← Book details Akan Aiki Na Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 4

Gabatarwa

Akan Aiki Na Complete Hausa Novel · about 25 min read

💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKI NA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚


*Labarin gaske*✍🏻


Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)
Miss green💚💚


_BISMILLAHIR_ _RAHMANIR RAHIM_

GABATARWA:dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah(S.W.T)Salati Mara Adadi Zuwa ga Manzon Rahma(S.A.W)


Tsokaci:Wannan littafin Ban rubuta shi don cin mutuncin wani/wata ba duk wanda yayi dai dai da rayuwarshi to yayi hak'uri akasi aka samu,Wannan littafin gaske ne ma'ana ba labari ne k'irk'irarre ba.


Sadaukarwa:Ga dukkanin mosayana Ummu Maher,Mu samman👇👇👇

Nabila dikko
Nabiha Aminu
Ummu Najma
Zahara'u Nasir Aliyu
Amina .m.Baso

duk ina godiya,da dukkanin mutanen da ban ambato su ba to suyi hak'uri.

Abbakar.Ak saraki
da
Ahmad isah Koko
Inq godiya sosai da kulawarku gareni🙏


*Babi na d'aya📝*


Malam!Malam!!Malam!!fito kaga i'kon Allah yarinyar nan ta suma,Malam ya fito da gudu yana kallon yarinyar ya kalli Inna Majaifiyarta yace maza ki d'auki Mumtaz ki ku fito bari in kirawo Alhaji mu tafi asibiti,Sunan yarinyar kenan Mumtaz.
Kafin Malam ya dawo Inna ta kalli k'afar Mumtaz sai taga jini yana malala kamar ruwa da gudu ta fito k'ofar gida tana kiran Malam.


*Wacece Mumtaz*
Mumtaz dai shine asalin sunan ta wanda Mahaifinta ya saka mata saka makon sunan Mahaifiyarshi ne ya saka wa Mumtaz, Asalin Malam Abdullahi Mahaifin Mumtaz y'an jihar Bauchine wanda sun kasance y'an kasuwa ne sosai gidansu suna siyar da kayan masa rufi ta hanyar ne suke samun na cin abinci kuma i'tace hanyar abincin su.
Kwatsam sai karayar Arzik'i ta samu mahaifinsu Malam Wannan abun ba k'aramin tada musu da hankali yayi ba.
dalilin da yasa karayar Arzik'i ta same shi shine Mahaifinsu su Malam Wato Alhaji Jibrin shine yanada wani aboki d'an asalin Maiduguri Alhaji Bukar kusan ma Amininshi shi ne sana'ar Alhaji Bukar shine siyar da dabbobi daga wannan gari zuwa wannan gari.
Kwatsam sai wataran Malam Bukar yakawowa abokinshi Alhaji Jibrin ziyara yaga yadda ya bunk'asa da kasuwancinshi na siyarda kayan masa rufi.
Abun ya tsayawa Alhaji Bukar har yaushe Jibrin zai zama haka a kasuwanci bayan ya fishi tunda ga nan Alhaji bukar ya kafawa abokinshi Jibrin tsana mai tsanani Ya fara bin bokaye don ya raba shi da dukiyarshi,Har yayi nasarar rabashi da komai nashi ya zamo duk abunda ya tab'a sai yayi asararshi tun daga wannan lokacin Alhaji jibrin Mahaifin Abdullahi ya shiga wani mummunan talauci ya zama na koda kayan da zaisa ma sun fara lalacewa sai ya shiga wanka sun bushe sannan ya saka su.
Ana haka wataran Alhaji jibrin ya fita neman tai mako gidan wani mai kud'i kawai sai ya jiyo kukan wata jaririya cikin bolar kusa da k'ofar wani gida kamar zai wuce kuma sai ya dawo ya duba yaga jaririya ce aka yar kyakkyawa da'ita kamar y'ar larabawa ya d'auketa hannunshi yana kakkarwa ya nufo gida,yana zuwa gida ya nunawa matarshi Adama mahaifiyar Abdullahi da yake ita kad'ai ce matarshi kuma Abdullahi shi kad'ai ne D'an ta don haka koda Alhaji jibrin ya kawo mata wannan jaririya ba k'aramin jin dad'i tayi ba sosai don haka ta rik'e yarinyar da hannu bibbiyu.
Abdullahi kuwa duk duniya ya nuna ba shi da wacce ya keso sai Wannan yarinya wacce Alhaji ya saka mata suna Maryam,Tun tana k'arama yake sonta duk abunda ya samo to na k'anwarshi ne Maryam koda ta girma sai abun ya koma soyayya sosai koda iyayen suka gani sunyi murna sosai.
don haka da taimakon y'an uwa da mak'ota aka hahhad'a akayi musu Aure.
Ranar bikinsu ne wani mummu nan labari ya samesu'cewae Mota ta buge Alhaji Jibrin ya mutu Har lahira.
Sunyi kuka sosai da mutuwar mahaifin nasu mai son Su da nuna musu k'auna.
Koda akayi Auren Inna Adama mahaifiyar Abdullahi tace su zauna agidan tunda gidan yana da girmanshi haka kuwa akayi suka zauna agidan.
Ana haka wataran Inna adama ciwon ciki ya kamatq cikin dare ko kafin a kaita asibiti tace ga garunku nan ta mutu har lahira tashin hankali sosai Abdullahi da Matarshi Maryam suka shiga,Ana hakane kuma Maryam ta samu Ciki watanshi biyar ya zube saboda rashin kulawa don har yanzu suna cikin talauci sosai.
Saida Maryam tayi shekara Goma sannan ta haifi Mumtaz wannan shine labarin Mahaifan Mumtaz.


*Ummu Maher ce* Miss green💚


*Vote*
*Share*
And
*Comments*📝
*Tyiping*🖌️

ABOUT MY WORK✍🏻
💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚


*Labarin gaske✍🏻*


Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green💚📗
بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

🏔🅙︎🅦︎🅐🏔


*BABI NA 2*📝

Malam kazo da sauri Mumtaz tana zubar da jini da sauri "Alhaji yace to Mumtaz d'ince babu lafiya yanzu Malam yake fad'amun bari muyi sauru mu tafi Asibiti kiyi sauri ki fito da'ita.
Umma tayi saurin komawa gida ta fito da Mumtaz suka tafi Asibiti,shan kwanarsu kefa wuya su hancin motarsu Amal ya kawo kai Amal tace Mama kamar Motar Dadyne naga yafita daga gidan kuma naga yana sauri sosai Allah dai yasa lafiya Mama tace to Amin.
Amal da zumud'inta ta nufo gidansu Mumtaz tana son ta nuna mata kayan da ta suyo akasuwa sai taga gidan Arufe an saka kwad'o ta ce Afili to yau kuma ina su Umma suka tafi dukkansu Allah dai yasa lafiya tayi saurin komawa gida don gayawa Mamanta.
Likitan tace Alhaji munyi iya k'ok'arinmu don ganin cikin jikinta ya tsira Amman hakan ya faskara sakamakon maganin zubarda ciki da tasha.
Malam da Alhaji harda Umman Mumtaz saida abun ya tab'asu sosai sakamakon jin wai Mumtaz ce take da ciki ne da'ita to waye yayi mata cikin? suka had'a baki wajen fad'ar hakan likitan kuwa har tayi tafiyarta ta barsu anan sunata sambatu su kad'ai.
Banko k'ofar da'akayi ne yasa Mumtaz bud'e idonta da k'er don jin yadda sukayi mata nauyi sosai kamar ba jikinta idon yake ba.
Umma tace Wallahi Mumtaz kin cuceni yanzu daman cikine dake kika d'aukomun abun kunya kinsan kuwa abunda kika Aika ta,yanzu duk i'rin tarbiyyar da muka baki abanza saida kika zubar mana da mutunci yanzu sai ki fad'amun waye yayi miki ciki,eyeh dake nake kike kallona munafuka,Kuka na shigayi ina cewa Wallahi Umma ban zubar muku da tarbiyyar da kuka bani,k'addarace tafad'amun Umma ta k'ara sha k'o Mumtaz tana tambayar cikin d'aga murya wanda duk wanda ke kusa zai iya jin ta.
Su Alhaji ne da Malam mahaifin Mumtaz suka shigo cikin d'akin saboda yadda suka jiyo hayaniya cikin d'akin,Alhaji yace haba Umma kiyi hak'uri ki k'eleta tayi mana bayani da kanta,Umma ta saki Mumtaz tana haki tare da hararar Mumtaz.
Alhaji yace Mumtaz ki fad'i tsakani da Allah Muntaz ki fad'a mana waye yayu miki ciki,domin idan kika b'oye mana Allah yana sama yana kallan ki don haka ki fad'ama na kinji.
Mumtaz ta share hawayen da ya b'ata mata fuska tace hak'ik'a zan gaya muku gaskiya,Alhaji yace to Mumtaz muna jinki?Muntax tayi shiru tabbas tana son gayawa i'yayenta gaskiya Amman tana tsoron Abubda zaije ya dawo domin tasan Iyayenta baza su tab'a i'ya jayayya da iyayen wanda yayi mata wannan Aika Aikar ba saboda nesa ba kusa ba sunfi duj yadda kake tunani kud'ine dasu kamar Bankin CBN saboda suna da kud'in da ko shugaban k'ada bazai had'a k'afa dasu ba,koda Kuwa Alhaji ne Mahaifin Aminiyarta Amal.
don haka sai tayi k'arya dacewa,Don Allah Umma ku ya feni hak'ik'a wadannan mutanen da suka saceni wata biyu da ya wuce har nayi tsawon wata biyu agidansu sune suka yimun wannan Aika Aikar mu biyarne y'an mata kuma duk saida suka lala ta mu.
Alhaji yace to meyasa Mumtaz baki gaya mana ba don mu d'auki mata ki kinga yanzu gashi sun sakaki cikin wani hali muma sun saka mu tabbas biri yayi kama da mutun tabbas nasan Mumtaz ba mazina ciya ce ba bazata tab'a Aikata abunda kuke zarginta dashi ba.
Malam ya shard'e wata zufa da ta tasomai yace hak'ik'a nafi kowa sanin halin Mumtaz yarinyace kamila maijin tausayin iyayenta akoda yaushe gata da Addini,hak'ik'a mungodewa Allah da yasa cikin ma ya zube saidai muce Allah ya bata lafiya dukkansu suka Amsa da Amin.


*Asalin labarin rayuwar Mumtaz da kuma abunda ya shafi rayuwarta dan gane da cikin da akayi mata*


★★ ★★
Tunda Muntaz ta taso da wayonta taga iyayenta suna cikin wani matsanancin talauci sosai,hakan yasa ta taso da jin tausayin iyayenta duk abunda tasan zata tai maka musu dashi tanayi indai baifi k'arfinta ba akan Aikin gida tun tana k'arama take Aikin gidansu,sannan Mahaifinta yana faskare dashi suke ci suke sha don haka duk ranarda Mumtaz taga Mahaifinta ya tashi zai tafi Aikin faskare sai ta tashi tace nima Malam zan bika,don gaskiya bazan iya bari kana shan wahala ba jibi yadda fa hannunka yake duk ya farfashe,Sai Malam yayi dariya yace Mumtaz kenan kinga duk aikinnan da nakeyi don ke da mahaifiyarki ne don hakk'inku yana kaina kuma sannan inason insakaki makaranta kiyi karatu kinji,sai Mumtaz ta wangale kyakkyawan bakinta tace Malam nidai i na girma inason inzama irin matar nan da kullum kake jinta aradion ka wadda take shiri nima inason inzama mai Aiki a gidan Radio don in taima ka muku da jama'ah baki d'aya.
Malam kuwa inda sabo ya saba don kusan kullum sai sunyi wannan hirar da y'arshi tilo aduniya wato Mumtaz ya lura yarinyar ta taso da wani ginshik'i azuciyarta wanda ta keso ta cika burinta akanshi Ma'ana tana son ta zama ma'aikaciyar gidan Radio ma'ana y'ar jarida don haka duk ranarda wannan zancen sai yaji yanason ya cika mata burinta,don haka sai yace Mata babu komai Mumtaz Insha'Allah zaki cika burinki na zama y'ar jarida don ni zan tabbatar miki da kin cika burinki don Insha'Allah zan sakaki makarantq don kema ki amfana da karatu kinji.
Suna wannan abun Kullum Umma sai ta lab'e tana jinsu cike da sha'awar y'arta da mijinta Allah ya sani suna son su bunk'asa rayuwar yarinyar wajen sakata makaranta don ta Amfana Amnan ya zamar musu dole wajen cikawa Mumtaz burinta bunk'asa karatunta har ta zama y'ar jarida kamar yadda kullum take muradi.


To fah wasa farin girki don yanzu wannan labarin ya soma kubiyoni don jin tarihin Mumtaz kachokan.


*Ummu Maher ce*


*Vote*
*Share*
And
*Comments*✍🏻
*Tyiping*🖌️


ABOUT MY WORK✍🏻

💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚


*Labarin gaske✍🏻*


Na
*Rabi'atu. B.Abdullahi*
(Ummu Maher)
Miss green💚📗

بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

🏔🅙︎🅦︎🅐🏔


*BABI NA 3&4*📝

Mumtaz ta taso da wata irin baiwa wadda take bawa kowa mamaki saboda yarinyar akwai gaskiya bata tab'a yin abu ta nuna rashin gaskiya kosa zaka kashe ta sai ta fad'i gaskiyar lamari,Ana haka Malam ya samu Aikin nik'a ya nayi albashinshi na farko ya saka Mumtaz makaranta da shi Mumtaz kuwa ta ringa murna saboda mahaifin nata ya cika mata burin ta nayin karatu,Kullum Malam i'dan zai tafi wajen nik'ansa tare suke tafiya da Mumtaz ya sauketa amakaran ta ya siya mata biskit da alawa sannan ya tafi wajen Aiki yana mata Bye bye i'tama Mumtaz bata tafiya sai taga Mahaifin nata ya tafi sannan take shiga aji.
Karatu sosai Mumtaz ta keyi don bata wasa a makaranta sam,ga ta bata surutu a'aji kawai i'ta karatu ta saka a'gabanta.
makarantar Mumtaz tayi nisa gashi Allah ya taimaki Malam yana biya mata kud'in makarantar ta akan kari baya bari lokaci ya k'ure bai biya ba kuma yana jin dad'in yadda take karatunta tana mayar da hankali,Mumtaz duk cikin ajinsu babu wanda ya kaita k'ok'ari da mayar da hankali wajen karatu gata da k'ok'ari don duk term ita take zuwa na d'aya ko Na biyu A'ajinsu haka duk Malam man makarantar sun san cewa Muntaz tana da baiwa sosai gata tun tana k'aramarta akwai ta da hankali da hangen nesa.
Mumtaz tana dawowa daga makaranta ta ajje jakarta ta cire unifoam d'inta na makaranta ta fito tsakar gida don taya Umman ta Aiki,ta gumin da taga Umman ta tayine tace Umma lafiya me yafaru kike ta gumi me akayi miki?ta jerowa Umman tata tambayoyi lokaci d'aya,Umman tata tayi saurin cire ta gumin da tayi tace Mumtaz kin dawo ne?Eh Umma na dawo Amman meya faru naga kin rik'e kunkuminki?Umma tace Mumtaz nasan kina jin yunwa ko?Eh Umma inajin yunwa sosai me kika dafa,Umma tace Mumtaz babu abunda na dafa shiyyasa ki kaga nayu tagumi kuma na buga na buga ban samu ba,Mumtaz tace to Kuma Umma shine kika saka kanki cikin damuwa ki daina damuwa kinji,Indai na girma na samu Aiki zaki huta indunga siyo miki kayan dad'i,Umma tayi murmushin da yafi kuka ciwo tace to Mumtaz Allah dai ya cika miki wannan burin naki,Mumtaz tace Amin Ummana.
Umma tace yanzu ki tashi akwai wata y'ar sauran kamu da na dama miki da kwad'on k'anzo ki tashi kici kinji Umman ta kalleni tana mai jin tausayin d'iyar tata.

Akwana atashi asarar mao rai wataran asamu aci wataran kuwa Iyalan Malam mahaifin Mumtaz basa cin abun abinci wataran haka suke kwana abunsu,gashi Allah ya basu yarinya mai hankali da tausayi ko ta samu ko kar ta samu bata tab'a d'agawa iyayenta hankali wai don tana jin yunwa ko wani abu haka take hakura taci koda bai mata ba haka ta ke hak'ura taci.
Har Allah ya kawo lokacin da su Mumtaz suka zana jarrabawar fita daga primary Mumtaz da iyayenta sunyi murna sosai gashi ta fito da saka mako mai kyau.
Mumtaz tace Malam ina Addu'ah Allah ya cika mun burina na zama y'ar jarida sai dai bansan aikin da zanyi ba in taimaka muku ba kuna shan wahala kaida Umma,wajen biya mun buk'atu na,Malam yace babu komai uwata Allah zai taima kamana matuk'ar ba muyi bacci ba muna rok'on Allah ya kawo Aikin da zai zi mun na sakaki makarantar gaba da Primary kinji ki daina da muwa,Mumtaz tace to Baba na Allah ya tai ma keka yacr Amin uwata.

•••••••••••••••••
Ranka ya dad'e har yanzu Mu'taz d'in bau kira ka ba Allah dai yasa lafiya mai martaba inajin tsoro kada wani abu ya samu yarima,Mai martaba yace gaba Fulani babu abunda zai sameshi kinsan yace i'dan ya dawo baya buk'atar muje d'aukoshi motar haya zai shiga kinsan halinshi don haka kada ki damu,Fulani tace haba Mai martaba yanzu haka zamu zubamai idanu gamu da motocin agidanmu wasu ma saidai mu bayar Anma d'anmu yana shiga motae haya so yakeyi duniya ta zagemu ace mun kasa kula da d'an cikinmu ballanta na Al'umma gaskiya nidai banasan wannan halin nashi Ai ba sai yayi haka ne duniya zata san cewa shi mai tausayi ne ba.
Fulani bata gama rufe bakin ta ba,Jakadiya tayi iso k'ofar d'akin tace gafaranki dai Yarima yana neman i'so,Fulani tace anyi mai iso ya shigo Yana shigowa ya gaida mai martaba da mahaifiyarshi Fulani,tace ikon Allah kaidai yarima kaji tsoron Allah wallahi duk yawan motocin gidannan kace wai kai bazaka hau ba sai motar haya zaka hau wannan wacce irin rayuwa ce haka.


*UMMU MAHER CE*


Please share
And
Comments✍🏻
*Tyiping*🖌️

ABOUT MY WORK✍🏻

💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚


*Labarin gaske*✍🏻

Na
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)
Miss green💚📗

بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

🏔🅙︎🅦︎🅐🏔

*WATTPAD LINK*
https://www.wattpad.com/?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends.
__________________👉🏻👉🏻

*BABI NA 5&6📝*

Nan Fa Fulani ta dage tanawa Mu'taz fad'a akan me zai dinga hawa motar haya,Mu'taz dariya ma Mahaifiyar tashi ta bashi Ya kama kunnenshi yace Allah yabawa Fulani hak'uri Allah yaja da ranki Uwargida Awajen Mai marta ba takawarki lafiya,Ai bai gama Rufe bakinshi ba Mai martaba Sarki Mahaifin Mu'taz ya k'elk'ele da dariya yace kaimu son i'rin wannan kirari haka nida kwanannan Zan k'ara Aure in Auro Baturiya Mai jan bakii,A'i Fulani k'ara har zuk'a tayi tana cewa daman Kai da d'an ka haka kuke da anfara magana sai kuyi sauri Ku Fara wayan cewa,Kai kuma da amfara magana sai kace zaka Auro baturiya ka Auro Agwa ma.
Dariya Mu'taz yayi shida Mahaifinshi Mu'taz yace haba a kwai wata baturiya da ta Kai Fulani wani Abu ai babu shi ya fad'a yana dariya,Fulani tace kwaji da shi dai.
Oyoyo Bros Wata y'ar budurwa ce da baza ta wuce Sha shida ba ta rungume Yayan Nata tana yimai sannu da zuwa cikin so da kulawa na y'an uwan taka.
Da ka ganta kasan k'anwar Mu'taz ce saboda yadda sukayi matuk'ar Kama da juna,Oyoyo My sister shima ya fad'a Mata yana Mai Jan hancin ta.
Bros ya naji kuna tsokanar My mom d'ita,Hanan Ashe kinji i'rin tsokanar da suke yimun KO?Hanan ta rungume Fulani tana cewa K'elesu My mom zamu rama,har wata baturiya ce za'ah had'a ta da my Mom d'ita Tauraruwar Mata kyakkyawa acikin kyawawa.
Fulani tace yauwa gaya musu dai suji?Hanan ta fakaici idon Fulani suka tuntsire da dariya i'tada yayan nata.
Fulani tace waifa akan na fad'a mishi gaskiya akan hawa motar hayar da yake yi shine Mahaifinku ya goyi Bayan shi,Hanan tace gaskiya My Bros kadaina hawa motar haya don Allah.
Mu'taz yace to Fulani kiyi hak'uri na daina,Fulani tace yau d'ana haka nakeso shiyyasa kullum nake k'ara sonka saboda kanajin magana ta.
Sarki Abubakar wato Mahaifin Yarima Mu'taz yayi dariya yace mu kuma da ba'ah sonmu sai ajefar damu ko?kuma tunda abun haka ne kwanannan Baturiyar nan zata shigo tunda abun haka ne.
Fulani tayi dariya tace Hhhh Mai Marta ba kenan Ai kaga y'ay'annan nawa sun isheni duniya da lahira don haka ba Baturiya ba ka Auro Balarabiya.
Mai martaba yayi dariya tare da cewa Hhhh Fulani kenan kishi KO?to naga ne miki kwantar da hankalinki Akwai wata mace da zata kaiki ai babu ita,Ai kuwa yaran nasu suka tun tsire da dariya .
Nandai suka ci suka sha suna maijin dad'in dawowar d'an nasu daga America,Bayan sun gama ne Mu'taz ya d'auki wayar shi ya kirawo Amininshi kuma d'an uwanshi Murat.
Kiran farko Murat ya d'auka yana jin muryar Abokin nashi ya ture Mima daga kusa dashi don yadda ta mak'alk'aleshi sai kace wata mayya ta kalli Murat cikin takaici daga zuwanta gidan za'ah Fara wulak'antata.
don Mima irin mutannan nan ne masu son Kansu matuk'a shiyyasa take mafarkin ace Murat ya zama Nata i'ta kad'ai,saboda yadda Murat yayi Mata yanzu ya tabbatar Mata da cewa Wanda ya bugo yanada wani bugire tare da wani matsayi arayuwar Murat.
Murat shine kasan Na dawo KO kazo mugaisa shine kak'i zuwa KO?Murat ya Sosa kanshi yana cewa Haba Life kayi hak'uri wallahi wani Uziri ne ya b'oye ni Amman yanzu ganinan zuwa ya fad'i hakan yana Mai kashe wayar ya nufi inda Mima take wacce ta gwalalo idanuwa tare da bud'e kunnuwa taji me'ake fad'a.
Ganin Murat yayi hanyar ban d'aki abun ya k'ara k'ular da Mima yau me Murat yake nufi da'ita daga zuwan ta saiya nemi wulak'anta ta,koda ya fito daga ban d'aki kud'i ya watsawa Mima Wanda baisan KO nawa bane.
Ba tare da ya kalleta ba yace inkin gama ki rufemun gida bai jira me zata ce ba yayi tafiyarshi tana ta masifa tare da nadamar zuwa don ba haka bokanta yace Zai faru yace Mata matuk'ar ta kwanta da Murat to komai yazama Nata domin Murat zai dinga binta kamar wani doki da akala.
Hira ce ta kaure sosai don tsakanin Murat da Abokin nashi kuma Amininshi Murat kuwa wani Abu ne acikin zuciyarshi a game da Aminin Nashi yana rok'on Allah ya nuna mishi Ranar da zaiyi maganin shi ranarda zai cika burinshi akanshi Ni kuwa Nace KO wani buri ne Murat yake b'oyewa oho?.
Hanan ce ta fito sanye cikin Doguwar wato Arabian gown gaban rigar yasha ado gata farar fata fatarnan Tasha jan lalle Wanda zaka rantse da shi aka haifeta dashi, Murat ya bita da I do kamar maye.
tana zuwa tayiwa kanta mazauni akusa da yayan Nata,ta kalli Murat ba tare da sakin fuska ba kamar yadda ta taho tace Ina wuni tana wani yauk'i kamar ba tason yin magana.
Murat ya shafa kanshi yanajin son yarinyar har Cikin zuciyarshi don duk wulak'amcin da Hanan take yimai bai tab'a nuna Mata ba saboda tun tana k'arama yake sonta.
K'anwa ta KO Nayi miki laifine kike kame mun fuska Murat ya fad'i hakan lokacin da ya d'auko tufa ya saka abakinshi yana jin dad'in tufar har Ranshi,Hanan tayi saurin cewa Wallahi babu abunda yake damuna kawai dai Kaina ne yake ciwo,cikin tashin hankali yace Hanan kinsha magani kuwa,Hanan ta tashi tana tafiya tana cewa Eh nasha yanzu ba tareda ta sake magana ba ta fita daga farlon don kwata kwata yanzu batason Murat tun Ranar da ya nemata da wata buk'ata ta tsaneshi ba kuma wai tsanarshi tayi ba A'ah kawai dai abun da yayi Mata ne ya saka gaba d'aya yanzun bata son ganin shi,har a zuciyarta tanason Murat sosai Amman yariga da ya b'ata rawarshi da tsalle.
Mu'taz ya kalli k'anwar tashi Bayan ta fita sannan ya kalli Aminin nashi yaga gaba d'aya hankalinshi yana kan k'anwar shi Hanan,KO meye ya shiga tsakanin su Oho?.
Shidai A'iya saninshi yasan cewa Murat da Hanan suna matuk'ar son junansu to meye ya faru,to KO Hanan ta gano Aminin nashi yana Neman matan banza Oho?A kullum Addu'ah ya keyiwa Abokin nashi na Neman tsari daga halinda Murat ya fad'a.
Mu'taz yace Murat ka k'eleta zata sakko kasan Mata kaidai Ka cigaba da Jan hankalinta asannu komai zaizo da sauk'i sai Abu na gaba da Zan gaya maka Murat kayi k'ok'ari kadaina kula matan banzan nan kasani Allah bata bacci kuma yana kallon ka don haka ka kiyaye dokokin ubangiji sai shima ya kiyaye ka daga fad'awa azabarsa.
Murat yaji haushin maganar Abokin nashi don haka ba tare da ya nuna mai ba aka cigaba da hira Inda Murat ya nuna wa Aminin nashi ya daina duk wani hali na banza.


★★★★★
Mumtaz kiyi sauri fa mutafi makaranta kinsan fa yau Malamin nan zaizo kinsan ba shida mutunci KO kad'an Amal ta fad'i hakan tana Mai shiga d'akin don ganin Aminiyar tata bata da niyyar fitowa,Wow wata yarinya a hango wacce ba zata wuce sha biyar ba tana shafa Mai A fatarta Mai kyau da tsantsi,Mumtaz kenan yadda mak'erin budurci ya k'erata komai Nata yayi kyau masha'Allah.
Mumtaz tace daman sauri na ke tayi kafun ki fito nasan kina zuwa zaki addabe ni shiyyasa nake ta sauri,Au haka zakice KO inji Amal dake shirin fita.
Mumtaz tayi saurin janyo ta tana bata hak'uri,Amal tace to sai kiyi sauri idan ba haka ba intafi,Nandai Mumtaz ta gama shiryawar ta suka fito don zuwa makaranta inda sukayi wa Umman Mumtaz sallama suka tafi ganin sha'awa.

*Wacece Amal*
Amal dai y'ar wani mutuncr Mai kud'i d'an Asalin jihar Kano ne matar sa y'ar Niger ce Buzuwa ce Jamal su biyu ne ita da Yayan ta Mai suna Ibrahim,Mahaifinsu Alhaji Abdullahi sun dawo Bauchi da A'iki ne saboda transfer da'akayi mishi saboda haka suka dawo Bauchi da zama,Alhaji Abdullahi bata son zama cikin masu kud'i wato bata son zaman G.R.A.saboda yace baka sanin halin da talakawa suke Cikin zama cikinsu kuma zai k'ara maka I'mani tare da tausayi da jin k'ai don haka koda ya su da mak'ofta suke da su Mumtaz don haka tunda ya bud'e i'do yaga halin da suke ciki Saiya ringa taima ka musu ya bud'ewa Malam shago a Bayan gidansu yana siyarda kayan masa rufi,Mumtaz kuwa tuni sunyi saboda Mai k'arfi tsakanin ta da Amal,hakan da Alhaji ya ganine koda za'ah saka Amal Makarantar gaba da Primary wato Secondary tare yakaisu yayi musu komai tare.


*UMMU MAHER CE*


Miss green💚📗✍🏻

Share👉🏻👉🏻👉🏻
And
*Comments*
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻

💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚


*Labarin gaske✍🏻*

*Na*
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green💚📗

بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

🏔🅙︎🅦︎🅐🏔


*WATTPAD Link*
https://www.wattpad.com/?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends.
____________👉🏻👉🏻👉🏻

*BABI NA 7&8📝*

Wannan dalilin ne yasa Mumtaz da Amal suka taso tare komai suke yi hatta abinci tare suke cinshi,suna son Junansu sosai da sosai.
hatta bacci wani lokacin tare sukeyi,I'dan safiya tayi Mumtaz ta koma gida duk ranar da basu kwana tare ba kuwa to Da sassafe zasu had'u don har mafarkin junansu sukeyi.
Mumtaz bata da tsoro ko kad'an,Amal kuwa akwai ta da tsoro don y'an gidansu ma sun santa da tsoro kamar farar kura.
Koda fad'a Akeyi da Amal to ka tabbata sai Mumtaz ta shiga ciki anyi da'ita saboda i'ta daman tun tana k'arama bata da tsoro ko kad'an hakan ne yasa yara suke tsoron Mumtaz.
Hajiya Mahaifiyar Amal bata san Wannan alak'ar tsakanin Mumtaz da Amal,A cewar ta wai Mumtaz zata shafawa Amal gayyar talauci,Shiyyasa take ta k'ok'arin rabasu ta k'arfi da yaji.
Saidai duk wannan abun da takeyi bai saka yaran sun daina son junansu ba,Gashi kullum Ibrahim Yayan Amal ya dawo daga wajen Aiki sai ya tambayi Mumtaz I'dan kuwa bai ganta ba to sai yaje gidan.
Hakanne yake k'ara tunzura Hajiya Wato mahaifiyar Amal,don gani takeyi duk Mumtaz ta kwace mata iyalai,don Alhaji Yanzu taimakon su Mumtaz yakeyi sosai.
Hajiya fa ta dage sai ta raba,Amal da Mumtaz iyakar k'arfin ta,don wataran ma Idan Mumtaz tazo gidan korar ta takeyi ko kuma tayi ta zagin iyayenta wai matalauta matsiya ta.
Zagi dai kala kala babu wanda Mumtaz bata shanshi awajen Hajiya,abun takaicin kuwa i'dan Mahaifin Amal yana nan bata nunawa Mumtaz wani abu ballantana ma har wani ya gane meke faruwa.
ko kud'in makaranta idan Alhaji ya bawa Mumtaz fakar idon Alhaji a keyi ta karb'e,Idan Amal tayi mata magana yanzu ta zane ta wannan abun ya tsayawa Amal aranta don tsakani da Allah bata jin dad'in yadda Mahaifiyar tata takeyiwa Aminiyarta.
Don haka rannan ta shiryawa Uwar tata tsiya ta d'au aniyar sai ta gayawa Dadynta don du abunda mahaifiyar tata ta keyi bai sani ba.
Rannan suna Zaune dukkansu Afarlo har Mumtaz,sai kuwa Amal ta kar kace bakinta tace Dady zanfad'a maka wata magana,Dady ya gyara zamanshi yace to Uwata ina jinki wani abune ya faru?.
Eh Dady daman nadad'e inason in fad'a maka akan abunda Momi ta keyiwa Mumtaz ne?Ai kuwa sai Momi tace to Uwar y'an sharri kedai kamar canza mun ke akayi mai bak'in hali kawai,kuma kirufa mana bakinki anan Noncense kawai.
Alhaji yace haba Hajiya ki tsaya mana yarinyar ta fad'i gaskiyar ta Tafara magana kin tsayar da'ita meye dalilinki?to banason i'dan ina magana da yara na kina saka mana baki kina jina ko?.
Momi kuwa abunnan ya k'ona mata rai ta kasa cewa komai sai zuciyarta da take mata zafi,Ita kuwa Mumtaz batason Amal ta fad'awa Dadynta wannan maganar don zai i'ya haddasa musu rigima k'arshe a dawo da abun kanta.
Alhaji yace ina jin ki Mamana me Mamanki ta keyiwa Mumtaz yanzu in d'auki mataki akanta,sai kuwa Amal tace Dady wallahi Mama kullum idan Mumtaz tazo nangidan saita zageta wai y'ar matsiya ta y'ar talakawa,Wallahi Dady wataran ma idan ka bamu kud'in skull karb'e na Mumtaz, ta keyi wataran ma ta hanata shigowa gidannan wai ita bata gaji Arzik'e ba.
Alhaji fa ranshi idan yayi dubu to yab'aci don me Hajiya zata dunga wannan jahilcin I'ta ta manta a yadda ya Aure ta take Mahaifin ta Saran icce yakeyi Amman bai talaucinsu ba ya Aureta amman yanzu har tana da bakin zagin y'ay'an mutane.
Kwala mata kira Alhaji yayi koda tazo yaci mata mutunci sosai yace kuma duk ranar da ta sake yiwa Muntaz wani abu to Wallahi bai yafe mata ba,Hajiya kamar ta shak'e y'ar tata saboda haushi.
Nandai taringa bashi hak'uri amman ko sauraron ta baiyi ba yayi tafiyarsh,yana mai jin haushin matar tashi don ko kusa bai kawo abunda ke faruwa zai faru ba.
Ibrahim ya kalli Mahaifiyar tasu yace Gaskiya Hajiya wannan halin bai dace ba kwata kwata,don Allah yayi mutun cikin talauci ba yana nufin baya sonshi ba,A,ah sai don Allah yagwada imanin mutun amman bai kamata mutane suna k'ok'arin nunawa ubangiji izza ba.
Hajiya tace yumun shiru sallamammmu kawai sunje sun tsaface ku dukkanku bakwa ganin laifinsu,kullum yabonsu kukeyi mutanenda talauci gadonsu ne abarsu suyi abunsu mana amman wai taimakonsu sukeyi.
toni bana cikin wad'anda aka sallama,don haka ni bana cikin wadanda aka sallama.


kuti hakuri nqyi tyiping kad'an wani uzuri ne ya rik'eni.


*UMMU MAHER CE*

*Share*
And
*Comments*
*Tyiping*🖌️
_ABOUT MY WORK_✍🏻

💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚

By Rabi'atu.B.Abdullahi👉🏻
(Ummu Maher)Miss green💚📗

بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

🏔🅙︎🅦︎🅐🏔


*BABI NA 9&10*📝
Ibahim yayi shiru yana sauraron Hajiya da gaba ki d'aya i'don ta ya rufe da masifa wai yanzu an asirceshi ya zama d'an hannu.
Ibrahim ya kalli Mahaifiyar tasu yace haba Hajiya Mumtaz fa yarinya ce mai hankali da tarbiyya bata damu da dukiya ba kwata kwata haka ma i'yayen ta mutanen kirki ne.
Hajiya tace yimun shiru mara kunya harni zaka kalla kace mun iyayenta mutanen kirki ne,to waye ba na kirki ba?tambayar ka na keyi kabani amsa mana?.
Amal tayi saurin cewa kiyi hak'uri Hajiya don Allah kidaina zagin Mumtaz a gaban ta babu dad'i i'rin wannan gaskiya Momi...tun kafun ta k'arasa ta wanke ta da mari tana masifa kamar wata zautatta.
Ke dan ubanki dani kike ko da ubanki?I'na cewa yanzu kika had'ani da ubanki wai na zagi Mumtaz k'anwar uwarki ko?to bari kiji wallahi tallahi ba don yau ke y'ata ce ta cikina ba yau da kinga i'skanci muraran.
Don haka this is the last worning idan kika k'ara kai k'arata wajen ubanku saina naka saki banza mara sanin ciwon kanta.
Duk abunda Momi tayi Mumtaz na kallon ta kuma tana jinta amman ba tace komai ba,saboda yadda ta d'auki Momi kamar mahaifiyar ta don haka Mumtaz ta tashi ta koma gidansu ba tare da tace komai ba.
Amal tabi k'awar tata da kallon tausayi don tasan Duk wanda aka yiwa wannan zagin to tabbas sai yaji aranshi babu dad'i,don zagine na cin mutunci duk mai hankali idan aka yi mishi wannan zagin sai yaji a zuciyarshi babu dad'i.
to haka dai rayuwa ta dinga tafiya har kawo i'yanzu da Mumtaz da Amal suke makarantar gaba da primary wanda Alhaji Mahaifin Amal shine ya d'auki ragamar karatunsu.

*Cigaban labarin*
Mu'taz ya kira Murat yafi sau goma amman bai d'aga ba, Cen aka d'auki wayar Mu'taz yayi saurin cewa haba abokina me yasa baka d'aga waya akan kari?.
Muryar wata yarinya yaji tana cewa to A'i saika k'ara kira mai wayar baya kusa,ta d'an d'aga murya kad'an tace Honey ana kiranka awaya.
Mu'taz kuwa don haushi bai jira abunda zaice ba,ya kashe wayar saboda haushin Murat ya keji sosai ba don Murat Amininshi neba da tuni ya rabu da shi yayi yadda yakeso tunda rayuwar daya zab'arwa kanshi kenan.
Ya rasa gane kan Murat da i'rin halinshi nasiha dai i'ya gwargwado yayiwa Aminin nashi amman haryanzu bai daina tsallake 2 nashi ba.
Kullum shine d'aukar Babys amota suna yawo shine gidan Club babu wanda baya zuwa yana sha shanci da k'arawa kai zunubi.
K'arar wayarshi ce yasa ya juya ya duba Life💘ya gani ajiki,sunanda suke kiran junansu dashi kenan don tun suna k'anana shida Murat suke kiran junansu dashi saboda yadda suka shak'u sosai da juna bacci ma tare sukeyi.
Murat yace Mu'taz don Allah kayi hak'uri Na d'an shiga Band'aki ne so shiyyasa,Mu'taz yace babu komai naji,Amman Murat meyasa kullum kake tuba kake koma wa ruwa ya kamata kayi k'ok'ari kadaina bin matannan ba Kai kad'ai bama duk wani Mai bin Mata k'arshen shi na dama.
Murat yayi wani gauron numfashi sannan yace Babu komai Wallahi wannan d'in ma akasi aka samu,Mu'taz yace babu komai Amman dai kayi k'ok'ari ka daina.
Duk abunda suke yi Hanan tana jinsu awayar ta samu waje ta zauna zuciyar ta nayi Mata k'una,tabbas zuciyarta tana son kasan cewa da Murat a matsayin miji.
Amman ya zamar Mata dole ta Rabu dashi tun yanzu gudun samun matsala,Amman ta Yaya zata rabu dashi don tana matuk'ar son Murat.


*UMMU MAHER CE*


*Vote*
*Share*
*Comments*✍🏻
*Tyiping🖌️*

ABOUT MY WORK✍🏻

💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚
Written by
Rabiatu.B.Abdullahi🤙🏻
(Ummu Maher)Miss green💚📗

بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_

🏔🅙︎🅦︎🅐🏔
Chapter 1 · 0% Book details