Gabatarwa
Busa A Mutu Part 2 Complete Hausa Novel · about 24 min read
ßµŠÅ Ä MµTµ
Littafi Na Biyu (2)
Part A
Na Abdulaziz Sani M /Gini
Marubucin Yaci Gaba Da Cewa
SA'ADDA boka Rufyan ya zo
jawabinsa sai hankalin yarima Muraisu ya
dugunzuma har kwalla ta zo masa, ya dubi boka
Rufyan cikin tsananin takaici ya ce, "Yanzu ke nan
kana nufin cewa nima mutuwa zan yi nan ba da
dadewa ba kuma idan ban auri gimbiya Husnaila
ba shi ke nan babu mai kawar da su azzalumaí
Huraisu?".
Koda jin wannan tambaya sai boka Rufyan
yai shiu ya kasa cewa komai, kawai sai ya mike
tsaye ya koma can gefe daya ya zauna yana mai
sunkui da kansa kas. Cikin fushi yarima Muraisu
ya mike zumbur yaje gabansa ya tsaya ya dubeshi a
fusace ya ce, "Saboda me ka ki baní amsar
tambayata?"
Boka Rufyan ya dago kai ya dubi yarima ba
tare da shakka ko tsoro ba ya ce, "Ai ba kowacce
tambaya ce ke da amsa ba. Ina so ka sani cewa
zamanmnu anan bashi da wani amfani, domin zaman
Jaki da kaya ne. Idan kana ganin za ka bi wadannan
matakai na samun matar da za ka aura ka tashú mu.
bi sawunsu gimbiya Husnaila.
Dik da cewą tsakaninmu da su akwai tazarata
a kalla tafiyar kwana arba'in, zan iya đaurc mana
kasa mu riskesu a cikin kwana shida da yini daya,
domin ka yakesu ka rabasu da Husnaila idan ka yi
nasara sai mu rakaka izuwa bakin dajin Kirzufa mu
-tsaya daga wajensa kai da Husnaila ku shiga
cikinsa, ba za ku fito ba sai bayan kwana ukun.
Sannan mu rankaya mu tafi izuwa can birnin Lairuf
domin a yi shagalin bikinku",
Lokacin da boka Rufyan ya zo nán
jawabinsa sai jikin yarima Muraisu ya yi sanyi, ya
koma can gefe ya zauna kuma ya yi tagumi inda ya
fada cikin kogin tunani.
Ba wani abu yake tunawa ba face gagarumin
aikin da ke gabansa wanda ya i karfin tunaninsa.
Abinda ya fara fado masa a rai shi ne, ta ya ya zai
iya tarwatsa wadannan dakaru guda dubu dari uku
shi kadai alhalin KAIFI DA TSINI baya tasiri a
jikinsu? Kuma idan za a kwana uku ana yaki da su
ba z4 su gaji ba? Abu na biyu, ta ya ya zai iya shiga
dajin Kirzufa ya har ya yi kwana uku a cikinsa
alhalin mahaifinsa ma da kyar ya iya yin sa'o'i a
cikinsa?"
Koda Muraisu ya zo nan a tunaninsa sai ransa
. ya baci ya ga cewa boka Rufyan ya raina masa
hankali, domin bai ga dalilin da zai sa ya umarceshi
yin abinda shi kansa ya san cěwa ba zai yiwu ba.
A fusace ya sake mikewa tsaye ya nufi kan boka
Rufyan gadan-gadan, kawai sai boka Rufyan ya
mike ya tareshi ya ce, "Idan ka so ka zare
takobinka ka kasheni yanzu take, amma ka sani
cewa zabi daya ne garcka cikin biyu. Walau ka
koma gida ka zuana ka įira ranar da makiya za su
Z0 Su cimu da yaki, kana ji kana gani, ko kuma ka
nemi matar aurenka wacce za ta haifa maka dan da
Zai kwatar mana 'yanci anan gaba. Ko ka ki ko ka
so baka isa ka sauya kaddara ba.
Babu makawa sai an ci mu da yaki kuma ba
lallai bane ni ko wadannan abokan tafiya namu
dayanmu ya yi nisan kwanan da zai ga ranar da za
a karbar mana 'yancin mu ba."
Koda jin wannan furuci sai jikin yarima
Muraisu ya yi sanyi a karo na biyu, ya koma inda
yake ya zauna yai shiru bai ce komai ba, ya shuga
sabon tunani. Nan take yaji duniyar gaba đaya tayi
masa zali, musamman da ya tuna cewa shi fa yanzu
bashi da uwa kuma a ko yaushe ma zai iya rasa
mahaifinsa.
"To wai shin na akan Wane dalili zai damu da
duniya tunda bashi da saran masoyi?"
Wata zuciyar kuma ta ce da shı, "To mene ne
am fanin kaina ka gushe kamar yadda iyayenka za
Su gushe ba. tare ta ka bar. zun ar da za a gania
Tinka tunawa da kai ba?"
Koda ya zo nan a tunaninsa sai hawaye ya
zubo masa. Yana dago kai ya ga kuyanga Sabirat
tsaye a gabansa. Sabirat ta zauna kusa da yarima
Muraisu ta dubeshi a nutse, sannan ta ce, ""Ya kai
jarumin kwarai, ka yi sani cewa namijin baya kuka,
kuma bai san tsoro ba. Shi ne wanda baya shakkar
shiga ckin kowanne irin bala'i kuma shi nc wanda
bai dauki RAI a bakin komai ba, muddin bukata za
ta biya."
Koda yarima Muraisu yaji wannan batu sai
dukkanin tsoro ya kau daga cikin zuciyarsa kawai
sai ya dubi Sabirat ya yi murmushi ya ce,
"Madallah da kuyanga ta gari wacce ke yiwa
ubangidanta tuni bisa abinda ya kamaceshi."
Gama fadin hakan ke da wuya sai Muraisu ya
mike tsaye ya dubi Boka Rufyan da Badakare
Kirzal ya ce, "Ma za ku samu akan hanya wacce za
ta kaini inda zan riski gimbiya Husnaila da
jama'arta a cikin kankanin lokaci"
Kafin Muraisu ya gana rufe bakinsa tuni
Kurzan da Rufyan sun mike zumbur sun kama
dawakansu sun haye. Saoirat da Muraisu ma suka
yi sauri suka hau nasa dawakan. Kurzal ne ya wuce
. kan gaba, Boka Kufyan na-biye da shi sannan su
yarima.
Dukkaninsu suka sukwani dawakansu da
gudun tsiya suka nausa cikin daji.
Nan fa Yarima, Kurzal da Sabirat suka rinka
ganin abin al'ajabi, domin cikin dakiku kadan suka
rinka shafe tafiyar sa'o'i. Nan da nan suka ga sun zO
wani wuri maj irin yanayi dabam da sauran
dazuzzukan da suka wuce.
Shi dai wannan wuri da suka zo ya kasance
daji ne mai yawan lumshi tamkar rana ba ta taba
baiyana ba a cikinsa. Bishiyoyin da ke cikinsa
kuwa duk dogaye ne masu fala-falan ganyaye, haka
kuma akwai duwatsu manya-manya in-in masu
tsawo da fadi.
Koda 1SOwar Su yarıma wannan wuri sai
Kurzal yai sauri ya sauko daga kan dokinsa ya kifa
kunnensa akan kasa yai nazari, sannan ya mike
tsayc, ya dubi yarima ya ce, 'Ya shugabana nan
gaba kadan tafiyar 'yan dakiku akwai mutanc sama
da guda dari biyu a labe cikin duhuwar bishiyoyi".
Koda jin haka sai Boka Rulyan ya yi
murmushi, sannan shuma ya dubi yarima ya ce, "Sai
ka shige ciki ka riskesu ka karbo gimbiya Husnaila
ta kowanne hali. Mu kam amu Jiraka ne nan har
iZUwa tsawon sa'a bakwaj.
Jdan ka fito da nasara sai mu rakaka izuwa
bakin dajin KirZula, acan mas mu jira izuwa
sa'adda za ku kwana uku a cikinsa ku fito, sannan
mu rankaya gaba daya izuwa gida. Idan kuma mu
ka ji shiru ba ka fito ba, mun san ccwa ka hallaka
sai mu juya mu koma gda".
Yarima Muraisu ya gyada kai ya ce, "Haka za
a yi". Kawai sai ya juya zai shiga cikin wannan daji
mai kwarjini, ai kuwa sai ya hada ido da kuyanga
Sabirat. Bisa mamaki sai ya ga hawaye ya zub0 a
idanunta.
Boka Rufyan da Barde Kurzal kuwa, ko
kwalla babu a cikin nasu idanun. Nan take Muraisu
yajı zuciyarsa ta sosu kuma ya cika da mamakin
dalilin da ya sa Sabirat ta zubar masa da hawayc,
alhalin bai kasance komai
face
ubangidanta.
gareta ba
Shin tsananin sabon da tayi da shi ne ya sa ta
Zubar da wannan hawaye ko kuwa so nc irin wanda
ke tsakanin mace da namiji?
Nan fa Muraisu ya kasa baiwa kansa amsa,
kawai sai ya kau da kai ga barin kallonta, ya kunna
kai cikin wannan daji yana mai zare takobinsa.
Karar zare takobin tasa ce ta fargar da
wadannan dakaru guda dari uku masu gadin
gimbiya Husnaila, su ma sai lkowanncnsu ya zare
tasa takobin.
A wannan lokaci gimbiya Husnaiíla tayi
tumbur a cikin wata korama tana wanka, Wasu
kuyanginta guda hudu suń rike manyan mayafai
sun kare inda take don kada wadannan Dakaru su
ga tsiraicinta.
Kwatsam! Ba za to ba tsammani sai gimbiya
Husnaila da kuyanginta suka ji an barke da
azababben yaki banda karar karafa babu sautin da
ke cika dodon kunne, har amsa kuwwa yakea cikin
dajin.
Ko kadan gimbiya Husnaila ba ta tsorata ba,
domin ba ta ma san mene ne tsoro ba a rayuwarta,
amma su kuyanginta sai suka firgice, jikinsu gaba
đaya ya kama kyarma. Nan da nan suka hada gumi
sharkaf. Koda gimbiya Husnaila ta ga halin da
kuyanginta suka shiga sai ta daka musu tsawa ta ce,
"Idan ba za ku iya ci gaba da aikinku ba zan sa
takobi duk na sareku".
Koda jin haka sai dukkanínsu suka nutsu akan
aikinsu. Ita kuwa Husnaila sai ta ci gaba da
wankanta tamkar a cikin gidanta take.
Cikin tsananin gudu yarima Muraisu ya.ratsa
cikin wadannan Samudawan dakau da nufin ya
wuce ta tsakiyarsu ya isa inda gimbiya Husnala.
take wahka, ámmna sai wadannan Dakaru suka ce
wane shi, nan take suka yanyameshi suka haushi da
sara da suka. Shi kuwa ya wanzu yana mai karcwa
da mai da martani.
Shi kansa sai da ya yi matukar mamaki bisa
ganin inin tsananih zafin naman da ya samu a yanzu
wanda a da can ya tabbatar da cewa bashi da irinsa,
in da ya sami matsala shi ne, tunda Dakarun suka
kewayeshi a waje daya aka ci gaba da gumurzu sai
ya kasa karawa gaba. Domin sun babbake hanya
babu ta inda zai iya wucewa.
Abinda ya fi daga masa hankali shi ne, duk
sa'adda ya sari dakarun ko, kuma ya sokesu da
takobinsa sai ya ji kamar karfe ya kaiwa hari,
domin tartsatsin wuta ne ke tashi gami da hayaki.
Su kuwa duk sa'adda suka sari jikinsa makamin
baya tasiri, amna sai jikinsa ya gaya masa, domin
ji yake kamar an sa shi a cikin turmi ana yi masa
lugude da tabarya.
Hakika Muraisu ya yi mamakid a ya ga karfe
bai ci jikinsa ba, domin shi dai ya san bashi da
wannan sihiri, amma da ya tuna cewa ai ya sami
zafin nama irin wanda bashi da shi a da sai ya gane
cewa lallai akwai sabon al'amari wanda ya zo masa
bako tuntuni.
"Mene ne sabon wannan al'amarin ?" Muraisu
ya tambayi kansa a cikin zuciya, amma sai ya kasa
ftar da amsa.
Lokacin da dakarun suka ci gaba da laflawa
Muraisu makanansu a dukkan jikinsa, sal ya
Zamana cewa ya kasa ci gaba da yaki, har ma ya
yarda takobinsa kuma ya fadi kasa.
Koda ganin haka, sai suka ci gaba da
tattakashi, nan da nan suka yi laga-laga da shi, jini
ya rinka tsartuwa daga cikin bakinsa da hancinsa.
Kafin cikar 'yan dakiku ya baje wanwar a
kasa yana num fashi da kyar ko yatsansa guda ya
kasa mnotsawa. A wannan lokaci ne. shugaban
dakarun ya yi mnusu inkiya suka ja da baya sannan
ya dubesu gaba daya ya ce, "Duk yadda aka yi
wannan jarumin ya fito ne daga kasar Lairus, kuma
ya zo ne domin ya sace gimbiya Husnaila ya tafi da
ita. Tunda dai makami ya ki ya yi tasiri a jikinsa,
ma za ku kamashi da karfin tsiya ku murde masa
Wuya ku jefa gawarsa cikin wancan ramin".
Shugaban dakarun ya yi nuni da hannunsa
izuwa ga wani rami mai zurfin gaske wanda ya kai
kamu dari da tamanin.
Kamar a cikin kunnen yarima Muraisu
shugaban dakarun' ya yi wannan bayani, domin ba
za to ba tsammani, sai suka ga Muraisu ya mike
Zumbur! ya daka tsalle sama ya dira a kan kafadar
daya daga cikinsu,
Cikin bakin zafin nama Muraisu ya kama kan
Badakkaren da ya dira a kafadarsa ya mrde masa
wuya. Take Badakaren ya sulale kasa matacce, ji
ka ke dam! kamar giwa ta fadi.
Zan dakata anan saikuma wani lokaci
ßµŠÅ Ä MµTµ
Littafi Na Biyu (2)
Part B
Na Abdulaziz Sani M /Gini
KAICO! Ashe tsuliyar dodo Muraisu ya tabo,
domin suna ganin ya kashe daya daga cikinsu sai
suka yì kukan kura suka afka masa gaba dayansu
aka sake kacamewa da azababben yaki.
Wannan karon dayansu bai samį damar koda
taba jikinsa ba, domin wata iriyar zulliya ya rinka
yi a tsakankaninsu
ya inka kama
hannaycnsu da kafafunsu yana kakkaryawa tamkar
yana karya sillen kara.
Gumbiya Husnaila da ke can cikin korama
tana ta wanka, sai ta fara jiyo ihun Dakarun
tsaronta. Al'amarin da ya matukar ba ta mamaki ke
Cikin hanzari ta karbi mayafi daga hannun
kuyanginta ta daura iya kirjinta, sannan ta fito daga
cikin koramar. Ko tufafinta ba ta tsaya sawa ba ta
durfai inda ake wannan gumurzu.
Su kuwa wadannan kuyangi na ta sai suka
ruga izuwa cikin daji a dimauce ba tare da sanin
inda suka dosa ba, saboda tsananin razanar da suka
yì domin sun san cewar bala'in da ya sa wadannan
samudawan dakarun ihu ba Karami bane.
Tun daga nesa gaimbiya Husnaila ta hango
dakarunta suna zubewa kasa tamkar ana sassabe a
gona.
Koda ta kara matsawa kusa sai ta ga ashe
wanda yake ragargazar su ma dan mitsitsı ne
akansu, bai fi ta kwatantashi da dan tsako ba a
cikin tsakiyar dubunnan Muzurai.
A iya rayuwar gimbiya Husnaila yau ne ranar
farko da ta ga abinda yai matukar ba ta mamaki,
amma ba wai burgcta ya yi ba.
Koda ta ga yadda Muraisu ke ta kakkarya
dakarunta suna zubewa kasa sai ta sunkuya ta
dauki mashin daya daga cikinsu ta ike ta tsaya
cak! Tana jiran ta ga abinda zai faru.
Kafin cikar rabin sa'a Muraisu ya zubar da
dukkan dakarun a kas suna ta koke-koke da iface-
iface, babu đayansu da ya iya mikewa tsaye.
Koda Muraisu ya ga ya gama da dakarun sai
ya yi arba da kyakkyawa Husnaila a tsaye a
gabansa ike da mashi, fuskarta a murtuke babu
annuri, kuma ga ta a tsayc kyam babu wata alamar
tsoro a tare da ita,
Koda ya ga kyakkyawar surar jikinta da kuma
wani kyakkyaw an gashin kanta sar ya rude ya
dimauce, bai san sa'adda ya nufeta ba gadan-gadan
da nufin ya rungumeta.
Koda ya ragc bai fi saura taku daya su hadu
ba sai ya kai ma ta raruma, ita kuwa ta goce ta soka
masa mashi a gefen kirjinsa.
Bisa mamaki sai ya ji mashin ya nutse a cikin
kirjin nasa, bai san sa'adda ya kwalla ihu ba.
Husnaila ta zare mashi jini yai feshi daga cikin
kirjin Muraisu, ya sake rusa ihu a karo na biyu. Jiri
ya debeshi ya yi luu!! kamar zai fadi kasa, amma
sai yaı ta maza ya tsaya bisa kafafunsa.
Husnaila ta sake saitashi da mashin ta tsaya
cak! A waje daya suka fara kallon-kallo. Daga can
sai ta dubeshi ta kyalkyale da dariya a cikin sautin
murya mai zakin gaske, sannan ta hade rai ta ce,
"Kai wayc, kuma me ka ke nufi da ni? Saboda mne
ka zo ka ragargaza mini dakaruna? Ka san kO ni
wace ce kuwa? Ka amsa mini tambayoyina da
gaskiya ko kuma na hallaka ka yanzzun nan!"
Koda jin wannan batu sai Muraisu ya bushe
da dariya sannan ya ce, "Ni ne yarima Muraisu dan
Sarki Salmar mai binin Laius, wato babban
makiyi ga dan uwanki Sarki Ishmar.
Ina mai sanar da ke cewa na baro gida ne
domin neman matar da zan'aura, kuna ba wata ba
ce wadda zan aura face ke din nan".
Koda jin haka sai Husnaila ta tuntsure da
dariya, 1lokaci guda kuma ta hade rai ta sunkui da kanta kas tana tunani. Muraisu ya katse ma ta
hanzari ya ce, "Ya ke Husnaila Sarauniyar mata,
me kike tunani ne?"
Husnaila ta dubeshi ta ce, "Mamaki nake bisa
daıyar da na yi yanzu, domin kaine mutum na
farko da ya ta6a ganin dariyata..
Hatta dan uwana kuwa Sarki Ishmar sai dai ya
Ce ya ga murmushina ko hawaye na, amma bai taba
ganin dariyatą ba ko kukana'".
Da jin haka sai Muraisu ya yi mumushi ya ce,
"Al ni mutum ne na musamman a cikin mutane, da
sannu za ki gasgata haka".
Husnaila ta ce, "Ai kuwa na ga alama tunda
ban taba sukar wani abu da makami ba ya rayu sai
kai. Shin za ka iya gaya mini sirrin da ke tattare da
kai?"
Muraisu ya cire wani rawani da ke ikin
damararsa ya daure kirjinsa lamau don tsaida jini,
sannan ya dubi Husnaila a nutse ya ce, '"Ina zaton
dai irin sihirin da ke tare da ke shi ne a tare dani,
domin gashi dakarunki sun kasa cutar da ni da
makamansu, amma ke gashi kin cutar da ni".
Husnaila tayi murmushin mugunta, sannan ta
ce, "Ka yi babban kuskure da kake tunanin za ka
aureňi, domin abu ne wanda ba zai taba yiwuwa ba
Babu wani da namiji da ya isa ya mallakeni, idan
kuma kana ganin za ka iya ka jarraba!"
Muraisu ya gyara tsayuwarsa sannan ya ce,
"Ai babu wani abu wanda ba zai yiyu ba a wannan
duniya, sai dai ba a jarraba b.
Ina da labari cewa dan uwanki ya tsarcki da
dukkan sihirin tsafinsa, amma ni nayi imanı cewa
sirin da nake da shi a yanzu ke baki da shi tunda
shi kansa dan uwanki har yanzu bai samu ikon
shiga dajin Kirzufa ba.
Ba shi da wani buri wanda ya fi haka. Ina
tabbatar miki da cewa har ya mutu ba zai cika
wannan buri na sa ba, ni kuwa mahaifina ya shiga
dajin Kirzufa, Đima kuma zan shigeshi yanzu,
kuma tarc da ke, kuma dana ma sai ya shigeshi. Ina
mai shawartarki da ki bani hadn kai mu tafi cikin
salin-alin, idan kuwa kika ki, to fa ko ta tsiya-tsiya
sai mun je".
Sa'adda Husnaila taji wannan batu sai ta sake
bushewa da dariya a karO na biyu, sannan ta hade
fuska ta ce, "Ai sai na ga yadda za a raba hanta da
jini!"
Kafin Muraisu ya budi baki ya ce wani abu
luni Husnaila ta dako tsalle a sama daga inda.take
kamar an cillota daga cikin baka ta sake kawo masa
mummnunan hari da wannan mashi a ciki.
Gimbiya Ilusnaila ta ce, "Ta ya ya aka yi ka
san cewa ni ce Sarauniyar kyawawa ta duniya?"
Muraisu ya ce, "'Saboda mu a wannan nahiya
lamu gaba daya babu kamarki".
Gimbiya Ilusnaila ta cC, "Ba zan iya gaya
maka ba, saboda ba kowacce tambaya ce ke da
amsa ba"
Muraisu ya ce, "Maganarki dutse ce, amma
akwai gyara".
Gimbiya Husnaila ta cc, "To mene
gyaran?"
"Bari na matso kusa na yi miki bayani, domin
wani babban siri ne wanda ba kowa ake fadawa
ba'".
Kai tsaye Muraisu ya tali inda Gimbiya
Ilusnaila take tsaye kamar wani abu zai rada ma ta
a kunnc.
Koda ya iso daf da ita sai ya shammaceta
cikin bakin zafin nama ya debo hodar banju daga
aljihunsa ya watsa ma ta a fuska.
Nan take Gimbiya Husnaila taji jiri ya
kwasheta, la tafi luu! za ta fadi kasa, sai ya
sunkuya uya sabata a kaladarsa ya juya da baya ya
nufi inda ya baro su boka Rufyan suka tsaya suna
Jiransa.
Barde Kurzal, kuyan ga Sabirat, boka Rufyan
na tsayc suna hangen hanyar da Muraisu ya bi cikin
zullumi da fargaba. sai kawai suka hangoshi ya
nufosu sabe da Gimbiva Jusnaila a kafadarsa, ga
raunı a kirjinsa daure cikin shátar jini, yana tafe
yana raba kafa kamar wanda ya sha giya ya bugu.
Koda ganin haka sai Barde Kurzal da boka
Kutyan suka ruga gareshi cikin matu kar farin ciki
suka taroshi.
AA Misau
Barde Kurzal ya karbi Gimbiya Husnaila ya
taho da ita inda Sabirat ke tsaye, shi kuma boka
Rufyan ya dauko Muraisu suka kawosu bakin wata
bishiya suka shimfidesu.
Cikin hanzari boka Rufyan ya kwance raunin
Muraisu yana matukar mamakin yadda aka yi ya
sami raunin alhalin ya san cewa Sarki Salmar ya
bashi gashin sihirinsa.
Nan da nan yai sauri ya sa ma sa gan magani
akan ciwon nasa, sannan suka bashi ruwa ya sha.
Ita kuwa Gimbiya Ilusnaila, tunda aka
shim fideta ta ci gaba da barcinta ko motsawa ba ta
Bayan Muraisu ya dawo cikin haiyacinsa sai
boka Rufyan ya dubeshi cikin jınjinawa ya ce, "Ya
kai namijin duniya, dodon maza, ya ya aka yi ka
Saml Wannan gagarumar nasara har ka daukO
gimbiya Husnaila daga cikin tsaron da aka ba ta?".
Koda jin
wannan tambayar sai yarima
Muraisu ya kwashc labarin duk abinda ya faru ya
Zalyane musu. Koda jin al'amarin sai duk su ukun
suka sake cika da mamaki, musanman boka
Rufyan wanda ytai shiru ya shiga tunani mai zurli.
Daga can sai ya dago kai ya dubi yarima
Muraisu yą ce, "Ya shugabana hakika shirin sarki
Ishmar ba na wasa bane, ban taba tsammanin yana
da karfin sihiri kamar haka ba. Ina tabbatar maka
da cewa duk wannan jarumtaka da Husnaila ta yi
ba gaskiya ba ce, tsabar karfin sihirin tsafi ne
kawai.
Tabbas itama tana da gashin sihiri a jikinta,
amma abinda na ke zargi shi ne, ba irin naka bane a
Jikinta, shi ya sa mahaifinta ya kasa shiga cikin
da in Kirzufa. Hakika ba don kayi wannan hikima
ba ta watsa ma ta banju a fuskarta da babu yadda za
a yi ka iya kamota har ka zo da ita nan wajenmu.
Ina son ka sani cewar dole ne yanzu ka
hanzarta zuwa dajin Kirzufa da Husnaila kafin
hodar banjun ta saketa nan da tsawon sa'a daya jal.
Idan har ta farfado ko duniyar nan za ta taru a kanta
ba za a iya taiya da ita ba, kuma idan ma ka shiga
da ita cikin dajin Kirzufa sai ka sa ido sosai a kanta
don za ta yi iya shammatarka tayi maka irin abinda
ka yi ma ta".
Koda jin wannan batu sai Muraisu ya mike
zumbur! ya dauki gimbiya Husnaila ya đorata akan
doknsa, sannan shima ya hau nasa dokin, suma Su
Rufyan sai suka yi sauri suka hau nasu.
Barde Kurzal ne ya wuce kan gaba suka
zaburi dawakansu da gudu suka bishi a baya. Basu
tsaya a ko ina ba sai sai a bakin dajin Kirzufa.
Lokaci guda su duka suka yi tirjiya, sannan
suka sauko daga kan dawakansu. Yarima Muraisu
ya sake đaukar gimbiya Husnaila a kafadarsa. Har
ya juya zai shigc cikin dajin na Kirzufa, sai ya
Waiga ya dubesu su ukun cikin wani iin kallo mai
nuna alamun bankwana, wanda ya sa duk su ukun
suka ji tsigar jikinsu ta tashi, kuma dukkaninsu sai
zuciyoyinsu suka karaya, nan take tausayin yarima
ya tumukesu, saboda sanin cewa masifar da zai
shiga yanzu ta ninka wacce ya shiga a baya sau
dubu.
Muraisu ya tsaida hankalinsa a kan boka
Rufyan ya ce, "Bani labarin mahaifina, shin hạr
yanzu yana raye ko kuwa ya mutu?"
Koda jin wannan tambaya sai boka Rufyan-
yai shiru ýa kasa cewa komai, kawai ya kurawa
Muraisu idanu.
Barde Kurzal da kuyanga Sabirat kuwa, sai
hankalinsu ya dugunzumna, suka kama raba idanu a
tsakanin Muraisu da Rufyan, jira suke kawai su ji
amsar da Rufyan zai bayar.
Tsawon 'yan dakiku Rufyan bai ce komai ba,
kuma bai fasa kurawa Muraisu idanu ba.
Koda ganin haka sai idanun Muraisu suka
domin
ciko da kwalla har hawaye ya subuto masa,
ya ji a jikinsa cewa MAZA SUN FADI!
Kawai sai ya juya ya durfafi cikin dajin
Kirzufa kai tsaye, a lokacin da ya ji dukkan tsoro
ya kau daga cikin zuciyarsa, ji yake ina ma
mutuwar za ta zo ta daukeshi da ya fis amun
nutsuwa.
Da shigar su Muraisu dajin Kirzufa sai ya fara
arba da dabbobin daji ii-ii, kuma manya-manyan
ababan tsoro, domin sun kasance na usamman ba
irin wanda ido ya saba gani ba. Tsananin kwarjinin
dabbobin ya wuce misali, ko kwatance.
Tsakanin Muraisu da dabbobin sai kallon-
kallo kawai, dayansu bai yi yunkurin koda zuwa
kusa da shi ba, shima Muraisu ko kallonsu bai yi
ba, kawai sau ya je karkashin wata bishiya ya
shimfide Husnaila, sannan ya koma gefe daya ya
tsugunna ya kura ma ta idanu, kuma ya fada kogin
tunani.
Abinda ya fara fado masa a rai shi ne, yanzu
ya zai yi da Husnaila idan ta farka ta tsinci kanta a
cikin dajin Kirzufa?
"Lallai akwai kazamar rigima a (sakaninmu"
Muraisu ya baiwa kansa amsa.
"Kuma saí tayi yunkurin guduwa...Amma
kuma ai boka Rufyan ya gaya mini cewar ba tưisa
ta fice daga cikin dajin ba har sai mun yi kWana
uku a cikinsa, saboda haka zan zuba ma ta idanu ne
kawai na ga iyakar gudun ruwanta. "
Haka dai Muraisu ya yi ta sake-sake a cikin
zuciyarsa har ya gaji, shima saí ya kishingida a
jikin wata bishiya.
Abinka da gajiyayye, bai dađe da kishingida
ba sai barci ya kwashe shi.
Bayan 'yan dakiku kadan kuma sai Husnaila
ta farka.
Koda la bude idanu ta tsinci kanta a cikin
wani iin daji na musamman sai ta takarkare ta
tsandara uban ihu. Muraisu ya farka firgigit! a
razane, dabbobin cikin dajin kuwa, hatta sauran
Rananan kwari da tsintsaye sai da suka razana, suka
kama guje-guje.
Duk dabbar da tayi arba da su Muraisu sai ta
yıyo kansu:
Nan fa aka kasa uban tserc tsakanin su
Husnaila da dabbobin dajin gaba daya.
Babu abinda zai baiwa mutumn mamaki face
Lsananin gudun da Muraisu da Husnaila ke yi
tamkar akan iska suke yinsa ba a kan kasa ba.
Duk su biyun sun yi matukar mamakin irin
gudun nasu, domin tamkar walkiya suke gifta
komai, sai dai karfin gudun nasu duk ya zama na
banza, domin duk sa'adda suka waiga bayansu sai
su ga dabbobi kusan guda dubu daf da su.
Duk inda suka dauke
dabbobin suke sa nasu.
sawayensu
anan
da
Babu abinda ya fi firgita su Muraisu face
cafka
kawo musu
yadda dabbobin ke
bakunansu, don su cinyesu, musamman wani katon
Zaki wanda idan ya wangame bakinsa sai ka ga
kamar ijiya mai zurfi da fadi aka bude.
Sai da su Muraisu suka shafe sa'a guda cif!
Suna falfala natsanaicin azababben gudu, sannan
suka hango wani katon tsauni a gabansu.
Basu tsaya jiran komai ba suka hau kan
tsaunin a guje, har sai da suka je can. samansa
sanann suka waigo baya.
Bisa mamaki, sai suka ga gaba dayan
dabbobin sun tsaya a kasan tsaunin đayansu bai yì
yunkurin hawowa ba.
Al'amarin da ya matukar basu mamakia ke
nan, Kawai sai suka zube kasa a saman tsaunin
suka kama haki, da fitar da numfashi da saurí da
sauri.
A sannan nc fa kishirwa ta ischsu, kuma
gashi
babu damar shawagi a kasan tsaunin tamkar an
basu gadin abinda ke kan tsaunin.
A dai-dai wannan lokaci ne Husnaila ta dubi
Muraisu cikin harara da fushi ta ce, "Ya ya aka yi
ka kawoni cikin wannan daji?"
Koda jin wnanan tambaya sai Muraisu ya yi
murmushi ya ce, "Ba wannan tambayar ya kamata
ki yí mini ba a yanzu, kamata ya yí ki tambayeni a
ina zamu samu ruwan sha?"
Husnaila ta sake murtuke fuska ta ce, "Ba
ruwa ne a gabana ba. Ka mayar da ni inda ka
daukoni, domin ina da bukatar na koma gida kafin
magariba tayi".
Koda jin wannan batu sai Muraişu ya bushe
da dariya har da bingirewa Kasa, sannan ya nutsu
ya ce, "Ai idan har kin ga kin fita daga cikin dajin
nan sai kin yi kwanaki uku cikakku a cikinsa!"
Cikin fushi da mamaki Husnaila ta mike tsaye
ta ce, "Ai kuwa idan ka ga na kara koda dakika
đari ne a cikin wannan daji sai idan bana
numfashi. "
Koda gama fadin hakan sai ta mike tsaye ta
fara saukowa kasan tsaunin. Muraisu ya bita da
kallo kawai ko motsi baiyi ba daga inda yake
zaunc.
Lokacin da ya rage saura bai fi taku biyar ba
ta iso kasan tsaunin, sai kawia ta ga wannan
ma ta haikan
Zaki ya taso
turmusheta. Ba shiri ta juya da baya da gudu ta
koma kan tsaunin inda Muraisu yake.
Koda ganin abinda ya faru sai Muraisu ya
kama yi ma ta dariya. Al'amarin da ya kara
tunzurata ke nan, ta kamu da tsananin fushi. Bisa
dole taje gefe daya, nesa kadan da inda Muraisu
yake zaune itama ta zauna.
Babban abinda ya i daurewa Husnaila kai shi
ne, ya ya ita da bata da tsoro ko kadan amma taji
tana tsoron dabbobin wannan dajı?
Kawai sai ta dubi Muraisu ta ce, "Wai shin
wannan wane daji ne muka shigo?" Muraisu ya yi
ajiyar zuciya sannan ta ya ce, "VWannan shi ne dajin
KIRZUFA! Kanar yadda na gaya miki da farko sai
mun yi kwana uku a cikinsa ni da ke, a sannan ne
na sami
Zan sauya miki rayuwarki, kuma
soyayyarki, mu tafi izuwa birninmu na Lairuf mu
yi aure".
Kafin Muraisu ya gama rule bakinsa tuni
Musnaila ta tofa masa yawu a fuska,
Cikin tsananin fishí ya mike tsaye zumbur! ya
zare takobinsa, itama saí ta mikc Zumbur! ta rike
mashinta suka fara kallon-kallo, har gaba dayan
jikin Muraisu na tsuma saboda fushi, domnin a íva
rayuwarsa ba a taba yi masa iin wannan
wulakancin ba a matsayinsa na dan Sarki, kuma
gawurtaccen jarumi.
Husnaila ta dubcshi a wulakance ta ce,
"Na
tsancka! Kuma na tsani dukkan zuril'arka, Har
abada ba zan ta6a sonka ba, kuma ní da dan uwana
Sarki Ishmar sai mun baje birninku, mun konc
dukiyoyinku, mun kame matanku da 'ya'yanku sun
zama bayinmu. Mazajenku kaf sai mun kashesu",
Koda jin wannan batu saí Muraisu yaji ya
tsani lusnaila kamar yadda yaji ya tsani
mutuwarsa. Duk wannan tsananin kyawu nata sai ta
rama kamar dodanníya a idanunsa.
IHar ya yunkura zai afka ma ta su yi yaki, sai
ya tuna cewa ai sihiri ne a jikinta wanda ya sa ba za
ta laba son wani da namiji ba face ta ci ta sha daga
abubuwan da ke cikin wannan daji na Kirzufa na
tsawon kwana uku.
Koda tuna wannan al'amari sai jikin Muraisu
ya yi sanyí, ya fasa afkawa Husnaila ya koma ya
zauna. Koda ganin haka, sai itama ta koma inda
take ta zauna.
A sannan ne fa kishirwa ta ci gaba da
addabarsu. Babu shiri suka mike tsaye suka kama
yawo akan tsaunin kowannensu na neman ruwa,
amma babu ko alamarsa.
Duk sa'adda suka leko kasan tsaunin kuma sai
suka ga wadanann dabbobi suna nan suna kewaya
tsaunin, jira kawia suke su sauko su afka musu,
Bisa dole suka hakura.
Lokacin da 'yan sa'oi suka kara shudewaa sai
magariba ta doso kai, gari ya fara duhu, a sannan
ne tsananin kishirwa tasa suka baje a kasa suka
kama num fashi sama-sama kamar za su muti. Sai
da kowannensu ya fara suma, kwatsam! ba zato ba
tsammani sai hadari ya gangamo aka fara tsawa da
walkiya gami da wata irin gagarumar iska mai
karfin gaske. Kafin a jima ruwan sama ya tsuge
karmar da bakin kwarya.
A sannan ne Muraisu da Husnaila suka
farfado, sai kowannensu ya wangame bakinsa suka
kama shan ruwan, har sai da suka koshi, sannan
suka dawo cikin haiyacinsu, sai dai babu inda zå su
fakewa wannan ruwan saman, dole suka hakura
ruwa yai ta dukansu har izuwa tsawon sa'a guda,
sannan ruwan saman ya dauke dif.
Nima Kuma Wanga Ruwa Yana Daukewa Nima Na Dauke Daga Typing hhhhh
Zan dakata anan sai kuma wani lokaci
Zamu cigaba
Insha Allah
Likes and comments
Domin hakan na sa mu cigaba
Ga masu shA award whtsp grp
https://chat.whatsapp.com/E0GMznXcaxwC0avNVdF30Q
BUSA A MUTU
Littafi Na Biyu (2)
Littafi Na Biyu (2)
Part A
Na Abdulaziz Sani M /Gini
Marubucin Yaci Gaba Da Cewa
SA'ADDA boka Rufyan ya zo
jawabinsa sai hankalin yarima Muraisu ya
dugunzuma har kwalla ta zo masa, ya dubi boka
Rufyan cikin tsananin takaici ya ce, "Yanzu ke nan
kana nufin cewa nima mutuwa zan yi nan ba da
dadewa ba kuma idan ban auri gimbiya Husnaila
ba shi ke nan babu mai kawar da su azzalumaí
Huraisu?".
Koda jin wannan tambaya sai boka Rufyan
yai shiu ya kasa cewa komai, kawai sai ya mike
tsaye ya koma can gefe daya ya zauna yana mai
sunkui da kansa kas. Cikin fushi yarima Muraisu
ya mike zumbur yaje gabansa ya tsaya ya dubeshi a
fusace ya ce, "Saboda me ka ki baní amsar
tambayata?"
Boka Rufyan ya dago kai ya dubi yarima ba
tare da shakka ko tsoro ba ya ce, "Ai ba kowacce
tambaya ce ke da amsa ba. Ina so ka sani cewa
zamanmnu anan bashi da wani amfani, domin zaman
Jaki da kaya ne. Idan kana ganin za ka bi wadannan
matakai na samun matar da za ka aura ka tashú mu.
bi sawunsu gimbiya Husnaila.
Dik da cewą tsakaninmu da su akwai tazarata
a kalla tafiyar kwana arba'in, zan iya đaurc mana
kasa mu riskesu a cikin kwana shida da yini daya,
domin ka yakesu ka rabasu da Husnaila idan ka yi
nasara sai mu rakaka izuwa bakin dajin Kirzufa mu
-tsaya daga wajensa kai da Husnaila ku shiga
cikinsa, ba za ku fito ba sai bayan kwana ukun.
Sannan mu rankaya mu tafi izuwa can birnin Lairuf
domin a yi shagalin bikinku",
Lokacin da boka Rufyan ya zo nán
jawabinsa sai jikin yarima Muraisu ya yi sanyi, ya
koma can gefe ya zauna kuma ya yi tagumi inda ya
fada cikin kogin tunani.
Ba wani abu yake tunawa ba face gagarumin
aikin da ke gabansa wanda ya i karfin tunaninsa.
Abinda ya fara fado masa a rai shi ne, ta ya ya zai
iya tarwatsa wadannan dakaru guda dubu dari uku
shi kadai alhalin KAIFI DA TSINI baya tasiri a
jikinsu? Kuma idan za a kwana uku ana yaki da su
ba z4 su gaji ba? Abu na biyu, ta ya ya zai iya shiga
dajin Kirzufa ya har ya yi kwana uku a cikinsa
alhalin mahaifinsa ma da kyar ya iya yin sa'o'i a
cikinsa?"
Koda Muraisu ya zo nan a tunaninsa sai ransa
. ya baci ya ga cewa boka Rufyan ya raina masa
hankali, domin bai ga dalilin da zai sa ya umarceshi
yin abinda shi kansa ya san cěwa ba zai yiwu ba.
A fusace ya sake mikewa tsaye ya nufi kan boka
Rufyan gadan-gadan, kawai sai boka Rufyan ya
mike ya tareshi ya ce, "Idan ka so ka zare
takobinka ka kasheni yanzu take, amma ka sani
cewa zabi daya ne garcka cikin biyu. Walau ka
koma gida ka zuana ka įira ranar da makiya za su
Z0 Su cimu da yaki, kana ji kana gani, ko kuma ka
nemi matar aurenka wacce za ta haifa maka dan da
Zai kwatar mana 'yanci anan gaba. Ko ka ki ko ka
so baka isa ka sauya kaddara ba.
Babu makawa sai an ci mu da yaki kuma ba
lallai bane ni ko wadannan abokan tafiya namu
dayanmu ya yi nisan kwanan da zai ga ranar da za
a karbar mana 'yancin mu ba."
Koda jin wannan furuci sai jikin yarima
Muraisu ya yi sanyi a karo na biyu, ya koma inda
yake ya zauna yai shiru bai ce komai ba, ya shuga
sabon tunani. Nan take yaji duniyar gaba đaya tayi
masa zali, musamman da ya tuna cewa shi fa yanzu
bashi da uwa kuma a ko yaushe ma zai iya rasa
mahaifinsa.
"To wai shin na akan Wane dalili zai damu da
duniya tunda bashi da saran masoyi?"
Wata zuciyar kuma ta ce da shı, "To mene ne
am fanin kaina ka gushe kamar yadda iyayenka za
Su gushe ba. tare ta ka bar. zun ar da za a gania
Tinka tunawa da kai ba?"
Koda ya zo nan a tunaninsa sai hawaye ya
zubo masa. Yana dago kai ya ga kuyanga Sabirat
tsaye a gabansa. Sabirat ta zauna kusa da yarima
Muraisu ta dubeshi a nutse, sannan ta ce, ""Ya kai
jarumin kwarai, ka yi sani cewa namijin baya kuka,
kuma bai san tsoro ba. Shi ne wanda baya shakkar
shiga ckin kowanne irin bala'i kuma shi nc wanda
bai dauki RAI a bakin komai ba, muddin bukata za
ta biya."
Koda yarima Muraisu yaji wannan batu sai
dukkanin tsoro ya kau daga cikin zuciyarsa kawai
sai ya dubi Sabirat ya yi murmushi ya ce,
"Madallah da kuyanga ta gari wacce ke yiwa
ubangidanta tuni bisa abinda ya kamaceshi."
Gama fadin hakan ke da wuya sai Muraisu ya
mike tsaye ya dubi Boka Rufyan da Badakare
Kirzal ya ce, "Ma za ku samu akan hanya wacce za
ta kaini inda zan riski gimbiya Husnaila da
jama'arta a cikin kankanin lokaci"
Kafin Muraisu ya gana rufe bakinsa tuni
Kurzan da Rufyan sun mike zumbur sun kama
dawakansu sun haye. Saoirat da Muraisu ma suka
yi sauri suka hau nasa dawakan. Kurzal ne ya wuce
. kan gaba, Boka Kufyan na-biye da shi sannan su
yarima.
Dukkaninsu suka sukwani dawakansu da
gudun tsiya suka nausa cikin daji.
Nan fa Yarima, Kurzal da Sabirat suka rinka
ganin abin al'ajabi, domin cikin dakiku kadan suka
rinka shafe tafiyar sa'o'i. Nan da nan suka ga sun zO
wani wuri maj irin yanayi dabam da sauran
dazuzzukan da suka wuce.
Shi dai wannan wuri da suka zo ya kasance
daji ne mai yawan lumshi tamkar rana ba ta taba
baiyana ba a cikinsa. Bishiyoyin da ke cikinsa
kuwa duk dogaye ne masu fala-falan ganyaye, haka
kuma akwai duwatsu manya-manya in-in masu
tsawo da fadi.
Koda 1SOwar Su yarıma wannan wuri sai
Kurzal yai sauri ya sauko daga kan dokinsa ya kifa
kunnensa akan kasa yai nazari, sannan ya mike
tsayc, ya dubi yarima ya ce, 'Ya shugabana nan
gaba kadan tafiyar 'yan dakiku akwai mutanc sama
da guda dari biyu a labe cikin duhuwar bishiyoyi".
Koda jin haka sai Boka Rulyan ya yi
murmushi, sannan shuma ya dubi yarima ya ce, "Sai
ka shige ciki ka riskesu ka karbo gimbiya Husnaila
ta kowanne hali. Mu kam amu Jiraka ne nan har
iZUwa tsawon sa'a bakwaj.
Jdan ka fito da nasara sai mu rakaka izuwa
bakin dajin KirZula, acan mas mu jira izuwa
sa'adda za ku kwana uku a cikinsa ku fito, sannan
mu rankaya gaba daya izuwa gida. Idan kuma mu
ka ji shiru ba ka fito ba, mun san ccwa ka hallaka
sai mu juya mu koma gda".
Yarima Muraisu ya gyada kai ya ce, "Haka za
a yi". Kawai sai ya juya zai shiga cikin wannan daji
mai kwarjini, ai kuwa sai ya hada ido da kuyanga
Sabirat. Bisa mamaki sai ya ga hawaye ya zub0 a
idanunta.
Boka Rufyan da Barde Kurzal kuwa, ko
kwalla babu a cikin nasu idanun. Nan take Muraisu
yajı zuciyarsa ta sosu kuma ya cika da mamakin
dalilin da ya sa Sabirat ta zubar masa da hawayc,
alhalin bai kasance komai
face
ubangidanta.
gareta ba
Shin tsananin sabon da tayi da shi ne ya sa ta
Zubar da wannan hawaye ko kuwa so nc irin wanda
ke tsakanin mace da namiji?
Nan fa Muraisu ya kasa baiwa kansa amsa,
kawai sai ya kau da kai ga barin kallonta, ya kunna
kai cikin wannan daji yana mai zare takobinsa.
Karar zare takobin tasa ce ta fargar da
wadannan dakaru guda dari uku masu gadin
gimbiya Husnaila, su ma sai lkowanncnsu ya zare
tasa takobin.
A wannan lokaci gimbiya Husnaiíla tayi
tumbur a cikin wata korama tana wanka, Wasu
kuyanginta guda hudu suń rike manyan mayafai
sun kare inda take don kada wadannan Dakaru su
ga tsiraicinta.
Kwatsam! Ba za to ba tsammani sai gimbiya
Husnaila da kuyanginta suka ji an barke da
azababben yaki banda karar karafa babu sautin da
ke cika dodon kunne, har amsa kuwwa yakea cikin
dajin.
Ko kadan gimbiya Husnaila ba ta tsorata ba,
domin ba ta ma san mene ne tsoro ba a rayuwarta,
amma su kuyanginta sai suka firgice, jikinsu gaba
đaya ya kama kyarma. Nan da nan suka hada gumi
sharkaf. Koda gimbiya Husnaila ta ga halin da
kuyanginta suka shiga sai ta daka musu tsawa ta ce,
"Idan ba za ku iya ci gaba da aikinku ba zan sa
takobi duk na sareku".
Koda jin haka sai dukkanínsu suka nutsu akan
aikinsu. Ita kuwa Husnaila sai ta ci gaba da
wankanta tamkar a cikin gidanta take.
Cikin tsananin gudu yarima Muraisu ya.ratsa
cikin wadannan Samudawan dakau da nufin ya
wuce ta tsakiyarsu ya isa inda gimbiya Husnala.
take wahka, ámmna sai wadannan Dakaru suka ce
wane shi, nan take suka yanyameshi suka haushi da
sara da suka. Shi kuwa ya wanzu yana mai karcwa
da mai da martani.
Shi kansa sai da ya yi matukar mamaki bisa
ganin inin tsananih zafin naman da ya samu a yanzu
wanda a da can ya tabbatar da cewa bashi da irinsa,
in da ya sami matsala shi ne, tunda Dakarun suka
kewayeshi a waje daya aka ci gaba da gumurzu sai
ya kasa karawa gaba. Domin sun babbake hanya
babu ta inda zai iya wucewa.
Abinda ya fi daga masa hankali shi ne, duk
sa'adda ya sari dakarun ko, kuma ya sokesu da
takobinsa sai ya ji kamar karfe ya kaiwa hari,
domin tartsatsin wuta ne ke tashi gami da hayaki.
Su kuwa duk sa'adda suka sari jikinsa makamin
baya tasiri, amna sai jikinsa ya gaya masa, domin
ji yake kamar an sa shi a cikin turmi ana yi masa
lugude da tabarya.
Hakika Muraisu ya yi mamakid a ya ga karfe
bai ci jikinsa ba, domin shi dai ya san bashi da
wannan sihiri, amma da ya tuna cewa ai ya sami
zafin nama irin wanda bashi da shi a da sai ya gane
cewa lallai akwai sabon al'amari wanda ya zo masa
bako tuntuni.
"Mene ne sabon wannan al'amarin ?" Muraisu
ya tambayi kansa a cikin zuciya, amma sai ya kasa
ftar da amsa.
Lokacin da dakarun suka ci gaba da laflawa
Muraisu makanansu a dukkan jikinsa, sal ya
Zamana cewa ya kasa ci gaba da yaki, har ma ya
yarda takobinsa kuma ya fadi kasa.
Koda ganin haka, sai suka ci gaba da
tattakashi, nan da nan suka yi laga-laga da shi, jini
ya rinka tsartuwa daga cikin bakinsa da hancinsa.
Kafin cikar 'yan dakiku ya baje wanwar a
kasa yana num fashi da kyar ko yatsansa guda ya
kasa mnotsawa. A wannan lokaci ne. shugaban
dakarun ya yi mnusu inkiya suka ja da baya sannan
ya dubesu gaba daya ya ce, "Duk yadda aka yi
wannan jarumin ya fito ne daga kasar Lairus, kuma
ya zo ne domin ya sace gimbiya Husnaila ya tafi da
ita. Tunda dai makami ya ki ya yi tasiri a jikinsa,
ma za ku kamashi da karfin tsiya ku murde masa
Wuya ku jefa gawarsa cikin wancan ramin".
Shugaban dakarun ya yi nuni da hannunsa
izuwa ga wani rami mai zurfin gaske wanda ya kai
kamu dari da tamanin.
Kamar a cikin kunnen yarima Muraisu
shugaban dakarun' ya yi wannan bayani, domin ba
za to ba tsammani, sai suka ga Muraisu ya mike
Zumbur! ya daka tsalle sama ya dira a kan kafadar
daya daga cikinsu,
Cikin bakin zafin nama Muraisu ya kama kan
Badakkaren da ya dira a kafadarsa ya mrde masa
wuya. Take Badakaren ya sulale kasa matacce, ji
ka ke dam! kamar giwa ta fadi.
Zan dakata anan saikuma wani lokaci
ßµŠÅ Ä MµTµ
Littafi Na Biyu (2)
Part B
Na Abdulaziz Sani M /Gini
KAICO! Ashe tsuliyar dodo Muraisu ya tabo,
domin suna ganin ya kashe daya daga cikinsu sai
suka yì kukan kura suka afka masa gaba dayansu
aka sake kacamewa da azababben yaki.
Wannan karon dayansu bai samį damar koda
taba jikinsa ba, domin wata iriyar zulliya ya rinka
yi a tsakankaninsu
ya inka kama
hannaycnsu da kafafunsu yana kakkaryawa tamkar
yana karya sillen kara.
Gumbiya Husnaila da ke can cikin korama
tana ta wanka, sai ta fara jiyo ihun Dakarun
tsaronta. Al'amarin da ya matukar ba ta mamaki ke
Cikin hanzari ta karbi mayafi daga hannun
kuyanginta ta daura iya kirjinta, sannan ta fito daga
cikin koramar. Ko tufafinta ba ta tsaya sawa ba ta
durfai inda ake wannan gumurzu.
Su kuwa wadannan kuyangi na ta sai suka
ruga izuwa cikin daji a dimauce ba tare da sanin
inda suka dosa ba, saboda tsananin razanar da suka
yì domin sun san cewar bala'in da ya sa wadannan
samudawan dakarun ihu ba Karami bane.
Tun daga nesa gaimbiya Husnaila ta hango
dakarunta suna zubewa kasa tamkar ana sassabe a
gona.
Koda ta kara matsawa kusa sai ta ga ashe
wanda yake ragargazar su ma dan mitsitsı ne
akansu, bai fi ta kwatantashi da dan tsako ba a
cikin tsakiyar dubunnan Muzurai.
A iya rayuwar gimbiya Husnaila yau ne ranar
farko da ta ga abinda yai matukar ba ta mamaki,
amma ba wai burgcta ya yi ba.
Koda ta ga yadda Muraisu ke ta kakkarya
dakarunta suna zubewa kasa sai ta sunkuya ta
dauki mashin daya daga cikinsu ta ike ta tsaya
cak! Tana jiran ta ga abinda zai faru.
Kafin cikar rabin sa'a Muraisu ya zubar da
dukkan dakarun a kas suna ta koke-koke da iface-
iface, babu đayansu da ya iya mikewa tsaye.
Koda Muraisu ya ga ya gama da dakarun sai
ya yi arba da kyakkyawa Husnaila a tsaye a
gabansa ike da mashi, fuskarta a murtuke babu
annuri, kuma ga ta a tsayc kyam babu wata alamar
tsoro a tare da ita,
Koda ya ga kyakkyawar surar jikinta da kuma
wani kyakkyaw an gashin kanta sar ya rude ya
dimauce, bai san sa'adda ya nufeta ba gadan-gadan
da nufin ya rungumeta.
Koda ya ragc bai fi saura taku daya su hadu
ba sai ya kai ma ta raruma, ita kuwa ta goce ta soka
masa mashi a gefen kirjinsa.
Bisa mamaki sai ya ji mashin ya nutse a cikin
kirjin nasa, bai san sa'adda ya kwalla ihu ba.
Husnaila ta zare mashi jini yai feshi daga cikin
kirjin Muraisu, ya sake rusa ihu a karo na biyu. Jiri
ya debeshi ya yi luu!! kamar zai fadi kasa, amma
sai yaı ta maza ya tsaya bisa kafafunsa.
Husnaila ta sake saitashi da mashin ta tsaya
cak! A waje daya suka fara kallon-kallo. Daga can
sai ta dubeshi ta kyalkyale da dariya a cikin sautin
murya mai zakin gaske, sannan ta hade rai ta ce,
"Kai wayc, kuma me ka ke nufi da ni? Saboda mne
ka zo ka ragargaza mini dakaruna? Ka san kO ni
wace ce kuwa? Ka amsa mini tambayoyina da
gaskiya ko kuma na hallaka ka yanzzun nan!"
Koda jin wannan batu sai Muraisu ya bushe
da dariya sannan ya ce, "Ni ne yarima Muraisu dan
Sarki Salmar mai binin Laius, wato babban
makiyi ga dan uwanki Sarki Ishmar.
Ina mai sanar da ke cewa na baro gida ne
domin neman matar da zan'aura, kuna ba wata ba
ce wadda zan aura face ke din nan".
Koda jin haka sai Husnaila ta tuntsure da
dariya, 1lokaci guda kuma ta hade rai ta sunkui da kanta kas tana tunani. Muraisu ya katse ma ta
hanzari ya ce, "Ya ke Husnaila Sarauniyar mata,
me kike tunani ne?"
Husnaila ta dubeshi ta ce, "Mamaki nake bisa
daıyar da na yi yanzu, domin kaine mutum na
farko da ya ta6a ganin dariyata..
Hatta dan uwana kuwa Sarki Ishmar sai dai ya
Ce ya ga murmushina ko hawaye na, amma bai taba
ganin dariyatą ba ko kukana'".
Da jin haka sai Muraisu ya yi mumushi ya ce,
"Al ni mutum ne na musamman a cikin mutane, da
sannu za ki gasgata haka".
Husnaila ta ce, "Ai kuwa na ga alama tunda
ban taba sukar wani abu da makami ba ya rayu sai
kai. Shin za ka iya gaya mini sirrin da ke tattare da
kai?"
Muraisu ya cire wani rawani da ke ikin
damararsa ya daure kirjinsa lamau don tsaida jini,
sannan ya dubi Husnaila a nutse ya ce, '"Ina zaton
dai irin sihirin da ke tare da ke shi ne a tare dani,
domin gashi dakarunki sun kasa cutar da ni da
makamansu, amma ke gashi kin cutar da ni".
Husnaila tayi murmushin mugunta, sannan ta
ce, "Ka yi babban kuskure da kake tunanin za ka
aureňi, domin abu ne wanda ba zai taba yiwuwa ba
Babu wani da namiji da ya isa ya mallakeni, idan
kuma kana ganin za ka iya ka jarraba!"
Muraisu ya gyara tsayuwarsa sannan ya ce,
"Ai babu wani abu wanda ba zai yiyu ba a wannan
duniya, sai dai ba a jarraba b.
Ina da labari cewa dan uwanki ya tsarcki da
dukkan sihirin tsafinsa, amma ni nayi imanı cewa
sirin da nake da shi a yanzu ke baki da shi tunda
shi kansa dan uwanki har yanzu bai samu ikon
shiga dajin Kirzufa ba.
Ba shi da wani buri wanda ya fi haka. Ina
tabbatar miki da cewa har ya mutu ba zai cika
wannan buri na sa ba, ni kuwa mahaifina ya shiga
dajin Kirzufa, Đima kuma zan shigeshi yanzu,
kuma tarc da ke, kuma dana ma sai ya shigeshi. Ina
mai shawartarki da ki bani hadn kai mu tafi cikin
salin-alin, idan kuwa kika ki, to fa ko ta tsiya-tsiya
sai mun je".
Sa'adda Husnaila taji wannan batu sai ta sake
bushewa da dariya a karO na biyu, sannan ta hade
fuska ta ce, "Ai sai na ga yadda za a raba hanta da
jini!"
Kafin Muraisu ya budi baki ya ce wani abu
luni Husnaila ta dako tsalle a sama daga inda.take
kamar an cillota daga cikin baka ta sake kawo masa
mummnunan hari da wannan mashi a ciki.
Gimbiya Ilusnaila ta ce, "Ta ya ya aka yi ka
san cewa ni ce Sarauniyar kyawawa ta duniya?"
Muraisu ya ce, "'Saboda mu a wannan nahiya
lamu gaba daya babu kamarki".
Gimbiya Ilusnaila ta cC, "Ba zan iya gaya
maka ba, saboda ba kowacce tambaya ce ke da
amsa ba"
Muraisu ya ce, "Maganarki dutse ce, amma
akwai gyara".
Gimbiya Husnaila ta cc, "To mene
gyaran?"
"Bari na matso kusa na yi miki bayani, domin
wani babban siri ne wanda ba kowa ake fadawa
ba'".
Kai tsaye Muraisu ya tali inda Gimbiya
Ilusnaila take tsaye kamar wani abu zai rada ma ta
a kunnc.
Koda ya iso daf da ita sai ya shammaceta
cikin bakin zafin nama ya debo hodar banju daga
aljihunsa ya watsa ma ta a fuska.
Nan take Gimbiya Husnaila taji jiri ya
kwasheta, la tafi luu! za ta fadi kasa, sai ya
sunkuya uya sabata a kaladarsa ya juya da baya ya
nufi inda ya baro su boka Rufyan suka tsaya suna
Jiransa.
Barde Kurzal, kuyan ga Sabirat, boka Rufyan
na tsayc suna hangen hanyar da Muraisu ya bi cikin
zullumi da fargaba. sai kawai suka hangoshi ya
nufosu sabe da Gimbiva Jusnaila a kafadarsa, ga
raunı a kirjinsa daure cikin shátar jini, yana tafe
yana raba kafa kamar wanda ya sha giya ya bugu.
Koda ganin haka sai Barde Kurzal da boka
Kutyan suka ruga gareshi cikin matu kar farin ciki
suka taroshi.
AA Misau
Barde Kurzal ya karbi Gimbiya Husnaila ya
taho da ita inda Sabirat ke tsaye, shi kuma boka
Rufyan ya dauko Muraisu suka kawosu bakin wata
bishiya suka shimfidesu.
Cikin hanzari boka Rufyan ya kwance raunin
Muraisu yana matukar mamakin yadda aka yi ya
sami raunin alhalin ya san cewa Sarki Salmar ya
bashi gashin sihirinsa.
Nan da nan yai sauri ya sa ma sa gan magani
akan ciwon nasa, sannan suka bashi ruwa ya sha.
Ita kuwa Gimbiya Ilusnaila, tunda aka
shim fideta ta ci gaba da barcinta ko motsawa ba ta
Bayan Muraisu ya dawo cikin haiyacinsa sai
boka Rufyan ya dubeshi cikin jınjinawa ya ce, "Ya
kai namijin duniya, dodon maza, ya ya aka yi ka
Saml Wannan gagarumar nasara har ka daukO
gimbiya Husnaila daga cikin tsaron da aka ba ta?".
Koda jin
wannan tambayar sai yarima
Muraisu ya kwashc labarin duk abinda ya faru ya
Zalyane musu. Koda jin al'amarin sai duk su ukun
suka sake cika da mamaki, musanman boka
Rufyan wanda ytai shiru ya shiga tunani mai zurli.
Daga can sai ya dago kai ya dubi yarima
Muraisu yą ce, "Ya shugabana hakika shirin sarki
Ishmar ba na wasa bane, ban taba tsammanin yana
da karfin sihiri kamar haka ba. Ina tabbatar maka
da cewa duk wannan jarumtaka da Husnaila ta yi
ba gaskiya ba ce, tsabar karfin sihirin tsafi ne
kawai.
Tabbas itama tana da gashin sihiri a jikinta,
amma abinda na ke zargi shi ne, ba irin naka bane a
Jikinta, shi ya sa mahaifinta ya kasa shiga cikin
da in Kirzufa. Hakika ba don kayi wannan hikima
ba ta watsa ma ta banju a fuskarta da babu yadda za
a yi ka iya kamota har ka zo da ita nan wajenmu.
Ina son ka sani cewar dole ne yanzu ka
hanzarta zuwa dajin Kirzufa da Husnaila kafin
hodar banjun ta saketa nan da tsawon sa'a daya jal.
Idan har ta farfado ko duniyar nan za ta taru a kanta
ba za a iya taiya da ita ba, kuma idan ma ka shiga
da ita cikin dajin Kirzufa sai ka sa ido sosai a kanta
don za ta yi iya shammatarka tayi maka irin abinda
ka yi ma ta".
Koda jin wannan batu sai Muraisu ya mike
zumbur! ya dauki gimbiya Husnaila ya đorata akan
doknsa, sannan shima ya hau nasa dokin, suma Su
Rufyan sai suka yi sauri suka hau nasu.
Barde Kurzal ne ya wuce kan gaba suka
zaburi dawakansu da gudu suka bishi a baya. Basu
tsaya a ko ina ba sai sai a bakin dajin Kirzufa.
Lokaci guda su duka suka yi tirjiya, sannan
suka sauko daga kan dawakansu. Yarima Muraisu
ya sake đaukar gimbiya Husnaila a kafadarsa. Har
ya juya zai shigc cikin dajin na Kirzufa, sai ya
Waiga ya dubesu su ukun cikin wani iin kallo mai
nuna alamun bankwana, wanda ya sa duk su ukun
suka ji tsigar jikinsu ta tashi, kuma dukkaninsu sai
zuciyoyinsu suka karaya, nan take tausayin yarima
ya tumukesu, saboda sanin cewa masifar da zai
shiga yanzu ta ninka wacce ya shiga a baya sau
dubu.
Muraisu ya tsaida hankalinsa a kan boka
Rufyan ya ce, "Bani labarin mahaifina, shin hạr
yanzu yana raye ko kuwa ya mutu?"
Koda jin wannan tambaya sai boka Rufyan-
yai shiru ýa kasa cewa komai, kawai ya kurawa
Muraisu idanu.
Barde Kurzal da kuyanga Sabirat kuwa, sai
hankalinsu ya dugunzumna, suka kama raba idanu a
tsakanin Muraisu da Rufyan, jira suke kawai su ji
amsar da Rufyan zai bayar.
Tsawon 'yan dakiku Rufyan bai ce komai ba,
kuma bai fasa kurawa Muraisu idanu ba.
Koda ganin haka sai idanun Muraisu suka
domin
ciko da kwalla har hawaye ya subuto masa,
ya ji a jikinsa cewa MAZA SUN FADI!
Kawai sai ya juya ya durfafi cikin dajin
Kirzufa kai tsaye, a lokacin da ya ji dukkan tsoro
ya kau daga cikin zuciyarsa, ji yake ina ma
mutuwar za ta zo ta daukeshi da ya fis amun
nutsuwa.
Da shigar su Muraisu dajin Kirzufa sai ya fara
arba da dabbobin daji ii-ii, kuma manya-manyan
ababan tsoro, domin sun kasance na usamman ba
irin wanda ido ya saba gani ba. Tsananin kwarjinin
dabbobin ya wuce misali, ko kwatance.
Tsakanin Muraisu da dabbobin sai kallon-
kallo kawai, dayansu bai yi yunkurin koda zuwa
kusa da shi ba, shima Muraisu ko kallonsu bai yi
ba, kawai sau ya je karkashin wata bishiya ya
shimfide Husnaila, sannan ya koma gefe daya ya
tsugunna ya kura ma ta idanu, kuma ya fada kogin
tunani.
Abinda ya fara fado masa a rai shi ne, yanzu
ya zai yi da Husnaila idan ta farka ta tsinci kanta a
cikin dajin Kirzufa?
"Lallai akwai kazamar rigima a (sakaninmu"
Muraisu ya baiwa kansa amsa.
"Kuma saí tayi yunkurin guduwa...Amma
kuma ai boka Rufyan ya gaya mini cewar ba tưisa
ta fice daga cikin dajin ba har sai mun yi kWana
uku a cikinsa, saboda haka zan zuba ma ta idanu ne
kawai na ga iyakar gudun ruwanta. "
Haka dai Muraisu ya yi ta sake-sake a cikin
zuciyarsa har ya gaji, shima saí ya kishingida a
jikin wata bishiya.
Abinka da gajiyayye, bai dađe da kishingida
ba sai barci ya kwashe shi.
Bayan 'yan dakiku kadan kuma sai Husnaila
ta farka.
Koda la bude idanu ta tsinci kanta a cikin
wani iin daji na musamman sai ta takarkare ta
tsandara uban ihu. Muraisu ya farka firgigit! a
razane, dabbobin cikin dajin kuwa, hatta sauran
Rananan kwari da tsintsaye sai da suka razana, suka
kama guje-guje.
Duk dabbar da tayi arba da su Muraisu sai ta
yıyo kansu:
Nan fa aka kasa uban tserc tsakanin su
Husnaila da dabbobin dajin gaba daya.
Babu abinda zai baiwa mutumn mamaki face
Lsananin gudun da Muraisu da Husnaila ke yi
tamkar akan iska suke yinsa ba a kan kasa ba.
Duk su biyun sun yi matukar mamakin irin
gudun nasu, domin tamkar walkiya suke gifta
komai, sai dai karfin gudun nasu duk ya zama na
banza, domin duk sa'adda suka waiga bayansu sai
su ga dabbobi kusan guda dubu daf da su.
Duk inda suka dauke
dabbobin suke sa nasu.
sawayensu
anan
da
Babu abinda ya fi firgita su Muraisu face
cafka
kawo musu
yadda dabbobin ke
bakunansu, don su cinyesu, musamman wani katon
Zaki wanda idan ya wangame bakinsa sai ka ga
kamar ijiya mai zurfi da fadi aka bude.
Sai da su Muraisu suka shafe sa'a guda cif!
Suna falfala natsanaicin azababben gudu, sannan
suka hango wani katon tsauni a gabansu.
Basu tsaya jiran komai ba suka hau kan
tsaunin a guje, har sai da suka je can. samansa
sanann suka waigo baya.
Bisa mamaki, sai suka ga gaba dayan
dabbobin sun tsaya a kasan tsaunin đayansu bai yì
yunkurin hawowa ba.
Al'amarin da ya matukar basu mamakia ke
nan, Kawai sai suka zube kasa a saman tsaunin
suka kama haki, da fitar da numfashi da saurí da
sauri.
A sannan nc fa kishirwa ta ischsu, kuma
gashi
babu damar shawagi a kasan tsaunin tamkar an
basu gadin abinda ke kan tsaunin.
A dai-dai wannan lokaci ne Husnaila ta dubi
Muraisu cikin harara da fushi ta ce, "Ya ya aka yi
ka kawoni cikin wannan daji?"
Koda jin wnanan tambaya sai Muraisu ya yi
murmushi ya ce, "Ba wannan tambayar ya kamata
ki yí mini ba a yanzu, kamata ya yí ki tambayeni a
ina zamu samu ruwan sha?"
Husnaila ta sake murtuke fuska ta ce, "Ba
ruwa ne a gabana ba. Ka mayar da ni inda ka
daukoni, domin ina da bukatar na koma gida kafin
magariba tayi".
Koda jin wannan batu sai Muraişu ya bushe
da dariya har da bingirewa Kasa, sannan ya nutsu
ya ce, "Ai idan har kin ga kin fita daga cikin dajin
nan sai kin yi kwanaki uku cikakku a cikinsa!"
Cikin fushi da mamaki Husnaila ta mike tsaye
ta ce, "Ai kuwa idan ka ga na kara koda dakika
đari ne a cikin wannan daji sai idan bana
numfashi. "
Koda gama fadin hakan sai ta mike tsaye ta
fara saukowa kasan tsaunin. Muraisu ya bita da
kallo kawai ko motsi baiyi ba daga inda yake
zaunc.
Lokacin da ya rage saura bai fi taku biyar ba
ta iso kasan tsaunin, sai kawia ta ga wannan
ma ta haikan
Zaki ya taso
turmusheta. Ba shiri ta juya da baya da gudu ta
koma kan tsaunin inda Muraisu yake.
Koda ganin abinda ya faru sai Muraisu ya
kama yi ma ta dariya. Al'amarin da ya kara
tunzurata ke nan, ta kamu da tsananin fushi. Bisa
dole taje gefe daya, nesa kadan da inda Muraisu
yake zaune itama ta zauna.
Babban abinda ya i daurewa Husnaila kai shi
ne, ya ya ita da bata da tsoro ko kadan amma taji
tana tsoron dabbobin wannan dajı?
Kawai sai ta dubi Muraisu ta ce, "Wai shin
wannan wane daji ne muka shigo?" Muraisu ya yi
ajiyar zuciya sannan ta ya ce, "VWannan shi ne dajin
KIRZUFA! Kanar yadda na gaya miki da farko sai
mun yi kwana uku a cikinsa ni da ke, a sannan ne
na sami
Zan sauya miki rayuwarki, kuma
soyayyarki, mu tafi izuwa birninmu na Lairuf mu
yi aure".
Kafin Muraisu ya gama rule bakinsa tuni
Musnaila ta tofa masa yawu a fuska,
Cikin tsananin fishí ya mike tsaye zumbur! ya
zare takobinsa, itama saí ta mikc Zumbur! ta rike
mashinta suka fara kallon-kallo, har gaba dayan
jikin Muraisu na tsuma saboda fushi, domnin a íva
rayuwarsa ba a taba yi masa iin wannan
wulakancin ba a matsayinsa na dan Sarki, kuma
gawurtaccen jarumi.
Husnaila ta dubcshi a wulakance ta ce,
"Na
tsancka! Kuma na tsani dukkan zuril'arka, Har
abada ba zan ta6a sonka ba, kuma ní da dan uwana
Sarki Ishmar sai mun baje birninku, mun konc
dukiyoyinku, mun kame matanku da 'ya'yanku sun
zama bayinmu. Mazajenku kaf sai mun kashesu",
Koda jin wannan batu saí Muraisu yaji ya
tsani lusnaila kamar yadda yaji ya tsani
mutuwarsa. Duk wannan tsananin kyawu nata sai ta
rama kamar dodanníya a idanunsa.
IHar ya yunkura zai afka ma ta su yi yaki, sai
ya tuna cewa ai sihiri ne a jikinta wanda ya sa ba za
ta laba son wani da namiji ba face ta ci ta sha daga
abubuwan da ke cikin wannan daji na Kirzufa na
tsawon kwana uku.
Koda tuna wannan al'amari sai jikin Muraisu
ya yi sanyí, ya fasa afkawa Husnaila ya koma ya
zauna. Koda ganin haka, sai itama ta koma inda
take ta zauna.
A sannan ne fa kishirwa ta ci gaba da
addabarsu. Babu shiri suka mike tsaye suka kama
yawo akan tsaunin kowannensu na neman ruwa,
amma babu ko alamarsa.
Duk sa'adda suka leko kasan tsaunin kuma sai
suka ga wadanann dabbobi suna nan suna kewaya
tsaunin, jira kawia suke su sauko su afka musu,
Bisa dole suka hakura.
Lokacin da 'yan sa'oi suka kara shudewaa sai
magariba ta doso kai, gari ya fara duhu, a sannan
ne tsananin kishirwa tasa suka baje a kasa suka
kama num fashi sama-sama kamar za su muti. Sai
da kowannensu ya fara suma, kwatsam! ba zato ba
tsammani sai hadari ya gangamo aka fara tsawa da
walkiya gami da wata irin gagarumar iska mai
karfin gaske. Kafin a jima ruwan sama ya tsuge
karmar da bakin kwarya.
A sannan ne Muraisu da Husnaila suka
farfado, sai kowannensu ya wangame bakinsa suka
kama shan ruwan, har sai da suka koshi, sannan
suka dawo cikin haiyacinsu, sai dai babu inda zå su
fakewa wannan ruwan saman, dole suka hakura
ruwa yai ta dukansu har izuwa tsawon sa'a guda,
sannan ruwan saman ya dauke dif.
Nima Kuma Wanga Ruwa Yana Daukewa Nima Na Dauke Daga Typing hhhhh
Zan dakata anan sai kuma wani lokaci
Zamu cigaba
Insha Allah
Likes and comments
Domin hakan na sa mu cigaba
Ga masu shA award whtsp grp
https://chat.whatsapp.com/E0GMznXcaxwC0avNVdF30Q
BUSA A MUTU
Littafi Na Biyu (2)