← Book details Bakar Inuwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 7 OF 7

Chapter 48

Bakar Inuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 271 min read

48

.........Duk yanda taso zamewa basa abincin fir yaƙi. Dolenta ta bashi kamar yanda ya buƙata, kunya kamar ta tsaga ƙasa ta nutse a ciki. Shiko ko'a kwalar rigarsa. Sai ma idan tayo ƙatuwar lauma ya harareta wai tafi ƙarfin bakinsa. Amma in namane dataso ragewa zai riƙe hanun da faɗin ‘Ban san mugunta Ustazah’.

    A haka dai yaci ya ƙoshi itama ya tsareta sai taci. Fuska ta marairaice tamkar zatai kuka amma yace saifa taci babu ɗaga ƙafa. Dole ta ɗan tsakura dan a takure take sosai. Bayan ta kammala ta tattare kwanikan ta fita da su. Numfashi ya sauke a hankali da barin aikin da yake a lap-top ya kwantar da kansa jikin kukerar yana lumshe ido da furzar da numfashi. Sai kuma ya kai hannu a wuyansa dan har yanzu akwai zazzaɓi jikinsa dauriyace kawai. ‘Oh Ramadhan Taura ka zama ɗan cali-cali kuma?’. Sai kuma ya sake sakin murmushi da girgiza kansa kaɗan. Shi kansa baya sanin sanda yake biyema Raudha. Abinda ya sani kawai bai son ganinta cikin damuwa kamar baya. Sannan addu'arta a koda yaushe na bashi nutsuwa. Yayinda idan tana a yanayin tsoro da kunya take hana fitinarsa zama lafiya ya dingajin kamar kawai ya...... “Ya ALLAH” ya ambata da kai hannu cikin sumar kansa. Sai kuma ya tashi zaune sosai ya cigaba da sarrafa system ɗin cike da ƙoƙarin son ture abubuwan dake neman fin ƙarfin jarumtarsa......


_______________★★_____________


     Alhmdllhi zamuce abubuwa sun fara daidaito tsakanin Ramadhan da Raudha, ta saki jiki dashi ba laifi suyi ɗan wasa da dariya. Idan kuma taga ya haɗe fuska ta kama kanta ta nutsu. kwana ɗakinsa dai bata sake yarda tayiba tun randa yay zazzaɓi. Amma yanzu tana ƙoƙarin tashi a kowace bayan sallar asuba ta haɗa masa breakfast da kanta. hakama abincin dare kafin ya shigo takai komai bedroom ɗinsa ta ajiye. Wataran ya leƙata da matsa mata tazo ta bashi abinci. wataran ya shareta yaci abinsa sai da safe idan tazo gyaran ɗaki ta tattare.

     A washe gari Ramadhan da Bappi suka gana, ganawar data zama ta farko a zahiri da har ƴan jarida suka fitar. Sai dai babu wanda yasan mi suka tattauna a zaman nasu sai ni (Bilyn Abdull cctv footage ɗin ku😉😂). Sosai kansu ya tushe da mamakin ganin rubutun Raudha dai-dai da takardar da aka turama Bappi ana jibi ɗaurin aurensa da Raudhan. An musu nuni ne da karsu yarda Ramadhan ɗin ya tare a gidan gwamnati har sai an cire ac ɗin dake a bedrooms nashi da falukansa saboda akwai poison a ciki. Ranar sun shiga tashin hankali musamman Anne datace Ramadhan bazai tare government house a kashe mata shi ba. Shi da Bappi sukaita lallashinta da mata nasiha harta nutsu, inda basuyi ƙasa a gwiwa ba randa Ramadhan ya shiga gidan gwamnati kwana biyu da aurensa da Raudha suka canja duk ac ɗin dake sashen harma dana office ɗinsa. Hakama sai da suka bincike lungu da saƙo na ɗakin barci da falukansa na sirri gudun ko an saka camaras a ɓoye. amma Alhmdllhi babu alamar hakan sai iya ta inda ya dace kawai da dole a samu a kowane gidan gwamnati saboda tsaro. Dan wani yaron Aunty Zuhrah ne yay aikin. Sun sake tsintar kansu a tashin hankali lokacin da suka samu poisons a cikin ac's ɗin. Ranar har hawaye Bappi yayi. Daga haka kuma ya ɗarsama kansa zargin akwai boyayyen al'amari. Sai dai kai tsaye bai fito ya ambaci sunan kowa ba. Babban fatansu kawai susan wanene wannan mai turo saƙo. Hakan yasa ganin wannan hand writing da yay dai-dai dana Raudha yay matuƙar ɗaure kansu.

    “Wannan ya sake tabbatar min yarinyar nan Alheri ce kuma akwai dalilin zuwanta garemu”. Bappi ya faɗa lokacin da suke ganawa da Ramadhan a office.

   Cikin sauke numfashi Ramadhan yace, “Tabbas akwai abinda bamu saniba kuma ita take ɓoye mana. Abin ɗaure kan anan kawai shine a gaba ɗaya tarihin yarinyar dana bibiya babu wani alamun alaƙarta da wani sai danginta ko anan cikin Bingo. Sai dai sister ɗin mom nata tanada alaƙa da matar forma president, a yanzu kuma matace ga Alhaji Yaro glass Vice ɗina, dama kuma sun taɓa zaman aure ta fita. Bappi inhar hasashena yana kan dai-dai akwai boyayyar manufa tsakaninka da abokan nan naka gaskiya”.

   Murmushi Bappi yayi yana ɗan jinjina kai. “Komai zai iya faruwa musamman idan akai la'akari da abubuwa masu yawa. Sai dai bana so zargin sunan kowa anan har sai muntabbar. Shawarata gareka anan lkawai ka cigaba da jan yarinyarnan Ameenatu a jiki, zaka iya jin fiye da abinda muke buƙata daga gareta. Amma tabbas ka shaida naji ƙarin ƙaunarta a raina da kimarta fiye da zaton mai zato. Dan zuciyata bata gayamin an haɗa kai da itane dan a cutar damu”.

   A hankali Ramadhan ya sauke numfashi wani abu mai sanyi na sauka masa a cikin zuciya. Jiyake kamarma ya buɗe ido ya ganta gabansa. Jin yau ɗin yake daban da kullum a rayuwarsa. Sai dai me, yana zuwa gidan ya iske ɓacin ran su Lubnah da har takaisa ga marin Lubnah ɗin. A kuma daren yasa driver maidata gida. Sai dai abun ƙarin takaici washe gari Maah tasa aka maidota.

   Wannan haushin ya sakashi tunda ya fita gida da safe bai dawoba sai dare. Washe gari kuma tafiya ta taso masa zuwa ƙasar faransa babu wani walwala tattare da shi sukai sallama da Raudha da ayanzu ta sake nutsuwa akan makaranta dan harta fara jin daɗin lectures din saboda taimakon da su Basma ke bata.

  Ta ɗan shiga damuwa da canjawar tashi, sai dai daga baya ta watsar da komai dan indai dan abinda su Lubnah sukai matane ita ya wuce a gareta basa ma gabanta. Fatanta dai ALLAH ya bata kariya daga cutar da waninsu.


   A washe garin daya wuce ta tashi da ciwon mara. Tasha azaba sauƙintama yasa Bilkisu dawowa gidan saboda ya fahimci suna ɗasawa da Raudha ɗin. Sai dai sunsha gargaɗi kamar babu gobe akan abubuwa da yawa. Hakama su Muneera sunsha nasu, dama tun marin da Lubnah tasha suka koma shiru-shiru a gidan dan sun san hali. Yanzu ko daya tafi sun ɗau alwashi kala-kala akan Raudha sai akai rashin sa'a Bilkisu ta dawo kusa da ita.  

   Bilkisu ce ta sanar masa halin da Raudha ke ciki ta hanyar massege. Hankalinsa ya tashi lokacin daya lura ta text ɗin. Sai kuma a lokacin ya tuna da zancen Dr Hauwa'u a wancan lokacin. Bai samu magana da Bilkisu ba sai dare bayan ya samu nutsuwa. Ta kwantar masa da hankali akan da sauƙi, dan Anne ta kira shine ta turo musu Maman Jabeer (Dr Hauwa) tazo ta dubata. Ta tabbatar masa tayi faɗa sosai akan ƙin zuwan Raudha ɗin bayan tun wancan karon tace taje bayan ta warke.

    Yaji babu daɗi sosai, dan kuwa akwai sakacinsa tunda shine bai nuna maida hankali akai ba matsayinsa na wadda take a ƙarƙashinsa. Bai ce a haɗashi da Raudha ɗin ba, sai dai ya tabbatar ma Bilkisu tayi ƙoƙari idan Raudha ta samu lafiya suje asibitin Maman Jabeer ɗin.


    Haka kuwa akai, bayan kwana biyu ta koma ragas kamar ba'ita ba. Dan haka sukaje asibitin da dare gudun idon mutane. Sai dai tana tare da dogaranta duk da hakan. 

   Sosai Dr Hauwa tai mata gwaje-gwaje na musamman yanda ya kamata. Cikin amincin ALLAH kuma ta gano matsalolin dake tare da Raudha ɗin harda imfection. Magunguna ta bata tare da wani bayanai a rubuce tace ta bama Ramadhan ba nata bane. 

     Kamar yanda akace shi ɗin zata bamawa kuwa bata buɗaba ta ajiye ta cigaba da sabgar gabanta. Tayi fes da ita, da alama kuma makaranta ta fara buɗe mata idanu da wasu abubuwan. Gashi bata wasa sam da karatu sosai take nuna ƙwazo dake bama su Basma dama class mate ɗin nata mamaki. Gashi taƙi yarda kowa yasan ita wacece, koda yaushe fuska a ƙunshe da niƙab. Bata shiga harkar kowa sai su Basma. Wasu na mata kallon girman kai wasu kuma tana ɗan birgesu duk da basu san wacece ita ba. Suma su Basma kuma sun kame bakinsu saboda gargaɗin Ramadhan da Anne. 


    ★Kasancewar yau juma'a da wuri ta dawo school. Ta zube a falo Bilkisu na mata dariya. “Aunty ahaka za'ai karatun kuwa?”.

   Dariya itama Raudha tayi tana ajiye ruwan data sha sosai. “Wlhy bazaki ganeba Aunty. Abunfa babu sauƙi sam. Dan masifa yau text har biyu mukayi ga submitting Assignment ɗin masifaffen malamin nan da nake gaya miki”.

    Cikin dariya Bily tace, “Haka ake shan yaƙi ai Aunty har a cimma nasara. Fatanmu dai ki fito da first class duniya tasan firt lady ɗinmu bata wasa bace”. 

  Dariya Raudha tai tana miƙewa. “Uhhm Aunty Rabani da wata first lady. bara na watsa ruwa nazo naci abinci ko breakfast banyiba yau”. 


   Bayan tayo wankan anan suka baje a falon bilkisu na sake nuna mata aikin yau da mata ƙarin bayani. Salla kawai ke tadasu har magrib. Sam Raudha batasan yau shugaban ƙasa zai dawo ba dan tunda ta shigo gidan basu buɗe tv ba. Bayan sallar isha'i taɗan sake watsa ruwa. Fitowarta kenan a toilet ɗin ta samu wayarta na ringing. Cike da zumuɗi ta ɗaga ganin Fatima. Tun jiya suka sanar mata yau zasuje Hutawa duba Abba (Dauda) da baida lafiya. Taso zuwa amma babu dama har kuka tayi. Sai dai ta ƙudiri niyyar idan Ramadhan ya dawo zata roƙesa alfarmar zuwa itama. Bayan sun gaisa dasu Fatima har dasu Inna Fatisa ke sanar mata ga ƙawarta Zubaida da tazo duba Abban su gaisa.

   Cike da mamaki tace “Zubaida fa? Dama bata mance ina duniya ba?”.

   “Ni na isa first lady ɗinmu. Ranki ya daɗe kin wuce a manta dake ai a ƙasar NAYA ”.

  Zubaida data amsa wayar ta faɗa.

“Mara kirki bazaki canjaba dai?”.

Cewar Raudha cikin dariya.

   Dariya itama Zubaida ɗin tayi, kafin su gaisa a mutunce. Zubaida ƙawartace ta islamiyya. Itama yarinyace mai ƙwazo da sanyin hali kamar Raudha. So da yawama akance halinsu yazo ɗaya ne shiyyasa suke abota. Duk da abotar tasu bawai takai mai tsanani bace da har suka san sirrikan juna musamman ma Raudha da ba'a jin cikinta. cikin tsokana Zubaida ke faɗin, “Halan kin kusa sauke mana babynmu ranki ya daɗe”.

    Raudha tai dariya tana ɗakko kayan da zatasa a Wadrobe. “Aiko gashi ma har yana motsi a ciki, ina fatan kun shirya zuwa suna”.

  Dariya sosai Zubaida keyi. Itama Raudha haka. “Uhm matsoraciya keda rakin nan naki ace cikin ya tsufa za'aji muryarki haka ragal”.

   “Tabɗi mi kika ɗaukeni. Ki shirya zuwa Bingo kiga yanda nake daram kuma ga ƙaton cikin ƴan biyunku tare dani. K cikinfa ba wani wahala kwantar da hankalinki ke huɗu zaki samo mana lokaci guda......”

    “Idan ita bata samoba ke zaki samoshi yau ɗin nan”. A mugun firgice Raudha ta juyo har towel ɗinta na ƙoƙarin kwancewa jin muryar wanda batai zatoba balle tsammani. Sanye yake cikin kananun kaya tausasa gaba ɗaya baƙaƙe. Ya ƙara wani fresh abinsa harda ɗan tumbi alamar hankalinsa kwance yake. Ga sumarsa data sake samun kulawa na gyara. Sam batasan ya dawo gidan ba balle shigowa ɗakin dan ko shigowar motocinsa yau batajiba sam kokuwa hankalintane bai a wajen, ta diririce da rasa inda zata tsoma ranta taji daɗi ganin ita yake nufowa. Har yazo gab da ita bata samu mafitar kare kanta da ko saka hijjab ba. Ta cikuykuyo wasu kaya zata yafa a jikinta ya riƙe yana mai zagayawa ta bayanta ya rungumota jikinsa.

    Wayar ya zare da kallon screen ɗin, tuni dama ta yanke kiran, sai dai hakan bai hanashi ganin da Fatima tai wayar ba. “Ai bansan kina bukatar ƴan uku ba Ustazah da tuni na ajiye ƙawancenmu gefe na baki ajiyarsu”.

   Innalillahi ina ƙasa Raudha ta shige ta huta. Ya sake kanainaiyeta jikinsa da kai hannun kan ɗaurin towel ɗinta zai kamar zai kwance. Da wani irin zafin nama ta wulƙito ta rungumesa jikinta na rawa sai ambaton “Innalillahi...” take har ƙarshe. Shiko mizaiyi inba dariya ba. Sai dai yay dauriyar gimtsewa abinsa ya sake kama towel ɗin data ƙanƙanme cikin hannu ta gaba ɗaya. “Dan ALLAH ka rufamin asiri karka cire Ya Ramadhan. Inba hakaba zan iya rasa numfashina”.

    “Sai in baki nawa mu rayu tare ai”.

Ya faɗa cikin raɗa da wata irin murya mai wahalar fassara ga Raudha.

   Raudha ta sake ƙanƙamesa saboda yanda zuciyarta ke masifar gudu cikin ƙirjinta. Tunda suke bai taɓa mata kalar abun nan ba. Iyakarsa taɓa hanunta fuskarta ya dan sumbata ko laɓɓanta. Amma bai taɓa gwada ɗora hanunsa a wani sashe na jikinta ba sai yau. Dan kuwa a bazata taji saukar hanunsa kan ƙirjinta. 

   “Na shiga uku”.

 “Baki shiga uku ba. Ai maganar kunya kuma ta kare insha ALLAH yau zamu neman ƴan huɗu............✍


End of book
Leave a comment

Post

Comments

104835043420935222197
Masha Allah muah😍🤗🤗

16 minutes ago


Contact Us
Arewa Books Publishers

WhatsApp: 09031774742

Email: [email protected]

Navigation
Home
About
FAQ's
Legal
Privacy Policy
Terms of Service
Social
Facebook
Instagram


Copyright 2021, Arewa Books | ALL RIGHTS RESERVED | Powered by thinkcrypt.io


*_Typing📲_*


*_Episode 49 & 50_*


..........Da asuba daya tadata suyi salla kuka ta dinga masa sosai. Duk sai tausayinta ya lulluɓesa. Shi kansa yasan ya tsaurara mata da yawa, dan dukan fushinsa na shekarun nan babu ƙwange sai da ya sauke shi tsaf. Bata wani yarda ya taimaka mataba tace zata iya.
   Koda ya haɗa mata ruwa sai ya fita a toilet ɗin ya barta. Zafin ruwan ya sata harar ƙofar tana ƙunkuni ta surkeshi ya koma salaf. A haka ta gyara jikinta ta fito tana faman sinne kai. Ga dariya ga tausayi duk suna cin Ramadhan lokaci ɗaya. Amma sai ya gimtse dan karya sake tunzurata.
      Da ƙyar ta yarda suka sake komawa barci bayan ta idar da sallar. Acewarsa su ɗan ƙara rage barcin idonsu dan anguwa zasuje. Taura house yake son suje hutun nan na kwanaki biyar da akai, amma bai sanar mata ba. Dan kuwa bazai yarda amarcin nan ya wucesa bai ɗana gadonsa na Taura house ba.

(Mutumin nan ko😂😜)

         ★Tun a daren jiya dama ya sanarma ƙanensa yau zasu wuce Taura house hutu gaba ɗayansu. Dan haka da safe ya turama Bilkisu text ta haɗama Raudha abinda duk tasan zatai amfani da shi su wuce su sai zuwa anjima zasu zo. Murmushi kawai Bilyn tayi. Sai dai kafin su fita tai ƙoƙarin haɗa breakfast ta ajiye musu. Mama Ladi kuwa ta zauna gadin abincin nan dan kuwa Anne ta kirata tun sanda suka gane Raudha ce ta aika musu takarda akan saka poison a ac ta ce mata ta dinga saka ido akan kowa na gidan kar'a cutar mata da su Raudha. Duk da tasan bata isa hana zartar da ƙaddarar UBANGIJI akansu ba.

        Yanzu kam Raudha ce ta fara farkawa. Ta buɗe idanunta da sukai mata nauyi matuƙa. Akan fuskar gogan nata ta saukesu. Idanunsa a lumshe, ƙyaƙyƙyawar fuskarsa tayi wani fayau. Duk da haushinsa na murzar da yay mata jiya babu tausayi da takeji haka ta shagala a kallonsa. Itama kanta tasan shiɗin ƙyaƙyƙyawa ne, ga yanayin jin daɗin rayuwa daya tashi a ciki, bai san wahalar komai ba sai ta karatu. Ahankali takai yatsanta saman girarsa data daɗe tana kwaɗayin taɓa tsagar wajen da zuciyarta ke bata wanzami yay masa. Sai dai me, koda ta shafa wajen sai taji santsi irin na tabon ciwo. Mamaki ya kamata, a zuciyarta tace, (Ashe ba tsaga masa akeba tabon ciwo ne) a fili kam mamaki ƙarara ya bayyana gareta da sake girmama sunan UBANGIJI, dan babu mai kallon wajen yace ciwone. Sosai tsagar ta fita da tsari kamar yimasa akai akan sani. A hankali ta sauke numfashi da maida gashin girar data yamutsa masa ta maidashi ya kwanta. Tana ƙoƙarin sake janyewa taji an riƙe hanun. Babu shiri tai saurin rumtse ido tana fisgewa amma yaƙi saki. Nasa lumsassun idanun dake cike da barci ya buɗe a hankali a kanta. Sai kuma ya sumbaci hanun nata daya riƙi ya turashi ƙasan kuncinsa yay filo da shi.  Ɗayan hanunsa kuma ya ɗaura a jikinta saitin ƙugunta.
     “Good morning sweetheart”.
  Wani bala'in kunyane da yafi na ɗazun da asuba ya lulluɓeta. Tai ƙoƙarin kauda kanta yay azamar tallafosa da hanunsa dake a ƙugunta ya hanata hakan. Cikin ɗan marairaicewa yace, “Ki amsa min mana Baby luv”.
        Da ƙyar ta iya buɗe baki tace, “Ina kwana”.
      Ahankali ya shafo kanta tun daga sumar gaban goshin har zuwa ƙeya yana ɗan murmushi. “Ya jikin ki? Duk da nima dai ya kamata a tambayeni nawa kodan yaƙushi da cizon dana sha”.
      Ina ƙasa Raudha ta shige ta huta. Tai ƙoƙarin jan hanunta da yay filo da shi amma ta kasa. “Kibar wani gulma Ustazah, nasan kina son mijinki kar kiyi sake wata ta ƙwace miki ni”.
      Kanta tai ƙoƙarin sinnewa a jikinsa. Yay murmushi yana riƙeta ya hana hakan. “Gara na faɗa miki gaskiya matsayina na abokinki babban amininki. Bazan so a miki kishiyaba kina ƙawata ta hanun damar, dan sai na fiki kishi kilama kullum dani zaki dinga cin dabe da ita a gidan ga muna lakaɗa mata duka ko ya kikace?”.
       Duk yanda taso riƙe dariyarta ta kasa. Ta saki murmushi tana turesa. “Kai Ya Ramadhan....”
      “K nifa bana wani kalar dangi ƙannena sun isheni, inama laifi da muke abota niba yayanki bane”.
   “Toni ai bazan iya faɗar sunanka ba”. Tai maganar tana sake son cusa kanta a ƙirjinsa. Haɓarta ya riƙo ya ɗago fuskar tata da sumbatar laɓɓanta. Cikin sake ƙanƙan da murya yace, “To basai ki canjamin da wani ba. Amma sam bana son Yayan nan kamar wani zamanin iyaye da kakanni, bayan kuma jiya na gama turmusheki a gadon na....”
       Dariya ta ɗan ƙyalƙyale da shi tana kaimasa ƙaramin duka a ƙirji. Shima sai ya rungumeta yana murmushi. Zuciyarsa fes da farin ciki.

       Duk yanda taso zamewa kar suyi wanka tare bai bata damarba. Amma kuma taƙi sakin jiki haka ya gama nashi ya barota a bayin. Sanda ta fito yana zaune yana waya. Dan haka tai wuff ta fice a ɗakin bayan ta saka hijjab.
       Ciwo take ɗanji kaɗan-kaɗan a ƙasanta amma ta daure ta shirya cikin wani material da yay mata ƙyau sosai da fiddo kalar fatarta. Tayi fayau da ita daka ganta kaga amarya, sai dai fuskar babu walwala sosai ga idonta duk wanda ya kalleta yasan taci kuka. Yunwa takeji amma batajin son cin abinci kuma. Bakinma ɗaci takeji yana mata kamar mai malaria. Tana fesa turare ya shigo, sanye yake cikin shadda ash color datai bala'in masa ƙyau. Sai maiƙo take da ɗaukar iadanun mai kallo. Ya murza hula baƙa data fiddo ainahin hasken fatarsa da ƙyallin angwanci. Duk da waya ya shigo yanayi hakan bai hana Raudha shiga jin kunya ba, ya ƙaraso inda take yana riƙe kwalban turaren da kunya tasata cigaba da fesa ƙasa-ƙasa dan karya tada mata asthma. Ajiyewa yay saman mirror ɗin ya riƙe hanunsa cikin nata idanunsa a saman ƙyaƙyƙyawar fuskarta da yakeji kamar ya haɗiyeta. Ga ɗaurin datai ya sake fiddo ƙyanta kamar dai ya haɗiyetan ya huta kawai. Ita dai kanta a ƙasa tana shaƙar daddaɗan ƙamshin turarensa na _Dolce & gabbana_ daya gauraya da _burberry brit_. shiko yanata wayarsa da murza yatsun hanunta.
      Tsawon lokaci harta fara gundura da tsaiwar kafin yay sallama da wanda yake maganar wanda ta fahimci kamar akan harkar kasuwanci ne. Saman mirror ya ɗaura wayar da kamo fuskarta cikin tafukan hanunsa ya sumbaci goshinta, sai kuma ya sakko a hankali ya sumbaci lips ɗinta dake ƙallin lips gloss. Shima ya duƙo kaɗan yana nuna mata nasa kumatunsa da goshi.
       “Kai Ya Ramad......”
Sai kuma ta kasa karasawa saboda ɗallin daya bama bakinta. “Dole na fara hukunta wannan bakin idan yaya ɗin nan bai fita a cikinsa ba”.
     Hannu tasa ta rufe laɓɓanta da zafi ya maimaye idonta na cika da ƙwalla. Hannunta ya kamo ya zuba mata link ɗinsa da agogonsa _hublot_ dayay mata ƙyau sosai kalar ash. Batai musu ba, dan koba komai tasan aiki garesa lada ne. Links ɗin ta fara saka masa sannan agogon.
     “Thanks bestie”.
Ya faɗa a hankali idonsa a kanta. Sai kuma ya janye yana ƙoƙarin barin wajen mirror ɗin. “Ƙarasa mu wuce so nake na more gida sosai lokaci nata tafiya”.
       Duk da batasan ina zasu ba cike take da ɗokin tafiyar. Ta ɗauka hijjab da zai shiga da kayanta ta saka tare da haɗa abinda zata iya buƙata a karamar handbag. Tana duba takalmi a akwatin lefenta ya sake shigowa. Bai yi magana ba yabi duk kayan wutar ɗakin ya kashe komai. Dai-dai tana gamawa yake faɗin, “Ko breakfast bazamu tsaya yiba mayi acan kawai”.
     Kanta ta jinjina masa, sai dai har yanzu taƙi yarda su haɗa ido. A hankali ya matsa gefenta yay musu hoto bayan ya faɗi abinda ya sakata ɗagowa ta kallesa a ɗan tsorace. Sai hoton ya bada wani style mai ƙayatarwa kamar anyisane da shiri.

        Bayan sun sallami su Mama Ladi suka fito compound inda jerarrun motocin da zasu fitan suke. Yau ce karo na farko da zasu fita tare da shi a bayyane. Sai gaisuwa ake miƙa musu cike da ɗunbin girmamawa wadda har Raudha takejin babu daɗi akanta. Dan kuwa da yawansu sun haifeta da girmarta. A motar da tafi kowace mota ƙyau da ɗaukar idanu ga tutocin ƙasar naya a jikinta suka shiga. Kafin wanda zasu musu rakkiya Taura house ciki harda cos da wasu ministers uku suma suka shiga. Ba wani tafiya mai tazara bace ba, amma ta fahimci an bama fitar muhimmanci matuƙar dan har a redion motar da driver ya kunna saiga sanarwar yau shugaban ƙasa Ramadhan B. Hameed Taura zaije hutun ƙarshen shekara gidansu a karo na farko tun bayan hawansa mulki na watanni kenan. Anan aka saka zantukan mutane daban-daban daketa masa addu'a shi da iyalinsa akan yasha hutu lafiya cikin farin ciki.
     Sosai ya ƙara samun nutsuwa a ransa dan kuwa zuwa yanzun ayyukan daban-daban da suka faro na talakawa sun kankama matuƙa. Abinda zai matuƙar birgeka duk wani mai kwangilar gwamnati sunansa da aikin da zaiyi a bayyane yake ga al'umma. Hakan yasa yake ƙara samun addu'a ga talakawa dan kuwa babu wani ƙunshe-ƙunshe balle a cucesu a ƙiyi musu aiki kuma su rasa daga ina matsalar take. Kai hatta kuɗin da aka bama masu kwangilan da wanda sukebin bashi sai sun kammala a cika musu duk an sanar da duniya babu wani rifa-rufa. Hakan da yay ya matuƙar taimakawa da saka tsoro a zukatan masu kwangilar dan sun san kam inma basuyiba sune a ruwa tsundum. Gashi har adadin watanni ko shekarun da aikin zai ɗauka kowa ya sani a bayyane. Bashi kaɗaiba hatta da gwamnoni da ƴan majilusu, ciyamomi, kansiloli duk aikin da zakai ma ƴan yankinka a jihohin nan 41 dolene ka sanar da komai talakawa su sani.

        Tarba ce ta musamman tawagar shugaban ƙasa ta samu a Taura house, dan kuwa wannan shine karo na farko da yazo gidansu a bayyane kuma da shirin kwanaki. Sosai bakin Anne da su Yafendo ke a buɗe, ganinsa ya musu wahala yanda suke buƙata tunda ya hau mulkin nan. Raudha dai gaba ɗaya a takure take. Jitake kamar kowa zai iya gabe abinda ya faru a tsakaninsu jiya. Ga anne da su Yafendo sai nan-nan suke da ita kowa na saka mata albarka. Bayan gaishe-gaishe da addu'oi Ramadhan da su Bappi suka fita salla dan tawagar datai masa rakkiya sun koma. Sai dai Taura house tako ina zagaye yake da securitys kai gaba dayama anguwar. Dole ne ka shaida shugaban ƙasa na nan koda matakan tsaron dake kewayen anguwar baki ɗaya, kai kace ko ƙuda bazasu bari ya gitta ba.
           Da ƙyar Raudha ta iya tsarki da ruwan sanyi tsabar zogin da wajen ke mata zuwa yanzun. Har jin kanta take kamar wadda zazzaɓi zai saukarmawa. Anne na lure da yanayin nata sai dai batace komai ba dan zuciyarta bai kai ga zargin abinda ke faruwa da Raudha ɗin ba kai tsaye. Gashi tunda suka shigo dama yanayin idanunta na wadda taci kuka ya tsayama Anne a rai. A ɗakin Anne sukai salla duk da kuwa an gyara sashen Ramadhan ɗin tsaf domin su.
      Bayan idar da salla gaba ɗaya gidan ƴaƴa da iyaye aka haɗu domin yin lunch a katafaren falon Bappi. Abincine mai rai da lafiya da gamsarwa a wajen iri-iri. Anyi hakanne kawai domin walimar zuwan Ramadhan ɗin da Raudha. Sai yanzu Raudha taga gimbiya Su'adah da sauran matan gidan, dan kuwa bata shiga gaishesu ba Anne tace sai zuwa yamma sun huta. Sai dai shi Ramadhan ya shiga ya gaida Gimbiya Su'adah ɗin kawai ganin bata a masu fitowa tarbarsa. Kasancewar salla zai fita yasa bayan gaisuwa babu wani abu daya shiga tsakaninsu ya fito suka fice massallaci.
     Har ƙasa Raudha takai tana gaishe da iyayen. Kowa ya amsa mata cike da kulawa banda gimbiya Su'adah da ko kallon inda take bataiba. Ƙasan ranta wani takaicine da baƙin ciki da kishin yanda Raudha ta kara murjewa komai na halittar jikinta ya ƙara girma sai kace ƴar 25years. Ga tsadadden material ɗin dake jikinta wanda ta tabbatar za'a iya sayen abincin watanni na gidansu Raudhan da kuɗinsa. Ita saima taga kamar yarinyar tana wani jin kanta.
     Oho Raudha batasan tanai ba. Ita abinda ya dametama ya isheta. Komai yinsa take cike da dauriya. Abincinma tana matuƙar bukatarsa amma ta kasa ci saboda bakinta babu daɗi. Sai juya spoon take a ciki tana ɓata fuska. Ramadhan na lure da ita. Kuma hankalinsa na kanta. Burinsa su haɗa ido amma taƙi kallon ko inda yake. yana zaune ne tsakkiyar Bappi da Pa. Sai Anne a gefensu da Yafendo da Inna. Ita kuma tana kusa da Bilkisu da Zainab ne. Su Lubnah sai faman jan tsaki suke ƙasa-ƙasa suma kamar su halaka Raudha sukeji musamman ganin suturar data sanya kosu da suka tashi gidan kuɗin basu saka ba. Tsadajjen agogon hanunta da zabba da bangles kawai duniyane. Balle ita kanta data kara wani kyau na musamman da su sam basa lura da shi sai yau duk da kuwa suna tare da ita.
          Da gangan Ramadhan yay kamar ya sarƙe yaja gyaran muryar data saka kowa maida hankalinsa a kansa ana rige-rigen jera masa sannu. Bappi dake shafa masa baya kamar wani ƙaramin yaro ya kai masa kofin ruwa bakinsa yana masa sannu. Kaɗan yasha yana jinjina musu kai da satar kallon Ustazahr tasa. Sai dai bata yarda ta kallesa ba tun bayan ɗagowar datai kamar yanda kowa ya ɗago lokacin daya sarƙe. Ita sanun tatama a kan laɓɓa tai masa ta tsuke bakinta. Ganin dai ba samun yanda yakeso zaiyi ba sai ya haƙura. Takaici ya cika Aynah da duk hankalinta ke akansu. Hakama Muneera da idonsu akan yayan nasu da abinda yake yawan kallo. Jin hawaye na neman zuboma Aina'u itace ta fara mikewa wai ta ƙoahi. Babu wanda yace mata komai, hakan sai ya ƙara baƙanta ranta. Dan a ganin bai kamata aƙi bata kulawaba kodan mata ta biyu da take shirin shigowa ga ɗansu kuma ɗan uwanta.
        Raudha da dama ba abincin take ci na kirki ba itace ta ukun tashi a wajen. Ramadhan ya ɗan bi yanda take tafiya da kallo. Hannu ya kai ya dafe goshinsa a zuciyarsa yana ayyana (Yarinyar nan zata tonamin asiri fa). Bayan sun kammala kowa ya tashi a wajen yaso janta sashensa dan ya fahimci mugunta taima kanta bata shiga ruwan zafin daya haɗa mataba da asuba, bayajin kuma da safe ta sake kula da kanta. Takaicin kansa yaji dabai tsaya akanta ya taimaka mataba duk boranta. Sai dai duk yanda yaso ya keɓe da ita ɗin hakan bata yuwuba dan su Basma na zagaye da ita a falon Anne suna hirar school duk da ba wani saka musu baki take sosai ba. Sai dai ganin Inna da Yafendo da Anne na wajen ya sashi haƙura ya shige shi acewarsa zai ɗan huta...........✍
        

_Ayi haƙuri da jina shiru, banda lafiya ne_.


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 51_*


........Anne ta cigaba da maida hankalinta ga Raudha har zuciyarta ta fara hasashen abinda yake dai-dai. Sai dai ta danne komai batace ba har la'asar da aka tashi salla. Ramadhan ya fito sanye cikin ƙananan kayan daya canja suka sake fita massallaci da Bappi dan Pa na sashensa shima da iyalinsa. Har lokacin su Rumaisa na tare da Raudha harma sun kara samun yawan ƴan hirar su Sumayya. Magana kawai yay musu su tashi suje suyi salla ya wuce abinsa yana satar kallon Raudha da tun fitowarsa tai ƙasa da kai tana wasa da yatsun hanunta da jan lalle ya ƙawata dogayen faratanta.

       Koda ya dawo bai samesu a falon ba, acan bedroom ɗin kusa da na Anne yaji hayaniyarsu. bai saniba ko Raudha na tare da su ko tana ɗakin Anne. Haka ya wuce sashensa ya buɗe garden ɗinsa dake a gyare tsaf da korayen tsirrai masu kamshi da ni'imar ruwa ya shiga. Tunanin kiran wayarta yayi, sai dai akashe ma akace masa. yaja guntun tsaki dakai hannu ya shafi sumar kansa. Duk saima yaji zuwa gidan ma ya gundiresa, dan ba haka yaso ba kwata-kwata. Ya riga ya gama tsara kasancewarsu a sashensa daga shi sai matarsa su huta yanda ya kamata, amma sai gashi hakan ya gagara.
       Tun Raudha na daurewa dai har abin yaso fin karfinta. Dan da ƙyar ta iya dauriyar zagaya duka sassan gidan gaishe da matan Pa. Cike da takan tsantsan da faɗuwar gaba ta isa sashen Gimbiya Su'adah wannan karon, fatanta da addu'ar ta ALLAH yasa karta shaƙa mata tsakin kuka kamar wancan karon. Dan yau kanta shima wani azabar ciwo yake mata bayan zazzaɓi da ƙasanta da takejinsa kamar ana yankata ana watsa barkono a wajen.
      Badai a mata turaren tsakin kuka ba, amma ta fuskanci cin zarafi wajen su Muneera dake zaune tare da Gimbiya Su'adah a ɗakin. A kuma nan suke tabbatar mata da auren mijinta da Ayna'u. Sosai hankalin Raudha ya tashi, da jin wannan zance sai dai ta bala'in dakewa kamar babu komai a ranta. Ta saki murmushi mai kayatarwa da faɗin, “ALLAH ya sanya alkairi”.
        Dukansu kallon mamaki sukai mata dan basuyi zaton tanada bakin amsawaba musamman yanda tsoron gimbiya Su'adah baya ɓoyuwa a saman fuskarta.
       “Idanma baki faɗa har zuciya ba dai sai anyi, nanda sati uku Aunty Aynah nakan karagar mulkin first lady ba illiterate irinki ba...”
      Bumm kakeji Bilkisu da basu san da shigowartaba ta buge bakin Muneera dake maganar. “K dai baki da kunya sam Muneera. K har kina da bakin kiran wani illiterate? Koda kikai karatun ubanmi kika sani. Dan duk gidan nan kinfi kowa jakanta, badan Pa ba kin isa ki gama jami'a ne iyanzu kullum cikin daukar Cary over. Ina tausayin randa zaki ɗanɗani azabar gidan aure dan duk abinda kayi kaima sai an maka shi mtsoww”.
      Tana gama faɗa ta kama hanun Raudha suka fice a ɗakin batare data saurari ihun da Lubnah da Ayna'u ke mataba. Gimbiya Su'adah kam uffan batace ba har bilkisun ta fice da Raudha. Hakama surutan su Aynah ɗin baisa ta tanka ba.

Kafin su karasa sashen Anne Raudha ta tsaida Bilkisu tana bata haƙuri dan sai mita take da cewa yau saita sanarma su Bappi abinda su Muneera ke mata da ɗaurin ƙugun Maah. Roƙonta taitayi akan tabar zancen ita hakan baya damunta, kuma Maah mahaifiyace a gareta ai, ta isa ta mata komai. Amma Bilkisu ta dage akan saifa ta faɗa an ɗaukama abun mataki. Da ƙyar Raudha ta shawo kan Bilkisu ta haƙura suka karasa ciki Raudhan na tafiya da ƙyar. Dan har cije lips take da haƙori sannan bata iya haɗe ƙafafun.
        Ramadhan dake bayansu batare da sun sani ba ya bita da kallo cike da tausayinta da wani ƙarin ganin girmanta. Koba komai yana son mahaifiyarsa, sai dai shima baya ƙaunar wasu halayenta amma babu yanda zaiyi yana ƙoƙarin mata addu'a. Suko su Lubnah lokaci yayi dazai ci ubansu gwargwadon iko.

       Yafendo data kasa haƙuri yanayin na Raudha ce ta fargar da Anne cikin raɗa dan suna tare a falo suna magana akan meeting ɗin da zasu zauna yau iya su manya dangane da abinda gimbiya Su'adah ta kawo na auren Ayna'u da Ramadhan.
      “Anya kuwa basai yanzu megidana ya taɓa Ameenatu ba? yanayinta yayi kama da hakan”.
     Anne dake bin Raudha da kallo ƙasa-ƙasa itama tace, “Tun ɗazu na lura da hakan wlhy Yafendo, sai dai kuma idan na tuna abinda ya faru tun washe garin aurensu da ɓarin da tayi saina ture hakan a raina. Ƙila wata matsalace daban kuma”
         “To lallai al'amarin akwai ɗaure kai, kodai akwai abinda bamu fahimta dai-dai ba tun a wancan lokacin, kokuma bai bar halin nasa na idan ya fusata ya sauke fushinsa kan mace ba?. Ya kamata a binciketa kam a bata kulawa dan yanayinta gaba ɗaya ya fallasa taji ciwo a wajen ko makamancin hakan”.
      Numfashi kawai Anne ta sauke suka bar zancen suka kama wani. Suna wajen har aka kira magrib, a lokacin Raudha na can kwance zazzaɓi ya mata rijif. Da ƙyar ta iya tashi tai salla. Tana idarwa ta koma saman gado ta kwanta harda jan bargo hawaye na zubo mata. Tambayar duniya Bilkisu da su Rumaisa sun mata amsa ɗaya take basu (babu komai).
      Bayan sallar isha'i suna falo zaune Raudha nata dauriya Anne ta fito daga ɗaki tai kiranta, da ƙyar ta iya dauriyar ganin ta saita tafiyarta amma hakan ya gagara. Har suka shiga ciki Anne batace mata komai ba, sai da ta zauna tana gaisheta ta haɗe fuska dan bata son Raudha tai mata gardama. Murya a dake tace, “Ameenatu faɗamin mike damunki tunda kukazo gidan nan naga baki da walwala kuma idonki ya nuna kinyi kuka?”.
        Da sauri ta girgiza kai tana haɗiye hawayen dake neman zubo mata na zugin da take ji tace, “Ba komai ALLAH Anne. Kawai dai banajin daɗi ne”.
      Shiru Anne tai cike da nazarinta. Sai kuma ta miƙe batare da tace komaiba ta nufi toilet ɗinta. Ruwa mai zafi ta haɗa yanda tasan zai taimaki Raudhan. Sannan ta fito ta kama hanunta suka shiga ciki. Duk yanda Raudha ke wani zame-zame ga kunya kamar zata halakata Anne bata saurareta ba. Babban towel ta bata ta ɗaura ta lulluɓa da gyalenta sannan ta sakata shiga cikin ruwan. Wani kuka maiban tausayi Raudha ta sanya har numfashinta na fisga kamar zata shiɗe. Ga kunyar Anne ga azaba, jikinta har wani karkarwa yake. Anne ta gama fahimtar matsalar Raudha amma mamaki ya hanata gaskatawa.
      Haka ta sake canja mata wani ruwan har sau uku, sai ga Raudha taji wata irin nutsuwa na saukar mata. Anne ta fito tana bata umarnin tayi wanka da ruwan ɗumi kafin ta fito.

       Ramadhan da tun shigar Raudha ruwan farko ya nufo ɗakin Annen ya tsaya cak jin ƙarar da Raudha ta ɗan saki sanda ruwan ya ratsata, ya dafe kai da riƙe ƙugu a fili yake faɗin, “Ameenatu kin kasheni, miyasa kikaƙi yarda na tainaka miki gashi nan kin gama tonemin asiri wajen tsohuwarnan da darunta baya karewa”.
     Duk da Anne kakace renon uwa tai masa ba kaka ba. Hakan kuma baya hanashi yin wasa da ita wani lokacin. Dole ya fasa shiga ɗakin dan yasan rikicin Anne yanzu saita sauke masa na cikinta. Tun ɗazu itace a ransa. Duk abinda yakeyi hankalinsa na kanta, sai dai kuma haushin yanda ma ta wani sharesa na cinsa, dama sanda ya gansu da Bilkisu yaga kamar tafiyarta ba dai-dai ba, sai dai bai samu damar gama ƙare mata kallo ba suka shige. Falon ya koma dole wajen Bappi suka cigaba da hirarsu har Pa. Dama zai kira Anne ɗinne kamar yanda Bappi ya sakashi, koda ya dawo sai ya ce masa bai gantaba amma yaji ƙarar ruwa a bayi....

       Babu abinda take sai sakin ajiyar zuciya a jajjere, Anne dake kallonta cike da tausayi ta nuna mata bakin gado tana miƙa mata shayi data saka aka haɗo mata, sai gasashshen nama da akaima haɗi na musamman dan zuwa yanzu ta tabbatar da abinda ke faruwa. Kokwanton da ranta keta mata yasata kiran Dr Hauwa tunda itace ta duba Raudha a wancan likacin da sukai zargin cikine da ita da kuma zubewar cikin. Dr Hauwa da take ɗaukar Anne matsayin uwa ta faɗa mata gaskiyar lamari akan kowancan karon ciwon marane kawai irin na period, hakama lokacin da akace tayi ɓari maganin zubda ciki tasha batare data sani ba, amma Ramadhan yace suyi shiru dan zaiyi bincike akan wanda ya aikata zuba maganin da Raudha tasha., kuma bayan shi Raudha ta karayi har sau biyu tama dubata akan hakan, itace kuma ta sanarma Ramadhan mafitar da zai iya dakatar da Raudha daga azababben ciwon marar da take fama dashi a kowanne period.
     Godiya Anne tai mata ta yanke wayar, shiyyasa kafin ma Raudha ta fito Anne tasa aka kawo mata wannan abincin da tasan zai taimaka mata. “Maza kici kafin a samo miki magani”.
     Yunwar takeji, amma sam bata son cin abincin. Sai ma wani irin barci dake fisgar idanunta. Haka ta daure taci abinda zata iya tace ta ƙoshi. A kusan tare Ramadhan da Anne suka shigo ɗakin. Sanye yake cikin kananun kaya da tun ɗazun ya canja. Anne ce kawai ta amsa masa sallamar da yayi cikin tsuke fuska. Raudha kam dake fama da kunyarsa dama bata yarda ta motsa ba, ba kuma ta ɗago ba.
        Zama yay a ɗaya daga sofa's ɗin. Idanunsa akan matarsa da yakeji kamar yaje ya rungumeta, sai dai ya daure ya fuske dan tunda yaga yanayin Anne yasan fushi take da shi. Yanzun ma maimakon ta kirashi da wayarta Bappi tasa ya kirashi yana sashensa yana ƙullawa da kwancewa akan yanda zaizo ya tafi da Raudha can.
        A hankali ya janye idanun nasa a kanta yana jingina kansa jikin kujera ya lumshe su. Cikin ɗan furzar da numfashi yace, “Anne gani”.
     Shiru kamar bazata kulashi ba, tanata ƙoƙarin sakama Raudha safa mai kauri a ƙafa bayan ta mulke ƙafar da wani mai da ita tasan amfaninsa. Sai da ta gama tsaf ta kamo hannayen Raudha suma ta shafa mata man ta saka mata safar hannu sannan tai magana batare data dubesaba tana rufe man. “Magani nake buƙata da zata sha”.
      Idanunsa ya buɗe tare da ɗagowa. Sai ya saukesu akan Raudha da sam taƙi kallon ko inda yake har yanzu. Kafin cikin ƙanƙan da murya yace, “Waye baida lafiya?”.
        Wani shegen kallo Anne ta zubo masa cike da harara kai kace idonta ne zai faɗo. Daƙƙuwa ta watsa masa a zafafe tace, “Ramadhan ungo wannan.”
       Tattausan murmushi ya saki mai sanyi yana lumshe idanu ya sake buɗewa a lokaci guda. Fuska ya ɓata sosai cike da marairaicewa kamar ba shugaban ƙasa Ramadhan ba. “Waini Anne kamarma fa kinajin haushi na..”
    Harara ta sake dalla masa tana janyo burner ɗin turare kamar zata jeho masa. “Oh saima yanzu ka fahimci haushin naka nakeji ashe....” ta ƙare maganar dayin kamar zata jeho masa har abin yaso bama Raudha dake kallonsu ta wutsiyar ido dariya. Amma saita gimtse yana sake kauda kanta dake mata tsananin ciwo gefe...
        Hannu ya ɗaga mata alamar surrender. “Kinga yi haƙuri ajiye burner ɗin. Ina arziƙi ranar Monday a ganni da fasashen kai azata matata ce ta fasamin”.
     “Oh to bara na fasa ɗin ai gara sumayi zaton hakane koba komai ta rage zafin muguntarka”.
      Tasowa yay daga kujerar murmushinsa na sake faɗaɗa. Ya zauna kusa da Raudha a gefen gadon yana mai ruƙo hanun Anne ya amshe burner ɗin. “Yi haƙuri tagaba goshin Bappi yanzu mi akeso nayi?”. Yay maganar da juyawa yana ɗaura hanunsa a goshin Raudha da kunya ta dabaibaye kamar ta nutse saboda yanda ya zauna gab da ita sosai duk da baya taɓa jikinta dai.
        Mikewa Anne tai tana mita ta fice. Ka tambayeta abinda ke damunta kasa a nemo mata magani kafin na dawo kuma ku tattara ku barmin ɗaki barci zanzo nayi”.
     Gwalo ya ma bayan Anne, kafin ya maido dubansa ga Raudha. Jawota kawai yay jikinsa ya rungumeta baki ɗaya. Rawa jikinta ya farayi kaɗan-ƙaɗan har yana iya jin gudun da zuciyarta keyi. Ga zafin da jikinta ya ɗauka sosai na ratsa shi.
    “I'm sorry Ustazah”.
  Ya faɗa a hankali cike da tausayinta. Ita dai babu bakin magana, sai ma lafewa da tai duk da tsoron dake tattare da ita nashi. Kusan mintuna uku suna a haka kafin ya ɗagota daga jikinsa, hannu yasa ya share mata hawayen dake sakko mata a kumatu. “Yi haƙuri kukan ya isa haka Sweetheart, amma miyasa ɗazun baki shiga ruwan dana haɗa miki ba”.
       A hankali yake maganar cike da nutsuwa. Da ƙyar Raudha ta iya buɗe baki tace, “Akwai zafi ne”.
       “Ai zafin shine zai taimaka miki Ameenatu, gashi ƙinyin haka ya saka miki zazzaɓi har kin tone mana asiri wajen Anne dama duk mai hankali da zai lura da tafiyarki a gidan nan ɗazun”.
      A ɗan tsoroce ta ɗago manyan idanunta a karon farko ta kallesa. “Ya Ramadhan kowa ya sani kenan?”. Tai maganar cikin rawar murya wasu hawayen na rige-rigen sakkowa. Dariya da tausayi ta bashi lokaci guda. Maimakon ya bata amsa sai ya sake rungumeta. Kusan minti biyu ya sake ɗagota. “Kinga tashi muje kisha magani dan tun ɗazu nasa aka kawo miki. Ga shi Anne dama ta koremu duk da nasan itama ba iya kwana zatai anan ba sai a bayan Bappi. Shiyyasa kema takeso kije jikin mijinki ki kwanta ki more..”
     Hannunsa ta turo dan yanda yay maganar da abinda hanunsa ke mata sai kunya ta sake lulluɓeta. “Ni ALLAH ka bari”.
       “Uhhm iyayi, nasan dai kinana daɗi ya rufeki bazaki kwana batare da mijinki ba.”
     “Innalillahi... ALLAH Ya Ramadhan ka iya sheri”.
             “Su Yaya anji jiki, wane Yayane zaiyi bidirin da nai a daren jiy.....”
   Hannu tasa ta toshe masa baki da sauri kafinma ya ƙarasa. Da ƙyar ya iya danne dariyarsa yana janye hanunta. “To shikeman nayi shiru”.
       Yasan ya kora su Basma tun ɗazu, Anne kuma tana sashen Bappi, sai kawai ya duƙa wai Raudha ta hau ya goyata. Ƙin yarda tayi itakam. Ganin zata cigaba da ɓata lokacinsa ya ɗauketa cak suka fice tanata mutsu-mutsu da roƙon ya sauketa bai saurareta ba. Dole tai saurin saƙalo hannayenta a wuyansa jin kamar zata faɗi. Ta lumshe idanunta da hawaye ke zaryar fitowa kunya kamar zata halakata, fatanta suje lafiya inda zasu batare da wani ya gansu ba..........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 52_*


..........Sai dai addu'ar tata bataci ba. Dan suna shigowa falon daya raba sashensa da nasu Anne sukai kiciɓus. Sai dai Ramadhan ya ɗauke kai kamar baiga Anne ba dan shima dai kunyar yaji. Ɗan murmushi Anne tai tana binsu da kallo kafin ta sauke ajiyar zuciya da numfashi tana mai binsu da addu'oin zaman lafiya da samun zuri'a masu albarka.
       Har ya isa ƙayataccen bedroom ɗinsa da komai na ciki yake kalar royal blue and golden bata yarda ta buɗe idanunta ba. Ya direta a saman lallausan gadonsa da yaji shimfiɗu masu inganci, anan ma da runfa ta net white color mai kwalliyar blue kaɗan-kaɗan.
      “ALLAH nauyine dake Ustazah, wannan ai sai kisa na rame”. Ya faɗa cikin kunenta tare da sumbatar kuncinta na haggu. Ita dai bata motsa ba balle ta buɗe ido, sai da ta ɓata fuska da tura baki yace tana da nauyi. Murmushi yayi da ɗallin lips ɗin a hankali.
       “ALLAH da zafi Ya Ramadhan”.
“Ai dama dan kiji zafin nayi. Idan kuma wannan yayan bai fita bakinki ba ALLAH sai nazo na darje ciwon na banbanta miki tazarar dake tsakanin Yaya da ni”.
      “Toni mizance dan ALLAH?”.
“Oho ya rage naki tashi kisha magani kisa kayan barci kar wannan towel ɗin yasa mura kamaki”.

        Da ƙyar ya iya sakata tashin tasha magungunan da tun bayan sallar magrib aka kawo masa su. Dan tun da yaga yanda take tafiya ya yanke shawarar nemansu. Kayan barci ya ajiye mata ya shige toilet, hakan ya bata damar sakawa da sauri-sauri tai amfani da designers turarurrukansa masu ɗan karen ƙamshi ta haye gadon da sauri tai kwanciyar kai da kafafu tare da yin addu'a kafinma ya fito taja bargo har saman kanta. Dan tasan kaɗan daga aikinsa ya fito da towel babu kunya a gabanta.
          Ilai kuwa hakan ya fito kansa tsaye, ya ƙaraso har gaban gadon saboda wayarsa dake ring. Kasancewar ata gefen can ɓangaren Raudha ta kwanta shi kuma sai ya zauna a gefen gadon ta ɓangaren data bari domin shi. Yana goge ruwan fuskarsa da jikinsa yana wayar da A.J dake kula masa da business ɗinsa a can America yanzun. Cikin harshen turanci suke maganar cike da ƙwarewa, dan haka Raudha ta shagala a saurarensa dan yanda harshensa ya karye bama zakace yasan wani yaren Africa ba. Wayar taɗan jashi lokaci dan harya miƙe ya koma gaban mirror. Yana gyara jikinsa yana cigaba da wayar harya shirya cikin tausasan kayan barci, kafin taji ya sake zama a gefen nata. Kaɗan ta ɗaga bargon ta leƙashi, sai tagansa da kofin tea daketa turiri sai kuma lap-top da yake ƙoƙarin kunnawa har sannan wayar na maƙale a kunensa. Shagala tai a kallonsa ƙasan zuciyarta na godema ALLAH daya azurtata da samunsa matsayin miji. Banda ƙaddara ita tasan ko a ƴar aiki bazata ishi Ramadhan kallo ba. Sai dai UBANGIJI shi mai rahamane mai kuma jinƙai. Sannan mai ƙaddara abinda yaso ga waɗanda yaso koda akwai tazarar nisa ta rayuwa ko yare ko addini ko yanki a tsakanin bayinsa.
       Yaja lokaci yana aikin sai dai ya ajiye wayar tuni, har barci barawo yay tashiri kan Raudha saboda maganin data sha.

            Ramadhan da idanunsa ke faman raɗaɗin barci, ya kai hannu bisa goshinsa ya murza da furzar da iska mai nauyi. Ya gaji matuƙa, gashi abinda yakeyin mai muhimmanci ne. Dan kayan da zasu fitarne a sabuwar shekara A.J ɗin keson ya duba abinda baiyiba su ajiyesa gefe wanda yayi su fara packaging ɗinsa yanda ya dace da mikashi ga yan talla kafin a fitar.
       A hankali ya rufe lap-top ɗin bayan ya kashe yana ɗan danna gefen wuyansa alamar riƙewa. kofin daya sha lipton da lap-top ɗin ya sauke kasa. kafin ya koma toilet ya ɗauro alwalar barci sanna ya hawo gadon da danna wani abu net ɗin ta buɗe gaba ɗaya ta lulluɓesu. Sai ɗan hasken fitilar cikin gadon daya kunna ya kashe ta ɗakin gaba ɗaya. Bargon da Raudha take ƙudundune a ciki ya ɗage, sai yaga ashe kai da ƙafa take kwance. Kansa ya ɗan girgiza kawai, yasan tadata yanzu wani aikinne kuma, sai kawai ya kwashi piilos ɗin shima ya maida inda tasa kanta dan bazai iya yarda da kwanciyar kai da ƙafa ba shida matarsa. Gara ace ɗaki suka raba ko gadon. Dan lokaci Amnah ko faɗa sukai da ita bai yarda da raba ɗaki ba. Dole ta kwana tare da shi ko zata kwana masa kukan baƙin cikin daya tusa mata. Inma itace tai masa laifin duk zafin da yakeji a ransa ya gwammaci su kwana waje guda ɗin, shi kuma yasan a inda zai fanshe haushinsa ai (🤣😂mugu ɗan masa🙊).

        Sai da ya janye bargo gaba ɗaya ya karemata kallon yanda kayan barcin sukai mata ƙyau kafin ya saki wani ɗan guntun murmushi da iya laɓɓa ya tsaya masa. jikin nata ya taɓa yaji zazzaɓin ya sauka, sai kaɗan da bai ida hucewa ba dai. Filon da take kai shima ya ɗaura kansa suna fuskantar juna. Ya sumbaci goshinta da laɓɓanta sannan yay musu addu'a yaja bargo tare da rungumeta yana sauke ajiyar zuciya.

        Da asuba ya rigata farkawa, sai dai yana motsawa itama ta farka. Gaba ɗayanta a jikinsa take lafe da alama hakan ya mata matuƙar daɗi, sai dai suna haɗa ido tai saurin ƙoƙarin janye jikin nata kunya kamar zata nutse. Riƙota yay ya hanata damar juyawar. Cikin ɗan daburcewa take ƙoƙarin faɗin, “Kayi haƙuri ni ALLAH ban san ma....”
      Ruf ya rufe mata baki da nashi batare daya bari ta ƙarasa faɗa ba (😜ƙazanta ko brush babu🤕🙄). Duk yanda taso kwatar kanta bata samu damar hakanba. Dole ta nutsu ta barshi ya gama yamutsata san ransa tsoro kamar ya kasheta. Dan a tunaninta za'a tafi next level ne😖. Da ƙyar ya iya yakar ƙansa ya barta jin an sake kiran salla na biyu, ya sauka a gadon da ɗan zafin nama ya faɗa toilet. Ruwa mai ɗumi ya sakarma kansa yana mai sauke nannauyan numfashi da rumtse idanu. Sunan ALLAH ya dinga ambata dan yasan lallai akwai matsalolima ba matsalaba. Gashi da alama Raudha tamkar Amnah take itama zatai shegen raki duk da ita daba sickler ɗin ba. Dole ya haɗa harda wankan lada. Koda ya fito yay mata maganar ta tashi bata motsaba dan kunya harya zura jallabiya yasa turare ya fice. Sai dai ya gargaɗeta karya dawo ya sameta a kwance bata tashi tayi salla ba, ta kuma sake shiga ruwan zafi inba hakaba ya dawo da kansa zai sake gasata.
          Raudha da gaba ɗaya a firgice take da Ramadhan ta miƙe da sauri bayan ta leƙo ta bargo ta tabbatar ya fita. Toilet ɗin ta afka itama. Ta watsama jikinta ruwa da ƙara gasa ko'ina duk da dai Alhmdllhi garas ta tashi yau sai dai rashin jin karfi na sabo.
            Koda ya dawo a saman sallaya ya sameta tana karatun alkur'ani. Hakan ya masa daɗi sosai, sai shima kawai ya zauna suka cigaba dayi tare. Duk da mamaki ya matuƙar ɗaure kan Raudha jin yanda yake karatu a nutse cikin daddaɗar muryarsa mai faɗi da amo da gaba ɗaya ta danne ƙarfin tata siririya mai zaƙi. Sunyi karatun da yawa sannan sukai addu'a. Kanta a ƙasa tace, “Ina kwana”.
    Bai amsaba, sai dai ya kafeta da idanu, ɗan dagowa tai kaɗan sai suka haɗa ido, zata maida ya riƙo habarta da hanun damarsa. “Karki kuskura ki rufe idanun nan”. Ya faɗa da sauri ganin tana niyyar lumshesu kuwa. Yanda taji babu wasa a furucinsa ya sata dakatawa. Sai dai taƙi yarda su haɗa ido....
      “Ni bana son irin wannan gaisuwar ga matata shiyyasa ban taɓa amsa miki ba”.
     Duk yanda taso jurewa kasawa tai, sai da ta ɗago ido ta kallesa sai karaf a cikin nashi da launinsu ya canja. Ƙwayoyin cikinsu bakaƙe masu ƙyalli ya juya mata cike da tabbatarwa. Ta risinar da nata tsigar jikinta na tashi dan ta rasa abin cewa kuma. Zuciyarta na tunanin (Banda gulma irin tashi wace gaisuwace kuma bayan wannan da aka banbanta tsakanin mata da miji da sauran mutane? Ita dai tunda ta taso a gidansu irin wannan taga anama Abbansu).
      A bazata kawai taji saukar lips ɗinsa saman goshinta. Kafin ta dire numfashi ya saukesu kan lips nata ya bata light k.. Harya janye kuma ya sake maidawa ya cafkesu da ƙyau yana matse hanunta dake cikin nashi tsam.
       A gwame ta dinga fidda numfashi kamar yanda nashi ke fita a harɗe, har saida yayi yanda yake so sannan ya barta dan kansa. Cikin rufewar idanu ya lalubi kunenta.
     “Wannan itace nake buƙata a kowacce safiya idan mun tashi, da kuma idan na dawo aiki shine sannu da zuwana”.
      (Tabb ashe kuwa akwai tsallen baɗake) cewar Raudha a zuciya. A fili kam yanda yay maganar babu wasa a ciki ya sakata jinjina masa kanta kawai batare da tace komai ba. Mikewa yay shima ya mikar da ita batare da ya sake cewa komaiba. Dolenta tabi yanda yakeso suka koma gado bayan ya cire mata hijjab ɗin ya barta da abayarta dan shima yana son kauda kansa ga abinda zuciyarsa ke bijiro masa.
      Fargaba ta hanata barci har sai da taji yana sauke numfashi a hankali alamar shi ya fara sannan tai nata itama tunda taga ba abinda take tsoron bane zai faru..........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 53_*


..........*_JIHAR ƊILLO (HUTAWA)_*

           A Hutawa kam kowa yaga M. Ɗan-azumi yanzu sai yay matuƙar mamaki. Dan kamar yanda ya ƙudiri ƙara sabon aure ya auro dalleliyar budurwa sabuwa dal a kwali. Kai daka ganta kasan ƴan kuɗin ta biyo. Baƙaramin tashin hankali Larai ta shiga ba, dan saika ɗauka ma wani sabon haukane ya hau kanta. Data nema birkice masa sai ya aikata gida taje ta huta. Roƙo iya roƙo ita da danginta amma ya birkice musu ƙememe dama fitinarta ta isheshi, ga baƙin cikin rabasa da masoyiyarsa Asabe da har yanzu ko ɗigon sonta baibar zuciyarsa ba. Ganin haka Baba Nafi ta ƙara kama kanta da mutuncinta a gidan, dan tun dawowar Inna da ƙaninsa da matarsa dama gidan ya sake zama sai a hankali. Gadai jin daɗi yanzu a cikinsa amma kowa zaman haƙuri yake da ɗan uwansa saboda fitinar sirikarsu dabance a rayuwa, shi kuma M. Dauda na biye mata dan duk haukarsa yana ƙaunar Innarsa.
          Tun auren Raudha alaƙar zuminci mai ƙarfi ke tsakaninsa da hakimi, hakama jama'ar gari sosai suke respecting nashi kowa burinsa ya zama abokin mu'amularsa (kaiko sirikin shugaban ƙasa fa ba wasa ba😝). Da wannan damar M. Dauda kan samu na hura hanci sai ya zaɓi wanda yaso ayi zumincin, shi da M. Gambo ne dai ana nan tif da taya, sai dai baisan M. Gambo nata masa zagon ƙasan ƙoƙarin kiran Asabe a wayaba kullum, wani lokacin harda mata ɗan text na soyayya dan ƴar sakandire ɗin nan dai shi da M. Dauda sunyita. Ita Asabe har zuwa yanzu batasan wanene ba. Dan tun tana sharesa da masa masifa idan ya kirata harta ɗan fara kulashi.
       Hakimi daya fahimci rawar kan M. Dauda bata risinaba saima giyar kuɗi dake neman ɗorasa a wani layin bayan wanda yake kai yasa shi ƙara jansa a jiki yana masa nasiha, ya kuma bashi sarautar data tilastashi kullum zuwa gidan Hakimi ayi fadanci dashi. Koda yake mugun ɗagawa da faɗi yake da sarautar, inma ka kira sunansa baka haɗa da sauratarba to kuwa kaji barbaɗin jaraba daga sama har ƙar zai zugeka yana hura hanci da kiran shi ya wuce raini ai. Surikin shugaban mai ƙasar yake baki ɗaya, Baba sama baba ƙasa yake kiransa kuma saiya risina yake gaisheshi koda a wayane balle wani ƙaton ƙawai da talauci yayma katutu. (😂🤣ALLAH ya bar mana Man Dauda).
      Ya sayi ƴar kwariɓar motarsa ana yanga da ita kwana biyu ta birkice, cike da masifa ya maidawa bakaniken daya saida masa yace wlhy koya dire masa kuɗinsa kokuma yasa azo daga Bingo a cukuykuyesa yasan dai uban matar shugaban ƙasa yake. Da farko makanike ya ɗau abin wasa, dan mahaukacima suka maida M. Dauda shi da yaransa. Saiko gashi ko mintuna ashirin baiyi da barin wajenba motar ƴan sanda har uku sunzo sun yayesu gaba ɗaya har yaran nashi. Dan kuwa M. Dauda yana zuwa police station d.p.o da ayanzu ya gama haddacesa shi da yaransa koda ɗunbin alkairin da suka samu a ranar auren ƴarsa da shugaban ƙasa sukai masa tarbar mutunci. Harda matsar kwallan munahinci wajen faɗa musu abinda akai masa a gareji. Rai ɓace d.p.o ya bama yaransa umarnin zuwa a kwasosu yana bama M. Dauda haƙuri.
       “Baba ai kun wuce ko kallon banza yanzu a ƙasarnan, kunefa iyayen masu ƙasar. Gamu nan tunda ɗanku ya hau mulki albashinmu ma ninkashi akai tsabar adalci na wannan shugaba. Ai mu babu abinda muke sai fatan alkairi a garesa, mun kuma tabbatar lallai matasa masu jini a farce ƙasar NAYA ke buƙata irinsa.. ALLAH ya ƙara masa zaman lafiya da matarsa nan da watanni asake zuwa taron suna NAYA muci musha muyi warkan. Dan muna alfahari first lady tamuce wlhy”.
     Daɗi kamar zai kar m. Dauda, ya dinga washe haƙwara yana sake baje babbar rigarsa dan ɗinkunan alfarma da Alhaji Hameed Taura yay masa na biki har kala goma sune suka zama na faɗi yanzu a gari. Lokacin da aka shigo dasu Gali a ɗage M. Dauda yake kallonsu da watsa hannaye gaba. “A rufeminsu har sai na manta da wanzuwarsu sannan a tunamin”.
     Cikin roƙo da magiya kanikawan nan ke roƙon Alhaji Dauda (dan tunifa dama gargaɗi yake abar kiransa M. Dauda😂😜). Amma ko kallonsu baiyiba. Cikin takun ƙasaita ya buga babbar rigarsa aka fice dan d.p.o ya bada motarsa a maidashi gida.

       Kwanakin kanikawan nan huɗu a ofishin ƴan sanda sannan ya bari aka sakesu da sharaɗin maido masa kuɗaɗensa nanda sati guda. Hakan kuwa akai sai gasu da kuɗaɗensa cif sun kawo, ya dinga antaya musu harara yana sake baje riga da hura hanci. Bayan ya koma gida ne ya nema kuɗin ya rasa da kwana biyu shine ya yanke jiki ya faɗi har saida aka kaisa asibiti. Wannan ne dalilin zuwa su Fatisa dubashi har suka sanarma Raudha, to ayanzu haka dai ya haɗa duk yaran gidan nasa da matan ya tabbatar musu idan kuɗinsa basu dawoba nera dubu ɗari bakwai wlhy suma cell zaisa a zubasu har sai sun magantu.

(🤣😂To bara muga ta inda kuɗin Alhaji Malam Dauda surikin shugaban ƙasar NAYA zasu fito).


*_BINGO CITY (TAURA HOUSE_*

            Barci sukasha sosai kamar yanda Ramadhan yaso. Ga Anne daga falo na musu gadi dan koda su Basma suka taho wai anan zasuyi breakfast korasu tai duk da tasan da wahala hayaniyarsu takai ga sashen Ramadhan ɗin. Dama tunda ya shiga ya gaisheta bayan sallar asuba yace kar ai musu breakfast da wuri. Dan haka ba'a ɗora ɗinba kuwa sai kusan sha ɗaya na safe. Zuwa sha biyu an kammala komai an kawo falon part ɗinsa an shirya bayan an gyarashi yanata ƙamshi duk da bawani datti yayi ba.
         A yanzu ɗinma kusan tare suka farka sai dai motsintane ya tadashi. Tai ƙoƙarin janye jikinta ya hana hakan. Cikin yanayin kasalar barci ya mika hannu ga side drawer ya ɗakko agogonsa yaɗan kalla time cikin lumshe idanu da buɗewa. Har sha biyu ta gota. Agogon ya ajiye da kai lips nashi a goshin Raudha da taƙi buɗe ido ya sumbata. Kafin ya saketa ya sauka baki ɗaya batare da yayi magana ba.
     Bata iya motsawaba sai da taji ya rufo toilet ɗin. Ta miƙe da ƙyar itama dan barcine da bata sabayi ba ace tun sallar asuba har kusan 1. Gadon ta shiga gyarawa a ɗan gurguje, ta maida net ɗin yanda ta gansa, sosai yake birgeta dan ya sake kawata gadon da ɗakinma baki ɗaya. Har falo ta fito neman kayan shara, cikin sa'a ta samu a cikin kitchen bayan ta karema falon da kitchen ɗin kallo. komai akwai na buƙatar ɗiya mace har tana mamakin sai kace mai mata.
     Shara ta gama tana tsaka da mopping ya fito. Bata yarda ta kallesa ba, sai shine dake binta da kallo ya nufi mirror yana faɗin, “Waya saki wannan aikin?”.
      Amsa ta bashi batare data yarda ta kalla inda yakenba dai.
     “Ba kowa”.
  Komai bai sake cewaba harta kammala ta fita da kayan, taɗan jima kafin ta dawo da fatan ALLAH yasa ya saka kaya. Sai dai addu'ar tata bataci ba dan har lokacin ɗaure yake da towel tsaye a gaban Wadrobe da alama kaya yake nema. Kaita kauda cikin sauri ta faɗa toilet.
     Baki yaɗan taɓe dan duk yana kallonta ta gefen ido. Ta jima bata fitoba, har sai da ta leƙo taga baya ɗakin. Da sauri-saurin tai shirinta cikin atanfa datai mata ƙyau matuƙa, ga ɗinkin ya fidda jikinta tsaf kamar ka saceta ka gudu. Ɗauri tai mai sauƙi amma ya mata ƙyar ta saka ƴan kunne kawai harda yafa mayafi sannan ta fito da nufin zuwa gaida mutanen gidan duk da kunya da nauyin ƙin zuwa akan lokaci na cinta. A tunaninta Ramadhan ma nacan, sai dai tana fitowa falo taci karo da gogan nata zaune cikin kujera ƙafa ɗaya kan ɗaya yana kallon labarai a television da alama sallar azhar yaje yayo kawai ya dawo.
     Tsamm tayi a ƙofar ɗaki kamar bazata karaso ba. Sai kuma cikin dauriya ta cigaba da takowa har inda yake. Kanta a ƙasa tana wasa da zobon hanunta tace, “Ya Ramadhan zanje naje na gaida su Anne”.
    Maimakon ya amsa mata duk da idonsa ba'a kanta yakeba sai taji ya riƙota ya zaunar saman cinyarsa. Mutsu-mutsu zata fara ya dakatar da ita ta hanyar yaye veil ɗinta gaba ɗaya. “Banda ƙauyanci miye na zuwa gaban miji da veil?”.
        Duk da maganar ta bata haushi sai ta dake. A sanyaye tace, “Wajensu Anne fa zanje”.
      Wasa yake da jelan kitsonta idonsa a tv, “Sunce sun yafe yau ko ƙofar corridor ɗin can bazakije ba nayi gaisuwan da taki ai tun ɗazun”.
      “Kai Ya Ramadhan wlhy bai kamataba ace banje na gaishesu ba. Gashi dama lokaci ya gama shigewa ai da kunya”.
        Maimakon amsa mata maganar ko barinta tafiya sai ya ɗagata daga jikinsa shima ya tashi, dining ya nufa da ita dan shi ta yunwar cikinsa ma yakeyi. Dolo ta haɗiye komai dan yaci serious kamar bashi ba. Tsorone yaɗan fara kamata na gudun karfa mutumin nan ya juya mata baya bayan ya rabata da mutuncinta. Dan taga tun jiya ya koma sha mata ƙamshi irin yanda yakeyi mata a baya. Da wannan tunanin tai saving nashi komai, zata zuba nata ya hanata yay mata nuni data zauna kawai. Dole tabi umarninsa zuciyarta fal tsoron abinda ba haka bane. Shi Ramadhan yana ɗan ɗaurewa ne kawai dan gujema abinda zuciyarsa ke kwaɗaita masa game da ita. Dan tausayinta yakeji matuka. Amnah mai shekaru da suke gab da nashi duk da tanada lalura bata iya jure ɗaukarsa akoda yaushe balle ita. Dan sauda dama idan yaje gareta sai tayi kuka balle Raudha da yakema kallon jaririya. Shi kansa yasan yayi juriyaa shekarun da babu Amnah, amma ya tabbatar ɓacin rai da tashin hankaline suka girmama juriyar tasa, yanzu ko daya ɗan ɗana bayajin zai ɗaga ƙafa duk da ƙoƙarin hakan da yakeyi.
      Tare sukaci abincin Raudha nata sinne-sinne. Shi dai bai kulataba. Daga ƙarshema ya amshe cokalin ya koma bata da kansa. Ina ƙasa ta shige amma babu damar gardama dan ya haɗe girar sama data ƙasa........✍

   

*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 54_*


..........Koda suka kammala falon suka sake dawowa, ya kuma ɗaure fuska yanda bazata roƙesa fitar ba. Dole ta kama kanta dan kuwa koda ya zaunar da itama karshen 3seater sai ya kwanta shi ya ɗaura kansa a cinyarta. Ya kuma kamo hannayenta duk biyu ya ɗora a sumarsa sannan ya canja musu tasha.
     Raudha babu bakin magana, tun tana cuna baki gaba har laushin sumar da takema kallon zatai ƙarfi saboda yanayinta na irin tamu ada ya fisgeta ta tura yatsunta a ciki a hankanli. Lumshe idanu Ramadhan yayi da sauke numfashi a hankali dan hakan abune da yake matuƙar so a rayuwarsa shima.
      A hankali ta cigaba da wasa da yataunta cikin sumar cike da shauƙi harta shagala ta manta dawa take tare. Haka ta cigaba da wasa da sumar kansa cikin shagala tana kallon film, yayinda shi nashi idon ke'a lumshe ya lula duniyar tunani.

      ★Kowa bai damu da rashin ganinsu a gidan ba har yamma, sai gimbiya Su'adah ce data cika tai fam da takaici, dan har Muneera ta aiko tai mata cid ɗinsu ta koma ta sanar mata ai duk yau ma bata tunanin Raudha taga rana. Gara Ramadhan kan fita yayo salla. Dama kuma shi yaje ya gaisheta da safe ma.. Har lunch ta shirya masa da kanta da maganin da Adda Asmah ta kawo waina fidda son Raudha a ransane ya tsaneta. Har sai ya mata korar kare a government house. Sai dai abinda bata sani ba na tsananin jan ra'ayinsa da mallakar zuciyarsane akan Ayna'u, malamin daya bata ya tabbatar mata Ramadhan yaci maganin nan sai ya manta har gimbiya Su'adah ɗin ma da kaf Taura family ya koma ƙarƙashin ikon ƴarta Ayna'u, hatta da mulkin ƙasar NAYA Aynah ce zata koma mai tsarawa da zartar da yanda za'ayi.
      Sai dai kuma Ramadhan ya kwafsa mata baije sashen da rana ba. Washe garima babu wanda ya gansu, sai randa suka cika kwana uku yaje sashen nata shi da Raudha da rana. Hakan baisa ta gaza tanadin na dare ba a cikin gasashshiyar kazar da taji kayan haɗi na ban mamaki aka aika masa har sashen Anne da kunun madara da yasha zuma a ciki a wannan rana. Ita kanta Raudha basu ƙyaleta ba. A baki Bilkisu sukaji abinda tafi so, amma kasancewar guri ya ƙure aka haɗa mata zoɓo mai sauƙi aka barbaɗe da magani sanin Ramadhan baya shan zoɓo shi kuma.
     Tunda Lubnah ta nufi sashen Anne da abinci sai kuma zuciyar gimbiya Su'adah ta shiga ƙunci, rasa mike mata daɗi tayi tanata faman kaikawo a bedroom ɗinta. Gaba ɗaya zuciyarta na nuna mata ƙiyayya da abinda ta aikata akan ɗan data haifa saboda tsanar matarsa. Sai dai kiyayyar da takeji akan Raudha nata ƙoƙarin danne gaskiyar dake son bayyana kanta ga kuskuren da idonta ya rufe ta kasa fahimta...

       Sam Anne bata kawo komai a ranta ba ta haɗa kayan wajen gimbiya Su'adah a cikin dinner ɗin su Ramadhan. Taya ma zatai tunanin za'ai amfani da uwa wajen cutar da ɗanta? Ita bama ta taɓa kawoma ranta wani cikin surukan nata na bin malamai koda akan Pa ba. Tama shedesu akan hakan ɗari bisa ɗari dan bata taɓa ganiba gaskiya. Ita kuma mutumce da bata yanke hukunci akan abinda bata ganiba sam.
          Raudha yarinyace mai tsarta, haka kawai taji gabanta na faɗuwa lokacin da sukai zaman cin abincin. ALLAH ta shiga ambato a zuciyarta, yayinda Ramadhan gashin kaza ya ruɗesa ya ɗan ɗiba da cokali mai yatsu ya kai bakinsa yana ambaton “uhhm”. Kallonsa tai kawai batare data iya cewa komai ba. Sai da zai kai lauma ta biyu ne ALLAH ya bashi ikon ambaton Bismillah. Ƙaramar ajiyar zuciya ta sauke, koda yace suci kazan catai ta ƙoshi, dan itakam idan tace zatai irin cin namansa ai matsala za'a samu. Bai wani ci da yawa ba ya tashi akan zaije wajen meeting idan an tashi yazo yaci. Amma ta tabbatar taci abinci inba hakaba ya dawo ɗura zai mata da kansa.

Gimbiya Su'adah ce ƙarshen shigowa. Ramadhan ya gaidata cike da kunyar tun safe bai koma sashenta ba. Koda yake Anne ma da suke tare sai ya fito salla take ganinsa. Ya ɗanyi mamakin yanda ta amsa masa a sake, ta kuma gaida su Anne itama. Kowa zaune yake a kujera har su Yafendo, shine kaɗai zaune ƙasan lallausan carpet ɗin falon domin girmamawa ga iyayensa.
     Ba Ramadhan ɗin kaɗai ba, hatta su Pa sakewar gimbiya Su'adah ya basu mamaki, duk da suna danganta hakan da abinda ta kawo take ganin zataci nasara. Su dai babu ruwansu, idan Ramadhan ya amince ya karɓa zasu tayasa so, idan baya so kam bazasu masa dole ba tunda yay musu biyayya akan Raudha kar su cika shiga hakkinsa.
  Bayan an buɗe taro da addu'a Bappi ya bama Gimbiya su'adah damar faɗin abinda tazo musu da shi kafin yau. Tunda ta fara bayani Ramadhan ya ɗago a rikice yana duban mahaifiyar tasa. Fara'ar fuskarsa kuwa tuni ta ɓace sai dai komai baice ba harta kammala. Bappi ya jinjina kansa da maida hankalinsa ga Ramadhan da ya maida kansa ƙasa.
      “Ramadhan kaji abinda mahaifiyarka tace. Tana buƙatar ka auri ɗiyar ƴar uwarta domin likita ya sanar matarka bazata sake haihuwa ba saboda ciki data zubar a kwanaki”.
       Ramadhan daketa jera kalmomin innalillahi a zuciya ya nisa da ƙyar. Abinda Maah bata sani ba ya daɗe da kammala bincike akan yanda Raudha tasha magani, sai dai takamaimai wanda ya bama su Muneera maganin suka zuba mata dama yake nema ruwa a jallo. Sai gashi a cikin sauƙi ta tabbatar masa da itace, domin inba itace ɗinba taya tasan mahaifar Raudha zata lalace harta gagara haihuwa....?
      “Ramadhan!”.
Inna dake gefensa ta kira sunansa. Numfashi ya furzar da ɗago idanunsa da suka kaɗa ya kalleta. Sai kuma ya maida kansa kasa yana ƙoƙarin danne ɓacin ransa.
      “Kiyi haƙuri Maah bazan bijirema umarninki dan baki isaba. Sai dai zanyi hakane tare da tabbatar miki wannan BAƘAR INUWAr da kike hangemin gwara ranar da kike gudanmin da ita. Ban musa miki wasu a dangin Ameenatu nada tabo na ƙaddarar rayuwa ba, amma ina son ki sani wlhy Ameenatu yarinyace kamila mai addini. Sannan ta kawomin mu..tuncin...ta har gida. Idan zan faɗa miki wacece wadda kikema kallon mutuniyar kirkin a yanzu zakisha mamakin hakan. Maah laifin wani baya shafar wani ko'a wajen UBANGIJI. Sannan ALLAH na fidda rayayye a cikin matacce. yana kuma fidda matacce a cikin rayayye. Hauhuwa kuwa ta ALLAH ce, amma insha ALLAH akoda yaushe zaki iya ganin zuri'ata basai na auri wata ba”.
     Dukkanin wata fara'a dake a fuskar gimbiya Su'adah ta ɓace ɓat, baka ganin komai sai ɗunbin ɓacin rai da azabar masifa. Gasu Pa kuwa gaba ɗaya murmushi ne kwance a fuskokinsu, bana bijirema gimbiya Su'adah da Ramadhan yayi bane. Na yabo da tabbatar da ingancin tarbiyyar Raudha da sukajine daga bakinsa. Wanda su sanin kansune Ramadhan baya iya boye abu inhar bai masa daɗi ba zai faɗa, hakama idan yayi masa zai yaba koda da murmushi ne. Koba komai hankalinsu ya sake kwanciya da yarinyar da suka jima suna kyautatama zato.
      Babu wanda ya sake cewa komai har ita. sai Inna ce tai musu nasiha da gaba ɗaya take nufin da gimbiya Su'adah take amma sai ta haɗa kowa da kowa a ciki. Daga haka taron ya tashi babu wani armashi. Dan ko bikin yaran gidan da sukaso tattaunawa a yau ɗin shima bai yuwu ba dole aka barsa sai wani lokacin dan ana jiran sauran gidajen angunan su kawo kuɗi ne. Ƴammata kusan shidda za'a aurar a gidan nasu Ramadhan. Ciki harda Lubnah da Bilkisu kuwa. Sai Sumayya, Rufaidah, Ai'sha da Ummita. Dukansu sunyi karatu wasunsu ma na aiki, Ummita ce kawai take kan karatun saboda manemin nata ya takurane yasa za'a haɗa da ita amma sa'ar Muneera ce ma. Koda yake ita kanta Muneera ɗin ta isa auren ai kawai dai dan akwai yayuntane.

       Babu wata walwala Ramadhan ya koma wajen Raudha, dan yasan ma'anar shirun mahaifiyarsa. Tuni ita har tayima shirin barci. Tana zaune ne a kan gadon tana assignment ɗin makaranta da aka basu na cikin hutu, sai dai sanye take da hijjab a saman kayan barcin nata. A kallo guda ta fahimci ransa a ɓace yake, cikin dauriya ta masa sannu. Bai amsa ba sai dai ya kwanta a gadon tare da ɗoro kansa saman cinyarta bayan ya ture takardun gabanta gefe.
        “K dole kin zama ƴar boko ko?”.
Ɗan murmushi tayi kawai dan yanda yay maganar kamar mai son huce haushinsa akan bokon nata ne. Cikin san kauda masa damuwarta tace, “Harka tunamin Abbanmu. Idan mukai masa laifi koya tashi baida ko sisi sai ya hana kowa zuwa makarantar boko ranar. Ya ringa faɗin, “Anma fasa bokon, daga yau bazaku sake zuwa ba, bandama shegantaka irin ta bature yabi duk ya katantane duniya ya hana kowa zaman lafiya, komai bazaka samesa yanda kake muradi ba sai kayi wani abu shege a.b.c.d kai nifa shiyyasa ma ana kaini ina tserowa a makaranta da ƙyar na haɗa sakandire ɗin ma”.
      A bazata dariya ta ƙwace masa. Har haƙoransa na bayyana baki ɗaya sai dai ya kai hannu yana karewa. “ALLAH na lura Abba ɗan darune?”. Ganin yanda ya karɓi zancen ya saka Raudha dake nata ƴar dariyar itama faɗin, “Tab damma baka sanshi bane. Wlhy duk randa darun Abba ya tashi gidan nan ranar kowa sai yaji a jikinsa. Ko ruwa ka cika kofi zakasha sai yace ka ƙara masa talauci kana baƙin cikin ya zama mai kuɗi”.
     Yanzu kam sosai yake dariya. Raudha da farin ciki ya cikata itama ta tura yatsunta duka a cikin gashinsa tana masa susa. Nan ta shiga bashi labarin M. Dauda sai dai na hankali wanda tasan mutuncinsa bazai zube a garesa ba. Cikin amincin ALLAH sai gashi ƙaunar mahaifinta ta sauka masa a rai har yanajin sassaucin takaicin halayyarsa tada da bincike yazo da ita.
       “Ya kamata ma muje mu gaishe da Abba Hutawa gaskiya”.
Cak Raudha ta dakata da susan da take masa a cikin gashi ta tsurama ƙyaƙyƙyawar fuskarsa ido idanunsa a lumshe suke yayin da hannayensa duka ke harɗe a ƙirjinsa yana kwance rigingine. Yanda ya nutsu zai baka tabbacin susar da take masa cikin gashi na masa daɗi. Ya buɗe lumsassun idanunsa da suka canja launi a hankali ya zuba mata su. Gira yaɗan ɗaga mata yana sassanyan murmushi. “Yadai naji kinyi shiru Ustazah?”.
     Hawayen da suka ɗan cika mata ido ta haɗiye, cikin ƙaƙaro murmushin itama tace, “Nagode da karamcinka”.
        “Cmon johre. An gaya miki Abban nakine ke kaɗai banson iyayi”.
   Yay maganar yana dungure mata hanci da ƙoƙarin miƙewa zaune. Toilet ya shiga, ita kuma ta sauke ajiyar zuciya da hawaye lokaci guda. Wani abu mai muhimmanci na sukar ranta. Koda ya fito wanka cayay ta kawo masa sauran namansa. Dan bacin ran daya shigo da shi ta riga ta gusar da shi. Kawo masa tai harda kunun, yako ci abinsa yay ƙat sannan ya koma bayin yayo brush, koda ya dawo assignment ɗin ta nuna masa inda bata gane ba.
       “Ustazah! Kibar batun Assignment ɗin nan nima inada nawa Assignment ɗin mai kawo lada ma.”
           “Please Ya Ramadhan dafa an koma hutu idan ALLAH ya kaimu zamuyi submitting”.
     Gadon ya hawo yana ɗaure igiyar rigar barcinsa. Ya zare mata hijjab ɗin jikinta sannan ya ɗauka takardar data rubuta questions ɗin da amsar data rubuta daban na wanda ta gane. “Yarinyar nan kanki fa naja”.
Ya faɗa cikin ɗage mata gira. Murmushi kawai tayi da maida kanta ƙasa. Shima hankalinsa ya sake maidawa ga takardun yana faɗin, “Ai gyaran ma kaɗanne”. Bayani ya shiga mata dalla-dalla harma akan abinda bata tambayesa ba, dan shima yayi course ɗin sanda yana jami'a. Sosai taji daɗin bayaninsa har tana sake zaƙulo masa wasu tambayoyin. Sai dai taƙi sakewa da jikinta sai faman karewa take da hannu kamar mai jin sanyi. Tsaf yana lure da ita amma yay kamar bai gani ba. Zata sake jeho masa wata tambayar ya turo kayan karatun nata ƙasa da jawota jikinsa yana faɗin, “K ni na gaji da aikin bautar bature zo kiji wata magana”.
    Gabantane ya shiga faɗuwa. Sai dai ko saurarenta baiyiba yaja musu bargo ya matseta a jikinsa yana shinshinar wuyanta da kai mata kiss's..........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 55_*


..........Yau ɗin ma dai kukan tasha sosai fiye dana ranar ma, a ganinta yauɗin ma babu banbanci da shekaran jiyan. Shidai aikinsa lallashi da jinjina ragwantakarta, duda dai yasan shi ɗin bana wasa bane. Bayan sallar asuba koda ya nuna sake ziyartarta kuka ta saka mishi iya gaskiyarta tana roƙonshi idan ya sake mutuwa zatai ita dai. Ta bashi tausayi ta bashi dariya kuma. Amma sai ya gimtse da nuna mata baifa san zancen ba a haka zata saba ai. Kuka sosai ta dingayi tana yarfe hannaye kamar wata ƙaramar yarinya. ALLAH ne ya taimaketa Bappi yay kiransa zasuyi magana, dan dama shirin office zaiyi daga Taura house can ya nufa. Ita kuma sai ƙarfe ɗaya zata wuce gaida su asabe daga can ta zarce gida.
       Badan yaso ba dole ya miƙe ya zura doguwar rigar jallabiya ya fita batare daya kalli Raudha dake maƙure cikin labule ba tana sharar hawaye. Ganin ya fice ta faɗa toilet, wanka tayi da ƙara gyara jikinta dan ita dai harga ALLAH zafi takeji sosai. Yau dai anyi jarumta an shiga ruwan zafi tanata raki ita kaɗai. Koda ta fito harta shirya ta gyara ɗakin bai dawo ba. Dan haka ta saka hijjab ta fita gaida jama'ar gidan.
     Kamar ko yaushe bata wani samu tarban arziki ga gimbiya Su'adah ba. Sai ma zageta tas da Lubnah da Aynah sukayi wai kwana uku batazo ta gaishe da Maah ɗin ba. Bata da abin faɗa dan tasan ita mai laifi ce. Yau ma da taimakon Bilkisu ta baro sashen bayan ta zage Aynah da Lubnah duk da kuwa duk sun girmeta. Masifa taitaima Raudha akan lokaci yayi da zata ƙarfafa ranta tabar zama su Lubnah na takata yanda suke so koda agaban Maah ne. Maah uwace, amma su ai ƙannene a gareta koda sun girneta tunda kanen mijinta ne. Murmushi kawai Raudha tayi amma komai batace ba.
        Ƙin komawa tai part ɗinsu duk da Anne tace Ramadhan ya baro wajen Bappi, suna nan a falon suna taya Anne shirya table Ramadhan ya fito cikin shirin office. Ɗanyar shaddace golden yollow a jikinsa daketa maiko harda babbar riga, sai dai bata cika girma ba dai-dai irin ta matasan zamani da suke yayi. Sai baƙin takalmi _chukka boot_ da hula tangaran daketa ɗaukar idanun mai kallon. Ko kunya babu ya miƙama Raudha dake ƙoƙarin gyara mayafinta agogonsa _zenith_ wai ta saka masa. Sai wani faman ɗaure fuska yake. Sai da taɗan dubi sashen da Bilkisu da Anne suke taga sun ɗauke idanunsu kamar basu san mike faruwa ba sannan ta amshi agogon ta ɗaura masa kunya kamar ta nutse.
      Kona gode babu ya raɓata ya wuce zuwa dining. Ta ɗan bisa da kallo ranta fes dan gara wannan fushin da azabar da tasan zata sake ɗanɗana a hanunsa. Anne ce ta sakata dole ta haɗa masa abinci, sannan suma suka zauna har Bilkisu da data karya anan.
     “Yaya kamar bakajin daɗi?”.
Cewar Bilkisu cike da kulawa. Anne da tun ɗazu hankalinta na kansa itama dai kallonsa tai. Ya ɗan yamutsa fuska da sake tsuketa. Sai dai komai baice ba. Anne ce ta sake maimaita masa tambayar Bilkisun. Cikin ɗan haushi-haushi yace, “Kawai bana son fitar ne”.
     Ƴar dariya Anne da Bilkisu sukai da lallashinsa. Raudha kam da tasan ainahin fushin murmushi kawai tai taƙi yarda kuma su haɗa ido. Shi ya fara miƙewa. Harya gama sallama da Anne zai wuce ya faki idonta ya sakarma Raudha ranƙwashi akai.
    Ba shiri ta saki karamar ƙara. Gaba yay abinsa ko waiwaye babu, Anne da komai ya faru akan idonta tace, “Mugunta dai babu ƙyau wlhy Ramadhan mita maka?”.
      Ƙin tankawa yay, sai ya ɗagama Anne yatsunsa biyu alamar bye. Ita dai Bilkisu dariya kawai take ranta fal nishaɗi haƙarsu ta kusa cimma ruwa. (Batasan tuni tacin ba itace bata da labari). Bayan mintuna kaɗan suka jiyo jiniyar tafiyar motocinsa. Hakan ya bama Raudha damar bararrajewa suka daura hira da Bilkisu da Anne. Kusan ƙarfe goma baƙuwar Anne ta iso......
         Sosai kunya ta lullube Raudha lokacin da hajiya take bayanin kayan da Anne tasa aka kawo mata nagartattu haɗin sakwattawa birnin shehu tun daga ƙasar Nigeria. Hajiya. Bata wuce ba sai kusan sha biyu, a lokacin Raudha ma ta mike taje tai shirin dan lokacin tafiyarsu ya gabato. Umarnin Anne ta bi na zuwa yima su Gimbiya su'adah sallama. Bayan ta kammala da kowane part harsu Yafendo ta nufi part ɗin surukarta a ƙarshe. Ita kaɗai ta samu a falo hakimce cikin kwalliya sai zuba kamshi take, duk da tasan bata kaunarta ta daɗe da bata lambar girma da yabo na iya tsara kwalliya da ado, dan sosai jikin gimbiya Su'adah ke ɗaukar wanka, ƙyaƙyƙyawa ce itama gata fara tas masha ALLAH, matsalarta kawai bata fara'a kamar wata sojiya😖.
      Kamar ko yaushe data gaisheta bata amsaba. Ta watsar da ita a durƙushe tsahon muntina, Raudha data ga karta makara tai mata sallama zata mike amma saita dakatar da ita. Cike da gadara da tsanar data kasa haɗiyewa tata tace, “Kin dage sai kin zauna da Ramadhan duk da na nuna miki hanyar salama kin runtse idanunki. Okay fine, sai ki shirya shigowar Aynah ku goga kishi, mai sa'a ta haye”.
     Wani irin dummm kunen Raudha ya ɗauka. Ta ɗan ɗago ido ta dubi gimbiya Su'adah. Sai dai wulaƙantaccen kallon data maka mata ya sata maida idanun ƙasa dole. wani irin abune yake sukar zuciyarta mai zafi da batasan ma'anarsa ba. (Kishi?) kai ina na kishi bane, domin *_babu so miya kawo kishi?_ maybe tsoro no kawai. To amma abinda takeji baya kama da tsoro sai jin ɗaci. Dan har wata hajijiya takeji kamar tana yawo da kanta a sararin samaniya. Sai dai ta danne a nutse taima Maah godiya da sallama ta mike ta fita duk da bata amsa mata ba.

        Gaba daya Raudha bata fahimtar komai a gidan hajiyar birni. Babu abinda ke mata kaikawo a rai da zuciya sai furucin Maah na auren Aynah da mijinta zaiyi. Tabbas ko taƙi kota so ta yarda ta fara son shugaban ƙasa Ramadhan. Irin son nan kuma mai kama zuciya da baya saki cikin sauki, duk da ita har yanzu bata da tabbacin shiɗin yana son nata. Tun tana dauriya har saida hawaye suka dinga ziraro mata, saukintama akwai ba'a gaban Asabe bane. Kagara tayi ta koma gida dan bata son tayar musu da hankali, gefe kuma tana kwaɗayin yin maganar da Mommy ko taji sanyi a ranta dai.
     Basu bar gidan ba sai bayan sallar la'asar. Driver ɗinta ta samu yana jiranta, dan hala tai sallama da su Basma da sukai mata rakkiya ta wuce. Kafin su karasa government house ma tasha kuka sosai a mota, suna zuwa ta danne ranta dai ta amshi tarbar da Mama Ladi da Mama tambaya sukai mata harma da sauran ma'aikatan sashenta da suka riski dawowar tata.
     Duk liyafar da aka shirya musu ta abinci ita da Ramadhan ɗin da dinner bataji ta birgeta ba. Gashi shi baima shigo gidan ba har kusan tara na dare. Tana falo tsaye shayi take haɗawa koshi ta ɗan sha ta kwanata sai gashi. Tafiya yake a kasalance babbar rigarsa saƙale a hannu yana ƙoƙarin kunce agogonsa tunkan ya ida hawowa. Sai da taɗan rumtse ido ta karanto addu'a da fatan ALLAH ya bata ikon shanye halin da take ciki kafin ta juyo garesa.
      Sannu da zuwa tai masa da nufarsa kai tsaye domin amsar kayan hanunsa. Babu musu ya mika mata komai sai dai bai amsa sanun datai masan ba. Sai ma yar harara daya sakar mata duk da a kasan ransa yaba ƙyawun da rigar jikinta tai mata yake. Rigace mai santsi sai dai sam babu nauyi tattare da ita kalar blue, sai dai an mata kwalliya da baƙi kaɗan-kaɗan, sai ta saka hula blue a kanta kamshin khumra mai sanyin daɗi na tashi a jikinta sama-sama. Cikin sauke ajiyar zuciya yabi bayanta ɗakinsa data nufa.
         Kusan a tare suka shigo, ta ajiye kayan inda ya dace da nufar fridge dan bashi ruwa. Yayinda shi kuma ya hau zame kayan jikinsa da suka damesa sosai. Kanta a ƙasa ta tsiyaya ruwan ta mika masa lokacin da yake zaune bakin gado yana kunce takalnan kafarsa. Bai dago ba har saida ya gama cirewa, kafarsa dake cikin baƙar safa ta bayyana. Ruwan ya amsa nanma yana ɗan hararta, ita dai sai tayi guntun murmushi da ƙoƙarin danne zafin da takeji a ranta.
      “Kayi hakuri dan ALLAH”.
Ta faɗa cikin sanyin murya lokacin da yake miko mata kofin ruwan daya shanye gaba ɗaya. Mikewa yay kamar bazai tanka ba. Sai da ya nufi hanyar toilet ya bata amsa kausashe...
      “Da kikaimin mi?”.
Ita dai babu bakin cewa komai, da zai tausaya matama daya barta da abinda takeji a ranta. Mikewa tai ta fice kafinma ya fito. Ta koma falo ta karasa haɗa shayinta tai zaman sha a dining dan tasan dole zai fito nan abinci koya buƙaci takai masa can........

      Shayin take sha, amma tunaninta sam baya tare da duniyar mutane. Tayi matukar yin zurfi a tunani har Ramadhan daya fito ya karaso dining ɗin bata sani ba. Yayi kyau cikin kananun kaya farare tas daga wandon har rigar. Sai baƙin Slippers daya kara fiddo hasken kafarsa. Idanu kawai ya zuba mata ransa fal mamakin mi take tunani haka da zurfi, dan shi a ganinsa yanda take da karancin shekaru kamar bata da wata damuwa da zata iya damunta a rayuwa. Hanunta da take zagayawa kan kofin ya rike cikin nasa ya matse da kofin. Zafi ya ratsata ta dawo hayyacinta firgigit. Sai kuma ta bata fuska da shagwabeta kamar zatai kuka. “Ya Ramadhan da zafi fa!”.
     Bakinsa ya ɗan taɓe da faɗin, “Ai dan kiji zafin nayi. mi kike tunani haka?”.
        Nannauyan numfashi taja a hankali, ji take kamar ta rushe masa da kuka. Amma sai zuciyarta ke tausarta akan ta daure har sai taji daga bakinsa tukunna. Cikin ƙoƙarin danne ainahin damuwarta tai ƙasa da kanta idanunta na tara kwalla. “Dan ALLAH kayi haƙuri ka yafemin, ALLAH inajin tsiro ne kawai shiyyasa. kuma akwai zafi wajen jinake kamar zan iya mutuwa”.
      Idanu ya ɗan tsura mata na wasu mintuna. Sai kuma ya lumshesu ya sake buɗewa a kanta yana furzar da numfashi.
       Jin yaki cewa komai ta ɗago ta ɗan dubesa fuska share-share da hawaye. Kauda kansa yay da rumtse idanu yana cizar lips. Sai kuma yaɗan murza goshinsa kafin ya zaro tissue dake a dining din ya miƙa mata.
     “Bani abinci barci nakeji”.
   “Baka haƙura ba dan ALLAH”.
              Fuska ya sake tamkewa. “Nifa bana son nacin magana abinci nace ki bani ko”.
     Da ƙyar ta haɗiye kukanta ta mike tai masa yanda ya buƙata. Sai dai abincin ma kaɗan yace ta zuba masa shima ta bashi shayi. Duk yanda ya buƙata haka tai masa. Kafin ta koma wajen zamanta ta cigaba da shan shayinta da duk ya huce da cokali. A haka Bilkisu da yasa ta dawo gidan da zama baki ɗaya har sai lokacin bikinsu ta fito ta samesu. Sannu da zuwa tai masa, sannan takai zaune itama dan dama bataci abincinba yau karatun alkur'ani tayi.
         “Su Muneera fa?”.
Ya tambayi Bilkisun batare daya daina cin abincinsa ba.
     “Yaya ai muna isowa kayansu suka kwasa driver ya juya dasu kamar yanda Pa ya basu umarni”.
     Kansa kawai ya jinjina. Raudha dakema Bilkisu kallon rashin fahimta dan batasan da barin su Aynah gidanba ta nuna mata Ramadhan da ido tana ɗaga mata gira. Kanta kawai ta maida kasa dan ta gane Bilkiaun na nufin ta tambayesa.
       Haka suka kammala cin abincin kamar wasu kurame. Ramadhan ya koma falo ya ɗan zauna yana kallon labarai. Raudha kuma ta shiga tambayar Bilkiau miyyasa Su Muneera zasu koma gida?.
      Ɗan harar wasa Bilkisun ta mata. “Aunty Raudha bansan jajibe-jajibe. Kedai kawai ki godema ALLAH an rabasu da gidan kawai suje can su karata da baƙin halinsu”.
    Raudha zata sake magana ta dakatar da ita tana miƙa mata waya. “Kinga ni share waɗan can shashashun bani shawara. “Surukinkine ya turosa wai dole saina zaɓa kalar bags ɗin da nakeso”.
    Cikin murmushi Raudha ta fara bin set na akwatinan da kallo. Sun haɗu iya haɗuwa. Da gani kuma daga kasar ketare aka turosu. “Humm ni wannan ai sai nai ruwan ido. Duk fa sun haɗu aunty Bilkisu”.
     Yar dariya bilkisun tayi itama. “ALLAH nima tun ɗazun na kasa ajiye hankalina waje guda na zaɓa. Shiyyasa nace ya jira sai kin dawo kin zaɓa sai na bashi amsa.”
     Har cikin rai Raudha najin daɗin yanda Bilkiau ta ɗauketa. Sai ta tuno da Queen Billy sabuwar ƙawar datai yau a school, a massallaci suka haɗu wajen alwala ta yarda wallet ɗinta batare data sani ba. Shine Raudha ta ɗauka ta bita massallaci da shi. Sai da suka idar da salla ta bata. Cikin jin daɗi ta rungumeta. Sai kuma ta saketa tana bata hannu. “Yi haƙuri dadine wlhy ya rufeni, dan duk abuna mai muhimmanci na cikin wallet ɗin nan sunana Bilkiau amma amfi sanina da  queen billy kefa?”.
        Daga cikin niƙab Raudha tai murmuahi, dan ta fahimci queen Billy zatai ɗan karen surutu. Itama hanunta ta mika mata. “Nice name dear ni sunana Amenatu Dauda”.
      “Sunanki mai daɗi zamu iya zama kawaye? Danni bakuwace yau kwanana biyar kenan da shigowa school ɗin nan har yanzu na kasa sabawa da kowa.”
    Nanma murmushi kawai Raudha tayi, dan haka kawai queen Billy ɗin ta birgeta. Itama dai yarinyace kamarta dan bazasu wuce sa'anin juna ba. Gata ƙyaƙyƙyawa. Taso Raudha ta buɗe nata fuskarta amma taƙi, acewarta wataran zata ganine. Sun faɗama juna department sannan sukai sallama..........✍
      


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 56_*


...........“Oh oh wai duk zaɓen akwatinne ya saki tafiya tunani Mrs Ramadhan ”.
   Firgigit Raudha ta dawo hankalinta. Sai kuma tai Murmushin da sauke ajiyar zuciya. Bilkisu tace “Uhm kodai mu bari sai da safe naga hankalinki nakan mijinki, nima gara na barki ki wuce kafin ya fara hararata”.
      “Kai auntu Bily”.
Raudha ta faɗa cike da kunya.
    “To ai gaskiya na faɗa, gashi sai murmushi kike kina tunani, kwantar da hankalinki gashi can zaune ko'ina baijeba”.
     Ita dai murmushi kawai Raudha tayi ta cigaba da duban akwatinan. Wasu Silver color ta zaɓa. Bilkisu tace, “Woow kinsan kala Auntyna wlhy ni kaina hankalina na kansu tun ɗazu. Sai ki ƙara biyu wai set uku yake so, dan da biyar yace nidai nace sunyi yawa gara ayi abin hankali sauran kuɗin aba mabukata.”.
        Cikin zuciya Raudha ke jinjina masu kuɗi na abinda suke so. A fili kam sai ta murmusa. “Hakan da kikai yayi aunty, da ana samun irinku da almabazaranci da dukiya ya ragu ai. ALLAH ya sanya alkairi yasa damu za'ai”.
         “To amin auntyna. Inshaa ALLAH lokacin kina fama da babynmu ma”.
      “Kai aunty Rufan asiri”.
Raudha ta faɗa tana mikewa. Itama Bilkisu mikewa tai tana dariya suka nufi falon inda Ramadhan ke zaune har yanzu yana kallon labaran...
       A falon duk suka zauna. Bilkisu taima Yayanta sallama ta wuce ɗaki danta basu waje suma su shakata. Ganin hakama Raudha ta dubesa tana hamma. “Yaya baka bukatar komai naje nima na kwanta”.
      Shiru bai tanka mata ba. Harta fidda rai da samun amsa taji yace, “Zo nan”.
     Mikewa tai duk a tsorace taje gareshi. Tana koƙarin zama a kujerar gefensa ya riƙota ta zauna saman cinyarsa. Kusan tare suka sauke ajiyar zuciya. Matso da ita yay ta raɓu jikinsa har tana jin saukar numfashi sa a dokin wuyanta. Ya kama hanunta ɗaya cikin nashi yana murza yatsun a hankali. “Ameenatu baƙya tsoron wata ta ƙwace miki ni? Idan kinamin irin wannan riƙon na rashin kulawa tuni zan koma ba naki ba.”
     A take idanunta suka cika da ƙwalla. Dan gani take yana mata ishara da aurensa ne kawai. Cikin rawar murya tace, “Dan ALLAH kayi haƙuri bazan sakeba. Ko zanji zafin zanyi juriya”.
       Numfashi ya sauke a hankaki yana sassauta muryarsa. “Ni ba ina miki magana akan hakan bane. Ɗazu fa a gida ficewarki kikai sabgar da ba'a aikekiba kika barni ni kaɗai da shirin office, maimakon kizo muyi sallama ma sai kikaƙi. Dazan wuce ko addu'a bakiminba. Na dawo gida kuma na sameki babu wani tarba kin sake barina ni ɗaya a ɗaki kamar ba mijinkine ya dawo ba. Haka aka koya muku kula da miji a islamiyyar?”.
     Kanta ta jinjina masa amalar a'a.
Juyota yay suna ɗan fuskantar juna. Ya tsura mata idanunsa masu kaifi da ƙarfi. Har yanzu yatsun hanunta na cikin nashi still dai yana murzawa.
          “Amma k miyasa kike son yima mijinki haka? Ko kina so wata tazo ta ƙwace ni?”.
     Ai babu zato sai kawai ta rushe masa da kuka tana faɗawa jikinsa.
          Murmushi ya saki mai faɗi, yasa hannunsa ya zagayo kugunta ɗayan yana shafa bayanta alamar lallashi. Sai dai baiyi maganaba tsahon mintuna har tagaji tai shiru da kanta. Ɗagowa tai tana goge hawayenta. shiko sai faman binta da ido yake.
       “Ustazah kishi fa kenan? Anya wannan zuciyar bata kamu da son Ramadhan B. Hameed Taura ba mai tsanani?”. Yay maganar yana ɗora yatsansa manuniya saitin zuciyarta. Kunyace ta kamata. Amma sai ta ɓata fuska da ture hanunsa.
       “Ni ba wani kishi”.
Karamar dariya da rabonta da gani a garesa tun jiya yayi har haƙoransa na bayyana sosai. Ya shafa fuskarta da faɗin, “To shikenan naji ba'a son Ramadhan balle ai kishinsa. Sai dai ina bada shawara a gyara kafin naki ɗage kafar tafiya aljannar”.
     Murmushi tayi cike da kunya ta sake sinne kanta a jikinsa. Daga haka suka shirya. Sai dai koda suka nufi ɗakinsa yayin kwanciya babu abinda yay mata sukai barcinsu lafiya.

       ★_______★______★

     Dauriya iya dauriya Ramadhan yayi akan kin sake kusantar Raudha, sai dai salon yanda yake mata abubuwa ya ƙara shaƙuwa a tsakaninsu. Ga Bilkisu na sake ɗaurata a layi sosai ita da mama ladi. Gefe kullum Asabe cikin yima yarta nasiha take akan abubuwa da yawa da abaya tasan ita ta tafka kuskure a kansu a rayuwar nata auren.
    Karatunta na tafiya lafiya cikin aminci, randa Ramadhan bai gajiba idan ya dawo sukanyi karatu ya kara faɗaɗa mata bayani akan abinda bata ganeba. Hakama Bilkisu na iya bakin koƙarinta.  Acan school kuwa sun ɗinke da Queen Billy da batasan wacece Raudha ba. Har yanzu ma bata yarda ta nuna mata fuskarta ba. Duk da tasan kota nuna ɗin da wahala ta ganeta tunda dai babu wanda zaice ga ainahin fuskarta a duk hotuna dake yawo a media ita da shugaban kasa saboda facemask da take sakawa a koda yaushe idan suna tare. Su Basma ma sun karɓi Queen Billy, dan tanada shiga rai saboda barkwancinta da yawan fara'a. Ranar juma'a da take cika kwana biyar ciff batare da Ramadhan ya sake neman komai daga garetaba ta dawo school a gajiye da yamma lis. A falo ta iske Bilkisu da Ramadhan daya dawo gida da wuri yau. Dan shima Alhmdllhi komai yana tafiya masa dai-dai babu abinda gwamnatinsa keyi yanzu sai shimfiɗa manyan ayyuka da yan ƙasa keta sambarka. Irinsu Alhaji Haladu Gwandu da su forma president da God Fathers nasu kuwa na gefe sun shaka sunyi fam da takaici. balle kuma vice president da kamar ya zama hoto ga wasu al'amuran na gwamnati. Dan shegen mugun halinsa da Ramadhan ya fara fahimta ya sashi ɗan janye jikinsa da shi abubuwa da yawa sai dai ya gani a takarda. Ga kuma binciken da suke kanyi akan abinda suka fahimta game da alakar matarsa da Raudha.
      Bilkisu ce kawai ta mata sannu, gogan ko ido kawai ya tsura mata yana kallonta ƙasa-ƙasa duk da fuskarta sakaye take da niƙab. Baki taɗan tura da kauda kanta daga garesa tace, “Ina yini”.
     Shiru yay bai amsa ba, sai ma sake karkatar da kai yayi. Bilkisu dake musu dariya ƙasa-ƙasa ta miƙe cikin sanɗa tabar wajen. Ganin haka Raudha data yaye niƙab ɗinta tana kumbura fuska itama tabar wajen ta nufi ɗakinta. Idanu yaɗan lumshe da saki tattausan murmushi yana shafar kwantaccen gashin fuskarsa da yayma gyara ɗazun da safe san dan samun yin sallar juma'a cikin annuri da haiba.
        Yana nan zaune a wajen har Raudha ta sake fitowa bayan kusan mintuna talatin. Sanye take da skirt da riga na atamfa, sun mata ƙyau sosai sun kuma kama mata jiki ɗam saboda ƙibar data ƙara. Dan sosai Raudha ke buɗewa ta ko'ina tana ƙara girma. Ga wani haske da tayi fatanta ya ƙara kwanciya luff da ɗan duhun da bazaka kirata fara ƙal ba.
       Tsabar jan magana ta gaban Ramadhan tazo zata wuce kanta ko ɗankwali babu. Sai gashinta dake tsefe data ɗaure da ribbon yanata reto. Yi yai kamar bai ganta ba. Sai dai ta kusan gama giftashi ya taɗota da ƙafa sai gata a jikinsa. Ƴar ƙara ta saki mai cike da zallar shagwaɓa. yay saurin buge bakin da yatsunsa biyu.
       “Wayyo Anne zai fasamin baki”.
Ta faɗa hawaye na ciko mata. Zata tashi ya maidata, kamar gaske ya wani tsuke fuska. Cikin ɗage gira da hararta ya sake kaima bakin nata ɗalli ta kare. “Na kula kin fara rainani a gidan nan. Harni zakima ƙwalele da halalina”.
      Idanu ta waro sosai sai kuma ta rufe fuska. “ALLAH dai yana gani ni babu ruwana. Kawai fa wucewa zanyi ni koma ganinka banyiba”.
     “Oh really?”.
Ya faɗa yana mikewa dauke da ita. Roƙonshi ta farayi tana wantsala kafafu akan itafa badashi takeba ALLAH yunwa takeji. Dan ALLAH yayi haƙuri bazata sakeba. Ko kulata baiyiba ya maida ƙofar ɗakinsa ya datse da key duk da yasan babu mai zuwa sashen. Cakulkulo ya fara mata daga kuka ta koma dariya da bashi haƙuri, bai ƙyaleta ba sai da suka dire cikin gadonsa. Salon daya fara bi da itane ya sata shagala da farko, sai da labari yay nisa a nanfa ido ya raina fata. Ta shiga magiya da roƙo akan abinda shi kuma anzo gaɓar da bazai iya ɗaga kafarba. Aiko taji ajikinta, dan har dana sanin shiga huruminsa tayi. Kuka kam ba'a magana.
           Sun fito wanka yake dubanta da murmushi yanda ta lafke a gado tana sakin numfashi da ƙyar kamar wadda ke a cikin ciwo. “K kuwa yarinyanan an miki wankan jego kina jinjira? Shikenan da'an ɗan taɓaki sai ki sharɓema mutane a haka za'a haifa ƴan huɗun?”.
       Shiru tai masa kamar tai kuka. Haka kawai yaji dariya ta taho masa. Bai iya dannetaba ya ƙyalƙyale kuwa. Haushine ya kama Raudha, a ganinta tsantsar muguntace ya gama wajiga rayuwarta ya dawo mata dariya. Sai kawai ta sakar masa kukan karya.
     “Okay kukama kike? To bari kawai na sakaki mai dalili mana da kiyi na banza gara kiyi na lada.....”
     Kafin ya rufe baki har takai ƙofa. Baki ya buɗe zaiyi magana gabansa yay wata irin masifaffiyar faɗuwa tare da kansa daya sara masa. Da sauri ya dafe kan yana ambaton sunan ALLAH. Raudha data zata wayau yake son mata tai tsaye kawai tana kallonsa da murmushi. “Ya Ramadhan na riga nasan wayonka ai. Shine harda pretending?”.
      Jin shiru bai amsa mataba ga kujera ya dafe har lokacin hanunsa dafe a kansa kamar maijin hajijiya yasata daina dariyar ta tsura masa idanu. Da sauri ta ƙarasa garesa ganin ya tafi kamar zai faɗi. Tarosa tai, sai dai yanayin jiki ba ɗayaba yafi karfinta musamman da jikin nasa ya saki sai suka zube ƙasa ya faɗa kanta. Ƴar ƙara ta saki da ambaton sunan ALLAH saboda wani raɗaɗi daya ratsa mata hanunta da suka faɗi a kansa. Tai ƙoƙarin dannewa amma ta kasa dan azaba. Kuka ta saki tana son turesa sai dai ina. A take jikinta ya fara rawa, ta turashi iya karfinta yay ƙasa da ƙyar, sai dai kafin ya dire a bazata taji ya ɗauke fuskarta da mari.
      “K! Baki da hankaline ni zaki ture?”.
    Ya faɗa a matuƙar kausashe da muryar da ko sanda basa shiri bata taɓa ji daga garesa ba. Lallai ta maru, dan yay bala'in shigarta, zata iya rantsewa kuma shine na farko a duniya daya taɓa marinta, tsabar azaba har kifewa tai akan table sai ga goshinta ya fashe. Idanu ya waro a ɗan tsorace yay kanta yana ambaton “Ya salam Ameenat....”
       Sai dai yana kai hannunsa jikinta ya sake tureta da ƙarfi ya sake dafe kansa dake juya masa. Duk yanda yaso yin addu'a bakinsa yay masa nauyi ya kasa furtawa. Duk da azabar dake ratsa Raudha a goshi da hannu haka ta sake nufarsa tana kiran sunansa a tsorace. Sai dai tana matsawa garesa ya sake hankaɗeta a matuƙar tsawace yace, “Fitarmin anan!!”.
       “Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un Ya Ramadh.....”
      “Nace ki fitar min anan!!”.
Ya faɗa a wani irin yanayi na fita hayyaci da tsananin ɓacin rai. Sosai jikin Raudha ke rawa kuwa yanzu. Ta fita a ɗakin da sauri kuka na kufce mata. Ga jini harya wanke mata fuska duk da taresa da tai da hanunta mai lafiya. Hanunta daya bugu kuwa wata azaba yake mata harya fara yawa da kumburi. Bata samu kowa a falon ba, sai dai karar buɗe ɗakinta da bugo ƙofar ta rufe ya fargar da Bilkisu dake gaban mirror tana kallon film a lap-top. Da sauri ta fito sai idonta yaci karo da ɗigon jini, a razane tabi jinin da kallo har ƙofar ɗakin Raudha, ai bama tasan kalar tsallen datai kawai ta ganta jikin ƙofar ba.............✍

😥🙏🏻aimun afuwa. Jin daɗi baya dorewa sai da ƙaddara. A lokuta da dama jarabawa itace ke ƙara. kai mutum ga ajin nasara. Ba'a samun wannan nasarar kuma sai da haƙuri da juriya.🚶🏻   


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻


Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_YADDA ZAKA SIYA LITTAFI A AREWABOOKS_*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾

*Recharge* - inda ake shiga domin saka kudi cikin account.

*Balance* - Zai nuna kudin account dinku da zaku iya sayayyan littafai cikin kasuwar ArewaBooks.

*Credit/Debit Card* - Hanyar farko kuma mai dadi wajan Recharge din account dinku.

A inda (Enter your amount) za'a saka kudin da akeson Recharge din sai a taba "Proceed". Zaibude muku inda zaku saka bayanan katin banki, kuna gamawa kudinku zaishiga account dinku kaitsaye (instant).

--------

Akwai wasu hanyoyin saka kudi a ArewaBooks account kamar:

*Bank Transfer*
*Airtime Transfer*

Saidai su ba kaitsaye bane (instantly) sai ArewaBooks ta tabbatar da Transfer din, amman bayakai 1hour za'a gansa a Balance.


*Bank Transfer* - kamar yadda akwai bayani a sama da kuma account number ArewaBooks.

_Account No_ - *1220077999*
_Account Name_ - *Arewa Books Publishers*
_Bank_ - *Zenith Bank*

Bayan anyi Transfer dinne sai a cike wannan Form din:

Amount Paid: - Nawa aka tura?

Name used for transfer: - sunan da aka saka wajan turowa

Transferred time: - lokacin da aka turo

Name of bank: - sunan bankin da aka turo dashi

Deposit date: - ranar da aka turo

Sai ayi SUBMIT.

*Airtime Transfer* - muna bada shawaran ayi amfani da *Debit Card* kokuma *Bank Transfer* akan *Airtime Transfer* , amma idan yakama babu mafita saishi tau muna amsar:

MTN,
9Mobile
Glo
Airtel

Amma kamar yadda akayi rubutu a sama afara tuntubar ArewaBooks a WhatsApp domin akwai percent da ake cirewa na canji(convert) kafin kudinka yashiga Balance.

*WANNAN SHINE BAYANAN*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 57_*


..........“Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un aunty Raudha jini kuma?”. Bilkisu data shigo ɗakin a birkice ta faɗa tana ƙarawo gareta. Kamata tai suka nufi toilet, ta haɗa ruwa mai ɗumi ta taimaka mata ta wanke fuskar da hanunta, jinin dai bai tsaya ba. Sai dai sun tare da tissue. A bakin gado ta zaunar da ita, ta ɗakko first aid box ta shiga ƙoƙarin tsaida jinin, da ƙyar aka rufe wajen da audiga da bange. Ita dai Raudha babu abinda take sai sakin ajiyar zuciya.
      “Aunty Raudha wai garin yaya? Ina Yaya kuma?”.
   Komai Raudha kasa cemata tai, sai hawaye take sharewa kawai. Hankalin bilkisu ya ƙara tashi, sai dai ta barta bata sake maganaba. Tana niyar mikewa ta maida first aid box ɗin ma'ajiyarsa ta lura da kumbirin hanun Raudha kuma. Gaba ɗaya saita sake ruɗewa ta kamo hanun tana kallo. “Ya ALLAHU, nan ma ai ciwon kikaji Aunty! Kinga bara na kira Yaya da mama ladi dan ta iya gyaran ƙashi”.
       Ita dai Raudha komai batace ba, babu jimawa suka dawo da mama ladi, bilkisu ta sake fita. Duk da ta fahimci akwai matsala ƙofar Ramadhan ta dingama knocking a ɗarare. Shiru babu ko motsi, sai ta ɗan tura ƙofar ta leƙa. Gabanta ne yay masifar faɗuwa hango Yayan nasu zaune akan tum-tum ya dafe kansa. Babu shiri ta shigo ɗakin da sassarfa. Muryarta har rawa yake ta durƙusa gabansa “Yayanmu dan ALLAH mike faruwa ne? Aunty Raudha taji ciwo sosai wlhy har a hanunta mi'akai mata”.
        Da ƙyar ya samu damar fisgo kalmar innalillahi... A cikin zuciya. Ya ɗago jajayen idanunsa ya zuba kan Bilkisu datai matuƙar razana. Dan rabon da su gansa a irin wannan yanayin tun rasuwar su Haseenah. Baya taɗan ja jikinta na rawa. Shima sai ya cije lips sinsa da ɗago hanunsa ya kalla. Sai kuma ya dafe kansa dake matuƙar juya masa. Kusan minti ɗaya ya sake ɗagowa ya dubi Bilkisu da gaba ɗaya ta gama tsorata. Cikin yanayin damuwa yace, “Ina Ameenatun?”.
       “Tana ɗakinta Yaya, nabar Mama ladi zatai mata gyara a hanunta dan harya kumbura, ga goshinta ya fashe da ƙyar na iya tsaida jini....”
      Ai bama ta ƙarasa ba ya miƙe hankali tashe. Sai dai hakan bai hana bayyanar nutsuwarsa ba. Fita yay Bilkisu tabi bayansa. Kai tsaye ɗakin Raudha ya nufa, sai dai yana ɗaura hanunsa bisa handle ɗin ƙofar ya dafe kansa da yay masifar sara masa. Da sauri ya shiga girgiza kansa yana ja da baya. Barin wajen yay ya sake komawa hanyar ɗakinsa. Bilkisu ta bisa da sauri tana kiransa. Wata razananniyar tsawa data sakata jan birki ya daka mata, yay shigewarsa ya bugo ƙofar da ƙarfi har Bilkisu na zabura.
          Kuka Bilkisu ta fashe da shi. dan kuwa ta fahimci lallai akwai matsala, sai da tayi mai isarta ta koma ɗakin Raudha. Ta jiƙe sharkaf da zufa kamar ba ac a ɗin saboda gyaran da mama ladi tai mata. Mama ladi dake naɗe mata hanun da bandage ta dubi Bilkisu. “Taji ciwo sosai, dan gocewar ƙashi ta samu. Garin yay hakan?”.
        Kafin Bilkisu ta bada amsa cikin share hawaye Raudha tace, “A toilet ne na zame”.
      Sannu Mama ladi ta shiga jera mata. Bilkisu dai wani irin tausayin Raudha ɗinne ya lulluɓeta. Dan ta tabbatar daga yayansu aka samu matsalar musamman da taga shatin yatsu a fuskar Raudha alamar marinta akai. Magani ta sha ta kwanta bayan tayi sallar magrib da isha'i, babu jimawa kuwa barci mai nauyi yay awon gaba da ita. Bakajin komai sai ajiyar zuciyarta.
        Tagumi Bilkisu tai zuciyarta nata kaikawo. tama rasa ina zata kama akan wannan al'amari. Kusan tara na dare sai ga kiran Basma ya shigo mata. Da farko kamar bazata ɗaga ba sai kuma ta daure ta ɗaga wayar na gab da tsinkewa. Wani irin dummm kunen Bilkisu yayi jin abinda Basma ta faɗa. Muryarta har rawa take wajen maimaita “Basma shi Yaya Ramadhan ɗin da kansa yace zai auri Aynah?”.
      Daga can Basma tace, “Wlhy kuwa Aunty B. A gabana Maah tai waya da shi yanzun nan sai farin ciki take tana saka masa albarka. Ni nama rasa wanda zan tunkara da wannan abun al'ajab shine fa na kiraki naji ko wani abu ya faru anan”.
     “Nan dai babu abinda ya faru, sai dai yana ɗakinsa. Amma dai wannan lamari da ɗaure kai. Basma anya Adda Asmah bata fara cin galaba akan Maah ba?”.
        “Aunty Kamar ya?”.
Saurin dafe kai Bilkisu tai jin zata saki layi. Ta manta ita kaɗai taji abinda Adda Asmah ta taɓa faɗa akan Mahaifiyarsu kwanakin baya sanda ake tsaka da rikicin auren Yayansu da Raudha. Kuma bata taɓa nuna ta saniba ko taɓa faɗama wani. Sai dai tana kallonta da abun kuma tun daga ranar taji bata sonta duk da yayar Maah ce. Hasalima tafi shiri da ita fiye da kowa a ƴaƴan gidansu, dan ita takan iya zuwa ta kwana gidansu Aynah ɗin ma ba kamar su Basma ba.
          

★★★_____★_____★★★

         Tabbas abubuwa sun kwaɓe a tsakanin Raudha da shugaban ƙasa Ramadhan. Ita gaba ɗaya tsoron haduwarsu ma takeyi, yayinda shi yasha gwada zuwa gareta da zaran ya iso kofar ɗakin sai yaji wani irin mugun tsanarta mai ban mamaki, dole yake juyawa ya fasa. Babu abinda Raudha keyi sai kuka, sai dai duk da haka tana ƙoƙarin zuwa makaranta. Bilkisu tayi-tayi ta faɗa mata ainahin abinda ya haɗasu taki. Takuma roƙota ALLAH akan karta sanarma su Anne. Rasa mi Bilkisu zatai tayi, sai kawai ta zubama sarautar ALLAH ido tana tayasu da addu'a.
       A cikin kwanakin da basu gaza gomaba da faruwar komai Raudha duk ta fige ta rame. Sai uban haske datai ta ƙara tsayi. Kullum babu fashi zataje ta gyara masa ɗakinsa, duk bayan kwana biyu ta wanke masa under wears ɗinsa dan tafi gane wankesu da hannu ba Worthing machine ba. Idan ta gama sai tai drying nasu a machine ɗin. Komai dare kuma sai tayi zaman gogesu bayan ta musu turare na turaren wutarta na kaya mai daɗin ƙamshi sannan ta maida ɗakinsa ta jere masa.
        Sam ya daina shigowa gidan da wuri, weekend kuwa har taci ta ƙare bai yarda sun gamu ba. Bata da aiki sai kuka da gayama UBANGIJI. Dan ta rasa wanema irin tunani zatai akan sauyawar tasa. Koda zuciyarta ta nuna mata dama sabbin halayyar daya fara mata yayine dan ya samu jikinta sai tai saurin ture tunani dayin a'uziyya. A haka suka sake cinye sati uku babu wani canji.

*_RAMADHAN_*

       A sashen Ramadhan shi kaɗai yasan tashin hankalin da yake ciki na tsananin son Ayna'u. Bashi da burin daya wuce mallakar Ayna'u matsayin matar aurensa. Kullum cikin yima su Bappi nacin akai kuɗi yake dan abun yanzu ya wuce Maah kawai har Anne da Pa da Bappi duk sun sani. Tun suna ɗaukar abun nasa wasa harya koma basu haushi. Dan ranar daya kai Pa ƙarshe akan lamarin ba karamin zagesa yay ciki da bai ba. Ya kuma masa dogon gargaɗi akan inya sake zuwa masa da batun Aynah sai ya matuƙar ɓata ransa. Dama kuma itama Maah yaja mata gargaɗi akan damunsa akai kuɗi da takeyi.
       Wannan zagi da Pa yay masa ya matuƙar ƙona masa rai, dan kuwa dai a fusace ya dawo gidan. Abin tsautsayi Raudha na ɗakinsa tana gyarawa dan yau ta fita school da wuri tama rigashi fita, shiyyasa bata gyara masa ɗakin ba sai da ta dawo tunda shi bai dawo ba. Ba karamin firgita tai da ganinsa ba, dan rabonta da shi tun randa abin nan ya faru sai dai ta gansa a tv ko hoto. Duk ya rame mata a ido yayi duhu. Wata irin tsawa ya daka mata data nema wantsalo zuciyarta ta baki. Tai nufi fita masa a ɗaki ya shaƙota ya jefa saman gado.

       Lallai Raudha ta tabbatar a baya wahalar da takesha a hanunsa ba wahala bace. Dan kuwa lallaɓata yake kuma cikin soyayya mai gusar da hankali. Amma a yau ta tabbatar da waye Ramadhan. Kuka take kamar ranta zai fita tsabar yanda ya wajiga rayuwarta. Daga ƙarshe ya korota a ɗakin. Da ƙyar ta iya kai kanta nata ɗakin, ALLAH ma ya sota Bilkisu bata gidan. Su mama ladi kuma indai ba ita ta buƙaci ganinsu ba babu mai hawo musu nan sai in zaiyi aiki. Ƙofar ta murzawa key sai dai bai rufu da ƙyau ba ta zube jikinta tana jan numfashi da ƙyar, tsabar kukan da taci har asthma ɗinta na ƙoƙarin tashi. Rarrafe ta dingayi hanunta rike da ƙirjinta, da ƙyar takai kanta jikin gado ta ɗauka inhaler ɗin akan bedside drawer. Tata ƙoƙarin ganin ta shaƙa hakan bai yuwuba, har takai numfashinta na neman fara nisa ALLAH ya kawo Bilkisu.
       ALLAH ya taimaka ƙofar data rufe bata rufu ba. Da lallai zatama iya rasa ranta a wannan lokacin. Taimakon gaggawa Bilkisu ta bata, da ƙyar numfashinta ya dai-daita. Raudha dake magana a wahale ta roƙa Bilkisu ta haɗa mata ruwa mai zafi sosai. Bilkisu batasan mike faruwa ba. A tunaninta ko duk halin tashin Asthma ɗinne data shiga da kuma gajiyar makaranta. Bayan ta haɗa mata ta fito ta taimaka mata zuwa bayin, duk da dai yanda taga Raudha na tafiya a bubbuɗe ya ɗaure mata kai matuƙa.
      Da ƙyar Raudha ta iya gyara jikinta, tai luff a cikin ruwan ɗumi tana hawaye da addu'ar ALLAH ya bata juriyar cinye wannan jarabawa. Amma tabbas zuwa yau ta fara fahimtar mijinta baya cikin hayyacinsa. Akwai abinda ke faruwa da shi da su basu sani ba. Zata tayashi da addu'a koma minene ALLAH ya yaye masa shi.
 
     Kamar wasa sai ga karamar magana ta zama babba, dan kuwa dai ciwo sosai Raudha ta kwanta washe gari ko makaranta bata iya leƙawa ba ma. Kusan kwananta uku a halin jiyya kafin ta warware ta cigaba da harkokinta. Sai dai fa a yanzu babu wanda take tsananin tsoron haduwa da shi a duniya sama da Ramadhan. Ko maganarsa taji a tv sai gabanta ya faɗi. A haka rayuwa ta sake turawa suka sake cinye sati huɗu, sati kusan na bakwai kenan da shiga halin da suke ciki. Zuwa yanzu kuma har an kai kuɗin auren Aynah saboda birkicewar da Ramadhan yay musu.
       Tuni Pa ya fahimci akwai sihiri tattare da yaronsa. Amma ya zaɓi barinsa a hakan dan yanaji a ransa dole sai Adda Asmah ta shayar da gimbiya Su'adah zumar mamaki sannan zata san ANNABI ya faku. Koda su Bappi ma suka fara irin wannan zargin Pa ɗinne ya gusar musu da zargin ta hanyar nuna musu babu wani sihiri uwarsa ke zugasa. Yayi hakane dan baya son suce zasu tashi tsaye akan Ramadhan ɗin, yafi son sai uwarsa taji a jikinta sannan. Amma kuma bai gaza da masa addu'ar kariya ba.
      Abinda hankalinsu kuma ya gagara kaiwa akai su duka basuyi tunanin ko abin ya shafi Raudha ba. Dan ita dai ko sau ɗaya bata kawo wa kowa ƙararsa ba. Ta kuma hana Bilkisu faɗa duk da itama Bilkisun ba komai ta sani ba har yanzun. Kullum kuma Anne ta tambayi su Basma sukance Raudha na lafiya harma tana gaishesu tunda kullum dai suna tare a makaranta. Hakanne ya ɗan basu nutsuwa suke ganin shi kaɗai abin ke dawainiya dashi kenan.

         ALLAH sarki Raudha, sai dai kuma abinda ba'a sani ita kaɗai tasan halin da take ciki, ga yanzu kullum da zazzaɓi take kwana. Ga kasala da batasan kota minene ba. Komai da ƙarfin hali take yinsa hatta karatun. Ita Bilkisu tana ɗaukar yanayin natane kawai da tunanin maganar auren Ramadhan ɗin. Dan haka ta maida hankali wajen bata shawarwari da nasiha.
      Bazatace auren Ramadhan baya damuntaba, dan tasan wacece Aynah tasan kuma burinta akanta, dan tunda Ramadhan ya fara birkice mata Aynah da Addah Asmah suka kirata sukai mata zagin ƙare dangi saboda fahimtar ita sihirinsu bai kamataba. A tunaninsu itama bin malaman take shiyyasata ta tsira. Basu san ALLAH ne bai ƙaddara mata shan zoɓon waccan ranar ba kawai. Ranar taci kuka matuƙa dan zagine da cin mutunci da bazai taba goguwa a zuciyaba kai tsaye. A kalamansu kuma ta fahimci lallai akwai ƙullin dake kan mijinta da alama kuma sunada alaƙa da shi. Bata da abin faɗa, dan koba komai dai ƴan uwansa ne. Adda Asmah ma na amsa sunan uwane a garesa tunda yayar mahaifiyarsa ce da itama zata iya kiranta da uwa. Haka ta cigaba da masa addu'a da ita kanta abun na damunta.
      Sai dai halin da take ciki na rashin jin daɗin jiki yafi kwashe kaso mafi yawa na damuwarta. Ko mahaifiyarta batasan halin da take a ciki ba. Sai dai a duk sanda sukai waya takance Mummy kimin addu'a. Idan asabe ta nuna damuwarta cikin tashin hankalin furicin Raudhan sai ta dinga kwantar mata da hankali akan babu komaifa saboda karatu take cewa hakan.
     Ita dai Asabe hankalinta ba wani ya kwanta bane. Amma sai ta dage da bin ɗiyarta da addu'ar fatan alkairi. Itama kuma Raudha bata wasa. sosai take a kan ƙafafunta tana gayama ALLAH damuwarta akowanne dare. Wani lokacin ma tana salla tana rawar sanyin zazzaɓi, haka ta dage da azumin alhamis da litinin. Ta kuma dage da saka har Abba (M. Dauda) turama kuɗi akan ya bada sadaka yasa a mata addu'a ita da Ramadhan. Da yake shi kan babu notika ɗaurarru maimakon ya fahimci akwai matsala sai ya kama dariya yana yana faɗin.
        “Ƴar nema taji daɗin gidan gwamnati bata son suyi shekara biyar kawai. Indai addu'a ce kin tara kin samu, yau kaf almajiran dake garin hutawa saina bisu kowacce tsangaya na tattare da malamansu sun saka rokon ALLAH, dan nima inason ku koma hawa na biyun ai. Amma Raudha ya kamata kima mijinki magana ko ministan bada kuɗin fansho ya bani mana. Zamannan ya isheni haka kinga wannan sarautar ba wani kuɗi ake samu ba sai uban fama da rawani da zazzare ido a fada. Ni badan ma kar hakimi yace na raina karamcinsa ba da wlhy tuni na ajiye. Ni kuma yan kuɗina kullum kasa suke, dan ma ALLAH ya taimakeni wanda Ƴaƴan Larai suka sata an ganosu ai da yanzu hawan jini ya shanye muku ni.
     Murmushi Raudha tayi tana share hawaye. “Karka damu Abbah insha ALLAH zan san abinyi. Amma nidai gara kayi haƙuri ka cigaba da zuwa gidan hakimin”.
     “To ai duk yanda kikace haka za'ai uwata farar haihuwa farar aniya your excellency. Insha ALLAH sai kunyi goma indai mulkin NAYA ne”.
    Dariya ta ƙyalƙyale da shi babu shiri dan ya bata dariya sosai. Da ga haka sukai sallama ta ajiye wayar. Bargo ta kara ja har kanta dan wani irin sanyi mai ratsa ƙashi takeji. Ga ƙasusuwan ta kamar ana mata daka a kansu. Saboda zazzaɓin yau ko lecture ɗin karshe bata zaunaba ta gudo gida. Sai dai ta iske Bilkisu bata dawo ba. Haka shima mai gayya mai aikin da rabon dama ta sakasa a ido tun randa yay mata murzar ƴan bori. Dan ko zaune take a falo da taji shigowar motocinsa take shigewa. Ta katange duk wani abinda zai haɗasu a inuwa ɗaya saboda kare mutuncinta da nashi. Tun kusan satin baya take tunanin yanda zata fara masa addu'oin warware sihiri, idan ma shine tare da shi sai dai bata san ta hanyar da zata bashi yasha ba tunda baicin abincin gidan yanzu sai yaso. Hakan yasa ta haƙura ta barma ALLAH komai ya kawo musu mafita.
     Barcine ya ɗan figeta da sam bama daɗi yake mata ba. Dan har a cikinsa tanajin ciwon dake nukurkusarta. Bude ƙofar ya sakata farkawa aɗan razane...........✍
     


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 58_*


..........A hankali ta saki numfashi tare da nannauyar ajiyar zuciya ganin Bilkisu ce ba wanda take fargabar haɗuwar da shi ba ko'a hanya bare a cikin ɗaki da ga ita sai shi. Zama Bilkisu tai kusa da ita tana kai hannu a goshinta. “Aunty Lafiya kuwa kika dawo da w....”
     Maganar tata ta maƙale jin jikin Raudha da zafi. “Ya salam baki da lafiya yauma ko? Dan ALLAH ki yarda muje ko cikin clinic ɗin gidan nanne inma bazamu je wajan Mommyn Jabeer ɗin ba. Aunty wai zaki cigaba da cutar da kankine akan Yaya Ramadhan ne? Kin hana na faɗama kosu Anne halin da kuke ciki, ni kaina ɓoyemin abubuwa da yawa kikeyi wlhy. Harga ALLAH nidai na gaji da shurun nan da kika dabaibayeni da haɗani da ALLAH akan nayi”.
       Murmushi Raudha tayi tana haɗiye hawayen dake son zubo mata. Ta tashi zaune cike da ƙarfin hali ta kamo hanun Bilkisu cikin nata. “Aunty B kiyi haƙuri dan ALLAH, ban hanaki gayama su Anne bane sai dan yanda kike kallon matsalar ba haka take ba. Aiki ne kawai yay masa yawa, sannan ni babu wani abu na rashin daɗi dake tsakanina da shi, kawai dan ba zaman gidan yake kamar da ba saboda ayyuka yasa kike ganin akwai matsalane. Kinga babu dalilin kai ƙara akan laifin da babu shi aunty. Nasan kina ganin kamar auren nan nasane cutarwa a gareni shiyyasa. Dan ALLAH kibar damuwa ALLAH ni banajin komai akan hakan duk da nasan dole ne naji kishi matsayina na matarsa. Amma karki manta Aunty ALLAH ya bashi damar yayi huɗu, a addinance ma da biyu aka fara, sannan uku, sannan huɗu. Sannan a yanayin da Ya Ramadhan ke ciki dama ya kamata ace yanada mace mai ilimi da zata jagoranci wasu abubuwa na mulkinsa bawai irina da iyakata secondary ba kuma mai ƙarancin shekaru. Karki manta aunty yanzufa nake shekara ta shatara kawai a duniya, koba komai kuwa Aynah nada kusan ashirin da tara ko talatin da ɗaya ko fin hakan ma, sannan tayi ilimi mai zurfi daga ƙasar NAYA har wajenta. Tako ina ta cancanci zama matarsa koda nauyin al'umma dake a kansa”.
      “Humm Raudha sam ban gamsu da wannan bayanin naki ba. Babu ruwan hankali da ƙarancin shekaru, hakama babu ruwan sanin yakamata da ilimi. Mutane nawane a zamanin da basuyi ilimin boko ba amma sunada basirar tsara abinda ko professor na yanzu bai iya tsarawa ba. Kai har a wannan zamanin akwai wanda basuyi ilimin boko ba amma wlhy idan sukai miki wani abun sai kinsha mamaki. Hakama shekaru, shekaru baga kowa suke taka rawar hankali ba ga mai su. Zakiga mutum da shekarun manya amma idan yana tafka miki baranɓarama ke kyace ɗan goma sha ne. Kuma kiga karamin yaro na gyara masa. So ni a tawa mahangar banga ta inda Aynah zata taimaki Brother ba wlhy. Ƴar uwatace ita kuma jinina, amma bazan ɓoye miki cewar inaji a raina akwai manufa acinkin wannan al'amarin ba Raudha. kuma insha ALLAH bazan gajiyaba wajen ganin na daƙile hakan sai dai in ƙaddararsa ce zama da ita”.
   Tana gama faɗa ta mike ta fita hawaye na sakko mata a fuska. Da kallo kawai Raudha ta bita sai itama ta fashe da kuka. Sai da tayi mai isarta sannan ta mike ta shiga toilet ta wanko fuskarta....

(ALLAH ka bamu ikon cinye jarabawa a duk yanda tazo mana🙏🏻😭).

*______________★_____________*

          A ɓangaren su Gimbiya Su'adah kuwa shirin biki suke na ƴaƴan gata, dan a wannan gaɓar ko auren Lubnah da Bilkisu bata bama muhimmanci ba kamar na Ramadhan da Ayna'u. Babu abinda zuciyarta ke raya mata sai cewar zata haɗa cikar birinta da maido ɗanta ƙarƙashin umarninta ta kuma rabashi da wadda ta zame mata ƙayar kifi a maƙoshi badan ta taɓa mata wani laifi ba ko kuskure.
      Hatta da Ramadhan yanzu wani gata take masa na fitar hankali ita da su fulani da uwar gayya Addah Asmah. Baya iya jera sati baizo gidan ba a sace. Takai yanzu ko sashen su Anne baya shiga sai dai suji labarin yazo a bakin Basma. Hatta yin waya ya rage dasu, komansa gimbiya Su'adah. Ko abu ya shige masa akan harkar mulki maimakon kiran Bappi da yakeyi ko Anne a da sai ya kira Gimbiya Su'adah yanzun. A mafi yawan lokuta shawarar tata bata haifar da ɗa mai ido a garesa. Dan kuwa dai gadarace kawai da son nuna isa take ɗorasa akai, ALLAH ne kawai ke taimakonsa da in yay maganar da Cos sai yay saurin faɗama Bappi shi kuma ya gyara, wani lokacin idan Bappi ya kirasa yace kar ai kaza ɗin nan kaza ya kamata ayi har haushi yakeji, ya dinga ƙunkuni kenan yana cika yana batsewar fushi. Idan kaga haƙoransa a waje yanzu to tare yake da su gimbiya Su'adah. Aynah kam kamar yanda bokan Adda Asmah ya faɗa mata a ɓoyeta kar Ramadhan ya ganta har sai an kaita gidan gwamnati haka akai, sai suka fake da cewar gyaran jiki ake mata, amma a zahiri umarnin boka suke bi, dan ya tabbatar musu inhar Ramadhan yay ido huɗu da Aynah kafin aure duk wani sihirin jikinsa sai ya warware.
    Game da Raudha kuwa a yanzu basu da lokacinta, dan su tunaninsu sun gama da shafinta lokacin komawarta gidansu kawai suke jira. Shiyyasa ko bibiyar lamarinta basa waniyi gaba ɗayansu.

        Mutane har yanzu basu farga da halin da Ramadhan ɗin ke ciki ba, sai dai yanayinsa na kullum fuska a cunkushe yanzu kansa wasu yin kananun magana. Ƴan adawa kuma suka samu na suka a garesa da sake dawo da furicin nan na mai girman kai garesa.

      Pa da duk abinda ake a gidan ya saka ido badan baya cikin damuwa da halin da ɗansa yake a ciki ba. Ya barine kawai azo gaɓar da gimbiya Su'adah zata gane kurenta. Sai dai a yanzu bita da ƙullin daya shirya musu akan shirin da suke gagarumi na auren ne. Dan ko events an haɗa yakai kala goma, sanin Taura family ba'a wannan almabazaranci sai suka fake da cewar duk a gidansu amarya aka ɗauki komai. Lokacin da gimbiya Su'adah tazoma Pa da zancen dariya sosai abin ya bashi. Amma sai ya gimtse kayarsa yace ALLAH ya bada sa'a.
     Daɗine ya kama gimbiya Su'adah, dan gani take yanzu fa kamar ta fara samun kan Pa ɗin a dalilin turaren da Adda Asmah ta kawo mata tace tai amfani da shi a duk sanda zataje gareta. Dukan wata bukatarta sai ya amsa babu musu sai ma shakkarta da zai dingayi. Murmushi tai tana ficewa cike da tafiyar takama. A ranta kuwa sakama Addah Asmah albarka take da yaba mata. Dan ta tabbatar wannan turare shike taimaka mata wajen hawa kan Pa ɗin yanzu a yanda takeso. Amma da tasan bata isaba indai wannan uban kafiyar ne da taurin kai.
    Bayan ficewarta nannauyan numfashi ya sauke da girgiza kansa, sai kuma ya saki murmushi tausayin ɗansa na ƙara ratsa masa zuciya. Mikewa yay ya fice sashen mahaifansa. Acan ya samu har su Yafendo suna hirarsu cike da farin ciki kamar yanda suka saba.
     Bappi dake shan fura ya ɗan tsura masa idanu cike da nazarin ɗan nasa. Sai kuma ya ɗauke kansa. Ita kanta Anne idanun nata a kansa suke, dan tun shigowarsa ta fahimci akwai damuwa tattare da shi. Bayan ya gaishesu Inna ke faɗin, “Bashari lafiya kuwa na ganka kamar mai damuwa?”.
     Ɗan murmushi yay mata yana furzar da huci. Sai kuma ya gyara zamansa sosai yana fuskantarsu. “Lafiya lau Inna, kawai nazo nayi magana da ku ne in ba damuwa”.
    Yafendo tace, “Faɗi kanka tsaye Bashari mike faruwa?”.
     Jin Anne da Bappi basuce komai ba ya sashi dubansu, sai dai yanda suka maida hankalinsu garesa suma ya sashi sauke ajiyar zuya. “Ba komai bane dama akan Ramadhan ne da wannan auren nasa.”
       “Ba mun wuce wannan babin ba mi kuma ya faru?”.
Bappi ya faɗa yana kallonsa fuska a tsuke.
      “Kayi haƙuri Bappah, bawai na dawo da hanun agogo baya baneba. Kawai ina son muyi wani abune dan ALLAH saboda wani nazari dana zauna nayi.” batare da ya jira cewarsa ba ya cigaba da faɗin. “Ni da ku duk munsan waye Ramadhan da kuma kammu, amma jama'ar gari da Ramadhan ke mulka har yanzu basu gama sanin waye shi ba. Auren Ramadhan da yarinyar nan Ameenatu dududu watanni na bakwai muke a ciki yanzu, ko shekara bamuyiba. Aurene da yasha soke-soke da kace nace a idanun mutane da bakunansu dalilin tazarar da su suke hange da mu babu ita a zukatanmu. Shin ya kuke tunani idan akace yanzu an fiddo maganar ƙara auren Ramadhan wa duniya, kuma da ɗiya irinsa mai irin matsayinsa kuma ƴar uwarsa sannan mai dukkan kishiyar abinda akai cece kuce Ameenatu bata da shi a baya?. Dama ance munyi haɗin auren Ameenatune da Ramadhan saboda mu gyara masa siyasarsa ace yana son talaka gashi harya auri ɗiyar cikinsu. To yanzu wannan auren nasa da har yanzu bamu gama sanin kansaba ake masa shiri na tashin hankali bama tunanin cikkakkiyar amsace ga ƴan ƙasa da abokan hamayya?. Ba ina fargar damu bane dan tunanin kar Ramadhan ya rasa kujera a zaɓe nagaba. Ina fargar damune domun kare mutuncin kammu dana Ameenatu yarinyar kirki da batajiba bata ganiba, hakama ina kare kunyar da zamu daurama bayin ALLAH da suka goya da bayanmu suka kuma tabbatar da tsarkake abinda mukayin badan sakamakon mu a hanunsu yake ba, sai dan bana son mu cire hope ɗin mutane akan mulkin Ramadhan. A yanzu Su'adah tazomin da wannan invitation card ɗin” ya ajiye iv ɗin gaban Bappi. “Bappah ka dubafa ka gani, events kusan goma ne anan aka shirya wanda ake fatan duniya ta gani ta shaida za'ama Ramadhan auren gata bama ƙasar NAYA kaɗai ba. Bayan kuma mu a wannan gidan duk bama hakan tun auren ƴaƴanmu na farko, sannan ko'a yanzun ma bawai shine kaɗai auren da za'a ɗaura ɗin ba”.
       Tsitt falon yay bayan Pa yayi shiru. Sai dai tsananin ɓacin rai ya bayyana ga fiskokinsu bayan duk sun ga katin da tarin bidi'oin dake a ciki. Anne da idanunta suka fara cika da ƙwalla tace, “Anya kuwa Ramadhan ma yana cikin hayyacinsa? Bana son zargi sam a rayuwata ballema dana san dai Su'adah mahaifiyarsa ce babu yanda za'ai ta cutar da shi....”
      Murmushi Pa yayi, cikin kunar rai yace, “Idan ita bata cutar da shi ba ai anyi amfani da ita da son zuciyarta an cutar da shi Anne. Bara yau na fito na sanar muku gaskiyar lamari akwai sihiri tattare da Ramadhan, sam abinda yakeyi ba'a cikin hankalinsa yakeba..”
        Salllami falon ya ɗauka da sautin kukan su Yafendo. Yayinda Bappi ya tsurama ɗan nasa ido duk da shima ya jima yana wannan zargin. Pa yaja numfashi mai cike da takaici. “Karku wani damu kanku ni hakan yamun daɗi ai, maybe a dalilinsa Su'adah zata dawo cikin hankalinta tasan abinda ke mata ciwo. Na jima da fahimtar hakan amma bana son kowa ya nemawa Ramadhan magani dan ALLAH har sai anzo gaɓar daya dace...”
        Da sauri Inna ta katse Pa, “Baka da hankali Bashari. Taya za'abar yaro a baƙar inuwar sihiri? Kenanfa kusan duk abinda yakeyi baima san yanai ba! Kai nifa ina mamakin canjawar yaron nan lokaci guda. Har takai yanzu zaizo gidan nan amma bamu sani ba. Barinsa cikin wannan tashin hankalin ai matsalane, sai ya iya shafar mulkin da yake kai ko kai baka san hakaba”.
     Karon farko Bappi ya saki murmushi, cikin takaici yace, “Sadiya kenan wannan na nawa kuma. Badan ALLAH ya bashi chief of staffs na ƙwarai mai amana da tsoron ALLAH ba ai da tuni halin da Ramadhan ke ciki ya bayyana a cikin mulkin nasa. ALLAH dai ya ƙyauta. Ni yanzu inaga kai Basheer faɗi dalilinka muji, idan mai yuwuwane saimu riƙe. Idan bazai yuwuba a sake shawara”.
      Kai Pa ya jinjina masa. “Bappi abinda yasa na roƙeku kar'a nema masa magani saboda dalilai uku ne zuwa biyu. Na farko ina son Su'adah ta gane kuskurenta akan Ameenatu, na biyu ina son ta gane wacece ƴar uwarta Asma'u. Na ƙarahen da bakinta nake son ta bayyana dana saninta a kansa. Dan haka ina roƙonku yin wannan aure a sirrance. A ɗaurashi a sirrance iya wakilansa da wakilan yarinyar. Akuma hana kowanne biki da suka shirya da an ɗaura aure ya dauka matarsa su wuce kawai, sauran dokokina a kansa sai bayan ɗaurin auren ne”.
     Shiru falon yayi kowa na nazari, bayan shuɗewar wasu mintuna Bappi ya fara jinjina kansa alamar gamsuwa. “Kamar hakan duk yayi gaskiya. Sai dai Jannatu mi kuke gani ku?”.
       Anne dake ta danne kukan dake taso mata ta haɗiye da ƙyar. “Dattijo hukuncinka ai namune. ALLAH yasa haka shine mafi alkairi”.
    Da amin duk suka amsa. Daga haka suka cigaba da tattauna abinda ya dace............✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 59_*


.........Bayan kwanaki biyar da wannan magana Bappi ya shirya da kansa yaje har masarautar Bina sukai magana da mai-martaba, sai dai bai sanar da shi ainahin dalilinsu game da sihiri dake tare da Ramadhan ba. Ya nuna masa suyi hakanne kodan gudun abinda zaije ya dawo ga mutanen ƙasa akan kallo da fasararar da zasuma al'amarin. Da yake mutum ne mai fahimta kuma yayi matukar yarda da Bappi a take ya amince ya kuma gamsu. Sai dai ya tsuke bakinsa ko fulani bai tunkara da zancen ba.

    Haka shirye-shirye ya cigaba da gudana har biki ya rage baifi saura kwanaki takwas ba. Su gimbiya Su'adah nata shirye-shiryen fara sanarwa a gidajen redio da television Pa ya dakatar. Cikin ɓacin rai ta nema dalili yace idan lokaci yayi zata sani ai. Acan bangaren mai-martaba ma ya dakatar da Fulani da Adda Asmah, dan koda mijinta ya tsawatar shi da yake ya zama mijin tace batajiba, saima tujara data zuba masa gwargwadon iyawa shiko ya sanarma mai-martaba da dama shine ya bashi umarnin shima.
     Wannan abu ya cuɗa musu zuciya. Babu kunya Gimbiya Su'adah harda kai karar Pa gaban su Bappi. Anne zatai magana Bappi ya girgiza mata kai, yace Gimbiya Su'adah taje zaiyo magana da Pa. Sai dai har yau da ya rage saura kwanaki biyar basuji komai daga bakin Bappin da suka san zai iya yiwa har mai-martaba magana ya janye sharaɗin daya sharɗanta akan duk wanda yay wani abu babu umarninsu a bakin auren Fulani ne. Tashin hankali kennan da ba'a saka masa rana. Domin kuwa wannan furuci na mai-martaba ya matuƙar birkita kowa a cikinsu har Ramadhan ɗin kansa da Gimbiya Su'adah ta kira a waya ta sanarma komai lokacin yana office. Da wannan ɓacin ran ya tabbatar mata zai shigo gidan da dare dama Bappi nata damunsa da son ganinsa ya sharesa.
       
     
       *_GOVERNMENT HOUSE_*..

Yau kam da wuri ya shigo gida saboda son zuwa Taura house da anyi magrib. Raudha najin shigowar motocinsa kuwa ta mike daga falo inda suke zaune suna tattauna tsare-tsaren bikin Bilkisu da ayanzu ta zame mata ƙawa dan dama bata da su sai school mate kuma ita iyakarta a gaisa babu aminiya. Saurin riƙota Bilkiau tai ta zaunar. “Ni banga amfanin wannan wasan ɓuyan da kike da shi ba, kiyi zamanki dan ALLAH karma ya samu kafar rainaki dan zai ƙara aure ko ya zata wani kishinsa kike ma”.
     Kamar Raudha zatai kuka sai dai komai batace ba ta koma ta zauna ɗin. A haka Ramadhan ya shigo ya samesu.
Akan Raudha ko ya fara sauke idanunsa, itama anyi sa'a kallon nasa take. Lokaci ɗaya zukatansu suka harba cikin bugu mai tsanani. Raudha da taga ya rame mata a ido sosai sai dai ya ƙara haske da ƙyau ta fara janye nata idanun fuskarta na nuna wani yanayi mai wajalar fassara. Shiko ido ya ɗan tsura mata tamkar mai nazari ko kuma yau ya fara ganinta. Sosai ya ga ta ƙara masa girma da cika. Dan duk da ciwo da take fama da shi a watan nan baki ɗaya saita kara buɗewa tai ƙiba da girma. Sannan komai nata ya ƙara girma ga haske tayi sosai mai tafe da wani sirrintaccen ƙyawu da duk hassadar mai hassada bai isa mata kallo guda ya ɗauke ido ba.
       Kansa ne yaji ya sara masa. Yay saurin janye idanun a kasalance, sai kuma yay ƙoƙarin barin wajen kamar da ƴar sassarfa dan ko gaisuwar da Bilkisu ke masa bai amsa ba. Ƙofar ya maida ya rufe tare da jingina a jikinta lokcin da ya iso bedroom ɗin nasa. Ya ja ajiyar zuciya da sauke nanauyan numfashi idanunsa har sun kaɗa sunyi jajur. Ya jima a wajen tsaye kafin yaja kafafunsa da ƙyar zuwa toilet, agogon kawai ya cire ya sakarma kansa shower. Sai da yay sharkaf daga shi har kayan dake jikinsa sannan ya ragesu yay wanka....

      Raudha da dama a cikin yanayi. dauriya take zaune a wajen ta miƙe da gudu tabar wajen hanunta toshe da bakinta. Da sauri Bilkisu ta bita har cikin toilet data shiga. Amai ta shiga kwarawa tamkar zata amayar da hanjin cikinta. Hankalin Bilkisu ya sake ɗagawa matuƙa ta riƙe Raudha. Sai da komai data ɗanci ya fita tas sannan aka samu lafiya. Bilkisu ta tamaka mata ta gyara jikinta da wajen suka fito tana jera mata sannu.
      Cikin sauke numfashi a wahale tana kaiwa kwance ta ce, “Kai aunty B ƙamshin turare nan na Yaya babu daɗi”.
       Sosai Bilkisu ta zaro idanu waje, sai kuma tace, “Kutt Aunty Raudha ƙamshin _Boucheron_ ɗinne baida daɗi? Anya kuwa kin shaka dai-dai?”.
      “Ni wlhy lafiya lau na shaƙa, kuma dai tun yashe muke zaune a falon na ƙamshin komai bai dameni ba sai daya shigo ne ƙamshin turaren nan mai kama da ka.....”
     Da sauri Bilkisu ta ruƙe mata hannu tana dariya, “Uhmm to lallai Taura grandchild bai zo da wasa ba.”
    Sam Raudha ba wani fahimtarta tai ba. Bakuma tabuƙaci ba'asin mganar ba tama lumshe ido dan barci ke ɗan figarta ga kanta daya fara ciwo.

*_TAURA HOUSE_*

          Cikin matuƙar bayyanar tashin hankali Ramadhan ya ɗago yana duban Bappi da ya gama masa jawabi. A take idonsa ya rufe yama manta da wanda yake tare.
      “Gaskiya bazai yuwuba Bappi, duk ma wada yake tunanin sharɗanta hakan ya janye dan ba yarda zanyi ba.  Tayama kamar ni za'ace a ɗaura aurena a sirri sai kace wani funafunci? Na muku biyayya na amince da zabinku kukai yanda kuke so nima dole a barni nai yanda nake so akan nawa zaɓin. Sannan maganar events banajin akwai ɗaya da za'a janye a ciki, ba sai kun dinga nuna hassadarku da adawa aka dangin mahaifiyata zan san kun isa da ni b.....”
      Ji kake “tauuuu!!” Wani bazafaren mari ya sauka a saman kuncin Ramadhan har sai da ya kifa kamar zai faɗi. Pa da yake a fusace zai ƙara masa Bappi ya dakatar da shi. “No Basheer barsa barsa. Kai Ramadhan mu kake faɗama muna adawa da hassada da dangin uwarka!!”.
       Har yanzu hanunsa a saman kuncinsa dan da gaske marin yay matuƙar ratashi. Cikin ƙanƙanin lokaci ya sake birkicewa gaba ɗaya, idanunsa suka rufe ruf. “Idan ba hassada ba a gayamin mi kuke musu? Kun rabani da su komai sai ku, tun ina 2years a rabani da uwata tayi kawaici ta bar muku amma hakan baisa kunga haƙurinta da kawaicinta ba. To wlhy daga yau ku sani ta ƙare, idan kuma kunce a'a to muzuba mu gani!!”.
    Ya ƙare maganar cikin ƙaraji da nufar hanyar fita.
          Da sauri Pa ya miƙe cikin wani irin fushi yay kansa shima. Sai da Bappi yay azamar riƙo hanunsa yana girgiza masa kai. Duk yanda Pa yaso yin magana Bappi ya hana shi, ganin yanda jikinsama ke rawa sai kawai ya rungumesa yana shafa bayansa murmushi na subuce masa na tsantsar zafin da yakeji a ransa. Da wahala kaga fushin Bappi. Mutum ne mai yawan fara'a da dattako, akoda yaushe fuskarsa ɗauke take da murmushi. Duk abinda kaga faɗansa akai an ƙuresane.

*_GOVERNMENT HOUSE_*

        Baƙaramin faɗuwa gaban Raudha dake zaune a gado tana karatu yayi ba. Babu haske mai yawa a ɗakin. ta zabi tai zaman karatu ne kafin lokacin da zata tashi ganawa da UBANGIJI ne. Ta zaro manyan idanunta akan Ramadhan daya shigo a tsananin fusace. “Innalillahi.....” har ƙarshe take ambata a jajjere harya iso inda take, wata irin muguwar damƙa yayma gashinta dake daure a tsakkiyar kai da hanunsa....
       “K!! Har kin isa saboda aurenki a hanani yin yanda nakeso akan auren wadda zanyi? Wacece ke? Mikika taka?!.. Wato kinje kin kai munafunci garesu dansu hanani, to ai in gaya miki babu ubanda ya isa. Yau zan tabbatar miki ke ɗin ƙaramar mara kunyace kuwa wlhy...”
      Kuka sosai Raudha keji jikinta na tsananin rawa. Ta shiga yarfa hannayenta duka biyu kuka mai ƙarfi na ƙwace mata ganin yana kunce belt ɗin wandon jeans ɗin jikinsa. Abu biyu ta kawo a ranta. Duka ko abinda yay mata ranar, dan haka tai yun ƙurin ceto rayuwarta sai dai hakan ya gagara. Dan tuni ya damƙota ya jefa saman gadon har sai da bayanta ya amsa dan azaba.......

★★★

     Ihun Raudha ya matukar tada hankalin Bilkisu da ke ɗaki har barci ya fara daukarta. Ta fito a waje zuwa ɗakin sai dai ta samesa a kulle. Bugawa ta shigayi tana kiran sunan Raudha. Sai dai wata shegiyan ashariya da batasan Yayan nasu ya iyaba sai yau ya mulmulo mata daga ciki. Ai babu shiri tabar wajen a guje. Sai dai koda ta koma ɗaki wayar Anne ta kira. Tana dagawa ta fashe mata da kuka da fara zayyana mata abinda ta sani.

     Sosai hankalin Anne da Bappi ya tashi, dan sun san ba kamar yanda Bilkisun ke tunanin Ramadhan dukan Raudha yake ba. Su sun san illolin daya dingama Amnah idan irin wannan ɓacin ran mai tsanani ya riskesa. sai dai suna ƙoƙarin rufe hakan ga kanensa idan ka cire Mardiyya da Safina dakan san wasu a wani lokutan.
       Hankali a tashe tsoffi nan suka baro gida a daren nan tare da Dr Hauwa da suka taso itama ta waya suka nufo government house. Dan Dr Hauwa ce ma da kanta taja motar.

     Lokacin da suka iso Ramadhan ya riga ya gama illata Raudha har jini ya ɓalle mata. Tunda ya fito a hargitse Bilkisu na son shiga tanajin tsoro. A durkushe suka sameta bakin ƙofar tana kuka. Tana ganinsu ta faɗa jikin Anne ta rungumeta.
      “Anne ya kasheta, wlhy ya kasheta Anne!!”.
     A tsawace Bappi yace, “Yana ina!?”.
Cikin kuka Bilkisu ta sanar masa ya koma dakinsa. Hakan ya bama Anne da Dr Hauwa damar shiga. Bappi kuma ya tisa keyar Bilkisu ta nuna masa bedroom ɗin Ramadhan.

       Hankalin Dr Hauwa da Anne ya tashi a yanayin da suka sami Raudha, dan haka babu wani kace nace Dr Hauwa ta fara ƙoƙarin ganin ta tsaida jinin. Tsahon lokaci ta ɗauka da taimakon Anne dake fama da tsufanta suka samu nasarar hakan.
      “Anne bazai yuwu mu barta anan ba. Inaga muje da ita can wajenki dan tana buƙatar kulawa mai tsanani yarinyar nan a wannan gaɓar tunda Alhmdllhi cikin dake jikin nata mun samu ya tsaya. Da dai anyi dilay kam da labarin da ake ba wannan bane”.
     Wasu hawayene masu sanyi suka sakko akan fuskar Anne. Farin ciki da cikin Raudha, da damuwar halin da jikanta yake sakamakon son zuciyar mahaifiyarsa.

     A can kuwa ɗakin Ramadhan shigar Bappi tayi dai-dai da fitowarsa wanka, ya sauke towel ɗin da yake goge fusakarsa zuwa suma kawai yaji saukar mari haggu da dama. Gaba ɗaya wutar kansa ta ɗauke ganin wanda ya maresan. Bappi, abinda bai taɓa faruwa ba ko a tarihin ƙuruciya. Dan ko laifi yayi yana yaro sai dai Anne ko Pa su dakesa amma ba Bappi ba. A karshe ma Bappin ke komawa lallashinsa da masa nasiha. Amma sai gashi yau da girmansa. Shekara dai-ɗai har 36 a duniya kakan nasa ya rufe ido ya yarfata masa maruka har biyu bayan wanda Pa ya masa ɗazun....
        “Ramadhan ka kiyayi haduwata da kai wlhy!!”. Bappi ya faɗa cikin gargaɗi da ke nuna tabbatarwa. Kafin yay wani yunkuri kuma ya juya yay ficewarsa.........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode. 60_*


.........*_TAURA HOUSE_*

         Tunda suka baro government house a sirrance da Raudha kai tsaye Taura house suka nufo. sai dai anan ɗin ma dai babu wanda yasan da dawowar tasu kamar yanda kowa bai san da fitarsu ba. Sake dukufa Dr Hauwa tai akan Raudha har sai da ta tabbatar komai ya daidaita. Abin tausayi har ɗinki akai mata saboda bidirin da Ramadhan yay a jikinta. Hakan ya sake kona zuciyar Bappi da Anne sai dai babu wanda ya iya cewa komai har Dr Hauwa ta kammala aikinta ta wuce.
     Barci Raudha take saboda allurar barcin da Dr Hauwa tai mata. Dan haka Bilkisu ta zauna ta zayyanema Anne komai data sani har wanda Raudha ma bata san ta sani ɗin ba. Anne harda hawaye tausayin Raudha mai tsanani na cin zuciyarta. Koba komai sune suka jefata a wannan masifar. Maybe dasun barta ta aura dai-dai da ita da duk hakan bai faruba. Sai dai kuma ƙaddara ta riga fata inji masu iya magana. Sannan kuma babu mai sawa ko hanawa daga abinda yazo a littafin ƙaddarar wani bawa koda yana kalon kansa matsayin SILA.

*_WASHE GARI_*
 
          Raudha ta jima bata farka ba har kusan tara, koda ta farka ɗin kuma Anne fidda kunya tai ta taimaka mata sosai kodan ɗinkin da akai mata. Ga Dr Hauwa ta tabbatar musu kar ai wasa da wani motsin Raudha mai karfi saboda cikinta a ɗofane yake. Hasalima bed rest shi tafi bukata fiye da komai a yanzun.
           Tabbas abu biyu da Raudha tayi ya matukar birge Anne da Bappi. Na farko tambayar duniya sun mata akan abinda ke tsakaninta da Ramadhan ta keƙashe ƙasa ta dage akan babu komai. Tushen abinda ya faru tsakaninta da shi a jiya harya doke ta (dan duka suka danganta abun saboda alkunya da kawaici irin nasu) amma sai Raudha tace wai faɗuwa tai a toilet. Batasan su da idonsu sukaje sukaga halin da take a ciki ba. (Saboda sun ɓoye mata cewar Bilkisu ce ta kaita asibiti suma acan suka amso ta). Na uku tunda ta tashi babu wanda yaga ko ɗigon hawayenta alamar ta dake, wannan ya sakama Anne ƙwarin gwiwar cewar lokaci yayi da zatai training ɗin Raudha a bigiren da sai Gimbiya Su'adah da shaiɗanunta sunyi dana sani. Ramadhan kuwa zai matuƙar gane kuskurensa, ba ita zata hukuntashi ba Raudha ce da kanta zata hukunta shi.

Hhhhh ashe akwai sabon show😋😉🤣.

*____★____★_____★_____★_____*

           Tsahon kwanaki uku Raudha na a Taura house babu wanda ya sani sai Bilkisu da Pa da su Anne. Koda Gimbiya Su'adah taga Bilkisu bataji komai ba tunda tasan dama tana shirin dawowa gida ai. Zuwa yau baƙi sun fara isowa daga masarautar su gimbiya Su'adah. Hakama a bangaren sauran matan gidan tunda kowa zai aurar da ɗa. Daga Taura ma dai wasu sun iso sai dai maza ne.
    Babu wanda ya sake jin labarin Ramadhan babu kuma wanda ya bibiyesa, a kwanaki ukun nan ma ko a labarai sai dai kaji ance Shugaban kasa Ramadhan ya kaddamar da kaza da yawun wane. Amma shi ko sau ɗaya ba'a nunasa ba sai a yau da kowa yasan za'a tafi hutu na ƙarshen shekara da Christmas. Kuma kakakin shugaban ƙasa ya sanar a Taura house shugaban ƙasa zaiyi hutun nasa baki daya.
        Hankalin Adda Asmah ya tashi matuka, musamman data kira bokanta yace sam karta yarda. Ita da suka gama cin burin kai Aynah government house kai tsaya ya Ramadhan ɗin zai musu haka, ya tabbatar mata ajiye Aynah a Taura house bazai taɓa haifar musu ɗa mai ido ba. Garama tayi duk yanda za'ai ta gyara barnar. Zuwa dare kuma tazo tare da Aynah zai mata wankan magani na ƙarshe da shine sirrin mallakar Ramadhan da duk ma wanda zai raɓesa, zai koma baijin magana ko umarnin kowa sai nata ita kaɗai Aina'u.
        A rikice tai kiran Number Gimbuya Su'adah. Ita kanta gimbiya Su'adah ranta ya baci dan yau bata maida hankali akan television ba balle tasan da labarin. Tana can suna tafka rigima da Pa akan kofa dinner sai sunyi har guda uku idan ance sauran an hanasu. Shi kuma yace isar da bataiba kenan.
     Ramadhan ta shiga nema, dan rabonta da shi yau kwana uku kenan tun randa ta kunna zuciyarsa akan kiran daya sanar mata su Bappi sun masa. Maimakon hankalinta ya tashi matsayinta na uwa ta nemesa sai ta share da cewar yana lafiya shiyyasa ko kuma aikin office ne ya rikesa.
         A lokacin kwance yake yana barci, dan tunda aka baro Raudha daga gidan ya tsinta kansa a wani irin yanayi mai matukar wahalar fassara a garesa. Ya rasa mike masa daɗi mi kuma zai kama. Ransane a ɓace? Ko damuwa da halin daya jefa ƴar mutane? Kokuwa halin da ke shirin riskarsa na auren wadda shi kansa har yanzu baisan dalilin da yasa yake mata wannan mahaikacin son ba. Bisa lallabawar cos yake fita office. Sai dai baya wani jimawa yake dawowa gida. Kuma kullum ya shigo sai yaje ɗakin Raudha da mama ladi bata gajiya da gyarawa. Hatta jinin da Raudha ta zubar a wancan ranar idan bama faɗa maka akaiba bazaka sani ba. Yakanje ya kwanta a saman gadonta. Sai dai baya haɗa mintuna biyu kansa zai shiga sarawa da karfi har sai ya fito ya koma nasa.
     Kunnawar da Ginbiya Su'adah tai masa yau ma ya sakashi tashi cike da fusata. Yay azamar dafe kansa dake juya masa da karfi. Sai kuma ya mike yana kallon agogo. Ƙarfe kusan sha ɗaya na dare. Amma tsabar yanda yake jin zuciyarsa tuni ya fice cikin ɓadda kama dan bazai iya jira sai gobe da zai huce Taura house ɗin ba ma, yanda yake komai saika ɗauka ana controling nashi da remote ne, dukya birkice, baya gane komai sai abinda su gimbiya Su'adah sukace yayi. Maimakon ma ko a motane yay fitar sirrin kamar yanda yakeyi, sai kawai ya fice da ƙafa ta karamin gate da taimakon odilan ɗinsa da baida ikon hanashi yin hakan saboda akwana biyun nan sam baya gane kan shugaban ƙasa, baya son yace wani abu kuma ga wani game da hakan saboda gargaɗi da Ramadhan yaja masa mai ƙarfi akan yanda yake fitar sirri inhar ya bari wani ya sani bayan shi duk hukuncin daya zartar a kansa yay kuka da kansa kawai. Cab ya tare sai taura house.
      
        A dai-dai lokacin da Ramadhan ke nufar Taura house Adda Asmah ce da Aynah sun dawo daga gidan bokanta anyo mata wankan maganin mallaka. Sam batai tunanin haɗuwa da Ramadhan ba, shiyyasa ta yanke shawarar biyawa ta Taura House takai maganin da bokan ya bata akan gimbiya Su'ada tai turare da shi matsayin na rufa idon su Bappi akan events ɗin da suke sonyi. Sai dai a zahirin gaskiya ba hakan bane. Na rabata da Ramadhan ne baki ɗaya yanda zai koma karƙashin ikon ita Addah Asmah ɗin.
       Kusan a tare Ramadhan da su Addah Asmah suka iso Taura house. Sai dai shi ya rigasu shigowa saboda an tsaya buɗe musu gate shiko yay wuff ya shige yanda ko mai-gadi ma bai lura da shi ba. Kai tsaye falon hutawa na gimbiya Su'adah ya nufa ta baya kamar yanda ta sanar masa ya sameta a can. Ko zama baiyiba Addah Asmah da Aynah suma suka shigo kamar yanda Gimbiya Su'adah ta sanarma Adda Asmah itama ta sameta anan. Adda Asmah bata san Ramadhan zaizo taura house ba. Haka zalika gimbiya Su'adah batasan Adda Asmah na tare da Aynah ba tunda tasan dokar dake tsakanin kar Ramadhan da Aynah su haɗu sai bayan an ɗaura aure.......

*_Tofa dole na dara kafin na cigaba🤣😂🤣😂, wannan fa shine ana dara ga dare yayi🤣. Ga boka yace kar.....🤭😂bara dai kawai na tsuke bakina muga yaya wasan zai kaya to._*

      ★Wani irin ihu Adda Asmah da Ayna'u suka fasa a tare cikin tsantsar tashin hankali. Dan kuwa sallamar Aynah dake gaban Addah Asmah tayi dai-dai da ɗagowar Ramadhan saboda ƙofar falon da aka buɗe batare da yayi tunanin wani zai shigo musu ba.
      Ita kanta Gimbiya Su'adah dake ƙoƙarin kunna buner ta saka turaren hayakin magani da boka yace ta dinga sakawa a duk sanda Ramadhan yazo gareta ta saki tare da yin wani uban tsalle tana dafe ƙirji.
         “Innalillahi wa-inna'ilaihirraji'un. Allahumma ajirni fi musibati.....” Ramadhan ya ambato a jere saboda suna haɗa ido da Aynah gabansa yay wani irin mummunar faɗuwar da har sai da kansa ya sara. Hannu ya kai ya dafe kan saboda yanda ihunsu ke shiga masa har tsakkiyar kwakwkwararsa. Duk da kunne sa daya toshe ihun bai fasa shiga ba. Kai bama shi ba, hatta duk wanda yake kusa da sashen gimbiya Su'adah dole ne yaji tagwayen ihun nan.
      Pa ne ya fara shigowa a kiɗime. dan kamar yanda ya saba duk dare kafin ya kwanta sai ya zagaye gidan ya tabbatar da komai normal jininsa kuma ya motsa yauma hakance ta kasance. Yana ta wajen babban gate ɗin gidan baki ɗaya yaga shigowar Ramadhan. Duk da ya rufe fuskarsa da hular jacket ɗin jikinsa da facemask hakan bai hanashi shaidashi ba. Dan babu wata ɓadda kama da Ramadhan zaiyi bai gane abinsa ba. Shiru yay ransa fal al'ajab, bai gama dawowa hayyacinsa ba kuma sai ga motar su Adda Asmah ta danno kai. hakan ya sashi kiran Anne da Bappi da Yafendo a waya yace suzo dan ALLAH. Shi kuma ya biyo bayan su Addah Asmah ɗin.
      Takan kowa Pa bebiba tsakanin Aynah da Adda Asmah data zube ƙasa kamar wadda ma ta suma. Yakai ga ɗansa dake jujjuya kansa cikin tafukan hannunsa alamar akwai abunda ke faruwa da shi. A dai-dai nan su Anne ma suka iso, suma duk kan Ramadhan ɗin sukayi hankalinsu tashe. Sai kawai sukaji ya fasa wata gigitacciyar ƙara da duk wanda ke a gidan nan ƙarya yake yace bai jita ba.
    Innalillahi kawai suke ta ambato, Pa ya riko Ramadhan dake shirin kaiwa ƙasa ya ringumesa a jikinsa. Rawa sosai jikinsa keyi kamar mazari. Hakan yasa Bappi ma tallafawa suka riƙosa.
        “Basheer kafin attention ɗin kowa ya dawo nan ɗin mu fita da shi”.
     Shawarar Bappi Pa yabi, suka kama Ramadhan da har yanzu yake faman jujjuya kai sukai waje da shi, fitarsu kamar ƙyaftawar ido jama'ar gidan suka fara tururuwar shigowa falon a gurguje. Su kum ganin Adda Asmah kwance duk sai sukai kanta. Da wannan damar Anne da su Yafendo suka zame jikinsu suka bar falon.

         ★★
    “Ya ALLAHU miya faru? Suma yay?”.
Cewar Anne dake shigowa falon Bappi idonta akan Ramadhan da suka shimfiɗar a ƙasan carpet Pa na kokarin shafa masa ruwa. Kai kawai Bappi dake zaune kan Ramadhan ɗin a cinyarsa ya ɗaga mata. Wani nannauyan numfashi Ramadhan ya ja a fisge sai kuma ya sake riƙe kansa zai fasa ƙara Bappi ya rufe masa bakki.
      “Tabbas akwai matsala, inaga akwai lamarin azzaluman aljanun sihiri tare da shi”. Cewar Yafendo tana kuka. Da sauri Anne ta fita a ɗakin tana faɗin bara ta ɗakko alkur'ani. Bappi na kiranta tazo ta ɗakko na ɗakinsa bama taji ba harta fice. Zaune ta iske Raudha na karatun alkur'ani da alama sallar shafa'i da wutiri ta idar. Ai tama manta da batun bedrest da Raudha keyi ta kamo hanuntan. 
        “Ameenatu taso ga inda ake buƙatar karatun nan naki can.”
    Hankali tashe Raudha ta dakata, ganin Anne a firgice yasa batabi ba'asi ba ta mike kawi ta bita. Sanye take cikin dogon hijjab fari har ƙasa. Dan haka baka iya ganin komai nata sai fuska da tafukan hannu.........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode. 61-62_*


...........Wani irin tsargawa kanta yay ganin Ramadhan shimfiɗe a ƙasa Bappi ya toshe masa baki, ga Pa a kansa yana karatun suratul baqara. Tuni jikinta ya fara rawa. Ta matsa da sasaarfa takai duke gabansa cikin rufewar idon manta waɗanda suke a falon. “Ya ALLAHU na shiga uku ni Raudha Ya Ramadhan mike faruwa da kai haka?”.
         “Kinga Ameenatu yi hakuri baya cikin hayyacinsa yi masa karatun kawai”.
    Ai Bappi baima kai karshe ba ta fara karatun itama cikin suratul baqaran. Wata muguwar zabura ya kara yunkurowa zaiyi saboda masu karatun sun zama biyu, ga zazzaƙar murya da ALLAH ya azurta Raudha da ita inhar tana karatu komai taurin zuciyarka saika nutsu a saurare. Tun sunayi yana fisge-fisge har ya fara lafawa a hankali. “Idan ma mu an koremu ai akwai wanda suke tare da shi tun yana yaro”.
     Bakin Ramadhan ɗin ya faɗa a kausashe, amma a tabbaci bashi bane sai kuma ya fara sakin tari mai ƙarfi. Raudha da Pa basu dakataba suka cigaba da karatunsu sudai. Yayinda Anne ke duke gabansa tana rike da kansa ita da Bappi. Tsahon mintuna talatin suka sake kwashewa suna karatun kafin jikinsa yayi laƙwas. Duk da hakan Raudha bata dakata ba har sai da takai karshen suratul baqara lokacin agogo ke nuna karfe ɗaya da wasu mintuna na dare.

      Ta matuƙar birgesu, sun sake jin kaunarta mai tsanani da taya gudanjininsu murnar samunta matsayin mata uwar ƴaƴansa. Bayan ta rufe da addu'a suka shiga sanya mata albarka. Ita dai kanta a ƙasa tana sharar hawaye. babban burinta tasan miya kawo mijinta gidan a wannan halin? Yama akai yazo? Miya faru da shi?. Waɗan nan sune jerarrun tambayoyin dake mata yawo bisa kai. Sai dai ta kasa furtasu ga kowa.
       Anne da tasan lokacin barcin Raudhan ya gota cikin sanyin murya tace, “Ameenatu kije ki kwanta kinga kema fama kike da jikinki. Tunda Alhmdllhi da alama komai ya dai-daita barci ne ya ɗaukesa. Kamar Raudha zatace a'a sai kuma tay yunkurin mikewa domin bin umarnin Anne. Caraf taji an ruƙo mata hannu, bama ita kaɗai ba kowa a ɗakin sai da ya kalli hanun Ramadhan ɗin, kafin ya firta. “Ameenatu ruwa! Bani ruwa na sha inajin ƙishi”.
      A hankali yake maganar amma hakan bai hanasu jinsa ba. Raudha duk kunya ta isheta. Amma saita daure ta dauka goran ruwan dake kusa da Anne, a sanyaye tace, “Ga ruwan to buɗe idonka”.
      Bakinsa kawai ya buɗe mata yana ɗan girgiza kansa, kamar zata sake magana sai kuma Bappi ya dakatar da ita ta hanyar ɗago kan Ramadhan ɗin yanda zata iya zuba masa ruwan batare da ya cutar da shi ba. Duk da kunyar da takeji haka ta daure ta ɗora masa gorar a baki. Sai ko gashi yana zuƙarsa da yawa harya shanye. A hankali ta janye goran shi kuma ya ɗan buɗe idanunsa yana kallonta. “ALLAH yayi miki albarka”. Ya faɗa a hankali tare da maida idanunsa ya lumshe.
     Kusan atare duk suka amsa da amin tare da sauke ajiyar zuciya. banda Raudha datai kasa da kanta ta amsa a kan laɓɓa. Bappi ne ya basu umarnin zuwa su kwanta, shi kuma zai kwana da Ramadhan ɗin sugani ko zuwa asuba zai dawo hayyacinsa su samu ya koma can government house kafin a farga. Dan sun tabbatar fitar ɓadda kamar daya sabayice yayo yau ɗin ma.

     Badan Raudha taso ba ta mike. Koda suka isa ɗaki Anne wanka ta sakatayi, ta bata tea tasha kamar yanda ta saba turketa a duk dare kafin ta sakata kwanciyar dole. Sai dai ta lumshe idanune kawai badan barcin ba. Amma ita kanta tasan idan tace zatai barci a irin wannan halin yaudarar kanta zatai kawai...

       A ɓangaren su gimbiya Su'adah kam kowa tunda baiga Ramadhan ba sai hankalinsa ya karkata akan Addah Asma'a da suka samu a kasa wanwar. Ruwa aka bata tasha, aka kuma dagata zuwa kujera sannan suka shiga mata sannu. Bayan numfashinta yaɗan daidaita Gambiya Su'adah ta sallemsu su duka falon ya rage daga ita sai Adda Asmah da Aynah.
      “Adda inaga kuje gida zanzo da safe na sameku, dan zamanku yanzu anan akwai matsala zai iya fargar da jama'ar gidan wani abu. Su kuma ku barni dasu game da Ramadhan zanma tufƙar hanci”.
      Addah Asmah da ba fahimtar komai takeba a yanzu gudun kar gimbiya Su'adah ta ɗagota ta jinjina mata kai ko maganin da suka kawo ɗin bata samu bata ba suka fice cikin taraddadin da ƙaulani. Numfashi gimbiya Su'adah saukewa, kafin ta nufi sashen su Anne. Sai dai tana tu karowa taji sautin karatun Raudha da Pa. Wani irin kunci da duhu zuciyarta ta sake shiga najin tsantsar tsanar Raudha da batasan yaya akai tazo gidanba ya riketa. Tunanin ko dama tare da Ramadhan sukazo ya sata juyawa ta fasa shiga baki ɗaya ta koma sashenta tana haɗiyar zuciyarta data cika kirjinta fam kamar zata fashe.

★_★★____________★★_★

              Da asubar fari Bappi ya fita raka Ramadhan government house, kamar yanda ya fita ta barauniyar hanya yanzun ma tanan yabi da taimakon odilan nashi da shi kaɗai dama yasan da fitar. Tunda yaga bai dawo akan lokaci ba hankalinsa yake a tashe. Shi kansa yasan irin waɗannan fitar da shugaban ƙasar keyi akwai haɗari a cikinta. Sai dai shi ko'a jikinsa. Ko'an nuna masa illar fitar ɓadda kamar baya nuna damuwa ko hango wata matsala. Amma har cikin rai odilan ɗin nasa na tsoron randa wani zai farga a cikin gidan ko waje.

         A taura house kam koda aka wayi gari babu wanda ya tada zancen. Musamman daga sashen Anne. Ita kanta gimbiya Su'adah tana son ma Pa magana tanajin tsoron a yanda ya tashi yau fuska kamar hadarin gabas. Amma har cikin rai tana buƙatar jin halin da yaronta ke ciki. Ta kira wayarsa amma ba'a ɗaga ba, ta rasa inda zata tsoma ranta ta huta har baƙi dai suka fara isowa irin su Safina da tawagar ƴaƴanta. Sai daga masarautar Bina kuma.
     Zuwa Azhar gidan ya fara ɗaukar baƙi sosai. Hakan ne ya tilasta Gimbiya Su'adah fasa fita gidan Addah Asmah dan tun jiya da suka bar gidan bataji daga garesu ba. Ta kira duk wayoyinsu a kashe. Ta aika Muneera ta dawo ta sanar mata Aynah da Addah basa gida wai tun safe suka fita baƙi ma daketa isowa babu wanda ya samesu a gidan sai ma'aitan gidan keta saukesu. Wannan zance ya sake tada hankalin gimbiya Su'adah matuƙa dan haka ta kira fulani da suke shirin tahowa da yamma ta sanar mata. Duk da fulani tasan komai sai ta ɓoye mata akan ta kwantar da hankalinta zata bincika. Amma tasan Addah Asmahn bazataje wani waje ba daban. A sanyaye tace to.
      Fulani ta sauke wayar tana taɓe baki. Dan yanzu sun ƙudiri aniyar daina faɗa gimbiya Su'adah komai akan shirinsu. A ganinsu sakacintane ya lalata komai a daren jiya kokuma akwai abinda take son gujemawa. Itako fulani burinta da alwashinta sai ta nunama Anne ba itace kaɗai keda iko da Ramadhan ba, yayinda Addah Asmah ke nuna itama shine burin nata. Sai dai acan kasan rai ba haka bane. Baƙar hassadar ƴar uwartace kawai ke cinta akan ta fita komai na rayuwa. A ganinta mallakar Ramadhan matsayin mijin ƴarta, zaisa abinda Gimbiya Su'adah ke takama da tinƙaho da shi ya dawo tafin hanunta ƙarƙashin ikonta.
        Faruwar komai a jiya yasa Aynah kwana kuka akan bazata iya haƙuri da Ramadhan ba a yanzu. Ita duk ma yanda za'ai ayi ƙoƙarin gyara matsalar nan da suka tabbatar komai ya watse. Wannan shine dalilinsu na tafiya gidan boka bayan tun dare sun kirashi yanata faɗa akan abinda tunkan su sanar masa yace musu ya sani tunda aljanin daya turama Ramadhan yaci ubansa hanun Raudha da Pa da ayar ALLAH. Tun tafiyar da sukai da asubahin nan suna can har yanzu anata sake tsumo Aynah da shaiɗanci kala-kala akan Ramadhan kawai....

To bara muga wazaiyi winning anan kuma🚶🏻🤕.

*_____________________________*

              Ƙarfe biyar na yamma dai-dai tawagar shugaban ƙasa Ramadhan ta iso Taura house bisa rakkiyar jami'an tsaro da wasu na jikinsa. Kamar wancan hutun tako ina anguwar ta zama ƙarƙashin mulkin mallakar jami'an tsaro ne. Sauƙin ma dama can anguwar manyace bawai hayaniya ko yawan shigi da fici ake samu ba. Sai dai abin ya shafi masu tururuwar zuwa biki. Dan duk waɗanda suka iso yau dasunci karo da jami'an tsaron nan sai tsoro ya kamasu duk da sunsan yanzu Taura house yana da wani sabon girma bayan wanda kowa yasan gidan da shi.
     Babu wanda yaga Ramadhan, domin motar da yake ciki har jikin ƙofar falon Bappi ta baya aka kaita, yana fita kuma ya shige ciki abinsa.

      Raudha na bedroom ɗin Anne kwance ta gama ƙwallar shan kunu da Annen ta tsareta tayi Bilkisu ta shigo ɗakin da sallama. Wayar ta dake hanunta tana game ta ajiye, dan dama game ɗin kawai takeyi amma hankalinta naga mijinta da tunanin miyake ciki yanzun? Yana ina? Jikinsa da sauƙi ko babu?.
        “Sai a daina mana shagwaɓa ga boss nan ya iso”. Bilkisu daba sanin abinda ya faru da Ramadhan ɗin tai jiya ba ta faɗa tana dariya bayan takai zaune kusa da Raudha. Murmushi kawai Raudha tayi da faɗin, “Kai aunty ni shagwaɓar mi nayi?”.
      “Ai ba abun jayayya bane bara na lissafa miki yanzu kuwa ɗaya bayan ɗaya ta Brothe......”
     Ta kasa karasawa saboda wanda ya shigo ɗakin. Da farko tsoro taji sosai ita kanta Bilkisun, sai dai yanda taga yanayinsa kamar a sanyaye ya sata ɗan sassautawa ta gaisheshi zata mike. Sai dai Raudha tai saurin riƙo hanunta idanunta na cika da ƙwalla. Sosai yanzu tsoronsa takeji, tsoro mai tsanani dan ita kaɗai tasan azabar da taci a hanunsa har sau biyu da bazata taɓa iya mantawa ba.
       Raunanannun idanunsa ya sauke akan hannayen da Raudhan ta sarƙe. Sai yaji wani irin tausayinta mai tsanani yana dirar masa daga tsakkiyar kai har tafin kafa. Da ido yayma Bilkisu alamar ta fita. Dan haka tai saurin son zame hanunta cikin dabara tana faɗin, “Aunty Raudha bara na dawo tanan sai Yaya ya zauna nan”.
     Sam Raudha bata yarda ba, saita ƙara ƙwaɓe fuska zatai kuka. Bilkisu da ita kanta tausayinta takeji tunda batasan ko yayan nasu bai dawo cikin hankalinsaba har yanzu ta zame hanunta ta gudu. Sosai jikin Raudha ya fara rawa ganin ya maida ƙofar ya kulle harda key. Babu shiri ta miƙe a kan gadon tana ƙoƙarin sakkowa. Sosai tayi ƙiba, tako'ina komai yayi zam, damma doguwar rigar jallabiyace a jikin nata baƙa. A hankali ya lumshe idanunsa tare da harɗe hannayensa duka a ƙirjinsa, sai kuma ya sake buɗesu ya zuba mata. Yanda take rawar jiki yasa ko'ina nata ke motsawa, ga rigar mai santsi ce, sai hakan ya ƙara taimakawa wajen motsawar jikin nata.
     Murmushin takaici da tausayin kansu ya saki. Baiga laifinta ba, dan yasan dolene taji irin wannan tsoron nasa. Ya ɗan furzar na numfashi tare da warware hannayensa daga ƙirji ya fara takowa gareta cike da nutsuwarsa da kasalar yanayin rashin jin daɗi da yake a ciki........✍


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻


Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_YADDA ZAKA SIYA LITTAFI A AREWABOOKS_*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾

*Recharge* - inda ake shiga domin saka kudi cikin account.

*Balance* - Zai nuna kudin account dinku da zaku iya sayayyan littafai cikin kasuwar ArewaBooks.

*Credit/Debit Card* - Hanyar farko kuma mai dadi wajan Recharge din account dinku.

A inda (Enter your amount) za'a saka kudin da akeson Recharge din sai a taba "Proceed". Zaibude muku inda zaku saka bayanan katin banki, kuna gamawa kudinku zaishiga account dinku kaitsaye (instant).

--------

Akwai wasu hanyoyin saka kudi a ArewaBooks account kamar:

*Bank Transfer*
*Airtime Transfer*

Saidai su ba kaitsaye bane (instantly) sai ArewaBooks ta tabbatar da Transfer din, amman bayakai 1hour za'a gansa a Balance.


*Bank Transfer* - kamar yadda akwai bayani a sama da kuma account number ArewaBooks.

_Account No_ - *1220077999*
_Account Name_ - *Arewa Books Publishers*
_Bank_ - *Zenith Bank*

Bayan anyi Transfer dinne sai a cike wannan Form din:

Amount Paid: - Nawa aka tura?

Name used for transfer: - sunan da aka saka wajan turowa

Transferred time: - lokacin da aka turo

Name of bank: - sunan bankin da aka turo dashi

Deposit date: - ranar da aka turo

Sai ayi SUBMIT.

*Airtime Transfer* - muna bada shawaran ayi amfani da *Debit Card* kokuma *Bank Transfer* akan *Airtime Transfer* , amma idan yakama babu mafita saishi tau muna amsar:

MTN,
9Mobile
Glo
Airtel

Amma kamar yadda akayi rubutu a sama afara tuntubar ArewaBooks a WhatsApp domin akwai percent da ake cirewa na canji(convert) kafin kudinka yashiga Balance.

*WANNAN SHINE BAYANAN*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 63-64_*


...........Ƙasa takai durƙushe cikin rawar jiki. Ta haɗe hannayenta waje guda alamar roƙo. “Ya Ramadhan dan girman ALLAH kayi haƙuri, na tuba kar kayi zan iya mutuwa yau. Wlhy wajen har yanzu yana ciwo”.
       Kasa jurewa yay, sai da ƙwalla suka taru masa a ido. Matarsa ta sunna ke tsoronsa saboda yaje gareta tamkar karen farauta. Ya kusanceta tamar babu zuciya a ƙirjinsa. Maimakon abinda Raudha tai tunanin sai taga saɓanin hakan. Dan shima gabanta yakai durƙushe. Ya ɗora duka hannayensa kan nata ya riƙe. “I'm vary sorry Ameenatu ki gafarceni dan ALLAH”.
     Ya faɗa cikin wata iriyar murya mai tsananin rauni da rawa. Da sauri Raudha ta buɗe idanunta dake rufe, danjin furucinsa da sautin muryarsa. Sosai ƙirjinta ya buga ganin hawaye a fuskar mijinta. Sai ta sake fashewa da kuka tana girgiza masa kanta. “Dan ALLAH Ya Ramadhan kabar kuka”.
         Hanunsa dake cikin nata ya riko, ya jawota ta faɗa jikinsa, sai kawai suka saki kukan a tare abin tausayi. Tsahon mintuna uku suna a haka. Kafin Raudha ta ɗago tana share hawayenta tana magana. “Kaga dan ALLAH kabar kukan Abokina. Kaga nima na daina. Kuma ni ban taɓa rikekaba dama na yafe maka. Kai harma wanda zakamin a gaba na yafe maka Ya Ramadhan. Dan ALLAH ka daina kuka kar wani ya shigo, idan wani ya ganka a haka bazan yafema kaina ba”. Ta ƙare maganar tana kai hannayenta saman fuskarsa ta shiga share masa nasa hawayen.
        Murmushi yay mata, wani irin kaunarta na ratsashi. Ya riƙo hannayen nata da take share hawayensa ya sumbata. Idanunta ta lumshe a hankali, saƙonsa na ratsa mata jini da ɓargo. Ciki disashiyar muryarsa yace, “Ustazah!”.
      Idanun ta buɗe a hankali tana kallonsa. Ya kafeta da nashi dake cikin yanayin shauƙi da bege. *_“I love you!. Am serious I love you more than you can ever comprehend. Kinada muhimmanci a duniyata. Ina miki irin son da bayan mahaifiyata da Anne ban taɓa yima wata mace a duniya ba sai ke. Bazance miki ban taɓa so ba, sai dai inajin naki daban. Ga Ramadhan nan Ameenatu, Ramadhan B. Hameed Taura ya mallaka miki kansa da duk abinda yake nasa sai yanda kikai da shi, dan ALLAH karkici amana, karkiyi butulci, karkiyi amfani da wannan soyayya da dama ki cutar da shi......”_*
      Gaba ɗaya jikin Raudha rawa yakeyi, gaba daya ya kashe mata jiki, ya sakata cikin taradadadi da kaulani. Ta fashe masa da wani irin sassanyan kuka mai tsuma zuciya.
        “Nima ina sonka Ya Ramadhan, ina ƙaunarka da iya gaskiyata. Insha ALLAH bazan taɓa cutar da ko dabban Taura family ba balle kai. Har abada ko wanda zai ci amanarka bazan barsaba ma balle ni kaina. Ina fatan ko mutuwa ta ɗaukemu rana ɗaya, lokaci ɗaya, mu zama maƙwaftan juna a kabari sannan mu kasance ma'aurata a aljanna.....”
       Fuskarta ya kamo cikin tafukan hanunsa ya haɗe goshinsu, sai kuma ya manna lips nashi akan nata tare da rungumeta a jikinsa.

       Da sauri Anne da Bappi dake tsaye jikin window suna kallonsu suka ɗauke kansu. Anne tasa hannu ta share hawayen da suke saukar mata a fuska na ɗunbin tausayin waɗan nan ma'aurata. Tun fitowar Ramadhan daga falon Bappi Anne ta biyosa da shirin dakatar da shi, dan ta ɗauki aniyar saita wanashi akan Raudha. Biyota Bappi yay da hanzari shima da zummar dakatar da ita, sai dai tana ƙoƙarin gitta window ɗin ɗakin nata dake tabayan sashen Bappin ta tsinkayi roƙon da Raudha kema Ramadhan. Cak ta tsaya, a kuma dai-dai nan Bappi ma ya iso, ganin taja birki shima yaja ya kai dubansa ga abinda take kallo. Wannan yasa komai dake wakana a kan idonsu ne akuma kan kunnuwansu. Hannunta Bappi ya kama suka bar wajen.

      “I need you Please”.
Ya faɗa murya a sarƙe lokacin da yake janye lips nasa daga kan nata. kai ta shiga jujjuya masa cikin tashin hankali, har hawaye sun sake cika mata idanu.
       “Please Ya Ramadhan forgive me wlhy akwai ciwo”.
    Da ƙyar ya iya rumtse idanunsa da suka kaɗa sukai jajur, dan tabbas bukatarta yake mai tsanani, bakuma zaiso cutar da ita ba. Amma dole ya samawa kansa mafita ba kuma a ɗakin Annensa ba, dan akwai kunya a raka baƙo ya ruga...
      “Shike nan naji, amma muje zan duba naga ɓarnar da nayi dan ALLAH”. Yay maganar a wani irin marairaicewa kamar bashi ba. Zatai magana itama ya girgiza mata kai tare da ɗora hanunsa kan lips nata alamar kartace komai. Dole tai shiru, ga tsoro ga fargaba. Haka ya kamata ya miƙar, batare daya bata damar cewa komai ba ya kama hanunta suka fito. Addu'a take a ranta ALLAH yasa babu kowa a falon, duk da tasan dai ta inda zasu ratsa ɗin ba falon da kowa ke iya shigowa bane sai iya ahalin gidan kawai.
       Ta ɗanji sanyi da basu haɗu da kowa ba, sai dai mai aikin Anne dake ƙoƙarin shirya abincin dare a dining. Koda suka fito kam kasa tai da kanta tana gaida Ramadhan ɗin. Hannu kawai ya iya ɗaga mata suka wuce, dan yasan inhar yay magana kai tsaye za'a gane yanayin da yake ciki. Ko'ina ƙal yake a sashen nasa. Sai ma kamshi na musamman dake tashi dan Bilkisu da Basma ne sukai bautar gyaransa. Suna shigowa cikin ɗar-ɗar Raudha tace zanyi fitsari dan ALLAH. Sakar mata hannu yay kawai batare da yace komaiba. Sai ma ƙoƙarin rage babbar rigar shaddar jikinsa yake.
      Babu wani fitsari da zatayi, tayi hakane danta kuɓutar da kanta daga garesa. Sai dai tasan hakan bamai yuwuwa bane. Amma tanada tabbacin yace zaiyi wani abu yanzu ɗinkin jikinta zai farke ne. Bayan kuma Dr Hauwa ta mata gargaɗi matuƙa akan ta kiyaye ta kuma kula sosai, shiyyasa Anne ke tsaye kanta kullum sau uku take shiga ruwan zafi.
       Jin sautin kiran salla ya sata lumshe ido daɗi na matuƙar ratsata. ALLAH ya kawo mafita kenan. Jin kamar ana taɓa ƙofar tai saurin fara alwala. Kallonta kawai ya tsayayi sai kuma yay murmushi.
       “Duk dai wayon Amarya Ustazah...”
     Baki ta tura gaba lokacin da take ɗagowa bayan kammala alwalar, “Toni wane wayo nayi”. Tai maganar da kauda idonta a kansa dan ya cire har ƴar cikin da ga shi sai wandon shaddar da singlet baka.
          “A'a ni minace kuma. Kefa daɗina dake fassara bawa a mizanin da bai kai ba. Ke dai jirani nai alwala kawai”.
        Gwalo ta masa batare da tunanin ya ganta ta mirror ba. Sai dai yay shiru kawai dariya na cinsa a ciki. Bayan ya kammala suka fito, shine yay musu jam'i, dan duk nasihar datai masa akan zuwa massallaci nunawa yay ai lalura ce zata hanashi. Tasan ya bijirene kawai dan son ransa. Amma badan baisan hakan ba. Bayan sun idar ta ɗauka alkur'ani zata fara karatu ya riƙe.
        “K ALLAH inaga zare miki ido zan komayi maybe zaki fara tsorona. Mai kan kwakwa kawai”. Ya kare maganar da mangare mata kai. Fuska ta kwaɓe tana shafa wajen. “Ni gasky ban yarda ba”.
        Cikin ɗage gira yace, “Ko? To zoki rama mana”.
      Tashin kuwa tai ta bisa, yana ajiye Alkur'anin zai ɗago ta bashi mintsini mai shegen zafi a damtsen hanunsa.
     “Kamm lalai yarinyar nan kinci abinci, ni kikama wannan muguntar?”.
      Dariya ta ƙyalƙyale da shi tana ƙoƙarin kwasa da gudu yay tsalle ɗaya ya cafkota. Jikinta ta fara fisga tana haɗiye dariyar dake cinta amma ina tazo hannu, gaba ɗayanta ya dauka cak yay kan sofa da ita. Duk yanda take watsal-watsal da ƙafafu bai saurareta ba. Sai ma dariya da yake mata harya direta. “Rama cuta ga macuci ai ibada ne yarinya”.
         Yay maganar da kwashe hijjabinta gaba daya ya ajiye. Hannayenta dake kai masa ƙananun duka a ƙirji ya riƙe tare da kwantowa kanta, sai dai bai sakar mata nauyinsa ba. Cikin ƙanƙanin lokaci ya ladabtar da zille-zillenta ta nutsu tana amsar saƙonsa. Sai dai acan kasan ranta a matukar tsorace take. Sai da ya tabbatar tayi laushi ya nema bin hanayar da take tsoro ta fara masa kuka da magiya. Dama ba zuwan zai ba. Amma ya tabbatar mata zai ƙyaleta idan tai masa abinda yace. Ko musu babu kuwa ta amince. Dan gwara hakan ita dai da abinda takewa tsoron.......

      Luf take shiru a jikinsa tana sauraren yanda yake sauke numfashi a hankali da sanya mata albarka. Yayinda hanunsa ke cikin sumar kanta yana faman wasa da ita duk ya birkita mata ita. Murya can kasa a ɗashe tace, “Ya Ramadhan sallar isha'i fa akeyi”.
      “Uhhm naji ai”.
Ya faɗa a shaƙe idanunsa rufe. Shiru tai bata sake cewa komai ba har kusan mintuna biyar sannan ya miƙe. Kai tsaye toilet ya shiga, hakan yasa Raudha lumshe idanu da sauke ajiyar zuciya takai hanunta saman cikinta tana shafawa. Bata san yaya zaijiba idan yasan tanada ciki, ita kanta a duk sanda ta tuna akwai ɗa mai alaka da shi tanajin tsantsar farin ciki. Badan shi shugaban kasa bane, badan shi jinin Taura family bane. Sai dai ɗunbin soyayyarta da take hangowa a cikin idanunsa. Motsin fitowarsa a bayin ya sata dawowa hayyacinta daga dogon tunanin data lula.
          Yanda ya fito yana goge sumarsa da jiki ya tabbatar mata wanka yayo, saurin ɗauke kanta tai ta maida gefe. Yay ɗan murmushi da ƙarasawa jikin Wadrobe ɗinsa domin duba kaya. “Madam tashi kiyi wanka muyi salla”.
       “Ni alwala kawai zanyi”.
Ta faɗa a shagwaɓe tana mikewa a gadon itama. Murmushi kawai yayi amma komai baiceba harta shige toilet. Sai dai kuma ashe cika bakinne kawai, dan itama dai hummm kawai............✍


*_Alhmdllhi barka da salla, ALLAH ya maimaita mana ya amshi ibadunmu baki ɗaya. ALLAH ya dawo mana da mahajjatanmu gida lfy, ya jiƙan iyayenmu, ya ƙara mana lafiya da zama lafiya. Inama kowa barka da salla ina kuma jiran naman salla dan nagafa sai nayi tuni za'a kawon kenan🤕👩🏻‍🦯_*.


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 65-66_*


...........Fitowarta dai-dai da ƙoƙarinsa na kammala busar da sumarsa. Ya kalleta kawai ya ɗauke kansa baice komaiba. Dan rigartace dai a jikinta data shiga da ita ala dole babu abinda tayo. Sai da ya shimfiɗa abin salla ya miƙa mata wandonsa mai taushi na adidas da farar t-shirt. “Saka muyi salla lokaci na shigewa”.
    Kanta a kasa batare data kallesa ba tace, “Bafa abinda ya sameta”.
      “Humm Ameenatu kenan, karki manta na rigaki zuwa duniya. Bayan rigaki shekaru kusan goma sha takwas na baki, kinga a lissafi kuwa lokacin da nake a mizanin shiga shekarun girma na ɗa namiji aka haifeki”.
      Kunya kamar ta nutse. Dan sam batai tunanin ya ganeba. Dama sotai ta masa dabara sai sun tada sallar ta gudu ɗakin Anne ta canja kayan tai salla.
        “Hallo! Ko sai na nuna miki shaida ne dan rigar kanta ta tona miki asiri tare da wannan”. Ya tura hanunsa cikin hular kanta ya jawo silin jiƙaƙƙen gashinta a ciki. Da sauri ta kwashi kayan zata koma toilet”.
       “Hii aini ba surukinki bane canjasu anan konazo na canja miki kina ƙara makarar damu”.
     Babu yanda ta iya dole tabi umarninsa, bayan ta saka kayan suka gabatar da sallar. Suna idarwa wayarsa ta hau ruri, yasan Anne ce dan haka ya miƙe zuwa bedside drawer ya zauna a bakin gadon yana daukar wayar....
        “Kai ka fita idona kawomin yarinya taci abinci tana fama da kanta”.
      (Mutum da matarsa ƙarfin hali kenan) ya faɗa a zuciya yana sakin murmushi. A fili kam yace, “Okay Gimbiyar Bappi yanzu kuwa maida wukar”.
     
          ★Gaba ɗaya Raudha jitake kamar ta nutse dan kunya. Kanta a kasa ta risina ta gaida Anne da Bappi. Zata zauna kusa da Bilkisu dake tare da su yaja mata kujerar kusa da shi tare da kamo hanunta yanda su Bappi bazasu gani ba. Sai dai ya makaro sun gani ɗin. A kuma kallo ɗaya Anne ta fahimci wayo yaje yayma Raudha, sai dai addu'arta ALLAH yasa bai aikata abinda zai cutar da itaba tunda ɗinkin jikinta bai gama warkewaba. Tunda tazo ɗaki taga babu su tai niyyar kiransa a waya Bappi ya hanata. Acewarsa yasan Ramadhan na cikin hankalinsa bazai sake yarda ya aikata abinda zai cutar da Raudha ba. Gara su barsu su sasanta kansu da wuri kodan su Gimbiya Su'adah ma.
        Bilkisu ce ta zuba musu abincin, dan Raudha dai ta kasa motsin kirki. Gani take kamar su Anne sun fahimci abinda duk ya faru tunda har abu yakai ga canja kaya. Kowa nacin abincinsa hankali kwance amma banda ita. Tsakura kawai take kaɗan-kaɗan.
      “ALLAH in bakici abincin nan ba zan tonaki yanzu su Anne susan mikika aikato a ciki da hujja”.
     Wani irin ƙululu cikinta ya bada. Harta kasa daurewa saida ta ɗan dubesa. Gira ɗaya ya ɗage mata da sakin wani munafukin murmushi daya tilastata maida kanta ƙasa da hanzari. Duk abinda suke su Anne na lure da su, sai dai kowa ya ɗauke kansa kamar bai san anaiba.
         Farfesun kan rago Ramadhan yace Bilkisu ta zuba masa. Kamar jira tana buɗe bowl ɗin Raudha tai saurin toshe hanci da rike numfashinta. Babu wanda ya lura da hakan Bilkisu ta fara zubawa, kasancewar kusa da shi take tuni ƙamshin ya ƙara karfi a kusa da ita. Har takai amai na yunƙuro mata. Ta mike zaram zata bar wajen ya rikota.
      “Lafiya kuwa?”.
Kanta ta shiga girgiza masa da nuna masa ya saketa amma yaƙi. Anne ce ta fahimci abinda ya ɗaga hankalin Raudhan da sauri tace, “Ramadhan saketa”. Tai maganar tana mikewa.
       Sam ya kasa fahimta, a zatonsa wani abune daban, ina kafin ya samu damar cewa wani abu ta kasa daurewa ta fisgi hanunta da ƙarfi. Sai dai kafin takai toilet na bayin ta saki aman a waje. Gaba ɗayansu sukayi kanta har Bappi, dama Ramadhan tunda ta fisge ya bita. Amai sosai takeyi a wahale. Shiko gaba ɗaya ya cimimiyota jikinsa duk a ruɗe. Sai tambayarta yake mike damunta?.
          “Ramadhan ka barta taji da abinda ya dameta mana Please”.
Anne ta faɗa cike da tausayin Raudha. Sai da ya tabbatar ta gama ya ɗagata cak ya nufi sashensa da ita. Anne zata bisu Bappi ya riƙo hanunta yana girgiza mata kai da murmushi a fuskarsa. “Barshi shi daya jawo yay aikin”.
     Murmushi kawai tai da girgiza kai tana mintsininsa da nuna masa Bilkiau da ido. Yay karamar dariya da ita kawai tajisa. Mai aikin Anne ce tazo ta gyara wajen. Su kuma suka koma kan table suna karasa cin abincinsu kowa da tausayin Raudha a ransa

     Bayan kamar mintuna goma sha biyar Ramadhan ya fito, a lokacin sun bar dining sun koma falo.
      “Yaya jikin nata?”.
Bappi ya tambaya cike da kulawa. Cikin damuwa Ramadhan daya koma duk wani kalar tausayi yace, “Bappi na barota kwance zan sama mata wani abincin a kuma kira Momyn Jabeer”.
          “No kiran Mommyn Jabeer ba shine mafitaba ai. Da alama kamshin naman kan canne bataso. Taci abinci saita kwanta ta huta ALLAH ya raba lafiya”.
         Wani irin yarrr yaji har saman kansa. Cikin rawar harshe yace, “Anne ban gane ba?”.
     Hannu Bappi ya mika masa da faɗin, “Ajiye goro na ganar da kai”.
    Ganin Bappi a serious sosai Ramadhan yay ƴar dariya yana shafa aljihu. Sai dai babu komai a ciki, hatta wayoyinsa na ɗaki. “Bappi na maka alƙawarin baka koma mi kakeso faɗi dan ALLAH”.
     “Tabb ai an daina aikin banza a NAYA kai dai ajiye kasha labaru”.
         Rasa mima zaiyi yay, sai kawai ya kwanto agogon hanunsa ya ɗora a hanun Bappin. Bappi ya ɗan juya agogon, sai kuma ya taɓe baki. “Ba laifi mai nauyine ai. Bilkisu bashi yasha”.
     Bilkisu dake dariya cike da ɗoki ta nufi Yayan nata tayi ɗan hugging nashi, sai kuma ta sakeshi. “Yaya na kusa zama Mummyne fa, Aunty nada cikin wata biyu da kwanaki....”
       “What?!!!”.
Ai kafinma ta ƙarasa bayani ya juya da sauri ya bar wajen zuwa sashensa. “Na yafe miki sauran labarin”. Ya faɗa yana ɗago hannu sanda yake gab da shiga.
        Mi su Anne zasuyi inba dariya ba. Pa dake tsaye tun ɗazu batare da sun sani ba yay murmushi kawai yana girgiza kansa. Ɗansa kenan abin alfaharinsa. Murɗaɗɗen mai wahalar fahimta ga wanda ke nesa da shi. Da yawan mutane akace musu Ramadhan mai sauƙin kaine a cikin gida zasu karyata. Domin shi mutumne mai yanyin mutanen da ake kira da girman kai kai tsaye. Dan kuwa tabbas magana ma sai yaso da wanda yay niyya yakeyinta. Dariya ko mutane da yawa kance basu taɓa gani daga garesa ba. Dan akan jima baiyi hakan ba sai a inda yaso. Sai dai ga wanda yaso kuma ya aminta shi mai sauƙin kaine da iya mu'amula matuƙa.

        Cikin ɗan barcin daya fara figarta kawai taji an rungumeta. Tare da fara bata zafafan kiss's tako ina da ina a jikinta.
        “Ya Ramadhan lafiya?”.
Raudha ta faɗa a kasalance dan da gaske barci ya fara ɗaukarta. Bai bata amsa ba. Sai rungumeta da yay tsam a jikinsa yana jero addu'ar nan ga wanda abin farin ciki ya sama.
       *الْحَمْدُ للهِ الَّذِي بِنِعْمَتِهِ تَتِمُّ الصَّالِحَاتِ .*
*_Alhamdu lillahil-lazee bini’imatihi tatimmus-salihat._*
     _Godiya ta tabbata ga ALLAH wanda saboda ni'imarsa ce kyawawan ayyuka suke cika._
*اَلْحَمْدُ ِللهِ عَلَى كُلِّ حَالٍ.*
*_Alhamdulillahi ala kulli halin_*
       _Godiya ta tabbata ga ALLAH a cikin kowane hali._
        Rigar dake jikinta ya ɗaga nanma yana sumbatar cikinta. Kafin ya kwantar da kansa akai wasu hawaye na tuna Haseenah na sakko masa. Ashe bayan Haseenah yana da rabon sake haihuwar ƙanen a duniya. Ɗagowa yay ya sake sumbatar cikin, sai kuma ya fara karanto addu'ar nemawa ƴaƴa tsari (iyaye dan ALLAH a dingayi, kai ko yaron cikine dake karanta ki shafe cikinki kafin ya fito ki ɗora dayi masa a zahiri😘😢. Domin kuwa MANZON ALLAH tsira da amincin ALLAH su tabbata a gare shi, ya kasance yana nema wa Hassan da Husain tsari da wannan addu'ar: ).
             *أُعِيذُكُمَا بِكَلِمَاتِ اللهِ التَّامَّة، مِنْ كُلِّ شَيْطَانٍ وَهَامَّةٍ، وَمِنْ كُلِّ عَيْنٍ لاَمَّةٍ.*
*_O'eezukuma bikalimatil-lahit-tammah, min kulli shaytanin wahammah, wamin kulli 'aynin lammah._*
       _Ina neman muku tsari da kalmomin ALLAH cikakku daga dukkan shaiɗan da wata dabba mai dafi, da kuma dukkan wani mai kambun baka, mai cutarwa_.
        Raudha dake murmushi takai hannu ta shafa kansa. “Irin wannan security ba ɗaga ƙafa haka?”.
      Tasowa yay gareta shima fuskar tasa da murmushi, ya kwanta kusa da ita tare da tokare kansa da hanunsa ya lakace mata hanci. “Uhmm barni gara na tofe abina tun yanzu kodan masu ƙarancin tsoron ALLAH. Yanzu nan Baby Luv kinsan da wannan abin farin cikin tun ɗazu kikaƙi sanarmin? Anya kuwa kina sona?”.
     Dariya tayi tana mai saka tafukan hanunta ta rufe fuska. “Kai Ya Ramadhan kawai kuma saina kama faɗama inada cikin ɗan fari dan banda kunya”.
        “Lallaima yarinyar nan”.
Ya faɗa shima yana dariya da son zame hanunta. Ƙin yarda tayi, sai ma juyowa datai da sauri ta sinne kanta a ƙirjinsa. Idanu ya lumshe a hankali tare da rungumota ya kanƙame ta shima. ji yake kamar ya haɗiyeta kawai ya huta. “I love you sweetheart”.
        “I love you too Noorullah”.
“Nice name dear I love more. Na huta an daina kaƙabamin Yaya babu dangin gabas babu na yamma. Dolene yau nayi celebrations biyu kenan”.
        Siririyar dariya ta saki tana mai ɗagowa ta sumbaci lips nasa ta sake maida kanta ta kudindine a jikinsa.
      “Hummm wlhy yarinya ki bani kwana uku kacal saina maidaki mara kunya ta bugawa a jaridar duniya”. Yay maganar yana mai rungumeta sosai a jikinsa murmushi yaki barin fuskarsa.
        Babu wanda ya karajin ɗuriyar Ramadhan da Raudha a gidan, kuma babu wanda ya nemesu. Garama ya kira Bilkisu daga baya ta kawoma Raudha sabon abinci taci ya busar mata da gashinta daga nan sukai kwanciyarsu............✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 67-68_*


...........*_WASHE GARI_*

          Washe gari babu kunya Gimbiya Su'adah tazo har sashen su Anne ta tuntuɓesu batun auren Aynah da Ramadhan. Dan Pa yaƙi bata haɗin kai kwata-kwata. Ramadhan ko taki cemasa komai duk da tasan yana cikin gidan. Hasalima har zuwa yay ya gaisheta. Yanda bata ɗaga masa maganar abinda ya faru ba a jiya shima baice komai ba. Yau ma bayan ya dawo sallar asuba yaje ya gaishetan. Nanma bataceba shima kumai bai ceba.
      Koda Bappi ya gama saurarenta cewa yay taje zataji komi da suka yanke shi da su mai-martaba. Ranta ya ɓaci, amma ta danne ta tafi. Duk yanda sukai da Bappin ta kira Adda Asmah ta sanar mata. Itako daga can gurgun tunaninta bata yay aikin boka ya tabbata kenan. dan dama yace zai rufe bakin kowa ai. Shi kansa Ramadhan bai isa yin ko tari ba akan batun.

       Hhh ALLAH sarki Addah Asmah. Batasan a yanzu matar Ramadhan da kakaninsa tsaye suke kansa ba. Dan a yau yini Raudha tai aikin karanta addu'oin warware sihiri dana kariyar ALLAH ita da Ramadhan suna tofawa a ruwa kamar yanda musulinci ya koyar damu. Suka kuma ajiye matsayin ruwan shansu. Yini guda suna a sashensu. Hatta abinci nan ake kawo musu. Yayinda Anne ta zaunar da shi ta sanar masa dokar Doctor akan Raudha na bedrest. Ya tabbatar mata babu damuwa zaiyi ƙoƙarinsa na kare hakan. Taji daɗi sosai tai masa nasiha ita da Bappi tare da addu'ar ALLAH ya kiyaye gaba.

    Washe gari gida ya cika da baƙi taf tako ina. Bakajin komai sai hayaniya. Sai dai duk wannan hayaniya da gidan ya dauka babu mai ganin shugaban ƙasa da first lady. Dan suna can sashensu suna baje kolin shafukan soyayya kamar su kaɗaine a duniyar. Basu da aiki sai zaman garden ɗinsa dake matuƙar ɗaukar hankalin Raudha takeji kamar a wata sabuwar duniyar take. Abu mafi ɗaukar hankalinta tsuntsaye da ake kiwo a wajen da ruwan da aka kawata mai bulɓulowa cikin dutse kai kace ba tsarawa akai ba. Sau ɗaya ya barta ta shiga sukai wanka a pool ɗin wai bayaso Unborn ɗinsa ya ɗauka mura tun yanzun. Ita dai dariyama yake bata. Dan baida aiki saita idan ta haihu babynsa kaza kaza. Kokuma ya kwanta a cinyarta yayta hira da cikin da ko a jikinta bai nuna akwaishiba dan cikin a shafe yake kamar babu hanji balle ɗa.
        A ɓangaren su Adda Asmah hankalinsu a tashe yake babu ango babu dalilinsa. Gashi har an fara event yau a cikin ukun kawai da mai-martaba ya basu izininyi tun a waccan ranar. Koda Fulani ta iso tasa a kira mata Ramadhan anƙi ganinsa. Gashi Bappi ya sashi kashe wayoyinsa duka sai mai muhimmanci kawai. Yo banda abin Fulani ma ganin shugaban ƙasa guda wasane kamar wani ganin Bilyn Abdull haka😏.
     Aiko ta shaƙa. Tazo har sashen Anne amma ƙofar sashensa a rufe. Hakan yasata tunanin koma dai raina musu hankali ake baya gidan aka ajiye waɗanan zaratan securitys ɗin zagaye da anguwa kamar masu gadin wuta. to komadai miye Shugaban kasa Ramadhan ya zama gwal ma ya fisa arhar gani a garesu.
     Dan ko kunshi da yace bilkisu ta kawo mai yiwa matarsa a sashen akai mata cikin garden, yayinda shi yake acan falon hutawarsa zaune shi da Ibrahim da A.J da sukazo biki suna shan hirarsu, dan Gimbiya Su'adah ta gama turama abokansa invitation kaf ta waya akan zaiyi amarya. Koda suka zo kuma baice da kowa komai ba akan hakan.

     Koda aka kammala ƙunshin ya gani yayta santi. Kaɗan-kaɗan ya kamo ya sumbata. Harda labarta mata yanda ya dinga satar kallon kafafunta da hannayenta lokacin da akai mata na bikinsu. Aiko mi zatai inba dariya ba har saida ya ƙulu. Tako shiga masa gwalo da kiransa gulmamme.
     Gyaran kai kam shi ya wanke mata da kansa ya gyara mata shi tsaf har taita mamaki. Yako tabbatar mata tsabar son da yakema gashine kawai ya sashi koya a wajen Anne. Harda cewa wataran zai mata kitso da sai tasha mamaki.
     

*_RANA BATA ƘARYA......_*

       Lallai wannan zance haka yake. Dan kuwa a yau juma'a bayan sakkowa masallaci aka ɗaura aurarrakin yaran Taura Family har su biyar. Sai dai wanda suka kasa kunne suji da Ramadhan a ciki sukaji tsit. Sai da aka kammala a karshe aka ɗaura na Ayna'u Musaddiq da angonta Aminullahi Ashiru. Ɗa ga tsohon gwamnan jihar TANDAZA, ya jima yana sonta tana masa ikkanci, dan har kuɗi sun taɓa kawowa ta bijire. Da yake uban baida fus a gidan haka ya hakura duk da kuwa bokine garesa Alhaji Laminu Tandaza. Sai dai kuma masu iya magana sunce matar mutum kabarinsa. Gashi kuwa UBANGIJI ya tabbatar da hakan.

      Gagarumar ƙurace ta tashi a gidan Adda Asmah jin sunan ango a bakin ƴan ɗaurin aure da ba haka suka saniba tun farko. A cikin kanƙanin lokaci ta hargitsa kowa. Zata taho Taura House ayi wacce za'ai ita da gimbiya Su'adah da take tunanin ta munafinceta Abban Aynah ya tabbatar mata ko gate ta tsallaka a bakin aurenta. Wannan tashin hankali ya saka Fulani hana Adda Asmah fita. Dan kowa yanda yaga Alhaji Musaddiq yau babu makawa zai tabbatar da abinda ya faɗa ɗin.
      Amarya Aynah kuwa suma tayi a take sai da aka nemi likitan ceto ranta.

      A Taura house kam babu wanda yasan mi ake ciki. Dan kuwa koda anguna suka shigo gaisuwa babu wanda yaji wani sabon abu da babu shugaban ƙasa Ramadhan da ganinsa dama bai zama lallai a idon kowanba.  Dan yanda ya fita tare da Bappi da mai-martaba wajen daurin aure haka suka dawo a mota ɗaya. Yana shigowa kuma ta ƙofar baya yabi zuwa sashensa dan ya tabbatarma Raudha kartaje ko'ina ana ɗaura aure gida zai dawo.
      Duk da dai taji gargaɗinsa. Anne tazo da kanta ta tafi da ita ta gaisa da wasu aminanta na amana dan ba wani ganin Raudhan sukai sosai ba lokacin nasu auren. Komai cikin dauriya Raudha keyinsa. Amma jikinta a matukar sanyaye yake tunda tasan yau mijinta zai zama nasune su biyu. A kwanakin nan duka kullum sai ta buya tasha kukanta. Kuma tsaf Ramadhan na lure da ita batare data sani ba. Sai dai bai taɓa nuna mataba ya barta da lokaci kawai. Zai daibi duk hanyar data dace ya mantar da ita idan suna tare kafin ta sake samun dama.
          Kasa ɗagowa tai ta kallesa lokacin daya shigo tana zaune ita da Basma da Rumaisa da Fadila a falo. Yayi kyau matuka cikin ɗanyar shadda data wadatu da jiƙaƙen ɗinki. Sai maiƙo da ɗaukar ido take gamai kallo. Gashi sosai babbar riga ke kawata adonsa da maidashi wani babban mutum. Sannu da zuwa su Basma sukai masa suna mikewa. Dama Anne ce tace suzo su ɗebe mata kewa kafin ya dawo tunda tasan babu mai shiga sashen nan da sunan yazo biki.
           Bayan ficewarsu ya tako a hankali zuwa gabanta yakai dukunne. Hannayenta ya kamo cikin nasa tare da saka ɗayan ya ɗago habarta. Itama tayi ƙyau matuƙa cikin wani lass mai azabar kyau da nauyin kuɗi. Ga ɗinkin ya zauna mata ɗas a jiki saboda kibar da tayi da ƙara haske da fresh. Taci kayan ado na ɗan kunne da sarka da zabba da awarwaraye ga ɗauri daya amsa sunansa ɗauri kai kace itace amaryar.
     Kukan da taketa riƙewa tun ɗazun ta sakar masa. Lumshe idanunsa yayi tare da mikewa ya ɗagata cak ya rungume a jikinsa yana murmushi.
     “Haba ƴar aljanna. Kwantar min da hankalinki Ramadhan B. Hameed Taura na Ameenatu Dawood Hutawa ne ita jaɗai insha ALLAH. Badan bazan iya karawaba wataran idan kaddarar hakan ta shigo, sai dai ina fatan rayuwa dake ke ɗaya dan tun asali zama da mace ɗaya ne tsarin Ramadhan. Sai dai tsarin ALLAH yana gaba da nawa Ameenatu. Amma a yanzu nakine ke ɗaya babu wadda aka ɗaurama Ramadhan aure da ita”.
       Ƙanƙamesa tai da sake fashewa da kukan da batasan na farin ciki bane kokuwa na minene. “I love you Noorullah”. Ta faɗa da ɗagowa lokaci ɗaya ta manne lips nata da nashi.
      Tab humm, batasan kuka ta kawo gidan mutuwa ba. Dan kuwa bawan ALLAH caraf ya cafke tare da ɗaukarta cak sukai bedroom. Yako shiga yamutsata son ransa. Yama manta da wata kwalliyar biki. Sai da labarin ya canja salo kuma ta ruɗe. Sai dai batasan dama haƙuri yake yana ɗaga kafa ba dan dole. Aiko tilas ta bari ya rage zafi yanda ya kamata. Da ga karshe dole aka sake nemo su Basma suka kawo mai sake kwalliyar biki.

Uhhm andai ji kunya😣😮🚶🏻.

       ★Bayan sallar la'asar sai ga Aunty Hannah mata ga vice president da tawagarta sun iso gidan bikin. A ciki kuwa harda Asabe da Hajiyar Birni dasu Fatisa. Wayyo dadi kamar zai halaka Raudha. Ta rasa inda zata saka kanta taji daɗi. Ga Anne ta saka an musu kyaƙyƙyawan karamci da tarba ta musamman ta abinci. Su aunty Hannah anata faman ɗaga kai da hura hanci ana yatsine-yatsine kai kace itace ma firt lady ɗin tsabar yanda guards ke dogare a bayanta da mata ƴan siyasa.
      Ina Raudha bata ita takeba. Farin cikin ganin Mummynta ya rufe mata ido ruff. Ko Hajiyar Birni da Hajiya mama sai da sukai mata tsogumi ta gaishesu. Anan suka kasance har bayan magrib. Da zasu wuce Anne ta haɗa musu shatara ta arziki musamman su Fatisa da sukaji kamar karsu rabu da ƴar uwarsu. Dan suma dai yanzu Alhmdllhi har sun kawo mazan aure ana shirin zuwa hutawa gaida Alhaji baba Dauda mai zamani surukin Mr president na ƙasar NAYA. Yaso zuwa daurin aure Inna ta tashi da amai da gudawa aka kwasheta asibiti a rikice tana can ana kara mata ruwa dole ya hakura. amma yasha takaici wai kallo ya wucesa daga shi har M. Gambo amininsa da shima ya gama saye zuciyar asabe batare data san shiɗin bane har yanzun. Dan yace bazai bayyana mata kansa ba sai ta yarda ya turo iyayensa. Itako tace su ba yaraba bata yarda da wannan ganganciba yazo gareta kawai su sasanta. To yanzu dai yace zaizo ɗin amma bai tsaida rana ba.

     Bayan wucewar tasu ma zazzaɓi ne ya rufe Raudha. Koda aketa shirin tafiya dinner ita tana can duƙunkune a bargo. Dama kuma bata saka ran zuwan ba tunda tasan Ramadhan dai bazaije ba. Kuma babu tabbas zai barta taje itama.

      ★Kafin a tafi dinner gimbiya Su'adah ta cigaba da neman number Fulani da Addah Asmah kamar yanda taketa fama tun bayan dawowar ƴan ɗaurin aure hakan baiyu ba. Dan duk kashe wayoyinsu sukai. Taso su Safina su leƙa gidan suyi ALLAH ya sanya alkairi hakan bata yuwuba dan Taura house yayi matukar cika kasancewar duka matan gidan uku sun aurar da yara.
     Ta turama Ramadhan gargaɗi sosai akan ya tabbatar yaje dinner ɗin nan amma sai dai baima gani ba dan yau yayi busy da yawa. Babu wanda yasan ainahin abinda ya faru sai fa da aka isa wajen dinner sai su Bilkisu Amare kawai da angunansu amma babu Aynah babu Ramadhan babu duk wani wanda ya shafi masarautar Bina dake a gidan Addah Asmah dan dama biyu aka rabu. Wasu sukayo nan Taura House wasu can gidan a cewarsu duk za'a haɗe wajen dinner da walima dakai amare.
       A sannan gimbiya Su'adah takejin mummunan labarin cewa ai kiɗa ya canja bada Ramadhan aka ɗaura aure ba. Ta matuƙar gigicewa a haukace ta shiga neman number Ramadhan amma har sannan switch up. Ta nufi sashen Pa ta iskesa da baƙinsa da basu wuce ba. Tsabar yasan miya kawota kuma yay kememe yaki tasowa. Haka ta wayance ta fito. Maida akalar kiranta tai ga Mai-martaba, shikam ta samesa. Sai dai yaja mata gargaɗi akan idan har tace wani abu yana cikin Taura house sai ya mata hukunci mai muni, tabar koma minene za'a tattauna bayan biki.
      Wannan al'amari ya matuƙar sake rikita gimbiya Su'adah, dan kuwa a daren nan jininta ba karamin hawa yayiba har sai da Safina ta taimaka mata da maganin barci.

      ★Wajen dinner kam bidirinsu suka sha kamar babu gobe. Dan gaba ɗaya anan aka haɗe amare da angwayen. An raƙashe an kwalle anci ansha sai dai Bily taji inama Raudha na wajen. Amma dai su Basma sun ɗauka komai a waya duk da anyi vedio recording. Su Ibrahim ne suka halarci wajen bisa wakilcin babban yayan amare shugaban ƙasa Ramadhan tare da cos. Hakama manyan mutane matan gwamnoni da ministers da ƴaƴansu duk sun halarta. Dan hatta da yaran su Alhaji yaro glass na nan anyi komai da su kamar babu wata a ƙasa. Karfe ɗaya aka tashi amare da tawagar jama'a yan biki sukayo gida. Masu gidaje a cikin Bingo suka nufi nasu muhalli anama angwaye da amare fatan alkairi da zaman lafiya da zuri'a masu albarka.........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 69-70_*


............Washe gari Raudha ta tashi batajin daɗi sosai. Dan har saida Dr Hauwa ta shigo ta dubata har dasu karin ruwa. Sai hankalin Ramadhan ya rabu biyu ga meeting da za'a zauna duk da dai babu Raudha a ciki. Ga jikinta kuma.

     Itako Gimbiya Su'adah tana can sun fice a sace ita da Safina zuwa gidan Addah Asmah, dan tana son tasan mike faruwa kafin a zauna zaman meeting duk da tasan har dasu Adda Asmah ɗin za'ayi. Lokacin da motar su gimbiya Su'adah ke shiga layin su Adda Asmah a lokacine driver daya ɗakko fulani zai kai Taura House shi kuma ke fita. Dan Addah Asmah tace fulanin tayi gaba suma zasu ƙaraso ita da mijinta da Aynah da kuma mijin Ayana ɗin da suke so ya saketa take a yau.
      Saboda yanayin hayaniyar mutane yasa Safina bata tsaya da motar ko'ina ba sai ƙofar falon baya data san su Adda Asmah nada ita. Dan kafin tai aure idan tana son haɗuwa da Faisal mijinta tasha satar fita ta wajen taje ta dawo wani bai sani ba. Ta wajen babu kowa, sai daga ɗan bayansu ta backyard suke jiyo ƙananun hayaniyar masu wanke-wanke. Ginbiya Su'adah takai hannu zata buɗe ƙofar wani furici mai kama da saukar aradu yay azamar taka mata birki, tai kuma saurin damƙe hanun Safina dake shirin yin magana tana girgiza mata kai....
     Su gimbiya Su'adah sun iso gidanne a dai-dai lokacin da Adda Asmah da Aynah ke tare a wannan falo, waya Adda Asmah keyi da bokanta akan abinda zasuyi idan anje wajen taro. Shine furucin ƙarshe data maimaita kamar yanda bokan ya faɗa ya shiga kunnen gimbiya Su'adah. Kasancewar sun gama wayar Adda Asmah ta ajiye a sanyaye tana duban Aynah data kafa mata ido.
      “Mom wai yanaga jikinki kamar yayi sanyi?”.
             “Tabbas dole jikina yay sanyi Aina'u. Sai dai zan iya aikata komai saboda ke. Kamar yanda malam yace na kirashi kafin muwuce wajen taron shine na kirashi, dan wannan dalilinne ma yasa nace Ammy (fulani) tai gaba zamu biyota. Yanzu har ita ta bar sanin sirrinmu tunda bazatace batason Su'adah kamar yanda take sona ba.....”
       “Hakane Mom, amma nidai sanar dani mike faruwa kawai?”.
    “Daɗina dake wutar ciki. Abinda kikaga ya girgizani da maganar malam ya tabbatarmin bincikensa na jiya ya nuna masa zasuyi taurin kai akan yarda da buƙatar mu, amma idan muka jajirce za'a iya samun nasa ƙila. Sai dai Ramadhan ɗin shine babbar matsala yanzu, saboda akwai yarinyar dake tsaye a kansa game da addu'a hatta azkar baya wasa yanzu safe da yamma, yace inhar tana tare da shi mawuyacine duk wani aiki namu yanzu yay tasiri a kansa dan tanada jajircewa. Hasashena ya bani tabbas shegiyar yarinyarnan ce ƴar karuwai. Maganarsa ta ƙarshe data firgitani itace zaɓin daya bamu akan Ramadhan ɗin, kodai akawar da shi kowa ya rasa shi da yarinyar, kokuma mu haƙur......”
       “Ina bazai yuwuba Mom, wlhy bazan iya haƙura da Ramadhan ba. Idan nai haka ko to tabbaci ban cika mace ba. Har yaushe zuciyarki ta fara tausayine Mom?.”
      “Nima ba tausayi nake jiba Aynah, domin zan iya komai a kanki, ciki kuwa harda kauda duk wanda ya tare min gaba. Tunda muka taso a gidanmu kowa yafi son Su'adah duk da kasantuwarta yarinya mai girman kai da ɗaukar kowa ba komai ba. Ba ƙyau tafini ba, amma ko kaya mukasa kafin a yabamin an yaba nata saboda ta iya tsara ado. Kullum a makaranta takan ɗauki maki na jarabawa fiye da nawa. A gida mahaifinmu yafi sonta fiye da kowane ɗa, dan hatta da shawararsa mai muhimmanci yakanyi da Su'adah baiyi da su Ammy ba. Mu duka ƴaƴan sarki ne amma ita kaɗai ake kira da gimbiya duk da nice babba. A koda yaushe wannan abu nacimun rai, taya zan fita komai amma yazam kullum itace da nasara sama da tawa? Hatta a shekarufa na fita. Abinda ya ƙara baƙanta raina da rayuwa lokacin da muke UK a school, tunda na fara ganin Basheer Hameed Taura na kamu da sonsa. Amma abin mamaki saina tsincesa tare da ƴar uwata Su'adah har sun fara soyayya ni ina nan ina ƙulla yanda zan tunkaresa da tawa soyayyar. Na shiga tashin hankali mara misali Aynah, har takai naji bazan iya jurewaba na tunkaresa da batun. Hummm karkiga irin korar kare da Basheer yamin tare da dogon gargaɗi, tun daga nan karatuna ya shiga hanyar taɓarɓarewa har muka dawo gida babu komai a result ɗina. Itako ta dawo da sakamako mai ƙyau cike da nasarori. Muna dawowa babu ɓata lokaci aka fara shirin aurar damu, ita aka aura mata wanda take so ni aka auramin mahaifinki batare da ina sonsa ba, dan iyayenmu ne suka ƙulla hakan. Watan Su'adah goma cif a Taura House ta haife ɗanta namiji santalele. Niko a lokacin ko ɓatan wata. Naji zafin hakan matuƙa amma naita ƙoƙarin dannewa. Bayan shekara biyu da yayensa ta sake Mardiyya, har lokacin ni babu labari. Nadai taƙaice miki sai a harhuwar Lubnah muka haihu tare, lokacin tanada yara har uku kenan niko 1 kuma mace ke. Na ƙara na biyu ma mace. Wannan ya ƙaramin tsanarta dan koba komai ta ɗarani da namiji kuma ƴaƴanta sunfi nawa. Daɗin daɗawa ɗanta shine ɗa tilo namiji agaba ɗaya Taura family. Nasha auna cutar da Ramadhan amma bai yuwuba saboda kakankinsa kullum nane suke da shi kamar sun san burina. Iyayi nayi Su'adah ta amshi Ramadhan a hanunsu amma sun hanata. Dan haka nasa akai aiki akansa aka tura masa wasu hatsabiban ajanu dakan maidashi tamkar wani mahaukaci. Sai dai mahaukacin ma naso ya koma baki ɗaya hakan bai kasance ba. Tun lokacin aurensa na farko naso ki auresa amma ya nuna baya ra'ayi, dan a yanzu babban burina shine ki auri Ramadhan ki ƙwato mana duk wani abinda Su'adah kejin tanada shi a hannu daya fini, amma kuma sai komai ya lalace bayan mun ɗakko hanyar nasara......”
       “To amma Mom duk da waɗan nan abubuwan shine kike tunanin bazamuyi abinda malam yace ba. Ramadhan nada taurin kai, na tabbatar da wahala ya yarda da aurena, sai dai in uwarsa ce tace zata tsine masa. Idan ma tace hakan shi wannan jakin da aka auramin zai sakeni ne ta cikin sauƙi.....”
        “Inko har duk abinda kika lissafo haka al'amarin zai zama to tabbas dolene Ramadhan ya mutu. Dan kawar da shine kawai zai sakama zuciyata salama akan Su'adah. Tunda bazamu samesaba to kowa ya rasa shikenan ƙurun-ƙus!!....…”
     Wani irin banko ƙofar da akai ne ya dakatar da Aynah data fara dariya, atake sukai diri-diri, gimbiya Su'adah da kanta ke wani irin juyawa tanajin hajijiya ta shiga nuna adda Asmah da hannu sai dai abinda take son faɗa ya gagara fita. Safina datai wani tsalle ta shaƙo wuyan Adda Asmah ta buga da bango, hakanne yasa itama Ayna yin kukan kura a kanta ta shaƙeta. Ƴan biki ne suka fara shigowa a guje saboda ihun da Addah Asmah ta buga na azaba, har goshinta ya fashe jini na zuba......

*_TAURA HOUSE_*

        Kowa ya hallara su kaɗai ake jira, mai-martaba da ransa ya gama ɓaci yana ƙoƙarin cewa a kirasu sai ga kiran daddyn Aynah ya shigo masa. Cikin tashin hankali ya shiga ambaton kalmar innalillahi.... Har ƙarshe, kafin ya ajiye wayar ya sanarma ƴan falon da duk hankalinsu ke kansa iya abinda Daddyn Aynah ya sanar masa. Zaram Ramadhan ya miƙe amma sai Bappi ya dakatar da shi.
      “Ina zaka kuma?”.
  “Bappi can gidan mana, kanajifa faɗa mizai haɗa Maah da Mom faɗa a duniyar nan?”.
      “Koma miye ai zamu sani yanzu, ko kana mantawa da matsayinka a yanzune wai. Koma ka zauna Basheer yaje ya taho da su”.
    Babu yanda ya iya ya koma ya zauna kamar zaiyi kuka. Zuciyarsa sai kaikawo take da tunanin mike faruwa? Miya faruwa? Mi akayi?. Hakama sauran kowa tunaninsa kenan sai dai babu mai bada gamsashiyyar amsa akai zaman jiran isowarsu.

          ★Kusan awa guda suna zaman jira dan sai da Pa yay jan ido suka yadda suka taho dalilin ita gimbiya Su'adah na tsoron nata mijin, itako Adda Asmah ta raina nata. Wujiga-wijiga suka shigo musamman gimbiya Su'adah da sai da Safina ta bata taimakon gaggawa acan amma da yanzu labarin ba wannan ake ba kuma. Kowa hankalinsa ya tashi da yanayin nasu, musamman ma Ramadhan da cikin rawar jiki yaje ya taya Safina riƙo Maah dake tafiya kamar zata zube ƙasa sai hakki take sama-sama. Shidai Bappi uffan baiceba, binsu kawai yake da kallo hakama mai-martaba. Pa kuwa yanayinsa na nuna ko'a jikinsa dan dama irin wannan ranar yake addu'ar tazo duk da bai san mike faruwa ba shima har yanzun.
      “Inaga muyi abinda ya taramu kamar zaifi”.
   Cewar Pa da alamun ɗaci a muryarsa. Bappi zaiyi magana Mai-martaba ya katsesa.
      “Gaskiya Basheer ya faɗa dan nima sonake na wuce akan lokaci”.
     Bappi ya haɗiye abinda yay niyyar faɗa kawai yana girgiza kansa. Daga haka aka buɗe taro da addu'a sannan aka fara abinda ya tara ɗin game da sauya maganar auren Ramadhan da Aynah.
       Bayan dawowar Ramadhan hayyacinsa, adare ranar Bappi ya sanar masa duk abinda ake ciki, amma sai ya dage akan shi bai taɓa jin son wata Ayna'u ba. Bakuma zai fara a yanzu ba bayan so na ƴan uwantaka dake tsakaninsu. Ya kuma tabbatar masa komi za'ai shi bazai aureta ba matarsa ta ishesa. Babu irin lallashin da Bappi bai masaba a wannan dare amma yace shifa yana akan bakansa.
    Washe gari ma daya dawo gidan kafin yaje ga Raudha maganar da suka fara tattaunawa da Pa da Bappi da Anne harma da su Yafendo da Mai-martaba a waya kenan amma Ramadhan yace yana kan bakansa. Baice zai auri Ayna'u ba kuma ayanzu bazai amsa ba. Dagiyarsa ya sake tabbatar musu akwai sihiri tattare da shi sanda ya dinga musu hauka akan auren Ayna'u garda ɓatawa da su Anne. Wannan dalilin ya sakasu sallamarsa suka tattauna abinda ya dace a tsakaninsu. Mahaifin Aynah shine ya kawo shawarar a rufe komai iya su ranar ɗaurin aure yanada wanda zai aurama Aynah dan a raba gardama komai ya zama ƙarshe basai anta jan zancen ba. Wannan shawara tama kowa, dan haka suka rufe komai hatta Ramadhan baisan da haka ba sai da aka ɗaura aure da wani daban ba shi ɗin ba.
        “ALLAH na gode maka da hakanma ta kasance, Ramadhan ka yafemin, duk halin daka shiga akan Ayna'u hardani a ciki, daban basu goyon bayaba da ba'a nema sabautamin rayuwarka har gashi yau ana iƙirarin kashemin kai ba...”
     Gimbiya Su'adah ta faɗa cikin kuka hanunta riƙe dana Ramadhan. Tsitt falon yay cikin rashin fahimtar kalaman nata..........✍
     

*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 71_*


.........“K Su'adah wace maganar banza ce wannan kike haka?”.
     Fulani ta katseta a harzuƙe.
“Ammy karki wani rufe gaskiya da son zuciya. Dole ne sirrin ɓoye ya fito fili, ban taɓa zaton Asmah zata zamemin BAƘAR INUWA ba sai yau. Ashe gara ranar da nake gudu da ita. Asmah bazan taɓa yafe miki ba, kuma insha ALLAH haka zaki ƙare rayuwarki a rashin nasarar da kike gani kina ciki......”
     A harzuƙe Adda Asmah ta yunƙuro zatai magana Fulani ta ƙatseta, hakan yasa mai-martaba bama gimbiya Su'adah damar faɗar duk abinda ke faruwa. Bako ta ɓoye ba, dan tun daga lokacin da riƙon Ramadhan ya koma hanun su Anne hanyoyin da Adda Asmah ta dinga sakata ita da Fulani har zuwa aurensa na farko, da kuma aurensa da Raudha zuwa son haɗasa da Aynah a yanzu da abinda suka jiyo ita da Safina yanzun. Bugu da ƙari dan ma kar Addah Asmah ta musa haka Safina ta ajiye wayarta da tayo recording duk maganganinsu kowa yaji.
      Sallallami kowa ya shigayi a falon, yayinda Adda Asmah ta haukace musu akan ita ƙarya ake mata. Saharri ne kawai saboda gimbiya Su'adah na borin kunya ta hana ɗanta auren ƴarta. Idanma kuwa tayi wani abun ai tare sukayisa. Wannan magana ta Adda Asmah ta sake tada ƙura, dan ko ba kunya gimbiya Su'adah ta daddage ta yarfama Adda Asmah mari,
       “Su'adah ni kika mara?!”.
“An mareki Asmah, kaɗanma kika gani wlhy, na tsaneki, na tsani ganinki, nayi dana sanin saninki matsayin ƴar uwata ciki guda. Kuma insha ALLAH Ramadhan yafi ƙarfinki har abada yafi kuma ƙarfin ƴarki, sai dai ki mutu da baƙin cikina dana zuri'ata. Munafuka kita zugani akan su Anne da suka riƙemin yaro tsakani da ALLAH kina cemin macutane ashe kece azzaluma mai cin amanar zuminci. Da iznin ALLAH ƙarshenki bazai ƙyauba.....”
      “K ce ƙarshenki baizai ƙyauba su'adah”. Adda Asmah ta faɗa tana kaiwa Gimbiya Su'adah mari, amma saita riƙe hanun ta murɗesa dan ko dai gimbiya Su'ada tafita ƙiba dama zuciya.
      Idanu Ramadhan ya sake rumtsewa kansa na juya masa. Yayinda su Bappi keta faman musu magana amma sunƙi sauraren kowa. Dan wata irin hankaɗawa ma Gimbiya Su'adah taima Adda Asmah tai taga-taga zata daɗi Aynah dake kuka ta riƙota.
       Nuna gimbiya Su'adah tai a kausashe. “Su'adah bakici bulus ba wlhy, ina matsayin yayarki kikaimin wannan abubuwan saboda kina auren mai kuɗi. Ni Asma'u nayi alƙawarin saina sabautar da rayuwarki data ahalinki baki ɗaya, dan wlhy sai kinyi dana sanin sanina. Sai kinsan na haifu cikin uwata da ubana, sai kin gwammaci daban kasance jininki ba!!”.
     Tana gama faɗa ta juya zata fita cike da borin kunya. Ana dakatar da ita bata saurari kowa ba taja hanun Aynah suka bar falon tana mai jaddadama gimbiya Su'adah bazata yarda da ƙazafin da sukai mata ita da Safina ba da mari ta jiraci sakamako.. 
      Wannan Al'amari ya firgita kowa ya kuma bama kowa mamaki. Mai-martaba da tun ƙuruciyar yaran nasa ya fahimci halin kowa ya share ƙwallar da suka cika masa idanu.
            “Ni nasan wannan ranar zatazo. Bammayi tunanin sauƙinta zai kasance hakaba. Tabbas Su'adah nada halayen banza da takejin zata iya taka kowa da komai idan taso. Girman kai, ɗaukar kowa ba kowaba duk halayyartace. Sai dai abinda mutane da yawa basa saurin ganewa daga gareta shine, abin kowa bai dameta ba. Su'adah bazaka taɓa jinta ta zauna surutu akan damuwa da cigaban wani ba, sannan dan taga wani da abu bazakaga ɓacin rai daga gareta ba balle damuwar kishinsa. Itako Asma'u da kuke gani, tanada sauƙin kai da son mutane, sai dai tanada nunkufurci da hassadar bata yarda kowa ya fita ba. Waɗan nan halayen nasu sune suka banbantasu, dan ita Hassada na cinye ayyukan bayi, tana maida mai son yin nasara bayan wanda yake gani bai kai ya fisa ba. Sai kaga mutum da halayen banza. Kai kullum cikin ibada da sauransu amma yanata samun nasariri kai sun gagara zuwa gareka karasa yaya haka? Nafi wane komai a rayuwa mizaisa ya dinga bani tazara? Amsar itace hassada. Hassada na ƙwace nasarori, ga wanda baida ita tana bashi nasarori koda bai kaika ba. Wasu suna tunanin Hassada itace kawai naga wane da abu banji daɗi ba. Hassada na zuwa kashi-kashi a cikin ayyuka.
         _Kaji kai kaɗai kake son kai nasara a rayuwa. Kaji kanajin zafin wanda kafi da komai na rayuwa ya samu wani abu kai baka samu ba. Ka dinga damuwa da yawan maganar cigaban wane. Mutum ya gina ƙyaƙyƙyawan abu ka ruguza masa. Misali mutanen da ke fidda mana littafi ko zuwa su saya dan su yaɗa hassada ce. Shiyyasa zasuga kullum suna wahalar banza da tunanin dakushemu mukuma munata nasara a rayuwarmu domin basu isa hanamu samun abinda ALLAH ya rubuto a ƙaddararmu ba._
      Hassada na shigowa cikin ayyukan mutane daban-daban ƙarama ko babba, ka sani ko baka sani ba. ALLAH ya rabamu da hassada. Ka tsarkake mana zukatanmu akoda yaushe. Ka wajabta mana tsoronka da soyayyar ANNABINMU (S.A.W).
     Nasiha sosai mai-martaba yayi a wajen harda Bappi, daga karshe aka sake rufe taron da addu'a kowa ya kama gabansa..
   
      A ranar aka miƙa amare ɗakunansu zukatan wasu duk babu daɗi. Musamman ma gimbiya Su'adah dake kwance babu lafiya, dan jininta ya hau matuƙa sai dai gyaran ALLAH. Amma Safina da Mardiyya na tsaye a kanta harma da Fulani.

    Raudha dai batasan mike faruwa ba. Dan koda Ramadhan ya dawo sukuku baice mata komai ba ita kuma bata tambayesa ba saboda ba daɗin jikin takejiba sam. Ko lokacin da aka kawo su Bilkisu har falonsa suyi sallama a taƙaice ya musu nasiha ya sallamesu. Bilkisu kuwa ta rungume Raudha suna kuka har abin ya bama wasu mamaki dan da'alama akwai shaƙuwa sosai a tattare da su. Ganin abun nasu bana wasa bane Ramadhan ya rabasu da ƙyar ya rungume matarsa duk da mutane dake wajen bai nuna ya san da su ba. Bayan wucewarsu ya jima yana lallashinta, daga ƙarshe ma yasata sukai kwanciyarsu.

      Dan hatta da Aynah ta tare nata gidan bisa tursasawar mai-martaba. Hasalima shi da kansa yay mata rakkiya har gidan mijin nata ya kuma tabbatar ma mijin ko da wasa yaji a ransa zai iya rabuwa da Aynah duk abinda zatai, to lallai sai ya hukuntashi shima bawai ita kaɗaiba.
    To Alhmdllh, mai-martaba ma dan bai san wanene Aminu ba, idan hatsabibanci Aynah takeji ya taketa ya shanye. Idan iskanci ne gidan ta taras.

*______________________*
 
        Har biki ya tashi lafiya kowa ya kama gabansa babu wanda ya sake tada maganar. Sai dai gimbiya Su'adah da jikinta keta sake tsanani duk da kulawar da take samu. Hakama Raudha ciwo ta kwanta sosai hakan sai ya raba hankalin Ramadhan biyu. Ga kwanakin hutunsu ya ƙare dama sati ɗaya ne kacal. Yanda jikin Maah ɗin keta ƙara tsanani ya saka Pa yanke shawarar tafiya taga likitan ta, dan haka randa su Ramadhan zasu koma government house aranar suma sukai shirin wucewa duk da Anne da taƙi yarda Raudha ta koma can gidan sai da Bappi ya lallaɓata. Aka kuma haɗata da su Basma.
     Tasha kuka duk da ita shaidace a yanzu mijin nata ya dawo dai-dai, sai damuwar da take hange cikin idanunsa da bata san ta micece ba. Ba kuma ta matsa da tambayaba tanata masa addu'ar dacewa dai da warwarewar matsalar tasa...
        
          Abubuwa sun lafa sai dai bazamuce duka ba. Gimbiya Su'adah na can likita ya ɗorata a magani, yayinda anan NAYA Addah Asmah keta faman shigi da fici na son ganin an hakala mata rayuwar Ramadhan dama Gimbiya Su'adah kanta duk da ƴar uwartace uwa ɗaya uba ɗaya. Sai kuma auren Aynah da take son rabawa wadda kullum cikin kiranta take tana kuka da roƙon taimakonta tazo Aminu zai kasheta. Dan bashi da aiki sai na mata fyaɗe safe da yamma. Idan taƙi yarda ya naɗa mata ɗan karen duka yayi yanda yakeso kuma. Baijin nauyin shigowa gidan da ƴammata da abokansa susha giyarsu da cocaine. Ya kuma dinga basu labarin abinda tai a America a club, hasalima anan ya fara ganinta har yaji yana buƙatar kasancewa da ita amma ta maresa. Shine dalilinsa na ƙudira aurenta. Ya kuma ɗau alwashin sai ya gama morarta ya saki videon wa duniya.
      Jin wannan zance Aynah tayi kuka tayi roƙo amma sam yaƙi saurarenta. Ta tabbatar masa komi yake so zatai masa akan karya tona mata asiri. Kota kanta bayayi saima ya zauna yayta kwasar dariya shi da abokansa.

      *_GOVERNMENT HOUSE_*

      Sukam matsalolin nasu da sauƙi Alhmdllhi, dan Raudha ma ta ɗanji ƙarfi harta koma zuwa makaranta ma. Idan akwai abinda ke damunsu a yanzu bai wuce ciwon gimbiya Su'adah ba. Sai dai kullum Pa na kwantar musu da hankali akan da sauƙi sosai. Hakan naɗan saka musu nutsuwa, har ma yake bama Ramadhan damar shan sharafin soyayyarsa. Duk da kuwa randa ya nuna buƙatar kasancewa da Ustazah ɗin nasa ansha daru. Kuka ta dinga masa da tsalle-tsalle dan ta kasa manta azabar data sha ta ƙarshe. Tunda suka dawo gidan daya tunkareta sai tace wajen bai warke ba ai. Ranar dai ya gaji da yawo da hankalin da take masa ganin zai cutu ya matseta ta ƙarfi ya duba.
    Tuni ta warke abinta zaren ɗinkin ma ya warware da kansa saboda kulawar data dinga samu wajen Anne. Azabar data sha ne kawai yasa take gudunsa. To ranar dai kam duk kukanta bai saurareta ba sai da ya sauke nauyi. Sai dai ya bita a hankali matuƙa yanda har taji nutsuwa tsoronsa ya ragu a ranta bakamar kwanakin baya ba.
     Daga ranar kuma suka sake dunƙulewa waje guda. Dan takai ma ita da kanta tana nuna so saboda cikinta yazo mata da wannan yanayin sosai. Cikin ƙanƙanin lokaci ta sake kara buɗewa tai ƙiba sosai da haske. Shi kansa har baya gajiya da kallonta da kiranta ƴar lukutarsa.
     Da yace ƴar lukuta zata fara masa kukan shagwaɓa ita bata yardaba. Shiko yayta dariya da tsokanarta. Sukanyi waya da Bilkisu kullum, tana kuma cigaba da sake ɗorata akan abubuwa na musamman har gashi yanzu Raudha ta ɗauka sabbin ma'aikata. Mai mata kwalliya da kula da duk wani ado da zatayi musamman idan hakan ta kama akan wata fita ta musamman duk da har yanzu Ramadhan bai taɓa yarda yaje da ita wani taro ba. Sai mai mata gyaran jiki itama. Ramadhan bai hanaba tunda ya san duk abinda zai ƙaru da sune shima ai, to shinema mai ƙaruwar tun school dai kawai Raudha ke zuwa, sannan koda yaushe komanta a rufe.

         Zuwa yanzu cikin Raudha ya shiga watanni na huɗu, ya fito mata ɗan duk da bawani ƙato can ba, wanda ma baida fahimta zai ɗauka tumbi ta fara ajiyewa saboda ƙibar da tayi. A kuma lokacinne gimbiya Su'adah ta dawo NAYA dan likitan riketa yay ta huta sosai acan.
      Ita da shi sukaje mata sannu da zuwa a wani dare cikin fitar sirri. Har yanzu bazamuce Gimbiya Su'adah na ra'ayin Raudha ba. Sai dai akwai sassauci matuƙa a yanayin data amsheta. Harda tambayarta tana lafiya kuwa wannan ƙiba tata lokaci guda haka?. Ita dai Raudha komai batace ba sai ɗan murmushi kanta a kasa. Hakama Ramadhan bai saka musu bakiba dan a ganinsa bai kamata yacema Maah ɗin Raudha nada ciki ba taga rashin kunyarsa a fili. Sai bilkisu ce ta sanar mata Raudha nada ciki ai. Duk da gimbiya Su'adah ta danne yanayin data shiga na farin ciki ƴaƴanta sai da suka fahimta har shi Ramadhan ɗin da Pa, sai dai babu wanda yace mata komai akan hakan.
      Raudha taji daɗin haɗuwa da Bilkisu da itama mijinta ya kawota duba Maah ɗin. Dan tanata son zuwa ma taga gidajen amaren laulayi ya hanata, Ramadhan kuma yace bazatajeba sai taji ƙarfi sosai. Makaranta ma yana barintane dan kar tai asarar abubuwa.
     Sosai Anne ta bata dabarun rainon ciki da shawarwari, tare da mata addu'ar fatan sauka lafiya. Basu baro gidan ba sai kusan ɗaya na dare.........✍

         

*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

*_Typing📲_*


*_Episode 72_*


.........Rayuwa ta cigaba da shuɗawa gwamnatin Ramadhan nata sakin manya-manyan projects naban mamaki. Ko'ina ka zaga a cikin ƙasa sai sambarka akeyi. Domin ƴan matsalolin dake shigowa tarin ƙoƙarin ayyukan da ake shimfiɗawa suna dannesu ƙwarai da gaske. Hatta da ƴan bani na iya abokan hammaya bakunansu sun mutu dan babu abin faɗa kuma, sai dai duk da haka sukan ɗanyi takale-takalensu a gidajen redio dana talabijin.
     Suna dire zance masoyan Ramadhan ke basu amsa dai-dai da su, amsar da su kansu basu da bakin sake maida murtani, dan kuwa dai kowa shaidane ga Ramadhan tun bai cika shekara akan gadon mulki ba manya-manyan ayyukansa sun fito fili ma duniya. Ga tausayin talaka. Ayyukan yi ga matasa da matan aure harma da ƴan mata. Ɓangaren lafiya da wutar lantarki da ruwa duk Alhmdllhi. Duk da ba komai ne ya wadaci kowaba hundred percent anci kaso mafi yawa na gyara. Makarantu tsaye ake akan albashin ma'aikata da cire kowane irin bara gurbi da zai iya dakusar da ilimin ta hanyar alfarma ko cin hanci da rashawa. Babban abin birgewa a matsayinka na ma'aikaci idan an cireka a gurbin da baka cancantaba za'a kaika wani gurbinne daya dace dakai bawai korarka za'ai ba a aiki balle kaje ka kama wata sabgar mara ƙyau kuma.
         A koda yaushe idan tunanin abu yazo masa yakan tunkari Raudha da shawara kafin ya fitar da shi ga abokan mulkinsa. Kasancewarta ta tashi ƴar talakawa, cikin takalawa da talauci yana taka rawar gani matuƙa wajen zaƙulo masa abubuwa masu muhimmanci na halin ƙunci da talakawa ke ciki a ƙasar. Idan kuma har yay bincike hakan yake samu. Wannan abu na ƙara saka masa ƙaunar matarsa mai yawa a zuciya, ko saɓani suka samu ta ɓata masa rai yakan rangwanta mata idan ya kalli hidimarta garesa....

        Duk fa wannan ƙoƙari na Ramadhan yana a idanun su forma president da god fathers nasu. Sai dai sunyi likimo ne na nuna goyon bayansu gareshi ɗari bisa ɗari har ya cika shekara biyun da suka ɗiba masa tun farkon fari. A cewarsu daga nanne wasan zai fara kuma. Tunaninsu ya ƙara tsaiwa ne akan abinda ya faru game da zubama Raudha maganin zubar da ciki da sanadinsa har yanzu kuku ke a hanun security na gidan gwamnati. Sunbi duk wata hanya daya kamata susan wani abu game da case ɗin amma an rufesa ruf sun gagara jin komai. Hakan yasa zukatansu ke basu akwai wani abu aƙasa da umarnin Ramadhan kuma aka cigaba da ɓoye kuku tabbas. Domin a bincike ɗaya da suka samu kansa suka tabbatar da hakan. Akwai yaransu cikin masu kula da cctv room na gidan, kuma sune suka sakasu lalata camara ta cikin kitchen da koda aka bibiya ba'a samu komai ba, sannan falon sama da bedrooms na shugaban ƙasa da first lady ke ciki babu cctv saboda sirrinsu ne, a ganinsu tunda har babu waɗannan hujjojin bai kamata ace ancigaba da riƙe kuku ba amma sai gashi har yanzu babu labarinsa.
     Waɗan nan dalilan suka sakasu tattara komai suka ajiye gefe acewarsu ya cika 2years ɗin da suka ɗiba masa tunda idan yasan wata ai baisan wata ba. Yana shaƙar poison a ac, yana sha a drinks wannan kaɗai ya ishesu. Kashe Bappi kuwa sun gama shirinsu tsaf akan hakan rana kawai suke jira.
         Itama Aunty Hannah wannan shine dalilinta na rage zuwa wajen Raudha ɗin, sai dai tana nan tana shimfiɗa mulkin da ko first lady ɗin batayinsa, wandama bai sani ba ya ga yanda ake bata tsaro idan zata fita saika ɗauka first lady ce, ga matan ƴan siyasa da masu mukaman gwamnati tun ta tattare ta saka a aljihu tanayin yanda taso dasu.
     Duk abinda take Hajiya Fanta naji kuma tana gani, sai dai ta bata lokacine acewarta ta gama nata kafin itama ta kammala nata shirin. Rashin sanin alwashin na hajiya Fanta kesa forma First lady Hajiya Bushira hamada da Aunty Hannah kejin duniyar da damar duka tasu ce a yanzu. Shiyyasa suke sake baje kolinsu yanda suke so.

To bara mu cigaba da binsu muga yaya wasan zai kaya🚶🏻😮😖.

*_TAURA HOUSE_*

            “Nifa nata ƙoƙarin naga na danne amma yaƙi dannuwa, hakan ya tabbatarmin zuciyata akan gaskiyarta take ba wasa baneba”.
       Pa dake kallon abokin nasa Alhaji Sageer Dogarai mai maganar yay ƴar dariya.
      “Alhaji Sageer yau kuma labaran almara ka koma kokuwa zaka fara tsara littatafai ne na marubuta, danni dai banko fahimci inda zancen naka ya kama hanyar zuwa ba balle dosa”.
     Dariya Alhaji Sageer yayi, tare da ƙurbar ruwan dake gabansu yana gyara zama. “Ko ɗaya Taura. Yanzu zan fiddo maka ainahin zancen dan na fahimci kai hausarma neman ƙwace maka take a harshe saboda yawon bin kasashe kamar ɗan sama jannati”.
    Dariya sosai sukayi a tare. Kafin su tsagaita Alhaji Sageer ya cigaba da faɗin.
      “Idan baka mantaba, a ranar ɗaurin auren yaran nan sanda muke shirin fita da kai bayan nazo na gaida Bappi, mun gamu da tawagar matar vice president”.
    “Ƙwarai anyi haka”.
“Yauwa Alhmdllh, matar da muka ɗan bigi juna har wayata ta faɗi itace tushen zancena. Sai dai zuciyata na cike da ruɗanin matar aure ce kokuwa?”.
       Ɗan shiru Pa yayi na nazari, sai kuma yaja numfashi da tunano ko wacece hakan ta faru. “Dogarai tabbas ban sanka da neman mata ba ko wani abu makamancin hakan tun bayan rasuwar matarka kuma komai bai sauya ba, to amma bazance zuciyata bazatai hasashen wani abu game da hakan ba. Dan a yanda na sanka bazakaima matar nan irin son da nake tunain zai dace da ita ba”.
        “Taura har yanzu ban canja ba, ina a yanda ka sanni wlhy. Ka ture batun yanda ka sanni akan son auren wayayyar mace mai zurfin ilimin boko, idan rawa ta canja dolene kiɗa ya canja shima a wasu lokutan. Ba wayewarta ko ilimnta na kallaba. Yanda naga kuna nuna jin kunyar juna kamar wasu surukai ne yaja hankalina sosai gareta, gata cikin shigar mutunci da kamala saɓanin sauran wanda ke tare da matar vice president. Wlhy har cikin raina sonta ya shigeni lokaci guda batare dana shirya hakan ba.”
        A karan farko Pa yay murmushi, dan yasan wanene Alhaji Sageer Dogarai. Abokinsa ne tunna kuruciya koma muce amini. Shekarar matarsa huɗu kenan da rasuwa yaransu biyu. Tunda ta rasu kuma bai sake aure ba duk da matan nakai masa tallar kansu tare da cece kucen jama'a da dangi akan ƙin sake auren nasa tunda bawai ya wuce hakan bane. Pa ya ɗan ɗage kafaɗa. “Bazance ban yarda da kai ba. Sai dai zance inhar kasan ba hakan bane a ranka dan ALLAH karka aikata abinda zai zubar da kimarmu. Domin kuwa ita wannan mata da kake magana surukatace. Mahaifiyace ga matar Ramadhan kuma a yanzu haka bata da aure dan sun rabu da mahaifin matar Ramadhan ɗin tuni. Yaranta huɗu, ta aurar da ɗaya akwai uku gabanta, sai dai tana shirin aurar da biyu yanzu haka ma”.
       “Alhmdllhi. Alhmdllhi”. Alhaji Sageer Dogarai ya faɗa yana kai goshinsa ƙasa domin yin sujudar shukur. Wannan ya sake tabbatar ma da Pa da gaske ne fa.

        ★Kamar da wasa ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa dai babu ɓata lokaci Pa ya tunkari Anne da Bappi da maganar. Sunji daɗi sun kumayi farin ciki, dan haka Bappi yace yabar komai a hanunsa.
     A ɓangaren Bappi ma bai tsaya jan al'amarin ba ya tunkari su Hajiyar Birni da shi, sai dai kamar yanda yay hasashe Asabe ta nuna bijirewa su Hajiyar Birni sukai mata can. Murmushi kawai Bappi yayi, tare da basu shawarar su barta tayi tunani, amma ta bama Alhaji Sageer Dogarai ɗin damar zuwa gareta tukunna sai ta yanke hukunci. Ta aminta da hakan, babu kuma ɓata lokaci Alhaji Sageer yazo gareta washe gari.
        Mutum ne kamilalle kuma mai tarin nutsuwa. Ba wani tsufa yayba dan shekarun nasa bazasu gaza dai-dai da Pa ba, ga iya magana dan a ƙankanin lokaci ya siye zuciyar Asabe har taji ta gamsu da shi. Sai dai bata amsa masa ba sai da ta garashi sosai. Shiko bai gajiya da binta ba har sai da ya samu amincewarta. Hajiyar birni kam ai likafa taci gaba burikanta nata tabbata bayan wahalar da taci a rayuwa da garari akansu. Wani lokacin bawa nayin gaggawa ne akan abinda baida masinaiyar UBANGIJI ya tanadesa cikin ƙaddararsa. Sai son zuciya ta sakashi tsayawa wajen nemansa koda ta hanyar data saɓama shari'a ne. Sai kaga yazo ya samu abin kuma daga baya.
      Alhaji Sageer ya matsa shifa ayi aurenau kafin nasu Fatisa. Itako ta dage akan a'a sai anyi nasu Fatisa. Bai haƙura ba ya cigaba da jajircewa har hajiyar birni ta tabbatar masa yanda yakeso haka za'ai. Sam Asabe bataso hakanba. Sai dai bata ƙaunar yima mahaifiyarta jayya ko kaɗan, sannan Aunty Halima na ɗorata akan shawarar ƙwarai na gara tai auren ko bikin ƴaƴan nata ya ƙara mutunci a idon mazajensu da al'ummar da zasu halarci bikin. Tasan gaskiya Aunty Halima ta faɗa mata, dan haka ta tara yaranta ta sanar musu Raudha kuma aka faɗa mata ta waya. Kamar yanda su Fatisa suka nuna kishin Abbansu a fili haka ma Raudha. Dan kuka ta dinga rusawa akan ita bata yarda Mummyn nasu ta sake aure ba.
       Shi dai Ramadhan ma da yaji tushen kuka. tagumi ma kawai yay yana kallonta. Sai da tayi mai isarta sannan yay magana.
       “Oh ni Ramadhana naga takaina. Ni karma a haifamin yara masu kukannan fa? Yanzu ke Partner dan ALLAH ba abin farin ciki bane Mummy tai aure? Kinada ilimin addini fa, kin kuma san babu sauran aure tsakaninta da Abba taya zata cigaba da zama kuma a haka bayan har yanzu shekarunta basuyi nisan da hakan zai kasance ba”.
      Baki ta tura gaba da juya masa baya zata kwanta ribda ciki ya riƙota. “K rufamin asiri, da wannan cikin zakiyi wannan kwanciyar?, ga Abba ya samu mai tayasa kishi ni ki halakamin nawa.”
     Dama ba kwanciyar zatai ba. Dan yay magana tai hakan, ta sake tura baki da buge hanunsa dake riƙe da cikinta daya sake fitowa sosai yanzu kowama zai iya shaida akwaishi.
        “Ni dai yi haƙuri karki cinyeni da baki, yarana suzo suga an gama gwaguyeni”.
      Filo ta ɗauka ta shiga kai masa duka yana karewa da dariya, sai kuma ta mike daga gadon ta sauka tana daddaga kafa. Saurin riƙota yay ya zaunar a cinyarsa. Zata ɓare masa da kuka ya ɗaura lips nashi kan nata daga haka labarin ya canja.
      Bai bartaba sai da ya tabbatar dukkan damuwarta ta gudu sannan suka shiga toilet suka tsarkake kansu tare. Bayan sun fitoma nasiha ya dunga mata har sai da ta fahimcesa ta sakama auren albarka. Suka kuma kira Asabe tare suka gaisheta da nuna mata goyen bayansu dan yanzu dama Ramadhan kanyi waya da Asabe da M. Dauda lokaci-lokaci. Hakanne ya ɗan ƙara sakama Asaben nutsuwar zaman Raudhan tare da shi.............✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 73_*


..........A wata juma'a datai dai-dai da saura kwanki huɗu cikar shekarr Ramadhan guda a mulki aka ɗaura auren Alhaji Sageer Dogarai da amaryarsa Asabe. Aure ne daya tara ɗunbin al'umma musamman daya kasance juma'a ne mutane duk sun halarci masallaci. Aure ne daya saka wasu farin ciki wasu saɓaninsa musamman aunty Hannah da tun farkota nuna adawawta akai, sai dai kuma babu abinda ta isa ta hana daga hukuncin ALLAH.
      Ƴar walima kawai akai amarya ta tare ɗakinta cikin aminci da mutuntawa. A kuma daren Ranar M. Dauda da abokinsa suka iso Bingo a haukace a dalilin M. Gambon ya samo labarin a shanun ƴan talla. Inda ALLAH ya taƙaita al'amarin ya kira Bappi ta waya kafin su tunkari ko'ina. Hakan yasa Bappi saurin taka masa birki yasa Malam Adamu zuwa ya ɗakkosu. Babu wanda yasan da zuwansu Taura House sai Anne da Bappi. Aka basu masauki mai ƙyau da abinci kafin safiya. Da farko M. Dauda ya nuna shifa ba wannan ya kawosa ba Bappi dai ya sake lallashinsa.

     Washe gari da suka zauna akan batun fir ya nuna shifa sai Alhaji Sageer Dogarai ya sakar masa matarsa inhar ana buƙatar zaman lafiya a NAYA. Iya nasiha yaƙi har sai da Bappi ya bama Ramadhan Umarnin sakawa a kawo masa Raudha gidan. Tana makaranta M. Adamu yaje ya ɗakkota. Gaba ɗaya hankalinta a tashe yake dan batasan mike faruwa ba. Gashi babu damar kiran Ramadhan ta damesa tasan yana office. Sai da suka iso taci karo da Abbansu ta sauke ajiyar zuciya. Yay sakalo yana kallonta da cikinta daya fito ɗas duk da ma hijjab ne a jikinta har ƙasa. Sai dai a yanda tai zaman sai da cikin ya fito.
       “Oh ALLAH sarki Raudha ashe wannan irin arziki ALLAH yaymin naketa shirme ma? Dama ciki ne da ke?”.
     Ina ƙasa Raudha ta shige dan kunya, Bappi yay murmushi mai faɗi da gyaran murya. “To kaga kariga ka fara zama babban mutum tunda ga jika kana shirin amsa duk da nasan bashi bane na farko. Ya kamata wasu abubuwan a ajiyesu hakanan kodan wasu dalilai Malam Dawood. Shi aure raine da shi, sannan ƙaddarace ta ALLAH. Ya riga ya ƙaddaro zaka zauna da mahaifiyar yaran nan na wani lokaci ku rabu, idan kuma da rabon sake zama sai kaga ta sake baro can ta dawo gareka ai”.
     Hawaye malam Dauda ya share dan harga ALLAH yana son Asabe, so irin wanda bai tabama wata mace ba. Dan ko auren nan daya kara na budurwa dal a leda bai maye masa gurbin rashin Asabe ba a ransa. Nasiha sosai Raudha da Bappi sukai masa, sai dai M. Gambo nata zungurinsa akan karya yarda wai. Tsaf Bappi ya fahimci M. Gambo, ya kuma gane shine matsalar M. Dauda. Dan haka a ranar ya saka aka maidashi Hutawa bayan ya haɗashi da shatara ta arziki.
      Sosai M. Gambo yaji zafin hakan, dan acewarsa ƙiri-ƙiri an nuna banbanci tsakaninsa da M. Dauda. hakan ya sashi ƙudirin abubuwan mugun abu da yawa cikin rai game da M. Dauda. Acewarsa in bai samu Asabe ba ai akwai hanyoyin ramuwa da yawa.
  
      Kwanan malam Dauda biyar a Bingo, dan har gidan gwamnati aka kaisa ya kaso kwarkwatar ido wannan karon. Bappi kuma ya riƙesa akan ya zauna har sai anyi bikin cika shekara guda na Ramadhan a mulki. Hakan ya masa daɗi sosai, ya kuma sakashi farin ciki. Su Fatisa ma har nan Taura house sukazo gaida shi, har kuma zuwa yanzu bayan su Anne babu wanda yasan da zamansa a gidan.

*_GOVERNMENT HOUSE_*

          Sosai aka shirya bikin cika shekara ɗayan nan har abun ya ɗan so bama mutane mamaki, dan lamarin tamkar wani arashi. An shirya ɗakin da taron zai gudana cikin tsarin ado na tutar ƙasar NAYA. Duk da gwamnoni suma zasuyi nasu a jihohinsu hakan bai hanasu halarta ba. Hakama sarakunan gargajiya da abokan kasuwancin Ramadhan.
        Su Alhaji yaro glass da muƙarrabansa harma da god fathers nasu kam sun halarci taron. Sai tarin manyan ƴan jam'iyya na kowace jiha. Kamar ko yaushe First Lady da mijinta shugaban ƙasar NAYA *_Ramadhan B. Hameed Taura_* suka iso wajen taron cikin shiga ta kamala ana take musu baya. Sanye take da hijjab har ƙasa fari ƙal mai hannu, sai kaɗan daga ƙasa ake iya ganin ƙasan doguwar rigarta mai kalar tutar ƙasar NAYA. Daɗin daɗawa akwai facemask a fuskarta tare da siririn farin glass iya hannayenta kawai ake iya gani da tsadajjen agogonta. Hakama shugaban ƙasa Ramadhan sanye yake cikin ɗanyar shadda fara ƙal daketa maiƙo da haska idanun mai kallo. Ta gaurayu da ɗinki na musamman daya ƙawatata ya kuma tabbatar fitar tutar ƙasar NAYA. Hakama hularsa zannah tayi matuƙar murzuwa. A kallo guda zaka tabbatar da tarin kwanciyar hankali da farin ciki tattare da shi. Yana riƙe da hanun matarsa har akai masa rakkiya wajen zamansa sannan mutane da suka miƙe dominsa na girmamawa suka koma suka zauna.
      Kamar yarda shari'a ta tanadar malamai sun gudanar da addu'oi kafin a fara gudanar da abinda ya tara mutane a wajen. Inda bayanin shugaban ƙasa yay matuƙar birge mutane da ƙara darajarsa a idanusu. Lokacin da aka buƙaci cewar first lady.
       Wata hamshaƙiyar mace ta miƙewa da takarda a hanunta ta tabbatar musu ga saƙon first lady ita  wakiliyarta zata isar bisa umarnin shugaban ƙasa amma matsayin miji ba shugaba ba basai tace wani abuba.
      Hakan ya bama wasu mamaki, ya birge wasu. Wasu kuwa sun gumtsi gulma da sauya zancen a muhali na daban. Oho hakan bai damu Ramadhan ba, shidai burinsa tsare mutuncin iyalinsa da kuma kishinta da yakeyi. Bayanan da aka gudanar matsayin na first lady ma sun kayatar kuma sun birge mutane daban-daban. Daga haka taro ya cigaba da guna. Anci ansha anyi hani'an first lady da shugaban kasa babu wanda yasha ko ruwa a wajen.
       Sai da ana gab da tashi a taron ne Raudha ta hango Abbanta tare da Alhaji Hameed Taura cikin shiga ta kamala tamkar bashi ba, dan kayan daya saka sun masa ƙyau matuƙa duk da jikin ya nuna ba'a saba sakawa ba. Taji daɗin yanda ya kame kansa a wajen har aka tashi lafiya.
    
     Duk yanda Raudha ke ɓoyen cikinta a hijjab hakan bai hana wasu ganewaba, tuni kuma yan jarida suka hau yaɗa cewar shugaban ƙasa gab yake da zama angon karni kuma Baba dan firt lady na ɗauke da ciki. A fanin ƴan adawa kuma sun gama baza zance first Lady dai turancine bata iyaba shiyyasa Ramadhan ya hanata magana a wajen aka samo kwararriya aka fake da kishi.
     Maganar tayi nisa sosai, sai dai cikin Raudha yaso danneta tare da manyan ayyukan da aka zano shugaban ƙasa Ramadhan ya shinfiɗa a shekara guda kacal.
      A ɓangare. su Alhaji Yaro glass sunyi zaman meeting akan cikin nan, inda kai tsaye suka ƙalubalanci Aunty Hannah data ɓoye musu hakan. Ta nuna batasan Raudha nada ciki ba itama, amma hakan bashike nuna batai murnaba. Dan ita tanada manufa akan cikin koba komai zasu kasance da wani kaso na dukiyar Taura family musamman idan aka dace Raudha ta haifo namiji.
    Wannan magana tata ta banƙanta ran su Alhaji Yaro glass, harya faraji a ransa Aunty Hannah bazatai dogon zangoba zai kawar da ita. Dan ya tabbatar shi ɗinma zata iya yin kalar tunanin da take furtawa akan dukiyar Taura family akansa kenan. Duk da kuwa Samha ce kawai a tsakaninsu har yanzun.
     To komadai miye, mudai ƴan kallone ai.🤣

Kwanaki biyu da yin wannan biki na cikar masu mulki shekara ɗaya akan madafun iko Malam Dauda ya koma hutawa da shatara ta arziƙi. Dan kuwa kujerar makka har uku, tare da kuɗi masu yawa da galleliyar mota da alƙawarin buɗe masa manyan shaguna a hutawa da kuɗi zasu dinga shigo masa akoda yaushe. Wannan farin ciki ya sashi danne son Asabe daya san har Abada bazai iya dainawaba.
        A randa M. Dauda yabar Bingo a ranar hoton wani video ya karaɗe yanar gizo da duk mai wayar da take iya buɗe data zai gani. Video ne daya kasance na Aynah a cikin club ana aikata masha'a da ita. Sai kuma wani shima a cikin ɗaki kusan su biyar duk mata. Abinda zai baka mamaki na club ɗin babu face mask kamar yanda Ramadhan ya sani.
      Aminu ya saki wannan video ne bayan ya saka dukan abokansa sunyi amfani da Aynah a wannan dare wasuma harta baya (Wa'iyazubillah😭) yayi hakane a dalilin kawo mata ƴammatansa da yay gidan ta nuna itafa ta gaji ya sallameta hakanan kokuma ta tona masa asiri ga iyayensa da yake yaudarar nuna musu shi ɗin mutumin kirkine. Shiko ya tabbatar mata kafin tayi hakan shi zai fara tona nata a sirin wa duniya sai yaga nata da nashi wannene zaifi gawurta da kayatarwa. Tayi kuka ta roƙesa iyakar roƙo amma yay kunnen uwar shegu da ita sai da ya saki.
      A lokacin da wannan video ya riski su Addah Asmah data haukata kanta a neman asirin hallaka Ramadhan da wulƙanta rayuwarsa data Gimbiya Su'adah har ƙasar China ta yanke jiki ta faɗi. Kwannta biyu kenan da dawowarta NAYA, wata kawarta ta rakata China wajen wani gagarumin masanin tsafi. Sun dawo zuciyarta cike da jin ɗunbin nasara saboda abinda matsafin ya haɗo musu, ta tabbatar idan har tai amfani da su Gimbiya Su'adah da zuri'arta sun zama labari kenan. Sai gashi a yau da take shirin zuwa Taura house da fuskar yaudarar roƙon gafarar gimbiya Su'adah danta aiwatar da aikinta wannan mummunan labari ya  baje ƙasar NAYA dama duniya tunda abune na media ako ina zaka iya ganinsa.
     A firgice ma'aikatan gidan nasu da kanwar Aynah suka rufu a kanta sai dai babu alamar numfashi tattare da ita. Dole Zulfah tai kiran asibitin da suke ganin likita dan ta nema no na daddyn su ma bata samuba kasancewar shi bayama kasar.
     

          Hatta da gimbiya Su'adah da ayanzu babu wanda ta tsana a duniya sama da ƴar uwar tata abin ya firgitata, balle kuma Fulani da itama ta yanke jiki ta faɗi ƙasa a sume dalilin tanada hawan jini.
     Raudha ma ta gani kafin Ramadhan, amma ta kasa nuna masa sai zama datai taita kuka dan abun ya ɗaga hankalinta. Musulma ɗiyar muslmai gaba da baya itace a wannan halin duniya ke gani babu ko kunyar mahaliccinmu. Kaicon wata wayewar, kaicon wata dukiyar, kaicon wata damar dan da wata BAƘAR INUWA ce da ita gara rana ma.
      Koda Ramadhan ɗin shima ya gani baiji abin saboba tunda a gabansa aka aikata, sai dai abinda ya bashi mamaki fitar videon bayan shekaru. Hakan na nufin dan kinyi barna ko kayi ka binneta da tunanin ta wuce mutane bazasu ganiba watarana UBANGIJI idan yaso sai ya tonota ta hanyar da kai bakai tunani ko tsammani ba. Sannan ya jiraka a madakata kazo ya hukuntaka dai-dai da laifinka dan shi bai kasance azzalumin sarki ba...........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 74_*


..........Faɗuwar Addah Asmah ta jawo mata shanyewar ɓarin jiki, yayinda lokacin da Aminu ya kawo Aynah har gida da takardar saki uku bayan dukan daya lakaɗa mata ya sake ruɗar da jikin na Adda Asmah har sai da takai Zulfah ta kira gimbiya Su'adah tana kuka akan tazo ta taimakesu Mom ɗinsu zata mutu.
     Jini ba wasa bane, dan duk yanda gimbiya Su'adah taso ignoring al'amari ya gagara gareta, har hawaye tayi itama ganin video na Aynah hawan jininta ya nema tashi. Tanda halayen banza ta wani fanin, amma tanada zuciya mai ƙyau kuma. Dama can zugar Addah Asmah ɗin ce da fulani ke sake kangarar da ita wani lokacin. Haka ta shirya Safina na roƙonta kartaje dan ALLAH Mardiyya tace danmi? Ita rayuwa ai ba'a maida sharri da sharri. Koba komai ai ALLAH ya nunama Adda Asmah ita ba komai bace ba, sannan duk makircinta a karƙashin hukuncin ƙaddara da jarabawa yake. Idan Maah taje gareta a yanzu Ai sake tabbatar mata zakaran da ALLAH ya nufa da cara ko ana muzuru ana shaho sai yayi ne. Sannan babu hanun daya isa canja ƙaddarar ALLAH sai dai kai wahalarka ka ƙare a wahale wanda kakeyi dominsa yana ƙara zama sama da kai.
     Da wannan zantuka na Mardiyya suka ɗunguma gidan Addah Asmah, inda suka isketa ita kwance Aynah kwance cikin jini na dukan da taci hanun Aminu. Da taimakonsu aka wuce da su asibiti, a kuma daren mai-martaba da fulani suka iso suma. Sunji daɗin ganin Su'adah da yaranta a wajen, suka shiga sanya musu albarka. A daren shima Daddyn Aynah ya iso, bai kumayi zaman ɓata lokaci ba akai shirin fita da su waje dan jikunan nasu su duka yayi tsamari sosai.
      Da Fulani suka tafi, gimbiya Su'adah tai kememe tace babu inda zataje hakama ƴaƴanta. Babu wanda yaga laifinta anan, dan ansan an cutar da ita...

___________________________

         Wannan hatsaniya na cigaba da yaɗuwa cikin Raudha na ƙara girma. Komai nata ya canja, idan kaganta sai kace ba ita bace. Auren su Fatisa hanata zuwa hutawa Ramadhan yayi, iyakarta nan Bingo sabon gidan Mummynsu da yake anan akai yinin biki kamar yanda Alhaji Sageer Dogarai ya roƙa. Anyi yinin biki laraba Raudah ma a kwance ta yini da zazzaɓi, amma dan jaraba tana a gidan ɓoye. Da dare Alhaji Sageer Dogarai da kansa ya maidata government house duk da kuwa anzo daukarta, kuma dama tana tare da guards nata. Ba kowa yasan Raudha na gidan ba ƴan biki, sai da zata wuce gida. Aiko abin ya bama kowa mamaki kodan yanda Aunty Hannah tazo ita tana baza mulki kaikace itace matar shugaban ƙasar ma. Washe gari Alhamis ƴan biki suka ɗunguma Hutawa, inda akai musu tarba ta mutunci dan yanzu M. Dauda Alhmdllhi, duk da dai ginin shagunansa ko muce super market bai gama kammaluwa ba har yanzun. Amm kuɗaɗen daya samu ba ƙaramin barje guminsa yake ba. Kujerar makka kuwa ya rike sirrin a ransa shi da Inna da Baba Nafi zasu.
      Ranar Juma'a aka daura auren su Fatisa da mazajensu. Auren daya bada mamaki kasancewar shugaban ƙasa Ramadhan ya halarta tare da wasu gwamnoni da ministers. Hakama Alhaji Hameed Taura da Alhaji Basheer Hameed Taura. Ga Alhaji Sageer Dogarai da tasa tawagar dan a cewarsa su Fatisa shima ƴaƴansa ne. Saboda Asabe ta riƙe masa nasa da amana, duk da kalubalen data ɗan fuskanta ga yaran a farkon auren, sai dai halin kirki data dinga nuna musu da nuna rashin damuwa da abinda suke matan ita da Yasmin sai suma suka risina suka bata haƙuri ta haɗa ta rungume ta zame musu uwa.

     Sam Raudha bata san Ramadhan zaije ɗaurin auren ba sai gani tai alabarai da aka nuna dalilin zuwansa wajen. Jitai fushin da take da shi ya kwaranye. Dan tunda yace bazatajeba take haushi da shi, ta kama matsar kwalla Basma na lallaahinta. Koda ya dawo gidan bayan la'asar kasancewar a helicopter yaje ya dawo saita rungumesa tana kuka da jera masa tagwayen godiya.
     Murmushi yay kawai ya kama hanunta suka shige ɗakinsa. Ya zauna akan sofa tare da ɗoraya bisa cinyarsa duk da ƙaton cikinta bai damu ba.
       Sai da ya ɗan sumbaci lips nata yake faɗin, “Partner yanzu kin lalace wlhy, komai kuka komai fushi kamar ba Ustazah ɗina mai haƙuri da juriya ba. Anya kuwa ranar shiga labour room ba akwai aiki gagarumi a gabana ba?”.
         Kwanciya tai jikinsa tana murmushi da hawaye. “ALLAH Noorullah dan baka san wahalar bane. Cikin nan ya isheni ji nake kamar na cire na huta”.
     Murmushi yayi mai kayatarwa, ya ɗaura hanunsa a saman cikin nata yana shafawa. “Kiyi haƙuri jarumata saura ƙiris insha ALLAHU. Kedai kawai mu cigaba da addu'a ALLAH ya saukeki lafiya ok”.
     Kanta ta ɗaga masa da sumbatar kumatunsa. Kafin tace, “Shine ka tafi Hutawa ɗaurin aure koma ka sanar min”.
       “Hhh haba ƙawata, ina sanar miki rigima zaki sakamin da shagwaɓa, ni banjeba ke bakije ba”.
     “To amma tunda kasan zaka basai kaje dani ba da an ɗaura auren sai mu dawo tare”.
          “Ke ɗin ce zaki yarda muje mu dawo a ƙanƙanin lokacin nan. Yi haƙuri ai dakin haihu insha ALLAH zakije ki kai musu baby su gani. Kimma san ya mukai da Anne?”.
      “A'a”.
Ta faɗa tana girgiza masa kai.
      “Wai Taura house zaki koma da zama har ki haihu yaro yay ƙwari. Cikin farin ciki ta miƙe zaune sosai a jikinsa. “Kai amma naji daɗi ALLAH, koba ko....”
    Baima bari ta ƙarasa ba ya mangare mata kai yana hararta. “Oh kinmaji daɗi kenan. To ai a take nace mata ban yardaba sai dai ita ta dawo nan”.
     Baki ta tura masa gaba. “ALLAH wannan buƙulune kawai zakamin”.
   Dariya ya ƙyalƙyale da shi mai kayatarwa. “Naji gara hakan, nida aka shirya yima buƙulun barina gaurofa. Muna nan tare ki haihu muyi rainon babynmu kamar yanda mukai na cikin”.
       “Uhmm kaji wai mukayi, nadaiyi abina”.
    Gira ya ɗage sama, yana mai kai bakinsa saitin kunenta. “To amma wake ƙarama babyn ƙarfi bani ba”.
    Kansa ta ture da sauri tana ƙoƙarin tashi ya hanata. Haka ya cigaba da tsokanarta yana kunnata tana masa shagwaɓa. Daga ƙarshe suka koma gado sannan sukai wanka tare kamar yanda suka sabarma kansu a yanzu musamman irin wannan wankan na lada.
           Kamar koda yaushe langyare masa tai, dan ba karamin jigata take ba a duk sanda hakan ta faru, sai takai ya mata tausa da lallaɓata tayi barci ake rabuwa lafiya. Yanzun ma bayan tayi barcin fita yay zuwa dinig yayi lunch dan yunwa yakeji sosai.

    

*____________________________*

        A kwana a tashi babu wuya wajen UBANGIJI. Raudha ta cigaba da rainon cikinta cikin kulawar ALLAH da Ramadhan, duk da nauyin Al'umma dake a kansa yana iyakar ƙoƙarinsa gareta itama. Ga gimbiya Su'adah kadaran kadahan tsakaninsu, ba gallazawa babu nuna damuwa. Dan ko Taura House taje zata gaisheta ta amsa ba kamar da ba sai dai iyakar gaisuwarce. Bazata kulataba bazata kuma hantareta ba. Hakama tsakaninta da Aunty Hannah, takan leƙo gidan lokaci-lokaci su gaisa, wani lokacin da mutanenta ƴan siyasa, wani lokacin ita kaɗai sai guards nata. Sau uku tana zuwa gidan Mummynta Asabe. Hakama gidan su Bilkisu dake nan Bingo duk taje. Su Fatisa ne dai har yanzu bata leƙaba saboda ba'anan Bingo suke ba.
      A haka cikinta ya shiga watan haihuwa raki da shagwaɓa ya ƙaru, dole kuma Aunty Zuhrah ɗiyar Yafendo ta dawo nan government House da zama dan Anne dai taƙi hakan duk da kuwa Ramadhan jikane. Tunda watan ya shiga kwanakin haihuwa ta daina zuwa makaranta, sai ta dai su Basma suzo su mata bayanin abinda akayi. Randa takejinta da lafiya ta fahimta, saɓanin hakan tace su barta karatunma baza'ayiba. Sukan mata dariya da tausayinta. Dan hatta uban gayyar idan ta birkice masa da rikici dariyarsa yake kwasa kafin ya koma lallashinta a shirya da ƙyar.
        Tun dai ana saka ran haihuwar har kwanakin da aka bata a sibiti suka gota, koda Ramadhan ya nuna damuwarsa Dr Hauwa tace karya damu ana samun irin hakan ai ba komai bane. Adai cigaba da mata addu'ar sauka lafiya ..........✍


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
     

*_Typing📲_*


*_Episode 75_*


...........Alhmdllhi a wani dare na juma'a da yay dai-dai da cikarta watanni goma cif ta farka da gigitacciyar naƙuda. Rikicewa Ramadhan yayi, da ƙyar ya iya control ɗin kansa ya saka jallabiya sannan ya fito kiran Aunty Zuhrah. Da taimakonta suka ɗauki Raudha zuwa clinic ɗin gidan, yayinda tuni su Basma sun sanar ma Anne. Babu bata lokaci a daren Anne da Dr Hauwa suka nufo gidan, inda suka samu har wata Dr ta shiga da ita ɗakin haihuwar. Babu ɓata lokaci Momyn Jafar ta rufa musu baya itama, aiko ta tarar Dr Ingoze na niyyar halaka yaro dama uwar. wata irin muguwar bangaza takai mata tare da sauke mata tagwayen maruka, daga haka ta hankaɗota waje ta koma kan Raudha.
    Kowa yayi mamakin yanda aka hankaɗo Dr Ingoze waje. Gashi Dr Hauwa tace security su rike mata ita har saita fito. Hakan kuwa akai zuciyar su Anne fal wasuwasi. Dama shi Ramadhan suna kawota ya koma ciki kamar yanda Aunty Zuhrah ta bashi umarni. Maimakon zama sai yay alwala ya fara nafilfili da nemawa matarsa sauƙin naƙuda da fatan sauka lafiya.
     Tabbas Dr ingoze tama Raudha lahani, sai dai cikin amincin ALLAH an samu damar ciro jaririn ta hanyar theatre kamar yanda Dr Hauwa ta yanke shawara. Dan ƙarfin Raudha ya nema karewa saboda yanda Dr ingoze ta dinga danna kan yaron yana ƙoƙarin fitowa kafin zuwa Momyn Jafar.
      Sai gabanin asuba suka fito, anci nasarar ciro santalelen yaro gashi ƙato alamar uwarsa taci ta ƙoshi. Sai dai babu damar ganin Raudha har sai ta samu isashen hutu kamar yanda Dr Hauwa tace. Atake murna ta gauraye gidan na gwamnati, kowa kuma nama Raudha fatan samun lafiya. Lokacin da jariri yaje hanun uban gayya Ramadhan hawaye yaji sun cika masa ido. Ya sumbacesa tare da rungume abinsa yana maijin kaunarsa na ratsashi. Wannan shine karo na biyu da ALLAH yay masa ƙyautar da kuɗi basa badata, hakama mulki da ɗaukaka. Ya bukaci ganin Raudha duk da Dr Hauwa taso dakatar dashi ya bata haƙuri, dole aka ƙyalesa ya shiga shi kaɗai ya dubata. Tausayinta ya kamashi, ya dinga jera mata tagwayen kiss's da addu'oi.

     Zuwa wayewar gari labari ya karaɗe lungu da sako na ƙasar NAYA akan shugaban ƙasa ya samu ƙaruwa. Ga hoton Baby nata yawo saboda su Basma da sukaita turawa ƴan uwa da abokan arziki. Sai yazam kowa ƙoƙarin ɗorawa yake a shafinsa, wasu idan sun gani suma sai su ɗauka daga haka ya karaɗe wayoyin mutane. Yaro yasha addu'oi yayinda ƴammata da yawa suka koka dajin kishin inama daga jikinsu ya fita. Sultana dake ƙasar America kam harda kwanciya ciwo dan har yanzu ciwon son Ramadhan na zagaye da ita. Kawai dai babu yanda zatai ne tunda ya faɗa mata iya gaskiyarsa shi baya ra'ayinta tayi haƙuri ta samu mai sonta..
     Karo na farko, lokaci kuma na farko da Gimbiya Su'adah ta kira waya tasa aka haɗata da Raudha data farka a washe gari da rana. Yajiki tai mata da fatan samun lafiya. Ita dai Raudha abun ma har hawaye ya sakata. Ramadhan dake gefenta yasa hannu yana share mata fuskarsa ɗauke da murmushi.
     Ɗansa dake hanunsa yanata barci ya kalla. Ya shafi lips yaron jajaye yana faɗin, “Ba kuka zakiyi ba Partner. ALLAH zaki godemawa a wannan gabar, ni shaida ne Maah ta jima dayin nadamar abinda tai miki, ta shanye a cikintane kawai saboda nauyin tunkararki. A yanzu kam koda abinda ke faruwa da Lubnah a gidan miji ya isa sake tsoratata”.
     Da mamaki Raudha ta dubesa. “Aunty Lubnah kuma?”.
     Kai ya jinjina mata batare da ya kalletaba ya cigaba da wasa da sumar yaron. “Eh Lubnah. Tun satin da aka kai Lubnah gidan aure bata sake farin ciki ba. Kuskure kaɗan miji zai lakaɗa mata duka tare da ƙanensa. Ke hatta da uwar mijinma ba ƙyaleta taiba itama dukan nata take. Duk da dukiya irin ta gidan su Mansur ƙiri-ƙiri suka sallami kaso ɗaya bisa biyun ƴan aikinsu aikin ya koma kan Lubnah. Cikin ƙanƙanin lokaci ta fita hayyacinta saboda azaba. Ameenatu, tun sanda Lubnah ta kawo Mansur garemu matsayin miji na nuna ƙin amincewata, saboda na jima dajin labarin mahaifiyarsa bata zama da sutukai. Hakama kanensa basu da isashen tarbiya. Amma sai Maah taƙi saurarena saboda Lubnah tace tana son sa akace ai nima wadda nake aure bata dace dani amma suka amsa. Dan haka Lubnah zata auresa ko ina so ko banaso. To ga sakamakonan sun gani, dan yanzu a dalilin dukan da surukar mijinne tai mata tai ɓarin cikin jikinta, maimakon Mansur ɗin yaji tausayinta sai ya maidota gida da takardar saki har uku wai yana zarginta da tarayya da drivernsu kiji sharri. Koda nai bincike uwarsace duk ta tsara hakan kamar yanda take koran matan ƴaƴan itama tai sanadin da za'a korota”.
        Sosai abun ya taɓa zuciyar Raudha duk da zaluncin da su Lubnah suka dinga mata a baya. Ta jingina kanta da kafaɗar Ramadhan tana kallon babynsu hawaye na zubo mata. Shima rungumita yay da hanunsa cikin son kore mata damuwarta yace,
        “Ustazah dawa yaron nan ke kama?”.
      “Dani mana”
Ta bashi amsa tana share hawaye. Ƙeyarta ya ɗan tallara kaɗan. “Son kanki yayi yawa madam. Kowa yaga Abdull-Hameed Ramadhan Taura yasan gida ya ɗakko, mufa jininmu ƙarfine da shi yarinya”.
     Murmushi tayi mai ƙayatarwa da cewa, “Uhm nidai basan cika baki. Dama da Pa kace yana kama ko Bappi sai na yarda”.
     Dariya yay yana mai sumbatar kumatunta. Hakama babyn ya sumbaci goshinsa. “Bakice komai akan sunan dana kirashi da shi ba”.
    Murmushi tayi mai kyatarwa da shafa kumatunsa. “Saboda shine ra'ayina shiyyasa nima”.
      “Woow sweetheart inajin daɗi idan muka kasance bisa tarayyar abu guda”.
     “Noorullah! Idan duk yarana zasu kasance da sunan Bappi ko Pa ko Anne ko Maah ko kai bazan taɓa baƙinciki ba. Fatana dai ALLAH ya bani ikon sauke nauyinka dake kaina ka kuma zamemin miji har a gidan aljanna. ALLAH ya raya Abdull-Hameed Ramadhan Taura ya albarkaci rayuwarsa. Yasa yay gadon ƙyawawan halayen Bappin da Pa da kai kanka”.
      “AMin ya rabbi sweetheart. ALLAH yay miki albarka ya ƙara miki lafiya. Yasa nan da wata shekarar mu sake dawowa labour room.....”
      Da sauri ta rufe masa baki ƙwalla na ciko mata ido. “Wannan ai fatan tsiyane”.
     Dariya ya kyaƙyale da ita yana ture hanunta. Miye na wani fatan tsiya anan ai nasan zaki iya Mrs Taura.
    Haka suka kasance cikin nishaɗi har saida Aunty Zuhrah tazo ta korashi ɗakinsa sannan.

         ★Sai da Raudha ta warke sosai aka fara shirye-shiryen taron suna, amma kowa dai yasan sunan yaron Abdul-Hameed anma Bappi takwara. Ramadhan yaso ayi suna a Taura house Bappi ya hana yace ayi a government house kawai. Badan yaso ba dole hakan aka shirya. Taron sunane daya haɗa manyan mutanen ƙasar NAYA lungu da saƙo, inda amaryar jego da baby sukaci ƙyau har suka gaji. Shi kansa angon jegon yayi tsaf dashi kamar yana shirin yin sabon aure. Anci ansha an kumayi bishasha, inda yaro ya samu ƙyaututtuka masu ban mamaki wasuma dan riya sukai badan ALLAH ba. Dan kawai wane yayi kar ace su basuyiba.. Hatta M. Dauda ba'a barsa a bayaba ya haɗo kayansa na jego harda saitin robobin wanka da saƙe saƙin wanka na icce da ƙatuwar garwarsa ya kawo. Wannan abu yasa su Aunty Hannah takaici duk da ba'a wajen taron ya bayarba. Sai dai ita Raudha farin ciki tai ita da Ramadhan.
        A zahiri taro ya tashi lafiya, sai dai a baɗini wasu sun iso wajen taron ransu da ƙulli. Ba su kowa bane sai su Alhaji Yaro glass da ko Aunty Hannah yanzu batajin sirrinsu. Bayan taro ya tashi lafiya wajen ƙarfe biyar na yamma a tsakanin government house zuwa Taura house aka buɗema motar Alhaji Hameed Taura wuta. Harbi ne irin na kwararrun maharba da ko a nesa suka harbo harsashi sai ya isa ga wanda suka hara ɗin. Sai dai in ALLAH ya kaddara da kwananka a gaba ka tsalle domin ikonsa.
     
         Tabbas masu harin sunyi nasarar kaima motar hari sai dai basu taki sa'a ba, amma duk da haka ɓarnarsu ta shafi Taura house. Bayan kammala walima Alhaji Hameed ya shiga mota shi da Anne da su Yafendo domin komawa gida. Sai dai kiran Daddyn Aynah ya riskesu akan rikicewar jikin Adda Asmah gashi ya kira Gimbiya Su'adah bata amsa ba. Hakanne yasa suna ɗan gota government house Bappi da Anne suka fita amotar suka shiga wata harda Yafendo, Inna kuma dake fama da ƙafa tunkan su tafi wajen walimar dama danta dagene Bappi yace a wuce da ita gida. Kasancewar motar da su Muneera ke ciki suka amsa ɗin yasa Muneera dawowa wajen Inna ita kuma. Su Alhaji yaro glass basu san da wannan canji da aka samuba suka sanarma yaransu tahowar Bappi da sanar dasu motar da yake ciki su shirya.
       Idan UBANGIJI bai ƙaddara mutuwarka ga makiyiba, komai wahalar mai wahala sai dai ya dawwama cikin wahalar farautar zafin rana data ɗacin zuciya babu nasara.

*_ALLAH ka shiga tsakaninmu da maƙiyanmu😭🙏🏻._*

       Take a wajen ma ALLAH yay ma Inna Rasuwa, dan sai gawarta aka nufi asibiti da ita. Driver da Muneera ne kawai ke numfashi. Shima driver ko mintuna biyar basu cikaba ya rasu.
    Karaɗewar labarin wannan hari da aka kaima Alhaji Hameed Taura cikin kanƙanin lokaci yasa ko zama basuyi a gidan Adda Asmah dake a mawuyacin hali itama suka taho. Hakama Raudha da Ramadhan da su Aunty Zuhrah duk sun rikice a government house. Dan kuwa babu abinda kake gani a yanzu akowane gidan tv sai harin da aka kaiwa Alhaji Hameed Taura. Amma abinda yaba mutane mamaki kamar yanda yan jarida ke faman shelantawa babu shi a motar duk da kuma daga government house kowa yaga motar ya shiga har shugaban ƙasa yay masa rakiya.
     Zamu iya cewa a wannan dare gaba ɗaya NAYA a hargitse ta kasance. Dan ba'a samu damar bizne gawar Inna ba saboda jami'an tsaro sun rike. Kuka Raudha take tana sambatu da ambaton “Su din azzalumai ne. Dama sun ce sai sun kashemu, miyay musu, mi kai musu kaima mijina?. Na tsanesu, da ace sun samu nasara kan Bappi yau da kaina zan kashesu, amma ko yanzu karka ƙyalesu Ya Ramadhan. Na rokeka karka barsu suma su dukansu”.
     Kalaman Raudha sun girgiza Ramadhan, dan haka ya tsareta ta sanar masa suwaye? Mita sani? Mi take boye musu. Shi tun sanda ta karema Bappi hari ya tabbatar tasan wani abu.
     Cikin kuka ta shiga girgiza masa kanta. “Wlhy bansan komai a sannanba Ya Ramadhan, sannan bansan su wanene ba. Nayi hakane saboda shima ya taimaki wani tsohon daya fisa shekaru a filin idi. Amma badan na sanshi ba. Badan nasan komai daga garesaba. Sai dai zan faɗa maka abinda na sani nima, amma wlhy ka yarda dani, ban yarda da aurenka saboda su ba. Nayine kawai dan yima mahaifina biyayya da gujema mahaifiyata tsinuwa da Gwaggo tace zatai mata inhar ban yarda da aurenka ba...........”✍


 *_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*   


*_Typing📲_*


*_Episode 76_*


..........Tsaf ta zayyane masa komai data sani na firar su Aunty Hannah da taji, har zuwa aikama bappi takarda, da batun canja driks nashi da ake kawowa cikin gidan.
     Ya daɗe da bincike akanta game da drinks saboda yanda kuɗi ke yawan fita a accaunt ɗinta, wanda duk watan duniya ake saka mata kason kudi na Taura family da ake bama kowa. Bai mata magana ba ya shiga bincike akan son sanin mi take da kuɗi, cikin ikon ALLAH kuwa yay azamar ganowa saboda companyn da take aikama kuɗin. Ta hanyarsu ya gane ana kawo drinks gidan, baiyi ƙasa a gwiwa ba yasa akai masa bincike akan wanda take canjawa da wanda take sakawar. An gano wanda take cirewar wasunsu akwai guba a jiki mai shiga jiki a hankali, wanda take canjawar kuma lafiya lau yake. Tun a sannan yasan Raudha tasan wani abu, shiyyasa koda suka samu rubutunta yazama irin na wanda aka aika musu wasiƙa bai tada hankalinsaba. Burinsa kawai yasan asalin tushe da mafari, yau kuma ta zayyane masa komai.
     Kyawawar runguma ya bata yana mai sanya mata tarin albarka. Sai dai hakan bazai hanashi kafa kwamitin bincike ba domin tabbatarwa. Badan bai yarda da itaba, sai dan haka dokar shari'a take shaidarta bazata wadatar ita kadaiba dole sai da wasu shaidun musamman da su forma president suka zama manyan kusoshin ƙasar. Dama Dr Ingoze dake hanun security na gidan ta tabbatar musu ita ba laifinta bane sanyata akai ta hakala Raudha da jaririnta inba hakaba itama za'a halaka kaf family nata.

*_WASHE GARI_* akai jana'izar Inna da driver aka mikasu gidansu na gaskiya. Ciki kuma harda Shugaban ƙasa Ramadhan da yaje har makabarta. Bayan sun baro makabarta kuma ya wuce ya duba jikin Muneera da batasan ma ina hankalinta yake ba. Sosai ta canja kamanni saboda yanda motar ta kife ta dinga katantanwa da su a kan titi ga harbin data samu har biyu a ƙafa ɗaya da ƙugunta. Cike da damuwa da tausayin ƴar uwar tasa ya koma gida.

       Sosai a wannan karon ma su Alhaji Yaro glass sukai baƙin ciki na rashin nasara. Har zukatansu suna sanar musu lallai Alhaji Hameed Taura na tsafi shiyyasa dukkan harin da suke kai masa sai ya kauce masa. Acewarsu to ai idan yasan wata baisan wata ba. Suna kusan sahun farko na zuwa yin jaje da ta'azziya Taura House. Sun kumaje har government house sunma Ramadhan shima dan ana gama jana'iza ya koma gida.

     Randa akai addu'ar uku ranar Raudha ta koma government house tare da sabuwar mai kula da ita. Dama Anne nata faɗan zuwanta tun randa akai rasuwar acewarta tana riƙe da laɓuɓun yaro yawo ba nasu baneba ai. Duk da ba wankan jego take irin na mutanem da ba tana samun kulawa sosai dan babu ɗaga ƙafa Hajiya Mama ta dinga mata wankan towel. Yanzun ma koda suka dawo haka ta dinga kula da ita da ƙyau ita da Abdull. Dan Ramadhan ya hana a ɓoye masa suna. wasu kan kirasa Abdull wasu suce Abdull-Hameed ɗin. Shi dai Bappinsa yake kiransa, itama kuma takance bappi wani lokacin ko tace babban mutum.
      A haka kwanakin jegonsu suka shuɗa duk da dai wajen da akai mata cs ya warke sarai Alhmdllhi. Ga gyara tana samu na musamman daga shahararriyar mai gyaran nan ƴar Nigeria dake jihar sokoto *_Maman Zara sokoto 07034251528_* (hummm kunga maman zarah ɗin nan karku bari kayanta su wuceku, ku garzaya domin kwasar rabonku, dan koda kuɗinka sai da rabonka kuwa) Gefe kuma Miss xoxo na kasheta da kayan gyaran jiki na musamman dana kamshi. Duk wanda yaga Raudha dole ya sake kallo, dan haihuwar ta sata buɗewa ta zama wata babbar mace da zaka iya bata shekaru ashirin da tara bawai sha tara ba. Shi kansa gogan nata haƙuri kawai yake da juriyar ɗauke kai. Amma inhar ya samu damar ritsata a ɗaki su kaɗai yana ɗan rage zafi ko rokonmi zata masa baya saurarenta. Dama aunty Zuhrah ce ke saka musu ido, ita hajiya Mama akwai kunyar surukuta shi kansa baya yi idan yasan tana kusa.
      Ana saura kwanaki uku suyi arba'in Anne ta sanar masa ya kamata yabar Raudha taje hutawa, ta kuma je Bina masarauta duka tayo kwana bibbiyu. Fuska sosai ya tsuke kamar yana gabanta, sai da yaji ta sake maimaita masa sannan yay magana cikin marairaicewa.
       “Amma Anne dan ALLAH...”
Kaga Ramadhan ni bance tilas ba. Ina dai tunatar da kaine abinda ya dace. Kai yanzu kana ganin ya kamata ace har yanzu matarka bata taɓa takawa gaishe da mai-martaba ba? Sannan tunda akai bikinta bata taɓa zuwa gaida mahaifinta ba?. Nasan dole ne ai muku uziri saboda a yanayin da kuke yanzu, amma bashi ke nuna bazakuje ayi zuminci ba. Kodan kaga tanada haƙurin shanye komai batare data matsanta maka ba”.
       Ajiyar zuciya yaɗan sauke, dan yasan tabbas maganar Anne gaskiya ce Raudha nada matuƙar haƙuri, kamar kuma hanata zuwa gaida mahaifinta tauyeta yayi tunda tasha nuna son hakan duk da bata taɓa tunkararsa ba.

      Da wannan shawara ta Anne ya shiryama su Raudha tafiya cikin kwanaki biyu. Zatai tafiyar bisa rakkiyar su Hajiya Mama da tawagar securitys. Koba komai hakanma ai ya taimaketa tunda tana son zuwan. Hutawa suka fara zuwa, inda Mal. Dauda ya rikice ya rasa inda zai tsoma ransa dan daɗi. Hakama Baba Nafi da Inna da sauran yaran gidan. Amarya ma dai ba'a barta abayaba, tace dolene ta tarbi first lady kodan baƙanta ran Larai abokiyar hamayyarta. Aiko kamar yanda ta shirya kunna larai tako kunnuta harta kasa riƙe baƙin cikinta ta dinga sakin magana da aibanta Raudha harma da Asabe. Uban gayya Mal. Dauda dake ƙwaƙume da Abdull babu wani jan lokaci ya sauke mata maruka, tare da tabbatar mata yau tata ta ƙare a gidan taje ya saketa. Dan ya rantse duk wanda ya nuna baya son mai sunan Innarsa Raudha to shima bazai taɓa yasosa ba, domin Raudha dai farar haihuwa ce. Da farko Larai ta ɗauka abun wasa, sai da Inna tace “Idan bazata tafi ba ƙara mata guda Dauda”.
      Haƙuri Raudha da Aunty Zulfah suka shiga badawa. Yayinda Hajiya mama ko'a jikinta. Take anan ma ta kira Asabe ta guntsa mata. Bawani daɗi Asaben taji ba. Dan acewarta saki koda kaine ka nema bashi da daɗi.
      Sosai maƙwafta sun shigo gaishe da first lady, dan ma wasu tsoron securitys dake zagaye da gidan na mal. Dauda ya hanasu. Washe gari da safe taje har gidan hakimi takai gaisuwa da masa godiya. Shiko ya amshi Abdul yana mai sanya masa albarka shi da ƴan fadarsa da matansa. Sunbiyo ta super market ɗin M. Dauda da Raudha taji har ƙwalla ya cika mata ido dan babu abinda zatace da Bappi sai dai addu'a. Da zasu taho jitai kamar karta baro garinta, M. Dauda ya shirya tsaraba mai yawa wai duk na Abdull, ita Raudah abinma dariya ya bata. Yaushe Abdull ɗin yazo duniyarma dazai fara shan kayan zaƙin nan dana ciye-ciye. Da tace a rage cayay bai yarda ba. Itama Inna ba'a barta a baya ba tama Raudha tsaraba da kayan sirrinsu na tsoffi masu kyau da dama ta tanada tunda Raudha ta haihu. Dan ko lokacin suna da sukaje dama takai mata wasu.

       Daga Hutawa Bina suka nufa cikin masarauta. To anan dai kam daga mai-martaba ta samu tarba ta ƙwarai. Fulani ce dai kadaran kadahan. Dan ko Abdull ƙin cewa a bata tai sai da Aunty Zuhrah ta ɗauka da kanta ta bata tace a sanya masa albarka. Sai kuma duk taji kunya. Mai-martaba kam acan suka baro masa Abdull, ba'a dawo musu dashi ba sai da ya fara ƙananun kukan yunwa.
     Anan ɗin ma dai shatara ta arziƙi mai-martaba da sauran matan sarki suka bama Raudha dan Ramadhan yana girmamasu shidai. Babu ruwansa da wata aƙidar dake tsakanin iyayensa da su.. Ganin sunzo har Bina ta kira Ramadhan ta roƙesa zuwa gaida Aunty Halima itama. Bai hana ba, dan tun farko ma daya san Aunty Haliman a Bina take itama da kwanan akai mata. Sai dai gsky a matse yake da matarsa, burinsa kawai ta dawo. Aunty Halima taji matuƙar daɗi dayin farin cikin zuwan na Raudha. Hakama yaranta. Kasancewar Ramadhan yace sukai har dare sai su biyo jirgi yasata baje kolinsu sosai a gidan Aunty Halima. Dan sai kusan tara suka nufi airport jirgin 9:30 zasu bi.

     Ƙarfe goma bataiba ma suka iso Bingo. Motocin da suka tafi tarbarsu da securitys suka kwasosu sai government house. A ranar ma dai Ramadhan yayi kawaicin kauda idonsa saboda yasan da gajiya tattare da su. Dan ko keɓewa bai yarda yayi da Raudha ba. A ɗakin da take jego ya shigo suka gaisa da su Aunty Zuhrah itama Raudha ta gaisheshi ya ɗauka Abdull ya fita. Kusan mintuna talatin yay kiran Basma a waya tazo ta ɗakko Abdull ɗin ta dawo da shi.
       Washe gari su Hajiya Mama suka tarkata yan kayansu kafin Ramadhan haƙurinsa yakai karshe ya fara rashin ta ido. Shatara ta arziƙi suma ya haɗa musu suka tafi Raudha na matsar kwalla. Tsabar ya shiryama wannan weekend suma su Basma cayay zuje Taura house suyi weekend. Raudha zatai magana ya dinga zuba mata harara da mintsini. Doleneta tai shiru..........✍

   

 Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulu mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd guess what😍munyi upgrading kayanmu gbdy domin jindadinku🥰bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida
💯 Natural/organic

maiso yy mgn
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki komai da komai
Akwai soap 3k
Student package 7k
Beauty kit 11k
Bridal kit 18k

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏


*_Typing📲_*


*_Episode 77_*


.........Bayan wucewar su Basma sai da ta tabbatar an gama shirya abinci a dining tabar sauran komai hanun mama ladi sannan ta shigo ɗakinta da yanzu ta dawo. Abdull dake a bayanta goye ta sauke saman gado, dan Anne ta gargaɗeta matuƙa akan ta dinga goyasa yanajin ɗumin jikinta batason wannan halayyar da matan yanzu keyi naƙi goya yaro ko ace za'a bama masu aiki suyita faman raino ke uwa kina hutawa. Wanka ta shiga, fitowarta babu jimawa tana ƙoƙarin neman kaya marasa nauyi ta saka Abdull ya farka ya fara ƙananun kuka.
        “Oh oh babban mutum yi haƙuri ina zuwa. Nasan matsalarka yunwace acici”.
       “Ai duk ke ya gado cin nan ba wani ba”.
   Ta tsinkayi amsa daga bakin Ramadhan da bataji shigowarsa ɗakin ba. Ɗan juyiwa tai tana kallonsa, dai-dai yana karasawa saman gadon ya dauka Abdull yana sawa a kafaɗa. Murmushi tayi da ɗauke kanta tana cigana da ɗakko kayanta. “ALLAH ya Ramadhan kaima kasan banda ci, sai dai in kai”. Ta ƙare maganar tana nufosu kaya a hannu.
     Kayan ya ɗanbi da kallo, cikin neman magana yace, “K har kina tunanin saka kaya a yau?”.
     Cikin rashin fahimta tace, “Kamarya? Kana son na zauna da towel ne na kwashi mura?”. Murmushi yayi mai ƙayatarwa, ya sauke Abdull daya koma barci saman ɗan gadonsa ya gyara masa kwanciya. Tana ƙoƙarin saka riga ya riƙeta. “Idan ma kinsa zan ciresu ne, minene na wahal da kai?”.
     Kunya ce ta kamata, cikin marairaicewa tace, “ALLAH ya Ramadhan ba kyau, kaifa yanzu ka girma sunanka Daddy”.
      Kai ya dungure mata yana murmushi, sai kuma ya zare ribbon ɗin kanta tare da tallafo kannata ya manne goshinsu waje guda suna shaƙar numfashin juna. “K miyasa kin iya fassara mutum. Ni karki lalatani bankai can ba”.
     Mintsini takai masa a gefen ciki, ya  janye jikinsa da sauri yana faɗin “Ouch yarinyar nan muguntar da kika koyo kenan a yawon arba'in ɗin”.
    Dariya Raudha ta ƙyalƙyale da shi da masa gwalo. “Ai kaɗan ma kenan”.
     Ƙwafa yay fuska a cuskule kamar gaske. “Haba yarinya zan rama ne idan kikazo hannu zaki gane kuranki”.
     Juyowa tai da sauri garesa fuska a narke, dan tasan wanene mijin nata. “Please Noorullah sorry”.
     “Ba wani sorry ai saina rama”.
  Da sauri ta nufosa ta ɗane masa baya duk da ta zama lukuta yanzun, “Ya ilahi, yarinyar nan kin koma biri ne?”.
    Ya faɗa yana juyota ta sakko suka faɗa saman gadon. “Gaba ɗaya kin zama ƴar lukuta amma ƙibar ta miki ƙyau”. Yay maganar a hankali yana busa mata numfashinsa a kan fuska. Kafin ta samu damar magana ya manne lips nashi kan nata. Itama a zalamen take, dan haka babu musu ta miƙa wuya ita shaidace mijin nata yayi haƙuri, kusan kwana hamsin ai ba wasa ba. Sai da taga zasu wuce hanyar da suka ɗakko ta fara ƙoƙarin janye jikinta. Amma ya nuna shifa sam bai yarda ba. Roƙon duniya da magiya ya nuna mata baiji bai gani. Dole ko ta miƙa wuya. Daga baya kuma ta shiga tsoro, dan tasan taji gyara babu ƙarya balle algus. Tafiya tai nisa Abdull ya sake farkawa yana kuka. Amma Ramadhan sam yaƙi nuna yama jisa, itako Raudha hankalinta duk sai ya koma kansa (uwa kenan. Uwa mafi uba koda uban sarki ne👍🏻).
          Lokacin daya kai inda yake buƙatar zuwa Abdull yaci kuka harya godema ALLAH, da ƙyar ta iya dauriyar tashi ta nufi bayi, Bata ɓata lokaci wajen gasa jikinta ba ta fito dan har yanzu Abdull bai bar kuka ba duk da tabar Ramadhan na ɗan shillashi cikin ɗan gadonsa.
     A yanzu ɗinma haka ta samesu, batace da shi komai ba ta yafa towel ɗin da take goge jiki a kafaɗarta ta ɗauka Abdull ɗin. Tashi yay shima batare da yace mata koman ba ya nufi bayin.
      Lokacin daya fito tana shayar da Abdull ɗin idonta kan yaron nata da ɗan wasa da sumarsa. Ramadhan ya zauna kusa da ita da riƙe kafar Abdull dake motsawa. “ALLAH sarki kakan Dadynsa kaji yunwa da yawa. Mamanka ce ta cika zalama da wuri take son a farauto maka ƙanne”.
   “Innalillahi... Kai Ya Ramadhan”.
“Ba wani Ya Ramadhan anan. Inba azalame kike ba miye daga zuwana duba Bappina zaki wani kadandaneni sai da nayi”.
      Ina kasa Raudha ta shige dan kunya. Ta ture kansa daga kafaɗarta, shiko ya ƙyalƙyale da dariya. “Uhhm tundafa kin samu kinmin kat aiƙyafa tureni, dama Ustazan nan shiru-shurunku aiba na lafiya bane. Yanzu haka nasa kina nan kina addu'ar a koma second r.......”
     Hannu tasa ta rufe masa baki, idanunta har suna tara ƙwalla. Ta dangwarar masa da Abdull a cinya zata miƙe tabar wajen ya riƙota yana dariya. “Yi haƙuri wasa nake my Partner, duk fa nine zalamammen”.
    Ita dai bata sauraresa ba, da ƙyar ya samu ya lallasheta cike da salonsa da yake kasheta da shi. Daga karshe suka ɗunguma falo sukai dinner aka sake dawowa filin daga....

      Rayuwa ta cigaba da tafiya cike da farin ciki da jin daɗi ga waɗan nan ma'aurata, hakama mulkin Ramadhan kowa nata san barka. Bayan sun gama amarcin jegonsu ta tattara ta koma makaranta. Ramadhan ya sake maida hankalinsa ga harkokin mulkinsa. Yayinda a gefe ya naɗa kwamitin bincike akan harin da aka kaima Bappinsa.

      Sai dai kuma mi a hankali rikice-rikice suka fara tashi a wasu yankuna na ƙasar NAYA. Ga yawaitar ƴan fashi a tituna da gidajen manya. Al'amarin kamar wasa sai ya dinga faɗi da gawurta harya fara fin ƙarfin jami'an tsaron dake a tsaye kan matasalolin. Sosai hankakin Ramadhan ke tashe. Tsabar ruɗani har wata rama yay yay duhu sosai. Ita kanta Raudha dake ƙoƙarin kwantar masa da hankali dauriya kawai take, dan zubda jinin ya fara yawan wuce hankali. Dan takai anabin manyan malamai ana musu yankan rago a cikin gidajensu. Komai daya shafi mulki sai ya fara tangal-tangal musamman manyan ayyukan da ake shimfiɗama talakawa. to ana ta rai waketa wani aiki. Mutane ma idonsu ya daina ganin ayyukan tashe-tashen hankulan kawai suke gani, akoda yaushe cikin zaman meeting ake tsakanin jami'an tsaro da masu faɗa aji, sai dai babu alamun samun wani sauyi.
    Ba Ramadhan kawai ba, hatta su Anne hankulansu a tashe yake matuƙa, dan duk mai hankali ya kalla abubuwan da idon basira yasan ƙirƙirarsu akai da gayya.. Ramadhan na gab da cika shekara biyu a mulki Bappi ya bashi shawarar sauke duka manyan shugabanin tsaro, hakan kuwa akai, aka sauke su aka ɗakko wasu aka ɗora...
      Hakan ya tada hankalin su Alhaji Haladu Gwandu matuƙa, dan shirine da babu wanda yasan dashi wayar gari kawai akai shugaban ƙasa ya zartar da hukunci. A gefe kum aka tara matasa takowane yanki aka basu aikin sakai sai dai gwamnati zata dinga biyansu albashi mai tsoka. Sannan aka saka maƙudan kuɗaɗe ga duk wani farar hula daya kawo sunan ɗan ta'adda uku ya tabbata kuma ɗan ta'addanne. Wannan shirifa ya zaburar da natasa da talakawa, burin kowa ya samu wani maraji ya kwafe sunansa a takarda da mafakarsa yakai hukumomin sirri da aka baza a kowace jiha ta ƙasar NAYA. Sai gwamitin bincike na musamman da aka ajiye su kuma a gefe akan son sanin ta inda makamai ke shigowa ƙasar ta NAYA.

     Lallai wannan shiri ya zaburar matuƙa, dan ya maida kowa jami'in sirri mai himma. Takai har ƙananun barayi ma basu da wata sakewa yanzun, dan kan barci ne makwafcinka na maka minshari. Burinsa kayi kuskure kaɗan yakai sunanka a sauke masa kuɗaɗensa. Tofa inji masu jimamin fitar magana, bincike fa ya fara daukar hanya, dan wasu sunaye da ba'ai zato ko tsammani ba sun fara bayyana kansu ta hanyar yaransu da aka fara cafkewa. Bincike yanayin nisa firgici da ruɗani na sake bayyana ga su forma president. Har wani zama na sirri suka ƙirkira da Ramadhan, bai musaba ya amshi baƙuncinsu, ya kuma saurari dukkan soki burutsinsu daya sake tabbatar masa lallai sune ke ƙulla komai kamar yanda yake hasashe shi da Raudha. Ƙin cemusu komai yayi hakan kuma sai ya ƙona ransu.
     Sunma rasa inda zasu saka hankalinsu suji daɗi dan sai tsinci ɗai-ɗai akema yaransu, abinda zai baka mamaki harda wanda suke cikin mulkin dumu-dumu. Ta ɓangare ɗaya suke ɗan jin sassauci idan suka tuna ta Ramadhan ta kusa ƙarewa tunda sunada tabbacin ya shaƙi gubar da suka shirya ya shaƙa ɗin ta shekaru biyu. Ya kuma sha a drinks sai dai ganin bai taɓa kwanciya ciwo ko canjawar jikinsaba na ɗan saka musu wasuwasi.
    Sai dai a randa suka bama zukatansu salama da wannan madogarar a ranar jami'an tsaro suka cafke Aunty Hannah a dalilin maganar drinks da kuku ya tabbatar itace ke bashi. Ranar Raudha taci kuka sosai, Ramadhan yayta aikin lallashi. Ya tabbatar mata dama sun gama da kammala wannan bincike shiyyasa aka cigaba da riƙe kuku. A ɓangaren Hajiyar Birni ma hankalinsu a tashe yake, dan Raudha ta kira tana kuka saboda zuwa yanzu kowane kafar yaɗa labarai babu wani sabon labari sai na kama matar vice president da ake zargi da haɗa kai da kuku domin halaka shugaban ƙasa. Asabe ma ta kira Raudha, hakan sai ya sake rikitata har Ramadhan yama rasa ta ina zai lallasheta. Kukan da taci ya jaza mata zazzaɓi sai da Dr Hauwa tazo dubata, a gwajin farko kuma ta tabbatar musu Raudha nada cikin wata biyu.
     Sake rikicema Ramadhan tayi, tayama za'ace tanada ciki bayan shekarar Abdull ɗaya da watanni huɗu. To shi dai abun yafi karfinsa. Ga rikicin mulki ga nata sai kawai ya haɗata da Anne............✍

Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulu mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd guess what😍munyi upgrading kayanmu gbdy domin jindadinku🥰bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida
💯 Natural/organic

maiso yy mgn
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki komai da komai
Akwai soap 3k
Student package 7k
Beauty kit 11k
Bridal kit 18k

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏


*_Typing📲_*


*_Episode 78_*


..........“Tabbas dole Hannah ta mutu kafin a miƙata kotu”.
    Forma first lady ta faɗa tana duban su Alhaji Yaro glass dake tare da ita harma da god fathers nasu a yau. Mr MM da duk yake a firgice yay saurin faɗin, “Ina bayanki your excellency maa”.
       Gaba ɗaya falon dubansu suka maida ga Alhaji Yaro glass da tunda ya shigo baice komai ba, sai ma uban tagumi daya rafka. Numfashi yaja mai ƙarfi ganin sun dawo da kallonsu garesa alamar amsa suke nema. Yaɗan ɗage kafaɗa da yarfa hannuwa. “Ni a gareni babu matsala, da nasan ma wannan ranar zata zo da dakaina zan kashe Hannah tun kafin zuwanta. Dan tun randa case ɗin kuku ya shigo ya kamata a ɗauka wannan matakin, amma sai muka ɗauka hakan ba komai ba. Sai dai ku sani ba Hannah ce kawai zata mutu ba harda Kuku, dan kuwa Hannah da Bushira kuku ya sani ba Hannah kawai ba”.
        “Amma kasan shi ɗin ɗanane jinina ko?”.
    Cewar Forma first lady Bushira hamada a harzuƙe.
       “Nima ai Hannah matata ce, cewa a kasheta bashike nufin bana sonta ba. Sannan idan baku manta ba matar Ramadhan jinin Hannah ce, amma da akace zata iya mutuwa a cikin shirinmu batai jayyya ba, ashe kuwa indai nasara muke bukata dolene mu ɗanɗani ɗacin rashin jinanannmu koda kuwa ƴaƴan da muka haifane”.
     A take kowa ya goya bayan maganar Alhaji Yaro glass. Hakan yasa Hajiya Bushira hamada yin shiru. Oga kwata-kwata da baice komai ba sai da duk suka gama hayaniyarsu sannan yay gyaran murya. Dukansu hankali suka maida garesa.
      “Idan har ta kisan wane da wane ne zamubi ta hanyar rufe sirrikanmu mutane da yawa zasu mutu a wannan gaɓar. Dan haka ba shine mafita ba, babbar mafita a garemu yanzu harin maƙiyinmu kai tsaye. Ramadhan shine kawai zamu hara kai tsaye mu sami nasarar daƙile duk wata damuwarmu. Amma dan mun kashe su Hannah kamar mun kashe macijine bamu datse kansa ba, domin kuwa kisan nasu tamƙar buɗe hanyar da masu bincike suke nemace kai tsaye muka bayar.
     A take ɗakin taron ya ɗauka kananun hayaniya. Dan kuwa zantukan shugaba sun fargar dasu abinda basu hango a farko ba. Dan haka a daren yau basai gobe ba Ramadhan zai baƙunci lahira.....

       “Idan shi bai baƙunceta ba, ku zaku baƙunceta ai”.  Cewar Alhaji Balarabe Andu daya daɗe tare da su da fuska biyu. Alhaji Balarabe Andu tsohon jami'i ne da tun komawar tsohon shugaban kasa Usama D. Hamada mulki na biyu ya shigo jikinsu. Koda yake zamu iya cewa tun a mulkin farko ma yana tare da su, sai dai basu sakin jiki da shi har sai lokacin mulki na biyu da suka tabbatat yana tare da tafiyarsu. Tun usul ya shigo tawagarne akan binciken wani gagarumin ƙulli da akai a wancan mulkin, sun buga sun buga suka kasa gane kansa. Shine yay shigar burtu ya zama ɗaya daga cikinsu. Yaso barinsu bayan kammala mulkin Usama D. Hamada, sai dai ƙullin da suka fara akan daura Alhaji Hameed Taura a mulki ya sashi dakatawa. Duk abinda suke yana biye da su, hatta da ac da suka saka poison a ciki na gidan gwamnati yaso zama silar da zai sa a cire sai Raudha ta rigasa, amma da taimakonsa su bappi suka cire batare da suma sun sani ba. Ya cigaba da tattara bayanan sirri akansu batare da sun sani ba, kuma ko ayanzu da aketa faman kama musu yara duk da saka hanunsa a ciki....
     A firgice duk suke kallon Alhaji Balarabe Andu, dan wasunsu sun ɗauki abin wasa ne ko almara ko subutar baki,
      “Alhaji balarabe kasan mi kake faɗa kuwa?”. Cewar Alhaji Haladu Gwandu.
     Alhaji Balarabe yay wani murmushi tare da rausayar da kai gefe ya tafa hannayensa yana kallon Alhaji Haladu Gwandu batare da yace komai ba. A take jami'an tsaro suka shigo falon suka zagayesu su da makaman da suka tile a tsakkiyar falon wanda a yau ɗin nan aka iso da su ƙasar NAYA.....

         ★Cikin ƙanƙanin lokaci ƙasar NAYA da kewaye ta ɗauki sabon labari na kama waɗan nan manyan mutane da wasun su ko'a hasashen zuciya bata taɓa kawo zasu aikata abinda ake zarginsu da shi ba. Bakin ƴan siyasa ya buɗe ta ko'ina bakajin komai sai kace nace. Abinda ma ya takaice kace nacen tsayawa akan jam'iyya mai mulki kawai waɗan nan mutane gaba ɗayansu suna tarayya ne a cikin mabanbanta jam'iyyu. Hakan na nufin kenan dama ƴan siyasa da yawansu a bayan fage kanwunansu a haɗe yake a zahiri kuma suyita gwara kan talakawan ƙasa da sasu luguden laɓɓa batare da sun hankalta ba. (Ƴan uwa idan zamuyi soyayya muyita dan ALLAH kuma saisa-saisa. Hakama kiyayya muyita saisa-saisa kuma domin ALLAH musamman irin ta siyasa. ALLAH yasa mu cika da imani).

     A yinin wannan rana kawai hankalin al'ummar ƙasar NAYA ya dawo kan shugaban ƙasa Ramadhan. Aka dinga sanbarka a garesa da wanke laifukan da ake kallonsa da su. Yayinda wasu keta faman bankaɗe-bankaɗen abubuwanma da ba'asan da su ba sai yanzu.
      A wani fanin Raudha na farin ciki, wani fanin kuwa tana baƙin cikin kasancewar yayar mahaifiyarta cikin tawagar waɗannan azzalumai. Ga laulayin ciki mai wahala da take fama da shi a wannan karon. Ga karatunsu ya ɗau zafi dan suna lavel 3 ne. har zuwa yanzu kuma bata taɓa kuskuren nunama wani ita wacece ba. Abdull bada shi take zuwa makaranta ba. Gida ake barinsa wajen Mama Ladi. Dama Alhmdllhi yana ɗan takawa zuwa yanzun, damma haƙora na maidashi baya idan yay zazzaɓi. Bayyanar cikin nan na Raudha kuma yasa Anne zuwa ta ɗaukesa a gidan ma baki ɗaya ya koma Taura House yaye. Sudai basu da ikon cewa komai, amma gimbiya Su'adah taji haushi dan ta ƙullama ranta itama abinda akai mata na ƙwace Ramadhan saita kwace Abdull, sai gashi Anne ta sake mata kwaf ɗaya kafin ta farga ta ɗauke ita (🤣😂Bashin gaba lol).

★★________★★★________★★

           Rayuwa ta cigaba da shurawa su Alhaji Haladu Gwandu na cigaba da zama a tsare a gidan yari, a gefe kuma ana sauraren ƙararsu a kotuna mabanbanta saboda laifukan nasu sunzo daban-daban. Kowanne akwai babban laifin da yake shugabanta da ake tuhumarsa a kansa kai tsaye. Wanda sukai tarayya akai shine cin hanci da rashawa da shigo da makamai.

     Ɓangaren shugaban ƙasa kam zamuce abubuwa sun fara dai-daita, domin ɓarnakun da tashe-tashen hankali ya kawo su akebi ana gyarawa kafin a ɗora sauran ayyukan da aka fara. A gefe kuma ya sake samun kwanciyar hankalin kasancewa da matarsa abar sonsa da alfaharinsa ƴar darunsa kuma dake fama da ciki. A haka ALLAH ya sake saukar Raudha lafiya, a wannan karon kam da kanta ta haihu yaronta namiji again, shima yaci sunan Pa wato Basheer. Suna kiransa Alhaji ƙarami. Duk da Ramadhan yaso kar ai taron suna dan bai manta abinda ya faru ana Abdull ba su Bappi sukace sai anyi. Haka dai akayi taro mai kayatarwa anan ɗin ma Raudha ta cigaba da shayar da yaronta.
          Yankema su Alhaji Usama D. Hamada tsohon president hukunci dai-dai da abinda suka aikata yayi dai-dai da sake kaɗa tamburan siyasa. Dan hatta yunƙurin kisan Ramadhan da sukai tsautsayi ya koma kan Amnah ɗiyar Alhaji Haladu Gwandu sai da jami'in tsaro Balarabe ya fallasa. Wannan hukunci da aka yankema waɗannan azzalumai ya zama makamin campaign na Ramadhan a wannan lokaci, dan kuwa yanda abubuwa ke tafiya bama sai ance maka shine zaiyi nasara ba kowace alama ta nuna hakan.
     Sai kuma wani babban abin farin ciki da Ramadhan ɗin ya aywatar a wannan lokaci shine hana bangar siyasa yin tasiri a ciki dabai na ƙasar NAYA. Duk ɗan siyasar da aka samu ya bama yara makamai ko kayan maye domin masa campaign ko makamancin hakan to takararsa ta ruguje bazaiyiba. Wannan al'amari shine ya saka ƴan siyasar shiga hankalinsu, matasan kuma dama mafiya yawansu sunda aikinyi wasu sabo dayine da kuma shegen kwaɗayi ke ingiza zukatansu.
      Alhmdllhi campaign ya wanzu cikin nutsuwa da burgewa, inda har akai aka gama babu wanda yaga matar shugaban ƙasa ko da a poster. Sai dai Ramadhan yasha fita da Abdull da Alhaji ƙarami da shima yake neman cika shekara guda da haihuwa. Zuwa yanzu mutane da yawa sun fahimci shugaban ƙasa Ramadhan baya ra'ayin matarsa a harkokin siyasa ne kawai, yana kishinta yana killace abarsa matsayin tashi shi kaɗai. Hakan ya matuƙar birege mutane, harma a wannan campaign ɗin wasu ƴan siyasar sukai koyi da hakan musamman ƴan takarkaru.
      Dan hatta abubuwan alkairi da Raudha ke shimfidawa a bayan fage bazaka taɓajinsa a bayyane wa duniya ba, acewarta tayine domin ALLAH badan wani ya sani koya yaba mata ba. Mijinta kuma ya bata goyon baya ɗari bisa ɗari.

       Alhmdllhi an gama campaign lafiya ankumayi zaɓe shima. Yayinda sakamakon zaɓe ya tabbatar da sake zaman *_Ramadhan B. Hameed Taura_* matsayin shugaban ƙasa a karo na biyu a ƙasar NAYA. Duk wani masoyinsa ya tayasu murna da fatan sauke nauyin al'umma a kansu. Inda a wannan karon ya shigo sabon tsarin da sabon tsare-tsare da ƙudirirrika na musamman. Yayi sauye-sauyen wasu a cikin ministers da suka kasance zabin su Alhaji Yaro glass a wancan karon. Hakama vice president an sake sabo tunda su Alhaji Yaro ana can ana cin gabza a prison😝.
         Rantsar da shugaban ƙasa baifi da sati uku ba su Raudha sukai GRADUATION a makaranta. A kuma lokacin ta bayyanama school mate nata ko ita ɗin wacece. Ansha mamaki, ansha al'ajab da kace nace ga ƙasar NAYA ma ba makarantar kawai ba. Gaba ɗaya hidimar bikin fitar tasu ita ta ɗauki nauyin komai. Ansha hotuna na tarihi kowa burinsa firt lady karta manta da shi duk da bata yarda ta buɗe fuskarta ba ko a wajen bikin kamar yanda Ramadhan ya bada doka. Yadai yarje mata ta sanar dasu ko ita wacece kawai..
      A randa suka kamma bikin gama karatu a ranar ta sake fahimtar tana da ciki, taci kukanta tai gum da bakinta, sai dai batasan mai gayya mai aiki shi ya san da abunsaba tunkan ta sani. Sai ranar kawai yake bayyana mata ta gama boye-boyenta shi ya jima da sanin ya samo ribar farautarsa ai.
    Galala tai tana kallonsa, shiko yay mata gwalo ya fice. Jitai kamar ta zauna taita kuka kawai. Ita wannan wane irin abune bata yaye yara sai sabon ciki. To babu yanda aka iya da hukuncin ALLAH, wasuma nema suke basu samu ba da kuɗi.
     Tun tana zumbure-zumɓurenta harta ware suka cigaba da rainon ciki Mama Ladi ta yaye Alhaji Ƙarami. A randa Raudha ta haihu a ranar ALLAH yayma Addah Asmah dake fama da jiyya har yanzu rasuwa. Ba kowa yaji mutuwarba. Dan dama masu jiyyar tata sun matuƙar gajiya. Yanda bata nema yafiyar kowaba babu wanda yace ya yafe matan har gimbiya Su'adah da yanzu akai sanyi. Bata sakema Raudha dai bakuma ta takura mata. Babbar damuwarta ma yanzu zaman Lubnah a gida da Muneera da a yanzu ta koma sai wheelchair saboda ƙafarta ta samu matsala a wancan haɗarin. Har kuɗi da gida da mota aka saka ga wanda zai auri Muneera amma duk wanda yazo ya ganta saboda raunikan da tayi a fuska sun canja mata kamani sai ya gudu. Bilkisu kuwa tuni harta haihu abinta ita da su Fatisa. Yanzu hakama shirye-shiryen bikin su Basma akeyi.

        A wannan karon dai Ramadhan ya dage baza'ai bikin suna ba, ya dai ɗauke matarsa bayan arba'in sukai tafitarsu America domin hutawa na sati biyu tare da yaransu uku vice president ya cigaba da riƙe ƙasar NAYA kafin ya dawo. Dan jinjirin shima yaci sunan Mal. Dauda. amma suna kiransa Dawood. Raudha da Ramadhan na cemasa Abbati.
      Satinsu biyu suka dawo NAYA harkokin mulki suka cigaba da tafiya yanda akai fata...........✍

             

*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*


*_Episode 79_*


...........*_BAYAN SHEKARU BIYAR_*

       Alhmdllhi abubuwa da yawa sun faru na cigaba a cikin waɗannan shekaru daga mulkin shugaban ƙasa Ramadhan. Ciki harda haihuwa da Raudha ta ƙara har sau uku. Bayan Dawood tayi ƴammata biyu tagwaye da sukaci sunan Saleeha da Zainab. Ta kuma sake Hauwa'u, sai auta da yaci sunan mai-martaba suna kiransa Saraki.
       Babu abinda ƴan ƙasa zasuce sai sambarka. Dan kafin shekarun mulkin Ramadhan su kammala ya shimfiɗa manyan ayyukan da har abada baza'a manta da shugabanci irin nasa ba. Daɗin daɗawa bai saukaba sai da ya gyara wasu da yawa a dokokin kundin tsarin mulkin kasar NAYA. Ciki harda dokar shugabanci. Duk shugaban da ya haura shekara sittin bazaiyi mulkin ƙasar NAYA ba koda kansila ne. A kowace ma'aikata ana son kaso biyu bisa uku matasa su sami rinjayen samun aiki bawai lallai sai a manya ofisoshi ba. Kokai wanene kar'a baka aiki a gurbin da baka cancanta ba. Babu wani ɗan siyasa da zai tilasta ƴan ƙasa amsar zaɓinsa a kowace jam'iyya sai wanda takalawan kasa suka zaɓa. Duk ɗan siyasar daya tara matasa da kayan maye da makamai domin bangar siyasa bashi ba mulki har abada. Duk shugaban daya hau mulki dolene ya tsaya akan lafiya, tsaro, ilimin ƴan ƙasa da samar da aikin yi koda ta kananun hanyoyi ne ba lallai sai manya ba. Babu wani shugaba da zai gama mulkin gwamna ya koma mulkin majalisa. Daga mulkin gwamna kanada zaɓi na neman takarar shugaban kasa ne kawai koka koma gefe ka saka ido tunda mulkin ba dole bane.
      Waɗan nan dokoki sun gamasar sun kuma saka jama'ar ƙasar NAYA farin ciki matuƙa. Aka dinga masa addu'a da fatan alkairi da sambarka. Wasu harda kukansu a randa ya miƙa mulki ga sabon shugaban ƙasa da yaci zabe wanda shima shekarunsa basu wuce arba'in ba kacal.
      Ramadhan da Raudha sunyi bankwana da jama'ar kasar NAYA suna kuka da neman gafarar kowa suma harda Abdull mai shekaru tara a duniya daya fara zama ɗan saurayi abinsa. Hakama kanensa ganin iyayensu na kuka da yayansu sai suka dingayi suna dagama al'ummar ƙasar naya hannu alamar bankwana garesu.

(Kai ALLAH sai naji kamar gaske nima sai da nai kuka😭😂🙏🏻)

        Koda forma president Ramadhan B. Hameed Taura ya iso Taura house da tawagar masu rakiya talakawa da abokan mulki da iyalansa tarba suka samu mai girma daga su Anne da tsufa ya ƙara kamawa. Hakama kanensa dake gidan aure kaf suna gidan. Ya rungume su Bappi yana mai zubda hawayen farin cikin sauke nauyi da fatan ALLAH yasa bai taho da hakkin kowa a kansa ba. Sosai mutanen wajen suma suka sake shiga matsar kwalla duk da Ramadhan ɗin ya sakasu wani acan gidan gwamnati kafin su iso nan dama.
      Anyi addu'oi godiya ga UBANGIJI, Ramadhan ya sake mika godiyarsa ga su cos da wasu manyan muƙarabbansa da alkairinsu bazai iya musltuwa da baki a garesa ba. Akaci akasha aka sake addu'ar bankwana kowa ya kama gabansa.
      Daga Raudha har Ramadhan zazzaɓi suka kwanta har kusan sati, dan har Ramadhan na tsokanar Raudha kodai ciki ne tace ALLAH ya kiyaye tayi kenan. Ganin alhini yaƙi sakinsu Bappi ya bashi shawarar daukar iyalan nasa suje su huta.

     Haka kuwa akai, Ramadhan ya tattara ƴaƴansa da matarsa suka wuce ƙasashen duniya shakatawa. Bayan sun ɗan zazzaga suka yada zango a ƙasar America inda yafi wayo. Sun sami tarba ta musamman ga abokansa da abokan kasuwanci ciki harda Sultana datai haƙuri yanzu haka itama yaranta biyu da A.J.
      Rayuwar America rayuwace da Raudha da Ramadhan bazasu taɓa mantawa da itaba. Dan kuwa ta riskesune batare da hayaniyar komai ba kasancewar a baya harkokin mulki na yawan cinye lokutansu. Yanzu ko idan yaran suka nema shiga musu hancima tuni suke tattarasu su aika gidan A.J ko Mufeed ko Sultana. Babu abinda suke sai more ƙara'in amarcinsu da basu sami damar yi a baya ba duk da yanzu kam akwai nauyi na ƴaƴa da canjawar abubuwa da yawa na rayuwa. Dan kuwa dai da gaske Raudha ta koma yar lukuta (kamar bilyn Abdull😂😝👍🏻lol). Shi kansa mai gayya da aikin ƙibar yayi harda tumbi dake tabbatar da shekarun kuruciya sun fara nisa a garesa, dan kuwa arba'in da biyar yake tunkara yanzu. Yayinda Raudhansa ke tunkarar ashirin da takwas. Amma yanda ta buɗe ta zama babbar mace sai kace takai talatin da biyar. (Mace kenan ai, da zarar ka haihu kuma ai sai addu'a. Kai kobaka haihunba inhar akace an wuce shekarun nan na ƙuruciya sai sambarka, duk da dai akwai masu karamin jiki da zakagansu duf-duf abinsu masha ALLAH. Koma dai miye kowa da irin halittar da ALLAH ya tsara masa).

_________________________

     Watansu biyu kenan da baro gidan gwamnati, suna dawowa daga America suka sake dawowa Taura house dan Ramadhan baida sha'awar zama wani gida daban sai cikin family nashi, musamman da yanzu gidan ya koma iyayen sune kawai kasancewar kowa yayi aure kanensa dan Muneera ma dai ALLAH ya iyakance mata tayi auren zuwa yanzun, hakama Lubnah tayi itama. Sai jikoki idan sunzo musu hutun weekend. Shine namiji dole ƴaƴansane zasu kasance a gidan famanet, dan haka ko a yanzu bada wani ra'ayin gina gida ko saye balle tunanin komawa. Ita kanta Raudha nan ɗin yafi mata daɗi tunda tun usil ta rayune a cikin family house.
      Wasu abubuwan sun canju, wasu ko ALLAH daya halicci bayinsa akansu kawai ne ka iya canjawarsu. Dan kuwa har zuwa yanzu babu wata shaƙuwa tsakanin Raudha da Gimbiya Su'adah. Sai dai tana nuna son su Abdull kam. Hakan yasa Raudha batajin komai a ranta tunda dai su Abdull jinintane ya wadatar sonsu ya zama ƙauna tsakaninta da surukar tata mai murɗaɗɗen hali.
     Sosai Bappi da Anne tsufa ya sake baibayesu, dan Yafendo ma tana fama da jiyya a yanzu. Hakama Inna ta Hutawa ALLAH yay mata rasuwa, yayinda shima M. Dauda ke fama da ciwon hanta sakamakon shaye-shaye sigarinsa. Raudha tsaye take akan maganinsa amma al'amarin nasa dai sai addu'a kawai.

         A ɓangaren su Hajiyar Birni itama dai tana fama da ƙafa sosai, dan takai yanzu ko'inama bata iya zuwa. Har ƙasar indiya Raudha tasa aka fita da ita taga likita. Sai dai an samu sauki amma ba'a warke ba abinka da harda tsufa.
        Hajiya Mama ma ta koma gidan mijinta na farko, hakam Asabe na zaune lafiya da mijinta da ƴaƴansa. Dan a yanzu hakama shirye-shiryen auren babban ɗan Alhaji Sageer Dogarai da Yasmin akeyi saboda sun dai-daita kansu. Babu abinda Asabe zatace da ALLAH itakam sai godiya. Ga su Fatisa na zamansu lafiya a gidan aurensu suma da yaransu abin sha'awa. Taga ribar yin tuba na gaskiya da dogaro ga ALLAH da maida dukkan lamura garesa.

     Ga yan prison kam sai muce ALLAH ya cigaba da rabamu da halayya irin tasu ta masu san zuciya, wasunsu baƙin ciki yasa zukatansu bugawa tuni sun bakunci lahira, dan kuwa da ransu ga Ramadhan na mulkin kasar NAYA amma basu da ikon ko ganinsa sai dai su karanta a jarida, wanda suka kai labari kuwa yanda ya sauka cikin salama ƴan ƙasa na kuka da begensa yay mugun haddasa musu ciwon zukata a dalilin hawan jini suma sukace ga garinku nan. Irin su Bushira Hamada da suka rage da rai rayuwar kawai ake cikin baƙin ciki dajin garama a mutu a huta da kallon wani takaicin da baƙin cikin rayuwar. dan a yanzu haka Aunty Hannah fama take da jiyya sakamakon zaftare kafa datai da fatanya wajen yin aiki cancer ta shigeta. Har prison ɗin Raudha takai mata likita na zuwa dubata lokaci-lokaci dan su Asabe kan kanje busting nata, itama Raudha ta taɓa zuwa sau ɗaya lokacin suna kan mulki. Bushira Hamada wai zata kashe Raudha aiko taci duka ranar hanun jami'an gidan prison ɗin. Daga lokacin Ramadhan ya hanata zuwa takuma bi maganar mijinta bata sake zuwa ba sai bayan saukarsu taje harda yara suka duba Aunty Hannah ɗin saboda jikin yayi tsanani sosai.
    
      A hutawa ma dai komai Alhmdllhi, idan ka cire ciwon M. Dauda dake fama da shi, duk da dai yana samun kulawa Alhamdulillahi. Sai dai Rasuwar Inna data gitta ce ta girgiza kowa Har Raudha da Ramadhan dama jama'ar Taura Family duka sun mata halacci sunje harda Gimbiya Su'adah a karo na farko. Hakan yama Raudha daɗi, dan bayan sadakar bakwai data dawo har ɗaki taje taima gimbiya Su'adah godiya.

     Rasuwar Inna baifi da watanni biyu ba Fulani ma ta rasu, nanma dai sun girgiza suka dunguma masautar Bina. Inda su Aynah dake zaune yanzu a masarauta itama dai tana fama da ciwo saboda abinda abokan Aminu sukai mata tun wancan lokacin yafi tabata, dan tasan dai Fulanin ce kawai ta rage gatanta kanwarta Zulfah tunda ta samu tai aure bawani zuwa takeba sosai sai hadimai ke dawainiya da ita saboda tsoron Fulani. Yanzuko babu fulani sai abinda ALLAH yayi kuma kenan tunda Hadiman ba tsoronta sukeba kamar da da idan tazo take takasu kamar itace ta haliccesu. Babanta ko tuni yayi aurensa yana zaune lafiya da matarsa dan harta haifa masa yara biyu maza kyawawa da yaketa alfahari da abinsa. Zulfah dai na tare da shi da matarsa dan ta ɗauketa uwa ita babu ruwanta.......✍


*_Typing📲_*


*_Episode 80 END_*


...........Cikin sauri-sauri take ƙarasa shirin nata. Tayi matuƙar ƙyau cikin ɗanyan shadda da taji wadataccen aiki. Sosai ta zama babbar mace da duk inda ta gitta dole ne a bata girma kodan yanda take cika idon mai kallo. Kwalbar turaren hanunta ta ajiye tana mai juyiwa jin an buɗe ƙofar ɗakin.
      Batai magana ba, sai dai ta tsurama ƙyaƙyƙyawar yarinyar da bazata wuce 4years ido ganin yanda taketa faman tura baki gaba cike da shagwaɓa. Sanin halin ɗiyar tata ya sakata takowa a hankali gareta, ta amshi bowl ɗin hanunta tana kallon abinda ke ciki. “Zee miya faru?”.
        Sake ɓata fuska yarinyar tai hawaye na ciko mata ido. A shagwaɓe tace, “Mamie ba Daddy bane da Saleeha suka cinye min”.
      Kai Raudha ta dafe, a zuciyarta tana tunanin yaya zatai da Ramadhan a gidan nan itako akan cin nama, ƙoƙari take duk yanda zata hanashi ci kamar yanda likita ya saka masa doka. Shiko yasan duk hanyar da zaibi yacisa. Komai batace ba ta kama hanun Zainab suka fita. Kai tsaye falonsa ta nufa inda take jiyo ƙiriniyar Jiddah da Saraki. Dan su Abdull sun wuce Islamiyya. Zee ɗin ma dan bata da lafiyane bataje ba, itako Saleeha ganin Zee bazataba itama ta maƙale.
       
    Kwance yake a tsakkiyar lallausan carpet ɗin falon, Jiddah da Saraki nata tsalle a kansa. Tun kan ta ƙaraso ƙamshinta ya sanar masa. Saraki ya sauka daga kansa da gudu ya nufeta. Ɗaukarsa tai tare da subatar kumatun autan nata. Shima ya sumbaceta da faɗin “I love you Mamie”.
      “I love you too Darling”. Ta faɗa cikin shafa kansa tana murmushi
   Fuska Jiddah ta ɓata tana hararan saraki, hakan yasa Ramadhan faɗaɗa murmushinsa tare da sumbatar goshinta itama yace “I love you sweetheart ”.
      Dariya Jiddah ta sanya. Ta rungume Daddyn nasu tana faɗin “I love you too Daddyn mu”.
        Raudha dake kaiwa zaune tai murmushi da girgiza kanta. Sai kuma ta ɗan taɓe baki da faɗin, “Duk mai kishi da autana dai zai rame a gidan nan”.
      Tashi zaune Ramadhan yayi sosai yana murmushi shima idonsa akan matar tasa, dan kwalliyar tata ta tafi dashi sosai. Kai kace wata anguwa zata. Ido ya kashe mata cike da salo yanda yaran bazasu gane ba. Itako ta hararesa tana nuna bowl ɗin hanun Zee daketa ɓata fuska.
      Idanu ya waro sosai tare da miƙewa ya koma saman kujera idonsa akan Zee. “Zee yaushe kika fara gulma a gidan nan? Mi kikaje ki ka ce?”.
        Cikin shagwaɓa Zee tace, “Daddy bakaine ka cimun dambun nama ba da Saleeha, kuma Mamie tace indai kaci na faɗa mata”.
       Sake waro idanun yay akan Raudha, “Ustazah wannan haɗin faɗan fa?”.
      Fuska ta marairaice masa sosai, a hankali tace, “Dan ALLAH ka daure kabi dokan Doctor, yaushe ka gama shan wahala, sugar ɗinka a shekaran nan kullum sama yake ba ƙasaba Please Noorullah”.
      Murmushi yayi yana kauda kansa. “Ko naci ko banci ba zan mutune Partner. Mizaisa naita azabtar da kaina wajen ƙin cin abinda nake so. Komai inabin dokarsa ai amma bazan iya ƙin cin nama ba gaskiya”.
      Ido kawai ta tsura masa kamar zatai kuka. Dan ita kam batasan taya zata masa bayani ya dinga fahimtarta ba. Su Pa nada sugar amma da yake suna bin doka nasu bai tsanani ba. Shiko sam yaƙi daina cin nama, gashi baya masa cin sauƙi, inhar ya samu zai masa cin tuwo ne. Kuma in zaici safe rana dare bazai gaji ba. Ganin yaƙi yarda su haɗa ido ta ɗauke kanta tana duban Zee da tuni ta ajiye bowl ɗin naman ta koma tsalle-tsalle tare da su Saraki.
       “Zee ina Saleeha?”.
Kafin Zee ta bada amsa Jiddah ta amshe da faɗin, “Taje wajen Granny Mamie”.
        Kowa a gidan yasan a gidan Saleeha ƴar ɗakin Maah ce, dan ita da Dawood (Abbati) ma basa kwana ko'ina sai can, hatta kayan sakawarsu kashi biyu bisa uku nacan. Itako ji take da su kamar mi. Abdull kuwa na gaban goshin Anne ne kowa ya sani.
        Cikin ɗan sauke numfashi Raudha tace, “Okay Zee ki ɗauka bowl ɗin can na saman dining kuje har auta a kaima Granny, ai an kaima Anne nata ko?”.
       “Eh Ya Abdull ya kai mata da zasuje islamiyya”. Cewar Jiddah.

  Suna fita Raudha ta mike ta koma kusa da Ramadhan daya maida hankalinsa akan labarai da ake nunawa a tv. “Wai fushi kake dan nace ka daina cin nama?”.
      Hararta yayi ya ɗauke kansa. Da sauri ta taro fuskarsa cikin hanunta ta hura masa iska ganin zai lumshe ido. “Noorullah Please ka fahimceni, rayuwarka nada muhimmanci a gareni da yaranmu dama duk jama'ar gidan nan. Ina fatan yanda su Bappi sukaga yaranmu muma muga yaran su Abdul haka a duniya. Please sweetheart i love you more”.
       Murmushi ya sakar mata mai sanyi, shima ya tallafo muskar tata. Shanyayyun idanunsa ya zuba mata, “My Heartbeat kinyi ƙyau”.
        Ƙaramar harara ta sakar masa ganin zai kautar da wancen zancen. Ta buɗe baki zatai magana ya manne lips nashi. Idanu ta lumshe a hankali kamar yanda shima ya lumshe nashi, ta san kuma ƙarshen maganar kenan dan haka yake mata a duk lokacin data ɗakko masa irinta. Sunyi matuƙar nisa a faranta ran juna sallamar su Abdull ya ziyarci kunnuwansu.
      A hankali Raudha ta janye jikinta, shima janyewar yay ya kwanta jikin kujera yana mai lumshe idanunsa da shafa kansa. Sai da ta saisaita kanta ta basu izinin shigowa kamar yanda suka horesu. A nutse matasan samarin uku suka shigo cikin fararen kayan Uniform.
         A nutse suka gaishe da iyayen nasu, Abdull ɗan shekaru goma sha ɗaya da hankalinsa ke kan Daddynsu ya kai zaune gefensa cikin damuwa. “Daddy baka da lafiya ne?”.
       Murmushi Ramadhan ya saki, a hankali ya shafa kan Abdull yana ƙoƙarin saisaita kansa. Muryarsa a dasashe kamar wanda mura take son kamawa ya girgiza masa kai. “Lafiya lau nake My son. Kawai dai inajin barci ne?”.
      Abdull yay ɗan murmushi, cikin nutsuwarsa kamar wani babba ya ce, “Oh Daddy babu ƙyau barcin la'asar fa”.
        “Ai bazanyi ba My dear. Kuje ku canja kaya kuyi alwala ku jirani muje Mosque. A kira Auta ma yana sashen Granny”.
       Yay maganar yana shafa kan Abbati da Alhaji ƙarami da suka lafe masa a jiki suma.
     “Okay Daddynmu”.
Abbati ya faɗa cikin ƙiriniyarsa dan kam shi dai babu sauƙine. Yanzun ma shirun nasa nada nasaba da dukansa da Raudha tayi kafin su wuce islamiyya saboda yayi faɗa da Alhaji ƙarami.
     
     Suna fita Ramadhan ya dubi Raudha yana murmushi. “Kinsa Abbana duk yayi laushi kamar bashi ba”.
     Murmushi tai itama tana ƙoƙarin miƙewa. “Daban masa hakaba da yanzu da gudu zai shigo mana kuma faɗan har islamiyya za'aje anayi dan nacinsa. Nikam dai idan ya biyo darun Abba (Mal. Dauda) wahala zaici”.
     Dariya sosai Ramadhan yayi, tare da kamo hanunta ya maidata ya zaunar. Rungumeta yay cikin raɗa da sakar mata kisses a gefen wuya. “Muje daga ciki kiji wani labari”.
     Cikin ɗan waro ido da ture kansa “Kai Ya Ramadhan sallafa kacema yara zaku”.
      “Wayo na musu ai, dan bazan iya sallar nan a hakaba kuma da sauran lokaci ai”.
          “Wai miyasa kakemin hakane? Duk sanda nai kwalliyata saika bata”. Tai maganar murya a narke cikin shagwaɓa.
       “Tukuyci nake badawa ai, tunda dama ni akaimawa ko”.
     Zatai magana ya sake rufe mata baki ya hanata. Babu yanda ta'iya dole ta amshesa hannu biyu. Daga ƙarshe suka shige bedroom.✍

Hummmm bari dai na tsaya daga nan kar bin ƙwaƙwƙwafin yay yawa kuma😜.

*_ALHAMDULILLAHI! ALHAMDULILLAHI!! ALHAMDULILLAHI!!!_*

_Godiya ta tabbata ga UBANGIJI daya bani dama da rai da lafiyar rubuta wannan ɗan littafi. Abinda na rubuta dai-dai ALLAH ya bamu ladan baki ɗaya. Wanda nai kuskure ALLAH ka yafemin ni da ku da kuka karanta._

*Kamar ko yaushe ina neman afuwan duk wanda na ɓatamawa a yayin rubuta wannan littafin. A yafemin, a yafemin, a yafemin. Nima duk wanda ya ɓatamin na yafe masa, sai dai banda wanda ya zalinceni akan ganganci ko son zuciyarsa. Shima inhar yazo ya roƙa gafarata ya sanarmin zan iya yafe masa da fatan zai kiyaye gaba. Zata iya yuwuwa wannan shine littafi na karshe da bilyn Abdull zata rubuta a duniyar rubutu😭🙏🏻 babu ruwan mutuwa dauka take a duk sanda taso.

*_Bazamu gaji da godiya a garekuba masoyanmu, kun nuna mana halacci kamar yanda kuka saba. ALLAH ya saka muku da alkairi ya bar zuminci, alkairin ALLAH yakai gareku a duk duniyar da kuke. Zafafa biyar na muku son so irin trillions ɗin nan wlhy. ALLAH ya saka da alkairi musamman wanda ke tare da mu tun farkon zafafa har zuwa yau. Kai harma wanda suka fara binmu yanzu duka mun gode sosai🙏🏻_*

_Kamar yanda na faɗa BAƘAR INUWA ƙirƙirarran labarine. Idan kaci karo da abinda yay kamanceceniya da rayuwarka kayi haƙuri bakai din ake nufi ba. Sannan bazan gaji da sanar da mai karatu cewar littafi nishadi ne, faɗakarwa ce, harma da ban haushi. Idan kaci karo da nishaɗi kayi badan dole saika samesa ba ko ka nema. Idan kaci karo da ilimi ka amfana gwargwadon fahimtarka. Idan abin haushine ka ɗauka adon labari ne. Rayuwar novel bawai babu ita a zahiri bane, sai dai ba lallai kowa ya sameta 100% kamar littafin ba, idan ma ka samu kasa a ranka akwai ƙaddara da jabawar da zata iya banbanta da hikayoyin marubuta_.

*Abinda kaso gani baka gani na rubuta ba amin afuwa ajizancine irin na ɗan adam da mantuwa. Wanda yazo ba'a yanda kaso ba shima kayi haƙuri ba komai ake samu a yanda ake son gani ba. ALLAH ya sadamu da alkairinsa a zafafa karo na 7 da zasu zo muku nan kusa insha ALLAH😘😘😘😘🙏🏻👍🏻*

*Mallakin Bilkisu Ibrahim musa (Bilyn Abdull)*


*_Yi ƙoƙari ka biya na kuɗi ne, kar kuci hakkin daba naku ba_*


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta app ɗin dake a play store, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp da zaran kinyi Searching littafin BAƘAR INUWA ⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*


*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_


Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*


Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77


*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________


*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
Chapter 7 · 0% Book details