← Book details Auren Gado Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 3 OF 3

Part din Hajiya ya shiga Wanda a nan ya sameta ta rarrafo da bin bango da kyar tafito domin muguwar yunwa takeji duk da tana cikin ciwo.

Auren Gado Part 1 Complete Hausa Novel · about 94 min read

Yayi matukar firgita ganin yanda ta fada cikin sati biyu da bai ganta ba, tana ganin shi taji wani irin sanyi da farin ciki don haka ta zaburo, Wanda tuni ta zube Tim a kasa tasa Kara. "Subuhanallahi Hajiya. Ya nufota da gudu domin ya taimaka mata Wanda yana matsawa yaga ta sume.
Cikin gaggawa ya Kira Asibitin da yasan suke zuwa yace likitan yazo domin bazai iya dagata ba Abunka da ba kadan ba.

Yadai taimaka ya jata saman kujera Saida likita yazo suka kaita dakinta da taimakon nurses da aka zo dasu, Abunka da kudi tuni aka fara bata kulawa cikin gaggawa, sun dade akanta kafin likitan ya fito yasamu manager, ya zare glass din idanun shi, " Ina me gidanka yake yakamata ya fita da ita kawai kai tsaye idan yana son ta samu kulawa domin da Alamun tasamu mutuwar barin jiki sakamakon hawan da jinin ta yayi sosai.
Hankalin shi ya tashi domin bai san ta Ina ma zai fara wannan fadawa khaleel ba halin da ake ciki,
Don haka ya Kira kawun su ya fadamai komai yayi salati yace gashi nan zuwa yanzu.
Saida ya dauki uwar gidan shi kafin ya tafi shima,
Halin da suka sameta a ciki ya mugun daga musu hankali, cikin gaggawa kawu modu ya ce a mayarda ita Asibiti zaifi kafin a Fita da ita. Fita yayi yana neman wayar khaleel, Wanda yayi dai dai da fitowar Hajiya shaeefa da salifa domin ganin meke faruwa a gefen mommy da manager yazo, basu taba zaton khaleel zai waiwayo taba sai sukaci karo da kawu modu yana saka waya a kunne, kallon shi sukayi a tsorace domin basuda gaskiya, aiki ya lalace bayan su sunyi farraku a tsakanin ta da duk wani Wanda zai taimake ta, how yanzu ba aje ko Ina ba ga modu a gidan... Murya kasa kasa salifa tace " mommy meye nake gani me Alhaji yazo yi nan? Aikin ya karye ne? Mun shiga uku. " ke don Allah yimin shiru wa ya isa ya karya aikin boka ai ko ita ban barta haka ba bare khaleel bari kigani bazai zoba ya Riga ya tafi shikuma wannan me ruwan mu dashi.
Ajiyar zuciya tayi, "Hmm har na ji tsoro domin nafara jin kamshin dollar's din da zan mallaka. Fitowar da akayi da ita ne yasa suka bisu da kallo , ba Wanda ya koma kansu har sukabar gidan da ita,
Juyawa tayi cikin gidan ta momyn ta bita, sai zagaye takeyi, " kingani Ashe batada lafiya ne wallahi khaleel zai zo mommy ni tsoro nakeji. " relax baby me zai faru idan yazo? Bare bazai zoba wannan nadewar da kikaga tayi bazata kuma mikewa ba bakin ta bazai taba budewa ba bare tafada mai me yafaru, don haka Ina zuwa bani jakata in fita yanzu.
Itadai tafara tsorata domin khaleel ba namijin da za ayi wa iskanci a kwashe lafiya bane.
Saida suka bata special room a Asibiti kafin kawun ya Kira manager yace bani number da yake kiranka da ita.

Lokacin suna zaune a falon su suna kallon season film na Philippines tana lafe a jikin shi kamar mage shikuma hannun shi na cikin wuyan shimin jikin ta, yaga kiran manager dama jira yakeyi, saurin tashi yayi ya gyara zama tareda ciro hannun shi cikin rigarta, yayi cutting call din ya kira shi, ya akayi ne? Lafiya kalau ga Alhaji. Ya bashi wayar, gaisawa sukayi kafin yace " khaleel kazo fa domin Hajiya jinin ta ya hau yanzu haka tana Asibiti anyi admitting dinta, jikin yayi tsauri wannan karon kayi kokarin dawowa ko a turota can.
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'un, Ina zuwa kawu insha Allahu. Ya kashe wayar hankalin shi tashe, ya dafe kai, jin yake bai kyauta ba Sam na barinta da yayi, dafashi tayi " me ya faru ne? Dago idanun shi yayi, " we're going back to Nigeria mommy ba lafiya tana hospital. Yafada cikeda damuwa, "Subuhanallah, Allah ya bata lafiya, bari in shirya mana kayan mu tom. Tafada tana mikewa, ya riketa, ta tsaya, " ki zauna inje indawo mana." no ni dai zan je kuma kaga bamusan Yanayin jikinta ba gwara mutafi gaba daya, koda zamu dawo tareda ita zamu dawo.
Rungume ta yayi " bakya tsoron me zatayi? " me zatayi? Uwace fa ta isa ne kuma kome takeyi tana yi ne saboda tana son mu don haka muje mu fara shiri. Kara damke ta yayi yana mai kisin din wuyan ta, har Saida taji tsigar jikin ta na tashi tayi saurin janyewa " karka hanamu shiryawa Malam let's go. Tafada tana dariya tareda ruko shi tana janshi yabita yana murmushin karfin hali, daurewa yakeyi karta ga tashin hankalin shi, amma a dame yake.
Duba time yayi yaga karfe hudu na yamma a kasar yace let me check in akwai available plight mu tafi yau kawai.
Yafada yana dubawa a wayar shi.
Tausayi yabata sosai domin duk kokarin shi na ganin ya daure abun yaki yuwuwa domin damuwar a bayyane take a fili.

Ita ta shirya musu kayan da zasu bukata,
Kafin ya shigo cikin sauri " let get ready akwai jirgi mai sauka Abuja. Yafada yana shigewa bathroom. Tashi tayi itama ta bishi har yafara wanka ta tsaya daga nesa tareda zuba mai ido cikin hanzari yake Abinda yakeyi, domin duk hankalin shi ya koma gida. Hmm khaleel ne zata biyoshi bathroom ya share? Lallai a dame yake, don haka bata matsa ba Saida ya gama ya matsota " quickly baby. Ya fita, tayi Ajiyar zuciya ta fara itama.
Ten minutes ta shirya domin ta lura a hanzarce yake, mai aikin shi da yabawa hutu ya Kira yace tadawo kan aikin ta na kulada gidan zai koma 9ja.
Sai zuwa tsakiyar dare jirgin su ya daga,
Like you know is a very long journey, don haka ko yanzu Saida suka Kwana a hanya da sassafe jirgin su ya sauke su a filin jirgin na babban birnin tarayya. Tayi matukar gajiya, fiyema da tafiyar su domin jikin ta mugun kasala takeji da batasan Ina ta samo asali ba. Domin ita batada ganda ko kadan,
Cikin doguwar Riga take maroon tayi matukar murjewa tareda Kara kyau, kafarta cikin low pass baki mai kyau sai Y'ar Karamar Jakarta data rataya,
All eyes on her, gayu sai baza ido sukeyi sunga mai zafi, ya ankare don haka tuni ya matso tareda rungume kayan shi a kafadar shi saboda kuraye,
Sai da tayi dariya domin ta gano shi yace "what? "Bakomai. "Hmm I don't know why kikayi irin wannan kwalliyar?
Bafa kwalliya a fuska ta. Yes yakamata kisaka katon hijab kinga nan ba can bane sunayin kamar su dauke min ke bazan iya ba zaki dawo da saka hijab malama,
OK malam, Tafada tana jin dadi tareda dariya, plight ya Kuma sama musu zuwa kano, Wanda ba Wanda ya fadawa ya shigo 9ja, har Saida suka sauka a kano ya Kira manager yace ya sa akawo musu mota suna Aminu kano airport.
Jikin shi na rawa yace gashi nan zuwa, da kanshi ya zo tarbar su.

Sun d'an jirashi a reception kafin ya iso,
Ya musu barka da Zuwa kafin ya dauki kayan su ya zuba a motar, suna tafe yana tanbayar shi jikin Mommy, yace tana Asibiti har yanzu su wuce ne kai tsaye? " no bari muyi dropping madam dina a gida first sai mutafi. " A'a mu wuce kawai ban gajiba nima inaso in ganta.
D'an hararar ta yayi kadan, yace toh su tafi. Tanbayar shi tayi da ido what? Ya share. Saida suka isa hospital din ya fito itama zata fito yace kidaina magana a gaban wani ke bakisan yanda muryar ki take ba ko? Oh shine matsalar? Sorry Zauji. Don't repeat that. cikin bada doka ya fada. Suka jero kamar taurari,


Adakin mommy ce kawai kwance sanye da na urorin dake taimaka wa jikinta, su kawu modu da uwar gidan shi suna zaune a waje domin dokar Asibitin. Suka iso, sunyi matukar mamakin ganin su haka da sauri, Dama ka taso Ibrahim? eh kawu ya mai jikin? Toh tana ciki kaje kaga likitan first. Wucewa yayi yabarta a wurin, ta gaidasu cikin girma, mama uwar gidan kawu ta rungume ta kamar Y'ar ta cikin jin dadi sannu Y'ar Albarka.
A zaune yake doctor na yimai bayanin basu gane kan Al amarin nan ba yau jiya da aka kawota da Alamar improvement amma yau jikin ya Kara nauyi bayan duk na urorin dake taimaka mata. Dafe kai yayi yace, Zan iya zuwa in ganta? Yafada idanun shi sunyi ja tun baiganta ba, likitan yace "yeah sure muje........ 🖊


*Matar Soja*
5⃣7⃣&5⃣8⃣


............... Tunda ya shiga ya hango ta a zube a gadon ya shiga tashin hankali, idanun ta ta bude a karon farko ta zuba mai idanu, so take ta motsa jikinta amma bazata iya ba, bakinta takeso ta bude bazata iya ba, domin har d'an karkacewa yayi kadan, ta rame a cikin Kwana kadan, wasu irin hawaye ne masu zafi suka biyo kumatun shi, for the first time yana regret na bijirewa umarnin ta koda zai mutu, saboda soyayyar uwa da d'a sai Allah, da kyar yaja jiki ya matsa wurin ta tareda dafata yasa kuka mai ciwo, "Am sorry mommy na am sorry", nasan da yaya Ahmed ne bazai taba barinki a cikin wannan halin ba, gashi ni na barki mommy, am not a good Son mommy am sorry.
So take ta lallashe shi tare da nuna mai baida laifi amma bazata iya ba, sai hawaye da kebin kuncin ta itama, dagowa yayi cikin sauri, ya share mata hawayen " please don't cry momy", zanfita dake ko ma wacce kasa ce zaki warke da izinin Allah. Yayi saurin tashi ya koma wurin likitan.
"Doctor zan iya tafiya da ita China kai tsaye ba wata matsala? eh babu saidai mun dorata akan medication na tsawon sati daya, muna so muga ni idan maganin ya karbeta nan da Kwana uku munga cigaba basai ka Fita da ita ba, so have some patience sir khaleel.
Haka ya fito a sanyaye idanun shi sunyi jawur, tundaga nesa taji ba dadi tana ganin Yanayin shi tasan ba lafiya,
Har ya matso tareda bawa manager umurni kai tsaye fuskar shi ba walwala, "take my wife home"
Ya juya yana Kara yiwa kawu bayani, jikinta yayi mugun sanyi y'an da yaki ko kallon ta kuma tana ganin damuwa karara a fuskar shi, daga dawowar su mommy tafara shiga tsakanin su ne ko kuma ciwon tane yasa ya shiga wannan mood din?
Kasa tafiya tayi ta matsa ina dakin inganta kafin in tafi? Tafada cikin kwantar da murya,
"Kije gida no need, batada lafiya banason Abinda zai daga mata hankali kuma.
Kallon tuhuma take mai ba tare da ta gano manufar shi ba ta juya cikeda sanyin jiki domin batada zabi,
"Hajiya ina zan sauke ki? Shiru tayi kadan tana tuna ai ba a gidan shi ya dauketa ba don haka ko yanzu gidan Aunty Raliya tace suje domin batasan me zata fada ba in taje gidan malam.
Tunanin Yanayin shi takeyi a zuciyar ta, they are just fine kafin suzo Asibiti, meya faru? Haka take ta tunani har suka isa gidan Aunty, akwatin ta ta cire tace yaje da nashi kawai.
Aunty Raliya tayi matukar mamakin ganin ta kamar daga sama Saida ta tsorata.
"Naziya saukar yaushe? "Yanzu muka shigo"... Tayi mata bayanin mommy ce ba lafiya tabar shi a Asibiti, "to ke meyasa baki wuce gidan kiba?
"Aunty ba anan ya daukeni ba da zamu tafi ko kin manta meya faru? toh Naziya naga kuna lafiya kalau da mijin ki me zaisa ki dawo gidana? " ko in tafi gidan malam ne ? Tafada cikin fushi kadan da ya hadu dana khaleel ga tanbayoyin Aunty Raliya ga wata irin anger da takeji a zuciyar ta, "Aunty Matar shi na cikin gidan wadda akeso ya Aura mezan je inyi a can?
A'a kanwata duk dai haka bata tasoba, welcome back little sister, irin wannan fushi daga ganin ki kinyo mana tsarabar d'an China ne ko bangkok?
Kinga y'an da kika koma kamar atabaki jini ya fito jikin ki kamar wadda aka saka a engine, ai da badon nayi miki kyakkyawan sani ba bangane ki Naziya.
D'an murmushi tayi kadan, duk da haka zuciyar ta nakan khaleel, Sai da ta huta, Aunty Raliya ta bata Abinci taci kadan ta watsa ruwa, Aunty Raliya ta zauna gefen ta "Naziya akwai matsala na lura, meke faruwa ne meke damunki? Shiru tayi da kamar bazata yi magana ba Amma bata iya boyewa Aunty damuwar ta, da in ina tafada mata Abinda ke damunta.
"Mtsww kin dagamin hankali a banza, kika sani ko ciwon nata yayi zafine shiyasa kika ganshi haka, banson shirme ni banga Abun damuwa a cikiba.
Ajiyar zuciya tayi, badon ta gamsu ba imfact fushi ma takeyi dashi, don haka baccin ta ta shaka sosai don tagaji da zaman jirgin.

A Asibiti sai bayan ta wuce ya bita da kallo yana hango reaction dinta yasan ta shiga damuwar canjawar shi, and he can't help it domin ganin mommy cikin wannan Yanayin duk ya dagula mai lissafi, sannan gashi yanzu Yanayin da yaga ta tafi ya kuma hargitsa mai tunani, bayason barin mahaifiyar shi kuma he wants to go to Naziya, haka yayi ta sintiri gasu kawu sun wuce gida yace sutafi su huta tunda yazo, dama ba azama damai jinya don haka suka tafi.
Ko yunwa bayaji duk da baici Abinci ba ko a jirgi, wallet dinshi ya ciro tareda wayar shi ya canja layin shi zuwa na gida yafara tunanin kiranta, lokacin tana bacci kuma tunda suka sakko 9ja batabi takan wayar ba don haka bata kunnata ba, jin ta switch off ya dafe kai, malam yakira suka gaisa, "Ibrahim kun dawo gidane naga number kasar mu? " eh malam mommy ce ba lafiya shiyasa muka dawo ba shiri.
"Assha subuhanallahi toh kuna ina yanzu? Yafada mai Asibitin da suke.
Malam na kashe wayar ya tashi daga wajen ya shiga cikin gidan yasamu Inna kulu, yace " Hauwa bari inje Asibiti mahaifiyar Ibrahim aka kwantar harma sun dawo suma. Ta jajanta Abun kafin tayi mai adawo lafiya, wani Almajirin shi babba da yazo gaida shi ya kaishi a roba roba har Asibiti.

Cikin girmama surukin nashi ya tarbeshi suka shiga har dakin mommy, malam ya jajanta tareda gaida ita tabisu da ido,
"Um um Ibrahim wannan ciwo nata tun yaushe ne? "Jiyane suka kawota Asibiti Amma bansan yaushe tafara ciwon ba. Yafada yana dukar da kanshi, "Assha, toh me likita yace akwai sauki ko Alamar samu? Ya mayarmai da yanda duk likita ya fadamai, ya girgiza kai yace Allah ya sauwake zata mike da izinin ubangiji karka damu ciwo jarabtace daga Allah Kuma jinya na kankare wa bawa zunuban shi don haka kataya ta da Addu'a, Ina ita Naziyar? Yace tana gida, ga shirme itada zata tsaya tayi jinyar mahaifiyar taku me ta tafi yi gida kuma?
"Ni nace taje ta huta zata dawo. Yafada kawai. Sannan malam yayi shiru.
Zuciyar shi shima tana wurin ta dan ba halin yabar Asibitin ne, bayan tafiyar malam ya koma dakin tareda zama ya zuba mata ido, zuciyar shi ta Kara karye wa "Am sorry Mommy for leaving you behind, ban kula da Amanarki da yaya Ahmed yabarmin ba. Hawaye ne suka zubo mai har kan hannun ta, ta bude idanun da su kadai suke aiki tana juyawa Alamar yadaina kuka, da tanada bakin magana da ta fada mai duk Abinda yafaru zatayi Amma babu, haka yayita kula da ita sai magrib ya fito domin bin dokar Asibitin ya shiga motar shi da yasa manager ya kawo mai,

Gidan shi ya tafi kai tsaye batareda tunanin komai ba, lokacin su Salifa sun baje a falon Mommy har da kawayen ta y'an iska ga mommyn ta a gefe tana waya akan akawo Mata sabbin gold tunda duniya tasu ce, sai da ta gama ta juyo tana kallon kawar Salifa da hannun ta ke cikin rigar salifan tace " kufa bakuda kunya Ko kadan ina wurin don iya shege bazaku bari intashi ba, ku yaran zamani bansan meke damunku bane ga maza agari ga Alhazai ga d'anyun jini kubi, don iya shege junan ku kuke lalubewa, kuma ku kashe min hayakin nan ya ishheni haka kuyita bankadar shisha kamar Abinci.

"Old lady bazaki gane dadin bin jinsi bane sai kin d'ana yaseen. "Aa barikin da nayi baikai can ba kudai kuje kuyita yi ni yanzu tunda dukiya tasamu banda matsala kuma kusa ido kwanan nan zata karasa domin boka yafadamin ya fara aiki ya sakar mata ciwo a hankali zata karas............ Kasa karasawa tayi ta maida kalmar ta ta hadiye mukuth kamar ta hada da makogoron ta, tayi saurin mikewa tana diri diri don ko motsin mutum basuji ba. Tun shigowar shi gidan yasan akwai matsala domin yayi horn har yagaji ba mai gadi yatafi yawon shi, don haka da kanshi ya bude ya shigo tareda rufewa da katon kwado,
Salifa tayi mugun nisa don ba karamin jin dadin tabawar takeyi ba har wani cije lips takeyi idanun ta sun sauya tuni,
Taji salatin mommy, cikin zin zafin yanda take kokarin hanasu jin dadi tace " my God mommy please ki bar nan munaso mu huta if you can't wat....... Ai tafi mommy firgicewa ta tattaro rigarta ta na rufe kirjin ta da kyar ta zabura, mommyn ta na rawar kafafu da murya tace "khaleel yaushe ka.. Ka.. Da... Wone? Kagan mu nan muna d'an jajanta jinyar balkisu ne zanyi girki muje dubata banaso mubar part din ba kowa ayi sata. Tanayi tana kame kame.

Tunda ya shigo yake kame a jikin kofar falon ko motsi baiyi ba tunfara maganar mommy har zuwa yanzu, bazai iya misalta tafasar da zuciyar shi takeyi ba, nade hannun shi suke Saida ya gama kare musu Kallo tsaf idanun shi sunyi mugun kadawa, dukkan su bamai fuskar mutunci ko shigar Arziki, ya juya ya kulle kofar da key tareda cirewa ya jefa pocket ya nufo tsakiyar falon yana karewa ko ina Kallo.
"Hmmm I gave you ten minutes kafin inyi fresh up I want you to clean all this mess. Ya fada yana nuna musu falon da yayi kaca kaca domin sun maida shi dandalin iskancin su.
Shigewa yayi domin akwai tsananin gajiya a jikin shi, sai da ya tube ya shiga bathroom ya hada hot water ya shiga, zama yayi ya runtse idanun shi, " mommy kinga me kika janyo mana ko? kinga irin zabin naki. Yafada yana mai zubo da hawaye, yanzu yaji zuciyar shi ta samu sukunin da zaiyi Abinda yake ganin ya dace don dazu inya biye zuciyar shi kisan kai zaiyi, ya tuna da maganar Hajiya sharefa. Zabura yayi ya dauraye jikinshi ya fito daure da towel.
Waldrp dinshi da yasan akwai kaya ya bude ya ciro kananan kaya guntun wando da Riga T-shirt bakake an rubuta handsome and Arrogant, da farin Zane,
Shigowa tayi cikin karairaya wai ita mai miji, domin sun zugota taje ta yi mai kissa tunda baice komai ba, baiga komai ba, don haka Jakar ta biyoshi dai dai yana daukar wayar shi yaji maganar ta.
"Darling welcome"... wani irin juyowa yayi a hargitse tareda sa kafa ya bata wani irin shoot da bata san yana zuwa ba, don haka wani irin tumbling tayi har jikin kofar ta buga kai Tim, ba shiri tasa Kara.
Wandon da ya cire ya dauka yasa cire belt din jikin shi. Ya rike wutsiyar Alamar da karfen yake son yin hukuncin, tuni har sun shigo a tsorace saboda ihun salifa.
Idanun shi a rufe yace " kuma kunshigomin dakin ne da dattin ku"? toh duk sai kunci ubanku yau sai kungane kun shigo inda bai dace da iskancin kuba,.
Rufe ido yayi yana musu kan mai uwa da wabi har mommyn ma tana zuba salati, "d'an nan zaka iya dukan balkisu Ashe ? Indai zaka b...ai wani irin hambarin da yabata Saida tayi zaman y'an bori, kin saka mahaifiyata cikin ciwo bayan ita ba Abinda take nufinki dashi sai Alkhairi kinzo kin kawo min karuwai cikin gida har gefen uwata kuna iya shege, a kuma gabanki suke lalacewar su don kina tsinanniyar uwa, I think my mother is worst, Alhamdulillah nasan bazata taba aikata irin wannan halin nakiba, domin ta bamu tarbiya mai kyau but you, look at your daughter in front of your eyes........
Wani irin bakin ciki ya kuma tokareshi ya Kara rufesu da duka sukayi falo suna zuba ihu, mommy da rarrafe da jan gindi ta Fita tana " ni ka daka khaleel ina Suruka..... "Kina karasawa sai na sumar dake wallahi" surukin uban wa ni na Auri Y'ar ki ko kitanbaye ta ko yatsar ta na taba Kallo, ke har kinada Y'ar da Khaleel zai Aura? look nace ku gyara gidan nan kunki wallahi billahi idan Nafita nadawo bakuyi ba zakusha mamaki na.... "Ya isa don Allah malam kai din wa da zaka zo kana dukan uwata da kawayena? Toh bazamuyi ba ka kashe mu kuma kokaki ko kaso ni Matar kace igiyata na wuyanka kuma bazaka biyamin bukata ba dole in nemawa kaina mafit...... Wani irin kwashe ta yayi da kafafun shi " tir Allah ya tsare ni in hada tsalkakakken jikina da najasa, wallahi da in zauna dake a matsayin mata gwara in mutu gauro, kuma inke kadaice mace khaleel bazai taba Aure ba, igiya ko na datseta duka ukun aje acigaba da karuwancin da license dama kin saba ko da mijin ki zai baki kulawa ba isarki zaiyi ba dabba Alade tunkiya kawai, and ke kuma, ya nuna mommy, "ba Wanda zai Fita wannan gidan sai mahaifiyata ta warke idan bata warke ba ko naga wani Abu yasameta wallahi za ayi gudu, don duk sai na nakasa ku. Ya bankada ta ya wuce tareda bude kofar ya Fita ya kuma kulle su a ciki.

Gefen Naziya ya nufa yana nan a garkame a y'an da yabar shi, ya rike kai that means ba nan tazo ba. Wayar shi ya ciro ya Kira manager yace" ina ka kaimun madam?
"Tana janbulo can tace inkaita.
"Nan ne gidana why zaka kaita can kuma bazaka fadamin ba. "Sorry sir bansani ba ne. Ya datse kiran cikin haushi ya Kara gwada kiranta ko yanzu shiru, ya nemi number Aunty Raliya, lokacin suna hira abinsu sun gama cin Abinci,
Daurewa kawai takeyi Amma zuciyar ta na wurin shi tayi mugun sabo dashi zaman su a can tsawon satunkan nan baya Fita ko ina suna likeda juna yasaba mata yau daga dawowa nan ya shareta, zata rama ne itama.
Karar wayar Aunty ce tasa ta kalla taga number shice ta basar Aunty tace "bani wayar to ni in dauka in baza ki daga ba.
Picking tayi tareda sallama, ya gaida ta cikin girma ta tanbaya mai jiki yace Alhamdulillah jiki, kafin yayi shiru yakasa tanbaya ko tana nan. Aunty tace " ga mutuniyar nan. Ta Ajiye mata wayar tareda Fita Abinta tana cewa nabarki lafiya nayi wurin neman lada tsaya yanga ke.
Tana kallon wayar taki dagawa ya katse ya kuma Kira taki dauka, yace " tofa khaleel ka shiga uku yau. Ya Kira yafi sau goma taki dagawa haka ya hakura ya kyaleta dole yaje karbar hukunci in yana son yazauna lafiya da zuciyar shi, a daren dukan su basu runtsa ba, khaleel Kwana yayi tsuki ga takaicin su Salifa ga kuma fushin Naziya, ga wani horo da jikin shi kemai wai bazai runtsa ba tunda bata kusa saboda sabo da yayi, zaune ya tashi yanajin kamar yayi tsuntsu yagan shi a gaban ta saboda kewar ta, "kin lalatani kinaso kuma ki gujeni baby no way wannan fushin is unacceptable, bazai yuwuba dole gobe kidawo nan I can't take it.

Daren ya mugun yimai nisa, haka itama Amma saboda Yanayin kasalar da takeji daga baya tayi baccin ta, Assalatun farko yayi masallaci da badon kar ace lafiya ba zuwa zaiyi yayi gadin ta har gari ya waye ya ganta hankalin shi ya kwanta. Zama yayi yana gadin safiya, sai yanzu ya tuna da su Salifa ma, ya koma ciki tareda dakko key ya nufi kofar ya bude, suna shahsheme a kasa, Hajiya sharefa kugu yayi tsami ko motsi bata iyayi salifa kuwa hannun ta a kunbure Kwana tayi kuka saboda azaba daga gani ta targade ne. Suma sauran sai nishi sukeyi zasu iya rantsuwar ba mahalukin da ya taba musu irin wannan wulakancin na khaleel.

Taka hannun salifan da yayi ne yasa ta saka Kara mai karfin da ta tashe su har mommyn tana "wannan y'a akwai ki da shegen raki saikace nima ba ciwon nan ne dani ba wannan akwai tambadadden.... Tayi tsit ganin shi duk suka mike tareda fara bashi hakuri " khaleel kabarmu mutafi yanzu kaga mun gyara ko ina wallahi bazamu kuma shigowa gidanka.... "Kuma nafada muku bazaku bar gidan nan a banza ba bayan kunyi sanadin kwanciyar mahaifiyata Asibiti", Kujera ya samu ya zauna tareda dora kafa daya kan daya yace yanzu inaso inji duk Abinda yafaru bayan bana nan kafin inbarku kufita gidan nan oya I'm all ear's. kayi hakuri bab.... "Kul kika kirani da wannan sunan ni ba sa'anki bane, call me sir khaleel ko sir Ibrahim. "Sir khaleel nidai naso in tafi mommy ce tasa ni zama wallahi ni na hakura da Auranka tunda naga baka damu dani ba, Amma mommy..... Ta bude mai bakin Jakar tsab momyn ta na mintsilin ta karta fada maganar takardaun Amma Kash tuni tayi b'ara, "takardun ka da managern ka yakawo suna nan ban tabasu ba wallahi. Dafe baki yayi yana mamakin greediness dinsu duk Abinda suke dashi wato bai ishesuba nashi suke hari da Dukiyar mommyn shi. "Wato 419 kuke yi kenan? Shine kukazo har gidana zakiyi in the name of Auren hadin zumunci, you know what? mommyna harga Allah so take zumuncin ku ya kullu shiyasa ta matsa mana domin Y'ar ki dagani har Yaya na, Ashe ku zuciyar ku sharri kuke nufin ta da shi, alright zaku ga karshen cin Amana kuwa. "Wayar shi ya ciro ya Kira manager yace ya zomai da police yanzu yanada y'an 419 a gidan shi. Tuni suka fara kuka mommy na rokon shi kawayen nacewa " mudai meye namu aciki kawai mu masoyane abarmu mutafi ba ruwan mu da rigimar gidanku, salifa kinga kunjefa mu a matsala daga Zuwa hutawa. Karku damu zaku huta a bayan kanta. Ya mike tareda Fita ya rufesu ganin suna kokarin biyoshi suna roko. "Mommy kinga masifar da kika jefamu ko nafada miki halin khaleel kingani bantaba zuwa prison ba yau zaki sa in shiga bayan inada Abinda zai isheni Rayuwa ta ko wacce kasa nakeso inada manyan babe da zasu kaini in more, now look what you have got us in to, wallahi bazan yafe miki ba mommy.
Ga Y'ar banza don wa nake duk wannan abun badon ke nake yi ba saboda banaso ki wahala.... "Oh really? All tanks to you now we are going to rot in jail".
Ke kibarni inji da kwankwaso na dakeyi kamar ya fita da gangar jikina.
Kuka tasa tace " ni hannu na bakya gani ya kunbura dakyar nake dagashi wallahi, nidai Allah ya isar min. "Gawa? Inji mommyn. "Ga duk Wanda ya tsargu. Tafada tana murguda bakin ta saboda tsantsar rashin tarbiya.
"Toh mu muyiwa wa Allah ya isa ke Ko uwarki ?, saboda jarabar ki yau kinja mana masifa mu bamuci ko fucika ba. Amma kunci ni shegu matsiyata la'anannu kawai jarababbun ba.. ai tuni dambe ya kaure suka fara jirgar ta mommy na ihu gashi bata Iya kwakkwaran motsi. Karku kashen ya'. Basu daina ba Saida khaleel ya bude kofar, sunyi mata lilis duk sun jijjimata da kunba, police yabawa izinin shigowa yace duk su kwashe su. Tana numfashin wuya dakyar haka aka jasu keeeee, aka watsa bayan mota, mommy sai rokon shi takeyi yayi biris, yanzu burin shi yaje yaga farin cikin zuciyar shi ko a wane halin take?

Wanda tunda ta tashi suka hada lafiyayya breakfast da Aunty suka shirya a basket, ta kintsa cikin wata tsaleliyar doguwar Riga Y'ar Oman ta nade kanta da mayafin, ba fushi yakeyi ba na ba dalili zai sha mamakin ta tayi kyau na fitar hankali dole duk Wanda ya ganta yasan Matar wanice, mijin Aunty a lokacin da zai Fita ya saukesu a Asibitin, tundaga harabar take baza idanun ta ko zata hango shi, Saida suka tanbaya dakin aka nuna musu, bashi ba Alamar shi yana can yana dealing dasu mommy, takara cika, sai a lokacin taga mommy, tayi matukar tausaya mata har wasu hawaye taji sun zubo a kuncin ta, kai Rayuwa d'an Adam ba bakin komai yakeba yanzu mommy Y'ar gayuce haka kwance ko motsi bata iyawa, matsawa sukayi bakin gadon ta dafa hannun ta, tace "Sannu mommy Allah yabaki lafiya. Ta bude idanun ta ta zuba mata ido sai hawaye, so take ta bude baki tafara bata hakuri Amma ba hali, hannu Naziya tasa ta goge mata hawaye, nurse ce ta shigo ta tanbaye ta za a iya bata Abinci? Tace eh su bata mai ruwa saboda bakin daya d'an juya.
Dama sunyi kunun gyada, "Aunty Raliya ta zuba mata, da taimakon nurses Suka d'an dagata saboda nauyin jikin ta jingina mata filulluka, cokali tasa tafara bata kunun Tanayi tana gogewa saboda dawowa yakeyi kamar jaririyar da ake koyawa cin Abinci, ido kawai take binta dashi da hawaye, sai sannu sukeyi mata, Aunty Raliya tace " kinga shirmen ki Naziya ki tsaya tunjiya saboda kula da ita kin kama kin tafi. "Aunty laifin shine ko bari baiyi na gantaba Ashe jikin yayi tsanani har haka ne, yanzu bazan koma ba zan tsaya da ita anan inkinje ki sa akawomin ko Kala biyu ne masu saukin sawa.

Tunda yagama dasu cikin gaggawa yayi wanka ya shirya cikin d'an kareriyar shadda Arsh guntun Riga tasha dinkin gayu na maza, ya fito yafada mota, hankalin shi ya kasu kashi biyu, mommy da Naziya, don haka ya yanke hukuncin zaije Asibitin first ya dubata don yasan inyaje wurin Naziya zai iya mantawa da kanshi acan, koda ya isa Asibitin yasha mamaki, Wanda tundaga kofar dakin kamshin ta yafara yimai welcome, wani irin Ajiyar zuciya yayi tareda murmushi kadan yace " my happiness tunkafin ya ganta....... 🖊


*Matar Soja*
5⃣9⃣&6⃣0⃣


................ Ita kanta ta san ya isowa tunbai karaso ba, don haka tuni ta Kara hade fuskar ta tamau domin tayi mugun daukar fushi dashi, tuni ya ji wata natsuwa ta ziyarci zuciyar shi, cikin takun kasaita ya shigo, hade da sallama kasa kasa idanun shi a sama, domin ba Abinda yake buri sama da yayi ido biyu da ita, yayi matukar kewar ta, sai jera Ajiyar zuciya yakeyi tunda ya sauke idanun shi akanta, gangar jikin shi tuni ta amsa gayyatar ganin ta da tayi tank God ma manyan kayane a jikinshi, a bu biyu yanzu zai hanamai rungume ta ya rafe zafi, nafarko Aunty Raliya na biyu momy, don haka ya saita kanshi yayi gyaran murya, tareda gaida Aunty, tamai ya gajiyar hanya da mai jiki, ya Amsa cikeda jin kunyar ta.
Kafin ya matsa gab da gadon, taki ko dago kanta sai bawa momy kunun take tana gogewa, he wants to touch her amma no way, don haka ya waske yana fisgo maganar "momy sannu. Ido ta juyamai Alamar amsawa, fita Aunty Raliya tayi domin amsa waya, yayi Ajiyar zuciya yayi saurin riko hannun ta batareda damuwa da idanun momy ba saboda he can't help it, tayi saurin dago kyawawan idanun ta masu rikita shi tace " meye haka agaban momy please stop. Tafada tana karkata kanta, " why kika ki tafiya gidanki kikatafi na Aunty Raliya? Hannun ta take kokarin kwacewa amma takasa don rai ita tasan kunya, momy Naji Nagani wani irin dadi takeji y'an da yarinyar ta nuna mata kulawa ga kuma Alkunya da zata iya mikewa itama zata basu wuri su zanta da junan su, Amma ko yanzu abun mugun faranta mata rai yakeyi har ya nuna a fuskar ta, "let me go please. Tafada" I want sai kin fada min dalilin da kika tafi gidan Aunty kuma nakiraki kinki daukar wayata kuma kinki kunna taki why?
Dago kanta tayi ta kalle shi cikin fushi tace ka sakarmin hannu idan kai bakajin kunyar idanun momy ni inaji please let go. "Never ever, if I let you go in zauna da wa? "Your second wife da kakeson kasancewa da ita that's why ka koreni batareda kama bari na duba lafiyar Momy ba jiya that's why na koma inda dama ka dakko ni kafin mubar kasar nan, ni nasan matsayina banda wani value a wurinka, kuma am not here because of you, nazo saboda nadamu da lafiyar momy tana warkewa shikenan.
Wani irin kallon what is wrong yake mata, momy feels bad saboda itane duk wannan mis understanding din ita tajawowa d'an ta, kallon Naziya tayi taga ita din dai data raina ita tafi dacewa da d'an nata ga hakuri da tarbiya, don haka taji duk duniya ba Abinda takeso yanzu kamar ta warke ta gyaro kuskuren ta,
Mikewa tayi da cup din ya Kara rikota, " Naziya please stop it, ko so kike ki dagamin hankali um? Dagowa tayi taga momy ta rufe idanun ta, ta ce "I said let go of me. Shima kallon momy yayi kafin ya Kara matsota cikin rage murya sosai dake dauke da damuwa, "meye nayi kike kokarin horani haka please am sorry koda ni bansan laifina ba kiyafe min but I can't handle your anger on me.
Fisgewa tayi ta yi bathroom domin dauraye cup din da spoon, ya runtse idanun shi tareda dafe kai " oh my god khaleel ka boni. Yafada tareda binta cikin sauri, tana kokarin fitowa ya maida ita tareda datse kofar, "kallon shi tayi fuskar ta a tamke "meye haka Aunty Raliya zata iya shigowa kuma kasan momy dai Nagani ko? " Hmm so what? In zaki yi kokarin horani da irin wannan new attitude din ya kikeso ni inyi behaving, tell me? Look am not use to this, and I can't take it any longer please forgive me if I wrong you.
Ji tayi yakara tunzura ta wato shi baisan laifin shiba, don haka cikin zafi ta dago tareda cewa " ba Abinda kayimin kawai bana son damuwa leave me alone OK.
"Hhhhh story, rubbish, you are insane Naziya, leave you alone, ni khaleel? You are dreaming wallahi, ban hakura dakeba tuntuni sai yanzu da kika gama shigewa cikin rayuwata kika yimin dalla dalla, hannun shi yasa cikin sauri ya fisgo kugunta ya hade ta da Kirjin shi, Saida yaji kamar ya shekara bai kusance taba saboda shauki da kewar ta, "Ahhhhhh Hmmmm. Yafada tareda kankameta kamar zai mayarda ita cikin jikin shi, kokarin kwacewa takeyi ya hanata dole tayi lakwas tana sauraran bugawar zuciyar shi tareda rawar da jikin shi keyi kamar bai saba rungume taba" baby banyi bacci ba jiya kinsaba min da yin bacci kina saman kirjina bayan kin shayarda ni zumar ki tareda madarar ki mai rikita kwakwal war mutum, why kike fushi dani why kika barni nikadai jiya why kike son ki gujeni bayan kinsan zuciya da gangan jikina bazasu dauka ba?
Samu tayi ta fisge haka kawai taji yanaso ya tayar mata da feelings a Asibiti a banza yabarta da Abin kunya, tana juyawa ya kuma hade jikin shi da bayanta yasa hannu ya rungumo Dukiyar fulanin ta tareda matsawa kadan yana gwama numfashi, "Am honey, kinji let go home yanzu zamu dawo please baby. Yafada yana goga mata jikinshi, she can feel how hard he is, tayi saurin bude kofar domin takai gab ta fisge ta gudu.
Matsawa yayi baya kadan ya dafe bango tareda runtse idanun shi ya dade a wurin kafin ya d'an dawo hayyacin shi,
Ta gyarawa momy kwanciya tareda komawa gefe taja kujera ta zauna, Aunty Raliya tashigo, Wanda har lokacin bai fitoba, tace "ni zantafi nabar yara Allah yakara lafiya Ina khaleel din? " gani Aunty yafada kanshi kasa domin yasan for sure yadago fuskar shi zata ga canjawar idanun shi, yace "bari muje in sauke ki tom, "Aa Wallahi ga mota nan megidana ya aiko yaron shi Allah ya bata lafiya.
Godiya yayi mata Naziya ta rakata ya zauna tareda bin bayanta da Kallo yana tausaya wa kanshi, Saida Auntyn ta tafi tadawo,
Still fuskar ba walwala, ya kalleta cikin da tausayin kanshi yace " muje ne? Banza tayi mai ta dauki Jakarta karama ta ciro wayar ta ta kunna.
Tafara game, karkace kai yayi yana kare mata Kallo tundaga fuskar ta har zuwa kirjinta har kafafunta data zame takalmin ta dora daya kan daya, jajur dasu mulmul, ya hadiyi miyau Kut a zuciyar shi yace " kinada Abinda duk zakija min aji yarinya is your time. Haka suke zaman kurame Wanda har doctor ya shigo tareda duba momy yafita, suka cigaba da zaman haka badon zuciyar shi nasoba sai dan baida yanda zaiyi, idanun ta akan su momyn khaleel din ma kebata tausayi yanzu da tanada baki da ta lallashi Naziya domin ta rikemata yaro hankalin shi ya kwanta,
Sallamar su Shukrah da malam harma da Inna da sadiq ne yasa ta zabura cikin matukar murna ta nufesu, shima mikewa yayi cikin girma mawa ya gaida surukan nashi, malam yace yamai jikin? Sukace Alhamdulillahi.
Matsawa tayi zata rungume Inna tace " ke bani wuri ingaida mai jinya mara kunya. Shukrah tayi dariya tace Aunty nidai Rungume ni nayi kewar ki. Suka rungume juna yana kallon duk wani motsinta kamar ya sace ta ya gudu yakeji, ganin ta yakeyi kamar ma bai taba Rayuwa da itaba,

Komawa sukayi gefe itada Shukrah su kuma suka matsa jikin gadon suka fara gaida ita, "Sannu Hajiya Allah yasa kaffara ne. Inji Inna da sai yau suka hadu da juna ido da ido, kallon iyayen Naziya takeyi tana hango tsantsar datti jantaka a fuskokin su, malam yace "kulu ciromin Ruwan zam zam din nan da kunnen magaryar. Yafada yana zama gaban gadon, a wurin ya balle Y'ar Karamar robar Inna tabashi cup ya juye ya fara Addu'a a ciki tareda mutsika ganyen magarya yace Naziya zo ki karba ki juye a gora kuna shafa mata a hannu da kafafun ta har fuska sau uku a yau.
Malam ya dade da sanin wasu mutane basuda yadda shiyasa bai hado komai ba yayi wannan agabanta idan taji sauki bakinta ya bude zai iya bata wani, a take Naziya ta yi y'an da malam yace Wanda tunda ake shafa mata a kafafun takejin wani irin sanyi hade da jin jikinta na rage nauyi kamar tace kar Naziya tadaina, a ranta nadama takeyi mara Amfani wasu hawaye take fitarwa na rashin bakin da zatayi godiya,
Khaleel kamar ya goya su yakeji y'an suka nunamai karamci da kulawa, yana Kara godiya da Allah ya hadashi da surukai nagari, basu dade ba suka tafi, yarage daga shi sai ita, matsowa yayi yace "am hungry madam in baza abani Abincin cikin rigaba abani Abincin da zanci. Yafada yana rage murya tareda kashe mata ido, mikewa tayi ba musu ta zubamai Wanda su Inna suka kawo shinkafa da naman zabbi,
Ta hado mai da ruwa mai sanyi domin akwai dispenser a dakin ta Ajiye ta juya.
"Kinsan tun jiya banci komai ba kuma kinsan bana iya cin Abinci nikadai yanzu kizo muci. "Ni ba wannan nakeso ba. Tafada tana tura baki. "Oh lobster or crabs? Yafada cikin mamakin y'an da ta juya cin wainnan Abubuwan. "Ni shrimps nakeso. Iyakar gaskiyar ta tafada, ya fara cin Abincin shi Saida yayi kat yasha ruwa, ya gyara zama, zuwa tayi tadaga plate din ta saka a, basket tadawo tareda tsayamai akai, "yunwa nakeji nima. Tafada cikin fushi domin yasan sarai me takeso, " bude idanun shi yayi yace ga Abinci nan kici in kuma nine muje sai kin koshi.

Komawa tayi can kusa da momy ta zauna, Abinta ta share shi, tashi yayi ya fita, Wanda yana fita y'an uwan shi suka shigo daga gidan kawun shi. Haka tayi ta karbar baki bayanan har zuwa magrib ta rage ita kadai, ta kuma shafewa momy jiki da ruwan Addu'ar, anan take shinfida dadduma tayi sallah domin kayanta a yalwace suke, bai shigo ba sai bayan isha'i.
Ya matsa tareda gaida momy kafin ya ce ta tashi lokacin tafiya yayi su tafi gida don ba akwana anan. "Ba inda zanje inbarta ita kadai intana bukatar wani Abu fa? " nurse na nan. "Am not going nama fadawa doctor zantsaya kuma ga ruwan maganin ta Anjima zankara shafa mata, kai katafi.
Kamar ya dora hannun shi a kai ya buga ihu yakeji, "look kinga banason musu kitashi mutafi. Momy naji kuma tana gani so takeyi tayi magana ba dama,
Tashi ma tayi ta haye gadon dake dakin extra ta kwanta tareda jan net bayan ta saukewa momy nata, tabashi baya.
Abun ya matukar konamai rai don haka a zuciye yabar Asibitin, yayi gida.
Inba haka tayi ba bazai taba barinta ta Kwana da Momy ba ita kuma so take ta kula da ita saboda tasan a duniya batada ya'ya sama da Ahmed da shi gas hi ba Ahmed Khaleel kuma namiji ne, kuma bai kamata wata nurse na wani kula da itaba,
Don haka ta zamo mata ya' koda bazata godeba zatayi domin Allah.
Wani irin farin ciki momy keji ganin y'an da Naziya ta jajurce wuni guda tana bata kulawa. Sai dai rashin jituwar su yasa abun ya taba mata zuciya, ba Abinda take buri yanzu sama da ganin farin cikin khaleel da Naziya.

Gida yatafi kai tsaye badon yasan zai iya bacci ba, ya kwanta yanata fushi a kujera ga gidan bakowa cikin shi sai masu aikin shi tsoffi da yadawo dasu, harma da mai gadi bayan ya kora Wanda suka kawo.
Har karfe goma na dare yakasa natsuwa haka ya canja zuwa kanan kaya ya dauki key din motar shi ya kuma barin gidan.
Naziya Saida ta kuma shafe momy tsab da ruwan Addu'ar ta kunna musu waya tasa kira'ar sudais cikin suratul bakara tareda Ajiyewa kusa da gadon momy ta koma nata ta kwanta bayan taja mata bargo, murmushi kawai momy keyi najin dadi ya' daga sama wadda tafi ma d'an ta damuwa da ita, haka tayi baccin ta mai nauyi cikin salama tareda jin duk wasu igiyoyin da suka daure jikin ta suna kwancewa a hankali. Ita kanta Naziya tana bukatar hutawar domin d'an baccin ma da takeyi na rana yau bai samuba don haka tana kwanciya yayi awon gaba da ita,
Kamar a mafarki takejin hannun mutum a Kirjin ta tareda jin nishi kasa kasa, wai don ma yana controling kanshi karya samata ihu a Asibiti. Jin jikinta na canjawa yasa tayi saurin bude idanun ta, dayake akwai d'an duhu sai hasken dake shigowa kadan daga window domin tayi switching light din, mugun tsorata tayi jin mutum laulaye da ita gaba daya hannayen shi damke da kirjinta gam, sanin zata iya samai ihu yayi saurin rife bakinta yana rage murya tareda cewa " it's me baby.
"Hmmmm tayi saurin dafe kirjin ta ta zabura tana sauke rigar ta daya kwashe mata. Matsowa yayi ya janyota tareda zaunar da ita saman kafafun shi " hey relaxed, kinga fushina ba inda zaije nadawo because I can't sleep, the house is too big for me, please baby I really needs you kinsan bazan iya hakurin da nayi a bayaba, karki yimin irin wannan horon.
Y'an da yake magana ya mugun bata tausayi don haka ta d'an natsu a jikinshi,
"Kai wai bakajin kunyar idanun momy ne in taganka fa? Ni dai kayi hakuri inna dawo gida kabari momy ta warke.
"I said I can't why don't you understand?
Yafada cikin tsawa da fada, "you are my wife ya zaki rika garani saikace ba halalina ba how many times kikeso in lallaba ki?
Momy Saida ta farka saboda tsawar da ya bugawa Naziya, cikin ikon Allah ta bude bakinta tace "khaleel! Kamar daga sama sukaji muryar ta duk da maganar bawai ta bude sosai bane, da gudunsu suka matsa kusa da ita, Naziya tayi saurin gyara kanta ta kunna wutar dakin suka ganta tana kokarin mikewa, wani irin farin ciki ne yasa ya ji duk wani bacin ranshi ya kau ya rikota tareda cewa "momy you talk, kuna kintashi zaune? Cikin so much excitement, itama ta matso kusa da ita tace "sannu momy tana boye hawayen idanun ta domin tsoro biyu ne ya hadu mata, ga fushin khaleel ga tsoron Abinda Momy zata yimata tunda kuma daga gani sauki yazo, kallon ta tayi kafin ta kalli khaleel dayayi kicin kicin tace "meya miki kike kuka? Khaleel meyasa bakada hakuri da daren nan kana yiwa yarinya ihu duk da gajiyar da tayi..
Wani irin hawayen farin ciki ne ya Kara shatatowa daga idanun ta, batayi zaton haka daga momy ba, shikan shi yaji mugun dadi don haka yace " tanbaye ta ni ba Abinda nayi mata impact in kukane ma nine yakamata inyi ba itaba, do you know momy tundazu nake lallabata muje gida ta nace ita nan zata Kwana tare dake saboda taurin kai.
Hannun ta datakeji ya saku sosai guda daya ta mika tareda riko hannun Naziya zuwa kusa da ita, " Zo kinji daina kuka inbakya son zuwa ba mai matsa miki kinji, Amma in saboda nine kitafi gida ki huta kinga am OK zan iya gyara kwanciya ta zan iya tashi hannu na dayan nan ne da kafar hagun nan nakejin su a rike, Alhamdulillah nagode wa Allah nagode miki keda iyayen ki Naziya Allah yasa ki gama da duniya lafiya. "Amen Amen Sukace, farin cikin su baya misaltuwa a wannan lokacin, tace "in kina son binshi kije da safe kya dawo.
"Banason zuwa momy ni ina nan. Tafada batareda ta kalli khaleel ba,
Fuskar shi ya tamke yayi banza da ita,
Tace "kije kiyi kwanciyarki kinji kibarni dashi nasan kin gaji.
Wannan canjin na momy yafi komai faranta mata zuciya don haka bataso tayi Abinda zata bata mata rai har su koma Y'ar gidan jiya don haka ba musu ta wuce Abinta, momy tace ya tashi ya kashe hasken ya kunna musu na wayar shi magana zata yi dashi kar hasken ya damu Naziya zatayi bacci. "Ya tashi cikin murnar ganin momy taji sauki ga kuma canjin hali da ya lura tayi tuni ya goge mai duk wani fushi da yakeyi ya hakura da Abin da ya kawoshi ya zauna tareda gyara mata zama don tace ta gaji da kwanciyar jikinta na ciwo,
"Khaleel bansan ta ina zanfara magana ba. Tafada tana dukar da kanta tareda share hawayen ta da hannun ta mai lafiya, yayi saurin rikewa tareda girgiza kai ya share mata hawaye tareda cewa "don't say anything momy kinga jikin ki bai gama dawo wa dai dai ba, banaso kiyi tunanin kinyi mana ba sai dai ba, ke mahaifiyar muce dole mubi Abinda kikeso, am sorry for everything momy. Shafa fuskar shi tayi tareda murmushi "nice zan baku hakuri banzamo muku uwa tagari b.... Rufe mata baki yayi " enough for all this talk momy ki huta, komai ya wuce kawai lafiyar ki itace damuwa ta. "Khaleel Salifa..... "Leave everything to me momy am here don't worry yourself. "Akwai Abinda nakeso infada maka akan Salifa. "Nasan komai momy ki kyalesu I will handle everything. "Hmmm tom don Allah karka kai Naziya cikin gidan nan su cutar da ita....... 🖊


*Jumu'at kareem to All my fans Allah ya sadamu da Alkharin dake cikin wnn ranar Amen *


*Matar Soja*
6⃣1⃣&6⃣2⃣


................Bai fada mata komai ba akansu kawai gyada mata kai yayi, sukaci gaba da magana kasa kasa, tana tanbayar shi me yasa yake son takurawa Naziya, "khaleel kabi yarinyar nan a hankali karka kure mata hakuri fa. "Momy so kike ki shagwaba ta inkina fadar irin haka please karki fada Agabanta taji, nifa ba Abinda nayi mata impact ita yakamata kiyiwa fada tana juyani y'an da takeso. Yafada yana d'an daure fuskar shi, murmushi MOMY tayi na farin ciki da kwanciyar hankali ta dafashi da hannu mai lafiya. " kasan bazan bari kasa min ita kukaba, wannan yarinyar farin ciki yakamata tayi ba kuka ba, khaleel kataba ganin ta daga kai tamun koda kallon banza, duk da Abubuwan da na rika yimata? Ka duba yarinyar nan iya zuciyar ta ta tsaya jinyata batareda ta duba duk cin mutuncin da nayi mata ba a rayuwa. Takarasa wasu hawaye na nadama na biyo kuncin ta, "duba kagani mahaifin ta batareda ya duba duk halin da na jefa Y'ar suba ya kuma daukar ta yabaka, saboda karfin Alkwari da soyayyar da sukeyi wa d'an uwan ka, yau maganar da nakeyi Albarkin Naziya nakeyin ta, da bata cikin rayuwata nasan wulakanta zanyi khaleel Hajiya sharefa tayi mun Abinda bantaba zaton kawa zata iya yiwa kawarta ba,All I want zumunci tsakanin mu ya Kara karfi Ashe.... Hmmm Salifa kuma..
Takarasa kalmar kuka na kufce mata. Tashi yayi ya rungume ta " is OK Momy please komai ya wuce ki manta dasu, kuma nima ki yafemin da na bijire miki kuma natafi na barki.
"Aa bakayi laifi ba khaleel hakan shine ya kubutar min da Rayuwar ka da lafiyar ka nagode da baka Yar da ka hada Rayuwar ka data Salifa ba, danayi danasani na har abada da hakan ya faru domin sam batada tarbiya. "Please Momy ki kwanta ki huta ya isa haka. Yafada yana gyara mata kwanciya ya rufeta tareda komawa kan kujera ya zauna, dafa fuskar shi yayi yana shafawa tareda kallon gefen Naziya dake juyi duk tanajin hirar su takasa bacci saboda farin cikin canji da saukin momy.
Ya dauki lokaci kafin ya ja numfashi ya mike ya koma inda take kwance, gefenta ya rab'a tayi dif kamar tana bacci ya kwanta yana kallon saman dakin na tsawon lokaci kafin ya juya ya rungume ta tsam yana Ajiyar zuciya.
Kai khaleel maye ne wallahi tafada a zuciyar ta, wato koda da idon momy dai sai yayi y'an da yakeso, bakin shi ya Dora dai dai kunnen ta cikin rage murya sosai yace "I no you are not sleeping Hajiya, are you happy momy na takamin birki akanki, Hmm duk wayan Amarya dai sai ansha manta don haka ki gama gudun ki zamu hadu. d'an motsawa tayi domin gadon karami ne Wanda ta zungureshi badon taso ba ya Kara manneta yana runtse idanun shi, "kinsan dai baki kyauta min ba ko? This is the worst punishment for me, gaskiya ina kwaruwa Umm.
Shiru tayi mai Saida taji hannun shi ta saman rigar ta yana kokarin zurawa tayi saurin juyowa domin bashi gargadi da ido, yayi saurin cafke lips dinta, yana kallon kwayar idanun ta, tareda juya mata ido Alamar tayi mai shiru. Ya dade yana shan bakinta kamar mayun wacin Zaki tana kallon tsantsar jaraba kafin ya cire ya dora bakinshi saman wuyan ta yana lasa tareda mayarda numfashi nadan lokaci. Tashi yayi ganin hakan bazai taba yimai ba ya dagata tareda cewa " let go. batason hayaniyar su dashi a gaban momy don haka tabishi tana mai gyara mayafin rigarta, ta dauki wayarta tana dubawa kusan karfe daya na dare.
Cikin Asibitin shiru sai hasken wuta ta ko ina ya bude motar shi ya zaunar da ita kafin ya shiga ya rufe ruf, fuskantar ta yayi tareda janyota zuwa kafar shi ya dora kanshi saman kirjin ta yana Ajiyar zuciya.

Ganin bazai ce komai ba tace" please meye haka wai? Idanun shi da sukayi ja ya dago tareda kallon ta na d'an lokaci kafin ya sanya hannu ya kwantar da kujerar motar yace " keep quit my friend, tunda bakisan damuwa ta ba Allow me to sleep OK. Kwanto da ita yayi kan kirjin shi ya rufe idanun shi Alamar baccin zaiyi da gaske. Kafin kace me yayi bacci ta tsaya tareda sauraran Ajiyar zuciyar shi a natse,. Mamaki ya bata batareda ya tabata ba yasha baccin shi har Asuba, Wanda momy ma batasan fitarsu ba tasamu bacci mai cikeda kwanciyar hankali da kuma saukin da taji a jikin ta,
Ganin Ana kiran salla ga jikinta yayi ciwo domin ya kanan nad'eta ya hanata motsi sam, ta d'an bubbuga shi, ya bude idanun shi, baccin bai ishe shiba tace "Ana kiran salla fa. Mika yayi tareda ita a jikinshi yayi salati tareda karanto Addu'ar tashi daga bacci. "You see is All your foult jiya bansamu bacci ba yau ma bai isheni ba saboda rashin jinki da munje gida nasan zanyi bacci mai dadi.
Batace mai komai ba tafara kokarin sauka a jikin shi, riketa yayi " wai ke meke faruwa ne? Kin zama kurma ne da kike bina da idanu ba magana, ko fushin ne da bansan laifina ba haryanzu? "Muje muyi sallah mutane sunfara fitowa. Sakinta yayi saboda lokacin sallah suka koma dakin, har lokacin momy bata tashi ba sabon brush ta bude tayi kafin tayi alwala ta fito. Tasamu baya ciki, domin dole sai yaje gida he can't pray batareda yayi wanka ba domin yasan ya fitarda Abubuwa duk da bai samu Abinda yake soba.
Sallah tayi ta zauna akan dadduma tayi ta Azkar dinta har gari yayi haske.
Likita yayi matukar mamakin saukin jikin momy lokacin da ya shigo, yace is a miracle a dare daya ansamu improvement sosai domin duk nauyin jikinta ya sauka saura gefe dayan kawai Wanda yace a hankali shima zai warke idan taci gaba da shan magani. Tayi godiya da kanta.
Karfe takwas Aunty Raliya ta kuma zuwa da basket din Abinci ta ga Naziya da momy suna hira sama sama ta rashin sabo domin Naziya kunyar momy takeji ita kuma so take tajata a jiki sosai.

Abun ya matukar farantawa Aunty Raliya rai, ta ko saki jiki da momy sukasha hirar su tanata godiya da sa Albarka, ta sake ta d'an ci Abincin da Raliya ta kawo,zuwa karfe goma Tace zata tafi sai ta kuma dawowa, Naziya ta mike tace zataje tayi wanka ta canja tadawo ta Kira nurse tareda bata umarnin ta kula da momyn kafin tadawo, suka fita tare, momy taso tace ta Kira khaleel mana ya kaita Amma batason ta kuma yi musu katsalandan a rayuwar Auren su tasan komai zai tafi dai dai, Allah dai yabata lafiya.

Saida suka fita aunty Raliya tafara yimata fada, meyasa zata ce zata bita? "Aunty ai yasan zan bukaci wankan yatafi batareda niba don haka bazanje gidan ba nidai muje gidanki, ai kayana da na dawo suna can. Shiru tayi kawai kanin mijinta da yakawota ya mayarda su, koda ta tafi tayi wanka ta shirya ta natsu ta karya. bata samu bacci mai dadi ba jiya saboda nacin khaleel don haka Saida ta kwanta na kusan hour biyu.

Khaleel kuwa bayan ya shirya Saida yaje office dinshi yaga meke tafiya domin baisamu sukunin lekawa ba ya d'an dauki lokaci kafin ya dawo Asibitin, Samun momy yayi da Aunty Zarah da tadawo jiya ta samu labari a wurin Aunty Raliya domin duk ta damu bata samun wayar momyn Kwana biyu, fuskar shi ya tamke ya shigo kamar yaga kashi don Allah yagani ya tsani Matar nan shiyasa ya mugun raina ta, hawaye takeyi tana Sannu aunty Allah ya wulakanta sharefa da zuri'ar ta matsiyata. Sallama yayi ciki ciki ya samu gefe daya ya zauna ta juyo cikin fada " khaleel Amma wallahi kai bakada kishin mahaifiyar ka, yaza ayi ace Suyi ma Aunty irin wannan Abun Amma ka zuba ido ka kyale su?

"Zarah kije ke kidauki mataki da kanki dama kece mai babban kaso a duk Abinda yake faruwa a rayuwar gidan mu, don haka karki manta inkin tashi yimusu hukunci ki hada da kanki kema kina bukatar hukuncin.

"Kingani ko Aunty wallahi Ibrahim ya mugun raina ni sai kace ba kanwar uwar ka nake ba kayita zuba min magan ganu son ranka, wallahi zandauki mataki akanka mtsww. "Hope dai badani kike wannan zancen ba da kuma tsakin, domin Zaki iya fuskantar bacin raina fiyeda tunanin ki, girma na kikayi ko kece kika haifeni da zanbaki girma? Look we don't need you here just leave, go and fix your life first, don munafunci ina kike lokacin da ita yayar taki ke bukatar taimako? Were are you? Sai bayan ta samu sauki ki debo dogayen kafafunki kizo kina kawo mana sanabe were are all your relatives, sai lokacin da munafunci ya tashi ku cikawa mutane gida, look am not like Ahmed duk wadda tasan ba zumunci zai kawota gidan muba she is not welcome, kowace ta tsaya gidan tsohon mijinta, especially you Amara.

Tuni Aunty Zarah ta hadiye bala'in ta ganin ya hau yana faman surfa mata that means ajiraye yake da ita, momy ce tace " khaleel that enough OK. Yace "Sorry Momy were is that girl? "Taje ta yi wanka ta canja tadawo. Dama yasan zatayi hakan wato bazata iya fada mai Abinda take bukata ba sai kawai Tayi Abunda taga dama don taga yana sonta yana lallaba ta, OK zai nuna mata koda yana son mace kuma baya daukar wulakancin ta why take mai yawo da igiyar Aure any how? Haushin ta ne ya saukewa Zarah tass tun ma baiji meya faru ba.
Komawa yayi kan kujera yana Danna wayar shi fuskar shi kamar hadari, momy ta kalle shi tace " khaleel bansan me ke ranka ba, Amma na rokeka haukar da kamun yanzu ta iso kar yarinyar nan tadawo ka rufemin ita dafada.
Shiru kawai yayi domin yakai wuya, zarah kuwa mamaki take ciwon ne ya janyo momy har take damuwa da Naziya haka?
Kallon ta Tayi tareda yin murmushi kawai. Domin ta Riga tadawo hanya sambal bata fatan ta kuma karkacewa,

Aunty Raliya tasa aka dawo da ita bayan ta tashi ta shirya cikin kana nan kayanta ta zura katon hijab saboda shigar domin duk native wears dinta na gidan khaleel, harda socks ta sa baki,
Bayan ta zura after dress a sama saboda koda zata bukaci cire hijabin a Asibiti,
Wata irin uwar kasala takeji da tashin zuciya, da batasan dalilin shiba don haka duk sai jikinta ya mugun mutuwa, koda ta shigo cikin Asibitin zuciyar ta tashi takeyi sosai musamman kamshin pharmacy dake tashi a Asibitin,
A cikin natsuwa ta shiga dakin bakinta daukeda sallama yana nan zaune a wuri daya, muryar ta da yaji tuni zuciyar shi ta sauka yaja numfashi tareda zuba mata ido, ta matsa tareda gaida momy da Aunty Zarah da ta zuba mata ido itama tana ganin mugun canji da murjewar da Naziyar Tayi,
Ta koma kusa dashi ta gaidashi tana yamutsa fuskar ta domin jitake kamar ta koma saboda tashin zuciya,shikuwa kallon al amarin ta yakeyi yana noticing komai duk Tayi sanyi lakwas, tana zama cikin ta ya mugun murdawa Amai ya taso mata, da gudu Tayi bathroom suka bita da Kallo dukan su kafin ya mike yana mamakin ta ko lafiya?
K'ak'arin Aman da takeyi yasa momy ta daka mai tsawa " kabi yarinyar nan kataimaka mata ka tsaya k'ik'am kamar sabon soja. Jefa wayar shi Aljihu yayi tana rikeda washing hand basin sai kwara Amai takeyi ya karaso tareda dafata yana mata sannu, yitakeyi kamar zata Amaye y'an hanjinta dama tea kawai ta karasha bayan ta tashi baccin, Saida ya bata ruwa ta wanke bakinta ya fito da ita, momy jitake kamar ta mike ta taimaka mata da kanta, kwantar da ita yayi akan extra bed din tana maida numfashi, ya zare mata hijabin, "ka Kira likita ya dubata ka tsaya nan kana kallon ta banson shirme. Momy ta fada, duk da zuciyar ta tagama fada mata damuwar bataso Tayi farin ciki saita tabbatar, inko cikine da tafi kowa farin ciki. Yana fita Zarah tace "Aunty ai wanna dagani ba tanbaya ciki ne da ita, don ni tun shigowar ta naga yellow din da Tayi nasan juna biyu ne. "Allah ya Y'ar da da zancen nan Zarah. Momy tafada tana shafa hannun ta mai lafiya,
Likita ya biyoshi ya shigo tareda nurse, yafara tsokanar ta " mai jinya ta koma patient. Jinin ta ya deba yabawa nurse yace taje takai lab ayi P T test.
Bayan minti talatin ta dawo da result,
Khaleel na zaune ya na mamakin what is wrong with her, ta rufe jikinta da hijabinta ta juya mai baya domin kamshin jikinshi ma is killing her, likitan ne ya shigo fuskar shi a sake, ya mikawa khaleel hannu "congratulations sir, a zuciye ya mike kamar mai jiran a taboshi "my wife is sick and you are congratulating me? "Relax Sir Ibrahim, your wife is pregnant.
Yafada yana Kara Washe baki, saurin juyowa Tayi idanun ta a waje "pregnant? Ciki kenan fa? Ita keda ciki? Ciki fa??.
Momy dake jingine ta gyara zama kamar ta sakko takeji ta daga Naziya ta goya sai kabbara takeyi, zata samu Karin zuri'a, zataga jikan ta Wayyo dad'i.
Khaleel kuwa d'askarewa yayi kamar Wanda ya suma, bai taba imagining ciki ba a Auren su yanzu bawai don baiso ba no sai don Abubuwan daketa faruwa da shi na farko rashin Ahmed nabiyu rigin gimun momy,
Yakasa koda motsi yanzu shine keda cikin jikin Naziya? That means he is going to be a Dad? Allahu Akbar. Yayi sujud shukhur, batareda ya duba inda yake ba. Kafin ya tashi ya rungume likita "likita da gaske am going to be a dad? Ya juya wurin momy da gudu ya rungume ta "momy Zaki zama granny. Wasu irin hawayen farin ciki ne suka zubo musu su duka itada khaleel din, Aunty Zarah Tayi dariya tace " congrats Son Allah ya inganta. Sakin momy yayi ya dawo tareda rike hannun Aunty Zarah "Sorry Aunty for all the trouble tank you for your prayers Amen Allah ya inganta min.
"Oh mun shiga uku khaleel bako kunya cikin farko? Koda yake kalli Aunty ma jikan Fari harda hawayen murna lallai zamusha Kallo. Tafada cikeda tsokana, " eh bakomai kifada duk Abinda zakice.
Naziya kuwa reaction din su ya taba mata zuciya sosai har batasan lokacin da itama hawaye ya zubo mata ba, ita bata tabaji ko ganin dokin ciki irin nata ba ace har momy na kukan murna wannan ciki ai Alkhairi ne a gareta, Allah sarki Ahmed Ashe bashi bane uban ya'yan ta Allah mai yadda yaso.
Matsowa yayi cikeda farin ciki yaganta tana hawaye. Da mugun sauri jikin shi na rawa ya karaso "Innalillahi baby ya Zaki fara kuka bayan kinada ciki please don't hurt my baby stop it. Hannun shi akan marar ta yasha yanajin wani irin farin ciki, ya dago kanshi "baby cikina na nan please ki kulamin dashi kidaina yawo ki natsu basai kinyi komai ba ko wanka zanrika yimiki kinji no need ki wahalar min da yarinya.
Gaba daya ya manta da duk mutanen dake dakin likita kuwa Abun ya matukar burgeshi, don haka bai tafi ba, Saida momy tace "doctor ka sallame ni zanje gida inkarasa warkewa idan akwai Abinda za arika yimin zan rika zuwa checkup.
"Tab bansan Wanda yafi wani doki ba keda khaleel Aunty. "Zarah gwara inkoma gidan tunda kinsan halin d'an naki kar yaje ya hana min ita sakewa yajamun Asara. "Tofa kaji likita. "Eh ba wani damuwa sai medication dinta kawai dama ba Abinda muke yimata shi irin wannan ciwon warkewar shi gaba daya dama sai a hankali. Amma Hajiya kiyi hakuri har zuwa karshen satin nan. "No likita discharge me. Juyowa khaleel yayi "no momy please kibari ki Kara samun sauki zan kula da ita karki damu.
Shiru Tayi na d'an lokaci Saida likita ya fita tace "khaleel kana ganin zan kuma shiga Rayuwar ku ne domin inkara hanaku zaman lafiya? So nakeyi inkasance tareda Naziya nasan wahalar laulayi tunda tafara da Amai ga gida bakowa at least ina kusa hankalina zai kwanta.
Gwanin tausayi Naziya ta sakko duk da batajin karfin jikin ta ta matso kusa da MOMY, " momy ina nan tareda ke Sai kinji sauki ba inda zanje. "Aa Naziya gida Zaki koma ki kula da kanki kinji" nidai tare zamu tafi. Tafada tana marai raice wa kamar zatayi kuka. Fita kawai yayi yabi likitan yace " doctor you have to discharge my momy kafin matata ta jamun Asara please, zaku iya hadamu da nurse da zata kulamin da ita kafin ta karasa warwarewa,and inaso ayi mana Ultrasound insan watan cikina da kwanakin shi da kuma lafiyar shi. " that's not a problem dama yakamata hakan, maganar nurse munada kwararru,madam ko yanzu zaka iya kawota muyi ultrasound din.
Godiya yayi ya koma tareda cewa " get ready Aunty Zarah zamu tafi gida baki daya bari muga doctor da Naziya, let go. Yafada tareda dagata suka fito yana makale da ita kamar gold takun ma ji yake kamar yayi mata shi, nan take akayi mata, cikinta kimanin sati bakwai zuwa takwas.
Abu daya ke takura ta shine kamshin perfumes dinshi, is killing her dauriya kawai takeyi, koda suka shiga mota juyawa tayi gefen window ta danna domin iska ya rika shigowa, kokafin su isa gida duk ta bata jikinta da Amai, da kuma motar shi, sai sannu suke yimata duk ta galabaita, don haka suna isa daukar ta yayi MOMY kuwa wheel chair sabuwa Aunty Zarah ta taimaka mata ta turata zuwa gefen ta, da mai aikinta ta gyare fess, taji dadin ganin masu aikin su duk sundawo, gidanta yadawo dai dai, mai aikin tafara tanbaya ko Salifa na gidan? Tace koda tadawo basa nan batasan me yafaru ba. "Ai Aunty kinsan halin khaleel kila yayi musu Abinda ya dace, what ever dai tunda basa gidan Alhamdulillahi.

Gefen Naziya kuwa daukar ta yayi ya kaita bathroom ya mata wanka tsab yana hadiyar yawu domin Allah yagani ya mugun yin kewar ta, dan komai yakara Masha Allah.... Yana mata wanka yana murzar ta duk ya rikice yana mata sannu, "please ka kaini dakin momy banason wannan pefurmse din naka, gaba daya gidan nan kamshin ka yakeyi zuciya ta na tashi I can't stay here please kafitar dani kafin in Amayar da y'an hanji na..... 🖊


"Wnn Abu dai bamai sauki bane wurin khaleel akwai rigima kuwa, baruwana, but I understand ur situation Naziya 😞


*Matar Soja*
6⃣3⃣&6⃣4⃣


................ Tagumi yayi yana kallon y'an da take saurin zura kayan ta, kafin ma yayi wani Abu ta dauki hijabin ta da wayar ta tayi waje, "what is that? Yafada yana mikewa, ko kafin ya zura jallabiya ya bita harta kai sashin momy so take tayi nisa da kamshin jikin shi inba haka ba ta fara Amai kenan. Suna zaune a falon Aunty Zarah ta kawo matsa tea a cup tana bata Naziya ta shigo, kanta akasa ta koma gefen su akan doguwar kujera ta kwanta batareda tace komai ba, tsayawa sukayi suna kallon ta kafin zarah tace " lafiya dai ko akwai matsala ne Naziya? " Bakomai aunty kawai zan kwanta ne anan. "Keda nakeso ki huta shine kika fara yawo bazamu shirya ba inba zaki natsu wuri daya ba. Juyowa tayi kamar tayi kuka idanun ta rau rau tace " momy bana son can ne wani irin kamshi yakeyi dake tadamun zuciya. "Ki fada musu kawai bakyason kamshin perfumes dina ne shiyasa kika gudo nan, ko kuma kinayi ne kawai saboda ki wahalar dani?
Dariya Aunty Zarah tasa tareda cewa "eh akwai Kallo da bana komai da nan zan tare ba ruwana da tv, kai baby bakason kamshin dady tab.
Dukar da kai momy tayi tana murmushi cikin wani irin farin ciki, kafin tace toh ka canja ka kumayi kokarin korar na cikin gidan da wani kamshin tunda bataso karta cutu. Kallon y'an da ta juya musu baya yayi ya kama baki yarasa me zaiyi, kafin ya mike ya fita gidan.
Momy tace "Zarah Kira mai aiki ta bata Abinci, me zakici Naziya? Tace shrimps takeso soyayye da miyar source.
Aunty Zarah ta kyalkyale da dariya " barewa tayi gudu d'an ta yayi rarrafe? Lallai wannan d'an tun baizo duniya ba ya gado tsoho. " inkin gama yiwa surukar taki iya shege ki wuce ki hada mata kinsan mai aiki bazata iya yin yanda zaiyi mata dadi ba, da kafafun na motsi da da kaina zanyi mata. "Bari inje tom. Tafada tana dariya, abun ita kanta ya mugun burgeta y'an da Y'ar uwarta ta dawo kan hanya, dama ita tuni ta tuba bata taba Y'ar da taje wurin wani malami kota aiketa dafe kudin takeyi don tasan intace bazata jeba zasu samu matsala kamar sauran y'an uwan dake fada mata gaskiya.
Don haka ta natsu ta hado mata Abinda takeso, lokacin bacci yafara daukar ta. Momy tace "tashi kici Abinci ina kula dake ba wani Abinci kikeci ba ko a Asibiti. Tashi tayi ta zauna akasa, har wani irin tsinkewa miyanta yakeyi saboda ganin abun da take marmarin ci.
Tafara ci kenan ya shigo da kwali kato, suka zuba mai ido har ya Ajiye tareda kallon y'an da take cin Abincin ta ko dago kai batayi tana wani irin lumshe idanun ta, ya jingina jikin kujera, Abun na matukar burgeshi, Saida ta cinye tas tasha ruwa kafin ta mike ta kai plate din kitchen. Dawowa tayi tana Ajiyar zuciya domin taji ta dam yanzu. "Momy ga shi na sayo Kala Kala ta zaba Wanda takeso inrika Amfani dashi. Yafada yana baje tirarukan masu shegen kamshi da tsada Sunkai kwalba Ashirin,
Ai kuwa da gudu ta tashi tunbai bude ba tayi dakin Ahmed dake part din tana fitar da numfashi dakyar ta samu zuciyar ta ta kwanta.
Binta sukayi da Kallo shima ya ce " what again momy? Aunty Zarah ta ce "kagane kamshin ne kawai bataso saika daga mata kafa har zuwa lokacin da komai zai dawo dai dai. "Till when please, nidai gaskiya da sake haba. Ya mike zai bita momy tace "dawo nan karka sata Asarar Abincin da taci yanzu yarinyar nan Ina lura da ita ba wani Abun kirki takeci ba, Amma baka damu ba, duk damuwar ka kawai ka takurata ka hanata sakat, idan ka shiga wurinta ranka zai baci.
Fita gidan yayi cikin fushi, ita kuwa samun gado tayi taci baccin ta hankali kwance.

haka y'an dubiya keta zuwa gidan suna duba momy y'an uwan ta kusan kullum suna gidan, yanzu ba wani hayaniya ko fada tsakanin ta dasu sai zumunci, haka kawu modu yanzu shima da iyalin shi suna yawan zuwa gidan domin kowa yasan Hajiya balkisu ta canja sosai, zumunci takeyi da gidan malam da Inna, sometimes in suna zaune da Naziya zatace "idan naji sauki kafafuna suka samu zan je har gidan inyi godiya inajin dadin Addu'oin da yake aiko min a jikina, Allah dai yasa agama lafiya.
Khaleel kuwa dole badon yaso ba ya hakura da Naziya, don tun yana satar dare ya shiga tana bacci, zata zabura tafara kelaya Amai kamar zata suma ya hakura da zuwa cikin gidan sai dai ya kirata a waya inkuma ya shigo yaganta yana daga nesa zaiyi magana ya juya, duk ya dawo gwanin tausayi, ankwashe kusan sati biyu a haka ita kuwa ta murtuke takara murjewa da cikar d'an yen ciki. Shiyasa bayako son kallon ta.

Zaune yake a office ya kasa yin komai, Allah yagani shifa ba karfe bane da zai zauna kusan sati uku ba mace bayan yasaba da ita, rabonsu da kebewa tun a bangkok, marar shi har wani nauyi take yimai, ranar bai tsinana komai ba har lokacin tashin shi yayi ya buga mota yayi gida, wani irin zazzabi zazzabi yakeji ma,
Duk ya sukurkuce,
Ita kuwa ranar taci adon ta domin Shukrah tazo ta zana mata lalle ta Y'ar fa mata kana nan kitso mai kyau, ta cancara ado cikin super wax dinta mai kyau taji dinkin yayi Riga da sket ta murza d'auri, tayi kyau fiyeda tunani kamar wata sabuwar Amarya, kana ganin ta kaga mace mai d'an yen ciki,
Dawowa tayi falon dauke da kwanon awarar da tasa Shukrah tayi mata kafin ta tafi, momy dake zaune kan kujera tana duba jarida domin hannun ta daya ya saku saura kafar kawai itama tana janta a hankali yanzu, tace "kici yaji a hankali Naziya karki haifo yaro ya cikamun gida da kuka. Murmushi tayi tana cewa "momy inban sa yaji ba baya mun dadi.....
Shigowa yayi da Sallama kasa kasa, tun shigowar shi ya zuba mata ido yana kallon y'an da tayi kyau sosai, Kirjin ta ya kalla da suka Kara kunbura kamar zasu faso,
Samun kusa da Momy yayi ya zauna tareda yin Ajiyar zuciya idanun shi akanta ya koma kamar wani maraya ya dora kanshi saman kafadar Momy, yana gai sheta, cikin tausaya wa tace "yadai Ibrahim? "Momy am sick. "Subuhanallahi. Tafada, itama Naziya da duk ta kasa natsuwa ta yi saurin dago kanta ta kalle shi domin Allah yagani kwanan nan tana mugun kewar shi so take taje gareshi tanajin nauyin momy gashi ya janye gaba daya, ganin y'an da take kallon shi yasa yace " Momy yaushe zaki Kara yimin wani Aure? Yafada cikeda tsokana. Ture shi tayi a kafadar ta tace " banson iskanci wane irin Aure Kuma? "Momy nifa kinsan na saba zama da biyu kawai kidawo min da fauziya ko ki karamin wani Aure.
Wasu irin miyan kishi ta hadiye tareda ture plate din awarar ta na mai kallon kurulla, dauke kanshi yayi tareda cewa "momy inkin yanke shawara please kiyi sauri kiyimin nagaji da zaman kadaici, and please kisa mai aiki ta kawomin coffee inaso inkwanta ne anan dakina, agyare yake? " yes agyare yake ai kasani, kuma kagama mafarkin ka ka farka ba wata mace a gidan nan again kayi hakuri da wadda kakeda banson iya shege.
"Nidai Momy kiyi min ko inkoma China in dakko miki suruka. Yafada yana juyawa, tayi mugun kunbura saboda kishi yana wucewa dakin shi ta mike tareda d'an gwarar da plate din awarar ta a kasa tayi kitchen. Momy tayi dariya domin tasan wasa yakeyi don ya tsokaneta kuma yayi nasara don gashi tama kasa boye kishin ta, cikin fushi ta hada mai coffee ta nufi dakin nashi lokacin ya kwabe dagashi sai towel ne a jikin shi, yasan kishin ta sosai don haka yayi expecting dinta don haka yanajin anturo kofa yayi biris yana cewa " come in. Y'an da ta d'an gwara jug din coffee din yasa ya juyo yaga takama kugu idanun ta sun ciko, wani irin maida yawu yayi yana kare mata Kallo da sama har kasa,,ace Matar shi ce wannan amma tana mai kwalelen wainnan kayan, kukan data samai ne yasa yadawo cikin hayyacin shi,
Cikin kwantar da murya yace me yafaru? batareda ya matso kusa da ita ba.
Da gudu ta matso kusa dashi tareda fadawa kirjinshi ta kankame shi gam tasa mai kuka mai karfi, "nidai ban yarda ba. Tafada tana murza fuskar ta a kirjinshi ya yi baya tareda zubewa a gefen gadon yana riketa jikin shi na rawa " baby why are you punishing me? Kince bakyason kamshina na hakura na Kyaleki yanzu kinzo kina daukar Alhaki na,yazaki zo kina bugamin wainnan balloons din masu laushi? "Kayi hakuri karkayi Aure please. Murmushin karfin hali, yayi "oh saboda zanyi Aure ne yasa kikazo wurina? Bakya jin kamshin nawa ne yau? Ko zuciyar ki bata tashi yau ne?
Ai kamshin baya damuna yanzu. "Hmm why to baki koma dakin kiba? " kunya nakeji ai. "Ok jekici gaba da zama da Momy ni zanje in Auro wadda zata zauna dani batareda tabarni ina walagigi ba kamar maraya, kinsani baby kinsani this is not easy for me amma kin kyale ni kusan tree weeks marana na ciwo look. Yafada yana zameta tareda zare towel ya nuna mata hajiyar, " kingani she needs you badly kin gujeta bayan kin saba mata da dumin ki da dadin ki. Yafada yana fitar da nishin sha'awar ta da kuma zakuwa. Hannun ta mai laushi ta saka ta kama kamar tanajin tsoro ta d'an murza kamar mai lallashi tace "Sorr..... Saurin kama bakinta yayi domin gudun karya kurma mata ihu momy tajisu, jikin shi na rawa ya dora hannun shi saman marar ta" Sorry baby I miss your momy badly kasa an horani.
Tsit kakeji na tsawon awanni baka kuma jin duriyar suba nidama na tsere don kar in makance, koda naga ankwashe hour biyu na koma naganta dunkule a cikin bargo, yana makale da ita kamar ya shige jikinta yana rage murya, " baby last round please please please.... "Um um wayau ne kace last dazu yanzu kuma kace last nidai a'a. "Oh baby wallahi kece kikaja fa how many weeks? Da wayo yasamu ya shige cikin bargon na kuma guduwa,, domin gwara inyi musu nisa Aunty Aisha ta hanani leken Asiri,
Har dare momy bata kuma jin duriyar suba, tayi dariya tareda wucewa dakin ta da taimakon mai aiki nurse dama zuwa takeyi kullum ta zo ta dubata ta tafi.
Dadduma ta hau ta yita addu'oin ta na neman kariya tareda yiwa Ahmed Addu'a, sukuma tayi musu Addu'ar Daurewar zaman lafiya.
Zuwa dare kuwa tattarawa sukayi suka gudu gidan su, soyayya ta dawo sabuwa fil, tattali da tarai raya kamar ya mayarda ita ciki, Washe gari koda ya tashi yayi sallah da kanshi ya hado mata breakfast ya bata yace su koma bacci kafin suje part din Momy, kallon shi tayi " bazaka je aiki ba? "Yes am the boss so na dauki hutu saina huta kafin inkoma sai duk kinbiyani bashina da kika dauka. "Nafa biyaka tunjiya. " waya fada miki ko yanzu kar'i nake nema yafada yana hayewa jikinta tasa Y'ar Kara, "cikina! Yayi saurin sauka tareda shafa cikin "sorry baby na dady wants more, kasan momyn takace ta mallake ni.

Basu suka fitoba sai karfe shabiyu, sunci adon su kamar ka sace su ka gudu saboda haskawa fuskar khaleel shar ya wani murmure tsab kamar bashi bane jiya kalar tausayi, momy na ganin su taji wani farin ciki, bakin ta kamar ya yage tayi hamdala, suka tsuguna tareda gaishe ta, tace "khaleel ya jikin? "Jiki kuma momy? Waye ba lafiya? Naziya da duk kunya ta gama rufeta ta dukar da kai tana murmushi, "kace jiya bakada lafiya, ka warke ne? Sosa kai yayi yace " oh momy kaina ne ke ciwo dama yanzu kuma yadaina saura kadan shiyasa ma bazanje office ba sai man da sati biyu. "Hmmm yayi kyau Allah ya bada lafiya, shikuma maganar Auren fa yasha ruwa kenan? Tafada tana dariya tareda kallon Naziya, da duk kunya ta rufeta, " momy ni na isa inkara Aure bayan inada mata am just kidding karkija a hanani sakewa kuma.
Haka sukayita raha a tsakanin su, ta mike ta wuce kitchen domin shirya musu Abinci, momy tace " karkiyi aikin wahala kibari mai aiki tayi. " momy zan iya ai. Yana binta da Kallo tareda shafa kanshi yana tuna duk wani moment nashi da ita tareda hamdala.

Saida ta wuce momy tace " khaleel ka kai yarinyar nan gidan su ta gansu tunda tadawo bataje gida ba sai dai su da sukazo duba ni suka ganta. "Zamuje zuwa gobe nasa akawo mata motar ta ma yau zata iso. "Masha Allahu dama yakamata ace Matar ka batada motar kanta, nace cikin motocin Ahmed ka bawa malam daya mana me zakayi da tulin motocin nan daka Tara ka samu wasu kudi ka ware ma ka bada tallafi ga Almajiran da yake koyarwa nasan da Ahmed na nan zai yi hakan. Farin cikin canjin halin momy yakeji sosai yace " momy duk karshen wata ina ware musu na Abinci, duk wani Almajirin Malam baya bara yanzu ana dafa musu Abinci ana basu suturu da Abubuwan rufa. "Toh Masha Allah Allah ya yi Albarka ya Kara budi ya sauki Naziya lafiya.

A ranar kuwa dalleliyar motar ta ta iso sabuwa dal ja mai duhu, tayi farin ciki sosai har momy saida ta lallaba ta fita tagani tareda tayata godiya, tace " madallah saura kuma koyon tuki. "Momy ai na koya a can da mukaje bari kigani ta bude ta shiga suna kallon ta, sai murmushi yakeyi yana kallon yanda ta bayyana farin cikin ta a fili, bai taba yin Abinda yajishi ya faranta mai ba kamar y'an da yau yaga fara'ar ta a bayyane, ga Addu'a da take zabgamai da tafi komai dadi a wurin miji, ta tayar tareda d'an tukawa kadan ta kashe tafito tana mai rungume momy saboda farin ciki, yau itace da motar kanta, " Aa sakeni kije ki rungume Wanda ya siya bani ba. Tafada cikin tsokanar ta, " kyaleta momy ai tsegumi ne yasa ta tsallakeni ina ware hannu. " to rasa kunya. Ta juya ta wuce cikin gidan ta tabasu wuri.
Matsowa yayi ya riko hannun ta "let's go ayimin godiyar a ciki not here yafada yana daga mata gira tareda cirata sama ba ruwan shi da idanun mai gadi, tako sagalo wuyan kayanta tsab, domin ta shirya biya da kudin da ba aganin su....... 🖊


"Toh a hankali dai munkusa kai karshen wanna labarim da ikon Allah don haka ina fatan Allah yabani Iko tareda juriya kukuma Allah ya Kara muku hakuri masoya yakaro kauna ya Kara budi ya warware wa kowa matsalolin rayuwar shi Allah masu Aure Allah ya karo d'an kon kauna, wainda basuda miji Allah yabasu nagari🙏.


*Matar Soja*
6⃣5⃣ &6⃣6⃣


.............. Alhamdulillah Rayuwar tayi dai dai a wurin wainnan ma'aurata khaleel a kullum cigaba yake samu cikin Naziya ya girma sosai ta shiga wata na tara khaleel kullum cikin shopping din baby yake har online yaga sababbi sai yayi oder daki guda ya ware ya shirya kayan harda painting dakin anyi shi irin na dakin yara gadaje hudu different design itadai tace Abubuwan sunyi yawa momy tace ba ruwan ta tabarshi yayi idan taga wani Abu ma ita ke tunamai ya siya, tace "Momy toh ni ko kyalle bai siyamin ba sai baby. "Dole ne wannan kwantar da hankalin ki. Saidai momyn ta siya miki ina zaki kai kaya wasu ma fa ko kalarsu bazaki iya tunawa ba a cikin akwatin ki madam. "Kaifa akwai Wanda yakai ka tara tsumma ko bazaka saka ba,wainnan na Aure ne ka shirya zaka hada akwatunan haihuwa yaro. "Kai lallai zan hado set biyu kuwa harda na Amarya. Yafada ya gudu domin tsokana don yasan ta tsani kalmar Amaryar nan, "ba ason kayan tom. "Ke dalla har yau baki gano halin shi ba ya gane kina nuna kishin kine shiyasa yake tsokanar ki share shi Amarya sai dai yajira ta Aljannah. , momy kafa ta warke tsab zumunci tsakanin ta dasu inna Abun ba'acewa komai, yanzu ta Ajiye aiki tunda tayi jinya, don haka takan ware lokaci kawai domin fita ziyarar y'an uwan ta, ta dunke sosai da gidan kanin mijinta nata wato Alhaji Muhammadu, Rayuwa ta koya mata darasi mai zurfi harta haddace, da kanta idan taga mai bukatar taimako tana taimaka mai, har gidan su Fauziya taje tabawa iyayen ta hakuri sosai suka ce bakomai ai haka Allah ya tsara, Fauziya na nan na aikin ta tasamu wani Alhaji mai mata daya zasuyi Aure abinsu, don haka Rayuwar ta natafiya y'an da Allah ya tsara mata, ta hakura da Khaleel domin tasan baya ta ita, in akwai mace guda a rayuwar shi to itace Naziya, baya ganin wata mace a suffar mata sai Naziyan shi,

Cikin gidan na koma tana zaune a tsakiyar falon ta, tayi kiba sosai ta bude ga kyau da shekinta na nan sai ma kar'i, da tayi, cikinta yayi katoto dashi kafafun ta sun kunbura, rigar less ce a jikinta fubu domin yanzu sune suturar ta, sukawai take iya jin dadin su, madara da milo ta kwaba wuri daya tana d'an gwala,
Momy ce ta shigo dauke da plate din tuwo da miyar shuwaka, tana jin sallamar ta tafara kokarin boye d'an cup din madarar ta, "turus tayi tace " fito da Abinda kike sha ingani. d'an tura baki tayi tace " kai momy bafa komai bane madara ce. " wato bazaki rufawa kanki Asiriba Naziya, anfada miki nauyin babyn nan ya wuce misali ki rage ciye ciyen nan bakyaji. matsowa tayi ta Ajiye tuwon tace " mikon nan dama nasan tunda najiki shiru anan akwai Abinda kikeyi to nagano ki ai.
Sallamar shi ne yasa momy tayi shiru tareda juyawa gefen shi " jinan Ibrahim yarinyar nan zata koma gefe na harta haihu tunda bazaka daina bata Abinda na hanaka ba yazaka rika biye mata kalli y'an da take Kara kunbura kullum.
"Wallahi ba ruwana momy ni ba Abinda nake bata impact nakwashe duk madarar dake gidan nan nima na hakurada shan shayin. " ina ta samu wannan tom. Ta nuna mai wadda ke cikeda cup. Murmushi yayi mai kyau ya matso kusada ita ta dunguri kanta " look baby karkija momy ta rabamu akan wannan Abubuwan da kike yi kinga yanda kika zama kuwa kinkusa biyuna fa, please ayi hakuri da madarar nan. Yafada kamar mai lallashin Y'ar yaye, " wallahi inban shaba jinake kamar numfashi na zai fita don Allah kubari inrika shan kadan bada yawaba. Kallon momy yayi da fuskar tausayi " momy ki taimaka mana kinji.
Tsaki tayi ta tura mata kwanon tuwon "sakko ki mike kafafu kici Wanda zai wanke miki yaro da nono tunkafin ki haihu maza. Tana tura baki ta sakko kasa,
Ta wuce kitchen din ta domin kawo mata ruwa, yayi saurin zama, " baby lokacin tashi office baiyi ba fa nadawo. Dago sexy eyes dinta tayi bayan tasa lomar tuwon ta tace " why? Duk da tasan me ya dawo dashi. "Oh don't pretend like you don't know, kwana nawa rabon da kibarni in huta, nakasa hakurine nadawo. Ganin momy yayi shiru, " kai matsa mata taci abincin ta tunda kai baka lurada taci bataci ba. "Momy nima fa bawanda yadamu da damuwa ta me nadawo yi meke damuna ba Wanda yadamu nazama maraya tun yanzu, toh inta haihu ba mai komawa kaina ma gaba daya. "Ka shirya ma gida zataje wanka tunda ni kun raina ni nafadawa Kulu harma nafara yimata shiri tana haihuwa daga Asibiti sai gidansu sai tayi Arba'in zata dawo.
Dariya yayi harda jingina a jikin kafadar Naziya kafin ya kalli momy da duk sun zuba mai ido suna kallon dariyar rainin wayan shi, "Amma dai momy wannan story ne kawai ba gaskiya bane? "Tatsuniya ce kaji, zaka gani in lokaci yayi. "Gwara ta zamo ta tsuniya kuwa don bazai yuwuba, ina ban Y'ar da ba wallahi, yaron nawa yazo duniya baza akawomin shi gidan ubanshi ba afaramin yawo dashi ina. Tuwon ta takeci tana kallon y'an da ya hakikance yana zuba rashin kunya akan d'an da baizo duniya ba. Saida taci dayawa momy ta kwashi kwanonin tafita ta kyalesu, yana ganin ta fita ya mike zunbur ya dagata sama daga ita har katon cikinta, yayi cikin dakin su na bacci.
Tsayar da ita yayi ya na kallon katon cikinta abun na burgeshi sosai, wayar shi ya ciro yafara daukar ta hoto, yasaba yanzu kusan kullum sai ya mata hotuna saboda gani yake ba macen da ta taba burgeshi da ciki sai Naziya cikin yakara mata kyau da cikar haiba, tazamo hamshakiya. "Nidai kadaina daukata haka bayan nayi muni wannan cikin yasa duk nazama wata giwa. "Keke waya fada miki? Ai bazaki gane y'an da kike burgeni bane badon na matsu inga baby naba da nace kiyita zama ahaka ina more Idona, look at my wife, ba raini kinga duk Wanda ya ganki yasan yes bakya tareda lauzy man nacika ki ta ko Ina. Yafada yana wani bubbudawa.
Rigar ta tube domin zafin dake taso mata duk da iskar Ac dake hura ko ina a cikin dakin, tarage daga ita sai under wear da bra, " nima ai ba raguwa bace kasani nima nayi kiwon ka look at you harda wani tunbi ka Ajiye fa, ka kwashe min farin fata ma. " I agree wallahi, domin bakaramar madara nake kwankwada ba, dole aga canji a jikina baby kedin ba ta wasa bace shiyasa kike juyani yadda kikeso, to yazanyi dole in lallaba ki. Yafada yana shigewa jikinta cikin dabara da wayau, tace " banson wayau fa da dadin baki. " Allah ba wayau sai gaskiya, nidai a samma Almajiri yana bara don Allah. Yafada yana mai dora hannun shi saman kirjin ta tareda hade bakin su wuri daya.
Na janyo y'an kafafuna na gudu domin banason ayi aika aika ina wurin,
Sai bayan hour biyu suka fito cikin wani adon yana faman tarai rayar ta,
Ta lafe a Kirjin shi tana nishi " nidai kajamun bayana na ciwo har wani budewa naji yanayi. "Sorry sorry kinga ki wartsake kafin momyn ki ta hauni yanzu da fada, guduwa ma zanyi office inada aiki da yawa, muje in rakaki wurinta in wuce.
Daga Kofar gidan ya juya ta shiga tana yatsunar fuska, momy na zaune tana kallon labarai a Aljazera tayi sallama.

Can karshen kujera takoma ta zauna dakyar, momy ta kare mata Kallo tace " kai zamani yazo ya wahalar da ita da tsohon ciki abanza, kai khaleel ai dama ina ganin d'an banzan yaron nan nasan me yadawo dashi gida. A zuciyar ta take surutun ta saida taga ta zamo kasa tareda janyo trow pillow ta kwanta akasa, tace " ina shi Ibrahim din? " ya koma office yanzu. "Hmmm. Taci gaba da kallon ta saida taga juyin yaki karewa tace " ke meke faruwa ne? "Bakomai momy. " idan da akwai matsala kifada muje Asibiti yanzu kinji. "Aa babu komai momy.
"To tashi a kasa ki shiga cikin daki ki kwanta kinji kar jikin ki yayi ciwo. Dakin momy ta wuce taje ta haye gadon ta ta kwanta da kyar, maganar gaskiya khaleel yaja mata domin jin bayan ta takeyi kamar zai cire, sai can taji ya tsagaita ta d'an yi Ajiyar zuciya ta gyara kwanciya, tana tunanin halin khaleel, kamar magnet haka ya koma mata gashi baya taba fushi indai akan hakan wannan Abun ne sai yasan y'an da yayi ya mata wayau ya more, All this months bayan dawowar su daga bangkok yaki Y'ar da yaje ko nan da can saboda ita duk da yanada appointment dayawa bai Y'ar da ya tafi ba sai dai yayita wakilta manager dinshi, domin yaso yaje da ita momy ta hana, saboda cikin tace ba inda zaije yakai mata yarinya da ciki sai ta haihu.
Har bacci mai dadi ya dauketa ta zabura tareda tashi zaune domin wani irin amsawa bayanta yayi da ma marar ta bana wasa ba, tuni ta sakko tsaye tafara kai kawo, momy dake falo duk hankalin ta nakan ta tataso ta shigo, y'an da taganta ne yasa tace " ke nakuda kikeyi, kinga y'an da kike gumi, ina kayan haihuwar taku ko baku hada ba ne? Tace an hada suna side din mu Amma momy ai EDD na bai kaiba.
"Banson shirme nidai ina zuwa ta wuce Abinta cikin sauri ta dakko Karamar akwatin ta fita da ita ta. Driver ta Kira tace ya gyara mota zasuje Asibiti,
. koda ta koma abun fa da gaske ne duk ta gigijce tayi saurin saka mata hijabin ta ta rikota suka fito tana yimata sannu,

Ba bata lokaci suka karbeta lokacin tanajin kamar marar ta zata fashe saboda azaba, sai salati takeyi tana Addu'a , Sukace ai Abun yazo gadan gadan don haka sai labour Room, saboda sauri ko wayar su bata kwaso ba, bare ta Kira khaleel din, shikuwa y'an da yaga Tanayi yasa yayi ta Kiran ta bayan fitar shi, wayar kuma na gefen ta, bata dakko ba don tayi ta ringing shiru. Haka ya daure yaci gaba da aikin dake gaban shi domin bayaso ya kuma barin office sai ya gama, can ya kasa daurewa ya Kira layin momy shima shiru lokacin tana Asibiti itama tata na gida.
Bai kawo komai ba ya ci gaba da aikin shi,
Bayan minti talatin ba tareda doguwar nakuda ba ta sunkuto katoton d'an ta kyakkyawan gaske mai farin fatar ta da fuskar ubanshi,.

Nurses sai santi sukeyi suka shirya su duka uwar da d'an, aka fitowa da Momy da sunkucecen miji, ta karba jikinta na rawa tace "Ahmed dina ya dawo kalle shi sak Ahmed saboda fatar shi da idanun shi, taganshi sak d'an ta mai hakuri, wasu irin hawaye suka zubo mata a fuskar ta, ta fara tofeshi da Addu'a tana Allah ya sa ka gado hakurin mai sunan ka. Momy da karfin hali tuni ita ta lakaba mai suna. Saida aka fito da Naziya dakin hutawa ta tuna da ita taga miji jiki na rawa bakinta har kunne sai lokacin ta tuna da zancen waya, tace " kinga saboda rudu ban dakko wayata ba. Saida ta shiga sadin da aka kwantar da ita ta shinfida yaron kusa da ita tace "Sannu Naziya kinji Allah ya miki Albarka kinga Abinda Allah ya Azurta mu dashi, bari insa driver ya dakko min waya ta a gida nabarta kema taki na can kar khaleel yakira bai san halin da ake ciki ba.
Ta fito tafadawa driver wayar ta na falon ta yasa mai aiki ta bashi ya kawo.
Yana shiga harabar gidan misalin karfe hudu khaleel na shigowa da motar shi, badon ya gama ba yadawo sai don yakirasu basu dauka ba, fitowa yayi cikin sauri ya gaida khaleel din yace "ranka ya dade su Hajiya na Asibiti yanzu ma wayarta tace indakko mata.
"What Asibiti? Meyasa tunda ka kaisu baka kirani kafada min ba? Come on bani hanya ya koma motar ya yi reverse ya fita aguje, kardai ya bantalo aiki ne gashi lokacin haihuwar bai gama cikaba sai nan da sati biyu, don haka a high speed ya isa Asibitin, ko wani rufe motar bai tsaya yiba ya wuce da sauri, ganin momy tsaye tana leken hanya ya karasa da gudun shi " Me ke faruwa momy ina babyn take meke damunta ne? Duk ya rude jikinshi har rawa yakeyi karyayiwa kanshi asara, daure fuskar ta tayi kamar mai fushi tace "kai meye haka tana ciki ga dakin can. Ko jira baiyi ba ya tafi a sittin tabi bayan shi tana dariyar rudewar shi,
Tunda ya tura dakin yayi turus domin ganin jariri kwance a gefen ta yana motsa hannu yana cilla kafafu yana kuka tareda tande baki saboda yunwa.
Idanun shi a waje na mamaki yakasa koda motsi saida momy tace " ko in shafa maka ruwa ka suma ne? Cikin tsokana, " momy baby..... my baby.... Da gudu ya karasa ya na kokarin sunkutar yaron ya kasa, "tsaya malam inbaka, kallon Naziya yayi data runtse idanun ta saboda marar ta dake ciwo kadan kadan, karbar shi yayi bakin shi har kunne saboda murna da farin ciki ya zauna gefen ta "baby look at our baby yafada yana kallon kyakkyawan yaron shi tareda riko hannun Naziya daya ya naji kamar ya mayarda su ciki, kukan da yaron yakeyi ne yasa ya ce "momy ko yunwa yakeji ne kinga y'an yake bude baki yana kuka. Yafada yana kallon jan bakin yaron d'an mitsili dashi,
"Ai wannan Yaro zaiyi ci tun da yafito yake wannan tande baki, ga uwar na fama yabari ta d'an huta sai a wanke nonon yasha. "Sai an wanke me za awanke they are clean momy tabashi kawai. Yafada yana kokarin kwantar da yaron, momy tabishi da kallon bakada ta ido, shi ko a kwalar shi, "kai bari ta huta kawoshi inbashi ruwan zam zam da Zuma.
Ta bude kayansu ta ciro wani d'an mitsilin cup da spoon ta fita ta dauraye ta dawo ta bude zam zam da kwalbar Zuma mai kyau ta diga ta zauna tareda cewa "mikon shi saika tashi ka Sanar wa su kulu da gidan kawun ku dasu zarah.
Cikin doki ya mike ya fara kiran number Malam suka fara gaisawa tace mikon nan don tasan baida kunya sai yanzu yayi Abinda zai sata a kunya ita, ta karba tace "Sannu malam ya kokari' to dai kayi Aboki kafadawa kulu tasamu miji na kwace. Yayi hamdala tareda godewa Allah yace toh Masha Allahu Allah ya barmana ya raya bari in shiga infada musu.
Kafin kace me kowa yaji wannan haihuwar kafin wani lokaci Asibitin ya cika makil da d'an gi saida momy ta koreshi, su Shukrah Aunty Aisha Aunty Raliya su Zarah sai hira akeyi, ganin yaron na d'an gine Asibitin na cika likita yace zasu iya tafiya ai komai normal ne daga, d'an har uwar don haka zuwa magrib sun gama hada kayan su ta kirashi bayan ya idar da sallah tace yazo ya kwashi Naziya yakai gidan malam an sallame su. Ta kashe waya, Aunty Zarah dake Rungume da yaron tace " tab Aunty bakiso zaman lafiya Khaleel din ne zai bari atafi da Naziya wani wankan gida y'an da yake wannan rawar kafar.
"Yoh biyemai zamuyi, kinsan y'an da nake fama dashi ne ni zanso taje tayi wankan ta mai kyau a gida cikin natsuwa. "ai momy tunda kina nan da kinbarta malam bazai bari ba ma don bayason wannan al Adar. Inji Raliya, ai kuwa malam ya Kira yakai karar Momy yace " ai baza ayi haka ba Ibrahim bana bin wannan Al Ada, dakinta zatayi wanka kaji karka damu.
Yayi Ajiyar zuciya ya buga mota yayi gidan shi saboda yasan yayi tsiya, suna jin shiru momy tasa zarah ta Kira driver ya kwashe su, tace wato saboda nace yazo ya kai ta gidan shiyasa ya gudu ko? Toh tun baizo duniya ba nake hawa mota d'an ubanshi, su Aunty sai dariya sukeyi itadai tayi tsit tana jiran karon su dashi, don ita tagama murna zata je wurin Inna, don wannan ce kawai damar ta idan ta wuce shikenan sai dai ziyara aje adawo gashi idan taje gida baya barin ta ta dade ya rika damun ta kenan ta dawo gidan shi kamar zata gudu,


Suna shiga harabar gidan sukaga motar shi momy tace su wuce nata gidan da Naziyar zataga tsiya, haka aka kaita har gadon momy Aunty Zarah ta shirya ruwan zafi tareda na jariri, Momy tace" Raliya taimaka wa Naziya tayi wankan bari inyiwa yaron. "Toh tace ta taimaka mata tayi wankan tsab ta gyara jikinta su Aunty Aisha suka gyare gadon tareda baza turare ko Ina na baza kamshi, Aunty Zarah ta shiga kitchen ta samu mai aikin ta shirya farfesun naman kaza da yayi lugub ta hado mata da tuwon shinkafa da miyar Agushi, tana fitowa ta shirya, momy tace su Aunty Raliya suje su kwaso mata duk Abinda zata bukata itada yaron su kawo nan kafin su wuce domin dare nayi.

Oga khaleel na can yana tunanin ta inda zai bullowa Al amarin yaji sallamar su Shukrah, tashi yayi cikin jin kunya dama a shirye yake kawai yana tunanin rigimar da zai tarar yagansu, "Aunty yaushe kukazo? Yafara kame kame " ai mundade da dawowa kayan Naziya zamu kai gefen momy tana can itama........... 🖊


*Matar Soja*6⃣7⃣&6⃣8⃣


...................Fita yayi zuwa cikin gidan fuskar shi a turbune, yasamu momy na magana da Aunty Zarah tana ganin shi tace "here he comes, ni na shiga daga ciki. Aunty Zarah tace " ka taro march khaleel. "Aunty wai me kuke nufi dani ne da zaku ajiyemin ita anan. "Ka gode Allah da ta tsaya ma a nan din kai dai ka lallaba Aunty kafin KO dakin ta hanaka shiga wannan ciccin magana da hura hanci kasan badamuwar tabane better come down. "Aunty mutum da iyalin shi sai anyi tajamai rai? "Ni kaga sauri nake inyi gidana ka gyarota baruwa na. Zama yayi a falon ya dora daya kan daya yana latsa wayar shi saida yaga su Aunty sun gama shigo da kayan suna kaiwa dakin momy Aunty Zarah tace "ku muje Raliya in sauke su Aisha mu muyi gidan mu. "Kutafi kubar mana Shukrah nayiwa malam magana, gobe driver yaje ya kaiki ki kwaso kayanki mu na nan zaki taya mu reno, ga dakin Ahmed can ki je kiyi wanka ki huta kinji.
Toh kawai tace ta wuce, su Aunty suka dauki jakun kunan su suka wuce, saida ya musu sallama ya dawo zai shige dakin momy tace "dakata malam bacci zatayi tagaji karkaje ka damesu. Sanin fushi want solve his problem, yace "Ayya Am momy gaisawa kawai zanyi infito kinji please, gaba tayi jin kukan yaron ya take mata baya, " tashi Naziya daure ki gwada bashi Mama mugani tunda yaki yin shiru.
Dago kanta tayi suka hada ido ya mata kuri tareda kallon kirjin, he is eager to watch her feeding his baby, kashe mata ido yayi momy ta fita da feeding bottle din yaron tace bari inyi boiling kan indawo bashi kinji. "Zantaya ta momy don't worry. Yafada yana matsowa, ta harare shi tayi gaba kawai, saida yaga ta fita yayi saurin kulle Kofar yadawo da gudu tareda zama gefen ta ya rungume ta itada babyn dake kan kafarta, " I love you hayati, tank you so much Allah yayi miki Albarka keda yarona, ya bata fake a kunci tareda manna mai shima yace "meyafi wannan farin ciki a Rayuwa? I have everything best wife and now this, best blessing in the world, sune ya'ya baby we are blessed Alhamdulillah, and Allah ya horemin Abinda zan wadataku insha Allahu batareda kun rasa komai ba a Rayuwa in ina numfashi you want lack anything, kinga am ready next year ki suburbudo min twins or triplets. Harar shi tayi tareda cewa "eh mana tunda haihuwar ba wahala badole kafada haka ba. "Hhhh oh come on baby keda daga fita ina dawowa sai naji good news, tell me how, ya akayi ne? " ai bazaka san ya akayiba tunda kaine ka takalo min nakudar tunfitar ka bayana bai daina ba. Tafada mai komai ya rungume ta gam yana dariya "wow kice akwai wani sirri dake kawo saukin labour amma kike min rowa, OK next time bazan daga kafa ba duk rakin ki. "Nice ma mai rakin? " no ni na isa infada matata jarumace tunda ta sunkuto min wannan katon babyn. karbar shi yayi ya ciro dabino ya mai huduba tareda diga mai ruwan abaki ya fara lashe bakin shi soo cute, yana kallon shi itama tana kallon baiwar da Allah yayi musu, tana godiya ga Allah a cikin zuciyar ta, saida ya kammala ya dora mata shi saman cinyar ta yace "bashi nono ingani kafin momy ta dawo, yasa hannu yana kokarin zage mata zip, ta rike hannun shi tace "wait basai ka cire ba zan daga rigar. " no salon ki danne mai hanci remove the shirt, bai saurareta ba ya zage tareda cire rigar, yaja Numfashi tareda cewa "Hmmm sun Kara kunbura baby. Tana runtse idanun ta taciro nonon a bra ta daga kan yaron ya taimaka mata ta manna bakin shi a kai, kamar yana jira ya cafke yafara ja kamar ankoya mai, tayi Y'ar Kara saboda zafin y'an da yakeja, "yadai? "Zafiiii. " oh meyasa ni idan na kama bakya yin karar? Bude idanun ta tayi tace " naka ai bazanji ba. Tafada tana kashe mai ido. Kuri ya mata na d'an lokaci kafin yace " look you just born karki dauki Alhakina kinga KO yanzu bakisan wane irin hali nashiga ba seeing my son sucking this. Yafada yana dan matsawa, idanun shi na wani lumshewa, ta buge mai hannu tace "zai kware fa. Saida yaron yayi bacci ta zare bakinshi nonon ya biyo domin yariga yakawo, d'an karamin hanky ta dauka zata goge mai baki ya, yayi saurin karba ya saka bakinshi ya sude nonon tas daya zubo, tana kallon shi, kafin ya duka ya lashe d'an mutsilin bakin d'anshi,
"Ruwan nonon kakesha? Fuskar ta a yamutse, dagowa yayi ya daga mata gira Alamar what? No be my property. "Na shanye ruwan.... Bare wannan mai dadin, wow baby zan rika taya yarona shan wannan sweet milk din, meyasa ni da nakesha ba ruwa sai yaro yazo ruwan kezuwa? Hmm bazan taba bari ruwan ya koma ba zaki dauki ciki ki haihu.
"Da gaske kakeyi ko wasa? "What? " shan nonon. Tafada tana kallon shi cikeda son gano gaskiyar zuciyar shi, "of course am serious, in naga dama ma ma ba fura zansiyo ina gutsira inashan nonon ba.
Kyalkyale wa tayi da dariya y'an da yake magana da zuciyar shi daya, kwankwasa Kofar momy yasa ya zabura " good night momyn ki zata fara fada na rufe mata kofa. "Zakazo ka bude ko sai ranka ya baci. Tafada da karfi cikin fada. Yayi saurin budewa ta tureshi ta shigo "bani hanya uwar me kakeyi harda rufe kofa don iya shege kabarni waje yarinya ta haihu yau ma bazaka daga mata kafa ta kwanta ta huta ba. "Haba momy biki fa takeyi mezanyi mata. "Fita don ubanka mara kunya. Tafada tana kokarin kaimai jifa saboda ya fassara ta, dariya yasa yana cewa "Allah ya barmin ke momy natafi nabarki da Ahmed da momyn shi, nayiwa d'an ki takwara. Fuskar ta ta Washe "Allah yayi Albarka ya raya Ahmed. Tana share hawaye da suke kokarin zubo mata. Naziya ma saida taji jikin ta yayi sanyi ta kalli yaron a zuciyar ta tace "Allah yasa kayi halin mai sunan.


Cikin kwanakin ba karamin gata da kulawa take samu a wurin Momy ba, harma da d'an gi, har malam yazo yaga Abokin shi Inna dai taki zuwa saboda Kara momy tayi tayi tace mezan zo inyi da wani miji bana bukata nabar miki Hajiya balkisu, tace toh nagode nikam ina son Abuna, su Aunty Raliya kullum sai sunzo zuwa yamma su tafi, angon k'arni baida sakat Yanzu saboda taron mutane a kullum, saidai yasa Shukrah ta kawo mai shi yaganshi uwar tayi tsadar gani,
Har zuwa ranar taron suna daya tara d'an gi da y'an uwa da Abokan Arziki, Wanda khaleel ya gwangwaje su da shatara ta Arziki Abin ba acewa komai sai sanbarka, momy ma bakaramin kudi ta ke kashewa little Ahmed ba Wanda sukewa lakani da Nur, domin shidin hasken zuciyar sune baki daya, harda sabuwar mota ya d'an karo mata, ranar suna, Ana tsaka da taron aka kawo mai ita, sai lokacin ya shigo cikin gidan duk da taron mutanen ya Kira Aunty Zarah yace " please ku Aramin mai jegon minti biyu, momy ta fito da fada, " kai wai baka ganin taron mutanen nan ka ratso kana wani neman ta mezata yimaka?
Dai dai tafito cikin Adon wani d'an kareren leshi mai shegen kyau da tsada tana walwali tasha kunshi kafafu da hannu ga wani head da aka nada mata ya zauna kamar wata sabuwar Amarya ba mai jego ba, kowa idanun shi ya koma kanta, harda uban gayyar, wani irin narkewa yaji zuciyar shi nayi ganin ta, zai iya rantsuwa ba wata mace kamar Matar shi a duniya, tuni aka fara kashe mata hotuna, kallon ta takeyi da wani irin sirri Wanda tuni ya fahimci itama tana kewar shi don haka bai damu da idanun mutane ba yafara takawa cikeda kasaita dajin yafi kowa sa'a ya matsa kusa da ita tareda rikota, ya ciro dalleliyar wayar shi ya mikawa Aunty yace "snap us Aunty. Akasa shewa domin bakaramin daceew sukayi da juna ba, ga shaddar jikin shi tayi Kala da tata, yaci hula tangaran, ita kanta tasan tasamu miji, yes she can shout out loud and say this is my husband, kowa yaji, ya mugun yimata kyau kullum Kara murjewa yakeyi, she really admire him, har wani kishi taji yana d'an tabata don akwai y'an mata na family dayawa a gidan datasan wata zata iya k'yasa mata miji, don haka ta rike Abinta kam,
D'an dukowa yayi a kunnen ta " let go out side I have a surprise. Yajata suka fita ana binsu da guda tuni momy ta kauce tana farin ciki, duk da harabar gidan akwai motoci birjik bai hanata hango wannan farar motar sabuwa dal ba taji flowers da balloons a gabanta an manna sticker katuwa mai daukeda "For you my wife.
Kafin ta ce wani Abu ya d'an ka mata key din "tank mom nur. Tareda dora mata kiss a bakinta, wasu irin hawaye na farin ciki suka fara gangarowa a fuskar ta, takasa cewa komai domin bakaramin kaya ya d'an karo masu ba, harda gwala gwalai na kece raini da batasan ta ina zata fara sakasu ba, Rungume shi tayi tareda cewa " ina kakeso insaka kaina saboda farin ciki this is too much my love.
Kara rungume ta yayi yana murmushi mai cikeda farin cikin my love data kirashi, " kin biya ni yanzu yanzu for calling me your love baby, I want you to love me more only me, ki nuna min so ki tarai raye ni ki maidani d'an lelenki that's all what I want from you.
"I love you dadyn Nur,zan nuna maka duniya ma zata shaida hakan because I really do love you, you are the best husband the best father and the best son, am very proud of you Allah yakara Arziki da budi yakuma tsaremin kai.
Dagata yayi cak yana juyi da ita duk da mutane na yawo a wurin ko ajikin shi, " Wayyo dadi kice inrika kawo miki surprise domin insamu Addu'a da wainnan sweet sweet words din. "Kai son irin wannan Abu a idanun jama'a? "Kai Aunty wallahi keda momy kunason hana ruwa gudu, sauka tayi cikin jin kunyar Aunty Zarah tace "Aunty nayi sabuwar mota. Tasa guda tareda cewa Masha Allahu Allah yasa Albarka, gaba yayi yabarsu ganin duk Anfito ana tayata murna, tabi bayan shi da Kallo, she feels like following him ganin ya shige gidan su,
Yanzu take blaming kanta na kin bashi kulawa sosai duk da suna gida daya batasan wane irin hali yake ciki ba, tasan momy na kulada cikin shi, Amma tasan halin shi ta gefen rashin hakuri ta wani wurin gashi bai samu damar complain ba,
Haka taron sunan ya ci gaba anci ansha sun samu sha tara ta Arziki, har zuwa lokacin da kowa ya watse yarage daga momy sai Shukrah domin har naman sunan ma da rana aka soyeshi aka rabe Abunka da manya, nidai nasamu naci hanji domin a cikin naman suna ba Abinda yakai hanji dadi, don haka ni acan na makale.
Tun karfe tara momy tace Shukrah ta koma dakin ta wurin Naziya tanaso tasha magani ta kwanta tagaji da yawa yau. Naziya tace "gaskiya momy kije ki huta tunda akayi haihuwar nan bakya wani hutawa. "Toh miji fa nayi badole ba, nasa sun kai muku duk kayan da kuka samu gidanku kafin sutafi. "Toh Allah yakara girma momy da lafiya. "Amen. Ta yiwa Nur Addu'a ta Kara rufeshi ta fita, tana fita Naziya ta mike tace "Shukrah zanje wurin Baban shi don Allah karkiyi bacci ya farka yayita kuka, har momy tagano bani. "Hhhhh ba ruwana idan nayi bacci yayita bare baki. "Don Allah karkiyi zandawo zuwa karfe goma nan da thirty minutes kinji. "Toh kiyi sauri. Matsawa tayi ta gyara jikinta da kyau tareda feshe jikinta da kamshi ta zunbula katon hijab ta sudada ta fice.


A zaune yake yana kallon hotunan su na dazu yana murmushi, kallon bangon falon yayi inda ya jera hotunan su a bango daya na farko nashi na tsakiya Nur sai nata a gefe, tunda aka haifeshi yamai wannan hoton yasa A gidan, bata ma sani ba,
"Allah ya jikan takwarar ka, yaya Ahmed banda kamar ka duk duniya kayimin komai kana raye katafi kabarmin Abinda zantuna dakai a kullum, Naziya itace kyautar da tafi komai da kayimin a duniya, look at your name sake he is just like you. Yafada yana danna hoton Nur ya bawa wayar kiss "I love you my family, I miss your mother soo much my son har bana iya bacci saboda kewarta. Yaji anturo kofa, a hankali yayi saurin juyawa, zabura yayi tsaye "baby!!!!, ist really you? Hijabin ta tacire tareda ratayawa a jikin hanger ta fara takowa cikin y'anga domin Kara siyemai zuciya. "Yeah nice ko sai na nemi izinin ina son ganin mijina? Jikin shi na rawa saboda tsananin farin ciki Da murna ya karaso da gudu ya rungume ta. "Wow my baby am very happy for this special visit, were is my son? " nabar shi da Shukrah nace bari inzo in shayar da dadyn shi shima tunda shi ya koshi. Saurin dagowa yayi ya zuba mata ido domin kalmar ta tasa yaji tsigar jikin shi na wani irin mikewa da yin zillo, yafara kallon rigar bacci dake jikin ta baka ta lafe saboda silk, kirjin nan dake cike sun wani irin tsone mai ido saboda kunburi, cikin wani irin rawar murya yace "da gaske baby you are going to feed me your special milk? "Yes if you really want t..... "Ofcos I love too ya sunkuceta sai kuryar dakin, sai samata Albarka yakeyi, sanin yayi matukar kewar ta ta dage tabashi taimako sosai har yasamu natsuwa, yana lafe a jikinta sai kissing dinta yakeyi ta ko Ina yace " tank you baby, ina momy kika zo nan? Kara rungume shi tayi tace "tayi bacci da wuri kasan tagaji dayawa, nabar wa Shukrah na gudo nan. "Naji dadi sosai baby ta damu dani sosai. "Bari in koma kar ya tashi yafara kuka Asiri na ya tonu. Tashi yayi ya zauna tareda kallon y'an take kokarin mayarda rigar ta, "kiyi wanka mana. "Sai naje can banda pad inna cire anan. "Wai yaushe wannan abun zai dauke ne yaufa sati daya. "Kai ance sai mutum yayi Arba'in fa. "What da sake fourty? "Bakowa bane fa ni bansan nawa kwana nawa zaiyi ba, "please idan ya tafi kifadamin I can't wait, kinga yanzu kinki bari ko gogawa inyi kadan am missing it "you are shameless. Tafada tana direwa a gadon da gudu, yabita..... 🖊


*Matar Soja*
6⃣9⃣&7⃣0⃣..... 🔚


*bazan rufe wannan lbr ba batareda godiya a gareku ba y'an uwa marubuta, kun nuna min kauna ta gaskiya kunbani goyon bayan da bazan taba mancewa ba*
Gareki my writer SA'ADATU BINT ABDULLAH,
tareda ke AUTAR MANYA, karamcin ki bamai faduwa bane Allahu yabar kauna da soyaya.
Hazika mai yayi fasihiya NIMCY LOVE jin jinar bangirma.
Hakurin ki abun kwatance ne my Aunty, BINTA UMAR ABBALE.
ina maganar hakuri karamci bazan manta dakeba MAMAN NURUL HUDA.
Addu'a tareda jinjinar bangirma mai rubutu da ilimi da hangen nesa HASSANA D'AN LARABAWA.
... GARKUWAR MARUBUTA uwa maba da' mama Allah yasa ki gama labrin tubali lafiya,
Kunada matukar yawa bazaku fadi dukaba sai dai kusani duk kuna zuciya ta Allah yasadamu da Alkharin sa Ameen.
Sakon ta Aziya garemu baki daya na marubuta biyu da muka rasa kwanan nan Allah muma yasa mu cika da kyau da Imani, ina kewar ki Zinariya Allah ya Albarkaci Abinda kika bari. Amen Amen


..............shiya rakata har cikin dakin Shukrah nata baccin ta, Nur yafarka tareda saka hannu yana wulwula kafafun shi na shirin yin kuka, da saurin shi yana dariya ya daukeshi tareda fita ya na mata ido ta biyoshi, dakin shi suka tafi ya shinfide shi a gadon shi ya na mai wasa, saida ta shige tayi wanka tafito takarbeshi yana kallon su ta bashi nono ya cafke yana sha, matsowa khaleel yayi tareda hadasu ya Rungume, "my boy na maka wayau nasha nima. A wannan daren baiyi wani baccin kirki ba yana nan makale da iyalin shi, harta ti bacci haka ya zuba musu ido yana godiya ga Ubangiji,
Tsabar gajiyar da tayi batasan gari ya waye ba, haryayi wanka ya shirya ya dauki yaron shi yafito falon dai dai momy na tanbayar Shukrah ina Y'ar uwar ki take? Bata kaiga bada amsa ba tayi wuki wuki domin ba Naziya ba har Nur batasan inda yake ba itama tayi baccin gajiya, "ga jikan ki nan Momy. Suka juya tareda zuba mai ido yana wani irin sheki da daukar ido, "kai ina uwar shi take? "Bacci takeyi Momy kinsan gajiyar taro. Kallon Shukrah tayi tace jeki nemi breakfast kinji, kai kuma mara kunya bani shi inyi mai wanka, Allah ya shirye ka, don iya shege don nayi bacci ka lallabo kazo ka takure yarinya bayan tagaji, kaga kabi yarinyar nan a hankali tana biki karkasa ta kwainuka. "Meye haka kuma momy? Ubanka modu ne. "Momy ba ruwana ita tabiyo ni dakanta fa narakota shine muka kwana anan. "Allah sarkin y'an sharri? "Oh yanzu baki Y'ar da ba Momy? " get away. Ta wuce Abinta. Yayi dariya tareda cewa "sai kin shafa kinga takoma gidan ta zaki gane itama tana kewa ta.

A haka sukaci gaba da jegon su cikin gata da kulawar momy Shukrah dai sati biyu tayi dakyar inna tace abata Y'ar ta haka, momy tace ai mungode ma ko a hakan kulu. Shukrah ansaka ranar ta da Almajirin malam sadiq, tuni anfara shirye shirye, Wanda khaleel ya biyawa malam da Inna Ummara harma da Shukrah, yace su hajji zasuje bana shida Naziya in Allah yakaimu, sunyi murna sunyi farin ciki sunyi Addu'a tareda sa Albarka.
Momy ce ta tsaya tsayin daka ta hadawa Shukrah kayan daki dana kitchen kafin su Inna sudawo Ummara, Wanda koda suka dawo suka tarar da Abin Arziki, malam Yayi ta fada yace abun Yayi yawa, momy tace Shukrah Y'ar tace da Ace tanada wani d'an ma shi zata bawa ta hada su biyu a gidan ta, domin ba Wanda yaki irin Arziki a gidan shi, suna dawowa aka fara shirye shirye, Nur nada wata biyu, Yayi bulbul, kullum suna hanyar gidan malam a cikin motocin ta sai wadda taga damar hawa, wani lokaci harma ta khaleel tukawa takeyi, kowa yaganta yasan yes tana cikin lokacin ta a gidan mijin ta, tazamo Y'ar gata gidan miji da cikin d'an gi,su suka dage suka gyara kanwar su wadda itama tabi tana gyara kanta domin tasani tana tareda gwarzon miji, da baya gajiya da ita.

A haka sukayi Auren Shukrah cikin girma da farin ciki kowa ya koma gidan shi ya tsuguna, Wanda saboda karamci malam yabawa kawu modu wakilcin uban Amarya shi yayi na ango Wanda ya mugun farantawa kawu dasu khaleel rai, harma da momy tayi farin ciki Wanda wannan dalilin yakara musu Y'ar da da shakuwa a tsakanin su.

Ina labarin su Salifa? Tuni momy ta roki khaleel tareda sa bakin Naziya yasa aka kyalesu, sunyi matukar nadama domin sunga jarabawa don Salifa tuni tafara wani irin ciwo duk ta rame ta fita hayyacin ta Wanda koda aka kaita Asibiti gwajin farko aka gano ta daukeda ciwon zamani, tayi kuka momyn ta harda suma saboda tashin hankali haka ta zauna jinyar ta gata itama kwankwason ta sai a hankali tun buguwar da tayi, fadin halin da suka shiga ma bata lokaci ne, don haka Allah yasa muyi kyakkyawan karshe a rayuwar mu.

Bayan wata shida da haihuwar Nur, a zaune take tana share hawaye yana faman lallashin ta, kallon pregnancy test strip din takeyi tana share hanci, dariya yake hadiyewa ya kalli d'an shi dake zaune yana wasa da kayan wasan shi yayi kamar d'an larabawa saboda sha'awa, "what is your problem Momyn Nur? " kaine matsala ta nafada maka tunfarko muyi planing kaki now look yarona six months ace inada cikin wata biyu, gaskiya kasan y'an da zakayi dashi. Hade fuskar shi yayi for the first time a rayuwar Auren su dayaji ta mugun batamai rai, ya mike zunbur ya fita sai gidan Momy yana huci.
Zaune take sanye da eye glass tana karatun jarida ya shigo a fusace ya zauna tareda dafe goshi. "Kai lafiya ka shigomin gida bako sallama?
"Please yarinyar nan ce fa momy zambata mata rai? "Wace yarinyar ka keda ko ka Haifa a gidan nan inji? " Momy Naziya, wai... She is crying because she is two months pregnant, tundazu take kuka ina lallashin ta, can you imagine she have the gut tace incire cikina momy my baby. Yafada yana nuna kanshi, Ajiye jaridar tayi tareda zuba mai ido nadan lokaci kafin tace "now tell me how you react to her, kayi mata hauka ko? Jinan kar inji kar ingani wai ka hau Y'ar nan da fada, yoh badole tayi kukaba yaro d'an wata shida ace ciki wata biyu. "Ni bance komai ba kawai nafito ne. "Better.
Mikewa tayi taje gidan tareda barin shi anan, tana ganin Momy ta goge hawayen ta, matsowa tayi tareda zama kusa da ita Nur nata washe mata baki tareda mika hannu ta daukeshi tana mai wasa kafin ta koma kan Uwar.
"Naziya. "Na am momy. "Ina ilimin ki yaje? Ina hankalin ki ya shiga, bakin ciki kikeyi saboda Allah ya miki baiwa,? Kinsan cewa yaran nan biyu dana Haifa ba a son raina bane, naso in tara yara Allah yagani sai ya kasance tundaga Ahmed da Khaleel ban kuma samun haihuwa ba, kinsan me, ina matukar farin ciki kuma ina son duk Abinda zaku taramin koda dubu ne inda rai da lafiya zanrike muku su, kika sani ko biyun sune rabonki? Karki kuma fadar a cire miki ciki koda daga Arba'in kika samu wani kinji ni.? " toh Momy kiyi hakuri. "No mijin ki zakibawa hakuri bani ba. Ta mike da Nur ta fita daga gidan dai dai yana shigowa, "ka Kara lallabata yarinya ce Ibrahim, ta wuce.
Yana shigowa ta tashi tareda nufar shi ta rungume shi gam, "Am sorry Abban Nur, bazan karaba kaji forgive me. "No problem karki damu am ready to take care of you and my child, cikin minti kadan sun gyaro Al amarin su tareda taimakon Uwa tagari a yanzu.

Alhamdulillah, cikin shekara biyar Naziya ta Ajiye yara Hudu bayan Nur, tayi twins maza sai Karamar su yanzu da take goyo balkisu wato Ummul khair, gaba daya batasan wahalar raino ba kakarsu ta dauke musu komai, haka take bin mijin ta duk inda zaije hankali kwance sun yawata kasashe a wannan shekarun, idanun ta sun bude sosai ta Kara wayewa tareda Aji, taso taci gaba da karatu Amma ganin khaleel bai so kuma ya bude mata hanyoyin samun kudi da yawa business center nata nakanta Wanda tafi karfin hidima tundaga dubu daya zuwa dari biyar har million, y'an uwan ta ma sun shaida ita din mai sa'ace.
Kudi na musamman tasa khaleel ya ware tareda gina wata babbar makaranta mai suna Ahmed foundation, wadda take taimakawa marayu da basuda karfi suke samun kulawa sosai batareda ko sisin suba,
Momy ta Ajiye aikin ta tuni bata zuwa sai kula da y'an jikokin ta, haka zata zuba Abinta a mota suje ziyara gidajen y'an uwa, har gidan malam sai suje su wuni susha hirar su sai sun ishi inna da barna tace "Hajiya balkisu ki kwashi mazajenki sun isheni da barna suna fama da jajayen kunnuwa. Haka zasuyi ta raha a tsakanin su, haka take zuwa gidan kanin mijin ta ma, ta canja sosai kamar ba itaba,
A cikin wannan satin su Naziya suka shirya fita bangkok kamar duk kowane karshen shekara yanzu saboda kasuwancin shi. A dai dai lokacin Ummul khair nada wata takwas kuma tagano tana daukeda wani cikin don haka ba wani dogon bayani ta cireta tareda Ajiye wa takwarar ta tabi mijinta domin su hole, tuni ta gano cewa Matar so ke gwarne don haka ta daina damun kanta domin duk cikin dazatayi khaleel na farin ciki, toh meye damuwar ta Sai muce Allah ya karo Arziki da zaman lafiya a tsakanin wainnan ma Aurata...... Pen's 🖊
Alhamdulillah nagode wa ubangiji da ya nufeni da ganin karshen wannan littafin
Dubun godiya gareku masoya aduk inda kuke, my Real fan's wato AUREN GADO paid grp one and two, domin kune real fan's dina domin kun nunamin kauna da soyayya ta hanyar rububin siyan wannan labarin, fatan Alkhairi agareku bazan taba mantawa da Alkharin ku da hakurin ku gareni ba,
Ina rokon Afuwa saboda yanayi na jinkiri da aka samu akan wannan labari, ba son raina bane kana naka Allah na nashi, this is the though time for me saboda situation dina, am sorry duk Wanda na batawa rai a wannan tafiyar, saboda ajizanci na d'an Adam, ku yafemin don girman Allah.
Darasin da na ke son y'an uwa su dauka a wanna lbr shine, kaso mutum don Allah,mucire hassada son zuciya handama mugodewa ubangiji da duk Abinda yabamu a Rayuwa, sannan kuma Muna fatan muyi kyakkyawan karshe irin na momy Allah ka nufemu da gyara kura kuranmu kafin mutuwa. Ayi Amfani da Abinda zai amfane mu a wannan lbr sannan mu watsar da duk Wanda baida Amfani kuskuren da ke ciki Allah ya gafarta min Alkharin dake ciki Allah yasa Al umma su anfana dashi,
Dubun godiya gareku masoya da nake bawa a pc kunada yawa, lallai soyayyar ku babbace a wannan labr da kuma gareni Nafisa na yinku over Allah ya karo Arziki ya kareku daga dukkan sharri.

*TAMMAT BIHAMDILLAH*
Chapter 3 · 0% Book details