Gabatarwa
A Rubuce Take Part 2 Complete Hausa Novel · about 27 min read
ÿþ*_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM_*
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*A RUBUCE TAKE*
(K'addarata)
*Book 02*
Page 01
Cikin mugun mutuwar jiki kasala da kuma fargaba ta hada kalmomin
"Wacce irin matsala kuma umma?,na shiga uku"
"Malam baiga komai akan yarinyar ba,komai ya rufe masa,bai hangi ciki ba,kamar yadda babu tabbacin babu shi".
Goshinta hafsat ta dafe,tana jin yadda zuciyarta ke tafasa,a zahiri tayi mugun tsanar yarinyar,ta zame mata qarfen qafa sosai,tanason kuma ta zama barazana ga rayuwarta,cikin tsananin fusata tace
"Umma,yayi mata koma meye,duk abinda ya dace da ita da zai d'ai d'aita rayuwarta ayishi,banason ganinta kwata kwata cikin gidan nan,yanzu haka fa abban mimi ya biya mata hajji,aikin hajji zasu tafi" ta qarashe maganar tana barkewa da kuka,don abun yayi mata ciwo ba kadan ba.
Salati umman tata ta sake kamar tana gaban hafsat din
"Kina raye kina kallo?,lallai sai munyi da gaske,sai mun tashi tsaye akan yarinyar nan"
*A B B A S*
"Ya salam" ya fada zuciyarsa na wani irin bugawa da matsanancin farinciki, kamar wanda aka yiwa albishir da samun haihuwa karon farko bayan wasu shekaru daya diba yana neman haihuwar ba tare da samu ba,ya bude idanun nasa fuskarsa na fidda wani irin murmushi yana sauke dubansa ga widad.
Ido suka hada shi da ita,ta narke fuska sosai,dab take da sakin kuka,suna hada idon kuma sai rauninta ya bayyana muraran,yasan tabbas yau akwai daru,amma koma meye a shirye yake daya shanyeshi,ciki a jikinta?,cikin da yasha yi mata wayo yana gaya mata ba tarayyarsu ce zata saka tayi ciki ba,shan ruwa a qoshi ne?,yasan lallai zai sha tuhuma.
Hannu ya miqa mata alamun ta taho har yanzu murmushi kwance bisa fuskarsa,amma sai ta kauda kai hawaye na ziraro mata,yasan za'a rina,yau saita Allahu,ya dinga danne dariyarsa sannan ya.miqe tsam ya isa gabanta,ya tsaya daga gefanta yana riqe da hannunta yana murzawa a hankali cikin nasa,idanunsa akan na dr
"Yanzu ya za'a yi?,ina fatan bazai bada matsala ba wajen tafiya"
"Bana jin gaskiya,zanyi qoqari ayi mata komai ku wuce tare,tunda bai nuna ba" ta fada ita kanta tana mamakin watannin cikin,da kuma yadda ya boye kansa da kyau,iya ganinka ba zaka hangeshi jikinta ba.
Komai da akeyi kawai tana binsa da ido ne, hankalinta gaba daya bai jikinta tunda akayi zancan ciki,tsoro da fargaba gaba daya sun hadu sun lullubeta,har suka gama komai yana riqe da hannunta,ya bude mata gaban mota ta shiga ya maida murfin ya rufe ya zagaya mazauninsa shima.
Ai yana shiga tana fashe masa da kuka,kamar wadda ke jira,ya dakata daga kunna motar ya waiwayo yana dubanta
"Ya salam ya Allah.....menene kuma?,ko wani abun na miki ciwo?"
"Wallahi idan abba yaji ka yimin ciki sai ya kashemu ni da kai" duk yadda yaso ya riqe dariyarsa amma wannan karon ya gaza,dariya ta kubce masa,har sai da yasa zara zaran yatsuntsa ya toshe bakinsa kada cibi ya zama qari,sai yaushe zata gama girma ne?,ashe har yau da sauran quruciyar nan tana nan?,ta yaya zai bullo mata,sai kawai ya juya fuskarsa zuwa kalar alhini shima yana dubanta
"Innalillahi......yanzu ya kike ganin za'a yi?" Da farko dariyarsa ta qular da ita,amma yanzun maganar da yayi saita wanke wancan
"Nima ban sani bafa....duk kaine ka jawo,saida nace banaso,kace wai idan nasha ruwa ne zaizo" ta fada yana harararsa,saiya narke fuska kalar tausayi ya langabar da kai
"To ai nima na zata hakanne,kuma ma kinsan me?" Kaita girgiza tana sharar qwalla,sai ya juyo yana fuskantarta sosai
"Sanda kika gudu kano?" Saita gyada kai tana dubansa
"Abba da kansa ya kirani yace nayi wannan abun fa da bakiso din" dukka idanunta ta fidda waje kamar zasu fado tana kallonsa a tsorace,ya jijjiga mata kai
"Da gaske nake" ya sake fada yana danne dariyarsa,bai ankara ba ya takai masa duka tana sake fashewa da wani kukan a sakalce
"Allah abbana ba dan iska bane da zaice maka haka" sosai yau din take sashi dariya,ya kare dukan da daya hannun yana dariya tare da fadin
"Allah.....Allah kinji nace Allah" ta sanshi farin sani,kaifi daya ne,baya qarya,yana fadin hakan sai kunya ta kamata,ta kifa kanta a cinya tana juya yadda abban nata zaice haka,yanzu.kowa.kenan yasan abinda suke aikatawa?,tana jinsa yanata magana amma bata dago ba bare ta amsa,yana dariya qasa qasa ya tashi motar sukabar asibitin,ransa fes,zuciyarsa qal,wani farinciki daya jima rabon da yaji irinsa ya cika masa zuciya,har hakan yana bayyana kansa saman fuskarsa.
Saida sukayi nisa a tafiyar yace
"Kona ajjiyeki gidan hajiya?" Ya fadi hakanne saboda yadda yaga sam.batason zaman gidan nasu,saita girgiza kai da sauri
"Aah,nidai ka kaini gida" murmushi ya subuce masa,ya gane mai take gudu,kada hajiya ta gano tana da ciki,daga haka yabar zancan ya dauke kan motar suka nufi gida.
Sanda ya tsaida motar da kansa ya dauki hand bag dinta yana riqe da ita zuwa ciki,ta langabe kai tana kallonsa
"Ka bani,zan iya dauka" kai ya girgiza idanunsa cikin nata,yana jin wata qaunarta tana fusgarsa
"Ban yarda ba baby,dama naji a jikina,wannan rashin lafiyan akwai dalili,muje kawai,ko na daukeki?" Ya fadi shima yana langabar dakai,kunya ya bata,ta kauda kanta gefe tana gulmarsa cikin ranta,wai shi kam bayajin kunya ne ma wai?,kamar ba ciki yayi mata ba?.
Kamar yasan maganar da takeyi ya saki murmushi kadan,ya kama hannunta ya matsa kadan yana cewa
"Muje baby".
Sanda suke shiga din akan idanun hafsat dake tsaye bakin window,tunda suka fita ta kasa zama,zuciyara nata qiyasta mata gurare daban daban da zasu iya zuwa,tana goye da shukra dake ta faman rigima,ji take kaman ta yago yarinya ta ajjiyeta,qunqunin yarinyar har tsakiyar kwanyarta,idanunta suka sauka kan handbag din widad da hannayensu dake sarqafe waje guda.
Wani matsanancin qunci zuciyarta ta shiga,duk yadda taso daurewa amma ta kasa,ta saki ashar,kasheta mutanen nan sukeson yi?,bayan abinda abbas din ya aikata mata shine zasuci gaba da sabgarsu kamar ma ba'a yi mata komai cikin gidan ba?,ba zata iya dauka ba,dole kowa yasan an tabota,sai kawai ta kunce yarinyar ta aza saman kujera ta nufi qofa da wani irin mugun sauri.
Idanunsa ya lumshe kadan,yana tsaye saman kanta yana mata wani duba dake cike da shauqinta,ko yaya ta motsa sai taja hankalinsa
"Zan dan fita,amma bazan jima ba zan dawo,me kike buqata?" Ya qarashe fada yana ritsata da idanunsa masu matuqar kwarjini da jan hankali,sai tadan rufe idanunta kadan ta girgiza kai
"Babu komai"
"Really?" Ya tambayeta yana dubanta,kai ta sake gyada masa
"Okay.....zan tafi" ya sake maimaitawa,saita sake lumshe idonta,tasna me.yakeso,amma jikinta a mace yake murus,ta gyara zamanta sosai ta nutse cikin kujerar sannan tace
"A dawo lafiya"
"Au 'yar hakace yau?" Murmushi tayi kawai tana boye fuskarta,saiya saki wani murmushin,ya duqa kadan a tausashe yayi kissing goshinta sannan yace
"Take care of yourself" kai ta jinjina,sai daya juya sannan ta bishi da kallo,zuciyarta na gaya mata wai da gaske ba abun kunya sukayi ba,ta dora hannunta saman cikinta a hankali tana shafawa cike da mamaki da kuma tsoron cewa wai ciki ne a jikinta.
Dai dai sanda muryar hafsat ta ratso har cikin falon nata da wani irin amo,sai ta bude idonta a hankali tana saurarenta sanda take magana cikin rawar murya
"Wallahi bazan yafe wannan zaluncin ba,sai Allah yayi min sakayya" wani mugun tsaki widad din taja tana tabe baki gami da gyara kwanciyarta cikin kujerar,ita gaba daya mutuncin matar ya gama zubewa a idanunta,tunda take bata taba ganin yadda akema babba rashin kunya ba kamar yadda itadin taga tana yiwa abbansu mimin,ko babu komai aiya girmeta,kuma ko ummu da take tsohuwa ai tana ganin yadda take girmama alhaji,har tabar gidansu bata taba gani ta karba abu daga hannunsa daga tsaye ba,ko ya fada tace a'ah, miqewa tayi cak tana daukar jakarta ta wuce bedroom dinta,haka kawai taji batason jin wata hayaniya kusa da ita.
Hannu daya abbas ya sanya cikin zallar bacin rai ya fincikota,ya riqeta gam yana tafe riqe da ita,bai tsaya ko ina ba sai da yakai sassanta ya watsar mata da hannun cikin falon,da yatsa ya nunata
"Wannan ya zamana shine lokaci na qarshe da zaki qara gangancin cewa zaki shiga sashenta ko zaki tabata,daga lokacin da kikayi wannan kuskuren zaki fahimci baki da wayo,tunda na fahimci sauna ce ke shashasha wadda batasan girmanta ba" sosai maganarsa ta doketa kamar saukar mashi saman zuciyarta,ita din abbas yake cewa sauna shashasha?
"Kowanne suna kakeso ka kirani dashi,daidanka ne,amma bazan fasa neman haqqina ba"
"Idan kika fasa neman haqqinki kin raina Allah" kalmar da tasa ta bishi galala da kallo har ya fice,sai ta sake fashewa da kuka,dole tayi iya yinta taga ta tarwatsa farincikinsu,ba zata zauna ita kadai bacin rai ya hallakata ba.
Yana tafe zuciyarsa cike da bacin rai,mahaifin hafsat shi daya yake tunawa,mutumin kirki da kowa ya yaba halayyarsa kafin barinsa duniya,yana sonsa yana girmamashi,har yau yana tuna haquri na qarshe daya bashi a kanta kafin barinsa duniya da 'yan awanni,yaja wani dogon tsaki,xuciyarsa na ayyana masa hukunci kala daban daban da zai iya dauka a kanta.
A hankali kuma yaji yana sauka musamman daya tuna kyautar da Allah yayi masa a yau daga wajen halitta mafi soyuwa cikin rayuwarsa,sai yaji dukkan haukan hafsat din wani abune mara muhimmanci da zai iya tattarasu ya watsa kwandon shara,idan ta gaji ta sauke kamar yadda ta saba.
*******Cikin kwanakin da sukayi cikin gidan kafin tashinsu saudiyya dan qaramin yaqi aka dinga gwabzawa tsakanin abbas da hafsat din,kullum cikin kuka qorafi da masifa,dai dai sanda 'yan abun nasa suka motsa(miskilanci),yayi watsin tsiya da ita,tamkar ma ba dashi take ba.
Ta fannin widad ma sai tayi kamar batasan me ake ba,dama ita dimma ba baya bace wajen miskilancin,bare a yanzun da take mugun jin xafin mummy hafsat din haka kawai,ta tsani ta ganta tare da uncle din nata,tana dannewa ne tayi kamar bai dameta ba tunda batasan ainihin me yasa takejin hakan ba,uwa uba ko meye zatayi saidai ta jiyota daha sashensa sashenta ko.farfajiyar gidan,bata doso sassanta,wannan yasa bata dameta ba,a kullum tunaninta da zuluminta sanda kowa zaisan tana da ciki,cikin wata irin wauta dake sanya abbas din ya qunshe kansa yayita mata dariya,a fuska kuma ya tayata jimami da alhini kamar gaske.
A lokacin hafsat din ji take kamar zata mutu,yaqi kulata sannan widad din da taso rage zafi da ita ya mata shamakin da ko giyar wake tasha ba zata doshi sassanta ba,ta sanshi farin sani,yana da kawaici yana da alkunya,amma duk sanda ka sake ka turashi inda bai kamata ka turashi din ba.....to kuwa abinda zai biyo baya bashi da sauqi.
Duk haukar da hafsat din keyi hakan bai canza komai ba,don kuwa kwanakinsu biyar suka wuce kano,kai tsaye kuma sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na mallam aminu kano.
Sosai widad din tayi mamakin ganin 'yan gidansu acan suna jiransu,tayi farinciki sosai amma kuma abinda tasan tana tattare dashi ya hanata sakewa,sai qumbiya qumbiya takeyi,duk kuwa da cewa cikin abaya sakakkiya take da hijabin daya tsaya mata iya qugu saqar qasar indonesia,wanda ya sake fitar da zallar kyanta da kuma yadda ta sake cika ta kuma sake yin kyau.
Duk wani motsinta yana kan idanun abbas har sukayi sallama da 'yan gidan nasu,suka kuma bi ayarin tawagar mai girma governor din bauchi wadda kusan duka iyalinsa ne da manya manyan qusoshin gomnati da matayensu.
A darare take gaidasu saboda rashin sabo,uwa uba kusan duka sun girme mata,sa'annin yayyenta ne aurarru,saidai suna da tsananin kirkin daya gaza boyuwa,kallo daya zakayi musu kuma kasan wayayyun mata ne da suka goge da sanin rayuwa,idan akace wayewa bawai wayewa ta rashin kunya rashin da'a da rashin kamun kai ba,a'ah.......wayewa ta ma'ana da sanin darajar kai da kimar kai wadda ke gauraye da ilimin zamani.
Yadda yaga taqi walwala kafin tashinsu sai yaji duk ba dadi,tana tsaye batasan da isowarsa wajen ba
"Suma fa duk sunayi..... qila jiya da daddarema duk sai da sukayi kafin mu taho nan" abinda taji an fada kenan a kunnenta,da mugun hanzari fararen idanunta a waje ta waiwaya,duk da tasan duk duniya babu mai gaya mata hakan kanshi tsaye sai uncle din nata.....uncle abbas dinta,shi dinne,tsaye a bayanta dab da ita,hannayensa zube a aljihun wandon wata lafiyayyar suit da tunda ya sanyata ta gaza dauke idanunta daga kansa har suka iso nan,murmushi ne kwance saman fuskarsa yana jifanta da wani kallo da su kadai sukasan ma'anarsa,saita langabe kai a shagwabe tana dubansa gami da yi masa nuni da mutanen dake gabansu kadan tana masa alamar kada suji fa,kafadunsa duka biyu ya daga ya watsa hannayensa in i don't care manner,ya sake matsowa kadan yana yin qasa da muryarsa
"Wannan tsoron naki xai sa kowa ya sani" ya furta yana duba agogon hannunsa
"Feel free,u are safe dear,okay?" Saita gyada a hankali,ya aika mata da wani murmushi na musamman sannan ya juya,saita sauke ajiyar zuciya ta bishi da kallo.
Batakai ga waiwayo ba taji maganar daya daga cikin matan mai suna hajiya sha'awa
"Badai har kun fara kewar juna ba?" Kunya sosai ta kamata,saita girgiza kai da sauri,kafin ta amsa mata sauran sun iso,cikin mintuna qalilan ta shige cikinsu ta kuma fara sakewa,saboda yadda suketa qoqarin janta a jiki tare da sakata a hirar su,hirar data dinga jin kamar ta girmeta,saboda hira ce ta manyan mata,amma ta qarfi da yaji haka suke sanyata a ciki.
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*A RUBUCE TAKE*
(K'addarata) Book 02
Ta hadu da mutane masu karamci,don haka bata wani jima ba ta sake sosai a cikinsu,zamu iya cewa tafiyar ta zame mata wani mabudi na alkhairi tare da sake sanin wacece ita,wanne aiki ne a gabanta?,wanne muhimmanci abbas ke dashi a rayuwarta wanda abaya duka hankalinta bai taba mata hasashen hakan ba,duk kuwa da yadda take jinsa sosai a jikinta zuciyarta da ruhinta.
Abun ya fara ne daga yadda suka maidata kamar qanwarsu,koda a aikin hajjin kowa qoqarin tallafarta tare da nuna mata abubuwa yakeyi,musamman daya zamana ita daya ce farkon zuwa wajen,cikij taimakon Allah sukayi hajjinsu lafiya suka gama,sai ya zaman lokacin komawa gida nigeria kadai ya rage musu.
A sannan taga kowacce hankalinta ya tattaru kan mijinta da sukazo tare,a lokacin suka lura da yadda ita din bata maida hankalinta sosai akan hakan kamar yadda su sukeyi,hajiya sha'awa ita ta fara fahimtar hakan,wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi,tuntuni suka gane quruciyar dake dawainiya da ita,wadda wasu abubuwan take gaza yinsu,babu wadda taji kunyarta acikinsu,dukka suka hadu kamar yadda zasu yiwa qannensu uwa daya uba daya suka fara dorata akan sabon saiti.....sabon karatu da sabon darasi.
Bata taba jin kunyar wasu mutane kaf rayuwarta ba irin yadda suka sanyata jin kunya,amma ta dole sukayi mata ta sake ta kuma soma bin karatun nasu.
Abinda bata sani ba kusan kowannensu tasan halayyar hafsat ciki da bai,wannan yasa hatta gidan babu wadda tayi masa zuwa uku, lokacin da sukaga widad din a mazaunin kishiyar hafsat qaunarta da tausayin yadda zata iya zama da ita ya shigesu,wannan yasa suka samu qarfin gwiwar dora mata abubuwa masu nauyi da yawa,wadanda sukasan koda bayan rabuwarsu zai zauna a kanta ya kuma bi jikinta.
Ranar farko kuma karo na farko da taji itama tanason kasancewa da mijinta kamar kowacce mace,ta dauki waya ta kirashi,a sannan suna tare da sauran abokansu da basu taho da matansu ba,saidai dukka kewarta ya isheshi,bayason ya fiya takura mata ko matsanta mata ne kawai,duba da situation din da take ciki,amma he really needs her,kullum kwanan duniya sake shigewa rayuwarsa takeyi.
Cikin karsashi ya daga kiran,saidai muryarta kawai ya kashe masa jiki,ya jingina da kujerar yana saurarenta sanda take magana dashi cikin narke murya
"Bakayi kewata ba ko uncle?" Maganar tata tadan tabashi,har sai daya murmusa
"Har bansan yadda zan misalta miki ba babyn uncle,kawai dai baison takurawa maman baby dama babyn" har ranta taji dadin amsarshi
"Indai hakanne to kazo mu tafi,yau a wajenka zan kwana" mutuwar zaune yayi yana mamaki,widad dinshi ce ke fadar haka da bakinta?,ya rasa amsar da zaya bata har sai data sake cewa
"Hello"
"Than you baby,gani nan zuwa" abinda ya iya fadi kenan jikinsa yana dan rawa kadan,wanda ba lallai ne kai ka fahimta ba
"Ina zuwa" kawai yace musu yana barin wajen.
Kiran wayarsa ya shigo wayarta sanda ta fito daga wanka,tana tsaye jikin madubin dakin nasu tana mulke jikinta da wasu oil perfumes da hajiya fanna ta bata sanda zasu fice subar mata dakin,hajiya khairi ke tsokanar hajiya fanna
"Allah dai yasa ba kyautar turaren banza kikayi mata ba,wala'alla ki dawo ki sameta nade a gado ma tayi baccinta"
"A'ah ai ba za'ayi haka ba,na tabbatar karatunmu yana shiga,nidai ina ganin canji" qas tayi da kanta tana murmushi,dukkaninsu kunyarsu takeji,tunda sun girmeta,tana jinsu suna tsokanarta har suka fice.
Wayar ta daga tace masa gata nan fitowa,ta gama shirinta a nutse,ta dauki duk wani abu da takega ya dace da wanda taga suna dauka suma idan zasu fita din,ita kanta tana jin banbanci da canji a tattare da ita,ta kammala komai a nutse ta fito.
Ko sau daya baiji ya qosa da jiranta ba har ta iso,kasa magana yayi sanda qamshinta ya gaurayeshi,sai ajiyat zuciya mai nauyi daya sauke kawai,suna shiga dakin ya maida qofar ya rufe da wani irin zafin nama,ko ina na jikinsa yana daukan rawa.
Zaucewa ya kusa yi sanda widad din ta miqa masa kanta yadda yakeso,ta kuma hada da bashi gudunmawa,sai kansa gaba daya ya kunce,jikinsa ya dauki rawa tako ina ya fita mata a hayyancinsa.
Bawai shi ba,ko ita din a yau ta gane da banbanci,ta fahimci kuma maganganun su hajiya fanna,bayan komai ya kammala wata kunya ta kamata,yayin da shi kuma ya hanata sakat,bakinsa kuma ya kasa yin shuru,ya dinga zuba sumbatu ya kasa tsuke bakinsa,domin kuwa ta shammace shi fiye da kima,ta kuma kaishi wata duniya da tunda hajiya ta kawoshi sararin duniyar nan bai tana zuwa can din ba,ko sanda yake kidansa yayi rawarsa shi kadai yaya ya qare?,bare yanzu data bashi tallafi ta kuma miqa masa kanta kacokam.
Wannan canji na widad ya tabashi fiye da kima,ya sake kuma cusa wata irin zazzafar soyayyarta a zuciyarsa,ya sake susucewa,har abun yake bawa widad din mamaki,yadda ya dinga cire kudi yana mata siyayya abun sai ya dinga daure mata kai,wanne irin so uncle din nata yake mata haka?.
Ranar da suka fita siyayyar data sake sanya widad sallamawa abbas rayuwarta da jikinta......ta sake yaqini da yadda yake yawan fadin yana sonta,cikin shagon gold ya mallaka mata wata sarqa da farashinta yakai naira dubu dari tara da hamsin.
Kanta ya daure sosai,a wauta da quruciya irin tata tace ba zata karba ba,sai bayan taje dakinsu da ita su hajiya sha'awa suka dinga mata dariya
"Karki qara cewa ba zaki karba ba,tunda ya siya baifi qarfinsa bane,kuma tukuici ne tabbas yake baki,lallai soyayyar da yake miki tana da girma da fadi,saiki sake kula ki kuma tabbatar duk abinda yakeso kina aikatashi sau da qafa,tabbas gaba saikin mallaki abinda yafi haka muddin zaki sallamawa mijinki tare da tsare duk wani abu da yakeso,ki kuma guji wanda bayaso" ta jima a kwance tana tariyo rayuwarta ta baya,da kuma abubuwa da suka faru a yanzu,ko addu'a ce da ummu da mommynta suka yita jaddada mata ta yiwa kanta mijinta da kuma rayuwar aurenta?,ba shakka akwai tasirin addu'ar data dinga yi tuquru,sai gashi tanata ganin abubuwan da ada bata iyasu ba batama san dasu ba.
Ranar da suka qara fita siyayya gefe ta koma kawai tana kallonshi,yadda ya zage yana siyan kayan babies kamar yasan me za'a haifa,har sai data gaji da ganin yadda yake diban kaya kamar baisan ciwon kudinsa ba tayi magana
"Uncle" ta fada a narke
"Baby" ya amsa bayan yabar dukkan abinda yakeyi ya waiwayo yana duban idanunta farare masu haske sosai,wanda suka dan qara girma kadan
"Wai don Allah bakajin kunya?,ciki fa ka yiwa mace" dariyar da bai shiryawa ba ita ta kubce masa,nutsatstsiyar dariya mai wani irin siririn sauti da tasa fararen haqoransa bayyana,sakalci da shirmen quruciya dai a cikin jinin widad qilan yake,sai tayi kaman ta daina sai wataran ta sakankance ta yanko maka wata wautar,kallonta yake kawai yana dariyarsa,yama rasa wacce amsa zai bata.
Turo baki gaba tayi ganin yadda yaketa mata dariyar yana kuma kallonta
"Kaiko a jikinka,ka yiwa mace ciki kuma kana siyan kayan jarirai,bakajin kunya ma mutane su gane". Takowa yayi gaba kadan ya tsaya a gabanta yana kallonta,ko yaushe qara kyau takeyi tana zama wata balarabiya,ba wanda zai kalleta ya yadda ta iya hausa,hakanan babu wanda zai kalleta ya yarda akwai ciki a jikinta
"To ko mutanen duniya zasu fara boye kawunansu ne?" Kai ta daga ta kalleshi don bata gane me yake nufi ba,saiya kashe mata ido daya
"Ai kowa ma ta yadda wannan cikin ya samu ta haka yazo,ciki harda ni dake da......." Da sauri ta rufe masa bakinsa bayan ta danyi dage kadan,saita janye hannunta da sauri
"Kuma me ya kawo wannan maganar?"
"Kece mana" ya amsata yana qunshe dariyarsa
"To naji,amma bakasan fa me za'a haifa ba kake diban kaya"
"Ko meye kika haifa wuud(qauna/soyayya matsananciya) inaso,idan ana haifar rabin mutum ma kika haifamin zan karba hannu bibbiyu" ido ta zaro tana kama haba
"Rabin mutum?,wai?" Yadda tayin ta bashi dariya,sai.ya janyeta cikin hikima sukaci gaba da zaban kayan unisex a tare,ya kuma tura mata option na zabar favourite colors dinta a dabarance,ta zaba din sosai,duk da tanayi tana waiwaye kamar wadda ke aikata wani abu ba dai dai ba.
**************Karfe sha biyu da mintuna na dare motarsu ta tsaya qofar gidansu na bauchi,a sanyaye widad din ta maida bayanta jikin kujera tana kallon gidan,wani mugun tsanar gidan na shigarta sosai,tana jin kamae ta balle murfin motar ta fice ta kama hanyarta,inda zai bata zabi....da salin alin zatace masa ya kaita gidan hajiya ko gidan uncle muhsin,to amma koda ta fada din tasan ba lallai yayi hakan,don zaice mata ne dare yayi,ko baya ga haka ma.....iya kusancin da suka samu a yanzu a tsakaninsu,bata tunanin zai bari tayi nesa dashi.
Shi ya fara fita daga motar yana cewa
"Ina zuwa" saita gyada kai kawai,tana jin yadda qirjinta yake bugawa,tana iya hangensa daga inda suke zaune a motar ita da umar qaninsa daya daukosu,yanata knocking.
Tun yana qwanqwasa a hankali har ya koma bubbugawa da dan tsauri,wasa wasa sai gashi sun kwashe mintuna masu tsaho yana bugawa,amma qofar ko gezau,babu alamun za'a bude musu gidan,har umar dake zaune cikin motar ya miqe ya fita ya soma tayashi bugun.
Tun ransa bai baci ba har ya soma baci,don ba cikin gida ba......muddin dai ba wani abu bane ya samesu ba a irin bugun da yakeyi yasan har maqota sun jishi,sannan ma ba ita daya bace a gidan,idan ita bata ji ba saboda tayi ciki......shi kuma lawal fa dake kusa kusa?(dan dan uwanshi daya dauko sanda zaiyi tafiya).
"Kira number lawal ka hadani dashi" ya fada yana duba agogon hannunsa,umar ya fidda waya ya fara kiransa,amma wayarsa na a kashe,sabanin ta hafsat daketa ringing kuma ba'a daga ba,a handsfree take don haka yaji me computer ta fada, kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai sunji motsi ana tambayar waje,abbas ya tsaya kam yana riqe da qugunsa yana kallon qofar,umar ne ya amsa mata da
"Mune" sai aka fara buda qofar gidan a hankali kamar mai ciwon hannu
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*A RUBUCE TAKE*
(K'addarata)
*Book 02*
Page 03
Sakin qofar tayi tayi gaba,abbas din yabi qofar da kallo sannan ya taka zuwa cikin gidan,ya cimmata sanda take juyawa abinta zuwa ciki,daure da zanin atamfa saman wata kodaddiyar rigar baccinta daya jima yana ganinta jikinta,jin takunsa ya sanyata dan dakatawa kadan ta waiwayo,suka hada ido.
Duk da dare ne da kuma qarancin haske,amma tana iyabhangen yadda taga yayi wani mugun fresh,qamshinsa ya cika wajen,ya mata kyau,amma data tuna a yanzun tare da wa yake sai taji komai ya gushe mata,kishinta ya motsa sosai,wanda tunda umar yazo ya dauki motar da zummar daukosu tahau kan zafinta,ita tunda suke tare dashi bata taba ganin yayi kyau da gogewa irin hakan ba,kuma ba wannan bane ai zuwansa aikin hajji na farko ba
"Me kikeyi mintuna kusan nawa muna tsaye muna bugu?" Ya fada ransa a dan bace
"Bacci ne fa ya daukeni" ta fada murya a cunkushe tana bata rai,sai ya janye idanunsa yana dan jan qaramin tsaki
"Ta yaya zaki kwanta kinsan muna hanya?, at least dai ai kya tsaya kiga shigowata" ya fada yana qoqarin buda gate din gidan da kansa yana yiwa umar maganar ya shigo da motar ciki dare yana qara yi.
Ranta ya sosu,ta tura kayan baki gaba tana jin kamar ta maida masa magana,ason ranta ta shige ciki,amma sai taji tana son tsaiwa taga yarinyar,ta sake tabbatarwa babu cikin da a kullum ta kwanta cikin mafarkinta take ganin kamar tana dashi.
Tana tsaye daga gefan har umar ya shigo da motar ya fakata a parking lot na gidan,ya kasheta sannan widad ta buda murfin motar ta fito tana jin ranta da zuciyarta duka babu dadi.
Rawa qafafun hafsat suka danyi,ta kadu sosai da yadda taga yarinyar ta sake canzawa,sanye take da wata lafiyayyar abaya baqa sidik mai sulbi, balarabiya sakkk!! Haka ta koma,hasken fatarta sai daukan ido yakeyi,ta sake cika sosai,ta zama cikakkiyar mace,kai bazakace widad din da aka mata aure da qananun shekaru bace,duka cikin watannin da basu wuce biyu da tafiyarsu ba irin wannan gagarumin sauyin na babu zato bare tsammani?.
Kasa amsa gaisuwar da take mata tayi,gaba daya a rude take har umar yayi musu sallama ya fice daga gidan bayan abbas ya masa izinin tafiya da motar ya kawo masa ita gobe.
Gajiya gami da tsanar data yiwa gidan ya sake kashe mata jiki,ta kallai abbas
"Uncle bacci nakeji fa" yadda tayi maganar a mugun shagwabe ya taba ran hafsat sosai,saidai a wajen widad din hakan ba komai bane,don kusan a haka yanzun ta saba magana dashi
"Muje sashena,nasan bangarenki akwai qura kam yanzu,dare kuma ya riga yayi bare ki gyara" ya amsa mata a tausashe yana mata wani irin sassanyan kallo da ya riga ya saba yi mata shi,har baisan yana fidda kansa da kansa daga idanunsa ba.
Turqashi!.....me abbas din yake nufi?,taje sashensa ta kwana?,aiko sama da qasa zata hadu ba zata bari hakan ta faru ba,wannan ba komai bane ba face zallar rainin hankali,ta gama fadi tashin gyaran sashen saboda shi sannan yace wata ce zata kwana?,uwa uba ma watansa nawa basa tare,hakan yana nufin zai karbe kwananta na yau ya bawa yarinyar?.
Taku biyu sukayi tasha gabansu,dubansu takeyi kai tsaye
"Ba inda zata ta kwana wallahi,bazan dauki wannan rainin wayon ba" ta fada tana fidda idanunta.
Ido yadan qanqance yana dubanta
"Me kikeyi ne haka?"
"Abinda idonka ya gane maka" kafin abbas din ya sake cewa komai widad ta zame hannunta a hankali ta fara takawa zuwa shiyyar sashenta,shi da hafsat din dukansu suka bita da kallo,sai ya motsa da sauri yabi bayanta,yayin da hafsat ta rakasu da ido qirjinta kamar zai qone saboda zafi da tsananin kishi.
A qofar sassanta tana gwada keys din hannunta ya cimmata
"Me zakiyi a ciki?" Murmushi ta sake masa a nutse
"Zan shiga na kwanta ne uncle dare yana sake yi" ta fada a narke
"Amma ai ba'a gyare yake ba,nace muje part dina ki kwanta a can kafin safiya" a nutse ta girgiza masa kai,fuskarta still da murmushi
"Zan kwanta a nan din uncle,awa nawa ne gari ya waye?,kada ka damu,kana buqatar hutu,kaje ka huta" gaba daya saita gama kwance masa kai,abinda ya kamata ace hafsta dince tayi ita ta gaza sai 'yar cikinta,wani irin qauna da kimar yarinyar ya sake qaruwa a idanunsa,ya santa gwanar tsoro ce,kawai dai tayi hakanne don ta samar masa da kwanciyar hankali da nutsuwa,ya fuskanci wannan din kusan a dabi'arta yake,batason hayaniya sam,sai ya rasa me zaice mata,ya matsa ya karba keys din ya gwada na qofar ya bude sannan ya tura yayi gaba tana biye dashi.
Sosai wajen yayi qura,da kansa ya dinga saka tsintsiya yana kade mata hanya har zuwa bedroom dinta,sai daya tabbatar ta gama komai ta kwanta sannan ya baro sashen.
Runtse idanunta tayi zuciyarta na matsanancin bugu da tsoron dake shigarta kamar zuciyarta zata faso qirjinta ta fito,tana ji har cikin Zuciyarta kamar ana tunkudata ta fice,amma can qasan zuciyarta tana kiran sunan Allah kadan kadan,abinda ya kawo sauqin yanayin da takeji din wanda keta azalzalarta kamar ana gaya mata cikin kunnuwanta.
Bai samu Hafsat din a wajen ba,sai bai wani damu ba,har yanzu Zuciyarsa tana cike da mamakin halayenta, kullum babu sauyi?, sai sake ta'azzara al'amuranta sukeyi?,da wanann tunanin ya isa sassansa.
Ba laifi babu datti hakanan babu qura,yaci gaba da takawa har dakin gadonsa,yana tura kansa,sautin sheshsheqar kukanta yana masa maraba.
Dauke kansa yayi kamar bai ganta ba,baqinciki yana cika masa zuciya,baiga me akayi mata ba da zata zauna a daren daya dawo yana buqatar ya huta ta tusashi da koke koke ba,idan ita bai rufeta da fada ba bazata sashi gaba tana masa kuka ba,sai kawai ya fara rage kayan jikinsa ba tare da yabi ta kanta ba,rabin hankalinsa yana ga widad da yadda yaga taqi sakewa,lallai tsoronta ya dawo,irin tsoron daya ninka na baya,sai wani bangare na zuciyarsa ya bashi ko juna biyun da take dashi ne,qaramin murmushi ya kubce masa sanda ya tuna da ajiyarsa dake jikinta,dai dai sanda muryarta ta ratsa kunnensa cikin sautin kuka
"Da wannan wulaqancin da kakeyimin gwara kacemin ka gaji da zama dani na tafi gid......."
"Hey..... stop it dallah!" Ya katseta da mugun sauri cikin bacin rai yana dubanta,bacin ran data gani a idanunsa sun ninka nata don haka dole tayi shuru tana binsa da kallo
"Banason rainin wayo da wulaqanci cikin daren nan,hutu nake da buqata,idan qorafi ya shigo dake ki tashi ki fita ki bani waje,idan kin fita idan kinga dama ki wuce gidan ban riqe miki qafa ba" sosai.maganar ta daga mata hankali sannan ta bata mata rai,ta sake fashewa da kuka ta miqe tana daukan yusra ta fice a dakin,yaja tsaki yabi bayanta ya kulle qofarsa ya dawo ya wuce bandaki,gaba daya ta gama fita a kansa,fushinta ko kukanta ya daina damunsa sam.
Wannan abun daya faru a daren ya sake tunxura zuciyarta,ta kasa kuma bacci sai data kira ummanta,cikin daren suka qulla abubuwa masu yawa da suke saka ran zasu aiwatar,ko akan widad ko akan abbas din,duk wanda nasararsu ta fada a kansa.
*********Da qyar ta wayi gari da wani irin matsanancin tsoro daya haifar mata da ciwon kai,inda Allah ya taimaketa washegarin saiga su nujood harda hajjaaa sunzo mata,ta samu tadan sake,daga qarshe hajjaa ta tafi tabar mata nujood ta tayata kintsa sashen da sauran gyare gyare,wannan ne ya sanyata tadan warware,saidai komai a darare takeyinsa,koda abune yayi babban faduwa yanzu zata firgita,har nujood ta fahimta ta tambayeta
"Hakanan nakejin haka,nima bansan dalili ba"
"Saikiyita kiran sunan Allah da addu'a"
"Inayi,daqyar nayi bacci jiya"
"Zan karbo miki addu'ar yawan firgita a wajen ya sayyadinmu" da haka suka fada wani zancan,tana ci gaba da addu'a cikin ranta duk sanda taji irin hakan,da haka ta dinga samun sassauci cikin ranta.
Dawowarsu daga saudiyyan sai komai ya sake canzawa,gaba daya hafsat din ta tattara sanya idanunta da komai ta aza akan abbas da widad wadda bata sakata a lissafinta ba kwata kwata,don abinda yake gabanta shi ya dameta,saidai duk wata tijara da abubuwan da zatayi tana jinta daga farfajiyar gidan,ko idan guri ya hadasu,ko daga kai ta kalleta batayi bare akai ga jallin tanka mata,tunda bata taba tararta gaba da gaba ta kama sunanta ba tun sanda abbas din yaja kunnen hafsat,ita a yanzun kawai burinta abbas yace ta shirya su koma kaduna,gaba daya ta tsani garin wani muguwar tsana,duk ranar da ba girkinta bane da qyar take iya bacci saboda wani irin tsoro da yake shigarta,da qyar take hana kanta fita a wasu dararen,saidai ta zauna bakin qofar falo tayita kuka tana jin fita kawai takeson yi.
A WANI DARE karfe sha biyu da rabi na dare,har ya shiga sassansa ya kwanta ya tuna kamar yau din da daddare batasha magungunanta na anti natal ba,ya sauko daga gadon hafsat na gefe tana kwasar baccinta ya fito.
Kamar mutum ya dinga hangowa daga nesa,sai ya sauya yanayin tafiyarsa cikin hikima da dabararsu ta jami'an tsaro,bai wani jima ba ya gane widad dince ke nufar qofa,cikin wani irin zafin nama ya cimmata cikin takun da basu gaza biyar ba,saiji tayi caraf an riqota,ta waiwayo suka hada ido,cikin matuqar kaduwa yace mata
"Ina zaki da daren nan?" Kamar jira takeyi ta fashe da kuka
"Fita nakeson yi,banason gidan nan uncle" mamakinsa ya qaru,to duka me yake kawo haka?,wannan shine karo na biyu daya taba ganinta zata fita din.
A tausashe ya kama hannunta yana son maidata ciki,saita kuma saka kuka
"Don Allah uncle" shuru yayi ya zuba mata ido,yadan lumshe idanunsa hadi da budesu
"Muje ciki magana zamuyi" dole ta sakar masa hannun ya riqeta zuwa ciki.
Bakin gado dukansu suka zauna yana dubanta
"Me yake faruwa?"
"Banason gidan nan" ta amsa masa kanta tsaye tana qwalla
"Me yasa?"
"Tsoro nakeji" shuru ya danyi,ya ciro wayarsa yana son kiran dr,saidai yaga dare yayi,amma duk da haka yanajin ya zama dole ya kirata din.
Bugu daya ta daga ya nema afuwan tashinta,tace batama jima da shigowa daga aiki ba sannan yayi mata tambayar
"Kwai matan da ciki yake sakasu jin zaquwa gajiya da tsanar waje" saita fara masa bayani,yana fahimtarta yana kuma nazartar widad dake zaune a gefansa ta cure waje daya,ya karanci bayananta,to amma a abinda yake gani a tattare da widad din kamar nata yanayin ya dan sha banbam da wadda dr take qoqarin masa bayani
"Amma ba komai,with time zata daina ne" daga baya sukayi sallama yayi mata godiya,sai ya miqe yana kallon widad
"Bari na kawo miki mimi,hakan yayi?" Kai ta gyada masa a hankali sannan ya juya a nutse ya fice,ta bishi da kallo tana sauke ajiyar zuciya,rabon da yarinyar ta kwana a wajenta harta manta,gaba daya uwar ta hanata kwana a wajenta.
Yana buda qofar hafsat din na farkawa,ta bishi da kallo ganin ya shigo ne daga waje,ina yaje?,badai satar kwana aka fara yi mata ba?,saita miqe ta zauna tana kallonsa sanda ya duqa zai dauki mimi daga gadonsu dake gefe,don yau din a nan bacci ya daukesu,sai yace ta barsu kawai
"Bacci take fa"
"Na sani,zata tayata antynta kwana" ya amsa mata ba tare daya kalleta ba,wani abu ya darsu a ranta
"Me ya samu antyn nata?,naga yanxun ita daya take kwana bata ko nemanta ko?"
"Basai wani abu ya sameta zasu kwana wajenta ba ai,tunda yaranta ne itama" ya amsata yana rufe yarinyar da dan qaramin lallausan bargonsu,wanda zamansa a dakin ne kawai yasa bargon ya tsira da mutuncinsa ya kuma dade da kyansa.
Bai sake ce mata komai ya juya ya fice,sai ta bishi da kallo qaramar dariya tana qwace mata,ashe har yanzu da sauran abun nan bai gama sanewa ba,tanason wannan aikin tabbas!, jaddada shi takeson ayi kafin a wuce zuwa matakin gaba,bata qaunar hada inuwa daya da yarinyar kwata kwata.
Sai da kwanciyar tace tayi mata sannan ya tashi yana kallonta
"Ki shirya kayanki jibi zamu koma" wannan shine albishir din da yafi faranta mata rai,duk da ason ranta bataqi ma yace gobe zasu tafi ba,amma babu komai,goben ai a wajenta zai kwana,bata da damuwa.
*H U G U M A*
*Arewabooks: Huguma*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*A RUBUCE TAKE*
(K'addarata)
*Book 02*
Page 01
Cikin mugun mutuwar jiki kasala da kuma fargaba ta hada kalmomin
"Wacce irin matsala kuma umma?,na shiga uku"
"Malam baiga komai akan yarinyar ba,komai ya rufe masa,bai hangi ciki ba,kamar yadda babu tabbacin babu shi".
Goshinta hafsat ta dafe,tana jin yadda zuciyarta ke tafasa,a zahiri tayi mugun tsanar yarinyar,ta zame mata qarfen qafa sosai,tanason kuma ta zama barazana ga rayuwarta,cikin tsananin fusata tace
"Umma,yayi mata koma meye,duk abinda ya dace da ita da zai d'ai d'aita rayuwarta ayishi,banason ganinta kwata kwata cikin gidan nan,yanzu haka fa abban mimi ya biya mata hajji,aikin hajji zasu tafi" ta qarashe maganar tana barkewa da kuka,don abun yayi mata ciwo ba kadan ba.
Salati umman tata ta sake kamar tana gaban hafsat din
"Kina raye kina kallo?,lallai sai munyi da gaske,sai mun tashi tsaye akan yarinyar nan"
*A B B A S*
"Ya salam" ya fada zuciyarsa na wani irin bugawa da matsanancin farinciki, kamar wanda aka yiwa albishir da samun haihuwa karon farko bayan wasu shekaru daya diba yana neman haihuwar ba tare da samu ba,ya bude idanun nasa fuskarsa na fidda wani irin murmushi yana sauke dubansa ga widad.
Ido suka hada shi da ita,ta narke fuska sosai,dab take da sakin kuka,suna hada idon kuma sai rauninta ya bayyana muraran,yasan tabbas yau akwai daru,amma koma meye a shirye yake daya shanyeshi,ciki a jikinta?,cikin da yasha yi mata wayo yana gaya mata ba tarayyarsu ce zata saka tayi ciki ba,shan ruwa a qoshi ne?,yasan lallai zai sha tuhuma.
Hannu ya miqa mata alamun ta taho har yanzu murmushi kwance bisa fuskarsa,amma sai ta kauda kai hawaye na ziraro mata,yasan za'a rina,yau saita Allahu,ya dinga danne dariyarsa sannan ya.miqe tsam ya isa gabanta,ya tsaya daga gefanta yana riqe da hannunta yana murzawa a hankali cikin nasa,idanunsa akan na dr
"Yanzu ya za'a yi?,ina fatan bazai bada matsala ba wajen tafiya"
"Bana jin gaskiya,zanyi qoqari ayi mata komai ku wuce tare,tunda bai nuna ba" ta fada ita kanta tana mamakin watannin cikin,da kuma yadda ya boye kansa da kyau,iya ganinka ba zaka hangeshi jikinta ba.
Komai da akeyi kawai tana binsa da ido ne, hankalinta gaba daya bai jikinta tunda akayi zancan ciki,tsoro da fargaba gaba daya sun hadu sun lullubeta,har suka gama komai yana riqe da hannunta,ya bude mata gaban mota ta shiga ya maida murfin ya rufe ya zagaya mazauninsa shima.
Ai yana shiga tana fashe masa da kuka,kamar wadda ke jira,ya dakata daga kunna motar ya waiwayo yana dubanta
"Ya salam ya Allah.....menene kuma?,ko wani abun na miki ciwo?"
"Wallahi idan abba yaji ka yimin ciki sai ya kashemu ni da kai" duk yadda yaso ya riqe dariyarsa amma wannan karon ya gaza,dariya ta kubce masa,har sai da yasa zara zaran yatsuntsa ya toshe bakinsa kada cibi ya zama qari,sai yaushe zata gama girma ne?,ashe har yau da sauran quruciyar nan tana nan?,ta yaya zai bullo mata,sai kawai ya juya fuskarsa zuwa kalar alhini shima yana dubanta
"Innalillahi......yanzu ya kike ganin za'a yi?" Da farko dariyarsa ta qular da ita,amma yanzun maganar da yayi saita wanke wancan
"Nima ban sani bafa....duk kaine ka jawo,saida nace banaso,kace wai idan nasha ruwa ne zaizo" ta fada yana harararsa,saiya narke fuska kalar tausayi ya langabar da kai
"To ai nima na zata hakanne,kuma ma kinsan me?" Kaita girgiza tana sharar qwalla,sai ya juyo yana fuskantarta sosai
"Sanda kika gudu kano?" Saita gyada kai tana dubansa
"Abba da kansa ya kirani yace nayi wannan abun fa da bakiso din" dukka idanunta ta fidda waje kamar zasu fado tana kallonsa a tsorace,ya jijjiga mata kai
"Da gaske nake" ya sake fada yana danne dariyarsa,bai ankara ba ya takai masa duka tana sake fashewa da wani kukan a sakalce
"Allah abbana ba dan iska bane da zaice maka haka" sosai yau din take sashi dariya,ya kare dukan da daya hannun yana dariya tare da fadin
"Allah.....Allah kinji nace Allah" ta sanshi farin sani,kaifi daya ne,baya qarya,yana fadin hakan sai kunya ta kamata,ta kifa kanta a cinya tana juya yadda abban nata zaice haka,yanzu.kowa.kenan yasan abinda suke aikatawa?,tana jinsa yanata magana amma bata dago ba bare ta amsa,yana dariya qasa qasa ya tashi motar sukabar asibitin,ransa fes,zuciyarsa qal,wani farinciki daya jima rabon da yaji irinsa ya cika masa zuciya,har hakan yana bayyana kansa saman fuskarsa.
Saida sukayi nisa a tafiyar yace
"Kona ajjiyeki gidan hajiya?" Ya fadi hakanne saboda yadda yaga sam.batason zaman gidan nasu,saita girgiza kai da sauri
"Aah,nidai ka kaini gida" murmushi ya subuce masa,ya gane mai take gudu,kada hajiya ta gano tana da ciki,daga haka yabar zancan ya dauke kan motar suka nufi gida.
Sanda ya tsaida motar da kansa ya dauki hand bag dinta yana riqe da ita zuwa ciki,ta langabe kai tana kallonsa
"Ka bani,zan iya dauka" kai ya girgiza idanunsa cikin nata,yana jin wata qaunarta tana fusgarsa
"Ban yarda ba baby,dama naji a jikina,wannan rashin lafiyan akwai dalili,muje kawai,ko na daukeki?" Ya fadi shima yana langabar dakai,kunya ya bata,ta kauda kanta gefe tana gulmarsa cikin ranta,wai shi kam bayajin kunya ne ma wai?,kamar ba ciki yayi mata ba?.
Kamar yasan maganar da takeyi ya saki murmushi kadan,ya kama hannunta ya matsa kadan yana cewa
"Muje baby".
Sanda suke shiga din akan idanun hafsat dake tsaye bakin window,tunda suka fita ta kasa zama,zuciyara nata qiyasta mata gurare daban daban da zasu iya zuwa,tana goye da shukra dake ta faman rigima,ji take kaman ta yago yarinya ta ajjiyeta,qunqunin yarinyar har tsakiyar kwanyarta,idanunta suka sauka kan handbag din widad da hannayensu dake sarqafe waje guda.
Wani matsanancin qunci zuciyarta ta shiga,duk yadda taso daurewa amma ta kasa,ta saki ashar,kasheta mutanen nan sukeson yi?,bayan abinda abbas din ya aikata mata shine zasuci gaba da sabgarsu kamar ma ba'a yi mata komai cikin gidan ba?,ba zata iya dauka ba,dole kowa yasan an tabota,sai kawai ta kunce yarinyar ta aza saman kujera ta nufi qofa da wani irin mugun sauri.
Idanunsa ya lumshe kadan,yana tsaye saman kanta yana mata wani duba dake cike da shauqinta,ko yaya ta motsa sai taja hankalinsa
"Zan dan fita,amma bazan jima ba zan dawo,me kike buqata?" Ya qarashe fada yana ritsata da idanunsa masu matuqar kwarjini da jan hankali,sai tadan rufe idanunta kadan ta girgiza kai
"Babu komai"
"Really?" Ya tambayeta yana dubanta,kai ta sake gyada masa
"Okay.....zan tafi" ya sake maimaitawa,saita sake lumshe idonta,tasna me.yakeso,amma jikinta a mace yake murus,ta gyara zamanta sosai ta nutse cikin kujerar sannan tace
"A dawo lafiya"
"Au 'yar hakace yau?" Murmushi tayi kawai tana boye fuskarta,saiya saki wani murmushin,ya duqa kadan a tausashe yayi kissing goshinta sannan yace
"Take care of yourself" kai ta jinjina,sai daya juya sannan ta bishi da kallo,zuciyarta na gaya mata wai da gaske ba abun kunya sukayi ba,ta dora hannunta saman cikinta a hankali tana shafawa cike da mamaki da kuma tsoron cewa wai ciki ne a jikinta.
Dai dai sanda muryar hafsat ta ratso har cikin falon nata da wani irin amo,sai ta bude idonta a hankali tana saurarenta sanda take magana cikin rawar murya
"Wallahi bazan yafe wannan zaluncin ba,sai Allah yayi min sakayya" wani mugun tsaki widad din taja tana tabe baki gami da gyara kwanciyarta cikin kujerar,ita gaba daya mutuncin matar ya gama zubewa a idanunta,tunda take bata taba ganin yadda akema babba rashin kunya ba kamar yadda itadin taga tana yiwa abbansu mimin,ko babu komai aiya girmeta,kuma ko ummu da take tsohuwa ai tana ganin yadda take girmama alhaji,har tabar gidansu bata taba gani ta karba abu daga hannunsa daga tsaye ba,ko ya fada tace a'ah, miqewa tayi cak tana daukar jakarta ta wuce bedroom dinta,haka kawai taji batason jin wata hayaniya kusa da ita.
Hannu daya abbas ya sanya cikin zallar bacin rai ya fincikota,ya riqeta gam yana tafe riqe da ita,bai tsaya ko ina ba sai da yakai sassanta ya watsar mata da hannun cikin falon,da yatsa ya nunata
"Wannan ya zamana shine lokaci na qarshe da zaki qara gangancin cewa zaki shiga sashenta ko zaki tabata,daga lokacin da kikayi wannan kuskuren zaki fahimci baki da wayo,tunda na fahimci sauna ce ke shashasha wadda batasan girmanta ba" sosai maganarsa ta doketa kamar saukar mashi saman zuciyarta,ita din abbas yake cewa sauna shashasha?
"Kowanne suna kakeso ka kirani dashi,daidanka ne,amma bazan fasa neman haqqina ba"
"Idan kika fasa neman haqqinki kin raina Allah" kalmar da tasa ta bishi galala da kallo har ya fice,sai ta sake fashewa da kuka,dole tayi iya yinta taga ta tarwatsa farincikinsu,ba zata zauna ita kadai bacin rai ya hallakata ba.
Yana tafe zuciyarsa cike da bacin rai,mahaifin hafsat shi daya yake tunawa,mutumin kirki da kowa ya yaba halayyarsa kafin barinsa duniya,yana sonsa yana girmamashi,har yau yana tuna haquri na qarshe daya bashi a kanta kafin barinsa duniya da 'yan awanni,yaja wani dogon tsaki,xuciyarsa na ayyana masa hukunci kala daban daban da zai iya dauka a kanta.
A hankali kuma yaji yana sauka musamman daya tuna kyautar da Allah yayi masa a yau daga wajen halitta mafi soyuwa cikin rayuwarsa,sai yaji dukkan haukan hafsat din wani abune mara muhimmanci da zai iya tattarasu ya watsa kwandon shara,idan ta gaji ta sauke kamar yadda ta saba.
*******Cikin kwanakin da sukayi cikin gidan kafin tashinsu saudiyya dan qaramin yaqi aka dinga gwabzawa tsakanin abbas da hafsat din,kullum cikin kuka qorafi da masifa,dai dai sanda 'yan abun nasa suka motsa(miskilanci),yayi watsin tsiya da ita,tamkar ma ba dashi take ba.
Ta fannin widad ma sai tayi kamar batasan me ake ba,dama ita dimma ba baya bace wajen miskilancin,bare a yanzun da take mugun jin xafin mummy hafsat din haka kawai,ta tsani ta ganta tare da uncle din nata,tana dannewa ne tayi kamar bai dameta ba tunda batasan ainihin me yasa takejin hakan ba,uwa uba ko meye zatayi saidai ta jiyota daha sashensa sashenta ko.farfajiyar gidan,bata doso sassanta,wannan yasa bata dameta ba,a kullum tunaninta da zuluminta sanda kowa zaisan tana da ciki,cikin wata irin wauta dake sanya abbas din ya qunshe kansa yayita mata dariya,a fuska kuma ya tayata jimami da alhini kamar gaske.
A lokacin hafsat din ji take kamar zata mutu,yaqi kulata sannan widad din da taso rage zafi da ita ya mata shamakin da ko giyar wake tasha ba zata doshi sassanta ba,ta sanshi farin sani,yana da kawaici yana da alkunya,amma duk sanda ka sake ka turashi inda bai kamata ka turashi din ba.....to kuwa abinda zai biyo baya bashi da sauqi.
Duk haukar da hafsat din keyi hakan bai canza komai ba,don kuwa kwanakinsu biyar suka wuce kano,kai tsaye kuma sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na mallam aminu kano.
Sosai widad din tayi mamakin ganin 'yan gidansu acan suna jiransu,tayi farinciki sosai amma kuma abinda tasan tana tattare dashi ya hanata sakewa,sai qumbiya qumbiya takeyi,duk kuwa da cewa cikin abaya sakakkiya take da hijabin daya tsaya mata iya qugu saqar qasar indonesia,wanda ya sake fitar da zallar kyanta da kuma yadda ta sake cika ta kuma sake yin kyau.
Duk wani motsinta yana kan idanun abbas har sukayi sallama da 'yan gidan nasu,suka kuma bi ayarin tawagar mai girma governor din bauchi wadda kusan duka iyalinsa ne da manya manyan qusoshin gomnati da matayensu.
A darare take gaidasu saboda rashin sabo,uwa uba kusan duka sun girme mata,sa'annin yayyenta ne aurarru,saidai suna da tsananin kirkin daya gaza boyuwa,kallo daya zakayi musu kuma kasan wayayyun mata ne da suka goge da sanin rayuwa,idan akace wayewa bawai wayewa ta rashin kunya rashin da'a da rashin kamun kai ba,a'ah.......wayewa ta ma'ana da sanin darajar kai da kimar kai wadda ke gauraye da ilimin zamani.
Yadda yaga taqi walwala kafin tashinsu sai yaji duk ba dadi,tana tsaye batasan da isowarsa wajen ba
"Suma fa duk sunayi..... qila jiya da daddarema duk sai da sukayi kafin mu taho nan" abinda taji an fada kenan a kunnenta,da mugun hanzari fararen idanunta a waje ta waiwaya,duk da tasan duk duniya babu mai gaya mata hakan kanshi tsaye sai uncle din nata.....uncle abbas dinta,shi dinne,tsaye a bayanta dab da ita,hannayensa zube a aljihun wandon wata lafiyayyar suit da tunda ya sanyata ta gaza dauke idanunta daga kansa har suka iso nan,murmushi ne kwance saman fuskarsa yana jifanta da wani kallo da su kadai sukasan ma'anarsa,saita langabe kai a shagwabe tana dubansa gami da yi masa nuni da mutanen dake gabansu kadan tana masa alamar kada suji fa,kafadunsa duka biyu ya daga ya watsa hannayensa in i don't care manner,ya sake matsowa kadan yana yin qasa da muryarsa
"Wannan tsoron naki xai sa kowa ya sani" ya furta yana duba agogon hannunsa
"Feel free,u are safe dear,okay?" Saita gyada a hankali,ya aika mata da wani murmushi na musamman sannan ya juya,saita sauke ajiyar zuciya ta bishi da kallo.
Batakai ga waiwayo ba taji maganar daya daga cikin matan mai suna hajiya sha'awa
"Badai har kun fara kewar juna ba?" Kunya sosai ta kamata,saita girgiza kai da sauri,kafin ta amsa mata sauran sun iso,cikin mintuna qalilan ta shige cikinsu ta kuma fara sakewa,saboda yadda suketa qoqarin janta a jiki tare da sakata a hirar su,hirar data dinga jin kamar ta girmeta,saboda hira ce ta manyan mata,amma ta qarfi da yaji haka suke sanyata a ciki.
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*A RUBUCE TAKE*
(K'addarata) Book 02
Ta hadu da mutane masu karamci,don haka bata wani jima ba ta sake sosai a cikinsu,zamu iya cewa tafiyar ta zame mata wani mabudi na alkhairi tare da sake sanin wacece ita,wanne aiki ne a gabanta?,wanne muhimmanci abbas ke dashi a rayuwarta wanda abaya duka hankalinta bai taba mata hasashen hakan ba,duk kuwa da yadda take jinsa sosai a jikinta zuciyarta da ruhinta.
Abun ya fara ne daga yadda suka maidata kamar qanwarsu,koda a aikin hajjin kowa qoqarin tallafarta tare da nuna mata abubuwa yakeyi,musamman daya zamana ita daya ce farkon zuwa wajen,cikij taimakon Allah sukayi hajjinsu lafiya suka gama,sai ya zaman lokacin komawa gida nigeria kadai ya rage musu.
A sannan taga kowacce hankalinta ya tattaru kan mijinta da sukazo tare,a lokacin suka lura da yadda ita din bata maida hankalinta sosai akan hakan kamar yadda su sukeyi,hajiya sha'awa ita ta fara fahimtar hakan,wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi,tuntuni suka gane quruciyar dake dawainiya da ita,wadda wasu abubuwan take gaza yinsu,babu wadda taji kunyarta acikinsu,dukka suka hadu kamar yadda zasu yiwa qannensu uwa daya uba daya suka fara dorata akan sabon saiti.....sabon karatu da sabon darasi.
Bata taba jin kunyar wasu mutane kaf rayuwarta ba irin yadda suka sanyata jin kunya,amma ta dole sukayi mata ta sake ta kuma soma bin karatun nasu.
Abinda bata sani ba kusan kowannensu tasan halayyar hafsat ciki da bai,wannan yasa hatta gidan babu wadda tayi masa zuwa uku, lokacin da sukaga widad din a mazaunin kishiyar hafsat qaunarta da tausayin yadda zata iya zama da ita ya shigesu,wannan yasa suka samu qarfin gwiwar dora mata abubuwa masu nauyi da yawa,wadanda sukasan koda bayan rabuwarsu zai zauna a kanta ya kuma bi jikinta.
Ranar farko kuma karo na farko da taji itama tanason kasancewa da mijinta kamar kowacce mace,ta dauki waya ta kirashi,a sannan suna tare da sauran abokansu da basu taho da matansu ba,saidai dukka kewarta ya isheshi,bayason ya fiya takura mata ko matsanta mata ne kawai,duba da situation din da take ciki,amma he really needs her,kullum kwanan duniya sake shigewa rayuwarsa takeyi.
Cikin karsashi ya daga kiran,saidai muryarta kawai ya kashe masa jiki,ya jingina da kujerar yana saurarenta sanda take magana dashi cikin narke murya
"Bakayi kewata ba ko uncle?" Maganar tata tadan tabashi,har sai daya murmusa
"Har bansan yadda zan misalta miki ba babyn uncle,kawai dai baison takurawa maman baby dama babyn" har ranta taji dadin amsarshi
"Indai hakanne to kazo mu tafi,yau a wajenka zan kwana" mutuwar zaune yayi yana mamaki,widad dinshi ce ke fadar haka da bakinta?,ya rasa amsar da zaya bata har sai data sake cewa
"Hello"
"Than you baby,gani nan zuwa" abinda ya iya fadi kenan jikinsa yana dan rawa kadan,wanda ba lallai ne kai ka fahimta ba
"Ina zuwa" kawai yace musu yana barin wajen.
Kiran wayarsa ya shigo wayarta sanda ta fito daga wanka,tana tsaye jikin madubin dakin nasu tana mulke jikinta da wasu oil perfumes da hajiya fanna ta bata sanda zasu fice subar mata dakin,hajiya khairi ke tsokanar hajiya fanna
"Allah dai yasa ba kyautar turaren banza kikayi mata ba,wala'alla ki dawo ki sameta nade a gado ma tayi baccinta"
"A'ah ai ba za'ayi haka ba,na tabbatar karatunmu yana shiga,nidai ina ganin canji" qas tayi da kanta tana murmushi,dukkaninsu kunyarsu takeji,tunda sun girmeta,tana jinsu suna tsokanarta har suka fice.
Wayar ta daga tace masa gata nan fitowa,ta gama shirinta a nutse,ta dauki duk wani abu da takega ya dace da wanda taga suna dauka suma idan zasu fita din,ita kanta tana jin banbanci da canji a tattare da ita,ta kammala komai a nutse ta fito.
Ko sau daya baiji ya qosa da jiranta ba har ta iso,kasa magana yayi sanda qamshinta ya gaurayeshi,sai ajiyat zuciya mai nauyi daya sauke kawai,suna shiga dakin ya maida qofar ya rufe da wani irin zafin nama,ko ina na jikinsa yana daukan rawa.
Zaucewa ya kusa yi sanda widad din ta miqa masa kanta yadda yakeso,ta kuma hada da bashi gudunmawa,sai kansa gaba daya ya kunce,jikinsa ya dauki rawa tako ina ya fita mata a hayyancinsa.
Bawai shi ba,ko ita din a yau ta gane da banbanci,ta fahimci kuma maganganun su hajiya fanna,bayan komai ya kammala wata kunya ta kamata,yayin da shi kuma ya hanata sakat,bakinsa kuma ya kasa yin shuru,ya dinga zuba sumbatu ya kasa tsuke bakinsa,domin kuwa ta shammace shi fiye da kima,ta kuma kaishi wata duniya da tunda hajiya ta kawoshi sararin duniyar nan bai tana zuwa can din ba,ko sanda yake kidansa yayi rawarsa shi kadai yaya ya qare?,bare yanzu data bashi tallafi ta kuma miqa masa kanta kacokam.
Wannan canji na widad ya tabashi fiye da kima,ya sake kuma cusa wata irin zazzafar soyayyarta a zuciyarsa,ya sake susucewa,har abun yake bawa widad din mamaki,yadda ya dinga cire kudi yana mata siyayya abun sai ya dinga daure mata kai,wanne irin so uncle din nata yake mata haka?.
Ranar da suka fita siyayyar data sake sanya widad sallamawa abbas rayuwarta da jikinta......ta sake yaqini da yadda yake yawan fadin yana sonta,cikin shagon gold ya mallaka mata wata sarqa da farashinta yakai naira dubu dari tara da hamsin.
Kanta ya daure sosai,a wauta da quruciya irin tata tace ba zata karba ba,sai bayan taje dakinsu da ita su hajiya sha'awa suka dinga mata dariya
"Karki qara cewa ba zaki karba ba,tunda ya siya baifi qarfinsa bane,kuma tukuici ne tabbas yake baki,lallai soyayyar da yake miki tana da girma da fadi,saiki sake kula ki kuma tabbatar duk abinda yakeso kina aikatashi sau da qafa,tabbas gaba saikin mallaki abinda yafi haka muddin zaki sallamawa mijinki tare da tsare duk wani abu da yakeso,ki kuma guji wanda bayaso" ta jima a kwance tana tariyo rayuwarta ta baya,da kuma abubuwa da suka faru a yanzu,ko addu'a ce da ummu da mommynta suka yita jaddada mata ta yiwa kanta mijinta da kuma rayuwar aurenta?,ba shakka akwai tasirin addu'ar data dinga yi tuquru,sai gashi tanata ganin abubuwan da ada bata iyasu ba batama san dasu ba.
Ranar da suka qara fita siyayya gefe ta koma kawai tana kallonshi,yadda ya zage yana siyan kayan babies kamar yasan me za'a haifa,har sai data gaji da ganin yadda yake diban kaya kamar baisan ciwon kudinsa ba tayi magana
"Uncle" ta fada a narke
"Baby" ya amsa bayan yabar dukkan abinda yakeyi ya waiwayo yana duban idanunta farare masu haske sosai,wanda suka dan qara girma kadan
"Wai don Allah bakajin kunya?,ciki fa ka yiwa mace" dariyar da bai shiryawa ba ita ta kubce masa,nutsatstsiyar dariya mai wani irin siririn sauti da tasa fararen haqoransa bayyana,sakalci da shirmen quruciya dai a cikin jinin widad qilan yake,sai tayi kaman ta daina sai wataran ta sakankance ta yanko maka wata wautar,kallonta yake kawai yana dariyarsa,yama rasa wacce amsa zai bata.
Turo baki gaba tayi ganin yadda yaketa mata dariyar yana kuma kallonta
"Kaiko a jikinka,ka yiwa mace ciki kuma kana siyan kayan jarirai,bakajin kunya ma mutane su gane". Takowa yayi gaba kadan ya tsaya a gabanta yana kallonta,ko yaushe qara kyau takeyi tana zama wata balarabiya,ba wanda zai kalleta ya yadda ta iya hausa,hakanan babu wanda zai kalleta ya yarda akwai ciki a jikinta
"To ko mutanen duniya zasu fara boye kawunansu ne?" Kai ta daga ta kalleshi don bata gane me yake nufi ba,saiya kashe mata ido daya
"Ai kowa ma ta yadda wannan cikin ya samu ta haka yazo,ciki harda ni dake da......." Da sauri ta rufe masa bakinsa bayan ta danyi dage kadan,saita janye hannunta da sauri
"Kuma me ya kawo wannan maganar?"
"Kece mana" ya amsata yana qunshe dariyarsa
"To naji,amma bakasan fa me za'a haifa ba kake diban kaya"
"Ko meye kika haifa wuud(qauna/soyayya matsananciya) inaso,idan ana haifar rabin mutum ma kika haifamin zan karba hannu bibbiyu" ido ta zaro tana kama haba
"Rabin mutum?,wai?" Yadda tayin ta bashi dariya,sai.ya janyeta cikin hikima sukaci gaba da zaban kayan unisex a tare,ya kuma tura mata option na zabar favourite colors dinta a dabarance,ta zaba din sosai,duk da tanayi tana waiwaye kamar wadda ke aikata wani abu ba dai dai ba.
**************Karfe sha biyu da mintuna na dare motarsu ta tsaya qofar gidansu na bauchi,a sanyaye widad din ta maida bayanta jikin kujera tana kallon gidan,wani mugun tsanar gidan na shigarta sosai,tana jin kamae ta balle murfin motar ta fice ta kama hanyarta,inda zai bata zabi....da salin alin zatace masa ya kaita gidan hajiya ko gidan uncle muhsin,to amma koda ta fada din tasan ba lallai yayi hakan,don zaice mata ne dare yayi,ko baya ga haka ma.....iya kusancin da suka samu a yanzu a tsakaninsu,bata tunanin zai bari tayi nesa dashi.
Shi ya fara fita daga motar yana cewa
"Ina zuwa" saita gyada kai kawai,tana jin yadda qirjinta yake bugawa,tana iya hangensa daga inda suke zaune a motar ita da umar qaninsa daya daukosu,yanata knocking.
Tun yana qwanqwasa a hankali har ya koma bubbugawa da dan tsauri,wasa wasa sai gashi sun kwashe mintuna masu tsaho yana bugawa,amma qofar ko gezau,babu alamun za'a bude musu gidan,har umar dake zaune cikin motar ya miqe ya fita ya soma tayashi bugun.
Tun ransa bai baci ba har ya soma baci,don ba cikin gida ba......muddin dai ba wani abu bane ya samesu ba a irin bugun da yakeyi yasan har maqota sun jishi,sannan ma ba ita daya bace a gidan,idan ita bata ji ba saboda tayi ciki......shi kuma lawal fa dake kusa kusa?(dan dan uwanshi daya dauko sanda zaiyi tafiya).
"Kira number lawal ka hadani dashi" ya fada yana duba agogon hannunsa,umar ya fidda waya ya fara kiransa,amma wayarsa na a kashe,sabanin ta hafsat daketa ringing kuma ba'a daga ba,a handsfree take don haka yaji me computer ta fada, kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai sunji motsi ana tambayar waje,abbas ya tsaya kam yana riqe da qugunsa yana kallon qofar,umar ne ya amsa mata da
"Mune" sai aka fara buda qofar gidan a hankali kamar mai ciwon hannu
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*A RUBUCE TAKE*
(K'addarata)
*Book 02*
Page 03
Sakin qofar tayi tayi gaba,abbas din yabi qofar da kallo sannan ya taka zuwa cikin gidan,ya cimmata sanda take juyawa abinta zuwa ciki,daure da zanin atamfa saman wata kodaddiyar rigar baccinta daya jima yana ganinta jikinta,jin takunsa ya sanyata dan dakatawa kadan ta waiwayo,suka hada ido.
Duk da dare ne da kuma qarancin haske,amma tana iyabhangen yadda taga yayi wani mugun fresh,qamshinsa ya cika wajen,ya mata kyau,amma data tuna a yanzun tare da wa yake sai taji komai ya gushe mata,kishinta ya motsa sosai,wanda tunda umar yazo ya dauki motar da zummar daukosu tahau kan zafinta,ita tunda suke tare dashi bata taba ganin yayi kyau da gogewa irin hakan ba,kuma ba wannan bane ai zuwansa aikin hajji na farko ba
"Me kikeyi mintuna kusan nawa muna tsaye muna bugu?" Ya fada ransa a dan bace
"Bacci ne fa ya daukeni" ta fada murya a cunkushe tana bata rai,sai ya janye idanunsa yana dan jan qaramin tsaki
"Ta yaya zaki kwanta kinsan muna hanya?, at least dai ai kya tsaya kiga shigowata" ya fada yana qoqarin buda gate din gidan da kansa yana yiwa umar maganar ya shigo da motar ciki dare yana qara yi.
Ranta ya sosu,ta tura kayan baki gaba tana jin kamar ta maida masa magana,ason ranta ta shige ciki,amma sai taji tana son tsaiwa taga yarinyar,ta sake tabbatarwa babu cikin da a kullum ta kwanta cikin mafarkinta take ganin kamar tana dashi.
Tana tsaye daga gefan har umar ya shigo da motar ya fakata a parking lot na gidan,ya kasheta sannan widad ta buda murfin motar ta fito tana jin ranta da zuciyarta duka babu dadi.
Rawa qafafun hafsat suka danyi,ta kadu sosai da yadda taga yarinyar ta sake canzawa,sanye take da wata lafiyayyar abaya baqa sidik mai sulbi, balarabiya sakkk!! Haka ta koma,hasken fatarta sai daukan ido yakeyi,ta sake cika sosai,ta zama cikakkiyar mace,kai bazakace widad din da aka mata aure da qananun shekaru bace,duka cikin watannin da basu wuce biyu da tafiyarsu ba irin wannan gagarumin sauyin na babu zato bare tsammani?.
Kasa amsa gaisuwar da take mata tayi,gaba daya a rude take har umar yayi musu sallama ya fice daga gidan bayan abbas ya masa izinin tafiya da motar ya kawo masa ita gobe.
Gajiya gami da tsanar data yiwa gidan ya sake kashe mata jiki,ta kallai abbas
"Uncle bacci nakeji fa" yadda tayi maganar a mugun shagwabe ya taba ran hafsat sosai,saidai a wajen widad din hakan ba komai bane,don kusan a haka yanzun ta saba magana dashi
"Muje sashena,nasan bangarenki akwai qura kam yanzu,dare kuma ya riga yayi bare ki gyara" ya amsa mata a tausashe yana mata wani irin sassanyan kallo da ya riga ya saba yi mata shi,har baisan yana fidda kansa da kansa daga idanunsa ba.
Turqashi!.....me abbas din yake nufi?,taje sashensa ta kwana?,aiko sama da qasa zata hadu ba zata bari hakan ta faru ba,wannan ba komai bane ba face zallar rainin hankali,ta gama fadi tashin gyaran sashen saboda shi sannan yace wata ce zata kwana?,uwa uba ma watansa nawa basa tare,hakan yana nufin zai karbe kwananta na yau ya bawa yarinyar?.
Taku biyu sukayi tasha gabansu,dubansu takeyi kai tsaye
"Ba inda zata ta kwana wallahi,bazan dauki wannan rainin wayon ba" ta fada tana fidda idanunta.
Ido yadan qanqance yana dubanta
"Me kikeyi ne haka?"
"Abinda idonka ya gane maka" kafin abbas din ya sake cewa komai widad ta zame hannunta a hankali ta fara takawa zuwa shiyyar sashenta,shi da hafsat din dukansu suka bita da kallo,sai ya motsa da sauri yabi bayanta,yayin da hafsat ta rakasu da ido qirjinta kamar zai qone saboda zafi da tsananin kishi.
A qofar sassanta tana gwada keys din hannunta ya cimmata
"Me zakiyi a ciki?" Murmushi ta sake masa a nutse
"Zan shiga na kwanta ne uncle dare yana sake yi" ta fada a narke
"Amma ai ba'a gyare yake ba,nace muje part dina ki kwanta a can kafin safiya" a nutse ta girgiza masa kai,fuskarta still da murmushi
"Zan kwanta a nan din uncle,awa nawa ne gari ya waye?,kada ka damu,kana buqatar hutu,kaje ka huta" gaba daya saita gama kwance masa kai,abinda ya kamata ace hafsta dince tayi ita ta gaza sai 'yar cikinta,wani irin qauna da kimar yarinyar ya sake qaruwa a idanunsa,ya santa gwanar tsoro ce,kawai dai tayi hakanne don ta samar masa da kwanciyar hankali da nutsuwa,ya fuskanci wannan din kusan a dabi'arta yake,batason hayaniya sam,sai ya rasa me zaice mata,ya matsa ya karba keys din ya gwada na qofar ya bude sannan ya tura yayi gaba tana biye dashi.
Sosai wajen yayi qura,da kansa ya dinga saka tsintsiya yana kade mata hanya har zuwa bedroom dinta,sai daya tabbatar ta gama komai ta kwanta sannan ya baro sashen.
Runtse idanunta tayi zuciyarta na matsanancin bugu da tsoron dake shigarta kamar zuciyarta zata faso qirjinta ta fito,tana ji har cikin Zuciyarta kamar ana tunkudata ta fice,amma can qasan zuciyarta tana kiran sunan Allah kadan kadan,abinda ya kawo sauqin yanayin da takeji din wanda keta azalzalarta kamar ana gaya mata cikin kunnuwanta.
Bai samu Hafsat din a wajen ba,sai bai wani damu ba,har yanzu Zuciyarsa tana cike da mamakin halayenta, kullum babu sauyi?, sai sake ta'azzara al'amuranta sukeyi?,da wanann tunanin ya isa sassansa.
Ba laifi babu datti hakanan babu qura,yaci gaba da takawa har dakin gadonsa,yana tura kansa,sautin sheshsheqar kukanta yana masa maraba.
Dauke kansa yayi kamar bai ganta ba,baqinciki yana cika masa zuciya,baiga me akayi mata ba da zata zauna a daren daya dawo yana buqatar ya huta ta tusashi da koke koke ba,idan ita bai rufeta da fada ba bazata sashi gaba tana masa kuka ba,sai kawai ya fara rage kayan jikinsa ba tare da yabi ta kanta ba,rabin hankalinsa yana ga widad da yadda yaga taqi sakewa,lallai tsoronta ya dawo,irin tsoron daya ninka na baya,sai wani bangare na zuciyarsa ya bashi ko juna biyun da take dashi ne,qaramin murmushi ya kubce masa sanda ya tuna da ajiyarsa dake jikinta,dai dai sanda muryarta ta ratsa kunnensa cikin sautin kuka
"Da wannan wulaqancin da kakeyimin gwara kacemin ka gaji da zama dani na tafi gid......."
"Hey..... stop it dallah!" Ya katseta da mugun sauri cikin bacin rai yana dubanta,bacin ran data gani a idanunsa sun ninka nata don haka dole tayi shuru tana binsa da kallo
"Banason rainin wayo da wulaqanci cikin daren nan,hutu nake da buqata,idan qorafi ya shigo dake ki tashi ki fita ki bani waje,idan kin fita idan kinga dama ki wuce gidan ban riqe miki qafa ba" sosai.maganar ta daga mata hankali sannan ta bata mata rai,ta sake fashewa da kuka ta miqe tana daukan yusra ta fice a dakin,yaja tsaki yabi bayanta ya kulle qofarsa ya dawo ya wuce bandaki,gaba daya ta gama fita a kansa,fushinta ko kukanta ya daina damunsa sam.
Wannan abun daya faru a daren ya sake tunxura zuciyarta,ta kasa kuma bacci sai data kira ummanta,cikin daren suka qulla abubuwa masu yawa da suke saka ran zasu aiwatar,ko akan widad ko akan abbas din,duk wanda nasararsu ta fada a kansa.
*********Da qyar ta wayi gari da wani irin matsanancin tsoro daya haifar mata da ciwon kai,inda Allah ya taimaketa washegarin saiga su nujood harda hajjaaa sunzo mata,ta samu tadan sake,daga qarshe hajjaa ta tafi tabar mata nujood ta tayata kintsa sashen da sauran gyare gyare,wannan ne ya sanyata tadan warware,saidai komai a darare takeyinsa,koda abune yayi babban faduwa yanzu zata firgita,har nujood ta fahimta ta tambayeta
"Hakanan nakejin haka,nima bansan dalili ba"
"Saikiyita kiran sunan Allah da addu'a"
"Inayi,daqyar nayi bacci jiya"
"Zan karbo miki addu'ar yawan firgita a wajen ya sayyadinmu" da haka suka fada wani zancan,tana ci gaba da addu'a cikin ranta duk sanda taji irin hakan,da haka ta dinga samun sassauci cikin ranta.
Dawowarsu daga saudiyyan sai komai ya sake canzawa,gaba daya hafsat din ta tattara sanya idanunta da komai ta aza akan abbas da widad wadda bata sakata a lissafinta ba kwata kwata,don abinda yake gabanta shi ya dameta,saidai duk wata tijara da abubuwan da zatayi tana jinta daga farfajiyar gidan,ko idan guri ya hadasu,ko daga kai ta kalleta batayi bare akai ga jallin tanka mata,tunda bata taba tararta gaba da gaba ta kama sunanta ba tun sanda abbas din yaja kunnen hafsat,ita a yanzun kawai burinta abbas yace ta shirya su koma kaduna,gaba daya ta tsani garin wani muguwar tsana,duk ranar da ba girkinta bane da qyar take iya bacci saboda wani irin tsoro da yake shigarta,da qyar take hana kanta fita a wasu dararen,saidai ta zauna bakin qofar falo tayita kuka tana jin fita kawai takeson yi.
A WANI DARE karfe sha biyu da rabi na dare,har ya shiga sassansa ya kwanta ya tuna kamar yau din da daddare batasha magungunanta na anti natal ba,ya sauko daga gadon hafsat na gefe tana kwasar baccinta ya fito.
Kamar mutum ya dinga hangowa daga nesa,sai ya sauya yanayin tafiyarsa cikin hikima da dabararsu ta jami'an tsaro,bai wani jima ba ya gane widad dince ke nufar qofa,cikin wani irin zafin nama ya cimmata cikin takun da basu gaza biyar ba,saiji tayi caraf an riqota,ta waiwayo suka hada ido,cikin matuqar kaduwa yace mata
"Ina zaki da daren nan?" Kamar jira takeyi ta fashe da kuka
"Fita nakeson yi,banason gidan nan uncle" mamakinsa ya qaru,to duka me yake kawo haka?,wannan shine karo na biyu daya taba ganinta zata fita din.
A tausashe ya kama hannunta yana son maidata ciki,saita kuma saka kuka
"Don Allah uncle" shuru yayi ya zuba mata ido,yadan lumshe idanunsa hadi da budesu
"Muje ciki magana zamuyi" dole ta sakar masa hannun ya riqeta zuwa ciki.
Bakin gado dukansu suka zauna yana dubanta
"Me yake faruwa?"
"Banason gidan nan" ta amsa masa kanta tsaye tana qwalla
"Me yasa?"
"Tsoro nakeji" shuru ya danyi,ya ciro wayarsa yana son kiran dr,saidai yaga dare yayi,amma duk da haka yanajin ya zama dole ya kirata din.
Bugu daya ta daga ya nema afuwan tashinta,tace batama jima da shigowa daga aiki ba sannan yayi mata tambayar
"Kwai matan da ciki yake sakasu jin zaquwa gajiya da tsanar waje" saita fara masa bayani,yana fahimtarta yana kuma nazartar widad dake zaune a gefansa ta cure waje daya,ya karanci bayananta,to amma a abinda yake gani a tattare da widad din kamar nata yanayin ya dan sha banbam da wadda dr take qoqarin masa bayani
"Amma ba komai,with time zata daina ne" daga baya sukayi sallama yayi mata godiya,sai ya miqe yana kallon widad
"Bari na kawo miki mimi,hakan yayi?" Kai ta gyada masa a hankali sannan ya juya a nutse ya fice,ta bishi da kallo tana sauke ajiyar zuciya,rabon da yarinyar ta kwana a wajenta harta manta,gaba daya uwar ta hanata kwana a wajenta.
Yana buda qofar hafsat din na farkawa,ta bishi da kallo ganin ya shigo ne daga waje,ina yaje?,badai satar kwana aka fara yi mata ba?,saita miqe ta zauna tana kallonsa sanda ya duqa zai dauki mimi daga gadonsu dake gefe,don yau din a nan bacci ya daukesu,sai yace ta barsu kawai
"Bacci take fa"
"Na sani,zata tayata antynta kwana" ya amsa mata ba tare daya kalleta ba,wani abu ya darsu a ranta
"Me ya samu antyn nata?,naga yanxun ita daya take kwana bata ko nemanta ko?"
"Basai wani abu ya sameta zasu kwana wajenta ba ai,tunda yaranta ne itama" ya amsata yana rufe yarinyar da dan qaramin lallausan bargonsu,wanda zamansa a dakin ne kawai yasa bargon ya tsira da mutuncinsa ya kuma dade da kyansa.
Bai sake ce mata komai ya juya ya fice,sai ta bishi da kallo qaramar dariya tana qwace mata,ashe har yanzu da sauran abun nan bai gama sanewa ba,tanason wannan aikin tabbas!, jaddada shi takeson ayi kafin a wuce zuwa matakin gaba,bata qaunar hada inuwa daya da yarinyar kwata kwata.
Sai da kwanciyar tace tayi mata sannan ya tashi yana kallonta
"Ki shirya kayanki jibi zamu koma" wannan shine albishir din da yafi faranta mata rai,duk da ason ranta bataqi ma yace gobe zasu tafi ba,amma babu komai,goben ai a wajenta zai kwana,bata da damuwa.
*H U G U M A*
*Arewabooks: Huguma*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)