu rauni saboda haka”

“Na fahimta...”

Ta amsa masa murya a sanyaye hakan sai ya kara masa raunin tausayinta dake zuciyarsa.

“Me kike son ki ci?”

Ta girgiza kai, ta bude motar ta fita.

Sai shi ma ya bude ya fita ya wuce gaba ta bi bayansa.


NOOR POV.

Babu kowa a office din, mutunen dazun da ban san waye ba yayi tafiyarsa. Kareem da kansa yaja min kujera na zauna sannan ya zauna a kujerar dake facing din tawa.

“Baki sha'awar cin komai? Ko kuma na miki takeaway”

Na girgiza masa kai, ji nake bana sha'awar komai nasa a yanzu.

“Noor”

Ya kira sunana a hankali a lokacin da na dago kai sai na tarar ni yake kallo.

“Kin sa na ji babu dadi, maganar da na yi ce ta bata miki rai?”

Nan ma na amsa masa da kai. Yanzu kam gaba daya hankalina ya koma gida gurin mahaifiya hukuncin da zan karba idan na koma shi ya tsaya min a rai.

“Ina tunanin gida ne, yau Mama sai ya sake karya min hannun babu wadda zai cece ni”

Na fada hawaye na sauko min, domin a lokacin ne na gane kuskuren da na aikata na biyo matar har nan.

“Ko zamu tafi tare da Saurayin na ki sai mu bata hakuri mu yi mata bayani? Bana son ta dake ki?”

Magana yake min kamar wadda ya damu da ni da gaske. Na girgiza masa kai ina kallon hannuna da aka daure.

“I'm sorry haka kaddara take wani lokaci, ba ma iya kauce mata”

“Ni kaddara ce marar kyau a gidanmu, shiyasa ni ce mai laifi kullum, shiyasa Babana...”

Na samu kaina da fadar haka, sai kuma na yi shiru domin be kamata na fadi ciwona a inda babu magani ba. Wani abun da ban yi zato ba, shi ne tashin hankalin da na gani a fuskar Kareem a lokacin da yake kallona, damuwa da tausayi sun bayyana karara a fuskarsa. Na sauke kaina kasa tare da saukowar ruwan hawaye.

“A duk lokacin da kika ji kina bukatar wani abu ki zo gurina kofata a bude take, ko gobe idan wani ya tambaye ki miye alakarmu ki fada masa abun da yayi daidai da ra'ayinki, karki ji haufi”

Ban ce masa komai ba, kuma ban dago ba hawaye kuma ba su fasa min zuba ba. Ta gilashin dake window na lura da Magariba ta yi saboda duhun da ya fara shigowa. Yunkuri yayi sai mike tsaye sai aka turo kofar office din aka shigo bayan ya kwankwasa.

“Ranka ya dade wai wani ne yake nemanka, sunanshi Zafeer”

“Shigo da shi”

Sai ya koma ya zauna da kyau bayan ya amsa, sannan ya kalleni.

“Share hawayenki kar ya ga kina kuka”

Na share hawayen na maida hankalina da dubana gurin kofar shigowa. Babu jimawa Zafeer ya shigo dakin yana kallon hannuna hankalinsa ya kara tashi.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihirraji'un Baby Noor me ya same ki?”

Na yi shiru wani sabon hawaye ya cika min ido ni da ban saba hawaye sosai ba. Kareem yana masa bayani amman Zafeer ko kallon inda yake be yi ba, da alama daga bakina yake son jin karin bayanin.

“Wata mata ce tace na kawo ta nan...”

Na fada masa gaskiyar yadda komai ya faru. Sai dai a yadda na lura gaskiyar tawa ta masa ɗaci domin kuwa rufe ni yayi da fada abun da be saba ba.

“Me yasa zaki yi haka? Wa kike son ki burge? Me kike nema a gurina da baki samu ba har zaki kwadayin wani ya zama saurayinki? Ita din me kika mata da zata ji Miki ciwo a hannu haka? Saboda me? Daga makaranta sai ki tsallake ki zo nan yanzu matar nan idan cin mutane take sai ta cinye ki”

Wani irin fada yake min da tsawa kamar ba Zafeer dina ba. Lallai na yarda ni sokuwa ce kuma an aikata babban laifi. Ta cikin ruwan hawaye na ke ganin Kareem ya mike tsaye yana fada.

“Haba Malam daga zuwanka sai ka rufe ta da fada, ta ki yarda na kaita gida saboda tana tsoron fada, tace a kiraka saboda tana tunanin zata samu sauki a gurinka sai kuma ka rufe da fada babu sauraren Uzuri, yarinya ce fa bata kai matsayin da kuke tunanin ta banbance daidai da akasin haka ba kuma babu wadda baya kuskure”

Zafeer ya kalleshi.

“Ai kai ka banbance daidai, tun da kana tsaye aka ji mata a hannun, sai yanzu zaka ce bana sauraren uzuri, uzurin me zaka ba ni?”

Kareem ya nuna shi da tsaya.

“Tsaya matsayinka ka kula da kalamanka, wata kila ba dan yarinyar nan ba, da baka da alfarmar shigowa office din nan, so respect yourself”

“Gaskiya ne, kai ya kamata ka fara respecting kanka ai, kamin ka ni, babu ruwanka da yarinyar nan babu ruwanka da ni, baka san abun da ke tsakaninmu ba”

Zafeer ya fada. Kareem ya kalleni ya kalleshi sai kuma ya dauke kai. sannan sannan ya kalleni a fusace.

“Mu tafi”

Na wuce da sauri ya biyo bayana, haka ya saka ni a gaba har muka isa titi. Ya tari Napep ya shiga sannan ni ma na shiga, gaba daya a rikice nake, yadda na ga ran Zafeer ya bace ya saka hankali kara tashi, shi kenan da yake goyon baya baya son bacin raina balle kuma Baba ko Mama ya ransu yake a yanzu.

“Noor”

Na kalleshi.

“Me yasa kika ce mutumen nan Saurayinki ne?”

Na yi shiru domin ba ni da wata hujja da zata gamsar da shi, indai har Hujjar dazun da na bashi labarin komai be gamsar da shi ba ban san me zai kare kaina sa shi ba.

“Saboda yana da kudi?”

Zuciyata ta buga da karfi, Zafeer ya fara lissafin da ban taba yi ba, ya zarge ni da abun da ban yi tunani ba. Sauke murya yayi kasa sosai kamar marar lafiya.

“Zan yi kudin In Shaa Allah Noor zan gina miki irin gidan da kike so, da irin tsarin da kike so, zan wadata ki da komai, zan maida ke sarauniya na maida ke abar kwatance, ki kara hakuri ki kara min lokaci kin ji?”

“Ba saboda haka ba ne, ni dai kawai na yi ne saboda na firgita matar”

Ina jin lokacin da ya sauke ajiyar zuciya ya kalleni a raunace.

“Dan Allah karki sake, rai na ya bace yau saboda abun da kika yi, ban jidadi ba kin saka na raina kaina, kuma kin saka na miki wani kallo da be kamata ba, Baby Noor ki zama mai sauraren maganar iyayenki kin ji? Ki zama mai bari idan aka hana ki, mai yi idan aka ce ki yi kin ji Baby na”

Na daga mishi kai har lokacin jin nake kamar ba Zafeer dina ba ne, Mai Napep din ya juyo ya kalleni.

“Lafiya?”

Zafeer ya tambaya be ce komai ba ya juya ya cigaba da tukinsa.

“Kin san inda matar nan take?”

“Ban santa ba”

Na amsa ina share hawayena. Zafeer yayi kwafa.

“Zafeer ka yi hakuri ba zan sake ba”

Na fada murya na rawa, sai yayi min ya girgiza min kai. Be sake ce min komai ba har sai da muka fita Napep din ya sallami mai Napep din a lokacin duhu ya fara sosai sai dak hasken wutar nepa da ya haska unguwar ya taimaka mana.

“Ina sonki Noor Allah ya saka min sonki fiye da yadda kike tunani, kuma na san kina so na kema, dan Allah karki bari shedan yayi nasara akanki, karki biyewa kyale kyalen zamani, with time ni ma zan yi miki komai”

Muna tafe yana fada min haka, ban iya furta komai ba har muka doshi gida, zuciyata kuma ta doshi bugawa kamar wadda azali ke kiranta. Daga nesa muka hango mota fake a kofar gidanmu, ni dai daga inda nake Ina iya shaidar Kareem ne tsaye a tare da Baba, domin akwai wutar nepa a unguwar, kuma na gane tufafin jikinsa na yau da motarsa sai dai abun da suke tattauna ne ban sani ba. Na kalli Zafeer sai na ga yanayinsa ya sauya kamar be ji dadin haka ba, ni dai da mamaki na karasa gurin faduwar gabana yana karuwa, hakan ya saka ni rage tafiyar da nake Zafeer ya kalleni.

“Muje zan masa bayani zai fahimta ba zai miki komai ba”

Kamar Kareem ya san abun da Zafeer yake fada sai na ji ya ce.

“Noor karaso nan, na yi magana da Baba na masa bayanin komai, kuma ya fahimta daman shi ne makasudin da ya saka na yi rigaku zuwa”

Na kalli Zafeer har sai da yayi min alama da na tafi sannan na tafi ina rike da hannuna.

“Allah dai ya tsare babu karaya ai”

Cewar Baba da far'arsa kamar ba shi ba. Zafeer ya gaishe shi, Baba ya amsa.

“Ashe kai ta kira...”

Zafeer ya risina.

“Eh ayi Hakuri dan Allah Baba”

“Babu komai, Allah kyau gaba Ai shi Alhaji yayi min bayanin komai”

Zafeer ya kalleshi ya kalleni.

“Shiga gida Noor”

Na nufi kofar gidan kamar yadda ya bukata na shige cikin gidan. Sai dai ban isa a inda Mama take zaune ba kamar tana jirana, Yaya Nabill ma dake kusa da ita ina iya karantar yadda yake cika yana batsewa.

‘Idan na tsira daga dukan Baba Mama fa?’

Na tambayi Kaina...
Follow the KHADEEJA CANDY channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01

*Duk mai son ya rika samun Littafin TA KI ZAMAN AURE yayi following wannan Channel din mai suna KHADEEJA CANDY a nan zaku rika samu duka littafaina in Sha Allah*


✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫 -8


Daga Yaya har Mama babu wanda ya ce da ni shigo ki zauna ko kuma juya ki koma. Ina tsaye a gurin na kasa kuka na kasa magana har Baba ya shigo.

“Shiga ciki ki zauna mana, ai duk abun da kike ba laifin ki ba ne uwarki ce ta ke goya miki baya, baki da matsala ke”

Cewar Baba sannan ya wuce ni ya shiga cikin gidan. Mama kamar tana jiransa ta ce.

“Daman ai kullum ni ce ice mai dadin hawa, nan gana Noor ko kisan kai ta yi ni zaka dorawa laifi, duk abun da kowa zai aikata kaina zai dawo, shin ni kadai nake da hakkin tarbiyantar da ita? Kai ba Uba ba ne?”

“Saboda ina uba sai aka ce na zauna gida na kula da yara? Tarbiya ai ta uwace no Cewa aka yi na fita na nemo, ke zaki kula da gida dan haka dole duk abun da yara suka yi na ce laifin ki ne”

Mama ta yi shiru na san kuma ba dan ta rasa abun cewa ba sai dan tana gudun fadan yayi nisa.

“Ni na gaji da halin yarinyar nan, tun da aka haife ta cikin wahala nake, kar taje nan gaba ta dauko min abun magana tun da har ta gane bibiyar maza a inda suke, daga bige hannu da kai ban san inda za'a tsaya ba, ko yanzu Allah kadai ya san gaskiyar abun da ya faru, kar taje ta dauko min abun kunya na kasa fita cikin jama'a, zan fadawa yaron idan ya shirya fito ayi auren daman ni dai ba wani abu na aje ba, balle na ce zan dauka na kai masa, ko zane daya Allah ya hore masa ya kawo a hada ya da tabarma ayi musu aure su je can su karata, ke dai ba iya tarbiyarta kike ba tun rana karama balle kuma yanzu da take kara girma”

A fusace Mama ta mike tsaye sai ganin na yi bulalar wayar wuta ta fado a jikinta.

“Wai Malam tunanin kake abun da Noor take dadi yake min? Ko kuma ganin kake ni nake zaunawa na tsara mata shirirtar da zata je ta yi a waje? Daga Islamiya fa ta bar yar'uwarta ta tafi gurin yawon shiririta, a can idan kasheta za'ayi an dade ba'ayi ba, kuma kamar Noor ace ta san ta tsame kafa ta bi wata su tafi restaurant, kanen ubanta ne a can ko na uwarta, babu sanarwa babu neman izinin kowa”

Baba ya rike gemu.

“Toh.... Ai ga irinta nan a gabansu kike fada min magana son ranki kina min tsawa saboda kin isa, ai tarbiyarce suke kallo suna dauka”

“Tarbiyar ce, idan baka Gamsu da ita ba Malam ka auro wata uwar ta zo ta ba su wata tarbiyar, daman ai ka saba aure aure”

Yau kai na ga dabam, Baba ce take fadawa Baba magana cikin bacin rai abun da bata taba ba a gaban idona. Baba kamar yana jira sai ya nufe ta yana nuna kansa.

“Ni kike cewa na saba aure aure...?”

Ya Nabil dake zaune yayi hanzarin mikewa tsaye ya tare Mama ya shiga tsakiyarmu.

“Toh ko dukana zaka yi? Nace dukana zaka yi?”

“Ba dukanka zan yi ba Baba amman ba zan zuba ido ina kallo ka daki Mama ba a gaban idonmu, Baba abun da kake babu dadi wani abun ba laifinta ba ne amman sai ka dora mata laifi komai aka yi a gidan nan cewa kake laifinta ne, ta ina yanzu laifin Noor ya shafe ta? Baba be kamata ace a gaban idonmu ka doke Mama ba wani abun ai ka daga mata kafa ko dan mu”

“Ayyy haka ne, lallai Nabil wuyanka yayi kwari, yanzu ni zaka zauna ka tsarawa magana haka son ranka? Ashe kai ma baka da mutunci toh sai ka doke ni na san ka girma marar mutunci, saboda ina talaka kake raina ni?”

Mama ta ja Nabil gefe ta tura shi.

“Fita can waje idan ya fita sai ka dawo...”

Tana rufe baki Baba ya dauke ta da mari.

“Ya fita sai na fita ya dawo wato ga mahaukaci ko? Ga mahaukaci na hauka”

“Baba...”

Ya Nabil ya zaburo da karfi yana hakki har sai da Mama ta rike shi.

“Kul kul kul ko yanka ni ubanka yayi ka kai hannu ka dake shi ban yafe maka ba Nabil, karka kuskura zuciya ta debeka ka aikata abu makamancin wannan”

Sai kuma ya fashe da kuka Mama ma ta saka kuka.

“Fice ka bar min gida, karka sake kwana min a gida daga yau, kuma kar a sake ba shi abincin gidana”

Baba ya fada yana nuna masa kofar waje. Ni kam na yi tsaye kamar hoto ina kallon drama da ake a cikin gidanmu, na san halin Baba na dukan Mama ko fada mata magana marar dadi, domin mahaifina irin mazajen nan ne da ba su girmama matansu sun maida matansu kamar ba yi, shiyasa duk auren da yayi babu mai dadewa suke fita su bar Mama. Sai dai abun da ban saba gani ba shi ne mayar da martani na magana da Mama ta yi a yau, da kuma yunkurin da Ya Nabil yayi, duk kuma saboda ni ne. Baba ne ya fara ficewa daga gidan sannan Yaya ya nufo kofar fita sai na jinin jikina na matsa jikin gini sosai gabana na faduwa hawaye na ta zirya a fuskata. Ashe dai ban tsira ba domin yana kawowa kusa da ni ya dauke ni da mari mai bala'in zafi da radadi har sai da na taune halshena. Kuma yaja ya tsaya a gabana, jira yake na yi kuka ko na kalleshi ko kuma na furta wani abun yayi min duka. Ban yarda na daga ido ba balle na kalleshi ban bar wata kalma ta fito daga bakina ba, kuma kuma ban yunkurin yin motsi ba har ya gaji da tsayin yayi ficewarsa.

Sannan na dago kai na kalli na kalli cikin gidanmu, Mama na jiyo tana fadin.

“Kin yi nasara an kuri dan'uwanki ga dakinsa can sai ki share ki zauna, ba ke kadai na haifa ba amman ke kika saka ni ciwon kai da ciwon zuciya kullum, girmanki ya kai ace kina da wayo da hankali amman yayi miki nisa, baki bar ni da bakincikin ubanki ba, ba ki bar ni da bakincikin neman abun da zan aurar dake da abun da zamu ci ba, wani kike lalabowa kina yafa min, kullum nuna miki ake amman sai ki rufe ido bako duban daidai na gaji da halinki Noor”


Na durkusa daga inda nake tsaye ina son na bata hakuri na kasa magana. Gurin da muke aje kayan wanke wanke ta nufa tana juyowa na ga wuka a hannunta, domin tabbatarwa sai ta nufi suminti ta koda wuyar sannan ta juyo ta kalleni.

“Kin ga wuka nan na koda, yau sai na kwantar da ke na yanka, na gaji da halinki yau din ba zaki kwana da rai ba...!”

Yanayin da na samu kaina a lokacin da Mama da nuna ni da wukar tana furucin da ya dursaso da tashin hankalina a kusa ya wuce misali. Ashe har na gundurar da Mama haka, rashin jin magana ta ya kai Mama tace zata yanka ni? Ashe uwa zata iya kashe yarta? Na mike tsaye ina jin kamar wata murya na fada min na juya na fice daga gidan, sai dai idan na fita ina zan je? Wa zan je na roka ya bawa Mama hakuri? Yau ta yi fushin da bata taba yi ba, yau ta furta min kalmar gajiya, ta furta sao ta yanka ni, na tabbatar babu wadda zai ceto ni a yau na kwana da rai.

Na fito na tsaya daga bakin kofar gidan na raba jikin ginin na rumgume hannuna ina tunanin inda zan je. Kamar ance dago kai ina dagowa na yi arba da Hana tana kuka ashe tana cikin gidan amman ban ganta ba duk abun nan da ake.

“Ki tafi gidansu Maman Zainab ki kwana, dan Allah karki gudu ki karawa kanki laifi, Baba yayi min duka saboda na ki fadar inda kika je lokacin da na dawo daga makaranta har sai da na fada sannan ya kyale ni, Noor miye amfanin abun da kike yi? Dubi yadda kika sakawa kowa bakinciki yau”

Ita ma dai bani da amsar da zan bata dan haka na duka na duka a gurin ina jin halshena yana zogi saboda marin da Yaya Nabil yayi min.

“Hannatu...”

Mama ta kira da karfi, sai ta juya da sauri ta koma cikin gidan ta bar ni a gurin duke ina tunanin makoma. Can kuma na mike tsaye na nufi gidansu Zafeer domin ban san wani abun da zan yi ba, sai dai tunawa da ba lallai ne Mama ta hakura ba ko da ya mata magana ya katse hanzarina, a madadin shiga cikin gidan sai na mike na kama hanyar gidansu Kareem. Tafiyar da zan biya 200 a kai ni gidan ita nake yi a kafa ba tare da gajiya ko kasawa ba. Zan iya shaidar kaina ina ba basira da gane abu ko da kuwa sau daya na gani, hakan ya saka na yi saurin gane gidan sai dai na shiga unguwar a lokacin da sawu ya fara daukewa ne, bana da agogo balle na iya fadar karfe nawa, amman tabbas dare yayi domin mai gadin gidan ma hanani shiga yayi bayan na kwankwasa.

“Toh dan Allah ka fada masa Noor ce tana waje”

Na bashi sako sannan na ja na tsaya ina jin tsoron wajen saboda babu kowa.

“Ki jira a nan ina zuwa”

Ya rufe gate din ya bar ni a gurin tsaye, bayan dan lokaci na sake jin an bude kofar.

“Shigo”

Na shiga cikin gidan, na doshi main door kamin na karasa Kareem ya fito sanye da pajamas ya nufo inda nake sai muka ci karo a tsakiyar gida.

“Noor lafiya?”

“Mama tace sai ya yanka ni, tace yau ba zan kwana da rai ba, ta nuna min wuka kashe ni zata yi, Yaya yayi fada da Baba har ya koreshi saboda ni, kanwata ma an mata duka saboda ni”

Ina maganar hawaye suna fadar yau ce ranar mu, jikina na karkarwa kamar mai jin sanyi. Shiru yayi yana kallona kamar mai tunani me zai fada ko ya aiwatar.

“Babana yana jin maganarka, Mama kuma tana jin maganar Baba, so nake ka tafi ka bawa Baba hakuri shi kuma ya bawa Mama hakuri ta yafe min, ka fada ma Baba ya fada mata daga yau ba zan sake ba, ka ce ina rokonta ta yafe min”

Na fada masa bukatata.

“Waya kawo ki nan?”

“A kafa na zo, ka yi hakuri ba zan sake takura maka ba daga yau ba zan sake batawa kowa rai ba”

Ni dai ban san ya aka yi ba na jini na jikinsa ya rumgume yana rarrashina.

“Ya isa haka Noor I'm sorry”

Ji na yi kamar na samu wata mafaka sai na fashe da kuka mai mugun karfi.

“Ya isa ya isa haka kar yarana su ji”

Ya sake ni da sauri.

“Shigo ciki na canja kaya sai mu tafi gurin mahaifin naki”

Na bi bayansa muka shiga cikin falon sai na tsaya daga bakin kofa ina kallon matarsa dake zaune tana cin abinci. Sama ya nufa be jima ba ya sauko sanye da jallabiya da hula hannunsa rike da keys.

“Wani taimako take son na yi mata, zan je na dawo yanzu”

Ya fadawa matarsa, sai ta dubeshi ta dauke kai.

“Kai ka ta shafa, idan ka aikata abun kunya yayanka ne a kunya ba ni ba, ni matsalarka bata gabana”

Amsar ta bata ba ni mamaki ba kamar yadda shi din ya ba ni mamaki ta hanyar dauke kai ba tare da ya ce mata komai ba ya kalleni ya ce

“Mu tafi”

Na juya na fara fita sannan ya fito, sai da ya janyo mota sannan na bude da hannun hagu na shiga domin na dama a daure yake. Tun da muka shiga motar be ce min komai ba, ni ma ban ce masa ba muka isa unguwar yanayin yadda na ga mutane sun rage ya tabbatar da dare yayi sosai.

“Ina zamu samu ganin Babanki a yanzu?”

“Yana zama a majalisa kamin ya shiga gida”

“Ina majalisar take?”

Na fada masa sai ya bude motar ya fita yana kara tambayar kwatancen domin be san kan unguwar ba.

“To jira ni a nan”

Na daga masa kai na bishi da kallo har na daina hangoshi. A kiyasina za'ayi minti talatin da fitarsa sannan na hango bullowarsa tare da Baba dake rike da fitila duk da kasancewar akwai wutar nepa. Na bude motar na fito ina kallon Baba.

“Ah ah Noor to ai da sauki ma tun da gurinka ta tafi, da ta fi duniya ai shikenan to zo mu tafi gida”

Na nufeshi ina jin tsoro, Kareem kuma ya koma cikin motar ya zauna har sai da muka yi nisa sannan ya biyo bayanmu. Baba ne ya fara sallama ya shiga cikin gidan sannan na bi bayansa.

“Ke Hajara fito ga Noor din gata nan ki yanka ta”

Da gudu na ga Mama ta fito har sai da na tsorata naja baya.

“Noor ina kika je?”

Ta tambaye ni tana kuka

“Ina kika tafi na aika nemanki ko'ina baki nan”

Ban samu amsa mata ba Kareem yayi sallama ya shigo sai Baba ya amsa masa sallamar. Kareem ya kalli Mama ya gaisheta

“Dan Allah ayi hakuri, abun da kika furta kin tsoratata ma bar gida ta tafi a kafa ta same ni har gida tace na zo na baki bakuri tare da Babanta, kuma tace na fada miki ba zata sake ba, dan Allah ki yi hakuri”

“Babu komai na yafe mata, ni ma na gane kuskuren fadar hakan da na yi bayan ta bar gidan, domin bayan gidan nan bata da wani masauki, kuma mace ce hankalin ya tashi sosai a lokacin da aka duba ko'ina ba ganta ba, wani lokacin rai ne yake baci ka aikata abun cikin bacin rai, Zafeer ma be dade da aikowa kiranta ba nace a fada masa bachi take, na mata haka ne saboda ta tsorata ta daina abun da take, ba dan ina da niyar aikatawa ba”

“Alhamdullahi, daman na san uwa dole zata nemi yarta duk runtsi, addu'a ya kamata ana yi ba sai tsoratarwa ba”

Kareem ya fada sai Mama ta mika hannu ta janyo ni ta rike.

“Ai Alhaji Noor din ce sai hamdala, ni ina ganin aurar da ita kawai zan yi na huta, shi yaron nan idan ya shirya ya fito idan kuma be shirya ba ko a Masallaci ne zan yi cigiya na bada ita sadaka, ita ta huta mu ma mu huta”

Baba ya fada, sai Kareem ya kalleshi ya ce.

“Noor din nawa take da za'ayi mata haka? A dai yi hakuri, ni zan koma ga dubu ashirin a siya wani abu”

Baba ya saki fitar hannunsa ya mika hannu ya karba.

“Ahhh Allah da iko yake, kai yaron nan gajiya da kyauta, dazun ma fa sai da ka ba ni wasu kudin, Allah dai ya saka da alheri ya rabaka da iyayenka lafiya Allah ya kara budi”

“Ameen Ameen”

Har ya juya sai kuma ya juyo ya kalli Baba dake kokarin yi masa rakiya.

“Am Baba dan Allah ina son na bada hakuri akan Nabil ka yafe masa shi ma dai ya dawo gida ya zauna, ku daina daukar zafi akan yaranku ayi hakuri dan Allah”

Baba ya amsa da sauri.

“In Shaa Allah, babu komai na yafe masa ya ci albakarcin ka ba komai”

“To na gode”

Ya juya ya fice Baba ya bishi yana addu'a, ni kuma na kalli Mama.

“Mama ki yo hakuri daga yau ba zan sake ba”

Sai ta kwantar da ni jikinta tana kuka.

“Na yafe miki Noor, bakincikin ne yana min yawa, amman dai idan bana duniya babu wadda zai fada miki gaskiya, Allah ya sauya miki rayuwa ya canja wannan hali na ki”

Ta nufi dakinta da ni tana rumgume da ni, wani dadi da natsuwa na ji marar misaltuwa saboda yafe min da Mama ta yi har ta rumgume ni.


KAREEM POV.

Ajiyar zuciya ya sauke bayan ya faka motarsa a harabar gidan, sannan ya ciro wayarsa ya shiga WhatsApp dinsa da datarsa take always on ya shiga chatting dinsa da Safeena ya rubuta mata sako.

“Safeena wannan ya zama karo na karshe da zaki sake kai hannunki jikin yarinyar nan, babu wani abu tsakanina da ita, duk abun da ta fada ko Hafiz ya fada sun fada ne kawai saboda su fusata ki, ina sonki kin sani, kuma na san kina so na, amman hakan ba zai baki damar ki aikata sakarci a gaban kowa ba, ko kuma ki yi yunkurin cutar da wani ba zan lamunce miki wannan ba, kuma babu ruwanki da yarinyar nan daga yau”

Yana aje mata sakon ya bude motarsa ya fita ya rufe sannan ya kama hanyar falon gidan. Shiga falon ke da wuya sakonta ya shigo wayarsa sai ya bude arba yayi da hoton bari da kuma rubutun sakon dake bin bayan hoton.

“I lost my baby today saboda bakincikin jin cewar kana son wata Kareem, mijina ya kasa gane kaina yau saboda kai, na fitunu da kaunarka da Kareem, amman kokarin cire ni kake a rayuwarka bayan duk budulcin da ka yi min na kin aurena”

Ya karanta sakon kusan sau uku sannan ya sake duba hoton barin da ta turo masa, a madadin ya ji dadi abun da yake nema ya samu wato cikin ya zube, sai abun ya tsorata shi, har ya fadi zaune a kujera yana mamakin kansa.

‘Ta ya yayi zurfi a zuciyar matar wani haka? Har bakincikin jin cewar yana son wata zai saka cikinta ya zube, me yake aikatawa haka? Wane irin mutum ya zama? Wane kalar uba ya zama? Wane kalar miji? Wane kalar ďa? Ashe tasirin sabon da zuciya take kwadaituwa da aikawa ya kai haka?’

Ya mike tsaye zuciyarsa na bugawa da karfi, idan ya mutu a cikin daren nan yana da wata hujja da zai fada ya fanshi kansa a gurin Allah? Me ya aikata haka? Zina ba halinsa ba ne me yasa zuciya ta kai shi? Ta ya yake kokarin lalata rayuwarsa? Su ne tambayoyin da suke masa yawo a kai idonsa suka cika da hawaye. Ya nufi sama da sauri ya tura kofar dakin yaransa ya tsaya daga bakin kofar yana kallon Tine dake bachi ya karasa ya zauna kusa da ita ya kai hannu ya shafa kanta yana tuna maganar matarsa.

“Kai ka ta shafa, idan ka aikata abun kunya yayanka ne a kunya ba ni ba, ni matsalarka bata gabana”

Ya hade yawu ya mike tsaye ya gyara mata bargonta sannan ya fice dakin a hankali ya ja kofar. Dakin matarsa ya nufa nan ma a hankali ya tura kofar ya shiga sai same ta kwance tana bachi Areef na gafenta shi ma yana bachi. Karasa yayi ya kalli dansa ya kalleta ya mika hannu ya shafa dansa sannan ya juya ya fice.
Follow the KHADEEJA CANDY channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01

*Duk mai son ya rika samun Littafin TA KI ZAMAN AURE yayi following wannan Channel din mai suna KHADEEJA CANDY a nan zaku rika samu duka littafaina in Sha Allah*


✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


*Talla👇👇👇*

KINADA DAYA DAGA CIKIN WADANNAN MATSALOLIN ❓👇👇👇
To kiyi saving numba ta ki danna wannan link👇 https://wa.me/message/N2S6DQEPETKQO1 Idan kinyi saving ki fadamun zanyi SAVING TAKI😍ko Baki Siya yanzu ba WATARANA zatayi maki AMFANI👇👇
1.INFECTION CIWON SANYI 👉LALACEWAR BREAST👉RASHIN HIPS & BUTT👉KIBA TAYI MAKI YAWA KINASO KIYI SLIMMING👉TUMBI YAYI MIKI YAWA KINASO KI RAGE ?👉 AKWAI KUMA INGANTATTUN KAYAN MATA APHRODISIACS MASU KYAU DA INGANCI GA kUMA SABAYA ASALIN MAI KYAU 3500 only 👌

KIZO KI GWADA KAYAN AMNOOR INA TABBATAR MAKI BAZAKIYI NADAMA BA 👉 KIYI SAVING NUMBER TA DM ME https://wa.me/message/N2S6DQEPETKQO1
Chapter 2 · 0% Book details