← Book details Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 3

Gabatarwa

Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 143 min read

Root Entry
WordDocument
0Table
Data
Normal
Normal Table
Table Grid
Medium Grid 3
Medium Grid 3 Accent 1
Medium Grid 3 Accent 2
Medium Grid 3 Accent 3
Medium Grid 3 Accent 4
Medium Grid 3 Accent 5
Medium Grid 3 Accent 6
AUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATIMAH.
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIKAI SALATI DA DAUKAKA DA AMINCI SU TABBATA GA FIYAYYAN HALITTA ANNABIN RAHAMA MUHAMMAD BIN ABDULLAHI DA ALAYENSA DA SAHABBANSA WANDA SUKA BISHI HAR ZUWA TASHIN ALQIYAMA.
Wannan littafin kifkirarran labari ba'a yishi Dan wani ko wata ba duk abinda akaci karo dashi Arashi ne kawai.
This Book is dedicated to you Ten sisters.
Allah ya Kara Mana zumunci.
Paga one
..........A hankali motar da shigo layin dai dai wani katafaren gate ta tsaya, yanayin yanda take fidda wani Dan Kara alamune dake nuna motar tayi dogon zangon tafiya, direban Bai Danna Horn ba bara a kaiga bude gate din gefen wata bishiyar dorawar tururawa ya karasa da motar, wasu dattawa ne su buyi suka fito daga bayan motar yayin da wani matashi ya fito daga mazaunin direba, Mika yayi dareban tare da salati.
Kofar gidan suka nufo da kafarsu Dan matshin be yayi nocking kamar day biyu kafin wani dattijo ya leko ta wata karamar kofa jikn gate din.
Da sauri ya bude kofar Yana fadin "A'a Alhaji barkan ku da zuwa kin Sha hanya sannunku" tare da Basu hannu sukayi musabiha suna fadar "wlh kuwa malam Sani ya muka sameku?".
Cikin fara'a yake fadar "Alhamdulillahi".
Kafin yayi gaba Yana cewa "Bari nayi Muku iso gurin Alhajin Allah ya taimaka Yana nan".
Harabar gidan suka shiga suka rufawa malam Sani baya zuwa bangaren Mai gidan inda yake ganawa da bakinsa.
Lokacin da suka karaso gurin kofar shi Kuma Malam sanin ya fito Yana fadin "Bismillah ku shiga, sannunku".
Yayi gada da sauri Dan cika umarnin Alhajin na Kiran babban Amininsa na kankankan Malam Bukar.
Da sallama suka shiga falon, Masha Allah komai najin dadin rayuwa akwai shi a falon tamakar fadar wani sarkin.
Cikin fara'a da sakin fuska Alh Jafar Mai Yadi ya nufo bakin nasa Yana fadar "A'a! Alhaji Sulaiman kune haka cikin wannan ranar ga nisa".
Amma kasan zuciyarsa mamaki ne fall a cikinta shi dai yasan ba wani abu daya taso da zai kawosu a irin wannan lokacin a kalla suna da sauran kwanaki uku kafin duzo duk da sun bada duk abinda ake da bukata lokacin kawai ake jira. Amma dai ko meye Allah yasa Alkhairi ne.
Bayan gaishe gaishe na al'ada daya daga cikin 'ya'yan Ahj Jafar ne yayi sallama ya shigo Yana gaishe da bakin Yana aje musu lemon da ruwa ya fita.
Wani matashin ne shima ya shigo da manyan warmers da wata yarinya da basket Mai dauke da plates da cokula da cups Suma suka gaishe dasu suka fita.
Tunda aka Fara shigo da wannan karamar arzikin Alhaji sulaiman ya sadda Kai kasa zuciyar idan tayi dubu to a bace take.
"Bismillah kuci abinci kafin mu shiga sallah tunda Azzahar ta gabato".
Alh Jafar ya fad'a Yana nufar kofar fita.
Bayan fitar Alhaji Jafar Alhaji Ismail ne ya kalli Yayansa Alhaji sulaiman "Nifa duk na rude wallahi har na rasa ta inda zamu Fara fad'a musu irin wannan magana duba da irin karamcin wannan bawan Allah".
Ya fad'a yana Jan siririn tsaki.
Dan matashin daya tukosu ne yayi magana "wlh Daddy naso kun hakura da zuwa ita Hajiyar tazo da kanta ta fad'a musu abinda ta kulla, ni ban taba ganin irin wannan ba anyi Abu cikin mutunta juna har an kawo wannan gabar Amma Rana tsaka irin wanna ta taso Babu Dadi ni wallahi tausayin Musbahun nakeyi ya shiga wani hali Amma ita ko a jikinta".
Shi dai Alhaji sulaiman Bai Kara magana ba haka Bai ko kalli abincin ba duk da yunwa da yakeji leonm da ruwa kawai ya sha, Alhaji isma'il da Al-Amin ne sukaci abincin suka fita zuwa masallacin kofar gidan.
Tare suka shigo gidan bayan idar da sallar har da Malam bukar domin shine limamin masallacin.
Sabuwar gaisawa suka karayi Amma wannan lokacin Al-Amin Bai biyosu ba.
Alhaji sulaiman ne yayi Qarfin halin Fara magana Yana kallon Malam Bukar "Dan Allah malam ayi hakuri da abinda mukazo dashi WALLAHI badan Nan gidan bane Babu abinda zai Kara dawo Dani garin Nan".
Yayi shiru ya kasa karasa maganar saboda wani abu daya tsaya Masa a makogwaronsa yana masa tukuki.
Shima Alhaji Jafar wani abune ya tsirga masa har tafin kafarsa ga wata irin faduwar gaba taba gaira ba dalili.
Shiru falon ya dauka na wucin gadi kafin Malam Bukar ya magantu "Alhaji ka Fadi ko menene ba wata matsala ita rayuwa ba yanda Bata zuwarwa bawa ko Dadi ko akasin hakan, Kuma duk musulmin kwarai ai yasan kaddara, ba damuwa ai and Zama daya".
Alhaji Ismail ne ya karbi maganar ganin yayan nasa bashi da niyyar cigaba da maganar.
"Ayi hakuri Malam kan maganar auren yaron gurinmu ne da yarinyar gurinku, wata fitina ta taso yau kwana uku kenan ana Abu daya mahaifiyarsa ta kafe kaida fata Bata amince ya auri Zahra ba duk yanda mukaso gyara abun ya gagara karshe ma cewa tayi idan har Musbahu ya auri Zahra Bata yafe Masa nononta daya sha munyi munyi da fad'a Mana dalilinta na wannan cin zarafin Amma ta kekashe taki fad'a karshema abun ya zamar Mata lalura kamar ta jinni". Tunda ya Fara kora bayani Alhaji Jafar ke maimaita Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, domin duk wani karfin gwaiwarsa ya Kare wannan wace irin musiba ce kullum idan auren yarinyar nan ya taso sai an Sami wani akasin ya taso shi Lamarin Nan ya rasa yanda zeyi dashi.
Malama Bukar ma rasa abin fad'a yayi duk wani kuzarinsa ya Kare.
Yayin da su Alh Sulaiman suketa nanata ban hakuri.
Cikin muna juriya da dattako Malam Bukar yace "haba Alhaji ba komai kasan komai nufi ne na Allah Daman Bai Qaddari shine mijinta ba, Allah yasa hakan yafi musu Alkhairi su duka'.
Gaba data suka amsa da Amin.
"Amma dai Abu baiyi Dadi ba wallahi ba Baki nayi musu ba Amma kafin a Sami Mai nagaratr yarinyar Nan zasu Dade suna nema" cewar Alhj Ismail.
Har gurin mota suka raka bakin, har suka daga bakinsu Bai Dena bada hakuri ba.
Bayan tafiyarsu falon su Malam suka dawo jiki a sanyaye duk Lamarin ya cakule wannan wace irin kaddara ce ke bibiyar karamar yarinya haka aure dai dai har uku ana fasawa.
Cikin nuna damuwa Alhaji Jafar ya kalli Malam Bukar yace "malam inshallah Allahu wannan karon zan aurar da Fatima tunda Naga lamarin bana arzki bane ko meye in Sha Allah sai Naga bayansa'.
Tunda Alh ya Fara magana Malam Bukar ke girgiza Kai shima lamarin ya kaishi makura yasan lamarin yarinyar akwai magauta a cikin Amma ganin an samu rata Mai yawa a tsakani ya dauka abun ya wuce ne.
Cikin nuna alhini Malam ya kalli amininsa yace "Dan Allah Alh kayi hakuri kada kayi Abu cikin fushi da kace zaka aurar da ita kada azo ayi aikin Dana sani".
Kujerar dake daura da Malam din ya zauna kafin ya sauke ajiyar zuciya.
"Ko daya banyi fushi da ikon Allah ba kawai dai na gaji da wannan wasan ne kullum na Zama karamin mutum saina Raba I.V na daurin sure azo ace an fasa wasu ma sai su zageni ace Dan bani na haifi Fatima ba na saka ido ana Mata wannan cin zarafin wlh da banyi alkawarin daina hada auren zumunci ba da yau ba sai gobe ba zan aurawa Abdul Hakeem ita. Amma yanzu ma Bata baci ba ka nemi shawarar Mahmud na Nan gurinka idan ya amince na bashi auren ta".
Cikin kaduwa Malam Bukar ya kalli Alh Jafar yace
"Wane Mahmud din, ba dai na Nan gurina ba?".
Cikin yadda da Kai Alh Jafar yace "shifa nake nufi ko akwai wani Mai wannan sunan a gurinka?".
Gargiza Kai Malam din yayi tare da fadar "Babu, Amma Alhaji al'marin Mahmud ba boyayye bane a gurinka kada duniya ta zagemu fa".
Gyara Zama Alhajin yayi kafi ya fuskanci amininsa sosai.
Wallahi Malam bana gudun duk abinda za'a fad'a na yaba da nutsuwarsa idan kaga ba'ayi ba to shima Allah Bai nufi mijinta bane Amma na jima Ina yiwa 'ya'yana sha'awarsa".
Kai kawai Malam yake jinjinawa shi lamarin duk yazo Masa a baibai ya jima Yana nazari akan lamarin Fadima kullum Abu daya yake gani mijinta ba Nan kusa take ba bil hasal ma wani lamari yake gani Mai girma dangane da mijin nata da wani irin Haske Amma koda Wasa Bai taba fadawa Alhajin ba sai dai Yana yawaita saka almajiransa gurin yi Mata addu'a.
Sun jima suna kullawa da kwancewa a tsakaninsu daga karshe suka tsaya a malam ya tambayi ra'ayin yaron idan yana so la'ba'as.
_______
A hankali take sakkowa daga stair din tamkar wani dawisu Tasha make-up da wata gawon Mai azabar kyau Sai karamar pos a hannunta daga bayanta 'yan Mata ne su biyu ko wacce Tasha nata gayun, tun kafin su karasa sakkowa kamshinta Mai saka nutsuwa ya gauraye ilahirin falon.
Falon a Cike yake da jama'a kowa ka gani ta amsa sunanta sai tsirarun yara.
Da sauri wata ta matso gurin su tana rangada buda, tana fadar "Masha Allah Amarya Allah ya kade hau da bala'i ya bada zaman lafiya Hajiya Zahra suga bayi farin banza jikar hardon fulanin Mubi jikar larabawan Jodan da larabawan madinatul munawwara kaga musu kyawun asali Amarya a gidan Mushahu alherin Allah yakai Miki".
Wata daga cikin matan dake zaune ta tashi ta sunga zubawa marokiyar kudin ita Kuma tana Kara Koda Amarya Zahra.
Aunty Hasana ce ta fito daga wani Dan korido ta karaso tana kallon kanwar ta ta, tana Kara tasbihi ga ubangiji daya halicci wannan kyakykyawar surar.
Hannaun Zahra ta rike tana kallon Baba Tabawa Mai aikinta yanda ta zage tana jero kirari kamar wata marokiya.
Dan murmushi tayi tana fadar "Masha Allah, Baba Tabawa yaushe Kika Zama marokiya bani da labari?"
Dariya tayi tana fadar " ai ko ban iya ba na koya mu Abu namu bikin uwar dakina guda kinsan biki na d farar kaza balbela ba gayya ce ba, yakuwar kan kabari kenan baking cikin 'yan taushe, murucin kna dutse Baki fito ba sai da kika shirya"
Dariya sukayi gaba daya, har gurin da zasuyi bridal shower din kawar Aunty Hasana da Baba Tabawa suka raka Zahra.
Sun chashe, sunyi hotuna kamar ba gobe sai dai duk Wanda yasan Zahra yasa Bata cikin walwala haka nan take Jin wata irin faduwar gaba da rashin dadin zuciya Amma ita kanta Bata San taka maimai me yake damunta ba gashi tun jiya take neman wayar Mushahun ta kasa samun shi, haka ta abokinsa Deeni itama shiru a yanda sukayi dasu yau ne ranar da zasuzo Dan har hotel din da zsau zauna sun Kama mukullan ma suna hannun magaji.
Dadin dadawa yau sukayi za'a kawo ya'yan yayar shi da wasu cussing dinsa.
Sai gurin karfe Tara suka Gama shagalinsu, Zahra Bata koma saman ba inda akayi musu masauki Sai ta nufi bed room din Aunty Hasana na kasa dakin ba kowa sai kamshin freshner da turaren wuta yake tashi ga danyi AC ya gauraye dakin. Head din ta cire ta aje kan bed side locker kusa lamp, gadon ta hau ta kwanta lamo kamar ba mutum akai Dan ko kwakwkwarwn motsi Bata sonyi wata irin kasala ce ta sauko Mata.
Ta jima a dakin kafin taji alamun bude kofar Bata daga Kai taga ko wanene ba kamshin da taji ne ya sanar da ita Auntyn ce.
Kusa da ita ta zauna tana Kai hannu jikin.wuyanta tare da tambayar "me yake damunki? tun safe Ina Kula da mood dinki Sam bakya cikin nutsuwa".
Ta fad'a tana kafe Zahrar da Ido.
Yunkurawa tayi ta tashi zaune tare da fadar "Nima bansan me yake damuna ba wlh Aunty Sam bana Jin dadin zuciya ta sai zafi take min Kuma gabana sai faduwa yakeyi".
Ta karasa fad'a tana shashhshekar kuka kasa -kasa.
"Meye Kuma abin kuka? keda zakiyi farin cikin Allah ya kawo lokacin bikin ba kamar lokutan baya ba da aka dunga samun akasi".
Kanta ta kifa a jiki Auntyn taci gaba da kukan ta marar sauti.
Bata hanata sai tayi Mai isarta kafin ta Sami zarafin magana.
"Aunty wlh Ina ji a jikina kamar wannan ma za'a Sami matsalar kinsan jiya saida nayi irin mafarkin da nakeyi idan za'a fasa aurena".
Ta fad'a tana Kara goge kwallar data ciko Mata Ido.
Kallon ta kawai Aunty Hasana take ita fa lamarin yarinyar Nan Yana Bata tsoro kada fa namijin Aljani ya aure ta suna zaune Basu Gane ba.
Karo biyu ana saka bikinta abun Yana lalacewa toga wannan ma, itama fa kawai daurewa tajeyi tunda Zahra ta fad'a Mata Musbahun Bai kira ba Bai kumazo ba ba wani Kuma nasa da yazo alhalin ba haka aka tsara abunba, Amma sai tayi ta maza tace.
"Haba Zahra ya Zaki ringa fadar irin wannan maganar kiyi addu'a ba abinda zai Sami aurenki wannan karon sai Alkhairi, Ina ga da abinda ya hanasu karasowar har yanzu ki jira zuwa gobe Mana maza kiyi sallah kici abinci a sakonki can ki dauko zuwa an jima sai kiyi amfani dashi.
_________'
GIDAN MLM BUKAR
Bayan idar da sallar insha'i Malam da sauran manyan Almajiransa suna Zama ana karatun littatafan fiqihu da hadisan Manzon Allah s.a.w.w, a Nan cikin baban falonsa ake karatun an kwata shi sosai a zuba kujeru na alfarma, saida aka Gama karatun sannan sukaci abinci kamar yanda aka Saba kafin Kuma kowa ya nufi nasa gurin duk da makarantar ta Sami cigaba sosai kamar ba makarantar amajirai ba anyi Mata tsari sosai a zamanace Dan har hostel garesu sama da kasa da gurin koyon sana'a Kuma ana musu abinci basa zuwa bara, sannan akwai malamai da aka dauka suna koyar da karatun boko tun daga mataki primary, junior, zuwa senior, secondary suna kokarin Fara turo dalibansu zuwa manyan makarantu, sun Sami wannan cigaban ne karkashin wata kungiyar NGO ne.
Lokacin da Mahmud da Habib zasu fita Malam yayi gyaran murya duk su biyun suka juyo, Mahmud yayiwa alama daya dawo shi Kuma Habib ya fice..
Nan kusa da Malam ya zauna ta lakwashe kafafuwansa kamar zaman daukar karatu.
A hankali Malam yake Kare masa kallo shi kadai yasa abinda yake kissimawa a zuciyarsa sai Kuma Allah daya hallice shi.
Sun dauki kamar minti uku a haka kafin Malam ya magantu.
"Mahmud"
Malam ya Kira sunansa.
Cikin ladabi ya amsa Masa da "na'am Malam".
"Kasan dalilin dayasa nayi kiranka?".
Cikin ladabi ya amsa da "A'a"
Cikin wani irin yanayi Malam yace "wani nauyin Kuka aka Dora min Wanda na rasa ta inda zan Fara maka bayani".
Zamansa ya gyara Yana Kara fuskacin Malam din Yana fadin "Malam ka fad'a min ko menene ni maiyi maka biyayya ne In Sha Allah".
"Ai kasan gidan Alhaji Jafar nawa za'ayi bikin yarinyar gurinsa ko?"
Kai ya gyada Masa tare da cewa "Eh na Sani ba Zahra za'a aurar ba?"
"Eh ita fa, to an samu wata matsala ne wadda ta haddasa kasa auren a wannan karon ma kamar lokutan baya Amma wannan sai yafi na bayan Muni domin kuwa saura ba kaiwa ga Fara bikin Amma wannan Saida abun ya kurace har an saka yarinyar a lalle sun Fara duk kwaramniyar su ta Mata a lissafi saura kwana uku daurin aure sukace sun fasa, shine shi Alhajin yace na meni shawararka idan ka amince zaka iya auren yarinyar ya baka za'a daura muku aure ranar juma'a inshallah Allahu".
Da sauri Mahmud ya dago Yana kallon Malama bakinsa har rawa yake yama kasa furta maganar dazai fad'a Kai ya shiga girgizawa dafa shi Malam din yayi Yana fadin "ka nutsu bazamuyi maka dole ba idan bass sonta sai a nemi wata mafutar"
Da kyar ya tattaro nutsuwarsa ya kalli malam yace
"Ba haka nake nufi ba, gani nayi yaushe nakai matsayin da za'a bani irin wannan yarinyar aure kamar tafi karfina ni almajiri ne wanda ban aje ba banba wani ajiya ba, kuma tana da ilimi Mai zurfi ba lallai ta yadda ta zauna dani ba".
"Ba wannan nake son jiba daga bakinka fadin Kai ko wanene ba taso ba Alhaji shi yafi sanin Kai ko waye amsa muke bukata zaka iya aurenta ko bazaka iya ba ?".
Cikin alamar sarewa yace "wane ni ice bana son wannan yarinya na karba na gode Allah ya saka da Alkhairi".
Ya fad'a cikin wata irin murya Mai sanyi.
"A'a kaje ka nutsu kayi shawara sai ka fad'a min duk huku cin daka yanke, tashi kaje dare ya farayi".
Yunkurawa yayi ya tashi Yana fadar "sai da fade"
"Allah ya tashe mu lafiya" cewar Malam.
Daga falon malam Mahmud bakin titi ya nufa inda yake tunanin ganin Habib Yana son ya karbi lifan dinsa zaije wata unguwa.
Gurin Ashiru Mai shayi ya Fara zuwa baya nan sai su salisu da Bashir Suma duk mutanen Mahmud ne hannu ya Basu saka gaisa sannan ya tambayesu Habib wani ne daga can gefe yace "ai yanzu ko runhu ka rike yana gurin Ubaidat kasan mutumin naka Yana neman dauko dala ba gammo".
Ya karasa fad'a Yana dariya Bashir ne yace "ko wani Abu ne Naga ko Zama bakayi ba"
Da tsaki yayi Yana Dan dafe kujerar kusa dashi Yana fadar "wlh lifan dinsa zan karba zan danje unguwa".
"Kai haba saboda lifan kake wannan zagaye zagayen ga nawa kayi amfani dashi mana".
Ya fad'a Yana Miko Masa makullin ya karba Yana godiya.
Kai tsaye zaranda hotel ya nufa.
AUREN HUCE HAUSHI
MAMAN FATIMAH.
Page two
________
Safa da marwa take tun bayan gama sallar insha'in ta, ta Kira layin wayar tafi sau shurin masaki Amma ta kasa samun Wanda take nema, gumi ne yake fama tsatsato Mata daga goshinta, ta kasa zaune ta kasa tsaye.
Gafen gadonta ta koma ta zauna Kara kiran tayi cikin ikon Allah sai Kiran ya shiga da sauri ta nufi kofar toilet dinta na daki ta shige.
Bata tsaya amsa sallamar wadda ta Kira din ba ta Fara magana "Asabe me yake faruwa ne tun jiya nake neman wayarki Bata shiga Ina cikin tashin hankali komai fa Yana nema dagulewa, ba alamun nasara a wannan karon tunda komai ya kankama".
Shiru tayi tana sauraran wadda ta Kira Asube ta jima tana sauraran ta kafin tayi dariya tace "haba yanzu naji magana da har hankalina ya tashi ki rike sauran maganar sai kin shigo gobe ma karasa".
Ta kashe wayar ta bude kofar toilet din ta fito cikin farin ciki da walwala sabanin yanda ta shiga.
Mahmud.
Ya jima a cikin hotel din kafin ya fito zuwa gurin securities din da alama sun saba sosai Dan yanda suke bashi girma sai abin ya baka mamaki makullin lifan din Wanda ya barwa ya miki Masa tare da fadar
"Yallabai an zubo petrol din".
Lokaci daya Kuma Yana Miko Masa kudi, kallon na mine yayi masa.
"Kudin sunyi yawa ne a sayan man Saida naje na duba maga yawansu". Ya fad'a Cike da ladabi, hannunsa ya zura a aljihun wandon jikinsa ya dauko wasu ya Kara Masa, sannan ya Kuma dauko wasu ya bashi alamar ya baiwa abokan aikinsa.
Godiya suka dunga jero Masa Dan inda sabo sun saba da Alkhairinsa.
Kai tsaye gurin Ashiru Mai shayin ya nufa duk da dare ya Fara Amma yasan yanzu 'yan term din nasa Basu Isa tafiya gida ba Dan sukan Kai har daya na dare suna hira.
Makullin lifan din ya mikawa Bashir Yana fad'a "Jazakumullahu khairan".
Habib ne yace "Wai Dan Allah Ina kaje a rufe wayarka tun dazu nake nemanka fa daga inje in dawo kawai na nemeka na rasa sai su Salisu ne sukace kazo nemana ka wuce unguwa".
Kusa da Habib din ya zauna na fadin "wash Allah wlh duk na gaji".
"Da kayi aikin me".
Cewar Habib.
"Bari kawai ba aikin da nayi Amma Wanda yake fuskantoni ba sauki kazo muje gida akwai sakonka da Malam ya bani na baka".
Ya fad'a Yana kikewa tare da mikawa su Bashir hannu yayi gaba gurin lifan din Habib.
Dakinsu Mahmud ya bude daki ne madaidaici da gado guda biyu da wardrobe ta jikin bango sai mirror irin na croom din Nan da AC, kasan dakin shimfide da tayil, lokacin da akazo aikin NGOs din ne aka yiwa Malam nashi falon da Kuma irin wadannan dakunan guda uku sai Kuma dakunan Yara almajirai sama da kasa.
Dakin sai kamshi yakeyi, sau da yawa Habib kanshi Yana mamakin wasu abubuwan na Mahmud sai dai ba fuskar da ze tambaye shi duk kuwa da amincin dake tsakaninsu.
Saida Mahmud yayi wanka ya saka kayan barci sannan ya
Zauna a gefen gadon Yana fuskantar Habib kafin yace.
"Kai inaga fa nan da kwana uku zan ankwance".
Ya fad'a yana wani killer smile.
Zabura Habib yayi ya tashi zaune sosai Yana fadar
"Kamar Yaya?"
"Kamar yanda na fad'a maka, tsayar Dani da Malam yayi kenan yace Alh Jafar ya bani auren yarinyar Nan da ake bikinta wadda Abdul Hakeem ya kawo Mana IV last week".
"Ban Gane ba bafa ta Yaya hakan zata faru?"
Kafada ya dage alamun shima Bai Sani ba.
"Dan Allah kayi min bayani yanda zan fahimta a sakani a duhu wallahi".
"Iya abinda na Sani kenan kawai ance an bani idan inaso inyi shawara".
Cikin madaukakin mamaki Habib yace "to Kai ya kace masa?'
"Me zance kuwa na karba na gode, kasan har abada ba jayayya tsanina dasu iyayene sak, sun min abinda kowane uba yakewa dansa sun min gata sun Kula Dani lokacin da bana Gane gabas bane Gane yamma bana Gane fari bana Gane Baki,
Sun zamar min garkuwar data Hana kowane harbi ya sokeni, Toni kuwa wanen irin butulu ne da zan watsa musu kasa a Ido sufa sun san waye ni Amma suka runtse idonsu suka bani basu nuna min kyama ba, sannan ka dubi yarinyar da aka bani diamond ce fa a cikin gold kasan bani da abinda zan tunkari irin wannan yarinyar da sunan soyayya bare har aje ga maganar aure".
Tunda ya fara magana Habib yake Masa kallom mamaki Yana jinjina karfin ikon Allah, lallai wani lamarin sai Allah.
Da kyar ya Sami zarafin fadin "Masha Allah! Allah ya Sanya Alkhairi Abu yayi Dadi amma fa ka daina fadar Wai baka da abinda zaka tunkare ta wlh kafin wanna lagwanin Wanda zata aura say millions shi har wani namiji ne kawai Abu daya Sani yana da kudi mu Kuma bamu dasu Amma muna da abinda bashi dashi".
"Kamar Yaya me muke da shi Wanda shi bashi dashi? ka duba fa kaga irin yanda yake shiga babban yaro ne ga manyan motoci mu Ina muka gansu"
Dan karamin tsaki Habib yayi Yana fadain "ana gabas kana yamma ana maganar nagarta da mutunci da cikar Kamala da siffar mazantaka kana wata maganar, mu an fad'a maka haka zamu dawwama bazamyu arzikin ba".
Dariya Mahmud yayi "maida wukar abin Bai Kai haka ba ko Daman haushinsa kakeji ne ban sani ba?"
Habib tsayawa yayi galala Yana kallon Mahmud kafin ya karayin wani tsakin "Allah ya sauwake zanji haushinsa Ina ruwana dashi kawai da Daman can no banga dacewar su ba Kai Nifa idan Malam yasa Yara suyi Mata addu'a har cewa nake suyi Mata addu'a Allah ya Bata gwarzon miji na nunawa sa'a".
"Amma wallahi Habib baka da mutunci shi wannan ba gwarzo bane?"
"Ina fa namiji Yana rausaya kamar mace".
"Kaga Yi closing din wanna chapter din yayi zamuyi da wannan lamarin kaga dai komai fa Sai a hankali Dan abinda nake Sami daga wannan organization din ba Isa wannan shidimar zasuyi ba ga yarinyar Mai zafi ni kamar ma tsoronta nakeji fa".
Ya fad'a Yana dariya.
Sun jima suna tattaunawa yanda zasu bullowa lamarin.
_______
Tunda garin Allah ya waye Amma take ta kaiwa da kawowa tsakanin kitchen da dakinta zuwa dakin Baki, Saida aka kammala abincin breakfast aka babba mutane sannan ta samu ta koma daki inda ta samu kanwar Babarta Inna Maimuna a uwar daki.
Kallonta tayi "Asma'u ya kamata ki karya kinsan Ina tunanin zuwa anjima gidan ze Fara cika bazaki Sami damar Zama kici wanti abun karki ba, waini ina Hajiya Mama ne Naga yau Bata leko ba?"
"Tana bangaren Alhaji Nima nayi wannan tunanin Amma ai lafiya ita keyin shiru".
"Hakan ne Kam".
Cewar Inna maimuna.
******
Katagum road
A dakin Aunty Hasana Zahra ta kwana ita da Autart Haneefa, sai kusan goma ta tashi daga barci wayarta ta Fara dubawa ta tarar da missed calls rababa Amma Sam babu nasa ko na wani daya dangance shi, duk na kawayen da abokanin arziki Bata bi rakansu ba ta shiga toilet wanka tayi, lokacin data fito Sajida ta Samu a dakin ta shigo Mata da breakfast dinta nan, tunda ta fito Sajida ke kallon ta har ta karaso gurin mirror inda sajidar ke zauna murmushi Zahra tayi Mata tana fadin "wannan kallon fa ko na canza Miki ne?".
Kai ta gyada Mata "gaskiya Kam ba haka na Saba ganinki ba, meye yake faruwa ne? nifa tun jiya nake nema Deeni da wannan cussing din na Mushahu Aliyu, ta Aliyun tana shiga ba'a dagawa Amma su sauran wayoyinsu switch off".
Da rausayar da kanta tayi tana Dan watsa hannuwa "wallahi bani da masaniyar me yake faruwa nima hakan take kamar ke Amma nasan dai kome aje ciki yau dole su shigo garin. Ni wallahi da Aunty Hasana zata yadda da an hakura da wannan mother's day din nifa duk abin ya fice min daga Rai gani nake shima wannan aure ba yuwuwa zaiyi ba nasan dole da wata a kasa ai ba haka muka tsara abubuwan ba Amma kin ko daya fa basuyi attending ba".
Ta karasa maganar idanunta na cikowa da hawaye.
Hannunta Sajida ta kamo ta rike tana fadar. "Hqba Bestie kada kiyi Kika in Sha Allah ba wani matsala sai Alkhairi kada ki Bata lokacin farin cikinki mana".
Aunty Hasana ce ta shigo da sauri alamar wani Abu zata dauka turus tayi tana fadar "ke me zan gani Zahra kukan dai? haba you have to be very strong Mana kada ki yadda aga rauninki a kowane janibi ki Zama jaruma Mai iya fuskantar ko wane kalubale, kada ki kara saka damuwa a zuciyarki zan fita Amma in Sha Allah bazan Dade ba ki shirya kuje sama naji suna cigiyarki".
A bangaren Mahmud kuwa bayan anyi sallar Asuba a masallaci ya zauna yayi azkar dinsa Saida gari ya Fara haske sannan ya fito lokacin su Malam sun Gama karatun da sukeyi da maza magidanta.
Da sallama ya shiga falon nasa lokacin Abubakar Yana mayar da littatafan mazauninsu, sai da ya zauna sannan ya Dan rankwafa Yana gaishe da malam, Amma sai ya moko Masa hannu sukayi musabiha Yana fadin. "hakan shine sunnar Annabin Rahama Muhammad s.aw.w."
Shiru falon ya dauka bayan fitar Abubakar Malam Bai tofa ba haka Mahmud shima, Malam ne ya kauda shirun "Ya ake cikin Mahamuda wace shawara ka yanke?".
"Ba damu Baba Malam na karba na gode ayi min godiya Allah yasa hakan yafi Alkhairi".
"Allahumma Amin. Allah ya Sanya Alkhairi ya Baku zuri'a Mai Albarka Allah yasa ace gara da akayi hakan"
A zuciyarsa yake ta amsawa da Amin.
Harya yunkura zai tashi Malam yace "koma ka zauna, Ina zaka bamuyi maganar inda zaka ajeta ba da sauran shirye-shirye".
Sadda Kai yayi haka Nan yaji wani irin nauyin malam din ya taso Masa.
Kansa Yana kallon kasa yace "so nake muyi shawara dasu Habib yanda muka yanke saiya fad'a maka".
"A'a ba haka za'ayi ba nizan bada sadaki da kayan goro da alewa sai Kuma shaddoji da za'a kawo an jima Suma dinkakkune tunda abun yazo a kurace, sai Kuma gidan Nan na Hayin Banki mukullin na gurin Binya tun jiya na bashi nace yau zakuje a duba abinda za'ayi Masa".
Mahmud kasa magana yayi shi wannan gatan har yayi Masa yawa komai anyi Masa.
Rarrafawa yayi kamar yaro har gaban Baba Malam ya rinka godiya har Saida yayi Masa fad'a.
********
Amma ce da Inna a uwar dakin Ammar bayan dawowar Ammar daga bangaren Alhaji cikin tashin hankali Innar ta kalli Ammar tana fadin ke Asama'u wace irin magana ce wannan yaushe hakan ta faru duk bamu da masaniya?"
Dan nisawa Ammar tayi.
"Wallahi Nima ban sani ba Amma yace kada yaji kada ya gani naja bakina nayi shiru yana zargin kowaye yake lalata lamarin auren yarinyar Nan na kusa yake tunda yace min Malam Bukar ne yayi binciken Dan haka bazai cewa kowa komai ba har sai bayan daura auren tukunna".
"Ya fad'a Miki waye mijin?"
Kai ta girgaiza Mata alamar A'a.
Nifa Ina gudun garin AUREN HUCE HAUSHI a kwaso bara gurbi Wanda za'azo ana Mana dariya".
"Gaskiya bana tunanin haka Inna mu bita da addu'a kawai Allah ya Zama gatanta yasa albarka a ciki.
AUREN HUCE HAUSHI
Story & written
MAMAN FATIMAH.
INA MIQA SAKON TA'AZIYYATA GA 'YAN UWANA
HAJIYA MARIYA ALIYU ( JIMMAN ADO)
HAJIYA BILKISU ALIYU (UMMA IKKI)
HABIBA ALIYU (UMMA HABIBA)
Na rasuwar mahaifinsu ALHAJI ALI DAN HAYA MAGAMA KAZAURE.
Allah ya jikansa ya jaddadda Rahama a gareshi tare da sauran musulmi.
Page three
.............. Tunda Mahmud ya fito daga gurin Baba Malam yake nazarin yanda zai bullowa lamarin, baya son ko kadan a Sami kurkure, guri ya Sami nesa da makarantar kasancewar Alhamis ce Yara basa karatun safe sai ya zamana yawancin su suna dakunan su.
Waya ya Ciro daga aljihun wandonsa yayi dialing din number Bata jima tana ringing ba kada daga magana ya Fara "kana jina Sameer sakon Dana turo maka kada a samu kuskure kayi kokarin ganin komai yayi yanda ya kamata fa".
Dan Jim yayi alamun ana fad'a Masa wani abu
"Ok to shi kenan take care".
Ya kashe wayar.
Nama ne da kayan miya ake ta shigo dasu cikin gidan da manyan kuloli sabbi Hajiya mama ce a kofar kitchen din na tsakar gida tana bada umarnin abinda za'ayi, yaran dake shigo da kayan ta kalla "wannan fa daga Ina?".
Magaji ne ya Bata amsa kafin yaron data tambaya ya fad'a Mata "tare muke Mama na abincin bakin Abba ne".
"Ikon Allah Naga ai an kawo wasu da sassafe dazu gasu nan har an kusa Gama aikinsu".
"Eh to shi dai yace a kawo wadannan ma".
Magajin ya fad'a Yana shiga dakin Amma.
"Kai dawa Kuma kake tafiya kana magana"
Cewar Inna maimuna.
Kusa da ita ya zauna Yana fadin "nida Hajiya mama ne kayan miya ne da Naman rago Dana kaji Abba ya Kara badawa aka kawo shine take magana ko yayi yawa kame?"
Dan murmushi Amma tayi "Abban Nan naku baya son a zauna lafiya wallahi magaji kamar zai aurar da Yara uku sai irin wannan shidima yake haka".
Kai magajin ya jinjina "Amma kenan kin manta yanda Abba keson Zahra ai kawai kowa ya zuba Ido ana auren uwar masu gida tab ai kowa sai yasan anayi Yasin, ki Bari kawai Ammah Nan zan kawo nama a ajiye min".
Ya fad'a Yana dariya ya nufi kofar fita saboda sallamar wasu Mata da yaji a kofar dakin.
Daki Mahmud ya koma ya samu Habib a tsaye a tsakar dakin da alama daga wanka ya fito, saida ya Gama wayar sannan ya kalli Mahmud.
"Wai ina kaje ne? Naga fitowarka daga gurin Baba Malam kafin na saka caji na nemeka na rasa, Bilya ne ya kirani Wai mu sameshi a hayin Banki shi Yana can yaje da masu aiki su duba yanda za'ay
i gyaran"
Dan Dafe Kai Mahmud yayi ya Dan fesar da numfashi.
"Ikon Allah Wai Daman kamar jira kuke ace za'ayi min auren Nan kowa sai rawar jiki yake yi, daga fad'a shine har ya want kwashi jiki da masu aiki ya tafi tun garin Bai Gama watstsakewa ba".
"Naka wasa ne Alaji, aini yanzu haka mun Gama magana dasu Bashir sunce mun gasu Nan zuwa har suna cewa shegen zurfin ciki ne da Kai baka fad'a musu ba jiya ko kunya kakeji irin ta Mata".
Ya karasa maganar Yana dariya.
Har ya nufi gurin mirror ya tsaya "kaji na manta ba Salis yace na tura Masa cikakken sunan da ze saka a IV da zeyi a waya ya turawa friends na kusa".
"Ok ba matsala ka tura Masa kawai da sunan aika Sani ba saina maimaita make ba".
Misalin karfe Sha daya na safe wata bakar Hilux sabuwa kar ta dira a kofar gidan Malam Bukar.
Lokacin yaran sun firfito suna sugogin su masu wanki nayi masu wasa nayi Amma idan ba fada maka akayi bazaka taba cewa yaran Almajirai bane kowa cikin tsabta Kuma a lokacin anyi hutun makarantar book shi yasa basayi tunda suma tsarin makarantar gwamnati suke bi.
Mutane biyu be suka fito daga motar da sauri 'yan samarin dake kusa taso da sauri suna fadin barkan ki da zuwa kasancewar sun saba dasu sosai sune wadanda suke kawo musu tallafi daga organization din.
Da sauri suka bude musu falon saukar bakin Malam kafin wani ya shiga ya fadawa Malam din.
Ba jimawa Malam din ya fito suka gaisa a mutunce, sannan suka gabarwa da kayan abincin da suka kawo sannan suka gabatar Masa da bukatar daukar Mahmud zuwa wani taron karawa juna Sani na makarantun tsangaya Wanda za'ayi a kano, tunda shine Wanda suka dauka aiki a Nan tsangayar yake wakiltar su kuma gobe juma'a za'ayi taron na Rana daya ne kawai.
Dan Jim malam din yayi kafin yace " Ikon Allah malam Sameeru ga koshi ga kwanan yunwa WALLAHI shi Mahmudan dai baze Sami damar halartar taron nan naku ba, domin a goben in Sha Allah za'a daura Masa Aure".
Cikin wani irin madaukakin mamaki Sameer dake kusa da Malam din Kuma jagaban tafiyar ya kalli Malam Yana cewa.
"Aure! Kuma Malam?".
Kai ya jinjina Masa alamar tabbatarwa, "yanzu haka suna can gidan da ze zauna ana dudduba gyaran da za'a Masa duk da gidan Bai jima da kammaluwa ba kasan kullum abin duniya sabuntashi akeyi".
Kai ya jinjina ya hadiye wani yawu da kyar shifa duk ya shiga rudu meye hakan Wai Kuma.
Fara'ar dole Sameer ya kirkiro Yana kallon Malam yana fadar "Masha Allah Abu yayi Dadi to ai mu wannan lamarin namu ne munzo a dai dai kenan tunda Abu ne na ma'aikacin mu koma kunya zatayi Masa malam kada kuyi komai yanzu zanyi waya za'ayi duk abinda ya kamata tun daga abinda ango ze saka har abinda za'aci duk Yana karkashin kularmu tunda mu yakewa aiki, Kuma zamu zauna sai an daura auren damu in Sha Allah. Maganar taron Kuma sai dai a daga zuwa wani lokacin Dan bamaso wani yayi missing gaskiya".
Tunda Sameer ya Fara Kora bayani malam ke jinjina Kai saida yake Aya sannan ya Sami zarafin magana.
"To malam sameeru anyi haka abin fa da yawa kids bakuzo da Shirin wannan abun ba kunzo Kuma kuyi ya kuyi makarbiya ai da wahala abun".
Dariya Sameer din yayi Yana fadar "malam ba abunda ze gagara kungiyoyin masu karfi ne, yanzu ma ga wannan saboda biyan sadaki".
Ya aje Masa cheque na Banki suka Mike Yana fadar "Bari na Nemo shi a waya sai muje muji meye shirye-shiryen nasu, a huta lfy".
Suka kad'a suka fita.
_____
Kyakykyawan guri ne Aunty Hasana ta kama inda za'ayi mother's day din gurin ya kayatu ba karya kudi dai an kashe su gurin Kama event center din, anyi taron Mata 'yan gayu kamar ba gobe amarya tasha kyau kamar a dauke ba boye.
Ga wani slow music da mc din ya saka na wakar Amarya da ango kowa ka gani cikin nishadi yake sabanin Amarya da Yayarta Banda ta Riga ta gayyato mutane harda wadanda sukayo Mata tafiyayya sukazo da ba abinda ze saka tayi wannan taron to Amma mutum Bai Tara Sani ga Allah ba.
An raba kayayyaki na alfarma na bikin, sai magariba taron ya tashi, zuwa yanzu 'yan Qananan maganganu sun Fara fita a tsakanin kawayen Zahra tunda har zuwa lokacin ba wani duriyar Ango ko wani nasa, sai Dan kus-kus ake abinda yafi bada mamaki bai wuce ganin anata faman programs ba normal.
Su Mahmud Basu samu kansu ban sai bayan sallar insha'i lokacin suka zauna Dan wuni guda suna ta faman sunturi daga can zuwa can abin dai ba sauki dan su sameer suna zuwa gidan suka babbago aikin da sai anyi sati ba'a Gama ba Dan sunce tsarin gidan gaba daya za'a sake, basunda ta cewa tunda oganninsu ne sai godiya suka dunga zubawa harda su Bashir.
Gurin karfe goma malam ya Kira Mahmud a waya yace yazo cikin gida ya same shi.
Saida ya leka falon iya Abu suka gaisa tana faman jansa tana ita ce ta karfen Dan haka ita zata koma sabon gidan a kawo Amarya nan.
Da haka ya karasa turakar malam Yana zaune a falo Yana sauraren wa'azi a TV, yayi sallama Malam din ya bashi izinin shiga, Nan kasa ya zauna Yana gaishe da malam din.Wasu manyan ledoji malam din ya nunawa Mahmd Yana fadin.
"Dauko wadan can kayan ka duba daya Wanda nasa a kawo maka ne biyun Kuma wadannan masu kungiyar ne ta taimakon tsangayu suka kawo ga lemuka can da ruwan roba sun kawo yafi catoon dari sunce kada ayi abinci ma duk za'a kawo, har na rasa da wane bakin zan gode musu, sai dai Ina rokon Ubangiji s.w.w yafi mu yabawa, naji su Habibu ma sun ce sun dauko aiki Mai yawa a wancan gidan ko?"
"Eh wallahi munyi-munyi su Bari suka Kiya Wai haka aikin Qungiyar yake in dai kana musu aiki idan wani Abu ya sameka Mai Dadi ko marar dadi su zasu tsaya maka".
"Alhaji yace min kun shiga dazu bayan sallar magariba har da bakin kunyi Masa godiya, kun kyauta haka ake so".
Lokacin Mahmud ya koma dakinsu Habib baya Nan gurin da yake aje makullin lifan dinsa ya duba ya kuwa you sa'a yana nan, lodojin ya zube a kan gado ya dauki makullin ya rufe dakin ya hau mashin din yayi gaba.
Bai dawo ba sai kusan Sha biyu da rabi har lokacin kuma Habib baya dakin yasan suna can suna kujuba kujuba.
Yauma Zahra taso kwana a dakin Aunty Hasana saboda tana bukatar kadaicewa Amma Sajida ta matsa Mata da mita Saida suka tafi Amma fa zuciyarta Bata da nutsuwa gashi tana ankare da Aunty Hasana tun jiya da dare a taje can gida cikin gari Bata da nutsuwa ko alama Amma tana ta kokarin ta basar sai dai ko Yaya mutum ya shiga damuwa indai kayi Masa farin Sani zaka fahimta, ita Abu mafi Bata mamaki yanda aketa kwaramniyar bikin ba wani canji sai dai abunda baza'a rasa ba duk da Daman ba wata muguwar bidi'a ba ta had'a, walima ce kawai Bata Sami ba saboda tace ita malam Tijjani Ahmad zeyi Mata Kuma bayanan yana Umara.
Tunda tayi sallah ta kasa tashi daga gurin tana kallon su Sajida sunata sabgarsu, Amma ita da wata irin faduwar gaba ta tashi ta rasa nutsuwarta kwata kwata da kyar ta tsahi sauko kasa gurin Aunty Hasana a fall ta sameta tana hadawa Abbansu Haidar break fast.
Gurin dining din ta karasa tana gaishe shi sannan gaida Auntyn.
Dakin Auntyn ta shiga kwanciya tayi tana ta faman sakawa da kwancewa zuwa yanzu dai tasan tabbas da matsala sai dai yanda ba Wanda ya fad'a Mata shi yasa itama ta zubawa sarautar Allah Ido taga iya karshen film din tasan ko menene yau dai za'a yita ta Kare tunda yau ne deadline duk wata kunbiya kunbiya za'a zazzageta.
Tun karfe goma Mai yiwa Amarya make up tazo Amma kememe Zahra tace ita bataso a kyaleta aka dunga yiwa kawayenta, ganin guri ze kure ne Sajida take ta fadawa Aunty Hasana Saida tazo sannan akayi Mata light makeup Amma fa duk da hakan tayi karshen kyau, farin material ne ta sakata Mai touching din sky blue sai aka daura Mata head shima sky blue din takalman da pos din duk sky blue din ne.
Wani san sanyan kyau tayi na ban mamaki, komai na Zahra Mai kyau lallai zaharar ce Dan duk cikin kawayen Bata da mahad'i.
A babban masallacin juma'a za'a daura auren Masha Allah, ango ya fito Shar abokansa sai mamakinsa suke Basu taba sanin kyawunsa da cikar haibarsa ya Kai haka ba sai daya fito sun Sha mamakin kwarai har wasu suka Fara kokonto a kansa, Yana kallon yanda idanun sukayi Masa caa.
Dan dakakkiyar getzener ta saka ga takalman da agogo ga hula, Sam bazaka taba cewa Wai alamajirin malam bane ba, ga wani irin kamshin tunda ta tumkaro taron abokanensa kamshin ya hade gurin.
Daga gefe sameer ne da abokinsa Naraddeen suna tsaye lokacin da Mahmud ya fito Sameer ya kalli Naraddeen din yace "wallahi wannan guy kwallon Dan duniya ne na rasa Gane kan alkiblar daya kalla Wai aure zai daura shi kadai kamar marara gata, ni so nake Naga karshen wannan wasan kwaikwayon nasa.
Daga inda yake tsaye ya kafe Sameer da Ido ko Bai fad'a ba yasan me yake nufi tun jiya yake tuhumarsa aka zuwa da abokinsa da yayi duk da ya nuna Masa wannan ba wata matsala bace Amma har yanzu Yana hukunta shida idanunsa.
Masha Allah dubban mutane ne suka shaida daurin Auren FATIMAH ZAHRA AHMAD SANI da Angonta MAHMUD MUHAMMAD DANGE akan sadaki dubu dari uku lakadan ba ajalan ba.
Daurin aure daya bawa dubun mutane mamaki bare wadanda sukazo daga bangaren Mushahu sunyi mamaki kwarai sunan Amarya dai shine Amma ba mijin daya gayyato su bane yayin da yan unguwa ya Zama abin kasawa a faifai ana yawo dashi, da yawa na ganin beken Alhaji Jafar na aurawa bakon da ba'asan asalinsa ba yarinya kamar Zahra yayin da wasu ke fadar ai Dan ba 'yarsa bace shi yasa yayin wannan danyan aikin.
.......
AUREN HUCE HAUSHI
Page four
___________''
Wata marokiya ce irin dattawan Nan da suke bin manyan marok'a ta biyo tawagar masu dawowa zuwa gida kasancewar gidan ba nisa daga masallacin juma'ar, itace ta rangad'a guda har sau uku ta Kara da fadin "Alkawarin Allah ya tabbata an daura auren Fatima Zahara'u da zukeken Angonta Mahmud Ubangiji Allah ya bada zaman lafiya da kazantar daki Bata shara ba, munzo much arziki mubar arziki a gurinsa.
Kamar saukar aradu haka maganar ta shiga kunnen Hajiya mama, batasan lokacin data tsallake mutanen falonta ta fito ba dankwalinta a hannu, tana fadin "me naji ana fad'a wa aka daurawa aure da Mahmud naji kowa".
"Eh haka ne Kam Alkawarin Allah ya ciki Zahara'u ta Zama matar Mahamuda"
Ta debo wata gudar ta Kara rabsawa.
Dai dai lokacin Hajiya kaltume aminiyar Ammah ta fito ta dukulawa wannan marokiyar kudi sannan ta Mika Mata babbar leda Mai abincin biki har da ruwa da lemo.
Cikin rashin nutsuwa Hajiya mama ta nufi dakin Amma ko sallama Babu ta Fara fadar "Hajiya kinji abinda naji ko kunnena ne ya jiyo min ba dai dai ba?".
Kallonta duk 'yan dakin suke kafin Ammar tace Mata "nima haka naji kamar yanda kikaji sai dai ko shirme takeyi ita Mai rokon tunda ba sanin su tayi ba".
"Eh gaskiya Kam sai dai hakan".
Ta juya ta koma daki. Bata zauna a falon ba uwar daki ta wuce, Asabe ce ta rufa Mata baya, a tsaye ta sameta ta Goya hannu a baya tana Dan Kai kawo a tsakanin gado da madubi.
Waiwayowa tayi tana kallon Asaben kafin ta zauna a bakin gado, kusa da ita Asaben itama ta zauna.
Tana fadar "Haba Hajiya Dan Allah ki nutsu bana son ki bada wata baraka a sabgar Nan keda na fad'a Miki Daman malam na BANDE yace wannan karon aure sai anyi Amma ba da Mushahun ba, Amma abinda yake daure min Kai malam na banden yace Wanda zata aura a nesa yake Kuma yaga haske so sai akan lamarin duk yanda yaso ya Bata lamarin abin Bai yuwu ba shine nace kawai a kyale tunda dai Wanda muke son a fasa da shin din aikin ya yuwu, nasan dai da wuya ta Sami irin Wanda ta rasa a bay".
"Haka ne Amma abin dubawar waye wannan din sanan me yasa aka kudundune zance? Wai fa Dan munafurci Hajiya Asma'u cewa tayi Bata Sani ba ke kin yarda Alhaji ze aurar da Zahra Bata da masaniya, ko meye ma dai kyawaun ya kare a auren Hadi tunda nasan ba wani sai Mushahun shi Kuma ya Kara gaba kamar sauran".
Ta fad'a tana kwafa, mikewa tayi tana gafar "Bari na fita sai Naga kul uwar daka".
"Allah ya taimaki uwar dakina, aikinki Yana kyau".
Asabe ta fad'a tana mikewa itama.
**********
Daga gurin daurin aure Kai tsaye gidan gonar Alhaji Jafar suka wuce har tawagar angon bisa umarnin Alhajin tun safe ya turo Mai sunasa (magaji) yaje ya fadawa Baba malam.
Anci an Sha kamar ba gobe mutane sunyi mamakin irin wannan karamar arzikin dan duk zarin mutum sai dai yaci ya Bari ruwa da lemo kuwa kamar banza.
Abokan Mahmud kuwa sai Dan biki suke Masa.
A gidan malam ma Masha Allah anci an Sha Yara sun san ana biki a gidansu, Iya Abu ma tayi nata taron komai baja baja makotanta ma sunsan ana hidimar arzki a gidan Kuma Suma sunzo Mata harda masu riko abin arzikinsu su kawo Mata.
******** A guje Faruq ya Fado falon Aunty Hasana,danta ne na uku Yana rungume da babbar rigarsa ta daurin aure daya saka Yana Fadi "Aunty Zahra wallahi Naga mijinki ba wannan Uncle din bane na kano wallahi wanna yafi shi kyau Baki gani ba yanda yake rabawa marok'a kudi ba, Kuma Dan gayu ne sosai Naga Uncle Abdul Hakeem ma ya rugume shi Yana ta dariya, Dana tambayi Auncle Imam yace min sunansa uncle Mahmud".
Tunda ya shigo Yana karadin Nan ta zuba masa Ido tana sauraren abinda yake fad'a, kana ganinsa kasan har zuciyarsa abinda yake fad'a din gaskiya ne, wani irin gingirin taji kanta yayi mata, nan ta sulale ta kwanta kan kujerar ta saka hannunta ta rufe fuskarta wasu hawaye na zubo Mata masu zafi.
Sajida da Amatu suka nufi gurin Faruq din suna neman Karin bayani.
Yayin da wasu da yawa suke ta sabgar ciye ciyensu Dan Suma Kam an kawo koma enough.
Kamar yanda ya fad'a haka Suma ya mayar musu Dan su harda Karin bayanin yayi musu kasancewarsa Mai surutun tsiya.
A hankali Sajida ta kamo hannun Zahra Dan Bata fatan wani daga cikin bakinsu su fuskanci an samu matsala gaskiya, kamar masu you shawara suka shiga dakin Auntyn saboda Nan ne baza'a shigo ba.
Bakin gadon ta zaunar da Zahra ita Kuma ta janyo stool ta zauna har lokacin Bata saki hannunta ba,tana Jin yanda ilahirin jikinta yake rawa.
Hannun ta Kara jimkewa cikin nata tana fadar.
"Cool down Mana bestie haba take it easy, kada ki tada hankalinki Taya Zaki kama maganar faruq kinsan dai ba wani hankali ya Gama Masa jiki ba".
Kai ta shiga girgizawa cikin muryar Kuka tace.
"Wallahi Saji akwai matsala kema Kuma kin sani sai dai kik'i fad'a idan ba matsala Ina su Maryam da mukayi dasu zasu zo tun kwana ukunda suka wuce Ina shi kanshi uban gayyar ina su Deeni dasu Aliyu, kowa ka Kira sai dai kaji switch off baka haka ba".
Ta fad'a tana fashewa da wani irin Kika.mai taba zuciya.
"Kiyi shiru Dan Allah kada ki janyo hankalin mutane Mana kinga ga Amatu can zataji dasu ki nutsu har muji meye gaskiyar maganar Mana".
"Ki barni nayi kuka wallahi na gaji nikenan kullum matsala daga wannan sai waccan na rasa a Ina matsalar take ni wallahi bana son kowa ma a kyakeni haka Nan bana son auren, bana so wallahi ni nagaji Allah Jordan zan tafi bazan zauna ba, bazan Kara Zama a kasar nan ba".
Ta fusge hannunta daga na Sajida ta yunkura ta tashi ita dai Sajida Bata San ta Yaya akayi ba sai ganin Zahra tayi ta kifa kan gadon tana wata irin fuzga da gudu ta karasa kusa da ita tana jijjigata tana fashewa da kuka tana fadin "ki tashi Dan Allah wayyo Allah na".
Baba Tabawa ce ta bude kofar ta shigo, Dan tunda tana kusa dasu Faruq ya shigo da wannan maganar duk da tasani Dan Aunty Hasana Bata rufe Mata komai ba ta fad'a Mata tun jiya, shi yasa data ga sun nufo dakin hankalinta ya kasa kwanciya ta biyo su tasan koya Sajida zatayi Mata kalamai ba kamar ita ba tunda abinda babba ya hango yaro koya hau iccen rimi bazai gano ba.
Turus tayi tana kallon Sajida dake Kuka bil hakki tan jijjiga Zahrar.
Da sauri ta karaso tana fadar "ke 'yan Nan menene haka?".
Hawaye jage-jage Sajida ta dago tana fadar "wlh Baba Tabawa kawai tana kuka tana maganganu tana tashi kawai sai Naga ta yanke jiki ta Fadi?.
Wani ruwa Baba Tabawar ta dauko a kan bedside fregde din Nan ta zubawa Zahrar a fuska Amma shiru ta Kara watsa Mata Nan ma shiru cikin tashin hankali ta lalubo Yar wayarta rakani toilet ta mikawa Sajida "ungo maza Kira min Aunty zakiga an saka Maman Ali yi sauri".
Bugu biyu Auntyn ta dauka tare da sallama, gani Sajida ta rasa me zatace ne yasa ta mikawa Baba Tabawa wayar.
Can Kuma tana ta faman" hello Baba"
Abinda taji kenan lokacin data Kara wayar a kunne cikin sauri Baba tace "yi sauri ki turo a Kai Zahara'u asibiti wallahi gata Nan a suma min yayyafa ruwa a banza".
Bata jira taji me za'a fad'a ba ta kashe wayar.
Abdul Hakeem Aunty Hasana ta lalubo a waya lokacin suna tsaye shi da Mahmud suna magana wayar Abdul Hakeem dince ta Fara ringing Sunan Aunty Hasana ya gani ya daga har zai Fara Mata abunda ya saba ta tsayar dashi tana fadin "Dan Allah maza kaje gidana ka dauko Zahra ku wuce asibiti mu hadu a can wai Suma tayi"
Kit ta kashe wayar.
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un yake ta Nanatawa da sauri Mahmud ya tambaye shi "lafiya meya faru".
"Bari kawai ba komai Ina zuwa yayi gaba da sauri jikinsa har rawa yake Yana tafe Yana laluben key din motarsa. Da sauri Mahmud ya biyo bayansa' Sam baiji key din ba sai daga baya ya tuna tana hannun mustapha yaje gari ya dawo.
Tsaki yayi daidai lokaci da Mahmud din ya karaso Yana fadar"Dan Allah Wai menene Naga duk a rude".
"Bari kawai Wai Zahra ce ba lfy zan kaita ASIBITI".
Kallon yayiwa Abdul Hakeem din kafin yace "shine Kuma zakaqi fad'a min".
Hannu yasa ya yafito Sameer, cikin bada umarni yace
"Dauko motar can kuje da Abdul zaku Kai madam asibiti". Ya juya ya koma gurin su Habib.
Har sukaje gidan Auntyn Abdul Hakeem Bai daina mamakin Mahmud ba, yanayin yanda yayi maganar kawai kasan da abinda ya taka umarni fa ya bada, su dai a zahiri ai Sameer ne uban gidan Mahmud tunda kowa yasan aikin NGO's ya kawo shi garin har suka hadu da Mahmud din suka dauke shi yake musu aiki a sauran makarantun tsangayun na cikin gari Dana kauye.
Da sauri Abdul Hakeem din shiga gidan Auntyn ta kofar baya gurin kitchen ya shiga koridon dakunan barcinta.
A tsaye cirko cirko ya samu su Baba Tabawar har lokacin numfashinta Bai dawo ba.
Da sauri ya karasa gaban gadon yasa hannu ya dauketa kamar wata Baby yayi waje da ita. Sajida da Baba Suka rufa Masa baya.
Da sauri Sameer ya bude Masa seat din baya ya sakata Sajida ta shiga ita da Baba shima Abdul Hakeem ya shiga gaba da gudu Sameer ya fizgi motar. Saida ya daidaita a titin sannan ya kalli Abdul Hakeem din "ina muka nufa?".
"F.M.C zamuje tunda yafi kusa".
Nan da Nan aba karbeta likitoci suka rufu a kanta, suna Nan tsaye Aunty Hasana tazo ita da Inna maimuna sai Hajiya kaltume.
Suma tsayawa sukayi a gurin Baba Tabawa tana maida musu yanda akayi ita dai Sajida ba baka sai sharar hawaye take.
Su Abdul Hakeem suna suna gefe daga zuwansu Mahmud ya Kira akai sau biyar idan ya Kira Sameer sai ya Kira Abdul Hakeem, daga Jon yanayinsa kasan Yana cikin damuwa abinda ya Kara daure Abdul Hakeem Kai yandq Sameer yake amsa wayar Mahmud cikin kulawa da bada girma.
Sun dauki a kalla minti arba'in kafin babban likitan ya fito sannan sauran Suma suka fito.
Su Abdul Hakeem sun bin bayan likitan kamar yanda ya bukata Amma ganin an gungoro Zahrar a gadon daukar marasa lafiya yasa suka nufe ta da sauri suda su Aunty Hasana.
Wanda ya turo gadon ne yace "ai ta farfado ba wata matsala ana so ne dai ta samu hutu sosai jininta ne yaso Hawa Amma cikin ikon Allah anyi controlling dinsa".
"Oh no 'yasu Allah ka dubi lamarin wannan 'yar maraiya duk da Bata tashi da rashin gata ba sai yanzu ka kawo Mata Tata jarabawar Allah ka shiga cikin lamarinta".
Aunty Hasana ta fad'a itama tana goge hawaye.
Baba Tabawa dasu Sajida suka amsa da "ameen ya Rabbi"
Dakin 'yan da'i da'a aka kaita tunda tana bukatar isolation.
Saida komai ya Zama dai dai an saka Mata drip sannansu Sameer sukaje gurin likitan. Fad'a yayi so sai akan yanda akayi har karamar yarinya kamar wannan damuwa tayi Mata yawa har har take barazana ga lafiyar ta.
A can gidan biki Kuma Amma ta rasa inda su Hasana da Inna suka tafi Dan hankalinta Bai kawo Mata Hajiya kaltume ma Bata Nan ba sai da abokiyar zamanta tazo sannna ta fuskanci itama Bata Nan din wayarta ta dauko ta Kira Hasana, lokacin tana zaune gaban gadon da aka kwantar da Zahrar.
Sunan Ammah ta gani sai lokacin ta tuna Ashe Bata fad'a Mata ba.
" Assalamu Alaikum Ammah".
"Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, wai Ina Kika tafi ne babu ke Inna maimuna ma Bata Nan Hajiya kaltume ma banganta ba".
Dan Jim tayi har Saida Ammah tace "kina jina?"
"Eh inaji Ammah duk muna tare dasu, muna Nan gurin Zahra Bata Jin dadi ne Amman da sauki yan haka barci take".
"Wane irin zance ne wannan kamar Bata Jin dadi Kinga Hasana fadi min gaskiya yanzu kina Ina?".
" Muna F.M.C wlh jikin da sauki sosai kawai sunce ana dai San ta huta ne, kada ki tada hankalin Dan Allah".
"To Allah ya kyau Amma Ina hankali ze kwanta".
Waje Aunty Hasanar ta fito gurin su Baba tabawa da sajida tace
"Baba tabawa Dan Allah kuje gida da sajida tasan inda aka aje abubuwan da zasu bawa kawayensu tunda yau zasu wuce sai ki fad'a musu tana gida gurin Abba, ta kalli Sajida ke Kuma duk tmbayar da saying Miki kice Baki Sani ba mu barsu a haka".
Kudi ta mikawa Baba tabawan sannan ta karasa gurinsu Inna maimuna da Hajiya kaltume, Suma bayi tayi musu na Kiran Ammah tace suje gidan Dan hankalinta ya kwanta.
*********
Da kyar Amma ta Bari akayi sallar magariba ta shiga bangaren Alhaji Jafar ta same shi da Hassan da Abdul Hakeem suna magana akan Zahra Hassan Yana ta mitar meyasa Abban yayi haka ai da hakuri kawai akayi har lokacin da Allah ze kawo Mata wani.
Dan murmushinsu na manya yayi Yana "fadin wannan ma in Sha Allah Babu Dana Sani a cikinsa ni nasan nagartar Dana gani tare da yaron yasa na bashi, Kuma ko bayan Raina zakuce na fad'a muku".
Jiki ba kwari Amma ta gaishe da Alhajin tana Masa ban gajiya tare da godiya.
Sannan ta Dora da fadin "Dan Allah ko zaka Bari naje Naga jikin nata?"
Tsai yayi Yana kallon ta "da kinyi hakurin zuwa Suma da anjima zasu taho gida yanzu ma daga cen muke ko zuwan mu Bai isar ba?"
Cikin Jin nauyinsa tace "A'a ya badatar"
Ta tashi ta nufi kofa da kallo Abban ya bita ita kanta tausayi take sashi da gani zuciyar ta ba Dadi.
Da sallama suka shiga dakin lokacin Aunty Hasana tana sallar insha'i ita Kuma zahra farkawarta kenan tana kokarin tantance Wai inane ma Nan din inda ta gani idan dai ba gizo idanunta ke Mata ba kamar asibiti.
Sallamar ce ta katse Mata tunani ta Dan dago kanta kadan sukayi arba dashi Ido cikin Ido da sauri ta runtse idanunta zuciyar ta na wata irin bugawa tana ambaton Allah a zuciyar ta, meya kawo wannan dodon nata gurinta, Kara rufe idanun tayi it fa wallahi zata iya rantsewa Allah duk duniya ba idanun da suke figitata kamar nasa.
AUREN HUCE HAUSHI
Strory
&
Written
By
MAMAN FATIMAH

Page five

_______ Shiru dakin ya dauka har zawan lokacin da Aunty Hasana ta idar da sallar.
Dan juyowa tayi kadan tana fadin "wa'alaikumus Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, sannunku da zuwa Bismillah ga kujeru nan ku zauna".
"To mun gode Aunty" Sameer ya fada.
Cikin ladabi da mutuntawa suka gaishe ta tare da tambayar Mai jikin, ta amsa musu da sauki, sai kuma dakin ya Kara daukar shuru Zahra dai tunda ta rufe ido Bata Kara gigin budewa ba, ita ji take duk ya cika dakin ita tun ganinta na farko dashi a duniya ya birkita Mata lissafi, Kuma saboda Allah meya kawo shi gurinta asibiti duk da tasan mutumin Ya Abdul Hakeem ne Amma sai taga kamar ba sai yayi Masa Kara ba, ko Kuma yazo wata sagbar ne asibitni ya Sami labarin shine ya shigo ya dubata.
Magaji ne ya shigo dakin da sallama sai Kuma ya Dan tsaya baiyi tunanin ganinsa ba Sam da fara'a ya karaso Yana fadin "Ashe Kuna Nan ai tare muke da Ya Abdul Hakeem ma".
"Ok" abinda Mahmud ya fad'a kenan
Shi Kuma Magajin ya karasa gurin Auntyn Yana gaishe ta.
Abdul Hakeem ne ya shigo Yana rike da wayarsa a hannu da sauri ya karasa gurinsu Mahmud din Yana fadin "A'a angon ne da kansa" Yana Mika masa hannu.
Saroro Aunty Hasana tayi ita wace iri ce kawai dai taga sun shigo sun gaisa wallahi Sam Bata kawo ba ita da akace Mata Alamajirin Baba malam ne ai ta dauka irin wannan gaddawan ne, yo ta Ina wadannan sukayi wani Kama da kolaye ai ita zallar ilimi ta gano da wayewa a tattare dasu.
Hanyar wajen ta nufa tana janye da hannun magaji duk sai taji kunya ta kamata Ashe sukanta ne.
Ita kuwa Mai gayya Mai aikin ai tana jin an ambaci ango ta bude idonta girjinta Yana wata irin dokawa "ango a nan to waye a tsakaninsu da suka shigo tare?
Abdul Hakeem ne ya kalli gurin gadon Yana fadi.
"Masha Allah! Ashe kin tashi, ya jikin?"
Ya fad'a Yana karasawa jikin garon Sameer ma Dan matsawa yayi Yana dubata Kai kawai ta gyada musu, tana kallon Ya Abdul Hakeem din, kallo irin na neman Karin bayani.
Yi yayi kamar Bai Gane ba ya juya yana yiwa Sameer magana suka fita.
Har suka fice Bai dago ba Yana ta faman tab'a waya sai da ya Mula Dan kan shi sannan ya tashi ya tunkari gadon.
"Ya jikin?"
Ya fad'a Kai tsaye, Bai Kuma jira ta amsa ba Dan ko kwakwkwaran motsi ta kasa sai tunanin da yake Mata Kai komo.
"Badai wannan bane ake nufin an daura min auren dashi Amman da Naga ta kaina".
Shine ya katse tunaninta.
"Ki kwantar da hankalinki ki daina saka damuwa a ranki da kannan shekarunki, ki kuma dagawa Ammah
nata hankalin, idan nine bakya so ba damuwa Nima kusan hakan take. Amma kada mu watsawa iyayen mu kasa a ido Mana tun yanzu gara ki nutsu ki kwantar da hankalinki daga baya sai a duba Mai yuwuwa tunda nasan bazaki so Zama da almajiri marar karatun boko mai zurfi, ga karqncin wayewa ga rashin madafa ta yau da kullum, Nima kasada ce tasa na yarda da tayin da akayi min tunda Naga nema ake a tozarta min da iyayen a kunyata su a idon duniya aci mutuncin su".
Ita da'i ko motsin kirki ta kasa da gaske gani take duk ya cika dakin, ga wani fitinan kamshinsa duk ya cika Mata hanci.
A bazato taji ya Dan shafi gefen fuskarta idan ba kunnenta ne suka jiyo Mata ba da'i dai ba sai taji kamar yace "my previous" a hankali sannan ya Mike Yana fadin "Bari a kawo maganin ki saimu wuce gida tunda doctor yace zamu iya wucewa, Amman yace ki rage yawan tunani Yana haddasa cututtuka".
Har dakin Amma Abdul Hakeem ya raka Zahra lokacin duk yawancin bakin sun tafi sai 'yan uwan Amma na Mubi Dana Jimeta sai Kuma Aunty Hasana da take dakon dawowar su, ai tunda magaji ya Kara Kora Mata bayani akan Mahmud ta tafi daga asibitin tunda Mai dungurungum din yazo ita bataga ta Zama ba.
Saida ta matsawa Zahrar tayi wanka Tasha tea da magungunan ta kwanta sannan tayi haramar wucewa gida.
Sai wurin karfe Tara sannan Hajiya mama ta shigo dakin tana fadin "wallahi daga idar da sallar ta barci ya dakeni sai Dana tashi zilai Mai wanke wanke take fad'a min an dawo da Zahra har sun shigo sun duba ta".
"Wallahi kuwa ai jiki da sauki yanzu Tasha magani ta kwanta"
"To Allah ya Kara lfy, Wai Hajiya wanene mijin yarinyar Nan ne naji ana fadar Wai cikin Almajiran baba Malam ne, shine nace haba yaushe Alhaji zeyi wannan danyen aikin ya rasa bazai bawa aure Sai a cikin Almajirai".
Inna maimuna ce tace "ai mu Hajiya ko waye Alhaji Jafar ya aurawa Fatima wallahi mun karba da hannu biyu mun gode tunda mun San har abada Babu cutarwa a tsakanin Asama'u da dashi da ita Fatiman da abinda ya Haifa bamu taba ganin banbanci ba, Dan haka mun karba da kyakykyawan niyyarsa Allah ta tabbatar Mana da Alkhairi".
Gaba daya suka amas "Amin"
Hajiya mamar ta Dan jima a dakin kafin ta koma dakinta.
Bayan Zahra tayi sallar Asuba ta gama Azkar dinta komawa tayi ta kwanta har lokacin kanta Yana Mata ciwo kadan kadan, sai gurin takwas da rabi Inna maimuna ta tasheta tana fad'a Mata tayi maza ta kimtsa Abbansu Yana nemanta.
A gurguje tayi wankan ta fito lokacin an kawo Mata kunun gyada da fanke, kunun gyadar kawai tadan Sha kadan ta shafa lotion dinta ta saka doguwar rigar atamfa ko dankwalin Bata daura ba ta fito cikin takunta na nutsuwa Wanda da yawa mutane ke gani a matsayin yanga da jiji da Kai.
A tsakar gidan suka rinka gaisawa da tsirarun yan uwansu na Mubi da sauran ma'aikatan gidan Mata.
Da sallama a bakinta ta shiga falon Abban nasu, tayi mamakin ganin kusan duk 'ya'yan Abban suna Nan sai su Ammah da Inna maimuna da kanwar Abban Maman lafia.
"Zo nan kusa dani Uwata".
Abban ya fad'a Yana murmushi, itama murmushin tayi ta karasa kusa dashi ta zauna nata fadar "Abbana Ina kwana?".
"Lafiya kalau Alhamdulillahi Uwata".
Sannan ta juya tana gaishe da jama'ar gurin.
Said Kuma dakin yayi shiru.
Abban ne yacewa Imam "Mai sunan Malam ayi Mana addu'a".
Ya jima Yana addu'a sanan aka shafa. Sannan Abban ya Dora da cewa.
"Alhamdulillahi ala kulli halin, dole ne mu godewa Allah s.w.a a cikin kowane Hali mutum ya Samu kansa, kowa yasan yanda lamarin Auren Uwata ya ringa kasancewa a baya abune ba Mai dadin maimaitawa ba, to wannan karon ma tarihine yaso maimaita kansa Amma na yanzu sai yafi sauran tada hankali ni Kuma Naga a wannan gab'ar bazan Kara bada wata kafa ba wadda za'a dunga walagigi da rayuwar yarinya karama ba kamar Uwata. Sunanta Ya kira Fatima dago ki kalleni, cikin girmamawa ta dago kanta kamar yanda yayi Mata umarni. Hannunsa yasa ya nuna kansa yace kina ganin zan iya zaluntar k?" Da sauri ta girgiza Kai hawaye na zubo mata.
Yace "To Fatima na daura Miki aure da bakon yaron Nan Mahmud na wajen Aminina Malam Bukar". Duk da taji haka daga bakinsa a jiya Amma Bai hanata kara shiga rudu ba saboda wannan taji daga bakin da bazeyi Mata karya ba, Nan da Nan ialahirin jikinta ya shiga rawa wallahi ita a jiyan jinsa kawai take gani take kamar almara ce kawai.
Muryar Abbansu ce ta Kara katse Mata tunani "kiyi hakuri Uwata kowa da irin jarabawar da ubangji yake Masa ki dauka taki jarabawar kenan, ki yadda da kaddararki sai Ubangiji ya jibinci lamarinki wannan ba hadin kowa bane hadin Allah ne, kiyiwan mininmi biyayya in Sha Allah zakici ribar rayuwa, ki cire yaron Nan Musbahu daga zuciyarki ki rungumi abinda Allah ya baki. Allah yayi Miki albarka yanda Kika yi min biyayya Allah ya Baki 'ya'ya Wanda zasuyi Miki biyayya kema, Allah ya albarkaci aurenku ya tsone idon makiya da mahassada".
Hajiya mama ce ta fasa Kuka tana fadin "Haba Alhaji wannan wane irin danyan hukunci ne? ya zaka dauki 'yar marainyar Allah ka baiwa Wanda ba'asan asalinsa ba, ai duniya saita zage ka Dan Allah ka janye maganar Nan da wannan ba gara kaba salmaun gidan Hajiya Dago ba tunda ya jima Yana son yarinyar Nan Amma ka Hana shi"
Kowa a falon kallonta yake ba Wanda ya tofa sai danta Hamza yace "haba mama menene haka kikeyi Dan Allah kiyi shiru da wannan maganar salmanun me Allah ya sauwake me za'a da wannan zuri'ar".
Hannu Abban ya dagawa Hamza Yana fadin "ya Isa haka tunda ka Bata amsa basai nace komai ba, Amman ki rubuta ki aje in Sha Allah sai wannan auren ya Zama abin kwatance Kuma abin alfahari duk Wanda ze zageni ya Dade Bai zageni ba, Kuma duk Mai ganin zalunci ne yasa na aurawa Fatima Mahmud na barshi da Allah wallahil Azeem ban taba kallon Uwata a matsayin 'yar wani ba kullum Ina Mata kallon 'yata malak malak a makaranta ne kawai ban saka Mata sunana ba shima nayi haka ne Dan tasan nata mahaifin ta rinka Yi musu addu'a".
Addu'a Abban yasa Imama yayi yaba kowa izinin tafiya Amma yace Ammah ta tsaya ita da Hajiya mamar da Inna maimuna da Maman lafia.
Aunty Hasana ce ta kamo hannun Zahra zuwa dakin Ammah tana kuka, yarinyar tausayi take Bata kamar yanda Abban ya fad'a ana walagigi da rayuwar ta.
Cikin bed room din Ammah suka wuce, bayan sun zauna ne Auntyn ta riko hannun Zahrar "kiyi hakuri kinji Allah Yana sane da halin da kike ciki, Dan Allah kad'a ki watsawa Abba kasa a Ido ki bijirewa auren nan wallahi irin wanna auren Yana albarka fiye da tunanin".
Wasu sabbin hawayen ta goge. Cikin shashhshekar kuka tace "wallahi Aunty nifa tsironsa nakeji idan muka hada Ido wani Abu nake gani a idonsa".
Sororo Auntyn tayi kafin tace "ban Gane ba tsoronss kamar Yaya, Daman kinsansa ne runtuni?.
Kai ta gyada Mata alamar Eh.
"Allah ya kyauta" kawai Auntyn tace.
"Ko meme ma dai wannan tsakaninku ne kin gyarota can".
Ta Mike tana fadin "Bari na koma gida sai zuwa an jima zamu shigo da Sajida da Amatu itama Bata tafi ba jiyan.
********Tun bayan suka dawo daga sallar Asuba Mahmud yake ta faman aiki a cikin laptop dinsa, Yana kallon Sameer Yana kwasar barcin gajiya. Bai gama aikin ba sai kusan karfe takwas na safe, kai tsaye toilet ya nufa ya jima a ciki kafin ya fito daure da towel a kugunsa karami Kuma a hannunsa ya goge sumar kansa me baka sidik Mai laushi Saida ya shirts cikin wani farin yadi filtex marara nauyi ya feda turarensa Alburaq sannan yaje gefen bedside ya dauki wayarsa ya kunna.
Abinci ya bukata a kawo musu, yana Gama wayar Kira ya shigo sunan Habib ya gani, ya daga da sallama daga cen Habib Fara fadar.
"Habe Dan Allah dukka tadawa Baba malam hankali baka kwana a gida ba abinda baka Saba ba Koda wasa duk dare zaka
dawo Amma jiya daga Bari kaje ka dawo shi kenan kayi layar zana Kuma ka Kama ka kulle waya".
Dariya yayi Yana cewa "kana tunanin Kona bi dare nayi Gudun auren dole ko?"
Shima Habib din dariyar yayi.
"Ka Gudun Mana idan ka Isa mai wannan tsaleliyar Ina zaya ya barta koka gudu ka dawo da kafarka, kawai da malam ne ya matsa yaji kana ina".
"Ok shi kenan Bari na kira shi Dan hankalinsa ya kwanta Ina Nan tare da Oga Sameer shine ya rikeni nayi Masa wani aiki".
Yana kashe wayar ya nufi sofa ya zauna yana janyo stool din da aka Dora abincin.
"Oh ni Sameer yaushe na rikeka? ka rikeni dai ka Hanani tafiya ka barni da kame kame ga madam can tana fama da kanta ba mataimaki gaskiya yau in Sha Allah sai kano".
Ya fad'a yana nufar toilet shima.
Can hayin bankin suka Fara zuwa gurin masu aikin gidan Masha Allah aikin yayi nisa kamar ba jiya aka Fara ba Sam an canzawa gidan fasali kamar bashi ba, duk abinda ake bukata Sameer ya danka shi a hannun Binya.
Sannan suka nufi cikin gari.
Wani mall suka shiga Mahmud ya jido kayan fruits dasu kayan tea sai chocolates dasu farm fresh yogurt da fresh milk. Leda uku aka cika manya Saida suka dauki hanya Sameer ya kalli Mahmud yana fadin "wadannan kayan fa yallabai na waye".
"Dubiya zamu saika Bata tunda ni dai kowa yasan bani da kudin sayansu.
AUREN HUCE HAUSHI
Page six
________Sun jima a gurin Baba Malam Yana yiwa Sameer godiyar dawainiyar da yasha akan wannan lamarin, sannan yayiwa Baba Malam din sallama akan zai wuce sai hutu ya Kare zasuzo da mutanen su suna son su kawo wasu ayyukan da za'ayi.
Har gurin mota Malam dasu Habib sukayi Masa rakiya, Baba malam Yana fadin "Bari muyi addu'a".
Nan yaja doguwar addu'a akan Allah ya tsare hanya, har Sameer ya shiga mota ya fito ya nufi Malam Wanda har ya Fara tafiya, sai Kuma yaja ya tsaya Yana jiran karasowar Sameer din.
Dan risinawa yayi Yana fadin "ko za'a samu Wanda ze rakani na Kara dubo jikin wannan yarinyar?"
Wani kallon kasan ido Mahmud ya bashi dashi "Wai yarinya".
"To! To! Masha Allah ai sai kuje da Mahmud din da Habibu kuga jikin, ai wannan tunani ne Mai kyau.Nima na shiga da safe gurin Alhajin naji yata kwana".
Har cikin harabar gidan Sameer ya shiga da motar, Abdul Hakeem Habib ya Kira kafin su shigo ma ya fito Nan Harabar gidan Yana jiransu.
Shi yayi musu jagora zuwa falon Abban, yayi murna sosai da ganinsu sun gaisa sosai sun masa godiya sosai da karamcin da yayi musu, yaji dadi sosai Dan har ya ringa tsokanar Sameer Yana fadar "wato tunda kazo gabatar da aikinku ban sake ganin kafarka ba a gidan Nan sai yau dana baku Mata ko? Dan na lura baka da aminin daya wuce Mahmud a garin nan. Masha Allah, Malam ya fada min duk Fadi tashin ku akan lamarin Allah ya saka da Alkhairi yabar zumunci".
Suka Amma da "Amin ya Rabbi".
Mahmud Alhajin ya kalla Yana fadin "kayi hakuri fa Mahmud munyi maka nauyin kuka".
Kai ya gairgiza Yana fadin "ko daya wallahi ba komai nagode, Allah ya saka da Alkhairi ya Kara lafiya Nisan kwana Mai albarka"
"Allahumma Amin. Allah yayi Albarka, ya baku zaman lafiya ya baku zuru'a Mai Albarka, sai ayi ta hakuri da lamarin Mata fa. Abdul Hakeem ku shiga ciki su gaisa da Iyayen nasu".
Wannan shine shigar Mahmud na biyu gidan, na farko lokacin da magaji yayi accident da mashin suka shigo shida Abdul Hakeem da Hamza ya duba shi a dakin Ammah, dan ma lokacin ba kowa a gidan sunje gaisuwar mutuwa.
Directly dakin Hajiya Mama Abdul ya nufa dasu, Zilai Mai musu wanke wanke ce tayi zuruf ta shiga dakin Ammah.
Tana fadin "Ammah Ina Jin fa ga mijin Zahara'u Nan sun shiga dakin Mama shida Abdul Hakeem da wasu inaga abokansa ne".
Ta juya ta fita.
Gyalen Inna maimuna Ammar ta dauka dake kusa da ita ta yafa a jikinta.
Da sallama Abdul Hakeem din ya shigo Yana fadin Bismillah ku shigo Mana, a nan kan carpet a kasa suka zauna suna gaishe dasu Ammar tare da tambayar Mai jikin.
Abdul Hakeem ne yace " Inna mijin Zahra ne da ubangidansa suka shigo duba ta shi yau ze wuce shine yace a rako shi ya Kara dubata da jikin nata".
"Kai Masha Allah an gode madallah Allah ya saka da Alkhairi ya maida ka gida lafiya". Inna maimuna ta fada sannan ta kara da cewa "to waye angon nawa Dan nice ta karfe ita wannan Farafarar ba wani abun azo a gani zata iya ba ni kuwa ko banza na tuka maka tuwon dawa da man shanu ko ba haka ba?" Ta tambaye shi tana kallonsu.
Duk dariya sukayi Amma shi gogan Dan murmushi yayi kadan Yana basarwa.
Abdul Hakeem ne ya nuna Mahmud Yana cewa.
"Ga angon naki nan nagama kamar kunyarki yakeji"
"A'a! Masha Allah tubarakallah Mai gidan nawa wanke hannu daka taba ne, kaga dago ka kalleni ni Kaka ce kada kaji wata kunya ta".
Kara sadda Kai yayi shifa duk jinsa yake wani iri Wai shine a zaune a dakin surukai Ashe da gaske ana jin kunyar shi wallahi da ji yake kawai fada ake ba wani nauyin da akeji Saida ya same shi yanzu yake gaskata hakan.
A kaikaice Ammah ta kalleshi "Masha Allah" ta fada a zuciyar ta, ita bataga wata makusa ba a tare dashi Kuma idan ba idon tane yake Mata gizo ba sai taga duk cikin Wanda zasu auri Zahrar a baya bataga Mai nagarat wannan yaron ba.
Albarka da nasiha dai ya Sha ta gurin Inna maimuna.
A haka suka fito daga dakin har suka fito compound din Abdul Hakeem Bai fito ba sai duba agogo Sameer keyi Yana mita.
"Nifa bana son nayi Rana a tafiyar Nan gaskiya, Naga alamar kuma neman kuke kusa nayi yamma ma".
Kafin Mahmud ya bashi amsa Abdul Hakeem din ya fito da sauri da key a hannunsa Yana fadin "kuyi hakuri key din ne ba'a gani ba da wuri ku karaso ciki kafin Zahrar ta fito ku gaisa".
Mahmud ne yace "Kai haba da an kyaketa ta huta ita da Bata da lafiyar kirki".
Karamin falo ne da kujeru masu kyau sosai da kayan kallon alama an tana deshi ne saboda Yara Mata na gidan da Kuma dai dai kun Baki.
Bayan fitar Abdul Hakeem, Sameer ya kalli Mahmud.
"Dan Allah my man yaushe idonka ya koyi kunya? Naga sai wani sadda Kai kake, nifa lamarinka ya Fara bani tsoro na rasa wace alkibla ka kalla kazo garin mutane ka Mike kafa kana wata irin rayuwa a takure nace zan dauki mataki ka aje min sharadi, da kasan bazan it's tsallakewa ba, yanzu Kuma Rana tsaka a tarko aure Kai kadai kamar marar gata sai walagigi kake alhalin kana da madafa".
Tsaki yayi " kana da matsala wallahi ko me zance fada maka bazaka Gane ba, amma idan lokaci yayi zaka fashinmta,yanzu duk bayanin da zanyi maka ba fashinmta zakayi ba, kawai mu bar maganar kawaai"
Kanshin turaren ne ya alamta musu zuwanta. sallama tayi cikin siririyar muryarta.
Sameer ne ya amsa Mata sallamar a zahiri Dan shi Dan gogan a saman lebensa ta amsa sallamar. Sameer din ne ya Dan Mike Yana fadar.
"Masha Allah jiki yayi sauki kam, "Bismillah". Yana nuna Mata kujerar gefen Mahmud. Kai ta dangirgiza Masa tana dan murmushi kasa kasa.
A Nan kan carpet ta zauna daga gefe tana gaishe da su a jimlace.
"Lafiya kalau"
Sameer ya amsa Yana fadin "ya jikin naki?"
"Alhamdulillahi" ta amsa masa.
Sai Kuma duk sukayi shiru, ganin lokaci Yana qurewa Sameer ya Mike tare da kallon Zahra Yana fadin " To madam bako zeyi halinsa Allah ya bada zaman lafiya. Amma fa sai kina hakuri da halinsa gaskiya ba kirki ya cika ba Ina son idan na dawo Naga canji na zahiri a tare dashi, sunan Sameer Sa'ad koko, zeyi miki cikakken bayanin koni waye a gurinsa Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a mai..albarka Allah yasa next year by now muna bkin suna"
Da sauri Mahmud ya kalli Sameer a zuciyarsa Yana fadin "Allah ya shiryeka Sam baka girma".
A hankali tace " Mun gode kwarai Allah ya tsare ya kiyaye hanya".
"Amin" ya amsa Yana kallon Mahmud.
"Ni zan wuce saina sake shigowa ayi kokarin ganin aikin Nan ya kammalu".
Ya fada Yana nufar kofar fita.
Sai lokacin Mahmud din yayi magana "pls ka jirani minti biyar Dan Allah".
"Idan ya wuce haka Kam...."
Ya fice ba tare daya karasa fada ba.
Tunda Sameer din ya fita take wasa da karamin zoben da yake hannunta. Bata dagon kalle shi ba shi Kuma Bai tofa tasa ba amman idonsa Yana kanta, Kare Mata kallo yake Yana fadar "Masha Allah tabarakakkahu ahasanil kaliqin".
Tsam ya taso daga inda yake ya sauko kasa inda take zaune.
"Ya jikin naki?".
Ta tsinkayi maganarsa kusa da ita daf Sam bataga lokacin daya taso ba.
Cikin daburcewa saboda kusancin nasu yayi matukar yawa ji tayi kamar ma iskar gurin ta tsaya sai munfashinsa take shaqa kawai.
A mamakance taga yasa hannunsa ya dago fuskarta suka hada Ido hudu dashi. Da sauri ta runtse idanunta zuciyarta na wata irin bugawa.
"Bude idon Kona Baki mamaki".
Marmar ta Fara da idon tana budewa a hankali Amma taki kallon nasa idon.
"Ya jikin?".
Ya Kara maiamaitawa, a hankali ta bude bakinta tace "da sauki"
Gamshin Lister mint ne ya daki fuskarsa. Banda Yana daf da ita ba yanda za'ayi yaji abinda ta fada.
"Allah ya Kara lafiya".
"Ameen"
Ta fada.
Hannunsa ya cire daga fuskarta yana Dan furzar da iska daga bikinsa ya Mike tsaye, a hankali ta sauke wani numfashi.
A bazata taji yace "bani wayarki"
Ba musu ta Mika masa, aljihu taga ya saka Yana fadin "ki shiga gida ki kwanta kiyi barci sosai kada ki yawaita hayaniya ki samu hutu sosai, zan tambayi magaji idan bakya hutawa yanda ya kamata ni Ina da inda zan kaiki ki samu isolation, tashi muje ki shiga gida ana jirana".
Saida ta shige ciki kafin ya juya ya nufi gurin da Sameer da Abdul Hakeem suke suna Hira.
Lokacin data shiga dakin ta Samu Aunty Hasana dasu sajida sunzo har da yaran duka.
Da guda ta karasa cikin suka rungume juna da Sajida Nan da Nan sai hawaye itama sajidar kukan ta fara.
Ammah ce tace "Naga abinda ya isheni meye haka zaku tasa mutane a gaba Kuna kuka, to kukan maganin me ze muku aikin Gama ai ya Riga ya Gama Saida hakuri da addu'a kawai".
Uwar dakin Ammah suka shige.
Magaji ne yayi sallama ya shigo da manyan ledoji guda biyu niqi-niqi da kaya Auntyn Hasan na tambayar"daga Ina?"
Ya fice da sauran Yana fadin "ina zuwa Aunty"
Wata ledar ya shigo da ita Yana fadar"kayan dubiya ne aka kawo Mata" ledar daya kawo daga karshen ya bude rafar 'yan dari bibiyu hura biyu ya dauko daga saman kayan, Aunty Hasana ya
Mikawa yana fadar "gashi nan inji abokin mijinta Wanda suka shigo dashi dazu".
Godiya su Inna maimuna sukayi tayi kamar Yana nan a gurin suna ta Saka albarka.
********* Bayan tafiyar Sameer can gurin aikin gidan suka wuce, ba karamin mamaki Habib yayi ba har ya kasa hakuri ya tambayi Bilyaminu lokacin Mahmud Yana ciki. "Dan Allah wane irin kudi gayen Nan ya bada haka Nan da Nan gidan ya juye ya Zama kamar daukowa akayi daga wata kasar".
"Wallahi Nima bazance ga abinda ake kashewa ba, iya kudin aiki Dana abinci kawai suke a hannuna, bakaga wash bakin fuska ba su biyu?'
"Eh nagansu"
Habib ya fada. "To ai tun jiya sukazo da komai na aikin bakaga Nata'ala ba shima lebura ya koma kaga ai da malam shi yasa a Kira saboda 'yan gyare gyaren amman da masu iyawar sukazo shima yaronsu ya koma".
Ya fada Yana dariya.
"Wallahi Bilya sai a kyaleka Kai kowama sai ka tab'a".
"Gaskiyar kenan ni wallahi burgeni ma yayi tunda baiyi zuciya ba ya tafi, ko banza nasan Yana lure da koma Dan gyaran nasa aikin".
*****A bedroom din ammah Zahra ce da Sajida suke tattaunawa akan abinda ya faru,sunyi iya nasu hasashen amma sun kasa gano bakin zare Sajida ce tace "nifa Zahra Ina hasashen wani Abu akan lamarin ki"
"Kamar me kenan?"
Dan Jim tayi kafin tace "Anya ba asiri ake yiwa duk wani Wanda yazo da niyyar aurenki ba? Ki tsaya kiyi nazarin abun Mana ko mafarkan da kike yi duk lokacin da maganar aurenki ta taso abin dubawa ne"
Dan murmushi Zahrar tayi "kin jiki kema bestie wane irin asiri Kuma,ana zaune lafiya to waye har ze bata lokacinsa da kudinsa gurin yi min wani Abu kawai daga Allah ne kinsan kowa da yanda Allah make jarabtarsa ni tawace tazo a haka".
"Eh na yarda daga Allah ne bana inkari Amma akwai sanadi, inaga gobe ma zan wuce duk da nacewa Umma sai Wednesday Amma na fasa wallahi Rimi zanje gurin Baban Umma na fada Masa ai kinsan shi farin sani Kuma zeyi duk abinda ya kamata tunda ke wani lokacin kanki ba Maths".
Kwarkwar tayi da ido Dan Allah Saji kada ki tafi ki Bari a Gama komai saiki tafin".
Wani kallo tayiwa Zahra "tafiya dole na tafi Amma zan dawo kwana kusa in Sha Allah, kinsan Zama da Baffa yasa Ina Gane wasu abubuwan tunda Yana fadw min ire -iren abubuwan da suka shafi sihiri Kinga yace min duk wani ciwon da yake da lokaci misali ace kullun sai dare mutun yake kasa barci kinsan da matsala, ko ace mace duk ranar girkinta Bata da lafiya ko duk ranar girkinta tana zubar da jini amma idan ta Gama aikin shike nan sai ya dauke babu, ko kamar taki matsalar sai an saka Miki ranar aure sai ana gaf da biki abun yake lalacewa, Kika sani ko Abban naku ma ya Fara irin wannan tunanin ne yasa ya yanke wanna hukuncin cikin sirri ki tsaya kiyi tunani Mana"
Sosai magungunan Sajida sun sakata a tunanin da Bata tabayi ba.
Sauke zazzafan numfashi tayi tana fadin "Allah ya kyauta ni duk kin sakani a tunani wallahi"
Haba "Bestie ai kinsan ruwa baya tsami a banza me ake nema a gurin mace Allah Bai Baki ba Amma sai an Yi abu kama-kama ya lalace zance da muka Dade munayj da Aunty Hasana kenan jiya Kuma ta bain go ahead na naje na faduwa Baffan rimin, tace ma zata fadawa Ammah, ma".
Kiran da Aunty Hasana tayi wa Sajida ne ya katse musu tattaunawar, ta tashi ta fita.
Washe gari duk bakin Ammah suka tafi, Inna maimuna kadai suka Bari sai Amarya taje dakinta zata koma gida.
Part din da bakin suka zauna Ammah tasa su Zilai suka gyara sosai tunda Daman nasu Zahra ne, kafin yamma gurin yayi tas kamar ba'ayi wata dabdala a cikinsa ba.
Bayan sallar insha'i zahra da Sajida suka koma part din.
Suna zaune a kan gado Autan Ammah musaddiq ya shigo dakin da sallama hannunsa rike da leda fara Mai kyau ya mikowa Zahra yana fadin "gashi Aunty inji wannan na gidan Baba Malam din yace a kawo Miki Kuma yana duba ki, Kinga Nima ya bani".
Ya Mika nata 1 k din dake hannunsa.".
"To angode madallah".
Ledar Sajida ta dauka ta bude waya ta gani sabuwa kar a ciki.
"Wow gaskiya ba karya ke! Irin wannan babbar harka haka, Dan Allah Yi min bayani naji yace wannan na gidan Baba malam din waye ko angon namu ne da ake Raina mana ya Fara tsula Mana abun arziki haka?".
Baki ta Zahra ta zunbura.
"Nace Masa Ina bukatar sabuwar waya ne da zai kawo min, ni wallahi a mayar Masa".
Ta fada tana kokarin amsar ledar faga hannun sajidar.
"Ke tsaya da Allah yi min bayani yanda zan gane, Ina taking wayar naji kina wata magana".
"Tana gurinsa tun safe ya karba ni bansan abinda zeyi da ita ba, ya dai ce na bashi kawai ni kuma na bashin shine Kuma maimakon ya bani tawa shine ya Aiko min da wannan".
Musaddiq Sajida ta kalla 'kai auta maza kaje kace tace ta gode Allah ya Kara nudi"
Sai da ya fita sannna ta juyo gurin Zahra. "Amman wallahi kin bani mamaki Allah ya tarfawa garinki nono ki nemi ki Bata rawarki da tsalle to kici gaba har ki nuna b'araka a gaban 'yan uba, Koda wasa kara ki Kara ba'a yiwa miji haka ko bakaso Abu baka nunawa a gabansa, kika san da Yaya yayi sawo Miki danya faranta Miki Rai Amma Zaki wani kwasale shi kice a mayar Masa kina son tun yanzu ki kashe Masa Gwiwa ko".
AUREN HUCE HAUSHI
JINJINA TA MUSAMMAN GA MALAMAN MAKARANTA ALLAH YAYI JAGORA YA QARA BASIRA DA JURIYAR SAUKEN NAUYIN DA AKA DORA MUKU NA AMANAR YARA QANANA
This page is deducted to you Families of late Alhaji Isah Musa Bakin kasuwa kazaure jigawa state.
PAGE SEVEN
_______Mika tayi tana salatin ma'aiki s a.w.w sannan ta Zoro kafafunta kasa, tunda ta farka tasan tabbas karfe biyu tayi na sulsulin dare har ya zamar Mata jiki. Dubanta ta kai inda Sajida ke kwance barcinta take sadidan cikin kwanciya hankali, sai taji Ina ma ita ce haka, wasu hawayen ne suka ciko idanunta a hankali tace "Ya Rabbi ga baiwarka Mai rauna ka jibinci lamarina dan Isar Manzon Allah s a.w.w. kada ka barni da iyawata ka iya min da iyawarka kada ka Bari makiya su yi min dariya ka bani rinjaye ka dorani akan duk Wanda yake son Hawa kaina".
Ta Mike tsam ta nufi toilet din cikin dakin sai Kuma ta fito saboda shaf ta manta kafin su kwanta taga famfon ya dauke Kuma da alama ba'a kunna layinsu na tanki ba. Cikin rashin tsoro ta bude kofar ta fita zuwa bayan part din Mama don ta kunno ruwan, gurin ta dosa gadan gadan sai Kuma tayi turus, magana take jiyowa daga wurin da sauri ta koma baya dan bata San abinda zata gani ba. Tana tsuma ita fa duk da Bata da tsoro amma tana tsoron ganin abinda yafi karfin idonta ko Kuma wani mugun abun.
Dole tayi hakurin yin sallar a koma ta kwanta tana ta sake-sake har kusan Asuba, ba Kuma taji motsin wani na tada hankali ba.
Saida Sajida ta tashe ta lokacin har an Fara sallah a masallacin gidan nasu.
A gurguje tayo alwala da alama Sajida ce ta shigo da ruwan.
Bayan sunyi sallah zaman Azkar sukayi har lokacin da gari yayi shahhh alamar wayewa, sannan suka koma suka kwanta. Dukkan su ba barci suke ba, Zahra ce ta danyi tsaki kadan ta tashi zaune.
Kallonta Sajida tayi.
"Yaya Bestie akwai damuwa ne?"
Dan juyowa zahrar tayi tana kallon sajidar tana Kara wani tsakin "nifa wallahi na fada Miki tsoron mutumin nan nakeji tun ranar Dana Fara ganinsa a gidan Baba malam nake Jin wata irin shakkarsa. Dan Allah a haka zamu rayu bana ko son kallon idanunsa? Kinsan wani tarin abin haushin jiya fa hannu yasa ya dago fuskata Wai dole saina bude idona na kalle shi ko Kuma ya bani mamaki, Kuma fa ranar Nan a asibiti har wani shafar min fuska yayi Yana fadar nayi hakuri da wannan hadin shima ba so yake ba, kawai yayi biyaya ne tunda baze iya yiwa su Abba musu ba, amma ni Ina iya fada musu bana so".
Baki Sajida ta rufe tana kunshe dariyar ta. Kai ta shiga girgizawa tana fadar Babbar magana ki fadawa su Abba bakyaso! Wato ke ga marar ta ido ko? Shima har yasan kimarsu da baze iya yin musu dasu ba saike ce marar kunya Zaki Fadi Baki so, ki rabu dashi kwaai abinda nake so dake yanzu ki koyi dakewa a gaban nasa sannan ki daina tsoron idanun nasa, Wai tsaya fada min menene a cikin idon nasa da yake firgitaki duk girmanki da wayonki da wayewar ki?"
Wani shagwabe fuska tayi kamar Mai Shirin fasa kuka.
"Bazaki gabe ba, ni kaina bansan ya zanyi ba saboda shi fa na daina zuwa gidan Baba malam tunda lokacin kullum Yana tare da shi kuma sai yayi ta kallona yana tsareni da wadannan idunuwan nasa kamar Mai jin barci".
Yanzu dariya sosai Sajida keyi harda kwalla tana fadar Babbar magana tab kice abin asali ya Samo shi ai kaya ne suka tsinke Masa a gidin kaba kece dai kike bulayi"
"Kamar yaya?"
"A'a bazakiji mutuwar sarki a bakina ba ai tunda an hada anyi Mai walahar...".
Sautin kiran waya ya dakatar da shegantakar da sajidar ke mata.
Wayar da aka kawo Mata jiya ce ta dauki kida, Sajida ce ta Mika hannu ta dauka M.M DANGE ta gani Yana yawo akan screen din.
Zahra ta mikawa tana fadar oga ne da alama a Sha soyayya lfy. Tayi waje tana fadin Bari naje nayiwa Ammah shara.
Bata daga Kiran ba har Saida ya kusa katsewa kana ta daga tasa a kunnenta. Daga can taji Yana fadar "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
A zuciyar ta a amsa Dan da gaske in dai zata ganshi ko taji maganarsa kasa samun nutsuwa take.
Sake maimaita sallamar yayi, da kyar ta amsa masa tare da fadar " Ina kwana?"
Shiru taji ba'a amsa ba kamar ma an sauka daga layin, amma ga mamakinta tana dubawa sai taga Yana nan, itama shirun tayi kudin sunata tafiya saita saka handsfree ta aje wayar kusa da daga gefe tana kallon ikon Allah.
Saida ya mula Dan kansa "yace ya jikin naki I hope kin shan maganinki?"
"Eh" ta fada a takaice.
"Fine"yace shima a takaicen.
Ita mamaki ma yake Bata har wani turanci yake jefawa a magana kamar gaske.
"Sai an jima ta fada tana kokarin katse Kiran.
"Kada ki kuskurs ki kashe min Kira" ya fada in serious tongue.
Shiru tayi tana mamakinsa sai wata izza yake Mata kamar wani abin azo a gani.
Muryarshi ta tsinkaya Yana fadin ki bude data na turo Miki sako idan da abinda kike bukatar ayi ko a Kara sai ki fada min, take care".
Kit ya kashe kiran.
"Kutt!" Ta fada "amman gayen nan yama Raina ni wlh Wai kada na kashe Masa waya"
Kwafa tayi "zakaga na kiraka ganin idon ka" ta Jafar da wayar tana mita.
Taso yin barci Amma ta kasa dole ta hakura, wayar ta Kara daukowa tana kare Mata kallo.
Number din Hameeda ta Fara sakawa tunda taga sabon layi ne ya dauke natan, ga mamakinta sai taga sunan Hameedar ya bayyana ba bata lokaci ta kira.
Tana ta ringing kamar baza'a dauka ba sai Kuma ta daga da sallama ai tana jin muryar Zahra ta Fara mita "yanzu Dan Allah kin kyauta tun jiya nake neman layinki Amma shiru na Kira Mama nace ta Baki tace min bakya Jin Dadi kina barci, wallahi Kinga yanda hankalina ya tashi kuwa ki Bari lokacin da Sajida ta fada min halin da ake ciki wallahi daba final muke ba Allah da barinta zanyi c/o na taho gida har fada mukayi da Salma Wai ai sai inje na baiwa Mushahun hakuri ya dawo ya aure maganganu dai gasu nan ki Bari kawai ai jibi zamu Gama in Sha Allah komai dare a gida zan kwana".
"Allah ya yarda ki Bari kawai wallahi Ina cikin yanayi akwai damuwa Dan Allah kizo ko naji sauki abubuwan".
Ta fada tana share hawaye, sukayi sallma Dan it ma Hameedar kukan take.
Wai ita Mushahu ya yiwa haka, duk wadanda suka fasa aurenta Bata taba Jin Wanda ya Bata Mata Rai ya Kuma tsaya Mata kamar wannan ba ai ko wace irin matsala ce ita ya kamata ya Fara fadawa ba ya yanke mu'amala da ita ba a lokacin da take matukar bukatarsa ya manta shakuwar dake tsakanin su da alkawarirrikan da suka yiwa juna.
Kwantawa tayi tana tunanin baya a haka wani wahalallan barci yayi gaba da ita.
**********Tun Yana tsammanin ganin ta bude data ta duba sakon har ya cire Rai da hakan.
Lambar Abdul Hakeem ya Kira sun jima suna waya kafin suyi sallama.
Laptop dinsa ya janyo yaci gaba da aiyukansa sai kusan azzahar ya Gama. toilet din cikin dakin ya shiga ya dauro alwala,a masallacin hotel din Yaya sallah lokacin daya fito Kiran Habib ya shigo Masa "Wai Dan Allah kana Ina ne tun dazu muke nemanka kazo masu aikin hada furniture's din Nan ne suka Gama da cabinet din kitchen".
"Ok gani Nan inaga kada kayi nisa zuwa an jima su Aunty zasuzo suga gurin"
Ya fada.
Yana nufar gurin da ya saba aje lifan din Habib.
Wayar Ammah Abdul Hakeem ya Kira ya fada Mata Mahmud yace a turo a gano gidan an Gama gyaran, dakin Mama Ammah ta shiga ta fada Mata sannan Kira Aunty Hasana ta fada Mata kafin ta wuce gurin Alhajin ta fada Masa tunda shiya dawo daga gidan gonar sai su Abdul Hakeem ya baro suna yiwa shanu Allura da Basu magunguna.
Wurin karfe biyar Aunty Hasana ta debesu a mota harda Sajida suka nufi Hayin bankin cikin jagorancin Habib, lokacin Inna Bata Nan taje MIYA gurin wata aminiyar ta da sukayi aikin Haji shekara daya.
Duk cikinsu ba wadda Bata kadu da ganin gidan ba domin ba karaya an narka mahaukatan kudi a gidan bazaka tab'a cewa renovation akayi Masa ba, bedroom's ne guda uku biyu suna kallon juna dayan Kuma daga gefe da alama yafi sauran girma Kuma shi kadai ne a rufe, sun zagaya ko Ina sai santin gidan Sajida tace tana ta daukar video, falon kadai abin kallo ne duk da ba komai a cikinsa sai fitilu da aka kunna sai Kuma AC da aka ware.
Hajiya mama ce ta kasa hakuri ta leka ta Kira Habib Nan falon ya shigo Yana fadin "gani Mama"
Yana Dan rankwafawa.
Aunty Hasana mama ta kalla "Hasana Dan Allah ki tayani tambayar yaron Nan tunda shi namu ne na gida baze cucemu ba, Wai wannan yaron sana'ar me yake daya iya Kama hayar wannan uban gidan"?"
Kara risinawa yayi Yana fadar "ba haya ya Kama ba Baba malam ne ya bashi kyauta, sai Kuma kungiyar yake yiwa aiki suka kawo masu aiki suka yiwa gidan 'yan gyare -gyare harda kayan daki ma suka zuba masa, Bismillah Bari na bude muku ku gani yanzu ba dadewa zuka Gama hadawa da kitchen din suka tafi".
Dakin ya bude musu ba Hajiya mama da take ta kwana biyu ba, ko Aunty Hasana da Sajida Saida suka Zama 'yan kauye Dan tunda suke Basu taba ganin irin wanna gadon a zahiri ba, ita kanta aunty Hasana lamarin Yana neman ya gagari tunaninta fa ance Almajirin Baba malam to Amma idan aka saka mizanin hankali abin yafi karfin yanda aka fada to wane irin NGO's ne da suke irin wannan aikin akan daidaikun ma'aikatan su haka?" Gaskiya abin akwai abin dubawa.
Lokacin da suka fito harabar gidan ne wata Hilux ta shigo da kaya a bayan motar mutane uku ne a motar bakar fata biyu fari daya Kamar balarabe Kamar kwara.
Kameme Hajiya mama ta hanasu tafiya sai da aka sauke kayan ta gani abinda da suka Gane irin katuwar plasima din Nan Mai cin Rabin bangon Nan ne kawai amman sauran tarkacen Basu Gane komai ba, haka suka kada suka tafi mama nata mitar "A'a da sake Alhaji ya titsiya yaron Nan saiya nuna Iyayen shi kafin a Kai Masa yarinyar Nan haka kawai aje ayi kitso da kwarkawata mutanen yanzu ba abin yarda bane sai kaga mutum har mutum Amman a Baki malam a ciki Kuma Fir'auna".
Maganar data Basu Aunty dariya kenan.


AUREN HUCE HAUSHI


STORY
AND
. WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH


PAGE EIGHT

Lokacin da suka shigo gidan ana ta kokarin daura alwalar sallar magariba.
Sai bayan sallar insha'i ne Mama ta shigo dakin Ammah suka hadu da Aunty Hasana suna fadawa Ammah yanda suka gano gidan da Kuma yanda abin ya daure musu kai.
Nisawa Ammar tayi tana fadar "Mama ki Sami Abban kiyi Masa bayani yanda ze fahimta kinsan yanda suke da malam bana tunanin wannan abun ze saka ya canza ra'ayinsa duba da yanda ya yanke hukuncinsa Bai nemi shawarar kowa ba".
"Aiko dai ya kamata ayi wani Abu gaskiya Nima lamarin ya tsaya mini a cikin zuciya".
Aunty Hasana ta fada.
Sun jima suna tattaunawar kafin Mama ta koma daki tabar Autty Hasanar da Ammah.
Zama Aunty Hasanar ta kyara ta fuskanci Ammar ta Kira sunanta "Anya wannan Mahmud din ba abinda yake boyewa kuwa Ammah Kinga gidan kuwa ga wannan uwar wayar daya canza Mata kinsan kudinta kuwa ? gaskiya I doubt much, ni dai kiyiwa Abban magana da kanki Kamar zefi daukar abun serious akan na Mama".
Can Kuma sajida ce tasa Zahra a gaba tana ta faman zuba.
"Innalillahi! Kinga gidanki kuwa? Allah ya bamu ya taku wallahi Zahra ki godewa Allah. Wallahi Allah ya Gama miki duk wata ni'ima ta ko Ina kinyi gaban da Nan kurkusa dai kafin a fiki za'a Dade ana lalube. Zahra Naga mijinki har mun gaisa ada Ina adawa da auren Amma tunda na ganshi Naga Yana yinsa nasan yanzu ne kikayi aure da mijin daya Dace ke.Kawai dai matsalar za'ace ba Mai kudi bane,amma a yanda gidan da zaya ajeki yake wallahi ko minister ne sai hakan, akwai abinda na gani a gidanki wallahi ban taba gani a gidanki kowa ba duk yawona sai dai a film amma dai a zahiri A'a ban taba gani ba Allah Bai kaini gurin ba".
Tunda ta Fara zuba Zahrar ke bin sajida da idon lokaci daya duk ta wani rude sai zuba take Kamar 'ya 'yan kanya.
"Kin Gama?"
zahrar ta tambayi sajidar.
"Eh na Gama aini an ma yanka ta tashi na fasa tafiyar zanyi waya da Mom taje can Rimin sumailar gurin Baffan kawai, tunda Daman zatazo nan din ba suna kwantagora".
"Ke Kika sani dai tunda Naga kina nema ki Zama wata daban ko dai an canza min ke da wata ne ko Kuma wani abun ya fada Miki ya goge Miki hadda ne?".
"Eh da alama Kam Dan ya fiki iya lafazi gaskiya inaga na Zama 'yar team dinsa fa tunda Naga ke Baki da wayo".
Ta fada tana dariya.
Washe gari tun safe Abba yasa aka Kai furniture's din Zahra gidan Daman Aunty Hasana sunyi magana da Wanda zasu hada musu kayan, kayan kitchen da sauran kayayyakin duk suna gidan Aunty Hasana daga can aka ringa daukowa, masu aikin su suka hada komai na gidan hatta kitchen su suka gyara komai, gidan ba karamin kyau yayi ba, ba karya duk Wanda yaga gidan yasan na 'yar gata ne.Dan wasu irin mahaukatan Turkish furniture's ne wanda kakanninta ta gurin uwa sukayi Mata duk wani abun more rayuwa akwai shi a gidan Nan, bangaren electronics ma sai a cikin lockers aka zuba wasu, komai yayi.
Lokacin da aka Gama gyaran Aunty Hasana da sajida ne sukazo gani ba karamin burgesu gidan yayi ba Dan sai yanzu ne ya fito a asalinsa na kyau da kayatar da Mai gani, komai na gidan unique ne Masha Allah.
A waya sajida ta daukowa Ammah komai. Ita kanta Ammah Kai Kawai take jinjinawa Dan ba karamin burgeta abin yayi ba, sai dai can kasan ranta rudani ne kala-kala domin abin ne duk yazo a hagunce.
Tana tsoron lamarin sosai sai da har abada baza iya jayayya da Alhajin ba Dan da gaske ubane tsayayye Wanda baya nuna banbanci tsakanin abinda ya Haifa da Wanda yake bashi ya Haifa ba, amma harga Allah tana zulumin wannan AUREN HUCE HAUSHIN da Alhajin yayiwa 'yar marainiyar Allah, mazan yanzu sunce suna sonka ma ya kukan kare idan Zama yayi Zama ballantana matar cushe ta San komai Daren dadewa ranar da yaga irin matar da yake so Sai dai zahra tayi hakurin zama Kawai, duk da tasan Bata da haufi akan yarinyar Tata Dan macece har mace abin alfaharin kowa ne namiji ace ya mallaki Kamar ta, to Amma shi lamarin so daban yake duk kyan mutum da asalinsa ba lallai ne ace yana burge kowa ba domin shi dai so makaho ne.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali duk jikinta yayi Mata wani irin Sanya ta kalli Aunty Hasana tace "Hasana Ina jin wani irin rauni a zuciya ta game da lamarin nan Ina tausayin yarinyar nan rayuwa tana ta walagigi da ita sai nake ganin Kamar laifi nane Dana kafe a barmin yarinyar Nan na hana kakanninta ita ni Kuma nayi sakacin da aka maida rayuwar ta Kamar kwallo ana ta dokata daga Nan zuwa nan".
Ta karasa maganar hawaye na zubo mata.
Abinda tunda Allah ya kawo Aunty Hasana duniya Bata taba gani ba a zahiri gurin Ammah Nan da Nan hankalinta ya tashi sajida ma kukan ta Fara duk da batasas takamaimai man abinda ya saka Ammah kukan ba, tashi tayi ta fice daga dakin jin an Fara Kiran sallar magariba.
Aunty Hasana ce tace "Haba Ammah duk yanda Kika jure bakin cikin baya na abubuwan da suka faru Baki taba zubar da hawaye ba sai yanzu da Allah ya nufa akayi ai godiya Zaki yiwa Allah daya kawo karshen wahalar ba kuka ba".
Gefen zani tasa tana goge hawayen.
"Hasana Ina hango abinda ke bakya hangowa ne,masu iya magana suna cewa matar shige Bata daraja ba irin wannan rayuwar na sowa Zahra ba to sai dai kana naka Allah Yana nasa Kuma nasan ne gaskiya. Ba komai haka Allah ya tsara komai mukaddari ne daga gare shi, naji Alhaji Yana maganar zuwa juma'a za'a kaita".
*******Tun bayan kammala karatunsu na bayan insha'i da suke na littafin iziyya yake zaune a kusa da Baba malam har kowa ya watse ya rage saura su biyu tunda malam yaga haka yasan da magana a bakin Mahmud ne.
"Ya ya akayi ne Mahmuda?"
Malam ya jefo Masa tambayar, Kara dukar da Kai yayi kafin yace "Daman maganar kayan lefe ne dazu Oga Sameer ya kirani yace ya hado tasa gudunmawar kenan, shine nace Bari na fada maka Dan kasan da zuwansu".
"Ikon Allah shi wannan yaron baya gajiya ne Kamar baisan ciwon nema ba tunda yazo ya riski maganar Nan yake Yi kan jiki kan karfi. Allah ya saka Masa da Alkhairi yabar muku zumunci".
"Ameen" ya amsa.
Harya Mike ze tafi sai malam din ya dakatar dashi, dawowa yayi zauna.
Gyaran murya malam din yafa kafin ta jefo Masa tambayar.
"Sai zuwa yaushe ne kake ganin zamuje ga mahaifan naka kaga dole muje musu tunda wannan lamarin ya faru".
Kai ya sadda kasa Yana fadin "zamuje in Sha Allah Amma Dan Allah a Kara min lokaci da kaina zanyi maganar ayi hakuri".
"To ba laifi Allah ya iya Mana kaje ka Samu su Habibu kuje acan gidan ku kwana kaga sun zuba dukiyar kasan yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba".
"To in Sha Allah za'ayi hakan amma ni Ina Nan sai dai su Habib din suje".
"To ai hakan ma yayi Allah yayi Albarka".
Saida ya dudduba dakunan yaran ya tabbatar da komai lafiya lokacin sha biyu ta wuce, dakinsu ya nufa wanka yayi ya saka kayan barci sannan ya hau gado ya bude laptop dinsa. Email dinsa ya shiga Yana duba sakknnin daya samu sakon daya shigo ne ya dauki hankalinsa.
"Ya Salam!".
Abinda ya iya ambata kenan sai Kuma sautin daddad'an ringtone dinsa ya karade dakin.
"Sameer!" Ya fada a hankali yasan za'ayi haka, ya haga wayar Yana fadin "Ta Yaya hakan ya faru?"
Daga can bangaren Sameer din yadan furzar huci Mai zafi Yana fadar "wallahi nayi duk yanda zanyi Amma abun yaki yuwuwa dole ka daura ka kawar da komai muje gaskiya Dan kasan tunda akaje Nan zuwan nake ne Kawai mafita".
"Amman ai kasan halin da ake ciki so kake ace na gudu nabar 'yar mutane Eyeh?".
"Cool down Mana my man abin Bai Kai nan ba aikin daine ya taso na gaggawa Kuma dole sai da Kai za'ayi Dan haka suyi hakuri su aje maka ita zuwa sanda ka dawo ko Kuma ka dauko abarka ku tafi, kaga ai tafiyar tafi yi maka armashi ko?"
Ya fada cikin zolaya.
"Dan Allah ka Zama serious mana, kayi duk abinda ya kamata a Nan goben ka hakura da zuwan ka turo wannan friend din n
aka tunda yasan gurin ya kawo kayan kawai, Kai Kuma ka Kira Baba malam ka fada Masa daga can sun nemi ganin wakilansu na kasa da jahoshi da kananan hukumomi nasan dai kome ake ciki baze wuce kwana buying zuwa uku ba kaga lokacin na tare a gidana nafi son na barta a Nan gidana akan na tafi Bata tare ba".
"Ko dai.......?"
Sameer ya fada Yana dariya.
"Allah ya shiryeka ko dai me? kasan ni salihn ne ba ruwana da wannan sabgar sai ku".
Kit ya kashe wayar sannan yayi switch off dinta.
Misalin karfe Sha biyun Rana wata tamfatsetsiyar mota Parker a kofar gidan malam.
Akwatuna Yara suka dunga saukewa suna shiga falon malam saida suka Gama sannan baki nufi falon malam din bisa jagorancin Habib sun gaisa sosai da malam suka gabatar Masa da kayan daga Sameer.
Malam yayi godiya ya saka Albarka ba adadi.
Falon malam ya bar musu sukaci abinci suka huta sannan Habib ya rakasu can gidan suka gaisa da Mahmud din.
Sai bayan Azahar suka tafi malam yayi musu Sha Tara ta arziki.
Kayan malam yace suje su duba su gani saboda da an jima za'a Mika musu can gidan Alhajin.
Kaya ne na gani na fada an zubasu Kamar ba gobe, an shigarwa da iya Abu ciki ta gani malam yace ta turawa makotanta na kusa suzo su gani anjima za'a Mika musu.
Bayan fitowa daga sallar la'asar ne Malam Bukar ya fadawa Alhaji yanzu su malam Mudi da Alaramma malam Haruna zasu kawo kayan Zahara'u.
Fada Alhajin yayi akan kayan da za'a kawo Yana fadar "Haba malam Dan me za'ayi min haka ko wancen da aka fasa auren Kai sheda ne ban karbi lefe ba da suka matsa cewa nayi suje da kayan idan tazo saiya ba matarsa".
Kai malam yanjinjina Yana fadin "Anyi hakan Kam amma wannan shima bamu muka hada ba wannan yaron Sameeru ne ya turo dasu dazu yace gudunmawarsa ce aba Amarya"
"Ikon Allah shi baya gajiya da dawainya haka daga wannan sai wance Allah ya saka da Alkhairi ya bar.zumunci na jima banga yaro mai karqmcinsa ba abin duniya Bai rufe Masa ido ba".
Da yamma su sajida suna zaune suna Shira ita da Zahra da wata kawar Zahra Mujiba Nan take makotansu suna dasawa da Zahra sosai sun Kuma yi sabo sosai da Sajida tun lokacin da sake zuwa hutu da Sajidar lokacin suna makaranta.
Ba zato ba tsammani Yara suka shigo da manyan jakunkuna dasu cylinder din gas, ai Zahra na ganin haka ta tashi da sauri ta nufi hanyar shigowa gidan da gudu ta karasa Kamar karamar yarinya suka rungume juna da Hameeda Kamar zasu fadi. Suna rike da hannun suka shigo ciki su Mujiba suna ta faman yi Mata sannu da zuwa, sai daga baya Salma ta shigo tana wani shankanshi Bata kula su Zahra ba Suma ba Wanda ya kula ta, directly dakin Mama ta nufa.
Kamar jira ake Salma ta wuce saiga su Magaji da manyan Akwatunan lefe suna shigowa da sauri Zilai Mai aiki ta warto Babbar tabarma ta baza tana rabsa guda tana fadin "Masha Allah! Alherin Allah ya sauka. Fara Mai farar aniya sukari bakai farin banza Fatima Zahara'u 'yar Muhammadu sani, jikar hardon fulanin Mubi, Amarya gidan Mahmud Kuma uwar gidansa Alherin Allah ya Kai Miki, Mama!Ammah ku fito ga abin arziki ya sauka". Har rige-rigen fitowa a key tsakanin Mama da Salma yayin daga dakin Ammah Inna maimuna ta fito.

AUREN HUCE HAUSHIN

WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH
PAGE NINE
____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu irin manyan jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai amale wane jaki. Allah ya Kara daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya"
Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda kin koma roko".
Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata. Uwar dakina murucin kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro yau ga xanzaro a bene" .
Ta Kara kwarara wata gudar.
Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce maza bude Mana muga karamar Arziki"
Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da zilai ne suke fama bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani kasheni komai na ciki classic ne.
Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun.
Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin zamane Allah ya hada arzikinsau.
Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana batsewa Kamar anyi Mata dole sai ta zaune a gurin.
Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah.
Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi gurin Zahra.
Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah wadaran naka ya lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke game kirki". Baki Hameedar ta murguda Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya ra'ayinta dole Nima sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu ruwana ba.
Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon Hameedar tayi "to rasa kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki".
Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa.
"Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da munafurci in dai yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa"
Tana Gama fada ta shige uwar daki.
A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra.
Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba kada Ammah taga Kamar Bata son auren ne ko wani Abu.
Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Ammah sallama Sajida ta rakata ita Haidar din Aunty Hasana.
Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan Sajida har tayi barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman yayi yawa sai ta dauko alqur'ani ta Fara karatu har Saida daya ta gota sannan tayi addu'a ta shafa.
Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata Kamar lokacin yake faruwa
************_
_
TUSHEN LABARIN
AZARE KATAGUM L.G.A
BAUCHI STATE
UNGUWAR FAMFON SHANU.
Yarinya ce 'yar kimanin sheKara goma Sha biyu haka, kyakykyawar gaske fara irin farin Nan Mai hade da Kamar golden yellow , idanunta dara-dara farare tas sai gashin kanta bakirkirin har gadon bayanta hancinta irin dogon Nan ne har baka bakinta Dan karami Mai dauke da 'yan jaja-jaja pink-pink din lebe, bazaka kirata doguwa sosai ba irin tsaka tsakiyar nan, jikin lublub Kamar Mai rayuwa a kasanshen sanyi komai nata Mai kyau ne Wanda idan ka kalleta saika Kara kallonta Dan Allah s.w.a yayi Mata sura Mai kyau na a gani a Kara kalla. Da sallama ta shigo cikin gida tana fadar "wash Allah Ammah wallahi na gaji wadannan littatafan sunyi nauyi da yawa inaga sai dai na kwafo time table kullum na ringa zuwa da Wanda zamuyi amfani dasu kawai". Ta fada tana kokarin Ciro jikar daga bayanta, dariya Ammah tayi tana fadin "ke dai anyi raguwa wallahi zahra ke Sam bakya da juriya jakar da Zaki Goya zuwa mota ma neman gagararki tajeyi".
Kwantawa tayi saman kujera tana fadin "Allah da nauyi dauki fa kiji".
Sulaiman ne ya shigo shima da tasa jakar a kafada Yana dariya.
"Kai Kuma dariyar me kake?"
Ammah ta tambaye shi.
Zahra ya nuna Yana cigaba da dariya. Baki ta zumbura tana dira kafa tana fadar "Allaha Ammah ki rabani da Ya sulaiman Kinga tundazu yake min dariya Kuma nace ya tayani daukar jikar ya Kiya".
"Wai Kai meye haka kazo kana ta dariya Kamar wani sabon kamu".
Jakarsa ya jefa kusa data Zahra kafin ya zauna Yana ba Ammah labari.
"Wato Ammah muna hanyar dawowa ne man motar ya Kare tunanin Malam Bala harya kawo mu gida man Bai Kare ba saboda yace ya biya gidan man yaga da layi idan yace zebi layin zamu Dade muna jiransa shine kawai ya taho, to muna zuwa wurin gidan sarki kawai man motar Nan ya Kare shine fa muka tako a kafa, ita Kuma gwanar iya son jiki ta wani shagwabe mini Wai na daukar Mata jaka na hada da tawa Kamar wani jaki, shine Dan tsabar rainin hankali Wai to na dauka zata karbi kudin gurin Abba ta biyani Kamar wani Dan dako".
Tsaki Ammah tayi tana hararar Sulaiman din "wannan shine abin dariyar Kuma wallahi kayi girman kwabo da meye amfanin hada babba da yaron ba saboda taimakon ba".
"A'a Ammah duka da wata biyar fa na girme mata, to Ina wani girma sa'anni muke ba gashi ajinmu daya ba da dai su Ya Sadiq ne su Aunty Janah, kuma fa duk su Hameeda kowa fa ya dauko tasa sai itace tafi kowa son jika za'a daukar Mata wa zata yiwa karatun ba kanta ba".
Ya fada Yana cire safarsa.
Fita Ammah tayi, ita Kuma Zahra ta shige bedroom din Ammah ba Wanda ya Kara bi takan sulaiman.wanka ta shiga tayi kafin taci abinci saboda Bata son ta makara a islamiyya Sam Bata son abinda ze taba lafiyar jikinta tunda a makarantar bokon suke sallar Azahar.
Lokacin data fito tana sanye da uniform din islamiyya da Jakarta tana kokarin shiga dakin Mama ta biya Hameeda ne taga Hameedar da wani Kaya a wata leda babba ta fito tana zumburar Baki.
"Ya Naga Baki shirya ba ko bazaki makarantar ba? Kinga fa yau zamu bada hadda".
Mama ce ta fito daga dakin tana hararar Zahra "to uwar kinibibi bazatan ba ki Kama hanya ki wuce, ko zata ai bazaku tafi tare ba ana gqninki waye ze kalleta na nuna Miki bana son kina shige Mata amman kin kasa ganewa, Haba yarinya sai kwawa"
Duk wanna maganar da Mama takeyi a hankali take fada Banda Zahrar da Hameedar ba Mai jin abinda take fada duk da Ammah na kofar kitchen dinsu Wanda yake kusa da bangaren na Mama.
Daki Mama ta nunawa Hameeda ta koma yayin da Zahra ta nufi Ammah tana fadin "Ammah na tafi"
"To Allah ya bada sa'a a maida hankali ki biyawa Mujiba ki tafi".
"To" ta amsa ta nufi waje da sauri.
Saida dama Ammah tana ankare da Mama Sam Bata son Zahra na mu'amala da Hameeda kwata-kwata sai Kuma Allah ya hada wata irin kauna tsakanin yaran salma ce Sam basa jituwa da Zahra da ita wata sakarai ce da zahra ko ruwa Mai dadi Salma bazata Bari Tasha a gidan ba, motsi ba motsi ba sai ta Fara fadin ai dai Nan ba gidanki bane ke 'yar riko ce.
Lokacin da Ammah taji maganar a bakin yarinyar tayi mamaki sosai Dan a lokacin wayonta Bai Kai ta iya banbance tsakanin Dan gida na ruko.
Da Ammah ta tsareta ta fada Mata wayace Zahra ba 'yar gidan bace sai tace " Mama ce ta fada tace min na duba Mana Naga ko kalar jiki mu ba iri daya bace mu daina tafiya ma da ita, Wai ta fimu kyau idan muna binta idan muka girma baza'a sure mu ba".
Kan Salma Ammah ta dafa tana fadin "itama 'yar uwarku ce kuyi zumunci da ita kinji" kai ta gyada alamar to.
Abin ya jima Yana baiwa Ammah mamaki Bata zaci haka a gurin mamar ba, tunda a zahiri ba komai a tsakaninsu sai mutunta juna duk da tasan sha'anin kishi ta ciki na ciki ne ta baka na baka.
Sai kusan magariba su zahra suka shigo hannunsu na sarkafe da juna ita da Hameedar, daga gurin Aiken ta wuce makarantar Amma Tasha bulalar makara.
Bayan sun Gama cin abincin dare ne suna hira a dakin Ammah Hameeda ta shigo ta gaishe da Ammah ta zauna sukaci gaba da hira lokacin Ammar tana dakin Abbansu ta Kai Masa abinci.
Lokacin data shigo dakin ya kacame sunata musu akan wani aiki da akayi musu yau a makaranta su matan suna ga yanda za'ayi shi Kuma Sulaiman Yana fadar ga yanda za'ayi, Ammar ce ta zauna tana fadin su kawo ta gani maths ne, Kuma duk hanyar da akabi za'a kaiga samun amsar Dan haka tace kowa yayi nasa yanda ya fashimta.
Har ta shiga bedroom dinta ta fito tana fadin "Na manta Abbanku yace na fada muku ranar Saturday zakiyi jarabawar share fagen shiga karamar secondary school ta kwamnatin tarayya, yace kuyi karatu duk Wanda baici ba baze saimasa ba Saida yaci gaba a makarantar da yake".
Murna suka farayi da gudu Hameeda ta nufi dakinsu Dan ta fadawa Mama.
******Alhaji Jafar Mai yadi haifaffan garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar fanfon shanu, su hudu ne iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da Nanna, kasancewar Babansu Malam Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji day na babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary.
Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai yawa ba daga gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar sakandire yake zaune a gida saidai dinkin hula da aikin hannu na riguna kusan dashi yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan Miya daaya kafawa Nanna jarinsu.
A hankali Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi Shawarar Nanna akan yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai ta dinga saka Masa albarka.
Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara bunkasa da taimakon wani uban gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo nasa kayan zeyi Masa kokarin shago kafin ya dawo.
Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da taimakon Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga cuku- cukun nema admission Nan University ta Bauchi cikin ikon Allah ya samu course din da ya nema Agricultural science.
Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka. Lokacin Yana shiga level 300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta fitar da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu.
Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma Nanna tayi tsalle ta dire ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba.
Wata ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400, Nanna ta aiki Amina kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso Mata na gaggawa.
Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta nufa tunda tasan shagon nasa.
Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana gaishe da Alhajin daya fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?"
Dariya tayi kyawawan hakoranta jerarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya ba komai fa Nanna ce ta Aiko ni".
Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya dauketa a mashin dinsa suka tafi gida.
Da dare Yana zaune a inda suke Hira yaga motar Alhaji Dauda ta tsaya a kofar gidansu da sauri ya tashi ya nufi inda yayi parking sai yaga harda bakon Alhajin Zakariyya suke tare, sun gaisa sosai kafin Alhaji Daudan ya fada Masa Amininsa Kuma Dan uwansa ne yaga Amina Yana so shine nace yazo muji da zafi -zafi akan bugi karfe.
Jafar yaji Dadi sosai zaifi kowa murna idan hakan ta kasance Dan ya yaba sosai da hankalinsa sosai.
Cikin gidan Jafar ya shiga ba jimawa ya fito Yana musu iso ciki sun gaisa da Nanna Alhaji Dauda ne yayiwa Nanna bayanin koma itama irin amsar Jafar ta fada idan tana so ba matsala ba inda aure baya Kai mace Nasarawa batayi nisa ba.
Cikin ikon Allah kuwa Amina taji Alhaji Zakariyya ya kwanta mata a rai Kuma zata iya aurensa duk da fada Mata Yana da Mata harda Yara biyu.
A cikin wata biyu akayi bikin Amina da Alhaji zakariyyan, Jafar yayi Mata komai da uba yake aka kaita can Nasarawa state cikin garin Akwanga.
Wannan kenan.
Haka Jafar yaci gaba da karatunsa har ya Gama ya dawo gida Yana jiran shiga camp.
Lokacin da saki post na tafiya service sunan Jafar ya Fado a cikin masu zuwa Jos yayi murna sosai ko banza Yana jiyo kamshin gida tunda suna makotan jahohi.
Bayan gama zaman camp wata makarantar 'yan Mata jeka ka dawo aka Kai Jafar, Baiyi wata biyu ba Allah ya hada shi da wata yarinya Rabi'a yaji yarinyar ta kwanta Masa tana Kuma da irin Qualities din da yake fatan Samu a gurin matarsa.
Zuwa lokacin gama service dinsu har magana tayi karfi inda iyaye suka shiga.
Wani gida Jafar ya saya kusa da gidansu ya gyara' ba'a dauki lokaci ba akayi bikinsa da Rabi'a suka tare a gidansu. Duk wata kulawarsa da soyayya ya tattara ya baiwa Rabi'a ba abinda ta nema ta rasa sai abinda baza'a rasa ba. Rabi'a irin matan Nan ne masu kissa kafin wani lokaci ta kanainaye zuciyar Nanna.
Kwanci tashi ba wahala a gurin Allah aurensu ya shekara Amma kalubaken da suka Fara fuskanta na Rashn zaman ciki a jikin Rabi'a kusan barinta uku. Ana haka Jafar ya samu aiki da ma'aikatar gona ta jihar Bauchi BARDA.
Cikin kankanin lokaci kofofin wadata suka budewa Jafar kafin shekara biyu ya gina gida Mai kyau sunje makka shida Nanna.
Nan da Nan likafa tayi gaba Amma dai matsalar su na Nan ta rashin haihuwa.
Yayin da abin ma ya Fara damun Nanna har ta gaji tayi Masa magana akan ko maganin hausa za'a fata nemawa Rabi'a ne.
Amma sai ya nuna Mata ayi hakuri tunda tana ganin consultant na Gynicology a gani idan ba wani cigaba sai ayi na hausan.
A Kuma ciki shekarar ne Alhaji Jafar ya koma Abuja da aiki inda arzikinsa ya Kara bunkasa gashi Allah yayi shi Mai sakakken hannu bashi da rowa ko kadan, in dai Yana gari to kofar gidansa Cike take da jama'a, sai Suma mutane suna tausaya Masa akan rashin haihuwa ga dukiyar dai Kama hankadota ake Amma ba magaji.
Ana haka Allah ya kawo ibtila'in ambaliyar ruwa a Adamawa state yankin MUBI.
Lokacin da gwamnati tarayya zata tura masu zuwa jaje sai sunan Alhaji Jafar ya shigo cikin tawagar vice president.
Sun jajje guraren da b'arnar ta afku anyi rubuce rubuce sosai da Alkawarin ka na gwamnatin tarayya sanan an bada kayan agaji ga wadanda iftila'in ya shafa a hanyarsu ta komawa ne Alhaji Jafar suna tattaunawa da Ardon filanin Yana Karayi Masa bayanin abinda ya faru.
Suka jiyo maganar mace daga bayansu lokacin ayarin sun danyi nisa dasu, da sauri Ardon ya juya Yama fadin "ho! 'yar nema Saida Kika biyoni Nan ko ma'u?"
Dariya tayi tana kare fuskarta da wani littafin Mai Dan fadi dake hannunta cikin shiga take ta Kamala Riga da siket na lace brown sai takalman ta da jaka da mayafinta farare.
Har kasa ta tsuguna tana gaishe da Baffan nata kafin ta Dan kalli gurin da Alhaji Jafar yake ta gaishe shi.
Baffan nata ta mikawa littafin hannunta tana fadar "Baffa ga project din nawa komai ya kammala".
Baki sake Alhaji Jafar ke kallonsu wannan 'yar yarinyar har ta Gama karatu ake nufi ko me"

AUREN HUCE HAUSHIN

WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH
PAGE NINE
____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu irin manyan jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai amale wane jaki. Allah ya Kara daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya"
Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda kin koma roko".
Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata. Uwar dakina murucin kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro yau ga xanzaro a bene" .
Ta Kara kwarara wata gudar.
Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce maza bude Mana muga karamar Arziki"
Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da zilai ne suke fama bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani kasheni komai na ciki classic ne.
Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun.
Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin zamane Allah ya hada arzikinsau.
Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana batsewa Kamar anyi Mata dole sai ta zaune a gurin.
Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah.
Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi gurin Zahra.
Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah wadaran naka ya lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke game kirki". Baki Hameedar ta murguda Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya ra'ayinta dole Nima sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu ruwana ba.
Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon Hameedar tayi "to rasa kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki".
Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa.
"Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da munafurci in dai yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa"
Tana Gama fada ta shige uwar daki.
A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra.
Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba kada Ammah taga Kamar Bata son auren ne ko wani Abu.
Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Ammah sallama Sajida ta rakata ita Haidar din Aunty Hasana.
Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan Sajida har tayi barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman yayi yawa sai ta dauko alqur'ani ta Fara karatu har Saida daya ta gota sannan tayi addu'a ta shafa.
Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata Kamar lokacin yake faruwa
************_
_
TUSHEN LABARIN
AZARE KATAGUM L.G.A
BAUCHI STATE
UNGUWAR FAMFON SHANU.
Yarinya ce 'yar kimanin sheKara goma Sha biyu haka, kyakykyawar gaske fara irin farin Nan Mai hade da Kamar golden yellow , idanunta dara-dara farare tas sai gashin kanta bakirkirin har gadon bayanta hancinta irin dogon Nan ne har baka bakinta Dan karami Mai dauke da 'yan jaja-jaja pink-pink din lebe, bazaka kirata doguwa sosai ba irin tsaka tsakiyar nan, jikin lublub Kamar Mai rayuwa a kasanshen sanyi komai nata Mai kyau ne Wanda idan ka kalleta saika Kara kallonta Dan Allah s.w.a yayi Mata sura Mai kyau na a gani a Kara kalla. Da sallama ta shigo cikin gida tana fadar "wash Allah Ammah wallahi na gaji wadannan littatafan sunyi nauyi da yawa inaga sai dai na kwafo time table kullum na ringa zuwa da Wanda zamuyi amfani dasu kawai". Ta fada tana kokarin Ciro jikar daga bayanta, dariya Ammah tayi tana fadin "ke dai anyi raguwa wallahi zahra ke Sam bakya da juriya jakar da Zaki Goya zuwa mota ma neman gagararki tajeyi".
Kwantawa tayi saman kujera tana fadin "Allah da nauyi dauki fa kiji".
Sulaiman ne ya shigo shima da tasa jakar a kafada Yana dariya.
"Kai Kuma dariyar me kake?"
Ammah ta tambaye shi.
Zahra ya nuna Yana cigaba da dariya. Baki ta zumbura tana dira kafa tana fadar "Allaha Ammah ki rabani da Ya sulaiman Kinga tundazu yake min dariya Kuma nace ya tayani daukar jikar ya Kiya".
"Wai Kai meye haka kazo kana ta dariya Kamar wani sabon kamu".
Jakarsa ya jefa kusa data Zahra kafin ya zauna Yana ba Ammah labari.
"Wato Ammah muna hanyar dawowa ne man motar ya Kare tunanin Malam Bala harya kawo mu gida man Bai Kare ba saboda yace ya biya gidan man yaga da layi idan yace zebi layin zamu Dade muna jiransa shine kawai ya taho, to muna zuwa wurin gidan sarki kawai man motar Nan ya Kare shine fa muka tako a kafa, ita Kuma gwanar iya son jiki ta wani shagwabe mini Wai na daukar Mata jaka na hada da tawa Kamar wani jaki, shine Dan tsabar rainin hankali Wai to na dauka zata karbi kudin gurin Abba ta biyani Kamar wani Dan dako".
Tsaki Ammah tayi tana hararar Sulaiman din "wannan shine abin dariyar Kuma wallahi kayi girman kwabo da meye amfanin hada babba da yaron ba saboda taimakon ba".
"A'a Ammah duka da wata biyar fa na girme mata, to Ina wani girma sa'anni muke ba gashi ajinmu daya ba da dai su Ya Sadiq ne su Aunty Janah, kuma fa duk su Hameeda kowa fa ya dauko tasa sai itace tafi kowa son jika za'a daukar Mata wa zata yiwa karatun ba kanta ba".
Ya fada Yana cire safarsa.
Fita Ammah tayi, ita Kuma Zahra ta shige bedroom din Ammah ba Wanda ya Kara bi takan sulaiman.wanka ta shiga tayi kafin taci abinci saboda Bata son ta makara a islamiyya Sam Bata son abinda ze taba lafiyar jikinta tunda a makarantar bokon suke sallar Azahar.
Lokacin data fito tana sanye da uniform din islamiyya da Jakarta tana kokarin shiga dakin Mama ta biya Hameeda ne taga Hameedar da wani Kaya a wata leda babba ta fito tana zumburar Baki.
"Ya Naga Baki shirya ba ko bazaki makarantar ba? Kinga fa yau zamu bada hadda".
Mama ce ta fito daga dakin tana hararar Zahra "to uwar kinibibi bazatan ba ki Kama hanya ki wuce, ko zata ai bazaku tafi tare ba ana gqninki waye ze kalleta na nuna Miki bana son kina shige Mata amman kin kasa ganewa, Haba yarinya sai kwawa"
Duk wanna maganar da Mama takeyi a hankali take fada Banda Zahrar da Hameedar ba Mai jin abinda take fada duk da Ammah na kofar kitchen dinsu Wanda yake kusa da bangaren na Mama.
Daki Mama ta nunawa Hameeda ta koma yayin da Zahra ta nufi Ammah tana fadin "Ammah na tafi"
"To Allah ya bada sa'a a maida hankali ki biyawa Mujiba ki tafi".
"To" ta amsa ta nufi waje da sauri.
Saida dama Ammah tana ankare da Mama Sam Bata son Zahra na mu'amala da Hameeda kwata-kwata sai Kuma Allah ya hada wata irin kauna tsakanin yaran salma ce Sam basa jituwa da Zahra da ita wata sakarai ce da zahra ko ruwa Mai dadi Salma bazata Bari Tasha a gidan ba, motsi ba motsi ba sai ta Fara fadin ai dai Nan ba gidanki bane ke 'yar riko ce.
Lokacin da Ammah taji maganar a bakin yarinyar tayi mamaki sosai Dan a lokacin wayonta Bai Kai ta iya banbance tsakanin Dan gida na ruko.
Da Ammah ta tsareta ta fada Mata wayace Zahra ba 'yar gidan bace sai tace " Mama ce ta fada tace min na duba Mana Naga ko kalar jiki mu ba iri daya bace mu daina tafiya ma da ita, Wai ta fimu kyau idan muna binta idan muka girma baza'a sure mu ba".
Kan Salma Ammah ta dafa tana fadin "itama 'yar uwarku ce kuyi zumunci da ita kinji" kai ta gyada alamar to.
Abin ya jima Yana baiwa Ammah mamaki Bata zaci haka a gurin mamar ba, tunda a zahiri ba komai a tsakaninsu sai mutunta juna duk da tasan sha'anin kishi ta ciki na ciki ne ta baka na baka.
Sai kusan magariba su zahra suka shigo hannunsu na sarkafe da juna ita da Hameedar, daga gurin Aiken ta wuce makarantar Amma Tasha bulalar makara.
Bayan sun Gama cin abincin dare ne suna hira a dakin Ammah Hameeda ta shigo ta gaishe da Ammah ta zauna sukaci gaba da hira lokacin Ammar tana dakin Abbansu ta Kai Masa abinci.
Lokacin data shigo dakin ya kacame sunata musu akan wani aiki da akayi musu yau a makaranta su matan suna ga yanda za'ayi shi Kuma Sulaiman Yana fadar ga yanda za'ayi, Ammar ce ta zauna tana fadin su kawo ta gani maths ne, Kuma duk hanyar da akabi za'a kaiga samun amsar Dan haka tace kowa yayi nasa yanda ya fashimta.
Har ta shiga bedroom dinta ta fito tana fadin "Na manta Abbanku yace na fada muku ranar Saturday zakiyi jarabawar share fagen shiga karamar secondary school ta kwamnatin tarayya, yace kuyi karatu duk Wanda baici ba baze saimasa ba Saida yaci gaba a makarantar da yake".
Murna suka farayi da gudu Hameeda ta nufi dakinsu Dan ta fadawa Mama.
******Alhaji Jafar Mai yadi haifaffan garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar fanfon shanu, su hudu ne iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da Nanna, kasancewar Babansu Malam Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji day na babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary.
Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai yawa ba daga gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar sakandire yake zaune a gida saidai dinkin hula da aikin hannu na riguna kusan dashi yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan Miya daaya kafawa Nanna jarinsu.
A hankali Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi Shawarar Nanna akan yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai ta dinga saka Masa albarka.
Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara bunkasa da taimakon wani uban gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo nasa kayan zeyi Masa kokarin shago kafin ya dawo.
Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da taimakon Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga cuku- cukun nema admission Nan University ta Bauchi cikin ikon Allah ya samu course din da ya nema Agricultural science.
Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka. Lokacin Yana shiga level 300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta fitar da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu.
Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma Nanna tayi tsalle ta dire ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba.
Wata ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400, Nanna ta aiki Amina kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso Mata na gaggawa.
Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta nufa tunda tasan shagon nasa.
Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana gaishe da Alhajin daya fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?"
Dariya tayi kyawawan hakoranta jerarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya ba komai fa Nanna ce ta Aiko ni".
Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya dauketa a mashin dinsa suka tafi gida.
Da dare Yana zaune a inda suke Hira yaga motar Alhaji Dauda ta tsaya a kofar gidansu da sauri ya tashi ya nufi inda yayi parking sai yaga harda bakon Alhajin Zakariyya suke tare, sun gaisa sosai kafin Alhaji Daudan ya fada Masa Amininsa Kuma Dan uwansa ne yaga Amina Yana so shine nace yazo muji da zafi -zafi akan bugi karfe.
Jafar yaji Dadi sosai zaifi kowa murna idan hakan ta kasance Dan ya yaba sosai da hankalinsa sosai.
Cikin gidan Jafar ya shiga ba jimawa ya fito Yana musu iso ciki sun gaisa da Nanna Alhaji Dauda ne yayiwa Nanna bayanin koma itama irin amsar Jafar ta fada idan tana so ba matsala ba inda aure baya Kai mace Nasarawa batayi nisa ba.
Cikin ikon Allah kuwa Amina taji Alhaji Zakariyya ya kwanta mata a rai Kuma zata iya aurensa duk da fada Mata Yana da Mata harda Yara biyu.
A cikin wata biyu akayi bikin Amina da Alhaji zakariyyan, Jafar yayi Mata komai da uba yake aka kaita can Nasarawa state cikin garin Akwanga.
Wannan kenan.
Haka Jafar yaci gaba da karatunsa har ya Gama ya dawo gida Yana jiran shiga camp.
Lokacin da saki post na tafiya service sunan Jafar ya Fado a cikin masu zuwa Jos yayi murna sosai ko banza Yana jiyo kamshin gida tunda suna makotan jahohi.
Bayan gama zaman camp wata makarantar 'yan Mata jeka ka dawo aka Kai Jafar, Baiyi wata biyu ba Allah ya hada shi da wata yarinya Rabi'a yaji yarinyar ta kwanta Masa tana Kuma da irin Qualities din da yake fatan Samu a gurin matarsa.
Zuwa lokacin gama service dinsu har magana tayi karfi inda iyaye suka shiga.
Wani gida Jafar ya saya kusa da gidansu ya gyara' ba'a dauki lokaci ba akayi bikinsa da Rabi'a suka tare a gidansu. Duk wata kulawarsa da soyayya ya tattara ya baiwa Rabi'a ba abinda ta nema ta rasa sai abinda baza'a rasa ba. Rabi'a irin matan Nan ne masu kissa kafin wani lokaci ta kanainaye zuciyar Nanna.
Kwanci tashi ba wahala a gurin Allah aurensu ya shekara Amma kalubaken da suka Fara fuskanta na Rashn zaman ciki a jikin Rabi'a kusan barinta uku. Ana haka Jafar ya samu aiki da ma'aikatar gona ta jihar Bauchi BARDA.
Cikin kankanin lokaci kofofin wadata suka budewa Jafar kafin shekara biyu ya gina gida Mai kyau sunje makka shida Nanna.
Nan
da Nan likafa tayi gaba Amma dai matsalar su na Nan ta rashin haihuwa.
Yayin da abin ma ya Fara damun Nanna har ta gaji tayi Masa magana akan ko maganin hausa za'a fata nemawa Rabi'a ne.
Amma sai ya nuna Mata ayi hakuri tunda tana ganin consultant na Gynicology a gani idan ba wani cigaba sai ayi na hausan.
A Kuma ciki shekarar ne Alhaji Jafar ya koma Abuja da aiki inda arzikinsa ya Kara bunkasa gashi Allah yayi shi Mai sakakken hannu bashi da rowa ko kadan, in dai Yana gari to kofar gidansa Cike take da jama'a, sai Suma mutane suna tausaya Masa akan rashin haihuwa ga dukiyar dai Kama hankadota ake Amma ba magaji.
Ana haka Allah ya kawo ibtila'in ambaliyar ruwa a Adamawa state yankin MUBI.
Lokacin da gwamnati tarayya zata tura masu zuwa jaje sai sunan Alhaji Jafar ya shigo cikin tawagar vice president.
Sun jajje guraren da b'arnar ta afku anyi rubuce rubuce sosai da Alkawarin ka na gwamnatin tarayya sanan an bada kayan agaji ga wadanda iftila'in ya shafa a hanyarsu ta komawa ne Alhaji Jafar suna tattaunawa da Ardon filanin Yana Karayi Masa bayanin abinda ya faru.
Suka jiyo maganar mace daga bayansu lokacin ayarin sun danyi nisa dasu, da sauri Ardon ya juya Yama fadin "ho! 'yar nema Saida Kika biyoni Nan ko ma'u?"
Dariya tayi tana kare fuskarta da wani littafin Mai Dan fadi dake hannunta cikin shiga take ta Kamala Riga da siket na lace brown sai takalman ta da jaka da mayafinta farare.
Har kasa ta tsuguna tana gaishe da Baffan nata kafin ta Dan kalli gurin da Alhaji Jafar yake ta gaishe shi.
Baffan nata ta mikawa littafin hannunta tana fadar "Baffa ga project din nawa komai ya kammala".
Baki sake Alhaji Jafar ke kallonsu wannan 'yar yarinyar har ta Gama karatu ake nufi ko me"

AUREN HUCE HAUSHIN

PEGE TEN
Story
Written
By
MAMAN FATIMAH
******Jujjuya littafin project din Ardo yayi, sai Kuma ya mikawa Alhaji Jafar Yana fadin "Duba ka gani Yallabai ni tunda ba ganewa zanyi ba,naji Dadi da Allah yasa aka Gama wannan karatun ba domin na saka auduga na toshe kunnuwa naba da ba'ayi karatun Nan ba, tunda Wanda yaso auren nata yace in dai zatayi karatun Nan shi ya fasa, shi Kuma Dan uwanta na wajen kanena yace karatu Babu gashi tunda tana ganewa Kuma tana so, kaga yanzu duk gurin nan namu ita me yiwa mutane Allura".
Kallonta Alhaji Jafar ya karayi,sannan ya kalli Ardon Yana fadin.
"Yaushe ta Fara karatun ne na ganta karama amma har ta hada diploma?"
Gyara tsayuwa Ardon yayi Yana fadin "wallahi am tun tana aji hudu na furamare Dan uwanta ta kaita aji daya na sakandire tunda yayi wani zuwa suka zauna da kannen nasa yaga tana da kokari shine yace Mata idan ta Gama makarantar tana son taci gaba da karatu, shine tace Masa tana son ta Zama malamar asibiti, to tunda sukayi haka ya kudurci aniyar tsayawa akan karatunta shi yasa da akayi Mata chaaaa akan maganar aure yace Bai Hana ayi maganar aure ba. Amma ya Dora sharadin saidai idan mijin ze barta tayi karatu abinda ya gagara kenan aka fasa Amma duk yan uwanta anyi musu".
"Masha Allah. Allah ya Sanya Albarka, haka ake so a rinka barin Yara Mata suna karatu barin ma na bangaren lafiyar da malaman makaranta, yanzu ba cewa kayi ita ke yiwa mutane allura ba da sauran abubuwa? To da batayi karatun ba da basai an tafi wai gurin an nema ba? Ba komai in Sha Allah zatayi auren ta Kamar kowa".
Ardo ya amsa da "Allahumma Amin".
Ma'un Alhajin ya kalla "Asma'u kin amince na tafi da project din naki na duba a hankali in yasa said dawo Miki dashi".
Kai ta gyada alamar Eh.
Sunyi sallama da Ardo tawagarsu suka wuce zuwa Yola inda zasu bi jirgi zuwa Abuja.
Wannan shine silar haduwar Alhaji Jafar da Ammah, ya koma maida project da Kuma kafa gwanatinsa cikin ikon Allah suka yarjewa juna.
Lokacin da magana tayi karfi Rabi'a taso tada hankalinta saida Nanna ta taushe ta da kalamai masu kwantar da hankali.
Cikin kankanin lokaci akayi bikinsu. Amarya ta tare cikin ikon Allah zaman Rabi'a da Asma'u ya kasance Zama Mai tsabta.
Wata uku da auren Asma'u ciki ya bullo duk masoyin Alhaji Jafar ya Taya shi murna sosai a lokacin ne Alhaji Jafar ya biyawa Rabi'a makka kusan abinda ya kwantar Mata da hankali kenan Dan ya fada Mata idan take tayi addu'a sosai akan matsalar ta.
A haka rayuwa ta dunga gurguwa har cikin ya Isa haihuwa Ardo dasu Inna maimuna sun so Ma'un to koma gida zaman haihuwa Amma Nanna ta Hana tace meye amfanin ta ita in dai sai Asma'u ta koma gida.
Cikin ikon Allah a wani dare nakuda ta tasowa Asma'u lokacin Alhajin Yana nan, Nan da Nan suka nufi asibiti wurin karfe biyu da rabi Amma kafin hudu Allah ya dauketa lafiya ta haifi takwaye mace da namiji.
Murna gurin wannan iyalin ba magana ranar suna yaran aka bar musu sunan su sai dai su Hassan da Hasana aka daka musu.
Kullum yaran suna tsakanin Rabi'a da Asma'u suka rainon 'ya'yansu. Lokacin da aka yayesu a lokacin Allah ya baiwa Rabi'a ciki itama ba'ayi wata biyu ba Asma'u ma ta Fara laulayi, cikin ikon Allah cikin Rabi'a ya zauna kusan lokaci daya suka haihu Rabi'a haifi Hamza yayin da Asma'u ta haifi Abdul Hakeem.
Bayan haihwar Hamza Rabi'a Bata Kara haihuwa ba Saida Asma'u tayi maza biyu sanan Rabi'a ta haifi mace Murjanatu, bayan Murjanatu Rabi'a ta Kara haihuwar Salma sai auta Hameeda ita Kuma Asma'u ta haifi Sulaiman sai auta Musaddiq, zuwa lokacin sunansu ya bace yayin da ake gadawa Hajiya Rabi'a Mama wasu na waje suce Hajiya Mama, Hajiya Asma'u Kuma Ammah.
WACECE FATIMAH ZAHRA?
'ya daya tilo ga kanin Ammah shaqiqi Muhammad Sani. Mahaifiyar Zahra Najwa Balarabiyar Jordan ce sun hadu da Muhammad Sani ne lokacin da yaje karatu kasar da farko mutunci suke da Najwa sai daga baya ya juye ya Zama soyayya har Allah ya nufesu da aure da taimakon wani malaminsu Dan kano Dan kusan ta bagarensa su Ardo wanda suke Kira Baffa ya Sani ya Kuma amince da Malam Muhammad Kabir ya Zama waliyyin Muhammad Sani a can.
Lokacin da Muhammad Sani ya Gama karatu ya zauna a can yayi aiki kusan shekara biyu daga baya ya tattaro nasu ya nasu suka dawo Nigeria, lokacin Najwa nada cikin Zahra wata bakwai a lokacin Kuma Ammah na goyon Sulaiman Mama na goyon Hameeda.
A Jimeta Muhammad Sani ya sayi gida saidai suje Mubi kawai suga iyayensa,ba dadewa Najwa ta haifi 'yarta Zahra wadda taci sunan mutum biyu mahaifiyar Najwa da Mahaifiyar su Ammah.
Haihuwar Zahra ba dadewa Muhammad sani ya Sami aiki a Abuja karkashi minstary of internal affairs da taimakon Alhaji Jafar.
Zahra nada wata biyar wani cikin ya bullo a jikin Najwa Mai wata irin masifar laulayi, Wanda ya tilasta Ammah ta dauke Zahra daga bakin nono.
Lokacin da komai da dai dai ta a gurin aikin nasa ya dauki Najwa suka koma Abuja.
Saida watan haihuwarta ya Kama ya kaita Mubi shi Kuma ya koma Abuja.
Lokacin data haihuwa iyayenta sunzo Nigeria da kanwarta Nawwara a Karon na biyu Mahaifiyar ta taso tafiya da Zahra Ammah ta dunga magiyar abar Mata ita harda kukanta.
Lokacin da suka Gama wanka Muhammad sani yazo ya tafi dasu tafiyar da har abada Basu dawo ba a hanya sukayi hadari sun bar Jos Basu karasa Abuja ba.
Yan uwa da iyaye sun shiga cikin tashin hankali marar misaltuwa Ammah tayi Kika Kamar ba gobe,ta rasa Dan uwanta shakiki, ba karamin Kai ruwa Rana akayi ba kafin Ummee kakar Zahra ta hakura ta barwa Ammah Zahrar.
Tunda daga lokacin Ammah ke baiwa Zahra wata irin kulawa ta musamman sai Kuma shima Mai gidan ya kwallafa ransa akan soyayyar yarinyar abinda ya haddasa tsana Mai tsanani tsakanin Mama da zahra inda ita mamar ke ganin Kamar nema ne yasa Alhaji ke kaunar Zahra, tana ganin idan Dan tana 'ya mace ne karama ai itama tana da nata kananan 'ya'yan mata Amma baya nuna kulawa akasu Kamar Zahra ko Dan tafisu kyaune tunda Babu inda ta baro uwarta.
Wannan kenan.
Ranar da za'ayi jarabawar share fagen shiga karamar secondary ta gwamnatin tarayya tun sassafe zu Zahra suka shirya ita da Sulaiman da Hameeda da Salma duk da Salma ta girmesu Amma yawan yi Mata repeating yasa suka taddo ta.
Har sun shiga mota Bala direba na niyyar shiga Zahra ta bude ta fito da sauri ta nufi cikin gida Sulaiman Yana kiranta tayi banza dashi ta shige da gudu ta karasa dakin Ammah tana fadin "Ammah na manta kayana da Ya Hassan ya kawo min har zamu tafi na tuna".
Daga toilet Ammar ta fito ta nufi bedside locker ta janyo ta mikowa Zahra ledar tare da fadar "Maza kada ku makara mana".
Kai Zahra ta gyada kafin tace "Ammah ki kara yi Mana addu'a Dan Allah Ina son naci jarabawar saboda Abbana yace idan naci makarantar zemin kyautar wani Abu"
"To naji maza Allah ya bada sa'a"
A kofa suka hadu da Sulaiman ya biyo ta tana fadin "Na rantsa da Allah zamu tafi mu barki ba Dan Abba ya fito ba da wallahi sai dai ki fito kiga bama gidan".
Kafin ya saki labulen ya juya Zahra ta Kai kofar da zata kaika compound din gidan.
Masha Allah anyi jarabawa an Gama sai jiran sakamako.
A haka sukaci Baga da zuwa makaranta har suka Zama common enterence a matakin jaha.
Lokacin da suka dawo zaman gida lokacin ne Alhaji Jafar da kansa ya yiwa Zahra passport da visa Saida ya Gama komai sannan ya fadawa su Ammah da Mama. Godiya Ammah ta shiga jerawa Mai gidan nasu,yayin da Mama tayi shiru Kamar bazatayi magana ba sai Kuma tace "yanzu Yallabai da kanka zaka rakata ai da Koda Hasana ko Hassan ka hadasu zasu kaita ko Kuma a fadawa cen kakanninta su turo a tafi da ita ai cacar kudin Kamar yayi yawa".
Daga Ammah har Alhaji Jafar din kallon Mamar suke ita dai Ammah shiru tayi yayin da Alhajin yace.
Saboda ban San darajar 'ya'ya ba zan hada Yara a tafiyar uwa duniya daga Nan har Jordan na kwanta a gida hanakli kwance ko?"
Kai ta gaigice tare da fadin "gani makudan kudi za'a kashe".
Wani kallo yayi Mata "kada ki kawo b'araka Rabi'a duk yaran dake gabana daya na daukesu yada zan yiwa abinda na Haifa haka zan yiwa marainiyar Allah. Da Kuma kike maganar cacar kudi idan zan jera shekara Ina Kai zahra Jordan kullum ba abinda ze girgaiza a cikin abinda na mallaka".
Ku tashi kuje.
Lokacin da zasu tafi anyi Mata tsara sosai Dan Nanna ma kilishi tasa aka yi Mai yawa na tsaraba.
Har kano su Ammah da yara sukayi musu rakiya.
Lokacin da sukaje Jordan din ba karamar murna kakanninta zukayi ba Dan Babu zato suka gansu, sun Kuma Kara yabawa da cika Alkawarin Alhaji Jafar Dan da kansa yayi musu Alkawarin ze kawo musu Zahra Dan ko a waya Bai fada musu zuwansu ba,sai address dai daya taba tambaya can wani lokaci.
A ranar Zahra taga zallar soyayya a gurin dangin Najwa Dan gidan cika yayi da 'yan uwa aka dasa sabon kukan rashin Najwar da kyar Abbie da Abbanta suka dinga Basu hakuri Dan ma Alhaji Jafar ba larabcin yakeji sosai ba saidai Wanda suke Jin turanci suka ringa magana dasu.
Lokacin da Alhaji Jafar din ze tafi masukin daya Kama a hotel Abbie hanawa yayi duk yanda yaso zillewa kin yarda yayi dole ya amince aka sauke shi a wani part dake kusa da nasa Ummee din, Dan ba karya dukiya dai Kam akwaita Dan shi kanshi Alhajin yayi mamakin yanda ya riskesu Bai taba kawo haka suke ba lallai yasan hadin Allah ne kawai da suka bawa Muhammad sani auren 'yarsu Dan tazarar Mai nisa ce a tsakanin su.
Kwanan Alhaji Jafar bakwai ya wuce Umara yayin da Ummee tayi Masa Alkawarin zasu hadu a Saudiyyar tunda zata kawo Zahrar Nan gurin iyayenta da 'yan uwa su ganta a cikin garin Madinatul Munawwara.
Satinsa daya da zuwa Suma su Zahrar sukazo Saudiyyar ita da Ummeen da Aunty Nawwara.
A Nan ma Saudiyyar Zahra taga gata iya gata Dan kowa Nan Nan yake da ita, Dan kanwar Ummee Hanifa sosai ta kafe sai dai a bar Mata Zahra ta tafi da ita Istanbul inda take aure Wai Bata yarda da zaman Nigeria ba.
Ankai ruwa Rana da ita kafin ta hakura Dan da gaske Alhaji Jafar ya bude Mata aiki Dan cewa yayi idan irin haka za'a ringa yi bazai Kara bawo musu ita ba saidai duk Mai son ganinta taje ya ganota Kamar yanda Ummee keyi, hakuri aka ringa bashi.
Saida aka Kai Zahra makka suyi kayi umara sannan suka fara Shirin baro kasar.l Sayyaya dai Zahra ta shata Dan wasu kayan sai a awon cargo akayo musu su.
Sarkar gwal da warwaro zobe kuwa kirar Saudiyya da Dubai zuwa kirar Bahrain sun Kai kala goma duk dai dai size din ta sai na Ammah biyu na Hasana ma biyu shi kanshi Alhajin anyone mass goma Sha Tara ta Arziki.
Ranar da zasu dawo Zahra Tasha kuka haka kakarta Ummee,har jidda sukayo musu rakiya Basu suka tafi ba sai da jirgin su Zahra ya tashi a sararin subahanahu wata'ala.
Saukar safe sukayi anan suka samu Bala direban Alhaji Dan Bai fadawa kowa sun taho ba sai Balan kawai, sau da yawa idan ya fada gashi Nan a hanya hankalin Nanna baya kwanciya har sai ya iso.
Lokacin da suka shigo harabar gidan suna tsayawa Zahra to garzaya cikin gida tana fadin "Ammah!!! mun dawo".
Da gudu Hameeda ta fito daga part dinsu, rungume juna sukayi suna ta tsallen murna Sai jikin zahra Hameedar ke shafawa gani take kamar canza Mata Zahrar akayi.
Da sauri Ammah ta fito tana "fadin wa nake gani ne haka Kamar bakin saudiyya zuwa ba notice?"
Alhajin ne ya Bata amsa.
"Surprised din ki mukayi ko Zahra na?.
Kai ta gyada masa.
Kayansu ne su Bala da Mai gadi suka Fara shigowa dasu kafin Alhajin ya nufi part dinsa na cikin gidan yayin da Ammah ta rufa Masa baya.
Har yayi wanka ya shirya Mama Bata shigo ba, har ya tambayar Ammah yayi Ina Rabi'a ? Tace Masa tana ciki watakila ko barci take.
Kusan kwana su Zahra sukayi tana baiwa Hameeda labarin abinda ta gani da inda sukaje a Jordan da saudiyya, wurin karfe biyu Ammah ta tashi zatayi nafila ta jiyo su suna Hira a dayan bed room dinta lokacin wuri biyu da rabi na dare, leko tace su kwanta basu san dare yayi sosai ba.
Washe gari an baje tsarabar Zahra an baiwa kowa dai dai gwargwado.
Amman tsarabar Hameeda daban take Dan har sarka Saida ta baiwa Hameedar.
Basifi sati biyu da dawowa ba jarabarsu ta fito ta Federal inda Zahra ta samu F.G.G.C KAZAURE yayin da Sulaiman ya samu F.G.C DAURA, Hameeda F.G.C AZARE. Salma ce kawai bata samu ba a cikinsu.
Sunyi murna Kuma sunyi bakin cikin rashin samun makaranta daya duk an watsa su Abban Kuma da ya Hassan sunce kowa ya tafi inda ya samu, ita Hameeda Bata da damuwa tana gida, su Kuma duka 'ya'yan Ammah duk sun fita waje danma hanyarsu daya sai an aje Zahra a karasa da Sulaiman.
Ranar da zasu tafi sun Sha kuka haka suka dauko hanya malam Bala da Ya Hassan ne suka kaisu.
Lokacin da aka Kai Zahra an tashi daga aji, wasu Yara House master dinsu ya kira da wata prefect yasa su Kai Zahra room din 'yan j.s one.
A cikin yaran da suka Taya Zahra daukar kayane wata yarinya tace Mata "sister kizo ki zauna a kwana ta tunda ni daya ce saman gadona ba kowa".
Kai kawai zahra ta gyada Mata tana ta sauke ajiyar zuciya.
Ita ta taimkawa Zahra ta shirya komai a locker dinta, Saida ta Bari zahra ta HUCE daga kukan da tsaha sannan tace Mata "ni sunana Sajida Musa ni 'yar kano ce unguwar Gwammaja kefa ya sunanki?".
Nan Zahra ta fada Mata komai nata tun daga Nan suke tare har suka Zama aminai komai nasu ya Zama daya banbanci su kawai Sajida na A Zahra na C.
Haka sukaci gaba da rayuwa a makarantar gasu Kuma Yara masu kwazo barin zahra ga kyau ga ilimi Nan da Nan tayi suna a makarantar kafin hutu tayi popular sosai a makarantar, idan kace 'yar larabawa kowa ya santa ba Kuma Dan Babu irin jiinsin nata ba A'a farin jini ne daga Allah.
Lokacin da akayi hutu Zahra ba karamar murna tayi ba Kuma cikin ikon Allah da wuri malam Bala yazo lokacin har ya dauko Sulaiman.
Bayan Azahar kadan suka shiga Azare sunyi murna sosai da ganin mutanen gida Dan Sulaiman har da kuka, Nan su Hameeda suka saka gaba suna tsokana.
Haka suka cigaba da karatunsu cikin amincin Allah, lokacin da sukazo hutun third term ne akayi auren Aunty Hasana aka kaita Jos, Ya Hassan Kuma Daman Yana karatunsa a Rasha.
Kowa inda yake yacigaba da karatunsa Salmace Allah ya taikata ta samu shiga FGC AZAREN itama a ss1.
A haka aka dunga juyawa har suka Gama secondary School dinsu suka dawo gida.
Dawowarsu ba dadewa Allah ya yiwa Nanna rasuwa rashin daya taba Abbansu sosai.
Dan ya Dade Yana fama da damuwa tunda a rayuwa da ita ya tashi baisan dadin uba namiji ba itace komai nasa.
Ganin abin nasa Yana neman yayi yawa yasa Abokinsa bakon malamin daya sauka Nan daura gidan Nanna da almajiransa dududu Bai zaifi sa'an Alhajin ba malam Bubar ya dukufa yi Masa addu'a tare da saka Yara kanana suna Masa addu'a, cikin ikon Allah sai komai ya daidaita.
Ranar wata laraba zahra ta shirya zata raka Hameeda duba Qawarta meenal gidan Dan majalissarsu Mai wakiltar su majalissar Jaha, wani material ta saka Mai ruwan sararin samaniya yayi matukar karbar jikinta haka dinki ma ya Dace da material din, simple makeup tayi ta saka turarenta Amber oud new edition na kamfanin Al haramaini.
Tunda ta fito Mama ke Mata wani irin kallo Wanda har saida ta rinqa Jin ta takura kafin Hameedar ta fito.
A kasa suka taka suna Hira har sulaje gidan,sun Dan jima suna Hira da marara lafiyar kasancewar breast lump ne aka cire Mata ba wani serious case bane.
Lokacin da zasu tafi suka Kara komawa gurin mamanta sukayi Mata sallama suna zaune ne da a falonta kafin meenal din tayi Mata magana ta fito. Wani handsome guy ne ya shigo falon da sallama ya Dan jefa car key dinsa sama, kana ganinsa kasan hutu ya Kama jikinsa.
Ciki ya shigo lokacin da Suke amsa masa sallamarsa kujera two seaters ya zauna a Kai wadda ke facing dinsu Hameedar.
Gaishe shi sukayi su Duke ya amsa Yana cewa "Hameeda daman kina Nan na Dade ban ganki ba gaskiya Ina ga tun kafin na tafi Colombia fa".
Dan rausayar da Kai tayi tana fadar "wallahi Kam Ya Sahal an jima Kam kune dai bakwa ganuwa Kuna uwa duniya kunyi shiru Kum barmu da zafin Kasarmu".
Ta fada tana dariya.
Dai dai lokacin mommyn su meenal din ta fito kallon Sahal tayi tana fadar Kai Kuma haka mukayi da Kai?"
Kaisa ya Dan Sosa da key din hannunsa Yana fadi "Iam so sorry Mom kada ki damu yanzu zanje na kawo Miki in Sha Allah."
Ya fada Yana mikewa da nufin tafiya Meenal tayi tsagal tana fadin "Dan Allah Ya Sahal ka tafi dasu tunda cikin garin kayi.
Suka yiwa mommy sallama da godiya suka fito da leda Mai Dan girma a hannun Meenal wadda mommyn ta Basu.
Har kofar gida ya kawosu suna tsayawa ya kalli Hameeda Yana fadar "Dan Allah ki bani aron sister din take Mana Kona ten minutes ne Mana".
Dan murmushi tayi tana fadar.
"Ka Fara yiwa Abban mu magana dai haka Naga anayi"
Ita dai Zahra ciki ta wuce Dan Kamar a kan.kaya take duk ya takura Mata da wani irin kallo har a cikin mota ma saita mirror yayi sitinta tunda Hameeda ce ta zauna a seat din gaba tana Masa Hira Amman gaba daya hankalinsa yana kan Zahra.
Ita dai zahra Bata San yanda suka Kare ba taga dai Lokacin da Hameedar ta shigo ta wuce dakin su.
Bayan kwana biyu da zuwa gidansu Meenal da yamma su zahra sun tafi islamiyya ne baki sukazo gurin Alhaji Jafar, ya sansu farin sani daya kanin Dan majalissar su ne dayan Kuma kanin Babansu.
Yayi mamakin ganinsu Saida suka gaisa ne suka bijiro da abinda ya kawo su na yiwa yaron gurin Dan uwansu Sahal kidiba yaga yarinyar gurinsa Yana so. Shine mahaifansa ya turosu ya gabatar da maganar Yana neman izininsa na Fara zuwa gurinta Shira.
Alhajin yaji Dadi sosai na yanda suka zo suka memi izininsa duk da Daman sharadinsa kenan, ya Kuma nemi Jin wacece daga cikin yaran suka gada Masa zahra ce, nan ya amince musu da addu'ar Allah ya hada kawunan su.
Tun daga lokacin Sahal ya Fara zuwa gurin Zahra cikin ikon Allah tayi na'am dashi Basu Dade sosai ba sukayi wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya tashi a unguwar yasan irin soyayyar da sahal yakewa zahra kusan Kullum da yamma Yana nan makale da ita, a haka har manya suka shiga maganar aka tsaida lokaci wata shida inda zasu tafi Colombia inda yake hada masters dinsa ita kuma zata Fara nata degree din.
Anyi lefe na garari Wanda ya dauki Baki fiye da tunanin Mai tunani, an kashe kudi Kamar ba'a San zafinsu ba.
Lokacin da bikin ya rage baifi saura wata biyu ba sai lamarin ya Fara canzawa kwata -kwata Sahal ya rage zuwa gurin Zahra haka ma sai a kwana a wuni Bai kirata ba, duk wani zazzari da yake na bikin su events din da yake ta faman damun zahra da maganar duk ya daina Kai tafi-tafi sai ayi kwana uku hudu har sati Bai kirata ba, da farkon abin tana kiransa taji ko lafiya a yanayin yanda yake amsa Mata wayar saita hakura da Kiran nasa, tun Ammah na zuba ido har ta samu Zahra a wani dare ta tsareta da tambayar ko wani Abu ya hadata da Sahal ne? Ta Bata tabbacin ba abinda ya hadasu sai dai ta fada Mata yanda suka ringa yi dashi a kwanaki idan ta Kira shi.
Addu'a Ammah ta Bata tace ta ringa yi itama zataci gaba da yi, Mata sannan ta umarceta da kada ta Kara kiransa a wayar ta zuba ido kawai.
Duk abinda Ammah take na shirye-shiryen Baki Bata fasa ba, tayi waya mutanan Jordan ma sunce suna Nan tafe Amma a daure a turo Zahra Kamar saura wata data bikin.
Ba'afi sati daya da waya da kakanninta na uwa ba sakon kayan dakinta ya sauka Nigeria daga Istanbul kayan da suka gigita Mama Dan ba kayan Wasa bane set din gado har hudu kujeru set uku bayan electronics kuwa wasu har ba'a San amfaninsu ba sai dai idan an duba manual din.
Alhaji Jafar yayi fada Kamar ya Ari Baki lokacin daya Kira Abbie akan danme zasuyi Masa haka toshi meye amfaninsa da bazasu Bari yayi Mata kayan dakin ba.
Hakuri Abbien ya shiga bashi akan su basuyi Dan su Bata Masa raiba, sunga abinda ya kamata suyiwa diyar Najwa kenan.
Ammah da Mama Alhaji Jafar ya Kira ya fada musu tunda an Riga an yiwa zahra kayan dakin da duk abinda ya kamata to ga fifty million Nan ya baiwa Zahra idan komai ya nutsa saita Fara business na abinda take son sayarwa sannan ya Bata shanu biyar.
Kuka Ammah ta saka saboda Dadi ta rasa bakin da zatayi Masa godiya, yanda take dawainya da wannan marainiyar Allah Bai taba gajiyawa ba.
Mama ce ta Ari bakinta tana ta yiwa Abban godiya da saka Albarka sai faman dariya tace bakinta yaki rufuwa, tun Ammah na ganin dariyar farin ciki ce har ta Fara wani tunani na daban, Nan da Nan ta Kori shaidan akan abinda zuciya ke sawwala Mata.
Lokaci na Kara tafiya daukewar ma'amala na Kara yawaita a tsakanin Sahal da zahra, yanzu ta Kai kwata-kwata sun daina waya dashi, ana saura kwana talatin da hudu a Fara biki Wanda yayi daidai da saura kwana uku zahra da Hameeda da Abdul Hakeem su tafi Istanbul. Dan direct gurin kanwar Ummeen Hanifa zasu tafi daga baya su Ummeen sun samesu a can, idan an Gama komai su rankato Nigeria Dan da gaske Ummee ta shiryawa bikin sosai.
Washe gari, tunda gari ya waje Mama ke Kai kawo tsakar gida duk da ba aikinta bane ba Kuma halayyarta bane hakan. Yayin da a bangaren Ammah ta rasa me yake Mata Dadi duk kasala ta baibayeta jinta take Kamar ma zazzabi na neman rufata...

AUREN HUCE HAUSHIN

PEGE TEN
Story
Written
By
MAMAN FATIMAH
******Jujjuya littafin project din Ardo yayi, sai Kuma ya mikawa Alhaji Jafar Yana fadin "Duba ka gani Yallabai ni tunda ba ganewa zanyi ba,naji Dadi da Allah yasa aka Gama wannan karatun ba domin na saka auduga na toshe kunnuwa naba da ba'ayi karatun Nan ba, tunda Wanda yaso auren nata yace in dai zatayi karatun Nan shi ya fasa, shi Kuma Dan uwanta na wajen kanena yace karatu Babu gashi tunda tana ganewa Kuma tana so, kaga yanzu duk gurin nan namu ita me yiwa mutane Allura".
Kallonta Alhaji Jafar ya karayi,sannan ya kalli Ardon Yana fadin.
"Yaushe ta Fara karatun ne na ganta karama amma har ta hada diploma?"
Gyara tsayuwa Ardon yayi Yana fadin "wallahi am tun tana aji hudu na furamare Dan uwanta ta kaita aji daya na sakandire tunda yayi wani zuwa suka zauna da kannen nasa yaga tana da kokari shine yace Mata idan ta Gama makarantar tana son taci gaba da karatu, shine tace Masa tana son ta Zama malamar asibiti, to tunda sukayi haka ya kudurci aniyar tsayawa akan karatunta shi yasa da akayi Mata chaaaa akan maganar aure yace Bai Hana ayi maganar aure ba. Amma ya Dora sharadin saidai idan mijin ze barta tayi karatu abinda ya gagara kenan aka fasa Amma duk yan uwanta anyi musu".
"Masha Allah. Allah ya Sanya Albarka, haka ake so a rinka barin Yara Mata suna karatu barin ma na bangaren lafiyar da malaman makaranta, yanzu ba cewa kayi ita ke yiwa mutane allura ba da sauran abubuwa? To da batayi karatun ba da basai an tafi wai gurin an nema ba? Ba komai in Sha Allah zatayi auren ta Kamar kowa".
Ardo ya amsa da "Allahumma Amin".
Ma'un Alhajin ya kalla "Asma'u kin amince na tafi da project din naki na duba a hankali in yasa said dawo Miki dashi".
Kai ta gyada alamar Eh.
Sunyi sallama da Ardo tawagarsu suka wuce zuwa Yola inda zasu bi jirgi zuwa Abuja.
Wannan shine silar haduwar Alhaji Jafar da Ammah, ya koma maida project da Kuma kafa gwanatinsa cikin ikon Allah suka yarjewa juna.
Lokacin da magana tayi karfi Rabi'a taso tada hankalinta saida Nanna ta taushe ta da kalamai masu kwantar da hankali.
Cikin kankanin lokaci akayi bikinsu. Amarya ta tare cikin ikon Allah zaman Rabi'a da Asma'u ya kasance Zama Mai tsabta.
Wata uku da auren Asma'u ciki ya bullo duk masoyin Alhaji Jafar ya Taya shi murna sosai a lokacin ne Alhaji Jafar ya biyawa Rabi'a makka kusan abinda ya kwantar Mata da hankali kenan Dan ya fada Mata idan take tayi addu'a sosai akan matsalar ta.
A haka rayuwa ta dunga gurguwa har cikin ya Isa haihuwa Ardo dasu Inna maimuna sun so Ma'un to koma gida zaman haihuwa Amma Nanna ta Hana tace meye amfanin ta ita in dai sai Asma'u ta koma gida.
Cikin ikon Allah a wani dare nakuda ta tasowa Asma'u lokacin Alhajin Yana nan, Nan da Nan suka nufi asibiti wurin karfe biyu da rabi Amma kafin hudu Allah ya dauketa lafiya ta haifi takwaye mace da namiji.
Murna gurin wannan iyalin ba magana ranar suna yaran aka bar musu sunan su sai dai su Hassan da Hasana aka daka musu.
Kullum yaran suna tsakanin Rabi'a da Asma'u suka rainon 'ya'yansu. Lokacin da aka yayesu a lokacin Allah ya baiwa Rabi'a ciki itama ba'ayi wata biyu ba Asma'u ma ta Fara laulayi, cikin ikon Allah cikin Rabi'a ya zauna kusan lokaci daya suka haihu Rabi'a haifi Hamza yayin da Asma'u ta haifi Abdul Hakeem.
Bayan haihwar Hamza Rabi'a Bata Kara haihuwa ba Saida Asma'u tayi maza biyu sanan Rabi'a ta haifi mace Murjanatu, bayan Murjanatu Rabi'a ta Kara haihuwar Salma sai auta Hameeda ita Kuma Asma'u ta haifi Sulaiman sai auta Musaddiq, zuwa lokacin sunansu ya bace yayin da ake gadawa Hajiya Rabi'a Mama wasu na waje suce Hajiya Mama, Hajiya Asma'u Kuma Ammah.
WACECE FATIMAH ZAHRA?
'ya daya tilo ga kanin Ammah shaqiqi Muhammad Sani. Mahaifiyar Zahra Najwa Balarabiyar Jordan ce sun hadu da Muhammad Sani ne lokacin da yaje karatu kasar da farko mutunci suke da Najwa sai daga baya ya juye ya Zama soyayya har Allah ya nufesu da aure da taimakon wani malaminsu Dan kano Dan kusan ta bagarensa su Ardo wanda suke Kira Baffa ya Sani ya Kuma amince da Malam Muhammad Kabir ya Zama waliyyin Muhammad Sani a can.
Lokacin da Muhammad Sani ya Gama karatu ya zauna a can yayi aiki kusan shekara biyu daga baya ya tattaro nasu ya nasu suka dawo Nigeria, lokacin Najwa nada cikin Zahra wata bakwai a lokacin Kuma Ammah na goyon Sulaiman Mama na goyon Hameeda.
A Jimeta Muhammad Sani ya sayi gida saidai suje Mubi kawai suga iyayensa,ba dadewa Najwa ta haifi 'yarta Zahra wadda taci sunan mutum biyu mahaifiyar Najwa da Mahaifiyar su Ammah.
Haihuwar Zahra ba dadewa Muhammad sani ya Sami aiki a Abuja karkashi minstary of internal affairs da taimakon Alhaji Jafar.
Zahra nada wata biyar wani cikin ya bullo a jikin Najwa Mai wata irin masifar laulayi, Wanda ya tilasta Ammah ta dauke Zahra daga bakin nono.
Lokacin da komai da dai dai ta a gurin aikin nasa ya dauki Najwa suka koma Abuja.
Saida watan haihuwarta ya Kama ya kaita Mubi shi Kuma ya koma Abuja.
Lokacin data haihuwa iyayenta sunzo Nigeria da kanwarta Nawwara a Karon na biyu Mahaifiyar ta taso tafiya da Zahra Ammah ta dunga magiyar abar Mata ita harda kukanta.
Lokacin da suka Gama wanka Muhammad sani yazo ya tafi dasu tafiyar da har abada Basu dawo ba a hanya sukayi hadari sun bar Jos Basu karasa Abuja ba.
Yan uwa da iyaye sun shiga cikin tashin hankali marar misaltuwa Ammah tayi Kika Kamar ba gobe,ta rasa Dan uwanta shakiki, ba karamin Kai ruwa Rana akayi ba kafin Ummee kakar Zahra ta hakura ta barwa Ammah Zahrar.
Tunda daga lokacin Ammah ke baiwa Zahra wata irin kulawa ta musamman sai Kuma shima Mai gidan ya kwallafa ransa akan soyayyar yarinyar abinda ya haddasa tsana Mai tsanani tsakanin Mama da zahra inda ita mamar ke ganin Kamar nema ne yasa Alhaji ke kaunar Zahra, tana ganin idan Dan tana 'ya mace ne karama ai itama tana da nata kananan 'ya'yan mata Amma baya nuna kulawa akasu Kamar Zahra ko Dan tafisu kyaune tunda Babu inda ta baro uwarta.
Wannan kenan.
Ranar da za'ayi jarabawar share fagen shiga karamar secondary ta gwamnatin tarayya tun sassafe zu Zahra suka shirya ita da Sulaiman da Hameeda da Salma duk da Salma ta girmesu Amma yawan yi Mata repeating yasa suka taddo ta.
Har sun shiga mota Bala direba na niyyar shiga Zahra ta bude ta fito da sauri ta nufi cikin gida Sulaiman Yana kiranta tayi banza dashi ta shige da gudu ta karasa dakin Ammah tana fadin "Ammah na manta kayana da Ya Hassan ya kawo min har zamu tafi na tuna".
Daga toilet Ammar ta fito ta nufi bedside locker ta janyo ta mikowa Zahra ledar tare da fadar "Maza kada ku makara mana".
Kai Zahra ta gyada kafin tace "Ammah ki kara yi Mana addu'a Dan Allah Ina son naci jarabawar saboda Abbana yace idan naci makarantar zemin kyautar wani Abu"
"To naji maza Allah ya bada sa'a"
A kofa suka hadu da Sulaiman ya biyo ta tana fadin "Na rantsa da Allah zamu tafi mu barki ba Dan Abba ya fito ba da wallahi sai dai ki fito kiga bama gidan".
Kafin ya saki labulen ya juya Zahra ta Kai kofar da zata kaika compound din gidan.
Masha Allah anyi jarabawa an Gama sai jiran sakamako.
A haka sukaci Baga da zuwa makaranta har suka Zama common enterence a matakin jaha.
Lokacin da suka dawo zaman gida lokacin ne Alhaji Jafar da kansa ya yiwa Zahra passport da visa Saida ya Gama komai sannan ya fadawa su Ammah da Mama. Godiya Ammah ta shiga jerawa Mai gidan nasu,yayin da Mama tayi shiru Kamar bazatayi magana ba sai Kuma tace "yanzu Yallabai da kanka zaka rakata ai da Koda Hasana ko Hassan ka hadasu zasu kaita ko Kuma a fadawa cen kakanninta su turo a tafi da ita ai cacar kudin Kamar yayi yawa".
Daga Ammah har Alhaji Jafar din kallon Mamar suke ita dai Ammah shiru tayi yayin da Alhajin yace.
Saboda ban San darajar 'ya'ya ba zan hada Yara a tafiyar uwa duniya daga Nan har Jordan na kwanta a gida hanakli kwance ko?"
Kai ta gaigice tare da fadin "gani makudan kudi za'a kashe".
Wani kallo yayi Mata "kada ki kawo b'araka Rabi'a duk yaran dake gabana daya na daukesu yada zan yiwa abinda na Haifa haka zan yiwa marainiyar Allah. Da Kuma kike maganar cacar kudi idan zan jera shekara Ina Kai zahra Jordan kullum ba abinda ze girgaiza a cikin abinda na mallaka".
Ku tashi kuje.
Lokacin da zasu tafi anyi Mata tsara sosai Dan Nanna ma kilishi tasa aka yi Mai yawa na tsaraba.
Har kano su Ammah da yara sukayi musu rakiya.
Lokacin da sukaje Jordan din ba karamar murna kakanninta zukayi ba Dan Babu zato suka gansu, sun Kuma Kara yabawa da cika Alkawarin Alhaji Jafar Dan da kansa yayi musu Alkawarin ze kawo musu Zahra Dan ko a waya Bai fada musu zuwansu ba,sai address dai daya taba tambaya can wani lokaci.
A ranar Zahra taga zallar soyayya a gurin dangin Najwa Dan gidan cika yayi da 'yan uwa aka dasa sabon kukan rashin Najwar da kyar Abbie da Abbanta suka dinga Basu hakuri Dan ma Alhaji Jafar ba larabcin yakeji sosai ba saidai Wanda suke Jin turanci suka ringa magana dasu.
Lokacin da Alhaji Jafar din ze tafi masukin daya Kama a hotel Abbie hanawa yayi duk yanda yaso zillewa kin yarda yayi dole ya amince aka sauke shi a wani part dake kusa da nasa Ummee din, Dan ba karya dukiya dai Kam akwaita Dan shi kanshi Alhajin yayi mamakin yanda ya riskesu Bai taba kawo haka suke ba lallai yasan hadin Allah ne kawai da suka bawa Muhammad sani auren 'yarsu Dan tazarar Mai nisa ce a tsakanin su.
Kwanan Alhaji Jafar bakwai ya wuce Umara yayin da Ummee tayi Masa Alkawarin zasu hadu a Saudiyyar tunda zata kawo Zahrar Nan gurin iyayenta da 'yan uwa su ganta a cikin garin Madinatul Munawwara.
Satinsa daya da zuwa Suma su Zahrar sukazo Saudiyyar ita da Ummeen da Aunty Nawwara.
A Nan ma Saudiyyar Zahra taga gata iya gata Dan kowa Nan Nan yake da ita, Dan kanwar Ummee Hanifa sosai ta kafe sai dai a bar Mata Zahra ta tafi da ita Istanbul inda take aure Wai Bata yarda da zaman Nigeria ba.
Ankai ruwa Rana da ita kafin ta hakura Dan da gaske Alhaji Jafar ya bude Mata aiki Dan cewa yayi idan irin haka za'a ringa yi bazai Kara bawo musu ita ba saidai duk Mai son ganinta taje ya ganota Kamar yanda Ummee keyi, hakuri aka ringa bashi.
Saida aka Kai Zahra makka suyi kayi umara sannan suka fara Shirin bar
o kasar.l Sayyaya dai Zahra ta shata Dan wasu kayan sai a awon cargo akayo musu su.
Sarkar gwal da warwaro zobe kuwa kirar Saudiyya da Dubai zuwa kirar Bahrain sun Kai kala goma duk dai dai size din ta sai na Ammah biyu na Hasana ma biyu shi kanshi Alhajin anyone mass goma Sha Tara ta Arziki.
Ranar da zasu dawo Zahra Tasha kuka haka kakarta Ummee,har jidda sukayo musu rakiya Basu suka tafi ba sai da jirgin su Zahra ya tashi a sararin subahanahu wata'ala.
Saukar safe sukayi anan suka samu Bala direban Alhaji Dan Bai fadawa kowa sun taho ba sai Balan kawai, sau da yawa idan ya fada gashi Nan a hanya hankalin Nanna baya kwanciya har sai ya iso.
Lokacin da suka shigo harabar gidan suna tsayawa Zahra to garzaya cikin gida tana fadin "Ammah!!! mun dawo".
Da gudu Hameeda ta fito daga part dinsu, rungume juna sukayi suna ta tsallen murna Sai jikin zahra Hameedar ke shafawa gani take kamar canza Mata Zahrar akayi.
Da sauri Ammah ta fito tana "fadin wa nake gani ne haka Kamar bakin saudiyya zuwa ba notice?"
Alhajin ne ya Bata amsa.
"Surprised din ki mukayi ko Zahra na?.
Kai ta gyada masa.
Kayansu ne su Bala da Mai gadi suka Fara shigowa dasu kafin Alhajin ya nufi part dinsa na cikin gidan yayin da Ammah ta rufa Masa baya.
Har yayi wanka ya shirya Mama Bata shigo ba, har ya tambayar Ammah yayi Ina Rabi'a ? Tace Masa tana ciki watakila ko barci take.
Kusan kwana su Zahra sukayi tana baiwa Hameeda labarin abinda ta gani da inda sukaje a Jordan da saudiyya, wurin karfe biyu Ammah ta tashi zatayi nafila ta jiyo su suna Hira a dayan bed room dinta lokacin wuri biyu da rabi na dare, leko tace su kwanta basu san dare yayi sosai ba.
Washe gari an baje tsarabar Zahra an baiwa kowa dai dai gwargwado.
Amman tsarabar Hameeda daban take Dan har sarka Saida ta baiwa Hameedar.
Basifi sati biyu da dawowa ba jarabarsu ta fito ta Federal inda Zahra ta samu F.G.G.C KAZAURE yayin da Sulaiman ya samu F.G.C DAURA, Hameeda F.G.C AZARE. Salma ce kawai bata samu ba a cikinsu.
Sunyi murna Kuma sunyi bakin cikin rashin samun makaranta daya duk an watsa su Abban Kuma da ya Hassan sunce kowa ya tafi inda ya samu, ita Hameeda Bata da damuwa tana gida, su Kuma duka 'ya'yan Ammah duk sun fita waje danma hanyarsu daya sai an aje Zahra a karasa da Sulaiman.
Ranar da zasu tafi sun Sha kuka haka suka dauko hanya malam Bala da Ya Hassan ne suka kaisu.
Lokacin da aka Kai Zahra an tashi daga aji, wasu Yara House master dinsu ya kira da wata prefect yasa su Kai Zahra room din 'yan j.s one.
A cikin yaran da suka Taya Zahra daukar kayane wata yarinya tace Mata "sister kizo ki zauna a kwana ta tunda ni daya ce saman gadona ba kowa".
Kai kawai zahra ta gyada Mata tana ta sauke ajiyar zuciya.
Ita ta taimkawa Zahra ta shirya komai a locker dinta, Saida ta Bari zahra ta HUCE daga kukan da tsaha sannan tace Mata "ni sunana Sajida Musa ni 'yar kano ce unguwar Gwammaja kefa ya sunanki?".
Nan Zahra ta fada Mata komai nata tun daga Nan suke tare har suka Zama aminai komai nasu ya Zama daya banbanci su kawai Sajida na A Zahra na C.
Haka sukaci gaba da rayuwa a makarantar gasu Kuma Yara masu kwazo barin zahra ga kyau ga ilimi Nan da Nan tayi suna a makarantar kafin hutu tayi popular sosai a makarantar, idan kace 'yar larabawa kowa ya santa ba Kuma Dan Babu irin jiinsin nata ba A'a farin jini ne daga Allah.
Lokacin da akayi hutu Zahra ba karamar murna tayi ba Kuma cikin ikon Allah da wuri malam Bala yazo lokacin har ya dauko Sulaiman.
Bayan Azahar kadan suka shiga Azare sunyi murna sosai da ganin mutanen gida Dan Sulaiman har da kuka, Nan su Hameeda suka saka gaba suna tsokana.
Haka suka cigaba da karatunsu cikin amincin Allah, lokacin da sukazo hutun third term ne akayi auren Aunty Hasana aka kaita Jos, Ya Hassan Kuma Daman Yana karatunsa a Rasha.
Kowa inda yake yacigaba da karatunsa Salmace Allah ya taikata ta samu shiga FGC AZAREN itama a ss1.
A haka aka dunga juyawa har suka Gama secondary School dinsu suka dawo gida.
Dawowarsu ba dadewa Allah ya yiwa Nanna rasuwa rashin daya taba Abbansu sosai.
Dan ya Dade Yana fama da damuwa tunda a rayuwa da ita ya tashi baisan dadin uba namiji ba itace komai nasa.
Ganin abin nasa Yana neman yayi yawa yasa Abokinsa bakon malamin daya sauka Nan daura gidan Nanna da almajiransa dududu Bai zaifi sa'an Alhajin ba malam Bubar ya dukufa yi Masa addu'a tare da saka Yara kanana suna Masa addu'a, cikin ikon Allah sai komai ya daidaita.
Ranar wata laraba zahra ta shirya zata raka Hameeda duba Qawarta meenal gidan Dan majalissarsu Mai wakiltar su majalissar Jaha, wani material ta saka Mai ruwan sararin samaniya yayi matukar karbar jikinta haka dinki ma ya Dace da material din, simple makeup tayi ta saka turarenta Amber oud new edition na kamfanin Al haramaini.
Tunda ta fito Mama ke Mata wani irin kallo Wanda har saida ta rinqa Jin ta takura kafin Hameedar ta fito.
A kasa suka taka suna Hira har sulaje gidan,sun Dan jima suna Hira da marara lafiyar kasancewar breast lump ne aka cire Mata ba wani serious case bane.
Lokacin da zasu tafi suka Kara komawa gurin mamanta sukayi Mata sallama suna zaune ne da a falonta kafin meenal din tayi Mata magana ta fito. Wani handsome guy ne ya shigo falon da sallama ya Dan jefa car key dinsa sama, kana ganinsa kasan hutu ya Kama jikinsa.
Ciki ya shigo lokacin da Suke amsa masa sallamarsa kujera two seaters ya zauna a Kai wadda ke facing dinsu Hameedar.
Gaishe shi sukayi su Duke ya amsa Yana cewa "Hameeda daman kina Nan na Dade ban ganki ba gaskiya Ina ga tun kafin na tafi Colombia fa".
Dan rausayar da Kai tayi tana fadar "wallahi Kam Ya Sahal an jima Kam kune dai bakwa ganuwa Kuna uwa duniya kunyi shiru Kum barmu da zafin Kasarmu".
Ta fada tana dariya.
Dai dai lokacin mommyn su meenal din ta fito kallon Sahal tayi tana fadar Kai Kuma haka mukayi da Kai?"
Kaisa ya Dan Sosa da key din hannunsa Yana fadi "Iam so sorry Mom kada ki damu yanzu zanje na kawo Miki in Sha Allah."
Ya fada Yana mikewa da nufin tafiya Meenal tayi tsagal tana fadin "Dan Allah Ya Sahal ka tafi dasu tunda cikin garin kayi.
Suka yiwa mommy sallama da godiya suka fito da leda Mai Dan girma a hannun Meenal wadda mommyn ta Basu.
Har kofar gida ya kawosu suna tsayawa ya kalli Hameeda Yana fadar "Dan Allah ki bani aron sister din take Mana Kona ten minutes ne Mana".
Dan murmushi tayi tana fadar.
"Ka Fara yiwa Abban mu magana dai haka Naga anayi"
Ita dai Zahra ciki ta wuce Dan Kamar a kan.kaya take duk ya takura Mata da wani irin kallo har a cikin mota ma saita mirror yayi sitinta tunda Hameeda ce ta zauna a seat din gaba tana Masa Hira Amman gaba daya hankalinsa yana kan Zahra.
Ita dai zahra Bata San yanda suka Kare ba taga dai Lokacin da Hameedar ta shigo ta wuce dakin su.
Bayan kwana biyu da zuwa gidansu Meenal da yamma su zahra sun tafi islamiyya ne baki sukazo gurin Alhaji Jafar, ya sansu farin sani daya kanin Dan majalissar su ne dayan Kuma kanin Babansu.
Yayi mamakin ganinsu Saida suka gaisa ne suka bijiro da abinda ya kawo su na yiwa yaron gurin Dan uwansu Sahal kidiba yaga yarinyar gurinsa Yana so. Shine mahaifansa ya turosu ya gabatar da maganar Yana neman izininsa na Fara zuwa gurinta Shira.
Alhajin yaji Dadi sosai na yanda suka zo suka memi izininsa duk da Daman sharadinsa kenan, ya Kuma nemi Jin wacece daga cikin yaran suka gada Masa zahra ce, nan ya amince musu da addu'ar Allah ya hada kawunan su.
Tun daga lokacin Sahal ya Fara zuwa gurin Zahra cikin ikon Allah tayi na'am dashi Basu Dade sosai ba sukayi wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya tashi a unguwar yasan irin soyayyar da sahal yakewa zahra kusan Kullum da yamma Yana nan makale da ita, a haka har manya suka shiga maganar aka tsaida lokaci wata shida inda zasu tafi Colombia inda yake hada masters dinsa ita kuma zata Fara nata degree din.
Anyi lefe na garari Wanda ya dauki Baki fiye da tunanin Mai tunani, an kashe kudi Kamar ba'a San zafinsu ba.
Lokacin da bikin ya rage baifi saura wata biyu ba sai lamarin ya Fara canzawa kwata -kwata Sahal ya rage zuwa gurin Zahra haka ma sai a kwana a wuni Bai kirata ba, duk wani zazzari da yake na bikin su events din da yake ta faman damun zahra da maganar duk ya daina Kai tafi-tafi sai ayi kwana uku hudu har sati Bai kirata ba, da farkon abin tana kiransa taji ko lafiya a yanayin yanda yake amsa Mata wayar saita hakura da Kiran nasa, tun Ammah na zuba ido har ta samu Zahra a wani dare ta tsareta da tambayar ko wani Abu ya hadata da Sahal ne? Ta Bata tabbacin ba abinda ya hadasu sai dai ta fada Mata yanda suka ringa yi dashi a kwanaki idan ta Kira shi.
Addu'a Ammah ta Bata tace ta ringa yi itama zataci gaba da yi, Mata sannan ta umarceta da kada ta Kara kiransa a wayar ta zuba ido kawai.
Duk abinda Ammah take na shirye-shiryen Baki Bata fasa ba, tayi waya mutanan Jordan ma sunce suna Nan tafe Amma a daure a turo Zahra Kamar saura wata data bikin.
Ba'afi sati daya da waya da kakanninta na uwa ba sakon kayan dakinta ya sauka Nigeria daga Istanbul kayan da suka gigita Mama Dan ba kayan Wasa bane set din gado har hudu kujeru set uku bayan electronics kuwa wasu har ba'a San amfaninsu ba sai dai idan an duba manual din.
Alhaji Jafar yayi fada Kamar ya Ari Baki lokacin daya Kira Abbie akan danme zasuyi Masa haka toshi meye amfaninsa da bazasu Bari yayi Mata kayan dakin ba.
Hakuri Abbien ya shiga bashi akan su basuyi Dan su Bata Masa raiba, sunga abinda ya kamata suyiwa diyar Najwa kenan.
Ammah da Mama Alhaji Jafar ya Kira ya fada musu tunda an Riga an yiwa zahra kayan dakin da duk abinda ya kamata to ga fifty million Nan ya baiwa Zahra idan komai ya nutsa saita Fara business na abinda take son sayarwa sannan ya Bata shanu biyar.
Kuka Ammah ta saka saboda Dadi ta rasa bakin da zatayi Masa godiya, yanda take dawainya da wannan marainiyar Allah Bai taba gajiyawa ba.
Mama ce ta Ari bakinta tana ta yiwa Abban godiya da saka Albarka sai faman dariya tace bakinta yaki rufuwa, tun Ammah na ganin dariyar farin ciki ce har ta Fara wani tunani na daban, Nan da Nan ta Kori shaidan akan abinda zuciya ke sawwala Mata.
Lokaci na Kara tafiya daukewar ma'amala na Kara yawaita a tsakanin Sahal da zahra, yanzu ta Kai kwata-kwata sun daina waya dashi, ana saura kwana talatin da hudu a Fara biki Wanda yayi daidai da saura kwana uku zahra da Hameeda da Abdul Hakeem su tafi Istanbul. Dan direct gurin kanwar Ummeen Hanifa zasu tafi daga baya su Ummeen sun samesu a can, idan an Gama komai su rankato Nigeria Dan da gaske Ummee ta shiryawa bikin sosai.
Washe gari, tunda gari ya waje Mama ke Kai kawo tsakar gida duk da ba aikinta bane ba Kuma halayyarta bane hakan. Yayin da a bangaren Ammah ta rasa me yake Mata Dadi duk kasala ta baibayeta jinta take Kamar ma zazzabi na neman rufata...

AUREN HUCE HAUSHIN


STORY
&
WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH.


PAGE ELEVEN
(11)
________Misalin Sha biyu da rabi na Rana kawar Mama kuma Aminiyar Asabe tazo gidan macece wayayya Mai kisisina Bata fiye zuwa gidan sosai ba sai lokaci lokaci, ta Dan jima a dakin Ammah suna hira har tana tsokanar zahra da Amaryar gobe ana dariya.
Chapter 1 · 0% Book details