← Book details Mabanbantan Zukata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 5 OF 10

Chapter 5&6 Ɗazu nayi mistake zan saka 4 sai na saka 5, zanyi wannan a matsayin 5&6

Mabanbantan Zukata Part 1 Complete Hausa Novel · about 17 min read

Ale Idi wanda jikinshi ke rawar tashin hankali ya shiga motar jikinashi na rawa, gidan baya Mahwish ya nufa da Najma yayinda idonshi ke ƙur a kanta yana ganin yanda ta kafeshi da nata idanuwan waɗanda suka yi jazur kamar gauta, du lokacin da idanuwan na ta suka shanye kamar zasu lumshe sai ita kuma ta ware su sosai tare da sakin ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya, wani abu ne ke sake buɗewa a ƙirjin Mahwish.
"Mommynah, kin san mi."
Ya faɗa ba tare da ya janye idonshi daga kan Najma ba.

Mommcy da ta riga ta ruɗe ganin yanda jini ke kwarara daga jikin Najma ta kalli ɗanta da a yanzu ta ke gani wani abu a tattare da shi, wani abu wanda kullum shine fatanta akanshi, wani abu mai muhinmanci a rayuwarshi wanda baya da, wato kwarin gwuiwa.
"A,a son ban sani ba minene faɗamin, da sauri please."
"Ina jin sauyi sosai a zuciyata idan ina kallon idonta, a,a ba idonta ba Mommy cikin idonta akwai wani abu kina iya ganinshi."

Da jin abin da ta faɗa sai Mommy ta zauɗo kanta sai tin fuskar Najma, iya ganinta bata ga komi ba, sai de ta jinjina tsananin jarumta irinta yarinya.
"Banga komi ba son, bana ganin komi sai tarin jarumtaka a tattare da ita."
A kuma daidai lokacinne motocin suka tsaya a harabar hamshakin asibitin( LAGOON HOSPITAL VICTORIA ISLAND).
Da sauri nosis suka iso da gadon ɗaukar marar lafiya aka ɗaura Najwa da Mahwish ya ɗauko a hannuwansa cikin jini, ko da ana tura ta akan gadon hannunsa na cikin nata su na tafiya a tare, lokacin da aka nufi ƙofar emergency da ita, anan ne aka zage hannunsa daga cikin na ta, sai de mi zare hannunta daga cikin na shi keda wuya ya ji wani irin jiri na ɗaukarshi, ba shiri ya duƙa a wajen yana haki gami da maida numfarfashi, cikin alamun soma galabaita ya ce da Mommcy.
"Ruwa."
Ko bayan da ya sha ruwan bai dawo daidai ba, sai ma soma rikice da jikinsa yayi nan take aka bashi gado.
Ale Idi kuwa nan bakin ƙofar emergency ya zauna tare da rafka takumi, nan take wani imani da tsoron Allah ya shige shi, ganin yanda lokaci ɗaya komi ya faru, daga wayewar garin yau zuwa fitowarsu gida da afkuwar lamarin kwata-kwata ba a wuce awanni huɗu zuwa biyar ba, sai ya dinga hango Najma a jiya daya taras ta dawo gida, da yanda ya bita a guje yana zaginta har bakin titi, sai kawai kuka ya sake kwace ma shi, a fili ya dinga furta.
"Faɗima ki yafe min, nasan na gaza wa rayuwarku ta wajaje da dama amma da yardar Allah daga yau na canza, na canza ta sanadiyar ƙaddarar data same ki Faɗima".
Wasu ma'aikata maza ne biyu suka zo inda ya ke zaune cikin tausasa harshe suka soma rarrashin shi da kalamai masu tausasa zuciya, da ya ke aikinsu ne nan da nan suka samar ma shi da ƴar nutsuwa, abin ka da asibitin masu kuɗi, harda sassanya ruwa da abin motsa baki suka aje ma shi, sai de bai iya taɓa komi ba illa ruwa me sanyi, shine ya shanye ruba ɗaya har da rabi, yana ganin kira na shigowa wayarsa da numbobin ƴaƴansa data Mama Saudah amma ya kasa ɗauka, dan bai san yanda zai soma yi musu bayani ba.


Mama Saudah.
"Bai daga ba ko Lawisa, ni dama nasan ba lafiya ba, jikina yana bani ku barshi kawai mu gani zuwa anjima a sake kira ƙila aci sa'a ya ɗauka."
Jiki a sanyaye Lawisa ta ce.
"Gaskiya ko ni na fara zargin da wani abu, idan ba haka ba tayaya za'ayita kiran kayin Baba amma baya ɗauka, Baban da a kira na farko yake ɗaukar waya koda kuwa flashing ne, to kodai inbi bayansu asibitin in gani."
"Eh wallahi Lawisa da gaskiyarki garadai a bi baya aga ko lahiya, bari in ɗauko babur ɗina sai mu je mu gani."
Sauran matan gidan ma du sunyi na'am da Lawal da Lawisa su je su duba amma sai Mama Saudah ta ce.
"A'a Lawal ni ina ganin zaifi kawai a haƙura mu jira dawowarsu, kasan dai halin Babanku idan da matsala ai da tuni ka ganshi nan ya dawo ko ya kira waya mu barwa anjima mu gani."
"A'a Mama bara dai mu je ɗin ko hankalinki ya kwanta kema, bamuso kina wannan kukan wallahi."
Cewar Lawisa tana gyala mayafi suka wuce ita da Lawal, da fatan alkairi kowa ya bisu sannan suka dawo su na tattaunawa akan lalurar Najma, da kuma yanda za'a samo mafita cikin sauƙi.

Aƙalla Lawal da Lawisa sun je ƙananun asibiti kusan biyar amma sam basu samu ganin Ale Idi ba, haka sukayita zagaye haɗi da tambaya ko wani ya gansu, amma ba wani labari, har ma'aikatar sa Najma ke aiki sai da suka je, amma aka hanasu shiga, du magiyar da suka yi ba'a barsu ba hakanan suka juya gida jiki a sanyaye, yayinda suke ta sake kiran number Ale Idi amma sam bata shiga kwata-kwata, yanzu wayar a kashe ta ke.


LAGOON HOSPITAL VICTORIA ISLND
Likitoci kusan su uku ne suka fito su na sharce gumi, daidai lokacin da Alhaji MUZAFFAR da Mommcy suka ƙaraso wajen, yayinda shima Ale Idi ya taso cikin rawar jiki yana tambayar.
"Doctor ta mutu ko, nasan ta mutu ai.!
Sai ya soma share hawaye, amma mi sai Doctor ɗin ya dafa shi tare da faɗin cikin harshe nasara.
"Na taya ka murna abokina, tana a raye bata mutu, mun gama yi mata ɗinki ta samu raunuka masu girma sosai, yanzu haka idanuwanta biyu munyi ma ta allurar barci amma bata amshi jininta ba, zata iya kai awanni biyu jafin ta fara aiki a jikinta, zaku iya ganinta amma banda hayaniya da surutu."
Ale Idi tare da Mommcy suka sauke ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya, da sauri ta damƙi hannu Alhaji Muzaffar suka rufawa Ale Idi baya.

Kwance ta ke saman gadon asibitin, cikinta da cinya harma da kafaɗunta nannaɗe da bandeji, fuskarta ta sake jin jazur idanuwanta ma haka, ta kafe waje ɗaya da ido tana kallo babu ko ƙiftawa.
Alhaji Muzaffar mutum ne me damuwa da dauwar nash kawai, baya sanya damuwar wasu a kanshi, a karo na farko a rayuwarsa da ya ji zuciyarsa ta cike, irin cinkewar da ta ke idan yaga Mahwish a cikin yanayin ciwo, al'ajabi gami da mamaki lulluɓe a saman kamilalliyar fuskarsa, fuskarsa wacce a waje babu wanda yasan damuwa ko farin cikinshi, iya iyalanshi kawai, su kaɗai ne suke gani damuwa akanta amma banda bare.
Ciki de izza ya soma takawa zuwa wajen Najma data tsare Ale Idi da ido tana yi mishi magana amma sautinta bai fita.
Karo na farko da yaji bakinshi ya ambaci sunan wa ta bare da kalmomin "Ƴata." ba iya shi da furucin ya daki kunnenshi a bazata ba, hatta Mommcy sai da ta ware idanuwanta a kanshi, kiran sunan bai ishe shi sai da ya ƙarasa wajenta ya ɗan ranƙwafa tare da shafa kanta da aka zame hular saboda wawakekiyar yarkar da aka yi ma ta.
Tsigar jikinshi ce ta soma tashi ganin yanda ƴar ƙaramar alhaki ta iya jure waɗanan manyan raunukan da ya ke gani, farko da Mommcy ke sanar da shi zuwanta asibiti da abin da ya faru bai kawo komi ba, amma yanzu da yaga yarinyar da hannayensa suka soma ƙirgen iya adadin shekarunda ba zata wuce ba, sai ya ji wani abu ya harbi dakakkiyar zuciyarsa, da kuma ya kirata da sunan ƳATA sai wani fata ya lullube zuciyarshi, fatan da shi kanshi bai san na minene ba, yanzu kuma da ta saka idanuwanta a cikin na shi, sai da zuciyarshi ta yi rawa, jarumta, juriya gami da ƙarfin hali ya ke gani kwance a cikinsu, abin da kullum ya ke buri da mafarkin gani a cikin idon na shi ɗan.
Dafa kafaɗarshi Mommcy ta yi ganin yanda ya kafe yarinyar da kallo.
"Kaima kana ganin abin da Mahwish ya ce min ya gani a tattare da ita ko."
Ba tare da ya ɗauke idonshi daga kant ba ya ce.
"Tabbas na gani."
Wayar da Ale Idi ya soma yi ne ta sa suka ɗago su duka suna kallonsa.
Waya ya ke da Inna Tabawa yana sanar da ita su na asibiti sun yi hatsari ne a hanya, kuka ta fashe da shi tare da tambayarshi wace asibitice suke gatanan zuwa.
Dawo da kallonsa yayi wajen su Mommcy sai ya tambayesu cike da girmamawa.
"Ranku ya daɗe nace ya sunan asibitin nan iyalaina na nan tafe zuwa dubiya."

Mommcy ce ta faɗa ma shi sunan sannan ta ƙara da tambayarshi miye sunan unguwar ta su sai ta aiki driver ya je ya ɗauko su.
Wani yanayi ne ya gifta akan fuskar Alhaji Muzzafar, ba tare da ya ce komi ba ya soma takawa cike da izza ya fice.

Jiki a sanyaye Mommcy ta bi bayanshi, ɗakin da aka kwantar da Mahwish ta nufa, tana buɗe ƙofar ta iske Papie zaune akan kujera ya tsurawa Mahwish wanda na'urori ke aiki ta ko ina a jikinsa ido, zama ta yi itama tare da kafe Mahwishi da ido, tsintar muryar Alhaji Muzzafar ta yi yana faɗin.
"Ki basu iya adadin kuɗaɗen da zasu ishesu jinya, amma karki kuskura ki sake kusantarsu, suɗin talakawa ne, bana son wa ta alaƙa ta kusa kota nesa ta sake haɗaku."
Cike da girmamawa ta gyaɗa kai, a can ƙasan ranta ta na jin wani iri, ta sani bama ita kaɗai ba du wani wanda ya ke cikin MUZZAFAR FAMILY basa hulɗa da talakawa, saboda wani lamari daya auku a can baya, haka kawai sai ta ke jin kamar zasu rasa wani abu wanda suka jima su na nemane a tattare da waɗannan talakawan, kamar zasu aikata kuskure idan suka nisance su......✍🏻
TAKU HAR KULLUM

MARYAM STAR.

Follow the MARYAM UMAR HAUSA NOVELS BOOKS LIBRARY 📚📚 channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb8OWPtBKfi1C9DGBa13
𝙈𝘼𝘽𝘼𝙉𝘽𝘼𝙉𝙏𝘼𝙉 𝙕𝙐𝙆𝘼𝙏𝘼❤️‍🩹❤️‍🔥

𝙎𝙏𝙊𝙍𝙔 & 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙏𝙀𝙉
𝙈.𝙎𝙏𝘼𝙍⭐⭐⭐

💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉 💪

𝗧𝗛𝗘 𝗦𝗛𝗜𝗗𝗢𝗥𝗜𝗔 𝗪𝗥𝗜𝗧𝗘𝗥'𝘀 𝗧𝗘𝗔𝗠💪✍🏻

𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚𝙧 7

Kamar yanda Mommcy ta ce, driver ta tura bayan Ale Idi yayi ma shi kwatancen gidanshi, babu ɓata lokaci ya tafi ya kwaso mutanen gidan kusan su goma sha, tun ciki motar su ke baza ƙauyanci sunata sambatun kyawun motar da kuma girmanta.
Lokacin da suka isa asibitin kuwa, bakunansu a buɗe suka soma santin kyawun asibitin, sai de lokacin da suka yi tozali da fuskar Ale Idi suka ganshi a sanyaye, sai suka dawo hayyacinsu suka cigaba da jimanta lamarin.
Dukaninsu sai da suka sha kuka sosai ganin yanda kamar Najma ta sauya nan take, dan ma lokacin da suka zo barci ya ɗauketa, Mama Saudah ko sai da aka fidda ita waje dan kuka ta yi sosai, sama-sama Ale Idi ya basu labarin abin da ya faru, sosai suka yi addu'ar samun sauƙi ga Najma suka kuma nemi ya nuna musu waɗanda suka taumakesu, bai musa ba ya nufi haɗaɗɗen word ɗin da aka kwantar da Mahwish sai de du magiyar da sukasha ba'a barsu sun shiga ba, dan murɗa-murɗan securitys ne kusan guda biyar ke gadin ƙofar, hakanan suka koma suka ci gaba da tagumi.

Najma bata farka ba sai marice lis lokacin an maida ƴan gidansu, daga Inna Tabawa sai Mama Saudah shima Ale Idi ya tafi yaɗan huta dan zazzaɓi ne rau a jikinshi.
Mommcy ce ta shigo ɗakin hannunta ɗauke da wa ta madaidaiciyar jaka, nan suka gaisa da Mama Saudah suka kuma yi ma ta godiya sosai na irin taimakon da tai musu, amsasu tayi da babu komi sannan ta miƙawa Mama Saudah da take ganin kamar Najma kwance akan fuskarta, jakar kuɗin tare da yi mata bayani akan kuɗin jinyar yarinyarta ne me gidan Alhaji Muzaffar ya biya.
Har kuka sai da Mama Saudah ta yi ganin yawan kuɗaɗen bayan taimako da suka yi na ceti ran Najma suka kawota asibiti cikin lokaci.
Mommcy ta juya ta fice tana sake kallon jar fuskar Najma, tana fatan daina jin abin da ta ke ji akanta, tunda ƙaddara ce ta haɗa su kuma ita ce ta rabasu a yanzunan.
Sai de abin da bata saniba shine, wannan ƙaddarar me tsawo ce, hasalima yanzu za'afara ba'ayi komi ba, haka zalika bayan nan akwai wani wajen inda zata sake haɗasu, ba tare da su kansu sunyi tunani ba.

Kusan lokaci ɗaya Najma da Mahwish suka farka, sabanin ita data farka tana jinta garas saboda allurar kashe zugi bata sake ta ba, shi da matsanancin ciwo ya farko, kwararrun doctors ne zagaye da shi sunata faman aikinsu, yayinda Mommcy ta kwantar da kanta akan cinyar Papie ta shiga rero kuka kamar ƙaramar yarinya.
Likitocin sun yi iya yinsu akan shi amma sai a hankali, da kyar suka shawo kanshi matsalar, hakan ya saka bayan sun fito suka nemi ganin Papie.

Ko da ya je bayani suka yi ma shi akan yanda ciwon kullum yake ƙara gaba, zuciyarshi na ƙara raunana, ta yanda ba lallai ya iya sarrafa kanshi ba saboda raunin da ta yi, da buƙatar su samo wanda zai iya kula da shi, sam basu gane bayanin doctor na samo wanda zai kula da shi ba, dan haka sai Mommcy tayi karaf ta ce.
"Waye wanda zai kula da shi fiye da mu, muna bashi duk wata kulawa ta musamman hasalima a tare da shi muke barci a gado ɗaya."

Murmushi baturen likitan yayi sannan ya zare glass ɗin idonshi tare da duskantarsu da kyau sannan ya ce.

"A halin yanzu kulawar da kuke bashi sam ba ita yake buƙataba, yana buƙatae farin ciki da tarairaya, sannan yana buƙatar abin da zai dinga bashi ƙwarin guiwa, saboda rauninsa yayi yawa sosai."

Cikin lafiyayyen turanci Papie ya ce da doctor.
"Du abin da ka lissafo babu wanda muka rageshi da shi, muna yi mashi duk abin da ya dace, sai de idan wasu sharuɗɗan daban zaka bamu."

"Sorry freind, shin yanada mata ne ko budurwa?."
Tambayar ta zo musu a bazata, sai da suka kalli junanau sannan suka haɗa baki wajen faɗin.
"A'a babu."

"Good, to yana buƙatar mace arayuwarshi, amma macen jaruma mai taurin zuciya, wacce zata iya tafiyar da rauninshi ta bashi gwarin gwuiwa haɗi da kulawa."

Kalaman doctor sun haska wani abu a cikin kawunansu, su duka biyun hotonta ne ya gilma musu, amma sai suka maze suka ci gaba da sauraren doctor.

BAYAN KWANA BIYU.
Kwanan Najma biyu a asibiti aka sallameta bayan anyi mata du abin da ya dace, anbasu kayan dressing ingantatu akan du bayan sati ɗaya za'adinga wanke ciwon ana canza dressing.
Godiya da sanya alkairi Ale Idi yayi, sanan suka kwashi inasu-inasu sukai gida.
Har zuwa lokacin Najma bata nuna ta damu da ciwon da ke jikinta ba, hasalima tafi damuwa da damuwar Abdul da ke ƙara girma a zuciyarta, tana jin muddin zata haɗu da shi babu abin da zai hanata aiwatar da ƙudurinta, yanzu haka Allah-Allah ta ke ta warke ta koma aiki tasan acanne kawai zata dinga ganinshi.
Tattara kuɗaɗen da Mommcy ta basu suka yi suka aje gefe, basu taɓa ko sisina saboda shawarar da Inna ta bayar cewa a aje sai Najma ta samu sauƙi.
Yanzu du wannan hayaniyar ta ragu sosai, duda ba komi aka fasa ba, musamman habaice-habaice da ya riga yabi jikinsu, ana zama a zagaye Najama kowa na son yi mata fira dan ganin ta sake ta koma yanda ta ke a baya.
Yanznma Lawisa ce ke basu labarin wani saurayi da ta taɓa yi ya biyota kan hanya, shine dan taƙi kulashi kawai ya kama zaginta, harda jifarta da munanan maganganu, aiko ta kanainaye shi da dinga ɗirma ihu ta tara mashi mutane tace rasin ɗa'a yayi mata, nan matasa suka lakaɗa ma shi shegen duka suka barshi a wajen.
Buɗar bakin Najma sai cewa ta yi.
"Idan nice ke sai na fara ɗauke fuskarshi da zafafan maruka da zasu makanta ganinshi, sannan in laƙa ma shi shairin da babu wanda ya isa ya fitar sa shi, sai na tabbatar da na rabashi da du wani farin ciki na rayuwarshi sanan in kyaleshi."
Sai kowa yai tsuru ana kallon yanda ta ke magana a kausashe har tana taune busasun laɓanta.
Daga kuma wannan maganar bata sake magana ba har tsayin kwanaki biyu.


Mahwish.
Sai da ya shafe kwanaki huɗu baya huyyacinsa, a rana ta biyar ne ya farko, daga yanda yaga kwarin idanuwan Mommcy sun zurma can ciki, ya tabbatar da ya jima a kwace dan sosai yake ganin ramar da ta yi, duda a kimtse ta ke ciki wani arnen leshi me tsada a ido zaka fahimci kwayun da ta yi, amma shi kallon farko yaga rashin nutsuwa a tattare da ita.
A hankali ya ɗaga hannunsa sai tin inda ta ke tsaye bayan doctor kaɗan, da sauri ta matso kusa da shi tare da saka hannunshi cikin nata ta matse da ɗan ƙarfi hawaye na silalo daga gefen idanuwanta, sumbatar hannunshi ta yi tana jin yanda tsananin ƙaunarshi da tausayinshi ke zagaye jinin jikinta, da ace tana da dama, data cire ciwon daga jikinshi koda na kwana ɗaya ne, shima ya huta yayi sayuwa kamar kowa ba tare da ciwo ba.
Sake sumbatar hannunshi ta yi, tana jin yanda hannun yai lagai a cikin nata, sosai ta ke tsananin tausayin Mahwish musamman yanzu da take ganin rauni na sake baibaye rayuwarsa ba kamar baya ba, yanzu sam bashi da wani karsashi, tana son ganin tilon ɗanta ya watayawa kamar kowanne ɗa.
Bayan Doctor ya gama dube-dubensa ya ma fitar da magungun da za'a bashi a lokacin bayan ya saka wani abu a cikinsa, sai ya fice yana jinjina lamarin Mahwish ɗin, ba shi ba duka doctors da nurses da ke aiki a wannan asibitin sun san Mahwish da lalurarsa, muddin su na ƙasar ba'a rufe sati ɗaya ba tare da ankawoshi cikin halin ciwo ba, su kansu likitocin su na mamakin yanda har zuwa wannan lokacin ya ke a raye bayan irin baƙar wahalar da ya ke sha tun tasowarshi. (Sun manta da Allah ne me yin yanda ya so a kuma lokacin da ya so, babu me kashewa sai shi, kuma babu me rayawa sai shi, babu mai jah da al'amarinsa buwayi gagara misali Ubangijin hallitu baki ɗaya mai raha da jin ƙai.).
Mommcy ce ta taimaka ma shi yayi brush sannan ya yaɗansha tea shima ɗan kaɗan, sai ayaba da yaci kwaya ɗaya shikenan haka ta haɗa ma shi maganin, to fa anan ake yinta, dan sam Mahwish bai ƙaunar magani a rayuwarsa, duda kuwa ya zama abokin rayuwarshi dan ƙa'ida ne kullum sai ya sha su tun daga safe har dare, kullum sai anyi dambarwa da shi akan shan magani kamar wani ƙaramin yaro.
Yanzunma kauda kai gefe yayi tare da marairaicewa ya wani sake narke noƙaƙƙiyar muryarsa irinta marasa lafiya sannan ya ce.
"Please Mommy bana so."
"Sorry Love ni kuma ina so please."
Ta faɗa itama a marairaice kamar yanda ya yi.
sake shagwaɓewa ya yi sannan ya ce.
"Ni fa Mommy na ɓata da ke, yanzu sa Papie nike shiri dan haka ba kece za ki bani ba."
Yan da yai maganar ya sakata mirmusawa ba shiri sanna ta ce cikin mirmushi.
"Haba Love, sarai nasan halinka fa, shima Papie ɗin idan ya zo zaka ce kun ɓata ne, dan haka tun da mun ɓata maza amshi ka shanye ko in zane ka."
Ta yi maganae tana ɗaga hannunta ɗaya sama alamar zata kai suka, shi dariyama ta bashi, idan akwai abin yasan ba zata iya yi ba sam a rayuwarta, bai wuce dukanshi ba, matar da ko tsawa bata iya yi mishi bare kuma duka, ko kallon banza taga ana yi mishi sai inda power ta ta tsaya, saje taƙune fuska yayi tare da ɗora hannu ɗaya bisa kai kamar zai rusa ihu sai kuma ya ce.
"Shikenan tun da kin daina yi na, bani insha amma daga wannan ba zan sake shan wani ba."
Yanzu kam sosai tai dariya ganin yanda yayi zuba mashi kwayoyin ta yi a hannu tare da bashi ruwa, har lokaci da alamun dariya akan fuskarta.
Dariyar da ta sanyaya ran Mahwish har ya shanye magungunan ba tare da yaji antakurashi ba kamar kullum, kamar yanda ta ke a yanzu haka ya ke da burin ganin fara'arta a kullum, murmushinta na matuƙar sakashi farin ciki.
Duda sam baya jin daɗin jikinshi hakanan yai ta mazewa suka ci gaba da dira, ko Doctor da ya zo da takardar sallamarshi sosai yayi mamaki da ganin yanda Mahwish ɗin ya ware kamar ba shi, fatan samun sauƙi yayi mishi sannan ya sallamesu.
Sai da suka jira Alhaji Muzaffar ya zo sannan suka ɗunguma suka yi gida.
Akan hanya su na tafene kawai amma sam hankalinshi baya kansu, yana kan abin da tun da ya buɗe ido yake so ya ji wani bayani amma ya ji shiru, magana ce ta kubce daga bakinsa ba tare daya shirya ba.
"Wai Mommy ina wannan yarinyar Najwa ya jikinta ta farka kuwa."
Ɗif su dukansu suka yi tare da zubawa Mahwish ido, a daidai lokacinne motocin suka tsaya a kusa da sashensu, basu ce da shi komi ba illa sunkutarshi da Papie ya yi suka fice zuwa sashensu.
A saman luntsumemiyar sofa ya zaunar da shi, yayinda Mommcy ta danna oder da ke shedawa ma'aikatan kitchen ana nemansu da gaugawa, ma'aikata ne su biyu mata kowace hannuwanta riƙe da ƙaron tire, cike da girmamawa suka aje tare da jiran umarni, da hannu Mommcy ta sallame su, bayan ta tsiyayi ruwan tattaciyar kwakwa me sanyin ta miƙawa Papie, murmushi ya sakar ma ta sannan ya nufi bakin Mahwish da cup ɗin, shima tattausan marayan murmushi ya sakar musu su duka biyun sannan ya kirɓa a sanyaye yana jin yanda sanyin ya ratsa du wa ta gaɓa da ke aiki a jikinsa.....✍🏻

Taufa, ina team Mahwish ina Team Najma, shin mi kuke tunani game da waɗanan mutanen biyu masu mabanbanyan zukata.❓❓❓❓

YAUDAI IDAN BANGA COMMENT DAYAWA BA GOBE BABU UPDATE DAMA ZAN SHIGA BUSY.

NI CE TAURARUWARKU

MARYAM SYAR ⭐⭐
https://whatsapp.com/channel/0029Vb8OWPtBKfi1C9DGBa13

𝙈𝘼𝘽𝘼𝙉𝘽𝘼𝙉𝙏𝘼𝙉 𝙕𝙐𝙆𝘼𝙏𝘼❤️‍🩹❤️‍🔥

𝙎𝙏𝙊𝙍𝙔 & 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙏𝙀𝙉
𝙈.𝙎𝙏𝘼𝙍⭐⭐⭐

💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉 💪

𝗧𝗛𝗘 𝗦𝗛𝗜𝗗𝗢𝗥𝗜𝗔 𝗪𝗥𝗜𝗧𝗘𝗥'𝘀 𝗧𝗘𝗔𝗠💪✍🏻
Chapter 5 · 0% Book details