PART C🗡️🗡️
Miftahuzzarbil Part 2 Complete Hausa Novel · about 9 min read
AUTHOR: ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI 🤴
TYPING: AHMAD MUNNIR.
POSTING: NAJIBULLAH MUHAMMAD ❤️
MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA...
Koda Miqdad ya gama karanta wannan jawabi sai na tsuguna qasa cikin karayar zuciya na dago kai na dube shi nace,"zai fi kyau ku bar ni anan don dole ne ma nayi kuskure.Dubi fa yadda dubunnan karafan nan suke a cakude farare da baqaqe.Kuma koma banyi kuskure ba ai kafin mutum yakai karshe saiya gaji da tafiyar a haka ya fado."
Miqdad ya tsuguna a gabana yace,"ya ke suhaila kiyi sani cewa ba zan iya tafiya ba na barki.Idan kuwa za ki hallaka a cikin kogon nan zan so mu halaka tare.Ni na san cewa dani da mahaifin ki zamu iya ketare wannan wuta albarkacin abin bautar mu.Tun da kin tsorata ni zan tsallakar dake ta hanyar ki rungume ni a kirji kuma ki daure jikin ki da nawa.Idan har zaki fado cikin wutar nan saidai mu fado tare."
Koda gama fadin haka saina dube shi nace,"haba ya ma za ai mu tsira da wannan dabarar? Ka tuna fa cewa nauyin jikin ka ma kadai zai gundureka ballantana ka kara da nawa nauyin."
Miqdad yace,"karki damu ina son ki yarda da ni kisa a ranki lallai zan iya."
Nayi shiru ina mai nuna alamun rashin gamsuwa,yayin da mahaifina Shaubatul Azman ya fuskanci haka sai shima ya durqusa a gabana ya kama kafaduna.Sannan yace,"yake 'ya ta ki saki jikinki ki tuna irin hadarin da ke can baya na kogin darma,amma saida Miqdad ya hayar dake.Tabbas na san zai iya kubutar dake."
Wannan jawabi ne yasa jikina yayi sanyi na aminta.Kawai sai na yarda na rungume Miqdad shi kuma Shaubatul Azman sai ya kwance rawanin sa ya daure jikina dana Miqdad tamau.Koda yin hakan sai ya dubi Miqdad yayi murmushi,sannan yace,"idan har ka tserar da rayuwar 'ya ta daga wannan hadari ka biya sadakin aurenta."
Cikin tsananin mamaki da farin ciki na dubi Shaubatul Azman na kama dariya,shima sai ya kama dariyar.Miqdad yayi murmushi yace,"ai kuwa zan nemo wannan sadaki ta kowane hali iyakar qoqarina."
Nan take jarumi Miqdad ya runtse idanun sa sannan ya daka tsalle sama ya kamo fararen qarafa biyu.Sannan ya cigaba da tafiya a sama yana kama karafan dake gaba.Sai da Shaubatul Azman ya lura da yadda jarumi Miqdad ke sauya hannayensa wajen kamo karafan.Sannan shima yayi koyi da shi.Idan muka yi tafiya mai dan tsawo saiya tsaya ya huta,sannan ya cigaba da tafiyar.Babu abinda ya bani mamaki face yadda ya jure nauyina da kuma gajiyar.Saida muka isa daf da karshen wutar nan sai rawanin dani a jikin Miqdad ya kwance.Ai kuwa saina su6uto na yi yo kasa.Cikin zafin nama na ruqo kafafun Miqdad sai gashi ina reto a sama kamar zan fado.
Nan fa na rikice na dunga kwala ihu.Miqdad ya daka min tsawa yace,"ki nutsu ko na karkada kafafuna ki fada cikin wutar."
Da jin wannan batu sai na yi tsit.Miqdad yace,"haba gimbiya 'yar sarakai wadda ta gaji zuciyar maza.Ki cigaba da kama kafafuna kina hawowa sama ni kuma zan taimaka miki na dawo dake kan kirjina.Idan kika yi haka zan gamsu cewa kema kina son ki ceci kanki,kuma kin cika mace mai zuciyar maza."
Koda jin haka saina ji wani sabon qarfi ya shige ni gami da kwarin gwiwa.Nan take na cigaba da hawa kan kafafun nasa duk da cewar shima reto yake a sama.Saida na kai iya kugunsa sannan yasa hannu daya ya dagoni sama ya dorani a kirjinsa ni kuwa na qara maqalqale shi.Duk wannan abu dake faruwa idanun mu a rufe suke kuma sarki Shaubatul Azman bai qaraso inda muke ba.Nan da nan muka dirga a karshen wutar bisa turba.Koda Miqdad ya ga cewa har ynx Shaubatul Azman na can baya sai ya sake tsalle ya ruqo karafan nan na sama ya koma da baya cikin sauri kamar dama can ya laqanci tafiya a wajen yasa Shaubatul Azman a kirjinsa kamar yadda yayi mini ya taho da shi da sauri suka riskeni.A wannan lokaci ne na jinjinawa Miqdad na dube shi nace da shi,"hakika ka cika gwarzon jarumi mai matuqar sadaukan taka da juriya."
Miqdad yayi murmushi sannan ya kama hannuna ya jani da gudu muka kara nausawa cikin kogon Shaubatul Azman na biye da mu.
Haka dai muka cigaba da riskar abubuwan hadari iri-iri har kala goma a tsawon kwana biyu.Kuma cikin sa'a duk muka tsallake su dayan mu bai halaka ba.Amma fa munga gawarwakin fadawan Ashikatul Ashiriya da yawa ba adadi.Ba zato ba tsammani sai muka tsinci kanmu a wata makekiyar fada wacce ta cika ta batse da dukiya ninkin baninkin dukiyar da muka gani a farkon shigowa wannan kogo na Baitul Husuk.Ni kam babu abinda ya fi bani mamaki face girman kogon domin har ynx a wani bangare dabam muke bamu shiga wasu wuraren ba.Har na kutsa kai zan shiga cikin dukiyar nan sai Miqdad yayi sauri ya ruqo hannuna kuma yayi wa Shaubatul Azman nuni da cewar duk muyi shiru mu daina motsi.Cikin sanda jarumi Miqdad ya nufi cikin wasu tukwane marasa adadi wadanda a cike suke taf da sulallan zinare.Miqdad ya zare takobin sa ya soka cikin sulallan.Kawai sai muka ji ihu daga cikin tukunyar.Miqdad na zare takobin saiga jini a jikin ta.
Nan da nan dakarun Ashikatul Ashiriya suka rinqa fitowa daga cikin tukwanen sulallan suka afka mana.Ashe tuntuni sunji motsin tahowar mu shi yasa suka yi lam6o.Nan fa wuri ya hargitse sarki Shaubatul Azman kuwa ya kaiwa Miqdad dauki aka fara azababben yaki.Ni kaina mayakiya na zama a wannan lokacin na dunga sara da suka saiga shi kuwa ina zubar da maza dama na dade da koyon yaki a wajen jarumi Haiman amma ban taba jarraba jarumtata sai a sannan.Muna cikin tsakiyar artabu da wadannan tsirarun dakarun ne na hango Ashikatul Ashiriya a can sama cikin wani daki tana karanta wadansu dalasimai na tsafi.Ai kuwa fara karatun nata ke da wuya sai wani irin haske mai tsananin qarfi ya haskake wajen da ake yaki gaba daya.Take kowa ya qame aka zama kamar gumaka ni kadai ce ban komai ba.
Ashikatul Ashiriya ta kyalkyale da dariyar qeta ta juyo ta dubi inda muke kawai sai ta hango ni a tsaye na ruqe quguna da hannu biyu ina kallonta.Cikin tsananin mamaki ta dube ni ta daka min tsawa tace,"ya akai ke baki qame ba?"
Maimakon na bata amsar tambayar saina zaro littafin nan na sirrin arzikin Kisra daga cikin rigata na nuna mata ina mai murmushi nace,"ya ke wannan sarauniya kiyi sani cewa indai ina tare da wannan littafi babu wani sihiri na cikin kogon nan da zaiyi tasiri a kaina."
Yayin da Ashikatul Ashiriya ta ji haka saita fashe da kuka sannan ta dube ni tace,"yake 'ya ta ashe kin manta da duk irin son dana nuna Miki a rayuwa.Ki tuna cewa nonona kika sha kika girma har kika kawo iyanzu.Na kasance a cikin tsananin qaunar ki tun daga quruciyar ki don haka har abada ba zan cutar da ke ba.Ina mai roqonki daki kawo mini wannan littafin yanzu nayi alqawari ba zan cutar da ke ba kuma zan cigaba da riqeki a matsayin'yar cikina."
Koda Ashikatul Ashiriya ta zo nan a zancenta sai na kyalkyale da dariya nace,"haba sarauniyar yaudara kiyi sani cewa na sanki na san halinki,idan kika qi abu har abada baza ki so shi ba,kuma nima kin koya mini wannan hali.Na rantse da son da nake wa mahaifina yanzu haka na tabbatar da cewa yaudara ta kike so kiyi in baki wannan littafi don ki halakar dani,kuma ki sami damar fita daga cikin kogon nan don haka ba zan ba ki ba.Ina tabbatar miki da cewa ajalinki na cikin kogon nan."
Koda jin wannan batu sai sarauniya Ashikatul Ashiriya ta zare takobin ta ta rugo gareni tana qaraji da nufin ta sare ni.Nima saina ruga gareta muka hadu a tsakiya muka fara dauki ba dadi.Nan fa muka rinqa kaiwa juna sara da suka.Hannuna guda na ruqe da takobi,dayan kuma na ruqe da wannan littafi na Mabudin arzikin Kisra.Bisa mamaki saina ga ta quntata ni ta hanani sakat,domin ta fini kwarewa a iya sarrafa takobi nesa ba kusa ba.
Nan da nan ta rikirkita ni har ta sami nasarar yi mini yanka guda biyu.Daya a damtsen hannu,daya kuma a cinya.Al'amarin daya sa nayi ihu na fadi kasa ita kuwa saita matsoni tana kyalkyala dariya lokacin dana ke ja da baya.Ashikatul Ashiriya ta ce,"haba yarinya ai duk wanda ya riga ka kwana dole ne ya riga ka tashi.Na rantse da darajar karagata koda Haiman na kara ba zai samu nasara ba a kaina bare ke."
Ina cikin jan jiki da baya ne bayana ya tokare da bango babu damar gudu.Koda ganin haka sai Ashikatul Ashiriya ta qara bushewa da dariya tace,"yauwa yanxu kam na rutsa ki kuma cikin ruwan sanyi zan kashe ki na dauke wannan littafi."
Take ta daga takobin ta ta kawo mini sara da nufin ta tsarge ni biyu.Cikin zafin nama na kare saran da littafin nan na Mabudin arzikin Kisra.Ko da takobin ta sari littafin sai hasken nan mai qarfi ya sake baibaye kogon gaba daya.Take ruhin kowa ya dawo aka cigaba da yaki.Ashikatul Ashiriya tayi sauri ta ruga cikin dakin nan don ta karanta wadansu dalasimai na tsafi.Ai kuwa saina bita da gudu na sa kafata na harde ta ta fadi qasa takobin ta ta su6uce daga hannun ta.Kawai saina daka tsalle na dira a kanta muka cigaba da kokawa mu murgina nan,mu hautsina can.
Nan fa ta samu ta hau ruwan cikina ta rinqa naushina a fuska ta hada mini jini hanci da baki,sai dana suma.Sannan ta dagani kuma ta cire littafin nan daga hannuna.Cikin sauri ta rinqa bude shafukan littafin harta zo kan shafin karshe inda aka yi bayanin yadda za'a bude wata kofa ta fita daga cikin kogon da kuma yadda za'a qone kogon gaba daya.Ashikatul Ashiriya ta karanta wadansu kalmomin tsafi saiga wadansu raquma da alfadarai sama da guda dubu dari uku sun bayyana.Bayyanar su keda wuya sai dukiyar nan ta cikin tukwane ta dora kanta a kansu.Ashikatul Ashiriya ta sake karanta wadansu kalmomin sai wata katuwar kofa ta bayyana ta bude kanta.Cikin sauri Ashikatul Ashiriya ta kada raquman nan da alfadaran suka fara fita wajen Kogon Baitul Husuk dauke da dukiyar.Ita ma saita ruga da gudu izuwa kofar don ta fice.Har yanzu ana ta fafata yaki da su jarumi Miqdad sai ragargazar maza yake baima lura da abinda ya faru gare ni ba,bare ya hango Ashikatul Ashiriya wacce ta nufi kofar fita da gudu.
A dai dai wannan lokaci ne na farfado daga dogon suman dana yi,kuma a sannan ne Ashikatul Ashiriya ta isa bakin kofa.Tana zuwa tayi arba da jarumi Haiman tsaye a gabanta ruqe da zabgegiyar wuqa.Cikin tsananin tsoro da fargaba ta ja da baya tana mai nuna shi da dan yatsanta wanda ke karkarwa tace,
"Ashe ba kai na kashe ba tun gabanin shigowar mu cikin kogon nan?"
Jarumi Haiman yace,"kwarai kuwa ni kika kashe amma ban mutu ba,kece dai za ki mutu yanzu."
MU HADU PART D DON JIN CIGABAN WANNAN KAYATACCIYAR HIKAYAR.**MIFTAHUZZARBIL**
LITTAFI NA BIYU.
TYPING: AHMAD MUNNIR.
POSTING: NAJIBULLAH MUHAMMAD ❤️
MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA...
Koda Miqdad ya gama karanta wannan jawabi sai na tsuguna qasa cikin karayar zuciya na dago kai na dube shi nace,"zai fi kyau ku bar ni anan don dole ne ma nayi kuskure.Dubi fa yadda dubunnan karafan nan suke a cakude farare da baqaqe.Kuma koma banyi kuskure ba ai kafin mutum yakai karshe saiya gaji da tafiyar a haka ya fado."
Miqdad ya tsuguna a gabana yace,"ya ke suhaila kiyi sani cewa ba zan iya tafiya ba na barki.Idan kuwa za ki hallaka a cikin kogon nan zan so mu halaka tare.Ni na san cewa dani da mahaifin ki zamu iya ketare wannan wuta albarkacin abin bautar mu.Tun da kin tsorata ni zan tsallakar dake ta hanyar ki rungume ni a kirji kuma ki daure jikin ki da nawa.Idan har zaki fado cikin wutar nan saidai mu fado tare."
Koda gama fadin haka saina dube shi nace,"haba ya ma za ai mu tsira da wannan dabarar? Ka tuna fa cewa nauyin jikin ka ma kadai zai gundureka ballantana ka kara da nawa nauyin."
Miqdad yace,"karki damu ina son ki yarda da ni kisa a ranki lallai zan iya."
Nayi shiru ina mai nuna alamun rashin gamsuwa,yayin da mahaifina Shaubatul Azman ya fuskanci haka sai shima ya durqusa a gabana ya kama kafaduna.Sannan yace,"yake 'ya ta ki saki jikinki ki tuna irin hadarin da ke can baya na kogin darma,amma saida Miqdad ya hayar dake.Tabbas na san zai iya kubutar dake."
Wannan jawabi ne yasa jikina yayi sanyi na aminta.Kawai sai na yarda na rungume Miqdad shi kuma Shaubatul Azman sai ya kwance rawanin sa ya daure jikina dana Miqdad tamau.Koda yin hakan sai ya dubi Miqdad yayi murmushi,sannan yace,"idan har ka tserar da rayuwar 'ya ta daga wannan hadari ka biya sadakin aurenta."
Cikin tsananin mamaki da farin ciki na dubi Shaubatul Azman na kama dariya,shima sai ya kama dariyar.Miqdad yayi murmushi yace,"ai kuwa zan nemo wannan sadaki ta kowane hali iyakar qoqarina."
Nan take jarumi Miqdad ya runtse idanun sa sannan ya daka tsalle sama ya kamo fararen qarafa biyu.Sannan ya cigaba da tafiya a sama yana kama karafan dake gaba.Sai da Shaubatul Azman ya lura da yadda jarumi Miqdad ke sauya hannayensa wajen kamo karafan.Sannan shima yayi koyi da shi.Idan muka yi tafiya mai dan tsawo saiya tsaya ya huta,sannan ya cigaba da tafiyar.Babu abinda ya bani mamaki face yadda ya jure nauyina da kuma gajiyar.Saida muka isa daf da karshen wutar nan sai rawanin dani a jikin Miqdad ya kwance.Ai kuwa saina su6uto na yi yo kasa.Cikin zafin nama na ruqo kafafun Miqdad sai gashi ina reto a sama kamar zan fado.
Nan fa na rikice na dunga kwala ihu.Miqdad ya daka min tsawa yace,"ki nutsu ko na karkada kafafuna ki fada cikin wutar."
Da jin wannan batu sai na yi tsit.Miqdad yace,"haba gimbiya 'yar sarakai wadda ta gaji zuciyar maza.Ki cigaba da kama kafafuna kina hawowa sama ni kuma zan taimaka miki na dawo dake kan kirjina.Idan kika yi haka zan gamsu cewa kema kina son ki ceci kanki,kuma kin cika mace mai zuciyar maza."
Koda jin haka saina ji wani sabon qarfi ya shige ni gami da kwarin gwiwa.Nan take na cigaba da hawa kan kafafun nasa duk da cewar shima reto yake a sama.Saida na kai iya kugunsa sannan yasa hannu daya ya dagoni sama ya dorani a kirjinsa ni kuwa na qara maqalqale shi.Duk wannan abu dake faruwa idanun mu a rufe suke kuma sarki Shaubatul Azman bai qaraso inda muke ba.Nan da nan muka dirga a karshen wutar bisa turba.Koda Miqdad ya ga cewa har ynx Shaubatul Azman na can baya sai ya sake tsalle ya ruqo karafan nan na sama ya koma da baya cikin sauri kamar dama can ya laqanci tafiya a wajen yasa Shaubatul Azman a kirjinsa kamar yadda yayi mini ya taho da shi da sauri suka riskeni.A wannan lokaci ne na jinjinawa Miqdad na dube shi nace da shi,"hakika ka cika gwarzon jarumi mai matuqar sadaukan taka da juriya."
Miqdad yayi murmushi sannan ya kama hannuna ya jani da gudu muka kara nausawa cikin kogon Shaubatul Azman na biye da mu.
Haka dai muka cigaba da riskar abubuwan hadari iri-iri har kala goma a tsawon kwana biyu.Kuma cikin sa'a duk muka tsallake su dayan mu bai halaka ba.Amma fa munga gawarwakin fadawan Ashikatul Ashiriya da yawa ba adadi.Ba zato ba tsammani sai muka tsinci kanmu a wata makekiyar fada wacce ta cika ta batse da dukiya ninkin baninkin dukiyar da muka gani a farkon shigowa wannan kogo na Baitul Husuk.Ni kam babu abinda ya fi bani mamaki face girman kogon domin har ynx a wani bangare dabam muke bamu shiga wasu wuraren ba.Har na kutsa kai zan shiga cikin dukiyar nan sai Miqdad yayi sauri ya ruqo hannuna kuma yayi wa Shaubatul Azman nuni da cewar duk muyi shiru mu daina motsi.Cikin sanda jarumi Miqdad ya nufi cikin wasu tukwane marasa adadi wadanda a cike suke taf da sulallan zinare.Miqdad ya zare takobin sa ya soka cikin sulallan.Kawai sai muka ji ihu daga cikin tukunyar.Miqdad na zare takobin saiga jini a jikin ta.
Nan da nan dakarun Ashikatul Ashiriya suka rinqa fitowa daga cikin tukwanen sulallan suka afka mana.Ashe tuntuni sunji motsin tahowar mu shi yasa suka yi lam6o.Nan fa wuri ya hargitse sarki Shaubatul Azman kuwa ya kaiwa Miqdad dauki aka fara azababben yaki.Ni kaina mayakiya na zama a wannan lokacin na dunga sara da suka saiga shi kuwa ina zubar da maza dama na dade da koyon yaki a wajen jarumi Haiman amma ban taba jarraba jarumtata sai a sannan.Muna cikin tsakiyar artabu da wadannan tsirarun dakarun ne na hango Ashikatul Ashiriya a can sama cikin wani daki tana karanta wadansu dalasimai na tsafi.Ai kuwa fara karatun nata ke da wuya sai wani irin haske mai tsananin qarfi ya haskake wajen da ake yaki gaba daya.Take kowa ya qame aka zama kamar gumaka ni kadai ce ban komai ba.
Ashikatul Ashiriya ta kyalkyale da dariyar qeta ta juyo ta dubi inda muke kawai sai ta hango ni a tsaye na ruqe quguna da hannu biyu ina kallonta.Cikin tsananin mamaki ta dube ni ta daka min tsawa tace,"ya akai ke baki qame ba?"
Maimakon na bata amsar tambayar saina zaro littafin nan na sirrin arzikin Kisra daga cikin rigata na nuna mata ina mai murmushi nace,"ya ke wannan sarauniya kiyi sani cewa indai ina tare da wannan littafi babu wani sihiri na cikin kogon nan da zaiyi tasiri a kaina."
Yayin da Ashikatul Ashiriya ta ji haka saita fashe da kuka sannan ta dube ni tace,"yake 'ya ta ashe kin manta da duk irin son dana nuna Miki a rayuwa.Ki tuna cewa nonona kika sha kika girma har kika kawo iyanzu.Na kasance a cikin tsananin qaunar ki tun daga quruciyar ki don haka har abada ba zan cutar da ke ba.Ina mai roqonki daki kawo mini wannan littafin yanzu nayi alqawari ba zan cutar da ke ba kuma zan cigaba da riqeki a matsayin'yar cikina."
Koda Ashikatul Ashiriya ta zo nan a zancenta sai na kyalkyale da dariya nace,"haba sarauniyar yaudara kiyi sani cewa na sanki na san halinki,idan kika qi abu har abada baza ki so shi ba,kuma nima kin koya mini wannan hali.Na rantse da son da nake wa mahaifina yanzu haka na tabbatar da cewa yaudara ta kike so kiyi in baki wannan littafi don ki halakar dani,kuma ki sami damar fita daga cikin kogon nan don haka ba zan ba ki ba.Ina tabbatar miki da cewa ajalinki na cikin kogon nan."
Koda jin wannan batu sai sarauniya Ashikatul Ashiriya ta zare takobin ta ta rugo gareni tana qaraji da nufin ta sare ni.Nima saina ruga gareta muka hadu a tsakiya muka fara dauki ba dadi.Nan fa muka rinqa kaiwa juna sara da suka.Hannuna guda na ruqe da takobi,dayan kuma na ruqe da wannan littafi na Mabudin arzikin Kisra.Bisa mamaki saina ga ta quntata ni ta hanani sakat,domin ta fini kwarewa a iya sarrafa takobi nesa ba kusa ba.
Nan da nan ta rikirkita ni har ta sami nasarar yi mini yanka guda biyu.Daya a damtsen hannu,daya kuma a cinya.Al'amarin daya sa nayi ihu na fadi kasa ita kuwa saita matsoni tana kyalkyala dariya lokacin dana ke ja da baya.Ashikatul Ashiriya ta ce,"haba yarinya ai duk wanda ya riga ka kwana dole ne ya riga ka tashi.Na rantse da darajar karagata koda Haiman na kara ba zai samu nasara ba a kaina bare ke."
Ina cikin jan jiki da baya ne bayana ya tokare da bango babu damar gudu.Koda ganin haka sai Ashikatul Ashiriya ta qara bushewa da dariya tace,"yauwa yanxu kam na rutsa ki kuma cikin ruwan sanyi zan kashe ki na dauke wannan littafi."
Take ta daga takobin ta ta kawo mini sara da nufin ta tsarge ni biyu.Cikin zafin nama na kare saran da littafin nan na Mabudin arzikin Kisra.Ko da takobin ta sari littafin sai hasken nan mai qarfi ya sake baibaye kogon gaba daya.Take ruhin kowa ya dawo aka cigaba da yaki.Ashikatul Ashiriya tayi sauri ta ruga cikin dakin nan don ta karanta wadansu dalasimai na tsafi.Ai kuwa saina bita da gudu na sa kafata na harde ta ta fadi qasa takobin ta ta su6uce daga hannun ta.Kawai saina daka tsalle na dira a kanta muka cigaba da kokawa mu murgina nan,mu hautsina can.
Nan fa ta samu ta hau ruwan cikina ta rinqa naushina a fuska ta hada mini jini hanci da baki,sai dana suma.Sannan ta dagani kuma ta cire littafin nan daga hannuna.Cikin sauri ta rinqa bude shafukan littafin harta zo kan shafin karshe inda aka yi bayanin yadda za'a bude wata kofa ta fita daga cikin kogon da kuma yadda za'a qone kogon gaba daya.Ashikatul Ashiriya ta karanta wadansu kalmomin tsafi saiga wadansu raquma da alfadarai sama da guda dubu dari uku sun bayyana.Bayyanar su keda wuya sai dukiyar nan ta cikin tukwane ta dora kanta a kansu.Ashikatul Ashiriya ta sake karanta wadansu kalmomin sai wata katuwar kofa ta bayyana ta bude kanta.Cikin sauri Ashikatul Ashiriya ta kada raquman nan da alfadaran suka fara fita wajen Kogon Baitul Husuk dauke da dukiyar.Ita ma saita ruga da gudu izuwa kofar don ta fice.Har yanzu ana ta fafata yaki da su jarumi Miqdad sai ragargazar maza yake baima lura da abinda ya faru gare ni ba,bare ya hango Ashikatul Ashiriya wacce ta nufi kofar fita da gudu.
A dai dai wannan lokaci ne na farfado daga dogon suman dana yi,kuma a sannan ne Ashikatul Ashiriya ta isa bakin kofa.Tana zuwa tayi arba da jarumi Haiman tsaye a gabanta ruqe da zabgegiyar wuqa.Cikin tsananin tsoro da fargaba ta ja da baya tana mai nuna shi da dan yatsanta wanda ke karkarwa tace,
"Ashe ba kai na kashe ba tun gabanin shigowar mu cikin kogon nan?"
Jarumi Haiman yace,"kwarai kuwa ni kika kashe amma ban mutu ba,kece dai za ki mutu yanzu."
MU HADU PART D DON JIN CIGABAN WANNAN KAYATACCIYAR HIKAYAR.**MIFTAHUZZARBIL**
LITTAFI NA BIYU.