Sashe 9
Canjin Rayuwa Part 4 Complete Hausa Novel · about 5 min read
2⃣7⃣Nurse tayi shiru tana matuqar mamakin lamarin. Can tace, to wai wanene yayi mata dukan jikinta? Tace, shine ya duke ta. Wlh haka yakeyi. Yayita auro 'ya'yan mutane yanacin zalinsu. Nurse din tace, kinga ko Mama da ace Allah zan hadaki da ainihin babbar likitar dake da wannan asibitin. Kiyi mata bayani, wlh zata gyara masa zama. Maman bushira tace, rufamin asiri. In ya sani ai na shiga uku, domin dama inacin darajar manyan 'ya'ya na ne, sai kuma irin wannan ranar in yayi ta'asarsa yazo ya matsamin in tayashi. Nurse tace, inda zaki iya da na hadaki da ita. Allah zatayi muku maganinsa, sai ya daina. Kuma ko daya sunanki ba zai fito ba. Tace, to shikenan ki hadamu don zan mata bayani, amma don Allah kamar yadda kkce, kar sunana ya fito. Tace, ba damuwa. Gobe ai kina nan ko? Tace, eh nizan kwana, amma na san shima zaizo da safe. Alhaji lawal, tunda yaje Gida ya tara sauran matan yasa su suka gyara gurin jinin. Shi dai tunda ya shige dakinsa ya zauna ya zabga Tagumi, ya rasa bakin magana. Da na sani ce cankas a zuciyarsa. Tsoronsa daya kar 'yar mutane ta mutu. Ranar dai bai runtsa ba, sai juyi yake. Washegari tun takwas ya nufi asibitin. Lokacin Zainabu tana varci don ta farka cikin dare har Maman bushira ke bata labarin yadda sukayi da Nurse. Zainabu tayi ta roqon ta akan cewa, ta taimaka mata don Allah don Allah ta fadawa mai asibitin.
Ya kalli Maman bushira yace, ya jikin nata? Tace, da sauqi. Yace, ta farka? Cikin son qara tsorata shi, tace eh ta farka, amma bata cikin hayyacinta. Domin bata ganeni ba ma. Alhajin ya sake rudewa. To likitan bai sake dubata bane? Ance asibitin kudi, kuma na bada duk abinda akace, amma ba zasu duba ta yadda ya kamata ba? Zai fara sababinsa tace, Alhaji gara fa kabi ahankali sbd likitan ya fara tambayoyi akan shedar dukan dake jikinta. Sannan zuwan su biyu nemanka. Yace, to ni dai bari ma inzo in tafi kawai. Ya ciro kudi ya qirga dubu goma ya bata, "ga wannan ki riqe a gurinki. In sun tambaye ni kice nayi tafiya. Sannan karki sake aji daga bakinki cewa, ni na duketa." Tace, to shedar dukan fa data fito a jikinta? Yace, kice musu bulala ce ta fito mata. Ba awai ciwon bulala ba? Tamkar Maman bushira ta saki dariya, sbd ganin yadda Alhajin ya birkice. Bayan tafiyarsa tace, ai zaka gane kuranka. Nurse dai tazo kamar yadda tace, kuma ta raka ta har gurin mai Asibitin a cikin ofishinta. Da ma takan zo qarfe goma ta tashi sha biyu. Bayan Maman bushira ta gaisheta ne, sai Nurse din tace, gata nan momy. Doctor din ta kalleta, malama kiyimin bayanin dana samu daga wannan Nurse din. Maman bushira tayi mata bayanin yadda abin ya faru har ya kaiga dukanta. Sannan tace, tashi muje in ganta. Sun samu Zainabu ta farka. Tana ganin likitar ta soma kuka tana cewa, don Allah ta taimake ta. Likitar tace, karki damu, hadin kanki nake buqata. Tayi ma Zainabu tambayoyi, ta amsa. Sannan tace, to babu damuwa qarfe nawa zaizo? Maman bushira tace, ai yazo har ya tafi. Kuma zaiyi wuya ya qara zuwa don a tsorace yake. Likitar tace, qarfe nawa za'a saleshi a Gida? Tace takwas na safe ko tara na dare. Likitar tace, babu komai.
2⃣8⃣Doctor Asma'u Adamu mace ce mai kamar maza. Tana da taimako sosai, musamman akan abinda ya Shafi mata. Duk lokacin data samu matsala makamanciyar wannan, ko ba'a Asibitinta ba ne, takan nemar wa mai haqqi haqqinta. Har ta kai ga kafa qungiya mai qwato wa mata 'yanci. Suna da lauyoyi da mai qwato wa mata 'yanci. Suna da lauyoyi da 'yan sanda da malamai da kuma alqalai a cikin qungiyarsu. Bada 6ata lokaci ba suka rubuta takarda suka aikawa 'yan sanda, inda suka gayyaci Alhaji lawal zuwa ofishinsu. Da yaso yayi gardama, sai suka tura masa 'yan sanda. Dole ya zo suka tasa shi har asibiti. Lokacin Zainabu tana zaune tana shan tea. A cikin kudin daya ba Maman bushira ta fita ta siyo kayan tea din. Sun duba jikinta kuma sunyi mata tambayoyi ta basu bayanin duk avinda kenan tun daga tun daga tursasa mata auren sa da akayi har zuwa yau dinnan. Sun tasashi har Gidansu Zainabu inda aka taso qeyar innar Zainabu. Likita Asma'u ta rufe innarsu Zainabu da fada. Tace, aje a rufesu, sai gobe za'a shiga dasu kotu. Nan fa hankalin Alhaji yayi matuqar tashi. Ya shiga bada baki, tare da roqon don Allah ayi masa afuwa tunda bata sonshi, yaji kuma ya haqura, zai sake ta. Likita tace, ai dama wannan dole ne, sannan kai zaka kula da ita har ta warke, sannan ka dauki nauyin cikinta, har ta haihu ta yaye. Yace, duk na yarda.
Ita kuwa inna, saida aka rubuta takarda dasa hannu kan cewa ba zata sake tursasa ta ba. Cikin su duk wanda ya sake, sai yayi zaman jarum. Bayan gargadi mai tsanani aka sallamesu, bayan Alhaji ya rubuta takardar sakin Zainabu, yayin da maman bushira ta shirya yanata-yanata, ta dauki kudin da Alhajin ya bata, taba Zainabu. Zainabu taba ta dubu uku daga ciki. Har taqi kar6a, Zainabu tace, lallai saita kar6a. Ta qara da cewa, taimakon da kk yi min, Allah ne kawai zai biyaki. Murna gurin Zainabu tamkar sallah, wannan sakin da akayi mata, matsalarta daya, wannan cikin dake jikinta. Kwana uku ta qara aka sallameta. Suka je ta kwashe nata-yanata suka nufi Gida. Kafin su wuce, dama likita ta tabbatar ma da Zainabu duk wata, gurinsu zata dinga zuwa ta amshi duk abinda aka yanke dashi. Shi kuma sun tabbatar masa cewa, sun saka ido akansa, in ya sake yiwa 'yar wasu haka, to ba shakka zai qare rayuwarsa a Gidan kaso.
[18/09 3:31 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
Ya kalli Maman bushira yace, ya jikin nata? Tace, da sauqi. Yace, ta farka? Cikin son qara tsorata shi, tace eh ta farka, amma bata cikin hayyacinta. Domin bata ganeni ba ma. Alhajin ya sake rudewa. To likitan bai sake dubata bane? Ance asibitin kudi, kuma na bada duk abinda akace, amma ba zasu duba ta yadda ya kamata ba? Zai fara sababinsa tace, Alhaji gara fa kabi ahankali sbd likitan ya fara tambayoyi akan shedar dukan dake jikinta. Sannan zuwan su biyu nemanka. Yace, to ni dai bari ma inzo in tafi kawai. Ya ciro kudi ya qirga dubu goma ya bata, "ga wannan ki riqe a gurinki. In sun tambaye ni kice nayi tafiya. Sannan karki sake aji daga bakinki cewa, ni na duketa." Tace, to shedar dukan fa data fito a jikinta? Yace, kice musu bulala ce ta fito mata. Ba awai ciwon bulala ba? Tamkar Maman bushira ta saki dariya, sbd ganin yadda Alhajin ya birkice. Bayan tafiyarsa tace, ai zaka gane kuranka. Nurse dai tazo kamar yadda tace, kuma ta raka ta har gurin mai Asibitin a cikin ofishinta. Da ma takan zo qarfe goma ta tashi sha biyu. Bayan Maman bushira ta gaisheta ne, sai Nurse din tace, gata nan momy. Doctor din ta kalleta, malama kiyimin bayanin dana samu daga wannan Nurse din. Maman bushira tayi mata bayanin yadda abin ya faru har ya kaiga dukanta. Sannan tace, tashi muje in ganta. Sun samu Zainabu ta farka. Tana ganin likitar ta soma kuka tana cewa, don Allah ta taimake ta. Likitar tace, karki damu, hadin kanki nake buqata. Tayi ma Zainabu tambayoyi, ta amsa. Sannan tace, to babu damuwa qarfe nawa zaizo? Maman bushira tace, ai yazo har ya tafi. Kuma zaiyi wuya ya qara zuwa don a tsorace yake. Likitar tace, qarfe nawa za'a saleshi a Gida? Tace takwas na safe ko tara na dare. Likitar tace, babu komai.
2⃣8⃣Doctor Asma'u Adamu mace ce mai kamar maza. Tana da taimako sosai, musamman akan abinda ya Shafi mata. Duk lokacin data samu matsala makamanciyar wannan, ko ba'a Asibitinta ba ne, takan nemar wa mai haqqi haqqinta. Har ta kai ga kafa qungiya mai qwato wa mata 'yanci. Suna da lauyoyi da mai qwato wa mata 'yanci. Suna da lauyoyi da 'yan sanda da malamai da kuma alqalai a cikin qungiyarsu. Bada 6ata lokaci ba suka rubuta takarda suka aikawa 'yan sanda, inda suka gayyaci Alhaji lawal zuwa ofishinsu. Da yaso yayi gardama, sai suka tura masa 'yan sanda. Dole ya zo suka tasa shi har asibiti. Lokacin Zainabu tana zaune tana shan tea. A cikin kudin daya ba Maman bushira ta fita ta siyo kayan tea din. Sun duba jikinta kuma sunyi mata tambayoyi ta basu bayanin duk avinda kenan tun daga tun daga tursasa mata auren sa da akayi har zuwa yau dinnan. Sun tasashi har Gidansu Zainabu inda aka taso qeyar innar Zainabu. Likita Asma'u ta rufe innarsu Zainabu da fada. Tace, aje a rufesu, sai gobe za'a shiga dasu kotu. Nan fa hankalin Alhaji yayi matuqar tashi. Ya shiga bada baki, tare da roqon don Allah ayi masa afuwa tunda bata sonshi, yaji kuma ya haqura, zai sake ta. Likita tace, ai dama wannan dole ne, sannan kai zaka kula da ita har ta warke, sannan ka dauki nauyin cikinta, har ta haihu ta yaye. Yace, duk na yarda.
Ita kuwa inna, saida aka rubuta takarda dasa hannu kan cewa ba zata sake tursasa ta ba. Cikin su duk wanda ya sake, sai yayi zaman jarum. Bayan gargadi mai tsanani aka sallamesu, bayan Alhaji ya rubuta takardar sakin Zainabu, yayin da maman bushira ta shirya yanata-yanata, ta dauki kudin da Alhajin ya bata, taba Zainabu. Zainabu taba ta dubu uku daga ciki. Har taqi kar6a, Zainabu tace, lallai saita kar6a. Ta qara da cewa, taimakon da kk yi min, Allah ne kawai zai biyaki. Murna gurin Zainabu tamkar sallah, wannan sakin da akayi mata, matsalarta daya, wannan cikin dake jikinta. Kwana uku ta qara aka sallameta. Suka je ta kwashe nata-yanata suka nufi Gida. Kafin su wuce, dama likita ta tabbatar ma da Zainabu duk wata, gurinsu zata dinga zuwa ta amshi duk abinda aka yanke dashi. Shi kuma sun tabbatar masa cewa, sun saka ido akansa, in ya sake yiwa 'yar wasu haka, to ba shakka zai qare rayuwarsa a Gidan kaso.
[18/09 3:31 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa