ZUMUNTAR KENAN 1 Da ka doso garin Giwa gidan za ka fara hanga daga gabas masu kudu na garin, tangamemen gida da aka yiwa jan rufi na zamani mai zagaye da girgijejen gate na bakin karfe da aka fi kira da Mahdi-ka-ture. Dauke yake da (estate) guda wanda ya hadiye gidaje na zamani (flat) guda goma sha biyar. Idan ka daga kanka sama, rubutu ne da aka yi da ruwan gwal mai sheki an rubuta ABUBAKAR BAMALLI GIWA ESTATE. Gidaje ne reras (dispersed) masu sanyin gani a ido da fenti ruwan gwaiduwar kwai. Gida daya ne ya bambanta da wadannan gidaje guda goma sha hudu wato gida na farko. Gida na farko ya fi duka gidajen girma, kuma shi kadai ne mai hawan bene. Mamallakiyar wannan babban gida tsohuwa ce ‘yar kimanin shekaru saba’in da biyar mai amsa sunan HAJIYA HADIZA GIWA, wadda ‘ya’ya da jikokinta ke kira da HAJJAH. Za ka yi mamaki idan ka ji cewa, duk girman gidan nan ita kadai ta yi rayuwa a cikinsa a matsayin matar gida, haka duka ‘ya’yayen nan goma sha biyar ita ta haife abinta daya bayan daya, babu dan miji babu dan kishiya a ciki. Wannan ya faru ne a cewar al’ummar garin Giwa a sabili da kaunar da marigayin mijinta Abubakar Bamalli Giwa ke mata, da kuma kyawawan halayenta da kyakkyawar mu’amala da kowa. Don haka ne bayan rasuwar A.B Giwa ‘ya’yansa ba suyi maraici mai yawa ba. Hajja ta zamo bango abar jinginarsu, wannan kuma baya nufin cewa sakar musu take yi, a’a, akwai tarbiyyar sannan akwai (discipline) ga duk wani da ko jikan Hajjah. Babu wanda za ta sakawa kara ya tsallake, babu wanda za ta cewa eh, ya ce mata a’ah. Babu wanda zai zartar da wani hukunci a kan gaban kansa ko iyalinsa ba tare da izininta ba. Mace ce mai kyakkyawan tunani tare da kaifin basira, ta yadda duk wani motsi da ‘ya’yanta ko jikokinta suka yi ta san me suke nufi. Mutum ce kaifi daya ba ta zance ta canza. Haka duk kaunar da take gwadawa ‘yan jikokinta ba za ta taba yarda karami ya kawowa babba raini ba. Jikokinta suna kaunarta sosai fiye da iyayen da suka haife su. Yawanci da daya da daya suka zame kayansu suka dawo nan (Babban gida kamar yadda suke cewa) wurin Hajja. Don a cewarsu, sun fi jin dadi gidan Hajja, abinci kala-kala kala-kala sai wanda suka zaba, tana kuma basu labaran hikaya da tatsuniyoyi na dabarun zaman duniya, tana rungume su komai girmansu ta rarrashe su ta ji abin da ya dame su idan iyayensu sun bata musu rai. Amma hakan ba ya nufin idan ka yi laifi ta sanya Baban Giwa ya hukunta ka, don dai ita dai ba ta iya dukan jikokinta in ba da mahuci ko rankwashi ba. Haka nan bayan ran A.B Hajiya Hadiza ta tsaya tsayin daka wajen tarbiyyar zuriyarsa, tare da kiyaye auratayya tsakanin jininshi. Har yau, har gobe Haj. Hadiza na bisa kudurin mijinta A.B Giwa na gama auratayya tsakanin jininshi, suna so ko basa so, in yaso daga baya su suke sanin yadda suke yi su shirya su so juna a bisa dole har su zo suna gode mata. Hakan ne ya haifar da yaduwa da fadada hadi da watsuwar zuri’ar A.B Giwa cikin garin Giwa da wajenta, inda kuma duk suka shiga dole a gane su, saboda kamanninsu da tsagin Mallancinsu dake gefe da gefen fuskar kowannensu, wanda wanzamin gidansu ke yiwa kowane yaro da kowacce yarinya ranar radin sunansa. Duk da cewa sun kebe kansu cikin Estate dinsu, sana’ar neman abinci ko aikin gwamnati na fiddasu cikin garin Kaduna ko Zaria A cikin gidan A.B Giwa, bayan jikokinta akwai dangin mijinta mai rasuwa, ‘ya’yan ‘yan’uwanta Kaltume da Kubra, dukkansu zawara ne. Kuma da yake sun manyanta sai suka zamo masu jibantar ayyukan gyaran gidan da harkar dahuwar abinci, duk da akwai wadatar masu aiki a gidan. Bangaren ‘ya’ya maza (Boys quaters) shi Hajja ta ware daga farkon gidan wadanda ga gidajen iyayensu amma sun gudo sun tare mata har girmansu. Sauran jikokinta ‘yammata da suka tasa duk ta aurar dasu a nan cikin Giwa ko Zaria da jininsu, mafi yawa na cikin Zaria, ‘ya’yan Hajja goma sha hudu ne, maza goma mata hudu. Abubakar Bamalli Giwa hamshakin mai arziki ne na da can-can shekaru aru-aru da suka wuce. Asalinshi Bamalle ne na garin Giwa, iyaye da kakanni, sana’arshi noma ne na kayan abinci (crops production) su masara, gero, achcha, dawa, alkama, shinkafa, dankali, doya da kayan miya, su yake nomawa duk shekara a loda a Daf-Daf zuwa kasuwannin garuruwa masu bukata. Ya mallaki tafka-tafkan gonaki sama da goma a cikin garin Giwa, wadanda shima gadarsu ya yi. Gidajen haya bila adadin a cikin Giwa da Kaduna, har ma da Zaria. A duk shekara ya kan nome amfanin gona mai yawan gaske, a nan ake loda su a buhunhuna zuwa kasuwannin garuruwa daban-daban. Zai yi tsayi in fayyace ko in lissafo sunayen zuri’ar Abubakar Giwa daya bayan daya, amma babban su shine Alh. Mukhtar Abubakar Bamalli wanda ke jagorantar reshen BAMALLI FOOD CROPS AND CASH CROPS PRODUCTION na Kaduna, wato wakilin kasuwancin kayan gonarsu na reshen jihar Kaduna baki daya, don haka zaman shi da iyalinshi ya fi yawa cikin kaduna, duk da gidansa na nan cikin A.B Bamalli Estate, in sun zo sallah ko biki budewa kawai suke yi su share su shiga. Sai Ahmadu A.B Proffesor ne a jami’ar Ahmadu Bello a tsangayar harkokin noma da kiwo, gidansa na nan cikin jerin gidajen malamai na A.B.U Zaria, kamar Baban Kaduna (Alh. Mukhtar) shima gidansa ne na biyu a A.B Bamalli Estate. Yadda Alh. Mukhtar ke zuwa da iyalinshi suyi kwanaki ko sha’ani, haka yake zuwa da nashi. Alh. Na’ibi Abubakar Bamalli ke bi mashi, gidanshi na nan cikin Estate shi ke kula da gonakinsu. Sai Ibrahim A.B, mai kula da gidajen hayarsu na cikin Kaduna. Barau A.B shine ke kula da Distribution (rarraba) amfanin gonakinsu zuwa garuruwa, shima cikin Estate yake shi da iyalinsa. Sani A.B, Sadi A.B da Salisu A.B, kowanne da bangaren da yake jagoranta cikin hanyar neman abincinsu. Sai Aunty Hauwa wadda ke auren dan aminin marigayi A.B wai shi Alh. Sabi’u Kwangila da ‘ya’yanta biyar, suna nan cikin Kaduna a unguwar Malali. Yaya Ladidi ke bi mata, ita kuma Zaria take aure unguwar Tudun Wada. Sai Yaya Hafsatu dake aure nan cikin Giwa. Aunty Rabi (autar Hajjah) ita ce kadai mai karancin shekaru a cikinsu. ‘Yar kimanin shekaru ashirin da bakwai, shekarar baya ne aka yi auren ta da Yaya Muftahu dan kanin A.B wanda aiki ya hulla shi Kano, yana aiki da gidan wayar Zain. Kwari irin na Hajiya Hadiza wannan ba zai rasa nasaba da jin dadin da take samu wurin ‘ya’yanta ba, domin a kulli yaumin kamar ana kara mata kwari da kuruciya ne, ba za ka yarda da tarin shekarun da take dasu ba a fuska da yanayin jiki. Ita kanta ba dukiya kadan ta mallaka wurin marigayin mijinta ba, iyayenta da kakanninta ‘yan asalin Zaria ne tushen unguwar Tukur-Tukur. Marigayin mijinta Alh. A.B Giwa shine dan garin Giwa ba ita ba, ita aure ya kawo ta. Haka bayan ranshi ba ta tsallake ta bar wannan muhallin da suke ciki ba ita da ‘ya’yanta. Tana kokarin hada kansu ba tare da sun yiwa mahaifinsu nisa ba, don kara killace zumuncin su. Basu aure mace ko namiji sai cikin zuri’ar su (jinin su). Wannan ne ya sanya suke kama da juna, inda duk ka gansu in ka san daya daga cikinsu za ka gane su. Farare tas-tas masu dogon hanci da yalwar idanu da garin jiki (girma da tsayi). Da an gansu an san su, in ba ta tsagin ba ta kamannin, in ba ta kamannin ba ta jin kai da yanga, daga matansu har mazansu. Mutane da yawa kan ce zuri’ar A.B sun fiya girman kai da dagawa, amma a zahiri nutsuwa ce kawai da Allah ya haliccesu da ita da tsabar sanin ciwon kansu, domin dukkaninsu ilimi na Muhammadiyya da na zamani ya wadaci kwanyar su. Har kullum arzikin A.B karuwa yake, domin basa wasa da hakkin Allah cikin dukiyoyinsu (Zakkah). Har zuwa inda yau ke motsi tun bayan ran marigayi A.B, ba a ko taba kwatanta auren bare cikin zuriyar sa ba, don a ganinsu auren bare zai bata musu family, zai jawo rarrabuwar kamanni, ya rarraba musu kan ‘ya’ya, kuma ya haifar da sauyin kamanni cikinsu. Hajjah duk da kasancewar mace ce mai fada a yawancin lokuta, amma fa in ka iyawa halinta ka fahimci likes and dislikes dinta, to ta fi ruwan sha saukin sha. To haka gaba daya ‘ya’yanta suke lallaba ta, suke faranta mata, ba ta da ciwuwwukan da tsofaffi ke fama da shi ko daya irin su sukari, ciwon kafa, hawan jini ko rikicewar girma. Musamman babban danta Alh. Mukhtar ya fi kowa iya zama da ita da tattalinta da yi mata biyayya a bisa dukkan umarninta. A cikin Estate din akwai babban masallacin da suke haduwa suyi dukkan salloli biyar a kan lokaci, bangaren maza daban, an sanya labule tsakaninsa da bangaren mata. Yaransu da manyansu da wuya ka ga suna sallah a cikin gida in ba da wata babbar lalura ba. An hore su da sallah da kula da lokacin yin ta. Da zarar Baba Barau (Limamin A.B Mosque) ya yi kiran sallah kowa zai aje abin da yake yi ya je ya daura alwala ya tafi masallaci ya bi jam’i, maza da mata, yara da manya, ‘yammata da samari. A gefen masallacin karamin clinic dinsu ne (dakin shan magani ne wanda suke biyan likita guda duk wata da Nurse suke kula da lafiyarsu da ta yaransu akai-akai). Haka main market Giwa bangaren kayan abinci duka rabi shagunan Bamalli ne, suna hada-hadar tafiyar da harkokin kasuwancinsu rai kwance, hankali kwance. Dukkan mazan fannin aikin noma suke karanta (Agricultural Engineering ko Agriculture Science) a jami’ar Ahmadu Bello. Matan ne kowacce da bangaren da ta karanta, Aunty Hawwa ta karanci Quantity Surveying ne, Ladidi Education, malamar makaranta ce. Yaya Hafsatu Home Economician ce, Aunty Rabi kuma aikin jarida ta karanta. Da yake Musbahu mijinta a Kano yake aiki ya samar mata aiki a Kano da gidan rediyon Freedom, ko haihuwar fari ba ta yi ba. Allah ya albarkaci wannan family da nutsuwa da biyayya ga mahaifiyar su Hajjah, babu mai zartar da hukunci a gidansa ko a kan iyalinsa face da sanin ta, da amincewarta. Haka igiyoyin auren da take kukkullawa a tsakaninsu basa ganin bekenta, domin duk wanda ya bi ko ba da son ransa ba, daga baya sai ya ga amfaninsa. Don haka duk cikin samarin da ‘yammatan da suka tasa babu mai tunanin yin budurwa ko nuna ga wanda yake so, sai wanda Hajjah ta ga ya yi mata dai-dai ta hada su. A halin yanzu dai yara uku ne mata a gabanta da basu haura shekaru bakwai zuwa takwas ba, duka jikoki ne, Ummi, Zanirah da Fa’iza. Samarin maza ‘yan sakandire da na jami’a sune Allah ya yi yawa dasu a gidan. Duk sun baro gidajen iyayensu sun tare a baskwata din Hajjah. Ba ta nuna damuwa sam, kamar yadda ba ta takura da zaman su, ita dadi ma take ji duk inda ta juya ta gansu, tana bari-bari ko suna hirarsu ta jika da kaka cike da kauna da fahimtar juna. Dadi take ji ta ga jikokin nan nata sun zagayeta, wannan ya tsokani wannan, wancan ya tsokani wancan, ta yi ta shari’a, ta yi ta bari-bari ko ta kai musu duka da mafici. Sai dai Hajjah ta raini jikokinta da kyakkyawar tarbiyya ta yadda babu yadda za ayi ka ga karami ya kawowa babba raini, ko ka ga da wuya macen da ta tasa ta zauna kusa da mazan ko kokaye-kokaye, haka nan duk motsin da dayansu zai yi, to a kan idonta ne. Yanzu kam hankalinta duka yana kan ‘yan matasan jikokin nan nata mata guda uku da suka saura a gabanta ta dage wurin tarbiyyar damu. Wato ni, Ummi (Khadija) da Zanirah. FA’IZ, Da ne ga babban dan Hajja Alh. Mukhtar, kuma rayuwarshi ta dawo gidan Hajja ne tun daga shekarun yaye ba kamar mu ba. Kaunar Hajjah da Fa’iz daban ce da duk sauran jikokinta, saboda shi kadai ne me sunan marigayi A.B wato (Abubakar), kuma a cewar ta kullum Yaya Fa’iz shine photocopy na A.B Giwa, daga kamanni har halayya. Fa’iz ya shiga ran Hajja fiye da duk ‘ya’ya da jikokinta. A cewar Hajjah, Fa’iz yaro ne mai shiga rai, kuma mai nuna mata kulawa fiye da kowa a zuri’ar. Komi Fa’iz ya samu na Hajjah ne, baya kyashin kadar da komai nasa wajen faranta mata, musamman kasancewarta ma’abociyar cin farin goro da mu’amala da man zaitun, habbatus-sauda da turaren miski a jiki da tufafinta. Tun yana karami ya san yadda yake samar dasu gare ta baya bari ta neme su bayan sun kare sai dai wani ya tadda wani, daga Abubakar-Fa’iz da take kira (Hafizi), kasancewar shi mahaddacin Alkur’ani a shekaru na goma sha biyar. Zai kuma iya karya harshe ya karanta shi tiryan-tiryan da dukkan kira’ar Hafizan da muke dasu a Saudiyyah, irin su Abdur-Rahaman Sudaith, Jabir da Abdur-Rahaman Bn Marwan Al-Juhainy da Khusairi. Fa’iz ne kadai ya yi karatun sakandire a birnin Madinah Al-Munawwarah, daga aljihun Gwamnati. Yana da shekara goma ya yi musabakar izfi talatin daga jihar Kaduna ya samu sponsorship zuwa wata sakandire a Madinah. Ya dawo gida yana da shekaru goma sha bakwai, ya kuma zabi gidan Hajjah a matsayin gidan zamansa maimakon gidan mahaifinsa Alh. Mukhtar a cikin Kaduna. Daki guda Hajjah ta ware ma mijinta Fa’iz a Boys Quaters da duk abin da zai bukata, sannan in ta ji shi shiru kullum kafarta na hanyar dakinsa don ganin “ko lafiya Hafizi baka shigo ba?” Sai ya ce, “Akwai abin da nake yi ne Hajja, zan shigo anjima kadan”. Haka suke a kullum. Zanirah kanwa ce ga Fa’iz, wato ita ma diyar Baba Mukhtari ce, zamanta gidan Hajjah ya samo asali ne tun wata tafiya da mahaifiyarta Mama ta yi aikin Hajji tana shekara hudu ta kawowa Hajja ita. Bayan dawowar Mama kiri-kiri Zanirah ta ki gidansu. Ita da Jabi Road sai hutu, shi din ma ba kowanne ba, sai wanda ta ga dama. Babban Yayansu shine Bashir wanda ke karatu a matakin farko na jami’ar Ahmadu Bello, sai Fa’iz wanda a bana ne ya kammala sakandire, Abdulhakim ke bin Fa’iz, sannan Shu’aib, Yahaya, sai Zanirah da autansu Abbas da muke kira (Junior). Khadija (Ummi) ita kadai ta fara cin sunan Hajja a cikin mu. Diya ce ga Aunty Hauwa dake Kaduna. Ummi tun tana shekara biyar Aunty Hauwa ke kawo ta hutu wajen Hajja su hadu ita da Zanirah suyi ta wasa, zuwan ta ya zama akai-akai duk hutun makarantar boko. Da dai Ummie ta gane irin dabdalar da yara sa’o’inta ke yi a gidan Hajja sai ta yiwa uwarta tawaye ta shiga ihu da tirjiya duk lokacin da aka zo tafiya da ita gidansu. In kuma aka takura mata tafiyar, to a ranar duk gidansu ba mai barci da shesshekar kakanta har da shidewa. Dole iyayenta suka hakura da kulafucinta suka bar ma Hajja. Ni FA’IZAH AHMAD ABUBAKAR GIWA, ina daya daga cikin jikokin A.B Family, kamar yadda na fada a baya, mahaifina shine da na biyu a ‘ya’yan Hajjah wato Professor Ahmadu Bamalli na jami’ar Ahmadu Bello. Auren zumuncin Bamalli shi ke tsakaninshi da Mamana Maimunatu da muke kira Momin ABU, shi kuma Baban ABU. Nice ta fari, sai Abdallah, Walida ke bin Abdallah. Yayin da Kausar ta kasance autarmu. Momi ma’aikaciyar jinya ce ita a asibitin koyarwa na Zaria (ABUTH). Tsananin rashin kulawarta gareni wai don nice diyar fari, kunya da kawaici mai sawa a hantari yaro ya sanya Babanmu ya dauke ni daga gabanta tun ina shekaru biyar ya bai ma Hajjah. Nima dama na fi son gidan Hajja, ko don su Zanirah. Sai muka dunkule mu ukun nan muka bude rayuwar da ta caza kwakwalen iyayenmu a gaba da kakarmu Hajjah. Ta yadda babu ranar Allah da za ta fito ta fadi bamu bar abin fadi ba, domin dukkaninmun nan kowacce da halinta, muka kuma hadu da maganinmu Ya Fa’iz ta yadda babu ranar Allah da ba zamu barta ba tare da Hajjah ta yi shari’a ko rabon fada a cikin ta ba. Ba zan manta ba, a ranar da zan koma Giwa ban iya na yi barci ba saboda doki da murna, da asubar fari kuwa na shiga bubbugawa Babanmu kofa ya fito mu tafi Giwa kafin su Zanirah su tafi makaranta. Don haushi Momi fitowa ta yi ta mammake ni ta kuma ce ba za a tafin ba sai sha biyun rana. Haka na wuni ina duba agogo ina zumburar baki, domin dai har sai da Baban ABU ya shiga cikin makaranta ya fito sannan muka taho Giwa (makyankyasarmu). Muna zuwa kuwa na gayawa Hajja abin da Momi ta yi min, ta ce (ya yin da ta rungume ni) “Ki barta daga yau ganinki ma sai ta cike form, tunda ba ta sonki ni ina sonki. Da kafarta za ta zo neman ki, ki zuba ido”. Ni kam na san abin da ba zai taba yiwuwa bane Momin ABU ta wanko kafa ta zo Giwa domin ni, sai in tata ce ta kawo ta. Na ce, “Hajja ina su Zanirah ne? Tunda na zo ban ji duriyarsu ba”. Ta ce, “Suna Islamiyya yanzu za ki gansu, kema in Allah ya kaimu gobe Babanku na Giwa (Baba Barau) zai amso miki form daga boko har Islamiyyar ku dinga tafiyar ku tare”. Na shiga tsalle ina murna. Daga nan na shiga kitchen din Hajja na soma bude kuloli da kwanuka ina tsame namomin dake kan abincin ina cinyewa, Hajjah na falo ba ta sani ba. Ni Allah ya halicce ni da shegen son nama kamar mage, Momin ABU kan ce kamar mayya. Don haka ko da nake Zaria Hajja kan sa ayi mani dambun nama mai yawa ta aike mani cikin samira duk sadda Babanmu ya zo gaishe ta. Dai-dai sanda na bude wani madaidaicin (food flask) ruwan kasa Hajja ta shigo. Na kai hannu zan dauke cinyar kazar dake kai Hajjah ta rike hannuna tana murmushi, ta ce, “A’a, an cinye na kowa to ban da na Hafizina, haba Fa’iza? Don ya ga naman nan tun kafin a dafa shi ba zai zama haramiyarsa ba, dole ne ya ci cinyar kazar nan”. Na dube ta rike da murfin flask a hannu daya, daya rike da cinyar kaza cikin mamaki na ce, “Hajja waye kuma Hafizi da ya fi kowa da za a sawa kowa abinci a kwanon samira shi a zuba mishi food flask?” Hajja ta ce, “Fa’izu mana, dole ne a girmama Hafizin Qur’ani. Balle Fa’iz da duk ya fiku sona, ku baku yi min sai dai in muku, Fa’iz fa? Naman nan ko idan kika sake kika ci in dai Fa’iz ne sai kin amayo shi”. Na soma yagar cinya ina ci abuna, na ce, “Hajjah ai dama ke kike daure masa yake cin zalin mutane, don bakya ganin laifinsa, kina fifita shi a kan kowa”. Hajja ta ce, “Ba na gani din, na fifita din”. Na cinye nama na bi lafiyar gado, ba jimawa barci ya kwashe ni, Hajja ta shiga harkokinta. Hayaniyar su Ummi da Zanirah ce ta tada ni.... “Ehu! Fa’iza? Don Allah Hajja da gaske? Da gaske kike Hajjah ta dawo nan da zama?” Ban ji amsar da Hajja ta basu ba, Zanirah ta fyallo a guje ta daka min duka a baya, na tashi wurgigi a firgice, sai kuma muka dafe juna muna kyalkyatar dariya. Bayan sallar isha kowacce ta bude kwanonta za ta ci abinci, Ummi ta ce, “Shegiya Fa’izah dama tunda na ga kwanukan nan lami na san kin zo garin”. Zanirah ta ce, “To meye don ta ci namanmu bayan kin samu ma ta zo? Da kafin ta zo ba cewa kike dama Fa’iza ta zo hutun nan muje muyi shi gidan Baban Kaduna ba? Wai inda ita tafiyar tafi daxi? Amma yanzu daga zuwan ta kin fara yi mata korafin cin nama?” Ummi ta harare ta, ta ce, “Ka ji ta kamar gaske sai wani kakkare ta kike, dama ban san halin bane, gobe ne zuwa jibi za a fara rabon dambe tsakaninku”. Dai-dai lokacin Fa’iz ya shigo yana sanye da ruwan madarar jallabiya da carbi a hannunsa, farin yaro tas kamar haifaffen Da’ifah, matashi mai garin jiki irin na zuri’ar A.B Giwa. Hancin nan mikakke har baka, kanshi akwai tarin suma. Gefe da gefen fuskarshi tsagin mallancinshi ya fito radau, dogo mai tsayi da kafadu tun a wancan kananan shekarun. Da gani daga masallaci yake rike da tasbaha a hannunshi na dama. Shigowar shi ta katse Ummi da Zanira daga musun su, ya wuce ko kallon mu bai yi ba kai tsaye zuwa kitchen ya dauki filas dinshi ya Jim kadan sai ga shi ya dawo a fusace, ya dangwara min ma’adanar abincin a cinya yana zazzare fararen idanusan wadanda tun a wancan lokacin suke da wata irin baiwa ta kwantaccen ruwa kamar hawayen da bai kai ga zubowa ba a cikinsu, da babbar murya ya ce, “Ke kwalamammiya amayo naman da kika ci ko billahillazee in yi kuli-kulin kubra dake yanzu a gidan nan, in lallasa ki dukan da uwarki ba ta taba yi miki ba”. Na ma rasa me zan ce don mamaki da takaicin ambaton uwata da ya yi, haka Ummi da Zanira sunyi wuri-wuri. Ya ci gaba da magana cikin bala’i. “Kazamar banza mai kashi a wando, wa ya ce ki sa min kazamin hannunki cikin abincina? Tunda ma kika saka wannan kazamin hannun naki wanda ya saba yin dama-dama da kashi cikin fo ba zan ci abincin ba....” Ya daga kwanon shinkafa da taliya da miya ya zazzage min a tsakar kaina, ya ja dogon tsaki ya wuce yana cewa, “Dama dai kwalamammiyar nan ba ta zo gidan nan bane za a tadda kwayar nama cikin abinci. Ni kam shekarar bakin ciki ta zo min in dai da wannan mai kashi a wandon zan zauna cikin gidan nan. Mtsw!” Ya yi ficewarsa yana ci gaba da bambamin fada da muryarshi mai karyayyen harshen larabawan Hijaz, Hausar shi ba ta fiye fita sosai ba. Na fashe da kuka nan take, don ni babu abin da na tsana a rayuwata irin a ce min mai kashin wando (da gaske mai kashin wandon ce a baya, har na kai shekara biyar ban san idan na ji poo-poo in dauko fo in hau ba, sai dai in saki abuna a wando. Hajja da Momi sunyi fadan har sun gaji, kuma a wancan lokacin babu pampers sai napkin, haka su Inna Kubra dake gidan za suyi ta aikin kashi da yi min wanka a famfon wajen wanke-wanke). Tun a wancan lokacin ne bama ga maciji da Fa’iz, kasancewarshi mai masifaffiyar tsaftar gaske da kyankyami. Ya dauki tsana da hantarar duniya ya dora a kaina, duk inda ya ganni sai tsawa da raraka yana toshe hanci. Ban samu sa’ida a zaman gidan Hajja ba sai da Fa’iz ya wuce babbar sakandire a Saudiyaya. Su kam su Zanira dariya ce ta kama su suna makewa bayan wucewar Fa’iz, don sun san halina in ina cikin fushi kayi min dariya a kanka zan huce. Da na kai karar abin da Fa’iz ya yi min wurin Hajja a uwar dakinta tana lazimi cewa ta yi Allah ya kara, ai na gaya miki amma da yake kunnen kashi ne dake sai da kika ci. In gaya miki wannan dabi’ar banza ce, ki daina ta. Kada ki kuma cin rabon wani bayan rabonki haramun ne. Ni bai burgeni ba ma da bai shake ki kin amayo shi ba. Washegari Baban Giwa ya amso min transfer daga makarantarmu (ABU Staff School Primary School) zuwa ta su Ummi wato GIWA SOUTH PRIMARY SCHOOL. A rana ta farko da na fara zuwa Giwa South Primary na dawo da damuwa mai yawa, basu yin Arabiyya ko kadan, babu Arabic a darassanmu sabanin Staff School da muke zuwa ni da Abdallah a Zaria. Shigowarmu gida ke da wuya na watsar da littafan a falon Hajja na zauna shirim ina ta zumbura baki. Hajja dake rike da littafin Bulugul-Maram da Medicated glass a idanunta tana karantawa ta dago ta dube ni ta ce, “Lafiya?” Na yi tsaki na ce, “Bari ke dai Hajja....” Kafin in karasa sai ga Yaya Aliyu, Yaya Bashir da Yaya Fa’iz sun yaye labulen falon sun shigo, kowannensu dauke da sallama a bakinsa. Sun sha anko na farar shaddah (Hilton) sai salki take. Hajjah ce ta amsa musu, kana ta ce, “Har an daura auren?” Suka zazzauna cikin duma-duman kujerun falon, Basheer ya ce, “Eh, alhamdulillah an daura Hajja. Sadaki naira dubu dari Baban ABU ya biyawa Usman (Dan Baba Barau da ‘yar Baba Ibrahim Maryam aka daurawa aure). Sai fatan Allah ya basu zuri’a dayyaba da zaman lafiya da yalwar arziki mai albarka”. Duka suka ce, “Ameen”. Yaya Aliyu da yake duk mun fi shiri da shi ya dube ni a nutse ya ce, “Hajja lafiya Fa’iza ke fushi?” Hajja ta ce, “Gaka gata nan tambaye ta mana, nima haka ta shigo min”. Ya dawo da idonshi kaina alamar sauraro ya ce, “Wa ya tabo min Fa’iza ta?” Na tura baki sosai na ce, “Bayan makarantar su Ummi ba a yin Larabci sai Turanci”. Duka suka sa min dariya ban da Fa’iz da ya ce, “Ji ta don Allah baka kirin da ita, duk gidan nan ita ce mummuna, ko meye gamin ta da Larabawa oho?” Bashir dariya yake shi da su Ummi, Yaya Aliyu ya ce, “Rabu dasu Fa’iza, ai black is beauty. Na rantse dukkan su babu wanda zai samu mata mai kyan ki. Na yi alkawarin canza muku Islamiyya wadda ake koyar da Larabci sosai kin ji Fa’iza na?” Kuka nasa sosai, ba abin da Fa’iz ya fadi bane ya sani kuka, a’a, na tsani ayi min gwasale cikin mutane. Shi kuma Ya Fa’iz na lura baya shakkar a gaban kowa ya ci mutuncina. Halinshi sam ba irin na Yayan shi Bashir da Yaya Aliyu Haydar bane, in ya raina ka kawai ya raina ka, in ya tsane ka sai ka gwammace ko hanya ba ta gama ku ba balle jini. Zama na a gidan Hajjah tare da Fa’iz daga farkon sa har zuwa inda yau ke motsi ba mai dadi bane, kai ka ce babu digon jinin juna a jikinmu. Fa’iz ya tsaneni on the ground of kazanta, ni kuma na tsane shi on the ground of mugunta. Shi Yaya ne ba mai dadi ba ga kannensa, akasin Yaya Aliyu mai son mu, mai janmu a jikinsa da nuna mana kauna ta ‘yan’uwantaka. A sannu nake fahimtar kazantar da Fa’iz yake yawan ambatawa a gareni da na soma tasawa. Na farko ban damu da sanya wankakkiyar suttura ba balle gogaggiya, ban san wani abu wai shi kintsi ko gyaran jiki ba. Uwata ba ta ja ni a jiki ta koya min wadannan abubuwan ba, ban san in gari ya waye in tatsa maclean jikin burushi in goge baki ba, sai dai in afa ruwan shayi da burodina in ci. Ga Hajja tsohuwa ce ba ta mai da hankali kan irin wadannan abubuwan ba, wanka su Ummi kullum sai sun yi amma ni sai in kwana hudu fatar jikina ba ta ga ruwa ba. Balle sabulu da soso, gani kuma daman bani da hasken fata irin na Bamalli, kalar jikina irin na mahaifiyata ne. Idan na cire kaya ban san wanne ne mai datti ba wanne ne mai tsabta ba, haka zan hada duka in danna su a wardrove dina babu ninki balle kintsi sabanin Zanirah da Ummi su da suke ma goyon Kaka. Dalili kenan da in Fa’iz na wujijjigani da wulakanci da kaskanci bani da bakin kare kaina sai dai in yi ta kuka da tunanin na yi gudun gara na tadda zago, ko in komawa zagon ne (Momin ABU), amma in na daga ido na dubi Ummi da Zanirah na tuna irin kewarsu da zan yi idan na bar Giwa, sai in manta da al’amarin Fa’iz in shigar harkokina, in kuma yi kokarin kaucewa duk wata hanya da za ta sada ni da shi a gidan don in zauna lafiya. Lokacin da muka gama makarantar firamare muna da shekaru goma sha biyu, muka samu gurbi a FGGC Gusau aji daya. Da yammacin ranar Yaya Aliyu ya shigo falon Hajja muna kallon shirin Risalah (The message) daga tauraron dan Adam ba tare da mun juyo ba duka suka amsa sallamar shi amma ban da ni, domin a lokacin ina gefen Ummi ina kuka sosai ni ba zan je makarantar kwana ba, Hajja da su Zanirah sun yi rarrashin duniya na ki yin shiru. Hajja ta ce da Yaya Aliyu a sanda ya zauna, “Yanzu nake cewa Ummi ta kira ka ku je kanti su hado duk abin da za su bukata nima nan na yi musu duk nawa tana din na su yaji da soyayyar miya, dambun nama na Fa’iza da su garin rogo ko za su bukace shi, to mutuniyar taka gata nan ta ja ta kafe ba ta zuwa makarantar kwana, ba ta kuma fada ba sai yanzu da aka gama musu komai gobe tafiya”. Yaya Aliyu ya matso gefena ya zauna a hankali yana dubana ina ta share hawaye da majina da habar zanina, jikina na tashin tsamin tashen balaga da rashin wanka. Ya ce, “Princess Fa’iza Bamalli, gaya mani matsalarki ta kin son makarantar kwana a yau, bayan a da baki ce hakan ba....” Cikin kuka na ce, “Yaya Aliyu Ummi ta ce ana saka yara yin kitso duk sati, yanke farce duk sati, wanka kullum, kuma dole kullum sai ka yi brush safe da dare, ni gaskiya za a takura min, wallahi ba zan iya ba.....” Su Ummi suka bushe da dariya har shi Yaya Aliyun. Daga bayanmu muka ji an saki wani dogon tsaki, dukkanmu muka juya, Yaya Fa’iz ne. A hasale ya ce, “Yaya Aliyu don girman Allah ka fita hanyar yarinyar nan mahaukaciya ce. Raina yana matukar baci idan na ga kana shiga sha’aninta. Ni wallahi ba don kamanninta da Baban ABU ba sai in ce canza ma uwarta ita aka yi a asibiti can inda take aiki suka hada baki aka bamu”. Fuskar Yaya Aliyu ta rine da bacin rai, ya dubi Fa’iz a hankali amma ya kasa cewa komai. Hajja ce ta ce, “Hafizi! Wacce irin magana ce wannan? Kada in kara jin makamanciyarta”. Ya sadda kai ya ce, “Allah ya huci zuciyarku Hajja, amma yarinyar nan na bukatar makarantar kwanan da ba ta so, don kwata-kwata ba ta san ciwon kanta ba, uwarta ta jawo mana baragurbi cikin zuri’a. Kaico! Auren bare bai yi ba wallahi.....” Ya juya ya yi ficewar sa. A fusace Yaya Aliyu ya mara masa baya, ya suka karke ya suka kare oho! Ya dawo fuskarshi babu annuri, ya ce (ba tare da ya dubi kowaccen mu ba) “Ku tashi maza mu tafi sayayyar”. Yanayin yadda na bude motar cikin matsanancin fushi ya sanya Yaya Aliyu juyowa sannu a hankali ya dube ni na ‘yan dakikai, sannan ya sanya ma motar giya muka harba kan titi. Babban Super Market din wanda ke kan hanyar fita garin Giwa kusan duk garin babu kantin da ya yi girma da habakar ta. Babu abin da babu na bukatun yau da kullum. A nan Ali ya yi parkin duk suka fita, ban ko yi motsin dake nuna inada niyyar fitan ba, zuciyata da tunanina duk da karancin shekaruna sun sanya min ayar tambaya a yau a kan Yaya Fa’iz da kiyayyar da yake yi mun da kuma dangantakar kiyayyar da raini ga mahaifiyata wadda baya jin kunya ko haufin jan sunanta a gaban kowa ya aibata ko ya zage ta. Mintuna biyu Yaya Ali ya yi yana nazarina kamin ya rankwafo tagar da nake a tausashe ya ce, “Fa’izah ba a fitowa?” Sai na ji ya yi min wani kwarjini mai yawa yadda ya yi maganar. A hankali na bude murfin motar na fito. Ya yi dariya ya ce, “Yau dai da alama mulki kike ji Fa’iza, ko duk fushin Fa’iz ne har yanzun?” Ummi ta kulu da bata lokacin da nake yi musu da tarairayar da Yaya Aliyu ke min na yi banza da su, ta ce, “Don Allah Yaya Ali ka rabu da ita sai wani lallashinta kake tana basarwa sai ka ce mu muka kar zomon, ita wace ce?” Ya yi murmushi ya ce, “Ita Princess Fa’izah Bamalli ya ya ranki?” Zanirah ta ce, “Me kenan Pincess?” Ya ce, “Princess yana nufin Gimbiya”. Ta tabe baki ta ce, “Sunan da Ya Fa’iz ya ba ta ya fi dacewa da ita ba naka ba”. A kaikaice da baki ya ce, “Wanne suna ne Fa’iz ya ba ta?” Zanirah ta ce, “Impertinence Fa’izah watau Fa’izah mai tsiwa”. Ya dubi Zanirah sannan Ummi, ya ce, “Wadda ta sake kiran Fa’izah da wannan sunan ban yafe ba, kun ji ko?” Suka daga mishi kai muka shiga cikin kantin. Ko da muka shiga cikin kantin kujera na ja na zauna ina kallon su, dauki banza dauki wofi, wani zubin su juyo su kalle ni suyi kus-kus su ci gaba da dauke-dauken su. Shi ko Yaya Aliyu sayayyarsa daban ce da tasu, kwando uku suka cika da kayan zaki masu tsada, hatta biron da zamu yi rubutu basu bari ba. Muna shiga mota kafin Yaya Ali ya tada motar Zanirah ta ce, “Ummi baki daukarwa impertinence rice pudding ba”. Na yi kan Zanirah da duka, yakushi da cizo, dama kiris nake jira. Yaya Aliyu ya dakan tsawa ya ce, “Meye haka ne Fa’iza? Don kinga ina lallaminki shine kika koma hauka?” Idona cike da kuka na ce, “Amma ita ba ka yi mata fadan sake kirana da sunan Yaya Fa’iz ba don kaima ka tsane ni kamar shi, shi kenan....!” Sai a lokacin ne na samu hawaye suka zubo. A tausashe Yaya Aliyu yana ta da motar ya ce, “Lallai Fa’iza har yanzu shagwabar tana nan? Haka za a kwalejin ana musu?” Ummi ta ce, “Ta yi mana in siniyoyi basu lallasata ba?” Muguwar harara na rafka mata ta toshe bakinta da hannun damanta tana “Allah ya huci ran princess”. Mun kusa shigowa unguwarmu ya ce, “Fa’izah don Allah don Annabi ki dinga hakuri da ‘yan’uwanki kin ji ko? Ko harshe da hakori dole a saba wata rana, ki rage zafin zuciya, kina da zuciya mai zafi”. Na ce, “Amma shi Ya Fa’iz ba mai yi masa fada kan tsana da tsangwamar da yake yi min a duk lokacin da abu ya shafe ni? Laifina ma kake gani Yaya Aliyu?” Yana girgiza kai ya ce, “Ba maganar Yayanki Fa’iz nake ba, bana so in ga kina halin yara, you are no more a child now, dambe da kokawa na su Walida da su Badar ne”. Na zumbura baki ban ce komi ba. Ya ce, “Kin hakura Princess ko kina so na kasa barci saboda fushinki?” Sai na bude dukkan idanuwana na dube shi. “Yanzu Yaya Aliyu in ina fushi sai ka kasa barci?” Ya yi murmushi ya lumshe ido tare da daga kai sama. Cikin mamaki na ce, “To saboda mene?” Ya ce, “Saboda me? Saboda abin da kwakwalwarki ba za ta fahimta ba a yawan shekarun ki”. “Mene shi wannan abun?” “Wannan abun muhimmi ne mai girma da yaro baya jin shi sai ya girma”. “To ai Zanirah ta girma in ji Hajjah, tun ranar da jini ya ziraro ta kafarta Hajja ta ce ta girma, to ita ka gaya mata mana?” Ya yi dan dummm! Zanirah ta soma kumbura hanci da hurashi ta ce, “Yaya Aliyu wallahi karya take Ummi ce?” Ummi ta ce, “Wallahi ita ce”. A dai-dai lokacin da Yaya Aliyu ya shigar da hancin motar A.B Bamalli Estate, ya yi kyakkyawan horn yaran dake kusa a kofar flat din Baba Barau suka rugo suka fidda kayan a boot suka shigar mana dasu gida. Yaya Aliyu Boys Qtrs dinsu ya wuce bai kara kula mu ba. Su Abba na jidon kaya suna ihu wai za su ci cornflakes din ‘yan bording school. Na ce, “Wallahi duk wanda ya bude mana kaya sai na kabari ya fishi jin dadi”. Ina kwance gadon Hajja na ji shigowar su Ummi, suka shigo da kaya niki-niki, Ummi cike da tsegumi take ce da Hajjah, “Wai Hajja ki duba ki ga duk yawan kayan nan da muka shigo sai da Yaya Aliyu ya sake sayen kwatankwacinsu wa Fa’iza ita kadai ranta”. Zanirah ma ta ce, “Kuma Hajja baki gani ba, wai don dan fadan nan da Ya Fa’iz ya yi mata dazu kafin mu fita ya yi ta lallaminta tana masa wulakanci da kada ido, ita ba ta yarda ba babba”. Hajjah ta yi kamar ba ta ji su ba ta shiga duba kaya, ta ce, “Ya ban ga kwaki ba bayan kun ce bakwa son wanda na sayo fari kuke so?” Ummi ta ce, “Tab! Waye zai sha miki kwakin? Ki jimu da tsohuwa da neman ta da zaune tsaye”. Hajjah ta dauki mafici ta yi kanta ta runtuma da gudu. Hajjah ta ce, “Ja’ira, gobe dai kun barni da ‘yan jikokina mu huta bakinmu alaykum. Haba! Yara uku duk kun bi kun isheni kamar ina zaune da zaratan ‘yammata”. Ummi ta zo ta kwanta a gefena ina kwance rigingine na yi nisa cikin tunanin irin kulawar da Yaya Aliyu ke yi mani. Hakika shi dan’uwa ne mai matukar kirki da dabi’un kyakkyawar mu’amalar zumunci. A lokuta da dama ina kwatanta kirkin Aliyu da wani cikin yayyenmu, amma ban ga kwatankwacin shi ba. Halinsa daban, simplicity dinsa daban da dukkan mazan zuri’armu. To amma kulawarsa gareni ta zarta wadda yake yiwa kowa, babban misali su Zanirah da tare muke rayuwa yana fifitani a kansu. Sai a hankali nake jin Yaya Aliyu na kwanta min a zuciya saboda kyawawan halayensa da kulawar da yake yi mun. Tunani na ya gangara ga abin da ya fadi dazu na cewa, wai ba zai iya barci idan ina fushi da shi ba, saboda abin da yaro baya ganewa sai ya girma. Shin mene ne wannan abun? I’m quite curious.... Kamar Ummi ta san abin da nake tunani, ta yi murmushi sai cewa ta yi, “Princess har an soma tunanin Yaya Aliyu? Ayi hakuri dai muje kwalejin mu gama, in kuma auren za ayi sai a fada mana mu fara shiri”. Na mike a fusace na soma dukanta ina yakushinta ta sa ihu, nan da nan Hajja ta shigo za ni na zamewa kamar ta fadi. Ta ce, “Wai ke wacce irin masifaffiyar yarinya ce ne Fa’iza? Ke daya duk kin buwayi gidan nan, daga ki yi da wannan sai ki koma ki yi da wancan?” Na sa kuka na ce, “Hajjah cewa fa ta yi wai ina tunanin aure, ‘yar iska ta dauke ni ko me? Bayan ni tunanin su Walida nake yi”. Hajjah ta ce, “To yi hakuri wasa take miki, ke kuma Ummi kada na kara jin makamanciyar wannan maganar ta fito daga bakinki zan saba miki fiye da zaton ki”. Ta juya ta fita. Zanirah ta bimu da kallo kurum, sai dai na lura tun shigowar ta dakin akwai abin da ke damun ta. **** Ranar da zamu tafi FGGC Gusau ta kama litinin ashirin ga watan Nuwamba, don haka sanyi ya yi tsanani ainun. Tun asuba muke ta shiri, murna kamar kanmu aka fara zuwa makarantar kwana. Mun yi tsaf cikin uniform abin sha’awa. Na hade gashina cikin (hair-bound) kalar tsanwa cikin sayayyar Yaya Aliyu ne. Hajja dake azkar din safiya a gefe bisa shimfidar sallarta ta shafa addu’a ta juyo ta dube mu. “Yanzu duk wannan azarbabin da kuke wa kuke zaton cikin yayyunku zai mike cikin wannan azababben sanyin ya kai ku makarantar?” Na ce, “Wallahi babu kam Hajjah, ai Isa direba ba zai ki ba. Ko ya kika ce Ummie?” Ummi ta ce, “Kwarai”. Zanirah ma ta shirya cikin uniform na GGSS Giwa, kasancewar ita makarantar ta daban ta gwamnatin jiha mune a gwamnatin tarayyah. Riga da zani da hijabi shudi da fari, ta yi kyau abinta. Na tuna da banki na da nake tara kudi a ciki da na baiwa Yaya Aliyu amanarsa tun wancan satin. Na ce, “Hajjah ko Yaya Aliyu ya tashi yanzu? Bankina”. Hajjah ta ce, “Tabdi! Aliyu makiyin sanyi ko na ruwan sha shine zai mike miki yanzun? Karfe shidda?” Na janyo farin cambas na daurawa kafata na yo tsakar gida da niyyar daukar suwaita ta a kan igiya da na shanya tun jiya. Cikin muku-mukun sanyin nan ma’abocin hazo da ya lullube sararin samaniya, sanye da bakar shirt da shudin wando jeans ya daura ‘thick-coat’ doguwa har gwiwarsa, hannayensa duka zube cikin aljihun coat din domin kare sanyi, yana jingine jikin tagar dakin Hajjah. A hankali na ambaci sunansa cikin mamaki.... “Yaya Aliyu?” Ya lumshe idanunsa da suka kumbura suntum saboda rashin isasshen barci. “In kun kammala Fa’iza ku fito in kai ku, ku nake jira tun bayan fitowata masallaci sallar asubahi”. Ban ce komi ba na karasa na dauki suwaita ta na koma ciki. Da na gayawa su Ummi Yaya Aliyu ne zai kaimu duk sun yi mamaki suma, Hajjah ba ta ce komi ba. Zanirah muka fara rakawa kasancewar nan wajen gari ne, bayan an kammala mata (registration) an ba ta hostel an hadata da wata prefect muka juyo zamu tafi, idon Zanirah ya cicciko da hawaye. Ta ce, “Yanzu Yaya Aliyu don Allah kwana nawa zan yi a nan?” Muka yi dariya duka ganin yadda hawayen ya soma malalowa a kundukinta. Yaya Aliyu don ya kwantar mata da hankali ya ce, “Haba Zanirah? Ga ki ga gida meye abin damuwa ne? Bayan haka ma na yi miki alkawarin duk sati biyu zan rinka zuwa in ganki, zamu ke zuwa miki visiting duk wata har da Hajjah”. Ta soma sharar kwalla muka rungume juna, sannan prefect din da aka hadata da ita ta ja hannunta suka shige ciki. Bamu tafi ba sai da muka ga kulewarsu. A kan hanyar Gusau Yaya Aliyu ke ta tsokanarmu ni da Ummi, sai dai jiki da bakin kowaccenmu ya yi sanyi, kai baka ce ‘yan karadin nan na Hajjah bane masu kama da jiniya don kwakwazo a falon Hajjah ba. Wala’allah hakan na da nasaba da rabuwarmu da Zanirah da tunanin sabuwar rayuwar da zamu je mu taras, ta doka da oda ba irin ta gida gaban kakarmu abin son mu Hajjah ba. Ya tsaida motar a wani masallaci muka yi sallah, ya ce, “Ku dan jirani ko?” Ya tsallaka daya titin ya dawo mana da gasasshen nama da gorar ruwa da ta pepsi, muka ci muka ci gaba da tafiya. Ummi na ta yi min hira na ki kula ta saboda kewar Zanirah. Ta yi tsaki ta ce, “Aikin banza ana ta yi miki magana kin yiwa mutane shiru ke wace ce?” Na ce, “Nice Pirincess Fa’iza Bamalli”. A hankali yadda Yaya Aliyu bai jimu ba. Ummi ta ce, “Umh! Ya Aliyu ka ji yau Fa’izah ta fadi sunan da ka rada mata?” Idonshi a titi ya ce, “Ki bari don Allah?” Ta ce, “Wallahi”. Ya ce, “Kara fadi in ji Fa’iza”. Na sanya fuskata cikin tafukana ina dariya. Ni yadda Yaya Aliyu ke nuna mana kauna da kulawa irin haka sai nake jin zuciyata na kara kaunarsa a kowacce dakika. Ina ma a ce Yaya Aliyu ya ce yana sona? Ina ma ya zamo miji a gare ni? Da wace irin sa’a zan yi a rayuwata? Kamar ya san kallon shi da tunaninshi nake, sai kawai ya juyo muka hada ido, na yi saurin juyar da kaina ga titi. Ya yi murmushin da ya motsa kyakkyawan sajen da ke gefe da gefen fuskarsa, ya ce, “Kallon na mene ne?” “A kan me zan kalle ka Yaya Aliyu?” “Nima abin da nake son sani kenan Fa’iza, dalilin kallon?’ Na zumbura baki na hura hanci. Ya yi dariya ya kara speed din motar, bamu kara tsayawa ba sai a FGGC Gusau. Bayan ya gama mana duk shige da fice da ake yi daga ofishin vice zuwa na principal, aka bamu hostel daki daya ni da Ummi, amma ba aji daya ba. Ina A tana B. Sai da Yaya Aliyu zai tafi Ummi ta ce, “Yaya Aliyu mai yasa aka raba mana aji?” Ya yi murmushi ya ce, “Saboda ku yi karatu sosai in bakwa ganin juna akai-akai, amma idan an hada ku za ku shagalta da hirar gida ku ki yin karatu”. Ummi ta ce, “Wa ya ce dasu gidanmu daya? Ga sunanmu ba iri daya ba, ni Khadija Sabi’u Giwa, ita Fa’izah Ahmad A.B Giwa?” Ya nuna mata tsagin mallancinta, ya kuma ja dogon karan hancinmu da hannayenshi hagu da dama, ya ce, “Kowa ya ganku ya ga wadannan to ya san tushenku daya, kuma in har bazazzage ne to ya san zuri’ar A.B ne”. Jinjina kai na yi cikin gasmuwa da kalamansa. Bayan Yaya Aliyu ya mana sallama, har ya juya zai tafi sai kuma ya juyo, idanuwanshi sun sauya launi daga farare sol zuwa na damuwa, “FA’IZAH!” Da wata murya tamkar ba tashi ba. A hankali na juyo na ce, “Na’am Yaya Aliyu!” Ya ce, “Zo”. Tare da yafito ni da hannun daman shi. Na saki hannun Ummi na je gare shi muka tsaya muna kallon juna kamin in sadda kaina kasa a dalilin nauyin da kwayar idanunshi yai min. ‘Yan dakika kamin ya ce, “Ki daina kazanta, ki aje wasan da ke kanki ki tsaya ki yi karatu, ki zama mai kokari irin Zanirah kin ji ko?” Idona taf da hawaye na ce, “Yaya Aliyu kazantar me nake yi? Mene ne KAZANTA?” Bai bata lokaci ba ya dora da cewa, “Kula da tsaftar jikinki, kamar yadda zuciyarki take da tsabta. Ubangiji yana son tsabta ta yadda har ya mai da ita cikon addini. Tsafta ta hada da tsaftar jiki, da ta suttura, da zuciya baki daya. Tsaftar jiki ita ce, kula da baki (yin brush a kalla sau biyu a rana, wato safe da dare). Tsaftar fatar jiki (yin wanka da sabulu mai kamshi shima a kalla sau biyu a rana, da yawan amfani da sinadaran dake kashe warin jiki na halitta (body odour), wadannan sinadarai duk na sanya su cikin sayayyar da na yi miki (mouth wash, deodorant spray da roll-on) da turaren fesawa a tufafi. Tsefe kai da wanke shi da yin kitso duk sati, kina jina Fa’iza ta?” Na daga mishi kai ba tare da na iya duban shi ba sakamakon wata matsananciyar kunya da ta taso ta Yaya Aliyu ta lullube ni a dalilin kalaman shi. Ba tare da ya saurari cewa ta ba ya ci gaba da cewa, “Don Allah Fa’za ki tsaya ki yi karatu sosai kin ji? Wallahi bana son na ashirin din nan da na talatin da kike dauka a jarrabawar firamare ko na goma sha kaza.....” Na dago na dube shi idanuna fal da hawaye, na ce, “Insha Allah Yaya Aliyu zan dage ko don ka ji dadi ka daina jin haushi in Ya Fa’iz ya kirani Jaka! Insha Allahu ba zan kara kaiwa na ashirin ba ma har in kare makaranta..... insha Allahu ba zan baka kunya ba.... insha Allah sai ka yi alfahari dani fiye da yadda Ya Fa’iz ke alfahari da Zanirah!” Ya yi murmushi ya ce, “Alkawari....?” Na ce, “Eh, alwakari, kawo ma mu kulla”. Na bashi dariya sosai kafin ya miko min yatsarshi ta karshe ta hannun dama, na mika masa nawa muka sarke. Sannan muka kyalkyale da dariya ba tare da Ummi ta san abin da ya bamu dariya ba, ta janyo ni ta baya. Yana daga mana hannu muna daga masa har sai da muka kule cikin hostel. Rayuwarmu a makarantar Gwamnatin tarayyah ta ‘yammata dake Gusau ta ci gaba da tafiya yadda ake so, mun dukufa, ba ma tamkar ni da bani wasa da alkawari ko ya ya yake, fatana Allah ya fidda ni kunyar idanun Yaya Aliyu in kai mishi sakamako mai kyau. Duk da ba class daya muke da Ummi ba amma a hostel ko da yaushe muna tare, tare muke tafiya school arena, class, prep da hostel, dining da sauran extra-carricular activities da makaranta kan shirya bayan working time. Bamu yarda mun yi kawa ko guda daya ba, tsakaninmu da kowa sallamar musulunci da abin da ya hadamu. Mun samu exposure na zama da mutane kala-kala ‘yan garuruwa da yare daban-daban, masu halaye da dabi’u daban-daban. **** Gabatowar karshen zangon karatu na farko muka fara gwaji wato (test), inda na kara zage damtse iyakar iyawata na yi dan abin a zo a gani. Wannan ne dalilin da yasa kafin zuwan jarabawa na dan rike wasu abubuwa da yawa, don haka da muka fara sai ta zo min da sauki, na cinye darasin Arabic da English tsaf, sauran subject din dai gasu nan dai la ba’asa ya fi la shai’in in ji Larabawa. Su Hajjah sun zo mana visiting (ziyarar dalibai) har da su Inna Kubra. Ranar hutu da murnar mu muka nufi bakin gate a zaton mu Yayanmu Aliyu ya zo daukar mu, don baki ganni ba fuska kamar gonar auduga don murmushi. Ina rike da (report card) dina wanda nake kyautata zaton na yi abin kirkin da zai faranta ran Yaya Aliyu, na sauke nauyin alkawari na yi abin a zo a gani. Amma murnata ta daka tsalle ta burma ciki sakamakon ganin mutumin da na tsana da gani a rayuwata, mutumin da na tsani jin muryarshi da ganin fuskarshi mara alheri a gare ni, dan uwan da da za a bani wuka a ce in caka mishi ba komai da na yi gaggawar aikatawa. FA’EEZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA. Sanye da makubar shadda ‘getzner’ dinkin samarin garin Kaduna masu ji da tashen samartaka, bakar dara mai gezar bakin gashi ya kara haske sosai ya yi fresh ta yadda ko ni da bani son shi a duniya na san Fa’ezz namiji ne abin so ga kowa, ba ga mata kadai ba har maza jinsinsa ba za su bar yiwa kansu fatan zama ko dakacen komawa kamar shi ba. Jingine jikin motar Yaya Aliyu kirar ‘Picanto’ (Kia), fuskar nan dinke babu alamun rahama kamar kullum, na damko hannun Ummi kam, kirjina na dukan tara-tara ba ma uku-uku ba. Fuskar Ummi kamar an aiko mata da Manzon rahama ta saki hannuna ta sheka da gudu aguje wai za ta rungume shi. Ya kuwa doka mata tsawar da ta sa ta tsugunnewa a kasa cikin gigicewa. Ganin yadda ya tsoratata ya gigitata ya yankwanata a gaban sauran daliban da ke gefe, ko me ya tuna? Ya yi dan murmushi gajere wanda ya fidda lotsawar gefen kuncinsa na dama. Ya ce, “To ai ke ce abin naki babu kan gado tsohuwa (sunan da suke tsokanarta don ita ce mai sunan Hajjah, shi kuma su Yaya Aliyu su ce mishi tsoho kasantuwar shi mai sunan marigayi Abubakar Giwa (A.B Bamalli Giwa). Ya ce, “Kai! Ummi ba a girma”. Sannan ne ta iya mikewa a darare. Ni dai ina daga gefe hannuwana sarke a kirji ina kallonsu, a zuciyata in ban da Allah ya kara ba abin da nake yiwa Ummi. Ya budewa Ummi kofa ta zauna a gidan gaba ya rufe, yana sanya kayanmu a boot din mota ya juyo inda nake tsaye ya dube ni, ina tsaye jikin bishiya kawai ina kallon su. Ya rufe boot din motar ya shiga mazaunin shi zai ja motar. Ummi ta ce, “Ya Fa’iz, Fa’iza fa ba ka ganta bane?” Wata muguwar harara ya yi mata, ya ce, “In na ganta sai me? Sai me zan yi? Ita ba ta ganin mutane? Ba ta san ta gaishe su ba ko don UWARTA! Ta koya mata rashin tarbiyya irin tasu ta kabilu”. Sai kawai ya ja motar ya badeni da kura. Ummi kira take “Fa’iza! Fa’iza!! Fa’iza!!!” Amma ko sauraron ta bai yi ba. Na durkushe a nan na soma kuka, na yi kuka har muryata ta dashe. Na daga kai na dubi dai-daikun daliban da suka rage kwata-kwata babu ‘yan Kaduna, Zaria balle garinmu. Daga ‘yan Kano sai ‘yan Jigawa, sai ko dai-daiku daga jihar Gombe da Adamawa. Na dora hannuna aka na rafsa kuka. Duk dokina na son ganin Hajjah, Zanirah da Yaya Aliyu ya gushe, sai wani irin tukuki da zuciyata ke yi. Wannan wace irin kiyayya ce Ya Fa’iz ke min? Wace irin kiyayya yake yiwa mahaifiyata da ta shafe ni? Wannan ma ai rashin imani ne ba kiyayya ba. Duk irin kin da nake wa Fa’iz babu yadda za ayi in baro shi a jejin da na san ba shi da kowa, a gari mai nisa da babu kowa nashi. Na rasa inda zan sa kaina don bakin ciki, kawai sai na samu gefen bishiyar darbejiya na share na kwanta a wurin ina kuka. Ina addu’ar Allah ya kashe Fa’iz in huta. “Ke me kike a nan a kwance a kasa? Ko ba a zo daukar ki bane?” Muryar wata malama ta doki dodon kunnena. Na dube ta idona jage-jage da hawaye na ce, “Eh”. “Yar wane State ce ke?” “Na zo ne daga Giwa”. “Giwa? Giwa ta jihar Kaduna? Oh! Ke Bamalliya ce ko?” “Eh”. Na amsa a gajarce. “Amma kin yi nisa sosai, yanzu ya za ayi kenan?” Na ce, “Zan kara jira a nan zuwa yamma na san za a zo min”. Ta ce, “Ba zai yiwu ki yi ta zama ke kadai a nan ba, ki tashi ki shiga daga Library tare da yaran can ‘yan Niger State, kinga za ki fi hango duk mai shigowa ki fidda naki”. A sanyaye na ce, “To”. Na mike na kade jikina na dauki jakar littattafaina na rataya, da yake duk sauran kayan sawarmu suna cikin kayan da Ummi ta tafi dasu. Ban dade da zama ba barci ya dauke ni a kan daya daga cikin kujerun labiraren, na farka ne karfe biyar na yamma sakamakon tashin da wata yarinya ta yi min wai in tashi in yi sallar la’asar. Sai kawai na fashe da kuka ganin yadda duhun yamma ya lullube sararin samaniyar subhana. Na bita toilet din dake jikin labiraren muka dauro alwala muka yi sallah, ni azahar ma sai a lokacin na yi ta. Har na idar da sallah kuka nake. Ta ce, “Ki daina kuka, ai tabbas za a zo daukar mu ne, kema da baki da nisa kamarmu? Ai iyayenki babu yadda za ayi su manta dake”. Cikin kuka na ce, “An zo an dauki Ummi, ni tafiya ya yi ya barni, in Allah ya yarda ba zan dawo makarantar nan ba....” Shigowar daya daga cikin masu gadin makaranta yasa muka yi shiru muka zuba mishi mayunwatan idanuwanmu da yunwa da damuwa suka hadu suka jeme su, ya kira yarinyar nan wadda da alama ta girmeni cewar ta zo an zo daukar ta daga Adamawa. Ta fita tana daga min hannu har ta kule. Na kifa kaina cikin cinyoyina na ci gaba da kuka a hankali, ban san sanda sarkin barayin ya zo ya sake sace ni ba. Karfe bakwai na magariba na farka sakamakon azababbiyar yunwar da ta sake murda min ‘ya’yan hanjina, don saboda dokin zuwa gida ko karyawa (break fast) bamu tsaya mun yi ba saboda tunanin tuni Hajjah ta gama shirin karbarmu da hadadden girkinta. Na dafa cikina da hannuna daya na runtse idona da karfi, ganin yadda duhun dare ya mamaye sararin sama, hawaye suka ci gaba da yi min lugude a fuska. Hannun mutum na ji ya cira ni tsaye, na bude ido firgigit na mike a razane cikin fadin “Wayyo Allah..... wayyo Hajjah....” Abinki da cikin da ba komai, sai hajijiya ta kwashe ni yuuuu! Gaba daya na fada ga mutumin da ke tsugune a gabana, na daddage na kara sakin ihu.... “Wayyo Hajjah na shiga uku na lalace.... na mutu!” Ya rungumeni sosai a jikinsa yana fadi cikin tattausar murya irin ta marasa koshin lafiya, “Relax, relax Fa’iza, relax”. Na dauki lokaci ina tunanin mai muryar, kwakwalwata ta shiga tariyo min inda na san mai murya mai taushi da rashin amo. In ban yi kuskure ba zan iya cewa ta YAYA ALIYU CE.... YA YA ALIYU HAIDAR NA’IBI A.B GIWA. Na lumshe idona na dan lokaci, bugun zuciyata na saisaita da zazzafan jikin Aliyu, zuciyata da ta yi zafi na yi min sanyi kadan-kadan. Tsayin minti biyar Yaya Aliyu na rike dani, ya ce cikin kankanuwar murya, “Fa’izah are you ok?” Na gyada kai, ya sake ni muka mike a tare yana rike da hannuna. Ya dauki jakar litattafaina da daya hannun nasa na hagu muka fita daga dakin karatun, ya bude gidan baya na shiga, ya fiddo cooler din abinci ya bude, kamshin girkin Hajjah ne ya doki hancina, ba girkin cikin gida ba, wannan girki ne da take yi lokaci zuwa lokaci da hannunta, da na dade da sani ya baibaye ni, ya tado min tsohuwar yunwar da na wuni da ita. Yawun bakina ya wani irin tsinke tun kamin in kai lomar farko sanda Yaya Aliyu ke zuba min a farantin cin abinci (plate), dafadukar shinkafa ce da aka yi rabinta da zallar tsokar kaza da ganyen alayyahu da kabeji. Ya bude wata foil paper din ya fiddo gasasshen naman nan na kan hanyar Gusau da ya saya mana a hanya a zuwanmu, duk ya ajiye min ya rufe kofar ya shiga mazauninshi ya ta da motar muka soma tafiya. Bayan ya miko min robar ruwan swan mai sanyi ya ce, “Kina iya kwanciya idan kina jin barci in kin gama”. Da gudu ya fizgi motar bayan ya daga ma masu gadi hannu ya kuma yi signing shaidar cewa an dauke ni. Amma fa ya sha fada daga malamin da ke kula da shige da ficen dalibai, har ya bawa uku lada. Magana daya yake fadi masu su yi hakuri ba laifinsa bane. A yayin da wata danja ta tsai damu kusa da wata fitila mai hasken gaske, garin kalle-kallena mai nuna ciki ya dauka na fara dawowa hayyacina, na dubi hannun Yaya Aliyu wanda ke bisa giyar motar, allurar karin ruwa na gani soke jikin jijiyar hannunsa jini na diga amma bai kula ba, tukin shi kawai yake. Da na kura ido sai na ga hanyar karin jini da wata siririyar allurar ita ma soke duka a hannunsa ya bi fatar jikinsa ya kwanta. Na dube shi a razane domin tun zuwan shi ban ga fuskarshi ba, ya rame sosai ya yi duhu ainun. Na daga murya da karfi cikin tashin hankali na ce, “Yaya Aliyu ka tsaya”. Ba tare da ya juyo ba, haka nan ban ga annuri a kyakkyawar fuskarshi ba ya ce, “A kan me zan tsaya? Bakya ganin tafiyar dare zamu yi?” Na ce, “Ni dai na ce ka tsaya ko? Baka ganin hannunka yana jini ne?” Ya ce, “Babu komi wannan, kina so mu yi kwanan hanya ne?” Na ce, “Eh, mu yi ba komai”. Maimakon ya tsaya sai ma ya kara ware speed zuwa (200), kada ki ga yadda ‘yan idanuwana suka yo waje, suka yi kwala-kwala. Cikin kuka na ce, “Yaya Aliyu baka da lafiya.... you are bleeding....” Ya ce, “Don Allah don Annabi Fa’iza ki saurara min, da me zan ji ne? Insha Allahu lafiya zamu je gida babu abin da zai faru sai wanda Ubangiji ya riga ya kaddara”. “To ka tsaya in cire maka allurar...” “Na ce ki barshi ko dole ne?” Yadda ya yi min maganar cikin tsawar da bai taba yi min ba ya sanya hantar cikina kadawa, ban kara tankawa ba don na lura yana cikin wani irin yanayi (tension) mai wuyar fassaruwa. Bai tsaya ba sai a Giwa, harabar adana motocin A.B Bamalli Estate. Tsakar dare muka iso gida, yadda na ga mazan Estate din duka a tsaye cirko-cirko manyansu da samarinsu a kofar gidan hajjah ya tabbatar min babu lafiya. Baba Barau ya hau shi da fada, cewa yake, “Baka da hankali ne iye Aliyu? Halaka kanka kake so ka yi? Wannan wace irin wauta ce ka cizge karin jini da na ruwa ka bar gadon asibiti, ce maka aka yi duk cikinmu an rasa mai zuwa dauko Fa’iza daga makaranta?” Aliyu zai wuce su kwayar idonshi na neman rufewa, ya yi kokarin yin magana amma ya kasa. Ganin yana neman shan kasa Baban Giwa ya kama shi, shi da Baba Salisu suka mai da shi cikin motar da ya fito bai samu ya rufe ta ba. Baba Salisu ya ja motar aguje suka fice da shi asibiti. Ni dai na shige cikin gida sai kuka nake saboda halin da na ga Yaya Aliyu a ciki a dalilina. Hajjah ta taso ta rungumeni ta ce, “Baki kyauta ba Fa’iza, don me za ki tafi yawo a neme ki a rasa? Ga shi kin ta da hankalin dan’uwanki yana kwance asibiti amma daga jin labarin nan ya tsinke karin ruwan da ake masa ya dauki mota kamin kowa ya farga ya fice ya biki”. Na dubi Ummi dake zaune da mamakin sabon sharrin Ya Fa’iz, ta sunkuyar da kanta. Na ce, “Ni Fa’izar ce na tafi yawo Hajjah?” Muryata kamar na aro, kamar ba tawa ba. “Kyale ta kawai Hajjah, babu inda ni da malaminsu bamu duba ba cikin makarantar nan amma yarinyar nan kamar aljana sama ko kasa an rasa ta”. Hajjah ta ce, “To ai shi kenan zancen ya wuce tunda dai an zo lafiya alhamdulillahi, sai a kiyaye gaba. Ke Fa’iza jeki ki watsa ruwa ki ci abinci kafin asubahi ta karasa”. Na juyo da idanuna a hankali na dubi Fa’eez dake tsaye jikin bangon falon sai murmushi yake yi mai taushi, da idanuna da suka jawur na ce, “Kwarai, baka ganni ba Yaya Fa’iz, amma rabbil samawati wal’arshi shi yana ganinmu, kuma shi ya san abin da ke boye da wanda yake a sarari. Wata rana na zuwa da zai bayyana shi fili kowa ya gani”. Na wuce toilet abina yana fadin “Me kike nufi? Karya nake miki kenan?” Ko juyowa ban yi ba na shige toilet na rufo kofar da karfi. A zuciyata tausaya mashi nake kan halin da ya jefa kanshi a ciki, shin meye amfanin wannan kiyayya da yake nuna mini? Ya san girman ZUMUNCI a cikin addinin Islma kuwa? Me kiyayyar da yake yi min da hakan da yake yi min za su amfane shi da shi? A ce mutum sam-sam baya tsoron Allah a al’amarinsa sai Hajjah mutum ‘yar adam? Ni kam gani nake in an boye ma Hajjah da sauran mutane abu ko gaskiyar abu ba za a boyewa Allah ba, Allah ka shirye shi, ka ganar da shi illar karya da cin zarafin dan’uwa musulmi ba ma dan’uwa na jini ba. Na kwanta barci a wannan daren amma sam na kasa, tunanin shin wane halin Yaya Aliyu ke ciki a asibiti shi ya addabe ni? Me ya same shi? Me yasa ya boye min cewar ba shi da lafiya? Me ya tunzura shi ya yi fushi haka irin wanda ban taba gani daga gare shi ba? Na san dai ba zai wuce abin da Fa’iz ya yi mani a yau ba. A zahirin gaskiya ina tausayawa Fa’iz idan Yaya Aliyu ya fahimci cewa da gangan ya gudo ya barni. A wasu lokutan Yaya Aliyu na (acting according to) sunansa (mafadaci ne kamar kowanne mai suna Aliyu zakin Manzo). A duk lokacin da ya shiga irin wannan tension din babu mai iya tausasa shi sai Baban ABU wato (mahaifina). Tsorona Allah tsorona kada na zama silar wargaza zumuncin dake tsakanin Yaya Aliyu da Yaya Fa’iz (Mai sona da mai ki na). Don haka ya zama dole in kare Fa’iz albarkacin ZUMUNCI. In boye abin da ya yin wanda ba Aliyu kadai zai batawa rai ba har Hajjah dake matukar girmama shi da iyayenmu maza. Dan’uwa kowanne iri dan’uwa ne wanda na sani na kuma tabbata cikin family dinmu babu irin wannan hatsaniyar, ba zan so kuma in zamo silar ta ba. Na juya ga Zanirah dake gefena tana barci, sai na ga ashe ba barcin take ba sharar hawaye take yi. Na ce, “Ba ki yi barci ba Zanirah?” Ta ce, “Eh”. Na leka fuskarta sosai na ce, “To shin Zanirah me kike wa kuka?” Cikin dasasshiyar murya ta ce, “Yaya Aliyu? Shin ko a wane hali yake yanzun?” Na ce, “Wai me ke damun shi ne Zanirah? Wane irin ciwo ne ya cucemu haka ya kwantar mana da Yayanmu Aliyu?” Ta share hawaye da bayan hannunta ta ce, “Yana da (ulcer) ne ba tun yanzu ba, ba ta tashi kada shi ba sai a ‘yan kwanakin nan muna makaranta, nima da Hajjah ta je mun (visit) take gaya mani. Ya dade a kwance, domin ta ci karfinshi sosai. Ana i gobe zamu dawo Hajjah ta ce numfashi ma sama-sama yake yinsa da taimakon oxygen a asibiti. Sun samu sun fara shawo kan matsalar aka daura mishi ruwa da jinin da kika gani, lokacin ni Yaya Sani ya dawo dani gida kowa da kowa yana asibitin, wurin azahar Fa’iz da Ummi suka shigo, mu duka muna waje suka shige ciki wurin Hajjah. Babu abin da Yaya Aliyu ya soma tambaya sai ina ka baro Fa’iza? Ya ce, “Wai bai ganki ba....!” Wallahi sai ya tsinke jinin da ruwan ya dauki flask din abincin da Hajjah ta kawo mishi a lokacin ya fizgi mukullin motarshi hannun Ya Fa’iz, bai hana shi ba, shima sai ya yi ficewarsa. Abinki da taron mata babu wadda ta yi tunanin hana shi (tsai da shi), musamman a cikin yanayin fusatar da yake. Ya yi waje, Hajjah na kira da su Inna Kaltume amma bai ko waiwaye su ba, kuma babu mai ilimin kiran likita ko nurses a cikinsu balle kiran security na bakin gate. Ya tashi motar suka bude mai ya fita ya tafi dauko ki, shima Ya Fa’iz tafiyar sa ya yi......” Ta ci gaba da kuka, nima haka. Cikin kuka na ce, “Yanzu Zanirah a ganinki abin da yayanki ke yi a kaina, ko in ce nau’in zumuncinsa gareni yana kyautawa? Zan rantse miki da sarkin sarakuna Fa’iz da niyya ya taho ya barni a Gusau”. Zanirah ta zaro ido, ta ce, “Shi Yaya Fa’iz din?’ Na yi mata alamar ta yi a hankali kada Hajjah ta ji. Na ce, “Kin san Allah ina tsaye gabansa ya ja motar suka tafi, wannan meye in ba kiyayya ba? Me na yiwa Yaya Fa’iz ya tsane ni a dangi Zanirah? Fa’iz ya nuna bai damu da rayuwata ba, ko da na bi wasu can sun sace ni ba asarar shi ba ce, ko da na fito daga cikin makaranta na bata bai dame shi ba, ko da yunwa za ta kashe ni ba ruwansa bane. Amma don Allah don Annabi Zanirah kada ki fadawa kowa tunda na kudurta zan rufa masa asiri wurin Hajjah da Yaya Aliyu to zan yi, bana so a samu kuskure daga gare ni kan kiyayyar da Yaya Fa’iz ke mani, na tabbata wata rana Allah zai bayyanawa duk dangi cewa, Ya Fa’iz bai dauke ni ‘ya a cikin gidan nan ba a kan dalilin da ban sani ba”. Sai na ga Zanirah na hawaye, muka yi ta kukan tare. Daga bisani da muka ga kukan ba zai amfanemu da komai ba, Zanirah ta ce, “Mu tashi mu yi sallar nafila mu rokawa Yaya Aliyu sauki”. Washe gari su Hajjah za su tafi asibiti da safe na marairaice na ce, “Hajja don Allah?” Ta ce, “Mene ne?” “Don Allah zan biku”. “Ki bimu ina?” “Asibiti wurin Yaya Aliyu”. “Ki yi me? Kai Fa’iza da rigima kike, to shige mu je”. Ba abin da na dauka illa hijabi da report-sheet dina muka tafi. Mun samu Yaya Aliyu yana shan tea da kaninshi mai binshi Mus’ab, ya hada mishi yana mika mishi bired da yankakken dafaffen kwai da (mayonnaise) yana ci. Hajjah ta washe baki ta ce, “A’a, Aliyu lallai jiki ya yi kyau lafiya ta samu. Mus’abu an iya jinya, sai a dage da cin abinci a kan lokaci kuma yadda ya kamata yanzu ko? Tunda an ji kamshin kofar lahira”. Shi da Mus’ab suka yi dariya, ya sauko daga gadon da yake an cire mishi karin ruwan, ya gai da Hajjah. Abin da na fahimta duka hankalinshi kaina yake, na tsuguna na ce, “Yaya Aliyu ina wuni?” Ya ce, “Ko dai ina kwana Fa’izah?” Hajja ta ce, “Jiya ai Fa’iza da Zanirah basu yi barci ba ina jiyo shesshekar kukansu. Kai, tsakanin Fa’izah da Zanirah ban san wa ya fi son Yaya Aliyun nan ba, ko mi.... Hajja Yaya Aliyu, Hajja Yaya Aliyu ne ya bamu, Hajja Yaya Aliyu ya ce yana gaishe ki.....” Na rufe fuska da tafukana cikin jin kunya na ce, “Hajjah ai shima yana son mu ne, yana mana kirki, kuma ya damu damu shi yasa muke son shi”. Hajjah ta ce, “To Allah ya bar zumunci, yasa a daidaita da Hafizina tamkar hakan”. A zuciyata na ce, “HAR ABADA Hajjah!” Amma a fili murmushi kawai na yi, zuciyata kamar ta fito ta bakin don haushin kalaman Hajjah. Yaya Aliyu ya ce, “Fa’iza ina alkawarinmu?” Na zaro (report card) dina cikin hijabina na mika mishi, ya duba ya yi murmushi. Hajjah ta ce, “Ai kamar an san za ka tambaya har an fito aka zura da gudu aka koma aka dauko shi, in ce ko dai an yi abin kirki ba irin na baya ba?” Ya dago kai yana dariya ya ce, “Anyi da kyau Hajjah, na tara cikin dalibai sittin kinga ko an ka da hamsin da daya”. Hajjah ta ce, “Lallai Asma’u za ta yi tsalle (Maman su Zanirah) har ta gode Allah, ita ce mai damuwa da sakamakon Fa’izah a kullum baya kai wa rabin na ‘yan’uwanta. To takwara fa (tana nufin Ummi)”. Na kyalkyale da dariya na ce, “Ta yi na ashirin da daya cikin mutum sittin, ai ta yi kokari domin a primary ana yin magana ko koyarwa da Hausa, a can ko ba a yi kuma an kaita ajin kasuwanci, ni kuma ajin Arabiyya ne tuntuni na iya Larabci tun a gida Zaria, shi yasa nake fahimta sosai cikin ajinmu. Amma ka ga sauran subjects din ai duk ban ci da yawa ba”. Hajjah ta ce, “Koh? Allah ya taimaka, gata nan ta kara habewa ta suntuma kamar yis, sai fada da karfi kamar diyar zaki amma babu karatun a zo a gani”. Na ce, “A’a, Hajjah tana kokari”. Duka suka yi dariya ganin yadda na bata rai, don cikin mu ukun nan babu mai son a soki ‘yar’uwarta ko a gabanta balle a bayan idonta. Yaya Aliyu ya bar dariya ya ce, “Gaya min Fa’izah ya aka yi suka taho suka barki?” Na ce, “Wallahi Yaya Aliyu ba yawo na je ba, na shiga teachers area ne gidan su wata ‘yar ajinmu in kai mata littafinta da na ara, shine da basu ganni ba suka taho suka barni”. Ya ce, “Next time kada ki kara yin irin haka, kin ji na gaya miki, kina wasa da ranki ne da lafiyarki masu muhimmanci ga wadanda ke da bukatar su. Shi kuma da yake babban sakarai ne ba zai iya jiranki ba? Allah Hajjah Fa’iz zai gamu dani da kyar ma in.....” “Na kashe zancen nan tun jiya Aliyu, kada wanda ya sake tado shi”. Ya ce, “An barshi Hajjah”. Har yamma muna wajen Yaya Aliyu, wannan ya shiga wannan ya fita. Sai biyar da rabi Aunty Zainabu Maman su Aliyu da Baba Na’ibi mahaifinsu suka zo, sannan muka bisu muka tafi. Aunty Zainabu ke tsokana ta, “Fa’izah hutu bai zo da dadi ba, Babban Yaya babu lafiya ina kwanciyar hankali?” Baba Na’ibi ya ce, “Ai laifin su ne tunda basa matsawa Yayan yana cin abincin cikin gida sai dai ya basu kwai da Indomie su soya masa, kowa ya gaya musu wannan taliyar abinci ce oho!” Na ce, “Wallahi Baba daga yau ba zamu kuma dafawa Yaya Aliyu Indomie ba, durar tuwo kawai zamu dinga yi masa, ko kuwa Hajjah?” Hajjah ta ce, “Ni ina ruwana ne?” Satin Yaya Aliyu guda a asibiti aka sallame shi. Hutunmu ya ci gaba da tafiya cikin dadi tare da Yayanmu mai son mu Aliyu, wanda shiga goma fita goma in zai yi cikin gida sai ya neme ni, ko ya riko min wani abu. Na ci ne ko na amfani, ko wanda zai amfane ni wajen karatu. Babban farin cikinmu Fa’iz an yi balaguro zuwa Kaduna. Duk gidan ‘yan’uwa mun zaga ba inda bamu je ba sai Kaduna da Zaria. Hutunmu ya rage saura sati daya mu koma makaranta Baban ABU ya zo suna hira da Hajjah a falonta muka shigo daga Islamiyya ni da su Zanirah, baki daya muka tsugunna muka gaishe shi, muka wuce dakinmu. Ya daga murya yana fadin “Lallai Fa’iza baki da kirki, kika yi tafiyarki Gusau ba sallama, kika dawo shima kina shirin komawa ba tare da an waiwaye mu ba ko? Ga su Walida kullum basu da zance sai na yaushe za ki dawo, kin kyauta kenan?” Na ce, “To Baba ai matarka ce ba ta nemana shi ya sa”. Ya ce, (cikin dariya) “Tana neman ki mana, jiya ma ta ce ka ga Fa’izah yau saura sati daya a koma makaranta amma shiru”. Na buga tsalle na makalkale shi ina cewa, “Zan bika, zan bika to Baba”. Zanirah ma ta ce, “Nima zan biku Baba ka sauke ni gidan Maman Ya Fa’iz (mahaifiyarta)”. Ya ce, “Ke fa tsohuwa (Ummi)?” Ta ce, “Ni area one za ni”. Ya dubi Hajjah ya ce, “Wai me yasa uwata ba ta son gidansu ne?” Haka dai muka debi ‘yan kayanmu muka bi Baba. Sai da aka fara kai Zanirah Kaduna (Jabi Road), ko shiga gidan ban yi ba don sanin cewa Fa’iz na nan. Amma Baba na karya kan mota zai fita a get din gidan sai ga shi ya shigo da litattafai a hannu, Baba ya dan rage gudu suka gaisa. Wai don ganin idon Babana Fa’iz ko kunya babu ya ce, “A’a, Fa’iza ba za a shigo a gai da Mama ba?” Ban ba shi amsa ba na dauke kai. Ummi ta ce, “Ka dai ce muna gaida ta”. Baban ABU ya ce, “Kun ci gidanku”. Ya auno mana umbola. “Ku zo har kofar gidan nan ba za ku shiga ku gai da Asma’u ba balle kannenku in Yaya Muntari baya nan?” Kafin ya rufe baki muka bubbude kofa muka fita, ni kuwa muna dan yin nisa da motar na zura da gudu na je na gai da Maman, sanda suka shigo falon shi da Ummi na sake kwasa da gudu na yi cikin mota kada wata kalma ta hadamu ko ya yi min zalincin nasa. Baba bai tsaya shawartar Ummi ba ya ja mota sai unguwarsu gidan Yaya Hauwa, wato gidansu. Ta ce, “Baba me zamu yi a gidan Maman Maryam?” Ya ce, “Haba Ummi, kowa na marmarin ganin uwarshi wata da watanni bai ganta ba, in ke bakya marmarin ganinta to ita tana bukatar ganin ki ko?” Ta zumbura baki irin na ‘yar fari, “Baba ‘ya’yanta fa fitsarin kwance suke yi, su bi duk su jike ni in na yi zarni a ce nice”. Ya ce, “To ai ba sai kin kwana ba, ku je zan jiraku ku gaida su ku fito mu tafi (Area One) din (gidanmu)”. Nan muka kama murna muka fice. Aunty Hauwa na tsaye jikin famfo tana wanke (under wears) din yaranta muka yi sallama da babbar murya. Ta saki wankin ta bude hannuwa ta rungumemu duka, fadi take, “Ka ga ‘yan Gusau an cakare har an cake! Irin wannan gayu haka kamar ba goyon tsohuwa ba”. Muka kyalkyale da dariya. Na dubi jikinmu ni da Ummi, ni kaina na san mun yi kyau. Wani riga da wando ne da mayafi ‘yan (Lahore-Pakistan a jikinmu, na jikina yellow na Ummi green, gashin kowaccenmu babu kitso kalmashe cikin tafkeken ribbon kalar kayan kowacce, wanda dama mahadin kayan ne tare ake sai dasu. Ashe Baba wayo ya yiwa Ummi, sai ga Yusuf da kayanmu ya shigo dasu wai Baba ya ce sai gobe zai zo ko ya turo direban makaranta ya tafi damu. Da daddare bayan cin abincin dare muka shiga bai wa Yaya Hauwa labarin rayuwar bording school daga A-Z, sam ban yi zancen Fa’iz ko halayen da yake nuna min da wani jininmu ba, ko da wasa ban taba yi ba. Haka abin da ya yi min ranar hutu, balle wanda yake yi min a Giwa. Haka Ummi ba ta tada zancen ba, ko da Yaya Hauwa ta sako sunan Ya Fa’iz cikin hirarmu bana tankawa (wannan shine babban kuskuren da na yi at the first place), ko kuma na kare shi idan Ummi ta so fadin rashin kirki da rashin alherinsa. Sai lokacin Baban Ummi Alh. Sabi’u ya shigo gidan, Sabi’u Kwangila shi ke rike da (Bamalli Farm) gidan gonar A.B Family dake cikin garin Kaduna, inda ake kiwon poultry da noman kayan marmari. Shi din kuma babban dan kwangila ne na karan kansa. Daidai gwargwado suna cikin rufin asirin Allah, ba abin da suka nema suka rasa, don ita ma Yaya Hauwa babbar ma’aikaciya ce, principal ce a makarantar Sarauniya Amina. Mahaifin Alh. Sabi’u shine babban aminin marigayi Abubakar Giwa, idan da wanda za a ce ya yi auren bare, ko ko auren da ba na jini ba to Aunty Hauwa ce, sai dai zumuncin dake tsakani irin tun na kuruciyar nan ne wanda aka zama tamkar jini daya. Ba shi kuma da niyyar yi mata wani abu wai shi KISHIYA, kamar yadda ya fahimci ba a yi sam a zuri’ar A.B Giwa, one-man-one-wife-one-life! Baba Sabi’u ya zauna gefen Aunty Hauwa ya ce, “Ummi ai mun yi fushi, tafiya ba sallama, dawowar ma sai da muka ci arzikin Zanirah, na tabbata da ba ta zo Kaduna ba ke da Fa’iza ba za mu ganku ba”. Ummi ta ce, “Don Allah Baba ka yi hakuri, wallahi ziyarce-ziyarcen ne ya yi mana yawa”. Ya ce, “Ai dole duk inda hakuri take in je in sayo ta in hadiya. Ya ya jarrabawa? Ta nawa-nawa aka yi?” Ummi cikin doki tace, “Wallahi Baba ta ashirin da daya na yi”. Ya yi salati ya ce, “Allah ya yaye miki wautar da ke kanki Ummi, wallahi ki kama kanki, ki nutsu ki shiga cikin taitayinki, lokacin abu ayi shi in ya wuce ya wuce kenan”. Ummi ta bata rai ta ce, “Baba na fa yi kokari na dauka za ka yaba min ne, a primary 40 fa nake yi”. Ya ce, “To da dan dama-dama sai a kara dagewa”. Washe gari da yamma Baban ABU bayan ya taho office gidan ya biyo har da kanwata Walida da Abdallah a bayan motar. Baba Sabi’u ya yi mana provision sosai, har da Zanirah da ba ta nan bai ware ta ba. Sayayyar da ya yi mana ko da Yaya Aliyu zai kara sai dai ya kara kadan. Muka nufi Zaria cike da farin ciki. Ita kanta Ummi sai na ga tana wani nishadi da annashuwa na musamman, na ce, “Yar banza ashe kina son su Yaya Hauwan?’ Ta ce, “To Fa’izah akwai wanda bai son mahaifan shi ne?” Na ce, “Ba gaki nan ba, sai an miki dabara za ki gun iyayenki”. Ta ce, “To ke kuma fa?” Na ce, “Ai ni dole ce tasa na barsu kema kin sani”. A gidanmu Momi na kicin tana girki muka yi mata sallama, ta washe baki tana yiwa Ummi sannu da zuwa ban da ni. Na ruga na rungume kugunta na ce, “Momi ni bakya nemana ko?” Muryata kamar zan yi kuka Ta yi ‘yar dariya dauke da wata irin matsananciyar kauna cikin kwayar idanunta, ta ce, “In neme ki in miki me? Su Walida basu ishe ni ba kenan?” Sai a lokacin na ga cikin Momi ya zama kato ya turo zani har baya kulluwa, na ce, “Momi haihuwa za ki yi?” Ta ce, “Me kika gani?” Na ce, “Cikinki na gani ya kumbura suntum”. Ta yi tsaki ta fice ta bar min kitchen din tana cewa da Ummi ta kashe mata heater din ruwan zafi mu fito mu rufo kofar kicin din. Walida ta zo kunnena ta rada min cewa, “Baba ya ce kanwa ko kani Momi za ta haifowa Kausar”. Muka kyalkyale da dariya. Dariyarmu ce ta sata juyowa ta dube mu, ta girgiza kai tana murmushi, na san sha’awa muka ba ta. A kullum ni da Walida kamar ‘yan biyu muke, domin Walida akwai manyan barage, sai dai ita fara ce tas ni kuma ina da duhu. Da ganin Walida ka san za ayi babbar mace mai babban jiki nan da ‘yan shekaru, ba mai cewa Abdallah ya girme mata da shekaru dai-dai har uku, don ni kaina ta dara ni jiki da tsaho. Haka yadda muke kaunar junanmu duka abin sha’awa ne wurin Mominmu da ta haife mu ma balle ga sauran al’umma. Duk kawaici irin na Momi a wannan hutun na fuskanci ta ji dadin zuwana, domin ban taba kai wa irin tsahon wannan lokaci ban je ba. Kwananmu biyar muka juyo Giwa da tarin tsarabarmu na tafiya makarantar kwana. A can muka tarar da Zanirah ta riga mu dawowa tuntuni. Washe gari Yaya Aliyu ya mai damu makaranta, amma duk da kayan da muka samo bai rage komai ba a sayayyar da ya saba yi mana, bai fasa komi ba. To haka rayuwa ta ci mana gaba tsakanin gida da makaranta. Duk burin iyayenmu ya ta’allaka ne a kanmu mu ukun nan da burin gina mana ingantacciyar rayuwa, kasancewar mu ‘yammata matasa kadai dake gabansu. Kauna ce muke gani daga kowanne bangare na iyayenmu, gata na duniya babu irin wanda bana gani daga iyayenmu, da kakarmu Hajjah da babban Yayanmu Aliyu Haidar. Wannan ne dalilin da yasa muka kara zage damtse don mu fita kunyarsu mu ba mara da kunya, mu nuna musu ba a banza suke wahalar da suke yi damu ba, we will insha Allah make them to be proud of it ta hanyar kara zafafawa kawunanmu da karatu. Sai dai gatan da ake nuna mana baya shafar tarbiyyar da muka taso a ciki, muka gada iyaye da kakanni, muka kuma tashi muka ga ana yi cikin gidanmu tuntuni. Ta fannin Yaya Aliyu, ya kara zage damtse da kokarin ganin na kara hazaka sosai da hikima da basira irin nasa. Ba zan manta ba a second term (zango na biyu) da na kai masa sakamakona na yi na shida, ya nuna min bacin rai sosai, ya daina kula ni, ya daina shiga sabgata, ko kallon inda nake ya daina. Ya daina sayo min gasasshen naman da ya zame min kamar taba. Maimakon hakan duk ya koma yiwa Zanirah wadannan abubuwan a madadina, ita da ta kawo (second position), duk na bi na damu, na shiga cikin kunci da takura na babu gaira babu dalili. Wannan ne ya zaburar dani na takurawa kaina da karatu a zango na gaba, iyakar iyawata na kawowa Yaya Aliyu (3rd position out of 60). Yaya Aliyu ya daga ni ya yi sama yana juyi dani a falon Hajjah, kayan dadi da nama kuwa sai da Hajjah ta yi ta fada tana zai sangarta ni, in na auri wanda ba shi da halin ciyar dani nama kullum fa? In shiga raina abin da ya kawo mani?” A zangon farkonmu na sabon aji JSS 2, su Momin ABU, Maman Kaduna da Yaya Hauwa, Aunty Zainabu da matar Baba Barau Aunty Marwa, da matan su Baba Sadi duk suka yo Bus guda suka kawo mana ziyara. Momin ABU rungume da sabon baby dinta kyakkyawa kamar Baban ABU, na rungume shi na rasa inda zan sa kaina don farin ciki. Bakina kamar ya yage don fara’a ina rungume da babyn, na ce, “Wai ya ya sunansa Momi?” Ta ce, “Ban sani ba, ni fa ba wurinki na zo ba Aku sarkin magana”. Na yi narai-narai da ido kamar zan yi kuka. Yaya Hauwa ta ce, “Rabu da ita Fa’iza, sunan shi Baban Kaduna (Mukhtar) shi kenan?” Na ce, “To, Ya Hauwa ya zamu ke kiran shi?” Ta ce, “Kowa a gida yana ce mishi ‘WALID”. Dadi ya rufe ni, na ce, “Yeh! Mun samu Waleed da Waleeda”. Ta fannin Fa’iz karatun Diploma a Kaduna Poly ya sha masa kai, a kokarinsa na hattama (ND) wato National Diploma. Fa’iz wani irin mutum ne da baya son karatun boko sam. Diplomar ma sai da suka takura masa su Baban ABU suka bude mishi wuta, don bayan kammala sakandire dinshi a Madina kin ci gaba ya yi, kai dai barshi da tukin mota. Duk wanda ke son zuwa unguwa Fa’iz ne direbansa, ba sai ka roka ba shi zai roke ka ka ba shi key din mota ya kai ka. Babu yadda bai yi ba Baba Muntari ya ba shi mota ya ki, don ya ce tukin mota ne yake hana shi karatu don haka duka bus-bus din A.B Estate mukullan su yana hannun Fa’iz. Kowa da (nature) dinsa, kowa da kaddararsa, to “tukin mota shine kaddarar Fa’eez Mukhtar Abubakar Giwa”. Yana kwanan makaranta ne a Kad Poly don haka yawancin hutun da muke zuwa muna samun sa’ida. Week end kawai yake zuwa Giwa ya koma lahadi, don haka marorinmu sun sarara cikin shekarun nan. Wannan hutun da muke zangonmu na karshe na aji uku na karamar sakandire (JSS.) mun dukufa karatun jarrabawar (placement). A wani dare a hostel na dubi Ummi wada ke nazarin wani littafin Islamic Studies na B. Aisha Lemu (For Juniors) na ce, “Ummi kin san tunanin da ya zo min kuwa?” Ta ce, “A’a, sai kin fada”. Tare da rufe littafin da ke hannunta. Na ce, “Wallahi tunani na yi, gara mu hada baki mu ki makarantar nan haka. Babu mai tunawa damu, babu mai zuwa mana a kan kari ko akai-akai, komai mune karshe. In ba don ma Yaya Aliyu da ke zuwa duk wata ba, ai da mun kade. Kina da masaniyar cewa Zanirah duk sati sai an je mata an kai mata girkin Hajjah da dambun nama, gaskiya ni ba zan dawo ba”. Ummi ta ce, “Ni babu ma abin da ya fi ban haushi irin ranar hutu, kullum mune karshen dauka bayan yunwa ta gama kwakwale mu”. Na ce, “Abin da nake so ki gane kenan, kawai mu bude wuta mu ce mu sai Sarauniya Amina (Queen Amina College Kaduna) inda Yaya Hauwa ke aiki. Makaranta ce ta hazikai kwarai, Aunty Hauwa ta taba gaya min dan JSS 2 a Queen Amina zai iya rubuta Formal Letter ba tare da kuskure ba, duk da ba ta federal govt. ba ce”. Ummi ta ja numfashi ta ce, “To shi kenan, sai mu bi ta kan Yaya Aliyu shi kadai zai yi mana wannan kokarin, kuma shi kadai ne zai mara mana baya, amma cewa za’a yi don muna son kusa da gida ne kawai”. Na ce, “Ai Allah ya ga zuciyata, ni dai abin tarihi da alfahari ne a gare ni a ce na zamo daya daga cikin daliban makarantar nan mai tsohon tarihi”. Ranar hutu muka shiga sallama da kowa kamar har mun tabbatar ba zamu dawo din ba. Bamu bar ko tsinkenmu ba, mune har da amsar address din wasu daga cikin ‘yan dakinmu da ‘yan ajinmu wadanda aka saba da juna tsayin shekaru uku. Yaya Aliyu ya ga kaya cancarakas! Har da su loka da katifu da filallika, ya ce, “Ku lafiya? Ina za ku da wannan kayan?’ Muka kyalkyale da dariya ganin yadda ya razana, muka shiga danna kaya a but muna fadin “Mun yi graduation ne Yaya Aliyu”. Ya ce, “Aure za ku yi?” Muka hada baki wajen cewa, “Eh! Yaya makaranta ta ishemu aure muke sooooo!” Ya zuba hannaye a bannet din motarsa yana fadin, “La’ilaha illallahu......” Na ce, “Muhammadur rasulillahi.....” Ummi ta ce, “Sallallahu alayhi wasallam”. A kan hanya muke yi masa bayanin shawarar da muka yanke. Ya ce, “Ke dai Fa’iza ko dai don ki dinga cin abincin Aunty Hauwa ne?” Na ce, “Wallahi a’a Yaya Aliyu, kawai ina so na zamo daya daga shahararrun daliban Sarauniya Amina wadanda tarihin Najeriya ba ya mancewa dasu (Old Student of Queen Amina College Kaduna)”. Ya ce, “I trust you my dear sissy”. A falon Hajjah Yaya Aliyu ya ta da zancen,ranar da muka kwana uku da komawa. Bashir da ya zo daga Kaduna ya ce, “Gaskiyar Fa’izah, don ko wannan jelen daga Giwa zuwa Gusau-Gusau zuwa Giwa ba karamin wahala bane”. Fa’iz ya ce, “Wane irin wahala Yaya Bash? Tunda Allah ya hore abin da za a sayi man fetir din da lafiyar da za a tuka motar ba shi kenan ba? Kawai dai Fa’izah jakar yarinyar nan ka san ba son karatu take ba shine ta zuge Ummi don ita ma ta maida ta jaka kamar ta, amma ta ya ya za a ce wai Govt. School ta fi ta federal Govt. Na san don su dinga ganin Aunty Hauwa ne kurum..” Aliyu ya yi saurin katse shi da cewa, “Ban tari hanzarinka ba Fa’eez, ban kuma ce Fa’eezah mutum ce ba jaka ba ce tunda uwarta ba A.B ba ce, don haka Fa’eezah ba mutum ba ce. Amma da ka ce wai don su dinga ganin Aunty Hauwa ne a kan me? Shin watanni nawa suke sharewa ma a nan garin ba tare da sun ziyarce ta ba ma sun taba damuwa? Ko ka taba jin tsakanin Ummi da Fa’iza wata ta taba tambayata yaushe zamu je wajen yaya Hauwa? In da ka ce Maman Kaduna to wannan sai in yarda” Fa’iz ya kyabe baki ya ce, “Kai ai Yaya Aliyu ai dama kullum kana bayan Fa’izah, ba ta taba yin ba dai-dai ba ka kwabe ta, komi ta yi, duk hukuncin da ta yi dai-dai ne a wurinka, alhali she’s (empty-mindend)”. Ya ce, “Yes! Fadi da babbar murya ina bayan Fa’ia a kullum, domin da ka ki da ka so FA’IZAH yarinya ce mai tunanin kanta, hikima da kaifin basira, da wuya tunanin ta in an auna shi za a ga rashin hikima a cikinsa. Kuma da kake cewa wani wai Allah ya hore kudin man fetir, to don Allah in tambaye ka, shin ka taba kashe kwandala ka sayi man ka zuba a mota ka kai ko ka dauko Fa’iza daga Gusau ko da sau daya ne? Ka taba kashe lokacinka ko da minti talatin ne ka je ka gano Fa’iza da Ummi a Gusau? Amma Zanirah! Ka gaya mani don Allah, sau nawa kake zuwa mata visit per-term? Ko ko ka taba kawo kwandala ka basu ka ce su sayi sabulun wanka a makaranta? Amma Zanirah sau nawa kake sayen kaya ka kai mata Fa’iz! A wane dalili don Sun nemi sauyin makaranta za ka sanya baki, don haka ba damuwar ka ba ce bai shafe ka ba ina fatan ka gane?’ Fuskar Fa’eez ta yi jawur da wannan wankin babban bargo da Yaya Aliyu yai masa, ya ce, “Amma ka san ni ba wani aiki nake ba baya ga karatu, ina zan nemo kudin da zan ke musu provision har su uku, kuma su suna da nisa?” Yaya Bashir ya ce, “Line perfect, wannan karatun naka ne kake kiran shi karatu? Wai National Diploma, amma a hakan ina kake nemo wanda kake yiwa Zanirah? Ina kake nemo wanda kake dinka sabuwar shadda duk sati? Tukunna ma, ina kake kai rabonka da ake baka na A.B family duk wata? Ban ga amfanin mutum ya tsaya yana faman cacar baki da mutumin da bai san ciwon kansa ba irin Fa’iz Bamalli....” Hajjah ta zaburo ta ce, “Ku kun san Allah ku kiyaye ni, haka kawai kun sa min miji a gaba kuna tsiga kuna tsattsaga kamar ku kuka haifi Fa’izar da Ummin? Sai ku bari in ya zo ya ce muku yana son daya daga cikinsu sannan ku yi masa wannan gore-goren naku”. Yaya Aliyu ya ce, “Ai shima baya fara ba, baya soma ba Hajjah, Ina! Ai alamar karfi yana ga mai kiba, kuma abin da ka yi shi za a yi maka. Makaranta ce ni Ali zan canza musu, zan ci gaba da kula da hidimarsu duka ba zan bambanta ba, ba zan fasa ba, don ni irin nawa ZUMUNCIN KENAN duka daya ake, A.B abu guda ne bana jikin-jikina kawai ba, in har ina da iko sai in ko bana numfashi Hajjah”. Ta ce, “To Allah ya ba da sa’a, ga fili nan ga mai doki”. Fa’iz ya ce, “Sai sukuwa Hajjah”. Yaya Aliyu ya danna mai harara ya yi ficewarsa yana murmushin tura haushi. **** Ina toilet ina wanka na ji landline din Hajjah na ta faman (ringing) babu wanda ya dauka ta yi ta ruri har ta katse, ta sake kama wani sabon kukan har tana neman ta sake katsewa. Cikin hanzari na ja tawul na daura duk jikina kumfa na fito falon aguje na dauki wayar na amsa da sallama. Sai ga Ya Fa’iz ya sanyo kai falon, cikin captan na makubar shadda Hilton, ya yi shar kamar ango sabon aure. Shigowar tashi da tunanin yanayin sutturar da nake ciki ya sanya ni rawar kafafu tare da sarkewar harshe wajen amsa sallamar. Muryar Maman Kaduna ce ta ce, “Fa’izah ga direba nan na turo yanzu ku biyo shi dukkanku tafiya zamu yi Kano gidan Rabi”. Na yi tsalle na dire na saki ihun murna, na ce, “To Mama”. Na ajiye wayar amma saboda rawar da hannuna ke yi na ajiye shi ba dai-dai ba. Dagowar nan da zan yi muka yi ido hudu da Fa’iz yana yi min wani irin asirtaccen kallo da shi kadai ya san ma’anarsa, sai dai na nemi kibiyar kiyayyar dake cikin idanun na rasa. Kallo ne na kurulla wanda ya wuce gejin kallon addini. Na tuna a yanayin da nake na saki wani dogon tsaki na juya na shige dakinmu, na shige toilet na rufe na ci gaba da wankana. Bayan na kammala na fito ina muttsika mai a fatar jikina (Norwegian Formula). Su Ummi suka shigo suna ta hira da kwasar dariya, na ce, “Ku don Allah mu shirya ga direba nan Mama ta turo zai debe mu zuwa Kaduna, daga nan mu tafi Kano wajen Ya Rabin Yaya Muftahu”. Nan su Ummi har da tsalle aka fada wanka, Zanirah na hada mana kaya cikin (luggage). Hajjah ta shigo daki ta ce, “Ku kuma shirin me kuke haka kamar za ku tashi sama?” Na ce, “Hajja Kano zamu”. Ta ce, “Kano? Wajen autata amma shine baku gaya min da wuri na tanadi tsaraba ba?” Na ce, “Hajjah muma yanzu-yanzun nan Mama ta yo waya ta gaya min na gaya musu, amma na san ita Maman za ta yi tsaraba ai”. Muka sha doguwar riga mai rubi biyu ‘yar Oman (tsarabar Baba Sadi ne ta Hajjin Bara), nawa baki da ratsin maroon, na Ummi baki da bula-bula mai hasken sararin samaniya, na Zaneerah ja da baki, muka debi ‘yan kayan da zamu butaka cikin travelling bag. Kamar jira yake mu kammala, malam Garba direban Maman kaduna sai ga shi ya aiko su Abba ya zo mu fito. Mun shiga mota Hajjah na daga mana hannu, nice a gaba su Ummi a baya, sai ga Yaya Aliyu ya fito daga gidansu ya ce, “Sai ina kuma ‘yammatan Hajjah?’ Na ce, “Sai Kano”. Ya ce, “Kano? Gaskiya Fa’iza ban yarda ba, na ji an ce samarin Kano kwarraru ne wajen fashin mata”. Cikin mamaki na ce, “Matar wa to za su kwace?” Ya yi hanzarin gyara zancensa da cewa, “Ke dai kada ki kula maza a Kanon, Idan Baban ABU ya ji kin yi saurayi zai gayawa Hajjah ne ayi gaggawar yi miki aure ke da su Ummi, ba zai bari ki yi Sarauniya Amina ba”. Su Ummi suka kyalkyale da dariya (ban da Zanirah). Na ce, “To na ji ba zan yi ba, amma su Ummi su yi?” Ya kada kafada ya ce, “Eh, ba komai su suyi, ai kinga su sun girme ki. Baki ga Ummi ta yi biyunki ba”. Malam Garba ya ja mota muka wuce muna mishi dariya ban da Zanirah da ta yi fuskar shanu tana ta sakin tsaki, to wa take yiwa? Allah masani. Da muka isa Kaduna already Mama ta shirya ita da Junior, bamu bata lokaci ba sauran yara suka yo mana rakiya bakin mota da kayan Mama Kano ta diba. Kusan karfe biyar na yamma muka iso Kano, unguwar da su Anti Rabi suke wai ita Gadon Kaya. Unguwa ce da ta tara duka masu karfi, masu karamin karfi, ‘yan kasuwa kawo ‘yan boko babu irin rukunin mutanen da ba za ka taras a unguwar ba. Duk da babu inda ban sani ba a Kaduna, ban ga kyakkyawan gari mai albarkar al’umma irin Kano ba. Gidan su Aunty Rabi yana ‘Yarda Avanue.’ Mama ke yiwa Malam Garba kwatance har kofar gidan. Abdul-Rahim dan Aunty Rabi muka fara gani suna wasan kwallo shi da wani yaro dan makotansu, duk da bamu san shi ba, amma tsagin mallancinmu da karan hancin sun tona shi, muka kama shi muka rungume. Aunty Rabi ta fito da gudu ta makalkale Mama kamar wata karamar yarinya, tana lale Maman Kaduna, lale da ‘yan Giwa, lale da ‘yammatan Hajjah. Ta yi mana jagora zuwa falonta, Yaya Muftahu ya fito daga nashi dakin shima yana mana marhaban, nan muka ga yadda ake karrama bako, ko da jini ne ba bako ba. Kwananmu daya washe gari suka kwashe mu don nuna mana Kano ciki da bai dinta, duka kofofin nan, Kansakali, da Kabuga, Gadon Kaya, Kofar Ruwa, Duka Wuya, Dan Agundi, Kofar Famfo da Na’isa babu wadda bamu ratsa ta cikinta ba mun daga kai mun karanta sunan ta ba. Kofar Nassarawa, Kofar Mata. Manyan wuraren tarihin Kanon Dabo irin su Gidan Makama (Museum), gidan Dan Hausa, Dutsen Dala da Gwauron Dutse, Gidan Zoo, Gidan Sarkin Kano da Fadar Masarautar Kano, har gidan Tsumburbura dake kan Dutsen Goron Dutse. Haka manyan shopping malls din Kano babu wanda Yaya Muftahu da Aunty Rabi basu kai mu mun ciko ledoji ba, tun daga Sahad, Country Mall, Well Care, Grand Square, Jifatu da Ado Bayero Mall. Lallai na yarda Kano ta amsa sunanta ta Dabo-ci-gari, yaro ko da me ka zo an fika. Mune har gidan Zoo da gidan Makama Museum. Sannan ranar juma’a mika ya da zango a fadar Sarkin Kano Alh. Ado Bayero muka yi gaisuwa ga Dabon Kano, duk da bai sanmu ba, ranar juma’a ya ware ta yana amsar gaisuwar talakawansa Allah ya yi masa rahma (amin). Gaskiya mun ji dadin ziyararmu Kano fiye da duk wani gari da muka taba zuwa. Ko da yake mu dama duk yawon namu iyakacinshi Kaduna da Zariya, don haka zuwan mu Kano da kwanaki uku kacal da muka yi tare da Aunty Rabi da iyalinta ba karamin dadinsa muka ji ba. Bayan mun dawo Yaya Aliyu ne ya tsaya ya sama mana gurbi a Queen Amina, duk da Yaya Hauwa ta so hanawa Hajjah ta ce ta kyale mu. Muka tattara muka koma muka fara karatu babu kama hannun yaro. A hutun karshen zangon karatu na karshe na aji hudu da muka zo, Fa’iz yana makaranta ya kama daki a cikin makaranta. Don haka na saki jiki nake rayuwata cikin walwala da nishadi. Ranar wata asabar Baban Kaduna ya zo gidan da maraice, ina uwar dakin Hajjah ina shirya mata kaya cikin (wardrove), ita kuma tana falo tana sallar walha na ji sallamar Baba Muntari. Hajjah ba ta amsa mishi ba, nima ban amsa ba kamar wadda aka dinkewa baki. Ina jin shi yana waya da Baba Barau, Sadi, Sadisu, Na’ibi, Ibrahim yana fadin duk su hallara falon Hajjah tunda Asabar ce kowa yana gida. Na ci gaba da abin da nake yi amma daga inda nake ina iya juyo hucin Baban Kaduna da ajiyar zuciyar da yake yi akai-akai. Ba a jima ba suka shiga shigowa daya bayan daya da sallama yana amsawa a wahale. Zuwa lokacin Hajja ta idar suna ta gaggaishe ta tana amsawa. Sannan ta dubi Baba Muntari da kulawa da kauna ta manyantaka, ta ce, “Wa ya tabo Muntari ne? Wannan sammako da taron gaggawa haka?” Baban Kaduna bai tanka ba ya ciro takarda cikin breif case dinsa ya mikawa Baba Na’ibi, Baba Na’ibi ya karanta ya mikawa Ibrahim, Ibrahim ya mikawa Barau, Barau ya mikawa Sadi, Sadi ya mikawa Sani, Sani ya mikawa Salisu, dukkansu suka hada baki suka ce da Hajjah. “Takardar withdrawal ce (kora daga makarantar Fa’iz Abubakar Mukhtar) daga Polytechnic a bisa hujjar rashin zuwa aji kwata-kwata, rashin contineous assessment (CA), sai za ayi jarabawa kawai yake zuwa. Idan kuma ya je yadda aka ba shi answer sheet haka yake ajiye ta baya iya rubuta komi a ciki, sai sunansa da registration number. An dora shi a kan (probation) tun shekarar baya bai gyara komai ba”. Duk suka yi shiru suna sauraron cewar Hajjah. Ta jima ba ta yi magana ba, sai daga bisani ta ce, “Ba zan ce komai ba sai na yi magana da Hafizin”. Baba Muntari ya zo iya wuya, ya ce, “Ki gafarceni Hajja, duk lalatar da Fa’iz ke yi don ya samu faragarki ne. Na yi na yi a daina bai wa Fa’iz mota kin ki. Ba shi da aiki sai tukin mota da gyaranta in ta lalace, duk kanikawan garin nan sun san Fa’iz, in ya ce miki yana makaranta to yana tashar mota. Jiya-jiyan nan (C.I.D) din da nasa ya dinga bibiyar min shi tun lokacin da ya ce miki ya kama daki a makaranta jikina ya bani ba haka kawai ba, don mutumin da karatun boko bai dame shi ba me ya kai shi tarewa a makaranta? To rahoto ya zo min cewa, Fa’iz ba a makaranta ya tare ba yana Kaduna Express (tashar motar Kaduna) ya zama direban peageout da express masu zuwa gari-gari ba ya makaranta.....” Gaba daya suka dauki salati har ita Hajjah. Ban san sanda dariya ta kubuce min ba, na yi hanzarin shigewa toilet na sheka abata na more. Ban dai ji karshen tattaunawar tasu ba sai fitar su bayan sunyi mata sallama. A raina na ce, hakki ba karya bane. Ina zaace hakkina ba zai lalata Hafizin Hajjah ba. Washe gari ina wanka Fa’iz ya shigo falon Hajjah, jikina duk kumfa amma haka na kwara ruwan na fito kar labari ya wuce ni, ina ji Hajjah na cewa, “Ubanka gata yake maka, kyakkyawar rayuwa yake so maka ba wani abu ba.....” Ina jin sanda yake ce mata, “Hajjah ina da matsala ne, hannuna kyarma yake duk lokacin da na rike biro. Hajjah bana iya rubutu”. Abin da ban taba ji ba a duniya, wato shesshekar kukan Fa’iz. Ya ci gaba da cewa, “Hajjah ko wacce makaranta ce na yarda a kaini, amma kada a rabani dake. Ba zan iya rayuwa bakya kusa dani ba Hajjah. Akwai wata makarantar irin ta ai a nan Zariya a kai ni mana. Wallahi na yarda zan je, amma ni bana son in yi nisa daku ko kadan, don Allah ki taimake ni Hajja, ke kadai ce za ki iya lankwasa shi”. Hajjah ta dauki carbinta tana kokarin ficewa daga dakin kada ya karasa karya mata zuciya. Hajjah Hadija da Hafizinta Fa’iz (Abubakar) sai Allah. Cikin dauriya ta ce, “Na gama maganar nan dasu tuntuni Fa’iza za ka Rasha (Russia) kana so ko baka so. In kuma ka isa, je ka ce dasu baka so ba za ka ba. Sun ce kasashen da suka ci gaba ba a yin rubutu da biro ya yin duk wani abu da ya shafi karatu, tafawa ake a computer (typing). Tunda dai ba ni na kawo maganar nan ba Ubanninka ne, to don Allah ka shafa min lafiya”. Shiru Fa’iz ya yi yana tsane hawayen idonsa da hankici. Abun duniya duk ya bi ya dame shi. Ya san yau an canza masa Hajjansa, ‘ya’yanta sun gama yi mata famfo, kuma ya santa kaifi daya ce, tunda ta ce haka ba za ta taba canzawa ‘ya’yan nata ra’ayi ba. Shi kam bai son ya tafi ne ba don komi ba sai don yarinyar nan Fa’izah ‘yar Maimuna za ta yi farin ciki ta sakata ta wala a gidan, don ya tabbata shine kadai matsalarta a zaman gidan. Shi kuma a duniya mai adawa ne da farin cikin Fa’izah, in da abin da ya ki jini a duniya to ya ga Fa’iza cikin walwala a gidan nan. To wai shin meye dalili? Me yasa ya tsane ta kamar ba jininsa ba? Me ta yi masa ya tsane tan? Meye laifin ta? Meye aibunta? Me take yi wanda bai so? BAI SANI BA! Tabbas akwai katuwar (?) alamar tambaya cikin kwakwalwa da zuciyarshi game da yarinya FA’IZAH A.A. GIWA. Watanni uku da suka biyo baya, Fa’iz ba shi da sukuni duk da yana cikin gidan kullum yana baskwata. Haka kuma a lokacin muna cikin zangon farko aji biyar. Damuwar har ta sabbaba masa ciwo, tun yana yi a tsaitsaye har ya kwantar da shi hajaran-majaran. Wannan ya ta da hankalin Hajjah ba kadan ba, ta yiwa Baban Kaduna maganar a kyale Fa’iz da tafiya karatun nan tunda abin ya kai ga taba lafiya. Baban Kaduna ya ce, “Don Allah don Annabi Hajjah ki fita daga maganar nan kada kema ya kwantar mana dake, amma sai dai ya mutu na huta ganin dana yana direban tasha in dai ba zai yi yadda nake so ba”. Sai Hajjah ta yi shiru. Cikin wani hutu da muka zo Fa’iz na shirya kayan shi cikin troller (akwatin tafiye-tafiyen bature) da muke kira (tura ni a tiles). Ummi ta yi sallama ta ba shi kaya cikin leda da Baba Na’ibi ya aiko masa ya yi guzurin tafiya. Ganin yana loda kaya a jaka ta samu kujera ta zauna a gefensa a darare, ga mamakinta bai mata tsawa ba, bai hantare ta ba balle ya kore ta. A hankali ta ce, “Yaya Fa’iz tafiyar kenan?” Ya dago ya dube ta ya yi dan murmushi, “Eh, Ummi ya zan yi? Baban Kaduna ya dage. Daga nan Kaduna na nufa, daga nan mu wuce Kano inda zamu tashi ta filin jirgin Malam Aminu Kano ni da shi”. Ummi hawaye ya cicciko idonta dai-dai sanda idonta ya kai ga wani karamin album saman kayanshi da yake hadawa. Ta dauka ta bude shafin farko ta shiga dubawa. Shafin farko hoton Fa’iza ne ta yi tagumi jikin varanda ‘terrace’ na gidan Hajja. Shafi na biyu kyakkyawan hoton Fa’izah ne ta yi tagumi a falon Hajjah. Haka shafi na uku Fa’iza sanye da koriyar suwaita mai kauri da jan siket kanta ba dankwali, wanda hakan ya sakko da jelunan kitson (shuku) dake kanta har bisa dogon wuyanta, tana rungume da (teddy bear) a gidansu dake Zaria. Sai kusan karshe ne ta ga hotunansu da sauran kannensa duka na Giwa da na Kaduna, har da su Walida amma 80% ba album din hotunan Fa’izah ne. A matukar mamakance Ummi ta daga ido ta dubi Ya Fa’iz hankalinshi baya kanta yana ta shirya kaya haikan. Ta zari mai rungume da Teddyn ta ce, “Hoton nan ya yi kyau Ya Fa’iz in dauka? Fa’izah ba ta san da shi ba ma sam, don Allah ina ka same shi?” A lokacin ne ya dago ya dube ta, ya zaro ido ya ce, “Ke! Wa ya ce ki taba mani album? Ina ruwanki da kayana?” Ya fauce album din ya danna a jaka ya ja zif. Ya shiga zuba mata bala’i ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba. Ummi dariya kamar ta kashe ta san (borin kunya ne yake nannade shi da hauka). Ta ce, “Ka yi hakuri Ya Fa’iz ban san baka so a taba ba”. Ta dauki wasu daga cikin hotunansa ta ce, “In dauki wadannan Ya Fa’iz?” Ya dube su daya bayan daya ya ce, “Me kika ce?” Ta mike da hotunan a hannunta za ta fita, har ta kai bakin kofa ya ce, “Tsohuwa!” A kufule ta juyo don ya kirata da sunan da ta tsana a rayuwarta, amma ga mamakin Ummi sai ta ga ya yi murmushi. “Don mi kike son hotona bayan duk kun tsane ni don kawai ina gaya muku gasiya?” Ummi ta girgiza kai tana dariya, ta ce, “Allah Ya Fa’iz bamu tsaneka ba, daman can kai ne ka tsanemu, kuma mu har mun manta ma wallahi. Mun san kuruciya ne ga shi yanzu tunda ka shiga Poly ai baka cika shiga lamarinmu ba balle ka takura mana. Wani abin ma in aka ce ka yi ai ba za ka yi ba”. Ya ce, “Ko? In ku kun manta ai Hussainar taku ba za ta taba mantawa ba. Domin na zalunceta na wulakanta ta na ci mata mutunci da yawa, wanda nima wallahi ban san dalili ba. Yanzu har nauyinta nake ji saboda halin RAI da muhimmancin ZUMUNCI, kunyarta nake ji wallahi-wallahi Ummi.....” Ummi ta yi sakatoto! Tana duban sa cike da shakkar ba da Fa’izu (Abubakar) take magana ba, wani ne dai mai matukar kama da shi. Ko kuma mafarki take yi. Ta ce, “Yaya Fa’iz wai kana nufin Fa’izah?” Ya girgiza kai ya ce, “It may be itan, it may also be kuma ba itan ba.....” ......”Ban gane ba?” Ummi ta tambaya her voice is trembling (muryarta tana rawa). Ya ce, “Ba za ki gane ba Ummi, kowa ma ba zai taba ganewar ba, amma Allah ya ga zuciyata na yi nadama da dana sanin abin da na yiwa Fa’izah”. Ummi ta dan yi zuruu! Tana dubansa, ta ce, “Na tabbata na kuma hakkake cewar Fa’iza ba ta rike ka ba sam a zuci Ya Fa’iz, kullum addu’arta Allah ya shiryi Ya Fa’iz ya ganar da shi illar ‘KARYA, MUGUNTA, ZALUNCI da muhimmancin zumunci”. Fa’iz ya dafe kai ya dubi Ummi duk idanuwansa sun sauya launi, ya ce, “Yanzu Ummi duk da wadannan sunayen Fa’izah ke kallo na? Kuma haka Ummi?” Tune din muryarshi wannan karon (in subdued) a karye. Ita ma Ummin ta karaya a wannan gabar, ban da girgiza kai alamar, “A’a”. Ba abin da ta ce. Ya yi mata alamar ta tafi kawai ta kyale shi. Washe gari kowa ya shirya za a tafi rakiyar Fa’iz, sai na zari mayafi na yi wuf na shige gidan Baba Barau na buya a kitchen. Neman duniya Ummi ta yi ba ta ganni ba, dole suka hakura suka shiga mota. Daga tagar kitchen din ina hango shigar Ya Fa’iz mota, yana dan waiwaye kowacce kusurwa ta A.B Bamalli Estate kamar mai neman wani abu. Daga bisani ya shiga motar Ya Aliyu ya ja suka fita a get din. Na yi wata irin doguwar ajiyar zuciya kamar an zare min kaya a kafa, kamar kuma an sauke dutsen Dala da Gwauron Dutse daga kaina. Na yi wata irin kakkarfar ajiyar zuciya. **** BAYAN SHEKARA DAYA Shekarar ta zo ne da tarin sauyuka masu yawa cikin A.B Bamalli Family. Tafiyar Fa’iz da tafiyar Yaya Aliyu bada jimawa ba jami’ar Lagos yin digiri na biyu. Don haka a hutu na gaba da muka zo mun yi kewar Yaya Ali ba kadan ba. Na yi kiba na yi bul-bul na dan yi haske dai-dai misali, sai sheki da kyalli nake yi, ke kuwa babu fargabar Fa’iz ko kadan wanda shine kadai matsalata a rayuwa. A wannan hutun da muka zo ranar wata asabar ina dakin Hajjah ina sallah na jiyo sassanyar muryar Yaya Aliyu a tsakar gida yana gayas da Hajjah. Bai tambayi kowa ba, bai tambayi komai ba daga gaisuwa sai “Hajjah ina Fa’izah ne? Ban ji motsinta cikin gidan nan ba”. Hajjah ta ce, “Tana ciki, nake jin sallah take. Ka san in aka soma doka nafilfilin nan sai Allah. Ai ma hushi ake da kai tunda ka tafi Lagso ba sako ba aike balle waya”. Ya kama kai abin ban dariya, ya ce, “Oh! Ni Aliyu Bamalli na shiga uku!!” Ya yo cikin dakin da gudu-gudunsa. Hajjah ta yi dariya ta ci gaba da abin da take yi. Zaneerah ta ya da tawul din da take tsane jikakken gashin kanta, ta zaro ido ta wara hannuwa tare da daka tsalle ta dire gabana ta ce, “Yaya Aliyuuu! Muryarshi a tsakar gida Fa’izah!!” Ta yi wuf ta yi bakin kofa zata fita. Na ce, “Ke Zanirah baki da hankali ne? Haka za ki fita daure da tawul?” Zanirah ta dubi kanta ta ce, “Oh! Na gode Fa’izah, kin san Allah duk na rude sabida murna”. Na bita da kallo a lokacin da take zurma doguwar riga a jikinta, jikinta har rawa yake yi. Ni yadda take rawar jiki a kan Yaya Aliyu da al’amarin sa, ko ni da ya fi nuna kulawarsa a kaina bana yin hakan balle irin wannan zumudin, ni haushinsa ma nake ji wallahi tunda ya tafi bai neme mu ba, ba waya ba sako. Tana kokarin fita yana kokarin shigowa, sai suka yi karo garam! Ya yi hanzarin ja da baya tare da ware ido. “Zanirah kin makance ne?” Da gudu ta nufe shi ya yi hanzarin kaucewa a hankali ya ce, “Zanirah kin girma, shekaru goma sha biyar, kada ki sake ki kara yi min irin wannan oyoyon kin ji ko?” Ko ni kaina ba don na nutsu ba da ba zan ji shi ba, domin cikin kwantaccen sauti ya fada. “Wannan sai su Hanifa sune yara (diyar Baba Sadi)”. A raina na ce, “Ai ko Hanifa ba za ta yi haka ba, ita ma Zanirar ban san yau ina ta samo wannan bakuwar al’adar ba wadda sam bamu tashi da ita ba. Amma da na yi la’akari da dadewar da muka yi bamu ga Yaya Aliyu ba, sai ban ga laifinta ba, at the same time, na yi mata uzuri da ajizanci wanda dan Adam baya rabo da shi. Zanirah na dariya ta ce, “Yaya Aliyu ka rage min fa, da watanni biyar cur!” Ya ce, “Yar gari, ashe kina sane?” Bai koma ta kanta ba ya shigo ya russuna har inda nake, kamshin daddadan turarenshi ya doki masunsunata. “A roka damu Alasabbinaki”. Na zumbura baki na gyara zaman carbina cikin hannuna na kau da kai. Cikin dariya ya sassauta murya ya ce, “Na yi laifi ne Princess? I’m so sorry. Wallahi ban yi da niyya ba....” Na kara turo baki na kau da kai. Yaya Aliyu ya yi dariya ya sa hannu cikin bakar leda ya bude, kamshin wani irin lafiyayyen balangu ya doki hancina. Na hadiye wani tsinkakken miyau ji kake mukut! Dariya ta kashe Yaya Aliyu. Ya sa hannu ya zare carbin ya tura min kunshin balangun gabana. Ai ban bata lokaci ba tuni na ja kunshin leda cinyata na juya mai baya, na manta da fushin na soma dauka ina dannawa wani na bin wani. Zanirah ta zo ta zauna za ta ci na doke hannun ta, ta ce, “Yaya Aliyu Fa’izah kadai ka sayo wa?” Muryarta abin tausayi. Ya ce, “Eh, domin shine favourite dinta, kowa ma na sayo mai abin da ya fi so a rayuwarshi”. Ya sa hannu a aljihu ya fiddo alawar cakulet mai kwakwa (Bounty) ya mika mata. Zanirah ta yi tsalle ta cafke ta yi waje, na tattara ledar namana na mike zan bita amma Yaya Aliyu ya rike gefen hijabina, gaba daya na juyo. “Wai me na yi ne don Allah Fa’iza? Na taho gari ya gari tun daga Lagos domin ki amma kike zumbura min baki?” Na bude baki cikin mamaki na ce, “DOMIN NI?” Ya yi saurin girgiza kai, ya ce, “A’a, DOMIN KU”. Na ce, “To sakar min hijabin na gaya maka kada Hajjah ta shigo”. Ya yi saurin saki. Na koma na zauna na ce, “To don me tunda ka tafi makaranta ba sako ba waya Yaya Aliyu? Don me za ka koma makaranta Yaya Aliyu?” Ya yi murmushi ya ce, “Fa’iza ke yanzu ba makaranta kike ba?” Na ce, “To in anyi degree ba shi kenan karatun ya kare ba? Da dadewa na taba jin an ce ka yi digiri”. Ya girgiza kai “Is just the beginning Fa’izah digiri na farko shine tushen duk wani ilimi. Ilimi ba shi da iyaka, ba shi da karshe sai dai ka yi iya wanda za ka iya ka bari. Ina so na yi ilimi mai yawa ba digiri kadai ba, ko baki son wata rana in zamo Farfesa kamar Baban A.B.U? In yi gida nawa na kaina a duk inda nake so a outside ba a A.B Bamalli Estate ba cikin kauyen Giwa? In yi family mai tsari irin na Baban A.B.U? In yi rayuwa mai tsari irin ta Baban A.B.U? Ba irin ta su Baba Barau ba Fa’izah”. Ban san sanda na tuntsire da dariya ba. Na ce, “Ai ni na yi zaton don ka gaji da kai mu makaranta da dauko mu ne da zuwa mana visiting shi ya sa ka koma karatun don ka gaji da saya min nama, Zanirah (Bounty) Ummi (Kit-kat), ka gaji da kai mu shopping da koya mana karatu, shine ka tafi”. Dariya mai suna dariya kam Yaya Aliyu ya yi ta har ya gaji, ya ce, “Fa’iza yaushe za ki daina wauta ne don Allah? Shin in tambaye ki, da can waye ya sani yi muku hidimar makaranta? Waye ya sani sai muku balangun da alawa? Waye yake sani in kula daku in ba don ina son ku ba? Na rantse da sarkin sarakuna ba zan taba gajiyawa da hidimta miki ba muddin rayuwata! Ko da bani da shi, zan yi aikin karfi da lafiyata in nemo in yi miki in har za ki yi farin ciki. Balle kuma alhamdulillahi Allah ya hore mana arziki na duniya dai-dai gwargwado, ta yadda har nake raina ‘yar hidimar da nake muku wanda har ke kike kallon ta kike kiranta hidima. Ko da duk abin da na mallaka zai kare wurin sai miki nama ba zan damu ba, saboda dalilin da har yanzu kika kasa ganewa. Kada ki kara saka wannan a ranki (wai ina yi muku hidima), kada ki kara tunanin hakan, sa a ranki wannan Dutyn Aliyu ne”. Ina wani irin murmushi mai fitowa tun daga karkashin zuciyar dan adam na ce, “Ba zan kara ba Yaya Aliyu”. ***** Washe gari muna gidan Baba Na’ibi (gidan su Yaya Aliyu) muna kallon wani wasan kwaikwayo na ANTAR-BN-SHADDAD da ABLAH, domin mu zuri’armu kaf daga shekara kasa da sha takwas, ba a kallon finafinan Turawa, na Hausa ko na India, ko na ‘yan kudu (Nigerian Film), sai hikayoyi na Larabci da Risalah, ko tarihin Sahabbai da ake yi a matsayin film kamar na Khulafa’ur-Rashidun. Domin wannan finafinai da na zayyano a sama a ganin Hajjah duk nau’i ne na illata tarbiyyar yara da hana su mai da hankali ga karatu. Daga na yake-yaken Larabci (Adventure) sai zaluncin da Isra’el ke yiwa ‘yan’uwa musulmi na yankin Gaza, sai Islamic Channel wadanda suke nuna halin da kasashe marasa karfi ke ciki, irin su Somalia da irin tallafin da NGO’s suke yi musu, irin su ‘Human Appeal Organization’ masu daukar nauyin irin wadannan kasashe ta hanyar abinci, ilimi, asibiti da tufafi. Wadannan al’umma masu ban tausayi abubuwa ne dake karawa yara imani da wadatar zuci. Sai ko labaran Larabci na Al-jazeera, CNN, BBC. Saboda yawan kallon al’amuran Larabawa da nake, da sauran labaran Larabci da kallon rayuwarsu a talabijin, dadin-dadawa ana yin Larabci as (Subject) a ajinmu, sai ya kasance na iya Larabci sosai, kuma shine harshe mafi soyuwa a gare ni tun ina (Area One). Tun ina karama Allah ya dora min kaunar Alifun-Ba’un, Alifun-Arnabun, Ba’un-Baqaratun. Maryam ta dube ni muna cikin kallon ta ce, “Wai me Antaru ya ce kenan Fa’izah?’ Na fassara mata, ban ida rufe bakina ba Yaya Aliyu ya shigo. Ya samu gefen mahaifiyarshi ya zauna, ta ce, “Ya ya dai Yayansu? Na ganka rather moody? In ce ko ka dauki abincinka ka ci?” Ya dan yi tsaki ya ce, “Mama na sha kunun alkama fa a wurin Hajjah yanzun nan”. Ta dube shi tsaf, cikin babbar murya ta ce, “Aliyu!” Da hanzari ya dago ya dube ta. “Na gaji kullum magana daya ta ki ci ta ki cinyewa. Yanzu kamar kai Aliyu sai an rarrasheka ka ci abinci za ka ci, sai ka ce wani karamin yaro, da gangan kake wasa da lafiyarka, to na daina, sai dai ka kashe kanka kai kadai, wallahi ka kwanta ciwo ko hanyar asibiti ba za ka ganni ba. Ko da yake in ka kashe kanka ai kai ka jiyo, wa ka yiwa asara?” Na juyo daga kallon T.V na ce, “Mama mu mana? Mu aka yiwa asara”. Zanirah ma ta ce, “Tabbas mu ya yiwa asara, we cannot, never found a caring brother like him, Yaya Aliyo don Allah daure ka dinga cin abinci in ka mutu mun shiga uku”. Na ce, “Mun shiga uku ko mun shiga tara?” Ummi ta ce, “Har mun lalace”. Zanirah ce ta mike ta yi kitchen da zafin namanta, ta shako plate da dankali soyayye da murtukekn kwai, ta zo ta zauna tsakanin Mama da Yaya Aliyu kasancewar suna zaune kujera daya ne mai cin mutum uku. Cike da kulawa ta mika mishi, kana cikin muryar lallashi da kulawa ga karamin yaro in ya ki cin abinci ta ce, “Yaya Aliyu don Allah ka ci”. Gaba daya aka kwashe da dariya har Maman dake bambamin fada, babu shakka yadda muke kula da Yaya Aliyu da hidimarsa, da yadda shima yake kula damu da al’amuranmu, yana yi mata dadi, don ko Maryam da suke ciki daya ba ta kulawa da al’amarinsa kamar yadda muke masa, haka shima. Ga shi tana masifar son Yaya Aliyu kamar ba dan fari ba. Ita cikakkiyar lauya ce mai zaman kanta, sam ba ta irin kawaicin Momina, mu’amalarta da Yaya Aliyu kamar ta Yaya da kaninta mai binta da suka fito ciki daya. Hakan ba karamin bani sha’awa yake ba, in yi ta dakacen ina-ma a ce nice. Na taso tsam daga inda nake zaune zuwa garesu na ce, “Mama tashi ki bamu fili in bai ci ba dura zamu yi masa”. Ita da Yaya Aliyu suka sa dariya, ta ce, “Lallai kam ‘yammatan Hajjah kadan daga aikin ku, kuma aikinku yana kyau, Allah ka bani tsawon ran da zan ga da wacce za ayi tsakanin ke, Ummi da Zanirah.....” A hargitse Yaya Aliyu ya yi ma Mama gyaran murya ga alama bai ji dadin abin da ta fada a gabanmu ba. Ta mike ta bar mana falon tana dariya tana fadin “Sannu-sannu ba ta hana zuwa sai dai a dade ba a je ba”. Sai da muka tilastawa Yaya Aliyu ya cinye abincin nan tas, sannan muka kyale shi. Ya ce, “Ummi ban ji yadda aka riski Queen Amina ba?” Ta ce, “Tambayi gimbiyar taka mana ni ai baka yi dani Yaya Aliyu, ka kawo mata nama, Zanirah pack din Bounty, amma ni ko sannu don ni lukuta ce tun ranar da ka fada Zanirah ke tsokanata ba a yayin lokutayen mata”. Ya murmusa a hankali, ya fiddo pack din kit-kat a aljihunsa ya cillawa Ummi. Ta dauke tana dariya tana godiya, ya ce, “Saboda Allah Zanira ina ruwan ki cikin wannan maganar har da kike tada ta bana nan?” Ta ce, “Rabu da ita Yaya Aliyu, ita ta fara ce min mai wuya uwa marikin lema, an fada din, ba a yayin lukataye sai ‘slim’ din ki yi duk abin da za ki yi”. Ya fiddo mata ido ya ce, “Kada na kara jin irin wannan maganar, babu kyau gorin halitta Zanirah, kada na kara ji”. Ummi ta ce, “Rabu da ita Yaya Aliyi, so take jikinta ya gaya mata ta ga ranar lukutin jiki, sai shegen cika bakin tsiya babu kwanji, don ta ji Hajjah na cewa ta girmemu to ba shekaru biyu ba ko goma kika bani in kika kara ce min lukuta lallasaki zan yi”. Yaya Aliyu ya rasa inda zai sa kansa don dariya, ya ce, “Ana girma ana cin kasa Ummi da Zanirah! Inda Fa’izah ke burgeni kenan, tunda kuka shiga aji hudu ta watsar da shirme ta bar muku”. Ummi ta ce, “Eh, ai daman a wajenka Yaya Aliyu Fa’iza ba ta laifi, ita ce ta iya komai, bayan ita din a bayan idonka tantiriyar kanta ce”. Yana dariya ya ce, “Bakya son a fadi gaskiya, amma Fa’izah ta fiku hankali, nutsuwa da kamewa. Ko zaman wuni guda mutum ya yi daku zai fuskanci haka”. Ummi ta sake kuluwa, ta tashi faram-faram ta fice. Yana kiranta yana ba ta hakuri amma ba ta juyo ba. Zanirah ko a jikinta, daman ita yarinya ce mai matukar sanyi cikin al’amuranta ba ta da fushi, ba ta da daukar zafi ko kadan a kan duk abin da za ka yi mata, da wuya ka ga bacin ranta. Kullum fuskarta cikin annuri take, ita dai barta a cika baki da kokarin karatu kamar Alhuda-Huda. Ya maido duban shi gare ni ya ce, “Fa’izah ba a bani labarin Sarauniya Amina ba”. Na ce, “To Yaya Aliyu me zan ce maka ga yara duk sun zubo min ido?” Maryam ta ce, “Lallai ma, su waye yaran naki?” Na ce, “Gaku nan mana juniors ‘yan JSS”. Ta ce, “Mts! Ke har yaushe kika fara SS din da za ki raina mutane?” Yaya Aliyu ya ce, “Ke rufe mana baki ko na hambareki, wa ya sako ki cikin zancen nan? Ko sa’arki ce?” Na faki idonsa na yi mata gwalo, ta dalla min harara. “Maza dauko biro da takarda ta rubuta min labarin Queen Amina”. Zanirah ta ce, “Ba za ta iya ba Yaya Aliyu, ba ta iya Turanci sosai ba”. Ya ce, “Da kowacce luggah Fa’izah rubuta min labarin Queen Amina, be it Hausa, Arabic, English, Fulfulde, Kanuri, Yoruba or Igbo, in har kika rubuta am sure zan iya karantawa in fahimta”. Da karsashi na karbi takardar da biro, na matsa nesa dasu na soma yarfawa Yaya Aliyu kyawawan rubutu da harshen Larabci tsaftatacce. Na mika masa ya shiga karanta musu a fili, ga fassarar abin da na rubuta. “Yaya Aliyu mun je Queen Amina lafiya, makarantar Sarauniya Amina babbar makaranta ce mai kyawun tsari, tsohuwa mai tsohon tarihi. Malamansu da dalibai duka masu kwazo ne. Bamu da kawaye, amma muna gaisuwar musulunci da duk wanda wata mu’amala ta hadamu da shi. An kai ni ajin Arabic, an kai Ummi ajin zane-zane (Art) saboda shi ta fi iyawa. Akwai club-club a Queen Amina, irin su Maths Club, English Club, Jet Club, Arabic Club, Hausa Club, Science da sauran su. Na raba kafa na shiga Clubs har guda biyu, wato Arabiyya da English Clubs, Ummi ta shiga Jet don Allah bai halicce ta da kwakwalwar rike karatu ba, Jet kuma ana koyar da sana’o’in gida ga dalibai ne. Aunty Hauwa ba ta kulamu ba ta neman mu, ta ce don ita muka dawo Queen Amina, don haka ba ruwanta damu mu manta mun santa, ba abin da take kawo mana daga gidanta ta ce mu karata”. Nice Kanwarka. Fa’izah A.A Giwa. Yaya Aliyu ya ajiye takardar ya ce, “Good, very good, a tafawa Fa’iza, na ce a tafa mata!” Raf! Raf!! Raf!!! Suka hau tafi. Ya yin da Yaya Aliyu ya shiga manna min sababbin wa-zo-bia a goshina har guda shida. **** To haka rayuwarmu ta ci gaba da mikawa, tafiya ta yi tafiya. Shigarmu ajin karshe a sakandire na dauke da wasu muhimman al’amura da ba zan taba mantawa dasu ba cikin tarihin rayuwata. Don haka ya zama dole in farka shekarar baki dayanta. Alal hakika a lokacin na fara wadatuwa da abin da ake kira “Hankali” wanda yawan shekaru ke samar da shi. A lokacin ne kuma na fahimci mu’amalata da Yayana Aliyu ba komi ba ce illa SOYAYYAH! Soyayya ce muraran yake nuna min cikin ‘yan’uwana baki daya ba tare da shi kansa ya sani ba, a gaban kowa baya iya boye kulawarsa gare ni. Duk dangi babu wanda bai kwana da sanin matsanancin son da Yaya Aliyu yake min ba ko ba a furta ba. Sai dai da bakinsa bai taba ko da kuskuren gaya min da fatar bakinsa ba, sai dai actions and emotions dinsa su nuna. Ko da cikin hira ya yi subul da baka sai ya yi kokarin gyarawa ya mai da zancen ko subutar bakin sa (otherwise). Shekaru na goma sha takwas kenan, duk wani budurci ya tabbata gare ni. Hankali da nutsuwa sun wadace ni. A zahiri, tunda na soma hankalin nima nake so da kaunar Yaya Aliyu, so ba na wasa ba. Cikin kannena da tsararrakina da danginmu duka zancena daya ne (Yaya Aliyu). Shin don mene ne ba zan so Aliyu ba. Mutumin da ya kwashe shekaru goma sha daya yana kula dani, kulawar da iyayen da suka tsuguna suka haifeni basu yi min ita ba. Yana bauta mini, yana dadada mini, yana faranta mini. In har ban so Aliyu Na’ibi ba, wallahi ni butulu ce cikin butullun ababen halitta wanda zuciya ba ta aiki a jikinsu. Tun daga aji biyar na sakandire na dauki wasa na aje gefe, na bude file na sanya shi na adana a cikin akwatun karfe. Na yi “facing” karatuna yadda duk wani dalibi na kwarai ke yi da taimako da shawarwari da kulawa tattare da kwarin gwiwa irin na Yaya Aliyu. Allah ya hore min baiwar kirkira (fiction) na labarai masu ma’ana da fadakarwa ko kuma articles, ina ba da wa ana sanyawa a magazine din makaranta, fili guda aka ware min a mujallar makaranta mai suna ‘KNOWLEDGE IS LIGHT’ tare da Fa’izah Ahmad Abubakar (English Club). Nice kan gaba a fita muhawara (Quizz and Debate) din duk da za ayi da harsunan nan uku, Hausa, Turanci da Larabci. Da farko in na yi rubutun ‘yan ajinmu nake bai wa su karanta in ajiye, daga bawa shugaban clud dinmu ya karba ya duba sai ya mika shi ga hukumar makaranta. A lokacin an canza Yaya Hauwa daga principal an kawo Haj. Amina Atiku. Ita ta fara dubawa ta ce “Akwai ‘sense’ da ‘exceptional talent’ a ciki”. Rubutuna ya burge principal dinmu sosai, ya kuma bawa malamanmu da yawa mamaki da sha’awa. Wani novel ne na rubuta labarin wata Bafillatanar yarinya da wani dan makarantarsu da yake taimaka mata a fannin karatu, kasancewarta dakikiya har ta zamo zakakura sahun gaba a masu kokarin makarantar. Jin dadin hakan ne ya sa ta yi masa alkawarin za ta aure shi da zarar sun gama karatun sun samu aikin yi. Tsawon shekaru takwas tana dakon alkawarin. Bayan nan suka rabu kowanne ya koma wata duniya daban. Ga shi ta yi alkawarin ne a shekarun odolscence (goma sha uku ba ta gama mallakar hankalin kanta ba, ba ta san mene ne alkawari ba da muhimmancinsa balle SO, kauna da auren kansa). Rayuwa ta mika, bayan rabuwarsu ta ci gaba da jiransa. Katsam Barister Haseen Danbatta ya fado cikin rayuwarta, wanda ya fassara mata hakikanin mene ne so, ya karantar da ita fannoninsa from every angle, dadinsa, dacinsa, zakinsa da rashin dadinsa, bambancin so, kauna, kusanci, shakuwa da halacci. A zahiri wannan shine mutumin da zuciya da ruhinta ke so, suka kuma aminta da shi. Gangar jikinta da tsokar zuciyarta baki daya ke buri tun kafin bayyanarsa. Ga shi iyayenta sun takura mata da ta fidda mijin aure haka nan, shekaru takwas tana jiran wanda ta yiwa alkawari ya kuma yi mata halaccin da ba ta taba jin an yiwa diya mace ba. Abin da mai karanta labarin zai tambayi kansa shine, shin za ta ci gaba da jiran wanda ta yiwa alkawarin ko kuwa za ta watsar da halarcin da alkawarin ta auri wanda zuciyarta da rayuwarta ke so? Labari ne tsakanin soyayya da alkawari da na sanyawa suna ARE VOWS MEANT TO BE BROKEN? Ga shi na yi shine cikin sassaukan Turanci dai-dai karantawar dan sakandire, kuma dai-dai iyawata. Gyare-gyaren da malamar English Language dinmu ta yi min a ciki ba mai yawa bane, grammertical correction ne ta yi. Sai ka rantse da Allah Abubakar Gimba ne ya rubuta. Principal dinmu ta kirani ta ce za a kaddamar da littafin ranar da zamu gama makarantar, kuma za a buga shi a dinga saidawa a makarantun da ake yin Literature da kasuwanni don sauran al’umma masu karatun Novels don nishadi. In yaso sai makaranta ta rike ribar, amma duk abin da aka samu wajen kaddamarwar nawa ne. Da wannan daddadan labarin na tarbi Yaya Aliyu a wani visiting da ya zo mana. Na zaci zai yi farin ciki, amma sabani ga tunanina ya yi shiru bai ce komai ba. Na ce, “Baka ji dadi bane Yaya Aliyu? Na dauka abin kirki na yi? Na yi zaton wannan abin farin cikin mu ne duka?” Ya ce, “Ba wai ban ji dadi bane da hikimarki ba Fa’izah, amma ina son ki san wani abu guda daya, taura biyu ba ta tauno, tunda karatu kika zo yi ba rubutu ba ki mai da hankali ki yi karatun nan. In kin kammala kin san dai hajjah ba barinku zuwa jami’a za ta yi ba AURE za ta yi muku. Sai ki yi ta rubutun da za ki yi a gidan aurenki, ni kuma na dauki nauyin wallafawa”. Na ce, “Yaya Aliyu na san wannan, amma komai da lokacin da na ware mishi cikin al’amuran rayuwata. Wallahi bana rubutun da malami cikin ajinmu, ko ana karatu sai a karshen sati (week end) da (prefs), a sa’ilin da bani da ‘test’ ko ‘exams’ a kusa. Wato lokacin da ya kasance farko-farkon ‘term’. Inda bana karatu da ban kawo maka positions masu kyau ba ai”. Ya ce, “Shi kenan Fa’izah, ai ko lauya nan ya ganki ya barki wurin dadin baki da kawo hujja da persuation. Allah ya taimaka. All the best my sister. Cross word!” **** A shekarar aka nada wakilan malamai bayan tafiyar ‘yan aji shida, na yi mamaki matuka da aka kira ni Fa’izah Ahmad Bamalli Giwa a matsayin AMIRA! Aka kuma nada Ummi Gate Prefect. A hostel su Naja’atu Room-mates din mu ke yiwa Ummi dariya, domin ita Naja ta amshi dankwalin Head-Girl ne, ya yin da Haulatu Sani ta karbi Labour Prefect.. Ummi ta ce, “Aikin kawai, a rasa dankwalin da za a baiwa mutum sai na bakin kofa? Wani ya ce ina son mukami da za a hadani da gate?” Muka tuntsire mata da dariya. Haulatu ta ce, “Khadija Sabi’u ke ce baki sani ba, cika idonki ya sanya (Vice-Principal) baki wannan dankwalin, don kin san an ce alamar karfi na ga mai kiba, ta san za ki yi fada (Ummi na da jiki sosai) ga masu yin latti da ‘yan komawa hostel during school hours. Zaki cikawa dalibai masu latti ido da kwarjini. Yawancin mata masu jiki fada gare su”. Ummi ta yi tsaki ta ce, “A kan me za a bawa Fa’iza Ameerah? Wa ta fi tsoron Allah? Yarinya mai shegiyar tsiwar tsiya”. Naja ta ce, “Ai kuwa Fa’izah ta cancanci dankwalinta. Dalili; -Duk da ta fimu nutsuwa da kula da addini. -Zuwa jam’i a kan lokaci. -Tun zuwanta Sarauniya Amina kullum sai ta share masallaci. -Ita take riga kowa zuwa masallaci da asubah. -Ta fi kowa iya Larabci, ta fi kowa iya karatun Alkur’ani, ta fi kowa iya kira’a da Tajweed. In ba a baiwa Fa’iza Ahmad ‘Amira” a makarantar nan ba ki gaya min wa za a bawa?” Bakin Ummi ya mutu. Naja’atu ta ci gaba da cewa. “Duk fadin Sarauniya Amina babu mai tsantseni da addini irin Fa’izah”. Ummi ta ce, “Tana takurawa kanta ne kawai. Duk sanyi ba ta jin sa sai ta je masallaci da asuba. Da rana baka huta ba, da yamma baka huta ba haka dare. Ai ba zuwa masallaci yin sallah ne ke sanyawa Allah ya karbi sallarka ba”. Haulatu ta ce, “Kin yi kuskure Khadija, duk taku daya zuwa masallaci lada ne da babu wanda ya san adadinsa sai sarkin sarakunan dake ba da shi. Sannan sallar jam’i ladanta ya ninka ta mutum daya, ko taka ba ta yi kyau ba Ubangiji zai duba ta na kusa da kai ya baka ladan, ai ba ma za a kwatanta ba. Kiwa ce kawai take damunmu Allah ya yaye mana”. Ni dai ban tanka musu ba har suka gaji suka watse. Washe gari Yaya Hauwa ta zo har ajinmu ta shigo da kaya a leda da wasika, ta ce, “In bai wa Ummi daga Fa’iz, jiya su Hajjah suka dawo Ukrain, sauran kayan bai yiwuwa a kawo su makaranta, in mun koma gida ta gani”. Na ce, “Ayya! Yaya Hauwa da kin mika mata ajinsu don ni za ta bari da daukar kayan zuwa hostel”. Yaya Hauwa ta yi dariya ta ce, “Ahaf! Na manta fa kayan da suka fito hannun Fa’iz-Abubakar ne, abokin fadan Fa’izah. Ya kamata ki yafi dan ‘uwanki haka girma ya hau ku ku manta kuruciyar baya, haka nan ‘yan’uwa kuke”. Na yi dariyar yake kawai. A raina na ce, “Meye zai kankare kiyayyar Fa’iz a zuciyata? Wallahi babu shi Yaya Hauwa! Fa’iz bai so na, bai son mahaifiya ta, bai ganin girmanta balle darajarta, ya ya kuwa za ayi in taba shiri da shi a rayuwata??? Mu dai irin tamu ZUMUNTAR KENAN! Na shigo dakinmu a gajiye tikis na ajiye (school bag) na zauna gefen gadona ina sabule socks (safar) kafa ta, na fada bayi na dan watsa ruwan sanyi a jikina, kasancewar ana tsakiyar yanayin zafi karshen watan Yuli. Na fito na sanya riga da wando na yadin (house wear) dinmu na dan kishingida ina hutawa. Ummi ta shigo da gudu-gudu da kaya da takarda ta fado min a jiki tana shesshekar wata irin dariyar farin ciki, ta kara min takarda a fuska bayan ta zube kayan a gadona. Sassanyan kamshin da takardar ke yi na turaren ‘Philips Lumea’ na daxe ban ji kwantaccen kamshi irisa ba, tun can wani lokaci mai tsayi da ya shude. Na lumshe gajiyayyun idanuwana a hankali na janye hannunta da takardar daga fuskata na dube ta cikin mutuwar jiki da ta zuciya gaba daya. Ta kwanta kusa dani fuskarta dauke da annurin farin ciki da zumudi bayyanan ne, irin dai wanda kika sani a duk lokacin da wata zuciya ma’abociyar bege ta samu sakon masoyinta bayan lokaci mai tsaho. Haulatu da Naja suka shigo suka zazzauna a gadon Ummi dake fuskantar nawa, daidai lokacin da Ummi ke fitar da kayan ledar da ta shigo da ita da Yaya Hauwa ta bani in ba ta na ki karbowa. Littafin zane ne irin wanda su Ummi ke amfani dasu, alkaluman zane, penti kala-kala ‘yan waje da agogon hannu (hand-wrist watch) samfurin (L’OREAL) ruwan silver da zobe shima na silver dandasheshe mai kyau. Ummi ta sanya a yatsanta babban ya yi mata cif duk yadda ta juya hannunta sai ‘dot’ din zoben ya yi walainiya. Ta rungume su Haulatu tana dariyar dadi gani kashe ni. Haulatu ta ce, “Hala sakon Yaya Fa’izu ne da kullum ake bamu labari mai cin zalin Fa’izah?” Ummi murna take, bakin ya gaza rufo, ta zaro hotuna cikiin ambulan din wasikar jikinta na rawa da karkarwa ta bude suka fara gani. Kyakkyawa Fa’iz Giwa ne sanye cikin jibgegiyar rigar leda mai kare sanyi wadda ta sauko har gkwiwarsa, yana tsaye cikin dusar kankara baka ganin komai jikinsa sai fuskarsa, domin hatta hannayensa cikin bakaken safar hannu suke. Hoto na biyu sanye yake cikin uniform na masu koyon tukin jirgin sama cikin karamin jirgi (jet) da wasu abokan karatunshi farare da bakake. Fuskarshi ta fi fitowa a wannan din sosai. ‘Yammatan uku suka ci gaba da kallon hotunan guda biyu suna kada kai kamar kadangaru, da kyar Naja’atu ta iya bude baki ta ce, “Khadija Yaya Fa’iz din ne?” Ummi ta rungume hotuna cikin lumshe ido ta ce, “Yes, Fa’iz Bamalli kenan Naja’atu. Yau kinga yayanmu Fa’iz, tabbas Ya Fa’iz ne. Ni kaina ya canza min sosai fiye da yadda na san shi. Ya Fa’iz ya kara kyau kwarai, ya yi kiba da haske, ya kuma kara girma cikin shekaru uku kacal, kai abin da mamaki”. Haulatu ta ce, “Amman yana da kyau fiye da ku duka, ko in ce fiye da dukkan zuri’ar A.B da na sani. Na so a ce yadda yake da kyau yana da mahadin sa wato kirki, amma kyau ba hali kyawun dan maciji ne Khadija”. (Can da jimawa Ummi ta sha basu labari na da Fa’iz tun daga kuruciya da rashin kirkinsa garemu). Ummi ta yi murmushi kawai, ta ce, “Haule yadda kika ji labarin Yaya Fa’iz da Fa’izah ne kurum ya sanya kika fassara shi da haka, amma yana da kirki in his own unique way! Da za ki ganshi a zahiri rantsewa za ki yi ba zai ko kusa da taba iya aikata abin da yake aikatawa ba. Ni kadai na fahimci Fa’iz ciki da waje, zan iya rantsewa babu wanda ya kai ni sanin Ya Fa’iz a gidanmu, akwai dalilin da yasa Fa’iz yake kyarar Fa’iza wanda babu wanda ya sani sai shi daya sai Allah da ya halicce mu. Amma wallahi ba gundarin halinshi kenan ba, koma da halinshi ne ni Ummi Khadija INA SON SHI HAKA! Zan iya jure kowane irin halinshi idan na yi sa’ar samun shi a matsayin miji. Ina son sa da yawa Haulatu, kamar yadda na fahimci shima yana sona kawai ba zai furta bane ko ya nuna kamar yadda Yaya Aliyu ke nuna ma Fa’izah. Ban san ina son shi ba Haule sai ranar da zai tafi”. Ta yi shiru tana kallon yatsar kafarta kafin ta yi murmushi a hankali ta ce, “Wannan ya faru ne a dalilin babu auren na-gani-ina so cikin zuri’armu da family dinmu duka, sama da komai Fa’iz daban ne wajen halayya da dabi’a. Wanda zai ce miki ya san dukkan halinshi wallah ya fadi karya, saboda kullum sabon hali yake sakewa tamkar wahainiya mai canza launi daga wannan zuwa wannan. Irin wadannan mutanen ma’abota kaskantar da kansu ga abin da zuciyarsu ke matukar so tsiraru ne a cikin al’umma!” Ta girgiza kai. Su kuma kamar masu daukar darasin tarihi, sai gyada kai suke, don haushi kamar na hada kawunan nasu su duka ukun na gwara, da suka tsaya suna sauraren shirmen Ummi da ba ta san inda ke mata ciwo ba. Ta ci gaba da cewa, “Ni dai ku tayani addu’a Allah yasa Hajjah ta hadamu ni da Fa’iz, don in ba Yaya Fa’iz ta bani ba? Bana jin zan iya aure a rayuwata. Na gwammace in mutu haka nan ban yi aure ba. Zan jirayi Fa’iz ko da shekaru nawa zai yi bai dawo daga Ukrain ba in dai har Hajjah ba ta yi tunanin aurar dani ga wanin shi ba”. A hankali na juyo da kaina sashen da su Ummi ke zaune, na dube ta tsaf. Shin mafarki nake ko ko a farke (idona biyu)? UMMI NA SON FA’IZ, FA’EEZ NA SON UMMI? “Wannan haka yake”. Daga can cikin wani sako na kwakwalwata aka bani amsar. Tabbas biri ya yi kama da mutum. Yawan zancen Fa’iz da Ummi ke yi har ya so ya baci. Bana jin akwai ranar Allah da za ta fito ta fadi, bakin Ummi bai ambaci kalmar ‘YA FA’IZ’ ba. Na kuma sha jin an ce ‘adadin soyayyarka da abu adadin yawan ambatonsa a bakinka.....!; “Amman Ummi kin cika banza, shashasha, dabba, mahaukaciya wadda ba ta san ciwon kanta ba.......!” Ban san sanda kalaman suka yo ambaliya daga bakina ba. Kafin hawaye su shimfido a kundukukina. Na soma shesshekar kuka sosai. Su duka suka dube ni a razane. Na mike tsaye na shiga nuna Ummi da babban yatsana, idona a rufe bana ko ganin abin da yake gabana, na surfeta tas da zagin da ba ta taba tsammani daga gare ni ba. A karshe na kare zancena da cewa, ......”Ummi in har kin yarda ki auri Fa’iz, ki sani karshen zumuncina dake ya zo, ko a hanya muka gamu babu gaisuwa tsakaninmu. Fa’iz kike so Ummi? Kyawun fuska ne zai rude ki ki manta da waye Fa’iz? Fa’iz Bamalli? Fa’izun gidan Babllan Kaduna ne fa, kyawun fuska zai rude ki? Mugu azzalumi, makaryaci, masharranci, mugun da bai san girman zumunci da girman iyaye ba. Mutumin da ya nuna mana kyara da tsangwama irin wanda wani dan’uwa bai taba nunawa wani dan’uwansa ba, Fa’iz HAFIZIN HAJJAH shi kike so Ummi?’ Muryata har dakushewa ta yi a wannan lokacin. Na dube ta da dukkan idanuna na ce, “Ummi kin manta baya? Kin manta duk abubuwan mugunta da tsanar da Ya Fa’iz yai mana? Shin farar fata koko zuwa Rasha ya rudeki ga son Fa’iz Ummi? Ko kuwa tukin jirgi da yake koyo.....?” A nan ne ran Ummi ya yi mugun baci, domin da kallona kawai take kamar ta ga mahaukaciya. Ta ce, “Ke Fa’izah dakata, cin mutuncin naki ya isa haka, ya ishe ki kin ji ko? Kada ki kara don kuwa ni ba ‘yar cikinki ba ce da za ki sani gaba kina min wannan hayagagar ba tsoronki nake ba. Da kin ki da kin so Fa’iz dan’uwanmu ne jininmu ne, ko me Fa’iz ya yi miki ya ci a ce kin manta haka nan as time goes on.... Haka kike da riko da gaba wanda ya wuce na musulunci? Wai ke baki san kuruciya bane? Ke abu baya taba zuwa ya wuce a wurinki? Fa’izah ina son Fa’iz fisabilillahi na fada a yau na kara da babbar murya I LOVE FA’EEZ! Kuma insha Allahu shine mijina, ki yi duk abin da za ki yi, kada Allah yasa ki kulanin, kada Allah yasa mu yi zumuncin. In na auri Fa’iz don Allah kada ki zo gidana, in na haihu da Ya Fa’iz don Allah kada ki zo barka, kada kuma ki kawo riga ki ce a sawa dan ko atamfa in yi zanin goyo! In ce dai shine zumuncin? Ni babu abin da Fa’iz ya yi min baya ga yanke gashi wanda daga baya ya zo ya zame min alkairi, domin ya zamo silar da na yi gashi irin wanda ban taba zaton zan yi ba (Fa’iz ya taba yankewa Ummi duka jelunan kitsonta da ya kamata a dakinsa ta dauki hotonsa ta boye cikin hijabi za ta fita). Wata mugunta ko cin mutunci ko wulakanci kika ce ke ya shafa, matsalarku ne. Tsakanina da Fa’iz daban, tsakaninki da Fa’iz daban, ban ga dalilin da zai hada ki yi mana jimilla cikin al’amarin ba. Don haka ni a wajena komai ya wuce lafiya-lafiya, lafiyar Allah muka rabu ni da Ya Fa’iz cike da begen juna da fahimtar juna. Insha Allah sai kin goya ‘ya’yana da Fa’iz, kin ji ko Fa’izah?” Ta fada cikin karaji da zazzaro idanuwa, duka a lokaci daya tamkar zararriya, ta daga hoton Fa’iz ta kai bakinta ta sumbata, ta kuma rungume a kirjinta ta ce, “Fa’izah, kin ce farar fata da kyawun Fa’iz ya rude ni ga son shi? Shin kin manta nima fara ce ba baka kamar ki ba? Kyawu na Bamalli duk ina da shi? Kina kuma tsammanin zuwan Ya Fa’iz Ukrain da tukin jirgi ne ya karkato zuciyata ga kaunarshi? Kin yi kuskure da wannan tunanin naki mara tushe Fa’izah. Bari in gaya miki sirrina da ko uwata da shi kansa Ya Fa’iz basu sani ba. Na fara son Fa’iz ne daga ranar da ya dauko ni a Gusau ya taho ya barki......” Wata irin sarawa kaina ya yi na rasa me zan cewa Ummi don bakin ciki. Da dai a gida ne ba makaranta ba daura hannuwa zan yi a ka in fasa mata kururuwa ko in rufe ta da duka. Tunda babu damar yin ko daya daga ciki sai na ce, “Kaico! Kin cuci kanki Ummi tunda kika sanyawa zuciyarki soyayyar wanda bai cancanta ba, bai san mutuncin dan Adam ba balle dan’uwansa na jini. Na tausaya miki Ummi, muddin kika yarda kika auri wannan mugun mutumin na rantse sunanki sorry....” Ta katse ni da cewa, “Ki ce ma sunana sarai asarar duniya ba sorry ba, ‘to be frank’ yanzu na saka danba a son FA’IZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA.....!” Na ce, “Kin bata wayonki Ummi, wallahi kika aure shi za ki kwashi kashinki a hannu. Na rantse mai hali.......” “Baya fasa halinsa fa Fa’izah!” Ta karasa tana min dariyar tura haushi. Ta kuwa tura din. Ta ci gaba da cewa, “A ganina wannan ba damuwar ki ba ce tunda dai ba ke za ki zauna min dashi ba, bai shafe ki ba kowacce irin rayuwa zamu yi ni da Ya Fa’iz, tunda abin sa-kai-ne. Ina SON SHI HAKA! Shine kadai ya tara dukkan abubuwan da nake so ga Da namiji, har ma ya zarta. Kafin a samu namijin da ya tara sura da ‘attributes’ din duk da ‘ya mace ke so irin Fa’iz za a jima Fa’izah. Don haka Fa’izah a yau ina mai farin cikin shaida miki cewa, ina son FA’IZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA!” Sai na ce, “Allah ya ganar dake Ummi. Kin riga kin yi nisa ba za ki ji kiran ba. Allah ya shirye ki, ya ganar dake makiyinka baya taba rikidewa ya dawo masoyinka, ‘no matter what.... sai in ya ga kiyayyar tasa ba mai ci ba ce.....” “wai ke sai kira kike FA’IZ MAKIYI! To makiyin wa? Ke ko mu? A lokuta da dama Yaya Aliyu kan ce bakya magana sai mai ma’ana da hikima a ciki, amma ga shi ni yanzu duk kin cika ni da rubbish (shirme). Wallahi duk kin isheni da surutu mara ma’ana. To wannan shirmen da kike shi zai sanya in tsani Fa’izun nima?” Ta yi dariya ta shiga tattare kayan ta cikin ledar da aka kawo su. Tabbas da da ne ba yanzu ba da GIRMA da HANKALI suka zo ba, babu abin da zai hanani rufe Ummi da dan iskan duka, yakushi da cizo irin wanda muka saba da zarar mun samu sabanin ra’ayi ko don in huce bakin ciki da takaicin da ta kunsa mini, amma ina! Girma ya zo!! In ma mun yi ba zai mana kyau ba!!! Sai na kyale ta na kwanta a gado na kama kuka mara sauti. Ni babban bakin cikina da muka yi a gaban su Haulatu muka farke sirrin gidanmu a gabansu, shin da me za su fassaramu ba dabbobi ba? Wasikar da Fa’iz ya aiko abin da ya rubuta a ciki kawai “Ga Hankicina ki bawa Fa’izah, sauran kayan naku ne ke da Zanirah”. Wannan wasika ta bai wa su Ummi da su Naja dariya. Wato su tsaraba wadda za ta amfane su, Fa’izah da ba a so ‘HANKICI! Suka kyalkyale da dariya. Haule ta ce, “Kai zan so in ga Fa’iz dinnan face to face, am sure he will be vey funny”. Ummi ta harareta ta ce, “Me kika ce? Ki ganshi ki yi mai uwar me?” Suka kara kyalkyalewa da dariya. Naja ta ce, “Sorry Khadijan Fa’iz, ai mu Fa’iz ya wuce da ajinmu ba cewa zamu yi muna so ba. Wutsiyar rakumi ta yi nesa da kasa!” **** Tun daga ranar na fita harkar Ummi, na ma tattara kayana na koma hostel din su Naja da muka fi dasawa. Ummi ba ta gaya min Fa’iz ya ba ta hankici ta bani ba, kawai na tsinci kyakkyawan farin hankici cikin kayana mai dauke da kalmomin Larabci guda (7) ‘AHUBBIK’. Na kai hankicin karan hancina na sunsuna, sassanyan kamshin turare dan gidan (Philips Lumea) da hakincin ke yi ya haifar da wani takaitaccen nishadi a zuciyata, ya gusar da duk wani bacin rai na Ummi da nake fama da shi a cikin ranakun da bama ga maciji. Haka nan Allah ya sanya mani kaunar dan kyakkyawan hankicin a raina. Sai dai kamshin Philips Lumea da hankicin ke yi na kan so in san inda na san shi amma Allah bai bani ikon tunawa ba. Na tura shi cikin jakar littattafaina ko cigiya ban yi ba. A raina na ce “Ina zaune ai ya zo ya tadda ni. In mai shi ta yi cigiya na ba ta”. Kullum bana iya barci ba tare da na shaki kamshin daddadan hankicin nan ba, haka in na fito aji ana rana, na kan rufa shi ne a fuskata zuwa hostel, bana ko tsoron mai shi ta gani. Kuma abin mamaki har kwanaki suka ja, aka debi wata kamshin da hankicin nan ke yi bai gushe ba. Wannan ya tabbatar min da ba karamin turare ne a jikinsa ba. Duk sanda zan wanke uniform sai na wanke shi, amma babu abin da ya ragu na daga kamshinsa kullum kamar ina kara fesa masa turare dan gidan (Philips Lumea) ne. A karshen watan Yaya Hauwa ta zo ganinmu, ta bani letter daga Yaya Aliyu, kuma wai lallai-lallai in rubuta amsa in ba ta a take. Don a satin ya zo gidanta ya fi a kirga yana tambayar amsar wasikar tana cewa ba ta zo ba, yana ta yi mata mita. Na yi dariya na ce, “Yaya Hauwa kyale Yaya Aliyu kawai, rigimar shi yawa gare ta. Yanzu haka duk zancen in bar rubutu in yi karatu ne bai san tuntuni na ajiye shi a gefe ba”. Ta ce, “Ah toh! Sako-makoko na dai isar don haka ragowar can ta matse muku kun fi kusa, wai harshe da hakori. Ban tambaye ki me ke cikin wasikarku ba”. Na rufe fuska da tafukana ina dariya cike da jin kunya. Ban bude wasikar Yaya Aliyu ba sai a washegarin talata da daddare bayan na gama komi da ya zamo min al’ada kafin kwanciyar barci. Na saka (nighties) na saki net (gidan sauro) na shige ciki. Sannan na bude wasikar Aliyu; “A gida, Giwa- Fa’izah, ko kin san mene ne abin da na dade ina cewa ba ki yi girman da za ki fahimta ba? To ba wani abu bane strange. Abu ne da ya zamo (known) ga kowa a Giwa, Zaria, Kano da Kaduna. Idan har zuwa yanzu shekaru goma sha bakwai baki yi kwakwalwar da za ki fahimtar ba sai in ce zan yi A BARI YA HUCE..... Yayan is in love! Fa’izah Aliyu is in love!! Please save a soul..... ki taimaki “tuzurun” yayan ki ki zama zabin Hajjah gare shi nan da watanni uku wato bayan kammala jarrabawarku ta karshe. Hajjah ta yi rantsuwa nan da watanni uku ko na shirya ko ban shirya ba za a daura min aure, ta gaji da karatun da ba shi da karshe. Don haka ne na ga tunda wuri gara mu fito fili mu bayyana kanmu maimakon hannunka mai sanda. Babu zancen fahimtar juna sai cika burin zuciyoyin da suka dade suna ragaita. -Aliyu-Na’ibi. Wata irin murna marar misali na shiga yi tare da dariya-dariya da ni kaina ban san irinta ba. Abin da kunnuwana suka dade suna jiran ji daga bakin Yaya Aliyu. Gaskiyar Mama Asma’u ne da ta ce, “Sannu-sannu ba ta hana zuwa, sai dai a dade ba a je ba”. Sai na kwanta a rigingine zuciyata da ruhi cike taf da begen Aliyu-Haidar. Kwakwalwata ta shiga wassafo min irin kyakkyawar rayuwar da zamu shimfida ni da Yayana Aliyu, irin kyawawan yaran da zamu haifa kasancewar Aliyu fari tas Fa’izah choculate colour. Na tabbata za suyi kyau, kyau mai suna kyau da babu irinsa cikin zuri’ar Abubakar Bamalli Giwa. Watanni uku kenan da kammala masters din Yaya Aliyu a jami’ar Legas a kan (Agricultural Engineering), cikin lokacin kuma ya samu aiki da ma’aikatar gonaki ta kasa. Sun aje shi reshen jihar Legas matsayin mataimakin M.D. Gida cikin lekki da motar shiga ta zamani da matasa masu matakin rayuwa dai-dai da tashi suke hawa. **** Shin wace irin amsa zan rubutawa Yaya Aliyu ne? Wallahi ban sani ba. Na shafa ko ina ban ji amsar da ta dace cikin kwakwalwata ba saboda kunya. Kuma wadda zan saka ta yi min gayyar ta watse (Khadija-Ummi) anyi ta ba dadi. Ina kuma ganin faduwa ce babba gareni in je ni neman sulhu. Sai dai in mu koma gida a haka amma ba zan ba da kaina ba ta kara kular dani a banza, don da alama babu sauran mutunci cikin al’amarinta in dai a kan wannan dan’uwan nata ne Musa a fuska, Fir’auna a zuci. A kullum sai na karanta wasikar Yaya Aliyu a kalla sau cikin carbi. Aike na duniya Yayan ya yi in ba da amsa na ki, don tsakanina da Allah da gasken ban san me zan rubuta mishi ba. Don haka ne wai na bari ayi hutu tunda ya matso in yaso sai mu rubuta ni da Zanirah. Yau saura sati biyu hutu Yaya Hauwa ta shigo makarantar wajen kawayenta malaman makarantar. Bayan ta gama abin da ya kawo ta, ta yi kirana staff office ta ce, “Fa’izah na gaji! Zaryar Aliyu gidana ta ishe ni, wai amsar me za ki ba shi ne? Ki yiwa Allah ki bani takardar nan in ba shi in huta ya sarara mini”. Na ce, “Yaya Hawwa ki kyale Yaya Aliyu don Allah sai mun zo gida. Saura kwana goma sha hudu ya rage”. Ta ce, “Ai shi kenan, ni tausayin shi nake ji wallahi. Ya damu fiye da zaton ki, wayar safe daban ta dare daban, ga ayyuka masu tsauri a gabanshi. Yarinya karama sai tamaula kike da ‘yan maza, ki ji tsoron gamuwarki da Allah Fa’izah ki tausayawa Da na”. Na kyalkyale da dariya na ce, “Yaya ni ba ‘yarki ba ce sai Yaya Aliyu kadai?” Ta ce, “A’a, ni na fara cewa haka? Duka daya kuke”. A ranar ne kuma hukumar makaranta ta sanar cewa, babu ‘yan set dinmu a masu zuwa hutu saboda karatun bita na jarrabawar karshe. Sai dai wadanda ke cikin Kaduna ne kawai za su fita su dawo sati daya jal. Muka debi kayan sawa uku cikin jaka muka yi gidan Yaya Hauwa. Tsakanina da Ummi sai harara. Kwanana daya gidan yaya Hauwa gidansu Ummi kenan, duk na kasa sakewa sakamakon rashin sabo da gabar da muka tsira a junanmu. Sai dai duk iyaka kokarina na yi Yaya Hauwa ba ta gane ba, don ko da za ta ji din na tabbata ni za a daurawa rashin gaskiya duk da nice mai gaskiyar, da rashin dadin zuciya ya isheni na dau wanka na sha atamfa super da mayafi, na yiwa Yaya Hauwa sallama da niyyar za ni gidan Baban Kaduna Jabi Road. Ta ce, “To dai kada ki sake ki je Giwa, kin san dai dokar makarantar nan, iyakacinku cikin gari. Ga ummi ta shiga wanka ki tsaya ta fito ku tafi tare mana”. Na ce, “Ai kwana zan yi, kin san kuma Ummi ba za ta yarda ta kwana gidan Baban Kaduna ba saboda abokin fadanta (Junior)”. Ta yi dariya ta ce, “Yiwa Idi direba magana ya kai ki yana nan cikin lambu wajen tsintsaye yana basu abinci”. Shigarmu harabar gidan ke da wuya idona ya kyallo mani motar Yaya Aliyu fake a harabar adana motoci. Gabana ya fadi, tabbas na yiwa Yaya Aliyu laifi babba kuwa, na yiwa Aliyu Haidar babban laifin da ban san (punishment) din da zan fuskanta ba, bani kuma da uzuri ko hujjar kare kaina. Na gyara murya zan ce da Malam Idi mu koma na hango fitowarsu shi da Baban Kaduna yana rike da brief case din shi. Dole na fito, duk gwiwoyina sunyi sanyi kalau. A dai-dai motocin Baba dake jere a cikin rumfar adana motoci na tsugunna har kasa na gaida Baba. Kallon da Yaya Aliyu ke min a yau ya kara sanya min mutuwar jiki da sanyin gwiwa har muryata karkarwa take ina gai da Baban. Ya ce, “Faduwa ta zo daidai da zama, yanzu Mamanku ke cikiyarku game da shirin da za ku soma na bikin da za ku sha nan da watanni uku. Ina kika baro Ummin?” Na ce, “Ummi na gidan Yaya Hauwa. Biki kuma Baba? Na wa?” Ya yi dariya ya ce, “Na Hassanar ku”. Ido warwaje na ce, “Zanirah?” Dariya ya yi, “It sounds like a film ko (kamar a shirin fim), to ya za a yi? Hajjah ta tada hankalinta aure za ta yiwa Zanirah, kinga kuwa babu mai ta cewa. Ko akwai?” Da sauri na shiga girgiza kai, na ce, “Babu kam, babu Baba”. Na mike da sassarfa zan shige Baba ya ce, “Baki ga Yayanki bane babu gaisuwa?” Yaya Aliyu ya ce, “Kyale ta Baba ai ta je kwaleji ta waye ne, kada ki sake ki bar gidan nan sai mun dawo Giwa yanzun nan”. A hankali na cira kai na dubi Yaya Aliyu, sanye yake da shadda (Hilton) ruwan toka mai gautsi. Sai sheki take cikin hantsin na safiyar Asabar. Ya rame sosai ya dan yi duhu, in ban yi kuskure ba sai in ce ko (ulcer) ce ta tashi ta kwantar da shi muna makaranta. Dara-daran idanunshi sun fada sun yi ciki sun yi ja ainun. Muka yiwa juna wani irin kallo na sakan biyu a hankali na ce, “Ina yini?” Ban damu da ya amsa ko bai amsa ba na wuce da sauri, har ina tuntube da kofar shigewar. Gaba daya yara suka diba ga Fa’iza, ga Yaya Fa’izah. Daya bayan daya nake daga su tika-tika dasu ina direwa. Na tambayi Junior Mama ita da waye? Ya ce ita da Yaya Zanirah ne sun zo su tare da Yaya Aliyu tana ta kuka wai za a yi mata aure. Na yi sallama a falon, Mama ce ta amsa. Zanirah na hango ta hade kai da gwiwa can a kusurwar falon tana rusar kuka. Na ce, “Wai Mama da gaske?” Ta ce, “Ni gara da kika zo, na kasa ma Zanirah, ni yanzu da ta zo ta sani a gaba tana rusa min kuka me zan yi a kai don Allah? Sanin kanku ne in Hajjah ta yi hukunci Babanninku basa musu. Wannan kukan duk aikin banza ne Zanirah kike yi ba zai sa ba, ba kuma zai hana ba”. Cikin kuka Zanirah ta ce, “To waye Mama? Waye mijin? An ce wa Hajjah yanzu ma irin zamaninku ne da ake irin wannan auren a kwashe lafiya? Ni ba aure nake ki ba, karewa ma ina da wanda nake so. Ta yi hakuri mana mu kammala makaranta zan kawo mata mijin”. Ni sai Zanirah ma ta bani dariya, don ni dai tun tasowar mu ban santa da wani saurayi ba. Na samu wuri gefen Mama na zauna na ce, “Wallahi Mama ni dama na san dole ne tsayin Zanirah ya dami Hajjah, duba ki ga duk ta fimu cika ido ga tsayi, Hajjah na yawan cewa “doguwa hankalinki a gwiwa, ni kar ki fado min a ka”. Mama ta yi dariya Zanirah ta zabga min harara. Mama ta ce, “Daman Zanirah ai ta girmeku, shekaru biyu ta baki kwarara, ke kuma kika bawa Ummi watanni biyar. Ni kam ban ga laifin Hajjah ba don an yiwa Zanirah aure yanzu, shekarunta goma sha tara ris, sai dai tunanin wanda ta baiwa auren. Na yi iyaka tunanina amma hankalina bai bani ba. Baban ku ma ya yi tambayar duniyar nan amma ta kafe sai ana saura kwana uku daurin auren sannan kowa zai ji”. Na ce, “Kai wannan tsohuwa da rigima take, ke Zanirah to mene ne abin kuka? Muma muna tafe, kin sani dai ko ba yanzu ba mawuyaci ne Hajjah ta kyale ki zuwa jami’a da shekaru kusa da ashirin, kai Hajjah ta yi dai-dai....” Zanirah ta taso kamar za ta make ni, ko me ta tuna? Sai ta juya ta yi bed room din Mama tana sharbar kuka wiwi kamar ranta zai fita. Ni dai Allah-Allah nake karfe uku ta yi na bar gidan zuwa Zaria kafin Yaya Aliyu ya dawo ya taddani, duk da Aunty Hauwa ta ce in bi umarnin makaranta duka gidajen biyu ba zan iya zama ba, can Ummi mun yi fada, nan Yaya Aliyu zai tirke ni. Ya kasa ganewa cewa nauyinsa da girmansa da nake gani ba zai barni in ba shi amsar wasikarsa ba. Na yi kokarin hakan amma na kasa. Karfe ukun na yi na dauki jakata na yafa mayafi, na yiwa Mama sallama na roke ta tasa Malam Garba ya kai ni Zaria. Zanirah ma ta dauko kayanta ta ce, ba za ta kwana a gidan ba ta fasa tunda Mama ta goyi bayan ayi mata aure da mijin da ba ta sani ba. Malam Garba ya ja mota, bai tsaya a ko ina ba sai a kofar gidanmu, yana aje mu ya juyo Kaduna. ‘Yan kannena kam sun yi farin ciki da ganina, suka shiga gyara mana daki. Daga momi har Baba babu wanda ya dawo aiki, Abdallah mai bi mani ya girma, yanzu yana aji uku na sakandire. Yayin da Walida ke aji shidan firamare ‘yar shekaru goma, Kausar na aji hudu, sai auta Walid yana Nursery. Yaran gidanmu akwai nutsuwa da kyakkyawar tarbiyya, suna masifar son junansu, ko ina suna tare. Idan Momi da Baba sun tafi aiki su kulle kansu a gida suyi ta karatu, in sun gaji suyi game suyi kallo, ga son baki, kula da sallah da son zuwa Islamiyya nan cikin (Area One). Walida ke fiddo ire-iren aiken da Yaya Fa’iz ke musu na kayan wasa masu aiki da batir da jirage masu tashi sama sosai na Abdallah masu aiki da (remote control). Zanirah ce kawai ta nuna sha’awarta ni ido kawai na bisu da shi. Momi kan yi abinci ne mai yawa ta cika musu cooler, don haka mun samu abinci mai rai da motsi, mun ci mun yi kat! Mun yi wanka ina shafa a gaban madubi daure da faffadan tawul, ya yin da Zanirah ke gefe ta mike kafafunta cikin ‘sofa’ sanye da doguwar riga a jikinta, ta zuba min ido kurum. Walida ta kyalkyale da dariya ta ce, “Aunty Fa’izah Yaya Zanirah fa kallon ki fa take yi”. Na dan juyo muka yi ido hudu da Zanirah, na ce, “Ya dai amarsu? Ko ta samu ne?” Ta tabe baki kamar taliya ta ce, “Amma kuwa wannan ango ya debo da zafi. Imagine Fa’izah yadda za ki yi zaman aure da wani alhalin zuciyarki, ruhi da gangar jikinki duka suna ga waninsa”. Na dube ta na ‘yan sakanni, na ce, “Hakuri da juriya ya zama dole gareki Zanirah, rashin so daga mace na dan lokaci ne, na namiji shine ke lasting”. Ta ce, “Ta ya ya zan yarda cewa mutumin da Hajjah ta bada ni gare shi yana sona?” Na ce, “Zanirah cewa nake Maman Kaduna da Baban Kaduna, Baba Na’ibi da Maman Yaya Aliyu, Yaya Hauwa da mijinta, su Baba Barau da Yaya Ibrahim, Sadi, Salisu, Sani, Aunty Rabi da Yaya Muftahu kadai sun ishe ki ishara. Zanirah babu yadda za ayi HAJJAH HADIZA GIWA ta hada aure ayi dana saninsa ko ayi dakacen wanzuwarsa, ko kuma ya zama mara dadi tsakanin ma’auratan. Sai dai ma daga baya a zo ana gode mata. Saboda haka ki kwantar da hankalinki ( a ganina fa) Hajjah ba za ta kai ki inda za ki wulakanta ko ki tozarta ba. Insha Allahu babu komi cikin wannan auren face alkhairi. Ko ni da nake ganin zamu yi auren “So” da Yaya Aliyu ina gudun kada in zo auren bai mani dadi ba kamar na sauran zuri’ar A.B ba. Don haka har yanzu na kasa bawa Yaya Aliyu amsa”. Ban juyo ba ina kallon ceiling ne dalili kenan da ban ga halin da kalamaina suka jefa ‘yar’uwata Zanirah ba. Ashe Zanirah fiddo ido ta yi warwaje, dafe kirji tare da bude baki duka a lokaci daya. Idanuwanta suka jirkice cikin dan lokaci tare da wuntsilowa daga cikin ‘sofa’. Sai dai ‘yar’uwa ta gaskiya wadda ZUMUNCHIN har cikin zuciyarta yake ta yi kokarin controlling kanta ta hanyar komawa cikin sofa ta kalmashe ta runtse ido, tare da dafe kanta dake neman rabewa gida biyu saboda sarawa da juyawar bazata da ya yi mata. Cikin sassanyar murya mai dauke da yankewar buri na rayuwa ta ce, “Wane Aliyu Fa’izah?” Na mai da hannuwana baya na sarkesu na doshi taga a hankali na tsaya ina kallon waje ta tagar ina murmushi, na ce, “Aliyu nawa muke da shi cikin A.B. Zanirah? Baya ga Aliyu Haydar Na’ibi A.B Giwa?” Na juyo gaba daya na fuskanceta ba tare da na gane rikicewa da gigicewar da Zanirah ta yi ba na isa ga jakata na zuge na fiddo wasikar Aliyu na mika mata ina fadin “Ban iya soyayya ba Zanirah balle kalamanta masu sanyi. Ban san soyayya ba Zanirah, ban san kalamanta ba. Na shafa duka duniyar kwakwalwata in nemo kalaman da suka fi kowanne dadi ga masoyi a duniya in rubutawa Yaya Aliyu na rasa baya ga (I love you too). Taimake ni ‘yar’uwa ki rubutawa Yaya Aliyu kalaman soyayyar da suka fi kowanne dadi da gardi a duniya ko da layi biyu ne kacal, ya san cewa ‘I do care for him too much’ ya san cewa ruhi, kalbi da gangar jikin Fa’izah gaba daya yana kaunar Yayanta Aliyu!” Hawaye wani na bin wani sharaf-sharaf a fuskar Zanirah, a ya yin da take karanta wasikar Aliyu ga Fa’izah, tasa gefen rigarta ta share da sauri ta yagi wani gefe a karshen takardar ta ce, “Bari in rubuta maki amsa Fa’izah, ko dama can wauta ta hana ki gane Yaya Aliyu na mutuwar son ki, amma kowa ya sani. Ki rike Aliyu da kyau, ki yi mai rikon magnet. Yaya Aliyu ba irin mazan da ake yiwa rikon sakaka bane. He has all the qualities and all the attribute to be love upon. Ina da kyakkyawan zaton cewa, muddin Yaya Aliyu ya zamo miji a gare ki babu ke babu ganin wulakancin namiji da ‘yan’uwa mata ke suffering, saboda Yaya Aliyu na daban ne. Babu ke babu kalmar nan da mata suke kira kamar ayar Alkur’ani wai “Duk wadda ta ce namiji uba ne.....” Domin Aliyu uba ne, uwa ne, aboki ne, dan’uwa ne, miji ne abin so da duk wata diya mace za ta yiwa kanta burin samu”. Sakin baki na yi da kunne duka ina sauraron Zanirah. Me ya kawo duka wannan dogon sharhin? Ya ya aka yi muryarta ta canza haka kamar ba muryar Zanirar dana kwana na tashi da sani ba, tana magana cikin fidda rai da yankewar buri? Na ce, “Za ki rubuta min amsar ne ko dauko diro zan yi in aje miki ki hau ki ci gaba da fadin how lucky I’m for having Aliyu as a husband?” Ta yi murmushi ta ce, “Zan rubuta mana sister nah”. Ta kammala cikin sakan biyu. Ta taso har inda nake tsaye jikin taga ta bani, ta juya ta shige toilet. “If all my body is full of mouth, it’s not enough to expess the kind of love I had on you Yaya Aliyu”. Na yi murmushi na rungume takardar ina fadi a cikin daga murya, “Na gode Zanirah.....” “Da ta yi miki me?” Gaba daya muka duba kofa ni da Walida, Yaya Aliyu ne! Walida ta bude baki tana dariya, ni kuma na yi wuf! Na shige uwar daki cike da takaicin a yanayin sutturar da ya same ni na sanyo riga da zani da dankwali. Ina kokarin sanya dan kunne ya tsaya a bakin kofar sai na samu kaina da kasa hada ido da Yaya Aliyu a yau, sai sunkuyar da kai nake. Ya yi dariya ya juya yana fadin ina jiranki main falo. Da ya fito dai-dai toilet sai na jiyo shesshekar kuka. La shakka Zanira ce take kukan da ba ta so a ji, ko a gani, shi yasa ta shige toilet take yin sa. Na tabbata ba zai wuce a kan aurenta bane. Ban yi mata magana ba, domin Zanirah mutum ce da ba ta son fadin damuwarta ga kowa, ba kuma ta son shisshigi cikin al’amuranta. Sai na fita falon a hankali duk jikina ya yi sanyi. Yaya Aliyu ya dubi Kausar da Walid da suka yiwa cinyoyinsa dabaibayi ya ce, “Oya!” Ya fiddo alawar Zanirah a da (Bounty) ya mikawa kowannensu, ya ce, “A tafi wajen Yaya Abdallah ga shi can yana exercise kuma ku yi, ko kwa rage wannan kumburin naku”. Duk suka ware da gudu. Abu ne da Hajjah ta raine mu da shi wato muddin bako ya zo kowanne iri ne abu na farko da zamu yi mishi shine, ba shi ruwa da lemo. Ban yarda mun hada ido ba har yanzu na yi kitchen na dauko lemon ‘Chivita’ da gorar ruwan ‘Faro’ masu sanyi da kofi na ja karamin center table gabanshi na aje mishi. Baya komi sai bina da ido, kamar yau ya fara ganina. Na daga gorar ruwan da har raba take don sanyi ina budewa na soma tsiyayawa cikin tambulan, amma kallon da Yaya Aliyu ke bina da shi ya haifar min da karkarwar jiki, na tsula mai ruwan a cinya. Ya mike da sauri ni kuma na saki kofin bisa tayal ji kake taratsatsatsa..... Muka yi tsaye cirko-cirko kamar zakaru, cikin murya mai sanyi ya ce, “Yaushe Fa’izah ta koma mara imani ne?” Ban san sanda na saki dariya ba. Duk yadda Yaya Aliyu ya kular da kai sai ya san yadda ya yi ya baka dariya. Na ce, “Ni da imanina bai je ko ina ba. Bari in baka wani”. Ya ce a harzuke, “Ke look! Bana bukatar ruwanki ba shi ya kawo ni ba. In shi ya kawo ni ai na san hanyar kicin din, kawai Malama ki bani amsar takardata. Da kuma dalilin wulakancin da kike min tsahon wata uku? Tun daga Legas na tako na kawo takarda a baki. An tabbatar min an bakin, to mene ne dalilin kin bani amsa just a single yes or no? Duka cikin kwanakin aikina nake jele daga Legas zuwa Giwa don kawai na karbi amsar ki amma Fa’izah babu. Anya akwai sauran imani cikin ranki? Na ce kar ki bar Jabi Road sai na dawo daga Giwa, na je na tarar kin gudo nan. Nan din ma ban yi fushi ba na biyo ki kin jike ni sharkaf da ruwan sanyi, anya Fa’iza ke ce?” Yadda yake maganar cikin sanyi, sai ya yi bala’in bani tausayi. “Fa’izah magana nake fa?” “To Yaya Aliyu ba ka zama?” “Ba a zaman, kawai ki bani amsata, kin amince ayi aurenmu da zarar kin yi graduating?” Na langanar da kai na ce, “Haba Yaya Aliyu”. Ya yi murmushi ya zauna, nima na zauna, muka dubi juna, sai muka sa dariya a tare. “Ke fa shu’uma ce Fa’izah, in mun yi aure zan sha wahalarki”. Na kau da zancen cikin jin kunya da cewa, “Zanirah fa tana ciki Yaya Aliyu in kirawo ta?” Ya ce, “In mata me? Ke, ina fa da abin yi, za ki bani amsata ne ko kuwa?” Na yi rau-rau da ido kamar mai shirin kuka na ce, “Haka ake ba da amsar Yaya Aliyu kamar a fagen fama? Don Allah ka yi hakuri na amsa duka laifuffukana”. Ya saki rai ya ce, “Ok!” Na koma kicin na kawo mishi wani ruwan, har da cake da dambun naman kaza ya soma ci yana hararata ina share fasasshen kofin tangaram ina murmushi. Na kammala na koma daki na dauko takarda na dunkule a hannuna na fito. Zuwa lokacin Yaya ya gama, na ce, “To Yaya Aliyu rufe idonka”. Ya mai da manyan idanunshi ya lumshe zara-zaran gassun girarsa. Ya bude su duka a kaina ya ce, “An ki a rufe, in rufe ki caka min wuka, tunda ba kya SO NA?” Ido waje na ce, “Lalala! Sharrin da za ka yi min kenan Yaya Aliyu?” Na jefe shi da takardar na yi daki a guje tare da kullo kofar har da murza key. Zanirah na tarar zaune bakin gado tana rubutu cikin karamin ‘DIARY’ din ta. Tana ganina ta boye shi cikin filo ta mike tana fadin “Fa’izah har yanzu Momi ba ta dawo bane?” Na ce, “Nima na rasa abin da ya tsare su, amma lokacin dawowarsu har ya wuce tuni”. Ta ce, “Ke da wa kuke ta magana ne haka a falo?” “Yaya Aliyu ne Zanirah, amma na ji tashin motarshi yanzun nan ya tafi, kina toilet sanda ya zo”. Jikinta a sanyaye ta koma gadon ta kwanta tana fadin “Zan dan kwanta in samu bacci kafin kiran sallah, in sun dawo don Allah ki tashe ni”. Wai Zanirah ta dauka kwanciyar nan da ta yi ban san cikin damuwa take ba. Damuwar ce ta yi mata yawa ba ta so na gane shine dalilin da yasa ta zabi ta kwanta din a dalilin dauriya da juriyarta sun kare. Umh! Na fa soma tunanin akwai wani abu tsakanin Yaya Aliyu da Zanirah, kai to mene ne.... kai babu komi.... to mene ne ma zai shiga tsakanin nasu? Oh! Ni Fa’izah! Anya ba son Yaya Aliyu Zanirah take ba?????? “..... Ina kammala makaranta zan kawo mata mijin..... Ki rike Yaya Aliyu da kyau, ki yi mai rikon magnet..... Yaya Aliyu ba irin mazan da ake yiwa rikon sakaka bane..... He has all the qualities and all the attributes to be loved upon.... ina da kyakkyawan zaton cewa, muddin Yaya Aliyu ya zamo miji a gare ki babu ke babu ganin wulakancin namiji da ‘yan’uwa mata ke suffering.... Saboda Yaya Aliyu na daban ne.... domin Aliyu uwa ne, uba ne, aboki ne, dan’uwa ne.... miji ne abin so da duk wata diya amce za ta yiwa kanta burin samu...... Imagine Fa’izah, yadda za ka zauna da wani alhajin zuciyarka da tunaninka, ruhi da gangar jikinka duka suna ga kaunar wani can daban.... Na tuno kalaman Zanirah! Na tallabi kaina da hannayena biyu sakamakon wata irin kwankwatsa da yake yi min tamkar zai dare gida biyu. Ko da yake an ce az-zannu zambun, wato zato zunubi ne bai kamata in yi saurin gaskata hasashena ba, har sai na ga diary din Zanirah da take boyewa, sai na ga abin da ta rubuta dazu, sai na ga damuwarta ta shekara da shekaru wadda a kullum ke zane a fuskarta. Ko mene ne ni zan yi kokari in magance mata damuwarta in har ba soyayyar Yaya Aliyu bane, zan taimake ta insha Allah ta fita daga halin damuwar da take ciki. ...... Shigowar Walida ya katse tunanina. Ta ce, “Yaya Fa’izah, Yaya Aliyu ke kiranki yana cikin mota zai tafi”. Duk da ina jin nauyin Aliyu ba zan iya kasa yi mishi sallama ba. Na rufe kaina da mayafi na bishi. Yana zaune cikin mota duka kafafunshi suna waje, ya jingina da makarin kujerar idonshi a runtse. Har na karaso bai bude idon ba, sai da na kwankwasa gilashin kofar motar ya bude dukkan manyan idanunshi a kaina, sun kada sun yi jajir har sai da na ji gabana ya yanke ya fadi, ko amsar da na ba shi ne ya tayar da hankalinsa maimakon ya yi farin ciki? Kallon juna muka yi cikin ido na ‘yan sakanni, kafin mu saki ajiyar zuciya a tare. Cikin sassanyar murya ya ce, “Abin da kika fada cikin takarda Fa’izah haka yake ‘heart and soul!” Kunya ta rufe ni, na rufe ido da yatsuna goma ina dariya...... Ya ce, “Na gode, na gode kin ji Fa’izah. Ina fatan lokacin da na yanke ayi aurenmu bai zamo takura a gareki ba, wato watanni uku masu zuwa bayan kammala jarrabawar ku ta karshe?” na yi shiru. “Akwai babban dalilin da yasa na yanke wannan lokacin duk da bana so na takura ki, akwai dalilin da yasa na yi hakan”. Na kara yin shiru idona a kan kananan duwarwatsun da suka rufe harabar gidan, da gaske ne har zuciyata ban shirya aure yanzu ba. A ranar na cika shekara goma sha takwas. A ra’ayina in samu ko karamar Diploma ne in yi kafin aure. To amma bana iya yiwa Yaya Aliyu musu saboda matukar so da kaunar da nake masa, ina son shi fiye da tunanina, fiye da tunanin duk wani dan adam. Bana iya musa mishi duk abin da ya umarce ni, don ina da tabbacin ba zai yi umarnin da zai zama cutuwa a gare ni ba sai wanda zai amfane ni. Har sau tari na kan ga kamar son da nake wa Yaya Aliyu ya ninka, ya dame ya shanye wanda shi yake mini. Wani lokacin na kan yi tunanin muddin muka yi aure ba zan iya batawa Yaya Aliyu rai ba ko inyi masa ba dai-dai ba daidai da kwayar zarrah, ko da shi ya bata min abu kadan zai yi ya shafe laifin daga idanuna da zuciya, komin GIRMAN sa. To amma dole in ji dalilin gaggawar tunda an ce ba a son garaje cikin aure, don gaggawar daga shaidan ce. Kamar wadda za ta gudu? Na ce, “Shin Yaya Aliyu to saurin na mene ne haka?” Ya saita kwayar idanunshi cikin nawa cike da damuwa ya ce, “Saboda SONKI Fa’izah! Na kai na kawo a sonki da kaunarki da son ganin mun zamo abu guda, na mannu da fatar jikinki which is always hunting my dreams.....” Na rufe fuska cikin jin kunya. Na ce, “Yaya Aliyu ai ba inda za ni, kullum muna tare. Ina laifin bayan candy da shekara daya? Bani da tunanin kowanne da namiji a duniya sai kai Aliyu Haydar......” Sai bayan na fada na san abin da na fada. Juyawa na yi zan tafi, Aliyu ya riko gefen mayafina. Ban juyo ba don haka ban san halin da yanayinsa ke ciki ba, ya ce, “Idan haka ne barshi a yadda na ce Fa’izah, watanni uku masu zuwa”. “Saboda me Yaya Aliyu? Gaggawa daga shaidan ce”. “What target do you have for making it longer haka Fa’izah? Wata babbar matsala ke neman fatali da farin cikinmu”. Ban san sanda na juyo gaba daya ba, na ce, “Matsala? Wacce irin matsala ce Yaya Aliyu?” Idonshi cikin nawa sun kada sunyi jajir, muryarsa a dushe ya ce, “Kina nufin baki sani ba? To Hajjah ke son in auri ZANEERAH!” Ji nayi wani abu ya kwashe ni yuuuu! Zai maka da kasa, na yi kokarin kama hannun Yaya Aliyu dake jikin motar gam-gam na rike. Muryata na rawa harshena na sarkewa na ce, “ZA-ZA-ZANIRAH Yaya Aliyu? Haba! Biri ya yi kama da mutum....” Na durkushe a gabansa kaina cikin cinyoyina, kamar in yi yekuwa a zo a tallafi rayuwata. Shi kansa Yaya Aliyu ya yi nisa a tunani, bai tanka min ba. Kowanne sakar da yake yi cikin zuciyarshi daban da na dan uwanshi. Kafin wata juriya da imani su shigeni ciki da bai dina. Na dago a hankali idanuna taf da kwalla na ce, “Ka je Yaya Aliyu Allah ya kai ka lafiya”. Ya dago ni daga durkushen da nake muka fuskanci juna. Don karfin hali irin na Aliyu murmushi ya yi min, nima ban san sanda na mayar mai da lallausar murmushi ba. “Kada ki sa abin a ranki fa. Everything will be alright. Don Baban Giwa (Barau), Baba Sadi da Baba Ibrahim da Yaya Hauwa basa goyon bayan zancen sam”. Na yi shiru ban yi magana ba, a zuciyata cewa nake, “Ni da kai kuma Yaya Aliyu ai sai wani babban ikon Allah, wanda in haka ta faru na tabbata na yi asara wadda ba mayarwa”. Zuwa can na ce, “Wallahi ka je kawai Yaya Aliyu, ni ba zan damu ba”. “How sure are you ba zaki damu ba.....” Na ba shi amsa muryata na gab da barkewa da kuka. “I am sure!” Ya gyada kai. Ya sanya hannu cikin aljihun motarshi ya dauko daurin kudi ‘yan naira dari biyu sardauna sabbi kar ya miko min. Na bata fuska gab nake da rushewa da kuka, don ji nake kamar sallamar karshe muke yi ni da Yaya Aliyu, kamar babban shinge na shirin shiga tsakaninmu, kamar wata sabuwar rayuwa zamu bude wadda dukkaninmu bamu taba tsammaninta ba. “Kada ki min musu, ki karba kawai. Ban da yau na taba dauko naira tsurarta na baki?” Na mika hannu biyu na karba. “Yaya Aliyu na gode, Allah ya kara budi”. Ya yi murmushi a cikin kallona ya yi min alama da hannunsa in tafi. Har na juya na soma tafiya ya ce, “Au! Fa’izah!” Na juyo hawaye shimfide a fuskata wasu na korar wasu. “Kika ce ba za ki damu ba, to meye na kuka?” “Ni ba kuka nake ba hawaye ne”. Ya yi murmushi, “Hawaye?” Nima sai na yi dariya, ga hawayen fal a fuskata. “Su zuba kawai suke, kuka kuwa zuciya ke yin sa”. “Na yarda dake”. Ya miko hannu. “Wannan kyakkyawan hankicin na hannunki za ki bani mana?” Na girgiza kai na ce, “A’a!” Da mamaki Aliyu ya ce, “Dalili?” Na ce, “Wallahi haka nan kawai nake son hankicin bana son rabuwa da shi, ina son kamshin sa”. “Wa ya baki?” “A dakin su kawata Naja na ganshi a hostel dinsu cikin kayana, wallahi ban san na waye ba”. “Mu gani?” Na mika masa ya karanta rubutun (AHUBBIK (I love you!”) ‘WA ANA AIDHAN (me too)” Na mayar masa muryata na karkarwa. Ya miko min hankicin na juya da gudu na karasa cikin gida, ban san tsawon lokacin da ya diba kafin ya bar gidan ba. **** Ban tashi sanin fitinar so ba sai a wannan ranar. Ban yarda it is injurious ba sai a wannan ranar. Ban san cewa its unbearable pain ba sai a wannan ranar da na tabbatar zuciyata ba za ta samu abin da ta dade tana SON ba, wato Ali Na’ibi. A gaskiya so abu ne mai dadi in ya zo da matsala marar dadi. Kamar yadda Ya IM ya ce na (GIRMA YA FADI) “It’s so sweet, yet so painful”. Wai sai na kama jin haushin ‘yar’uwata Zanirah (kishi), a ganina duk ita ta yi saurin girman da ya gundiri Hajjah har ta yi tunanin aurar da ita, kuma ta rasa wanda za ta likawa duk gidan sai Aliyuna, Yaya Aliyu, Aliyu Haydar Na’ibi A.B Giwa. Daga ni har Zanirah, kowacce ta kasa barci sai juyi a kan gado. Da abin ya isheni kawai sai nasa kuka wiwi. Tunanin in na rasa Yaya Aliyu, idan ba Aliyu ne ya zamo mijina abokin rayuwata ba shin ya ya rayuwata za ta ci gaba da kasancewa? Ya Allah kada ka baiwa Hajjah ikon karfafa zumuncin akan wannan, ya Allah ka fidda Aliyu zuciyar Zanirah. Don na laluba na duba na hanga ko ina ban ga ta hanyar da zan iya cin kankanta in bar mata ba in ita ba ta ci girma ta bar min ba, sai dai duk mu rasa, ko duk mu samu. Zanirah ta mike ba zato ta kunna fitila dakin ya gauraye da haske. Ta shiga kallona tsaf, ba ta ce komai ba sai ta shiga toilet ta dauro alwala ta zo ta burma hijab ta hau doka nafilfili. Hankalina ya kara dugunzuma ya tashi, don a ganina Zanirah na rokon Allah ne a kan ya mallaka mata Yaya Aliyu ni ya hanani. Sai na kara rikicewa da kukan tun karfin gunjin da zan iya a hankali yadda sauran jama’ar gidan ba mai ji na. Ba shiri Zanirah ta sallame sallarta ta ce, “Fa’izah wai lafiya ne?” Na dan saurara da kukan na ce, “Na fara kukan rabuwar mu ne Zanirah....” Da alama ba ta yarda ba har zuci, sai ta yi murmushi ta ce, “Allah yasa hakan ne har zuciyarki. Da sai in ce rabuwa ta zama dole ai, tunda babu yadda za ayi mu dauwama tare a matsayin mu na ‘ya’ya mata. In babu aure akwai mutuwa, akwai kuma kaddarorin Ubangiji iri-iri”. Mu karasa a littafi na 2 Tare suke,Takori [11/02 9:41 PM] Sumayya Takori: ZUMUNTAR KENAN 2 Washe gari muka raka Momi bikin walimar ‘yar aminiyarta Dacta Ladi, cikin Tudun-Wada. Lancin din da aka yi na ‘yammata a (Congo Conference) ya taimaka ainun wurin rage mana damuwa dukkanmu, kowaccenmu ba ta dawo haka ba sai da saurayi. Suka biyo mu har gida, Momi ce ta lallabasu ta ce su dawo gobe lokacin magariba ta yi ido na ganin ido ya fi. Washe gari kuwa da safe muka tattara muka koma Kaduna. Har muka kare satin ni da Zanirah kowanne ya kasa sakin jiki da dan’uwansa. Abin da bamu taba tunani ko a mafarki zai taba faruwa a rayuwarmu ba. Kai SO din nan bala’i ne, masifa ne ba karama ba tunda har ya iya farraka (shiga tsakanin) ni, Ummi da Zanirah. Ranar da zamu koma makaranta mun shirya tsaf cikin uniform. A bakin gate zan shiga motar Baban Kaduna ya ajiye ni makaranta, ita kuma za ta shiga school bus direban Baban ya maida ta Giwa (GGSS Giwa) sai ta riko hannuna. Ta matse gam cikin nata, hawaye ya fito daga idanunta ta yi azamar dauke su da yatsunta. Ta ce, “Fa’izah ki fidda damuwar dake damun ranki ki yi (facing final exams) dinki yadda ya kamata, wannan ce damarmu ta karshe ta gina (future) dinmu, kada mu bari abin da bai kaita muhimmanci ba ya rushe”. Na murmusa ina kokarin mai da nawa hawayen na ce, “And you too Zanirah!” Amma a zuciyata cewa nake, “Kin manta ne Zanirah, an ce “LOVE IS OVERALL!” To haka rayuwar ta kasance mana ba dadi a makaranta ma, kullum zullumina kammaluwar jarrabawarmu, isowar karshen karatun nan. Gab da zamu zana JAMB na shiga samun katunan fatan alkhairi daga Yaya Aliyu masu dauke da kalamai masu karfafa zuciya tare da kwantar da hankali. A kalamanshi ya fi ambata ‘nasararki na nufin nasarata, kwanciyar hankalinki shine tushen samun nasarar, nasara ba ta zuwa da sauki, nasara sai an sha gwagwarmaya ake samun ta. Soyayyar da ba a samu tangarda ko bambance-bambancen ra’ayi ba, ba ta kai wa gaci. Fa’izah ki sa a ranki ba zamu yi aure bane kawai in dama tun fil azal Allah ya rubuta ba zamu yin ba” Wannan kwarai ya taimaka min wajen samun nutsuwa na zana jarrabawar JAMB lafiya cikin kyakkyawan zaton samun kyakkyawan sakamako, wanda zai fitar dani kunyar iyaye da masoyana. Tsakanina da Ummi sai kallo da ido in an haxu a hanya, haka nan kunnuwana basa huta jiye min irin sakonnin da take samu daga Fa’iz akai-akai ba. Daga bakin Naja’atu da Haulatu. Tare da tabbatar min Ummi ta yi nisa a son Fa’iz ta yadda za ta iya batawa da kowa ma a duniya bani ba, don haka in daina tunanin zan iya hanata ko zan rinjayeta ta bi ra’ayina. Yaya Aliyu ya kawo mana ziyara muna wata biyu da dawowa, bai fi saura sati uku mu kammala makaranta ba kenan. Hankalina ya yi mugun tashi da ganin yadda Aliyuna ya koma kashi da rai, ido a lungu, dama jikinsa fyalan-fyalan babu kwari haka yake, dogon Bamalle mai suffa irin ta Baba Na’ibi. Baki a bude nake tambaya “Shin Ya Aliyu ulcer din ta kwantar da kai ne bamu nan?” Ya girgiza kai ya ce, “Ko daya Fa’izah. Illah Hajjah da Baban ABU dake neman zauta ni. Hajjah ta rantse ta kuma ta rantse ba ta san zancena dake ba, ba kuma za ta yi miki aure yanzu ba.....” A tsaye nake amma sai ji na na yi ragwaf, na yi zaman rakuma a gaban Yaya Aliyu. Idanuna ke fitar da wasu irin hawaye amsu zafi da yaji da ban taba fitar da irinsu a rayuwata ba, a yayin da nake cewa, “Ni kam Yaya Aliyu na hakura, ba zan iya jayayya da Hajjah ba, na hakura har ga Allah. Dama an ce duk soyayyar da ta yi tsayi irin haka da kyar ne take kai labari.... Na hakura..... ko ba komai ba zan yi bakin ciki ba don ka auri ‘yar’uwata jinin jikina Zanirah ba..... ina da yaqinin ban barka a hannun da zan yi tararrabi ba, you are in safe hands, domin Zanirah nice, ni Zanirah ce, babu bambanci daga kamanni da halayya, sai ma wanda ta fini. Zan so ka yi farin cikin jin cewa Zanirah na matukar son ka, irin son da tunaninka bai taba baka ba......” Ya katse ni cikin tsawa..... “Fa’izah baki da hankali? Kina hauka ne, kina so ki kashe ni ne? Shekaru goma sha biyu da na kwashe ina dakon soyayyarki, dai-dai da rana daya zuciyata ba ta taba hutawa ba da azabar soyayyarki da abin da za ki saka mini kenan wai kin barwa wata ni?” Na sunkuyar da kai kasa yayin da hawayen suka sunce a kundukukina suna rige-rigen tadda kasa, aguje suke bulbula wani na bin wani suna masu tuna mini kaunar da Yaya Aliyu ya shekara nuna mini. Wahala wadda uwa da uban da suka haife ni basu yi min kwatankwacinta ba in an dauke hakkin haihuwa. Duk da bai ambaci wahalar da ya sha a kaina ba sai ‘kauna’ da ‘soyayya’ ya zama dole ni din in tuna da wannan. To amma babu abin da zan iya a ciki. Tsana ga Zanirah ko kuwa kin biyayya ga Hajjarmu? Gyatumar da iyayenmu ma basa tsallake umarninta? Ina mai girgiza kai a gaggauce na rarrafa ga Yaya Aliyu yayin da na kama tafin kafarshi ina kuka, na ma manta a cikin ofishin vice muke, ina fadin “Ka yi hakuri Yaya Aliyu, ya ya kake so in yi toh? Kana nufin in baka hadin kai mu yi butulci ga Hajjah da Baban Kaduna da Mama Asma’un da ta tsuguna ta haifi Zanirah amma ta fifitani a kanta? Ko ko Hajjar da ta sha wahalarmu, wahalar da iyayenmu basu sha ta ba? Ba zan iya ba! Ka yafe ni Yaya Aliyu!! Na san ka so ni, ka bautu a son da kaunata tsayin shekaru, to haka Zanirah ma ta kwashe shekaru tana begen zama a muhalli na. Na tabbata za ta yi maka biyayya fiye dani tunda son ta ya rinjayi naka. Sanin kanka ne Zanirah mutum ce mai sanyi da saukin hali, nutsuwa da hankali tamkar kai, it must surely be a perfect match as usual within A.B family. Nima Allahu ya bani gwarzon miji tamkar kai mai hali da aqida da kamannin Yaya Aliyu. Kundin shafukan rayuwata will be incomplete without the scenes of Yaya Aliyu.....” Na juya ina tafiya da baya-baya ina masa murmushi ga hawaye na bulbula. Aliyu bai iya ya ce mani komi ba illa buga hannuwanshi duka a jikin garu (bango) ya kifa kai a jikinsu yana rusar kuka, kukan da bai taba yi a rayuwarshi ba, kukan da wani namiji kwatankwacin Aliyu dai bai taba yi a kan mace ba...... “Hajja kin cuce mu..... kin yanke mana buri a dab da wa’adin cikarsa..... kin guntile ingantacciyar soyayyar da aka dasa ake mata ban ruwa ta yi yado ta ba da yabanya ana gab da cin amfaninta..... Anya zamu iya yafewa Hajjah? Meye amfanin soyayyar da take nuna mana tunda a karshe cuta take zama? Babu!! (Rabuwar mu da Yaya Aliyu kenan). **** Na yi matukar kokarin ganin na manta da Yaya Aliyu, na fidda son Aliyu a raina, na yi kukan, na yi addu’ar, amma a kullum son Yaya Aliyu ke dawo min danye jagab, sabo fil a zuciya. Meye sauran farin-cikin ne a yanzu a zama a A.B House a yanzu ni Fa’izah! Ummi mun rabu saboda Fa’iz, Zaneerah mun rabu saboda Aliyu, shin me zan koma in yi a Giwa? In ina da zuciya kare bai cinye ta ba daga yau na bar Hajjah Hadiza Giwa, zan koma gidanmu, ko da uwata da ubana za su kasheni ne tunda Hajja ba ta so na. Zanirah da Fa’izu ta fi so tuntuni. Wannan haka yake ‘ya’yan Baban Kaduna take so, domin shine mai kudi, shine mai huce takaici, wato masu gidan rana. Yana kaita Hajji duk shekara ko ya ya ne? Shin ma wai me nake tsinta a kauyen Giwa ne da babu a Zaria? Zariar ma muhalli irin (Area One). Ba komai bane illa sabo da su Ummi. Tunda rayuwar ta zo da guguwar sauyi kowa ya koma gaban uwa da uban shi. Yaya Aliyu! Yaya Aliyu!! Yaya Aliyu!!! A kullum na tuno irin soyayyar da muka gudanar, a gaba dayan tsayin rayuwarmu, kulawar da ya yi mini, wahalar da ya sha a kaina, sai na yi kuka na gode Allah. Hawayena sun kafe, na kama kukan tunkiya, wanda babu hawaye sai sauti. Babu abin da ya firgita ni kamar migraine (ciwon kan barin kai guda) da ya same ni a kowanne dare, ga wani zazzabi-zazzabi mai zafin gaske da nake kwana da shi da safe ya wartsake. Ban karanta ba, amma na kan ji an ce wadannan alamu ne na ciwon hauhawar jini (hypertention). **** Ranar da muka zana takardar karshe wadda ta kasance ‘Islamic Studies’ na daga hannuwana sama na yiwa Allah godiya da ya nufe ni da kammala makaranta lafiya ba tare da na taba karya doka ko guda daya da makaranta ta kafa ba, ba tare da na taba batawa kowa da zama ya hadani da shi ba a kan sani, sai bisa ajizancin dan adam, kamar yanda ban taba yin laifin da aka dauki bulala aka shimfida a fatar jikina ba tsayin shekaru uku. Na dawo hostel na shiga rarrabar da kayana ga juniors dinmu, na rabar da komai nawa har sutturar da nake amfani da ita a makaranta ban bari ba. Ban bar komai ba sai ‘hankici’ na da sutturar jikina wanda ya zame min tamkar jarabi. Na rufa shi a fuskata a wannan ranar, na yi kwance bisa gadon boarding school kwanciyar dana kira kwanciya ta karshe a sakandire. Na juya rigingine al’amuran na gifta min tamkar majigi, kamar yau ne Yaya Aliyu ya kawo mu QUEEN AMEENA COLLEGE KADUNA. Yau ga Allah ya kawo mu ranar barin ta. Shekaru uku tamkar kwana uku. Kwanakin, satittikan, watannin da shekarun sun shude ba za su kuma dawowa ba. Sai dai al’amuran dake cikinsu masu yawa ne a gare ni da ba zan iya mantawa dasu ba. Tunanin tashin hankalin da zan je in taras a gida gobe ya addabe ni. Kowa ka gani a harabar makarantar ‘yammata ta Sarauniya Amina a washe gari bakinsa har kunne yake, farin ciki ya wadace shi. Sabanin ni da ta kasance bakar rana a gareni. Duk da dimbin tarihin da ranar ta ajiye min mai dadi ga iyaye da ‘yan’uwana. Baya ga kyautar wadda ta fi kowa Da’a da kulawa da al’amuran addini (Amirah). Ni Fa’izah Ahmad Abubakar Bamalli Giwa, na karbi kyautar dalibar da ta fi kowa iya harsuna biyu mafiya shahara a duniya, wato Turanci da Larabci. Wannan duk karami ne a kan yabon da na samu a kan kananan rubuce-rubuce na ‘Literature’ Littafina ARE VOWS MEANT TO BE BROKEN? Gwamnatin Kaduna ta saya akan kudi masu yawa, Sarkin Zazzau ya saya, dansa Yariman Zazzau Mansur Modibbo ya saya a kan kudi masu firgitarwa. Galadiman Zazzau ya saya, Iyan Zazzau ya saya duka don rabawa a labiraren makarantun sakandire na jihar Kaduna. Wai-wai-wai. Ni Fa’izah na ga hasken camera a wannan rana, kamar ta bikin sallah. Haka na hau steps na rungumo kyaututtuka da award dina na literature. Babu abin da ya daga min hankali kamar rashin matallafi ko wani da ya shafe ni da zai karbe ni ya nuna min kauna cikin dangina da ya fito daga dimbin mutanen da ke hall din. Wannan ya tabbatar min daga Giwa har Kaduna da Zaria babu wanda ya zo mana. A yayin da na ke saukowa daga ‘steps’ din saukowar na tafiya ne dai-dai da bugun zuciyata, hardewa nake ina rangaji kamar zan ci da baki. Kafafuwana da hannayena baki daya sun sage. Ko kowa bai zo ba na zaci Yaya Aliyu zai yi kokari ya zo a wannan rana. A yayin da nake cikin wannan hali na takaicin rashin ‘yan’uwana, a yayin ne Ummi ta ratso daruruwan mutanen ta iso gareni ta tallafeni ni da kyaututtukana duka ta rungume mu muka karasa mazaunina tare, ana sakar mana hasken camera da saitin vedeo. Bayan taro ya watse na hangi Ummi can nesa dani tana magana da fadawa. Na cira kafa na ci gaba da tafiya rungume da kayana. Ba wasu kaya bane kyaututtukan da na samu ne da jakar takarduna rataye a kafada ta, sai hankcina a hannun hagu ina mai share gumin babu gaira babu dalili dake shararo min, abin mamaki tun daga tsakiyar kaina gumin ke tsattsafowa yana biyo goshina. Ummi ta biyo ni da sauri har tana hadawa da gudu-gudu don ta cimmani kamar babu abin da ya faru tsakaninmu, ta ce, “Ya kika taho kika barni Fa’izah? Kinga abin mamaki babu wanda ya zo mana anya lafiya?” Na kalle ta kawai na ci gaba da tafiyata. Daga bisani ganin ta jeru dani muna ci gaba da tafiya sai na ce, “Ai ina ganin Ummi tafiyarmu tare ba za ta yiwu ba, don ni nan Zaria na nufa”. Ummi ta dube ni baki sake ta ce, “Ki je Zaria ki yi me?” Nima cikin mamaki na ce da ita, “Ah! Mutum da gidan ubansa har a tambaye shi abin da zai je yi?” Ta ce, “Ban fahimce ki ba, amma ko ina dai za ki kafata-kafarki, don yau wata haka-haka nake ganin ki”. Na ce, “Haka-haka kamar ya ya? Na yi miki kama da sabon kamu kenan”. Ta ce, “Allah ya baki hakuri, ni ban ce ba, amma muje sai a kaimu Zariyar ko kuwa?” Na dube ta da mamakin yadda ta manta mun samu sabani a junanmu. A raina na ce “Shin Ummi kina tunanin zamu koma kamar da alhalin kina son makiyina ni da uwata?” Ban ce mata komai ba muka rankaya zuwa bakin titi. Mun yi tsayuwa fiye da ta rabin awa babu taxi, in ma sun gifta mu a cike suke. Ban so zan yiwa Ummi magana ba, amma hakan ya zame min dole. “Kawai mu hau okada, tunda ba wasu kaya garemu masu yawa ba”. Hakan kuwa muka yi. Ban ga kowa a harabar gidan Baban Kaduna ba, babu motocin Baba ko daya, babu yara ko daya masu yi mana oyoyo idan mun zo! Tun daga nan gabana ya soma faduwa, na fiddo naira dari biyu na baiwa masu okada muka karasa bakin gate muka gai da Malam Hassan maigadin gidan. Ya ce, “Ku kadai kuke tafe?” Har muna hada baki wajen cewa, “Eh, wallahi Malam Hassan. Ina jama’ar gidan suka tafi ne? Mantawa aka yi yau muke graduating? Babu wanda ya je mana daga Giwa, Zaria har nan cikin Kaduna?” Ya ce, “Hala mantawa kuka yi yau ake daurin auren Zanirah da Alh. Aliyu???” Wallahi baya ga wannan ban sake jin komai ba, ban sake sanin inda kaina yake ba. Sai tsintar kaina na yi a asibitin Jinya dake cikin garin Kaduna, Ummi na gefen kaina tana mini firfita. Na soma kokarin tuno abin da na ji (DAURIN AUREN ZANIRA DA ALIYU). Na fashe da wani gursheken kuka a cinyar Ummi, ita ma Ummi kuka take, na tabbata kukan tausaya mana ne ni da Yaya Aliyu, cewa take “Ya aka yi haka Fa’izah? Garin ya ya ni ban san zancen ba? Ya ya aka yi haka? Na dauka ke za a baiwa Yaya Aliyu?” Na mike zumbur ina layi na ce, “Ummi ya zama dole in je Giwa a yanzun nan, dole ne in je Giwa kada Zanira ta dauka ina bakin cikin auren ta da Yaya Aliyu ne, ta wuce haka a gareni, tashi mu tafi Ummi”. Ummi ta share hawaye ta mike, halin da nake ciki ne yasa ban bambance motar suwa muka shiga zuwa Giwa ba, ashe motar Yariman Zazzau ne Mansur Modibbo wanda ke biye damu da abokinsa tun daga Queen Amina har Jabi Road. A kan idonsu na fadi, kuma su suka kawo ni asibiti tare da Ummi. A hanyar mu ta zuwa Giwa Mansur ya ce, “Shin wace ce ita wannan Zanirah da labarin aurenta ke sumar da Fa’izah yake sanya Ummi kuka?” Maganar tashi sai ta bamu dariya har ni da ke cikin hali na kaka-ni-kayin zuciya. Ummi ta ce, “Duk wani bayani da zan yi maka a yanzu ranka ya dade ba za ka fahimta ba, Zanirah is our bloody sister”. Ya ce, “To na hakura da jin wace ce real Zanirah sai na dawo. Ni dai fatana Ummi don Allah ki rinka shigar dani kin ji? In na kai ku yanzu juyowa zan yi sai sati mai zuwa zan dawo, saboda zan yi tafiya zuwa Abia State na san kafin lokacin Fa’izah ta dawo normal!” Ni kam kallon shi ma ban yi ba fuskata na cikin cinyoyina, tunda na rasa Yaya Aliyu babu abin da zan nema a wani Da namiji, domin ko kusa ba zan samu mai hali abin so da irin kyakkyawar zuciyarsa ba. It’s indeed a great loss! Addu’a nake a cikin zuciyata, “Ya Allah ka sanya min hakuri da dangana, ka bani juriya da karfin zuciyar fitar da Yaya Aliyu Haidar daga Zuciyata”. Dai-daikun jama’ar da na gani a harabar A.B Estate ya tabbatar min har an gama daurin auren Zanirah da Yaya Aliyu! Wayyo Allah ni Fa’izah na rasa Yaya Aliyu kenan, tabbas na rasa shin, na hakura har ga Allah daga yau na bar wa Zanirah Yaya Aliyu. Sunan Allah Ya zuljalali wal ikrami nake taunawa a harshe da hakorina. Babu shakka zuciyata ta yi sanyi illa jikina dake faman karkarwa, amma a kan fuskata farin ciki ne bayyananne. Ni kadai na yi sallama falon Hajjah domin na baro Ummi waje tare da su Mansur Modibbo wanda su da gaske suke neman iri suka zo gidan Bamalli. Lallai iska na wahalar da mai kayan kara (na fada cikin raina). Gaba dayansu ‘ya’yan Hajja Hadiza su goma sha biyar in ka dauke Yaya Rabi auta dake Kano, Baba Muntari, Baba Na’ibi, Baba Ibrahim, Baba Barau, Baba Sadi, Baba Sani, Baba Salisu da su Yaya Hauwa, maza goma mata hudu kenan, duka zaune falon Hajjah wanda yake makeken gaske suna tattaunawa ko a kan mene ne oho! Na tsugunna na gaida su daya bayan daya. Hajjah ta ce, “Yar albarka, kuna raina wallahi, yanzu nake cewa a je a dauko ku don ita kanta amaryar yanzu ta shigo daga tata makarantar?” Ni dai na ce, “Uhm! A raina na ce, ‘dole ki ce min ‘yar albarka mana tunda kin san yankan bayan da kika yi min, kin barni da cizon yatsa.... ai dole kisa min albarka!’ Amma a fili sai na ce, “Wallahi kuwa mun yi mamakin rashin zuwa kowa, sai da muka je Jabi Road, Malam Hassan ke gaya mana daurin auren Yaya Aliyu da Zanirah ake yi, shi yasa ma bamu damu sosai ba muka taho da kanmu kawai”. Na mikawa Babana kyaututtukan da na samu cikin ledar Ghana must go da cheque din kudaden da na samu. Su Baba suka shiga dubawa suna kwararamin albarka tun karfinsu. Sai dai duk abin nan da ake na lura Yaya Hauwa na hankalce da duk motsina da na jajayen idanuwana, tana bina da kallon tausayi da karfafa gwiwa. Fuskarta cike da tausayi ta ce, “Fa’izah duk wannan ramar ta mecece?” Ta fada tana taba kasusuwan wuya da suka bullutso min da hannun damanta. Na yi murmushi na ce, “Kai Ya Hauwa kin manta daga kurkukun jarabawa na fito?” Ta yi murmushi kawai irin nasu na manya. Ba zato Baba Na’ibi ya ce, “Na yi zaton Fa’izah ce za ta zamo matar Aliyu?” Duk sai kowa ya yi tsit, yana mai jinjina maganar. Sai Hajjah ta bude baki a hankali ta ce, “Na’ibi!” Ya dago ya dube ta cikin amsawa. A nutsenta ta ce, “Ta ina Fa’iza ta dace da Aliyu?” Baba Na’ibi a dan daburce ya ce, “Ban gane ba Hajjah?” Ta yi murmushi ta ce, “Abin nufi a nan, shin Fa’izah ba mace ce mai tsiwa, taurin rai, ginshira, dagewa bisa duk abin da ta kudurtawa ranta (dertermination) kekasasshiyar zuciya a kan duk abin da ta tsana ko mutumin da ta tsana ko halayyarsa. So wanda ya wuce hankali ga duk abin da take so? Shin Aliyu da Zanirah ba mutane ne masu sanyin rai ba da saukin zuciya? Saboda haka sun dace da juna, za su zauna da juna lafiya, za su ji dadin zama da juna babu hayagaga. Amma halayen Fa’izah ba kowanne namiji ne zai iya zama da ita ba sai NAMIJIN DUNIYA, mai halaye irin nata ba mai sanyin rai irin Aliyu ba. Ma’abocin juriya da karfin jiki da na zuciya baki daya. Amma in an hada Aliyu mai sanyi da Fa’izah mai tsiwa da jumurda, bakwa tunanin Fa’izah ce za ta zama mijin, Aliyu ya zama matar saboda matsanancin son da yake mata? Wato ya zamo sai yadda ta yi da shi kenan saboda gudun fitinarta da bacin ranta? Kasancewar shi mutumin da bai son tashin hankali da hayagaga ko kankani? Kuna gani fa tun yanzu duk abin da Fa’izah ta gindaya mishi baya iya tsallakewa duk ya lalace a gindinta, bini-bini yana binta kamar bita-zai-zai wace kalar rayuwa kuke tunanin za su shimfida a gidan auren su? Baya iya musa abin da ta ce, baya iya tsawata mata in ta yi ba dai-dai ba, tun suna yara nake hankalce dasu. Ina rayuwar aure za ta yiwu tsakaninsu ba tare da raini ya shiga tsakani ba? Aliyu da Zanirah kuwa da wuya za a ji kansu, za ku ga irin rayuwar da za suyi ta namijin da ya isa da gidansa, za ku ce dama na gaya muku ne”. Gaba daya suka yi shiru suna masu jinjina maganar, haka nima ina mai gaskata kowacce kalama a cikin zancenta. Tuni na gane hikimar hada auren Zanirah da Aliyu da tsohuwar mai tarin hikima da fasaha ta yi. Wato muddin na auri Yaya Aliyu ba zai iya lankwasa ni ba ko kadan, saboda matsanancin son da yake min. Tana masa gudun zama mijin ta-ce ne kawai gara ta ba shi wadda zai iya da ita don son zamar da shi mai kima da karfi a gidansa. Amma Zanirah halinsu daya (simple personality) wadda ba ta zafafawa cikin al’amuranta. Tabbas halayen Zanirah baki daya irin na Yaya Aliyu ne, hakuri, sanyin rai da sanyin zuciya. Abin da babba ya hango yaro ko ya hau ganuwa da Dala da Gwauron Duste ba zai hango ba. Sai dai ta wani bangaren Hajja ta yi (underestimating) dina. Ni ina son Yaya Aliyu ne saboda kirkinshi, halayensa da mutuncinsa da son addini. Ban taba tunanin in yi amfani da son da yake mini in mun yi aure in mai da shi sahoramin miji ba (mijin-ta-ce). Sai na bude baki a gaban Babannina duka na ce, “Hajjah kina da gaskiya. A da kam mun so juna da Yaya Aliyu so ba na wasa ba. Sai dai daga yau wallahi na hakura, na barma Zanirah da zuciya daya, zan kuma ci gaba da binsu da kyakkyawar addu’a Allah ya karkatar da son da yake mini kanta. Ban ga laifin ki ba Hajjah, Allah ya basu zaman lafiya.....” [12/02 6:09 PM] Sumayya Takori: Hawayen da suka shimfido min su suka sanya na mike na yi daki aguje ina kuka wiwi. Yaya Hauwa ta taso za ta biyo ni ta rarrashe ni amma Hajjah ta ce ta kyale ni kawai in yi kukan zuciyata za ta yi min sanyi, kukan sabo ne da fitar SO. Na ci kuka na a gado na share hawaye, na jiyo zubar ruwa a (toilet) wanda ya tabbatar min Zanirah wanka take yi. Idona ya kai ga abin da na jima ina fakon Zanirah don in dauka sai yau na hange shi cikin kwabar kayanta wato ‘DIARY’ dinta. Na yi hamzarin daukowa ban yi nawa ba wajen bude shafin farko. Kwanan watan ya nuna Zanirah ta yi rubutun nan ne tun muna JSS (karamar sakandire). “Ban san abin da ke damuna ba, amma kamar son Yaya Aliyu nake in na yi la’akari da yawan tunaninsa da nake da mafarkinsa cikin barcina, da kwadaituwa da son ganinsa akai-akai. Me kenen hakan ke nufi? Sai na shiga bude sauran shafukan a gurguje. Duk yawanci abin da ya shafi kuruciyarmu ne. Sai wani da ya dauki hankalina wanda kwanan watan ya tabbatar min Zanirah ta yi rubutun ne ranar 10/10 wato ranar da muka je Area One ni da ita (Zaria). “Dole ne in yi jihadin fitar da Yaya Aliyu a raina, domin ina son shi ne a yayin da na fahimci zuciyarsa, rayuwarsa, ruhinsa da gangar jikinsa sunyi nisa a soyayyar ‘yar’uwata (Fa’izah.) Fa’izah da zumunci basu cancanci in yi tarayya dasu a son komai a duniya ba. Yadda nake son Fa’izah bana son abin da zai sosa ranta. Na tabbatar da Fa’izah ta san ina begen Yaya Aliyu, babu abin da zai hana ta bar mini.... zan ci gaba da lallamin zuciyata har sai ta mance da Yaya Aliyu.... in har Fa’izah za ta iya yi min wannan halacci ni me zai hana na kasa? In anyi duniya don Rasulillahi daga yau na cire son Aliyu a raina domin Fa’izah.......” Da na kawo nan sai na rushe da kuka sosai, hawaye na zuba a kan littafin. Dai-dai lokacin da Zanirah ta bude kofar toilet ta fito, kukan da ta tarar dani ina yi ya kara tsuma raunanniyar zuciyarta. Ta tsuguna nan a bakin kofar ta shiga rera kuka ita ma, muka taru muka yi ta yi kamar akuyoyi. Cikin gunjin kuka Zanirah ta ce, “Fa’izah ki yafe ni...... wallahi ban ci amanarki ba.... Ban taba sanin Yaya Aliyu ne mijin da za a daura mana aure ba..... da na san shine wallahi da na bar garin da in zauna in ga wannan rana.... wallahi ban san cewa Yaya Aliyu bane ban sani ba Fa’izah.... ban san za a daura ba.....” Na mike da azama da sassarfa na isa ga Zaniraha muka rungume juna muka ci gaba da rusa kuka tare ba mai jin na wani. Na ce, “Zanirah kada ki ce haka, (waman qaddarralahu haqqan qadrihi.) Kada ki kara fadin haka Zanira, ban taba zargin ki da wannan ba, mune muka yi kuskure, kuskurenmu ne ni da Yaya Aliyu da muka yarjewa zuciyoyinmu muka basu fili a kan abin da suke so, alhalin muna da masaniyar ko in ce mun kwana da sanin cewa babu auren soyayya a zuri’ar A.B muka bi ta kai muka take. So we are to be liable for the outcome, ban zarge ki ba ko kadan Zanirah. Baki da wani laifi, babu wata amanata da kika ci. Addu’ata da fatana Allah ya karkato da son da Yaya Aliyu ke mini da wanda nake masa kanki, ya baku zuri’a dayyaba... Ya bani miji kamar naki Zaneerah...!” **** Yaya Aliyu bai tashi zuwa Giwa ba sai karshen wata kamar yadda ya saba, wanda ya yi dai-dai da sati biyu kenan daurin auren shi. Tun daga gidan mahaifinsa, mahaifinshi Baba Na’ibi ya kira shi ya yi masa gamsasshen bayani. Ya kara zancensa da cewa, “Aliyu ka bi Hajjah da duk yadda take so in har kana so ka taimakemu mu rabu da ita lafiya. Hajjah mahaifiyarmu ce da ta tsuguna ta haife mu daya bayan daya. Bamu da ikon bijirewa tsarinta da mahaifinmu Allah ya ji kan rai ya dorata a kai, ka sanyawa zuciyarka hakuri da dangana tamkar kowane Da cikin gidan nan da ka budi ido ka gani. Domin a yadda Hajjah ta dage a kan auren nan naka da Zanirah, ta kuma kawo hujjojinta masu ma’ana mu kanmu mun ga gaskiyarta mun mika mata goyon bayanmu wanda a baya bamu bayar ba. Ta sanya tariya sati biyu masu zuwa, na biya sadaki dubu sittin, ga lefe kuma da Babanka Ibrahim ya yi maka, su Hauwa ya tura Kano suka hado komai, gobe in Allah ya kaimu za su Zaria (gidanmu kenan). Don Babana ne alwalin Zaneerah.” Aliyu Na’ibi a zaune yake bisa kilishi dai-dai kafafun mahaifinsa, amma sai ga shi tsaye gaban Baba Na’ibi ba tare da ya san lokacin da ya yunkura ya mike tsayen ba. Wani kakkauran gumi ya wanke shi daga kwanyar kansa har zuwa yatsar kafarsa. Ya bude baki zai yi magana yawu ya kafe kat, a bakinshi. Bakin ya bushe fayau! Iyaka kokari Ali ya yi wurin tattaro kalma daga can kasan makoshinsa...... “Don me kuka yi min haka Baba?” Da karsashi da tausayin da ake son boyewa karfi da yaji ya ce, “Don mun isa daku dukkanku”. Aliyu ya ce, “Bana son Zanirah da irin soyayyar da kuke nufinmu da ita, ban taba sonta da aure ba Baba”. Baba Na’ibi ya mike tsaye idanunshi tinjim da kwallah ya ce, “Aliyu babu bambanci tsakanin Zanirah da Fa’izah, abin da ya yi Fa’izah shi ya yi Zanirah. Uwar da ta haifi uban Fa’izah ita ta haifi uban Zanirah. Tare suka taso tun suna kanana, komai nasu iri daya ne sai a halayya da suka bambanta. Ka yi hakuri ka jure sauyin da Allah ya yi maka ka yi koyi da mai sunanka”. Ya ce, “Matsalata Baba ba zan iya daina son Fa’izah ba.....” Sai a wannan lokacin hawaye suka sakko bisa kundukukinsa. Baba Na’ibi cikin dimuwar wai yau Aliyu ke kuka a gabansa, kukan ma a kan mace. Sai ya ce a harkuze, “To Aliyu ka yi yadda kake so, ka yi duk abin da kake ganin shine dai-dai, tunda mu bamu san dai-dai ba. Sai dai ina tabbatar maka da abu uku, na daya muddin ka wulakanta Zanirah sai Allah ya saka mata, domin ita ma yadda ka tsinci al’amarin haka ta tsince shi bakin iyayenta. Na biyu muddin ka tsinka igiyoyin nan guda uku da muka damka maka sai dai ka nemi wasu iyayen amma ba cikin zuri’ar A.B ba. Na uku muddin ka dagawa gyatumar mu hankali tsakanina da kai sai Allah ya bi min kadina na haifar ka da na yi na raine ka har ka yi girman da za ka soka wa uwata tsinke cikin idanu”. Hawayen Aliyu na zuba ya ce, “Ta ya ya Baba za a daki mutum sannan a hana shi kuka?” Baba Na’ibi ya ce, “Har karya shi za ayi a ce in ya yi nishi Allah ya isa! Na dai gaya maka daga yau babu sauran wata hulda tsakaninka da Fa’izah sai ta ‘yan’uwantaka. Zanirah kuma idan ka wulakanta ta don kanka, sai dai a kullum kake tunawa ita ma ba ta taba cewa tana sonka ba dole a kai mata. Amma da yake ita mai biyayya ce ba ta dagawa ubanta hakarkari kamar yadda ka daga min ba”. Haka ya fice daga dakin Baban cikin mummunan yanayi da ba zai misaltu ba. A take ya zari mota ya bar garin kwata-kwata ya koma inda ya fito (Ikko), fadi yake kamar zararre, “Ku rike amaryarku can bana so...... Ta ya ma za ayi na auri Zanirah?” Gidan babban amininshi Isa Kaita ya aje motarshi. Isa ya kai shi filin jirgi ya bi jirgi zuwa Lagos. Mu muna can dakinmu na ‘yammatan gidan muna jiran ango ya shigo ya bamu kudin alibidi da lancin din da zamu yi a Zaria da Walima a gidan Baban A.B.U. Labari ya iske mu ai Yaya Aliyun ya zo ya kuma koma Lagos ba tare da ya kwana ba ma. Ban da salati ba abin da Hajjah ke yi tana fadin “Zai zo ya same ta”. Amarya Zanirah ta yi kamar ba ta san ma me ake cewa ba, ta yi bakam. Ta dauki remote ta karo sautin wakokin yaran Larabawa na (Ad-difl - wal-bahr). A take na gano matsalar Yayan namu, wato ya ji labarin wannan rikitaccen al’amari na Hajjah. Ni kam da na mai da al’amurana ga Allah da addu’a, nafilfili dare da rana da addu’o’i na musamman cewa, in soyayyar Aliyu ba alkairi ba ce a gareni Allah ya sanya min hakuri da dangana, ya yi min zabin alkhairi mafi kyau, domin zabinsa shine zabi. Abin da nake maimaitawa kenan cikin sujjada ta a ko da yaushe. Tuni nake da tabbacin Ubangijin nan maji rokon bayinsa ya amsa mini, zuciyata sarai, duk wani duhu da kunci sun gushe. Babu abin da zuciyata ke kwadayi kamar ganin daidaituwar auren Zanirah da Aliyu. Na kudurtawa zuciyata zan yi amfani da mahaukacin son da yake min in ciyo galabarshi a kan Zanirah. Na dauki wayar Hajjah na yi kofar gida can inda babu kowa tsakanin motoci, na danna lambobin Yaya Aliyu wadanda tuni na haddace su. A washegari kenan da tafiyar shi. Ta yi ringing har bakwai bai daga ba. Kafin ya daga a fusace a na takwas, “Wai wane ne? Mene ne?” Wani sanyi da ya ratsa zuciyata ya tabbatar min har yanzu ina son Aliyuna, na kasa magana. So shu’umi ya rugurguza duk wata kalma ta bakina. Aliyu ya sake cewa, “Hello! In ba wani abu ba kuma sako bane zan ajiye ina sauri zan tafi Ibadan ne”. Cikin jarumta na ce, “Yaya Aliyu, kana da ikon zuwa Ilorin, Abeakuta, Benue da Akwa-Ibom ma amma bayan ka zo ka dauki Zanirah kun tafi tare. Ni wannan wane irin so ne da kake neman lika min kashin kaji cikin ‘yan’uwa? Yanzu kowa ya bude baki cewa yake, “Aliyu ya ki Zanirah ne domin Fa’izah”. To muddin son da kake ikirarin kana yi min na gaskiya ne ba kuma ka kaunar tashin hankali na da kasancewata cikin zargin jama’a, to ka dawo ka tafi da matarka yau ko gobe. Ko da baka son Zanirah ba haka ne hanyar da za ka nuna ba Yaya Aliyu. Wannan hanyar da ka bi ka nuna cewa ka ki bin abin da iyayenmu ke son ka da shi ne. Ka yi butulci ga alkhairin da suke hango mana ta hakan. In kuma don ka batawa Zanirah rai ne ka yi hakan, wallahi Zanirah baka gabanta, harkokin gabanta take. Dakacen auren take yi, sai don ba yadda za ta yi ne. Ni din dai nice cikin damuwa..... tunda ni dangi za su tsana, ni zan shiga bakin duniya...!” Da fadin hakan na kashe wayar baki daya ba tare da na tsaya sauraron amsar da zai bani ba, wadda na tabbatar ba shi da ita din. **** To Ali kam ya nuna ya haifu cikin uwarshi Zainabu, da ubanshi Na’ibi, kuma mai son farin cikin Fa’izah. A washegari ya dawo Giwa, inda ya saki kudi aka yi shagulgulan al’adarmu namu na Mallawa. Ya nuna tamkar komi bai faru ba, kamar Zanirah zabin shi ce ba zabin iyaye ba. Amma zuciyar ta fi duhun dare duhu. Babu yadda ya iya fadan da ya fi karfin ka aka ce sai ka mai da shi wasa. Iyayen nan bashi da saman su, Hajjar nan ta fi karfin komi a garemu in har muna da iko, in har bamu da shi, zamu yi iya kokarinmu mu nemo masu shi suyi mata. Sai dai abu ne da har illa masha Allahu ba zai taba kankaruwa daga zuciyarsa ba wato SON FA’IZAH! In ka ga ramar da Yaya Aliyu ya yi kamar wanda ya taso daga gadon asibiti bayan doguwar jinya. Jirgin karfe taran dare aka ajiye za su bi zuwa Lagos. Aliyu ya dubi Hajjah ya ce, “Tunda har anyi mai wuyar Hajjah, ba a bari in koma ni kadai in shirya in dawo in dauke ta? In gyara muhallina daga na saurayi zuwa na mai iyali. Saurin da gaggawar na mene ne? Cikin abokan aikina duka babu wanda na sanar mawa na yi aure kawai sai a ganni da mata kamar na sato ta? Yanzu haka a tsakiyar aiki nake zuwa Ibadan a bani lokaci ko da sati daya ne in je in dawo don Allah.....” Hajjah goyon Mahillah diyar Baba Barau take a bayanta ba ta ko dube shi ba. Ta sunkuci fidarta dake shake da cereal ta yi daki tana bambamin fada har da kumfar baki. Ta ce, “Karewar gyaran gida mai da gidan fadar shugaban kasa. Karewar rashin so Aliyu sayar da kan Zanirah garin Yarabawa. Amma kafarka-kafar Zannura”. Aliyu ya yi tsit! Na fashe da dariya, Zanirah ko tsabar takaicin yadda Hajja ke mai da ta matar cushe kamar jakar da ta rasa miji na san shi yasa ta zub da kwalla. Kamar za ta fashe da kuka ta ce, “Ni dai gaskiya Hajjah ki daina ce mun Zannura.....” Hajjah ta ce, “Zannuraini an fada, ainahin sunanki kenan (ma’abociyar haske biyu)”. Zanirah ta zumburi baki ta ce, “Hajjah Zunnuraini sunan namiji ne (Usman kenan)”. Hajjah ta ce, “Allah ya bamu albarkacinsa. Abin da yasa na saka miki suna Zannura saboda an haife ki Ranar Arfah, kuma kwanan watan ya yi daidai da ranar da Najeriya ta karbi ‘yancin kanta daga hannun Turawa, ga ki fara kal kamar auduga, ga kyau ga kyan hali. In baka so Zanirah ba ina jin babu zuciya da mazantaka a tare da kai”. Kalaman Hajjah sun girmi kunnuwan dukkanninmu daya bayan daya muka zame kowa ya bi hanya daban mai billar da shi wani sashe na gidan. Yaya Aliyu kuwa tunda ta dauko bayanin asalin sunan Zanirah ya bar dakin don haushi. Ta fannina nima na nuna ni ‘yar halas ce, nayi ma Zanirah gudunmmuwar (kayan amfanin kitchen) masu karko da tsada ‘yan Japan. Turare mai tsada ‘versace’ da ‘hugo boss’ na ango Yaya Aliyu, na ce, “A sha kamshin amarci lafiya Aliyu da Zanirah”. Sai a wannan lokacin ne Yaya Aliyu ya dago ido ya dube ni da wata muguwar harara da ban tsammana ba. Zanirah dake gefen shi cikin farin (swiss lace) mara nauyi mai yarfin (silver) dinkin buba da zani, kunshi baki sidik ya kama tafukan hannaye da kafafunta. Gashin nan ya sha relaxing ya kara baki ya kwanta a dogon wuyanta, amarya dai sak! Ta dago kanta a hankali daga kan yatsun kafarta ‘yan sirara itama ta harare ni. Ga mamakinmu duka sai cewa ta yi, “Wanea irin amarci kike fade Fa’izah? A ya yin da zuciyoyi biyu basu dai-daita da juna ba? Auren da ake lallashi da takurawa mijin ya so ka, shi kike ambatawa amarci Fa’izah? Kaico da auren da ake roko da lallashin mijin ya dauki amaryar yana gudu. ZAMANI YA CHANZA, ya kamata iyaye da kakanni irin Hajjah su gane hakan, su ajiye traditionality su bi modernity in dai ba fadar Allah da manzo bane. Domin maimakon a gyara zumuncin sai a bata, ko a zalinci daya a kasa kwatar masa hakkinsa don a dorar da zumunci”. Ta mike ta yi waje tana mai fidda zafafan hawaye. Na kasa cewa komi sabanin Yaya Aliyu da ya kyabe baki ya gyara kwanciyar sa cikin kujera. Tsam! Nima na mike na bar wurin. Ummi ta bimu da kallon tausayi baki dayanmu. Karfe shida saura minti talatin, iyakar rakiyar mu dasu Zanirah filin jirgin saman Kaduna, inda suka hau jirgi mai zuwa Legas. Sai a wannan lokacin ne zuciyata ta soma turiri, tana kurma ihun yarda da zancen Zanirah ZAMANI YA CHANZA.... ya kamata Hajjah da ire-irenta su ajiye traditional false beliefs su yarda love is a natural nature that cannot be totally eradicated. Yanzu ne na tabbatar na rasa Aliyu har abada! A lokacin da tayoyin jirginsu suka rabu da kasa. Sai na fashe da kuka a lokacin da wani bakon tunani ya bakunce ni, wato yanayin idanun Zanirah (oily eyes). Sau da dama Yaya Aliyu kan ce “Fa’izah ina ma kema irin kwayar idon Zanirah gare ki? Wallahi da na ji dadi na.....” Hawayena suka sake ninka na da.... Ga Zanirah nan complete din ta ka samu Aliyu. Hawaye na ya sake ninka na da, na kifa kaina a kafadar Ummi muka ci gaba da kukan tare. Inda wanda ya san sirrin son da nake wa Yaya Aliyu, to Ummi ce, don tare muka rayuwa a makaranta fiye da Zanirah dake Giwa a lokacin da muka mallaki hankalin kanmu. Babu irin tsarin da ban yiwa rayuwar aure na da Yaya Aliyu ba. Yadda za ta kasance, yadda zamu yi ta, yadda zamu gudanar da ita da yadda zamu tafiyar da ita, amma a yau Hajjah and her false beliefs (a ganina) sun rushe komai. Lokaci guda wata irin sabuwar zuciya ta shige ni mai dauke da sabon perception. Na san dadin ‘So”, haka na san dacin rasa shi. In Allah ya yarda ba zan yarda in auri wanda bana so ba! Ba zan yi auren zumuncin ba, ba zan yi auren A.B Family ba. Zan zamo mutum ta farko da za ta canza A.B Family, zan zamo mutum ta farko da za ta yi auren soyayya a cikin zuri’ar Abubakar Bamalli Giwa. Bare zan aura wanda zuciya da ruhina ke so da kauna, wanda zai jiyar dani dadin soyayya da zakin dake cikinta. Ko duk duniyar nan za ta taru a kaina ba zan yi auren A.B House ba sai wanda zuciyata ta aminta da shi. Nake so, yake sona da irin soyayyar da muka yiwa juna ni da Yaya Aliyu. **** Yau wata guda kenan da tafiyar su Zanirah in har na lissafa dai-dai, amma babu ko duriyarsu. Aliyu dai ya yi waya wa Hajjah cewa yana bakin aiki a Ibadan, don haka ba zai samu zuwa gida karshen watan nan ba sai na sama, suna tare da amaryar a Ibadan. Uhm! Namiji kenan. In ji Umma Sulaiman Shu’aibu ‘Yan Awaki. Kudan zuma, indararon roba ta ko ina zuba kake. Allah ya gyara. Takurawar da Mansur Modibbo ke min a gida Giwa da Zaria yasa duk garuruwan suka fice min a rai. Domin dai ni tunda na rasa Yaya Aliyu bana jin zan iya wata aba wai ita soyayya nan kusa. So dai guda daya ne, na sha shi na warke, bana fatan Allah ya kara maimaita mini. Ko ina fatan hakan ba cikin garuruwan nan uku ba, Zaria, Giwa da Kaduna. He must be a stranger! Very far away!!! Ban gama jinyar wancan ciwon ba yake nema na da in dasa wani, “Shin shi wannan bai ma da tausayi ne Ummi?” Na tambayi Ummi a yammacin wata asabar. “Wai da me zan ji ne? Yeah! I would love to marry a stranger, but he must be from far..... and he’s a stranger but not from far....” Don haka na rika yin baya-baya da shi da kora da hali wanda ya fi kora da sanda, duk da mahaukacin son da yake min kuwa. Ba wai don yana da wata makusa ba, dukkan halayen shi ababen yabo ne. Ni da Ummi mun kasance cikin kewar Zanirah, kullum kamar wadanda aka yiwa mutuwa. Hajjah kanta daurewa take tana sabgoginta, amma rashin Zanirah a gidan ita ma yana dukan ta. Daga mu yi tagumi, sai mu kwanta. Mun daina barin yara su kunna T.V a gidan balle radio. Sai mu ce sun dame mu. Mun dai mai da gidan kamar gidan mutuwa, farin cikinmu ya takaita, ba Zanirah ba Aliyu. Muna cikin kewar da ba za ta misaltu ba, ko yaushe muna kwance a daki kamar tsumma. Don haka na ji dadi da Hajjah ta kawo shawarar wai mu tafi Kano gidan Yaya Rabi mu huta gajiyar baki kafin fitowar takardun karatunmu mu ci gaba da karatu. Dukkanmu ba karamin mamakin wannan magana ta ci gaba da karatu muka yi ba. Na yi tunanin ko Hajjah ta yi hakan ne don ta samu na manta da Yaya Aliyu gaba daya. Abin da ba ta sani ba shine, tuni na bude kundi na sanya Aliyu a ciki (as a past tense). Wallahi ko da zan mutu babu aure, babu huldar da za ta shiga tsakanina da mijin Zanirah (other than) ta ‘yan uwantakar da ta hada. Muka shirya tsaf sai Kano. Yaya Rabi mutum guda har da rabi don zumunci da son dan uwa. Zan iya cewa duk ‘ya’yan Hajjah babu wanda ya kaita kirki. Zama da ita da raha irin ta mijinta Yaya Muftahu ya wanke mana damuwa kakaf. Don sai ya zamanto Yaya Rabi ta cike mana gurbin Zanirah, Yaya Muftahu ya cike mana gurbin Yaya Aliyu. Sai muka kwantar da hankalinmu muka bude sabuwar rayuwa mai dadi. A irin hirarrakin da muke yi da Yaya Rabi ta kan so a sako hirar su Zanirah, ko da wasa Yaya Rabi ba ta taba sanin mun so juna ni da Yaya Aliyu ba. Irin maganganun da take sakin baki tana fadi a kansu a gabana ya kan kona min rai ya tado wani kwantaccen ciwo da na riga na samu ya warke. Akwai sanda za ta ce, “Allah kadai ya san irin soyayyar da suke barzaa yana muzurai yana cewa baya so din” Ko ta ce, “Uhm! Su Zanirah ana can Ikko ana romansewa”. Ko ta ce, “A gaskiya Zanirah ta caba miji. Ga kyau ga kuma kyawun hali. Aliyu Mutum ne wanda zai shagwaba matarsa, ya bita da duk yadda yadda ta yi da shi, ba irin Bashir, Fa’iz da Mus’abu bane”. Na kan kau da kai ne kamar ban ji ta ba. Ummi ta yi dariya kawai. Haka nan ban taba tankawa ba sai Ummin. Tsakanina da Ummi yanzu mun koma mun dinke kamar da. Domin ta lura in har tana son hulda dani to fa sai ta ajiye zancen makiyina Fa’iz a gefe. Ba ta zancen Fa’iz a gabana kamar yadda duk hotunan shi da ire-iren kayan da yake aiko mata ta tattara su ta aje a wata katuwar jakar Hajjah a Giwa. Amma dai ai na ji TAKORI ta ce, “ZUCIYAR MUTUM, BIRNIN SA!” [12/02 6:09 PM] Sumayya Takori: Daki guda Yaya Rabi ta ware mana mai dauke da bayan gida, kananan gadaje biyu, sai jar kilishi da ta malale ilahirin dakin da jan labulaye. Karamin bed-side fridge, sai mudubin dogon yaro mai sheki da kayan shafe-shafe da feshe-feshe, da kwabar adana suttura (wardrove) ta jikin bango. Kamar yadda mazan Kano samari da magidanta basa ganin kyawawan ‘yammata su kyale, to haka fita ta gagaremu ni da Ummi. Har suna aka sakawa gidan Aunty Rabi a layin wai Gidan Mallawa. Kiri-kiri muna gani za a gayyaci Yaya Rabi biki ko suna amma mu haramtawa kanmu zuwa muna ji muna gani, domin muddin muka fita, to kuwa la-shakka ba zamu dawo mu kadai ba maza basu biyo mu ba. Kofar gidan Yaya Muftahu baya rabo da mota da vespa, wanda mu bamu saba hakan ba sam a namu garin sai hakan ya dame mu ya zamo mana sabo ya takurawa walwalarmu. A hankali na soma fuskantar Ummi na canjawa, ta fara saurararsu. Da na yi mata magana sai ta yi murmushi kawai har mulmulallun kumatunta suka lotsa, ta ce, “In mun koma inda muka fito ba shi kenan ba? Abu ne na dan lokaci. Namiji abokin rayuwar mace ne ba za ta taba rabo da shi ba”. Cikin watanni hudu a gidan Aunty Rabi jikina ya soma wani irin canzawa, tsayina ya fito na mike sosai. Yawan kaimu (Zaynab Saloon) da Ya Rabi ke yi a (Mukhtar Mohammed Link) yasa gashina ya ware ya yi tsayi da taushi duk da ba (relaxing) muke ba wankewa ne da (steaming) kawai. Haskena ya dan fito duk da bani da haske. Kamannina na Mallawan usli ya fito sosai, na yi kumatu subul-subul, saboda kwanciyar hankali. Kugu da kirjina duk sun canza kiyasi, tabbacin budurwa matashiya ‘yar shekaru goma sha takwas. Shin ma na taba gaya muku ko wace ce Fa’izah Ahmad Abubakar Bamalli Giwa??? Ban taba ba, illa kawai kun jera ni a sahun kyawawan Bamalli. To eh, ba zan yi musu ba a nan, sai dai akwai wasu ‘yan bambance which I didn’t clarify (da ban farrake ba) ga masu karatu na. Ni kaina ban san ina da wadannan qualities din ba sai da na shiga shekara goma sha takwas da zamana a Kanon Dabo. Duka A.B Family ni kadai ce mai duhu (choculate). A yau, kaina na tsurama ido cikin mudubin dogon yaron gidan Aunty Rabi bayan fitowa ta wankan la’asar. Ina da madaidaicin tsayi, wato ba doguwa ba ce ni, ba kuma gajeriya ba. Doguwar fuska mai dauke da mulmulallun kumatun hutu subul dasu masu nuna bana cikin wahalar rayuwa ko kadan, wadanda Allah bai halacci kwayar kurajen (pimples) ko daya a kansu ba. Idanuwana farare sol da bakin zanen ido mai walainiya na daukar hankali. Madaidaicin baki wanda ba kankani bane can-can ba kuma kato bane, jerarrun hakora farare sol, jere reras a cikin shi. Karan hanci siriri kamar an saka ruler an daidaita mata shi a tsakanin idanunta. Tunda ya taho daga sama a mike yake bai lankwashe ba ya dire kyam saman bakinta. Tsagin Mallanci 2-2 dake gefen fuskar Fa’izah su suka fitar da Mallancin ta sosai da an ganta babu tambaya zuriya’ar Abubakar Giwa ce. Sumar kaina kan sakko har bisa kafadu, ya kwanta lamban. Wanda kitson shi kwararriyar ma sai ta hada da dabara. Duk da haka kuma cikin kwana hudu ya warware da kanshi ba tare da ta sanya kibiya ta warware shi ba. Don haka ta hakurewa kanta yin kitso kullum sai dai ta kalmashe shi cikin ribbons (bound). In Aunty Rabi ta daddage ne take kalbace shi yar-yar ta kama bakin ta matse da dutse da roba sannan yake zama. Ba ta taba tsugunnawa wata mace ta kama mata kai da sunan kitso ba tun tasowar ta baya ga Hajjarta. Yalwar gashin kanta shi ya taimaka wajen inganta gashin ido da na girarta. Hakan bai ishe shi ba sai da ya bi ya kwanta a fatar jikinta kafataninsa. Irin wadanda Sadanis basa yiwa (halawa) ya yin aure. Don haka a kullum Fa’izah cikin (shower-shaving) take duk sati biyu zuwa uku don fitar da kyan fatar jikinta da kwantaccen gashi ke boyewa. Idan tana tafiya kai ka ce rangaji take, komai ya yi masha Allah, komai nata danye ne sharaf. Jikinta kamar mai shiga wankin fata a inji, domin jikinta ya fi fuskarta haske. Ga zazzakar murya kamar diyar Shata, Fa’izah mace ce mai tsiwa, don in ta fara tsiwarta da mitarta har hacinta tsattsafar da gumi yake yi. Ba a yi mata ta kyale. Tana da kafiya da taurin rai, ba kankanin abu ke sanyata kuka ba. Tana da wuyar lankwasuwa a kan abin da ta kudurtawa zuciyarta. Watanni hudu kenan muna zaman garin Kano, ko in ce zaman jiran fitowar jarabawa, zama mai dadi da ma’ana. Hankalinmu a kwance, rayuwar baya duka ta zama tarihi, komai ya zamanto kamar bai faru ba. Don yanzu har na kan iya zama ayi hirar su Zanirah dani ayi dariya ba tare da na ji komai a raina ba. Zan iya cewa, soyayyar Yaya Aliyu babu ita ko kadan ta bace daga raina. Zamanmu da Yaya Rabi (accounter) a bakin G.T na Gyadi-Gyadi (branch) mun karu da abubuwa masu yawan gaske. Ga dai girke-girke na zamani muna koyo, kwalliya kala-kala, tattalin miji da nuna masa soyayya mai tsafta mai tafiya da ZAMANI da CHANJE-CHANJEN sa, tsafta, kissa da tarairaya, duk mun nade su cikin kanmu daga gidan Yaya Rabi. Wai yanzu ma kokari muke Hausar mu (accent) dinta ya yi dai-dai da na ‘yan Kano, domin masana luggogin Nigeria sun tabbatar da cewar Hausar Kano ita ce mafi karbabbiyar Hausa a Nothern Nigeria baki daya. Domin a lokuta da yawa in muna magana Yaya Rabi da Yaya Muftahu da dansu Abdul dariya suke mana, wai “Kauyawan Giwa”. Shi yasa muka yi zuciya muka koya a hankali. Yau lahadi, daga Yaya Rabi har Yaya Muftahu basa zuwa aiki. Mu kan kasance ne wunin ranar da yamma a shagunan Breirut Road irin su Captano, Arebian Sweets da ire-irensu, ko manyan shagunan Kano irin su Country Mall, Ado Bayero Mall ko Grand Square da Well-Care don yin sayayyar amfanin gida da ta kayan makulashe. To yau ma hakan, dawowar mu gidan kenan, muka kai ledojin hannayenmu kitchen ni da Ummi, muna adana kowanne a freezer masu bukatar firinji, muna saka su. Yaya Hauwa ta kira wayar Ya Rabi ta sanar da ita jarrabawar mu ta fito. Amma dole ana neman mu a makaranta zamu karbi ‘testimonial’ da ‘statement of result’ ko da zamu duba ‘online’ ne. Don haka washegari muka nufi Kaduna da direban Muftahu. Abdulrahaman ma ya saka naci sai ya bimu saboda su Junior autan Maman Kaduna mutanensa ne. Muka tattara duka Kaduna ta diba, su kuma kowanne ya nufi office a safiyar litinin kenan. A Jabi Road komai ya canza, tun daga bakin gate na tabbatar Baban kaduna Allah ya kara masa budi da falala hade da nasara cikin al’amarinsa. Hyundai, Jeep-Jeep har guda uku sai neman fashewa suke yi don koshi da kyalli a harabar adana motoci. Haka korran (grass carpet) sun malale harabar gidan da furanni kala-kala masu dadin kamshi. Komai na falon ya canza sai kyalli yake yi. Ita kanta Mama ta kara kirbewa dama ga ta masha Allah tun-tuni, kamar za ta tsage cikin (sofa-bed). Kai! Wadannan mutane suna cikin daular da babu wani cikin A.B Family dake cikin rabinta. Na girgiza kai tare da sallama, da gudu na karasa jikin Mama a (sofa-bed) muka rungume juna domin mun jima bamu hadu ba, tun bikin Zanirah, ga kuma soyayya mai karfi tun fil’azal wadda ta zarta ta jini kawai, har ma da haduwar jini da Allah ya hada a tsakaninmu. Mama ta ce, “Oh! Su Fa’izah an gudu Kano don ba Zanirah ko duriyarku ba a ji, ko waya babu, kun kyauta kenan?” Na ce, “Kin san Baban ABU ya hanamu rike waya Mama, kuma na je ne don na huta na samu nutsuwa. Amma wallahi Mama kullum kina raina”. Ta ce, “Na sani, na kuma yarda Fa’izah”. Ta dubi Ummi ta ce, “Sai tsohuwa!” Ummi ta shagwargwabe fuska ta ce, “Allah Mama ki bari....” Muka sa mata dariya ganin yadda ta yi da fuska kamar za ta barke da kuka. Mama ta ce, “Mutuminki kullum ya yo waya korafinsa daya, yaushe za ki baro Kano? Yau dai ga Ummi a gidan nan, anjima zai yo waya bakina ya huta cewa, ban sani ba”. Cikin matsananciyar murna Ummi ta makalkale Mama tana dariya kamar ba surukar ba, ta ce, “Allah da gaske Mama Ya Fa’iz na tambaya ta? Don Allah Mama ya muryarshi ta koma? Ban taba magana da shi a waya ba tunda ya tafi”. Mama ta ce, “Muryar Fa’izu ta karye (kwata-kwata) da Ukrainian language da Belarusian. Da kyar nake fahimtar Hausar shi. Su Shu’aibu ba ma sa ganewa gara ma in yana Larabci ko Turanci”. Ummi ta yi zugum (her passion for him heightened). Tana duban Mama hannuwa tallabe da fuska ta ce, “Kin san Allah Mama, na yi dana sani tunda fari da na san haka ne da na shiga Arabic Club da Fa’iza tayi-tayi dani in shiga a makaranta na ki, don a ganina yawa ne in tsaya koyon Larabci tunda ba a fiya amfani da shi a nan Nigeria ba”. Mama ta ce, “Ayya! Kin yi babban kuskure, domin Larabci shine harshe mafi soyuwa a wurin Ubangiji da ya zabe shi a cikin harsunan duniya ya saukar da Alkur’ani da shi. Har yake cewa, “An saukar da shi Alkur’ani BALARABE....” Kuma Annabi (S.A.W) ya ce, “Ku so harshen Larabci saboda uku. Na daya ni Balarabe ne, na biyu Alkur’ani Balarabe ne. Na uku harshen ‘yan Aljanna shine LARABCI!” Ummi kamar ta fashe da kuka, na yi dariyar mugunta na ce, “Rabu da ita Mama, ba zan taba manta sanda su Ummi suke min dariya don ina Alifun Ba’un ba. Wahid-Ithna-thalatha ban iya 123 da ABCD ba, ga shi na muku wayo. An ce ana jifan tsuntsu biyu da dutse daya, don a ci amfaninsa. Yau Ummi Turancin me za ku nuna min? Sai dai in nuna muku LARABCI”. Na yi mata gwalo. Ummi ta yi zugum, da alama kalma ta kare a bakinta. Na yi dariya mai isata har cikina ya kulle. Ummi ta zo iya wuya ta tashi ta fice daga dakin, muka ci gaba da yi mata dariya. Mama ta ce, “Sai yaushe za ku je wa Hassanar ku ne?” Tana nufin Zanirah. Na ce, “Kai-kai! Mama so soon haka? Ai ba a zuwa gidan amare sabon aure sai sun haihu”. Mama ta lakace min hanci ta ce, “Ai su da yake sun damu daku zuwan su uku duk kuna Kano. Ba kuma don kowa suka zo ba sai don su ganku”. Na ce, “A’a Mama, da da gaske sun damu damu da sun bimu inda muke. In babu jirgi akwai mota, tsakanin Kaduna da Kano awa biyu ne kacal. Ke dai basu gama amarci bane ma je suna in da rabo”. Mama ta ce, “Kamar mai gani har hanji an zo ana ta laulayin ciki kamar wadanda suka yi tuntube da shi a dokin kofa. Ku yaran yanzu ko kadan cannot excercise patience. Mu zamanin mu sai amarya ta shekara biyar dakin miji ba ta samu ciki ba”. Duk da zuciyata ta dan sosu ban bari Mama ta gane ba. In Aliyu bai son Zanirah, ai ita Zanirah tana mutuwar son shi. Za ta san duk hanyar da ta bi ta janyo hankalin abinta gare ta. Sai na samu kaina a yau ina mai dan KISHIN Zanirah Mukhtar Abubakar Bamalli Giwa! Karfe tara na dare duka al’ummar gidan na bisa tebir suna cin abincin dare, har mu da muka bakunci gidan. Da tuwon laushi miyar alayyahu da aka wadata da naman Turkey (talo-talo) aka kuma shirbine ta da man shanu dan asalin GIWA. Na lura Abdul zubi kawai yake ba kakkautawa, ban san sanda na yi dariya ba. Yahya mai bin Fa’iz ya ce, “Kalau kike dariya ke kadai?” Na ce, “Baka ganin yadda yaro ya samu abincin zage-zagi ya rude baya so ya bari ya fara hadiye na bakinsa kafin ya kara loma?” Abdul ya yi murmushi, ya san da shi nake. Can kuma ya ce, “Yanzu ba zan ce miki komi ba sai mun koma Kano kina cin bandashe (gurasa da kuli-kuli) tukunna”. Kowa yasa dariya. Daga daki Mama ta fito tana fadin “Ku yi sauri Fa’izah, cin abincin ne kuma ya koma hira da shewa? Aiken ku zan yi unguwar Sarki ku amso min ankon ‘yar Hajiya Saratu da kun gama, dare yana yi”. Karar wayar landline dake gefe ya sanya kowannensu yin wurgi da cokalinsa ya nufi inda wayar take, kokawa fa ta kaure domin Ummi, Yahya, Shu’aib da Junior kowanne ya ci alwashin shi zai fara daukar wayar ko ta halin kaka. Mama ta ce, “Yau ina ganin sakarci, to bari in raba gardamar nan. Duk cikinku babu mai tabbacin kiran nasa ne ko ba nasa bane, tsammani kuke Fa’izu ne, kuma ba lallai ya tabbata shi din bane haka ne?” Duk suka tsaya suna tsuma, ta ‘kauna’ da ‘doki. “Don haka ke babbar Yaya (ta nuno ni) dauki wayar ki jiye mana waye kamin wani ya dauka don a raba gardamar”. Na yi dariya cikin ginshira na tsiyaya ruwan FARO mai sanyi a tambulan na soma kwankwada. Sanyin ruwan na sanyaya makogarona, yana taimakawa wajen digesting (narkewar) daddadan tuwon da na ci. Na yagi tishu na goge baki da hannu. Ummi ta kufula ta ce, “Kina gani fa Mama sai ta gama yi mana yanga”. Mama ta ce, “Kai, dadina dake gajen hakuri Ummi”. Na yi murmushin tura haushi sannan na mike na nufi wayar landline da har lokacin ba’a bar kira tana tsinkewa ba, wayar na daga na amsa da “Assalamu Alaykum!” Shiru kake ji, ga shi da alama ba a ajiye ba. “Hello!” Shima shiru. Na sake sallama aka yi shiru, ina shirin mikawa Mama wayar cikin kufula da mamakin wannan ikon Allah, ka kira waya kuma ka yi shiru kudinka na tafiya a banza. Muryar mai cike da ginshira ke tambayar “Impertinence Fa’izah ko?” (Fa’izah mai tsiwa?). Tuni jijiyoyi masu ba da jini shi kuma ya yi circulating dinshi ga sassan jiki sun tsaya cak! Da ba da aiki. Jijiyoyin cikin kai masu ba da doka da oda su ma sun yi yajin aiki na (temporary). Muryar da ba zan taba mantawa da ita ba, muryar dan uwa amma MAKIYI. Muryar FA’EEZ, HAFIZIN HAJJAH, FA’IZU MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA. Ban amsa ba. “Kaif halikum Fa’izah? How are you Fa’izah?” Maimakon na amsa sai na yi azamar cire wayar daga kunnena na mikawa Ummi jin wani mugun fushi ya taso min wanda duk kokarin zuciya ba za ta iya boye shi a gaban kowa ba, including UWA-MAHAIFIYA dake gabana tana karanta duk wani motion dina a kan wayar danta da kyawawan idanunta, masu cike da matsananciyar kauna gare ni. Irin kaunar nan da baki baya iya bayyana ta, domin Allah ne ke assasa ta. Sai na zare wayar sannu a hankali daga kunnena na mikawa Ummi, tare da zare jikina daga cikinsu na yi dakin Mama don bakin ciki kamar in rushe da kuka. In da abin da na tsana a duniya to abin da zai tuna mani da shekarun da na kasance cikin fargaba da ukubar Yaya Fa’iz ne. Balle ya tuna min da shi kansa. To gaba daya yau muryarsa na ji a cikin kunnuwana, muryarshi ta dawo min da ranakun can baya marasa dadi da na rufe babin su ta dawo da tsanarsa danya a zuciyata. Haka na yi sallar isha ina ta sake-sake. Da na idar na bishi da muguwar addu’ar Allah ya gama shi da masifar duniya da ta lahira a can inda yake. Yasa a fatattako shi daga karatun ko garin tukin jirgin, jirgin ya fado ya ragargaje da shi. Amin summa amin. Don kam hakika ni mai bakin ciki ce da duk wani ci gaban FA’IZ GIWA kamar yadda yake a gare shi shima. A daren Ummi hanani barci ta yi da labarin hirarta da Fa’iz. Da hanzari na taka mata birki.... “Excuse me please. Shin Ummi ina ruwa na ne? Me ya shalle ni cikin wannan al’amarin naki? A duk lokacin da za ki yi hira, ki yi wadda ta shafe ni ban da ta Fa’iz! Na tsani Fa’iz!! Na tsani duk wani abu da ya shafe shi ban da iyayen da suka haife shi da ‘yan uwansa wannan (Individualistic matter) ne (sha’anin mutum daya). A duniya bani da abin ki, abin tsana, abin neman tsari da kariya daga sharrin sa bayan shaidan, sai Fa’ezz Bamalli”. **** Washe gari karfe goma na safe Queen Amina College ta yi mana, inda muka hadu da malamanmu da muka jima bamu gani ba. ALHAMDULILLAH, takarduna sunyi kyau har fiye da na Ummi, na tashi da Credentials a gaba dayan ( 9 Subjects) dina. Ummi tana da seven credits, sai dai tana da A a Fine-Art. A shekarar duka muka samu gurbi a jami’a, inda Yaya Aliyu ya samarwa Zanirah gurbi a jami’ar Lagos (UNILAG), inda za ta karanci likitanci (Medicine). Daga Baba na har mahaifin Ummi babu wanda bai yi mamaki da umarnin Hajjah ba na ta amince a nema mana gurbi a jami’ar Bayero ni da Ummi mu koma Kano da zama wajan Aunty Rabi, sai hutun karshen kowanne zango ta amince mu je Giwa da sauran garuruwan Zaria ko Kaduna. Yaya Muftahu shi ya shiga ya fita ya samar mana gurbi a fannin da kowacce take so, inda aka bani B.A Arabic, Ummi kuwa B.A Hausa. Duka a Faculty daya wato (FAIS) sai dai tsangaya (Department) da suka bambanta. BAYERO UNIVERSITY KANO Rayuwar mu cikin jami’ar Bayero, sabuwar rayuwa ce a garemu da ta zo da sabon salo irin na kowanne JJC (Joiny Just Come) a jami’a. Abubuwa da yawa (which are normal) ga sauran daliban jami’ar (is abnormal to us), irin su shan hannu da maza da wasu matan marasa kamun kai ke yi da sunan jami’anci, shan taba sigari da samari da matasa ke yi wanda ba a yi sam a A.B Estate. Shan lemo a shago a tsaye ga matan aure da ‘yammata, ko saka wando ga wasu matan Hausawa duka abin kallo da waiwaye ne a gare mu kafin mu saba. Mu kam bamu saba gani ba a inda muka taso, don haka muka shiga dari-dari. Sannu a hankali idonmu ya zo ya bude tangarau muka fahimci (reality) na rayuwar jami’a ba (peer group infuluence) bane (koyo abokan karatu ko tsararraki) kawai (imitation) ne wato (kwaikwayo) ‘to fit together’ (a zama iri daya). Akwai wadanda karatu ne ya kawo su ba (imbibing) wato kwaikwayon abubuwan da canjin zamani ya kawo ba. Akwai kuma ‘yan ‘imitation’ din ko da a ce ransu bai so don kar a ce musu kauyawa. Irin wadannan su nake gani a matsayin kauyawa ba wadanda suka kalla a kauyawan ba. Su kuma ina kallon su ‘yan ra’ayin rikau. Irin wadannan mutanen a duk inda suka tsinci kansu basa canza ‘doctrines and principles’ dinsu kuma da wuya a rinjaye su daga kan abin da suka riga suka yarda da shi. Yau bamu fito lacca da wuri ba sai wurin karfe biyu na rana, in ban da kururuwa ba abin da cikina ke yi, don ko karin kumallo ban dauka ba. Babu yadda Yaya Rabi ba ta yi dani ba don in zauna in karya amma na ki, saboda sanin halayyar Dr. Ramadhan Alkali, muddin ya riga ka shiga aji to ka rasa laccar sa kenan. Ni kuma ba zan so in rasa laccar ba, don a cikinta ne zai fadi (exam concentration area) din kwas dinsa. Tafe nake a hanzarce don kokarin isa ga ‘coke village’ in samu abin da zai warware min hanji. Idanuwana sun rufe saboda yunwa ban kula da budurwar dake tsugune tana goge takalminta da ya yi kura da tishu don ganina ya dushe tsabar yunwar dake addabata, muka yi karon ba zato da budurwar saura kadan ta kifa. Ta mike a hanzarce za ta yi bala’i. Wa zan gani? Haulatu Shehu, kawarmu (Head-Girl) a Queen Ameena, Haulatu S. Shehu. Na ce, “Haulatu Sani?” Ta ce, “Fa’izah Ahmad?’ Na ce, “Ya Jamilal Munzar! (wato ya mafi kyawun masu gani)” A guje muka sheka muka rungume juna tare da juyi rikija-rikija muka rankaya coke village tare. Hirarraki da tambayoyi tamkar su kashe mu. Kamin wannan ta kai aya wannan ta antayo tata tambayar. Ta ce, “Fa’izah kuna cikin garin Kano amma ko ki neme ni?” Na ce, “Ayya Haulatu, ban san gidanku ba, kin ganni nan bayan unguwar su Aunty Rabi Gadon Kaya (Yarda Avenue) ban san ko ina ba, ban da kantuna da muke zuwa sayayya”. Ta ce, “Ina address din da na baku tun muna makaranta da phone no?” Na ce, “Mun baro su cikin littafinmu a Giwa”. Daga nan hira ta barke. Ta ce, “Lallai ne Ubangijinmu ke nufin mu da zumunci tunda har ya sake hadamu a nan. Allah abin godiya. Ina Ummi?” Na ce, “Ummi tana makarantar nan ita ma a Hausa Department”. Ta ce, “Ni ina Mass-Communication, kai ni Haulatu na zo jami’a a sa’a tunda na kara haduwa daku. Tun rabuwarmu babu ranar Allah da za ta fito ta fadi ban tuna ku ba”. Na ce, “Duk kin canza Haulatu, kin yi kiba kin kara kyau da haske, ko kin yi aure ne?” Ta ce, “Har da albarkarsa na like jikina. Matar Abdullahi Yakasai ce. An daura min aure bayan candynmu. Bikin ne dai ba ayi ba har yanzu Abdullahi ya tafi (Law School) sai ya kare nan da wata shida”. Na ce, “Sunan kanina, Allah ya sanya alkhairi Haulatu. Sunan kanina mai bina kenan”. Ta ce, “Kwarai, kin taba gaya min kina da kani Abdallah, yanzu ajinshi nawa?” Na ce, “Abdallah ai an zama samari, yana SS I, Walida na JSS 2”. Ta ce, “Me kike karanta?” Na gaya mata harshen Larabci. Ta ce, “Kin burge ni Fa’izah, Allah ya kara fahimta, ya kara mana kaunar Manzo (S.A.W)”. Kai hirar da muka kwarara ni da Haulatu a ranar tana da yawa. Duk tarihin mijinta Abdullahi wanda ya kasance dan’uwanta ne ta bangaren mahaifiyarta sai da ta gaya mini. Sai da muka yi (missing) lacca guda saboda dadin hira, dama Haulatu uwar surutu ce barin in sun hadu da Ummi. Haduwar Ummi da Haulatu sun kusa shidewa don murna. Daga ranar amintarmu ta ci gaba da Haulatu daga inda muka tsaya a sakandire school. Naja’atu na ABU Zaria in ji ta. Duk inda ka ga Zarah ka ga wata wato ni, Ummi da Haulatu. Mun je gidansu a ‘Yankaba ba sau daya ba, ba sau biyu ba, ita ma ta zo mana, har kwana take in lokacin jarabawa ne mu yi karatu tare, musamman da gidan Aunty Rabi ya fi kusa da makaranta. Ta saba da Aunty Rabi sosai. Albarkacin Haulatu babu inda ba ma takawa a cikin Kano, daman an ce sai da dan gari a kan ci gari. Ummi ta yi manema har ba adadi, ni kuwa rashin sakin fuska da kora da hali wanda ya fi kora da sanda shi ya sanya duk wanda ya zo wajena da sunan so baya marmarin sake dawowa. Ummi kan ce lokaci ne, lokacin abu ayi shi. Ni ba auren su zan yi ba kawai suna rage min lokaci. Sai in kama baki in yiwa Ummi kallon mamakin yadda jami’a ta sauya ta lokaci guda. A haka muka kare 100 level bayan jarrabawar da ta kusa tsaga mini kwanya muka fara 200 level. Idon mu ya kara budewa sosai a sanadiyyar ratsawar ilimi da cudanya da masu shi. Hausar bakinmu ta dai-daita da ta ‘yan Kano, kai ka ce nan ce mahaifar mu. Mu muna using N a muhallin R, wannan shi ke sa Haulatu da sauran abokanan karatunmu ke cewa muna Hausar Giwa. In Haulatu ta tashi tsokanata sai ta ce, “Kin tuna Ummi ranan nan a anguwan sarki? Ba za ku bar wannan maganan ba? Yaya Rabi kin ga Ummi na tsokanana ko????” **** [13/02 6:26 PM] Sumayya Takori: Ranar litinin din nan rana ce da ba zan taba mantawa da ita a tarihin rayuwata ba, domin wani dan karamin bangare da ta taka cikin tarihin nawa. Na shigo aji a makare ainin domin sai da muka biya muka ajiye Yaya Rabi a asibitin Malam wajen awon tsohon cikin da take dauke da shi, muka kuma mai da ita gida sannan Yaya Mufty (sunan da Yaya Rabi ke kiran mijinta Muftahu) ya kawo mu ya ajiye ya koma (office). Jikina har bari yake domin na ji jiya ‘yan ajinmu na fadin anyi sabon lecturer mara daukar wargi, madadin Farfesan dake daukarmu darasin. Sanye nake da shudiyar danyar atamfa (exculusive) mai ratsin ruwan hoda da mayafi launin sararin sama mai haske. Bayan wannan babu komai a fuskata sai farar powder da na muttsika da vaseline (lip balm) a siraran labbana wanda ya kara musu taushi da kyalli. A rayuwata bana rabo da zizara kwalli a idanuna, kwallin (kajal) baki yana kara lafiyar ido, yana kuma kara fiddo min da gazar-gazar din gashin idona. Ina kokarin zama a kujera ya ce, “Get out please..... (fita waje don Allah)”. Wata kunya ta taso ta lullube ni ganin yadda idanuwan maza da matan ajin ya dawo kaina. Malam ya sake daga murya ganin na yi kasake! Na kasa zama na kuma kasa fita. Ya ce, “Get out I said (fita na ce)”. Na daga ido cike da kwalla a hankali na dube shi. Baki ne mai kyau na a buga a kalanda ko ayi tallan advertisement board da fuskarsa. Bai da tsayi can-can, yana tsaka-tsaki. Fatarshi goge da zuzzurfan ilimi a kananan shekaru. Gwiwoyina suka sage tamkar an rarrade su da murfin kwano haka na cira kafa kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki na yi tattaki a hankali na bar ajin. Wani abin mamaki sai ya kasance ban ji haushin mutumin nan ba a bisa korar karen da ya yi min a kan lattin awa daya. Sai ma haushin kaina mai tsanani da na bar Yaya Muftahu ya fara kai Yaya Rabi awo maimakon ya fara kawo ni. Haka nan na samu kaina da gwada yadda yake magana a sarke “get out.... get out I said!” Na yi murmushi na kwashi takarduna na yi (main library) don in yi assigment maimakon in zauna zaman tunanin malami mara daukar wargi, mai magana a sarke da in’ina. **** A gida nake bai ma Yaya Rabi labarin karonmu da sabon laccara mai tangardar harshe. Ummi ta ce, “Na ko so in ganshi, baki dan kakkaura mai yanayi irin na Yaya Bash yana driving wata (vauxhall) shudiya. Gaskiya gayen ya yi a rayuwa Aunty Rabi. Sai dai na yi mamakin yadda karamin yaro kamar wannan ya kai ga matsayin senior lecturer?’ Rabi ta ce, “Meye abin mamakin a ciki? Mai first class ko 2.1 zai iya zama lecturer komai kankantar shekarunsa. In kuma a waje ya yi karatun speed din ba daya bane. Mufty shekara daya kacal ya yi masters a Aston University”. Ummi ta zaro ido ta ce, “One year Aunty Rabi?” Ta ce, “Baki bina bashin rantsuwa ki shafa ki ji wai shafa-labari shuni”. A washe gari ma cikin ikon rabbi na yi latti. Malamin jiya shine a ciki, sai na ji hantar cikina na rawa, kafafuna suka fara hardewa. Tun ganina na farko jiya da mutumin nan wani sabon al’amari ya bakunci ruhi da zuciyata, ba zan ce so bane, zan iya cewa kwarjini yake mun, kuma yana razana ni da kwarjinin. Yadda zuciyata da hantar cikina basu bar karkarwa ba, haka kafafuna basu bari ba. Yau ma dai ta jiyan aka kwata, wato ya koroni waje. Wannan karon kam raina ya baci, domin karkarin lattin nawa na mintuna goma ne kacal. Muna cin abinci a (Al-Amir) na aje cokali na ce, “Wallahi Ummi wulakancin dan iskan malamin nan fa ya soma isata, asarar lacca biyu kenan ya yi mani”. Haulatu ta ce, “Wai wane ne?” “Oho! Na san sunan shi? Yana nan wani dan kakkaura”. Ummi ta ce, “To mu ji alkhairi tunda tsiwar taki ta iso kan malamai. Wani ya ce ki makaran?” Wannan ta wuce. Haulatu ta gayyace mu cin abincin dare a gidansu a washe gari ta taya Abdullahinta murnar kammala (Law-School) lafiya. Muka shirya tsaf muka cakare muka cancare cikin swiss lace ruwan kwaiduwar kwai (beig) da ratsin silver. Haulatu ta riga ta gaya mana za ta turo direban gidansu ne ya tafi damu, don ya Mufty ya je Giwa, matar gidan kuma tana fama da kanta ba ta (driving). Don haka da Abdoul ya shigo ya ce, “Wai wadanda Haulatu ta turo a dauka su fito”. Sai na zuba mishi rankwashi aka, muka zari mayafi muka yiwa Aunty Rabi sallama muka fita. Ni dai na ga mota ‘Vauxhall’ (one door) ba Honda din gidan su Haulatu ba. Kofar direba a bude ya zuro kafafunshi waje, sautin Abdurrahaman Sudaith na tashi a hankali a motar, ya sanya (ear piece) yana bi idanunshi a rufe ya jingina bayansa da kujerar kamar mai barci. Kamshin turaren ‘oud’ na mota na tashi kadan-kadan. Ganin bai da niyyar bude idon, bai kuma san da tsayuwar mu a wurin ba sai na yi masa sallama a hankali. Tare da cewa, “Mun fito”. Duk idanun ya bude wal! A kanmu. Hasken lantarkin farin bulb din da ya haskake harabar gidan ya haska mishi fuskokinmu. A sannu a hankali ya dauke ido a kanmu ya yi dan murmushi yana yiwa motar key yana fadin “Bismillah ku shiga muje, kamar ma na taba ganin daya daga cikinku”. Tuni zuciya da ruhi suka shiga aikin da suka saba a duk lokacin da suka yi arba da wannan bawan Allah. Lecturer dinmu ne (Mr. No name), don ban san sunan shi ba, mai kora ta a bainar jama’a in na yi latti. Meye hadin sa da Khaulatu? Ganin na tsaya na kasa shiga motar saboda mamaki sai ya dago ya dube ni muka hada ido na yi hanzarin russunar da nawa domin sun zama masu rauni kwarai a cikin nasa. Ya ce, “Ki shigo mu tafi, tana jiranku, o.k?’ Na bude bayan mota na zube. Ummi ta shiga gaba. Ya rufo kofar side dinsa cikin taushin murya ya ce, “FA’IZAH NAKE SO TA DAWO GABA BA UMMIN AUNTY RABI BA!” Wani sauti kululuuuu! Da cikina ya bayar kenan na mamaki, tsoro da tu’ajjabi. Ummi na dariya ta bude kofar gaba ta fito ta dawo baya ta zauna tana min alamar in fita ina girgiza mata kai alamar a’a. Ya ce, “Bana sayar da kai Fa’izah, ni aminin Barister Abdullahi Turaki ne. Shi ya turoni in taho daku an aiki Malam Saleh, ina fatan Fa’izah ta gamsu?” Ni da Ummi duka sai da muka murmusa. Na bude mota na fito na koma gaban. Ya ja motar a hankali muka bar harabar gidan, ya hau titi dodar. Daga ni har Ummi mun yi tsit kamar a ce kyat! Mu bude murfin mota mu arce. Sunayenmu da ya ambata wai har ma da Aunty Rabi. Na yi murmushi kadan daga aikin ( talkative ) Haulatu. Mun yi nisa da Gadon Kaya mun hau titin Audu Bako, jefi-jefi yana karkata mudubin shi don hango motocin dake bayan shi. Da danja ta tsai damu sai ya juyo sosai ya dube ni ,”Are you o.k?” Daga mishi kai na yi. Har muka zo ‘Yankaba bai kara magana ba, sai ni da Ummi kan yi magana na abin da ya shafe mu. Haulatu da Abdullahi ke zaune a harabar gidan bisa fararen kujerun roba suna hirar su hakora na shining (dariya). Kai da ganin wadannan ma’aurata ka ga masoyan da ke ji da juna. Har dai-dai inda suke ya yi parking, ya yin da duk suka mike suka nufo motar suna dariya. Ya zagaya ya budewa abokinsa, Haulatu ta bude mana ni da Ummi. “Mr. and Mrs”. In ji lecturer. “Na cika uzurinku, kyawun alkawari cika shi”. Abdullahi ya ce, “Wannan lazim ne Sadiqy (aboki)”. Haulatu ta ce, “Ni dai ba ruwana, kada ku shafa min kashin kaji, daman ta ce Dan iska ne”. Na dafe kirji da hannuwa biyu na ce, “Ke Haulatu!” Yadda na yi din da irin fiddo idon da na yi cikin razana ta gaske ya sa gaba daya har Ummi suka tuntsire da dariya. Abdullahi ya ce, “Kada ki jawo mata ‘carry over’ Sweetie”. Ya ce, “Ko spill over’ ba ta karasa a gidan mijinta”. Da wadannan hirarrakin muka rankaya dakin saukar bakin su Haulatu. “It’s a get together dinner of five....” Haulatu ta fada tana wara yatsunta biyar tare da janyo warmers guda biyar Arabian cuisines, kabsa, kebabs, manakees cikin biredin (pita), sai mankees, shawarmah da burger. Ta bubbude kowanne tana serving a plate, cewa take “I did it to you with my naked hands my dear Abdullahi! Congratulation on becoming a Lawyer”. Gaba dayanmu bamu san sanda muka zuba tafi ba, ni Ummi, da Mr. Lecturer. Shi kuwa Abdullahi murmushi yake bakin kamar ya tsage. Na kasa sakin jiki ko kadan abubuwan duk sun daure min kai. Sanda Mr. Lecturer ya bude wata foil paper ya turo gabana saura kadan in saki fitsari don mamaki. Gasasshen naman saniya ne mai romo da ya ji tumatir da albasa, har da cabeji sai turiri yake. Ya kuma dakatar da Haulatu daga serving dina shi ya yi serving dina da kansa, wannan gasasshen naman da ‘kebabs’ (tsire) plate dina wato har appetite dina ya sani, wa ya gaya masa ina son gasasshen nama? A yadda ya saki jiki a gidan na fahimci ba bakon zuwansa bane. Har wajen su Hajiyar Haulatu tare da shi muka je muka gaishe su muka dawo falon. Ya dauki tambulan ya cika da lemun matsattsun kayan itatuwa (tropical juice) ya miko min cikin lumshe ido da bude shi duka a lokaci guda. Ban iya na yi musu ba na karba, amma kurba daya na kasa saukewa saboda gardin lemon, ko ko in ce gardin hannun da ya fito daga gare shi. Cikin duka (Arabian Dishes) din nan gasasshen naman da ‘kebabs’ kawai na iya ci saboda na zama bakuwar zuciyata. This is the exact stranger I’m dreaming of. Sannan actions and emotions dinsa sun nuna abin da ke karkashin zuciyarsa, tun kafin ya furta, he care too much, sai shisshigi yake yi mun. Shishshigin da ba zan iya tankwabewa ba. Zuciya da gangar jiki duka sunyi amanna, sun karbi shisshigin sun dora a kan kujera mai matsayin da baya kwatantuwa. Watakila da zai iya lashe ni zai yi saboda kulawa. Hakan yasa duk na bi na takura na kasa sakin jikina daga sanya baki cikin hirar shi da Ummi, wanda duka tambayoyi ne a kan abin da ya kawo mu Kano. Haulatu ta ce, “Fa’izah fa ta bi ta takurawa kanta saboda malaminta”. Gaba daya suka maido hankalinsu gareni suna murmushi. Ta ce, “Dama kin saki ranki, kin saki jikinki wannan malamin....” Ya yi hanzarin cewa, “Abdullahi killace bakin matarka kafin in bubbuge shi”. Abdullahi ya miko hannu ya rungumo kwibin matar shi yana fadin “Kada ki kara magana Honey. A yiwa Yaya Malam biyayya don tare zan tafi in barku. Sai dai ban goyi da bayan a buge min bakin amarya ba tun ban biya farashinsa ba (siyen baki)”. Ban san sanda na yi dariya ba, ni dai haka nan soyayyar Haulatu da Abdullahi ta ke burge ni. A gaban kowa basa iya boye su masu begen junansu ne, sai dai in ba za ka iya gani ba ka kau da kanka. Haka yake yi in ya je wajenta a makaranta ya yi ta bamu kunya, wani zubin su bamu sha’awa, wani zubin su bamu dariya. Tattalin Haulatu yake kamar kwan da aka nasa yanzu-yanzu. Haka ita ma. Ganin dariyata sai Abdullahi ya ce, “Ko ke fa? In ya sake ce miki ‘get out’ ki zo nan ki gaya mun ni dashi ne kin ji Fa’izarmu”. Cikin dariya na ce, “Ai ban ga laifin shi ba Yaya Abdullahi. Ni ya dace in nemi afuwar shi a bisa lattin da nake mishi, wallahi ba halina bane yin latti akasi da uzuri aka samu. I’m sorry Malam”. Wani irin lumshe ido ya yi bai ce komai ba. Ya kara kwanciya a cikin kujerarsa. Wannan karon wayar hannunshi yake latsawa kamar bai san bikin da muke yi ba. Haulatu ta cika baki da shawarma cikin tsokana, “Wallahi Ummi wulakancin dan iskan malamin nan fa ya soma isata? Ko kin san asarar lecture biyu ya yi min? Oho! Ina na san shi? Yana nan wani baki dan kakkaura mai in-ina”. Na kai tafukana da suka sha adon jan lalle na rufe fuskata suna ta dariya. Shi kuwa murmushi kawai ya yi. Ya ce, “Haulatu ba a sirri dake?” Na ce, “Daman kin san shi ai kika rufemu a bai-bai?” Ta ce, “Ah toh! Ba ga shi yanzu na baku mamaki ba”. Abdullahi ya ce, “Lallai dan iska, yau kuma ‘yan iskan idanun bisa aminiyata suka fada?” Ya dago kai daga kan wayarshi ya ce, “Ya ishe ka haka nan Abdullahi! Kai ka tashi ma ka tafi lokacin tafiyar ya yi ko a nan za ka kwana yau?” Ya ce, “In na kwana na yi laifi ne?” Bai kula shi ba, suka ci gaba da kwasar girkin Haulatu sai da kowa ya yi kat. Shi da kansa ya yi serving dina. A yadda yake sarrafa hannayensa wajen serving din za ka fahimci lallai namiji ne wanda zai tattala matarshi matuka, wanda zai lallaba matarshi fiye da Abdullahin Haulatu. Abdullahi ya mike yana fadin “Haulatu zan wuce, zo ki ji mana”. Ummi ma ta mike ta ce, “Ni toilet za ki nuna mani a cikin gida”. Gaba daya suka fice. Daga ni sai malamina Mr. no name. A sannan ne na fahimci sun fita ne duka don su barmu mu biyu. Ya dan motsa a cikin kujerarshi sannan ya ce, “Fa’izah!” Wannan kira ya dade yana amsa kuwwa a sassan jikina. Ban iya na amsa ba sai kara dukar da kai ina murza zoben hannuna. “Har yanzu ban yi abin da zai sa a sake dani ba? Ko sai na kai ga durkuso bisa gwiwoyi na? Domin wannan afuwar Fa’izah?” Na dan fiddo ido, “Ta ya ya malami zai durkusawa dalibinsa?’ “Ta dalilin yana SON dalibar soyayya mai yawa.....” Ya fadi cikin kwaikwayar muryata. Da a ce ban ga yadda yake ciccijewa yana cin magani a aji ba, sai na rantse cewa ba shi bane. Lallai so ba dama ne. Jin na yi shiru ina tauna maganarsa sai ya katseni da cewa, “Shin Fa’izah ta tsai da gwani ne tsakanin Giwa, Zaria, ko Kaduna?” Sai na yi dariya cikin jin kunya, “Don me ka yi tunanin wannan? Mu ‘yan Giwa bama hada taura biyu a baka”. Murmushi ya yi tare da girgiza kai, “Mu ‘yan Kano muna hadawa, kenan rabon kanawa ne ya hana?” Murmushi na yi cikin jin shauki. “Fa’izah I’m serious. I’ve interest on you. Shin za ki iya auren malamin makaranta?” Dagowa na yi na dube shi da dukkan idanu, “Babana ma malamin makaranta ne”. “But you are born with a silver spoon in your mouth (kin fito daga gidan masu hannu da shuni), kaman hakan zai zama takura”. Ya fadi cikin murmushi. “A’a, ban fito daga (silver spoon) ba, na fito daga BABBAN GIDA (point of correction) mai babban suna”. Tafi ya yi min sau uku, “Mene ne bambancin guda biyun?” “Akwai bambanci da yawa. Babban gida kudi bai yi yawa ba, amma babu yunwa babu rashin suttura a cikinsa. Sannan masu shi dattijan kwarai ne masu magana daya. Idan kuma ka ce tajirin gida kana nufin gidan hutu”. Wannan karon dariya yake yi sosai wadda ta sanya ni shagaltuwa a kallon sa, kyawunsa na kara kayatar da zuciyata. “Na yarda dake Fa’izah, to amma fa sai kin ki ji kin ki gani a tafiyarmu. Abin da na gani ina so da zuciya guda ba zan iya munafuntar shi ba, ina da tabo Fa’izah, wanda na san as soon as an fara ganinmu tare za a kawo sukar sa. Duk da an ce waka a bakin mai ita ta fi daxi, ina jin kunyar kaifin idanunki....” Ya yi dan murmushi.... “Ina son mata Fa’izah, ina son su da yawa..... na yi amanna da cewa har gida za a biyo ki a gaya miki wannan, sai in ba a ganmu tare ba. Amma na yi miki alkawari Fa’izah tsakanina da mahaliccina from you it will cease to exist (son matan) na yi miki alkawarin bari har abada in har kin amince ki zamo uwar iyalina. Daga ganina dake na farko zuciyata ta gaya min ke ce (life-companion) dina mafi cancanta. Kaunarki ta fara ne daga ganina dake na farko (love at first sight) na rasa nutsuwar zuciyata a tsayin wunin ranar da daren baki daya. Da nake kwatantawa Haulatu kamanninki da level din karatunki take ce min ke best friend dinta ce tun a secondary, da take yawan bani labari. Shine ta hada mana wannan dabarar ta dinner (to dine here together) ta kuma turani in dauko ku. Gaba daya tarihinki na jishi wurin Haulatu, na kuma kara tabbatarwa kaina INA SON FA’IZAH! Shin Am I accepted Fa’izah?” Kaina na sunkuyar ina murmushi. Abin nan da masu iya magana ke cewa, labarin zuciya a tambayi fuska, don zuciyata ta yi na’am tun ma kafin ya furta. Har nake jin cewa, ba son mata ba ko mata dari gare shi zan iya zama ta casa’in da tara in har nice uwar ‘ya’yanshi. Domin yanada duk abubuwan da za a so shin a kansu. Ga dai ilimi, ga kuruciya, ga kyau na a manna a jarida, ban ga makusarsa ba. “Ko da ban furta ba, kallo daya za a yi min a tabbatar da na fada a matsananciyar kaunar ka. Daga lokacin da idanuwana suka fada a kanka Malam”. Magana nake a zuci, ban san cewa a fili nake yi ba. Ganin ya lumshe idonsa ya bude ya ce, “Na gode”. Ya tabbatar min ya ji abin da na ce. Wannan sai ya tuna min da lokacin da na karbi tayin soyayyar Yaya Aliyu a Zaria, ga shi ban ci ribar waccan ba, na amsa ta biyu, kada Allah ya kara dandana min dacin ta. Cikin dan lokacin nan mun tattauna abubuwa da dama mun kara fahimtar juna. Har zuwa lokacin na kasa tambayar shi sunan shi. Sai wurin karfe goma Haulatu ta fargar damu, da kyar muka katse hirar muka fito zuwa mota. Ina ganin Ummi da Haulatu na gulma suna rada da dariyar shegantaka ko kula su ban yi ba. Don na san da ni suke. A kan hanya ma hirar muke yi. Ya gaya min ya yi dukkan karatunshi ne a Taiwan inda ya karanta harshen Larabci ziryan. Shi da Abdullahi ‘ya’yan family friends ne, haifaffun garin Dambatta. Da kyar muka iya yin sallama don sai da Ummi ta shige ta barmu. Sai shigowar hancin motar Yaya Mufty ne yasa muka yi sallama ya jira fitowar shi da yin parking din shi suka yi hannu, sannan ya shiga motarsa ya tafi. Har zai fita get ya dawo ya yi min horn na juyo “Phone no na manta Fa’izah”. “Ni da Ummi bamu da waya”. “Saboda me?” “An hana mu rikewa ne”. Hannu yasa ya dauko tashi a gefe, “Ki rike wannan saboda ni Fa’izah. Na yi alkawari ba zan zamo mai hana ki karatu ba!” Ya cire layin ya miko min (Sony experia) sabuwa dal. Na rasa abin da ya hanani kin karba, na kuma rasa wanda ya sani yin godiya. Wala’alla soyayyar kenan? **** Fada na duniya babu irin wanda Aunty Rabi ba ta yi min ba a wannan daren. Ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, har sai da na saka kuka. Na farko daren da muka yi, na biyu tsayawa a waje da namiji tsayin karfe sha dayan dare. Na uku wayar da ta ganni da ita, da izinin wa na karbo ta? Don bakwa gaban iyayenmu ba zan ci amanarsu ba. Abin da ya zaunar daku gidana shine karatu ba (flirting) ba. Wannan wayar dole ki mai da masa abarsa gobe. Gaskiya ba dani ba, ba a gidana za a karya dokar A.B House ba, gara ma ku sake tsari. Gobe abu na farko da za ki fara da zarar kun shiga makaranta shine mayar da wannan wayar. Yaya Muftahu bai ce komai ba. Haka na kwanta zuciyata ba dadi da haushin Aunty Rabi. Duk kula mazan da Ummi ke yi ba ta taba yi mata fada ba sai ni da na yi sau daya, ni da nake da niyyar aure ma ba flirt irin na Ummi ba. Da zuciyata daya nake son malamina, da gaske auren shi zan yi in Allah ya yarda. I love you. If you hate it, kill with an arrow. But please not in the heart because that’s where you are. Gud night. Sakon da ya fara shigowa cikin wayar kenan da na saka layin da ya bani cikin kwalinsa. “Why will I hate it?” Na tambayi kaina cikin murmushi. “I do love it too!” Na baiwa kaina amsa. Don haka na baiwa Malami na amsa. “You inspire in me a love so deep and powerful that cannot be destroyed by any arrow! How I wish there is a way you could see into my soul. My love on you is far to strong Mallam!” Daga wannan na kashe wayar gaba daya. **** Washe gari tun asuba nice farkon yin wanka a gidan. Ban jira Ummi ba balle Yaya Muftahun dake sauke mu ya wuce office, na yi tafiya ta ni kadai saboda fushin da nake yi da Aunty Rabi, ban yi ko tunanin wani abu wai shi kalaci ba. Babban burina in dora idona a kan lecturer. Kusan nice farkon shiga laccarsa ta karfe goma ta safe. Kai! Ni Fa’izah na shiga uku!!! Don I become infatuated to him fiye da kima. Akwai wani sirri dake cikin kwayar idanunsa da ba duk maza Allah ya mallakawa ba. Sai dai kuma cikin rashin sa’a bayan ajin ya cika (class-representer) din ya ce ya mai da ita (fixed) karfe biyu na rana. Kamar na fashe da kuka dai-dai lokacin da wayar da na jefa a jaka ta kama tsuwwa. Cikin rashin kuzari na amsa da tunanin yadda zan yi in mayar da ita din kamar yadda Aunty Rabi ta yi umarni. Muryar mace ke tambaya, “Dacta ne?” “A’a, ba shi bane, wace ce?” “Ke me maganar wace ce?” “Matarshi ce!” Sai ta kyalkyale da dariya ta ce, “Ki ce Haulatu Sani Galadanci na gaishe shi, kuma inda hali yana jiranki a office dinsa. Saboda ke ya dage laccar ku zuwa anjima. He can’t wait to see you.... cross sword....!” Kunyar Haulatu ta kama ni ainun yadda ta yi ta canza murya ta shammace ni na yi tabargaza, na yi shuka a idon makwarwa. Jiki babu nauyi na nufi inda Haulatu ta kwatanta min cewa nan ne ofishin nasa. A ofishin akwai hoton gwamna mai ci a lokacin da na shugaban kasa, sai na Alh. Dr. Ado Bayero. Sanda na yi sallama rubutu yake yi amma bai kasa amsa min ba. Na samu kujera na zauna har ya kare, sai ya turo min folder din da yake rubutun nasa hannu biyu na amsa. Ko da na duba (note) dinsa ne da na yi missing har guda biyu cikin hand-writing dinsa mai kayatarwa da ban sha’awa. Idona ya kai ga dan karfen dake like saman kofar shigowa ofishin da ban rufe ba. Sunansa ne radau DR. NAZIRU SANI GALADANCI. Wato Dr. Yayan Haulatu ne uwa daya uba daya ta yi min irin wannan ninkewar? Kai abin da mamaki. Har mun yi sallama na kai bakin kofa sai na juyo na ce, “Na yi mantuwa ne”. “Ta me Fa’izah?” Na dawo a nutse na ciro wayarsa daga jakata na mika masa, yasa hannu ya karba yana fadin “Ya kika dawo min da ita?” “Aunty Rabi tana ta fada ne, ita ce ta ce na dawo maka da ita, ba za a barni na rike waya ba sai na yi aure”. Ya yi kasake cikin kallona da murmushi, “Sai na ji na kara son ki, na kuma kara yarda da cewa da ki kai ke din ‘yar babban gida ce. Abin da ban taba ji ba a wannan zamanin ‘yammata kamar ku a jami’a iyayenku sun hanaku rike waya, kuma kun bi, anyway. Ki ce ma Aunty Rabi ta yi hakuri, ba za ki sake rike waya ba sai kin zama matar Dr. Nazir insha Allahu” [13/02 6:26 PM] Sumayya Takori: Da sassarfa na karasa ficewa daga ofishin ina murmushi. Yinin ranar zungur na kare shi ne cikin tunanin Dr. Nazir da maimaita ambaton sunansa cikin zuciyata sakan bayan sakan, minti bayan minti, awa bayan awa son Dr. Nazir karuwa yake yi a raina. Yana kara habaka a birnin zuciyata. **** Soyayyarmu da Dr. Nazir ta yi nisa da karfin da ta zama sananniya a tsangayarmu. Tsegumi kam iri-iri an kawo min a kan yawan ‘yammatan da Nazir ke dasu cikin makarantar. Na kan toshe kunnuwana ne kamar yadda ya ce, ko in yi hannun riga da duk wanda ya kawo min tsegumin. Dr. Nazir ya ware muhimmin lokacinsa wurin yi min (extra class) bayan kowacce laccarsa. Nazir ya iya koyarwa. A dalilin koyarwar da yake yi min ‘points’ dina a jarrabawa ya kara karfi fiye da na baya. Nazir ba shi da karfin idanu (short sight), a dalilin hakan yake amfani da farin gilashi mai kara karfin gani (lenses) ya yin rubutu ko karatu, ko ba da lacca. Amma in ba fadi aka yi ba za ka yi zaton na kwalisa ne. Don yana mai kyau sosai. Nazir mutum ne da ya iya tsara magana da hafizin harshen da Ubangiji ya hore masa. Iya maganarsa da kirkinsa ya taka rawa mai yawa wajen sanya zuciyata ta zamo kangararra, bana ji bana gani. Da kaina in ban ganshi ba sai na bishi office, har sayayya mu kan fita wasu lokutan. Tun Ummi na hana ni har ta gaji ta rabu dani. Wai ni Fa’izah tsatso daga A.B House nice mai bin saurayi har office, nice mai fita da saurayi. Wannan ba karamin kona ran Ummi yake ba. Har ta gaji ta tseguntawa Aunty Rabi. Aunty Rabi ta samu Yaya Mufty take sanar da shi, inda ya ce, “A kawo mishi sunan Nazir cikakke zai yi bincike a kansa. In mutumin kirki ne a kyale ni, kwana nawa ne zamu gama karatun mu koma gaban iyayenmu? Domin Hajjah ta soma fadan mu dawo gida haka karatun ya ishe ta. Abu ya ki ci ya ki cinyewa tamkar cin kwan makauniya”. Aunty Rabi ta ce, “In kuma ba mutumin kirkin bane ba fa Mufty?” Ya ce, “Zan san abin yi a kai”. Ni kam duk surutunsu da harare hararen su basa damuna, na yi nisa a son Naziru. Wani irin so nake dandana mai wuyar fassarawa, wanda ya zarta na Yaya Aliyu fintinkau! Idona ya rufe a son Naziru, lokutana baki daya na Dr. Nazir ne. Tambayar da jama’ar dake tare damu ke wa Ummi shin Fa’izah ta san Dr. Naziru (use and dump) ne? Ta ya ya yarinyar ‘yar gidan mutumci wadda ta san ciwon kanta irin Fa’izah ta yarda cewa Dr. Nazir auren ta zai yi? Shin Fa’izah ta san yawan ‘yammatan da Dr. Nazir ya yaudara ya watsar a Kano? Shi fa dama duk inda kyakkyawar mace take nan idonsa yake, zai nuna mata so ya yi ta yi mata facaka, amma da an ce ya fito ayi aure ba kya kara ganin keyarsa”. Ummi ta kan girgiza kai, don bakin ciki ta rasa me za ta ce, sai dai ta ce, “Fa’izah kam ta yi nisa ba za ta ji kiran ba”. A yammacin wata talata mun dawo daga Ado Bayero Mall (Shoprite) ni da Nazir ya sauke ni dai-dai inda ya ga su Ummi a zaune a (seaters) na dalibai karkashin wata bishiyar dalbejiya mai inuwa, bai ko tsaya sun gaisa da su Ummi ba don ya san Ummi ba ta goyon bayan tarayyarmu daga ita har shakikiyarshi Haulatu, ita ma ta bi sahu don tsoronta na kar mutuncinta ya zube idon su Aunty Rabi dake matukar ganin mutuncinta, ranar da Nazir ya yi (dumping) dina. Ko ba don wannan ba Nazir baya sakar ma dalibanshi fuskar da raini zai shiga tsakani. Ko mata da yake nema tamkar bunsuru ba dai cikin tsangayarmu ba can a wasu tsangayoyin ko waje yake neman abinshi. Na yi musu sallama duka suka amsa min a sanyaye, na aje ledar hannuna gefen Haulatu ina fadin “Wash Allah! Na gaji da yawa. Dr. N (sunan da nake kiransa) ba dai yawo ba, shi dai a je shopping burinsa kenan”. Suka dubi juna suka kau da kai. Cikin nutsuwar da ban san tana da ita ba Ummi ta ce, “Fa’izah rayuwar da kika zabawa kanki kenan? Tarayya da maza irin su Dr. Naziru? Yau da Hajjah za ta ji wannan mummunan labari ina kike tunanin za ta tsoma ranta? Da kin sa zuciyarta ta yi bugawar farat daya. Wallahi-wallahi tun wuri ki sake hanya tun dare bai yi miki ba. Nazir ba dai-dai yake da tsarin rayuwarki ba, kuma aurenku ba zai taba yiwuwa ba. In kin manta kin fito daga zuri’ar A.B ne nake tuna miki”. Haulatu ta cafke “Ina mai matukar jin kunyar ranar da Yaya Naziru zai yi dumping din ki, (as if you had never been in existance), shi yasa nake so ki kwaci kanki tun kafin zuwan wannan ranar, domin mai hali baya fasa halinsa, kuma sannu ba ta hana zuwa sai dai a dade ba a je ba. Nazir dai dan uwana ne, karewa ma shi ya sha nono ya saki na kama, uwarmu daya ubanmu daya. Amma bana goyon bayan ki mallaka mishi soyayyarki. Abin dai da baki son a ta da to dole ne a fadi, ba auren ki zai yi ba”. Na yi murmushi na ce, “Kun gama? Shin ina kaunar da kuke ikirarin kuna yi min din Haulatu da har ba za ku so abin da nake so ba don cikar farin cikina? Kuna kina da Dr. N ne don tsoron kada ya yi min yadda yake yiwa sauran ‘yammatan da ya nema a baya, shin ku Allahn musuru ne? Kun san gaibu? Kuma shin shi halin dan Adam baya canzawa ne? Dr. N ba munafuki bane irin yadda kuke zato, tun ranar da muka hadu ya gaya min abin da kuke gudu din, ya kuma tabbatar min daga kaina ya daina, ina rokon Allah ya taimake shi ya dainan. Manzo mai tsira da aminci ya ce, ‘ku kyautatawa mutum zato domin zato zunubi ne ko da ya kasance gaskiya’. Kuma duk iskancin da kuke tsammana mishi wallahi bai taba kai hannunshi jikina ba ko bisa kuskure. Bai taba ba. Wannan ya nuna Dr. N son Allah da Annabinsa yake yi mun, ba kuma zai gwada iskancin nasa a kaina ba saboda ba yaudarata yake da niyyar yi ba. Zancen mutuncina da kuke, kada Allah yasa a ga mutuncin nawa in har sai na bar Dr. N. Ke kuma Haulatu yadda kike aibata dan uwanki don tsira da naki mutuncin wallahi kin bani mamaki, in kin yi ne don ki burge wallahi baki burge ni ba. Ai naka-naka ne komin lalacewar shi, hannunka baya taba ribewa ka yanke ka yar. Ku zuba ido tunda duk kun zama ‘yan adawa da yardar Allah kunya za ku sha”. Na suri ledar shopping dina na bar musu wurin, na barsu suna kallon-kallo a junansu an rasa mai karfin halin musawa ko maida martani. **** Abdullahi ya ce, “Ka rufa min asiri Naziru, Haulat ta zo min tana kuka in rokeka ka rabu da kawarta in ba auren ta za ka yi ba. Naziru ka yiwa Allah ka rabu da yarinyar nan ko don zumunci da sanayyar dake tsakani”. Dr. Nazir Sani Galadanci sai ya yi murmushi yana harhada takardun daliban dake bisa tebirinsa. “Wata fuskar..... ta fi gaban mari. Za ka sha mamaki na Abdullahi”. **** Ranar da muka kare zana jarrabawar zangon karshe na aji uku (300 level), ranar muka yi shirin tafiya Giwa, a dalilin dan uban aiken da Hajja da Baban ABU suka ishemu da shi lallai mu zo gida ana neman mu. Mun yi sallama da Aunty Rabi da alkawarin ita da kanta za ta rako iyayen Nazir Giwa a duk lokacin da suka bukaci hakan, domin Aunty Rabi ta tsinke da irin kaunar dake tsakanina da Dr. N, duk da binciken da Yaya Mufty ya yi ya nuna cewa Dr. Naziru Sani Galadanci yana layin samarin da iyaye ke tsoron ya dora mayaudaran idanunshi bisa ‘ya’yansu a fadin garin Kano da jami’ar Bayero. To an ce fadan da ya fi karfinka sai ka mai da shi wasa. Don haka dukkaninsu suka koma lallabani da bina da siyasa. Ashe abin da ban sani ba a nufin Hajjah karatun daga iya nan an barshi kenan mu da Kano sai zuwa da yawo babu wanda ya gaya mini. Na ga dai Ummi cikin damuwa, da zamu tafi kuwa sanda Yaya Mufty ya kunna mota kuka take yi wiwi har da sharbe, ni kuwa sai na ji gabana ya yi wani irin mummunan faduwa a sa’ilin da Yaya Mufty ya hau kan titi. Kaduna muka fara isa. A sa’ilin da Yaya Mufty ya sanya hancin motar cikin gate din gidan Baban Kaduna, a sa’ilin ne na ji wani irin faduwar gaba da ban taba ji ba a rayuwata. Muka yi sallama a babban falo, duka ‘ya’yan Hajjah in ka dauke Rabi auta dake Kano babu wanda babu a falon. Suna zaune duk sunyi jigum-jigum. Da na juya ido zuwa mahaifina Ahmadu A.B sai na ganshi cikin jan ido kamar gauta. Babu abin da ya zo raina face mutuwa ga tsohuwa Hajjah. Idanuna suka yi kwalkwal na dubi Maman Kaduna cikin hawaye. “Hajjah ta mutu ko Mama?” Na rushe da kuka bana ji bana gani, kuka mai tsananin gigitar da zuciya ma’abociyar imani. Wata irin tsawa Baban ABU ya daka mini, “Ke bama son sakarcin banza. In mutuwar ta yi abin da za ki yi mata kenan? Sakayyar da za ki yi mata kenan zubar hawaye?” Baba Barau ya ce, “Ita Hajjah din za ta so ta mutu Fa’izah ba ta rungume ‘ya’yanku ke da Ummi ba tunda ta rungume na Zanirah?” Sai ga mai kuka na dariya bayan ga hawaye shabe-shabe a fuskar “Zanirah ta haihu Mama?” Gaba daya na basu dariya ban da Baban ABU. Na ce, “Amma Mama shine baku gayawa Aunty Rabi ba mun zo mun ga danmu?” Mama ta ce, “Mace ce, ai abin bana yau bane. Ita Rabi ta sani lokacin kuna jarrabawa shi yasa ta ce ba za ta gaya muku ba murna da doki za su hanaku karatu in kun zo kwa gani, to kin ji. Yau shekarar (FA’IZA) daya tana gudunta ko ina”. Na yi shiru cikin tunani, wato sunana Yaya Aliyu ya sanyawa diyarsa da Zanirah. Na ce cikin murmushi, “Allah ya raya takwara, zuwa Lagos ya kama mu kenan”. Ni sai a lokacin idona ya kai ga huhunan goro da alawa dake jingine gefe guda wani a kan wani. Na ce, “A’a, wannan kuma fa? Auren Maryam za ayi ko Hanifa?” Baban Kaduna da Baban ABU suka kau da kai kamar basu ji ni ba. Baba Ibrahim ne ya ce, “Auren Ummi ne ya tashi gobe insha Allahu, don haka makaranta ta kare babu sauran komawa Kano”. Ummi ta zare ido cikin firgici da kaduwa. Ni kuwa sai na rungumeta ina murna ina fadin “Don Allah Mama waye angon?” Mama ta ce, “Da masoyinta mana mai sonta tun tana karama”. Babu wanda zuciyata ta kawo min sai FA’EEZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA!” Ban san sanda na ce, “Amma a rasa wanda za a bawa Ummi sai Fa’iz?” Sai bayan na fada ne na tuna cewa, UWA da UBAN da suka tsugunna suka haifi Fa’iz ne a gabana. Suna zaune ne idanuwansu cike da kauna, kuma suna son dansu kwatankwacin yadda kowanne iyaye ke son dan da suka haifa duk munin shi ko munin halinshi. Ya yin da ni nake kokarin aibata musu shi a gabansu. A sanyaye na ce, “Allah ya sanya alkhairi”. Cikin sanyin jiki na wuce daki zuciyata cike da sake-sake. Wani bangaren tausayin Ummi nake ji. A ganina sun cuce ta sun aura mata mutumin da bai cancanci a hada auren shi alkhairi ba. Sai na tuna Ummi fa na son Fa’iz, kuma so hana ganin aibu. Yadda nake son Dr. N da tabban da yake da shi, haka Ummi ke son Fa’iz da kowanne tabo mai alaka da shi da halinsa. Iyayenmu suka bini da kallon nazari ganin yadda yanayi na ya sauya gaba daya a lokaci daya. Wajejen karfe hudu na yamma masu aikin gidan ke ta kaiwa da komowa sun kasa zaune sun kasa tsaye. Suna diban katon-katon na lemuka suna jerewa a firizan dake dakunan Baskwata (boys quaters) guda biyu dake like da juna. Na dan matsa na leka, ko falon dan ‘Prince Charles’ sai haka. Kwata-kwata falon bai yi kama da sauran falukan da na saba gani ba a wurare daban-daban. Komai na falon cream colour ne in ka dauke kayan kallo bakake samfurin SONY, hatta ‘curtains’ (labulaye) cream colour ne. Haka sauran kayan alatun dake falon. A.C har biyu, ta tsaye (standing A.C) da ta manne a bango (split), sai sassanyan kamshin (Bakhour) da Yahya ya sanya a dakin ke tashi. Kujerun (leather) ne suma cream colour masu laushi. Yadda wannan dakin yake, haka na kusa da shi yake komai da komai, sai bambancin kala. Na daya dakin ruwan makuba ne (grey). “Shin Yahya Baba amarya ya yi ne?” Sai ya kyalkyale da dariya, “Mama ce za ta bari Baba ya yi amarya?” “Yo ina na sani? Na san dai ba naku bane, duk da gasu a Baskwata”. Ya kara kyalkyala dariya, “Kin manta ne gobe su Yaya Bashir da Yaya Fa’eez za su dawo? Sai dai Bashir ya kammala, Fa’iz ma’aikaci ne ganin gida kawai zai zo”. Na ce, “Hummm! Lallai. Ni za ni in kwanta, anjima in su Baba za su koma Giwa kasa a tashe ni don Allah”. Ya ce, “Insha Allah”. Na juya zuwa cikin gida zuciyata cike da sake-sake. Da mamakin kaunar da Baban Kaduna yake yiwa ‘ya’yansa (beyond comment) sunan wani ganyen shayi. Abin haushin dukkansu babu na gari, don gara ma Bashir din shi shaye-shaye kawai yake. Shi dayan munin hali har ba a magana. Sai dai duk yadda na so in yi barcin Ummi ba ta barni ba. Hakika tana cikin farin ciki da ban taba ganinta cikin irin shi a duniya ba. Murnar auren ta da masoyinta Fa’iz Allah ya cika musu burinsu. Ta yi kukan dadi, ta yi na sosai. Duka dalilin daurin aurenta da Fa’iz gobe......” Na yi murmushi na ce, “Ki yiwa Allah ki barni in yi barci, ki bari ya dawo sai ku yi tare tunda karfe daya baya amo. Ki barni da abin da ya dame ni fargabar zuwan iyayen Dr. N, don ban san irin tarbar da Hajjah za ta yi musu ba”. Ta ce, “Matsalarki ce wannan”. Karfe bakwai na magariba muka bi Baban Giwa sai Giwa, Yaya Mufty ya wuce Kano. Tun daga gate din A.B Estate gaba daya komai ya canza, an sake fasalin ginin an mayar na zamani sosai, haka cikin gidan Hajjah an canza komai sabo dal kamar gidan amarya. An sake fenti gida kamar ba a cikin garin Giwa ba kamar a Lagos ko Abuja. Irin wannan sauyin na A.B Estate na faruwa ne a duk lokacin da A.B family za su yi wani gagarumin biki. Na ce, “Uhm! Ummi ana ji da aurenku tabbas”. Ta ce, “Fadi da babbar murya”. Abin da ya bani mamaki yadda su Inna Kubra, Indo da su Kaltume da sauran kannenmu na Giwa ke min oyoyo da (AMARYA).... Ka ga amaren sai kyallin goshi suke.... ni dai murmushi kurum nake ina cewa cikin raina “Auren Ummi guda ai dole a kiramu Amare, tunda mune Amara kirazan biki”. Idona bai hasko min kowa a falon ba sai Zanirah, rungume da buleliyar ‘yarta tana shayar da ita. Yaya Aliyu na gefenta yana waya. Habawa! Da Zanirah ta cizge ‘yar a nono ta dangware masa a cinya ta yi wani tsalle muka dire a tare muka makalkale juna bayan mun shararo a guje muka shiga juyi a tsakar falon Hajjah. Wai! TAKORI ta ce, TUNA BAYA SHINE RIKO! Yaya Aliyu ya mike rike da ‘yarsa ya hau Zanirah da fada..... “Wai ke baki da hankali ne? Kashe min ‘yar za ki yi? An girma ba a san an girma ba, kuna abu kamar kananan yara? Ko su Hanifa ba za suyi wannan shirmen da kuke yi ba....” Zanirah aka kwantar da kai aka shiga lallashin maigida... “Haba Baban Fa’izah! Shekaru uku currr! Ni, Fa’iza da Ummi???” Yaya Aliyu ya yi murmushi yana ci gaba da jijjiga Fa’izar don ta koma barcinta da hayagagar mu ya katse mata, don shi dama fadan shi baya nisa. Ya koma ya zauna ya ce, “Fa’izah ya karatu? Shi kenan an kare ko?” Muka dubi juna ni da Zanirah da Ummi duka muka yi murmushi. Na mika mishi hannu ya bani diyata kuma takwarata Fa’izah. Na dauke ta na sumbace ta na kura mata ido. Allah kareem dani yarinyar take kama sosai, ko da yake dukkanmu kamar tamu daya ce. Na ce, “Ya Allah ka raya mana little Fa’izah”. Kowa ya yi murmushi ya ce, “Ameen”. Yaya Aliyu kallona kawai yake, na san ba zai wuce mamakin kyakkyawan girman da na yi ba. Na samu Yaya Aliyu a kofar gida kan fararen kujerun roba yana yiwa ‘yar shi wasa, na labarta mishi zuwan dangin manemin aurena Dr. Nazir gobe. Yaya Aliyu ya yi shiru yana mai nazarin zancena. Akwai wani yanayi a tare da shi ya kada min ‘ya’yan hanji, wani yanayi da na kasa fassarawa. Yanayi ne mai nufin “BA ZAI TABA YIWUWA BA!” Na yi zugum! Ina dubansa hannuwa a kumatu zuciya cike da taraddadi. Ya yi ta maza in ji mata ya ce, “Fa’izah kin yi babban kuskure da kika saka soyayyar Dr. Nazir a ranki, alhalin kina sane da cewa babu auren (na gani ina so) cikin zuri’armu. Balle auren bare, wanda ba a taba ko da wasan kwatantawa ba. Tun bayan na mahaifiyarki wanda ko shi tunda ran A.B ne. Shin abin da ya faru a baya ni dake bai ishe ki ishara ba? Ki guji mu’amalar soyayya da kowa ki baiwa Allah zabi cikin al’amuran rayuwarki baki daya?” Idona ya cicciko da kwalla kadan ya rage su shimfido a kundukukina, na ce, “Yaya Aliyu ka taimake ni ina son Naziru, ina tsoron halin da zan shiga in na rasa shi. Fadar A.B ba fadar Allah ba! Bani da wanda zai taimaka min ya shige min gaba idan ba kai ba. I cannot afford losing him...” Yaya Aliyu ya zuba min ido na san mamakin halinmu na mata yake yi, a raina na ce, “Har an fika Aliyu Haydar?’ Ya saukar da kai bisa yatsun Fa’izah karama dake bisa cinyarsa, ya ce, “To ni dai Fa’izah babu abin da zan iya a kan wannan rigima da kika je kika jajibo. Zan yi dai iya kokarina in ga cewa ba a yiwa dangin Nazir wulakancin da za su tafi damu a baki ba idan sun zo. That is all. Ki jira hukuncin Hajjah a gobe”. Tun daga nan jikina ya kara yin la’asar. Na tashi na bar Yaya Aliyu don a ganina ba shi da abin da zai iya yi min din da gaske kamar yadda ya ce. Karfe tara na dare na kira Maman Kaduna nake sanar da ita zuwan dangin Nazir a gobe, don na manta ban sanar da ita a Kaduna ba. Na kare da cewa (cikin murya mai ban tausayi) “Mama na san ko da kowa bai goyi da bayan in auri Dr. Nazir ba, to ban da ke don ke uwa ce mai son duk abin da ‘ya’yanta ke so. A ganina lokaci ya yi da za a kawo CANJI a kan auren zumunci da ake tilasta mu yi, domin ZAMANI YA CANZA. A duk lokacin da zamani ya canza, dolen al’umma ne ta tafi tare da canjinsa in har tana so ta ci gaba. Auren zumunci ba laifi bane amma idan akwai son ran ma’auratan, in ko babu na daya daga cikinsu ya zama auren MUGUNTA, domin dole za a zalinci daya. Ke kadai kika rage min da zan kawowa kukana ki share min hawaye...... ki taimake ni Mama su amshi maganar Dr. Naziru da muhimmaci da karramawa. Wallahi ina sonshi Mama ba zan iya hakura haka in barshi ba a kan tsarin Hajjah... Ki taimake ni Mama don Allah, he’s the stranger that I’m always praying for!” Mama shiru ta yi na lokaci mai tsawo, kamin ta aje wani gwauron numfashi wanda ya kara samun suspence ya sagar da gwiwoyina. Domin numfashin da Mama ta sauke na nufin ba za ki taba cin nasara a soyayya ba Fa’izah. Ba za ki cimma ko daya cikin burarrakinki a rayuwa ba. A karshe ta yi tashin gwauron zabi ta murje jin nauyi da kawaici ta ce, “Fa’izah! Sai dai ki yi hakuri kam. Amma wannan yaron BA ZA KI AURE SHI BA! An riga an yi muku mazaje ba tun yau ba”. Da maganganun Mama na kwana zuciyata jagule ta kasa sukuni. Wadanne irin mazaje Mama ke ikirarin an mana? Mu bamu sansu ba? Mama na nufin ba zan auri Nazir ba? Mama na nufin ba zan taba cimma burirrikan rayuwata ba? Ya ALLAH ka sa kada shima in rasa shi kamar yadda na rasa Aliyu-Haydar. Ya Allah kada ka nuna min wannan ranar..... ranar da za a ce shima Dr. N na rasa shi. Ni sai yanzu ne ma na san ina son Dr. N, hankalina ya yi matukar tashi da al’amarin dake shirin faruwa dani. Ya ya zan yi iyayena su amshi Dr. N? Na yi tunani iyaka tunani bani da mai mara min baya cikin dangina kakaf, kowa tsoro yake kada in shafa mishi kashin kaji. Na yi kuka na yi kuka har na ji babu dadi, idanuwana suka shiga yin wani yaji-yaji saboda kuka. Tunanin halin da Dr. N zai kasance in ya tsinci labarin ba za a bashi ni ba, da wanda nima zan kasance da abin da iyayena ke nufina da shi, shine babbar damuwata. Shin me ya mantar dani matsalar gidanmu tunda fari? Na yi zurfi a son Naziru? Me ya mantar dani rigimar gyatumar mu mai ran karfe? Babu ko tantama SO ne, SON NAZIRU ne. Ya makantar dani ya kurmantar dani har bana iya tunanin me zai je ya zo, har bana tuna baya balle abin da gobe za ta haifar. A wannan rana na yi fatan a ce ina ma ban fito daga A.B family ba! Ina ma ban kasance cikin zuri’ar Abubakar Bamalli Giwa ba [14/02 3:41 PM] Sumayya Takori: **** Karfe goma na safe su Ummi suka yi shirin tafiya taren su Bashir a filin jirgi. Tun asuba da na yi sallah fuskata babu walwala, kallon kowa kawai nake zuciyata a cunkushe da bakin ciki da bacin rai maras dalili. Hajjah yau ko gaishe ta ban yi ba, babu wanda na yiwa magana. Na zubawa allon talabijin ido kuri kai ka ce program din nake saurara, amma ina! Zuciyata ba ta tare da gangar jikina, abubuwa masu ban al’ajabi da ban tsoro kawai take wassafa min masu shirin faruwa dani. Kafin karfe goma na safe gidanmu ya cika ya batse da dan Adam, sai busa algaita ake ‘yan daurin aure suka fara layin shigowa gai da Hajjah suna fita, ‘yan’uwa ne da abokan arziki. Kafin Babanninmu su shigo sun sha ankon farar shadda (getzner) sai sheki suke. Suka zube a falon Hajjah suka kwashi gaisuwa suka fita. Ina daga uwar daki ina hango ficewarsu ta taga daya bayan daya. Mintina talatin bayan fitarsu na ji gabana YA FADI! A dai-dai lokacin da dakikar agogo ya nuna karfe goma sha daya na rana, a lokacin ne aka daura aurarrakin masu ban mamaki, da suka ajiye kundin tarihi da wani aure bai aje ba cikin zuri’ar Abubakar Bamalli Giwa. Wani maroki mai zakin muryar tsiya yake fadi da murya mai karsashi da kwarzantawa cikin babatun magana “ALHAMDULILLAHI! ALHAMDULILLAHI!!” Sai da ya fada har sau uku. “An daura auren FA’IZAH AHMAD ABUBAKAR GIWA da FA’IZU MUKHTAR ABUBAKAR GIWA. HADIZA da MUHAMMADU BASHIR, a kan sadaki lakadan ba ajalan ba. Allah yasa anyi a sa’a, yasa anyi sai bakin rai, Allah ya sanya alkhairi ameen.....”da sauran babatu irin na maroka. Maimakon in kira yi sunan Allah sai na kwarara ihu da iyakacin muryata na zube a wajen a sume. Ban kara sanin me ke faruwa a duniyar ba. *** Jirgin Boeng 708 ya sauka a filin jirgin saman Mal. Aminu Kano da misalin karfe daya na ranar da ta kasance Asabar, wato awanni biyu da daura auren. Jirgi ne da ya taso daga Ukrain zuwa Nigeria bayan shafe awanni masu yawa yana keta hazo, kafin ya wulwulo kasa ya tsaya a cyprus ya sha mai sannan ya keto kasarmu mai dimbin albarka. Sai da passengers kaf suka gama fita kafin Pilots din su fito cikin fararen uniform dinsu. Shine na karshe a saukowa. Fari sol! Mai madaidaicin jiki, zai fi kyau ka ce ba shi da kauri sai fadin kirji wanda da ka kalla za ka san gym ya samar da shi. Ma’abocin wasu ilhamomi da nasibobi da dama da ba duk maza Allah ya mallakawa ba. Ya saya fararen idanunshi cikin gilashi mai duhu ainun samfurin ‘KAREN MILLEN. Sajen da ya zagaye gefe da gefen fuskarsa baki sidik kwantacce wanda a da baya da shi bai boye tsagin mallacinsa ba. Sai ya kara fiddo ilhama da cikar zatinsa ya fiddo cikakken Bamallen sa, kuma Bafillace. Dan kimanin shekaru talatin da hudu, wanda ya dama, ya kutsa cikin ilmummukan zamani daban-daban. Dogon hanci gare shi kamar ruler aka sa aka ja shi aka daidaita shi a tsakanin idanunsa. Idanunsa dara-dara wadanda suka dan shige loko kadan farare tar masu sheki da maiko (oily eyes) wadanda duk cikin zuri’arsu maza da mata shi kadai aka ya yiwa wannan ilhamar. Idan lissafin da yake yi dai-dai ne yau shekarunsa takwas da barin gida ba tare da ya sake ko da waiwayarta da sunan hutu ba. A zubin halitta da kirar jiki ya fi kama da Ahmadu A.B, a halayya kacokan Abubakar Giwa ya kwaso ba wani cikin zuriyarsa ba. Don haka, ka ce ga hakikanin halayyar FA’EEZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA, abu ne mai matukar wuya. Za ka san halinsa ne kadai idan ka zauna da shi, zaman ba na kwanaki ko watanni ba, sai dai shekaru. Shekarun ma sai idan kwana kake tare da shi daki daya ka kuma tashi tare da shi, halin da ake kira halin MAZAN JIYA ba na YAU ba, and difficult to be studied by sociologists and psychologists. Idan aka ce su karanci irin pilot Fa’iz za su yi placing dinsa ne kawai (upon hypothesis) but not a dependent variable. Daga fitowar shi daga jirgi har shigewar shi wani ofishi (pilots changing room) idanun Khadija-Ummi na kansa, tana mai yiwa Allah tasbihi da godiya mara iyaka da wannan miji da Allah ya ba ta wanda ke ninkaya cikin zuciya da mafarkinta, ba ta taba tsammanin akwai ranar zahirantar mafarkin nata ba. A hankali ta ji danshi a kan fuskarta, wanda ba ta ko tantama hawayen farin ciki ne. Har zuwa lokacin da ya gama shige da ficensa a (airport) din tare da abokan aikinsa, ya canza kaya zuwa kaftan na farar lallausar shadda (Hilton) da ruwan kasar hula a kansa, takalmin fata dake kafarshi shima ruwan kasar ne. Ya janyo trolley dinsa zuwa inda ya hango fuskokin masu kama da tasa fuskar, wanda komai daren dadewa suna gilmawa cikin idanunsa, wato fuskar zuri’ar Abubakar Bamalli, wanda ya fi so da gani shi ya fara ganin, wato Aliyu Na’ibi. Da sassarfa Aliyu ya karaso suka rungume juna shi da Fa’iz, rayuwarsu ta baya ta dinga dawo masa tar-tar kamar a majigi. Abubuwa da yawa ba zai manta dasu ba. Cikin taron nan kaf na mata da mazan Bamalli, manya da yara, wadanda ya sani da wadanda bai sani ba, musamman kananan yara, ya hanga ya duba bai ga Zahrar cikin taurarin ba. Ya ga Zanirah, ya ga Ummi, Mus’ab, Junior Yahya, Shu’aib, Walida, Abdallah da wata karamar yarinya mai tsananin kama da Fa’izah (Khausar), da sauran kannensa ‘ya’yan Baba Barau, Sadi, Salisu, Sani da Na’ibi. Mutum daya ce kawai babu, wato KANWAR kuma abokiyar fadan da a yau ta juye ta rikide zuwa matarsa ta sunnah. Ko da wacce irin fuska za ta karbi al’amarin? Ko da wace irin fassara za ta fassara shi? Ko da wanne irin hannu za ta karbe shi? Abin da ya sani ya kuma kwana da da sani ne cewa, Fa’izah! Ba ta da makiyi a duniya irin sa!!! To amma ai shi sonta yake yi tun can din ma. Har kuma gobe son ninkuwa yake yi irin kaunar da bai taba yiwa kowa a duniya ba, in ka dauke Mama da Baban Kaduna wato iyayensa. This is his own style of love! To amma da wane language (yaren) zai yiwa Fa’izah bayanin hakan har ta yarda ta fahimce shi, ta karbe shi a matsayin miji a gareta? Ya kuma wanke wancan dattin da ya dade yana yabawa kansa a idanunta? Don haka kallo daya za ka yiwa pilot Fa’eez ka karanto matsananciyar damuwa cikin fararen kwayar idanunsa. Duk da yaken da yake yiwa Aliyu da sauran ‘yan’uwansa. Yasa hannu ya karbi little Fa’izah hannun Zanirah ya dora a kafadunsa yana murmushi, kallo daya ya yiwa Ummi ya bude baki yana mamaki, ganin yadda kibarta ta zaizaye gaba daya, abin da babu wanda ya taba tsammani. Shi da ita murmushi suka yiwa juna, wanda ga Pilot Fa’iz murmushin ‘yan’uwantaka ne. Kuma ba annuri a fuskarsa har suka shisshiga motocinsu, yana motar Aliyu ne, Aliyun na tuki shi yana gidan gaba, Ummi da Zanirah da ‘yarta a baya. Sai dai tunda suka hau titin Zaria Road dodar wanda zai sada su da garin Zaria, kowa ya fahimci Pilot Fa’iz Bamalli cikin matsananciyar damuwa yake. Ya sanya fuskarsa cikin tafukansa Allah kadai ya san me yake tunani a zuciyarsa. Ummi ta yi tagumi a kujerar owner side da take zane. Wane irin mutum Fa’iz ya koma? Wane irin ango ne wannan babu wani alamar kulawa ko kwayar murmushi ga amaryarshi da aka daura musu aure yanzu-yanzun nan? Wane irin mutum ne shi da zai bar kasar haihuwarshi shekaru har shida da wani abu ya dawo babu alamun farin ciki a fuskarshi? Me ke damun shi? Anya Fa’iz na farin ciki da dawowar sa cikin ‘yan’uwansa? Anya Fa’iz lafiyarshi kalau? Anya Fa’iz na murna da auren su kamar yadda take tsammani? Ta jerowa kanta duka wadannan tambayoyin lokaci guda, ba ta da amsar ko daya, don haka ta sunne kanta cikin cinyoyinta ta soma kuka a hankali. Daga Aliyu, Zanirah da sauran kannensu dake cikin motar zuwa uban gayyar, babu wanda ya tambayi Ummi dalilin kukanta. Ga Aliyu shi kam abin ne ya zo mishi wani irin banbarakwai cikin sarkakiya. Bai san irin bayanin da zai ma kowannensu ba. Babbar fargabarshi yadda Fa’izah za ta karbi zancen aurenta da Fa’iz. A karo na farko ya ji haushin kansa kan munafuntarta da ya yi jiya, don me bai gaya mata gaskiya ba? Don me ya rufe mata? In kowa ya rufe mata shi bai dace da hakan ba. Ita kuma Ummi tunaninta da Fa’iz aka daura mata aure amma ganin halin ko in kula da ya nuna mata ya sanyata kuka. Shin da wane yare zai yi mata bayanin cewa da Bashir ne? Ya ya Ummi za ta tallafi maganar bayan yana da masaniyar cewar ta tsani halayyar Basheer fiye da kowa? Ta ya ya nitsattsiyar yarinya ‘yar kauyen Giwa ta cancanci tantirin dan duniya irin Yaya Basheer? Kaico da tunanin Hajjah! Kaico da bahagon tunanin iyayensu wurin hada irin wannan rikitacciyar auratayyar zumunci ko bata zumunci? Su kam sun haye! Yanzu na ‘yan bayansu yake ji. A zuciyar Zanirah cewa take yi, “Ina ma ban zo garin ba kwata-kwata balle in ga wannan rikitacciyar rana......!” A dai-dai lokacin da Aliyu ya karya kan motar cikin tafkeken (gate) din ABUBAKAR BAMALLI HOUSE.....” **** WANE NE NAZIRU GALADANCHI? Major General Sani Galadanchi shine mahaifin Dr. Nazir. Da na farko wurin iyayenshi, kamin haihuwar shi sun kwashe shekaru masu tsaho basu samu haihuwa ba. Da Allah ya kawo Naziru sai hakan ya zamo musabbabin nuna mishi tsantsar gata wanda babu kwaba ko tsawatarwa a cikin sa. Nazir ya tashi yaro dan hutu tun yana sakandire, sune samarin da ake kira ‘yan (high life) a lokacinsu. Haka nan bayan haihuwar Nazir sai da suka kwashe shekaru takwas zuwa tara kafin su samu haihuwar Haulatu. Daga Haulatu yara ne maza uku daya na bin daya duk bayan shekaru uku. Duk da jin dadi da sakewar da Nazir ke samu bai sa shi yin wasa da karatu ba, domin ya ga amfanin ilimin wurin mahaifinshi. Ya so ya tafi soja don ya gaji ubansa amma Baban ya dage kan harshen Larabci yake son ya karanta, baya son shi da aikin soja, babu kwanciyar hankali a cikinsa. Su shan sigari wannan duk a wurin Larabawa ya koya, sai dai sam in ya zo hutu baya sha a gida sai ya koma. Bai fara neman mata ba sai da ya kammala degree ya fara masters a zuwan shi bautar kasa garin Lagos, inda ya yi wani aboki Tim ya koyar da shi mu’amala da mata, don haka da ya koma Taiwan sai idonshi ya bude da hakan. A can ya kammala PHD ya dawo Kano ya fara aikin da yake yi a Bayero. Rasuwar Tim ta hanyar muguwar cutar (SIDA) Aids bai sanya Nazir Sani kintsuwa ba sai haduwar shi da Fa’izah A.A Giwa. Bai taba neman kowacce diya mace da niyar aure ba sai a kan Fa’iza, kamar yadda bai taba son wata diya mace tsakani da Allah ba baya ga Fa’izah. Bai taba tunanin zai bar yaudarar mata ba sai a kan Fa’izah. Daga ranar da ya dora ido a kanta, bai kara kula wata yarinya da sunan iskanci ko yaudara ba, domin yana ganin kintsattsiyar yarinya kamar Fa’izah ba ta dace da watsattsen miji kamar shi ba. Don haka ya kimtsa kansa, tun hakan bai zamo dalilin da za a hanashi Fa’izah ba. Tunda ya tabbatarwa kansa aurenta zai yi domin Allah da soyayya. Ya yarda ya amince da duk zargin da ake masa na cewa shi din dan iska ne, ya yarda ya kuma amince bai taba musantawa ba, kamar yadda bai taba cewa yana da wani hali na kirki ba. To amma wanda duk yake tarayya ta jiki da Naziru Sani, zai yi shaidar cewa mutum ne wanda baya wasa da sallah, kuma zuciyarsa daya ce da ita yake zaune da kowa, sannan ba shi da tsoro. Baya tsoron uban kowa, sannan abin hannunshi bai rufe mishi ido ba sam. Daga ranar da suka yi magana da Abdullahin Haulatu, ranar ba ta zagayo ba sai da Dr. Nazir ya gabatar da maganar Fa’izah ga iyayenshi, ya kuma roke su da aje mishi neman auren ta sati mai kamawa. Hajiyar su Haulatu ta yi matukar farin ciki da Allah ya nuna mata ranar da Nazir ya kawo mata zancen aure da bakinsa da ranta kafin mutuwar ta. ‘Yammata iri-iri ta sha nemawa Naziru yana fitittikewa, shi aure ba yanzu ba sai ya ci lokacinsa matarshi ma ba a haife ta ba. Da farin cikinta da rawar jikinta ta isar da sakon Nazir ga General, shima ya yi farin ciki sosai, suka yi ta yiwa Allah godiya. Tabbas addu’ar iyaye ba ta faduwa kasa banza a kan ‘ya’yansu, ko ba jima ko ba dade. A washegari ya tura kanin mahaifinsa da kanensa biyu da wan Hajiyarsu wurin iyayen Fa’izah. Haulatu ce ta ce dasu Kaduna za su wurin Alh. Muntari don shine madaurin auren su, ta karbi address wurin Aunty Rabi. Tarba ta girma da mutunci Mama ta yiwa iyayen Nazir ita da Baban Kaduna da suka ce daga Kano suke neman auren Fa’iza wa dansu Naziru, malami a inda Fa’izar take karatu. Sai mama ta kalli Baban Kaduna shima ya kalle ta aka rasa mai yin magana. Tun daga nan jikin dattijan ya fara sanyi. Da kyar Baban Kaduna ya ce, “Na yi mamaki da kuka zo neman aure ba tare da kun yi bincike a kan gidan su yarinyar ba. Ban da haka duk wanda ya san zuri’ar Abubakar Giwa, ya san basa auren bare. Ban fadi haka don yaron wajena ne mijin Fa’izah ba, sai don cewa ka’idar gidanmu kenan da muke bi tun iyaye da kakanni. Ina mai bai ma Naziru hakuri, ya yi hakuri, ya yi hakuri Fa’izah TA YI AURE!!!” Da wannan bakin labari Hajiyar Dr. N ta tare shi a dawowarsa daga wajen aiki. Labarin da ya yi masa bugun da wani labari bai taba yi masa ba. Ya dauki mukullin motarshi ya nufi kofa Hajiyarsa na kira, bai juyo ba yake fadin “Barni in je Hajiya, Giwan za ni in tambayi Fa’izah dalilin da yasa ni ban yaudareta ba ita ta yaudare ni...... ta san auren gida ake musu amma ta yi min haka.... me na yiwa Fa’izah da za ta zabi ta yi min wannan yankan kaunar ta yi dai-dai da zuciya da farin ciki na?” Gudun da yake shararawa a kan titin da zai kai shi garin Giwa ya fi kama da na ‘yan sumogal. Zagin duniya ya sha shi daga motocin gaban shi da bayanshi. A dai-dai kwanar da zai karya ya shiga Giwa suka yi arangama da motar shanu ta bi ta kan motarsa ta murkusheta irin murjewar da sai wani babban ikon Allah za a fidda mai rai a cikinta. **** GIWA Ban motsa daga inda nake ba, tun daga lokacin da na fadi na suma. Karar da na yi ya janyo hankalin Hajjah da sauran mazan dake zarya a tsakar gidan. A guje Hajjah ta shigo har tana tuntube da kofar daki tare da su Baba Barau da suka shigo a lokacin da ‘yan kanzaginta su Inna Kubra. Hajjah ta tsugunna da hannuwanta biyu ta girgiza ni tana kirana “Fa’izah...... Fa’izah!!” Baban Giwa (Barau) shi ya fita ya zo da ruwa a kofi ya shiga yayyafa min amma ban motsa ba, ga idanuna a bude ina kallon su tarrr! Hajjah ta shafi fuskata zuwa idanuna shima ban motsa ba, ta kama hannuna ta ji shi sanyi kalau, jijiyar ta saki. Ta dubi fuskata babu alamun rai a tare dani sai ta rushe da kuka. Inna Kubra ta soma karanto addu’a tana tofa min a fuska. Ya yin da Baban Giwa ke tofawa cikin kofi, ya kammala ya shara mini duka a kaina, sai na kwanto sharaf jikin Hajjah kamar matacciya. Ko dan yatsana na kasa dagawa, babu wata gaba dake motsi a jikina. Wannan ya tabbatar musu da cewa dogon suma na yi, irin wanda shock ke sanyawa, mai wuyar farfadowa. Hajjah ta rungume ni tana kuka ta ce, “Na shiga uku ni Hadiza, me ya yi zafi Fa’izah? Muddin kika mike Hafizi na isowa za a warware auren nan, ba zai yiwu garin neman gira a rasa ido ba. Wayyo ni Hadiza, wallahi na manta shaf da kiyayyar Fa’izah da Fa’izu da ba a yi auren nan ba”. Baban Giwa ya zauna gefe ya zuba min ido duk sunyi tsuru-tsuru, ya ce, “Uhm! Ai na fada Hajjah babu wanda ya saurare ni, yanzu in ta mace ai shi kenan hankalinki ya kwanta. Tun lokacin na Aliyu na gaya miki kada a kara aurarrakin nan kin ki ji. Yanzu ai an dau darasi ko?” Baban ABU wato mahaifina ya daga labule ya shigo yana cewa, “Zancen banza kake Barau, ba suma ba, ko mutuwa Fa’izah ta yi babu mai karya dokar Abubakar Giwa ko bayan ran Hajjah, mu zamu tsaya a kan wannan principle har karshen rayuwarmu. Tashi ka fita ka baiwa mutane wuri sakarai matsoraci girman wofi tun ranka bai baci ba wallahi”. Baba Barau ya kwantar da murya ya ce, “Nima ban ki hakan ba, amma a dinga duba soyayya tsakanin yaran nan kafin a kara kulla kowanne aure tsakaninsu. Fa’izah da Fa’izu basa ga amciji tun tali-tali har zuwa girmansu. Baban ABU rai! Yana gaba da komai, sai da shi ake komai”. Fa’izun ne ya bankado labulen dakin ya shigo a sukwane kamar an jefo shi tare da Yaya Aliyu, don tun fitowarsu mota Khalid yaron Baban Giwa ya ce dasu wai Fa’izah ta yi kara ta mutu! Bai iya ya ce komai ba duk da ya ji kadan daga abin da suke tattaunawa, illa bin Fa’izar da ke yashe a kasa mushe ko mai rai da kallo. Manyan fararen idanuwanshi gaba daya sun fito waje sun yi jawur, har wani brown-brown suka koma. Jikinsa sai mazari yake bakinshi na motsi, amma ya kasa magana. Aliyu ya ce “Shin Baba me kuke yi haka dukkanku tun dazu da aka rasa mai kaita asibiti? Fa’izah ba mutuwa ta yi ba!” Sai ya sunkuya ya ciccibe ta gaba daya, Fa’iz ya hade girar sama da na kasa ya ce, “Ko da ban karanta ba na san maganin wannan suman...” Da sauri Yaya Aliyu ya dire ni gefen gado ya yi baya, ya ce, “To likita mai mata Bismillah” Ya yi waje abinshi. A ranshi kam dariya ma abin ya ba shi yana ta yin ta ciki-ciki, wai matar dake tsakanin rai da ajali ake ma kishi? Bai san gara ta dauwama a suman ba da ta farfado ta ganshi. Ya karbi diyarshi da ke ta tsala ihu hannun Ummi a falo ya yi waje. A hankali su Baban ma suka shiga ficewa daya bayan daya ba tare da kowannensu ya sake tofawa ba. Hajjah ta share hawaye ta ce, “Yanzu Hafizi ya za ayi Fa’izan ta farfado?’ Fa’iz cikin jin haushinsu duka ya ce, “Ban sani ba Hajjah”. Ita ma a fusace ta ce, “Amma ka hana a kaita asibitin?” Ya fiddo ido ya ce, “Hajjah bakya gani daukarta ya yi ne?” Hajja ta hasala ta ce, “Zancen banza zancen wofi, yau ga sakaran kawai. Sannu mai mata, hala gawa za ka aura? To in gaya maka gaskiya auren nan kunce shi za ayi ba zai zama sanadiyyar rasa ran Fa’izah ba. Da na san haka abin zai zama tun farko da ban saurare ka ba.....” [14/02 3:41 PM] Sumayya Takori: Surutun Hajiya kara kular da shi yake. A kufule ya ce, “To na ji Hajjah, in ta farfado din sannan ki san abin yi ko ba yanzu ba da lafiyarta ake nema ba komai ba”. Hajjah ta wuce tana fadace-fadacen ta da mita wanda Fa’izu bai saurari ko daya daga cikinsu ba. Pilot Fa’iz Giwa babu abin da ya gama shi da asibiti. Amma tsabar kishin kada Aliyu ya daukar mishi mata ya gwammace kada a kaita asibitin. Shi kam yanzu ya fara son Fa’izah ma da damarar rayuwa da ita. Sai dai ta mutu su je lahira suyi aure su zauna tare, amma Hajjah ta canza masa farat daya kamar ba Hajjar shi ba wadda ta fi kowa son shi a duniya including iyayenshi, ta fi shi son duk abinda yake so, ta fi kowa farin ciki da ya ce a aura mishi Fa’izah ba. Ta yi murna, ta sa mishi albarka har da kukan farin cikinta. Amma da ya dubi halin rai kwakwai mutu kwakwai da Fa’izar ke ciki sai ya yi mata uzri. Firjin dake gefe ya bude ya fiddo ruwa mai sanyi ya zuba a kofi ya tsugunna ya karanto Ayatul-Kursiyyu, Falaqi, Nasi da Ikhlas. Ya karanto karshen Suratul Al-Imran wato daga (Rabbana faghfirl lana wa af-anna) ya karanto ayoyin karshe na suratul Hashri tare da addu’ar Yusuf (A.S) a lokacin da ya shiga kunci a kurkuku, da addu’ar Yunusa (A.S) duka ya tofa a cikin ruwan, duk wata addu’ar yayewar kuncin zuciya da ta zo bakinshi ya tofa a ciki. Ya shafe min fuska da ruwan har cikin kirjina dai-dai santar zuciyata. Na lumshe ido a hankali amma ban motsa daga yadda nake ba, Fa’iz ya samu kanshi cikin tsananin rudewa da firgita, bai san sanda ya kwalawa Ummi da Zanirah kira ba. Dama suna falo suna ta tsuma. Zanira a guje Ummi da sassarfa suka fado dakin. Ya ce, “Shi kenan da gaske ne ta mutu, ku ce da su Baba su zo su binneta....” Fa’iz kuka yake sosai da hawaye da zuciyarsa. Haka Ummi da Zaneerah. Ko kusa da Fa’izar sun kasa karasawa. Aunty Hauwa ta shigo dakin da saurinta, da alama zuwan ta gidan kenan. Tana ta fada kamar ta ari baki, “Wane irin hauka ne wannan Fa’iz? In ka hana Aliyu kai Fa’izah asibiti me kenan ka yi? Ko meye ribar ka cikin hakan? Wai ma tukunna Fa’iz da na sani ne kuwa? Crying for the sake of Fa’izah’s unconsciousness?” Ta yi murmushi, duk ita daya ta ciccibeni gaba daya ta yi waje. Fa’iz bai ce komi ba, illa rakamu da kyawawan idanunsa dake cike da hawaye sun kuma kada sunyi jair. Sai kuma ya tashi da hanzari ya bita. Aliyu ya yi dariya ya aje little Fa’izah ya bisu ya ja motar zuwa asibitinsu wanda ke bayan gidan duka cikin A.B Estate wato A.B Clinic and Maternity. Likitoci biyu ne suka rufu a kaina suna kokarin ceto numfashina. Fa’iz ya shiga kai kawo tsakanin gabas da yamma, kudu da arewa. Ya yin da Aliyu ya jingina da kofar (Emergency Room) da nake ciki yana hango fuskata cikin (oxygen) da aka makala mini. Aunty Hauwa ta yi tagumi a kan kujera ta rasa abin da yake mata dadi. A haka jama’ar gidanmu da ‘yan daurin aure duka suka taddamu wannan ya harari Fa’iz wannan ya tausaya mishi, babu wanda ya iya ce masa ko da sannu da zuwa bayan shekaru masu dama da suka kwashe basu sanya shi a idanunsu ba. Shi kam Babana kujera ya samu ya kame yana kallon kowa daya bayan daya. A lokacin Baban Kaduna wato Alh. Mukhtar ya iso asibitin. Da Dr. Habib ya fito ya nemi son ganin daya daga cikinsu Baban Kaduna ne ya shiga. Ya ce, “Muddin Fa’izah ba ta farfado ba nan da awanni uku, to zai yi wuya in ba coma bane ta shiga. Sannan jininta ya hau, mugun hawa kuwa, zuciyarta ta tabu. Kokarin da muke yi yanzu shine na jininta ya sauka, numfashinta da bugun zuciyarta su dawo dai-dai. Na roke ku idan an samu Fa’izah ta farfado ku guji gaya mata awkward incidence ba ta hanyar da ta dace ba. Domin sudden unpleasant shock ya kan harbi kwakwalwa har ya haifar da depression’. Baba Muntari ya shiga sharar zufa, babu shakka ya shiga tashin hankali. Ya ce, “Ba komi likita, shi kenan ai in an samu ta farfado din shi kenan. Kuma ni ban san abin da aka gaya mata na tashin hankali ba, aurenta kawai aka daura da dan’uwanta yanzu-yanzun nan, bayan wannan ban san komai ba, dama can tana da makamancin ciwon hawan jini ko (something associate) ne bamu sani ba?” Dr. Habib ya ce, “Lafiyarta kalau. Sudden shock ne wanda zuciyarta ta kasa karba kawai. To ko auren ne ba ta so?” Baban Kaduna ya ce, “Mai yiwuwa. Biri ya yi kama da mutum, domin wasu daban sun zo neman auren ta. Bari in je in same su in ji”. Ya mike ya firto fuskarshi babu annuri sam. Barau ya kira gefe suka yi magana don da shi ya fara cin karo, ya kuwa gaya masa komai a gurguje cewa, Fa’izah ba ta son Fa’iz tun tana kankanuwa, Fa’iz ya tsani Fa’izah, tunda aka haifeta basu taba zama a inuwa daya ba dai-dai da sakan daya. Aliyu ta so ta aura kuma da bata samu ba ta dangana saboda Zaneerah. Tun sanda Hajjah ta fara fito da zancen ya same ta cikin sirri ya ce kar a soma wannan kada gyara zumunci ya zama bata zumunci. Su da aka yi musu haka suka zauna lafiya, to fa in babu soyayya a tsakani haka babu kiyayya, kuma su na jiya ne ba na yau ba, zamani kullum canzawa yake yi. Zai fi kyau a dinga karbar canjin da ya zo da shi idan babu sabon Ubangiji ko halaka a cikinsa”. Jikin Baba Muntari sanyi kalau kuma ransa ya baci domin shi ba haka Fa’iz da Hajjah suka gaya mishi ba kafin ya karbi waliccin auren nan. Ya dauka cewa ko da hakan (doctrine) din su ne kuma umarnin Hajjah ne, to babu wani abu makamancin wannan tsakanin Fa’izu da Fa’izah. Ofishin Dr. Habibu ya koma ya dauko takarda da biro ya fito ya doshi Fa’iz wanda ke tsaye gefe yana kallon su cikin dimuwa, don ya amince ba ALHERI Baba Barau ke gayawa Baban Kaduna ba, ganin yadda fuskarsa ma’abociyar kamala ke tattarewa tana yamutsewa. Don haka ganin ya nufo shi da takarda da biro fuskarshi babu alamun rahama, sai ya ji hanjin cikinsa suna dunkulewa wuri guda. Fa’iz ya daga dara-daran idanunshi da suka kada suka yi jawur ya dubi Baba kallon rashin fahimta, ya motsa baki zai yi magana amma ya rasa me zai ce ne. Baba ya ce, “Karbi ka rubuta min saki uku yanzun nan Fa’izu”. Fa’iz ya ja da baya ya soma hawaye ya ce, “Baba Fa’izah za ta farfado ne, amma ni ba zan yi saki ba....” Baba ya ce, “Fa’iz har ka yi kaurin wuyan in fadi ka musa min? In ka kashe ta za ka auri gawarta?” Fa’iz ya shiga girgiza kai ya ce, “Shin Baba a kan me za ka yanke wannan danyen hukuncin gare ni? Ka sani muddin ka takurani na rubuta takardar nan shi kenan, in na tafi ba zan kara dawowa kasar nan ba, kuma ba zan.....” Wani irin mari Baba ya share shi da shi, sai ga habo ta hancinsa. Ya kai hannu zai sake sharara mishi Babana ya rike hannun tamau. Suka juyo suka fuskanci juna su biyun, kowanne zuciyarshi na tafasa, inda Baban Kaduna ya yi amfani da gadarar shekaru biyu da ya tserewa Baban ABU da su ya ce, “Ni sa’anka ne Ahmadu? Ko ko akwai irin wannan wasan tsakaninmu?” Babana ya ce, “Babu ko daya, amma a nan kam ka yi zalunci in ka takurawa daya don amfanin daya. Aure kuma Fa’iz ba zai saki ba in dai a kan don kar wannan yarinyar ta mutu ne. Mutuwa lokaci ne kuma tana kan kowa, sannan lazim ce baka isa ka kara mata dakika daya daga wanda Ubangiji ya riga ya rubuta mata ba. Ni dai ni na haifi Fa’izah in kuwa ni din ne to in ta mutu na yafe, zan dawwama da farin cikin cewa da igiyar auren Fa’iz ta mutu cikin cika burin mahaifinmu Abubakar Bamalli. Sai dai fa abin bai kai da duka ba, Fa’iz ya wuce duka! Sai dai in Fa’izah ta kashe kanta a kan shirmen banza ta mutu kafira ba ruwana, amma aure ko ka kunce sai na sake daurawa. Ba a haifi dan da ya isa ya ki bin umarnin A.B Family ba, ba a haifa ba in dai ina da rai, ba kuma za a haifan ba. Fa’izu jeka abinka sai na neme ka, kada ka kara wahalar da kanka zuwa asibitin nan”. Fa’iz ya juya da sauri ya fita duk gaban rigarsa ya baci da jinin dake fita daga hancinsa. Ya dauki motar Aliyu da suka zo a ciki ko rufewa bai yi ba ya yi ribas da gudu ya fita daga estate din baki daya ya bar garin Giwa baki daya ya nufo Kaduna. Yadda ya shigowa Mama falo ya firgitata, sai dai kuma ba ta yi mamaki ba sam, habon ne da bacin da rigarsa ta yi da jini ya daga mata hankali, amma ba ta nuna ba. Tozali na farko da Abubakar Fa’iz dinta bayan shekaru takwas. Amma ta ganshi cikin wannan halin mara dadi da kyawun gani. Ta yi tagumi ta zuba mashi ido sai zufa yake. Daga bisani ya mike ya ware karfin A.C falon gaba daya da fanka, ya yi kwance rashe-rashe a tsakiyar falon yana lumshe ido yana budewa a hankali, shi kadai ya san abin da ke cin zuciyarsa, sai ko Ubangijin da ya halicci zuciyar ya sirrantata ya sanya mata hijabi don ta zama sirrin dan Adam da Ubangijinsa. Ita Mama zato take ma Fa’iza ce ta fasa masa hanci, ta ce cikin ranta, ai tayi da sauki da ba kan duka ta rotsa maka ba. Ta shige kitchen ta sakar masa labule ta janyo masa kofa. **** Karfe biyar na yamma agogon dake dakin asibitin ya nuna, wanda ya yi dai-dai da lokacin da na ja dogon numfashi tare da ware dukkanin idanuwana kan likitoci biyu dake kaina. Dr. Habib da Dr. Imoh suka dubi juna suka yi murmushi tare da zare na’urar da suka makala mini. Kwata-kwata na mance komi, ban san abin da ya faru dani ba da har ya kawoni gadon asibiti. Dr. Imoh ya ce, “Ya ya dai Fa’ija?’ Na yi murmushi na ce, “Bani da lafiya ne na ganni a clinic?” Dr. Habibu ya ce, “Of course Fa’izah! Za ki dinga fama da migraine (ciwon kan barin kai guda) lokaci zuwa lokaci. A duk lokacin da kika ji ya tashi, akwai kwayoyin da zan baki ki dinga hadiya kin ji ko?” Na gyada kai. Suka juya suka fita suka jawo min kofar. Nurse ta shigo ta gyara min kwanciya ta fita. ‘Yan’uwa da iyayena suka shiga shigowa mutum uku-uku suna duba ni suna fita. Shigowar Ummi da Zaneerah daga karshe ya tariyo min abin da ya faru awanni shida da suka gabata. “....... An daura aurena da FA’EEZ, FA’EEZ BAMALLI.!..... Fa’izun gidan Baban Kaduna...... Fa’iz Yayan Zaneerah, Fa’iz mugu, azzalumi, makaryaci, maketaci mai cin amanar ZUMUNCI da tozarta shi a gaban ko a bayan idon kowa... Munafuki, masharranci.... Fa’iz da na sani? Fa’izun Hajjah? Fa’iz da na tsana tamkar mutuwata...... Fa’izun da ya nuna min tsanar da a duniya babu wanda ya nuna min kwatankacinta, mai cin mutuncin mahaifiyata! Fa’iz! Fa’iz!! Fa’iz Mukhtar Abubakar Bamalli Giwa......!!!” Na mike zaune sannu a hankali ina bin Ummi da Zanirah da kallo, wadanda bayan kalmar sannu da jiki basu kara ko tari ba. Na kai hannuwana duka biyu na rike kaina dake juyawa yana sarawa tamkar ya tsage. Idanuwana suka kada suka yi jajawur suka kankace, na dubi Ummi, Zanira, Yaya Aliyu da Babana da suka shigo daga baya. A lokacin ne hawaye suka soma zuba min tarara! Na bude baki zan yi magana na kasa. Wani kunci da bakin cikin da ba zan iya fassarawa ba ke azalzalar tsakiyar kirjina, na kai hannuna na dafe kirjin na ce cikin rishin kuka, “Baba anya kana sona kuwa? Da hadin bakinka aka yi min haka? Da saninka aka daura min aure da Ya Fa’iz? In kun hanani Nazir ku rasa wanda za ku lika min duk cikin zuri’armu sai Hafizin Hajjah? Baba kana sane da tsakanina da Fa’iz tun tali-talin kuruciya har girma! Baba Fa’iz fa ya tsaneni nima haka!! Makiyinka baya taba rikidewa ya zama masoyinka, har abada Baba. Don me baku hada shi da Ummi dake son shi yake son ta ba? Ya ya kuke so na yi da nauyin so, kunya da alkawarin da na yiwa Dr. Naziru?” Na shiga rurin kuka mai tsima zuciyar duk mai imani, balle MAHAIFI. Amma Baba bai ce komi ba, karewa ma fita ya yi daga dakin baki daya. Su Aunty Hauwa duk suka sake shigowa, ashe suna kofar dakin basu tafi ba. Yaya Aliyu ya dubi Aunty Hauwa cikin bacin rai ya ce, “Gaskiya-gaskiya ba a kyauta ba”. Aunty Hauwa ta harare shi ta ce, “Saboda me baka gayawa wanda ya fita ba? Ko kuma kana so ka kara da ta biyu ne?” Ya yi tsaki ya girgiza kai ya ce, “Ki bar maganar wasa Aunty Hauwa, ko kadan babu wannan tsohuwar ajiyar a zuciyata, illa gaskiya duk inda take dole in fade ta, ba a kyautawa Fa’izah ba! Ko babu komi yanzu Fa’izah matar Fa’izu ce, kinga kuwa ai babu sauran zance”. Aunty Hauwa ta yi murmushi, ban ga alamar ba a kyauta min din ba a fuskarta. Yaya Aliyu ya ce, “Fa’izah bani da ilimin (psychology) amma ina da tabbacin yadda kika ki auren nan haka Fa’iz yake kin shi ko ma fiye. Haka na dauka kafin ya dawo tun sanda iyayenmu suka fito da zancen. Amma Fa’iz ya zo da wani sauyi mai ban mamaki da na kasa fassarawa, he’s completely a changed person, unpredictable. Hajjah kanta yanzu ba ta son zancen auren ganin halin da kike ciki, haka Baban Kaduna da Baba Barau. Baban ABU da Baba Na’ibi da sauran hadin sune kawai, kuma su kadai ke son abin a yanzu. Yanzu Baban Kaduna ya gama fada da Baban ABU a kan a raba auren tunda yanzu ya fahimta abin da babu wanda ya fahimtar da shi a baya. Don haka ki kwantar da hankalinki ki saki ranki ki koma cikin nutsuwa da walwalarki, babu inda auren nan zai je tunda kaso mafi rinjaye kuma (most powerful) yanzu basu so. Ki bisu da duk abin da suka umarceki da dadin rai, ki kwantar da kai ki roki Fa’iz in har baya sonki ya baki takardar saki, na rantse miki in har yanzun baya sonki zai baki ko don maslahar kansa, ni kuma idan har ya baki, ni kuma na yi alkawarin duk yadda zan yi zan yi in ga kin auri zabin ranki, wa ma kika ce yake da suna?” Maimakon kalaman Yaya Aliyu su faranta mini ji na yi sun bakanta mini kamar akwai rainin hankali a cikinsu, musamman da na ga Aunty Hauwa ta bamu baya tana danna waya, ba shakka dariya take. Na dubi Yaya Aliyu a hankali da rinannun idanuna jage-jage da hawaye. Akwai wani irin yanayi a tattare cikin kwayar idonsa wanda ban saba gani ba in yana magana. A duk sanda Yaya Aliyu ke magana, kwayar idanunsa kan nuna gesture wanda ke tabbatar da abin da yake fadi. Amma a yau, ina shakka, Ali Na’ibi ya ki mu hada ido in hango wancan gesture din dake cikin kwayar idanunsa, ya juya wani bangaren ne daban baya kallon idanuna, kuma fuskarshi ta yi jawur abinki da farin mutum, farin Bafillace, Bamalle. Tsagin Mallacin ya fito rada-rada a gefen fuskarsa, kamar wanzamin A.B ya tisa. Idona a kanshi bana ko kiftawa na ce, “Yaya Aliyu ka rantse min da Allah ba da yawun Fa’iz aka daura mana aure ba”. Yaya Aliyu ya dan rikice kafin ya ce, “To Fa’izah me ya kawo rantsuwa, baki yarda dani ba kenan? Za ki dora min kaffara a kan abin da bani da tabbacinsa”. Na ce, “Duk ba haka bane Yaya Aliyu.....” Aliyu ya dubi su Ummi da su Aunty Hauwa kowacce sai ta sunkuyar da kai aka rasa mai yi min rantsuwar da nake so ya yi min din, duk da na san basu da masaniya a kan komai, musamman Ummi. Aunty Hauwa ta ce, “Fa’izah ki saurare ni, duk kin bi kin ta da hankalinki a kan abin da bai kai ya kawo ba. Fa’izu dan’uwanki ne ko babu aure tsakaninku ba zai cutar dake ba, ko baya son naki aure Ibada ne ba don biyan bukatar rai ake yinsa ba ko soyayya kadai. Ki dubi girman zumunci da nonon da iyayenku suka tsotsa tare ki kwantar da hankalinki ki manta da kuruciya..... daban take da GIRMA! Dukkaninku jiya ba yau ba!! Babu wanda bai mallaki hankalinsa ba, abin da kuke yi a da duk kuruciya ce.....” Wani irin kallo na yiwa Aunty Hauwa wanda ita kanta ya tsoratata. Ya kuma ba ta mamaki a yadda dai matsayinta yake a gare ni da yadda muke girmama su. Na ce, “Uhm! An daura fa! Nima shaida ce a kan hakan. Sai dai wallahi yadda aka daura haka za a sunce. Wallahi-wallahi in har ina numfshi babu inda auren nan zai je daga kaina ba zaku sake ba A.B. Da in yi zaman aure da Fa’iz na gwammace in kare rayuwata haka nan single! Da in zauna da Fa’iz gara min zamana a kabarina, gara na ga mutuwata, gara min zama da bakin kumurci.... gara na rasa rayuwata dungurugum!!!” Wani irin juyi da barin kaina ya shiga yi ya tabbatar min (migraine) da likita yake magana ya tabbata. Na dafe kaina na shiga kuka sosai. Na ci gaba da fadi cikin gunjin kuka. “Ya ya ma hakan zai taba faruwa? Wallahi ba zai yiwu ba!” Ni kadai kamar mahaukaciya nake ta wannan sambatun sun yi min shiru. Wannan ya kara tunzura zuciyata. Tunanin halin da bawan Allah. Dr. N zai kasance a ciki idan ya tsinkayi wannan labarin ya kara sanya ni tsandara kuka da kara duka a tare. **** Kwana biyu kacal duk na rame fiyet na zabge na fita a hayyacina. Sai ka rantse na yi shekara ne a kwance. Likita ya bamu sallama tare da kashedi iri-iri ga su Babana. Baban Kaduna ya ce, “Af! Ai aure ba makawa za a kwance shi me ya yi zafi?’ Wata sabuwa in ji ‘yan caca! Hajjah ta dawo ta girgije ta sanya ranar biki kwanaki bakwai masu zuwa, kasancewar ana jiran Basheer da zai dawo kwanaki uku da zuwan Fa’iz. Ashe daman rudewar ganin halin da na shiga ya sanyata canza alqibla a baya? Uhm! Zan ga wanda za su yiwa bikin kuwa. Babban rangwame ga zuciyata ban sa fuskar azzalumin ko sau daya a idanuna ba balle keyarshi. Wannan ya tabbatar mani lallai ne shima yana tsoron haduwar mu which I believe must be the most dangerous approach bayan gushewar shekaru masu dama. Ummi kam ta rungumi kaddara, ta bi umarnin iyayenta, a cewarta, iyayenmu ba za su taba zaba mana abin da zai zama cuta garemu ba. Ba za su taba kaimu mahalaka ba (Ummi fa ba ni ba). Karfe tara na dare na kadaice kaina cikin (store) kuka nake kamar raina zai fita. Irin shirye-shiryen da na ga A.B baki daya na yi ya tabbatar mani biki babu fashi za su yi shi. Ba ruwan kowa dani, ba mai shiga sabgata don da alama basu ma dauke ni a cikakkiyar mai hankali ba. Da na yi na gaji, babu mai rarrashi, babu kuma abin da kukan zai tsinana mini, sai na daura dukka hannuwana biyu a ka na shiga kwarara ihu tun karfina, ina bubbuga hannuwana jikin buhunhunan masara da shinkafa dake lode a store din. Jama’ar gidan duk suka baro abin da suke yi suka taru a kaina ban ga alamar akwai mai shirin lallashi na ba ko tambayar ba’asin ihun da nake yi. Kallo na suka tsaya yi tamkar masu kallon talabijin. Ummi ta yi tsaki ta ce, “Allah wadaran rashin tawakkali da rashin hankali da sakarci wallahi! Shin cikinmu don wa kike wannan haukan Fa’izah? Aure dai baya wurinmu kuma bamu muka daura ba balle mu warware miki, don haka ki kyale mana kunnuwanmu su huta”. Hajjah ta fito daga kitchen ta ce, “Don son Annabi wanda duk ke son gamawa da duniya lafiya ya tafi a wurin nan ya kyale Fa’izah!” Na sake sheko ihun tun karfina, na ce, “Hajja kun cuce ni, ku doke ni ku hanani kuka? Ku kulla min igiyar aure da mutumin da na ki jini a duniya fiye da mutuwa ta, bayan kin raba ni da wanda nake so da farko da na karshe, sannan ki ce ba zan yi kuka ba? Shin in ban yi kuka ba ya rage min radadin da zuciyata ke yi kashe kaina kike so in yi don bakin ciki ko me?” Baban Giwa ya ratso mutane bayan ya karyo reshen dalbejiya ya ce, “Uwar waye ta cuce ki ba dai uwarmun ba ko? Ja’irar yarinya har nake daga hakarkari nake son ayi miki son ranki don a zauna lafiya, ashe baki da mutunci baki da da’a? Hajjah kike cewa ta cuce ki?” Ya zuge ganyen baki daya ya shiga dankara min dukan da ake kira dukan mutuwa, wanda tunda nake a rayuwata ko makamancinsa ba a taba kwatanta min ba, amma bakina bai mutu ba, bai huta ba da fadin “Hajjah kin cuce ni.... kin raba ni da burin da na ciwa rayuwata.... ba zan taba yafewa ba muddin rayuwata.....” Hajjah ta soma kuka da idonta a yayin da ta kama hannun Barau ta ce, “Kyale ta haka nan, Fa’izah ba ta cikin hankalinta, ka kyaleta na ce kada ka yi abin da za ka zo kana nadama, in kuma baka bari to ka sauke zuciyarka a kaina ka karasa min dukan”. Baba Barau ya yar da tsumagiyar ya yi waje fuuuu! Kamar kububuwa, jikinsa har tsuma yake. Na tabbatar da Babana ne yau sai dai a dauki gawata in ya so shima a kashe shi. Hajjah ba ta yi fushi ba ta kama ni za ta mikar dani, cikin kurarin kuka na ce, “Kada ki kuskura ki taba ni..... Daga yau ba zaki sake ganina ba balle ki yi iko dani. Ki tuna Ubana kika haifa ba ni ba, don haka ko kashe ni aka yi babu ruwanki......” Zaneerah da Ummi suka saki kuka, “Fa’izah kina da hankali?” Na ce, “Kwarai, Baba Muntari da Aunty Hauwa ke rabon ciwon hauka har na je Kaduna na samo. Ko me za ku ce ku ce wallahi banni zaman aure da Fa’izou......” Jini ke bulbula ta hancina yana shiga bakina inda Baban Giwa ya shauda min dalbejiyarshi a kan hanci. Na kai hannu na share a yayin da na zaro jajayen idanuna suka kumbure suka suntume suka yi luhu-luhu jajir. Na ce, “Ku bace min da gani ko in kakkarya ku na rantse yanzun nan, manyan munafukai algungumai, ai daku aka kulla komai amma babu wadda ta gaya mini. Tsakanina daku sai Allah ya isa!” Ai kamin in rufe bakina na nemi kowaccensu daga yaran har manyan na rasa. Na ci gaba da gunza kuka ban ko damu da radadi da zugin da jikina ke yi mani ta ko ina ba. Muryar Yaya Aliyu daga tskar gida ya tabbatar mani ya shigo gidan. A yayin da Ummi ke fadi mashi cikin kuka........ “YAYA ALIYU FA’IZA TA HAUKACE!” Wadannan sune kalamai mafi firgitarwa da Aliyu Na’ibi ya taba ji a tsayin rayuwarsa. Baya ga dogon salati da ya ja ya dire ya tsarkake Ubangiji ya yiwa Annabi salati, sai ya sanya hannu ya zare hularsa da takalmi ya ce, “Tana ina?” Hajjah dake sharbar kuka zaune a kofar kicin ta yi mashi nuni da hanyar store. Aliyu ya shigo a hankali ya kunna fitilar da na kashe ya zauna gefena a hankali, ya dubi yadda na yi jina-jina, face-face cikin hawaye, jini da majina, ya matso kwallar da ta tarar masa cikin ido. “Shin wane ne da wannan danyen aikin haka Fa’izah?” Na ja shesshekar kuka cikin dusasshiyar muryar da ta dushe gaba daya, “Kadan kenan tun yanzu kan DAN DA KOWA KE SO. Nan gaba in na batawa Fa’iz mai yiwuwa a nakastani ko a hura wuta a babbaka ni Aliyu? Ba dukan kawo wuka ba, ko yankani A.B za ku yi gunduwa-gunduwa ba ni auren nan. Na gwammace in bi yawon dandi, da dai in yi karashen rayuwata a matsayin matar FA’EEZ BAMALLI!” Aliyu ya kaskantar da murya ya ce, “Fa’izah! Abin bai yi zafin haka ba ai. Kash! Ki bar furta kalmar nan ta “DANDI” ba don ni ba, ba don halina ba, ba don halinsu ba su duka iyayenmu. Sai don darajar da Allah ya yi miki ta ‘ya mace mai cikar mutunci ‘yar manyan mutane, kuma ‘yar gidan mutunci kamar A.B. Su wadannan da kika bi kika tadawa hankali meye ruwansu ne? Me ya shafe su? Aure dai sun yi kuskuren daurawa. Amma igiyar warware shi da kwance shi ba ta hannunsu balle su kwance ko su warware. Duk wannan kakabi da zagi da tashin hankali ba nasu bane, ba su ya kamata ki yiwa ba tsakaninki da Fa’iz ne can. Amma ina ruwan Ummi, Hajjah ko Zanirah?” Na galla masa harara na ce, “To shin ina na ganshi balle in yi mishi Yaya Aliyu? Ni kam yadda nake ji a zuciyata baki dayan A.B nake jin haushi. Har kai din wallahi”. Murmushi ya yi, ya rausayar da kai, “Ta ina laifin wani ke shafar wani? Har da Yaya Aliyu? Fa’izah” Fa’eez shi ya nemi aurenki da kansa domin gyara zumuncinku da ya gurbata a baya”. Ban san sanda na lailayo ashar ba na ce, “ZUMUNCIN me? In dai wannan shi ake kira gyara zumunci to ba shi bane, sai dai kara lalata shi. Na ji zan iya yafewa Fa’iz dukkan abin da ya yi mani, amma ba ta hanyar aure ba. In dai har an yarda a raba auren nan in auri Dr. N na YAFEWA FA’IZ DUK ABIN DA YA YI MANI A BAYA!” [15/02 4:13 PM] Sumayya Takori: Aliyu ya ce, “A da har an tayar mani da hankali da aka ce dani wai “Fa’izahna ta haukace! Ashe lafiyar kanwata lau. To share hawayenki ki bar ta da hakarkari tunda kin ce haka shi kenan. Yanzu abin da za ayi Fa’iz za ki yiwa wannan bayanin ta lallama da salama da kwantar da kai. Kin san an ce..... mai nema shine a kasa har kullum. Don haka kada ki ji komai don kin roki Fa’iz wani abu wannan hakkinsa ne a yanzu. Shi ke da ikon yi ko ki. Don haka dole ki aje rawanin kiyayyar gefe ki roki Fa’iz. Yanzu Fa’iz ya canza, ba shi da wannan muguwar azzalumar fuskar da kike fadi, ke tsoronki ma yake ji! Kin san an ce abin da ya baka kuka wata ran shi zai baka dariya. Haka abin da ya baka tsoro wata ran shi zai baka dariya. Baki ga ya kasa zuwa ba? Amma ina ruwan su Zaneerah, Ummi da tsohuwar Allah HAJIYA HADIZA?” Na girgiza kai hawaye na zuba na ce, “Yaya Aliyu kai kadai ke sona a cikin gidan nan tunda har ka goyi da bayana ka gane abin da nake so su gane suka kasa ganewa, wato Fa’iz ba mijin aure bane, ba masoyi bane abin neman tsari ne. Don haka na dauki shawararka, ka je ka baiwa su Hajjah hakuri domin na zage su sosai”. Aliyu ya yi murmushi ya ce, “Har na ji dadi, ni Aliyu Baban Fa’izah! Allah yasa nima tawa Fa’izar ta yi min biyayya haka tamkar mai sunan ta. Share hawayen nan duka A beg...” Nasa habar zanina na share hawaye tas, duk jikina rawa yake da karkarwa. Aliyu ya ce, “Kada ki damu da su Hajjah, su tunaninsu kin samu motsi a kanki ne. Don duk kuka suke miki na tausayawa. Ni kam na san babu yadda za ayi Fa’izata ta haukace a kan Fa’iz, faruwar hakan na nufin kenan FA’IZ ya yi galaba a kan FA’IZAH!” Na ce, “Never. Idan har na yi hauka saboda Fa’izu na ji kunya na fadi babu nauyi, kuma ban haifu cikin Maimunar da yake zagi ba tunda ban rama komai ba, tunda na bar Fa’iz cikin nasa hankalin. Wata ma zai je ya auro wadda ta fini ya ci gaba da rayuwarshi normal ni ko in kare a pyschiatric da Asylum”. Cikin murmushi sosi Yaya Aliyu ya ce, “Yauwa, ashe dai kin gane. Amma in ya baki takarda kika yi auren ki da Dr. Nazir kinga ai kin tusa mishi haushi ko baya sonki zai ji kishi, tunda akwai igiyar aure da ta taba gittawa a tsakanin ku, ko ya ya ne. In hakan ta faru da kyar ma zai iya zaman kasar ko ya kika ce?” Na yi murmushi da kumburarriyar fuskata na ce, “Shin Yaya Aliyu ina zan ga FA’IZ BAMALLI?” Yaya Aliyu ya ce, “Fa’eez na cikin kasarmu mai dimbin albarka yanzu haka. Za ki ganshi yau, gobe, jibi ko gata. Muddin ranakun nan suka wuce baki ga Fa’eez ba, to kirayi auren ku da suna tabbatacce na muddin rai. Domin sune ranaku na karshe da za a kammala bikinku a kai ki gidansa kina so ko bakya so. Don haka ki yi duk kokarin da za ki yi ki ga Fa’iz cikin kwanaki uku”. Na yi zugum ina kallon sa, na ce, “Shin don me ka boye min tun a daren ranar Yaya Aliyu? Wallahi-wallahi da duk yadda za ayi ba zan bari a daura auren nan ba......” Na ci gaba da kuka. Aliyu ya rasa me zai ce mini? Shi kam dabararsa ta kare kuma. Sai ya ce, “Ni kaina Fa’izah yanzu ba na ce miki ga hakikanin inda Fa’iz yake ba, rabona da shi tun ranar da ya dawo”. Da lallami da ban baki gami da dabara irin na Yaya Aliyu yasa na tashi daga store na je na kwanta a gadon Hajjah. Daga Ummi har Zaneerah babu wanda ta yi gigigin shigowa don kam su tsorona ma suke ji. Yarinyar da za ta bude baki ta zage Hajjah cikin A.B ai abar tsoro ce, balle nasu iyayen karan-kada miya. Yau da Baban ABU ya ji kalaman nan da na kade har ganyayyakina. Cikin daren na dinga shesshekar kuka ni kadai ina watangaririya a kan gadon Hajjah, daga wannan gefe zuwa wancan. Na turza na turza cikin kowanne lungu na zuciyata wurin bin shawarar Yaya Aliyu ta ki amince min da hakan, wato in kwantar da kai in roki Fa’iz Allah-Annabi amma na kasa. Ya ya zan iya zub da mutuncina ga Fa’iz in nemi wani abu daga gare shi, ashe ma ya isa kenan! Never (fau-fau). Dole ne ma ya bani, in ba ta tsiya ba ta tashin hankalin da bai taba gani a rayuwarsa ba! Shima ya sani ko a lahira ba zamu yi makwabtaka ba balle zaman inuwa daya a duniya ko a lahira!!! Wai ta ya ya ma Fa’iz zai nemi aurena, kamar yadda Yaya Aliyu ke cewa? Ni fa Fa’izah da ya tsana? Ni kazama dakikiya ‘yar Maimuna? Uhm! Ko don yanzu na yi idon gani na zamo abar kwatance cikin mata? Da da nake a ‘yar’uwarsa kankanuwar yarinya mai rauni da bukatar kulawar yayyu irin sa me ya hana ya kauna ce ni? Ta ya ya yake tunanin ni Fa’izah zan mance kiyayyar da Fa’iz ya nuna mini tun ina ficiciyata har na kawo yanzu? Sanda yake aikowa su Ummi kayayyaki BAN DA NI. Ya tambayi lafiyar kowa BAN DA NI. Ya nuna banbaci kiri-kiri da fifiko tsakanina da sauran ‘yan’uwana...... Ya yabesu ni ya kushe ni..... ya zagi uwata a duk sanda ya so, ya dauko Ummi daga makaranta ni ya barni a jeji ko in mutu ko in yi rai ba damuwarshi ba ce. Ba don komai ba sai don saboda tsabagen tsana da kiyayya! Shin meye dalilin auren yanzu? Don na yi girma na yi kyau na zama kyakkyawa..... Don na yi kwakwalwar karatu wadda a da bani da ita..... Don na yi kyawun da duk cikin A.B babu kwatankwacina balle tsarana! Kaico da masu halin son zuciya irin Fa’iz Giwa. Wani da shan wahalar raino, ilmantarwa tare da real kauna ga Fa’izah shekara da shekaru bai samu ba sai shi. Wani da kwashe shekaru yana hidimtawa Fa’izah da inganta rayuwarta positively ba a bashi ba sai shi. Ga masoyi na gaskiya irin Dr. N mai wuyar samu a wannan lokacin, mai sadaukarwa so da kauna dukkan hakkokin da Allah ya ce a basu bai samu ba sai shi. Tabbas muddin na yarda na zauna da Fa’iz ko na saurari wata kalma daga gare shi ko da guda daya ce na tabbata wadda ba ta san ciwon kanta ba, ba ta san darajar kanta ba, ba ta san darajar wadda ta dauki cikinta wata tara ta haife ta shayar cikin wahala da kakani-kayi. Muddin ban auri Dr. N ba na cika butulu duba da tarin kauna da soyayyar da ya mallaka mani, na zama mayaudariya. Ya zama dole kenan in kaskantar da kaina ga Fa’izu ya warware igiyar da aka zarga a tsakaninmu? Juyawar da barin kaina yake yi ya tsananta cikin ‘yan dakiku, a yayin da zuciyata ta halarto min da cewa, rokon Fa’iz a bisa abin da bani da iko a kansa wannan dole ne! Kaskantar da kai ya zama dole gare ni, tunda durkusawa wada ba gajiyawa bane. Amma ba don ni ba illa don farin cikin Dr. Nazir Sani Galadanci. **** A washe garin ranar idanuwana na bisa kofa, yinin ranar zungur ban ko leko falo ba, illa kunnuwana da na kasa suna zuko min duk mai shigowa da mai fita a gidan Hajjah ko zan ji muryar Fa’izun? Shiru! Har yamma. Kafin in ji Aliyu na ce da Hajjah “Fa’iz ya je Kano dauko Yaya Bashir”. Hajja ta shigo dakin da nake kwance hannunta rike da kwano shake da gasasshen nama da ruwa-ruwan shi, an kuma barbade shi da yajin daddawa wanda ya ji kayan kamshin gargajiya mai dadi, ta zauna gefena a hankali da gani a darare take. Allah sarki Hajjah! Duk zagin da ta sha bai sa ta yi fushi dani ba don ina ji da safe tana gayawa bakinta ‘yan taya murna da suka zo mata daga Zaria, kada wanda ya shigo ya ta dani barci nake a barni na huta. Ita kanta ta fada fiyat! Kamar wadda ta tashi daga zazzabin kwana biyu. Ta ce, “Fa’izah ki yiwa Allah ki bude ido ki ci naman nan, na san kina jina ba barci kike ba, tun asuba nake aikin gasa miki don na san shi akdai za ki iya ci tunda kin ki cin komi tun jiya, shin baki tsoron irin ciwon Aliyu ne?” Na yi mata banza na kara cusa kaina cikin filo na bude sabon kuka. Hajjah ta yi zugum da kwano a cinya, daga bisani ta aje shi a kasa ta ce, “In kin kin cin abinci wanka fa Fa’izah? Rabonki da wanka yau kwana hudu. Shin Fa’izu ya san wainar da kike toyawa ma, in don shi kike yiwa kanki wannan ukubar?” Ban san sanda na zaro kai daga cikin filo ba na yi kutubal da shi na mike zauna, na ce, “Hajjah don na yi kyau, don na yi haske na daina kazanta na zama abin gani har a so ayi sha’awa Fa’iz ya ce miki yana son aure na ko? To daga yau duk wani abu da ya shafi gyaran jiki zuwa wanka na barshi har abada! Na koma Fa’izar da ya sanni a baya, kazama ‘yar Maimuna!!! In ce dai in na shiga warin hammata da warin baki ya ce baya so, ya je ya auro ‘yar Rasha ni kuma a barni da mai sona tsakani da Allah ba don wani abu da na mallaka ba....” Na ci gaba da kuka na gasken-gaske. Hajjah ta ce, “Ayya Fa’izah, kin yi kuskure babba, zato zunubi ko da ya kasance gaskiya. Daga ranar da Hafizi ya bar Najeriya bai kara ganinki ba ko a hoto sai ranar da ya dawo bayan an daura muku aure”. Da hanzari na tari numfashinta, “Tunda haka ne ki kwance auren mana ko dole ne? Na ji ko da ban auri Dr. Nazir ba na yarda na amince ki hada ni aure da Malam Hassan maigadin gidan Baban Kaduna, ko Isa direban gidan nann....” Hajjah kam ta koma yi min dariya, ta ce, “Yo ai shi kenan, wannan abu mai dan karen sauki. Sai ki je wurin Hafizin ki amso takarda ki kawowa Ahmadu da ya kulla auren ku, ni kuma na yarda ayi aure da Malam Hassan maigadi tunda ai mutumin kirki ne bawan Allah, ko ba jinina bane na san asalinsa da tushensa, na zauna da shi tun ba a haifeku ba, babu cuta ba cutarwa”. Ta mike ta fice ta bar kwanon naman a wurin yana ta turiri da kamshi. Na dade ina juya maganar Hajjah bayan fitar ta. Don me kowa na ce ya rabani aure da FA’IZU ABUBAKAR sai ya bude baki ya ce in amso takarda wurin sa? Bayan suna da masaniyar cewa ba zan taba iya rokon Fa’iz wani abu ba, ko kalma ta hadani da shi a kafatanin rayuwata? Ni na kai masa auren da zan je na karbo ba su suka kai ba? Don me su ba za su je su karbo ba in har da gaske suke suna son gyara kuskure da laifin da suka yi mini wanda ba zan iya taba yafe shi ba ko in amince da shi? Don me sai na karbo takardar aure zai warware ina ce in an maidawa Fa’iz sadakinshi shi kenan aure ya warware? Cikin kuka na fitar rai mai soya zuciya na ce da Hajjah, a lokacin da na mike na bita har uwar dakin barcinta tana shirin ta da sallar walha. “To ki bani sadakin mana ki gani in ban mayar mishi ba?” Tana kokawar sanya hijabin sallarta ta ce cikin alamun nuna gajiyawa da magana daya, “Shin ni Hadiza meye nawa ne cikin lamarin nan Fa’izah? Sadaki dai Barau ya karba, bayan daurin aure kuma ya dankawa ubanki na Zaria. Saboda haka su za ki je ki yiwa wannan tijarar da kike yi mini amma ni in kika sa min hawan jini Allah zai saka mini....” Ta soma kokarin fashewa da kuka. Na juya na fice da gudu na bar mata dakin tun Allah bai jeho wani cikin ‘ya’yanta ya aika dani lahira ba tare da na kara sanya N.S a idanuna ba. **** BIKI-BIDIRI Ga al’adar mutanen Giwa da yammacin Laraba ne muke kamu, washe gari alhamis kuma ayi budar kai. Don haka ban yi mamakin jin hargowar jama’armu ba daga ko ina cikin garin Giwa, Zaria, Kaduna da makotansu sun cika A.B Estate. Masu kidan kwarya sun soma wasa korai da gyaran murya cikin lasifaka, masu guda na yi, maroka na ma Hajjah kirari duk inda ta gifta. Na tabbatar dai al’amarin nan da nake dauka almara nema yake ya tabbata, za su hadani rayuwa da Ya Fa’iz ne ko babbaka su zan yi. Lallashin ma babu mai lokacin yi min shi, shima Yaya Aliyun tun ranar da yasa kafa ya bar gidan ban kara jin ko tashin muryarsa ba. Ummi da Zanirah babu wacce ta kara shiga sabgata, na kan ga dai Fa’iza ‘yar Zanirah ta rarrafo dakin da nake tana wasanta, ta yi ta gaji ta fita ko sanin da halittar dan Adam bana yi a dakin, domin ruhina da kulliyar tunanina baya wannan duniyar tamu, yana cikin wata duniya ta kunci, azaba da tafasar zuciya da zabalbalar kwallah. A yau na yi amanna da cewa, zan zama matar Fa’iz in na bari tsofaffin nan suka shafa min lalle. Na yi tunani iyaka tunani bani da mafita, bani da mai mara min baya, babu mai duban hujjata da idanun basira in dai a kan Fa’izu Abubakar ne. Wani yaro cikin ‘ya’ya da jikoki da suke matukar so duk da tarin aibobinsa. Don haka na yakewa kaina mafita ta karshe. Na janyo (travelling bag) dina na shiga shirya kayana da ba za suyi min wahalar dauka ba a gurguje. Adda Hanne kanwar Maman Kaduna da tawagarsu suka yane labule suka shigo da guda da sallama, duk suka cika dakin taf! Tsokanar duniya babu irin wacce basu yi min ba, in gadon dakin ya daga ido ya dube su to nima hakan. Kaya nake ninkewa daga sif ina dannawa a jaka. Adda Hannatu ta yi kwafa ta ce, “Ke ‘yar tawaye, mun zo kama ki ne kinyi kamar baki ganmu ba saboda kin isa”. A yayin da ta bincire hancin kwalbar turare “intimately beckham” suna ta raha suna darawa cike da unexpressable nishadi da farin ciki bayyananne a zuciyar su da fuskokinsu. Na dago jajayen kumburarrun idanuna na yi musu wani kallo a kaikace ta kasa-kasan ido a hankali na ce, “Ku kama uwarku dai”. A yayin da na sunto dankwalin kaina na yi damara a kugu gashina dake daure cikin (bound) ya sunce gaba daya ya cika fuskata da wuyana baki daya, ban damu ba, ban kula ba, jikina har tsuma yake ina jiran mai kwarin kashin da za ta fara matsowa gare ni. Adda Hannatu ta ce, “Eye! Dambe za ki yi damu Fa’izah! Lallai da aka ce kin haukace ashe ba ayi kuskure ba. To bismillah ma ga mai kwarin kashi tsakanin ni da ke”. Zaneerah cikin zafin cewa da na yi su kama uwarsu ta ce, “Eh, uwarmu zamu kama mana, tunda dai babban Yaya uba ne kamar yadda matar babban Yaya ta zama UWA...... wadda za ta cika mana gida da ‘ya’ya ta sauke tukunya ta dora mana abinci...... ta sa mana kula ta sabe mana babbar riga ta yiwa ‘ya’yanmu tarbiyyah irin ta gidanmu ba irin tata ta rashin neman albarkar iyaye da son gamawa da duniya lafiya ba.......” Daga haka suka shiga kwararo min turaruka ta ko’ina gaba da bayana har tsakar kaina zuwa yatsan kafata, har kuma cikin idanuna. Ashe dama kowaccensu da guzurin abinta cikin mayafi, ba Adda Hanne kadai ba. Azabar turare cikin kwayar idona ta rudani ta gigita ni na soma kara ina murza idanun da dukkan hannuwana, ina fadin “Idona.... idona..... wayyo Hajjah sun fasa min ido”. In sun fasa to ke da baki nan kin fasa karatun nan, sai dariyarsu suke. Kasa na sulale na kwanta ina birgima ina murzar ido dake neman tsiyayewa. Sai da suka kusa karar da kwalabensu kana na sha duka kitif-kitif-kitif daga hannun kowaccensu, wai ban yi wanka da kwalliyar tarbarsu ba sai zagin da na yi musu guzuri da shi. Kai wannan rana na ga wulakancin duniya da takaici da bakin ciki wanda ke kokarin fin karfin juriya da karfin halin da nake tinkaho da su. Nake amfani dasu ko yaya ne wajen ganin na kwato hakkina daga iyaye da dangina na A.B baki daya. Sai da idanuna suka lafa daga zugin da suke yi min na kuma tabbatar da basu tsiyaye din ba kamar yadda nake tsammani. Na shiga toilet dinmu wanda dama like yake da dakin barcinmu na wanko fuska da ruwan famfo mai sanyi, tuni zuwa lokacin an kece da kidan kwarya mai dadin amo da dadin sauraro. Wanda sautinsa ke amsa kuwwa cikin kwakwalwata yana zabalbalar min da ita. Ji nake shine amo mafi rashin dadin sauti da na taba ji a rayuwata tunda uwata ta haife ni. Mawakiyar waka take yi cikin lasifika tana kiran sunana tana hadawa da na Fa’izu Abubakar-Hafizin Hajjah, angon Fa’izah sanyin idaniyar Hajiya Hadiza Giwa..... Kin isar, kuma kin cika, baki taba gazawa ba uwar zuri’ar Abubakar Bamalli.... Allah ya ja kwananki ya kara miki lafiya ki ci gaba da kulle tsintsiyar Abubakar Bamalli. Takawarki lafiya uwar maza uwar Muntari, uwar Na’ibi uwa ga Ahmadu, uwar Ibrahim, Sani, Salisu da Sadi. Ki bani mota ki kaini Makkah Hajjah Giwar mata, Giwar mutanen Giwa..... Da gudu na fito daga bandakin ba don komi ba sai don tagarsa tana tsakar gidan dai-dai inda tsohuwar ke zaune tana wakar mai kama da banbadanci tana rawa daga zaune, saboda ba ta iya mikewa saboda kibar da ta yi mata katutu. Sai na ji kamar tana amfani da wakar tata ne da karin (tune) ko kuwa (melody) mai gaya min cikin tsakiyar kaina cewa, abin da Hajjah ta yi dai-dai ta yi, ina so ko bana so kuma ba zan taba yin nasara a kan A.B ba, sune suka riga suka yi a kaina. Wannan tunanin kamar anyi min wata irin allura mai kashe lakar jikin dan Adam ta karar da kuzarinsa, ta raba shi da BURIN sa da duk wani buri da ya ciwa rayuwarsa. Hawaye na malala ta kowacce mabubbuga ta idanuna yana kwarara a kan fuskata na tube kayan jikina dake kamshi na fita hankali ma zan ce ba na tashin hankali ba na canza wasu. Sai da na saurara na tabbatar su Adda Hanne da iyalanta su Zaneera da ‘yan kanzaginsu sun shige gidan Baba Na’ibi dukkaninsu don su kama Ummi, na sulale ta gareji ina jan trolley dina wadda ban cika da kayan da za su wahalar dani ba na bi ta baskwata inda babu ‘yan biki, mazan kuma duk basa nan, na bi ta hanyar da suke bi zuwa masallaci na fice daga gidan. Maigadin yana can yana baiwa tantabaru abinci. Tafiya nake bana ko waiwaye da wata irin sassarfa mai hade da gudu-gudu kamar zan tashi sama, bana ko ganin abin da yake gabana, ban kuma damu ba wai don mota ko babur sun buge ni ba, gara su buge nin in mutun in huta da nufin A.B a kaina. Don dai ba zan iya kashe kaina bane tunda na san abin da zan tarar idan na aikata hakan, babu mai kamasho ciki da za a raba bana mutuwar kafirici tare ni kadai zan dauki dakon abuna. Amma shiga ta duniya ba ni kadai zai yiwa illa ba, zai yi laga-laga ne da zuciyar duk wani da ya kwana ya tashi cikin zuri’ar Abubakar Bamalli, su rasa kwanciyar hankali da nutsuwarsu irin wanda na rasa tunda kowannensu cikin farin ciki yake da yankan kauna da kisan mummuken da suka yi mini, ni kadai ce cikin halin kaka-nikayi. Nema na su rasa alhalin sun san ba mutuwa na yi ba shine kadai kokari na karshe da zan iya, tunda kalmar fatar bakina da duk wani bore na ya gaza, abin dariya ne ma abin a zauna ayi ta dariya. Tunda su dai burin su ya cika, gara in mutu da su tausaya mani, su dubi al’amarina da zuciyar hankali da tunani. Da wannan tunane-tunane da zancen zuci da tafiya a kan hanya da kan titi bayan horn da zagi iri-iri da ga motoci da babura na bude ido na ganni cikin tashar motar garin Giwa. Ni da kaina na tabbatarwa kaina bani da wurin zuwa cikin danginmu kaf din su a karbe ni, in ka dauke gidan Baban Kaduna. Sai dai kuma ai abin da kunya da nauyi, gudun auren dansu nake yi da suka tsuguna suka haifa, kiyayyarsa ke neman kashe ni da raina. Kuma su zamo sune mafakata idan ina da kunya? Bugu da kari wanda ake bata kashin domin sa ba zai wuce can din ba, tunda baya Giwa wanda na rantse da in ga azzalumar fuskarsa na gwammace in yi arba da (arm robbers) cikin talatainin dare zai fiye min alheri da kwanciyar hankali fiye da sake arba da Fa’iz a sabuwar duniya da nake rayuwa bayan ta kuruciya ta shude da shi a ciki da duk wani al’amarinsa da na sani. Duk da na san babu jituwa ko kankanuwa tsakanin Hafizin Hajjah, Fa’izu Abubakar da iyayensa da suka haife shi, Baba Muntari da Maman Kaduna, wani sako na kololu zuciya da kwakwalwata ya tuna mini da cewa DA har gobe sunansa DA a zuciyar iyayensa, ko da kuwa Hitler ne mai daukan rayukan al’umma babu dalili. Da wannan tunanin sai na fada motar garin Zaria, wadda za ta kai ni har ABU in har DA shine DA a zuciyar iyayensa komin muninsa ko munin halinsa da munin ayyukansa, to kar in nemi gidan Baban Kaduna gara in koma ga tawa uwar wadda bana baiwa muhimmanci cikin rayuwata da hujjata ta banza mai cewa, ita ma ba ta bani kulawar da Allah ya ce ta bani. Na tabbata idan duk duniya ta taru ta ki ni ta juya min baya a lokacin da bani da kowa, bani da gata, uwar da ta haife ni ko ba za ta kulani ba, ba za ta kore ni ba. Wadda ta sunkuya ta kawo ni duniya Fa’izun ke kamo sunanta yana zagi a duk lokacin da ya so, a dalilin ta haife ni kuma bare ce ba ta hada jini da iyayensa ba. Bayan wannan ba ta yi masa laifin komai ba. Babban abin da ke damuna a wannan duniyar hujjar Fa’iz ta aure na? Har ya iya bude baki ya furta hakan bai ji kunyar kowa nawa ba? Duk da ba a auren na gani ina so cikin zuri’armu shi ya furta kuma an ba shi saboda fifikon da yake da shi a zuciyar Hajjah! Ko da zan mutu, zan so kafin isowarta (mutuwar) in samu amsar wannan tambayar, mene ne dalilin Fa’iz na aure na? Tunda na amince an halicce shi ne da kiyayyata ya girma ya rayu cikinta, ya bar kasar Nigeria cikin rainonta (kiyayyar), ya kuma yi gammon abarsa ya tafi da ita Rasha, ya kare shekarun da ya yi baya gida cikin soyayya da Ummi..... da kiyayya gare ni. Na ce, kyawun da na yi ne wanda a da bani da shi, da tsabtar da na yi a yanzu wadda yake goranta min bani da ita a baya, yake kyara da hantara da wulakanta ni a kanta, su suka sa ya zo yanzu ya ce zai aure nin. Hajjah ta ce ba su bane, ta kuma kafa hujjar ta da cewa, tunda Fa’iz ya tafi har ya dawo tsayin shekarun nan ko hotona bai taba gani ba, balle ya ga canzawar da ni nake ikirari. To mene ne? Mene ne hujjarsa? Yana nufin alkhairi gare ni? Yana yi min tanadin alkhairi? Yana nufina da alheri da wannan auren ko ko ya yi shi ne don karasa cimma mummunar manufarsa a kaina ta ganin ya raba ni da duk wani farin cikin rayuwata? Na wulakanta na tozarta na tagayyara a rayuwa? Ina ruwan Fa’iz da duniya ta da burinsa kawai ya raba ni da jin dadina dake cikinta? Tunaninnikan da nake ta yi kenan suna ci gaba da soya min zuciya, fuskata jage-jage da hawaye, domin iyaka tsinkaye da dan tunanin da Allah ya hore mini sun kasa bani amsar tambayoyina ko da guda daya daga ciki, har mai tasin da nake ciki ya hau kan titi dodar ya kama hanyar Zaria. Mu karasa a A littafi na 3 Takorin ku ce. [16/02 12:52 PM] Sumayya Takori: ZUMUNTAR KENAN?-3 Mai taxin ya gaji da gaya min gamu cikin Zaria, ina zamu dosa? Na zama kamar mutum-mutuma, kurma, makauniya don tunani, saida ya bubbuga kujerar danake zaune nace masa gida mai lamba tamanin cikin gidajen malamai na jami'ar Ahmadu Bello. Gidan da ya zamto mahaifata, dandalin quruciyar rarrafe da tata-ta ta, kafin in gujeshi zuwa inda nake ganin ya fishi farin ciki da walwala, a yau gani na dawo da qafafuna, na kuma gwammace in qarashe sauran rayuwata cikinsa ko da ace yafi kurkuku rashin Dadi da taqaita farin ciki. Wata irin doguwar ajiyar zuciya na saki, na ciro kudin da suka rage min kaf ko qirgawa banyi ba na baiwa mai tasi, ya fitar min da jakata daga bayan motar sa, ya yi min godiya mai yawa ya ja motarsa ya bar harabar wajen. Zan iya kimanta lokacin da qarfe takwas na dare sanda nake tsaye qofar gidanmu, domin ina iya hangen tanqareren agogon falonmu wanda hasken qwan lantarki ya wadata, kuma an dage labulen wawakekiyar tagar falon. Rashin motar Baba ya tabbatar mini bai shigo cikin gida ba, ya shiga cikin (city) kamar yadda ya saba duk bayan sallar isha'i. Don haka naji dan sanyi da qwarin gwiwar cira qafa da tura jakata. Sai dai a take wani irin tsoro da shakka suka lulluve ni, idan Momi ta yarda ta qyaleni in zauna Baban ABU zai qyaleni ne bai gayawa iyaye da 'yan uwansa ba? Kuma wane mataki zai dauka a kaina tunda ga dukkan alamu bai dauki al'amarin nan da sauqi ba? Hakan dai nayi shahadar quda da yin qarfin halin danna qararrawar qofar shiga falon (door-bell), sai da na danna sau uku kafin a buxe. Walida ce, zata yi magana nayi hanzarin kai hannu na rufe bakinta, muryata na rawa na ce. "Ki rufa min asiri Walida, shin Baba na gida?" Ta girgiza kai. "Momi fa?" Ta nuna min (kitchen). Na ce, "To don Allah Walida kar ki gayawa kowa ina cikin gidan nan, zan zauna xakin Abdallah, ai yana makarantar kwana ko?" Ta gyada kai tare da leqawa ciki ta tabbatar momi firar doya take, tayi min alamar in shiga. A hankali ta murda qofar dakin Abdallah na shige wanda ke daga can gefen tafkeken falon, ta mayar ta rufe kenan Momi ta qwala mata kira. "Walidaa!". Ta ruga a guje tana faxin. "Yes Momi". Momi ta ce, "Ke da wane a waje ku ke magana?" Ta dan diririce na rashin sabo da yin qarya, kafin ta ce. "Joseph ne yake neman Cinyere na ce bata zo ba". Ba tare da ta juyo ta dubeta ba ta ce. "Ga abincin ku can kan leda ki ta da Walid ku ci, ya yi bacci ko?" Ta ce, "Kai Momi, ki qyale shi ya fa sha kunun tsamiya mai yawa kafin ya yi baccin". Ta juya don ta kira Kausar ta tarar tayi bacci akan litattafanta itama, ta gayawa Momi kana ta dauki plate din ta bude qofar a hankali ta shigo. Nayi tagumi ne a gefen gadon Abdallah na zubawa kayana ido, da 'yar muryarta mai sanyi ta ce. "Yaya Fa'izah". Tare da zama a kusa dani, ta dora hannunta bisa cinyoyina. "Wai shin me ke faruwa ne? Duk akan auren ki da Ya Fa'iz ne?" Na share hawayen da suka cika mini ido, na ce. "Shin Walida kin mance sanda Fa'iz ke azabtar dani ne? Sharri kala-kala da azabobi iri-iri wanne ne Fa'iz bai min ba, bai kuma gana min ba? Qiyayyar duniya wacce iri ce Fa'iz bai min ba? Amma ki ga don zalinci ya zo ya kalallame Hajja da su Baba suka xaura mana aure...". Wasu azababbun hawaye suka mirgino akan kundukukina. "Don haka ni kam Walida anan zan ci gaba da voyewa har zuwa sanda suka gaji da nemana suka warware auren nan, ko kuma su kai gawata idan baqin ciki ya qarasa ni, da dai in zauna ayi bikin nan jibi...". Na ci gaba da share hawaye ina fyace majinar dake ambaliya daga hanci na. Walida tayi zuru tana kallona. Da alamun tayi nisa a tunani. Ni na san Walida yarinya ce mai kaifin basira duk da kasancewarta mai qarancin shekaru, kwata-kwata bana ji ta cika shekaru goma sha huxu. Wala'Allah abinda take saqawa ya zam mai amfani a gareni. Ta ce, "Yaya Fa'izah, ban zauna a Giwa ba ko kaxan balle in san halin Ya Fa'iz a da can, ko rayuwar da ku ka yi tare, bana ma kuma marmarin zaman, sai dai nakan ji ana labarin a cikin 'yan uwa ko in munje gidan Baban Kaduna ko yaro ne ya takurawa xaya sai kiji manya na faxin, "Kada ku zama Fa'iz da Fa'izah mana, kuyi riqo da ZUMUNTAR ku". Sai dai wallahi a yadda Baba ke son auren nan naku ya kuma dage ya tsaya wajen ganin wanzuwar sa na rantse duk inda ki ke sai ya nemo ki, balle cikin gidansa. Ni kam banga abin ta da hankali da qin Ya Fa'iz ba, da kin xora idonki bisan Pilot Fa'iz Giwa a akwatin talabijin sanda aka nuno shi a tashar CNN, ranar da wani jirgi ya faxi a Mozambique da kinyi alfahari da kasancewar shi miji a gare ki. Wanda ba isarki ko cancantar ki ce ta baki shi ba, face darajar Zumuncin da kasancewar ku JINI XAYA. Miji ne na liqawa a goshi, kuma abin tinqahon kowacce xiya macen da ta san ciwon kanta. Da kinyi nadamar wannan azabtar da kankin da tada haqarqarin da kike yi kan wai ba kya son sa. Ko kin san Ya Fa'iz na yanzu bai yi kama da Fa'izun gidan Baban Kaduna ba na da can da kika sani a baya? Wallahi in banda Fa'iz ke son ki, da na ce yafi qarfinki a halin yanzu kam! Umm!! Ni dai ina baki shawarar ki haqura ki fauwalawa Allah al'amarinsa da yinsa, kada ki zamo mai shisshigi cikin iyakar Ubangiji, wato yarda da qaddara mai daxi ko mara daxi. Wallahi Yaya Fa'izah ni shaqiqiyar ki ce, don haka ba fata nake miki ba, muddin yaya Fa'iz ya barki ba za ki samu ko da wanda ya kama qafarsa ba...". "Ni kam na shiga uku!!!". Abinda na faxi kenan a fili kamar in xora hannuwa aka in fasa kururuwa. Me yasa kowa ba ya ganin hujjata da qima, girma da muhimmanci? Me yasa kowa ke son Fa'iz? Me yasa kowa ya buxe baki yabon Fa'iz yake yi? Sun manta cewa maqiyinka baya tava dawowa ya zama masoyinka? Wanda ya ce bai son ka jiya, gobe ya ce yana sonka to tabbata wani abin ya hango. Na dubi Walida cikin matsanancin vacin rai a ido da zuciyata, na ce. "Yau na amince kina daga cikin maqiyana Walida! Kin nuna min ba ki qaunata Fa'iz kike so kamar sauran dangi, kema kina cikin sahun su Ummi, Hajja da Zaneera... Yaya Aliyu kaxai ke sona har gobe cikin A.B, kin kuma nuna min kema......". "...Walidaaa!". Momi ke qwala kira. Walida ta miqe a razane, a kixime muryarta na rawa ta ce. "Wallahi-wallahi daga yau ina bayanki Yaya Fa'iza... tunda har baki son Yaya Fa'iz har haka, nima daga yau na tsane shi... na tsane shi!!!". Wani irin murmushin qaunar 'yar uwata ya suvuce a fuskata irin wanda ke fitowa tun daga qarqashin zuciya, itama murmushin tayi mini. "Daure ki ci abinci Ya Fa'iza, zan ke kawo miki abinci ko yaushe. Don Allah ki daina kuka. In kinga ban shigo ba to ina makaranta ne boko ko Islamiyya. (Toilet) xin Abdallah a buxe yake, kuma famfo yana zuwa". Ta fice da sauri ta ja qofar ta tadda Momi, ina jiyo Momi na faxin. "Me kike a xakin Abdallah tun xazu ina ta kira?" Ta ce, "Momi littafina da ya ara nake nema "An African Night Entertaiment" nake jin ma ya tafi da shi". Shigowar Baba ya katse su. Na xauki kwanon abincin da Walida ta kawo mini nayi loma guda na sakwara da miyar Ugu. Tamkar nayi loma da curarren maxaci duk da zaqin nama da na mai tauraro da miyar tayi cau. Yadda zuciyata take baqiqqirin haka bakina yake xaci xau. Na runtse ido na a hankali na kishingixa bisa gadon Abdallah tare da jan bargo har kaina, sakamakon wani irin sanyi da naji yana ratsa qasusuwana, yana son shiga har cikin bargo na alamar shigar zazzavi. Zuciyata na wani irin tuquqi, maqaqi da azalzalar baqin-cikin da ba zan iya kwatantawa ba. ***** A GIWA Acan Gida babu wanda ya farga da rashina a gidan har garin Allah Ya waye, duk jama'ar gidan baqi da 'yan gidan kowa harkar gabansa yake yi, ana ta shirye-shirye. Musamman kasancewar ranar ta Alhamis a matsayin ranar buxar kai. Aliyu ne ya shigo falon Hajjah tare da xan uwanshi kuma babban abokinshi, wato Muftahun Yaya Rabi da ya zo a lokacin don su gaisa da Hajja, isowar shi Giwa kenan. A babban falon dake shaqe da A.B family maza da mata, Muftahu ya zo ne da labarin rasuwar Dr. Nazir Sani Galadanci, manemin auren Fa'izah. In banda Salati babu abinda Yaya Aliyu keyi yana mai qara jinjina wannan mummunan labarin, tare da qara tsinkewa da al'amarin Ubangiji. Muftahu ya nemi ganina don yi min bayani, Ummi dake kokawa mutuwar Naziru haiqan har kamar ta shixe ta yarfe hawaye da majina, ta ce. "A wannan halin da Fa'iza ke ciki ne zaka ba ta labarin rasuwar Dr. Nazir Yaya Muftahu? Ka rufawa kanka asiri, idan Fa'izah bata ce kai ka kashe mata Nazir ba, la-shakka zata ce haxa baki ku kayi aka kashe Naziru don ta yarda da auren Ya Fa'iz". Muftahu ya ce, " amman dole ne ta ji?" Ummi ta ce, "Ji kam ya zama dole ko ba jima ko ba daxe, amma ba yanzu ba, kuma ba daga bakin kowa ba sai na wanda zai iya ma haukar Fa'izah tamkar Yaya Aliyu ko Ya Rabi, amma ba kai ba". Da sauri Aliyu Na'ibi ya ce, "Wallahi babu ruwana, ba a bakina ba nima, indai har ka dage sai ka faxan Muftahu ga hanya, tana uwar xakinsu tana neman kashe kanta don bala'i da qin auren Fa'iz ko falo ba ta fitowa". Muftahu ya ce, "Bari inje, inji dai ba zata bugeni ko ta zage ni ba?" Suka ce a tare, "Uhm!". Hajja ta ce, "Muftahu ka qyale Fa'izah don Allah, shin Fa'izar da ta rufe ido ta zageni tas kan Naziru kai waye da bazata zage ka ba, zaka je mata da labarin mutuwar Nazirun?" Muftahu bai tsaya ba a yayin da ya danna kanshi a xakin bakinsa xauke da qatuwar sallama. Ya yi dube-dubenshi ya fito, ya ce. "Au, ai ma bata nan". Ummi ta ce, "Ko dai ta shiga bayan gida?" Ya ce, "Ga bayan gidan nan a hangame, ai babu kowa a ciki". Ta ce, "Duba sosai dai can qarshen gado ko ta naxe cikin bargo". Muftahu ya yi dube-dubensa har da duba qasan gado ya kuma haxa da kira. "'Yar Zaria a Kano!!!". Shiru ta ziyarce su, sai ma amsa kuwwar muryarsa da ta dawo cikin kunnensa. Ya ce, "To wataqila dai idona ne, Aliyu zo ka duba". Baki xayansu suka miqe suka shiga xakin inda Fa'izah ta ce xaukar ni inda ku ka ajeni. Zaneera sai da ta qara shiga (toilet) ta duba bayan qyaure da cikin baho, ta ce. "Kai! Tikisa!! Da qyar fa idan Fa'izah na cikin xakin nan". Leqa nan leqa can cikin A. B Estate baki xaya babu Fa'izah. Hajja ta tuna kalaman Fa'izah. "Daga yau ba za ki sake ganina cikin gidanki ba balle ki yi iko da ni...". Hajja ta fashe da kuka tana faxin. "Ni Dijah na shiga uku, wace irin zuciya ke da yarinyar nan wadda babu ahuwa da rangwame a cikinta? Tabbas Fa'izah ta gudu ne, ba ta gidan nan, ba ta garin nan". Zaneerah ta ce, "Ina! Babu inda Fa'izah za ta iya zuwa da ya wuce Kaduna, Kano ko Zaria. Bayan waxannan wurare na tabbata Fa'izah ba zata yawon banza ba, kuma ba zata kai kanta mahalaka ba duk rintsi duk kuwa abinda ke damunta". Aliyu ya zaro waya daga aljihunshi, haka Muftahu. Muftahu Aunty Rabi ya kira, ya ce. "Maman Abdul 'yarki wurin ki ta iso ko?" Ta ce, "Wacce 'yar tawa Mufty? Kasan 'ya'yan nawa yawa ne da su". "'Yar rigima mana matar Fa'izu!". Da fari Rabi kam dafe qirji tayi kafin ta ce. "Ni Rabi'atu, rabona da Fa'izah tun ranar da suka haura qafa suka bar Kano, amma gani nan tafe. Nima shirin kayana nake yi yanzu haka". A sanyaye Muftahu ya zura wayarsa a aljihun gaban rigarshi, ya ce. "Fa'iza ba ta Kano fa". Zanira ta fashe da kuka, "Ni kam wannan aure dole ne? Me ya yi zafi ne haka da ba za a haqura ba? Wallahi ni nasan Fa'izah da kafiya da taurin zuciya, tunda ta ce bata auren nan wallahi bata yi xin ne, babu wanda ya isa ya tanqwasa ta". Cikin alhini Aliyu ya ce, "Haka Fa'iz Giwa, tunda ya ce bai sakin auren Fa'izah yanzu ya saka xamba a aurenta, na tabbata ko duniya zata taru akansa ba zai saketa ba, sai dai mutuwa ta raba su A wannan gava ni na saduda Hajjah, dabarata da tunanina sun qare wajen tanqwasa Fa'izah tunda har anzo gejin da Fa'izah ta soma zartarwa rayuwarta hukunci ba tare da shawara dani ba, ya tabbata cewa nima ta sanya ni a rukunin sikelin da ta xora kowa. Sai ki yanke hukunci na qarshe, in har bata Kaduna ko Zaria". Yana faxi yana kiran Maman Kaduna. Ita xin ce ta xaga suka gaisa cikin matsananciyar girmamawa ta 'ya'yan A.B ga iyayensu maza da mata, Aliyu nauyin Mama ya dabaibaye shi, shin yaya zai yi ya tambayeta yarinyar da ta bar gida domin qiyayyar xanta? Jikinshi na bashi yaqinin ba yadda za ayi Fa'izah taje Kaduna, shin giyar wake ta sha ma? Ya yi ta maza jin shiru ta ratsa a tsakaninsu, ya ce. "Shin Mama ina Pilot ne?" Ta ce, "Yana vangarensa yana shirya kayansa, wai shirye-shiryen tafiya yake yi jibi can Russia, anyi masa kiran gaggawa kan wani muhimmin aiki. Yaya Fa'izar? Ince ko ta ware?" Gaban Aliyu ya bada damm! cikinsa ya ba da sauti, ya ce. "Don Allah Mama yi min magana da shi yanzun nan ko Yaya Bashir". Mama ta ce, "Na ce lafiya dai? Bashir yana kan hanyar tahowa na san ma ya kusa isowa yanzun, ka gaya mini mene ne? Me ya faru Aliyu?" Tausayin Mama ya kama Aliyu, daga jin muryarta kasan ta daxe bata cikin nutsuwa da kwanciyar hankali duk akan Fa’iza. Aliyu ya rasa yadda zai yi don ta wuce ya yi mata qarya, ya ce. "Wallahi Mama Fa'izah ce bata kwana gidan ba, gamu nan a Giwa kowa hankalinsa a tashe". Mama tayi murmushi mai fitar da sauti, ta ce. "Ina da kyakkyawan zato da shaida akan xiyata, ba zata iya wuce Zaria zuwa Kano ba duk nisan da zata yi". Ya ce, "Wallahi bata Kano, yanzu Ya Rabi ke faxa". Mama ta ce, "Ka jarraba Zaria mana. Yanzu kam bai kamata mu faxawa Fa'izu ba tunda Zariyan yake shirin zuwa gaida Maimuna wataqila ya tadda ta can". Aliyu ya sake neman gidan baban ABU, momi ce ta xauka suka gaisa tana tambayar Little F. Aliyu kam duk gaisuwar ta gundire shi, ya ce. "Shin momin Walida, please Fa'izah Zaria ta kwana?" Da farko Momi Maimunatu shiru tayi sakamakon mugun faxuwar gaban da ya dirar mata. Ta samu ta haxa sauti wanda zai ba da ma'ana, ta ce. "Ko da zancen nan bai shafeni ba Aliyu da Fa'izah ta zo gidan nan da tuni na sanar daku ko don gudun tashin hankalin ku. Rabona da ganinta tun zuwansu daga Kano da suka zo suka kwana biyu nan ita da Ummi". Aliyu ya ce, "Ya Salam!!". Tare da tura wayarsa a aljihun baqin wandon (jeans) mai matuqar qwari dake jikinsa. Ummi ke tambayar, "Bata je ba ko?" Sai kuka, kazalika sauran 'yan uwa da 'yan buxar kai da suka ci kwalliya kyawu na bugun kyawu, duk hawaye ya vata kyakkyawar fuskar Bamallin su. Muftahu kam girgiza kai yake. Ali Na'ibi, ya jingina da bango, yayin da maganganun da suka yi da Fa'iza ke nausar kunnensa tamkar a lokacin ne take yi. "...ko yankani za kuyi A.B bani auren nan... na gwammace in bi YAWON DANDI... da dai in qarashe rayuwata a matsayin matar FA'EEZ BAMALLI!!!". Aliyu ya kama kai, ya ce, "Kash! Kinyi kuskure babba Fa'izah, ko masu yawon dandin basu da aure akansu, kada kiyi kuskuren da ba zaki iya gyarawa ba mana...". Ya fisgi hannun Miftahu suka yi waje inda ya xauki motarshi aguje suka bar garin Giwa. Allah Sarki Aliyu xan uwa na gaskiya, gidan karuwai ya riqa bi kala-kala da Miftahu wai yana neman Fa'izah, yana mai suffanta musu ita tare da nuna hoton ta. Amma babu wanda ya ce ya ga gilmawar ko mai kama da Fa'izah, amma babu alamar gazawa a tare da shi. Miftahu kam ko fitowa daga mota bai yi ba, tausayin Aliyu kaxai ya ishe shi. Haka ya zage gidajen karuwan garin Kaduna da Zaria kaf yana cigiyar Fa'izah har duhun dare ya shigo, ya ba da cigiya a ofishin 'yan sanda da kafafen yaxa labarai masu yawa. Ya ja birki dai-dai titin Sir Kashim, ya xaga waya ya kira Fa'iz Giwa, a fusace Aliyu ya ce. "Ka ji daxi ko xan gata! To tunda baka fasa auren nan ta ruwan sanyi ba, zaka fasa in an kawo maka gawarta. A yanzu Fa'izah kwata-kwata bata a Kano, Giwa, Zaria ko Kaduna, sai ka san inda zaka nemo ta". Bai bashi damar yin magana ba ya kashe wayarsa, shi kuma bai kira shi ba. **** [17/02 5:24 PM] Sumayya Takori: Fa'eez da ya tafi dauko Yaya Bashir a Airport a washegari wanda ya sauka ta Kano, qarfe hudu na yamma suna kan hanyar Kaduna daga Kanon. Bashir ya yi kwance a bayan (Henessy) yana kwarara hamma, yayin da Fa'ez ke ta tuqi kamar Allah Ya aiko shi ba mai magana da dan uwansa cikinsu. Tun can Fa'iz da yayanshi Bashir ba sa ga maciji. Bashir ya fiddo taba ya cinna mata (lighter) wadda aka yi da qarfen azurfa ya soma fesar da hayaqi. Sanye yake cikin (Italian suit) baqaqe, da gani kaga baqon Russia cikakken Injiniya a vangaren wutar lantarki Eng. Bashir Mukhtar Abubakar. Fa'iz ya yi maza ya toshe hanci da hannunshi, yayin da ya rage gudun motar ya sauka bakin kwalta ya kashe motar gaba xaya, ya fito ya mai da qofar ya rufe ya zauna a saman bannet xin motar. Tunanin halin da ya baro Fa'izah a asibiti jiya yake yi, wata zuciyar na ce da shi kawai in ta farfaxo ya haqura ya saketa. To amma abin tambayar anan shi ne, idan ya biye ta zuciyar ya saketa yaya zai yi da soyayyar da ta zamo masa qaqa-nikayi? Shekaru dai-dai har goma sha... yaya zai yi ya dinke zumuncin iyalin Abubakar Giwa da ya yiwa givi saboda wauta da quruciya? Yaya zai yi ya xinke varakar da ya wanzar a A.B House? idan ya saketa tayi nasara kenan akansa wannan karon? (She's always a loser on him and so she will remain till eternity.... Wata rana na zuwa insha Alla da Fa'iza zata san babu mai sonta duk duniya kamar shi da ta riqa maqiyin da babu ya shi a duniya. Shi kam ya tabbata alhakin mahaifiyarta ne da nata Allah Yake hukunta shi da shi ta hanyar xora mashi azabar SOYAYYAH... soyayyar kuma ba ta kowa ba ta Fa'iza Ahmad Abubakar Giwa. Wata yarinya da ya addaba, ya kyara, ya hantara babu gaira babu dalili sai a dalilin KABILA NCI, wauta da quruciya. "To in ka qi sakinta ta mutu fa a dalilin qiyayyar ka?" Wannan kam bai san makomar shi ba a wurin Ubangiji. Bai tava faxawa a soyayya ba, bai tava son mace ba a kafatanin rayuwarsa, mata kala-kala kuma iri-iri ya gani a rayuwarsa musamman abokan aiki da ke qarqashinsa da ake kira 'yan matan jirgi (Caterers) na qasashe daban-daban, musamman yankin Asia inda yafi yiwa jigila da suke binshi da tayin soyayya ta banza ko ta aure, amma tunanin kucakar qanwar nan da ya baro a qauyen Giwa, ya dishe hasken duk wata diya mace daga qwayar idanunsa. Har zuwa tahowarsa yanzun, bai manta da Alicia ba, wata (caterer) dake aikinsa shi kaxai ransa, da zai iya cewa ya tava kulawa da soyayya a dalilin abotarshi da Yayanta pilot Johari, mutanen Berlin ne. Da qyar ya samu ya taho gida shi kadai a dalilin kafewa da tayi sai ta biyo shi Nigeria sunyi aure a garin nasu Giwa, iyayenshi su Musuluntar da ita. Alaqar shi da Johari, ta faro ne tun daga karatu a (Ukranian Institute of Aviation) wanda shi yazo karantar tuqin jirgi Rasha daga Berlin ne, shi ne kuma ya samar mishi aikin da yake yi yanzun da kamfanin tashin jirage na mahaifarsa (Berlin Airlines) aka xauke su take, abinda ya hana shi dawowa gida kenan bayan kammala karatunsa. Don haka zai iya cewa idon Johari ne yasa yake kasa (ignoring) Alicia har kowa dake tare da su ya xauka soyayya yake yi da ita. Shi kuma yana biye mata ne don Johari yafi qarfin komai a wajensa in yana da iko. To sai dai mutum bashi da iko da ZUCIYA, barta akan abinda take so, komin munin shi da wahalar samunshi. Abubuwa da yawa sun faru wadanda zai ce su ne silar soyayyar da yake yiwa Fa'iza ko ba sune ba. Muhimmi a cikinsu shi ne, bayan SO na haqiqa akwai son ya gyara wannan qasaitaccen zumuncin na A.B family da yasa almakashi mai kaifi ya farka ya zama wound wato (gyambo) a zuciyar FA'IZAH AHMAD ABUBAKAR, yana so ya warkar da wannan gyambon ne da SOYAYYAH. Ko da zai rabu da Fa'izah zai rabu da ita ne (only) in ya yi nasarar warkar da wannan gyambon da shi ne silar samuwarsa a zuciyarta, wadda itama bata da ikon sarrafata, domin SO da QIYAYYA duka halittar Allah ne da basu tava zama wuri guda. Wani sashe na zuciyar Fa'iz Giwa ya ce. "Shin me Fa'iza take taqama da shi ne haka da yasa ta ci galaba mai yawa haka a kansa, in ba don sharrin SO ba? In ba don son ta ba da ya sameshi rana xaya baiga abinda ma zai sa shi yin aure a halin yanzu ba, bai shirya masa ba (at all) yana cin kuruciyarsa ne. In ba don so da ba ya shawara ba, bai ga dalilin da zai sa ya baro aikinshi wanda kullum ranar Allah samu ne mai xumbin yawa a gareshi, ya zauna yana ganin baqin ciki ba. Ko ma me zata yi tayi ta gama, however, yana son matarsa, saki a tsakaninsu yana ganin wataqila shi ne abu na qarshe da ba zai tava yi ba a rayuwarsa, sai in mai yanke hanzari ce ta cika umarnin Ubangijinta (mutuwa). Mutuwar tashi ma, zai so ace daga hannun Fa'iza ce ba don Allah baya yafe haqqin rai ba, a ganinsa in tayi hakan wataqila gyambon zuciyarta zaya warke. Tunani na qarshe da ya ziyarce shi, shi ne ta gama suman, qafarshi qafarta, kwas xin nan da zai tafi Amsterdam sati uku masu zuwa, tayi ta suman tana farfaxowa yana da ruwan da zai yi ta yayyafa mata, indai ba mutuwa zata yi ba Falillahil-hamdu. Bai kai qarshen tunaninsa ba Bashir ya bude murfin motar da qarfi, ji kake butt! Ya fito yana fadin. "Kai, don ubanka ance ma ni bawan gidanku ne da za ka tsaida ni a gefen titi zafin rana na duka na?" Fa'iz ya yi tsaki ya ce, "Kada ka sake zagar min uba Yaya Bash! Ta yaya zaka kunna min hayaqi cikin mota in zauna ina shaqa, na tayaka sha kenan? Iyaye kuma tunda ba ka ganin darajar su ni ina son kayana, kada ka sake ka sake zaginsu a gabana, na rantse ba zai yi maka dadi ba". Bashir ya dubi Fa'iz sosai yana cikin wani irin yanayi na tashin hankali da bai tava ganinsa ciki ba, har wata rama ya yi, kafin ya baro Russia ba haka ya sanshi ba sam. Jikin Bashir ya yi sanyi, ya koma mota ya zauna ba tare da ya yi magana ba sai da Fa'iz ya mula, ya kammala shan qamshinsa da harare-hararensa kana ya ja motar aguje tare da sakin qira'ar Abdurrahman-Sudaith a rediyon motar cikin Suratul Nisa'i. Wannan ya taimaka wajen sanyaya zuciyarshi dake tafarfasa babu gaira babu dalili. Bashir dai binsa yake da ido, da zuciya, ya kasa shiru, bayan sun jima suna tafiya yana kallon Fa'izun wanda idanunshi suka kaxa suka yi jawur. "Wai kai me ke damunka ne?" Fa'iz ya harare shi ta cikin madubi, "Ai ni babu abinda ke damuna face tawa matar da ta tsane ni tamkar mutuwarta, duk da bani da wani hali abin qi, baya ga shirmen quruciya na can baya, wanda da ace zata saurare ni ta saurari kalaman dake qunshe cikin baki da zuciyata da ta fahimce ni, kai kuwa ke da damuwa. Baya ga baqin munanan xabi'un da kayo guzuri, shan giya, taba da bin matan bariki tamkar tsohon bunsuru, kai da wai an kaika ne domin ka zama ubana, mai dorani bisa hanya sahihiya, ka rikide ka zamo tantiri, wacce irin qiyayya ce ba zaka gani daga taka matar kamila Hadizatu ba?" Bashir ya tashi zaune daga kishingidar da ya yi a kujerar baya tare da wurgi da abinda ke hannunsa ta taga gaba daya, ya antayo ashariya cikin harshen (Ukrain) wadda Fa'izun a duk zamansa a Russia shekaru goma vai tava jin wani ya yi ba, haka ya lailayota da turanci wadda Fa'izun bai san akwai ba ma, sannan ya shimfidota da Hausa ji kake. "Abu kazan uban nan! Uban waye ya xaura min auren? Sharrin da zaka je kayi min a gida kenan Fa’iz? Wato dama ido ka sa min a duk motsina ko me? Duk tambadar da kake yi da Alicia na tava daga ido na dube ka da zaka ce ina neman mata? Ai dama gwano baya jin warin jikinsa...". Fa'iz ya yi saurin miqa hannu ya kashe qira'ar da ya kunna na karatun Alqur'anin dake tashi, ya juyo ga Bashir bayan ya kashe motar baki dayanta. Ya yi rantsuwa da Allah ya sake rantsewa ya ce. "Wallahi-wallahi ka sake zagar min iyaye sai na sauke ka a dajin nan yaya Basheer!". Basheer ya dubi qwayar idon Fa'iz sosai har wani blue-blue take, jijiyoyin kansa sun tashi rada-rada saboda fushi da mazantaka, ya ce a ransa. "Anya Fa'iz qanina ne?" Fa'iz qato ne qwarai murzajje mai wasu irin qarfafan damatsa da ginannen jiki na Bamallin usli tamkar (Late) Abubakar Giwa a sanda yake nashi tashen quruciyar, yana nome manyan gonakinsa da hannunsa ba tare da ya nemi mai tayashi ba. Irin mazan da jarumtakar su ce kadai tasa duka rabin rayuwar su cikin iska suke yinta, ruwa, hazo, zafin rana, sanyi ko duhun dare baya hana su lulawa cikin sararin samaniyar Subhana. Wanda duk ya yi qoqarin dambe da su, mace ko namiji labudda uwarshi ta haifi wani kawai amma ba shi ba. Savanin shi Basheer da (gulder), hayaqi da zina da ya jefa kanshi a Russia rana daya suka haxu suka tsotse masa jiki da kuzarinsa. Sai dan banzan bakin tsiya da kaudi wanda ba a kashe shi a magana. Inda suka bambanta da Fa'iz kenan, wanda kafin ya yi qwaqqwarar magana ma aiki ne jawur, sai lokacin da ya sa kansa. Bashir ya ja bakin (glass) ya mannawa idanunsa, ya koma yadda yake da, wato kishingida, yana ta huci shi kadai kamar kumurci, bai qara magana ba. Fa'iz ya ja motar a guje, bai tsaya ba sai a qofar gidansu dake unguwar Jabi Road cikin garin Kaduna. **** A uwar dakin Mama take lallashin Bashir yana kunkuni cewa yake. "Aure? Aure?? Wane irin aure yanzun nan haka sabida Allah, mutum yana tsaka da cin kuruciyar sa, ko an gayawa Hajjah zamanin da irin na yanzu ne? Kuma a rasa wanda za a aurawa wannan lukutar yarinyar mai shegen qarfin tsiya sai ni? Salon in na mata ba dai dai ba ta hau ruwan cikina yadda take danne su Zanirah? To ni yanzu ma daga gama karatu ban kama aiki ba anzo an dora min aure, ku ne za ku dinga yi min dawainiyar auren? Sannan ni wallahi ba zama nazo yi ba, na zo ne kawai in ganku in koma. Dama ace 'yar siririyar ku ka aura mini 'yar wajen Baban ABU sai in karva da godiya, me ma take ne da suna Fa'eez?" Fa'eez dake gefe ya juya musu baya yana kallon tangamemen hoton Fa'izah da Zaneerah, sun sha goggoro ranar bikin Zanirah da Mama ta kafa a falon, ya wani irin juyo cikin (slow-motion) ya qwalalowa Bashir kyawawan idanunshi, ya ce. "Yaya Bash! Ahir! 'yan iskan idanunka bisan matata! Na gaya maka, na qara (warning) dinka, o.k?" Mama ta dafe kai, "Fa'iz, yaushe ka koyi rashin kunya ne for Allah's sake waye baya kuskure a bisa rashin sani? Ka bari Bashir ya dora idonshi bisan ummi kamin ya yi wadannan sambatun banzan mana. Bashir, kana magana ne akan wasu kwailayen yara mitsi-mitsi daka tafi ka bari shekaru takwas a baya da suka wuce. To wadannan...". A yayin da ta miqe ga daya 'enlargement' din dake can hanyar kofar fita na Zanirah da Ummi, shima ranar bikin Zanirah ne sun sha ankon beig swiss laces mai ratsin silver da goggoro kalar adon leshin, wato (silver), wanda in ba ka daga idonka sama ba baza ka hango shi ba saboda anyi (placing) dinsa da nisa, ta taka kujerar cin abinci, ta dauko ta sauko fuskarta cike da annuri ta dora ma Yaya Bash akan cinyarsa. "Ga Ummin Hajjah". Bashir ya kurawa Ummi ido na 'yan dakiku yayin da kalmomin da suka shiga fita daga bakinshi bai san dasu ba... "How does this girl turn to slim?" Duk da tension din da Fa'iz yake ciki wanda Bashir din ya hada masa sai da dariya ta kama shi, ya yi murmushi cikin takaici ya tashi ya bar dakin yayin da Mama ke kyalkyala dariyar jin dadi tana kallon idanuwan Bashir da ke neman zazzagowa akan hoton. A ranta ta ce. "In banda anfi karfin Ummi me zata yi da Bashir don Allah? Ita kam tana fatan Ummi ta zam silar kimtsuwar xanta daga halin da ya tsunduma kanshi babu gaira babu sabar, don duk komi yana dawowa kunnenta, duk da Fa'iz ba duka yake gaya mata ba sai dai ya ce tayi masa addu'a, ya canza hali rana daya. Ta daga hannu sama ta godewa Allah Al-khaliku sarkin qaga halitta da ya suranta Ummi kirar da ta fi karfin namiji ya wulakantata. Ta sani da yawa kamilallun mata 'ya'yan gidan tarbiyya suke shirya mazajensu masu mugayen dabi'u irin na Bashir, don haka ta kara godewa Hajjah tare da binta da kyakkyawar addu'a a zuciyarta na Allah Ya ja kwananta cikin zuri'arta har kansu (junior) ko ana so ko ba a so. Allah Sarki Maman Kaduna, a wannan ranar bata yi bacci ba, kwana tayi akan kafafunta tana kai sunan Fa'iza ga mai duka, kan ya karkato da hankalinta taso Fa'izu. Mama hawaye take da idanunta, a yayin da take rokon mai cusa soyayya da ya cusa soyayyar Fa'iz a zuciyar Fa'izah. Soyayyar da babu kamarta a duniya wadda ta fi gaban wadda take yiwa Nazir Galadanchi. Babu abinda ke damun Mama irin ganin yadda Fa'iz ke neman ya susuce kamar baya ji sosai, sai kayi magana sau uku kafin yasan da kai a gabansa, tunani yake ko da yaushe. Tun dawowar shi bai iya ya tsaya ya ci wani ginannen abinci ba kullum sai tea, lemo, snacks. Jiya kam da ta shiga boys qutarers nemansa yana wanka ta tadda hotunan Fa'iza sunfi kala goma anyi enlarging dinsu an kafa a kowanne kusurwa na daki da falonsa, musamman cikin bedroom, tayi tunanin ina ya samo hotunan? Da ta tambayi Yahya ya ce shi ya aika ya karba mishi wurin Walida. Mama kam ta tabbatar hakkin Fa'izah ne ya kama Fa'iz. Babu mamaki in ya tuka jirgi a wannan lokacin ya saito shi cikina garin Giwa wanda hakan babu makawa zai murkushe musu dan garin na iyaye da kakanninsu da bai taka kara ya ba balle ya karye. Mama ta tabbatar nutsuwar Fa'iz kawai samun zuciyar Fa'izah, ko da bai furta ba bai kuma nuna (weakness) dinsa ba, har gobe Fa'iz Abubakar, namiji ne mai amsa sunan namiji ko a cikin daruruwan maza baka fiya gane (weakness) dinsa ba, balle akan mace. Ita din ma don ta sa mai ido ne, amma da fatar bakinsa bai furta mata ba. Wanda hakan kuma (samun zuciyar Fa'iza) ba shakka ba karamin aiki bane ga duk wanda yasan Fa'izah da Fa'izun wurin kafiya da taurin kai. Wadannan sune halayen da Hajja ke hange har take ganin hada masu irin halayyar gamayyar aure shi ne dai-dai. A yau kam Mama ta qalubalanci tunanin Hajjah akan-kanta. Hada masu halayya daya aure cikin A.B ba dabara bace so-karvau. Zanira da Aliyu kam hadi ne na Allah, laushi na dukan taushi. Amma masu taurin zuciya da kafiya ba dai-dai bane hadasu aure, in daya ya taso daya ba zai sauka ba, haka in daya ya hau daya ba zai yarda ya fado kasa ba yayi lallami ya kaskantar da kai ba ga dan uwansa. Yadda Fa'izah ke ganin ta watsar da kanta inta kwantar da murya ta roki Fa'iz SAKI, haka Fa'eez Giwa ke ganin zub da kima ne da aji, muddin ya kwantar da kai ya baima Fa'izah haqurin abinda ya yi mata a baya. Duk da abin ya zo ya zame masa jidali, ya hana shi ci, sha da sukuni da jin dadin komai dake cikin rayuwar duniyar baki daya. Ya hana shi barci da walwala balle komawa bakin aikin shi. Don haka Mama ke addu'ar Allah Ya sauke na Fa'izah, domin muddin Fa'izah ta sauke dole ne shima Pilot din ya sauka. To a washegari ne kuma Aliyu ya kada mata 'ya'yan hanji da albishirin gudun Fa'izah. Bata iya ta fadiwa Fa'iz ba sai dai shi a lokacin ya damu da ya ga Fa'izah ko da gani da ido ne a kalla zai samu sauki daga azabtuwar da zuciyarshi ke yi a dalilin rashin ganin nata, inyaso ko ganinta ya yi kawai daga nesa ya haura takalmansa ya bar mata garin da kasar baki daya, in ta rage bala'in ta bishi Amsterdam su zauna. Indai sun kasance gida daya ai maganar kafiya da kiyayya sai ayi ta yin mai dalili, ba yanzu da ko harararta baya hange ba. Ya kurawa jerin jakunkunan da ya danqara dalolin shi ya sayo da sunan lefe ido. Shin wacce Fa'izah yake tunanin za ta daura zaninshi? Ko da yake a lokacin yana kan aiki a Istanbul ne, giyar son ta buge shi, ya shiga hada su a kasuwar (AKMERKEZ Shopping Mall) ba tare da ya yi shawara da kowa ba ko yasan 'size' da take amfani da shi a yanzu. Ya dubi shekaru ne kawai ya kintata, kuma da ya ganta bata zarce yadda ya kintatan ba. Ya bude yana duba su a hankali har da (underclothes). Fadin abinda ya kashe akai bata baki ne, amma ta wace hanya zai bata ta karba tunda a zuri'ar su ba'a lefe? Shi ne abinda ke damunsa. Ya mayar ya zuge ya koma ya jingina da filo ya lumshe idonsa, abin duniya ya bi ya dame shi, ya rasa ta hanyar da zai bullowa matsalar aurensa. Hausawa kan ce, "Tun ran gini ran zane". Haka "Juma'ar da za tayi kyau tun daga Laraba ake ganeta". Sannan "Kowa ya sayi rariya yasan zata zub da ruwa". Kuma "Tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka". (So he has to bear the outcome of his wrong doings...) Ya nisa "Ba abinda lokaci ba ya magani". Wani sashi na zuciyarsa ya yi (whisphering) wato rada. Dai-dai lokacin da wayarsa dake kan bed-side take ta tsuwwa. A fusace ya dauka domin bai son wani abu ya katse tunanin nan da yake yi, tunanin kaxai sassauci yake saukar mishi tunda ba zai iya gayawa kowa halin da yake ciki ko abinda ke damunshi ba, sai dai su tattauna shi da zuciyarsa su baiwa juna shawara, su kuma lallashi juna tunda babu mafita sai jajircewa, ya rike igiyoyin aurensa gam-gam har zuwa lokacin da Allah zai tausasa zuciyarta wadda babu wanda ya san yaushe ne? Sai Zuljalali wal ikrami. "Na'am!". Abinda ya ce kenan ba tare da ya duba fuskar wayar ya ga wane ne mai kiran ba. "Ka ajiye duk abinda kake yi haka ka taho gobe. Yanzu na samu sakon ana kiranmu (interview) jibi da British Airlines. Ka sani wannan dama ce ba ta wasa ba, don Allah Abubakar ajiye komai ka taho don Allah. Night flight na gobe zamu bi zuwa Great Britain". Abokinsa ne Ba'indiye Maajid Abduljalal ke magana kamar zai fashe da kuka. "Amma Maajid za ka cuce ni, ka san abubuwan da suke gabana kuwa?" "Zan cuce ka ko zan taimake ka? (This is a life-time opportunity) Abubakar, ina shawartarka (don't miss it...) koma mene ne ke a gaban naka ajiye shi, ba Fa'izah bace? Don Allah kada ka ba da maza (achievements are greater than women). Ka yarda dani, ka karfafa zuciyarka muyi wannan fafutukar tukunna, sai ka dawo ka ci gaba. Na yi maka alkawarin (I'll stand by you) inga cewa kun dai daita da matarka idan mun dawo (and I promised to help you to the end of the battle my friend, be a man) Fa'iz, ina jiranka. Akwai (morning flight tomorrow) daga Abuja, nima shi zan bi daga Berlin zamu hadu a Airport din Wales, ina jiranka". Ya kashe wayar ba tare da ya bashi damar ya yi korafi ko musu ba. Ya ajiye wayar cikin matuwar jiki, sai kuma ya daga ya kira British Airlines ya yi 'booking' duk da jikinsa a mace yake. Wani sashe na zuciyarsa ya yarda da Majid babu tantama zai halacci wannan (interview) to amma wani iri yake jin jikinsa kamar in ya tafi ba zai dawo ya tadda Fa'iza ba. Halin rai da karfen nasara. Ya duba agogonshi 'Jovial' mai ruwan kasa-kasa ya tadda karfe uku na yamma. Dole ne yaga Fa'izah ko daga nesa ne kamin ya tafi Birtaniya. Domin a yadda yake jin jikinsa da zuciyarsa da kyar ne in zai dawo ya tadda Fa’iza. Don haka maganar ginshira da jan aji babu su yanzu, zai fuskanci Fa'izah (no matter what!) Ya mike kamar wanda aka yiwa allurar kuzari ya fito da sauri ya kwalawa kaninsa Shu'aib kira. "Ka rufe kofar nan ka kwashi jakunkunan nan dake daki na ka zuba min a boot ka aje mukullin, zanyi tafiya sai na dawo". Ya isa sashen Mama yana yi mata bayani a gurguje, sai ga hawaye a idon Mama. "Ni dai raina baya son tukin jirgin nan Fa'iz, hankalina ba ya kwanciya, kullum kana kan iska. Me zai hana ka dawo gida kwata-kwata ka nemi wani aikin mai sauki kayi?" Ya yi dariya ya ce, "Kai mama kenan, insha Allah ba abinda zai faru. Ki bar mutum da zuciyar sa akan abinda suke so, kiyi addu'a Allah Ya tsare, Ya dafa mana, Ya kare miki mu a duk inda muka shiga. Ki cire duk wata fargaba da tsoro, mutuwa daya ce tak! Hanyoyinta ne yawa gare su, amma inevitable ce (mara makawa). Yanzu ina zan ga Fa'izah inje Mama ko da babu gaisuwar arziqi?" Mama gabanta ya ragargazo ya fadi. A irin wadannan kalaman masu tsinka zuciya da Fa'izu ke furta mata da halin da yake ciki a fuska da zuci zata iya kara masa damuwa da sabon labarin gudun Fa'izah? Ko da yake wani sashe na zuciyarta na gaya mata wai Fa'izah na Zaria, amma ya akai tasan hakan? Ya za'ayi ta tabbatar da hakan? Yadda Fa'izah taki jinin auren nan ina ne ba zata ba don ta guje masa? Fa'iz ya sha jinin jikinshi da shirun Mama, ya ce cikin raunanniyar murya. "Mama Fa'izah ta kashe kanta saboda kiyayyata ne ki ke jin nauyin gaya mini? Na tabbata Fa'iza in akwai abinda yafi haka zata yiwa kanta, indai akaina ne Mama...". Ya kasa karasawa, muryarshi na karkarwar da ta baiwa Mama tsoro akan wanda take ciki. Tayi hanzarin katse shi. "Lalalala! Fa'iza ta warke tuntuni. Hasalima ka samu sauqin tafiya domin tana A.B.U". Ta hasaso ne kawai ta fada, domin ta rantse ba za'a ji mutuwar sarkin nan daga bakinta ba, ya je wani ya gaya masa. Tayi saurin dauke kanta daga kansa, saboda hawayen da ke neman fallasa ta sun ciko idanunta, kiris suke jira su malala. Ya yi dan murmushin tausayawa kansa, amma yafi tausayin Mama da matsalar shi ta zo tayi mata karan tsaye bata ji ba, bata gani ba. Ya juya ya doshi kofa, a zuciyarsa babu tsoron Fa'izah ko miskala-zarrah. Babu tunani ko fargabar abinda zata yi masa. To me zata yi masa da ya wuce zagi na fatar baki tunda dai a doke ba zata doke shi tayi nasara ba, sai dai hannunta ya yi ciwo. Zagi yana tofo? Ko yana tsiro a jikin dan Adam? "Kuskuren Pilot Fa'iz Giwa kenan na farko, da ya sani da ya tafi neman aikinshi salin-alin shi ya fiye mai ALHERI". Inji Sumayya Abdulkadir (Takori). [17/02 7:57 PM] Sumayya Takori: *** A ZARIA Yaya Rabi da suka taso daga Kano ita da direban Ya Muftahu ta yiwa direban umarnin ya tsaya a Zaria zata ajiye tsarabar Momi na ta Gurasa data yo mata daga Kano kamin su wuce Giwa su hadu ita da su Yaya Aliyu su shiga neman Fa'izah. Malam Garba direban Muftahu yayi (parking) dai-dai kofar shiga falonmu kasancewar gidajen malamai na Jami'ar Ahmadu Bello falo zaka fara taddawa da ka zo gidajen. A dai-dai wannan lokacin na kammala cin abincin rana da Walida ta lababo ta kawo min ne. Na daga labulen dakin Abdallah ina kallon daidaikun motocin dake giftawa suna wucewa ta kofar gidanmu da yake titi ne a shimfide wanda in ka bishi zai shigar da kai cikin makaranta don ko kusa nasan ba lokacin dawowar Baba bane, don shi sai wajejen taran dare yake shigowa. Nikam wannan zaman kadaicin ya fiye mani zaman Giwa ina kallon bakin ciki kala-kala. Sai dai tunanin halinda N.S ke ciki ya addabeni ko a wane hali ya samu kansa da jin wannan bala'i da ya fada mana babu zatonmu ba tsammani? Naji haushin barin wayata da Nazir ya bani da nayi a Giwa, ko banza da yanzu ina magana da N.S muna neman mafita. Ko da yake ko da na taho da ita din babu katin da zan ke saka mata tunda ko giyar wake nasha ba zan aiki Walida wani waje ba balle har Momi tayi (spotting) dinmu. Shin a duniya ina da masoyin da ya kai Walida a yanzu? Tun bullowar bakin al'amarin nan gareni ita kadai ta tausaya min, ta taimaka min ta kuma bani goyon baya don ita ta yarda nice tata, kuma farin cikina take so ba na kowa ba. Duk da itama da fari ta so ta tirje amma Hausawa sunyi gaskiya da suka ce ce naka sai naka. Na sa hannu na share hawayen da suka zubo min. Babu zato babu tsammani naga shigowar motar su Ya Rabi, kafin inyi wani motsi na neman buya munyi ido hudu da ita, tana rungume da jaririnta Sadiq mai sunan A.B da ta haifa. Wai sai na saki labulen da sauri na kwanta a kasa ina haki. Yaya Rabi ta fito daga mota tayi kofar falo tana danna kararrawa, Momi tazo ta bude, ta ce. "A'ah! Manyan baki daga birnin Dabo, saukar yaushe?" Rabi ta ce, "Ke tsaya Momin Walida, ina Fa'izar da aka ce ta gudu?" Momi ta ce, "Wai 'yarki? Ai, ashe gurinki ta gudu?" Yaya Rabi ta dubeta shekeke abin har da alamun raini a ciki, ta ce. "Wurina ko wurin ki? Amma Aunty Maimuna baki kyauta ba, kina ganin yadda hankalin bayin Allahn nan ya tashi musamman Hajja, Baiwar Allah me tayi muku da zafi haka, don ta nufe ku da alheri? Shin dama tsakanin Fa'iz da Fa'izah akwai bambanci ne da za ki goyi bayan Fa'izah ta ki zaman aure da Fa'izu? Ai dama shi bare a cikin A.B har abada sai ya nuna shi bare ne. To sai dai ki bar naki auren akan na 'yarki, amma wallahi baki isa komai ba. Mtsw! Ni bani hanya in wuce". Momi na ta dubeta galala kamar ta ga hauka sabon kamu, duk da maganganunta sun mata zafi amma ta danne zuciyarta, a tausashe ta ce. "Shin Rabi ina ruwana da harkar Fa'izah balle aurenta? Tukunna ma da kika zo kika sani a gaba kina zagi Rabi ina kika ga Fa'izar a gidana da har nake goyon bayanta?" Rabi ta doka tsaki ta ce, "Yanzu fa naga Fa'izah da idona, yanzu nayi ido hudu da Fa'izah, kina tunanin ina da matsalar ido ne?" Momi ta ce, "Kayya Rabi, ba dai gidana ba, in kuma kina musu to ga hanya shiga ki duba ko’ina" Rabi tayi tsaki ta shige har tana bige kafadar momi tana fadin. "Biyo ni in nuna miki Fa'izar". Ba musu Momi ta bita salaf-salaf kamar ana janta, yayin da Rabi ta murda marikin kofar dakin Abdallah, sai gani kwance a dandaryar kasa bisa (carpet) nayi flat duk na jeme nayi zuru-zuru nayi baki kamar ba ni ba. Momi ta shiga salati da sallallami tana fadin. "Na rantse da Allah ban san da Fa'iza cikin gidan nan ba, bansan ta ina ta shigo ba, bansan yaushe ta shigo ba". Yaya Rabi kam bata bi takan momi ba, kallona take cike da takaici, yayin da nake barware wani irin kuka, ta ce. "Amma kin bata wayonki Fa'izah. Yanzu kan mutumin da ya kusan sati a makwancinsa ki ka kode, kika moje, kika sukurkutar da kyawun halittar ki haka alhalin baki san iya nisan taki rayuwar ba? Kaicon kafaffiyar zuciya mara amfani irin taki. Dr. Naziru kam ya amsa kiran mahaliccinshi tuni, don haka baki da sauran hujjah ta kin karbar aurenki da hannu bibbiyu kuma baki da sauran kaunar da zaki baiwa Nazir bayan binshi da kyakkyawar addu'a". Kwakwalwata ce ta debi wata 'yar hayaniya, tana yi min hargagi, tana yi min ihu-ihu, kararraki har da rugugi da taratsi da kalaman dake fita daga bakin Ya Rabi. Rarrafe na shiga yi akan gwiwoyina zuwa inda take tsaye ina tambayarta cikin kwanciyar hankali. "Ke Rabi, wanne Nazirun ne kike cewa ya mutu? Naziru Galadanci na?" Na fashe da dariya duka a lokadi daya, na dubi Momin Walida. "Kiji muguwa Momi, wai taje sun hada baki sun kashe min N.S don in auri dan uwanta. Ta lallabo nan tana fadin bani da sauran madafa ko hujja ta kin danta. To ko babu Naziru kina zaton zan bar shima Fa'izun da rai ne? Idan har babu Naziru kisa a ranki Fa'iz zai bishi ne duk ranar da ya shigo hannuna... na rantse, na kuma rantsewa da wanda raina yake hannunsa Rabi, shima Fa'iz sai na kashe shi idan da gaske ne kina ikirarin Naziru ya mutu". Na kara saka dariya har da hawaye, a hankali kuma sai na koma kuka tun ina yinshi a hankali da shassheka har muryata ta dushe ta daina ba da amo. Na ciro dankwalin kaina na rufe fuskata da shi. "Wayyo Naziru, wayyo Nazir me yasa kayi min haka a dai dai lokacin da nafi bukatar ka? Ka tuna alkawarurrukan da kayi mani baka cika ko daya ba? Kana so ka tabbatar min da gaske ba zan taba cimma duk wani burina a rayuwata ba? Kana so in tabbatarwa kaina banzo duniya cikin masu sa'a ba? Kana so inyi amanna da cewa ba zan taba samun duk abinda nake so a rayuwa ta ba? Kana so in rasa imanina na cewa nima Ubangiji na so na kamar sauran bil'Adama da Ya halicce mu tare? Ko ko ni Allah baya so na...". Da sauri Momi ta juya man baya tana hawaye. "Yi maza ki gyara furucinki Fa'izah, ce ne Astagfirullah, fadi da babbar murya na tuba Ya Ubangiji, na tabbata Kana sona, son da kake yi min ne ya sanya baka barni da dabarar kaina...ba". Rabi ta fashe da kuka ta kama ni zata rungume ni, na ingijeta da karfi. "Kada ki kuma zuwa kusa dani, yau na tabbatar ba Fa'iz ne kadai mai kina da mahaifiyata ba har da ke Ya Rabi". Na soma ja da baya, Momi ta miko hannu. "Ji ni nan Fa'izah, ki daina fadin maganganun da kike fada, Rabi tayi abu ne akan rashin sani, Allah baya kama laifin da aka yi bisa rashin sani, kuma babu mai laifi sai ke, ko me Rabi ta ce min ke kika jawo min, ke ki ka shafa min kashin kajin da bani da yadda zanyi in goge shi cikin danginku. Baki kyauta min ba, kin sani cikin bala'in da ba zan iya fitar da kaina ba". Ta soma kuka, Ya Rabi ma kukan take da na durkusa na saki wata kururuwa dukkansu ficewa suka yi daga dakin da gudu. Fa'iz Mukhtar Abubakar Giwa, ya yi parking mota kirar 'Sienna' ta Baban Kaduna da ya tuko daga Kaduna zuwa Zaria. Ya fito sanye cikin wata shadda-shadda boyel-boyel ruwan madara kirar (filtex) kanshi babu hula, sakamakon hakan, tarin sumar kanshi ta bamallin usli wadda bai fiya tajeta ba sai dai kula da ita ta kwanta tayi linkif a kansa sai sheki take bakikkirin, murdaddiya kuma kamar yana (relaxing) dinta, kamar kuma haka take a halicce. Ya yi sallama a falon gidanmu inda ya tadda Momi da Ya Rabi na kuka da girmansu da komai. Da sauri Rabi ta ce. "Ka koma Fa'eez, Fa'eezah TA HAUKACE! Muddin kaje inda take a halin yanzu abin ba zai yi kyau ba. Duk ni na jawo da na fada mata rasuwar Dr. Nazir, ni Rabi'atu wa ya aike ni?" Fa'iz ya yi dan dawurwura da manyan idanunshi akansu. "Waye haka Nazir?" Ba kuma tare da ya tsaya jin amsarta ba ya murda kofar dakin Abdallah gaba dayanshi ya shiga gaba gadi ba tare da tunanin komai ba ko wata fargaba cikin ransa. Durkushe nake akan gwiwoyina na aza kaina bisa gadon Abdallah ina sharar kuka babu ji babu gani, fatana kawai adai-dai wannan lokacin nima mutuwar tayi min adalci ta zo ta dauke ni, ta sada ni da masoyina, muyi aurenmu a kiyama ya fiye min wannan rayuwar da bani da sauran masoya a duniya sai rundunar makiya da burinsu a duniya shi ne zubar hawayena da shigata cikin kaka-nikayi, wato iyaye da 'yan uwana na jini. Na dago ido shargab da hawaye, jajur kamar gauta, don naji alamar tsayuwar mutum a kofa, ya kuma jima cikin dakin ba tare da ya yi motsi ko magana ba. Ban tabbatar ba, amma wannan matashi mai jini a jika ya yi min kama da FA'IZ BAMALLI dana sani wasu shekaru masu yawa a baya. Fari sol, har da surkin jaja-jaja kamar Bahurghade, ingarman mutum dan asalin garinmu Giwa, kuma jika ga Hajja Da ga Baban Kaduna da mama Asma'u. "Yau ko ni ko kai tunda Dr. Nazir ya tafi kai din zaman me zaka yi a duniyar banda zaman ka ci gaba da kuntata mini?" Da na mika hannu ga bangaresn dama na sai naji ya fada kan kwalbar lemo (7up) da Walida ta kawo mini na gama sha dazu,, na riketa katamau ina kallonshi kallon kura taga nama, kallon tsintsu daga sama gasasshe. Ya soma daga min hannu yana fadin cikin lumana. "Ki saurare ni tukunna... (just once) Fa'izah, kada ki aikata abinda zai sa kizo kina da kin sani. Na roke ki, ki saurari kalaman fatar bakina tukunna, daga nan na yarje miki ki zartar da duk hukuncin da ya yi miki....". "Ko uban da ya haifeka ban sauraron shi balle kai, kai da duk wani dan A.B ma kwansu da kwarkwatar su indai akan na karbi aurenka ne". Na daga kwalbar nan na wulwula na faskara mashi a goshi, ya yi saurin sunkuyawa ta wuce ta saman kanshi ta daki tsakiyar kansa. Kan kace meye wannan jini ya wanke shi tun daga tsakar kansa, goshinsa har zuwa wuyansa, amma don rashin zuciya zance ko bakin naci Fa'iz bai fasa dosoni ba, sake dosoni yake yana fadin. "Ashe da gasken kin haukace? Fa'izah (are you lunatic?)" Ya warware hannu ya shimfida min mari. Wani irin marin da ya tafi da ji da ganina na wucin gadi, na kuma ga gilmawar taurari goma. Amma bakina bai mutu ba. "Muddin ka iso gareni sai dai wani ba kai ba, baka ba da saki amma idan ka tafi inda Nazir ya tafi na saku ko babu takaba, iyakaci nima a kasheni. Na gwammace mutuwar da zama da kai wai a matsayin miji sau dubu gara mujiya da kai Fa'izu Mukhtar Abubakar Bamalli Giwa". Wani irin karfi da ban zata ba ya shigeni, na isa ga madubin dogon yaro dake like jikin bango wanda Abdallah yasa kusoshi shida ya kafa a dakinsa na soma kokarin banbaro shi daga jikin bangon, ban damu da yankewar da tsokar hannuna ke yi da gilashin ba har na samu nayi nasarar raba shi da kusoshin da suka tokare shi suka zame masa garkuwa daga fadowa kasa. Fa'izu Abubakar, ya tabbatar tsandara mishi mudubin nan zanyi, wanda hakan na nufin tsattsagewar jikinshim ta ko ina, alhalin ba karfinsa nafi ba, don haka yayi amfani da wani irin zafin nama wurin isowa gareni, ya kama mudibin ya yi mishi fisga daya ya wancakalar dashi a gefe ya kwankwatse, na sake doka tsalle don isa ga fashasshen gilashin in samo wani bangare daga jikinsa, ya isheni farkewa jikan Hajja ciki babu nadama, na jini baki daya cikin murdaddun damatsan Fa'iz Giwa, ya rungume ni gaba daya katamau cikin faffadan kirjinsa. Ban san sanda na tsala ihu ba. Wani irin ihu shi ba na karaya ba, shi ba na razana ba, haka shi ba na mika wuya ba. Ni kawai ban san na mene ne ba, ko mene ne ma'anarsa. Saboda wasu abubuwa ne naji cikin jikina masu kama da jan wutar lantarki (shocking) tun daga tsakar kaina har (toes) wato babban dan yatsan kafata shocking din azaba ne ake yi min irin wanda kiyayya ke haifarwa. Gam-gam Fa'iz ya rike ni. "Fa'iza saki dai kike so daga gare ni ko?" Zuciyata na bugu tashi na lugude, cikin masifa da bala'in da ba zai kwatantu ba na ce. "Indai kai dan halak ne cikin uwarka da ubanka... to ce ne an sake ki Fa'izah!". Fa 'iz yayi shiru yana gwama numfashi, kafin da ya tattara dukkan karfinshi yayi watsi dani gefe guda. Yana girgiza kai ya ce. "In aka yi hakan za'a zauna lafiya?" Cikin gyada kai mai nuna tabbatarwa. "Har da kwanciyar hankali, za'a zauna cikin A.B family gaba daya, (no more crisis... no confrontations...)". Murmushi yayi, wani murmushin da na kasa fassara ma'anarshi ko abinda yake nufi, ya ce. "Kin san ba'a saki cikin tashin hankali, ko cikin fushi, in aka yi hakan sakin bai saku ba. (Words and promises made in anger are like fire... you cannot reverse the damage they have done). Don haka share hawayenki, kije kiyi wanka ki fito kiyi sallar la'asar, ki kawo min biro da takarda. Shi kenan Fa'izah?" Haba! Ai ban san sanda na mike nayi toilet ba na sunce na sakarwa kaina shaya, sai a wannan lokacin ne radadi da zugi daga goshi da tsakar ka ya isowa Fa'iz. Ya kai hannu tsakiyar kanshi ya fitar inda yaga yadda jininshi ke ambaliya. Ya murda kofar dakin da sauri ya fito falo inda Momi da Ya Rabi ke zaune jigum-jigum. Momi ta mike tayi salati, ta tsarkake Ubangiji, tayi masa tasbihi, ta kadaita shi. Ta ci gaba da fadin. "Ba lafiyarta kalau ba, kuzo ku fitar min da ita daga cikin gida, ku kaita (psychiatric) kada tayi mana lahani cikin dare". Fa'iz ya samu kujera ya zube juwa da hajijiya suna kwasarsa. Ya yi murmushi. "Momi da hankalinta fa, bacin rai ne. Kuma tana da gaskiya da babu wanda ya tsaya ya kalla, amma shi kenan komai yazo karshe ai". Yaya Rabi ta cire dankwalin kanta ta daure mai goshin, ta sa mayafinta tana share mishi jinin wuyanshi da keyarsa, yayin da Momi ta dauko akwatin taimakon farko (first aid box) da yake ma'aikaciyar jinya ce, ta gyara wurin, ta cire kwalbar da ta nitse a wajen, ta dinke inda ke bukatar dinki duka idanun Fa'iz na lumshe har ta gama. Ta goge duk wani jini da auduga da ruwan (hydrogyn) tas. Ya mike tsaye sanda ya jiyo murda kofa daga (toilet) alamar na gama wankan na fito, yana ce da Momi ta kai min wasu kayan in sanya. Momi tana girgiza kai ta ce, "Wanda ke neman kashe mutum za'a kaiwa kaya ya sanya? Ni kam bana kai kaina mahalaka ina ji ina gani ba, kai dai kace kaji ka gani, bari in dauko maka ka kai da kanka, sai ince ga su". Ta shiga dakinta ta dauko doguwar rigarta da dankwali na shadda ta kawo masa, ya amsa ya murda kofar Abdallah ya shiga. Na takure can kuryar kuskurwar dakin ina mai kallon ceiling da zani kawai daure iya kirjina. Yau sati biyu kenan rabona da wanka, don haka ji nake ta ko ina wata iska mai dadi tana ratsani. Tsami da tashin da jikina ke ta yi kwana da kwanaki duk na samu saukinsa. Gashin kaina da na jika jagab da ruwa ya taimaka wurin suturta fatar bayana, ya kwanta lamban akan dogon wuyana ya sauka a kafaduna. Bai yi magana ba ya mika min rigar na amsa. Fa'iz ya kalleni na 'yan sakanni, ya ce. "Ina takardar?" Na mike na nufi littattafan Abdallah kan (study-table) dinsa na yago takarda harda daurawa akan littafi, na dauko biro. Ya zauna gefen gadon ya karbi littafin, ashe ma yana da nashi biron a gaban aljihun rigarshi kyakkyawa dashi (biron) ya dora akan takarda ya soma rubutu. Na koma jikin bango na tsaya hannuwana biyu sarke a kirjina ina kallonshi kasa-kasa. Ya ce a hankali, "Nawa kike ganin ya kamata in rubuta?" Na dan fiddo ido, da sauri kuma na ce. "Uku mana!". Har sai da na bashi dariya, ya yi murmushi, ni kuma na sake hade rai. Sai ya mai da fuskarsa ya kintsa ta. "Har uku, kina ganin su Baba ba za suyi fada ba?" "Akan me za suyi fada kai da abinka?" Murmushi yayi ya kalleni ya maida kai ya ci gaba da rubutu, ya kammala ya ninke ya maida bironsa aljihunsa ya mike ya iso har inda nake, ya miko mini. Hannu biyu nasa na amsa kamar wadda aka bawa damin kudi don rashin ta ido har da cewa. "Na gode". Ko da yake ni wannan ta fiye min gida da mota dole in gode in kara godewa. Ya yi murmushi ya dauki hanyar fita, har ya kai bakin kofa ya juyo. "To yanzu kin yafe mini?" Na ce, "Ni me kayi min? Dama auren ne bana so da kai". "Ba wannan nake nufi ba Fa'izah.. Na can baya nake nufi, shekaru goma da suka wuce a gidan Hajjah". Nayi shiru cikin TUNA BAYA...Wai TAKORI ta ce TUNA BAYA SHI NE ROKO. Fa'iz ya wahalar dani da yawa har yadda mai karatu ba zai fahimta ba. Ya ki ni, ya nunan kiyayya, ya nunawa uwata, ya yi mata izgili kala-kala da kalamai na raini a wancan lokacin wadanda 80% su suka rura wutar kiyayyarsa gareni fiye da wanda ya yi min ni kaina. Uwa tafi gaban wasa, haka ba'a hadata da komai, ni tawa mai sauki ce tunda na yar da kwallon mangwaro na huta da guda. Fa'iz ya cuce ni sosai, ya vata min sosai (he so much hurt me heart and soul) ya bata min baka da zuci ta yadda a wancan lokacin har nayi furucin BAZAN TABA YAFEWA FA'EEZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI BA! To amma mutumin da ya hakura da auren da yayi don yana so duk da mugun rotsen da ya sha ai ya cancanci yafiyar tunda dai daga yau shi kenan da kyar ma in wata hulda zata sake hadamu baya ga gaisuwar zumuncin da ta zama dole ko a lahira sai anyita. Sai na daga jajayen idanuna na dubi dan uwana Abubakar (Fa'iz) har zuwa lokacin idanunsa akaina yake. Wani irin yanayi ne cikin kwayar idanunshi mai nuna gajiya, damuwa da matsananciyar yunwa wadda ta ci karfin mutum ta nuna cikin kwayar idanunshi. Ban taba ganin Fa'iz ba tun bayan tafiyar shi ko a hoto sai yau, ya kara wani irin girma da kyau da haiba mai ban mamaki. Ya zama (giant) ma'abocin kwarjini da kamala da alamun samun (exposure) na rayuwa cikin kowanne fanni a fararen kwayan idanunshi. Fa'iz ba Fa'iz ba, in ba don halin ba me zai hana ni inso wannan kyakkyawan kammalallen matashi? Na kau da wannan bahagon tunanin na ce cikin taushin murya. "Ka je kawai, babu komai". Fa'iz ya tura duka hannuwanshi cikin aljihu, ya ce a tausashe. "Baki yafe din ba kenan?" "Abinda ya wuce ya wuce a wurina, bana son TUNA BAYA...". Ya lumshe ido, "Har yanzu baki fadi ba da bakin ki Fa'izah cewa kin yafe mini". Na ce, "To Ya Fa'iz, NA YAFE MAKA DUNIYA DA LAHIRA!". A hankali Fa'iz yake lumshe idonsa yana bude su, ya yi shiru ya kasa cewa komai. "Show me in another way... na kasa gasgata kunnuwana Fa'izah". “Like how? (Ma'ana, ta yaya?" Na tambaye shi. Sai ya zaro hannunshi na dama dake sanye cikin aljihun rigarshi kaftan na yadin (filtex) ya miko mini (yana nufin muyi musabaha). Abinda bana so din shi ne ya dawo min, wato TUNA BAYA..., "Ba don komai Baba ke son in tafi ba sai don Mama da ta tsane ni kan shegiyar yarinyar nan Fa'izah!!!" Ban iyawa! Hada hannu da Fa'iz Bamalli... Wani kwayan mutum guda daya da ya takurawa zuciyata a lokacin da bata da kwarin daukar kunci da kuntatawar. Wata zazzafar kwalla ta shiga tsatstsafo min. Fa'iz idanunshi suka kada, jikinshi ya soma dan shaking a sanda yake fadin. "Baki yafe min ba, wallahi Fa'izah yafiyar ki bata kai zuci ba. Akwai abinda baki sani ba, ban taba kin Momi ba, ban rainata ba, kuru... kuruciya ce da yarinta amma babu komi a raina a game da Momi ko da take (outsider) amma na yarda nayi kuskure kuma babu wanda ya san gobe sai Allah, kuma kana naka ne Allah Yana nashi. Yanzu babu lokaci, ina kan uzuri da na baki labarin abinda ya faru tun kafin a haife ki...". Ya tsuguna a gabana ya dora hannu bisa tafin kafata, amma ya kasa sake furta komi, wani ajin yana motsawa yana so ya maida shi Fa'izun shi yana so har gobe har gaban abada kada Fa'izah ta juya shi ko ta ga (week-point) dinshi. (Na yaushe kuma Fa'iz? TAKORI). [18/02 2:48 PM] Sumayya Takori: Sai ya mike a hankali yaja da baya ya juya ya doshi kofa, sai da ya kai bakin kofar sai ya juyo kadan cikin fadin. "Allah Yaji kan NAZIR S.". A lokacin ne mutuwar da Ya Rabi ta ce min Dr. Nazir yayi ta dawo min danya sharaf, tuni hawayen dake makale cikin idanuna suka tsinke baki daya. Addu'a ce mai kyau ya yi ga masoyina na hakika, wato Dr. Nazir Sani Galadanci. Don haka na ce. "Ameen Ya Rabbi". A yayin da ya sanya kafarshi waje zai fita daga dakin. Wani sauti ne ya fito tun daga karkashin zuciyata na zuciyar 'yan uwantaka va tare da yayi shawara dani ba. "Haka zaka fita kayan ka duk jini?" Sai bayan na furta ne naji kunya da alamun nadama, sosai idanunshi ke nuna cikin juwa yake karfin hali kawai yake na duk maganar da yake yi, a hankali yayi murmushi ya dan juyo ya dube ni. "Za suke tuna min da irin kyakkyawar sallamar da muka yi da matata (a da) kanwata FA'IZAH A.A GIWA. Don haka kada ki damu da su, ko nazo sanya (uniform) ba zan zubar da su ba, zan tafi da su har Great Britain". Yayi murmushi (a karo na biyu) “ki sanya kayan da Momi ta baki” ya fice da sauri. Oho kuma wai inji wohoho! Kai ya shafa, ni dai tunda na rabu da alakakai falillahil-hamdu. Dama abinda yasa ni tambaya ganin yawan jinin ne tunda haka yake so meye ruwan Fa'izatu? Momi ta dube shi a yayin da ya kai kofar fita zuciyarshi a jagule, ta ce. "Yanzun Fa'izu haka za ka shiga cikin mutane kaya duk jini? Ka zo ga na babanku ka saka sai ka tafi". Ya yi murmushin da Hausawa ke kira yake. "Babu komai Momi, da naje (Airport) canzawa zanyi zuwa (uniform) ai". Rabi ta ce, "Daga nan sai ina?" Ya ce, "Ina da (interview) ne Aunty Rabi a kasar Birtaniya". Idanun Rabi sukai rau-rau, hawaye na son zubowa ta ce. "Haka zaka yi tukin jirgi Fa'iz da rauni a cikin kanka?" Cikin kosawa da son ya tafi kafin likin da yayi ya balle, ya ce. "Babu komi Ya Rabi, bi'izinillahi Rabbi". Ta ce, "To baka hakuri da tafiyar zuwa sati mai zuwa kafin nan Fa'izar ta sakko ku tafi tare? In ta zauna nan me zata yi mana?" Fa'iz ya sake murmusawa cikin takaicin kalaman Aunty Rabi, ya ce. "Shin cikin ku Ya Rabi wa ke da jan wuyan sanyata ta bini ba ma gidana ba har wata duniya a yadda take ji da taurin kan nan? Yanzun ma dabara nayi mata muka rabu lafiya, ki rufa min asiri in tsallake in bar Nigeria Ya Rabi". Yasa kai ya fice abinshi. Bai isa (Airport) ba sai ana kiran sallar magariba, a yayin da ya karya motar ya shiga filin jirgin ne zugin da radadin da tsakar kanshi ke yi ya tsananta. Ya kashe motar a wuri na musamman ya fita ya dauko jakar kayanshi na (boot) ya rufe motar, cikin sauri ya gama cike-ciken takardun da zai yi. A yayin da ya shiga (pilot's changing room) domin sauya kayan jikinsa zuwa na matukan jirgin sama ya tuna da abinda ya ce da Fa'iza, ya yi murmushi. A lokacin ne cikinshi ya soma kugi, wani irin kugi da bai taba yi mishi ba, yana tuna mishi rabon shi da kwakkkwaran abinci tun dirar shi Nigeria daga Russia. Yanzu kam da zuciyarshi tayi sanyi, hankalinsa ya kwanta da samun kalami mai dadi daga Fa'izah yana jin zai iya hadiyar abinci ko abin sha. Abinda bai taba samu ba tun tasowarsu (kalami mai dadi daga Fa'izah) ko da yake shima din haka bata taba samun rana irin ta yau daga gareshi ba. Don haka ya yi (marking) ranar (as precious). Wata rana mai dumbin tarihi a cikin ranakun rayuwarsa. Fa'izah tayi kuskure da take tunanin zan iya sakinta koda daya ne balle uku rigis, saboda shima haukan da ake zaton mata ya sameshi ko me? A yadda yake jinta a zuciyar nan tasa, yake jinta a ko'ina na ruhi da bargon jikinsa? Shi kam bai san ma yana son Fa'izah ba sai yau din nan, ashe ada hasashe yake, ba don wani kyawunta ko kyakkyawan girman da tayi ba, a'ah yin Allah ne kurum, shi ya daura masa ta yadda bashi da harshen da zai fassara soyayyar Fa'izah a zuciyarsa, tun ranar da ya bar Giwa zuwa kasar Rasha. Ya tuna rotsen da tayi mishi, sai ya girgiza kai ya yi murmushi. Kuruci dangin hauka kenan. Fa'izah na ganin hargaginta da (power) dinta shi zai kwatar mata 'yancin da take so, har yaji tsoronta ya sake ta? Tsoron sa Allah-tsoron sa ranar da zai dawo gida Nigera daga wannan tafiya da zai yi wanda ya tabbata idan taji tsiyar da ya shuka mata a takarda ta nemi tsire shi da mashi, wannan ne hukunci na karshe da yake tunanin Fa'izah zata yanke masa in ya dawo. Bai kai karshen tunaninsa ba (computer) ta shiga ankarar dashi lokacin tashinsu yayi. Za su tashi ne karfe uku na sulusin daren ranar ta Alhamis daga (airport) din Abuja zuwa Wales din kasar England ba kamar yadda ya kintata da farko ba, wato karfe goman dare, don haka lokacin haduwarsu da Majid ma ya canza don sunyi 'transit' a ‘Scotland'. Karfe sha biyu na safiyar washegari suna Wales. Kowa dake cikin jirgin ya fita in ka dauke (pilot) Fa'iz Giwa, yayi shiru shi kansa bai san me yake tunani ba har saida wani abokin aikinsa ya ankarar dashi za'a rufe jirgin, sannan ne ya daura idon shi akan jakar kayanshi ya dauka ya mike ya fito. Monica da kawarta Divya, suna daga cikin fasinjojin jirgin da Fa'izu Abubakar ya biyo zuwa Scotland, zai sake kwasa zuwa Ingila. Sunzo ne musamman daga Abidjan domin halartar kallon wasan kwallon kafa na gani da ido a (Chelsea UK). Ta gabansu Pilot din ya gifta a (reception) jaye da 'yar jakar kayanshi a hankali akan (marbles). Tsakanin Monica da Divya, an rasa wadda zata fara dauke ido a kansa har ya kulewa ganinsu ya bi (lifter) zuwa (underground). Monica ta tabo Divya. "Kin sanshi ne? Irin wannan kallo haka?" Divya ta girgiza kai, "Kamar nasan fuskarsa, ya taba debo mu daga Paris zuwa Ukraine". Divya ta ce, "Bahaushe ne fa tamkar mu ba Balarabe ba, sai dai ta ko ina babu fuska". Monica ta hadiyi miyan da ya tsaya a makoshinta, ta dafe kirji ta rufe ido tana ta faman gyada kai kamar kadangaruwa, wata irin soyayya na cinta Fa'izun bai san suna yi ba wai kunu a makota. Sun hadu da Majid a filin jirgin saman Wales, ba abinda Majid ya fara hangowa sai lafceciyar (plasta) akan Fa'iz da goshinsa. Hannu ya mika ya rungumo kafadunsa suka karasa wani dakin hutawa na musamman dake cikin filin jirgin, suka zauna a tare cike da gajiya da tsamin jiki na kwanan zaune. Majid Abduljalal Balaraben Syria ne wato (Shaam), tare suka yi karatu da Fa'iz a Russia da Johari da wani bakar fata Solomon Bayaraben Nigeria (they are very close to each other) don haka sun san tarihin juna, sun kuma san damuwar junansu. Majid bai tabbatar ba, amma jikinshi ya bashi anyita ba dadi da Fa'izah. Hasashen shi ya hasaso mishi ita ce ta yiwa Fa'iz wannan raunin. Fa'izu ya ja numfashi ya sauke, da gasken-gaske cikin damuwa yake mai yawa, wadda ta kasa boyuwa akan kyakkyawar fuskar shi. Maajid ya bubbugi kafadunshi, ya yi murmushi ya ce. "WO-MAN! Inka fahimci kalmar ko? Tana nufin Wo! MAN ka shiga uku kenan!". Duk halin da Fa'iz yake ciki sai da Maajid yasa shi dariya, ya yi mai isarsa kafin ya ce. "Maajid! Maajid!! Ya aka yi kasan cewa Fa'izah ce ta rotsa ni?" Ya ce, "Oho maka wannan kuma! Ni dai na san kai ba makaho bane balle ince faduwa kayi ka ci da baka ka fasa goshi ka fasa kai, na kuma san ba dambe kayi ba aka fi karfinka da (giantness) din nan naka Fa'iz. Na kuma tabbata ba gidan giya kaje wani yasha ya bugu ku kayi rigima ya rotsa maka kwalbar ba". Sai ya sake tintsirewa da dariya, ya ce. "To amma saboda Allah me yasa ka kirani adai-dai lokacin da kasan ina tsakiyar yakin neman soyayya a tsakiyar rikici da Fa'izah? Shin ko kasan wannan kadan ne da ace ban yi mata karyar saki ba da ta kwankwatse ni gaba daya da gilasai?' Majid ya yi tsaki ya ce, "Kai ka so duka wannan shirme na Fa'izah. Ni kam yana daga cikin abinda ya hanani aure yanzu, wato fargabar irin macen da zan debo ma kaina, don ni dai ba zan auri matar da bata so na ba wallahi. Idan wani ya ki ka da wuni, wani da kwana zai soka. Ba'a san maci tuwo ba sai miya ta kare, don haka mu bamu fara cin tuwon ba ma balle miyar ta kare, yanzu ne muka fara laluben har sai mun lalubo mai son mu. Mu matuka jirgin sama, muna bukatar mata masu matukar son mu, wadanda kullum muka fita sai sun kai goshinsu kasa sun roka mana kariyar Ubangiji saboda kullum rayuwarmu cikin sadaukarwa take, za'a dawo ko ba za'a dawo ba. In zamu fita su faranta mana, hakazalika in mun dawo. Sannan ba nymphos ba (masu yawan bukatar Da namiji) ka gane? Don haka ne naga wautarka da rashin azancin ka wurin nemo auren yarinyar da tun fil'azal kai tafi tsana sama da komai a rayuwarta wai a matsayin (life-time partner) dinka. Kada ma kayi gigin kawo mana Fa'izah a yanzu, ta hada maka zafin da zaka tura rayukan al'umma cikin (solar-system). Ka barta tukun, zuwa wani dan lokaci har ta sauke zafin kanta". Ya yi murmushi mai hade da sautin dariya. "Yau Majid so kake ka kasheni da dariya. Da alama kana da (good experience) akan WOMEN din nan. To ga tambaya, shin ya za'ayi Fa'izah ta so ni? Ni dai (I can't do without her no matter what). Ko kasan duk haukan kiyayyar da Fa'izah ke yi a kaina bana jin ciwo? Ka san cewa har iyayena Fa'izah ta zage su tas akan idona ban ji komai ba, me yasa?" Da sauri Majid ya amsa. "Don kana sonta mana, so irin na halaka ga maza, wanda ya zarce halastaccen so ya hada da ribatar zuciya, so na fiye da kima don iyaye ba'a hada su da wata abar banza (mace). Duk da ance so hana ganin laifi to amma banda iyaye. (They made us what we are today! They are, therefore, incomparable to any worldly material). Ka farka daga gigin son nan Fa'iz ka zama jarumi akan Fa'izah kamar yadda kake jarumi akan komai. Sai dai in kiyayyar Fa'izah ta ci gaba wata rana zaka kita kaima. Kiyayyar Fa'izah a gareka ta yi yawa, tafi wadda ka ce kayi mata. Ni dai in ni Maajid ne bazan jure ba, mace ta fasa min kai... ta zagar min iyaye, mace! Mace!! Mace!!! Woman, Imra'ah! Ana maa Adhry!!! Macen ma wata karamar yarinya Fa'izah da ta tashi a kauye irin Nigeria? Ba zan dauka ba". "Baka taba fadawa a son Woman din da ka rainawa kura bane Maajid shi yasa kake duk wannan cika bakin da kake yi. Nima da irinka ne, haka nake da wannan akidar. Ban taba zaton akwai macen da zata sani zub da kaina ba sai da Allah Ya dora min lalurar ciwon son Fa'izah. Ko kasan har kasa na dire gwiwoyina ga Fa'izah? Maajid SO BA KARYA BANE. Sai dai ta wani bangaren ina cizawa ina hurawa. Iyaye duka iyaye ne a zuciyar kowanne Da na halak Maajid. Na zagi uwar Fa'izah yafi sau shurin masaki akan idonta a kunnenta kawai don bata fito daga family dinmu ba, ban taba tunanin yaya take ji a ranta ba, duk da yarinyar ce a lokacin. Kuma kasan saboda mene? Ba wani abu bane kawai Maman nata (we are not bloodly related). Babanta yaje bautar kasa yayo (secret marriage) da ita daga Taraba da yake na gaya maka a zuri'armu ba'a auren (outsider). Bayan wannan Aunty Mainuna bata yi min laifin komi ba, baya ga ALHERI. Ko kallon banza nayi mata murmushi take mayar min a da can tana fadin yarinta ce, idan na girma zan gane wani baya auren matar wani, itama bata taba zaton zata auri bazazzagi ba tana cikakkiyar bafulatana. Da Allah Ya tashi saka mata Maajid rana daya sai Allah Ya yiwa al'amarin nawa juyin waina da kaunar abinda ta haifa tun ranar da aka haifeta.......". Labarin mai tsaho ne Maajid, (just bear in mind I have reason to love and respect Fa'izah and her mother to such an extent, and I'm ready to do everything to undo the hurt I caused to them). In kuma ci gaba da jajircewa ga rike igiyoyin auren Fa'izah da duk iya karfin da Allah Ya halicceni da shi har sai na dinke ZUMUNCIN A.B family ya koma yadda ABUBAKAR BAMALLI ke son ganinsa, hakan kuma zai ci gaba ko babu tsohuwa Hajjah (to the last journey) insha-Allah, ni na lalata ni zan gyara, duk da ance ba'a bari a kwashe dai-dai, jikina na bani ni zan kwashe daidai Maajid, sai Fa'izah ta so ni fiye da sonda nake mata in Allah Ya bamu tsawon rai da lafiya". Jinjina kai Maajid yayi, ta wani bangaren ya yarda ta wani bangaren bai yarda ba. "To da ka dire mata gwiwoyin a kasa, ka roketa me? Ta so ka?" Ya yi dariya ya ce, "Ina! Karewa ma kwarjini tayi min na kasa fadin abinda nayi niyya". Maajid bai san sanda ya fashe da dariya ba. "Amma ka ba da maza Pilot. Zan so ganin wace ce Fa'izar nan da zata ki namiji kamar ka ko yankar naman jikinta yake yi kullum, sai dai in ba mace bace. Tukunna ma cewa nake shekarun yarinyar basu fi ashirin ba? In har kana da tsokar zuciya a jikinka Abubakar, kuma kana son in yarda kai namiji ne mai mazakuta a jikinsa ba bonono kake mana ba mata-maza ne, ka share Fa'izah kayi kamar ka manta da al'amarinta kada ka koma inda take sai nan da (atleast) watanni uku. A kalla Fa'izah tayi haukarta ta gama ko da bata bari duka ba to 80% zai ragu tunda ta zame maka mutu-ka-raba daga kai har iyayenku. Sannan ne zaka neman sulhu cike da juriya da kai zuciya nesa, ka hadiye duk wani borenta so zallah zaka yi ta (portraying) ka zama kalar tausayi ka nuna baka da katabus sai yadda aka yi da kai, ka kwanta kace “in takani za kiyi to ga bayan taka”. Amma yanzu abinda yafi haka ma Fa'izah zata yi maka indai labarin da ka bani can baya da yanzu gaskiya ne, UWA ba abin wasa bace, ai na dauka ita kadai kayi ta yiwa shakiyancin. Tunda kace ita Maman (have reason with you) baka da matsala da ita kun fahimci juna tuntuni. Wacece Fa'izah? Me take takama dashi da zata ce bata son ka Fa'iz baya ga kyawun da take da shi? Me aka yi aka yi ta? Sai dai in muna-mata ce ba mace ba wadda tasan me ake so a namiji. Takamar diya mace kowacce iri ce kafin a daura mata aure ne, amma yanzu Fa'izah ta zama nama, bata da sauran abin tinkaho. Duk yawan kiyayyar ta fa muddin ta dauki ciki Fa'iz ta kare, domin a lokacin ne zata shiga fargabar ba zata so danta ya yi maraici ba, kuma ba zata so a kirata bazawara ba, ko kada ku rabu ta rabu da 'ya'yanta, Zata shiga tunanin yanzu fa ta zama (second-hand) ba zata je gidan da babu mace ba, kuma kasan ba son kishiyar nan suke yi ba, kuma idan ta fita, ba zata samo yaro kamar ka ba ko da ta samu mara mata din. Zata shiga fargabar me zata je ta tarar gidan mutumin nan dama ta zauna da wanda bata so din ita azo a tadda ita tunda ku zama da mace fiye da daya al'adarku ne. Kiyayyar diya mace tana da wasu magunguna guda uku wadanda in kana dasu, wallahi sunan kowacce diya mace "sorry" ko ko ince (finished product). Na farko mace na son yawan kyauta na abinda tafi so daga hannun mijinta, kyauta wadda zata ratsa mata zuciya ba gayan kudi ba. Sannan mace Allah ya yi ta da son a nuna an damu da ita, duk inda kake, ka nuna mata tana ranka kana tuna ta da so da kauna. Tana kuma son a darajja ta (kada ka nuna mata danginka sun fita, suna kuma kada ka nuna musu ta fisu) ka barwa kanka wani sirrin na zuciyar ka. Tana so ka kwantar da kai ka bata hakuri in ka bata mata rai. Da fari zata nuna shariya ne, amma zuciyarta sanyi take, tana hucewa a hankali. Idan ka matso 'yar kwalla zaka ji ta ce, "Shi kenan, ya wuce". In ka kawo kyautar nan in ranta yana bace zata ce, "Ni bai dameni ba" ko "bana so ka bar abinka" amma a cikin zuciyarta sonka karuwa yake yana fidda rassa. Haka kayi kokarin ka fahimci duk wani (likes and dislikes) dinta shima ka dage da gujewa/aikatawa. Ka rike amanarta, kada ka dinga zancenta da kowa ko da 'yan uwanka. Duk inda kake, ya zamanto kana yawan nemanta tare da nuna mata ita kadai ce a gabanka saurin mata basa burgeka ko da ba hakan bane (in reality) a zuciyarka. In kayi riko da wadannan Fa'iz kiyayyar Fa'iza komin girmanta babu inda zata je. Fa'eez ya dube shi cikin mamaki. "Who taught you all these?" Maajid ya yi murmushi. "Matar Yayana (psycologist) ce muna dasawa da ita sosai. Tana yawan bani 'theory' akan mata da abinda suke so. Ko baya ga haka ni ba irinka bane da inji kadai kasa gaba. (All work without play make jack dull boy) ina karance-karancen Novels domin samun nishadi (mostly authorized by women). Kuma ina soyayya da mata kala-kala a kasar mu. Ina zaunawa da kanne na mata ina jin hirarrakinsu da damuwoyin da suke ciki da mazajen su, ina sakar musu fuska ni ba (terror brother) bane irinka". Fa'iz ya kyabe baki ya ce, "In ka gama surutunka don Allah tashi muje mu samu (hotel) in kwanta in huta. Zazzabi ke neman rufeni sabida jinin dana zubar. An gaya ma Fa'izah na kamar sauran matan da ka fahimta ne? An gaya ma Fa'izah zata tsaya ta saurari mutum har yayi mata wani dogon sharhi in ta tsane shi? Koko an gaya maka Fa'izah abin hannun maza ya dameta da zan bata abu, ta amsa bata kwada mini ba? (Above all) ma ta yaya kake tunanin ni Abubakar Mukhtar zan yiwa mace kuka har in tsaya lallashinta ta samu kafar wulakanta ne?" Maajid ya kunna sigari ya dasa ma lebbansa, ya ce cikin murmushi. "Meye kuma ya rage baka yi ba? Yanzun nan fa ka gama ce min ka durkusa da gwiwoyinka a gaban Fa'izah ba matse maka baki nayi ba". "Tsugunno daban, kuka daban. Ko da na tsugunnawa Fa'izah bance mata komi ba balle inyi mata kwallah. Da in yiwa Fa'izah kwallah don ta so ni wallahi gara mun dauwama a haka. In na sami sararin aiki inje gidansu ko ta taga ne in leka in ganta in dawo bakin aiki na kada Allah Yasa ta biyonin, an gaya maka a matse nake da mace kamar ka?" Maajid ya fashe da dariya, ya ce. "Ba'a rabu da Bukar ba an haifi Habu. Amma da ka tabbata sakarai, haka kawai Allah Ya halatta maka abu ka haramtawa kanka? Fa'izah dai mace ce dake shekarun shekarunta na (teenager) ba abinda tafi bukata a yanzu irin kasancewa da namiji da zama gidan mijinta, musamman da kace duk tsararrakinta an kaisu dakin aure. Ka zauna nan kayi ta rikon aure, ta yi saurayi mai debe mata kewa koda da hira ne asarar wa?" Ya kai mishi wani mugun kutufo a kwibi, ya ja jakarsa keey...! Ya taka da gudu ya shige (lifter) ya barshi a baya. Fa'iz yayi tsaye kafafunshi harde da juna yana bin (lifter) da ta dauki Maajid zuwa sama da kallo har ya daina hango farar fatar Maajid da fararen kayansa da kwantaccen bakin gashin kansa na Larabawan Syria, yana mai auna maganganun da suka fito daga bakin Maajid din cikin ma'auni na hankali da tunani. Ya tabbata duk abinda Maajid ya fadi gaskiya ne, to amma ta yaya zai bullowa Fa'izah su kasance tare? Bama a gida Nigeria ba a duk inda ya sanya kafa? Barma (bomb) din da ya taho ya barota dashi ya fashe me zai je ya tarar bayan fashewar (bomb) din? Dole ya bi shawarar Maajid na tilasta kansa kin ganin Fa'izah da dosarta har bayan watanni uku kamar yadda Maajid ya ce. "Kai to kuma har wata uku! Wata uku fa ba kwana uku ba!! Fa'izah zata iya yin saurayi a tsayin lokacin. Yadda take kin shi din nan zata iya yin saurayin da zai debe mata kewar mataccen nata. Ya rike kanshi da hannunshi biyu yana girgizawa da sauri... "No! Babu mai barinta, iyayensu ba zasu bari wani abu ya taba mishi aure ba tunda tana tsakiyarsu. To itama bata da hankali ne? Ai aure yafi gaban wasa". A wannan karon hawayen kawai yake ganin idan ya yi (shading) zai samu sassaucin kishin da ya tokare shi ya hana shi hadiyar miyau. In kuma ya sake ya bari suka zubo ya tabbata Fa'izah ta maida shi kamar sauran maza da Maajid yake misali masu yiwa mace kuka don ta so su. Kada Allah Ya nuna masa wannan ranar. *** [18/02 2:48 PM] Sumayya Takori: A ZARIYA Na fito falo fes dani cikin doguwar rigar Momi, baki na kamar gonar auduga, ban zauna a ko daya daga cikin kujerun da suka yiwa falon kawanya ba sai a tsakinin Momi da Ya Rabi, suka dan matsa gefe suka bani fili a darare duk da ita Momi babu alamun jin tsorona a fuskarta, ta bani filin ne kada in dire akan cinyarta. Duk sai suka bani dariya, ga Aunty Rabi mai yi min kallon hauka sabon kamu. Na tsugunna gaban Momi da gwiwoyina biyu, na ce. "Don Allah Momi kiyi hakurdi ki yafe ni, duk bacin ran da na sanya ki da kashin kajin da na shafa miki na zama cikin gidanki ba tare da saninki ba. Wallahi ni kaina wani abin idan ina yi ban san sanda nake yinsa ba, ji nake kamar ana kitsa min shi a tsakar ka, bana cikin hayyaci na. Ya Rabi kema don Allah kiyi hakuri, kuma wallahi Momi bata san ina gidan nan ba". Nan suka dubeni baki bude kamar sunga wadda ta warke daga cuta. Yaya Rabi ta muskuta ta ce. "Yanzun kin kyauta kenan da abinda ki ka yiwa Yayanki da yazo miki sallama zai yi tafiya? Fa'izah kisan kai za kiyi? Kisan ma na mijinki dan uwanki, rabin jikinki? Fa'izah kina son gamawa da duniya lafiya da kike ta da hankulan rayukan iyaye da masu kaunarki akan sanin kanki?" Na kara kwantar da kai da kaskantar da murya sai ka rantse duk duniya ba za'a samu mai kirki na ba. "Kiyi hakuri Ya Rabi, komi ya wuce bi'izinillah. Tsakanina da Ya Fa'iz yanzu sai gaisuwar mutunci da mutuntawa, na bashi hakurin ciwon da na ji masa tunda YA SAKENI!". Rabi ta shiga salati tana sallallami tare da tafa hannuwa, kafin ta kai karshen salatinta take direwa ta dauko sabo. Kafin ta fashe da kuka ta ce. "Kin cuci kanki kin cuce mu Fa'izah, hakkin iyayenki da na Hajjah ba zai taba barinki zama lafiya ba. Kin bata wayonki, kin fita zakka cikin A.B, kin zame mana bakin bunu bata baibaya. Bace min da gani tun ban lallasaki ko na tattaka ki ba...". Ko a jikina wai an tsikari kakkausa. Sai na sa hannu biyu na mika mata takardar, Rabi ta mike tsaye kamar an fisgota ta fisgi takardar daga hannuna, na tabbata in na tsaya tabbas zata tattakanin, sai na mike tsam koma daki na murza key. Na shige cikin bargon Abdallah tunani dubu dari da hamsin ya aureni 70% na Dr. Nazir ne. Mutuwar shi ta dawo min danya, inama ana mutuwa a dawo! Ga damar da nake nema kwana da kwanaki ta samu, amma wanda nayi ta hakilon akansa mai sawa da hanawa ya yi ikonsa akansa. Na rufe ido ina kuka, tunanin kyakkyawar soyayyar mu cikin Jami'ar Bayero da wajenta ke gifta min filla-filla. Na yiwa Allah godiya da na zamo silar kimtsuwar Nazir Sani, ya kuma mutu akan niyyar AURE. Babu abinda zanyi domin nuna soyayyata a gareshi bayan nema masa rahma da gafarar Ubangiji a halin yanzu. Momi dai ban san halin da take ciki ba don bata yi magana ba, sunkuyar da kai tayi, sai Ya Rabi ke ta fadace-fadacenta wanda ko a kwala ta. Kukan rashin Nazir nake baka da zuci, na jiyo muryar Ya Rabi na cewa. "Shima Fa'iz ya yi karamin tunani, ba'a biyewa mace, da maza na biyewa mata da cikinmu babu wadda ba bazawara ba. Idan hankali ya bata shi ake sawa ya nemo shi, haka nan komai aka yi shi cikin fushi, sai anyi nadamar aikata shi". Ashe Momi na hawaye take yi, can na jiyo tata muryar tana fadin. "Yo ai shi kenan, sai ta yi ta zama idan zaman gidan iyaye dadi ne ga baligar mace. Duka sa'o'inta babu wanda ya ba da kunya sai Fa'izah Bakin Buni Bata Baibaya a cikin A.B. Fa'izah bata dauko zuciyata ba sam, zuciyata mai tsafta ce da ban taba kwana da wani a cikinta ba balle in tashi da shi tsayin shekaru a cikinta. Duk wanda yayi min ba dai-dai ba ko nice da gaskiya uzuri nake yi masa da ajizanci irin na dan Adam. Dukkanmu masu kuskure ne da gazawa a wani bangaren, balle Fa'iz akan Fa'izah ne kawai za'a ce bashi da kirki. Na kuma yi mishi uziri tun a wancan lokacin da rashin haxuwar jini ne kawai, ko cikin 'ya'yanka ba ma 'yan uwanka ba sai kaji wani yafi kwanta maka. Da babanta ya ce min Fa'iz ya ce Fa'izah yake so da aure jikina ya bani akwai wani al'amari mai girma tsakanin Fa'iz da Fa'izah da babu wanda ya sani sai Allah. Nayi addu'ar Allah Ya hadasu da alherin dake tare da junansu, Ya rabasu da sharrin juna Ya kuma sanya albarka a cikin aurensu. Amma ga abinda Fa'izah taga ya fiye mata, titsiye miji ya saketa. Ba zan yi mata baki ba sai dai duniya kanta makaranta ce mai azuzuwa kala-kala. Kuma na roke ki Rabi, kada ki sanya sunana cikin sha'anin nan, har gobe ni 'yar kallo ce a cikin al'amuran ku, ki bar iyayenta suyi hukuncin da ya dace da ita". Momi ta share hawaye. "Babu wadda ta baiwa uwarta kunya a cikin A.B sai Fa'izah don ta tabbatar muku da gaske ni bare ce a cikin ku...". "Ki bar fadin haka Aunty Maimuna". Rabi ta katseta cikin jin tausayi. "Dole ince haka Rabi, shin da me zan doshi babanta da shi yau ya yarda ban san da zaman Fa'izah cikin gidana ba? Duk muna zaune aka yi saki akan idonmu, wallahi duk mu za su dorawa laifi...". Bata idasa maganarta ba tayi shiru saboda sallamar Baba. Prof. Ahmadu A.B, ya shigo da sallama, duk ya rame yayi duhu saboda tashin hankalin rashin sanin halin da nake ciki, da kuma ina na shiga. Ya samu kujera gefen Momi na ya zauna, ya ce. "Wash Allah! Taimaka mini da ruwa mai sanyi Mainmunatu". Momi ta mike tayi (kitchen) don ta kawo masa ruwan, sai a lokacin ne ya lura da autar Hajja a gefe, ya ce. "A'ah! Rabi yaushe a garin? Kin zo kuma kin tadda tashin hankalin da diyarki ta saka mu ciki ko? Fa'izah ta bani kunya, ta bada min kasa a ido. Ban taba zaton tana da wannan halin ba na kafiya da kekasasshiyar zuciya wanda ba'a taba samun irinshi a zuri'ar A'B ba. Sai dai ta wani bangaren na yi mata uzuri tunda ance Barewa bata yi gudu danta ya yi rarrafe ba, kuma duk abinda ka yiwa iyayenka ko bajima ko ba dade naka 'ya'yan za suyi maka (auren Momi da yayi ba tare da yardar nashi iyayen ba). Allah Ka bamu ikon yiwa iyayen mu biyayya, ameen. Rabi ta ce, "Ai tana nan cikin gidan dakin Abdallah, ba wani waje taje ba. Sai dai Fa'iz din yazo ya saketa har nan". Baba ya zabura ya mike, "What! Shi Fa'izun ne ya yi mana haka? Duk ta da hakarkarin da nake yi akan auren nan, tunda aka fara maganar auren nan bamu ci abinci ni da ubansa ya fada mana ba, shi ne ya biyewa shirmenta?" Momi ta karaso da gorar ruwan 'Rogolis' da tambulan din karau a hannunta da gorar lemon (5alive) ta aje a gefe don tasan bacin ran da Baba ya samu kansa a ciki ba zai barshi ya sha ruwannan da yake son sha ba. Bacin ran ya kashe kishirwar. Ta ce, "Kada kaga laifinsa Baban Abdallah, ta nemi rabashi da ransa in bai saketan ba me zai yi mata ya ceci kansa? Rotsa masa kwalba tayi aka fa?" Baba ya mike yana salati, ya kara da. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Tana ina tambadaddiya ku gani in babballata itama jikinta ya gaya mata, kisan kai zata yi? Shi kuma ya tsaya yana kallonta?" Rabi ta tabbatar muddin na shiga hannun Baba a wannan lokacin sai tarihina yadda komi nashi yake tsima kamar ana kada mishi gangi, don haka ta tare kofar dakin Abdallah tana fadin. "Yo Yaya in ka daki Fa'izah a yanzu aikin me aka yi? Wacce riba za'a ci? Baka huce ba tunda aikin gama ya gama, bakin alkalami ya bushe. Mu duba takardar idan ya yi na Musulunci ayi kokarin gyarawa". Ta shiga wurga ido neman inda ta cilla takardar saboda tashin hankali, kafin ta ganota a tsakanin kujerar da take zaune. Baba da kyar ya zauna a kujerar da ya mike sai wata irin zufa yake yi, makwallatonsa na kaiwa da komowa, duk ilahirin jikinshi rawa yake. Ya karbi takarda daga hannun Rabi ya warware, ga abinda dansa Fa'izu Abubakar ya rubuta cikin takardar. Baban Giwa ko Baban A.B.U. Fa'izah ta takura min in saketa alhalin ban iya hakan ko giyar wake na sha. Igiyar aure dai kowa ya sani uku ce, to ni Fa'izu Mukhtar Abubakar na ninka (ribanya) igiyoyin aurenmu da matata Fa'izah Ahmad Abubakar ukku sau uku =(9) kenan. A kara tausar Fa'izah don Allah kada wanda ya kara dukanta indai akaina ne, domin nayi mata laifin da na cancanci horo daga gareta fiye da wannan da take mani. Ko kun manta baya? Na tafi kasar Ingila saina dawo a san abin yi. Danku, mai neman albarkar ku. Fa'eez Giwa. Nan da nan Baba ya washe baki yana dariya, ya kuma mikawa Rabi takarda. Cikin zumudi ta karbi takardar tun kan ta gama taya yayanta dariyar farin-cikin da yake yi, tun kafin ta kare karantawa take dariya har ta gama. Kana ta mikawa Momina itama ta karanta duk suka sa dariya. Rabi ta ce, "Aje a hakan, kada wanda ya ce mata ba haka ba. In ya dawo ya fada mata da kansa ". Baba ya yi dariya a zuciyarsa hamdala kawai yake yi. Ya dauki ruwansa da Momi ta aje masa wanda ya kasa sha ya shanye tas, ya dau mukullin motarsa ya fice zuwa masallaci. Ya Rabi ta kalmashe takarda cikin jakarta ta shigo dakin da nake tana yatsina fuska. "To Gimbiyar bala'i, in kin ga dama ki taso mu wuce Giwa tare ko hankalin gyatumar bayin Allah Ya kwanta, jininta da ya hau ya sauka saboda kaunar ki alhalin ke din ba kya son kowa sai kanki, har kuwa da iyayen da suka yi nakudar ki suka haife ki. Gobe ake yinin Ummi bai kamata ace babu ke ake yi ba koda yake ke zakka ce". Na yunkura ina fadin, "Zuwa kai kamar da kasa, sai dai wallahi ba zan kwana gidan Hajjah ba sai dai gidan Baba Na'ibi?". Ta ce, "Yanda kike so ai haka za'ayi miki don kam kinfi karfin kowa". *** A GIWA Washegarin ranar ya kama yinin bikin Ummi. Ni, amaryar kanta da Zanirah da sauran kawayen amarya duka gidan Baba Na'ibi muka kwana. Babu wanda ya nuna min wani canji ko a fuska ko a mu'amala kamar komi bai faru ba, ashe Ya Rabi ta bi ta bayan gida ne ta yiwa kowa bayanin yadda abin yake. Duk da babu wanda ya nuna min wani abu ko alamar jin haushi ko ta da abinda ya gabata ni din akan kaina jina nake wani irin sukuku! Duk jina nake kamar bare a cikinsu, kuma kenan ashe abinda nayi din ban kyauta ba kenan tunda nake jin kaina matsayin mai laifi a garesu da babu wanda ya budi baki ya ce nayi laifin. Gani nake kamar dukkansu A.B kallon tsana da kyama suke min tunda na ki dan uwansu na kawo sauyin al'amari cikin zuri'ar su wanda tun Ahmadu A.B shekaru ashirin da uku a baya ba'a samu kwatankwacin sa ba. Ummi sai faman ja na take a jiki, dinkuna ma duk iri daya tayi mana, wanda duk tasa nima shi take takura min in sanya, dai-dai da kalar agogo bata bambanta ba. Zanirah kam wani baya-baya take dani tare da yi min wani gani-gani, ni dai naki yarda in biye mata tunda ta samu labarin cin zarafin da na yiwa Yayanta ta koma min haka. Ba na yarda in nuna nasan tana yi ma duk da raina baya yi min dadi. Allah wadaran surutun Ya Rabi. 'Yan uwa da abokan arziki kowa yazo yadda yake kiran Ummi da "Amarya" haka nima suke kirana, amsawa nake da karfin gwiwata tunda nasan ina da 'guarantee'. Su Walida, Hanifa, Maryam manyan kanne kirazan biki sun kasa zaune sun kasa tsaye, sunyi ankon shadda ruwan zuma da bakin gwaggwaro sunyi kyau matuka. Walida idan muka hadu da ita ta takarkare tana rabon abinci sai ka rantse da Allah bikinta ne ko nawa, saboda rawar kai da rawar kafa. Ashe Walida tasan komai, ni ina mata dariya itama a ranta ni take yiwa. Ummi ce ta gargadeta kada ta sake aji mutuwar sarki a bakinta. Da yamma can goshin magariba muna sanye da wani (swiss-lace) mara nauyi ni da Ummi (turquise blue). Jama'a sun fara bajewa don gab ake da kiran sallar magariba a falon Aunty Zainab, Ummi zaune a gefe tare da sauran kawayenmu, hatta Haulatu ta halarci bikin Ummi, Naja'atu da Zubaida duk suna falon ana ta zuba hira. Ni ina gefe kwance a doguwar kujera, Fa'izah ce akan ruwan cikina diyar Yaya Aliyu ina mata wasa tana ta dariya. Yayin da Zanirah tana zaune da zungureren cikinta a gaba tana faman zuba (souvenirs) a leda ita da su Haulatu, kowacce da abinda take zubawa a leda wata kek, wata meat pie, wata cincin, wata soyayyen nama suna dai yin kullin nasu cikin tsari mai burgewa. Walida ta shigo ta ce wai muje inji Yaya Bashir duk mu ukun yana dakinsu na da na gidan Hajjah. Gaba daya muka mike, Ummi aka sake gyara goggoro aka duba madubi aka dauki (spray) aka feshe jiki, tuni dakin ya dume da kamshi mai dadi. Aka sa hoda aka fente fuska, nan da nan ta hau sheki. Nayi dariya na ce, "Iyen ba! Kaga amaren babban Yaya, haduwar ba sauki". Ta kyabe baki ta ce, "Ohon miki! Kece gwauruwa, sai ki zuba mana ido in munyi 'ya'ya kunyi kai daya sai ku ci naku zamanin tare dasu ko?" Na ce, "Ina! Ta Allah ba taki ba. Allah Ya kiyaye insha Allah nima bazan kara shekara gidan iyayena ba Allah Zai kawo min nagari na kowa, kuma zabin zuciyata". Da hirarrakin da muka karasa dakin su Yaya Bashir kenan. Ummi ta faki idona tayi min gwalo. A tare muka yi sallama Yaya Bashir ya amsa, kowaccenmu ta samu kujera ta zauna. Yaya Bashir na fadin. "Ummi tawa dawo nan mana". Yana nuna kusa dashi. Tayi murmushi tana sunkui da kai, bata amsa tayin nashi ba ta zauna a gefena, shi da Yaya Aliyu ne, wanda tsam ya taso daga inda yake zaune ya zauna a masangalin da Zanirah ke zaune ya zauna cike da kulawa yake tambayarta. "How is my baby kicking?" Cikin murmushi ta amsa, "Gashi nan yana ta yi kamar zai kwance min zani". Murmushi yayi suka ci gaba da hirarsu. Bashir ya taso daga inda yake ya nuna min kujerar da ya mike. "Ke gwauruwa, ja jiki ki bani wurin zama kusa da mata ta mana". Sum-sum-sum na mike na bashi kusa da matarshi, a zuciyata ina da na sanin biyo su don kamar da gayya suke yi, don su ci min fuska. Sai dai tun can ina girmama Yaya Bashir, saboda yadda baya nuna bambanci tsakaninmu da Zanirah da kowa cikin gidan Hajjah. Na hada hannuwana biyu na tallabe haba ina kallon su suna barkwancinsu suna dariya, babu wanda ya damu da ni, kamar ma sun manta da ni a dakin. Takaici ya isheni, na mike zan fita, Aliyu ya ja gefen zani na zan gifta su. Na juyo amma ban yi magana ba. "Dama ba wani abu yasa aka yi kiran tare da ke ba, maganar liyafar Kaduna ce ta gobe, mu zamu sa ankon shadda (hilton) da su Ummi, ke kuma tunda kin saki naki auren (don bana ce an sake ki ba) sai kisa wannan". Ya nuna min leda bacco shake taf da kaya. "A wajen Maman Kaduna na amso miki cikin kayan da tsohon mijinki yayi niyyar baki tsiya ta hanaki kwantar da kai ki ci arziki, ya tattara ya barki bayan ya dankara miki sakin wulakanci tara rigis! Wai 3x3 =9. In basu yi miki ba ki fada aje a buda a canjo miki don babu abinda zai yi da su, in zai yi sabon aure na tabbata sababbi zai yiwa sabuwar matar duk da nasan ko zai yi ba nan kusa ba, don kinsan matuka jirgi mata ba damunsu suka yi ba, kullum a tsaye suke kwana cikin iska, ba lallai ya damu da yin aure nan kusa ba". Suka kwashe da dariya baki daya. Kallon Yaya Aliyu kawai nake yi ina lissafa shi cikin sahun boyayyun makiyana wadanda ke sanye da fatar damisa suna (pretending) ta akuya ce. Yaushe Yaya Aliyu ya koma haka? Yaushe ya zabi Fa'iz ya barni? Hawaye suka zubo min wadanda duk kokarina na kasa maida su. Naso insa kai in wuce ba tare da na ce dasu komai ba, amma zuciyata ta ki amincewa ko da ban iya na rama ba, bazan nuna karaya ba. "Koda bani da wanda zan aura a halin yanzu, nafi karfin suturar da zan sanya a jikina. Allah Ya hore min abinda zan dinka ma kaina inyi fitar bikin Ummi ko da bai kai nasu tsada ba a kalla dai ba za'a ce an ganni tsirara ba. Don haka ba sai na daura na Fa'izun ba, ko a sanda yake mijina bai yi arzikin da zai dinka min sutura ba, ya baro yi min sutura a sanda nake da bukatarta balle yanzu da igiyar ta tsitstsinke, alakar ta bi rariya. Don haka Yaya Aliyu, ina ganin ku nemo wanda za kuyiwa gorin sutura ba dai ni Fa'izar ba". [18/02 4:11 PM] Sumayya Takori: Suka sake kwashewa da dariya alamar 'game' din nayi masu dadi dukkansu. "Sai Hajiya Fa'izah!!!". Suka ajiye jinjina da hannayensu. Ganin sun mai da ni mahaukaciya na fito na barsu ina matsar hawaye zuwa falon Aunty Zainab. Fa'izah baby ke ja min zani, ban san sanda na tureta ta fadi gefe tana kuka ba. Aunty Zainab Maman Yaya Aliyu ta tare ni tana tambayar me ya faru nake kuka? Ina kuka na zayyane mata wulakancin da suka yi mani dukkansu. Ta ce, "Fa'izah duk ke kika jawowa kanki. Da kin kwantar da hankalinki da Fa'izu da duk hakan bata faru ba. Kin san dai duk cikinsu Fa'iz ya fisu komai har shi yayan kobon (Aliyun). Amma ki ka rufe ido ki ka badawa idonki toka da bala'i da rashin arziki har ya gaji ya tafi ya barki. Don haka baki da hujjar jin haushin su Ummi ko mazajensu anan". Kokari nake in danne tasirin maganganun Aunty Zainab a zuciyata ta hanyar turawa gidan Hajjah a dauko min wani tsalelen leshi na (pitch colour) asalin shi marigayi N.S ya dinka mani kudinshi sun kai Naira dubu tamanin da biyar, ya dinka min shi ne wai inyi fitar fatin bikin shekarar haihuwar wani abokinsa da aka yi a Kano mai suna Dr. Gadanya. To a lokacin a ranar sai na tashi da zazzabi, dalilin rashin zuwana kenan na linke na goge leshin na boye can kasan kayana. Ina da takalmi da jaka 'yan (Thailand) suma mahadin leshin duk ban taba sanyawa ba. Abinda yayi mani cikas inda zan samu goggoro ba tare da na kula wadanda muka yi amfani dasu a yau ba. A take na dau mayafi na fita, naje saloon aka gyara min kai da (setting) na burgewa na kuma je aka nado min goggoron yadda nake son shi (light pitch) aka yi min gyaran akaifa da wankin kafa nayi sumul da ni. Na dawo gida na kulle kaina cikin kallabi kai ba zaka ce an taba shi ba na hada kayan da goggoron na boye a sif din Aunty Zainab. Wurin sha biyun dare barci ya soma fizgata sannan su Ummi suka shigo ina kwance a gado, ta cire goggoronta ta kwado min, shi kansa goggoron kamshin turaren Bashir yake yi. Na ja wani wawan tsaki na ture goggoron daga kusa dani, ko me zan jiwa haushin oho! Tana so ta gaya min ne ta hada jiki da namiji, ko me zan jiwa haushin oho! Banza an bata sidin turawa shi ne zata zo ta yiwa mutane fiffika, har warin tabar da aka ce yaya Bashir yana sha take yi. "Banza mahaukaciya". Ban san sanda furucin ya amayo daga cikina ba. Tayi dariya ta ce, "Duk haukana ai ban kai ki ba. Yaya Bash ya ce a gaya miki kada ki samu damuwar rashin (partner) gobe don 'couple evening' ne za'ayi miki mijin roba da yaya Sa'id Ibrahim Bamalli". Ashariya naso danno mata, amma sai na fasa. Ta cancanci bakar magana itama, don haka nayi gyaran murya daga kwance. "Babban hauka ya wuce ka kaiwa miji kanka a soron gidan iyaye? Don haka ban fiki hauka ba, ke naki salon na zamani ne, nawa kuwa (old-fashioned) ne. Ni kam ku bar mijin robar ku na yafe ba a matse nake da namiji ba da har sai nayi riga malam masallaci. Party ba don kowa zani ba, sai don kar ku dauka wulakancin ku da cin fuskar ku ya hana ni sakewa ne ko ina bakin cikin rashin miji har hakan ya hana ni shiga mutane, ina fatan kin gane?" Ummi ta tafa hannu tayi dan fitoo, ta ce. "Yeho! Yarinya wallahi kinci a baki kyautar amsarki. Indai wannan shi ne hauka, don Allah a nada min sarautar mahaukatan duniya akan umarnin iyayena nake ba kuma zan taba ganin ba dai-dai ba, tunda na bisu, su nakewa biyayya. Ke kuma mai hankalin da yafi na kowa da kika tasarma kisan kai fa? Waima tukunna ina hankali ga matar da ta titsiye mijinta da duka da zagi ya saketa? Matar da ta dauki kwalba ta rotsawa mijinta ai ta tabbata tsinanniya". (Baki kasan me zaka fada baka san me za'a mayar maka ba-TAKORI). Zaneerah ma aka cire mayafi aka jefo min. Eh naji kamshin (212) din yaya Aliyu kam babu shakka amma itama ta cancanci a tanka ta duk dai da ban san ita din dame zata mayar min ba. "An dai ji kunya wallahi, tsofai-tsofai ga goyo ga tirtsetsen ciki amma ba'a fasa jaraba ba, shima Yaya Aliyun...". Daga labulen dakin yayi yana fadin. "Zaneerah ina wayata da na baki ki sa min caji?" Dif! Kake ji na dauke wuta, kamar ba ni ce mai magana ba. Ya dube mu suna ta sheka dariya kamar sun samu motsatstsiya ya ce. "Me take cewa ne?" Na mike gaba-gadi na dauki dankwalina na daura na bar musu dakin. Ina jinta tana cewa dashi. "Zaginmu take yi". Ya ce, "Baya tsiro ai, da tuni jikin nata mijin ba masaka tsinke". *** Washegari tun safe su Ummi ke shirin wucewa Kaduna liyafa, sai shirya kaya ake ana zuge (troller). Motocin da za su kwashe su zuwa Jabi Road basu zo ba sai bayan azahar suka shiga suka tafi da kawayenmu duka daga can ne za su shirya zuwa wajen da aka tanada don yin liyafar. Ina kwance a doguwar kujera ban ko motsa ba ina kallon fitarsu daya bayan daya. Yaya Aliyu ya shigo yana balle 'links' din hannun rigarshi ya ce da Zanirah. "Madam, muje ko?" Ta tashi wata tikisa da ita kamar alkubus, shi kuma aka sakalo hannu kugunta aka tallafeta, a haka suka fice ko kallona basu yi ba, suka fice. Inda ya bude mata gaban 'Porsche' dinsa ta shiga, ya rufe ya zagaya shima ya shige. Bashir aka kama hannun amarya mai kama da Princess Diana don kyau da daukar ado suka fice. Har sun kai kofa ya juyo yana ce da ni. "Af, gwauruwa, mijin robarki fa yana jiranki a waje Yaya Sa'idu, an baki kaya don kidifiri kin ki amsa. No worries, na jikinki ma inaga ba laifi, kya samu waje ko tebirin iyaye da su". Wani gululu yazo ya tokare ni yaki wucewa, ya tsaya min a makoshi, amma Fa'izah (is always) Fa'izah, ina da 'ki-fadi' sai na ce. "Allah Sarki Yaya Bashir ka sallami mijin robar Fa'izah ko babu shi Fa'izah (can survive), kasan mace Allah Ya yi mata juriyar iya rayuwa ba tare da namiji ba, namijin ne bai iya rayuwa mai dadi sai da mace. I.e namiji zai saki mace, ta zauna gidan iyayenta ba tare da ta yi wani auren ba kuma ta zauna lafiya. Amma shi namiji a ranar da yayi sakin ma zai iya kawo wata, ka gane?" Ya ce, "Ohonki kuma! Tsoron shan kunya ya hanaki zuwa (party) baki da sauran bakin surutu". Da haka ya fice. Na mike tsam bayan fitarsu nayi wanka, na dauko lesi na na sanya, na saki dogon gashina a gadon bayana, na karkata goggoro na tsayar dashi dai dai goshi na. Na janyo takalmi da jaka na cikin kwalinsu mai tudun dunduniya siririya da siririyar igiyar daurewa na fitar na sanya, na rike 'purse' din mahadinsa wadda kudin mota kawai na zube a ciki. Nan da nan na hau walkiya kamar wata dan daren goma sha hudu. Na kawo (fashion earing) kalar adon lesin na daura (shimmering pearls) hannu, wuya, kunne da idon sawu sai walainiya nake duk motsin da nayi. Ni kaina yau nayi mamakin yadda nake, ban taba tunanin haka Allah Ya kyautata surata ba sai yau. Na fito harabar gidan Baba Na'ibi babu kowa don haka na tura wani almajiri yayo min hayar taxi kafin minti goma sai gashi ya dawo cikin motar tare da mai taxin. Na ce da mai taxin ya yi duk iya gudun da zai iya ya kaini (Indoor-sport hall) na garin Kaduna cikin awa daya, ko nawa ne zan biya shi. Nan da nan ya ce in shigo mu tafi. Dakin taron ya cika ya batse babu masaka tsinke da kyawawan iyalin A.B tabbacin a yau mallawan na biki kasurgumi da basu taba yin kwatankwacinsa ba. A cikin tafiyar nutsuwa na shiga ratsa taron jama'ar suna kallona tabbacin basu tsammaci zuwana ba ma balle wannan shiga ta firgitarwa. Ashe wajen cike yake da abokan Fa'eez na Kad-Poly irin su Surajo Nuhu wanda a halin yanzu ma'aikaci ne a Central Bank da wasu daga cikin abokan su da yawa suka mike suka tarboni muka jero tare sai tafi suke yi da dariyar farin ciki, yayin da Sa'adu Bori dake cin kasuwarsa a wajen ya karkatar da akalar wakarsa gareni ya kyale su Ummi, cewa yake. "TAKAWARKI LAFIYA GIMBIYAR ABUBAKAR FA'IZU GIWA... AMARYA FA'IZA AMANAR FA'IZ GIWA...". Suraj tunda na tako kafata cikin (hall) din yake min (spraying) da dollers madadin Fa'izun su kenan. Ni kam ko a jikina, a raina fadi nake wahala ce bata ishe ku ba, ko kallo basu isheni ba. Wajen ya hautsine da kirarin abokan Fa'iz masu video da masu camera suka juyo da akalarsu kanmu gaba daya abokan Fa'iz daukana suke hotuna wasu vedio da wayoyinsu. Ina kallon bakin su Yaya Aliyu dake (high-table) yaki rufuwa, haka Mama da tarin hamshakan matan Kaduna da ta gayyato. Anan Yaya Rabi, Aunty Hauwa da Mama da kanta suka taso suka tarbeni suka hana ni isa ga mazaunin su Ummi. Girgiza kai nake cikin son kecewa da kuka ina yi musu nuni da ka su barni in wuce, amma sunki hakan. Mama ta rikeni gam-gam, haka Ummi da Bashir, Zanirah da Yaya Aliyu tasowa suka yi daga mazauninsu ya saura babu kowa a gaban Sa'adu bori cikin filin sai mu 'ya'ya da jikokin Hajjah da kawayen Maman Kaduna sai ko Surajo da ya rufa min asiri suka shiga yi mana "spraying" ni da Surajo sai ka rantse da Allah shi ne angon nawa, kazalika Ummi da Bashir, Zanira da tirtsetsen cikinta da Yaya Aliyu rungume da ita, duk suka bude bakin jaka suka shiga yi mana 'spray' tako'ina. Dadi ne ko mene ne ya yi min yawa, sai gani kuka ya kece mani. Tausayin Mama har kokon raina da jinjina kaunar da take mani na kasa jurewa nima ban san dalilin tausayin nata da ya rufeni ba, na zame da gudu na karasa mazaunin su Ummi na zauna na kifa kaina a tebirin na shiga kuka mai yawan gaske wanda ni kaina bansan dalilinsa ba. Suraj ne yazo ya zauna a kujerar Yaya Bashir ya ce. "Fa'izah, Fa'iz bai kyauta ba na sani, don me ya yi mana haka? Rana irin wannan mai dumbin tarihi ka tsallake ka tafi wani aiki kai kafi kowa aiki?" Haushinsa ya kara kamani da shisshigin da yake ta yi mini tunda na sako kafata a filin wajen nan shi bai yadda ba asiri ya rufawa abokinsa, kuma abin kirki yayi. Na dago idanuna jike jagab da hawaye, "Kada ka kuma yi min zancen wani Fa'iz, nazo (partyn) nan ne don Ummi da Bashir, don me zaka zo kana tambaya ta wani Fa'iz bayan mun rabu tuntuni?" Dariya Surajo ya yi, "Aradu bonono Fa'iz yayi miki wai rufe kofa da barawo, waye ya ce miki Fa'iz zai iya sakin ki? Ko jiya shi ya kirani daga England ya ce in taimake shi inzo in tsaya tare da ke, bai yarda da kowa ba cikin abokanmu sai ni. Wane irin saki babu ko dadin ji? Kina hauka ne?" Wani irin rugugi naji cikin kwanyar kaina, da kyar in ba motsin kwakwalwa bane. Na zazzaro ido ina duban Surajo ina auna abinda yake fadi cikin hankali da tunani. Nasan Surajo mutum ne mara wasa, na sanshi da can don ya so Ummi aka nuna ba za'a bashi ba ya hakura. Abubuwan da suka faru suka shiga dawo min sabbi kar, wato yanayin Fa'iz bai nuna damuwa ko bacin rai ba a sanda yake min rubutun cikin takarda, babu wata alama ta nuna damuwa a fuskarshi. Me ya hana Baba bai lallasa ni ba, kuma su Aunty Rabi babu wanda ya yi fushi dani a lokacin? Sai ma cewa da tayi in taso mu tafi bikin Ummi Giwa? Me ya hana ni karanta takardar da kaina abin kamar tsafi?" Raina ya yi mugun baci, hankalina ya jirkice, idanuna suka kada suka yi jawur suka wani irin cicciko da kwalla. Suraj Nuhu, ya yi danasanin karambaninsa, ya tabbatar ya yi babban kwafsi, kuma abinda ba'a aike shi ba don son ya burge. Ya shiga in-ina yana fadin. "Fa'izah da gangan nake, na rantse miki bamu yi maganar komi da Fa'iz ba, ni na kawo kaina...". Ina! Surajo ya barota domin kuwa mikewa nayi gaba dayana tsam nayi hanyar fita, yayin da ya biyoni yana magiyar in saurare shi, amma kurar da ta debo shi ban kalla ba. Su Ummi suka dakata da abinda suke yi suka biyo mu da idanu. Aliyu ya saki hannun matar shi ya biyo bayanmu, ya riqo hannun Suraj ya ce ya rabu dani, kana ya haushi da fadan. "Don me yasa ka gaya mata Surajo? Wa ya aike ka yi mata zancen Fa'iz? Ka san haukar Fa'iza kuwa? Muna zaman zamanmu lafiya ka sayo mana tashin hankali". Surajo cikin matsananciyar nadama ya ce. "Ni ina na sani? Na gaya mata ne kawai Fa'iz ne ya yi min waya cewar yana Wales inzo in tsaya da ita, shi kenan abinda na fada". Yaya Aliyu ya dafe kai yana fadin, "Shi kenan Surajo ka baro mana likin, sai gyaran Allah. Wallahi ko lallashi ba zan je ba ta je can duk inda zata je zata dawo da kafafunta, ai ba yau ta fara ba”. Da daren washegari aka raka Ummi gidanta a Kabala Custain. Washegari Zanirah da Aliyu da ‘yarsu Fa'izah suka wuce Lagos, na Giwa suka nufi Giwa, na Zaria ma haka, haka na Kaduna. Miftahu da Ya Rabi suma suka dauki hanyar Kano da yaransu biyu, amma Ya Rabi ta ce da Yaya Mufty su tsaya Zaria su ga halin da nake ciki. Hajja kam ta ce da su don Allah kowa ya kyale ni inyi kida na da rawata ni kadai, kada wanda yaje inda nake balle ya wani lallasheni in bata masa rai a banza. Amma Ya Rabi ta kasa jurewa. Ko cikin 'ya'ya Fa'iza ta daban ce a wurinta, tana da matsayin da babu mai shi cikin tarin 'ya'yan nata. *** Da na baro Indoor Sport Hall Zaria na nufa a taxi bana ko ganin abinda yake gabana don tsananin takaici da tashin hankali. Fatana inga takardar sakin nan nawa da idanuna in karanta abinda ke ciki. Har aka zo kofar gidanmu ban sani ba ina sharar hawaye da dankwalin leshi na, sai da mai taxi ya ce. "Hajiya, ba nan ne gidan ba?" Na bude na fita na fiddo kudin da ban tsaya kirgawa ba na dai tabbatar yafi abinda zai nema na zube mishi a kujerar gaba nayi ciki. Na danna kararrawa (door bell) Momi ta zo ta bude duka hannuwanta cude da fulawa ina jin alkubus take yi. Ganina haka hajaran majaran fuska babu alamun rahama ta tabbatar cikin ranta da kyar in ba (bomb) din ne ya tashi ba. Ta matsa min hanya na shige, ta koma kicin ta ci gaba da aikinta. Gidan babu kowa sai Walid autan Momi, duk suna Kaduna cin biki. Na fadi nan bisa carpet na shiga kururuwa kamar na rasa iyayena biyu a lokaci daya. Momi bata ce min cikanki ba, haka ko lekowa bata yi ba. Wannan ya kara kunna ni, na mike na shiga tamaula da kayan falon su filillikan kujera, flower rose. Ganin ina shirin yi mata ta'adi da kayan kallonta ta fito a fusace ta nuna ni da yatsa. "Wallahi-wallahi ki kiyayeni cikin gidan nan, kinga dai babu kowa, babu mai kwatar ki don haka sai inyi miki dukan tsiyan da zai taimaka ya dawo dake cikin hankalinki, don da alama Fa'izah ke dabba ce, dabbar ma ta daji wadda bata san ciwon kanta ba. Allah Yasa Fa'izu yankan kai yake yi, ya yanke naki kowa ya huta wannan bala'in". Na hade kaina cikin gwiwa bayan nayi fatali da goggoron. "Momi bai kamata kice min haka ba, duk abin nan da nake yi saboda in kare mutunci da martabar ki ne daga idanun wanda bai san kina da su ba, don ni ta tawa mai sauki ce ban dauki kaina a bakin komai ba balle in dauki wulakancin da Fa'iz ya shekara yi mini abinda zai hana ni shakar numfashi a duniya. Ba zan taba son shi ba Momi, ba zan taba ganin farinshi ba tunda ya wareki daga cikin iyayensa. Duk abinda yayi min a baya kin manta Momi...". "...Na manta don ubanki, sai ki sani in tuna! Wallahi ki ka sake yi min kururuwa a gida sai na kakkarya ki, kin kuma koma inda ki ka fito kinji na gaya miki". Sai na tura kai cikin kafafuna nayi ta rasgas kuka a hankali, babu mai lallashi balle wanda zan yiwa in huce. A kuma yanayin Momi na na tabbata zata aikata abinda ta fadi na sake na sake daga mata sauti. A haka Babana ya taddani, ya zauna cikin kujera yana fadar. "Kiyi kukanki mai dalili, yi kukanki da babbar murya Fa'izu bai sake ki ba! Da yake shi ya haifu cikin uwa da ubanshi ya san darajar iyayenshi da karfin ikon su a kansa. Allah Ya dawo dashi lafiya kafarki kafarsa, inda duk ya sanya kafa na rantse da wanda raina yake hannunsa". *** Kwana biyu aikina kenan ina abinda naga shine rangwame a gareni wato (kuka) duk na koma jemammiyata ta baya a dakin Abdallah. A haka ne Ya Rabi da Ya Mufty, kan hanyarsu ta komawa Kano sai gasu a Zaria, Aunty Rabi ta shigo ta iskeni dakin Abdallah, ta aje mayafinta da babynta akan gadon Abdallah, ta ce. "Kai! Fa'izah bakya gajiya, zuciyarki bata gajiya da kuntatawa kanta a banza a wofi alhalin hakan ba zai sa ba, kuma ba zai hana ba! Shin duka wannan na kiyayyar ne, ko na haushin Fa'iz dan albarka bai yi saki ba?" Nayi banza da ita, can kuma na ce. "Ki bani takardar in gani da idanuna". Da murmushi fal a fuskarta ta ciro takardar a jakarta ta ce. "Gata". "Don haka in zaki hutar da kanki da zuciyarki to ki hutar, in kuma kina ganin kukan ki da tayar da hakarkari da hankalin ki shi zai sa Fa'eez ya yi saki to anan kam kinyi kuskure. Haka in ma duka da kwalba ne shima aikin banza za kiyi tayi don kuwa Fa'iz jinin Hajjah ne, rabin zuciyarta, magajinta. Idan ya ce 'eh' baya taba dawowa ya ce, 'a'ah'. Shin don Allah in tambaye ki, meye abin ki ga Fa'iz?" Na dago sharkaf da zufa, kashirban da hawaye da majina bayan na karanta takardar. "Ai ba zaku taba gano aibunshi dani nake hangowa ba tunda danku ne, ba kuma ka taba ganin aibun danka komin muninshi ko munin halinshi. To tunda ba zaku gani ba da duk hujjar da na kawo to ni na tsane shi ne, bana sonsa, fakat! Da inyi zaman aure dashi gara min zama a dokar daji da bakin-kumurci. Allah da Ya halicce ni Shi Ya daura min kiyayyarsa da duk wani mai irin halayyarshi. Yadda kuma ake ikirarin shi jinin Hajja ne baya magana biyu sai a gaya min in ni tawa uwar shege na tayi ta kawo muku". Ya Rabi ta jinjina kai cikin kidima tana fadin. "Babbar magana. Ni na kawo kaina, dama ba yadda Hajja bata yi dani ba kar nazo ke mahaukaciya ce amma banji maganar uwata ba dole naji wohoho! Sai ki mutu kuwa! Muddin Fa'iz ya dawo kafarki-kafarshi zuwa Russia, wallahi nima na daina lallaminki, mu zuba mu dake aga wanda ya haifi wani. Dabba kawai, shashasha, mara hankali". Na ce, "Ko uwar Rasha ne ba zani ba, wallahi ba zani ba ko gunduwa-gunduwa za'ayi dani". Rabi tayi dariya, "Ai har uwar Rashar ma zaki, tunda matukin jirgi kike aure ina ne ba za'a saka ki a jirgi a kaiki ba?" Na ce, "Koda na rasa bawan Allah Dr. Nazir, mai ilimin da ya amsa sunan ilimi, banga me zanyi da direba ba Ya Rabi. Kamar ni in kare a mutumin da bai da ilimin komai sai na tuki? Direban tasha, wallahi na yi asara!!!". Rabi ta ce, "Kin kuwa yi asarar. Yanzu ke ko babur zaki iya tukawa ne balle aje ga mota zuwa jirgi? Ke kinga shegen bakin ki baya mutuwa, ni na gaji da magana don ba malamar jami'a bace. Ranar da ki ka bi Fa'iz daga ke sai shi na tabbata murus bakin zai mutu mu don kin raina mu ne ki ka cika mana kunne da babatu. Don haka sai anjima, mijina yana jirana. Sai mun zo rakiya filin jirgi...". Tamkar ta soka min mashi a kirji haka naji. "Ko kuma an aiko muku da sakon mutuwar danku kunzo zaman makoki ba? Ki sani, ranar da duk Fa'izu ya yi gigin sake sako kafarshi cikin gidanmu kamar yadda na dauke kafata daga nasu gidan, wallahi sai buzunsa Ya Rabi!". Ta ce, "Ko? Lallai kin fitsare, inama ina nan za'ayi wannan (BOXING)? Kai da na kadawa (Winner) tuta. In kuma kanwar ta kar tsamin ne sai kiyo min waya inzo jinyarki". *** Zaman Zaria fa yayi min zafi, Walida, Abdallah duk suna makarantar kwana. Kausar da Walid makaranta suke zuwa safe da yamma. Babu Ummi babu Zanirah balle tsohuwa Hajjah mai samu farin ciki. Ko da yake Hajjah ni na gujeta don a ganina ita ce ummul-haba'isin sanya rayuwata cikin halin kuncin da take ciki bayan shafa min bakin jini da hakan ya yi a idanun iyaye da 'yan uwana. Daga uwata har ubana kowa fushi yake dani, Walida kadai ke kula ni a gidan, haka nan kullum Baba zai fita sai ya ce. "Tunda haka kike so, wato ga dakin uwarki ga naki, inta wuce dakina ki bita da ido kina kissime-kissime ai sai kiyi ta zama". Wannan magana ba karamin kona min rai take yi ba, tun ina kuka har na saba. A zuciyata kuwa Allah Ya isa ga Fa'iz tafi dubu biyar. Na rame, na fige, na zama 'yar firit dama jikin ba wani jiki ba. Nayi niyyar komawa Giwa amma na kasa saboda kurarin da nayi a baya cewa ba zan sake zuwa gidan Hajjah ba. Wuri daya ne nake tunanin idan naje zanji sanyi, wato wurin Maman Kaduna, to amma in ina da kunya ai bana dosheta ba alhalin kiyayyar danta na neman zauta ni. Ko babu komi ranar da Fa'izun ya ga damar dawowa me na isa nayi mishi akan idon uwarsa? Gara dai ya kwaso jiki ya kawo namu gidan. Haka Zanirah da Aliyu suka yo min waya wai hakuri suke bani abinda suka yi min ranar bikinmu a Giwa su wasa ne suke min. Tsaki nayi na kife wayar nayi tagumi da hannu bibbiyu. Bayan kwana biyu kuma, sai Ummi da Bashir suma suka bugo, amma su ba hakurin suke bani ba, korafi suke wai naki inje inga gidansu, to inzo in raka Ummi awo tana da ciki dan sati biyu. Na ce, "Sai ku bari ya cika wata daya tukunna mu fara zuwa awo, kunji ko 'yan abu kazan uba marassa kunya". Ummi ta ce, "Da fatan (this very big) ashar (is for me alone not with my husband) don mu albarkar miji muke nema ba ma zaginsa". Watanni biyu suka shude tun ana zuba ido har kowa ya gaji babu Fa'iz babu duriyarshi, babu ko wayarsa. Don haka na yanke shawarar tunkarar Baba da shawarar da na yanke, wato komawa karatuna a Kano. Da farko baban ya fara ne da zunduma min zagi bayan ya gama saurarona, kana ya ce. "Sai dai in karuwanci kuma za ki sannan in barki, tunda kin ki zaman aure. Sannan ina mai tabbatar miki muddin ya kasance wani mummunan abu ne ya samu Fa'iz sakamakon raunin da kika yi mishi da kwalba, to ki tabbata sai na rotsa miki kwalbar 7up a wannan kodaddiyar fuskar da kike tinkaho da ita. Kazalika in Fa'iz yayi zuciya ne yaga cewa gara ya fasa auren, sai na dauke ki ke da kayanki na kai mishi sadaka, ko aikace-aikacen gida ne kiyi masa. **** A WALES (UK) A bakin wani (swimming pool) dake cikin hotel din da suke ciki cikin birnin Wales din kasar Ingila, bisa fararen kujeru da ‘yar jar lema da tayiwa kujerun inuwa ta rage hasken hantsi daga idanuwan wadanda ke zaune cikinta. Pilot Fa'iz Giwa ne da Maajid da Johari tare da wasu abokan su wadanda duka matuka jirgin sama ne ke zaune suna karya kumallo bayan sun fito daga (interview) din da ta kawo su kasar Ingila da British Airlines. Maajid na shan (tea) cikin wani kankanin kofi, amma hankalin shi naga Fa'iz dake faman juya cokali cikin (coffee) mai zafi idon shi na kan wata siririyar baturiya dake sanye cikin dan kamfe da 'bra' kadai, tana tafiya lange-lange kamar zata karye saboda rashin kauri da kumari ko kuwa kamar da an busheta da baki zata fadi don sirinta. Amma a zahiri, idan ka dubi cikin kwayar idanunsa ba ita yake kallo ba, idanunshi ne kawai a saitin da take, tsabar tunani ke jagwalgwala kwakwalwarshi wanda kuma ke neman fitar da shi daga duk wani jin dadi da yake ciki ya kuma zamo barazana kuma ga walwala da farin-cikin sa, harma da nutsuwarsa da hayyacinsa cikin duk al'amuran da yake gabatarwa tun barowarshi gida wanda ba wani abu bane face kanwarsa/matarsa FA'IZAH A.A GIWA. Wadda damuwa da al'amarinta da neman sanin hanyar warwarewar damuwar al'amarinta da shi ya zamo wani abu kadai da ya tsaya ya yi karantsaye ya addabi rayuwarsa. Har yake neman zautashi ba don ya kasance jarumi akan komai ba musamman wajen shanye damuwa komin girmanta. (Still) idanunshi na kan Ba'ireshiyar cikin rashin sanin abinda yake yi ya dauki attaruhun kwalba ba tare da ya ankara ba ya zuba cikin kofin Gahwarsa ga zatonsa sukari ne yake zubawa. Maajid na kallon shi bai hana shi ba sai ido da ya gwalo kamar za su fada cikin kofin shayinsa. Pilot Javed Saddyqy ya dubi Maajid cikin yamutsa fuska tare da nuna Fa'iz din da abinda yake yi da baki. Maajid ya kada masa ido alamar ya kyale shi. Idon shi daina kan Baturiya wadda ke ta faman yi mishi gizo da Fa'izah surarta na rikidewa tana zama Fa'izah. Ya sake daukar cokali ya motsa shayin yana shirin kaiwa bakinsa. Anan ne Suhayl Khan mutumin India ya ce da Saddiqy wanda shima Ba'indiyen ne cikin harshen Tamil. "Fa'iz ya samu makuwa ne halan?" Alama Saddyqy yayi mishi ta yayi shiru ta hanyar daura dan yatsarsa bisa lebensa, a lokacin yana rike da kofin ne a hannunsa amma tsayin mintuna uku bai kurba ba idanunshi akan Baturiya. Anan sai Javed ya sanya kafa ya dan take mishi yatsun kafarshi dake kusa da tasa, ya ce. "Ba zaka sha bane?" Fa'iz ya kai kofi da azama bakinshi ya yi mishi kyakkyawar zuka. Ba shiri ya saki kofin a kan tebirin ya ce. "Aaah!". Suka kwashe da dariya gaba daya, wadda zafin gahwah da zafin attaruhu suka hadu suka hana Fa'iz jinta duk da karfinta (dariyar tasu). Maajid ya samu abinda yake so, ya buga tebirin da hannunsa da karfi yana fadin. " Woman na nufin WO! MAN, ka shiga uku kenan. In har baka dauko Fa'izah ba kun zauna a garin nan tare Fa'iz kai ba namiji bane ungulu ne da kan zabo, duk wannan cika da batsewar naka [18/02 4:11 PM] Sumayya Takori: Shin wace ce Fa'izah? Me take takama da shi da take neman haukatar mana da Fa'iz haka? I dare you (Ina baka karfin gwiwa) kafin Fa'izah ta haukata ka, ko ta maida kai Fa'izah ta koma Fa'izun". Su da basu san dawar garin ba sai abin ya basu dariya da yake da Turanci yake maganar. Fa'iz ya kufula, a fusace ya ce. "Uban waye ya ce da kai tsoron Fa'izah ne ya hana ni tahowa da ita?" Maajid ya ce, "Yo in ba tsoro bane mene ne wannan? Yarinya tana matarka, karkashin ikonka amma ka tsaya kana shayinta? Anya kuwa zaka iya lankwasa Fa'izah Fa'iz? Ni wannan so ya yi yawa, ka bata (power) sosai ko da ace laifin naka ne kamar yadda kake ikirari. Muna da sati biyu kwarara na kintsawa kafin mu fara aiki da British Airlines, kayi amfani da su kaje ka dauko Fa'izah ta zauna a damanka zuwa duk inda ka cilla kafa cikin duniya ko ma samu nutsuwar ka, ko da ace haukan gaske zata yi ba na karya ba, a Turai akwai (psychiatrics) da (Asylums) iri-iri (gidan mahaukata). Fa'iz kam tsiyar Maajid ta ishe shi, yana neman tona masa asiri gaban abokan su bayan ya kasance mutum mai son sirri a rayuwarsa, musamman idan abin ya hada ne da (personal-life) dinshi ba harkar karatu ko aiki ba. Sai ya mike ya dauko robar ruwa ya kuskure bakinshi ya furzar. Amma bai daina mishi azabar yajin da yake mishi ba,. Maajid ya ciro karan sigarin dake bakinshi ya mika mishi. "Sha wannan, zai kashe 'shatter' (yaji)". Ya dalla mishi harara, sai Javed Saddyqy ya tsiyaya sanyayyen lemun 'shany' cikin tanbulan ya mika mishi. Ya karba ya kwankwade ya dire kofin Javed ya kara bincire hancin 'Rany' ya cika tambulan again ya sake mika mishi. Wannan karon ma ba musu ya amsa ya kwankwade ya dire kofin. Sunyi haka har sau hudu, sannan Fa'iz yaji dai dai, ya ce. "Shukran Yaa Siddiqy" wato (thank you Saddyqy). Ya wuce su ya nufi (lifter) da zata kaishi dakinsa dake hawa na goma sha uku. Ya bude dakin ya shiga ya maida ya rufe. Kai tsaye na'ura mai kwakwalwa ya nufa, yana duba tsarin tashin jiragen su cikin satin inda ya samu akwai jirgin British da zai tashi zuwa Abujar Nijeriya a safiyar gobe. Kuma a goben ne hutun kintsawarsa zai fara. Kafin ya dawo ya kama aikin da aka dauke shi cikin nasarar da dukkaninsu basu zata ba. Ya tabbatar aurensa da Fa'izah alheri ne a gareshi, domin daga ranar da ya furtawa Hajjah yana son Fa'izah a aura masa ita don ya gyara zumuncinsu da ya bata yake ta ganin fatahi wato budi ta kowanne bangare cikin hanyar samun abincinsa, kai har ma da wata irin nutsuwa cikin zuciyarsa. Zama yayi a bakin kayataccen gadon dakin yayi shiru, ya rasa abinda ke masa dadi, haka ya rasa abinda ke cunkushe masa zuciya. Baya farin ciki da komai kamar yadda ya rasa walwalar sa dungurungum. Kada dai zancen Maajid ya kasance gaskiya ya zama FA'IZAH maimakon FA'EEZ. Tabbas yana tsoron haduwarsa da Fa'izah a karo na biyu, amma haduwar (is something inevitable) wato wani abu da ba makawa sai ya faru, don haka ya zama dole ya aro jarumtar dake neman kufce masa ya koma ya kawo karshen kalubalen da suke ciki shi da Fa'izar da gidansu baki daya da kowa cikin zuri'arsu da suka zame musu wake daya mai shegen doyi. Don haka cike da karsashi ya shigar da kanshi cikin jerin fasinjojin da jirgin British zai kwasa a safiyar gobe zuwa kasar haihuwarshi Najeriya. Da ya kammala ya janyo jakar tafiye-tafiyen shi ya soma shirya kayansa, cikin tarin nutsuwa da Ubangiji Ya halicce shi da ita. A karo na farko yayi tunanin gwada daya cikin (theories) din Maajid na lallashi ga Fa'izah duk da ya san ba wani tasiri zata yi ga Fa'izah ba. Rufe jakar yayi ya mike ya sauya kayan jikinsa, ya dauki wayoyinsa da (mastercard) dinsa ya fito daga dakin ya rufe. Mota ya dauka a harabar adana motocin dake cikin hotel din wadda ta kasance ta haya ce kirar 'camry' ya hau bisa kwalta a hankali. Bai tsaya ba sai a bakin wani (Jewellery shop) a tsakiyar birnin Wales ya fito cikin wandon jeans ruwan kasa-kasa da riga ARMANI itama ruwan kasar ce amma mai haske, yayin da wandon ya ciza sosai, saye a idanunshi gilashi ne 'prada' baki mai duhu wanda bai faya amfani dashi ba in ba a lokacin aiki ba. Ya tabbatar ajiyar da yake da ita cikin (mastercard) dinsa sun isa da ya shiga wannan kantin domin ba kantin (fashion jewellery) bane, kanti ne na duwatsu masu madaukakiyar daraja (diamond, sapphire, gold, emirald) kadai. Kamin ya isa ga kofar shagon wadda ta kasance ta gilashi tuni ta bude kanta. Ya tsaya yana nazarin siraran sarkokin farin 'diamond' a wani bangare dake cikin shagon, ya zabi wadda yake ganin zata yi dai-dai da siririn wuyan Fa'izarsa, haka zoben dake hade da ita yayi bala'in dacewa da zara-zaran yatsunta daya gani ranar da suka kantara masa kwalba... Ya yi murmushi shi kadai, ya kai hannu ya shafo lallausar sumar kansa daidai inda kwalbar ta huda, ya kame yazama tabo, ya dauka ya biya. Aka sanya su cikin gidansu mai martaba aka bashi tare da risidi (reciept) bayan an ciri kudin daga (credit-card) dinnasa. Akan hanyarsa ta komawa hotel din da suke, ya shiga shagon "NEXT” ya yiwa Fa'izah sayayyar sutturun NEXT samfuri daban-daban, riga ne, siket ne, wando ne, jacket ne, sweater ne duka 'yan gidan 'NEXT' masu daraja ko daga kallon su a ido ba sai an tambaya ba. Daga nan shagon turaruka ya tsaya ya daukar mata gigitattun turarukan ESCADA (sentiment and magnetism) sannan ya dawo hotel ya hada cikin kayansa. A daren ya hada komai nasa cikin jakunkuna manya har uku, daya sayayyar Fa'izah ne taf, daya na Mama da kannensa, sai ta kayansa. Washegari ya biyo jirgin British mai zuwa Abuja. **** Da ya sauka a Abuja waya ya yiwa Yaya Sa'id yaje (airport) ya dauko shi, kasancewar Yaya Sa'idu Na'ibi kani ga Yaya Aliyu aiki yake a Abuja da (Federal Ministry of Agriculture) zuwa gidansa. Ya kwana ya huta suka sha hirarsu ta zumunci duka akan 'yan uwa washegari ta kama asabar dama Sa'idun zashi gida Giwa, sai suka taho tare. Ya sauke shi Kaduna (Jabi Road) shi kuma ya wuce Giwa. Ba zato Mama ta ga Fa'iz yana sallama a kofar falonta. Wani dogo kuma katon saurayi (giant and gentle) ma'abocin kwarjini, cikar zati da kamala da ya gama zama mutum, wanda in ka kalle shi dole ka sake, mace ne kai ko namiji saboda wasu ilhamomi da Allah Ya yi masa da ba duk maza Allah Ya mallakawa ba. Abubakar Mukhtar Abubakar (Fa’iz), kamar yadda cikakken sunansa yake, mutum ne (extraordinary) tun yana kankaninsa har girmansa, komai nasa daban yake da na sauran maza tsararrakinsa cikin A.B Bamalli House. Mutum ne mai matukar kyau da kwarjinin da idan ya shigo wuri sai kowa dake wurin ya ji shi (inferior) wato kasa dashi, ko da ya girme shi da shekaru, sai an san ya shigo saboda haibarsa, sai an san yana wuri saboda zatinsa. Sai an san namiji ne saboda kamalarsa. Duk da ya kasance mai kin ji da kiriniya a lokacin kuruciyarsa, shi ne da mafi soyuwa a zuciyarta cikin ‘ya’yanta guda tara, wanda kuma tafi shan wahala akansa kafin ya tsaya ya ginawa kanshi (future), wanda sai da ya shekara goma bai iya rubutu ba, ya kuma yi karatu ba tare da rubutu ba. Idan ta hada rayuwar Fa'iz gaba daya, daga yarinta zuwa girma, akwai baiwarwaki masu yawa a ciki. Ya kuma ci ace tun yana yaro sun gane yana da karama a fannin sarrafa abin hawa da (passion) akan duk wani al'amari da ya shafi injin hawa. Kai dai barshi da kabilanci da wariyar launin fata ga wanda ba ahalinsa ba ko ba jinin sa ba. Ta sauke idonta cikin nasa a hankali tana murmushi, shi kuma sai ya zarce da dariya yana fadin. "Ga bakon Mama babu sanarwa". Ta amsa, "Ina maraba da wannan bako nawa duk da nasan wannan zuwan ba nawa bane". Sai ya yi dariya cikin bagararwa ya zauna kasan kafafunta suka shiga gaisawa. Mama ta kasa zaune ta kasa tsaye da hidimar saukar (unexpected) bakonta, Abubakar-Fa'iz. Fitinannen danta (a da) amma dan lele a yanzu tunda ya auri abin sonta Fa'izah, ya kuma tsaya ya fuskanci rayuwa ya gina kansa irin yadda, ko ma fiye da yadda suke so ya fuskanta. Kalolin abinci har biyar da ta jere a gabansa sai da suka bashi dariya cikin jin dadin kulawar mahaifiyarsa gareshi yake fadin. "Duk ni kadai, ni Abubakar dan gatan Mama!". Ta harare shi idanunta cike da kauna. "Ko kunya baka ji ba da abinda kake fada wai dan gata na, ina ruwana da kai, (after all) nasan ba wajena kazo ba. Amfani nayi da Hadisin Manzo da ya ce, "Bakonka-Annabinka..." da kuma kasancewar mai yin bata kusa da ina ruwana da hidimar ka?" Dariya yake yi wadda ya manta rabonshi da yin irinta, watakila tun kafin Fa'izah ta shigo tayi sallama cikin sabuwar rayuwarsa ta baya. Ya ce, "ya yi min yawa ne Mama". Ta yarfar da kai, "Ko da baka cinye duka ba dai ka daure ka dan tsakura, don wadda kake rawar jiki da dokin ganin ba baka zata yi ba". Murmushi ya yi, ya dauki (spring roll) mai taushi ya sanya a bakinsa ya gutsira yana ci. 'Yan kannenshi su Junior duk sun zagaye shi suna tambayar shi yadda sama take. Ya ce, "Kuje ku tambayi malamin 'Geography' dinku (I'am not an astronomist)". Shu'aib ya ce, "Yaya Fa'iz nine planet suna yi muku magana a sama?" Shi kuwa Yahya cewa yayi, "Wai Yaya ta saman su kuke bi ko ta kasansu?" Junior ya ce, "Yaya bakwa take su?" Ya zuba lemu 'Don-simon' cikin tambulan ya ce. "Kai don Allah ku saurara mini, na ce (I'm not a geographer, neither an astronomist) amma ku bari na muku alkawari ranar dana shiga duniyar wata (journey to the moon) na dawo zan amsa muku wadannan tambayoyin naku". Sai Yahya ya ce, "Amman da Fa'izan gidan Baban ABU ce ta tambaye ka da ka gaya mata ko Yaya?" Fa'iz ya dauke wuta, cikin mamakin kalaman yaron, dariya ta kama Mama amma bata yin ba sai a zuci. Ya tsurawa yaron ido yana kallo cikin hada amsar da ya kamata ya bashi, kafin ya samu ya harhada sai Shu'aib ya ce. "Kasan ko tun ranar da Fa'izah suka zo da Aunty Ummi daga Kano muna gyaran dakinka ta zo ta leka dakin ta tambaye ni na ce mata ku za ku dawo, bata kara zuwa gidan nan ba". Yahya ya ce, "Ai bata son sa, kaga wannan tabon na goshinsa ma ance ita ta ji masa". Junior ya ce, "Kai ya akayi ka sani?" Ya ce, "Rannan ina dakin Aunty Zainab (Maman su Yaya Aliyu) naji Ummi na gaya mata har tana cewa tayi asara...". Da sauri Mama ta cira ido ta dubi goshin Fa'iz a hanzarce, Fa'iz bai san sanda yasa kafa ya kaiwa Yahya wani mugun hauri ba, Mama tayi sauri ta rike kafar gam, ta ce. "Kada ka karya min yaro, ba shi ya kar zomon ba balle ka rataya masa, ba a bakinsa na fara ji ba. Waye bai san Fa'izah ta kwada maka kwalba ba? Ni dai rokona akan ka duk rintsi kada ka biye mata domin ka cancanci hakan daga gareta ko ma fiye. Ka ringa yi kana TUNA BAYA... domin TAKORI ta ce "TUNA BAYA SHI NE ROKO" sai dai ina da yakinin yadda komai a rayuwa ke zuwa ya wuce (with time) kiyayyar Fa'izah mai wucewa ce tunda kaima sanda kake kinta baka kayyade lokacin daina kin nata ba. Zuwa ya yi da kansa, don ma anfi karfinta ne amma da ko kusa baka cancanci auren Fa'izah ba, Aliyu shi ne mutum mafi dacewa da auren Fa'izah ba kai ba Fa'iz!". Banda Mama ce, UWA! Wa ya isa ya dubi tsabar idonsa ya gaya mishi haka Ya yi kwafa kamar zai hadiyi zuciya ya mutu don takaicin kalaman Mama, ya yi shiru yana gwama numfashi kamin ya dubi Mama cikin sanyin jiki. "Wa yafi karfin nata? Gaba daya cikin ku wa yafi karfin nata a yanzu Mama? Cikin ku duka an rasa mai sanya baki a bani matata kamar yadda aka baiwa kowa tasa, saboda ita ishasshiya ce kowa yana tsoronta. To ni kam na zo daukar aurena ne (dead or alive)!" Mama tayi dariyar da ta kara kular dashi, ta ce. "Kofar hanyar Zaria a bude take ai kullum Fa'iz, kai da baka tsoronta sai ka je ka dauki abarka, munji mu tsoron ta muke ji kada muje ta fasa mana kai kamar yadda ta fasawa jarumi Fa'izu Abubakar". Haushin maganganun Mama koko ya ce shagube ko gugar zana yasa shi mikewa ya nufi dakinsa ba tare da ya kara tofawa ba. Yayi wanka, ya zuba shaddah 'getzner' koriya sharr. Ya bi jikinshi da turaren (212). Bai dauki sanya hula da muhimmanci ba kasancewar sa mai tara sumar kai da bata (extra) kulawa, don haka yau din ma bai sa ba. Ya zura lafiyayyun takalma budaddu bakake sidik kirar Thailand. Ya jawo kayanshi da ya zo dasu ya ware tsarabar da yayowa Fa'izah wadda dama ya wareta cikin (troller) guda. Ya daga ido ya dubi jerin akwatunan dake girke a gefe masu suna lefen Fa'izah wanda har yau babu wanda yace ya kawo a kai mata duk da an kai na Yaya Bash da alama ma da baya nan anzo an bude an zari wasu. Ya kwalawa su Shu'aib kira, ya ce su fidda akwatunan su zuba mashi a 'Roll-Royce' din Baba da ita zai fita. Suka kwashe har ta tsarabar, ya fito ya nufo dakin ya isa sashin Mama ya shiga ya zauna cikin lumtsuma-luntsuman (leathers) dinta. Tana jera kayanta a sif ta amsa mishi sallamar kafin ta juyo. Tayi murmushi ganin yadda ya hade kamar wani angon so, nan kuwa angon ki ne, shi kuma sai ya fara sakin tsaki. Ta ce, "Ya akayi? Sai ina kuma ango sha kamshi? Ko sai Zariyan?" Ya ce, "No Mama, ina son zuwa gidan yaya Bashir ne, bana nan suka tare". Ya sha mur sosai ya ja fasali ya ce. "Yanzu Mama da ita mutuniyar kirki ce da bamu je tare ba?" Tayi dariya ciki-ciki kamar bata gane wa yake nufi ba, ta ce. "Ita wa?" "Fa'izah mana!". Tayi 'yar dariya, "Mutuniyar kirki ce mana". Ya yi tsaki, "Ban ga alama ba. Yanzu don Allah Mama da gaske kike ba zaki sa baki Fa'izah ta sakko mu tafi tare ba? Na gaya miki British Airlines sun dauke ni aiki, zan fara sati biyu masu zuwa don haka (most of my stay now will be in Wales, London and Scotland) ba zan iya zaryar zuwa gida akai-akai ba sai bayan watanni uku-uku. Zai fi sauki idan muna tare a duk inda nake don samun cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankalin gudanar da aikina yadda ya kamata. Ki taimaka min Mama, ni kadai ba zan iya ba, kunyi min aure amma kun barni ni kadai da yakin kwatar sa, baku cika ladar ku ba". Mama ta ce, "Kaga babu ruwana cikin rigimar ku, can muku. Wanda ya jawo ruwa shi kadai zai doka. Yadda Fa'izah ke ganin bakin kowa kan maganar auren nan banda ni, sannan kazo ka tsoma ni ciki, salon ta ce na bi bayanka don ba ita na haifa ba? Bayan sanda kake tsula mata tsiyar ka baka nemi taimakona ba idan kuma na hana ka ba ka ji. Kowa ya debo da zafi, bakinsa". Kamar zai fashe da kuka, "Amma Mama haka za'a zuba mata ido tana yin abinda taga dama, ni me na yi mata da zafi haka? Don kawai ina cewa ta dinga tsafta kamar su Zanirah? Ni ba dukanta nake ba, ba zaginta nake ba...". Ta tare shi, "... in ita baka zageta ba, ai ka zagi uwarta, kana tsammanin 'ya'ya mata suna yafe wa in an taba musu uwa?" "To ba na ce ayi hakuri ba? Waye kuruciya bata sa shi yin kuskure? Babba ma yana aikata kuskure balle yaro karami kamar Hafizin Hajjah!". Sai ya bata dariya a yanayin yadda ya yi maganar, ya kuma bata tausayi duka a lokaci daya. Ta dan dube shi tayi murmushi, da gaske cikin damuwa yake, duk jarumtakarsa damuwar ta kasa buya. Lallai ta yarda SOYAYYAH halitta ce mai zaman kanta, kuma (reality of man's existance)... sannan bata shawara da kai idan ta shirya yin awon gaba da kai, da ta tabbata bai barta tayi wannan tasirin mai yawa a kansa ba, kasancewarsa namiji daya da daya mai ra'ayi da akidu da 'principles’ masu zafi. A yanayin yadda tayi magana yanzu ya fahimci ta fara jin tausayinsa ta kuma fara fahimtarsa amma bata so ya gane hakan. Cewa tayi. "Kai da baka tsorontan me ya hana ka yin maganar? Ba matarka bace? Ko ko zaman dadiro ka nema ba hakkin ka ba?" Ya yi wani irin murmushi, yanzun kam ya fuskanto inda Maman ta sa gaba, wato itama zaman Fa'izar a gidansu ya dameta illa alkunya da kara irin ta mallawan usli don haka ba zata bari aji daga gareta ba sai dai shi din. Ya mike zai fita, wannan karon cike da kuzari, sai ta ce. "Akwai kudi a aljihunka ne? Motar babu mai, naji Hadi yana fade dazu". Ya shafa aljihunshi akwai kudi, amma 'pounds sterling'. Ya ce, "Ban je canji ba sai zuwa gobe insha Allah". Ta bude jakarta ta fiddo bandirin 'yar Sardauna dauri uku ta mika masa, bai yi musu ba ya sanya hannu biyu ya amsa yayi godiya. Ita kuma tayi hakan ne don sanin halin sa, ya gwammace ya zauna baya da ko sisi da ya tambaye su ko kwandala. Ummi da angonta Yaya Bashir suna cikin (kitchen) suna hadin (burger) da suke so su ci. Da ya fito sashen Mama a bakin kofa suka yi karo da Shu'aib ya tambaye shi kwatancen gidan Yaya Bashir. Ya ce, "Yaya Fa'iz muje mana in raka ka, nan ne Kabala Custain ba nisa". Ya ce, "Amma da kanka za ka dawo? Don ni daga can ba gida zan dawo ba". Shu'aib ya daga mishi kai suka jera suka fito suka shiga motar Baba, Fa'iz ya ja motar a hankali suka fita daga gate din gidan nasu. Ummi ce ta fara hango shi ta tagar (kitchen) din wadda ke santar harabar adana motar su. Tayi ihu harda dan tsalle ta ce. "Ya Fa'iz in town". Suka fito da sauri ita da Bashir suka game dashi a main falonsu. Daga matar har mijin bakin su yaki rufo sai jera masa sannu da zuwa da yaya hanya suke yi yana amsawa da ka, yana dan yatsine fuska. Ya bi daya daga cikin lafiyayyun kujerun falon ya nitse. Takaici ko kishin yadda yaga Ummi da Bashir ne suna rayuwarsu babu abinda ya dame su duk sunyi haske sunyi kiba, koko tunanin tashi 'yar bala'in amaryar ne yasa shi yatsine fuska oho! Da irin tarbar da shi zata masa? Allah kadai Yasan ZUCIYAR MUTUM (sunan wani littafin TAKORI). Suka zauna kusa da shi suna manne da juna. Ya dube su sai ya saki fuska. "Mr. and Mrs.". Suka hada baki wurin cewa, "Allah Ya taimaki angon Fa'izah!". Ummi har da jinjina da hannunta. Bashir dariyar shegantaka yake mishi ganin yadda ya zabge amma ba zai fasa halinsa na rainawa mutane wayau ba da ginshirar babu gaira babu dalili ya ce. "Shin Pilot Giwa yayi ciwo ne?" Ya ce, "Lafiyata kalau, me ka gani?" Tare da cin laya kada su kawo mishi shegantakar da ba zai dauka ba, amma sai da Ummi ta ce. "Kaima dai dear! Fa'izah's calamity mana! 'Yar banza Bakin Bunu Bata Baibaya...". Ji yayi kamar shi ta zaga, kuma dai shi baya son a dinga shigar masa rigimarsa da Fa'izah ko ace tayi ba dai-dai ba, zai fi son ka zauna a gaban sa kayi ta yabonta kana bashi labarin rayuwarta fiye da nuna kana taya shi takaicin abinda take yi akansa. Ya share zancen da cewa. "Shin kuna lafiya? Na same ku lafiya?" Bashir ya ce, "Gani ya kori ji". A yayin da yake tuttula mishi (fresh milk) din Peak cikin tambulan din dake hannun Ummi, ta mika mishi ya daga mata hannu. "Barshi, bana tare da yunwa, Mama ta bani abinci na ci". Ummi cikin rashin jin dadi ta ce, "Amma ta yaya zaka shigo gidanmu ka fita ko ruwa baka kurba ba?" Kamar zata fashe da kuka, sai ya mika hannu ya karba ya shanye ya dire kofin bisa (center table). "Na yaba da tsarin gidanku, Allah Ya ba da zaman lafiya. Ni zan wuce". Ya mike. Dan uwa rabin jiki, Yaya Bashir sai yaji tausayin Fa'iz ya kama shi duk da basu cika shiri ba ya gano damuwar dake tare dashi da halin da ya shiga ganin irin rayuwar da suke yi shi da Ummi suka mike suka fito tare da shi. Bashir ya ce, "Wai ina Fa'izar ne?" Ba tare da ya juyo ba, kamar yadda bai fasa tafiya ba ya ce. "Tana nan". Ummi da Bashir suka hada ido suka yi murmuishi, shi kuma ya sake hade rai da fuska har da tsuke baki kada su kara tambayarsa game da Fa'izah, kowa yayi (minding business) dinsa. Ita kuma Ummi bata fahimci hakan ba, sai ta ce. "Don Allah ka kawo min ita mu wuni yaya Fa'iz, na matsu in ganta, nayi-nayi tayi hakuri ta ki saurarona...". Sai kawai ya samu bakinsa da furta, "Me kika yi mata?" Alhali bai yi niyyar yin furucin ba. Ummi ta ce, "Matsalar mu ce, amma ka tambaye ta mana, ai kunfi kusa". Sai yaji kamar shaguben da yake gudu suka yi masa. Ita kuwa Ummi tsakaninta da Allah ta fada, ta kara da cewa. "Sai yaushe za ku tare mu zo rakiya?" Ji yayi kamar Ummi ta zage shi, ya ce. "Ummi, ina wasa dake? To babu rana babu wata!". Dai-dai sanda suka kawo inda ya yi (parking), Shu'aib na zaune bencin megadi suna hira yana jiransa. Ya bude boot din motar yasa Shu'aib ya fitar musu da tsarabar da ya kawo musu. Electronics ne na amfanin (kitchen) cikin kwalayen su guda biyar samfurin 'Binatone' microwave, juicer, mixer da 'rice boiler' sai 'blander masu karshen (quality). Shu'aib ya shigar musu da su gida ya dawo suka shiga motar suka tafi, Ummi da Bashir na godiya suna daga musu hannu har suka fice daga harabar gidansu suka hau titi. Yana tukin ya dan juyo ya dubi Shu'aib ya ce. "Yo kai in haka ne ai zaka yi min amfani wajen sauke kaya, shige muje Zaria kawai". [18/02 4:11 PM] Sumayya Takori: **** A ZARIA A wannan rana wadda ta kasances asabar din karshen watan Agusta cikin 'Area One', Walida da Abdallah duka suna gida sunzo hutun karshen zangon karatu na biyu daga makarantun su daban-daban. Ina kwance cikin dakin Walida wanda yanzu ya zama nawa tunda ita ba zaman gidan take ba, sanye da riga da zani na atamfa mai karshen tsada (Exclusive Sharaton) ruwan ganye mai ratsin hoda, kaina ban daura kallabin atamfar ba yana dai ajje gefen gadon, na hade gashin kaina cikin tafkeken 'hair-bound ina karanta sabon littafin Takori ne mai suna 'KWANA SITTIN'. Zuciyata ta tafi gaba daya cikin rayuwar (schezophrenic_Safeenah) mai tsananin ban tausayi. A wani bangaren, ba Safeenar nake tausayawa ba kamar Kabir Danbatta, na rasa shi da Dr. Dangi wa yafi dacewa da amsar ragamar rayuwar Safeenah? Kowannen su masoyinta ne na hakika. Muryar oyoyon da Walida ke yi ya katse min karatun, na bi hadaddun jakunkunan da Shu'aib ke shigowa da su dakin namu yana dora daya kan daya da kallo ina kissimawa cikin raina, wane irin baki ne muka yi masu tafe da jakunkuna 'classic' haka kuma har dozen? To kwana nawa suke nufin za suyi a gidan namu? Kamshin sassanyan turaren (212) na maza ya sirnano cikin hancina, wani irin kamshi da ban taba jin mai sanyi da dadinsa a duniya ba. Wadanne irin baki ne momi tayi haka? Abinda nake tambayar kaina kenan. Daga inda nake kwance na jiyo muryar ma'abociyar ginshira, na tambayar Walida ina Momi da Baba? Walida ta ce, "Momi na gurin aiki, Baba na cikin makaranta. Amma Yaya Fa'izar tana ciki tana karatu". Da murmushi fal a fuskarsa ya ce. "Karatu? Ko dai kuka Walida?" Ta ce, "Wallahi karatu take, kullum ma karatu take, ta je kasuwa ta sayo littattafan TAKORI na da dana yanzu, su take karantawa kullum, ta daina kukan tuni...". Muryar FA'IZ, FA'IZ GIWA, FA'IZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA! Da kwarin gwiwarsa ya yi sallama a dakin cikin 'husky voice' din da Allah Ya yi musu baiwarta zuri'ar Abubakar Bamalli Giwa bakidaya. Ya samu wannan kwarin gwiwar ne daga labarin da ya samu a bakin Walida masu nuna na kwantar da hankalina tunda har ina karatu? Duk da kwakwalwarsa bata fahimci littattafan TAKORIN da Walida take bayani akai ba, ya dai fahimci NOVELS ne wanda ba zai ce na Hausa ne, na Turanci ko na Larabci ba, tunda bai san mene ne ma'anar TAKORIN ba, bai ma taba jin kalmar ba cikin kowanne yaren. Abinda ya fahimta shi ne TAKORIN 'is an author' tunda yaji ance NOVELS dinta. Banda wannan kwarin gwiwar da ya samu ya samu karin na Momi da Baba duka basa nan yadda zasu ji dadin babbaka juna a wuta idan ta kama. Babu mai ceton dayansu. Yau za ayita ta kare (he can no longer tolerate it anymore!!! Kamar yadda ya ce da Mama ne ya zo daukar aurensa (dead or alive) haka yake har zuciyarsa. In har littafin labarin SAFEENAT MAHMOUD ALKALERI wato KWANA SITTIN na Sumayyah Abdulkadir ya amsa, to nima Fa'izar da ake yiwa sallamar na amsa. Ya shigo kansa tsaye Walida na biye dashi kamar bakinta zai tsage don murnar ganinsa ta iso har gadon da nake kwance, da murnarta take fadin. "Aunty Fa'izah ga Yaya Fa'iz!". Wani irin kallo nayi mata wanda nake jin tunda Momi ta haifeta babu mahalukin da ya taba yi mata shigensa, ba shiri ta juya har tana cin karo da (stool) din madubi, saura kadan ta kifa. Da sauri Fa'iz ya riko hannunta ya rike gam. "Ina zaki matas? Ke da nazo muyi zance? Zauna hira za muyi kafin su Momi su dawo". Walida a daburce take, ya jata suka isa har gefen gadon da nake kwance suka zauna har rigarshi ta rufe min kafa kadan. In banda kamshin sassanyan turaren shi ba abinda ke tashi a dakin. Ya bige da tambayar Walida sha'anin makaranta tana bashi amsa a darare, kokarin zamewa take ta barmu yana kara shimfido mata tambayoyi akanta da kannenta su Waild, Kausar da yayanta Abdallah da nasu karatun. Ganin ba zai barta ta tafi ba ta ce, "Yaya Fa'iz bari in kawo maka ruwa da lemo in kaiwa yaya Shu'aib abinci falo". Ya ce, "Kada ki damu Walida, na cika cikina a Kaduna, haka shima Shu'aib. Yaushe Momi za ta dawo?" Walida ta kalli inda nake bamu hada ido ba, amma taga yadda kwayar idanuna suka kada suka yi jajawur, numfashina ke sauka da sauri-da-sauri har wani irin huci nake kamar mesa babu rahma cikin su dai-dai da kwayar zarrah. Walida ta kara rudewa ta ce, "Na jona ruwa a (heater) Yaya Fa'iz ka barni inje in kashe kada ya kone fada Momi zata yi min". Ya ce, "To kiyi sauri nima ba zama zanyi ba, sako zan baki wurin Momi sai mu wuce". Ta ce, "Toh". Da saurinta ta fice har tana sake tuntube da dokin kofa. Ya girgiza kai ya mike ya sauke ido a kaina, tsayin mintuna biyu yana kallona kawai babu ko kiftawa. Nima kallonsa nake, wani irin kallo da ni kaina na kasa fassara shi, na takaici ne ko na kiyayya koko na gara da Allah Ya kawo ka? Ni kaina ban sani ba. Daga ni har shi babu mai niyyar daina kallon, duk da shima na kasa fassara nashi kallon. Shi ba kallon so ba, ba na kiyayya ba, ba na jin haushi ba. Yafi kama da kallon iko da raini. Ta wani fannin tamkar kallon, "Baki da yadda za kiyi dani" koko kallon "Nafi karfinki da ke da duk abinda kike takama da shi. (In another notion) kallo ne na "Yarinya na ci dubu sai ceto, kiyi duk abinda za kiyi" Sai da ya mula don kansa ya ce. "To ni Aunty Fa'izah zan wuce Giwa, tunda na iso Hajjah bata ganni ba, lefenki na kawo miki, wanda kowa ya kasa kawo miki tunda kin zama Faskari, mai faskarawa mutane kai. Sai tsarabar da nayo miki a tafiyar da nayi, tunda babu gaisuwa ko ta Musulunci a tsakaninmu. Daman nazo ne in shaida miki zaman nan ya isa haka! Ranar (monday) kwana ki shidda kenan masu zuwa ki kimtsa kayanki da duk abinda kike bukata za ki tare a gidanki kamar sauran 'yan uwanki, don gaskiya fisabilillahi kin takurawa su Momi da alama har su Walida kin takura musu, nima kuma kin takura min. Haka kawai ina da mata amma bani da maraba da gwauro. Gara mu kauce haka muma mu manta komi, da duk abinda ya faru a baya, mu fuskanci sabuwar rayuwar dake tunkaro mu, muka kuma bude ido rana daya muka ganmu cikinta. Wato rayuwar aure. Sai mu rungumeta, mu kasance cikin godiyar Ubangiji da neman dacewa duniya da lahira". Da ace Fa'iz yasan tashin hankali da bala'in da kalaman dake fita daga bakinsa suke kara jefani da ko da wuka a makoshi bai yi gigin furta su ba. Domin kalamai ne da ban taba jin mafi muninsu a duniya ta ba. (Hada rayuwa ta har abada da shi FA'iZ-ABUBAKAR) koko ince makiyina. Mugun dan uwa da kullum ketowar alfijir da faduwar rana sai nayi dakacen INAMA ban hada jini da shi ba. Wani kwayan mutum guda daya da ya maida mahaifiyata marainiyar wayonsa, ya maida ni kwallon takawarsa a duk sanda ya so, ko gare-gare abin wasan yara. Mikewa nayi gaba daya na littafin KWANA SITTIN ya fado daga ruwan cikina, na ce. "Da uwar wa zaka tafi wurin direbancin?" Tsalle daya nayi sai gani a bakin kofar dakin nayi maza na rufe na murza 'key' na zare shi na cilla shi waje ta taga cikin wani irin zafin nama da ni kaina ban san inada shi ba. Ya yi maza shima ya cafe mukullin cikin irin nashi (exceptional) zafin naman wanda yafi nawa kafin ya kai ga ficewa ta tagar. Ya shiga sosa keya da (key) din ya daure fuska sosai kamar ba shi ne ya gama maganar da yayi cikin raha ba. "Meye haka? Gafara ki bani hanya na wuce". Na ce, "Wucewa kam zaka yi ta, tunda har ka yi nasarar amsar mukulli. Amman fa bayan rubutun saki uku ris a gareni FA'IZA A.A GIWA". Murmushi ya yi, "Wannan ne kuma ba zaki samu ba har abada Fa'izah, har kuma yaumil-ardhi. Domin ban aureki don in saki ba. In haka ne tun farko ba zan fara ba. Karewa ma, ni ba lallaminki nazo yi ba kamar wancan karon, UMARNI ne ki hada kayanki ranar litinin za ki tare a gidanki kamar kowacce mace mai aure. Ba kuma neman afuwarki ko kiyi min uziri nazo ba tunda ke abu ba ya karewa a wajenki kamar cin kwan makauniya. Ki matsa na ce, tun hannuna bai kai fuskarki ya yi mata tabon da bata da shi ba...". Sunkuyawa nayi kafin ya kai karshen maganarsa na dauko littafin da Walida ta kammala rubutu dasu, na yago takarda a ciki na mika mishi. "Ko da can babu wani wasa makamancin 'game' ko 'April-fool' da ya taba shiga tsakaninmu balle yanzu da kowannen mu ya mallaki hankalin kansa. Za ka wuce din babu haufi, kuma babu makawa, amma fa bayan ka yi rubutun nan". Na sake mika masa takarda. Fa'iz ya sanya (key) cikin aljihun kaftanin shaddar dake jikinsa. "Kenan har wani hankali kika mallaka yanzun? Ko daya! Kina nan yadda kike; Jiya 'i yau, kazama, dakikiya, 'yar kauye, mummuna. Don haka daina cewa wani wai kin mallaki hankali, ina hankalin yake nan kana tura kanka cikin jahannama kana ji kana gani?" Na ce "In shiga wutar mana, tunda ba tare za'a sanya mu ba ina ruwanka?" Ya ce, "Naga alama abin naki nema yake ya wuce na rannan, to ba zan rubuta ba kiyi duk abinda za kiyi". Anan kam dankwalina na janyo nayi dammara dashi a kuguna kamar wata sabon hauka, na doshi Fa'iz da takarda har na iso gabansa. Sai dai kuma zuciyata cike da taraddadin murdaddun damatsan Fa'iz da na hango ta cikin kayan jikinsa. Ina tunanin idan ya cafke ni da su wa zai kwace ni? Babu kowa a gidan sai yara na kuma kama kofa na kulle? Da alama shima ya shirya yau. Idona ya kyallo min biro a aljihun gaban rigarsa, na cizgo shi, na matsa gabanshi sosai har muna iya jin hucin numfashin juna. Kallon zakaru masu shirin dambacewa muka tsaya muna yiwa juna. Sai na samu kaina da ganin wautata anan, shin in nayi duka ta ina zai shigi wannan 'giant' din? Fa'iz kato ne sosai mai tsayi da kauri, kaurin da ba kiba ke haifar dashi ba 'diet' ne da hutu na yanayin rayuwa mai nagarta. Don haka na fashe da kuka tabbacin Fa'izun yafi karfina kamar yadda ya ce, babu yadda zanyi dashi. Sai na ce a raina. "bari kawai kaifin harshe na ya zama makamaina". Cikin kuka na ci kwalarshi amma fa kada ki so ki tona bugun da zuciyata ke yi, na ce. "Idan har ka haifu cikin uwa da ubanka ka rubuta min takardar nan Fa'iz...". Ban kai karshen kalamina ba ya fidda hannu ya shimfida min wasu irin gigitattun mari hagu da dama. Na nemi ji na da ganina na wucin-gadi na rasa. Naga giftawar wasu taurari masu hasken dake tafiyar da ganin dan-Adam na lokaci mai tsawo, ji kake fauuu! fauu!! fau!!! Yasa tsayayyun kafadunshi ya ingije ni gefe guda na fadi warwas akan dandagaryar kafet. Ya nufi kofa ya zaro dan mukullin a aljuihunshi yana kokarin sanyawa jikin kofar, nayi kukan kura na wawuri abin zaman kwalliya (stool) na jefe shi dashi, ya same shi a baya. Yasa hannu ya rike kafadarshi ya kuma juyo cikin dan bude ido ya ce. "Kin gama?" Na tsala ihu na taso nayi kanshi da duka da duk iyakacin karfina da hannayena hagu da dama. Ganin duka wannan bai min ba, domin kamar ba jikinsa nake duka ba, sai na kai kaifafan hakorana damtsenshi shi, cewa yake. "Fa'izah baki da hankali ko?" Irin bude kofar da aka yi ba zato ya sanya Fa'iz hankadani tsakiyar gado wanda ke nufin da can dukan nawa da cizon nawa bai dameshi ba sai gudun kada a shigo a ga ina dukanshi. Gaba dayanmu muka bi kofar da kallo cikin firgita. BABA NE! Ya ce, "Kai amma Fa'izu anyi sullutun banza! Ka tsaya kanwar bayan ka na lallasa ka kana tsaye sororo, shashasha, sahorami". Cikin kuka na ce, "Baba shi fa ya mareni, yayi min dukan tsiya har da rufe kofa don ma kada wani yazo ya taimakeni, dubi yadda ya dauki tebirin nan ya kwada mini a baya...". Baba kam bai tsaya saurarona ba ni da karerayi na ya dauko dorinar da yakewa su Walida barazana da ita in sunyi laifi yayo kaina. Fa'iz ya kama bulalar da karfi ya rike, ya ce. "Haba Baba! In Fa'izah na haukan shirmenta bai dace kowa ya biye mata ba". Na ce cikin gunjin kuka, "Kai ne shirmammen, mahaukacin, amma ni lafiyata kalau". Baba ya yi salati, ya fisge bulalar daga hannun Fa'iz ya shiga tsula mini ta ko'ina ina ihu ina zagin Fa'iz ban fasa ba. Fa'iz ya sake damke bulalar ya ce, "Baba ya isa haka nan. Ka yiwa Allah da darajar marigayi kayi hakuri". Idanun Baba sun rine da bakin ciki da takaici, ya ce. "Fa'iz ko ka cikani ko in kakkarya Fa'izah da hannuna, ina amfanin wannan jarababbiyar yarinya cikin A.B?" Ya fisge bulalar daga hannunshi, ya ci gaba da shimfida mini da iyakacin karfinshi. Da Fa'iz yaga Baba na shirin illata ni (and he has no regret for it) Sai ya fado kaina gaba daya yayi min rumfa da faffadan kafadunshi, ya zagaye ni da hannayenshi ya rungume ya ce. "Sai dai ka nakasta mu tare Baba! Amma ba zan zuba ido a kashe Fa'izah akan gaskiyarta ba!!". Baba ya yada bulalar ya fice yana fadace-fadace, bai dai yi min baki ba, sannan bai yi tir da haihuwarta ba amma ya ce ni zakka ce a cikin A.B, wake daya mai shegen doyi, mai son bata musu zuri'a, to nayi kadan, ba'a haifeni ba. Na tattara dukkan karfina da yayi mini saura wurin ture Fa'iz da lullubar da yayi mini da jikinsa, na mike duk jikina yayi rudu-rudu yayi birdin-birdin nayi hanyar kofa. Fa'iz mikewa yayi ya riga ni isa ga kofar ya rufeta da nashi mukullin, cikin kuka na ce. "Ko kai maye ne Fa'iz ka saki kurwata hakanan! Bar ganin ka hadani da iyayena, Hajjah da dukkan 'yan uwa na har yanzu ina da sauran mai mara mini baya wajen ganin ka rabu dani ka sakeni da ka ki da ka so. Shin wai ni kadai ce mace a duniya ne? Koko cewa akayi daga kaina an daina haihuwar 'ya'ya mata? Ka matsa ka bani hanya in wuce tun baka jawo an fitar min da raina daga gangar jikina ba". Fa'iz yayi murmushi hadi da rausayar da kai cikin ginshirar tasa, ya gyara tsayuwarsa hannuwansa duka biyu zube cikin aljihu ya ce. "Ba ke kadai ce mace a duniya ba Fa'izah, kuma ba'a ce daga kanki an daina haihuwar 'ya'ya mata ba. Karewa ma, akwai mata da suka fiki komai a ko'ina cikin duniya. Sai dai ke kadai ce wadda aka jarabci zuciyata akanta, aka jarrabeni da sonta da kaunarta. Don haka ina mai baki hakuri ki saurari abinda nake son bayyana miki, ki daina daukar fansa a bisa abinda baki sani ba...". "Mene ne abinda ban sanin ba? Na kwana na hantse da sanin cewa ni ce mutum ta farko da ka fi tsana a rayuwarka. Dalilin ka na zuwa kace kana son nawa yanzu ne ban sani ba, ba kuma na bukatar sani. Abinda nayi amanna dashi shi ne... makiyin ka baya taba dawowa ya zama masoyinka sai in yana da wata boyayyar manufa akanka. To ALLAH YA FI KA!!!". Na karashe cikin rishin kuka wanda ke tafe tun daga karkashin zuciyata. Shiru Fa'iz yayi, bakina kawai yake kallo cikin mamaki, nawa da na kansa. Wata zuciyar na gaya masa ya hakura da Fa'izah ko ita ce autar mata, wata na tankwabe hakan. Cikin wannan halin kalamaina suka ci gaba da dukan dodon kunnensa. "Wanda duk ya baka shawarar wadannan gayyar tsiyar da tarin akwatunan shirgin ka za su sayi zuciyata wallahi yayi maka karya, domin ba tsirara ka ganni ina yawo ba, ka baro gini tun ran zane. Wanda duk ya ce maka hadani da iyayena suyi ta dukana shi ne zai sa in soka ya yi maka hudubar banza, domin babu abinda dukan Baba ke karamin baya ga TSANAR KA...! Aure kuma kaje ka rike, kayi ta rikewa. Ka ninka shi ba sau uku ba, sau dari. Sai dai fa kama daina mafarkin zan bika ko kofa ta kashi. In Allah Ya yarda, insha-Allah ba zan sake cewa ka sakeni ba. Sai dai jikin Fa'izah da ya kwadaitar da kai ga AURENTA ba zai taba zama mallakin ka ba. Ya gwammace ya zama na arnan bariki, 'yan daudu da 'yan ashana...da dai ya zama mallakinka". Ban rufe baki ba daga furucin naji saukar tafukan Fa'iz a fuskarta, mari ta ko'ina hagu da dama. Ya fisgoni ya angiza ni na fadi akan kafafuna, kamin in wartsake in gane abinda ya ci gaba da gudana babu Fa'iz a dakin sai takalman shi. Kamin inyi tunanin abin yi (next) Fa'iz ya shigo tare da Baba fuskarshi tayi jajawur idanunshi sun rine har wani blue-blue suke cikin bala'in da ban taba gani ba. Ya ce, "Fa'izah ga Baba, maimaita abinda ki ka fada mini yanzu a gabansa". Na fashe da kuka, "Ni me na ce? Na ce ne ba inda zani, ba zan bikan ba". Baba ya ce, "To-to ya isa haka". Ya duka ya dauki dankwalina dake yashe a kasa ya rufa mani aka, ya ce. "Oya, ku tafi kusan nayi, kada wanda na kara ganin kafarshi cikin gidana, in ba harkar arziki ta kawo ku ba. Tunda ka hana a dake ta me zan iya yi mata? Ni wannan yarinyar ta isheni jarabarta ta isheni, Ku wuce ku tafi gidanku don Allah don kiyayya kusa masu ku soke junanku, aure ba za'a kwance shi ba. Ke kuma Fa'izah inji kin saka kafarki wani wuri ba inda Fa'iz ya aje tasa ba sai na tsine miki albarka... Sai na yafe ki!!!". A firgice na cira kai na dubi Baba. Kuka nake har naji babu dadi, na gyara dankwalina, bana ko batun takalmi balle mayafi, tuni na riga Fa'iz kaiwa bakin mota, na bude baya na shige. Na kifa kaina jikin kujerar gaba ina rusa kuka na gani kasheni! A can cikin gida kuwa gardama ce tsakanin Fa'iz da Baba. Ya ce shi ba zai tafi dani ba a yanzun ya fasa. Ayi duba da halin da nake ciki. Wane farin ciki zai tsinta a tare dani?" Baban ya ce, "To Fa'iz in ka saki auren ne kamar yadda take so ka bani takarda wadda zan nunawa Hajjah da sauran dangi Fa'iza tayi zama mai dalili a gidana, domin Hajjah har ta fara nuna fushinta da zaman Fa'izah tare da mu bamu mikata Kaduna ba. In kuma kana aure, to Fa'izah bata kara zamar min gida ta kara kwana daga yau. In baka tafiya da ita inda kake kasan inda zaka ajeta amma ba dai gidana ba! Yarinya daya tal na neman zautar dani kamar ita kadai na haifa? Na gaji wallahi". Fa'iz ya sake kwantar da murya ya ce, "Baba Fa'izah ta rantse ba zata zauna dani ba. Ta yaya zan kaita inda ake ganin mutunci na ake girmamani ta dizgani ko ta rufe ni da duka don Allah Baba? Ni kam a kyale Fa'izah, ayi mata addu'a ta samu saukin bacin ranta kafin mu tafi. Amma bai dace in tafi da ita cikin wannan hali ba". Baba ya ce, "Na gama maganar nan Fa'izu, Fa'izah ba zata sake kwana mini cikin gida ba sai in baka aure. To wannan kuwa, bani da yadda zanyi da ita". Fa'iz ya fice fuuu shima nashi ran a bace. Ba haushin Baba yake ji ba, zuciya yayi mai cewa ya yiwa Fa'izah duk abinda take so don a zauna lafiya. Kamar yadda Baba ya gaji shima ya gaji. In so cuta ne to hakuri ma magani ne. Bai taba ganin yarinya mai taurin kai da taurin zuciyar Fa'izah ba da kullaci wanda baya jin lallashi. Ya bude kofar motar ya shiga ya zauna, har ya tayar da ita ya juyo yaga ban rufe kofar ba. Ya fito yazo ya rufe ya sake ta da motar aguje, ban san inda ya nufa ba sai dai jikina ya bani ba Kano bane, ba Kaduna bane. Ya manta shaf da Shu'aib dan rakiyarsa. Shima Shu'aib din yana kallon mu muka fita bai yi gigin binmu ba. Nayi kuka nayi kuka har na gode Allah, na kuma ba uku lada. Hawaye sun kafe, murya ta dishe, haka idanuna sunyi luhu-luhu. Don haka nayi shiru na zubawa sarautar Allah ido ta hanyar kurawa tsirrai halittar Ubangiji ido dake giftamu aguje suna tsere da junansu (bishiyoyi da dazuzzuka). Ko ma mahalaka Fa'iz zai kaimu, a wannan lokacin ban damu ba. Domin na fidda rai da rayuwar farin ciki tunda iyayena da suka haifeni ma basa so na, na kuma tsani rayuwar ita kanta muddin tare da Fa'iz zan yi ta. Na kuma tsani wani abu wai shi farin ciki ya sake ratsowa cikin rayuwata.. [19/02 4:34 PM] Sumayya Takori: **** A ZARIA A wannan rana wadda ta kasances asabar din karshen watan Agusta cikin 'Area One', Walida da Abdallah duka suna gida sunzo hutun karshen zangon karatu na biyu daga makarantun su daban-daban. Ina kwance cikin dakin Walida wanda yanzu ya zama nawa tunda ita ba zaman gidan take ba, sanye da riga da zani na atamfa mai karshen tsada (Exclusive Sharaton) ruwan ganye mai ratsin hoda, kaina ban daura kallabin atamfar ba yana dai ajje gefen gadon, na hade gashin kaina cikin tafkeken 'hair-bound ina karanta sabon littafin Takori ne mai suna 'KWANA SITTIN'. Zuciyata ta tafi gaba daya cikin rayuwar (schezophrenic_Safeenah) mai tsananin ban tausayi. A wani bangaren, ba Safeenar nake tausayawa ba kamar Kabir Danbatta, na rasa shi da Dr. Dangi wa yafi dacewa da amsar ragamar rayuwar Safeenah? Kowannen su masoyinta ne na hakika. Muryar oyoyon da Walida ke yi ya katse min karatun, na bi hadaddun jakunkunan da Shu'aib ke shigowa da su dakin namu yana dora daya kan daya da kallo ina kissimawa cikin raina, wane irin baki ne muka yi masu tafe da jakunkuna 'classic' haka kuma har dozen? To kwana nawa suke nufin za suyi a gidan namu? Kamshin sassanyan turaren (212) na maza ya sirnano cikin hancina, wani irin kamshi da ban taba jin mai sanyi da dadinsa a duniya ba. Wadanne irin baki ne momi tayi haka? Abinda nake tambayar kaina kenan. Daga inda nake kwance na jiyo muryar ma'abociyar ginshira, na tambayar Walida ina Momi da Baba? Walida ta ce, "Momi na gurin aiki, Baba na cikin makaranta. Amma Yaya Fa'izar tana ciki tana karatu". Da murmushi fal a fuskarsa ya ce. "Karatu? Ko dai kuka Walida?" Ta ce, "Wallahi karatu take, kullum ma karatu take, ta je kasuwa ta sayo littattafan TAKORI na da dana yanzu, su take karantawa kullum, ta daina kukan tuni...". Muryar FA'IZ, FA'IZ GIWA, FA'IZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA! Da kwarin gwiwarsa ya yi sallama a dakin cikin 'husky voice' din da Allah Ya yi musu baiwarta zuri'ar Abubakar Bamalli Giwa bakidaya. Ya samu wannan kwarin gwiwar ne daga labarin da ya samu a bakin Walida masu nuna na kwantar da hankalina tunda har ina karatu? Duk da kwakwalwarsa bata fahimci littattafan TAKORIN da Walida take bayani akai ba, ya dai fahimci NOVELS ne wanda ba zai ce na Hausa ne, na Turanci ko na Larabci ba, tunda bai san mene ne ma'anar TAKORIN ba, bai ma taba jin kalmar ba cikin kowanne yaren. Abinda ya fahimta shi ne TAKORIN 'is an author' tunda yaji ance NOVELS dinta. Banda wannan kwarin gwiwar da ya samu ya samu karin na Momi da Baba duka basa nan yadda zasu ji dadin babbaka juna a wuta idan ta kama. Babu mai ceton dayansu. Yau za ayita ta kare (he can no longer tolerate it anymore!!! Kamar yadda ya ce da Mama ne ya zo daukar aurensa (dead or alive) haka yake har zuciyarsa. In har littafin labarin SAFEENAT MAHMOUD ALKALERI wato KWANA SITTIN na Sumayyah Abdulkadir ya amsa, to nima Fa'izar da ake yiwa sallamar na amsa. Ya shigo kansa tsaye Walida na biye dashi kamar bakinta zai tsage don murnar ganinsa ta iso har gadon da nake kwance, da murnarta take fadin. "Aunty Fa'izah ga Yaya Fa'iz!". Wani irin kallo nayi mata wanda nake jin tunda Momi ta haifeta babu mahalukin da ya taba yi mata shigensa, ba shiri ta juya har tana cin karo da (stool) din madubi, saura kadan ta kifa. Da sauri Fa'iz ya riko hannunta ya rike gam. "Ina zaki matas? Ke da nazo muyi zance? Zauna hira za muyi kafin su Momi su dawo". Walida a daburce take, ya jata suka isa har gefen gadon da nake kwance suka zauna har rigarshi ta rufe min kafa kadan. In banda kamshin sassanyan turaren shi ba abinda ke tashi a dakin. Ya bige da tambayar Walida sha'anin makaranta tana bashi amsa a darare, kokarin zamewa take ta barmu yana kara shimfido mata tambayoyi akanta da kannenta su Waild, Kausar da yayanta Abdallah da nasu karatun. Ganin ba zai barta ta tafi ba ta ce, "Yaya Fa'iz bari in kawo maka ruwa da lemo in kaiwa yaya Shu'aib abinci falo". Ya ce, "Kada ki damu Walida, na cika cikina a Kaduna, haka shima Shu'aib. Yaushe Momi za ta dawo?" Walida ta kalli inda nake bamu hada ido ba, amma taga yadda kwayar idanuna suka kada suka yi jajawur, numfashina ke sauka da sauri-da-sauri har wani irin huci nake kamar mesa babu rahma cikin su dai-dai da kwayar zarrah. Walida ta kara rudewa ta ce, "Na jona ruwa a (heater) Yaya Fa'iz ka barni inje in kashe kada ya kone fada Momi zata yi min". Ya ce, "To kiyi sauri nima ba zama zanyi ba, sako zan baki wurin Momi sai mu wuce". Ta ce, "Toh". Da saurinta ta fice har tana sake tuntube da dokin kofa. Ya girgiza kai ya mike ya sauke ido a kaina, tsayin mintuna biyu yana kallona kawai babu ko kiftawa. Nima kallonsa nake, wani irin kallo da ni kaina na kasa fassara shi, na takaici ne ko na kiyayya koko na gara da Allah Ya kawo ka? Ni kaina ban sani ba. Daga ni har shi babu mai niyyar daina kallon, duk da shima na kasa fassara nashi kallon. Shi ba kallon so ba, ba na kiyayya ba, ba na jin haushi ba. Yafi kama da kallon iko da raini. Ta wani fannin tamkar kallon, "Baki da yadda za kiyi dani" koko kallon "Nafi karfinki da ke da duk abinda kike takama da shi. (In another notion) kallo ne na "Yarinya na ci dubu sai ceto, kiyi duk abinda za kiyi" Sai da ya mula don kansa ya ce. "To ni Aunty Fa'izah zan wuce Giwa, tunda na iso Hajjah bata ganni ba, lefenki na kawo miki, wanda kowa ya kasa kawo miki tunda kin zama Faskari, mai faskarawa mutane kai. Sai tsarabar da nayo miki a tafiyar da nayi, tunda babu gaisuwa ko ta Musulunci a tsakaninmu. Daman nazo ne in shaida miki zaman nan ya isa haka! Ranar (monday) kwana ki shidda kenan masu zuwa ki kimtsa kayanki da duk abinda kike bukata za ki tare a gidanki kamar sauran 'yan uwanki, don gaskiya fisabilillahi kin takurawa su Momi da alama har su Walida kin takura musu, nima kuma kin takura min. Haka kawai ina da mata amma bani da maraba da gwauro. Gara mu kauce haka muma mu manta komi, da duk abinda ya faru a baya, mu fuskanci sabuwar rayuwar dake tunkaro mu, muka kuma bude ido rana daya muka ganmu cikinta. Wato rayuwar aure. Sai mu rungumeta, mu kasance cikin godiyar Ubangiji da neman dacewa duniya da lahira". Da ace Fa'iz yasan tashin hankali da bala'in da kalaman dake fita daga bakinsa suke kara jefani da ko da wuka a makoshi bai yi gigin furta su ba. Domin kalamai ne da ban taba jin mafi muninsu a duniya ta ba. (Hada rayuwa ta har abada da shi FA'iZ-ABUBAKAR) koko ince makiyina. Mugun dan uwa da kullum ketowar alfijir da faduwar rana sai nayi dakacen INAMA ban hada jini da shi ba. Wani kwayan mutum guda daya da ya maida mahaifiyata marainiyar wayonsa, ya maida ni kwallon takawarsa a duk sanda ya so, ko gare-gare abin wasan yara. Mikewa nayi gaba daya na littafin KWANA SITTIN ya fado daga ruwan cikina, na ce. "Da uwar wa zaka tafi wurin direbancin?" Tsalle daya nayi sai gani a bakin kofar dakin nayi maza na rufe na murza 'key' na zare shi na cilla shi waje ta taga cikin wani irin zafin nama da ni kaina ban san inada shi ba. Ya yi maza shima ya cafe mukullin cikin irin nashi (exceptional) zafin naman wanda yafi nawa kafin ya kai ga ficewa ta tagar. Ya shiga sosa keya da (key) din ya daure fuska sosai kamar ba shi ne ya gama maganar da yayi cikin raha ba. "Meye haka? Gafara ki bani hanya na wuce". Na ce, "Wucewa kam zaka yi ta, tunda har ka yi nasarar amsar mukulli. Amman fa bayan rubutun saki uku ris a gareni FA'IZA A.A GIWA". Murmushi ya yi, "Wannan ne kuma ba zaki samu ba har abada Fa'izah, har kuma yaumil-ardhi. Domin ban aureki don in saki ba. In haka ne tun farko ba zan fara ba. Karewa ma, ni ba lallaminki nazo yi ba kamar wancan karon, UMARNI ne ki hada kayanki ranar litinin za ki tare a gidanki kamar kowacce mace mai aure. Ba kuma neman afuwarki ko kiyi min uziri nazo ba tunda ke abu ba ya karewa a wajenki kamar cin kwan makauniya. Ki matsa na ce, tun hannuna bai kai fuskarki ya yi mata tabon da bata da shi ba...". Sunkuyawa nayi kafin ya kai karshen maganarsa na dauko littafin da Walida ta kammala rubutu dasu, na yago takarda a ciki na mika mishi. "Ko da can babu wani wasa makamancin 'game' ko 'April-fool' da ya taba shiga tsakaninmu balle yanzu da kowannen mu ya mallaki hankalin kansa. Za ka wuce din babu haufi, kuma babu makawa, amma fa bayan ka yi rubutun nan". Na sake mika masa takarda. Fa'iz ya sanya (key) cikin aljihun kaftanin shaddar dake jikinsa. "Kenan har wani hankali kika mallaka yanzun? Ko daya! Kina nan yadda kike; Jiya 'i yau, kazama, dakikiya, 'yar kauye, mummuna. Don haka daina cewa wani wai kin mallaki hankali, ina hankalin yake nan kana tura kanka cikin jahannama kana ji kana gani?" Na ce "In shiga wutar mana, tunda ba tare za'a sanya mu ba ina ruwanka?" Ya ce, "Naga alama abin naki nema yake ya wuce na rannan, to ba zan rubuta ba kiyi duk abinda za kiyi". Anan kam dankwalina na janyo nayi dammara dashi a kuguna kamar wata sabon hauka, na doshi Fa'iz da takarda har na iso gabansa. Sai dai kuma zuciyata cike da taraddadin murdaddun damatsan Fa'iz da na hango ta cikin kayan jikinsa. Ina tunanin idan ya cafke ni da su wa zai kwace ni? Babu kowa a gidan sai yara na kuma kama kofa na kulle? Da alama shima ya shirya yau. Idona ya kyallo min biro a aljihun gaban rigarsa, na cizgo shi, na matsa gabanshi sosai har muna iya jin hucin numfashin juna. Kallon zakaru masu shirin dambacewa muka tsaya muna yiwa juna. Sai na samu kaina da ganin wautata anan, shin in nayi duka ta ina zai shigi wannan 'giant' din? Fa'iz kato ne sosai mai tsayi da kauri, kaurin da ba kiba ke haifar dashi ba 'diet' ne da hutu na yanayin rayuwa mai nagarta. Don haka na fashe da kuka tabbacin Fa'izun yafi karfina kamar yadda ya ce, babu yadda zanyi dashi. Sai na ce a raina. "bari kawai kaifin harshe na ya zama makamaina". Cikin kuka na ci kwalarshi amma fa kada ki so ki tona bugun da zuciyata ke yi, na ce. "Idan har ka haifu cikin uwa da ubanka ka rubuta min takardar nan Fa'iz...". Ban kai karshen kalamina ba ya fidda hannu ya shimfida min wasu irin gigitattun mari hagu da dama. Na nemi ji na da ganina na wucin-gadi na rasa. Naga giftawar wasu taurari masu hasken dake tafiyar da ganin dan-Adam na lokaci mai tsawo, ji kake fauuu! fauu!! fau!!! Yasa tsayayyun kafadunshi ya ingije ni gefe guda na fadi warwas akan dandagaryar kafet. Ya nufi kofa ya zaro dan mukullin a aljuihunshi yana kokarin sanyawa jikin kofar, nayi kukan kura na wawuri abin zaman kwalliya (stool) na jefe shi dashi, ya same shi a baya. Yasa hannu ya rike kafadarshi ya kuma juyo cikin dan bude ido ya ce. "Kin gama?" Na tsala ihu na taso nayi kanshi da duka da duk iyakacin karfina da hannayena hagu da dama. Ganin duka wannan bai min ba, domin kamar ba jikinsa nake duka ba, sai na kai kaifafan hakorana damtsenshi shi, cewa yake. "Fa'izah baki da hankali ko?" Irin bude kofar da aka yi ba zato ya sanya Fa'iz hankadani tsakiyar gado wanda ke nufin da can dukan nawa da cizon nawa bai dameshi ba sai gudun kada a shigo a ga ina dukanshi. Gaba dayanmu muka bi kofar da kallo cikin firgita. BABA NE! Ya ce, "Kai amma Fa'izu anyi sullutun banza! Ka tsaya kanwar bayan ka na lallasa ka kana tsaye sororo, shashasha, sahorami". Cikin kuka na ce, "Baba shi fa ya mareni, yayi min dukan tsiya har da rufe kofa don ma kada wani yazo ya taimakeni, dubi yadda ya dauki tebirin nan ya kwada mini a baya...". Baba kam bai tsaya saurarona ba ni da karerayi na ya dauko dorinar da yakewa su Walida barazana da ita in sunyi laifi yayo kaina. Fa'iz ya kama bulalar da karfi ya rike, ya ce. "Haba Baba! In Fa'izah na haukan shirmenta bai dace kowa ya biye mata ba". Na ce cikin gunjin kuka, "Kai ne shirmammen, mahaukacin, amma ni lafiyata kalau". Baba ya yi salati, ya fisge bulalar daga hannun Fa'iz ya shiga tsula mini ta ko'ina ina ihu ina zagin Fa'iz ban fasa ba. Fa'iz ya sake damke bulalar ya ce, "Baba ya isa haka nan. Ka yiwa Allah da darajar marigayi kayi hakuri". Idanun Baba sun rine da bakin ciki da takaici, ya ce. "Fa'iz ko ka cikani ko in kakkarya Fa'izah da hannuna, ina amfanin wannan jarababbiyar yarinya cikin A.B?" Ya fisge bulalar daga hannunshi, ya ci gaba da shimfida mini da iyakacin karfinshi. Da Fa'iz yaga Baba na shirin illata ni (and he has no regret for it) Sai ya fado kaina gaba daya yayi min rumfa da faffadan kafadunshi, ya zagaye ni da hannayenshi ya rungume ya ce. "Sai dai ka nakasta mu tare Baba! Amma ba zan zuba ido a kashe Fa'izah akan gaskiyarta ba!!". Baba ya yada bulalar ya fice yana fadace-fadace, bai dai yi min baki ba, sannan bai yi tir da haihuwarta ba amma ya ce ni zakka ce a cikin A.B, wake daya mai shegen doyi, mai son bata musu zuri'a, to nayi kadan, ba'a haifeni ba. Na tattara dukkan karfina da yayi mini saura wurin ture Fa'iz da lullubar da yayi mini da jikinsa, na mike duk jikina yayi rudu-rudu yayi birdin-birdin nayi hanyar kofa. Fa'iz mikewa yayi ya riga ni isa ga kofar ya rufeta da nashi mukullin, cikin kuka na ce. "Ko kai maye ne Fa'iz ka saki kurwata hakanan! Bar ganin ka hadani da iyayena, Hajjah da dukkan 'yan uwa na har yanzu ina da sauran mai mara mini baya wajen ganin ka rabu dani ka sakeni da ka ki da ka so. Shin wai ni kadai ce mace a duniya ne? Koko cewa akayi daga kaina an daina haihuwar 'ya'ya mata? Ka matsa ka bani hanya in wuce tun baka jawo an fitar min da raina daga gangar jikina ba". Fa'iz yayi murmushi hadi da rausayar da kai cikin ginshirar tasa, ya gyara tsayuwarsa hannuwansa duka biyu zube cikin aljihu ya ce. "Ba ke kadai ce mace a duniya ba Fa'izah, kuma ba'a ce daga kanki an daina haihuwar 'ya'ya mata ba. Karewa ma, akwai mata da suka fiki komai a ko'ina cikin duniya. Sai dai ke kadai ce wadda aka jarabci zuciyata akanta, aka jarrabeni da sonta da kaunarta. Don haka ina mai baki hakuri ki saurari abinda nake son bayyana miki, ki daina daukar fansa a bisa abinda baki sani ba...". "Mene ne abinda ban sanin ba? Na kwana na hantse da sanin cewa ni ce mutum ta farko da ka fi tsana a rayuwarka. Dalilin ka na zuwa kace kana son nawa yanzu ne ban sani ba, ba kuma na bukatar sani. Abinda nayi amanna dashi shi ne... makiyin ka baya taba dawowa ya zama masoyinka sai in yana da wata boyayyar manufa akanka. To ALLAH YA FI KA!!!". Na karashe cikin rishin kuka wanda ke tafe tun daga karkashin zuciyata. Shiru Fa'iz yayi, bakina kawai yake kallo cikin mamaki, nawa da na kansa. Wata zuciyar na gaya masa ya hakura da Fa'izah ko ita ce autar mata, wata na tankwabe hakan. Cikin wannan halin kalamaina suka ci gaba da dukan dodon kunnensa. "Wanda duk ya baka shawarar wadannan gayyar tsiyar da tarin akwatunan shirgin ka za su sayi zuciyata wallahi yayi maka karya, domin ba tsirara ka ganni ina yawo ba, ka baro gini tun ran zane. Wanda duk ya ce maka hadani da iyayena suyi ta dukana shi ne zai sa in soka ya yi maka hudubar banza, domin babu abinda dukan Baba ke karamin baya ga TSANAR KA...! Aure kuma kaje ka rike, kayi ta rikewa. Ka ninka shi ba sau uku ba, sau dari. Sai dai fa kama daina mafarkin zan bika ko kofa ta kashi. In Allah Ya yarda, insha-Allah ba zan sake cewa ka sakeni ba. Sai dai jikin Fa'izah da ya kwadaitar da kai ga AURENTA ba zai taba zama mallakin ka ba. Ya gwammace ya zama na arnan bariki, 'yan daudu da 'yan ashana...da dai ya zama mallakinka". Ban rufe baki ba daga furucin naji saukar tafukan Fa'iz a fuskarta, mari ta ko'ina hagu da dama. Ya fisgoni ya angiza ni na fadi akan kafafuna, kamin in wartsake in gane abinda ya ci gaba da gudana babu Fa'iz a dakin sai takalman shi. Kamin inyi tunanin abin yi (next) Fa'iz ya shigo tare da Baba fuskarshi tayi jajawur idanunshi sun rine har wani blue-blue suke cikin bala'in da ban taba gani ba. Ya ce, "Fa'izah ga Baba, maimaita abinda ki ka fada mini yanzu a gabansa". Na fashe da kuka, "Ni me na ce? Na ce ne ba inda zani, ba zan bikan ba". Baba ya ce, "To-to ya isa haka". Ya duka ya dauki dankwalina dake yashe a kasa ya rufa mani aka, ya ce. "Oya, ku tafi kusan nayi, kada wanda na kara ganin kafarshi cikin gidana, in ba harkar arziki ta kawo ku ba. Tunda ka hana a dake ta me zan iya yi mata? Ni wannan yarinyar ta isheni jarabarta ta isheni, Ku wuce ku tafi gidanku don Allah don kiyayya kusa masu ku soke junanku, aure ba za'a kwance shi ba. Ke kuma Fa'izah inji kin saka kafarki wani wuri ba inda Fa'iz ya aje tasa ba sai na tsine miki albarka... Sai na yafe ki!!!". A firgice na cira kai na dubi Baba. Kuka nake har naji babu dadi, na gyara dankwalina, bana ko batun takalmi balle mayafi, tuni na riga Fa'iz kaiwa bakin mota, na bude baya na shige. Na kifa kaina jikin kujerar gaba ina rusa kuka na gani kasheni! A can cikin gida kuwa gardama ce tsakanin Fa'iz da Baba. Ya ce shi ba zai tafi dani ba a yanzun ya fasa. Ayi duba da halin da nake ciki. Wane farin ciki zai tsinta a tare dani?" Baban ya ce, "To Fa'iz in ka saki auren ne kamar yadda take so ka bani takarda wadda zan nunawa Hajjah da sauran dangi Fa'iza tayi zama mai dalili a gidana, domin Hajjah har ta fara nuna fushinta da zaman Fa'izah tare da mu bamu mikata Kaduna ba. In kuma kana aure, to Fa'izah bata kara zamar min gida ta kara kwana daga yau. In baka tafiya da ita inda kake kasan inda zaka ajeta amma ba dai gidana ba! Yarinya daya tal na neman zautar dani kamar ita kadai na haifa? Na gaji wallahi". Fa'iz ya sake kwantar da murya ya ce, "Baba Fa'izah ta rantse ba zata zauna dani ba. Ta yaya zan kaita inda ake ganin mutunci na ake girmamani ta dizgani ko ta rufe ni da duka don Allah Baba? Ni kam a kyale Fa'izah, ayi mata addu'a ta samu saukin bacin ranta kafin mu tafi. Amma bai dace in tafi da ita cikin wannan hali ba". Baba ya ce, "Na gama maganar nan Fa'izu, Fa'izah ba zata sake kwana mini cikin gida ba sai in baka aure. To wannan kuwa, bani da yadda zanyi da ita". Fa'iz ya fice fuuu shima nashi ran a bace. Ba haushin Baba yake ji ba, zuciya yayi mai cewa ya yiwa Fa'izah duk abinda take so don a zauna lafiya. Kamar yadda Baba ya gaji shima ya gaji. In so cuta ne to hakuri ma magani ne. Bai taba ganin yarinya mai taurin kai da taurin zuciyar Fa'izah ba da kullaci wanda baya jin lallashi. Ya bude kofar motar ya shiga ya zauna, har ya tayar da ita ya juyo yaga ban rufe kofar ba. Ya fito yazo ya rufe ya sake ta da motar aguje, ban san inda ya nufa ba sai dai jikina ya bani ba Kano bane, ba Kaduna bane. Ya manta shaf da Shu'aib dan rakiyarsa. Shima Shu'aib din yana kallon mu muka fita bai yi gigin binmu ba. Nayi kuka nayi kuka har na gode Allah, na kuma ba uku lada. Hawaye sun kafe, murya ta dishe, haka idanuna sunyi luhu-luhu. Don haka nayi shiru na zubawa sarautar Allah ido ta hanyar kurawa tsirrai halittar Ubangiji ido dake giftamu aguje suna tsere da junansu (bishiyoyi da dazuzzuka). Ko ma mahalaka Fa'iz zai kaimu, a wannan lokacin ban damu ba. Domin na fidda rai da rayuwar farin ciki tunda iyayena da suka haifeni ma basa so na, na kuma tsani rayuwar ita kanta muddin tare da Fa'iz zan yi ta. Na kuma tsani wani abu wai shi farin ciki ya sake ratsowa cikin rayuwata.. [19/02 4:34 PM] Sumayya Takori: *** Ban tashi kaduwa da al'amarin Fa'iz ba sai da na ganni cikin jihar Niger (Minna). Ya samu gefen wani titi yayi (parking) ya doshi wasu masu kirar wukake da ludaya na garin Minna ya yi cinikin wata sharbebiyar wuka gayawa jini na wuce, irin ta yankan shanu, suka yi 'yar magana da makerin, sai naga an fara rubutu a jikin wukar. Ya kunso wukarshi cikin takarda ya biya kudi ya shigo ya ajeta a gefenshi ya kunna mota. A raina na ce. "Eh, gara kayi min yankan rago ya fiye mini da hada rayuwa da kai. Mugu, azzalumi, munafiki, mara imani. Ko kuma kayi min yankan kifi gunduwa-gunduwa zai fiye min kwanciyar hankali fiye da in karashe rayuwata matsayin matar Fa'iz Bamalli Giwa. Uhh! Daga wurin masu wuka kun san ina Fa'iz ya dosa? Fa'iz shahararren kogin Nigeria da nake ji cikin tarihi da 'Geography' sanda nake sakandire, wato 'RIVER NIGER' ya nufa damu wanda an tabbatar yanki ne daga kogin Nilu (Nile). Can ya dosa damu gadan-gadan ya zagaye masu kamun kifi zuwa can inda babu mutane ko daya. Ya danna wani madanni jikin motar glassai bakake suka maye gurbin farare (tinc) suka rufemu ruf. Ya kwantar da kujerarshi baya sosai ya bita ya kwanta yayi matashi da hannayensa ya yi 'facing' dina (fuskantata) sai kuma ya yunkuro ya taso ya dauko wukar nan ya cireta daga cikin takardarta tana walwali da walkiya. Duk da abinda na ce a baya na gara min ya kashe nin, yayi min yankan rago ko na kifi gunduwa-gunduwa amma a wannan lokacin da matuwar ta iso muraran sai na samu kaina da matsawa gefe na soma marmasa kalmar shahada tare da duk irin addu'ar da tazo bakina. Walwali take da walkiya inba za'a ce idona bane yake min gizo da sai ince har huci wukar take yi. Sunan Allah nake kira a halshena da zuciyata, idanuna sun kankance sunyi wuri-wuri, amma babu hawaye a cikinsu sai firgita da razana. Na tabbata yanzu Fa'iz ya fini hauka, na dubi rubutun da aka yiwa wukar a sace, "FA'EEZAH". Na fiddo ido kuru-kuru na sake makurewa jikin kofa. Fa'iz ya cillo mini wuka akan cinyata ya tube riga baki daya, har singiletin jikinsa itama ya cire yayi kira da kakkausar murya. "Fa'izah!". Subhanallahi-subhanallahi, Hasbunallahu wani'imal wakeel kawai na shiga furtawa, na runtse idanuna. Ban taba ganin namiji a tube ba balle kato mai girma irin Fa'iz, yayinda haiba da kwarjini na Fa'iz Giwa yayi min lullubi, ya kara fuskantata ya ce. "Dauki wukar nan ki caka mini ko ki yanka ni karewar kiyayya kenan, ko kya huce bakin cikin zamowa na miji a gareki, ko kya yafe laifin da kike ikirarin na miki, wanda kika kasa yafewa! Kika kuma ki saurarona inyi miki bayaninsa. Idan kika yi hakan na tabbata zaki huce ba karya...". Nayi salati na dire ba tare da na kai karshen sa ba na dauko sabo. Na ture wukar daga cinyata ta fadi kasan kujera, na soma murda murfin motar ko na samu ya bude in san inda dare yayi min amma ko gezau kofa bata yi ba, yasa (lock) ya kulle ta gaba daya. Cikin dakiya da tsare gida ya ce. "Haba Fa'izah, (be brave) mana! Babu wanda zai sani, babu wanda zai ganki. Na tabbata in kin yankani zaki huce kiyi rayuwa mai dadi da nagarta. Ki samu rangwamen kullaci na dake zuciyarki na zagin Momi, mugunta da azabar dana kwashe shekaru ina yi miki, takardar saki dana hanaki, tare da huta auren direban tasha tunda ni dai hannuna ba zai iya rubuta saki ga Fa'izah ba ko da ace na iya rubutu!!!". Idona rufe na ce, "Fa'iz ka bude min kofa in fita, naga alama ka haukace. Wallahi ba don komai na yarda na sanyo kafata a motar ka ba sai don furucin Babana, na yafeni da ya ce zai yi". Na fashe da kuka. Ya sake matsowa ya dauki wukar dana yasar, ya ce cikin taushin murya. "Fa'izah, ki kwantar da hankalinki ki yanka ni, kinga in ba hakan kika yi ba baki huce haushi na ba, baki kuma ci nasarar kiyayyarki ba. Kamar yadda bakin cikina ba zai kyale zuciyarki ta samu sassauci ba don kuwa ni ba sakinki zanyi ba...". A yayin da ya zura min kotar wukar cikin hannuna, nayi maza na yi baya da hannuna na kwalla kara tun karfina. Ihun da ake kira kunu a makota babu wanda yasan ina yi. Ihu nake ina karawa ko Allah Zai kawo wani giftawa yaji ya kawo min dauki. Sai dai ga dukkan alamu ihu na ya tsaya ne cikin motar kadai ko ta taga baya fita. Ya ce (in subdued) wato cikin raunin murya. "Ki yiwa Allah ki aikata abinda na umarce ki, sai ki jani ki tura cikin kogin nan. Babu wanda zai ganki, wukar ma ki jefata cikin ruwan. In yaso ki samu wani ki roke shi ga kudi zan bar miki ya tuka ki zuwa Kaduna ko Giwa tunda baban ABU yasan tare muka fita...". Na girgiza kai da sauri, "Ko da nake kinka babu yadda za'ayi in kashe ka da hannuna tunda ba ni nayi maka ran ba. Sai dai na kasance cikin addu'ar Allah Ya kashe ka in huta wannan bala'i". Wannan karon murmushi ya yi, sannan ya cira ido a hankali ya dube ni. "Kin kasa gane abinda nake ankarar dake har yanzu, wato babu wanda zai ganki, ki kashe ki tura RIVER NIGER shi ne maganin kiyayyarki ga Fa'iz. To tunda kina tsoron kama wukar taki...". "Ka daina cewa wukata, ba tawa bace, kai ka san inda ka samo abarka...". "Ai don ke aka yi ta. Ko baki ga sunanki ne a jiki ba? Wai ma shin, ina haukanki da rashin imaninki yaje ne da kike yin baya-baya dani yanzu ba kamar dazu da wannan bakin ke gartsa min cizo ba?" "Na rantse da Allah ka isheni, ka maida ni inda ka dauko ni, ko kuma ka bude min na fita". Ya sha mur sosai, "Ki fita kije ina? Wajen 'yan daudu da 'yan ashana? Fa'izah babu wannan damar in har kin barni da rai. Baya ga wannan kyakkyawar dama da na baki, (remember that opportunity comes only once in life!) Muddin kika bar wannan damar ta subuce miki, to kiyayyarki ta karya ce... Kina son FA'IZ BAMALLI. Ba kuma zaki iya kaiwa 'yan bariki, 'yan daudu da 'yan ashana jikin da ya zam mallakin Fa'iz ba! Za ki bar mishi abinsa ne ya yi yadda yaga dama da shi daga yanzu har gaban abada! Muddin baki aikata abinda na umarce ki ba kina son rayuwar Fa'iz Bamalli Giwa ta ci gaba da wanzuwa a doron kasa...!". Ai jin hakan da ya fada, ya sani daukar wukar na riketa gam-gam cikin yatsuna amma na kasa motsa hannuna ko kadan. Sai Fa'iz ya matso gaba gareni sosai har hucin numfashinsa na dukan fuskata tare da sassanyan kamshin 212 dake tashi sannu a hankali daga jikinsa. Ya daga gira, tare da dan ware ido, ya kuma buda hannuwansa. "Uhm? Ina jiranki, (I'am ready)". Na runtse ido tamau, yayin da hawaye suka shigo kwaranya babu kakkautawa, a kundukukina, fadar Ubangiji (S.W.T) ke zuwa mini cikin kunnuwa na ta "WANDA YA KASHE A KASHE SHI" haka wanda ya kashe kansa ya mutu kafiri da sai in kashe nawa kan kowa ya huta, shi ya huta ni in huta, iyayenmu su huta. Sannan muddin na kashe Fa'iz dukkan dunguma-dunguman zunuban da na tabbatar ya wanzu yana dauka a rayuwarsa rubdugowa za suyi kaina. Baya ga haka in Baba ya nemi bayanin inda Fa'iz ya shiga bani da hujjar kare kaina. Ga wuka an rubuta sunana a jiki, idan ma na cilla ta cikin ruwan wani ya tsintota fa, ko masu kamun kifin nan? A hankali na saki wukar kasa, na sanya kaina cikin cinyoyina na shiga shakar kuka. Fa'iz murmushi yayi. "I achieve what I want to achieve, ... all of a sudden... it's obvious that you LOVE ME! (A fili ya ke kina so na, na cimma abinda nake son cimmawa)". Ya dauki wukar ya sauke (glass) ya cillata waje, ya mayar dashi yadda yake. Ya dauki farar (singletinsa ya maida, ya kuma maida shaddarsa. Ya tsallako ya dawo kusa dani ya zauna kafadunmu na gugar juna, ya shiga wakar 'YAN ASHANA' wadda marigayi Dr. Mamman Shata ya rera. Iyakar zuwa wuya na zo, ga yunwa dake cina kamar me. Babu abinda na iya baya ga rufe ido da yin shiru. Na kuma saddakar na saduda duk iskancina Fa'iz ya dameni ya shanye. Da Aunty Rabi na nan da ta kada mishi tutar da tayi alkawarin kadawa WINNER, ya tabba ni ce na fadi 'game' din, (I'am the LOSER!!!) Wasu hawaye masu zafi suka shiga biyo kuncina. A lokacin ne naji ni cikin danshi sosai a inda nake zaune, alamu ne na isowar (period) dina wanda ban zata a wannan lokacin ba. Na tabbata tashin hankali ne ya kawo shi ba wani abu ba, don lokacina bai karasa ba. Na jike sharkaf kamar wadda tayi fitsarin zaune. Don haka ko wani kwakkwaran motsi na kasa, nayi fiki-fiki dani idanuna sunyi ciki sun zurma don bala'i da kaduwa. Na kai idona ga agogon motar ya nuna karfe shidda na yamma. Shin yaushe zamu kai gida in mun fita jihar Neja yanzu? Gani da shegen tsoron 'yan fashi, bansan sanda na sake tsandarewa da kuka ba. Duk dai ni na jawowa kaina, da na kama Fa'iz na kulle a dakin Walida. Da na barshi ya wuce abinsa tun shigowarsa da ya nemi tafiya da duk hakan bata faru ba. Akuyar cikina ta sake yin kukan yunwa da karfi, ji kake farrr! Fa'iz ya dan saurara kana ya yi dariya, ya ja kujerarsa ta koma dai-dai ya yi tsalle ya haure ya koma mazauninsa ya tashi motar. Bai tsaya ko'ina ba sai tsakiyar birnin Minna. Ya karya kan motar ya shiga wani katafaren gidan saukar baki, a samansa an rubuta (MINNA GUEST INN). Ya yi (parking) a wuri na musamman da aka tanada don adana motoci cikin wata rumfa kamar tanti Hankalina ya kara tashi, me Faiz yake nufi? Hotel ya kawoni? Ni karuwa ce? Tunanina ya kasa boyuwa cikin raina sai da ya bayyana a kunnensa. "Ni karuwa ce da zaka kawo ni hotel?" Wani irin kallon biyu ahu yayi mini bai ce komai ba. Ya kashe motar ya soma tattara 'yan shirginsa dake cikin motar ya ce. "In zaki fito, ki fito. Gara da na kawo ki hotel ki zama babbar karuwa mai (class) ban kaiki matattarar 'yan daudu da 'yan asahana ba, ki zama (low level or classless prostitute)". Na kara tsananta kuka na, baki shi ke yanka wuya, da na sani banyi furucin nan ba da Fa'iz ya mayar garkuwarsa a komai. A wannan lokacin (I'm speechless) kalma ta kare a bakina. Alal hakika ina tsoron kwana cikin motar ni kadai saboda ina da labarin garin Minna cike yake da mayu tare da tunanin koda na kulle motar ba za'a rasa masu (master key) ba. Ya ce, "Ke kina bata min lokaci fa, abinda kike tunani ba shi bane, dube ki don Allah, me zan dauka anan kayan najasa? Dubi yadda ki ka batawa Baba motarsa, ni taimakon ki zanyi, a kuma wankewa Baba motarsa...". Idan na ce banji kunya ba kema kin san nayi karya. Eh, Fa'iz na da damar fada min duk abinda yaga dama. Nayi Allah Ya isa tafi cikin carbi, amma a zuciyata. Na mike da kyar, duk kafafuna sun kumbura suntum saboda zama, ya zaro ido sanda na idasa fita a motar, ya ce. "Kai-kai-kai! Ke tsaya nan, koma ki zauna kada ki bata masu (tiles) ki jawo min idon mutane, sai nayi (booking) daki tukunna zan dawo". Ban yi musu ba na koma na zauna, ko ni naso hakan sai dai babu wani alamun sassauci a fuskata. Na koma inda na tashi na zauna nayi tagumi, na gama saki da al'amarin Fa'iz ni yanzu tsoron shi nake ji ma. Tunanina na ya gangaro yadda zai yiwu in kwana daki daya da Fa'iz? Na kama kaina da hannuwa na biyu na rike, saboda barazanar tsage min da yake yi. kaina sarawa yake ta ko ina, ga kugin da cikina ke yi min babu sassautawa. Kuka ya kafe daga kwayar idona, nayi amanna babu yadda zanyi da Fa'iz yafi karfina a wannan lokacin duk ma wani yunkurin hauka ko tashin hankali da zanyi akaina zai kare don haka na alkawartawa kaina kunshe bakina don mu wanye lafiya. Nayi zama na kamar awa daya, in saka wannan in kwance kamin ya dawo ya bani zani na bakin yadi da ake kira kofilin ko (plain yard) ya dora bisa cinyata ya ce. "In kinga dama kina iya fitowa". Ban yi musu ba na fito na daura, na kwanto dankwalina na daura daga wuya. Sai a wannan lokacin ne Fa'iz ya lura ko takalmi babu a kafata balle mayafi. Ina kallon sanda ya kada kai, ya saci kallona ta gefen ido. Haka nake tafe tamkar mai tafiya bisa fasassun kwalabe saboda hardewar da kafata ke yi, duk da babu mutane sosai ko ince sunyi nesa damu a harabar (guest inn) din ji nake tamkar idanun kowa akaina yake. A lokacin duhu ya shigo, hasken fitilu ya wadata ko ina, haske ne kamar rana. Dadi daya naji da na lura babu wanda ya damu da harkar wani a wajen. Ganin irin tafiyar da nake, sai ya rage taku duk da bai tsaya mun jera tare ba. Wata sabuwa inji 'yan caca! Ganin mu nayi a bakin matattakala wanda ke nufin bene zamu hau. Nayi tsaye jimm! Rike da kafar benen ina tunanin ta yaadda zan hau shi. Ban yi aune ba naji Fa'iz ya sunkuce ni ni da kazantata ya soma taka matattakalar dani dauke a hannayensa cikin sassarfa, bai tsaya ba sai a hawa na biyu, daki mai lamba (82) yasa mukulli ya bude sannan ya dire ni, ya ce. "Ga daki nan, ki kintsa ki huta. Duk yadda naso mu koma gida a yau ba zai yiwu ba sai sanda Allah Yayi. Duk wanda ya buga in ba muryata kika ji ba kada ki bude, ko da yake 'yan ashana ne ba damuwa". Ban tsaya sauraron kalolin rashin mutuncinsa ba na nufi (toilet), shi kuma ya ja kofar ya fita yana murmushi. Kai Fa'iz sai a barshi, duk abinda zan iya nema dama wanda banyi zato ba na gani a (toilet) din, sinkin (always pad) (pantis) har shidda, dogayen riguna guda hudu, body lotion, brush da macleans har da mouth-wash, da saitin kayan wanka na 'suddenly' har da abin tazar kai, ga towels kala-kala a (toilet) din. Nan da nan ban bata lokaci ba na hada ruwan wanka cikin kwami na wanke ko'ina na jikina da ya yi tsami ya warware. Na gasa kumburarrun kafafuna da suka suntume saboda zaman mota. Sannan ne na fito daga kwamin na bude ruwan ya tafi na zura daya daga cikin dogayen rigunan da ya aje mani kalar kofi. Na wanke wadanda na tube na shanya. Na dauki brush da maclean ina goge hakorana kenan naji bugun kofa. Tare da cewa. "Zo ki bude ni ne". Ban san abinda ya ruda ni ba na kasa tsayawa in wanke kumfar baki na ko duk sabon tsoron Fa'iz daya shigeni ne oho! Da burushin a bakina da kumfar duka nazo na bude kofar. Fa'iz ya shigo rike da manyan ledoji, ban yarda mun hada ido ba na juya na koma na kuskure bakina. Na dubi kaina a madubin bandakin inda na tabbatarwa kaiwa na karamin ramewa nayi ba rana daya kacal da Fa'iz ya sanyani a duniyarsa. Duniyar bala'i da masifa. Haka na fito ina ciccin magani, inda kamshin wani hadadden gashasshen nama ya bugi hanci na. Miyau na yayi bala'in tsinkewa, na hango shi bisa (three seater) ya ja (centre table) ya dora ledar (foil-paper) mai cike da gasasshen naman mai ruwa-ruwa da yaji tumatiri da albasa yana ci yana korawa da lemon (7Alive). Na hadiyi miyau, ji kake mukut! Na samu daya kujerar na zauna ina kau da kai. Ya yi murmushi ya dauko wata ledar ya ja (table) irin nasa ya dora mini, ya mike ya shige (toilet) ya barni ina kintsa hanjin cikina wanda baya yarda aja masa aji. Bayan gashasshen naman akwai (fried sphagetti) da hadin salad. Na kusa tashi da duk abinda ke cikin ledar nan sannan na mike na isa ga dan firjin dake dakin na bude. Ya cika shi da nau'in lemuka kala-kala (squash juice) da (fruit cocktails), na dauki kwali daya na kwankwadi iya yadda zan iya nayi wata katuwar gyatsa, sannan nayi hamdala ga Allah. Sai naji bude kofarsa daga (toilet) da alama wanka yayi ya sanya ruwan madarar jallabiyya yayi sharr yayi (fresh) (very handsome) da shi. Nayi maza na dauke kaina bayan da muka hada ido. Shima cin magani yayi kada in kawo masa wargi, bai san nayi rantsuwa cikin zuciyata har ya maida ni inda ya dauko ni ba zai ji wani furuci ko wata kalma daga baki na ba. Ban zauna a kujera ba bisa carpet na zauna na mike kafafuna na dauki (remote) ina canza tasoshi har saida nazo (Bollywood) na tsaya ina kallon shirin da suke yi a lokacin mai suna (Baabul). Shi kuma sai ya dasa sallah bisa dardumar da ya sayo. A raina na ce, "Lallai direban tasha ya canza, da can mutum ne wanda baya wasa da sallah, amma yau sai da ya zauna ya take ciki yayi wanka sannan zai yi sallolin dake kansa. Ya jima yana sallar da ban san la'asar ce ko magariba ko isha ba, kamin ya yi sallama ya kunna sautin Abdurrahman Sudaith cikin wayarsa yana saurare cikin Suratul An'ami. Ya kuma shiga gyaran akaifarshi da ‘nail cutter’ yana bin karatun da wani irin sauti mai dadi da na kasa tantance Fa'iz ko Sudaith wane ne hafizin gaskiya? Dole na rage sautin talbijin tunda dai ni ba shaidan bace. A hakan wani irin barci yan soma fisgata, barci mai dadin gaske wanda na tabbata gajiya da samun nutsuwa ne suka saukar dashi. Ni dai sai juyi nayi na jini bisa tsakiyar ni'imtaccen gado, lalluve da lallausar bargo. Ban farka ba sai washegari misalin karfe goma na safe. Nayi mika, nayi salati, nayi tasbihi ga Ubangijina na nufi (toilet) na cika baho nayi wanka. Na tarar kayana da na tube na wanke jiya sun bushe don haka maimakon daya daga cikin dogayen rigunan su na mayar. Atampha ce (exclusive Sheraton) riga, zane da kallabin su. A (toilet) din na shafa (lotion) din E45 cream da ya sayo nayi daurin kallabina tsaf, sannan na fita ina cin magani ina harbin iska. Zaune yake cikin kujerar zaman mutum daya, ya daura kafa daya kan daya, yayi kyau har ya gaji cikin (light blue) din jeans, na tabbata suma siyo su yayi jiya tare da nawa kayan. Don dogayen rigunan daya sayo min ma kalar makuba maroon, milk da black daga gani sayen (boutique) ne. Rike da 'yar karamar radio yana sauraren harshen Hausa na Rediyo Najeriya Kaduna. Na samu wuri can nesa dashi na zauna na zuba tagumi. Da alama Fa'iz bai da niyyar tafiya ma kwata-kwata, na dai ja bakina na kara tsukewa cikina ya soma kiran ciroman garinmu Giwa. Ya rage sautin rediyon cikin sassaucin kallo. "Madam, babu gaisuwa?" Kokari yake mu hada idanu amma na ki. Ya yi murmushi . "Kiyi hakuri, na canza miki wurin kwanciya ne jiya saboda kada wuyanki ya kage". Ya sake yin shiru. Ya tabbata ba zai samu amsa ba. Hakan bai hana shi karawa ba. "Me kike son kiyi (break-fast) da shi?" Ya dan canza fuska, wato ya dan sha mur. "Fa'izah ba zaki magana ba?" Na sunkuyar da kaina hawaye suka soma mirginowa a hankali ta kasan idanuna. Ya aje rediyon ya taso ya iso har inda nake, ya kama hannuna na dama ya rike cikin nasa, nayi kokarin janye hannuna amma ya rike tamau, gam-gam. "Me zaki ci eye Fa'izah na?" Da wani irin karyayyen sauti, mai kassara gabban jiki da sanyaya zuciya. Da hanzari na mike na nufi (toilet), duk da nasan bani da abinda zanyi a ciki. Gaba daya jikina rawa yake yi, haduwar fatar jikimmu wani 'chemistry' ne da bazan iya fassarawa ba, mai dauke da wani irin (shock) tamkar (electrical shock). Na maida kofar bayin na rufe, na jingina da ita, na lumshe ido a hankali cikin kokarin (regaining consciousness) wanda ya yi min wahalar dawowa. Sai da na samu nutsuwa sannan na fito. Wannan karon bashi a falon. Na dauki takarda da biro nayi rubutu layi biyu kacal, ina kokarin ajeta a inda ya tashi ya bude kofar ya shigo da sallama ciki-ciki. Nima ciki-cikin na amsa, ko kadan bai ji ta ba, don dai amsawar ta zama farillah ne. Ina kokarin dagowa ya dafa ni, "Me ki ke rubutawa?" Kamshin '212' dinshi da kamshin bakinsa na (mouthfreshner) mai karfi da yayi amfani dashi ya cika hanci na. Ban son irin wannan kusantar da yake son assasawa a tsakaninmu ko kadan kuma ba zan lamunta ba. Nayi saurin aje takardar na ja da baya da zafin nama. Ya yi murmushi ya dauki takardar ya bude ya soma karantawa a fili. "Don Allah don Annabi Yaya Fa'iz ka kaini Kaduna wajen Mama. In kuma ba yanzu zaka tafi ba, to don Allah bani kudin mota in tafi, ina da abinda zanyi da yawa". Ya aje takardar ya dube ni da shanyayyun idanunsa. "Kina da wani abin yi ne dama wanda yafi mijin ki muhimmanci? Na duaka miji shi ne (foremost) a rayuwar kowacce diya mace indai tagari ce. Nima ina da abin yin na tattara na watsar saboda matata Fa'izah, ko bance ita tafi komai muhimmanci cikin rayuwata ba tana da hakki cikin lokuta na, wani neman duniya ko sabgogin duniya wadanda ba sa karewa basu isa su sa nayi watsi da wannan hakkin ba. Ko da yake nasan ke baki dauke ni a matsayin mijin ba, balle ki bani wannan muhimmancin. Zamu tafi, amma sai kinyi min magana cikin dadin rai, irin wadda macen da ke son mijinta take masa. Son samu kice I LOVE YOU YAYA FA'EEZ!!! Har sau uku. In ba haka ba, mu karashe sati biyun hutuna anan, daga nan mu wuce Birtaniya, ke da gida sai kinzo haihuwa. Kin san dai ba mai nemanki don an san muna tare. Don haka zabi na gareki". Ya juya ya soma fiddo abinciccikan daya sayo a ledar su, yana dorawa a (centre-table). Ya ci abinshi cikin kwanciyar hankali ya dora da Gahwah mai zafi (Coffee). Ya shige uwar dakin ya bi lafiyar gado da yake dakin ciki da falo ne. Amma ya sauke kafafunshi a kasa. Ni fa na kammala, ke nake jira. Na zauna na ci son raina na koshi, har da kara tea bayan na shanye kofi guda. Naji ni dai-dai, nayi hamdala ga Allah. Na kwance daurin da nayi na dankwalin atamfata na yafa da yake dankwalin babba ne sai ya rufeni ruf. Na nufi kofa na tsaya. Ya mike ya fito falon ya jingina da kofar da ta raba uwar dakin da falon, ya ce. "Au, baki ji abinda na ce ba ko? Tunda kunya kike ji dauki biro da takarda ki rubuta min kinji sabuwar kurma?" [19/02 4:34 PM] Sumayya Takori: Ban musa ba, sai dai a raina na ce, "Inji kunyar ka? Amma da nayi asara. Kunyar maras kunya ai asara ce!". Na dawo na dau takarda da biro na jingina da bango na soma rubutu. Da na kammala na aje nan, na sake komawa bakin kofa na lafe. Ya dauki takardar ba tare da ya bude ba ya sanya a aljihu ya taho yana fadin. "Kin manta da guzurinki". (Yana nufin sanitary pard). Ban bashi amsa ba ya shiga (toilet) din ya kullo duka kayan a ledar da ya shigo dasu ya fito ina ta manna masa harara kamar kwayan idanuna sa fado. Ya yi murmushin sa (broad smile) ya ce cikin rada. "Wannan hararar, wata rana kallon so zai koma, wannan hararan, wata rana in wata tayi min Fa'izah dukan tsiya zata yi mata, sai inda karfinta ya kare akan duk wanda yayi min ita. Wannan hararan, ni a ganina 'I love you ne, I can't do without you ne'. Ba abinda lokaci baya magani". Ni dai bance komai ba, kulawa ma yabawa ce koko Hausawa sunce sai an kula kashi yake doyi. "Saura ki sake batawa Baba mota, wannan karon Shu'aib zansa ya wanke. In yaso in ya tambayi na mene ne? Sai in turo miki shi kiyi masa bayani". Kokari yake mu hada ido, na ki. Na koma na sanyo (slippers) din bandakin don bai sayo da takalmi ba. Muka sauka kasa ya basu mukullin su muka wuce, 'parking lot'. Nayi-nayi in bude kofar gidan baya, na kasa ban sani ba ko kulleta yayi, dole na hakura na shiga gaba, shima ya shiga mazauninsa ganin naki rufe kofar daga inda yake ya sunkuyo har muna gugar juna ya rufo kofar ruf. Maimakon ya ja motar, sai ya bude takarda ta ya soma karantawa a fili. "I hate you. And I would never love you forever... In mafarki kake, ka farka...!!!" Ya zuba min shanyayyun idanunshi masu cike da wata irin fitina, maimakon kalamaina suyi tasiri mara dadi a kansa. Sai naga kamar dadi sukai masa. Na juyar da kai domin ba zan iya jure kalon abubuwan da ke cikin idanunshi ba masu kama da (magnet) mai jan zuciya tamkar jan wutar lantarki, wadanda a fakaice wasu irin sakonni ne suke bayyanawamasu nuna matukar bukatar miji zuwa ga matarsa ta sunnah. Sai naji wasu bangarori na jikina suna kokarin karbar wannan sako, idan har banyi da gaske na zama jajirtacciyata ba kamar yadda nake wannan mutumin zaiyi saurin cin galabata dole in kara jajircewa. Wanda ba komi bane illa kokarin ganin ban yarda mun sake kadaicewa ba. Domin nima din 'adolscent' ce mai bukatar mahadin rayuwa, don dai auren ya zo ba a yadda na so ya kasance bane. Ya kasance ya zo min tareda wani mutum da ba abinda zai yi ya burgeni a rayuwata, ko ya wanke dattinsa dake raina. Ya yi murmushin da yafi kama da takaici ya tada motar. Bai sake magana ba har muka fita garin Minna. Yayin da ni kuma na tsayar da idanuna gefen da bishiyoyi suke zuciyata cike da farin cikin ko yaya ne dai kalamaina sunyi tasiri. *** Wajejen karfe uku sai gamu cikin garin Kaduna. Ya karya kan motar ya dauki hanyar anguwar Kabala Custain. Ni sam bam ma san nan gidan Ummi yake ba. Yayi (parking) bayan maigadin gidan ya bude get din gaba daya. Su Yahya ne suka fito ashe duk suna gidan sunzo musu wuni, abin mamaki har da su Walida, Abdallah, Kausar da Walid autanmu. Nan gidan ya rude da sowar kannen mu kamar zasu hadiye mu. A sannan ne na gane gidan Ummi da Yaya Bashir ne ganin tangamemen hoton su (window size) ranar (cocktail) din (Indoor sport hall) kafe a kayataccen falon. Sai na wuce kai tsaye zuwa uwar dakin matar gidan babu wanda na kula a cikinsu sai cika nake ina batsewa. Na zauna a gefen gadonta ina kallon dakin kallon kurilla, na jiyo alamar tana (toilet) ne wanda ke makale da dakin nata tana wanka. Ummi tunda taji ana oyoyo Yaya Fa'izah, oyoyo Yaya Fa'iz tayiwa wankan baja-baja ta fito a guje duk rabin jikinta kumfa ta fado mini. Na ture ta na ce, "Ke baki da hankali ne za ki jikani? Don kawai nazo gidanki? Ba tambayar mutum ya yake? Ko wane hali yake ciki?" Ta daga ni tana dariya, ta rasa inda zata sa kanta don farin ciki. Na bita da kallo har cikin ta ya tasa. Na kama baki cikin tsananin mamaki domin na dauka da da wasa take kamar a bakin kofa ake tuntube da cikin? Ta sunkuya ta zauna a gefena hannuwanta duka biyu tallabe da fuskarta tana murmushi, ta ce. "Fa'izah matar Yaya Fa'iz! Sai kyallin amarci kuke don na hango shi ta taga, daga ina kuke haka? Naji labarin Baba ya kore ku, tsammanin mu kun bar kasar babu sallama ga kowa". Na hade girar sama da na kasa, na ce. "Kin san Allah ki fita daga harkata, wane irin an kore ni kamar wata shegiya? Maras kunya fitsararriya, kyallin amarcin uban wa? Amarcin yaci ta kaza-kazan sa". Na mirgino ashariya. Ummi ta dafe baki, sai kuma ta fashe da dariya. "Oho dai! Mun gane kiyayya taci uwatar, Pilot yayi fari yayi kiba, Fa'izah ta rame saboda wuyar amarci amma ta zama kyakkyawa. Shin wai a ina aka yada zango ne?" Ganin tana neman maishe ni mahaukaciya na mike nayi (toilet) don inyi wanka in sauya kunzugu na ko naji dadin jikina. Na fito daure da tawul tana make-up a (dressing mirrow) fuska kamar jikakken kwaki don turbunewa na ce. "Bani kaya in sauya, ko ba hali?" Tayi dariya kawai, ta dauko min atamfa Vlisko mai ruwan ganye mai karamin dinki na karba na saka nayi kwalliyata sosai nayi sharr, tuni kuma tausayin 'yar uwata ya kamani ganin yadda take ta rawar jiki dani cike da kauna. Sai na ware nima muka shiga hirar arziki. Duk sanda ta sako zancen Fa'iz cikin hirarmu bana yarda ince mata komai, dolenta ta kyale, muka koma hirar makaranta da dakace iri-iri na cewa yanzu an shiga zangon karatu na farko na sabuwar shekara babu mu, Haulatu na can tana ta (missing). Ko da wasa Ummi bata yi zancen marigayi N.S ba, nima banyi ba. Na ce. "Wai ina Yaya Bashir ne?" Ta ce, "Ya koma Russia zai harhado kan takardunshi don na ce ni ban yarda yayi aiki a can ba, sai dai ya je, ni in zauna anan duk sanda ya samu dama ya neme ni, dalilin komawar shi amso takardun kenan ya dawo nan ya nemi aiki". Nayi dariya na ce, "Kin hadu, wai kema mai tsarawa miji rayuwa ko?" Ta ce, "Ba wani tsarin rayuwa ko dai gaskiya. Na rantse miki shashanci yake a can ba aikin da yake yi. Ya jima da gama karatu babu yadda Mama bata yi ba ya dawo yaki, wai jiran Yaya Fa'iz yake ya kammala da yake karatun Fa'iz yafi nashi nisa. Gara Fa'iz idan ya ce zai yi aiki a waje yana da hujja a Nigeria bamu da wasu Airlines na arziki, kuma ba zaki hada albashinsu da nagartarsu da 'Internationals’ ba. Shi kuwa Yaya Bashir su Nigeria ke bukata suzo su amfanar da al'ummar su yafi, (Global; security) ya karanta. Na samu da dabara da taimakon Allah da na addu'a na tsayar da hankalin Yaya Bashir a kaina, anan bai fita ko'ina sai tare da ni, don kar in zarge shi. Firinji kuwa (fridge) duk gidan daya ne na (kitchen) don kar ince yana boye (gulder) wani wuri. Don haka ko ya dawo ya samu aiki zan ci gaba da sa masa ido sosai duk da cewa na tabbata a yanzu yaya Bashir ya bar shashanci 90%". Na jinjinawa Ummi a fili da zuci, kaga mace duk gabuntarta a fannin mu'amala da miji kada ka rainata. Ban taba zaton Ummi na da hankalin da yau na sameta da shi ba. Na ce, "Bani abinci Ummi, yunwa nake ji, tun karin kumallon safe rabona da abinci, kin san kuma ba iya jure yunwa nake ba". Ummi ta dafe kirji, kai Fa'izah, amma kin iya rashin mutunci, kin shagaltar dani ko ki tuna mani da dan uwa na dake waje cikin yara ko ruwa ban bashi ba, kanki kawai kika sani, (selfish!)". Ummi ta fita falo da fara'arta sai taga wayam! "Ku! Ina Yaya Fa'iz?" Ta tambayi Walida. "Ai tun dazu ya debi Shu'aib, Junior da Yahya suka wuce wai Zaria za su raka shi. Haushi ya kashe Ummi ta harari Walida. "Shi ne baku gaya min ba? Ban bashi ruwa ba, ban bashi abinci ba". Ta fada kamar ta fashe da kuka. Abdallah ya ce, "Shi ne ya ce mu kyale ki hira ku ke, kun jima baku hadu ba. In ya dawo daukan Yaya Fa'izah gobe ko jibi kun gaisa". Ba haka ta so ba, sai dai tayi farin cikin jin cewa ya bar mata 'yar uwarta barin rayuwarta su kwana su hantse tare, wani abu da suka rabu da samu tun barowar su Kano gidan Yaya Rabi. Da kuzarinta ta fada (kitchen) don dora sanwar dare. Ta dawo ta ci gaba da yi min sababi, ta gaji ta koma wa'azi na hakkin miji akan matarsa da girmama shi da kula da cin shi da shansa da shimfidarsa. Amma ga mamakina na kasa tanka mata duk da nasan gaskiya take fada ban dai furta komai ba mai nuni da na amshi wa'azinta ko a'ah? Ba zata gane ba, ba zan iya bane, da zata gane ta adana yawun bakinta a gaba zai yi mata amfani, ta barni yadda ta ganni, rayuwata da tata ba zata taba zama daya ba. [21/02 9:00 PM] Sumayya Takori: ZUMUNTAR KENAN?-4 Washegari da safe, mun karya kumallo cikin farin ciki, ni Ummi da ragowar kannen mu. Daga nan muka tare a falon Ummi muna hira muna shan dariya. Na mike na barsu nayi (toilet) din Ummi nayi wanka na sha kwalliya da daya daga cikin lesukan Ummi da ta ci biki dasu. Na dawo falon na cimma su kafin in zauna kararrawar kofar shigowa tayi kara. Sai na fasa zama a raina na ce bari in hutar da kowa. Na karasa a natse na bude kofar. Fa’iz ne cikin shadda wagambari babbar, ruwan makuba tare da abokinsa Surajo na Central Bank, shi kuwa cikin kananan kaya. Da ganinsu kaga matasan da rayuwa ke garawa tare dasu, suna cikin lokacinsu, kuma ana damawa dasu a fannonin da suke. Muka hada ido da Fa’iz na yi maza na kawar da nawa na wuce ciki na zauna kusa da Ummi ban kara kallon su ba. Na kuma bi na maida fuskata kamar hadari sai ka rantse ba dani ake hira da dariya yanzun nan ba. Su Ummi suka shiga gayar dasu daya bayan daya, a sannu kuma su Walida duk suka bar falon. Na maida idona kan t.v (Indian movie) ne ake yi mai suna 'Welcome-Back' na John Abraham. Dai-dai lokacin da aka nuno jarumin shirin, wato John Abraham yana magana. Abin mamaki dana juyo sai naga shi da Fa'iz suna matukar diban kama, illa ace yafi Fa'iz haske sosai da tarin suma. Nayi maza na kawar da wannan tunanin na mike ina kokarin barin falon. Kallo Fa'iz ya bini dashi shi da Surajo, Suraj ya ce. "Madam Fa'izah ba gaisuwa?" Bai san cewa haushinsa nake ji ba tun ranar (Cocktail) ko kallon sa banyi ba na ci gaba da tafiya. Ya ce, "Ba don ni ba, don Allah don Annabi ki koma ki zauna, wajenki muka zo". Duk wanda aka hada da Allah da Annabi, indai cikakken Musulmi ne da yayi amanna dasu dole ya aikata abinda aka umarceshin. To hakan ce ta faru dani. Na koma na zauna don ba yadda zanyi, amma ban kalle su ba. Ummi ta girgiza kai da alama na bata haushi ta harareni ta mike tayi ciki. Suraj ya ce, "Na dauki Fa'izah a sahun yara nutsatstsu, masu hankali da sanin yakamata. Kowanne irin laifi Fa'iz yayi mata ya kamata ace lokaci da isowar hankali sun shafe shi hakannan. Riko, ba ta'adar dan Musulmin kwarai bane. Allah Ubangijin mu mai afuwa ne, kuma yana son masu afuwa. Fa'iz dan Adam ne kamar kowa, ajizi kamar kowanne bil'Adama. Babu wanda yake sama da aikata kuskure, sai fiyayyen Halitta. Sai ake son kullum mu kasance cikin Istigfari, domin Allah Ya yafe mana kura-kuranmu, mu fita daga cikin rafkanannu. Laifi kuma na tsakanin dan-Adam da dan uwansa, sai aka ce mu nema daga junanmu. Mun nema anki yi mana, mun ce a saurare mu, anki sauraron mu. Anyi mana mummunar fahimta, sabanin ta hankali da tunani. Ya kamata a sanya al'amarin mu a mizanin hankali, laifin da muka aikata bisa sani, ko bisa kuskure a bamu dama mu kare kanmu, kafin a cigaba da hukuntamu akanshi, kada ya zamo da daukar hakki". Idan na ce jikina baiyi sanyi da kalaman Surajo ba, kema kin san karya nake. Amma ba zan iya ba da kai ba, ba duka na yarda dasu ba, (it's not the hightime). Don haka ban basu amsa ba, kamar yadda ban dube su ba. In iskar da ta debo su ta isheni kallo, to suma hakan. Sai ma na dauki (remote) na karo sautin t.v kamar banji me yake fadi ba. Fa'iz ya mike a fusace yayi waje, Suraj ya mara masa baya cikin tsananin mutuwar jiki da sarewa da al'amari na. Ni da kaina nasan ban kyauta ba, duk abinda zanyiwa Fa'iz a dalilin kiyayyarsa, bai dace inyi a gaban abokinsa irin Surajo ba, da suke matukar martaba juna da girmama juna. Yadda Fa'iz yayi fushi, na tabbata akwai abinda zai biyo baya na daukar mataki na karshe don kawo karshen rashin da'a ta. Don na lura bai iya daukar mataki ba idan ranshi ya baci, idan na tuna karon mu a 'river-niger'. Don haka wunin ranar zungur nayi shi ne sululu! Cikin rashin kuzari, Ummi dai bata ce min komai ba don itama haushina take ji, tana kuma tsoron ta shiga maganar ince zan bar mata gidanta. Don haka sai ta bini da ido tun safe har dare bata shiga shirgina ba. Nima kuma sai banji dadin hakan da tayi min ba. *** Karfe takwas na dare muna cin abincin daren da Ummi ta girka mana muka ji kararrawa (door-bell). Kasancewar na riga kowa gamawa ni na doshi kofar na bude, ina kwance ne da fari cikin kujera duk abin duniya ya isheni na rasa abinda ke min dadi. Duk da rashin wadataccen haske a wurin hakan bai hana ni gane fuskarsa ba, ma'abociyar zati da kamala. Hannunshi duka biyu zube cikin aljihun bakin wandon 'ARMANI' dake jikinsa. A jikin sa t-shirt ce ruwan bula mai haske (Tommy Hilfiger) ya saya idanunshi cikin bakin 'prada' mai duhu ainun ta yadda ba zaka iya tantance halin da kwayar idanunshi ke ciki ba. "Ki dauko mayafi ki wuce muje, Baba ke kiranki". Cikina ya hautsina ya ba da wani irin sauti kulululu! Idona ya yi rau-rau gab da rushewa da kuka. Na saki kofar na fito har gabanshi na durkusa na soma kuka. Idan ubana ya tsine min albarka wacce irin rayuwa nake tsammatarwa kaina? Wace irin rayuwa zan ci gaba da yi? Mene ne makomar rayuwata? Ya daga kai sama, kamar mai irga taurari, Allah kadai yasan me yake tunani. Sautin kukana na karuwa, yana tafiya da bacin ransa. Na tabbata na kawo shi bango ne bashi da sauran dabara akaina shi yasa ya sake maida al'amarin ga mahaifina. Amma ganin irin kukan da nake sai ya ce. "Is o.k, ba Baban ABU ne ke kiranki ba, Baban Kaduna ne". Anan ne naji dan sanyi, na mike na dauko mayafi da takalmin Ummi ko sallama ban musu ba don hankalina ya dugunzuma ya tashi, bana so ko kankani wata magana akan Fa'iz ta sake hadani da iyayena, nafi son mu ci gaba da ci muna sidewa a tsakanin mu. Har aga wanda zai shanye miyar. Tunda Baba ya fara ikirarin zai tsine min, na fara shiga taitayina. Na bude kofar gaban motar na shiga, Ummi ta biyo bayana da shirgina a leda, abin mamaki kayayyakina dake gidanmu da akwatinan da ya kawo min da sunan lefe da tsaraba su na gani a bayan motar-baki dayansu wasu ko a leda ba'a zuba su ba. Ga takalmana da jakunkuna na Giwa da na Zaria da takarduna na makaranta. Hakan ya tabbatar mini tafiyar dani ta tabbata. Hawaye suka cicciko idona. Ya je Giwa kenan ya kwaso kayana duka, haka wadanda suke Zaria. Ummi na daga min hannu muka bar harabar gidanta, sai na samu kaina da daga mata nima, don watakila rabuwar kenan. Tunda muka hau titi babu wanda ya ce uffan, babu kuma wanda ya kalli dan uwansa. Ga mamakina ba Jabi Road muka nufa ba, haka ba filin jirgin sama ba, Fa'iz ya karya kan motar ne zuwa anguwar Malali G.R.A anguwa mai kyawun tsari. Na ciro kaina daga kallon gefen hanya na zube su a kanshi ban san yaushe furucin ya subuto daga bakina ba. "Ina zamu je?" Fa'iz bai kula ni ba. Ya mika hannu ne ya karo karfin na'urar sanyaya mota. A hankali kuma ya rage gudun motar yana tafiya (slow-slow) kamar baya son mu kai inda zamu. Cikin sanyi ya soma magana. "Fa'izah, bana so in rika hadaki da iyayenmu, a bisa dalilai da dama. Na farko za'a dake ki ne, duka kuma ba zai taba sawa ki so ni ba. Na biyu za'a tsaneki, kasancewar kowa na son ki tare dani. Amma ke har yanzu kin ki saduda ki zubar da makaman yakin da kika diba, ki fahimci aurenmu na har abada ne. Tunda baki tashi kinga an taba yin saki a cikin gidanmu da kewayenmu ba. Na san kiyayya halitta ce, kamar yadda soyayya take halitta mai zaman kanta. To amma komai na duniya mai canzawa ne ke naki al'amarin yaki ya canza, yinsa kike tamkar cin kwan makauniya babu azanci babu tunani balle tsoron Ubangiji. Nasan zafin kiyayya to amma kada ki manta ni dan uwanki ne na jini wanda jininku ke gauraye da na juna. Idan babu so na soyayya akwai so na 'yan uwantaka. Me zai hana ki ture wancan matsayin da ba zaki iya bani ba ki bani wanda Allah Ya umarceki ki bani? (Na 'yan uwantaka da na darajar aure). Kina amfani da abinda ya wuce a sabuwar rayuwar ki wanda ba zai amfane ki da komai ba, da zaki saurare ni ma da kin gane (you are totally mistaken!). (For how long) kiyayyar taki gareni zata kare? Tunda ni tawa ta kare? Kina kwasarwa kanki zunubai iri-iri wurin Ubangiji akan sanin ki, don ba zan ce cikin rashin sani ba tunda akan idona kika sauke Alqur'ani da sauran littattafan addini. Bana jin zafin duk abinda kike mini ko kadan, illah tausaya miki azabar Allah. A dalilin bacin ran da kika sanyani dazu, naji dole in kawo karshen tatsuniyarmu ta zama kurunkus! Daga yau yawon gidajen 'yan uwa da iyaye ya kare mana baki dayanmu. Za muyi rayuwa ne (on our own) kowa yayi irin wadda yake ganin zata fisshe shi. Ba zan kuma hanaki ba, ki ci gaba da abinda kike yi tunda kinga shi zai fisshe ki. Na daina rokon SO sai rashinsa, na daina rokon zaman lafiya sai akasinsa, na daina rokon kwanciyar hankali sai tashinsa, na daina rokon yafiya sai rashinta, na daina rokon a daina ki na sai a cigaba da kina. Wannan shi ne hukunci na karshe, kuma rayuwa mafi kyau da na zaba mana, don ba zan kwashe ki in kaiki inda ake ganin mutuncina ki ci gaba da zubar min dashi ba". A dai dai lokacin da ya tsaya gaban wani karamin (flat) mai jan get, yayi (horn) wani buzu yazo da sauri ya bude. Gidan karami ne, amma fa wanda akayi amfani da hikima da fasaha wajen gininsa da tsarinsa tamkar (European-building). Rufinsa ja ne, fentinsa ciki da bai fari da ruwan madara. Ainihin ginin gidan a tsakiyar gidan aka yishi fili fetal ya zagaye shi ya sanya shi a tsakiya. Gini ne na hawa daya (flat). Korran shuke-shuke sunyi kyakkyawan layi a gefe sun bi katangar gidan har wajenta, haka akwai wayar lantarki ta (security) akan katangar gidan. Grass carpet ne lullube da harabar gidan korra sharr sunyi lub-lub alamun suna samun matukar kulawa. Wannan shi ne ainahin gidan da Pilot Fa'iz Mukhtar ya kwashe shekaru biyu kacal yana ginawa cikin garin Kaduna, ba da sanin kowa ba sai mahaifinsa Baba Muntari wanda shi yake turowa da komai ake masa ginin daga Ukraine, hatta zanen gidan shi ya turo masa ko kwabon Baban Kaduna babu a cikin ginin Fa'iz, cikin tsararriyar unguwar Malali GRA. Ya bude motar zai fita, sai kuma ya juyo ya dube ni. Bani da alamar fitowa illa kuka da nake yi a hankali wanda yafi kama da kukan amarya mara gata, wadda iyaye da 'yan uwa basu rako gidan miji ba. Me na yiwa A.B haka da zafi? Wane irin rashin so ake min cikin zuri'armu? Me Fa'iz yake musu wanda ni bana musu? Daga can kololuwar zuciyata naji wata murya tayi (whisphering) rada cikin kunnuwana, "BIYAYYAH". Wannan ya tabbatar min na dai tabbata matar FA'EEZ MUKHTAR ABUBAKAR tunda har yau gani cikin gidanshi matsayin matar gidan. Na karbi kaddarar Ubangiji wanda Shi Ya nufi Fa'iz da zama miji a gareni. Bani da inda zani, bani da yadda zanyi, mu zauna a hakan, zaman dolen da ya zaba mana. Sai dai bana jin har illah masha-Allahu zan so shi, soyayya guda daya ce kuma na tabbata na yita na gama. Na karbi Fa'iz a matsayin mijin kaddara, na kuma ci alwashin ba zan kuma yi masa musu ko rashin kunya ba tunda ina kwadayin rahamar Ubangiji kamar yadda na yarda da tunasarwarsa gaskiya ce tsagwaro. Sai dai SO daga gareni bana jin har abada Fa'iz zai samu haka har in koma ga Ubangiji na Fa'iz ba zai samu dariya ta ba balle walwalata. Biyayya ita ce wajibina nayi alkawarin yinta da dukkan iyawata. Na bude murfin mota na fita ba tare da na dauki komai ba, na doshi kofar da na tabbatar ita ce ta shiga falon gidan. Ya karaso yasa (key) yana budewa. Wani saurayi ya bullo daga bayan gidan ya fadi yana gaishe shi yana amsawa, sannan ya juyo yana min sannu da zuwa. Ban amsa ba sai daga kai nayi. Fa'iz ya ce da shi, "Yaya suke yau? Ince ko an basu abinci sosai?" Ya ce, "Ranka ya dade an basu sunci sun koshi sun sha ruwa tun yamma yau suka kwanta". Ya yi murmushi ya ce, "Sai da safe to Malam Ya'u. Ka zo da wuri don Allah don zan aike ka kayowa Madam cefane". Ya ce, "An gama Yallabai. Mu kwana lafiya". Na rasa suwa ake magana akan su. Bai sake dubana ba ya bude kofar ya wuce ciki ya janye (curtains) ya sarkafe su a masarkafinsu. Na tube takalmana na shiga, duhu dindim, naji kafafuna bisa wani sassanyan (marbles) mai sulbi kamar bayan tarwada. Yasa hannu ya kunna fitila daga bayan labule haske ya gauraye falon, kamar rana, sai dana runtse ido, sai ya rage fitilun ta hanyar kashe wadda tafi kowacce haske ta tsakiyar falon, hasken ya koma dai-dai. Ya yi murmushi ya ce, "Ga dakinki Fa'izah, ga dakinki, bayan shi a ko'ina na gidan nan baki da shamaki. Wannan falon saukar baki ne, naki yana hade da dakin barcin ki, nima haka. A falonki (kitchen) yake, ba abinda su Yaya Rabi basu zuba miki ba irin na 'yan uwanki, amma sunce in gaya miki ba zasu rakoki ba, saboda halin ki ba irin na 'yan uwanki bane. Haka ba zasu ziyarce ki ba sai ranar da suka ganki da ciki irin na Ummi. Suna yi miki fatan ALHERI". Wata harara na zabga masa, shima ya mayar min da wadda ta fita zafi, ya ce. "Daga fadar sako? Allah Ya huci zuciyar ki; O.K?" Na samu daya daga cikin tausasan kujerun (leather) da suka yiwa falon kawanya na luntsume. Ina kallon yadda aka shirya dakin abin sha'awa, na tabbatar aikin Aunty Rabi ne da Aunty Hauwa, sai na lalace ina kallo kamar a talbijin. Komai (orange) da (lemon green) kamar ka lashe, sannan babu tarkace amma kaya ne masu daraja baki daya tun daga kan (dining table) na tsurar bakin gilashi a can gefen falon ga na'urar sanyaya daki ta girke, doguwa (split) tana ta buso sanyi mai dadi, kayan lantarkin 'Samsung' kaloli ne kawai suka bambanta da na Ummi, ita nata komi (milk and brown) ne. Ya dauko wayarsa yayi magana, ashe buzu mai gadi ya kira. Ya zo bakin kofa da sauri yana sallama. Ya ce, "Kaga na manta Ya'u ya wuce, ungu mukullin mota ka kwaso duk kayan dake bayan motar da wadanda ke cikin (boot) ka kawo mata. Ka shigar dasu dakin can". Ya karba yana fadin, "An gama Yallabai". Da buzuwar Hausarsa. Ya dubeni kasa-kasa kamar ba zai yi magana ba, sai kuma ya ce. "Ki tashi ki shiga nawa dakin har ya gama, ko zama za kiyi sai ya gama kalle ki cikin falon nan?" Nayi mamakin dalilin fusatar shi haka bayan banyi wani abu da zai fusata shin ba. Na zambura baki, sannan na mike, kada inje ya faska min marin da ya saba faska mini. Don na lura yana matukar son tada hankalin fuskata da tafukansa. Dakin daya kira nashi nan na shiga ina shan kallo. (INa ruwan 'yar kauyen Giwa). Ina jin Baba Buzu yana ta shiga da su, sai da ya gama tas ya rufo motar ya kawo masa mukullin. Suka yi sallama shi kuma ya rufo kofar falon da (keys) ya ce. "Malama fito min daga daki kada ki shafa min najasa a gado". Kamar wata rakumi da akala sai na fito nayi wanda aka bani, babu musu, ba busa ba daga hannu. Ni kaina har mamakin (silence) dina nake yi. Ko da yake shaidan ne kadai za'a ce masa ga allah Ya kautar da ido. Ganin bana jin barci, na ce bari kawai in shirya kayana a (wardrove). Ina jinshi ya kunna t.v a (main) falo yana sauraron labaran ALJAZEERAH na soma ninke kayana ina tsara su ina adanawa. Na cikin akwatunan da dinki suke bukata na barsu a ciki na jera akawatunan haka cikin (wardrove). Ina tsaka da aikin nawa ya shigo, ya tsaya daga bakin kofa, ya canza zuwa pyjamas farare sol, hannunshi daya cikin aljihun 'pjs' din daya rike da kofar. "Yunwa nake ji, ya za'ayi?" A raina na ce, "Wannan wace irin tambaya ce? Ban biyo shi don in yi sana'ar kuku ba ko zaman aure irin na mata da miji, sai don amsa kiran Baban da yace min, ashe wayo yayi mani duka na hakura na fauwalawa Allah na mika wuya ga hukincinsa, yanzu kuma yazo yana son dora mini abinda ba dole na ba. Wanda ko kusa ba zan karba ba. Ai ita wannan din (girki) ba fadar Allah bace, al'ada ce, don haka ba zan karbeta ba. Allah cewa yayi su kawo a dafe su ciyar damu, babu ayar da ta ce a sayo mu girka, ni kuma da fadar Allah kawai nake amfani. Don haka nayi masa shiru, ya gaji da jiran jin ta bakina, ya tabbatar ba zan tanka ba, sai ya ce. "To a gasa min kaza da (chips) (favourite food) dina kenan. Don naga alamar ke a koshe kike. Akwai kajin a (freezer) din (kitchen), dankalin ma akwai a (kitchen). Duka Ya'u ya sayo, kayan gwari (su tattasai da tumatir) ne kawai babu gobe zai sayo miki, dazu da yaje sun tashi". Ya juya ya fice. Ban amsa ba, amma a zuciyata na yanke shawarar zanyi, tunda sawa da hanawar duk a cikin umarnin Ubangiji suke. Sai na saki aikin da nake yi na fito zuwa (kitchen) din. Ashe kallo na sama, babu irin na'urar girkin da iyayenmu basu jera min ba, komi na cikin (kitchen) din (orange) ne (freezer) da (cooker) sune (lemon-green). Na ba da ajiyar kallon zuwa gobe da safe na fara abinda ya shigo dani. Cikin minti goma sha biyar na gama da yake dankalin ma a (fryer) na soye shi bai dauki lokaci ba. Na jera a (tray) yana zaune na dora a (dinning). Naga mamaki a fuskarsa da na juyo zan koma daki sai na tuna ban ajiye ruwa da lemu ba, kada inci gaba da aikina ya kara taso ni. Na koma firjin dake dab da (dining) na ciro masa (Pepsi) da ruwan Faro. Har na kai bakin kofar daki na, ya ce. "Aunty Fa'izah saura ruwa da lemo". Na cuno baki na harari tebirin sai shima ya kalle shi. Dariya yayi. "Aunty Fa'izah ta soma zama (full-house wife): It's a job weldone!". Da sauri na shige daki bana son zuciyata taji yabon da yayi mata. Wani gashin kaza yake ci yau da bai taba cin mai dadi da taushinsa ba, koko santin hannun daya sarrafa shi ne, bai sani ba. Kunnensa har motsi yake musamman da abin ya hada da yunwar wuni guda. Tun barowar mu Minna bai ci wani kwakkwaran abinci ba, sai ruwa da lemo yake daddaka. Tunda ya fara bai yi motsin kirki ko magana ba, sai da ya zuge kasusuwan katuwar kazar nan gaba daya. Da ya kammala kasa jurewa yayi sai da ya dangana da kofar dakina. Ya rausayar da kai yana rike da kofar. "Aunty Fa'izah, daga yau, a duk inda muke, zaki gasa min kaza da (chips) da wadannan yatsun naki, a kowanne dare matsayin (dinner) dina. Zan samu Fa'izah na?" Ban amsa ba, sannan ban kalle shi ba, na ci gaba da jera kaya cikin (wardrove) kamar bada ni yake magana ba. Ya gaji da sauraron amsata, ya aro (extra) hakuri ya kara akan wanda yake da shi, murmushi ya karawa zuciyarsa. Wani bangare na zuciyarsa na cewa, "There's alot of improvement. Is a matter of time!". Washegari ban tashi da wuri ba sai misalin karfe tara na safe. Badon komai ba sai don sanin babu nauyin sallah akaina. Nayi wanka ba tare da wata kwalliya ta kuzo ku gani ba. Babbar rigar shadda mai aikin surfani na sanya, nayi daurin kai sassauka da kallabinta, na fesa turare 'Escada sentiment' na nufi (kitchen). Ruwan tea na fara dorawa a (water heater) sannan na debi dankali dai-dai cikin mutum biyu na soma ferewa. A haka ya cimmani cikin madafin. Ya hade cikin bakar shaddar rini mai ratsin ruwan makuba, yayi sharr yayi (fresh) kamar sabon ango sai fesa kamshin '212' yake. Ya saki murmushi mai kayatarwa cikin fadin, "Good morning Aunty Fa'izah". Na ci gaba da firar da nake yi, ban kalleshi ba sai ta gefen ido, haka bai samu amsar gaisuwarsa ba. Bana son wannan kulanin da yake yi, na fi son tunda zama tare ya zama dole, to kowa ya ci gashin kansa kamar yadda ya ce a farko kamin in shigo gidan kowa yayi wadda zata fisshe shi, koko rayuwar da yayi amanna da ita. Ya dauki wata wukar cikin fadin, "Bari in tayaki ba don halinki ba". Ya fara ferewa da gani bai iya ba, sai zaftare tsokar dankalin yake. A haka aka yi firar aka zo wajen daddatsawa, nan ma ba iyawa yayi ba sai yanka su yake ba fasali, wani kudi wani bashi. Bai ankara ba ya sharce dan alinsa da wukar. Nan da nan jini yayo ambaliya. Ya yi saurin ya da wukar ya tara danyatsan a famfo jinin na bin ruwa. Sai naji tsigar jikina na tashi ganin yawan jinin dake fita. Kamar yadda ya ce din ne idan babu soyayya akwai kauna ta 'yan uwantaka. Ban san sanda na wuce daki na dauko turaren dana fesa ba na dawo na kashe famfon (sink) din da ya kunna na soma fesa turaren akan yankar. Ban fasa ba sai da gudun jinin ya tsaya. Na gutsiro (tissue) na danne yatsar, duk kokarin da zan iya nayi wurin ganin bamu hada ido ba. Shima bai takura da sai mun hada din ba, kawai cewa yayi. "Thank you!". Na bi na tattare fuska na hade wuri guda cikin raina cewa nake, " Ni bana son wani tayin aiki, a barni da likitancin da ban karanta ba". Amma a fili aikina na ci gaba da yi bance komai ba. Sai ya jingina da kabinet din (kitchen) din yana kallon yadda nake ayyukana cikin nutsuwa da hada hankali guri guda. Na bude firji na debo kwai ina fasawa sai ya baro jikin (cabinet) din ya iso gareni. Cikin murmushi ya ce. "Let me help you". Na ce ciki-ciki, "Barshi nagode". Bai karbi godewar da nayi ba ya dauki daya, maimakon ya hada shi da uwansa ya fasa ko ya fasashi da wuka, sai ya hada shi da goshina ya juye a fadi ka mutun da nake juyewa. Ya sake daukar daya, ya hada shi da tsinin karan hancina shima ya juye ya yar da bawon a (dusbin). Nan da nan ya fashe su duka guda takwas din a goshi da hanci na, ko a ina ya koyo wannan fashin kwan oho! Nan take na soye shi tas na gama duk abinda nake yi yana tayani. Amma cikin raina bana godewa, a kyaleni yafi mun. Karar kararrawar shigowa tasa na samu yadda nake so, wato ya fita ya barni. Can na jiyo tashin sautin su shi da Surajo ne. "Na dauka tuni ka kama hanya?" Cewar Fa'iz. "Ni na isa in tafi, ban zo naga dakin Madam rikici na sayi baki ba?" Tare suka zauna kujerun falon rike da hannun juna. Kai sai yaushe zaka wuce? Ko kazo kenan". Ya ce, "Two weeks off gareni, yau kuma kwana na hudu, saura kwana goma inaga". "Tare zaku wuce amma?" Surajo ya tambaya. "Don Allah ka rufa min asiri kada ka ballo min liki irin wanda ka saba ballowa, na samu an daina yi min hayagaga ko ba'a bini ba na gode". [21/02 9:01 PM] Sumayya Takori: Abin ya baiwa Surajo dariya, in wani ne ya bashi labarin Abubakar Mukhtar (sunan da suke kiranshi) zai koma haka akan mace karyatawa zai yi. Soyayya ba karya bace, a yau ya kara yarda da hakan. Ya shiga girgida kai kamar kadangare. "Tana ina ne? Ban ji motsinta ba. Ga hotunan (cocktail) din ku fa na wanko". Ya amsa ya aje gefe ba tare da ya bude ba yayi mai nuni da (kitchen) da girar shi. Dariya Surajo yayi, "Kace har girki ake mana!". Shima dariyar yayi, "Mai dadi kuwa". Suka yi ta dariya kamar wasu shashashan madina, sai da suka yi mai isarsu tukunna. Surajo ya ce, "To yanzu yaya za'ayi batun tafiya UK?" "Sai yanda ta yiwu Surajo, bani da sauran dabara, duk abinda zan iya nayi, na bada hakuri, nayi fada, nayi wa'azi, nayi nasiha. Zan iya cewa (there are lots of improvements) sai dai bata yi min magana, sannan in nayi bata amsa min da baki, sai dai tayi a aikace. Kuma ba musu, ba rashin kunya, duk abinda nasa ta daga jiya zuwa yau tana yi". Surajo ya ce, "To Alhamdulillahi, hakuri (still) ba abinda baya bayarwa. Kuma ina ganin inta bar kasar zuwa inda bata da kowa komai zai tafi (normal)". Ya ce, "Nima tunanin da nake kenan, amma Surajo (how easy is that)?" Dai-dai lokacin da na fito daga (kitchen) dauke da fadi ka mutu ina jerawa akan (dining). Duk suka yi shiru kamar ruwa ya cinye su. Jikina ya bani zancena suke yi. Zan koma (kitchen) Suraj yayi gyaran murya. "Madam ba gaisuwa yau ma?" Ina tafiya ban tsaya ba na ce, "Ina kwana?" Ya ce, "Lafiya lau, sannu da aiki". Na ce, "Yauwa". Na shigo don dauko filas din ruwan zafi. Suka dubi juna suka yi murmushi. Tare suka karya kumallon shi da Surajo yana tambayarsa abinda yaji masa ciwo. Ga ammakin Fa'iz sai ya kasa gaya masa kada yayi masa dariya don a hakan ma bai daina mamakin canzawarsa da rauninsa ba, gani yake yayi min sako-sako da yawa. To abin ne shima yazo amsa 'beyond comment' (sunan wani ganyen shayi), idan yana gaban Fa'izah manta kansa yake da (identity) dinsa. Cewa yayi yankewa yayi da reza ya ce. "Kai me ya hadaka da reza kamar wani wanzami?" Ya ce, "Don Allah ka kyaleni haka Surajo, kwakkwafin ka ya isheni". Wata irin dariya Surajo yayi wadda ke nuna ko dai bai gano ba to ya kusa ganowar. Ni kyale su nayi na koma daki na kwanta don rama bacci. *** Ban jima da kwanciya ba bacci ya dauke ni, ba ni na farka ba sai azahar. Nayi wanka nayi (brush) ba don banyi na safe ba sai don inji dadin cin wani abu. Domin da mahaukaciyar yunwa na tashi. Na fito falo na duba (dining) na tarar da (plate) daya da basu taba ba, na hada 'tea' mai kauri na fara warware hanji na dashi sannan na zauna na soma ci. Na kammala na kwashe komi na hada da wadanda nayi amfani dasu a (kitchen) na wanke. Na adana komi wurinsa. Dana kammala sai kadaicin ya isheni, na kasa zama wuri daya. Tunanina ya bani in zagaye gidan cikinsa da wajensa in gani, sai na sanya mayafi da (slippers) na fito harabar gidan na zagaya baya. Dawisu ne guda biyar (peacock) mata da maza, wasu a kasa, wasu akan katanga sun bude kyawawan jelunansu abin gwanin ban sha'awa. Sai na gane sune ake maganar su jiya sun kwanta da wuri. Na debi dawar da na gani cikin buhu a kofi ina cilla musu da dai-daya. Sai ga wani saurayi ya bullo yayi min sallama, na amsa muka gaisa. Jiya ban kalle shi ba balle in san kamanninsa, da yayi magana ne na gane shi. "Kai ne Ya'u?" "Eh, ni ne Madam. Wannan aikina ne, don Allah ki bari zanyi, basu dade da cin abinci ba". Nayi murmushi na ce, "Ka dinga share kashinsu daga yau kawai Ya'u. Ina so na karbi ragamar ciyar dasu da hannuna, ina son Dawisu Ya'u". Sai yayi dariya ya ce, "Hakan ba zai zama matsala gareni ba wurin Yallabai?" Nayi murmushi nima, "Ba zai ji ba insha Allahu". Ya ce, "To Allah Ya ba da lada Aunty". Na amsa, "Amin Ya'u". Ya wuce ya barmu, na ci gaba da jefa musu dawa duk suka yo gabana suna dauka da bakunansu masu kyau suna kara baza bindi. *** Cikin wannan yanayin kwanaki suka ci gaba da mirgina mana har muka kwana goma, ranar Juma'a da yamma naji kugin mota, sai dai ba irin na motar Fa'iz bane. Na mike na daga labulen falo, sai na hangosu Walida, Shu'aib, Yahya, Junior, Abdallah, Kausar da sauransu suna fitowa daga mota, direban Mama Malam Sani ya kawo su, kowanne da 'yar karamar 'troller' din dana tabbata kayan sanyawarsu ne a ciki, yadda dai na gansu a gidan Ummi. Wani irin farin ciki naji ya rufeni don dama ina fama da kadaici da kewar su. Har da hadawa da gudu wurin bude musu kofa, kowanne yabi lafiyar kujera yana wash-wash, 'ya'yan hutu malam. Manyan su Shu'aib ne kawai basa cewa wash din, sai gaisheni cikin girmamawa. Na nunawa Junior dakin dake kusa dana Fa'iz shima (bedroom) ne (single) ba falo, ba abinda babu na ce su mazan su kai kayansu can, matan suzo mu hadu a nawa dakin sai ina-naka-saka nake dasu. Kausar ta kwantar da kanta a cinyata kasancewarta shiru-shiru ba kasafai ta fiya magana ba. Na ce, "Wai daga ina kuke ne?" Walida ta ce, "Gidan Aunty Ummi". Na ce, "Tun (last week) dana baro ku kuna can?" Suka ce, "Eh". Kausar ta dago kanta daga cinyata ta ce, "Koro mu fa suka yi ita da Yaya Bashir, yau ya dawo bayan hutun mu bai kare ba". Abdallah ya ce, "Kora da hali dai ba kora ta ku tashi ku tafi ba". Nayi musu kallon son jin karin bayani, dariya na son kama ni. Walida ta dora bayani. "Saboda Yaya Bashir ya dawo ta barmu a falo tun safe, sannan bata dora mana (break) da wuri ba, suka kyalemu yunwa na cinmu. Da ta fito bata hada mana ruwan wanka ba, ta ce kowa yayi da ruwan sanyi wai hitar (toilet) din gidan duka ta lalace. Ki dubi sanyin nan da ake. Shi kuwa Yaya Bashir din kai tsaye daya fito ya ce mu hada kayanmu mu koma gida, wai mun cika mishi kunne". Dariya nake kamar cikina zai fashe, Walid ya karasa. "Tunda dama hutun sati biyu muka je sai yaya Junior ya ce muzo nan kawai mu karasa kwana biyun mu sai mu koma gida, don dama Monday duk zamu koma (school) ke kam mun san ba za kiyi mana abinda Aunty Ummi tayi mana yau ba". Na janyo autan Momi jikina ina dariya, "Ina kuwa zanyi muku Walid? Ni farin ciki nake da zuwan ku, inma kun dawo gidan kwata-kwata ne (you are most welcome) dakunan gidan zasu ishemu". Duk suka hau murna sosai. Na ce, "Yanzu me zaku ci?" Abdallah ya ce, "Chicken burger?". Yahya da Junior suka ce, "Shinkafa da salad". Shu'aib ya ce, "Quaker oat kawai zansha da 'peak' ta ruwa". Kausar da Walid suka ce, "Wake da shinkafa da mai da yajin tafarnuwa". Taashin hankali gobarar gemu, (inji hawwa lawan meturare) tawa ta sameni ni Fa'izah. Na fada cikin raina, naja numfashi. "Uhm! Gaskiya abin naku (is too much). Dankari! Sunan wata jarida, dole Ummi tayi muku kora da hali har da sandan ma in tana dashi, in haka kuke kullum to tayi bala'in kokarin rike ku har kwana goma. 70% na abubuwan da ku ka lissafo bani da kayan hadinsu, kuma ko inada su jikina akwai jini da bargo ba zan iya ba. Chicken burger da Indomie kawai zan yi muku dukkan ku. Shi kenan?" Gaba daya suka ce, "Eh, ya isa". Banda Yaya babba (Shu'aib) shi harar su ma yake, ya ce. "Ai basu da hankali ne". Na ce, "Naga alama Yaya Shu'aib". Gaba dayanmu muka shiga (kitchen) banda Shu'aib, aka zage ana aikin hada burger, mai yanka tumatir da salad daban, mai baking da blending tsokar kazar da za'ayi amfani da ita shima daban. Haka mai tsaga biredin da shafa masa mayonnaise da salad cream shima daban. Nan da nan aiki ya kammalu kowa da (plate) dinsa ina ta rabo Fa'iz yayi sallama ya shigo. Sai kuma ya tsaya turus! A bakin kofa yana kallonmu, hannunsa dafe da habarsa. Yake fadi cikin kidayawa da dan alinsa. "1,2,3,4,5,6,7... duk a dan gidana? Ina zamu kaiku? Gaskiya ba zai yiwu ba, ba kuma zata sabu ba wai bindiga a ruwa. Banda dukkan ku taron mahaukata ne ana zuwa gidan mutane ba (notice in this century?) Kuma wai kwana? Ba daya ba har biyu? (Look at you all with your noses like hippopotamus's". (Dube ku duka hancinanku kamar na bauna). Suka aje lomar burger hankali tashe, rai bace. Ya samu kujera ya rage tsawo, ya dora kafa daya kan daya yana karkada 'yan mukullayen motarshi, ya sake fadin. "Wai da ba gidan Ummi na ganku ba?" Walida tayi rau-rau da ido, "Ai sun koromu...". "Au, shi ne ni aka zo aka tare min? Ga gidan dan iska ko? Abokin wasan ku?" Suka yi shiru tsuru-tsuru dasu abin tausayi, da alama wani abu ya bato masa rai a waje yazo ya huce a kansu. "To kuje kuci abincin duk kuzo in kaiku Jabi Road, ba mai kwanar min a gida". Kausar ta sha mur, Abdallah ya turbune, Junior ne mai karfin halin musantawa. "Haba don Allah Ya Fa'iz! Ka barmu mana? Don kwana biyu kawai?" Yahya ya yi kicin-kicin da fuska, "Kaima in kaje gidanmu ai Mama bata korar ka, daki ma take baka". Fa'iz ya fiddo ido waje saura kadan dariya kufce mana ni da Shu'aib, ya ce. "Kuji min marasa kunyan yara, ina fade kuna fade? To wallahi ba zaku kwana ba, ko ana dole? Bana son bakuntar, aje na gode. In ba wuni ba kada wanda ya kara zuwar min gida kwana, OK?" Tsit suka yi, sannan suka karasa cinye abinda suke ci. Duka suka mike cikin sanyin jiki suka dauko jakunkunansu suna ja a hankali duk suka bani tausayi. Wato mai hali baya fasa halinsa. In ka jima baka hadu da mutum ba, tambaye shi wani abin amma banda halinsa. Shi kuma irin tasa ZUMUNTAR KENAN! Idanuna suka cicciko da kwalla amma na rantse ba zanyi magana ba tunda nasan don inyi maganar ne kawai da bashi da alfarmar samunta haka kawai shi ne yake neman dalili. Suka yi waje, ya tashi ya bisu yana, "Oya! Kuyi sauri ku shige muje". Kamar ya samu wasu tumaki, haushi da takaici ya sake kamani. Na kudurta a raina duk yadda za'ayi yau ba zan gasa kazar da (chips) ba ladan korar min kanne. Sai dai nima ya kore ni. Anan kan kujerar da nake zaune ina sakawa da kwancewa barci ya kwasheni, har ya dawo ya rufe ko'ina ya kashe kayan wuta ban sani ba. Sai ji nayi yana tashina ta hanyar kiran sunana da jan babban yatsan kafata. "Yaya banga (chicken) akan (dining) ba?" Na mike na kalle shi cikin matukar fushi amma na kasa magana, na mike tsam kawai na shige dakina na rufo kofa, garam! Da safe ma kin fitowa nayi in dora karin kumallo duk da jiya ya ce in dora da wuri zai je Abuja da sassafe kan visar sa. Har bakwai da rabi ban bar gadona ba, duk da ba barci nake yi ba. Ya tabbatar bazan fito din ba balle in bashi ko ruwan zafi, sai ya iso kofar dakina yana balle 'links' din hannun rigar shaddar 'hilton' dake jikinsa fara sol. A bakin kofar ya tsaya yana fafin. "Ran Aunty Fa'izah ya dade, an tashi lafiya?" Shiru babu amsa, don haka ya dora gundarin bayaninsa. "Jiya nasan ban kyauta ba dana kori su Junior. Ina da dalilai na nayin hakan (which are all for our own goodness: Na farko kin sani Allah bai halicce ni da son hayaniyar yara ba. Na biyu ke ba kirki ne dake ba abubuwan da kike aikatawa ba lissafi a cikinsu, yaran nan kuma suna da fahimta sannan basu da mantuwa, gasu da daukar zance komi aka yi akan idanunsu sai ya koma kunnen Mama da Baba. Hatta rotsen da kika yi min a (Area One) Yahya ya gayawa Mama Junior ya gayawa Baba na kuma rasa ta inda suka jiyo. Haka kike so suje suce kina hararata, ba kya kulani wani zubin har tsaki kike mini komai da ya kamata ace mata na yiwa mijinta ni sai na roka sannan a hagunce ake yi min...". Tsakin da baya so na sake saki na juya masa keya na ba banza a ajiyarsa. Kai ni surutan da yake yi ma sun isheni nasa hannu na toshe kunnuwana. "Ina (breakfast) dina? Na gaya miki Abuja zan tafi". "Banga damar girkawa ba". Ya ce, "To Allah Ya bamu rai da lafiya". Na ce, "Amin Ya Rabbi". Ya juya ya fita ya janyo min kofar a fili, na ce. "Umma ta gaida Assha". Bai jima da fita ba na mike nayi bayan gida wurin Dawisu don basu abincin safe. Ina watsa musu hatsi daga nesa suna kara matsowa gareni cikin alamun nuna sabo, wato sun fara ganeni. Ya'u ya iso ya gaida ni ya ce. "Aunty na kawo cefane yana can kofar falo". Na ce, "Ina godiya Ya'u, anjima a sake musu ruwa, wannan ka gani duk yayi kura". Dariya abin ya baiwa Ya'u, amma sai ya ce. "Aunty kina son 'yan gidan nan naki, zan kara himma wurin kulawa dasu". Na ce, "In kayi hakan kaima Allah zai kula da kai". Na koma na kwashe cefanen da ya aje dokin kofa na shiga (kitchen) na adana kowanne a muhallinsa. Fa'iz bai dawo ba sai dare, sanda ya shigo gidanma bacci nake, ban san ya shigo ba. Na fito ne da daren don samawa cikina abinda zai ci naji yana kwalamin kira kamar tashin duniya. Duk da na firgita da irin kiran amma na share na shige kicin sai gashi ya biyo ni (kitchen) din a sukwane hannayensa rike da tulin hotuna. Fusatar dake fuskarsa ba zan iya bayyanata ba. Ta gefen ido nake kallonsa ina ci gaba da abinda nake yi, sai ji nayi ya finciko ni ta baya, saura kadan in fadi Allah Ya taimakeni na dafa (cabinet) na mike a lokacin na lura hotunan da Surajo ya kawo ne rike a hannunsa, fuskarsa a murtuke, idanunsa sun kada sunyi jajir yake magana harshensa na sarkewa. "Meye na daukar hoto da Suraj haka (very so close) har jikinku na gugar juna? Meye na tsayawa kusa da shi haka kusa da kusa a bainar jama'a? Da na ce yazo ya tsaya min cewa nayi kuyi hoto? Shi kuma Ya'u da kullum kike bare baki kina hira dashi da izinin uban waye? Ina ruwanki da duk namijin da na kawo na aje cikin gidan nan da har kike dafa musu abinci? Cewa nayi dake bana basu kudin da zasu ci abinci ko me?" Wani matsanancin haushi da takaici suka taru suka rufe ni, naji in ba rushewa nayi da kuka ba bazan huce wannan cin mutuncin da rainin hankalin na Fa'iz ba. Na kasa cewa komai sai ido dana zuba masa cikin matsanancin haushi. "Ina magana kin zuba min wadannan kwala-kwalan idanun naki, ba zaki amsa ba? Na ce shi kuma Ya'u ina ruwanki da shi har yake gaya min kince masa kaza da kaza? Na kirashi na aje domin baiwa tsintsaye abinci hirar da kike yi da shi ta mece ce? In hirar kike so kiyi dani mana? (Am I not applicable to meaningful talks than him?) Ni baki yi hirar dani ba sai da wani gardin kauye can daban. Ba zai yiwu ba to! Daga yau Ya'u ya bar gidan nan. Shima buzun in kika sake kula shi wallahi tafiya zai yi, ki zauna ke kadai ba zaki kasheni da raina ba... Akwai masu bukatar rayuwata ba don ke kadai aka halicceni ba!!!". Bayan takaici da haushi da buyaginshi ya bani, sai ya dawo bani dariya saboda da iyakacin gaskiyarshi yake wannan hargagin, akwai (gesture) a tare dashi mai nuna abinda yake fadin, haka yake har zuciyarsa. Dariya ta cika min ciki ban san sanda nayi murmushi ba irin murmushin nan na tura haushi da maida kai shashasha domin na rantse da fari na firgita, matukar firgita kuwa. Ko da kwartaye biyar aka kamani yanayin da ya zo min dashi sai haka! Ko ni nace a daukemu hoto da wani Surajo oho! Balle kuma bawan Allah Ya'u. Naga idan na kula shi ma (is a waste of time) don haka da sauri nabi ta gefensa zan fice daga (kitchen) din, sai jin hannuna nayi rike cikin nasa, cikin wani irin riko mai tsauri dana kasa fincikewa kamar ba mutum ne ya rike ni ba. "Ina magana kin maidani dan iska?" Yanayin da yayi maganar muryar kamar ba tasa ba kuma cikin wani irin 'tune' da ban taba jin wani mahaluki yayi magana dashi ba. Abubuwa biyu sautin da yayi amfani dashi din ya haifar a gareni. Faduwar gaba da wani irin bugun zuciya, hannun nasa da jikinsa duka rawa suke yi yana wani irin tsuma. Wani matsanancin tsoro ya shigeni. Na daga kai a hankali na dube shi don tantance ko dai wani ne ya rikide yazo min da suffarsa don ya cutar dani. Daga idon dana zo ina dakacensa, domin kamar jira yake na dago idon yayi hanzarin ya sanya bakinsa cikin nawa ya soma 'kissing' ba ji ba gani kamar wani mahaukacin zaki. "Na tuba Fa'izah, na bi Allah na biki. Kiyi min duk abinda kike ganin in kinyi shi zaki huce bacin-ranki, amma ki barni in rayu dake muddin rayuwata...". Kalaman da yake maimaitawa kenan ba adadi, babu 'comma' ba 'full-stop'. Saura al'amuran da yake kokarin bijiro dasu masu nauyin fada ko misaltawa ne, kuma ban shirya karbarsu ba daga nan har gaban abada. Don haka na tattara karfina da Allah Ya hore min a wannan lokacin wanda ya kasance fiye da nashi na angaje shi na taka da gudu nayi dakina na shige na rufe da 'key' ban kuma yarda na zare key din daga jikin kofar ba har safiyar washegari. Kwana nayi jinyar tsallake rijiya da bayan da nayi jiya wanda ko a mafarki ban kawo shi cikin rayuwar dolen da nake yi da Fa'iz ba. Wanda ya hankaltar dani ga cewa in sauya taku. Hanyar dana dauka ta yin sako-sako ga rayuwar da muke yin bisa tilas ba zata bille dani ba, ba kuma mai billewa bace ba. Idan kuma na ci gaba da binta, la-shakka ina cikin hatsarin da bazan iya maganinsa ba idan ya sameni. Nayi kuka har na gode Allah. Daga baya bacci mai nauyi ya dauke ni. Can cikin barci na naji yana buga kofar ba da karfi ba. Na bude ido na ga hasken rana ya ratso ta labulen taga nayi mamaki matuka, sallar asuba ta kufce min cikin shagala! Ina rokon Allah Ya yafe mini. Na fada (toilet) da sauri nayi alwala, saida nayi sallah sannan na koma nayi wanka. Sannan na shiga (kitchen) don kwana nayi da bakar yunwa. Har kicin din ya biyoni ya tsaya daga kofa yana sanye da kayan wanka na 'versace' da alama fitowarshi kenan daga wanka. Daga inda nake ina iya jiyo kamshin 'bathrobb' din da yayi amfani dashi na 'desire dunhill’. "In kin kammala ki shirya muje Jabi, Area One (Zaria) da Giwa kiyi musu sallama don jibi zamu tafi". Na wani irin juyo nayi masa kallon kayi hauka ka warke, na juya na ci gaba da aikina. Ya girgiza kai ya juya ya kyaleni. Duk yunwar da nake ji sai naji ba zan iya cin abincin ba ma saboda tashin hankali. Amma sai wata zuciyar ta ce bishi kawai kuje wajen Maman, wannan ce kawai mafitarki sai kiyi amfani da damar ta inda bai zata ba. Sai kawai na aje komi na fito na sauya kaya, kwalliya sosai nayi da 'pitch swiss-lace’ mai ratsin baki, na yafa bakin gyale na rufo dakina. A falo na cimmasa yayi nasa shirin cikin riga da wandon shadda getzner dark-green dinkin tazarce kanshi ba hula. Sai 212 ke tashi a falon. Ya hadu ya cakude da 'escada sentiment' da nayi amfani dashi wani sanyin ni'ima ya baibaye dukkanin mu, da ganinmu kasan ango da amarya ne ba karya. Ko kallona baiyi ba yayi waje, na bishi a baya naki rufo falon na shige mota. Ina kallon yadda yayi kwafa, ya fito ya rufe ya dawo, sannan ya tada motar muka fita harabar gidan buzu na daga mana hannu muka nufi gidan Baban Kaduna. Su Yahya dake ball a harabar gidan babu wanda ya taremu da murna ko tsalle kamar yadda suke yi da, tabbacin haushin yayan nasu da abinda yayi musu bai sake su ba. Sun dai yi mana sannu da zuwa suka ci gaba da 'ball' dinsu. Ya kalle su ya gyada kai yayi murmushi bai ce dasu komai ba, muka wuce kai tsaye falon Mama. Mama waya take sanda muka shiga kafarta daya kan daya a hamshakin falonta. Ta daga ido ta dube mu muna shigowa, fara'arta ta karu, ta ce. "Kinga 'yan halak, gasu nan sun zo". Ta miko min wayar tana fadin, "Rabi ce daga Kano". Na karba sannan na zauna a kusa da ita daga gefe na kara a kunena na ce. "Hello Ya Rabi". Kafin in karasa ta fasa min guda aka mai barazanar tarwatsa min dodon kunne. Da sauri na dubi Mama da danta don tsammani nake suma sun jiyo mahaukaciyar gudarta Ya Rabi, sai naga hankalinsu baya kaina sam, gaisawa suke. Yaya Rabi ta ce, "Diyata 'yar albarka, ya aka kare da BOXING? WHO IS THE WINNER?" Nayi tsaki, "Tsiyarki kenan Ya Rabi, ba a maganar arziki dake". [22/02 1:58 PM] Sumayya Takori: Tayi dariya sosai, "Ni kuwa ake maganar arziki dani, ‘yar Abubakar uwar Abubakar da Fa'izah, uwa ga Zanira uwa ga Ummi, sha lelen Muftahu autar Hajjah. Kirarina kenan, na zama duwawu dole a zauna dani. Tafiya ta tashi ko? Birtaniya ko Murtaniya? Na so ace nazo rakiya Allah bai yi ba, naji tafiyar taku ne ba shiri, a tabbatar in za a dawo da baby aka taho min sai inzo in zauna zaman dabaro mai dalili...". Nayi tsaki na katse wayar don nasan in ta Ya Rabi ne sai mu kwana muna yi bata gaji ba. Ga haushin da take kara kuma mini ta barni inji da wanda nake fama dashi. Mama ta dubemu duka tana murmushi bayan ta karbi wayarta. "Komai lafiya ko?" Tana duban Fa'iz. Ya hade gira ya ce, "Tambayeta mana Mama!". Mama ta ce, "Fa'izah ta ina Fa'iz ya kuskuro ki ko ince yake bata miki?" Na girgiza kai kaina a sunkuye. "Babu Mama". Ta dube shi, "Fa'iz Giwa fa?" Ya ce, "Mama ba sharri ba, tunda dai gatanan a zaune a gabanta zan fada. Da abinda take yi min na kisan mummuke gara min ta bude baki tayi ta zagina kamar da, ko ta ware hannu tayi ta dukana kamar yadda ta faro. Bata yi min magana, bata shiga sabgata, ba ruwanta dani ko rayuwar da nake yi cikin gidan. Bata yi min biyayya sam, ta maida kanta kurma domina". Na dago idanuna da suka yi jawur na ce. "Wallahi Mama ina iyaka yina, ina masa girki duk abinda ya ce dani bana musawa nake masa, to ban san kuma wace irin biyayya yake nufi ba...". Ya katse ni tare fidda ido, "Girkin banza! Mama baya ga girki me take yi min na hakkin maza akan matansu? Fa'izah bata kula ni, bata taba zuwa shimfidata ba, bata gaida ni, ga tsaki da harara kamar wani sa'an wasanta". Maganar ta dan girme mu ni da Mama, amma dukkanin mu sai muka yi kamar bamu ji ta ba. Na kawo wata daban. "Saboda Allah Mama ya yake so nayi? Ya zo ya sani gaba da bala'in wai don me zanke kula Ya'u leburanshi? Bayan a karkashinmu yake, dole ne ko gaisuwa ta hada mu, wai kuma don me zan ke basu abinci bayan ciyarda barori wani abu ne da muka taso muka tarar a gidanmu a matsayin kyakkyawan koyi koda ana basu albashi. Ban kula shi ba sai ya koma wai don me nayi hoto da Surajo ranar Cocktail? Bayan bani na gayyato shi ba, ban kuma je fatin nan don kowa ba sai don kaina ko ku baku san zan je ba. Ban san ma sanda aka dauki hoton ba da abinshi ya zo. Sannan kannena suka zo min zumunci ya kore su, yanzu duk haushina suke ji kamar yadda suka kullaci Ummi. Sannan ya kawo wata magana wai wani tafiya, ko ina oho! Ni kam kiyi masa magana ya fita harkata, babu inda zani gaskiya in har ba so yake ya kuntata rayuwata ba (by all means from every angle). Na yarda na amince zan zauna a can Malali ko ni kadai ce yaje duk ranar daya samu dama ya kawo min ziyara babu damuwa". Ya fiddo ido cikin kidima, "Baki isa ba, Allah kinyi dan kadan, duk abinda kike ji dashi ina shirye da dauka amma banda wannan". Fada yake yi sosai har jijiyar kansa na mikewa kamar ma ya manta da Mama a wurin. Mama tasa masa ido tana kallo sai da yayi mai isarsa tukunna, daga ni har ita babu wanda ya tanka, sai dai jikina naji ya soma rawa, kuka na son kece mini. Ya yi shiru ganin na soma sharar hawaye da mayafi na. Sannan ne Mama ta nisa cikin bacin rai ta soma magana. "To tunda zuwa kayi ka kare mana tanadi ni da ita, to tattara iyalinka ku tafi ka fini iko dasu. Ni dama ban kirawo ku ba balle kuzo ku daga min hankali". Ya soma bata hakuri tana kaucewa, daga karshe ta ce. "Laifi duk naka ne Fa'iz. Meye don Fa'izah tayi magana da yaron gidanta tunda kana da tabbacin ba zata yi maganar banza dashi ba? Don ta girka abinci ta basu domin kyautatawa bai kamata ka nuna jin zafin ka ba, sai ma kayi alfahari da ta zamo mai kyautar abinci ga na kasa da kai ba kace ta daina ba. Hoto kuwa duk muna tsaye aka yi shi, kasan baka so ayi hoto dashi don me ka turo shi? Suraj ya rufa maka asiri babu wanda yayi zaton ba kaine a wurin ba, meye laifi anan? Magana da kace bata yi maka ina ce komai sai ta dauro za'ayi? Ka sani Fa'izah ba mai son yawan magana bace tun tuni. Tunda har da bakin ka ka furta bata yi maka musu, sannan tana girka maka abinci, sai me ya saura? Dan Adam da ba'a iya maka har kana fadin gara maka zagi da duka da wannan. Yau da Fa'izah zagin naka take da duka da rashin kunya, ko kuma bata baka abinci dole ne in tsawatar mata. Don Allah ka koyi hakuri Fa'izu, zafin zuciyar nan baya da amfani ko kadan, kabi komai a sannu, a baya ka zaci wannan din da kake rainawa cikin kankanin lokaci haka? Har kullum addu'armu na tare da ku, komi zai yi dai-dai a gaba insha Allahu". Da alama jikinsa yayi sanyi, amma ba duka ba. Ya ce, "To amma Mama tsaki da harara fa? Gaskiya ba zan jure ba, don ban taso naga kuna yi ba ga su Baba ko wani cikin A.B baki daya. Wannan ai raini ne. Ko don Fa'izah ana sonta kowa na tsoron masifarta?" Abin ya bawa Mama dariya, amma ta gimtse. "In ma hakan ne bamu yi laifi ba tunda ai amarya ce, amarya kuwa kowa yasan bata laifi. Kuma ka dinga tausaya mata tunda dai auren nan kasan ba da saninta akayi shi ba, zuwar mata yayi kamar saukar aradu. Don haka ni yadda ta dawo yanzun naji dadi, ta fara nuna mana ta haifu, bata fi karfinmu ba kamar yadda muke zato, huce bacin ranta take yi kuma ta fara hucewar to ka bimu a sannu in kana son mu ci gaba da hucewa". Yayi kwafa ya ce, "Me nayi mata? In zaki yankata ta fadi laifin da take ikirarin nayi mata bashi da yawan hukuncin da nake karba. Banda ni din nine Fa'izun Hajjah Abubakar-Saddiqu, na Baban Kaduna da ABU wa zai yi hakurin dana yi? Ko anan aka tsaya an san ni jarumi ne wanda mace bata isa ta girgiza ba ko ta sani abinda ban yi niyya ba. Don haka nayi niyyar mu tafi tare wajen neman abincina, kinyi kadan ki canza min ra'ayi. Wallahi Mama yarinyar nan ba abar tausayi bace, ki daina jin tausayinta kina ganinta haka kamar wata mumina. Musa ce a baki Fir'auna a zuci, rashin mutuncin dake cikin bakinta da zuciyarta yafi bakinta girma". Mama tayi dariya tana mamakin yaushe bakin Fa'iz ya bude yake zaro Hausa haka? Abar da ada sai dai kaji yana yi mata baragada in ya jima yana magana, lallai Fa'iza bata kama kurwarsa da wasa ba. Ta gyada kai ta ce, "To ke Fa'izah kinji wannan?" Na ce, "To Mama tunda ya ce tsaki nake masa to yayi tafiyar sa shi kadai mana ya huta da jin tsakin? Maimakon inje ina yi mai ranshi na baci? Tunda cikin hutu su Junior suke sai muyi zaman mu tare a gidan har su Walida a karo, amma ni ba inda zan iya matsawa inbar iyayena da 'yan uwana zuwa inda ban san kowa ba tunda duk abinda nake yi masa baya gode ko daya, haka idan na bishi rai zai yi ta baci gara inyi zamana". Mama ta ce, "Kwarai kuwa, ba inda Fa'izah zata, zata zauna har ka samu hutu. Ni dama bana son yawon jirgin nan, tukunna ma kai da baka zama wuri guda, a tafe kake kwana a tafe kake wuni, meye amfanin bin naka da kake so tayi?" Kamar zai yi kuka ya ce, "Amma ba kullum nake kwana a tafe ba ko Mama? Abin cikin tsari ne, (we have breaks!)". Mama ta ce, "Oho maka! Na gama magana, ku tashi ku tafi don Allah. Allah Ya yi muku maganin abinda ke damun ku, Ya yaye muku shaidanun dake yawo akanku. Duk 'yan uwanku kowanne na zaune lafiya da abokin zamansa ba mai jin kanshi da dan uwansa sai ku. Ku taka a sannu, duniya ba'a yi mata gaggawa". Mun mike kenan Baba ya shigo, zuciyata kamar farar takarda nake gaishe shi. Fa'iz bai bari na dire gaisuwar dana debo ba tun kamin Baba ya zauna ya soma karanto masa yadda akayi, da hukuncin rashin adalcin Mama. Shi dai Baba da dadin ganinmu tare har ana zancen tafiya Birtaniya sai ya hau hamdala ga Allah a zuci, a fili kuma ya ce. "Tunda bata so a kyaleta man Fa'iz? Ba a son tilastawa cikin zamantakewar aure, watarana da kanta zata ce zata bika ne". Tun daga ranar da aka yi mana aure Fa'iz bai ji na bashi bakin ciki da takaici irin yau ba. Ya mike cikin fushi ya zari mukullin motarshi ya yi hanyar waje. Baba da karin tura haushi ya ce. "UHm! Na ce ba?" Fa'iz ya dakata amma bai juyo ba. "Ka nemo motar hawa a kyale min tawa ta huta. Haba, ya za'a ce in hau abu, kaima ka hau, wannan sam ba tsarina bane. Duk kabi ka zage min gari da motar ma bana so, ka je ka rike ka kirgo kudinta ka biya ni, fakat". Ya ce, "Zan kawo abinda ya samu, shi kenan?" Baba ya ce, "Wane irin abinda ya samu? Naira miliyan biyar cur na sayi mota ta, haka za'a bani ko Naira biyar ban yarda tayi ciwon kai a ciki ba. Mota ta 'R-Class' ce kaje ko'ina ka tambaya haka kudinta yake". Takaici a wurin Fa'iz baya faduwa, ya ce. "Haba Baba, ai babu ciniki tsakaninmu. Yaushe ma na fara aikin da har zan tara abinda kake fadi? Duk ajiyar da nake yi ta kananan ayyukan da nayi kai na turowa aka yi aikin gidan nan da muke ciki". Baba ya ce, "Kai ka sani. Albarkacin shekara biyu da tayi a hannuna, na shigeta sau bakwai, a kawo min naira miliyan uku, cash ba ta 'credit card' ko 'cheque' ko 'internet banking' ba. Ni nasan bankin da nake mu'amala da abina". Mama dariya take har da kyakyatawa. Fa'iz bai kara tankawa ba ya fice. Na bi bayanshi nima dariya ta cika min ciki amma na kame kaina tunda ni ke da nasara. Ina shiga motar kafin na kai ga rufewa ya fisgeta kofar ta rufe kanta da kanta, saura kadan ta guntile min 'yan yatsu. Tunda muka hau titin da zai kaimu Zaria bai ce min komai ba, kazalika bai kalleni ba. Ya maida hankali sosai a tukin da yake yi (at a speedy level). Momi kurum muka samu a gida muka gaisheta, bai iya yayi hira da ita ba duk kokarin da yake na boye bacin ransa. Daga bisani ya tashi ya barmu ya ce zai je cikin (city) ya dawo sai mu tafi. Bayan fitarsa Momi ta zuba min ido tana kallo. "Wato mai hali dai baya fasa halinsa. Ana murna kwana biyu an jiki shiru ashe wata sabuwar tsiyar kike shukawa a inda babu mai ganinki balle ya tsawatar. To in kowa baya ganinki ko Fa'izu bai kawowa kowa kararki ba, Allah da Ya halicci kowa da komai Shi Yana ganinki da duk abinda ki ke aikatawa na zahiri da badini. Daga ganin yadda Abubakar yake kumburi wanda ba halinsa ba, kinyi rashin mutuncin naki ne". Na ce, "Wallahi Momi banyi masa komai ba, lafiya muke zaune tunda muka bar gidan nan. Tsakanin shi da Mama ne, don kawai ta ce sai ya sake dawowa na bishi inda yake, shi kenan yake fushi". Momi ta harzuka, ban kai ga direwa ba ta ce. "Ubanki za ki zauna kiyi eye? Na ce ubanki za ki zauna kiyi, ke ba zakiyi zaman aure irin na kowacce mace ba? Shashasha maras mutunci. In don ni kike yin wannan dabbancin wallahi kin dauki alhakina don ni babu abinda Abubakar yayi min wanda ban dauka a yarinta da kuruciya ba tunda dai ni dai gaba da gaba bai taba fuskantata ya zagenin ba sai dai inji a bakinki, wanda tun lokacin ba sauraron ki nake ba, bani kuma da tabbacin ko karya kike don bacin ke ban taba jin wani ya ce Fa'iz ya zageni ko baya sona ba. Akwai abinda baki sani ba wanda in kin sauke iskokin dake kanki kinbi a hankali watakila nan gaba za ki sani. Baka taba jin ZUCIYAR MUTUM... baka kwantar da hankalinka a kanshi ba. Don masu iya magana sunce ZUCIYAR MUTUM.... BIRNINSA!. Kin san Allah ki ka sake sako kafarki gidan nan sai nasa Babanku ya kakkaryata, ba dakin Abdallah ba ko cikin kuratandu kika shiga indai a gidan nan ne sai dai ki bi yawon duniyar daga yau babu mai hana ki". Idanunta suka cicciko da kwalla amma bata bari sun zubo ba don sanin hatsarin da zubar tasu ke tattare dashi a tare dani. Nayi murmushin da na tabbatar zai kwantar da hankalinta, gaba daya jikina yayi sanyi kalau. "Ba gidan nan zan dawo ba. Tunda muka tafi ma ai ba a gidan Baban Kaduna muke ba, Walida bata gaya muku ba? Muna gidanshi ne a Malali GRA". Ta dan zuba min ido kamar bata yarda da abinda na ce ba. Na ce, "Wallahi Momi da gaske nake, kuma ki tambayi Mama. Ko ya tafi a can zanyi zamana nayi miki alkawari, in kin ganni gidan nan ko gidan Baban Kaduna ko Giwa ko Kano wajen Ya Rabi gaishe ku nazo yi". Anan ne ta saki fuska ta ce, "Shi kenan. Su Walidar basu dawo bane, daga can suka wuce Lagos wajen su Zanirah". Dai dai lokacin da muka ji sallamar shi a dakin, abin mamaki ya saki ba kamar yadda muka zo ba. Ya ce, "Momi zamu wuce, ni kuma gobe zan wuce Wales din kasar England, na samu aiki da 'British-Airline' zan jima ban zo ba sai na samu (break) mai dan tsaho". Momi ta sanya albarka tayi addu'a da Allah Yasa matakin arziki ne, Ya kara rufa asiri, Ya kiyaye sharrin karfe da na iska, Ya cire haramun daga cikin abinda za'a samu alfarmar Manzo (S.A.W). Ya fadada murmushinsa cikin jin dadin addu'arta yana fadin. "Amin Ya Rabbi Maman Walida". Na mike, ta dubeni ba yabo ba fallasa. "Akwai garin semo da bushasshiyar kubewa da bushasshen kifi in kuna bukata". Na ce, "A'ah Momi, ba yanzu ba dai, zan aiko in ina bukata". Ta ce, "Ke kika sani". Da muka shigo Kaduna ya tsaya wani babban 'Shopping Mall' bai yi min ko tayin shiga ba shi kadai ya shiga abinsa. Ya jima sosai kafin naga yaran kantin sun biyo shi da manyan ledoji, suka zuba a bayan motar, sai katon-katon na abin sha (ruwa da lemo) kala daban-daban. Akan hanyarmu ta shigowa Malali ya tsaya ya tsayi gashasshen nama muka karaso gida duk jikina a sanyaye yake. Muna shiga Ya'u ya taremu, sai na samu kaina da kara jan lullubina na rufe har rabin fuskata ban san dalili ba ko don ya nuna baya so din ne da gaske? Bazan so ya zamo nayi sanadin hanyar abincin wannan bawan Allah ba, wanda ga dukkan alamu ita ce madogararsa kadai. Ya kwashe komai daga bayan motar ya shigar (kitchen). Yayi mana sallama ya fita. Ya maida kofar falon ya rufe da (key) ya dawo ya zauna bisa (carpet) ya kunna t.v tashar CNN yana rike da (remote) ya dawo ya zauna, ya janyo ledar namansa yasa a gaba yana ci yana sauraron labaran, bai kara kallo na ba kamar yadda bai nemi 'chips & chicken' ba. Na mike ba don an sani ba na shiga (kitchen) na soma sarrafa su kamar yadda na saba, amma na yau (with additional aroma and taste) saboda kamar ina neman hanyar shiri ne ko yaya ne dai na kasa gane kaina. Wata zuciyar ta ce tunda ni nayi nasara nawa ra'ayin aka yi masa fin karfi aka bi, bari in dan kyautata. Dana kammala na aje a (dining) kamar yadda na saba, na ce. "Ga (dinner) din". Kamar ba da shi nake ba kallon t.v kawai yake duk da na tabbatar ya ji ni saboda ba wai yasa muryar t.v din da yawa bane, a'a dai-dai jinsa, raina ya dan baci na wuce na shige daki na sayo kofa amma ban sa mukulli ba. Can naji motsin kwanuka a (kitchen_, na daga labule ta taga ta wadda kana hango duk abinda ke faruwa a (kitchen) sai na hango shi ya dora 'yar tukunya akan (cooker) ya saka indomie guda biyu bai ko cire ledar maggi da chili din dake ciki ba ya kawo ruwan zafi wajen kofi uku wanda ya sha kan indomin har baka hango ta ya zuba, ya rufe. Ya fita daga kicin din ya koma ya ci gaba da sauraron labaransa. Kamar inje in duba wannan lamari wata zuciyar ta kwabeni abinda ba ruwan ka ance dadin kallo gare shi, na koma nayi kwanciyata. Anfi minti talatin kafin inji shi ya koma (kitchen) din, ban san abinda ya faru kuma ba bayan nan. Bayan kamar minti biyar naji fitarsa a mota, tsegumi har tsunkuli na yake nayi (kitchen). Na bude tukunyar daya dora a wuta. Indomin ta hadu ta dame ta zama kunu zance ko koko ko tuwo, gatan nan dai ba suna ba fasali. Na tabbata ba zai iya ko tabawa ba balle ya sanya a bakinsa shi ne ya fita yaje ya sayo. A raina na ce, "Ashe dai girkin banza na da amfani tunda sai da shi ake rayuwa". Na kara duban dabgen da yayi nayi dariya na mayar na rufe na koma daki. Nayi zaton zan kuma jin duriyarshi kafin nayi barci, amma har garin Allah ya waye banji ba. Haka dana tashi yin sallar asubahi na fita falon ko zan ganshi sai abincina na daren jiya (chips and chicken) kadai na tarar akan (dining table) inda na ajiye shi ko matsar da shi ba'ayi ba. Daga nan nayi brush na koma daki, ban tashi ba sai karfe tara na safe. Da hanzari na nufi (kitchen) na soma aikin hada masa karin kumallo, amma na yau 'is special' kamar na daren jiya duk da raina ya sosu da rashin cin da bai yi ba. Cikin dan lokaci na kammala 'scottish egg, plantain with syrup, bread with jubnah' da ruwan na'a-na'a. Cikin dan lokaci kalilan na kwashe na jiya na shirya su a inda ya saba karyawa a kwanaki goma sha ukun da muka yi tare. Na koma daki nayi wanka nayi shiri cikin atamfa sufa ja mai ratsin kore da baki wanda dinkin ya zauna a jikina sosai, zanin ya bude daga kasa. Na fesa turare 'escada sentiment' na kalmasa dauri sassauka, na dubi kaina a mudubin dogon yaro na yi wani irin 'fresh' (looking takeaway) ko ni kaina na baiwa kaina sha'awa. Sai na samu kaina da tambayar kaina kwalliyar ta mece ce? Mene ne dalilinta? [22/02 1:58 PM] Sumayya Takori: Dana gaza samarwa kaina wadannan amsoshin guda biyu, sai kawai na fita, ina juyowa muka hada ido yana kokarin fitowa daga nashi dakin janye da (travelling bag) mai matsakaicin girma 'troller' ruwan zuma. Dammm! Naji kirjina ya buga, bugawar da ba'a kirjin kadai ta tsaya ba ta hudo ne har cikin zuciyata. Sanye yake da riga fara anyi rubutu da shudin zare 'TOMMY HILFIGER' da shudin wandon (jeans) turrare, sumar nan ta kwanta tayi luf a saman kansa sai sheki take, inda duk ya motsa sassanyan kamshin '212' ke tashi.. Ya saya kwayar idanunshi cikin gilashi 'porsche' mai duhu ainun, don haka kai tsaye ba zan iya cewa ga halin da kwayar idanunshi ke ciki ba. Ya ajiye jakar a kusa dashi ya zauna a kujera sosai ya zage zip dinta, ya ciro katin ATM ya dago ido ya dubeni ina tsaye a inda nake ban ko motsa ba. "Ko zaki iya zama?" Abinda ya ce dani kenan. Tamkar wata rakuma da akala na bi umarnin furucin nasa, na zauna a kujerar dake fuskantarsa. ATM card din ya aje mani gabana, ya yagi takarda yayi rubutu itama ya turo mini. "Ga PIN dinsa nan na rubuta a jikin takardar na bankin UBA ne, in kina da bukatarsu sai ki kira Shu'aib a waya ki turashi ya debo miki adadin da kike bukata. Anjima Surajo zai kawo miki waya ni na tafi ban san kuma ranar da zan dawo ba. In kina da matsala ki kira Mama ki gaya mata, Ya'u zai ke kawo miki (recharge-card) duk sati, ban yarda da fita ko bakin (gate) ba in ba lalura ta rashin lafiya ba tunda rayuwar da kika zaba kenan". Ya mike yana zuge jakarsa. Idona ya cicciko da kwallah. Ba zan ce bai yi min dai-dai ba, kuma bazance yayi min dai-dai ba. Na san akwai hakkokin shi da yawa akaina, wadanda na sanya kafa na shure na take akan sanina, wadanda hujjojina babu ruwan Allah dasu. Auren Fa'iz dake kaina kadai ya sani dole in bude baki yau inyi magana saboda halin rai, yau yake da tabbatas gobe babu shi. Sannan sha'ani na tafiya wanda bana fatan hakan. Muryata na rawa na ce, "Ga abincinka fa ka karya mana sai ka tafi". Ya dubemu duka ni da abincin ya hararemu duk da ance aikin banza wai harara cikin duhu don kuwa bakin gilashi ne a idonsa, ya ce. "Ki rike kayanki, na gode. Akanshi dai kike yi min tsaki in na saki, to insha-Allahu ba zan sake cewa ki dafa min wani abu ba, sai kin ganni ma balle ince ki bani abincin. Zan tafi inda ba sai nace a bani za'a bani ba, balle aje ga goranta min ko yi min tsaki". "Kayi hakuri don Allah...". Na fadi cikin kuka. Ya dubeni cikin mamaki, nasan bai zata ba. Ni kuma harga Allah banyi hakan ko fadi hakan don wata manufa ba, sai don kar ya tafi da fushina in kasance cikin fushin Ubangiji da tsinuwar Mala'iku har yaje ya dawo, wanda ban san ranar dawowar tasa ba. Ya koma ya zauna, sannu a hankali yake zare gilashin idonshi, ni kuma ina ta sharbe. Ya kirani da wata irin kankanuwar murya. "Fa'izah!". Na cira jajayen idanuna na dube shi, ban amsa ba amma idanuna sun nuna ina sauraron sa ne. "Komi ya wuce?" Ya tambaya. Na sunkuyar da kai ina jan zaren carpet bance komai ba, amma na daina kukan sai ajiyar zuciya. Ya baro kujerar shi ya iso gabana yayi zaman dirshan, ya kamo hannuna na dama ya sarke cikin nashi. Na dago kai na dubeshi kana nayi sauri na maryar na sunkuyar. Ko da can bama iya hada ido da wadannan 'sexy' idanun balle yanzu? Da aka samu karin ilhamomi masu yawa a cikinsu? Ya sumbaci goshina, idanuna, karan hanci da bakin da yakan ce rashin mutuncin dake cikinshi ya fishi girma, mun dade cikin wannan halin, da dukkannin mu bamu taba tsintar kanmu cikinsa ba, zuciyoyi da ruhinmu sun hade sun cure wuri guda, muka samu kanmu cikin mantawa da duk abubuwan da suka faru cikin rayuwarmu. Dai dai lokacin da kararrawar shigowa falon ta soma kara. Mikewa nayi cikin sanyin jiki, don dama neman hanyar mikewar nake yi na rasa, saboda gangar jikina da zuciyata sun gaza karbar sababbin al’amura masu girma irin wadannan da Fa'iz ke bijirowa dasu a wannan lokacin, wadanda bazan ce ban sani ba ko ban san sune suke wanzuwa a cikin aure ba. Sai dai ban taba yi ba ko kusantar yi ba a kulliyar rayuwata, daga yarinta har zuwa girma, sai ko yanzu da Fa'iz ke son tabbatar min da cewa, lokacin yin nasu ya zo. Goyon bayana da hadin kaina kadai yake jira, domin tabbatuwarsu, 'and I lack such a courage!' (Na rasa wannan kwarin gwiwar). A ganina ‘it’s not the hightime. ..... (lokaci bai yi ba). Don haka wanda ya danna kararrawar nan in banyi masa addu'ar alheri ba hakika ya cancanci inyi masa fatan ALHERI. Na bude kofar ba tare da tambayar ko waye ba haka ba tare da waiwayar halin da Fa'iz ke ciki ba, Surajo ne. Nayi murmushi na bashi hanya ya wuce amma kallo daya zai yi min ya tabbatar a rikice nake, kuma hankalina a tashe yake domin na tabbata ya zo ne domin ya dauki Fa'iz ya kaishi filin jirgi. "Madam rikici, ke kika rike Pilot ko? Kina sane da cewa karfe goma sha daya zai tashi? Don Allah a ringa lura da lokacin aiki cikin lokutan ayyukan soyayyar kada a koro ko ku koma direban tashar da kuka saba". Fa'iz ya harare shi yana gyara zaman gilashin sa a kyawawan idanunsa, bisa doron karan hancin sa. Ya kwalawa Ya'u kira, ya shigo da sauri, ya dauki jakar suka fita. Surajo ya aje min kwalin waya (Samsung-tablet) ya janyo kofar falon. Na bisu da kallo cikin shatatowar hawaye dana kasa maida su ko rage gudun zubarsu akan kundukukina. Ko hawayen menene? Bazan iya cewa ba. ***** BAYAN TAFIYAR FA'IZ Wani ikon Allah ko abin mamaki tun tafiyar Fa'iz sai naji sam bana jin dadin gidan. Kewa da kadaici suka yi min sallama. Da yana nan, ko banyi masa magana ba shi zai mani, zanji motsin dan Adam cikin gidan ta hanyar karakainarsa, a falo da (kitchen) da nasa dakin. Amma yanzu gidan ya zame min kamar makabarta ko motsin kyankyaso babu. Kusan kullum ina baya wajen Dawisu ina jefa musu abinci, har kujera nake kafawa in zauna. Yanzu har sun saba dani har kofar falo suke biyoni in na haura lokacin da nake fitowa basu abinci. Sai suzo kofar falo su tsaya su bude bindinansu abin ban sha'awa suna juya su gabas da yamma, kudu da arewa cikin nuna baiwar kyan da Ubangiji Ya yi musu da bai yiwa wani tsuntsu a duniya ba. Yaran gidanmu duka an hana su zuwar mana dagani har Ummi. Haka 'yan uwa ba mai zuwa don kamar yadda na fada a baya sunce sai ranar da suka ganni da ciki irin na Ummi ko 'ya'ya irin na Zaneerah. (In fact) ina kewar Fa'iz duk da bana so na yardarwa zuciyata cewa kewar tasa nake yi. Duk da bamu dade tare ba, sati biyu kacal muka yi tare, abubuwan dake cikin sati biyun masu yawa ne (it seems like a journey of two year full of blissful adventures) da suka kasa goguwa a zuciya da kwakwalwata. Fadansa na bani dariya, haka kishinsa na babu gaira babu dalili. In ka debe wadannan na fahimci wasu abubuwa wadanda ada ban sani ba, wato Fa'izu Abubakar, mutum ne mai saukin kai, barkwanci, dadin mu'amala da dadin zama amma fa ga wanda yake so kadai, shi yasa iyaye da dangi duka kowa ke sonsa. Idan baya yi da kai ko ya tsaneka zaka dauka ne cewa babu wanda ya kaishi rashin kirki da rashin dadin mu'amala a duniya. Hakazalika yawan kiran sunana da yake yi cikin gidan Fa'izah-Fa'izah-Fa'izah kai kace shi ya rada min suna Fa'izah ko Aunty Fa'izah. (I also missed his regular sayings) "O.K?" Wannan ban san me take nufi ba har ya zamanto nima ta zauna min a baki ko magana na yiwa Ya'u na gama sai na ce "o.k?" A da kam nasan ba haka Fa'iz yake ba sam, magana ma wuya take masa balle mu'amala da mutane, ban san sanda bakinshi ya bude ba domin ada sai ya wuni baiyi magana ba. Ina kewar Fa'iz ne a bisa dalilai da yawa dani kaina ban san adadinsu ba, ko ba komai ina jin motsinsa cikin gidan da maganganunshi ko a waya ne nasan dai ba ni kadai bace cikin gidan. To amma ya tafi, ya bar min kangon gidan da abin da ke cikinsa, gidan yayi shiru, yayi tsit sam babu dadi kamar babu mahalukin dake rayuwa a cikinsa. Ina kwance tsakiyar kafet din falona na tada kai da filon kujera kwanaki uku da tafiyar Fa'iz, aka danna kararrawar son shigowa fallon. Daga nan inda nake kwance nake tambaya, "Waye?" "Ni ne Shu'aib". Na bude ina dariya, "Yaya Shu'aib kaida wa?" Shima dariyar yake yi, ya shigo na bashi hanya ya wuce ya zauna a kujera muka soma gaisawa. Sannan ya ce. "Yaya Fa'iz ya turo ni inzo in karbi ATM dinki in amso miki kudi a bankin UBA ko kina da bukatarsu, in kuma hada miki (tablet) dinki in sanya miki 'Interner data' in dora ki akan 'social networks' akwai 'group' na A.B family a (whatsapp) kowa yana ciki ki dinga hira da 'yan uwa madadin kiyi ta zama shiru". Ban yi musu ba na mike na dauko masa 'Samsung tablet' din na kawo mishi ko ni zanso hakan. Amma jaganar karbo kudin a UBA na ce. "Shu'aib bar kudin nan a muhallinsu, me zanyi dasu? Bana bukatar komi sai abinci gashi nan dankare nau'i-nau'i a 'store' da 'freezers, ga Ya'u na kawo katin waya. (I need nothing)". Ya gyada kai cikin gamsuwa, hannunshi da idanunshi akan tablet din yana ta shiga 'applications' muna ci gaba da hirar mutanen gida da na Giwa. Na mike na kawo masa lafiyayyen 'yoghurt' din 'L&Z Dairies' dake cike da (fridge) dina da sabon cup-cake din da nayi jiya. Na ce, "Shu'aib, ina Hajjaty?" Sai bayan da na fada ne kunyar kaina da nadama suka zo suka rufe ni, muryata ma a lokacin tayi kasa sosai. Dariya yayi, "Hajjah tana nan lafiya ko jiya na je Giwa sun tafi Umrah ita da Baba Na'ibi". Ya cigaba da shan L&Z Dairy yana lumshe ido saboda gardin madarar ya aje gorar, ya ce. "Wai kuwa don Allah Aunty Fa'iza yaya kike yi Yaya Fa'iz yayi miki magana?" Shu'aib kusan sa'a na ne domin bai fi shekaru biyu ya bani ba, tsakaninsa da Fa'iz kuwa shekaru bakwai ne , mukan tattauna matsalolinmu da junanmu tun sanda muka fara hankali. Nayi murmushi na ce, "Kamar Yaya Shu'aib?" Ya ce, "Yo mutum ba fara'a kullum fuska kamar bindinga, babu alamar rahama sai muzurai. Duk inda yara suke ya tashe su. Shi ne nake mamakin yadda zai zauna da iyali yayi mu'amala ta dadin rai dasu. Don na tabbata in ba mace mai tsantsar hakuri ba, babu wadda zata iya daukar ginshirar Yaya Fa'iz ...". Dariya nayi, "Baka da dama Shu'aib! Ni dai toh!! Ba zan ce baya magana ba, amma yafi yi a waya da abokansa!!!:. Na jawo wata hirar don hirar Fa'iz da yake sani ya na sanyani cikin wani hali, da ni kaina ban san shi ba. Ban san irin shi ba, mai wuyar fassarawa ne. Har la'asar muna tare da Shu'aib bayan ya hada min 'Whatsapp, wattpad, Facebook, Twitter da Instagram. Sannan ya zuba min duka numbobin 'yan uwa, muka yi sallama na juye duka 'cup cake' dinnan nace ya kaiwa Mama. A ranar na soma (chatting) dasu Ummi nima da (family group) dinmu ta watsapp. Sati biyu bayan nan Mama ta sake aiko Yahya ya kawo min wasu jarkoki cike da magani mai zaki wai Mama ta ce in sanya a (fridge) in maida su ruwa sha na (tsumi). Da zuma iri-iri 'yan asali da abubuwa dai daban-daban wani ta ce asha da nono,. wani da peak-milk. Zuciyata tayi ta raya min meye nufin Mama na bani wadannan magunguna? Amma da nayi tunani mai zurfi Mama dai uwata ce wadda ba aurena da Fa'iz ne ya hadamu ba. Mama uwata ce ta tun fil'azal ba zata bani abinda zai cutar dani ba, sai na dukufa shansu dare da rana yadda tayi 'prescribing' kowanne a rubuce a 'yar takarda har suka kare. Satin ya kare ta sake aiko da wasu, haka muka yi tayi har watanni biyu. Rannan a (chatting) nake tambayar Ummi ko tasan magungunan mene ne mama ke dirka min? Ta ce in fasalta mata su. Na fasalta har 'prescription' dinsu. Tayi alamar dariya ta hanyar turo 'emotions' na dariya ta ce. "Mama nayi mana gatan da Hajjah, Aunty Hawwa da MOmin ABU suke kunyar yi amna. Ke dai kiyi ta sha Fa'izah ba zai cuce ki ba. Nima nan haka take aiko min dasu jarka-jarka kulli-kulli. Kiyi godiya kawai ga Allah da yayi mana baiwar uwar mazaje tagari mai kaunarmu tsakani da Allah. Daga nan Mama ta koma aiko turaruku iri-iri 'yan Borno. Ni kam karba kawai nake ina faman turara daki. Amma sai Mama tayo waya ta ce. "Fa'izah! Turarukan dana aiko miki fa ba na turara daki bane, jikinki zaki ke turarawa, kullum da yamma bayan kin fito wanka. Akwai abin turaren wuta na lantarki (burner) cikin lokas din (kitchen) dinki ki dauka kiyi amfani da ita, nasan hankalin ki bai kai wurin ba". Na ce, "Akwai wata dana samu ne a falo da ita nake amfani, insha-Allah zanyi yadda kika ce. Mama Allah Ya kara girma". Murmushi tayi ta aje wayar. Tunda nayi nisa a sha da amfani da magungunan da Mama ke aikowa, sai na soma samun wani irin sauyi a jiki da zuciyata. Na nemi kiyayyar da nake yiwa Fa'iz na rasa tana (decreasing gradually) a kullum. Sai wani irin bege da son ganinsa. Da tsananin son kebewa dashi da son jin koda muryarsa ne amma babu. Tunda ya tafi ko sau daya bai kira ni ba har na soma zargin anya ba asiri Mama ke yi min ba, inso danta in kaunace shi? Nayi saurin kawar da wannan tunanin tare da yin istigfari a zuciyata. [23/02 11:32 AM] Sumayya Takori: *** Na wayi gari ne yau cikin matsanancin nishadi, irin wanda ban taba tsintar kaina a ciki ba. Don haka na share ko'ina na goge lungu-lungu da sako-sako na gidan ya zama tas, sai sheki yake kamar lomarka zata fadi ka sanya baki ka side, duk da gidan ba wani datti yayi ba, don akai-akai nake kula da tsaftarsa. Na samu kaina da son shiga dakin Fa'iz, ko na rage kewar sa data addabe ni. A hankali na murda kofar na shiga dakin ga mamakina a bude ya barshi, sallama dauke a baki na. Fa'eez ya kawata dakin baccinshi da duk wani nau'in kayan jin dadin rayuwa. Duk da A/c a kashe yake, amma dakin da sanyinsa, wanda ya hadu ya cakude da sassanyan kamshin '212'n da Fa'eez ke amfani dashi (on a regular basis). Babu komi dake cikin dakin da aka saye shi cikin Kadunan, bayan gidan Fa'iz kadai abin kallo ne, wanda bai cika girma ba. Banda katifar ruwa data mamaye gadon shi, karamin 'frame' din dake aje dai-dai santar inda yake sanya kanshi guda biyu kanana su suka dauki hankali na. Sannu a hankali nake takawa zuwa garesu, yayin da kafata ke nitsewa cikin (center-carpet) mai tsananin taushi dake gaban gadonsa. Wanda ya sha bamban da sauran carpet din dake cikin gidan baki daya. A hankali na russuna na dauki 'frame' din. Wani dadadden hoto na ne mai rungume da (teddy bear) wanda da alama ya kaiwa gwanaye ne sun wanke shi sun adana a cikin 'frame' din ya zama kamar daukar jiya-jiya. A kusa dashi wani hoton nawa ne cikin (swiss-lace) da goggoro, wato ranar partyn 'Indoor-sport hall' na nan Kaduna. Na tsuke giran sama da ta kasa wanda hakan ba karamin kyau ya kara min ba tamkar anyi shi ne 'in-style' ba bacin rai ba. Na tambayi kaina wannan shi ne 'SO' kenan? Wanda ni bana jin shi? Don ko cikin wayata ba zan iya ajiye hoton Fa'iz ba balle a dakin barci na, inda nake ta da kai da mayarwa, a yayin kwanciya da tashi daga barci. To me ya hana inso Fa'eez? Babu! Illa shi SO din abu ne wanda ke yin kansa, ko ince yin Allah ne, ko kuma wani hali na mutum ko wasu (personal-attributes) kan zamo sila na samuwarsa, and Fa'iz 'lack any loving attribute to be loved upon'. Wato bashi da wani hali da za'a so shi don su, sai wani sashe na zuciyata ya ce dani. "A bisa rashin saninki kenan a da, banda yanzu, da kika fara lakantar ainihin waye FA'EEZ BAMALLI?" (And I came to the conclusion that) ba wani abu ne ya hana ni son Fa'iz ba illa tunanin baya... Inada RIKO, bani da mantuwa, sannan inada gudun wulakanci. Ina son momi na, Ina ganin muddin na sake da Fa'iz nan gaba zai koma min Fa'izun Hajja, wato Fa'izunsa na baya, zai sake sanya ni cikin 'problem' sannan zai sake tsanata... Na cigaba da kallon dakin tare da komi dake cikinsa ba tare da na bude kowacce ma'adanar kaya ba (locker). Ba don komi ba sai don nasha jin Hajjah na fadin, "Yiwa miji bincike ba ta'ada ce mai kyau ba, duk mai yiwa mijinta bincike wata rana sai ta binciko abinda zai daga mata hankali, ya hana ta bacci, ya sanyata bakin ciki wanda bata da maganinsa. Watarana sai ta binciko abinda ba alkhairi ba!". Duk da baya dakin amma kamshinsa 'permanent' ne. Turaren '212' tamkar shi kadai aka yiwa. Komi na Fa'iz kamshinsa ne a jiki hatta takardunsa, bedsheet da labulayen dakin nasa. Na kasa fita a dakin Fa'iz, sakamakon wani shauki (emotion) dake dibana, zan so ace a lokacin yana cikin dakin ne ko yana falo yana kwala min kira in kawo masa kaza da 'chips' dinsa. Shaukin dake dibana ne ya debe ni ya kwantar a gadon Fa'iz, ya janyo tattausan bargonsa ya lullube ni dashi. Da filon shi na tada kai na lumshe ido ina cigaba da shakar daddadan kamshin na '212' (men). Na soma zargin kaina da son Fa'iz a karo na farko. Wadannan (emotions) din (are for real!) YAA SATTAR!!! Ya Sattaru, idan mafarki nake ina rokon ka da ka farkar dani. Na bude dukkan idanuna dake lumshe, da karfi nayi wurgi da filon na zauna dabas a tsakiyar gadon ina wurga ido kamar mara gaskiya. Eh, mara gaskiya ce (in fact!) Domin son karyata 'emotions' din nawa nake da gangan suna fin karfina. Na sakko daga gadon cikin barin-jiki, amma ga mamakina na kasa fita a dakin Fa'iz! Ina son dakin!! Ina son nayi bacci a dakin ko na samu nutsuwa. Na koma na kwanta cikin mutuwar jiki da zuciya, naja bargo na rufe har kaina. Bacci mai karfi ya fisgeni. Tafiya nake cikin wani kungurmin daji, ba gida gaba ba gida baya, na bullo ta gabas aguje nake a dalilin wutar dake bina, wuta bala-bala wadda ke tafe ta hanyar cin busassun kirare na jejin. Ina gudu ina kiran sunan Allah amma wutar nan bata bar bina ba. Gudu nake kamar raina zai fita har na sare, karfina ya kare. Ina gab da faduwa a yayin da muka iso gab da wani tafkeken kogi, na daga kafata da niyyar in fada ruwan kawai ya cinyeni in huta, ya fiye min cinyewar wutar. Sai ji nayi wani sassanyan hannu ya rungume ni. Wannan hannun ya ce. "QUL YAA NARU KUNI BARDHAN WA SALAMUN ALA IBRAHEEM... (Yaa ke wuta ki zamo mai sanyi da aminci ga Ibrahim)". "Na yafewa Fa'izah dukkan abinda tayi min wanda na sani da wanda ban sani ba, wanda tayi akan sani da wanda tayi bisa kuskure, daga ranar da aka daura mana aure... har zuwa ranar da zan daina numfashi...!". Kamin in dago inga wane ne? Wutar nan tabi ruwan. Bata ba dalilinta. Haske ya mamaye duhun dake mamaye dani. Na dago a hankali a lokacin zuciyata tayi fari kal! Babu sauran wani kunci ko wani kullaci a cikinta. Na dubi wanda nake rike a kirjin nasa, wani kirji ma'abocin tarin ni'ima da sanyi da sanya salama, ba wani bane FA'IZ ne, FA'IZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA. Idona ya bude 'vivid' na tabbatar mafarki ne nake yi. In banda gumi ba abinda nake shirbinawa. Illahirin jikina duka rawa yake, na rasa abinda ke min dadi. Na kifa fuskata cikin tafukana na soma kuka. Wannan mafarki shi ake kira kukan kurciyaa...! Wani irin sarawa kaina ya shiga yi saboda kuka. A hankali na mike na nufi kofa don fita daga dakin ko na samu sa'ida cikin zuciyata. Sai nayi tuntube da wani abu kamar littafi gab da bakin kofar dakin. Na russuna na dauka, littafi ne na ajiye tarihi da mihimman bayanai (Diary) da alama garin fita ya yarda shi ba tare da ya sani ba. Anan bakin kofar nayi zaman dirshan ina buda shafukan littafin. Rubutu yayi na abinda ya kunshi tun daga ranakun kuruciyarsa, da tafiyarshi kasar Russia. 'Tittle' din rubutun shi ne; "ONLY ALLAH KNOWS WHAT FUTURE HAS IN STORE FOR US". A wani shafi Fa'iz yayi wani rubutu wanda da alama tun tali-talin kuruciyarsa yayi rubutun domin kwanan wata na kalanda wanda aka buga littafin cikinsa ya nuna hakan. Rubutun yayi matukar bani dariya. "MEYE DALILIN DA YASA NA TSANI FA'IZA? BAN SANI BA! ILLA SAI DON CEWA ITA DIN KYAKKYAWA CE, TA FINI KYAU, A LOKACIN DA NAFI DUK ZURI'AR A.B KYAU SAI TAZO TA DAMENI TA SHANYE, KOWA YA KARKATAR DA KAUNAR DA YAKE YI MIN GARETA; MAIMAKON FA'IZ KOWA SAI FA'IZAH!". Murmushi nayi na cigaba da buda shafukan. Wannan rubutun na shafi na gaba ga abinda ya rubuta. "A Giwa ne. Misalin karfe goma na safe. Ina zaune falon Hajjah ina kallon fadan Isra'el a CNN. Wayar falon Hajjah dake ruri a gefena ban dauka ba sakamakon tunanin da yayi min rubdugu a wannan dan tsukin. Wanda bai wuce SON FA'IZAH ba! Fitowarta da daukar wayarta cikin kumfa ya sanyani kai dubana gareta. Duk da kasancewarta yarinya karama a wannan lokacin, 'yar shekaru goma sha hudu amman ta mallaki suffa kyakkyawa irin suffar da nake so ga 'ya macen da nake burin mallaka matsayin matar aurena. Tun daga wannan lokacin son Fa'izah ya ci gaba da ruruwa a zuciyata kamar gobarar daji. Nayi kuka nayi nadamar da bata da amfani, musamman da na fahimci kakkarfar soyayyar dake tsakaninta da Yaya Aliyu. Tsananin kishin Aliyu da nake, ya sanya ni hantarar Fa'izah a kullum a duk lokacin da yake zaune. A wauta ta a wancan lokacin Aliyu yaga bakin Fa'izah ya janye daga gareta, ya daina sonta amma ya ki. Asali ma sai kareta yake, yana bin bayanta cikin kowanne hali. Akwai ranar da suka amso takardun jarrabawar firamare, don Aliyu yaji haushi kawai nace takardun Fa'izah basu yi kyau ba, komi 'fail' 'poor'! To Aliyu yaji haushin, amma ba irin wanda nake so ya ji ba. A ranar ne yaga "love colour" na matsananciyar soyayyar Fa'izah cikin kwayar idanuna. Hankalin Aliyu ya tashi kwarai domin yana gudun abinda duk zai kawo mishi matsala a soyayyar shi da Fa'izah. Musamman ni dana kasance dan gatan Hajjah, wanda dana furta sai aikatawa. Aliyu ya dubeni cike da masifa, cikin harshen Turanci ya ce. "Ina gargadinka Fa'iz! 'Don't dare say it'... wato kada ka taba furtawa sai kayi nadama anan gaba". Na yiwa Aliyu kallon ko ni ko kai har su Fa'izan suka zargi wani abu. A ranar munyi musayarta ba dadi nida Aliyu da muka fito waje, har saida maganar ta hada da manya. Inda naji dadi shi ne inda Baba Barau ya ce babu wanda zai kuma yin auren soyayya cikin A.B tun daga kan Baban ABU wanda shima yayi ne ba bisa sanin mahaifinshi marigayi Abubakar Giwa ba. Ya kara da cewa. "Fa'izah ta mai rabo ce. Don haka kada wanda ya sake ya furta mata yana sonta cikin mu duka". Akwai ranar da na sanya Fa'izah cikin bacin ran da ya rudata har ta rungume Yaya Aliyu. A ranar ni kadai nasan abinda naji. 'In fact' kishi ne matsananci . Abinda tayi min bai bani haushi ba illa haushin Aliyu. A ranar ne nasan na fara kuka 'for sake of Fa'izah's love' (saboda son Fa'izah). Fa'izah in tana kuka sha'awa take bani, in tana tsiwarta burgeni take, (I drive pleasure in making her cry). In tana kuka kyau take mini, sha’awa take bani. Shi yasa na kasance kullum cikin kirkirar abinda nasan zai sata kuka. Bakin cikin tafiya ta Russia? Ba na komai bane ba don komi ba illa tsoron kada Aliyu ya aure Fa'izah kafin na dawo. Na karyata kaina a wurin Hajjah da su Baban ABU, Baban Kaduna da Baba Na'ibi ranar da suka kawo min ziyara ta farko kasar Russia, na gaya musu cewa dukkan abinda nake cewa Fa'izah tayi, don inga hawayenta ne wadanda ke sanya ni nishadi, su kuma sanyani MURMUSHI. Komai na Fa'izah ina son shi, sannan 'is special' agareni. Duk abinda nayi mata nayi ne domin KAUNARTA da 'pretending' kaunar, 'as I have no option' banda yin hakan. Na farko ban isa in furta ba, na biyu kishin yadda Aliyu ya kankane komai nata, na uku ita kanta Fa'izar ta dauke ni makiyinta ne na a buga a jarida, ba abinda zanyi ya goge hakan daga zuciyarta. A zahiri, na soma son Fa'izah ne daga ranar data dawo Giwa. Ta cinye min naman miya. Babu abinda na tsana irin inga Baban ABU na dukan Fa'izah. A duk lokacin da naga hakan kukan zuci nake da azabta a zuci da gangar jiki. In shige daki inyi ta kuka. Akwai ranar da Aliyu ya kamani ina kukan ni kadai a daki bayan na yiwa Fa'izah sharrin da ya sanya Baban yi mata dukan kawo wuka, ya tuhume ni amma sai na ce masa bani da lafiya ne. Ranar da naji Hajjah ta ce mu tafi da su Ummi Kaduna (party) babu tunanin hanyar da zan bi in soke zuwanta da banyi ba amma na rasa. Cikin ikon Allah ta nemi da inzo rabon fada, anan ne na samu hanya ba don komai ba sai don KISHIN KADA WANI YA SO TA CIKIN A.B saboda yadda tayi kyau. Duk da kasancewar ta yarinya karama a wancan lokacin, tafi duk 'yan matan A.B iya tsara kwalliya, tafi su kyau mai daukar hankali. Sau da yawa nakan ji samarin cikinmu na fadin DAMA A BASU FA'IZAH! Na kan ji kishi kamar in kashe su, amma sai inga bari kawai in batata a wurinsu ta yadda zata yi bakin jini, koda an basun suce 'a’ah, inyaso ni sai ince a bani in karba da hakuri, don haka nayi furucin tana bin Yaya Aliyu B-Q, ko ince bata da kunya bata da kokari, kazama ce, kuma masifaffiya. Sai kuma tazo tana kazantar kowa ya gani hakan ya nuna ba kage nayi mata ba. Nayi wauta da tazo ta zame min bala'i, ko ince alhaki ya zame min dan kwikwiyo. Wautar da ta jawo Fa'izah ta tsane ni fiye da kowa a duniya har take addu'ar ALLAH YA KASHE FA'EEZ BAMALLI IN HUTA! Ni kuma Ya jarrabce ni da matsananin SO irin wanda ban ta ko gani ko cikin hikaya da labarun almara ba. A zahiri na nunawa Fa'izah kiyayya domin SONTA da yayi min katutu, bani kuma da yadda zanyi dashi. Duk kiyayyar da na nunawa Fa'izah KISHI NE da PRETENDING. Amma da hankali ya zo min, na gane na kuma fahimci wannan ba hanya ce da ake nuna KISHI ba, ga wanda aka yimawa KIYAYYA NE. Bayan ni a wauta ta nayi ne don samarin A.B su ki Fa'izah baki dayansu. Da sun kammala sakandire ni in aureta, tunda ta rasa mai so. Na manta da cewa ma babu batun nagani ina so a cikin A.B, a ganina koda an basun dai suce basa so. Tunda babu wanda zai so mace mai wadannan halaye da na kaga mata, har shi Aliyun, don dai yana da wata irin zuciya ne data sha bamban da ta sauran 'yan Adam. Ashe ni ban san wannan na nufin gina kiyayyata mara iyaka a zuciyar wadda na yiwa KIYAYYA DON SO. Ban tashi jin son Fa'izah na neman hallaka ni ba sai da nayi nisa da ita. Na kasa karatu na kasa ci, na kasa sha, barci ya kaurace min fau-fau. Da hoton ta na 'teddy bear' nake kwana nake tashi. Nayi kuka domin son Fa'izah, abinda ban taba yi akan mace ba: Nayi abinda ban taba yi ba a rayuwata domin SON FA'IZAH, wato "NADAMA". A shekarun karatuna, baki daya, kowanne sakan, kowanne minti, kowanne dakika da kowanne awa son Fa’izah da kaunarta ke kara habaka a tare dani. Ba komai ya hana ni yiwa Fa'izah aike tamkar su Ummi ba illa TUNA BAYA... Yadda Fa'izah ta tsane ni, yadda ta ki jinina, na tabbata ba zata amshi abin hannu na ba ko za'a kasheta. Tsammani ma zata yi wata cutar na kunso zanyi mata. To amma nayi mata aike da abu mai daraja a gareni, nake kwana nake stashi tare da shi. Nayi mata aike da HANKICI na, wanda ke nufin sakon kaunata zuwa gareta, domin na sanya anyi rubutu da harshen Larabci a jiki, an rubuta 'AHUBBIK' wato ina sonki da dukkan zuciyata! Daga ranar da aka daura aurenmu da Fa'izah na tabbatar Fa'izah alkhairi ce a gareni, kuma wani bangare ce ta cigaban rayuwata. Daga ranar na soma ganin budi takowanne bangare, aikina, nasara da cigaba cikin duk abinda na sanya hannu, mutunci da martabata a idanun iyayena suka karu. A dalilin aurena da Fa'izah ne mahaifiyata ta dawo da soyayyar ta gareni wadda ada ta haramta mini saboda na ki karatu kuma na takurawa Fa'izarta. Ta kuma fifitani a tsakanin sauran 'yan uwana. Kiyayyar da Fa'izah ke nuna mini tana kara min kaunarta ne a koda yaushe, tana nuna min ta san ciwon kanta, tasan mutuncin mahaifiyarta, tasan makiyinta, ta san masoyinta (in comparison to yaya Aliyu!). Tana hangen abinda ka je ya zo, tana hangowa kanta dacewa da rayuwa da wanda soyayya ce ta hadasu ba kamar ni data rika a matsayin makiyi ba, tunda (that's the way I proved myself to her). Kuma masu iya mmagana sunce "Makiyinka baya taba dawowa ya zama masoyinka". Wannan ne dalilin da yasa nake yi mata 'UZURI'. A hakikanin gaskiya ba kin Fa'izah nake ba, WAUTA ce ta KURUCIYA domin in samu ABINDA NAKE SO, wato ita FA'IZAH. Idan kowa yace baya so. Ni kaina nasan mutum ne miskili da akan rasa gane inda yasa gaba, mutane irina ba sa karantuwa (from every perspective). Ubangijin da Ya halicci zuciya Shi Ya sirrantata, Ya sanya ta zamo HIJABI a tsakanin 'yan Adam da abinda ke zuciyar su. Don su sirrinta al'amuran da Ya boye cikin zukatansu. Ina kaunar Fa'izah da dukkan ruhi, zuciya da bargon jikina 'but I cant express, neither explain. Bakin da ya furta sharri, zalunci da rashin kirki, ya dawo yana furta SO (will never be trusted) don haka Allah Yayi zamu cigaba da rayuwa ni da Fa'izah. Burina ya cika tunda ta zamo mata agareni kuma wani babban JIGO na rayuwata, kuma wani BANGARE na jin dadin rayuwata tunda mallaki na ce ko da har abada ba zata yarda da ni ba. Zaman mu tare a hakan ya fiye min zaman kuncin da na dandana a Ukrain ina azabtuwa daga soyayyarta. THE ISSUE OF MOMIN ABU Sha'ani na da Momin ABU kamar yadda Fa'izah bata fahimce shi ba ko ince bata sani ba. Babu kuma wanda ya taba tararta ya gaya mata, Momin ABU bata daga cikin Zuri'ar Abubakar Bamalli. Kamar yadda ya faru tun muna kanana, an tura Baban ABU bautar kasa Jihar Taraba, kamar yadda Baban Kaduna yake bamu labari, yana (service) din ne a gidan marayu na Jihar Taraba (Taraba State Orphanage Home). Maimunatu marainiya ce, da ta tashi ba uwa ba uba, ba dangi a gidan marayu. Kamar yadda Baban ABU ya baiwa su Baban Kaduna labari, ni kuma a lokacin bani da wayo da nayi wayo ne naji labarin a bakin Hajjah. An tura Ahmadu A.B bautar kasa Jihar Taraba, acan yaga Maimunatu, inda yake (serving) wato Taraba State Orphanage Home. Tana daga cikin 'yan mata goma a gidan marayun da suka kai minzalin aure, sannan mafi nutsuwa da kamalar cikinsu. Ya je ne a matsayin malamin (secondary school) dinsu, yana koyar dasu kimiyyar noma, wato (Agricultural Science). Maimunatu hazikar yarinya ce wadda Allah Ya yiwa baiwar kwakwalwar fahimtar karatu. Kamar yadda yake a cikin (psychological nature) na kowanne malamin makaranta. Wato kaunar hazikin dalibi da girmama shi hakan ce ta faru tsakanin Baban ABU da Momin ABU har kuma ya rikide zuwa soyayya mai tsafta da inganci. Wadda tausayi da kauna, shi ne tubali da ginshikinta. Kamar yadda Hajjah ke bamu labari, ta ko'ina Ahmadu A.B ya hanga ya tauna baiga ta inda marigayi mahaifinsa A.B zai amince masa auren Maimuna ba. Bar ta auren zumuncin gidansu da suka maida shi farillah, kuma shika-shikan rayuwarsu, rashin ASALI wani babban abu ne domin kashi tamanin cikin dari na yaran dake gidan marayu har abada ba'a sanin asalinsu ko ganin wani nasu. A haka suke zuwa duniya su koma, cikin kiyayewar Ubangiji. Wannan yasa Ahmadu A.B cikin tsaka mai wuya da tunanin abin yi. Na farko ba zai iya barin Maimunatu ba, maganar ma ace ya hakura da ita bata taso ba, domin ba karamin sonta yake ba, kuma shakuwar dake tsakanin su ta wuce tunanin kowa. Sai ya yi tunanin wadda yake ganin zata fisshe shi saboda KURUCIYA irin wadda ta faru dani akan Fa'izah! Ahmadu yaje kotun Musulunci an daura musu aure da Maimuna ta yin amfani da malaman shi na Jami'ar Ahmad Bello. Ya dauko Maimunatu ta kawowa Hajjah, a lokacin da cikin Fa'izah wata bakwai. Mafari kenan dana tashi cikin nunawa Momin Fa'izah wariya da kabilanci a tsakanin su Mama, Aunty Hauwa da tsararrakinta. Shi din ma na fatar baki ne, ko kallon banza ban taba yi mata ba, sannan a bayan idonta musamman idan Fa'izah ta bani haushi. Hali ne na zuri'armu baki daya (kabilanci) da 'ethnocentrism' duk wanda ba daga zuri'ar A.B ya fito ba, to fa ba cikakken mutum bane. Da Hajjah da marigayi suka ji kowacece Maimunatu hankalinsu ya tashi kwarai, sunyi fushi da Baban ABU fushi mai tsanani, sannan 'punishment' dinsa shi ne 'suspension' daga duk wani abu da ya shafi zuri'ar A.B zuwa wani lokaci da basu kayyade ba. Duk Ahmadu ya ce yaji ya gani, indai zasu barshi ya cigaba da rayuwa da ita. A lokacin hatta zuwa daurin auren cikin gida an dakatar dashi, haka itama, zuwa wani sha'ani na mata kamar biki ko suna duk ba’a bukatar su. Zance ko da Baban ABU ya damu to kadan ne tunda gogaggen dan boko ne wadanda (time matters a lot for them) wato lokaci abu ne mai matukar muhimmanci a garesu. Sai ya yi amfani da lokacin 'suspension' din nasu ya koma makaranta ya nemi (degree) na biyu. Ita kuma ya sanyaata a (school of Nursing and Midwifery). Ba da bata lokaci ba yana kammalawa A.B.U suka dauke shi 'lecturing' ya kuma samu gida a cikin makaranta, domin ada a gidan haya suke domin gidansa na A.B Quaters an hana shi mukullin an rufe. A lokacin tuni an haifi fa’izah har tayi wayo. Kafin A.B ya rasu ya yafewa dansa Ahmadu, ya kuma karbi Maimunatu a matsayin surukar kaddara, bayan haihuwar danta na biyu, wato Abdallah, saboda kyawawan halayenta da zuri'a da tazo musu da ita mai albarka mai kama da nasu 'ya'yan. Domin Abdallah sak mahaifinsa, Fa'izah kuma Aunty Rabi ta debo, sai dai ta dauko duhun Maimunatu. Dama kuma abinda basa so kenan na auren bare, domin zai haifar da sauyin kamanni a cikinsu. Amma tabbas da Maimunatu na da iyaye, da sun maida ta ga iyayenta ko Ahmadu zai mutu, sun karbeta ne saboda MARAICIN ta. Nayi nadama, nadama mai yawa akan duk abinda na yiwa Fa'izah! Nadamar da bani da tabbacin akwai ranar da Fa'izah zata karbeta, tunda ba zata taba tsayawa ta saurari kalaman bakina ba. Fatana Allah Ya bani iko da damar nunawa Fa'izah kuskurena da karbarsa kafin na kwanta dama... Ya yaye min wannan ginshiran, domin ni kaina yana wahalar dani...". Da na kawo nan kuka na rikice da shi sosai, na kasa ci gaba da karatun, na ya da littafin. A guje nayi daki na ina kuka wiwi, na fada tsakiyar gadona na ci gaba da rasgar kuka. Nayi kuka-nayi kuka har naji babu dadi. Wannan shaukin ke kara mamayar zuciyata yana kara habaka. Wanda da nayi tsai da zuciyata na fahimci abinda bana so in fahimta da gangan. Wato SON FA'IZ ne yake mamayata cikin kowanne dakika na bayan da ya barni. Wani irin so mai cin rai, da tafarfasa zuciya. *** [23/02 11:32 AM] Sumayya Takori: *** Washegari haka na tashi sukukui! Babu kuzari ko yaya a cikin jikina. A wannan lokacin, babu abinda nake tunani illa hanyar da zan bi na gyara girgidadden aurena tun lokaci bai kure min ba. Kaunar Fa'iz da soyayyar sa ke lallasa ni ta duk hanyar da suka ga dama. A duk lokacin da na daga ido na dubi tangamemen hotonmu (window size) da aka manna a (main-palour) kamar za muyi magana, sannan tsananin kamar mu da juna ta fito sosai a hotunan. Kyau ne ke bugun kyau na mallawan usili, sai kwarjini da ya dara mini da wasu ilhamomi na daban da aka halicci Fa'izun dasu da ban taba ganinsu a tare da wani da namiji ba. Nakan tuno abubuwa da dama na irin cin kashi da rashin arzikin da na shekara yiwa iyayena da 'yan uwana akan auren mutumin da na tabbatar ban dace da kowa ba cikin duniyar nan face shi, sai inji na tsani kaina da mata masu irin halina na kafiya da taurin zuciya, riko da zuciyar rashin afuwa da yafiya, bayan dukkaninmu da Allah ba Ya hakuri damu, Yana afuwa a garemu albarkacin mai albarka, da bamu kawo yanzu ba. Hakika da Allah Baya afuwa ga al'ummar Annabi Muhammadu (S.A.W) da tuni an shafemu a doron kasa kamar yadda aka shafe al'ummar sauran Annabawa da suka gabacemu saboda kura-kuran da muke tafkawa Ubangijinmu da tsakanin mu kanmu 'yan Adam. Misalin karfe uku na yamma na dauki waya na bugawa Momi, jikina a matukar sanyaye, kamar yadda zuciyata ta mace, babu karsashi ko kankani a tare dani. Jin muryar Momi tana yi min sallama wani matsanancin tausayinta yazo ya lullubeni. Kenan ita bata da kowa a duniya da zata kalla ta ce nata ne, bayan mijinta. Baiwar Allah koda wasa bata taba gaya min ba don kar hankalina ya tashi. Ni Allah Ya bani dangin kamar ruwa masu kaunata da son yiwa rayuwata gata amma nake wulakanta su ina bata musu rai akan abinda sunyi ne amma sai nafi kowa cin ribar sa. Wato zaba min miji daya da daya a cikin 'ya'yansu wanda sun tabbata ko bayan ransu zai rikeni amana kamar rikon da uwa da ubana za suyi min. Momi taji nayi shiru, bayan ta jima da amsa wayar, ta ce. "Lafiya?" Na ce, "Lafiya". "Kin kirani kuma kinyi min shiru". Na sharce hawaye da suka yo wani irin ambaliya akan kuncina, sai naji ba zan iya tambayarta komi akan rayuwarta ba, kada in tado mata abinda ta riga ta manta dashi, tana cikin rayuwarta mai tsafta. 'And a total submission to ALLAH' da yadda Ya kaddara mata rayuwar. Na kasa 'controlling' kaina da tausayin Momi, kawai sai na fashe da kuka gaba daya. Kuka kawai nake ta rusa mata a wayar har na gaji don kaina bata katse ba, kamar yadda bata nemi taji dalilinsa ba, balle ta lallashe ni akansa. Sai da nayi mai isata sannan naji muryarta cikin sanyi tana magana. "Na rasa ke wace irin yarinya ce, na rasa a cikin mutane ke wacce iri ce, na rasa abinda yake damunki, ba mamaki gata ne yayi miki yawa. Menene aibun Fa'izu? Me kika fishi? Dame kike takama nayin butulci da irin wannan miji da Allah Ya baki? Har sai yaushe zaki shiga hankalin ki kisanAnnabi Ya faku? Duk sa'o'inki da tsararrakin ki kowanne na dakinshi cikin kwanciyar hankali, ga albarkar aure, sai ke don dai ki tabbatarwa da danginku da cewa uwarki bare ce abinda suke gudu a bare dai-dai ne. To ni dai wannan hali naki ba a wurina kika gado ba (kafiya da taurin kai na rashin tunani) ke kadai kika san inda kika kwaso abinki. Yanzu da kika ki kwantar da kai kibi Fa'izu ribar me kika ci? Meye ribar zaman da kike yi? Ke ba ga ladar aure ba, ke ba kwanciyar hankali ba, ke ba ga komawa karatun ba, ba wan ba kanin wai karatun dan kama... Saboda ke shashasha ce kuma dabba, wadda bata san ciwon kanta ba ko?" Hawaye ya ci gaba da wanke min fuska, ita bata san cewa tausayinta da nake ji ya rinjayi tasirin fadan da take yi min. Muryata cikin sanyi da shasshekar kuka mai yawa, na ce. "Don Allah Momi kiyi hakuri, ni yanzu babu abinda yake damuna. Hakuri zan baiwa Fa'iz din ma in ya dawo. Insha Allahu nayi alkawarin daga yau ba zaku sake jin wani abin assha daga gareni ba. Shima Baba zanzo in bashi hakuri. Walida nake so ki taimaka min tunda sauran sati biyu su koma wannan hutu, ba wanda ke zuwa min daga Giwa har Jabi Road, ni kadai cikin wannan katon gidan... Don Allah Momi...". Na rushe da kuka sosai wanda ya tayar da hankalin Momi, maimakon kalamaina su sanyaya mata domin kukan nawa mai zafi ne irin na kauna da tausayin DA ga MAHAIFIYARSA, yafi karfin ace akan fadan da tayi min nake yinsa. Wani irin kuka ne mai fitowa tun daga karkashin zuciya na wani abu mai nauyi da ya taba rayuwar mahaifanka. "Don Allah don Annabi Momi kiyi hakuri, ba zan kara ba... ba zan sake ba... Na tuba na bi Allah na bi ku... Zan bi Fa'iz sau da kafa kamar yadda kike bin Baba, ba zan sake tada muku hankali ba... Ni kaina na gaji, na gaji da wahalar da kaina, ina son mijina yanzu. INA SON SHI Momi...". Banga Momi ba, amma nasan murmushi tayi, (a very deep smile) kasancewarta mai yin murmushi mai fidda sauti. Ta jima bata yi magana ba, daga baya kuma ta yin. "Ki yiwa Abubakar waya, ki nuna nadamarki gareshi. Wannan zai sa shi watakila dawowa nan kurkusa. Amma in ba haka ba, mawuyaci ne yasan hakan, har ya yi marmarin dawowa gareki. Babu kunya tsakanin mace da mijinta, akwai inda ya dace aji kunyar, amma ba a irin nan ba, musamman idan baya ganin ki". Na ce, "Ba zan iya ba Momi, wallahi bazan iya ba, ina jin kunya, ina jin nauyinshi sosai domin sai a yanzu na fahimci abubuwa da yawa wadanda ada ban fahimta ba. Tsiyar dana tsula tana da yawa, tijarata gareshi mai yawa ce, da kyar in zai yarda ya kara hada rayuwa dani...". Na ci gaba da kuka mai tada tsigar jikin mai kaunar ka, musamman UWA! A sanyaye Momi ta ce, "Ai sai kiyi tayi, tunda kinga shi zai fisshe ki. Ki tsaya jin kunya ya dawo da matar dake son shi, ina ce shi kenan ko? 'It's not too late for you to correct your misdeed' ba'a tsufa da tuba muddin ana raye. Mutuwa ce kadai shinge ga tuba da nadamar bawa. 'Atleast ya san kinyi, koda ba zai karba ba... Walida da Kausar duka na nan zuwa". Jikina duka ya saki a yayin da Momi ta kashe wayar. Na kifa kaina cikin kujera na rasa me yake min dadi. A yinin ranar baki daya, na kare shi ne cikin tunanin ceto kima ta a idon Fa'iz da sauran son, in akwai. Yamma lis misalin karfe shidda na yamma, direban Bababn ABU ya sauke Walida da Kausar a harabar gidan. Walida tayi sallama ta aje (trolly) dinsu, ta dube ni duk nayi firgai-firgai dani, tun safe banyi wanka ba ga yunwa, tun kofin ruwan lipton dana zuba ma cikina da safe. Da yake yarinya ce mai hankali bata yi magana ba, gaisheni kawai tayi ta aje mayafinta ta shige (kitchen) ita kuwa Kausar wai wanka zata yi. Uffan na kasa ce masu, ashe Walida girki take yi, sai bala'i kamshi mai tada tsohuwar yunwa naji yana bugun hanci na kafin ince wannan ta aje min (tray) a gabana, (fried-rice) da taji kayan lambu tayi sharr da farfesun koda na tiriri da tashin kamshi. Nayi ajiyar zuciya na dubeta cike da kauna a raina, na ce. "Dan uwa rabin jiki". Na sa cokali na soma ci hannu baka hannu kwarya. Rabona da su tun ranar da Fa'iz ya kore su. Kausar ta fito ta dau wanka ta dau gayu da tirare dai-dai sanda na kammala cin abincin. Ta samu kujera ta hakimce ta kunna t.v tashar 'Bollywood' na galla mata harara na ce. "Inda Walida ta fiki kenan, hankali da sanin ya kamata. Wawuya kawai, kashe talbijin din nan bana son hayaniya". Kausar ta zumburo baki, "Ni fa hutawa nazo yi ba aikatau ba. Tun ranar da maigidan ya koremu ban kara marmarin zuwa gidanku ba. Yanzun ma ba don Momi ce ta takura min ba da banzo ba". Na kama baki na ce, "To yi mana rashin kunya ke da aka turo ki taimakeni mu sada zumunci. Tashi maza-maza ki wanke (plates) din da aka yi amfani dasu da tukwanen, kiyi 'mopping' (kitchen) din ko mu raba gari yanzu-yanzun nan har bakin 'gate' a jiyo mu". Ta mike tana kumburi kamar zata fashe tayi (kitchen) din Walida na yi mata dariya. Na ce, "Lallai Momi tana fama da wannan yarinyar, Allah Yan shiryeta". Walida ta ce, "Ai in tana yi Momi cewa take gadon Fa'izah". Nayi murmushi sosai cikin raina na ce, "Fa'izar da". Da daddare muna kwance a gado daya, Walida Kausar nata barci abinsu cikin kwanciyar hankali amma ni sai juye-juye nake daga wannan gefen zuwa wancan. Na kasa barcin magan-ganun da muka yi da Momi ke cina ta ko’ina, suna babbaka ni. A karo na farko nayi tunanin jarraba shawarar Momi na. To amma in kira Fa'iz ince masa me? Ince Fa'izu Abubakar, yanzu ina son ka? Da wane baki? Da wane harshe? Da wacce siga? Na ciza na hura na kasa samo sigar. Ina cikin rukunin mutanen da basa iya fadin abinda ke zuciyarsu a fatar baki, sannan ni mutum ce mai tsananin kunya da kama kaina. Wata zuciyar ta ce, "Fa'izu ba matsayin miji kadai yake takawa a gareki ba. Dan uwa ne na jini. Ba lallai sai kince sonshi kike ba, 'actions show feelings atimes...". Da wannan shawarar da wannan tunanin na kira Ummi, cikin barci mai nauyi ta daga bayan wayar ta sha (ringing) ta gode Allah. Har bana jin abinda take fadi sosai sai da na harhada na gane cewa take. "Waye?" Ajiyar zuciya na saki mai nauyi, tattare da jin nauyi, na ce. "Ni ce, kiyi hakuri 'for' damun barcinki. Lambarshi nake so ki bani". "Shi wa?" Ta katseni cikin kaguwa. Sai na kasa bata amsa, don naga alamun rainin hankali cikin tambayartata. To lambar wa zance ta bani ba ta mijina ba? Ko zance ta bani lambar wani kato ne bayan mijin da Allah Ya halatta mini? Sai na kasa ce mata komai. A fusace ta ce, "Wai lambar wa zan baki? Yaya Bashir yana kirana". Na tattara sauran karfin halina da guntun kashi na a katara na ce. "Yaya Fa'iz". Sai cewa tayi, "Wanne?" Cikin iya shege. Kamar na fashe da kuka na dai daure na ce. "Na Hajjah". Dariya Ummi ta saki mai ban haushi da bakanta zuciyar wanda aka mawa. Sai da tayi ta harda hawaye duk da bana ganinta ina jinta tana share shi, sai da ta mula cikin ginshira irin ta su ta 'ya'yan A.B sannan ta ce. "Gashi kuma ya gargademu baki dayanmu kada mu sake mu baki lambarshi don gudun kada kisa mai (bomb) a kunnen wayar ya tashi da shi, kin san makiyinka har kullum nesa-nesa kake yi da shi musamman wanda ka sanshi farin sani cewa makiyinka ne dole ka sha masa lahaula". Cikin tsananin takaici na ce, "Umm!". Ta ce, "Na'am Fa'izatu!" "Bana cikin kayan 'yan wulakancin ki. In banda dole banga me zai sa in neme ki ba balle har ki wulakanta ni...". "To ni na ce ki neme ni?" Ta katse ni. "Sanda ki ke shuka rashin mutuncin ki wa kike nema? Wane irin zagi da wulakanci ne baki yi min ba a lokacin da kike tsula tsiyarki? Sai yanzu da taki ta kawo ki ne kika san ina da amfani?" Na ce, "Shi kenan Ummi, zan nemi Zaneerah, nasan ba zata yi min abinda kika yi min din nan ba. Na dauka abokin kuka shi ake gayawa mutuwa, dalilin da yasa na neme ki kenan". Ta ce, "A'ah ba shi ake gayawa ba, abin dariya ake gaya masa kuma ni abokiyar dariya ce ba ta kuka ba, Allah Ya raba mu da duk abinda zai sa mu kuka...". Ban tsaya jin karshen iskancin nata ba na kashe wayata. Na kudure a raina ba zan sake neman Ummi a duniya ba. Don haushi sai da hawaye suka zubo min. Ban yi kasa a gwiwa ba na kira Zaneerah dake Lagos, (with full confidence on her) don kowa yasan Zaneerah 'is nice' kuma yarinya ce mai sanyi da sanyin hali fiye da kowa cikin A.B baki daya. Bugun farko layin ya shiga, amma har ya katse bata daga ba. Ban hakura ba na sake kira a karo na biyu, ya jima yana ringing shima kafin naji sassanyar muryar Zaneerah ta ce. "Hello!". Da sauri na ce, "Kinyi barci ne Zaneerah?" Ta ce, "Ko nayi barci ko banyi ba ina ruwanki Fa'izah? Kiyayyar Yayana da ta shafe ni... Ba kya nemana balle YAYA ALIYU! In maye na cin kowa baya cin kansa, Yaya Aliyu bai cancanci burus din da kika yi dashi ba in ni na cancanta saboda Yayana Abubakar. Diyata mai sunanki wadda aka sawa sunan domin KAUNAR ki balle wadda na sake haifewa ita ko darajar Allah Ya raya ko da 'text message' ne bata samu ba. A lahira da kallo akan ZUMUNCI da kuke yin wasarere dashi a yanzu akan wasu hujjoji marasa madafa. Yanzu ma zancenki da irin butulcin ki muka gama ni da Yaya Aliyu. Umh! Ina sauraron ki yanzun da wacce kika zo?" Sai kalamai suka kare a yawun bakina domin na yarda na amince nayi amanna da gaske ni din mai laifi kan laifi ce ga Zaneerah wadanda bazance ban san nayi ba, sai dai a wancan lokacin basu dameni bane domin ina da damuwata ta kashin kaina da ta dame ta kowa, ta mantar dani kowa da komai har da YAYA ALIYUN. Gaskiyar Zaneerah a LAHIRA da kallo akan zumunci, zamani ya canza al'umma da dama muna wasa da zumunci da hakkokinsa ta yin amfani da uzrorin kanmu da suka sha gabanmu, wadanda in ka bibiya duk na neman duniya ne wadanda ba zasu karemu gaban mahalicinmu ba ranar da yake binciken wannan amana da hakki mai girma mai suna ZUMUNCI da Ya bamu a hannayenmu cikin Alqur'ani da Hadisi. Zumunci abu ne mai girma. Allah Ya kawo mu wani zamani da baka neman dan uwanka na jini don jin lafiyarsa ko ta iyalinsa da halin dayake ciki, sai kana bukatar amfanuwa dashi 'in any way or the other'. Ina rokon Allah Yasa al'umma MU GYARA mu dawo da zumunci a muhallinsa irin na iyaye da kakanninmu a inda baka bambance dan wa da dan kani ko da shi ne beran masallaci saboda talauci, ko da shi ne karuna saboda arziki ba zaka bambance dan wa da dan kani ba koda da fatar baki ne ba za'a bambance maka ba sai dai ace "DUKA DAYA!" Na nisa cikin mutuwar jiki da ta zuciya da tunanina yazo nan. Na rantse na manta waya muke ni da Zanira kuma kudin wayata na tafiya. Zanira bata aje ba haka nima sai dai kawai taji shasshekar kukana. Allah Sarki Zaneerah, Zanin Hajjah, Zanin Mama, Zanin Yaya Aliyu... Sai ta kama dariya, dariya sosai mai nuna maida komai wasa, kuma ta fada ne don ta huce fushinta ba don ta kullace ni ba 'And she's relieved by expressing it'. "Ni fa komai ya wuce kuma har ga Allah nayi miki UZRI dai-dai har saba'in Fa'izah Fa'iz Abubakar...". Murmushi nayi, wani irin dadi ya ratsani da wannan suna mai sanyi data kirayeni da shi. "Bani da bakin da zan wanke kaina, sai dai ince KIYI HAKURI, KIYI HAKURI, KIYIHAKURI ZANEERAH...!" "Kema kiyi hakuri 'for hurting your feeling with my words'. Na fada ne don in huce bacin raina kuma na huce". "Nayi miki alkawarin zuwa har Lagos in Yaya Fa'iz ya dawo inga 'yata da takwarata, in baiwa Yaya ALiyu hakuri. Yanzu ma ina bashi wani na bin wani, kamar yadda na baki. Bayan nan ki bani lambar Yaya Fa'iz ko ki tambayo min Yaya Aliyu in baki da". Sai bayan da na fada ne wata kunya ta rufeni, wai macece take neman lambar mijinta a wurin 'yan uwa da dangi wannan abin kunya har ina! Ai kiyayyah ba hauka bace, sai ko in ta hadu da tabin hankali. Abin kunyar ma kuma ga kanwar mijin uwa daya uba daya. Allah ka agajeni. Wata irin guda Zaneerah ta sakar min a kunne wadda har saida ta dode min dodon kunne, nayi saurin kauda wayar daga kunena. Sannan na jiyota tana cewa. "Mafarki nake ko ido na biyu?" Na amsa da karsashi, "Idonki biyu Zaneerah, don Allah ki bani. Kada kiyi min abinda Ummi tayi min, kada ki hukuntani da laifina bayan na riga na amshe shi, na kuma aikata shi ne bisa kuskure. Don Allah Zaneerah...". Na karasa cikin karkarwar murya da rishin kuka. "Saurare ni Fa'izah". Ta fada cikin jin kai da kauna irin ta dan uwa shakiki. Na rage sautin kukan ina sauraronta. "Wallahi kinji nayi rantsuwa ta 'yan Musulmi kenan Yaya Fa'iz ya hana kowa ya baki lambarsa. Ya hana ni, ya hana Yaya Aliyu, ya kuma yi rantsuwa duk wanda ya baki ya yanke zumunci dashi har abada! Ki karbi uzurina domin ina daga cikin mutanen da yake mutuntawa, ya kuma yarda da amanarsu". Sai na zamo 'standstill, wordless, speachless, motionless! Me Fa'iz yake nufi da hakan? Kuma me yake nufi da katse duk wata hanyar sadar dashi gareni? Bani da sani akan hakan, haka itama Zanirar. Don haka tambayar ta ma baya da amfani. Hawaye ya sake ciko idona. Muka yi sallama kowanne jiki ba kwari. Tana fadin sai sunzo ganin gidan Malali, ko da yake ta gani a hoto wai Mama ta tura mata ta watsapp. A wannan daren, mai cike da sauyin sabbin al'amura masu dama a gareni, dai-dai da minti daya ban runtsa ba. Kuka nake yi wanda ni kaina ban san dalilin sa ba. Nayi kuka nayi kuka har na ji babu dadi. Idanuna suka shiga radadi, da zugi dole na sassauta musu. Anya ba asiri Fa'iz yayi min ba? Domin ko ga marigayi Nazir S. da Yaya Aliyu dana so a baya, so mai azalzalar zuciya ta, yake azabtar da ruhina bai kama kafar na yanzun akan Fa'iz Bamalli ba. To ko Mama ce tayi min asirin? Nayi saurin kawo A'uziyyah da Istigfari a bisa wannan mummunan zato da yake darsuwa a zuciyata. Na tabbata Mama, ko wani cikin zuri'armu ta ABUBAKAR BAMALLI GIWA ba zai taba yi min asiri wai don in so Fa'iz ba. Domin bamu san shi ba, bamu san hanyar nemoshi ba, bamu san inda ake yinsa ba haka bamu san yadda ake yinsa ba. Abinda muka sani shi ne idan muna da bukata, mu tashi cikin dare mu tsarkake kanmu da tufafinmu mu daura alwala, mu fuskanci alkibla muyi sujjadah ga Ubangiji mu fada mishi bukatar mu. Wannan ce tarbiyyar da aka rainemu da ita yaranmu da manyanmu. Ko da zata yi yunkuri akan inso Fa'iz sai dai tayi addu'a na Allah Ya daidaita tsakaninmu in da ALHERI (sunan wani littafin Takori). Idan kuwa har ta yin to ta tabbata an amsa addu'arta, ina sozn Fa'iz a yau, wani irin so da bazan iya fassarawa ba!!! Abinda na yarda da shi a tsayin daren baki dayansa shi ne. NA SOMA SON FA'IZ A DAN ZAMAN DA MUKA YI TARE na gajeren lokaci wanda yayi tsayin dare dubu da goma sha hudu a idanu da zuciyata. Dabi'unsa, saukin kansa, barkwancinsa, rayuwarshi gaba daya, addininsa, nutsuwarsa, ‘his unique personal attributes’ da tsananin KISHINSA akaina a fili da boye su suka ja ni ga kaunarsa. [24/02 11:09 AM] Sumayya Takori: *** Cikin wannan mawuyacin hali da sabuwar rayuwa mai wahalar da dan Adam a zuci da gangar JIKI da RUHI, duk da tarin jndadi da daular da ke zagaye dani, na cigaba da gurgurawa har tsayin wata guda. Ya zamanto ba abinda ke burgeni, ba abinda zan ci inji dandanonsa sai dai inci don in zauna da hanjin cikina lafiya, ba abinda nake son ji da gani sai FA'EEZ da MURYARSA... Wadanda ya haramta min haihata-haihata ya kuma toshe duk wata kafa da zan same su daga iyaye da 'yan uwa. Hutunsu Walida tuni ya kare amma nayi tsalle na dire na hana su komawa gida balle su koma makarantar, in sun bar gidan ban san makomar rayuwata cikin wannan fankacecen gida ba. Domin dai komai na gidan tun zuwansu su suke tafiyar dashi, girki da tsaftace shi. Abinda nasan ina iyawa kawai shi ne jefawa Dawisu kwayoyin dawa da sake musu ruwan sha idan yayi kura. Na daina ado, na daina wannan kwalisar. Hana rantsuwa nasan ina wanka, wannan kullum ne insha-Allahu. To sai dai bayan shi fa ko Vaseline baya ganin tattausar fatar jikina. Don ma Allah Ya so ni lokaci ne na zafi, da ban san yaya fatata zata koma ba, saboda rashin kula da hakkinta. Ina yin burushi sau biyu a rana, da safe kafin inci komai, da daddare in zan kwanta. Ina sauya kayan jikina bayan kowacce kwana uku, shima idan na gaji da mitar Walida ta cewa bana fesa deo-spray kayana suna tashi. Na zama wata irin Fa'izatu mara sanin inda rayuwarta ta dosa. Na zama mara lissafi ko tunanin wasu hanyoyi na inganta rayuwa. A ganina duk wani jin dadin, walwalar da ingancin rayuwar zai samu ne idan naji muryar Abubakar Mukhtar, na kuma ganshi da idanuna. Ko da bai sake cewa yana sona ba 'atleast' in nemi gafararsa, inyi zaman aure dashi irin na iyaye da kakanninmu. Wanda babu I LOVE YOU din sai tarin mutunta juna da darajja juna da sauke hakkin juna da Allah Ya dora a tsakani. Tunda na riga na bar damar ta kubuce min. Dama na sha jin ana cewa, tana zuwa ne sau daya a rayuwa. Hatta Yaya Rabi na tambaya lambar Fa'iz, na daure duk wani dizgi, shagube da izgilancin ta. Amma 'yar tahalikar nan bata bani ba. Ta rantse ta maya idan na sake tambayarta sai ta kwankwatsa wayarta in daina damunta. Mutum daya ya rage in tambaya ban tambaya ba, wato MAMA, don ita Hajjah bata rike waya, ko tana rikewa 'issue' dina da Hajjah a yanzu yafi karfin in nemeta a waya, ko in nemi lambar Fa'iz daga gareta. Ina jin bayan hauka da suka manna min a baya, idan nayi hakan zasu manna min fitowa daga turu. Kafin nan kafin in doshi Hajjaty a halin yanzu wani 'issue' ne na musamman mai zaman kansa, ban san da wane kalami, da wace fuska, da wane harshe zan doshi Hajjah in nemi gafararta ba, a bisa rashin kyautawar da nayi ta yi mata har da kauracewa. Anya Hajjar ta cancanci hakan? Da wannan dumbin tunani marar madafa ko zabi ta kowanne bangare na hada komai na tattara wuri guda na mikawa Subhana, Sarkin da babu abinda ya gagare shi. Ni na raunana, al'amarin ya gagareni iyawa da sarrafawa don haka na mika masa dukkan al'amarin yayi min iko da iyawarsa, bani da tsimi bani da dabara, duk suna ga Sarki ALLAH! Walida da Kausar suka kasa gane kaina, na farko bana zama dasu muyi hira, kamar yadda muka saba a baya. Bana sanya kaina cikin komai na al'amarin gidan, kullum ina daki nade cikin bargo kamar daddawa, bana umh bana uhm-uhm, sai gululun ido. Wadanda suka fada ciki suka zurma. Fa'iz kawai suka mace da son gani, ko son jin wani abu da ya dangance shi. Bazan iya kwatanta rayuwar da nake yi ba da halin da nake ciki, sai dai ince sunana FA'IZATU!!! Wadda son FA'IZU ke neman hallakarwa!!! *** Mun wayi gari yau da gingimemen hadari, mai dauke da sassanyar iska, wadda ke kadawa tare da yayyafin ruwa kadan-kadan yaf-yaf akan rufunan gidajen unguwar Malali GRA, wanda hakan ya tada kamshin kasa mai dadi da dadin shaka a hancin kowanne bil'adama. Dai dai lokacin da nayi wani juyi akan gadona domin gyara kwanciya don karin jin dadin kwanciyar tawa, naji ban zunguri Kausar ko Walida ba wadanda suke kwance gefe da gefe na. Hakan ya sanya ni bude ido sosai tare da tashi zaune. Can na hango su jikin gado suna shirya kayansu kaf a cikin (troller) din da suka zo da ita. Sosai na wartsake na dube su cikin mamaki, a lokacin da suka gama kintsa kayan suka ja zip suka zuge jakar. Na tashi zaune sosai na ture bargon na ce. "Ku, lafiya? Ina zaku je?" Walida ta mike tsaye tana gyara lullubin da tayi da mayafin Abaya baka. "Lafiyar kenan, tafiya zamuyi". Na ce, "AMma ba haka muka yi da Momi ba, munyi da ita zaku kara sati daya, na rantse daga shi ko kwana daya ba zan ce ku kara ba. Kuji tausayina Walida, kuyi hakuri mu zauna". Idona ya raina fata, ya kuma cicciko da kwallah. Kausar ta ce, "Allah ko minti daya ba zamu kara ba, balle yaya Fa'iz yazo ya taddamu a gidan nan ya sake korarmu. Tunda yau zai dawo zaman me zamu yi?" Da farko ban fahimci me Kausar take nufi ba, abinda na fahimta shi ne Kausar yarinya ce mai riko kamar ni, har yau haushin korar Yayan nata take ji. Don haka cikin lissafina ban lissafa da abinda ta ambata ba sai fahimta nayi kawai bata so ta ci gaba da zaman. Ina wannan harhaden ma'anar ne, Walida ta dora da bayanin da ya warware maganar Kausar. "Tun karfe bakwai ya kira wayarki, ni lokacin na tashi sai na dauka, Ya tambaye ni yaushe muka zo na ce da shi yau watanmu guda a gidan nan. Ya ce in sanar dake yana bisa hanyar dawowa karfe hudu na yammacin yau. A gayawa Yaya Bashir yaje filin jirgin saman Kano ya dauko shi ta can zai sauka. Ya ce ina kike? Na ce baki tashi ba, ko in tashe ki in baki? Ya ce in kyaleki kiyi baccinki, amma in gaya miki sakon". Jina nayi kamar ina yawo akan gajimare, cikin wata alkarya ta madara da zuma saboda dadi, farin ciki, godiyar Ubangiji, murna. Sauran abinda naji a cikin zuciyata a lokacin (unexpressable) ne. Ciki kuwa har da faduwar gaba da bugun zuciya. Wanda suka fito a tare da farin cikin, murna da godiyar Ubangijin suka saukar da wata irin nutsuwa da salama cikin zuciyata. Na lumshe ido a hankali. Ina rokon Allah a zuci idan mafarki nake kada Yasa na farka sai nayi tozali dashi din. Koda cikin mafarkin ne. Sai kuma na soma jin motsi cikin kaina, mai cewa in tashi in taka rawa, inyi juyi, in kuma rungume 'yar uwa shakikiya da ta kawo labarin, in bata tukuici da duk abinda na mallaka. Maimakon hakan, sai na mike na sanya hijabin sallah ta dake bisa darduma, wanda nayi sallar subhi dashi dama da alwalata, na sauko na dungura goshina gaban Subhana, na tsarkake shi, na tsarkake tsarkin mulki da iyawarsa! Duka walidar da Kausar suna kallona, sai suka kama yi min dariya suna tambaya. "Duka farin ciki ne Yaya Fa'izah?" Ban iya na tanka musu ba. Na lula a wata sabuwar duniyar ta daban, ta tunanin wacce irin tarba zan shiryawa Hafizin Hajjah? Fa'izun gidan Baban Kaduna? 'The one that is always hunting my dream?' Wanda tunanin ranar dawowar tasa ke zuwa min a farke, wato (ido biyu), cikin barci, ranaku da darare guda casa'in da nayi ba tare da na sanya shi cikin idanuna ba? A yau ga ranar tazo, 'so it will be a hectic and busy day; that needs planning and coordination'. Na daga ido a hankali na dube su ina murmushi wannan karon, wani irin murmushi da bana jin na taba yin ni'imtaccen sa a rayuwata. "To ai tafiya bata ganku ba, ajiye mayafin za kuyi ku tayani aiki ko? Mu gyara gidan, mu yiwa maishi girkin sannu da zuwa. Kuyi min kwalliya irin wannan da kuka caba, mai 'eye-shadow' da mascara, jambaki da lip gloss, ko 'yan matana?" Walida ta saki dariya, Kausar kuwa zumburo baki tayi da ya sha AVON lipstick yayi jajawur, Walida na fadin. "Kin burgeni Yayata, baki taba sa ni farin ciki irin na yau ba. Allah Yasa ki dore da hakan, Yasa ki cigaba da hakan har zuwa karshen rayuwar ku, ko mu ma 'yan baya ma yi koyi dake ko?" Murmushi nayi cikin matsanancin nishadi, "Sai kuyi ta addu'a ya yarda ya amshi tuban nawa, ba kwa ganin yadda yayi 'deleting' dina 'from the screen of his sight and mind?" Walida murmushin tayi itama, “Ni na gaya miki zai yafe miki, yana sonki yadda ba kya zato. Idan daso kuma ba aibi, sai dai 'FUSHI' wanda ba inda yake zuwa. DOn baki san me ya ce min dazu ba". Na kamo hannunta da sauri na zaunar a kusa dani. "Me ya ce miki Walida? Eye, gaya min? ". "Cewa yayi "Gyara mata bargon rufar garin da sanyi, tunda ruwa ake". Da na duba sai naga da gaske bargonki ya yaye daga kafafunki, na gyara miki. Ya ce, "Kin gyara?" Na ce, "Eh". Sannan muka yi sallama. Don haka zai fi kowa farin ciki da kika gane kuskurenki, ki ka amshi laifinki. Ki ka kuma yi dammarar gyarawa. Na lumshe ido a hankali ina mai gasgata kowace kalma dake fita daga bakinta. *** Muna (kitchen), abinda zamu karya kumallo dashi muka fara hadawa, sai dai nasan ko naman Dawisu na ne na gidan nan yau aka soya, aka farfesa min ba zan iya ci ba, farin cikin da nake ciki, doki da kuzarin da har yayi min yawa ba zasu barni in iya kai komai baki na ba, bayan ruwan lipton, shima don ya warware min hanji, ba don ina da 'appetite' akanshi ba. Kausar dake firar dankali ta ce, "UHm! Yaya Fa'izah in miki wani tsegumi mana?" Walida ta sanya bawon kwai da ta fasa cikin 'dustbin' ta ce. "Uwar tsegumi, yau kuma gulmar wa za'ayi?" Kausar tayi dariya, "Ba na kowa bane, naki ne. Don ni bana gulmar mutum sai dai in fadi akan idonshi don nasan illar yi da mutum". Cikin matsanancin nishadi nake wanda har baya kwatantuwa, don haka dariya suka bani. "Ina jinki Kausar, me ya faru?" Ta dubi Walida tana dariya alamar akanta zata yi maganar kuma Walidar bata sonta. Ta ce, "Kwanaki ko? Na ji Baban Kaduna yana gayawa Baban ABU a dakin Hajjah, an yiwa Yaya Walida miji". Duka Walida ta kai mata nayi hanzarin boyeta na riketa. "Wallahi ba zaki dake ta ba, ai ba ke take baiwa labarin ba ni take baiwa. In ba zaki iya ji ba ga hanya ki fita. Ina jinki Kausar, wane ne mijin?" Kausar dake tuntsira dariya ta ce, "Ki canka". "In canka Kausar?" "Eh, ki canka". "A cikin A.B ne?" "Eh mana". "Mus'ab?" "Gaba dai". "Abba?" "Can gaba dai". "Sani?" Ta ce, "Saura kiris". Na ce, "Shu'aib?" Tayi dariya, "Wannan ya mata nisa, yafi karfinta". Na harareta na ce, "Badar?" Tayi dariya, "Lallai kin manta magajin Ya Fa'iz wajen ginshira irin na 'ya'yan A.B". Ta fara kular dani, na ce, Ke na baki gari wane ne?" "A nawa zan fada miki?" "Au, sai mun tsadance?" "Eh Mana!". Na ce, "To #500 zan baki cash ba cheque ba". Ta mere baki, "Allah Wallahi yayi kdan". Da yake a zake nake da son jin abinda zata gaya min, na ce. "To #1,000". Murmushi tayi, "Shi kenan sai mun gama aiki". Walida dai na jinmu bata kara tofawa ba sai anan ne tayi tsaki, muka ci gaba da aiki duk na kosa a gama ta gaya min don Kausar miskilar yarinya ce, na san ko na ci gaba da na ci ba gaya min zata yi ba sai sanda ta ga dama". Muka kammala muka baje a kasa kan ledar cin abinci muka fara karyawa, ko ince suka fara don ni abinda na ci din ba wani na azo a gani bane. Ganin Kausar bata da niyyar gaya min har suka gama na kwada mata duka a baya, na ce. "Ke don Allah ki gaya min mana, ko so kike sai jini na ya hau?" Ta tintsire da dariya, ta kai kofi mug bakinta mai cike da kunun farar shinkafa ta kurba ta hadiye, ta ce. "Gaskiya sai naci na koshi Ya Fa'izah". Don haka nayi zuciya na kyaleta. Amma da suka gama ta shiga wata sabgar haushi ya kume ni, na ce (kamar zanyi kuka). "Uhm! Ke nake sauraro fa Kausar". Ta ce, "Kai don Allah Ya Fa'izah, kya bari abincin da naci ya tsirga mini mana". Ta sha toka abinta muna haka wayata tayi kabbara (call tune) din kenan. Na mika hannu zan dau wayar ina fadin. "Ke don Allah kada ki fada min in kina kaunar Annabi, ko ba dade-ko ba jima zanji ne ai". Kamin in dauka Walida dayake tafi kusa da wayar ta daga, ta ce. "Hello Yaya!.." "Eh ta tashi, abinci muke ci ma yanzun". "O.k toh". Ta kashe. Cikin zabura nake tambayarta, "Wane ne?" "Yaya Fa'iz ne. Ya ce in kin gama cin abincin ya sake kira". Kamar in maketa don takaici, muryata kamar ta wadda ta sha duka. "Amma ai kina ganin mun gama ko? Tun dazu muka gama ci fa!". Na karasa cikin karkarwar murya kukan takaicin Walida na neman kubce min ba da niyya ba. Ga idona ya ciko da kwalla. 'Yan banzan yaran nan sai suka kyalkyale da dariya. Karfe goma sha biyu da rabi na rana sai ga Shu'aib, Ya'u ya biyo bayansa niki-niki da kaya, jakunkuna saiti biyu samfurin (Argos). Na mike ina yiwa Shu'aib sannu da zuwa, Ya'u na shigo da jakunkunan falo. Ya zauna yana satar kallon Walida, ita kuma yana shigowa sai naga ta bar falon bata gaishe shi ba kamar yadda Kausar tayi, sai yasa murya yana kiranta amma bata dawo ba. "Ke 'yar kauyen ABU... Ina Yaya Sa'id Na'ibi A.B Giwa?" Cikin mamaki na ce, "Au, dama Yaya Sa'id ne mijin da Kausar ke fadi tun safe take ja min rai ta ki gaya min?" Yayi dariya, "Nima haka naji ana fada, ni na ce a bani an hana ni wai tunda ni na furta ba za'a bani ba. Yaya Sa'idu za'a baiwa, amma ai munga wanda ya furta aka bashi ba tare da an tuna cewa shi ne ya furta din ba, saboda mu ne ba'a so kawai sai Yaya Fa'iz". Murmushi nayi ya kuma matukar bani dariya da maganarsa. Ashe dai ba ni kadai nasan Hajjah tafi son Fa'iz akan kowa ba kowa ma ya ganeta ayi magana ta ce shima yafi kowa sonta, mu bama mata sai dai ta mana, Hafizinta fa? Komai nashi nata ne, komai ya samo ita yake fara tunowa kafin iyayen da suka haife shi. Ban kai karshen zancen-zucin nawa ba Shu'aib na tsinkaya yana fadin. "Ga kayan mijinki nan sun riga shi isowa, yanzu haka daga Airport din Malam Aminu nake, shi sai yamma zai iso wai sai biyar jirginsu zai sauka. Yaya Bashir zai je ya taho dashi ni yanzu haka Giwa zan wuce". "Allah Ya kiyaye hanya Yaya Shu'aibu". Na fada ina shiga (kitchen) don kawo mishi abinda zai ci a hanya ko da ba abinci bane ya samu na motsawa a baki. Ya'u ya shigo da kayyakin cefane har da buhunhunan kayan abinci ya shiga (store) dasu wanda hade yake da (kitchen), sai nama nau'i-nau'i, nasa Kausar ta adana kowanne daban a (freezer). Shu'aib ya mike zai tafi yana godiyar 'snacks' da dambun naman da na zuba masa a leda, ya ce. "Af! KInga ko na manta da sakon Mama a mota, bari inje in dauko". Ya koma ya dauko ya dawo ya miko min. "Ta ce kowanne akwai takarda a cikinsa, yana dauke da yadda za'ayi amfani da shi". Na amsa da hannu bibbiyu ina zabga godiya kamar shi ne Maman. Na ce, "Ka turo min Malam Isah (direban gidan Baban Kaduna) ko ta waya ne zai maida su Walida Zaria anjima". Murmushi Shu'aib yayi, "Ai yayarmu, haka za'a kora su 'so early' don maigidan ya dawo har an gama cin amfaninsu za'ayi (dumping) dinsu?" Na harare shi cikin wasa, "NI ban kore su ba, su suka kori kansu. Tun safe suka hada kaya za su tafi da kyar na samu suka kai yanzu". Shi dai ya fice yana min dariya, ya barni da guntuwar kunyata a katara. Cewa yake. "'Yau Mama zata sha labari idan na dawo daga Giwa, zata yi murna da farin ciki kwatan-kwacin na a zuba ruwa a kasa a sha. Fa'izah, ta sauke tata GINSHIRAR ta Bamalli, saura Pilot Fa'eez Giwa". Na ce, "Lala! Shu'aib ba ma haka da kai kada mu soma, kada kayi min sharri. Su Walida su suka nemi tafiya ni ban kore su ba". Ya ja motarshi kowannenmu cikin matsanancin nishadi marar misali. Ni da Walida muka share ko'ina na gidan nan kal-kal, muka goge, muka kade, musamman (side) din Fa'eez, da kaina na wanke (toilet) din shi na kawata da (toiletries) da turaren bandaki ko ina sai tashin kamshi da (atmosphere) mai dadi. Na canza (bedsheet) din dakin da wani (light-blue) mai hade da (duvet) da Baban Kaduna ya bamu tsarabar Umrah ni, Ummi da Zanirah. Na feshe (bedroom) din da (room-freshner) na 'HARAMAIN'. Na kunna na'urar sanyaya daki duk da sanyin da garin ke dashi, nasan daga 'Europe' zai fito, don haka zai bukaci sanyin. Sannan muka yi sallar azahar muka fada (kitchen). Da taimakon su Walida komai ya tafi dai-dai cikin dan lokaci, munyi faten acca da bushasshen kifi, baked moi-moi, tuwon shinkafa da miyar yakuwa da alayyahu da kabewa da tantakwashi zallah. Sai gashin 'Turkey' wato tolo-tolo. A fannin abin sha munyi coconut and milk shake, carrot drink, sai zobo mai abarba da pinaplple flavour. Dukkansu fresh da na sarrafa da kaina. Na ce a raina, "Yau babu 'chips', babu 'chicken', 'you need change HAFIZIN HAJJAH, as everything around us would completely change. Babu abinda LOKACI baya canzawa. 'With TIME change is possible in everything we do". (Lokaci yana canza komai). Sannan na koma 'snacks', ba tun yau ba, ba tun jiya ba na sha jin Hajjah na ba da umarnin a yiwa Fa'iz (samosa) 'best snacks' dinshi kenan. Don haka shi kadai muka yi, muka adana komai inda ya dace. Walida da Kausar suka gyara min komai suka goge min (kitchen) tas suka wanke duk kayan da muka bata, sannan suka shiga wanka. Karfe hudu Isa direba yazo suka tafi muna cike da kewar juna, sai da Walida tayi hawaye. [24/02 11:09 AM] Sumayya Takori: Wankan da nake ninkaya ina yi cikin kwami yau (unexpressable) ne. Wani irin wanka (slow-slow) da ban taba yin irinsa a rayuwata ba. Fatar jikina ta wanku har santsi take da silki tamkar mai canza launin fata... "Kazo ga jikin nan FA'EEZ, zan baka abinka, ba na yawon dandi bane naka ne, mallakinka ne, a yau sai yadda kayi dashi... Nayi kuskure Yaya Fa'iz, kuskuren da nayi farin cikin amsar shi tun a duniya na kuma yi dammarar gyara shi tun a duniya kafin Mahalicci ya tambaye ni shi". Karar wayata ne ya katse min sambatun da nake yi, na mika hannu na daga. Mama ce. "Yaya magungunan da na aiko miki dasu dazun Fa'izah? Kin shanye ko?" Cikin jin kunya irin wanda bai taba faruwa tsakaninmu ba, na ce. "A'ah!". "Dalili?" Ta tambaya. "Aiki nake tun safe Mama, su Walida sunce yau Yaya zai dawo". Wata matsananciyar kunya tazo ta lullube ni, na kuma kasa fadin wane yayan? Tunda yayun namu yawa gare su. Tayi murmushi na manyance, "Shi bai gaya miki da kansa ba sai su Walida?" Nasa hannu na kautar da zirin gashina dake disar da ruwa a jikina, na ce a hankali. "Ya yo waya ina bacci, ya sake yowa ina cin abinci, daga nan bai sake yowa ba. Kuma laifin Walida ne da bata bani wayar ba, sai ta ce wai ina bacci, ko ta ce abinci nake ci don shirme irin nata". Mama ta ce, "Ai shi kenan. DOn Allah kiyi amfani da kayan lefenki kinji Fa'izah! Ya gaya min baki taba amfani da duk abinda ya dauka ya baki ba. Sakon da Shu'aib ya kawo kuwa kada kiyi wasa da yadda na ce a cikin takarda kinji Fa'izah na?" Tausayin Mama da wani bala'in son danta ya kara kamani, na kara kwantar da kai a cinyoyina na kasa magana. SHin ita din wacce irin UWA ce mai maida nata ba nata bane? Ta ce, "Ba abinda kike bukata ta fannin kayan girki?" Na ce, "Ba abinda Shu'aib bai kawo min ba Mama, har da wanda bana bukata duka ya kawo". "Yayi kyau". Inji Mama. Muka yi sallama cikin girmama juna. Ni na fara aiwatar da umarninta. Wata irin kwalliya na soma da Voyal din Hilton pitch and maroun, kasancewata wankan tarwada sai kalar ta wani irin kwanta ta bi fatar jikina. Na dauki voyel din ne cikin kayan da Mama ta kira da lefe na a dinkensa na ganshi, dinki mai kayatarwa da daukar ido na doguwar riga budaddiya, sai dai daga sama ta kama jikin tsam. Na nada dankwalin a kaina ya kwanta lambam. (Make up) dina bai yi yawa ba, (very cool and sexy). Don karawa aya zaki na dauko takalmi cikin kayan, (flat) ne pitch dan Italy na zura siraran kafafuna. Turaruka kala-kala nayi amfani da su, duk dakin ya dumame da kanshi mai sanyi da sanyaya zuciya. Na karashe shanye romon kazar Mama, na shiga (toilet) nayi (brush) na fito na dawo falo na kishingide cikin (three seater) ina kallon tashar ALJEZEERAH. Dai dai lokacin da agogon bangon dake 'main palour' yua buga karfe hudu da minti talatin. A lokaci daya na murdo radio daga I-pad dina ina sauraron sashen Hausa na BBC, ni kaina ban san wanne nake sauraro ba tsakanin Radio da talbijin. Sai dai babu wanda hankalina ke kansa cikinsu, hankalina ya karkasu ne. Wani ya tafi ga tunanin wace irin tarba zan yiwa Fa'izun in ya shigo? Sannu da zuwa ko sannu da hanya? Sannu da hanya ko ina wuni? Ni kaina ban sani ba. Wata mutum ce ni din a yau dake ninkaya cikin maliyar SO, take neman a karbeta ko yaya ne a zuciyar da bata da tabbaci a kanta. Daya kashin kuma ya lula ne cikin tunanin tarbar da shi zai yi min. 'Will I be accepted? Appreciated? Trusted? Believed? Ignored or abandoned??? Karfe biyar ta buga na soma waiwaye ina duban kofa, haka duk motsin da masu karanta labaran Aljezeera da na BBC suka yi tsammani nake shigowar mota ne, ko kararrawar shigowa falo. Biyar da rabi... shida na yamma babu Fa'eez babu mai kama da shi. Bakwai na dare ta shude babu labarin Fa'eez Bamalli balle sallamarsa. Na soma karaya, kwalliyar ta soma gushewa da kanta, Gwiwata ta soma sagewa da kagara da zakuwa. Mutumin da akace zai zo biyar na yamma, shi ne har karfe takwas na dare, babu shi babu alamarsa. Da kyar na iya mikewa na bada faralin magariba da isha. Takwas da rabi na samu wayar Mama, ina dagawa ta dora da tamabayar da ta girgiza ni ko ince ta firgita ni. "Fa'eez Malali ya soma isowa kenan? Ni ina nan ina ta zuba ido shiru, to kice da shi in ya huta Babanku na son ganinsa da safe kafin yaje ko'ina...". Ban san sanda hawaye ya barke min ba, na soma shasshekkar kuka da ma kiris nake jira. Hankalin Mama ya tashi. "Ke lafiya? Babu lafiya yazo ko kuwa?" Cikin kuka na ce, "Bai fa dawo ba kwata-kwata, kuma babu wayarshi babu ta Yaya Bashir. Nayi (trying) ta Yaya Bashir din a rufe take. Shi kuma wadda ya kira da ita dazu da na duba sai naga ashe anyi (hidden No.) din". Mama tayi dan jim! Kafin ta ce, "Ya isa! Nan da karfe tara in bai iso ba zan turo Malam Isa ya dauke ki, Babanku sai ya bi sawun su Kanon shi da Shu'aib, idan yayi tafiya irin wannan ba inda yake fara sauka sai nan Jabi Road, daina kukan hakanan, watakila suna Kanon". Nayi shiru ina goge hawayena tana bani hakuri, da cewa kukana yana tayar mata da hankali. Jikina a matukar sanyaye na aje wayar gefe, lokaci guda hankalina ya kai ga abinda ake fade a tashar ALJEZEERAH, tare da wanda BBC ke fadi duk a lokaci daya, wato; "JIRGIN BRITISH DA YA TASO DAGA HAVERFORDWEST AIRPORT DA KARFE GOMA NA SAFE, YA FADI A SYCHELLS ISLAND TSAUNIN DAKE HADAKAR KASAR SINGAPORE DA...... Ihu da kururuwa na saka, wanda ya tafi tare da yin fatali da I-pad din da kafata ta kwankwatse a kasa, na mike tsaye ina ta kururuwa hade da INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'OUN. Na dora hannuna duka biyar a kaina, wani irin azababben kuka na saka dake ketowa tun daga cikin hanji da koda ta, cewa nake. "Noooooo!". Na yunkura na doshi kofa hannuwana aka, juwa ta kwasheni ta kayar. Ban daddara ba na sake yunkurawa, burina in bar gidan zuwa inda za'a ce min ba dai dai naji ba, ko kuskuren hanyoyin sadarwa ne. Juwar ma bata yi kasa a gwiwa ba wajen sake kayar dani. Sai na soma rarrafe akan gwiwoyina dai-dai lokacin da wayar da ta fashe a kasa ke nata kuwwar duk da tsagewarta. Da rarrafen na isa gareta na sata a 'handsfree' dukkan hannuwana da jikina baki daya rawa suke da karkarwa. Tun kamin inyi magana naji muryar Surajo cikin karaji da kuwwa yana tambayata. "Fa'izahhh! Fa'eez ya sauka karfe hudu na yamma?" Na kara rikicewa da kuka, cikin in'in'ina..., "Naji...naji...nima...nima Suraj...jir...jirginsu ya fadi ko?" Surajo ya ce, "Hasbunallahu wani'imal wakeel! Ni'imal maula wa ni'imal naseer!!! Gani nan zuwa yanzun, nima bisa hanya nake". Na durkushe anan na cigaba da kuka ba kakkautawa, hawaye na hade da majina. Dai dai lokacin da ALJAZEERAH suka shiga hasko jirgin a tsaunin daya fadi, ban san sanda na kwarara ihu da dukkan muryata ba. Abinki da unguwa irin GRA Malali, ba ruwan kowa da kowa balle wani yasan halin da nake ciki ya kawo min dauki, buzu yayi nisa domin na tabbata akwai tazara tsakanin bakin gate da cikin gidan wadda mota ma sai tayi tafiya zata iso. Ya'u kuwa tin dazun yayi min sallama da cewa ya tafi gida. Haka nan yanayin gininmu mawuyaci ne ko zubar ruwan sama aji balle a jiyoni, daga ni sai Ubangiji na muka san halin da nake ciki. A wannan halin Isa direba ya cimmani har cikin falon, ko yayi sallama ko bai yi ba ni ban sani ba, na dai ganshi tsaye a kaina, shi kanshi yayi wujiga-wujiga, idanunshi sun firfito sunyi jawur. "Mama ta ce inzo in tafi dake...". Ko tunanin rufe gidan banyi ba balle yafa mayafi na bi bayan Isa, sai shi ne ya dawo ya rufe kofofin. Tunda muka hau titi nake rasgar kuka, babu abinda nake tunawa illa musgunawa da kaskanci gami da rashin albarka, dana shekara yiwa mijina Abubakar Fa'iz tun ranar da aka daura mana aure. Muka kuma rabu, ba tare da na nemi cikakkiyar gafararsa ba, ashe Allah Ya rubuta iya tafiyar kenan, iyakacin sallamar kenan, iyakacin zaman kenan SAI A DARUS-SALAAM....! Na tuna yadda naci burin sauya akalar rayuwarmu, (from negative to positive). (So, kauna da mutunta juna. Ashe Allah Ya riga ya kaddara cikin kundin rayuwata BAZAN TABA CIN WANI BURI A RAYUWATA IN SAMU BA... BA ZAN TABA SON WANI ABU KO WANI MUTUM A DUNIYA IN SAMESHI BA!!! Inama ban zo duniya ba... YA LAITANI KUNTU TURABA...!!! Idan kuma zuwan duniyar kaddarata ce, inama ban kawo wannan lokacin ba, ina ma ban kawo wannan ranar ba, inama na rungumi KADDARA TA ta auren Abubakar ZABIN IYAYENA kowanne irin hali gareshi na yiwa iyayena biyayya kamar yadda Ummi ta ce! Kamar yadda Ummi tayi, kamar yadda Zaneerah tayi... gasu nan da manyan rabo tun a duniya kafin aje Lahira, da tabbataccen farin ciki da kwanciyar hankali wanda na tabbata ni har tawa mutuwar ta riskeni ba zan same su ba...!!! Inama mun rabu ne bayan na bashi jikin da yake rokon na bashi ya dauki budurcina da nake tattalawa shekaru ishirin da uku yana mai sa min ALBARKA??? Inama ban taba yin ramuwar gayya a rayuwata ba? Inama ban taba nunawa Fa'iz kiyayya ba... Inama mun rabu lafiya... da ko ba komai na tsira da wannan koda ban haifi kyakkyawan Da irin Fa'iz ba... inama...inama...inama... Inaman tana da yawa!!! A halin yanzu bani da abinda zan fuskanci Ubangijina dashi, ranar da tawa mutuwar ta riskeni. Banyi biyayya ga mahaifina da iyayensa ba tun farko, na sanya shi cikin bakin ciki da bacin rai maras misali. Na bashi kunya... na ba mahaifiyar shi da 'yan uwanshi... wadda ta sadaukar da kacokan rayuwarta da inganta rayuwarmu kuma komi tayi tayi ne 'for our own betterment' bata da ribar da zata tsinta a ciki, ta riga ta gama rayuwarta, ta gama cin ribarta ta Allah kawai take jira Hajjaty... bata cancanci abinda nayi mata ba ko sakayyar dana yi mata. Har kaurace mata nayi, don ta bani abinda tafi so a rayuwarta. Babu wanda ta yiwa zabi irin wanda tayi min, tabbacin ni din ma tana so na! Shin ni FA'IZAH cikin butulallun 'yan Adam wace iri ce??? Anya ba ni ce SHUGABAR su ba??? A yau FA'EEZ din ya bar min duniyar baki daya, in ci ta yadda nake sonta, da tsinke koda cokali, koma da cokalin kaya (fork). Banga amfanin sauran rayuwata ba, rayuwar da babu FA'EEZ a cikinta. Wanda suna ma daya aka sa mana, kamar yadda kamanninmu suke daya, duk da zuciyoyinmu basu samu daidaito ba tun muna kanana. Na tabbata na kuma yi amanna da cewa baki daya zuri'ar A.B ni zasu zarga da gushewar Fa'eez a doron kasa, tunda na sha faden ina addu'ar ALLAH YA KASHE FA'EEZ BAMALLI IN HUTA. Duk da cewa tsakanina da Ubangijinnawa ban taba yi ba sam. Kuma ban taba fadin hakan daga karkashin zuciyata ba, sai, dai a fatar baki. Banga amfanin sauran rayuwata ba! Idan nayi la'akari da manya-manyan kura-kuran da na tafka ban yi 'repenting' dinsu ba. Wadanda nake ikirarin LOKACI zai bani damar goge su, gaskiya ne babu wanda yake sama da KUSKURE sai dai lokacin da nake ikirarin zai canza komai... bai bani wannan damar ba...!!! Kuka da gunjin da nake gunzawa da shekawa a fili da zuci, yasa ban san tuni munzo gidan Baban Kaduna ba sai da naji Isa na kira. "Munzo fa Hajiya...". Na sunce kullin kaina na zagayo dashi wuyana don sai a lokacin na lura ko mayafi ban dauko ba. Na rarrafa na fito daga motar. Bana ko ganin abinda yake gabana. Banyi mamakin rashin haduwa da kowa a harabar gidan zuwa ciki ba, bana ganin hanya, illa kafata da tuni ta riga ta gane kowanne sako da kowanne lungu na gidan Baba Mukhtar A.B Giwa. Gaba dayansu suna tattare a babban falon gidan inda na sanya kafata, manyan gidan da yaransu, babu wanda baya kuka na fitar rai a falon cikin matukar kidima na doshi Mama Asma'u, wadda idanunta suka yi luhu-luhu don kukan da harshe ba zai iya bayyanawa ba... Nayi zaton ma zan tadda FA'EEZ a falon. In hadiye bakin cikina. Amma yanzu na tabbata FA'EEZ YA RASU A HADARIN JIRGIN SAMA!!! Na kama Mama cikin gigicewa ina wani irin kuka hawaye na min lugulgude da ambaliya a fuska... "Mama da gaske Fa'eez ya mutu??? Da gaske bazan ci ribar wannan SON ba ma a wannan karon???" Mama kuka kawai take, ko amsa daya cikin tarin tambayoyina ta kasa bani, Ta kankameni a kirjinta kawai amma ta kasa magana. Baban Kaduna ne ya shigo yana dafe fa kansa, yana fadin. "INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN... da gaske jirgin ya fadi, daga Kanon muke, Bashir din ma ya kamo hanya ne don ya gaya mana yayi (accident) yana asibitin koyarwa na Zaria babu yadda yake... Bamu san wa yaje ya gayawa Hajjah ba ta fadi! Barin jikinta ya jikkata. Allah daga gareka muke kuma gareka zamu koma... Ba Ka daurawa rai abinda ba zata iya ba, amma wannan jarrabawoyi da kayi a garemu masu tsauri ne... muna rokon sassaucinka da afuwarka idan mun kasance ne masu saba maka a kan sani ko bisa rashin sani. Hakika Kai Kaine Sarkin da bashi da mahadi, muna rokonka kudurah da iradarka akan wadannan jarrabawoyi namu zuciyoyinmu sun gaza dauka, kwakwalen mu sunyi rauni ga rungumarsu... Yaa ASSAMADU, KADIRAN ALAA MAN YA SHAA'U muna rokon sassaucin ka....!!!" Wani rugugi da hargagi naji a cikin kaina. Na tabbatar dai yanzu FA'EEZ YA RASU!!! Bayan wannan ban sake sanin me ke faruwa a duniyar ba... Ban sake sanin inda kaina yake ba...! *** Sanyin ruwan da ya ratsa kwanyar kaina, ya dangana da hakarkarina, ya zagayo zuwa wuyana da kirjina, shi ne ya maido ni hayyacina. A hankali nake bude idanuna ina lumshe su da son tantance halin da nake ciki? A ina nake? Me ya same ni? Cikin mafarki nake, ko kuwa idona biyu? Cikin 'yan sakanni na fahimci a gadon asibiti nake, akan cinyar mutum mai taushi, fanka na wulwulawa, A.C na burari. A hankali kwakwalwata ta soma tariyo abinda ya faru, da kuma musabbabin abinda ya kawoni gadon asibiti, wanda ba zan gushe cikin addu'a da fatan Allah Yasa mafarki nake ba! Nayi salati cikin wara idanuna sosai da jin muryoyi mabambanta na tashi cikin kunnuwana, daga mutanen dake zagaye dani. A lokacin memory dina (is back on network) duk abinda ya faru, ya kuma yi musabbabin zuwan nawa gadon asibitin ya dawo 'fresh' a kwakwalwata. Na yunkura zan mike zaune cikin fashewa da sabon kuka, sai naji an kamani an maidani kwancen. "Koma ki kwanta, 'relax Fa'iza, relax... 'Main Hoon Naa... (I'm here now)! And I will be here for ever, I'll not die and leave you... We are meant for each other!!!" Wata tattausar murya ke fadi, cikin turanci mai gardi da taushin amo. Sai kuma dariyar Mama akunnena da muryar Momina na fadin. "Ta gama suman, ta koma iya shegenta. Da dai ba ita din ce ba...". Muryar Walida, "Kai Momi! 'She's no longer the FA'EEZAH YOU KNOW... Na rantse tana son mijinta". Muryar Shu'aib, "Kaji Momi da wani zance mara dadi, ai mijinka-mijinka ne, kana son shi ko baka sonshi". Na daga kai a sukwane, na dubi wanda ke rike dani, kuma wanda nake kwance akan cinyoyinsa, wanda ke shafa min ruwan a fuska, wuya zuwa kirjina... FA'IZ (ABUBAKAR), FA'IZ BAMALLI NE, FA'IZU MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA...! Mijina abin sona, sanyin idaniyata, cikon farin cikina... 'The one that is always hunting my dream!!! Makiyina, abokin fadana ada can, masoyin da babu kamarsa a yanzu...Wanda zaton guhewar sa a doron kasa kadai ke neman aikawa dani nima. Mikewa tsaye nayi cikin wani irin zafin nama na rungume shi. Wata irin runguma kakkarfa, mai tafiya bisa umarnin zuciya da jagorancin gangar jiki, cikin kuka mai yawa wanda ya kasa tsayuwa daga idanu da zuciyata, amma wannan karon NA GODIYA GA UBANGIJI NE da ya kaddara zan sake ganin Fa'iz kafin Allah Ya dau raina. Zan rungume shi cikin jiki na kafin saduwata da Ubangiji na! Sosai yayi min masauki a katafaren kirjinsa, ya rufe ni ruf da gaba dayan gangar jikinsa ya zagayeni da hannayensa, ba tare da la'akari da iyayenmu da kannemu dake zagaye damu ba, su din dariya suke suna karawa, har da masu yin tafi, cikin nasu farin cikin, da godiyar Ubangiji. Na dago kaina na dube shi ina kuka, na shiga bugun kirjinsa da hannayena biyu. "Don me kayi mana haka yaya Fa'iz? Don me? Me yasa ka tsoratani ka tayar min da hankali irin wanda zai iya sawa zuciya ta buga! Kasan baka cikin jirgin kace kana ciki kawai don ka tayar da hankalinmu? Eye Yaya Fa'iz me yasa? Me yasa?? Me yasa???" Na koma na rukunkume shi da karfin gaske na cigaba da kuka kamar mai tsoron kada ya sake tafiya ya barni, ko wani al'amari makamancin wannan ya sake rabamu. Baice komai ba, idanunshi ya rufe bai bude ba, ina iya jiyo bugun zuciyarsa mai bugawa da sauri-da-sauri. Wannan wata rana ce mafi soyuwa cikin ranakun rayuwarsa da ba zai iya fassarata ba, ranar da yake tsammanin har ya koma ga mahaliccinsa ba zata taba zuwa ba! Ya rasa abinda zai yi ko zai ce da zai nuna dumbin farin cikin da yake ciki. Yau Fa'izah ce rungume da shi gaban BABA da MAMA, BABAN A.B.U da MOMIN A.B.U... Wata rana cikin ranakun rayuwarsa mai dumbin tarihi in ka cire ranar da ya karbi aninin zama cikakken matukin jirgin sama, da ranar daurin aurenshi da FA'IZAH A.A GIWA. Duk dakin asibitin ya dauki tsit, bayan shasshekar kukana dake tashi a hankali a dakin da bugun zuciyar Fa'iz Abubakar. Abinda ya iya cewa a wannan lokacin cikin sassaucin murya, inka cire ni Fa'izar dake rungume dashi, babu wanda ya iya yaji a dakin, ni din ma don na kasance cikin masu karfin ji ne. "FA'IZAH, ashe kina sona kike wahalar dani?" Ya fadi tare da kai hannu ya dago habata, ya dubeni cikin ido. A hankali Baba Muntari ya zame ya fice daga dakin, Baban A.B.U yabi bayansa, Momi da Mama suma ficewar suka yi, Shu'aib da Yahya suma suka fice. Amma Walida da su Junior suna tsaye kyarr idanunsu na kallon soyayya mai dumbin tarihi cikin zuri'arsu. Kallo daya Yayan yayi musu, suka fice cikin murmushi da susar keya (It's a show that they don’t want to miss). TAKORI. Muka yiwa juna kirr da ido, kamar kowanne so yake ya karanto adadin kaunarsa cikin idanun dan uwansa. Abubuwa da yawa sun faru cikin rayuwarmu wadanda duka marasa dadi ne, kowanne kuma yana 'blaming' dan uwansa da shi ne SANADI. Amma a yau mun yarda mun amince haka rayuwarmu ta zo a rubuce babu wanda shi ne SANADI. Mu din da rayuwarmu gaba daya kamar wani rubutaccen KUNDI ne wato LITTAFI mai dadin karantawa da koyarda darussa da dama. MUhimmi shi ne na 'YAN ADAM MU DAUKI RAYUWA DA SAUKI BAMU SAN INDA KADDARA ZATA KAIMU BA. ZA KA KI ABU, BAYAN WATA KILA ABIN NAN ALKHAIRI NE A GAREKA, ZAKA JARABTU DA SON ABU, ALHALIN SHARRI NE A GAREKA. DON HAKA NE IN ZAMU YI SO KO KI MU YI SU SAISA-SAISA. MAFI A'ALA SHI NE MU BAIWA UBANGIJINMU ZHABI A DUKKAN AL'AMURANMU NA DUNIYA BA WANDA MUKE SO KO MUKA JARABTU DA KIN SA BA!!! Ubangijin da ya halicce mu shi ya halicci SO ya kuma halicci ki ya sanya su a zukatan bayinsa. Kamar yadda ya halicci komai mace da namiji (feminine and masculine) ya kuma ya halicci komai da kishiyarsa (opposite) dukkansu kuma halittar Allah ne da babu dan Adam da ya isa yayi yadda yaga dama dasu face UBANGIJIN da ya halicce su. Mu karbi rayuwa a duk yadda ta zo, mu kasance cikin GODIYAR UBANGIJI. *** Mintuna masu dama suka shude kafin Fa'iz, yayi magana. 'It's not my fault' (Ba laifina bane). Akan me zanyi irin wannan mummunan 'joking' gareki har ma da IYAYENMU? 'I missed my flight', karfe goma na safe zan tashi nayi zaton na safe ne shi yasa na gayawa Walida da yaya Bashir zan taso goma na safe. A daren ranar kuma na kwana akan 'internet' ina gudanar da wasu muhimman ayyukana. Koko ince rai bata tafiya a lokacin da Ubangijinta bai kirata ba. Abu in aka ce miki da karar kwana to babu dabara. Idan kuwa rai bai zo wa'adinsa ba, ruwa da iska, mutum da aljan basu isa suyi ajalinsa ba balle abin hawa. Wani irin bacci ne mai tsananin nauyi ya kwasheni bayan nayi sallar Asuba da yake ma banyi bacci ba sai da na bada faralin Asubahi gudun kada in kwanta ya wuce ni, dana idar na ce bari in dan kishingida zuwa takwas na safe in shiga wanka in wuce Airport. Wallahi shi kenan, nayi ta baccin da ban tashi farkawa ba sai karfe goma sha daya na rana. Don haka da na tashi banji dadi ba, don na riga na fadawa Walida da Yaya Bashir na sake yin 'booking' na samu na goma na dare. Ina zuci-zucin in kira Shu’aib in gaya masa canjin da aka samu abokina Jeved yayi min waya matarshi Barya na labour in taimaka mishi inje in tsaya dasu a asibiti shi yana bisa aiki a Lusaka. Sai hakan ya janye min hankali na tafi garesu aka ce sai dai ayi mata 'CS’ ba zata iya haihuwa da kanta ba. Don haka ina wajensu har karfe takwas na dare. So ina komawa gida bayan an ciro mata yaron shi kuma Javed ya dawo, wanka kawai nayi na wuce 'Airport' karfe goma na dare muka taso zuwa Asuba muna Abuja, ban samu jirgi ba aka ce sai sha biyun rana kuma ban tsaya kiran Yaya Bashir ba kawai na biyo wani wanda muka sauka tare wanda shima Kaduna zai zo akazo daukarshi filin jirgin saman Abuja. Lokacin da na iso Maigadi ya ce duk gidan suna asibiti, lokacin ne na kira Shu'aib yazo ya sameni. Da ya ganni sai ya rungume ya fashe da kukan da ban san dalilinsa ba. Shima Malam Amadu (maigadi) kuka ya saka yana fadin. "Alhamdulillahi". A lokacin ne suke gaya min sunyi zaton ina cikin jirgin da ya fadi wanda dalilin hakan Yaya Bashir yayi hatsari, Hajjah ta samu paralysed, ke kuma kinyi dogon suma tun daren jiya har zuwa lokacin baki farfado ba, kina gadon asibiti. Muka garzayo muka taho. Na ganki cikin wani hali daya bani mamaki wai a dalilina kika shige shi. Ina tantama har yanzu... Ina shakkah... I still doubt! Fa'izah tabbatar mini, kin fadi ne don baki so na mutu......kin fadi ne don kina son mu rayu tare ko akasin haka? Am I not dreaming..?.". Hannu na kai na rufe mishi baki, 'before I start kissing him passionately'. Fatana ya yarda ni ce... ya yarda nayi nadama... Nadama irin wadda Ubangiji Yayi alkawarin karbarta. Na tuba nabi Allah na bishi... Na tuba na bi umarnin Allah! 'He is the one I love today and always... Burina Allah Ya barmu tare har zuwa karshen rayuwar mu. Mu rayu tare idan wa'adi yazo mu cika tare. Ina rokon Allah Ya cika min wannan buri... Yasa na rayu tare da FA'IZ rayuwa mai tsaho da nagarta... Sauran al'amuran da suka biyo baya (unexpressable) ne. Wata sabuwar duniya ce kuma wata rayuwa ta daban da biro ba zai iya bayyanawa ba. Wadda daga ni har shi bamu taba tsintar kanmu a ciki ba sai 'kintace' wato (Imaginations) tun lokacin da muka fara kamuwa da son junanmu. Muke kissimata cikin mafarki da ido biyu, muke kintacen ta da 'how deep it will be, how passionate, and how romantic! It's indeed the pleasurable one, EVER! Cikin wannan duniyar ne wadda bata kintatuwa 'no matter how efficient the description of a WRITER' wato duk kwarewar mai rubutu baki iya rubuta ta ba, muka kwashe awanni biyu, ban gaji ba, bai gaji ba, ZUCIYA da GANGAR JIKI kadai ke aiki a tare. Har sai da suka samu 'healing' na ciwon da ya kassara su, yayi 'overwhelming' Abubakar shekara da shekaru, ya kayar da Fa'izatu watanni uku. Ubangiji da Ya halicce mu, Shi kadai Yasan adadinsa a zuciyoyinmu. Dr. Alkasim Bello, kwararren likita a A&E na asibitin da muke, ya kwankwasa kofar Nurse na biye dashi. Bai shigo ba sai da Fa'iz ya yi mishi izinin shigowa. Amma hakan bai sa ya rabani da barin jikinsa ba. Murmushi Dr. Alkasim ya yi, "Darling didn't die, Fa'izah will not die...". Maganarshi ta bamu dariya dukkanmu. Yayi rubutu a (file) dina ya rufe ya dubi Fa'iz fuska fal fara'a. "Kana iya daukar amarya ku tafi Mr. Fa'iz, She's o.k, is a normal shock. Allah Ya kara dankon kauna". Babu kowa a (reception) din cikin 'yan gidanmu tabbacin duk sun tafi gida. Mukullin motar Baba yana hannunsa, don haka shi ke janmu zuwa Malali. Tafiya sosai mikakkiya, don asibitin yana unguwar Rimi ne. Ina gefensa yana tukin cikin sukuni da kwarewa. Na lalace a kallonsa tamkar wani furen fulawa don kyau. Ubangijin da ya halicce shi ya suranta shi, ya kyautata halittarsa da haiba da kamala. Idan na dube shi kallo daya kaga nitsatstsen mumini mai kiyaye iyakokin Ubangijinsa. Wanda kuma ya dama, ya kutsa cikin ilmin zamani mai tsada da daraja. A goshinsa tabon Sujjadah ne, ya taru yayi baki sidik cikin nuna babu ranar Allah da zata fito ta fadi bai russuna ga Ubangijinsa ba, Ma'abocin wata iri tsafta bayyananniya da ko cikin faratansa ya nuna. Komai nashi garai-garai kuma tsaf-tsaf kamar a lashe. Babu abinda nake yi cikin zuciyata sai tasbihi ga Ubangiji na da Ya mallaka min wannan ‘giant-handsome’ a matsayin miji a gareni mai so na da kaunata ba. Idan bance nafi sauran mata sa'a ba to hakika ina cikin sahun masu sa'ar ta kowanne bangare a rayuwa. Sautin Sheikh Mahmoud Khaleel Al-khusairi ke tashi a rediyon motar cikin Suratul-Ankabut. Watakila jikinsa ne ya bashi kallonsa nake yi kamar zan cinyeshi, ya juyo a gicciye ya saci kallona. Murmushi yayi, wanda ya fadada shi har fararen hakoransa suka fito. "Da yanzu wata na nan da lullubi aka, ta fara takaba". Na galla masa harara wadda ta fito ne hakikatan daga zuciyata, na dauke kai na mayar gefen titi. "Na matsu mu isa gida, (am running at a speedly level) amma motar bata sauri. Na matsu inji dalilin da yasa makiyinka yake kokomawa mutuwarka, har ya sume dominta". Juyowa nayi na kalleshi na 'yan sakanni, na sake maida kaina a titi cikin jin zafin maganganunsa. Na sadda kaina kasa, sai hawaye suka fito, suna diga akan tafukana. Sanyin na'urar motar yayi min yawa domin har raba ke naso daga kofofin A.Cn. Ga sanyin da jikina yayi da kalamansa, suka hadu suka haifar min da zazzabi-zazzabi, na soma jin kaina a sama, ban bari mun hada ido ba, don bana so yaga hawayena. Ya karya kan motar ya shiga layinmu, wannan karon yana tafiya ne cikin (slow-motion). Tamkar baya so mu karasa gidan. "I'm hungry, yaya za'ayi kenan? Gashi nayi alkawarin bazan sake cewa ki dafe min wani abu ba, 'above all' kema din baki da cikakkiyar lafiya, kin jigata kin wujijjiga da mutuwar maigida ba zaki iya girkin ba ko na janye alkawarin nawa. ‘I still wonder’ dalilinki na damuwa da mutuwata maimakon kiyi farin ciki na baki duniyar ki sha sharafinki...". Wannan karon ma shiru nayi, banyi magana ba, hawayen ne dai suka ninka na baya. "Insha sharafina, ko in shiga uku na?" Zancen zuci nake, ban san cewa ya subuto fili ya shiga kunnensa ba. Yi yayi kamar bai ji ni ba, ko da gasken ne bai ji ni ba bazan iya sani ba. Domin cewa yayi. "Kina jina? Na ce don mene kika damu da mutuwa ta?" Har tsakar kaina naji shock, cikin kwanyar kaina naji kunya, wata irin kunya da ban taba jin irinta a rayuwata ba. Wadda ta haifar min da dabarbarcewa. Ya sake maimaita tambayarsa. Wannan karon, tambayar tasa tana dauke da 'intonation' na ba da umarni kuma da gaske amsata yake bida, ko rai ya baci. CIkin karkarwar murya da in-ina na ce. "Uhm... uhm abincin yana... yana gida, na riga na dafa... ba sai ka sayo ba!". Dariya yayi mai hade da kallo daga can kasan ido. "Shi kluma cefanen fa?" Nima sai abin ya bani dariya, ganin ya saki daga daure fuskar da yayi. "Tambayar da nayi miki daban take da amsar da kika bani Fa'eezah!. 'Anyway' jikina ya bani kinyi kewana, idanuwanki sun nuna, kwayar idonki ta fada, kazalika kasusuwan da suka yiwa cikakken wuyanki ado, suka kuma maida dara-daran idanunki lungu. Don haka ne na zamo 'curious' wajen son jin dalili? Dalilin da ya sumar dake don NA MUTU! Alhalin sanin kowa ne mutum yana murna ne da mutuwar makiyinshi...". Na katse shi cikin kosawa, "Indai cefane ne ai Shu'aib ya kawo, Ya'u ya sanya su a (kitchen) da (store) da firinji, don Allah ka rabu dani haka!". Sai hawaye. Dai-dai sanda ya sanya hancin motar cikin gate din gidanmu. Buzu ya bude bakin shi yaki rufuwa don murnar isowar Ubangidan shi lafiya. Ya sanya motar a ma'adanarta, ya kashe fitilunta amma ita motar bai kasheta ba. Na murda mabudin motar don in fita, ko motsi ya ki yi. Na juyo a hankali na dube shi, da idanun bidar dalili. Har yanzun murmushi yake, ya ce. "Cefanen? Guda nawa ne?" Na ce cikin kauda kai, "To bude min kofar mana tukunna muje ciki kaga yawan cefanen da idanunka?" [26/02 8:44 AM] Sumayya Takori: Rausayar da kai yayi, a cikin kallona, ya lumshe idanunsa ya bude. "Yaya akayi kika sauya haka? 'What a sudden and awkward change! I need an explanation if you want to go out". Idanuna suka wani irin lumshe da kansu, na debo karfin zuciya na bude su tangararau akanshi. "Allah Ya hana bincike, kaga Allah Yaya Fa'iz yunwa nake ji... ka bude min kofa". "Allah Ya hana bincike, amma ke kika yi?" Na fiddo ido na ce, "Binciken me nayi maka?" Murmushi yayi (again), "Za ki rantse da Allah baki shiga dakina ba?" "Na shiga mana, amma ban bincika komai ba wallahi, gyarawa kawai nayi". Ya miko min hannun shi na dama na alamar karbar abu. "Bani DIARY dina!'. Na kai tafukana na rufe fuskata cikin matsananciyar kunya. "Koda na gani, ba lallai ne ya zamo na karanta ba. Kuma ma ai duk rabi Larabci ne ba iyawa nayi ba". Ya girgiza kai, "Fa'eezah! Kin dauka ban san cewa tun kina 'yar ficikar ki kike yara Larabci ba? Kin zaci ban san cewa (B.A Arabic) kike karantawa a BUK ba???" Baki na saki galala! Ina kallonsa. "Rufe bakin kada kuda ya fada". Dariya nayi na juya masa keya. "Duk wani motsi na rayuwarki nasan dashi, haka duk wani abu da kike aiwatarwa a kan wadannan fitinannun idanun ne, ko ba haka kuke cewa ba keda 'yan uwanki Ummi da Zaneerah?" "To mai yasa kake sa min idon? Ko kasan sa min idon da kake yana daga cikin abubuwan da suka sa na ki jininka a lokacin? Ina ganin kana sa min ido ne domin ka kuntaci rayuwata". "Kina so ki ji dalili?" "Eh". "To amsa min tambayata, ta shin kin karanta min DIARY bada izinina ba ko?" "Eh, na karanta, shi kenan? Amma wallahi ba bincike nayi don na samo shi ba, tuntube nayi dashi a dokin kofa". Murmushi yayi, "...Fa'izah matar Fa'iz! Insha Allahu jirgi ba zai zamo ajalina ba sai SON FA'IZAH!". Na dago cikin (slow) na dube shi, kwayan idanunmu suka hadu, suka sarke da juna. Babu komai cikin kwayar idanunshi sai 'gesture' wato motsi mai nuna zahirin abinda ke zuciya. Tsigar jikina ya tashi yarrr! Jikina yayi bala'in sanyi, ban san yaushe kalaman ke fitowa a hankali daga baki na ba. "Balle ma in Allah Ya yarda tare zamu mutu, tare za'a binnemu, kuma ba ta hadarin jirgi ba. Tukin-jirgi, hanyar abincin mu kenan ba hanyar ajalinmu ba, yanzu muka fara tukashi muna saukewa daga kuruciya har tsufa, ranar da ba zamu iya ba 'ya'yanmu su karba, haka har jikoki". Ni kadai nasan abinda naji... da na tsammaci mutuwarka! Da ka mutu a wannan lokacin Yaya Fa'iz I'll no longer be in existence. Na tabbata in 'so' bai kasheni ba kewa da 'kauna' za su kasheni...' Wata irin runguma Fa'eez yayi min da saida kasusuwana suka amsa. Hawayen dake makale tun dazu suka balle mini suka shiga shan sharafinsu a kundukukina zuwa gadon bayan sa. Ya kai hannu ya shafo hawayen, "Daina zubar dasu haka nan Fa'izah. Na tabbata ba ni ne baki so ba HALINA NE. Wanda a zahiri ba halina bane KISHI NE. Ba ke nake sanyawa ido ba, SOYAYYAR DA KIKE YIWA YAYA ALIYU NE! Ina kishin Aliyu Fa'izah, yadda bakya zato, har gobe ba zan daina ba. Domin wani mutum ne shi da kika so da zuciya daya saboda HALINSA! Na yarda na amince halin mutum jarinsa ne daga yau nima na zama dan kirki, dama ke kadai nakewa rashin kirkin, kema kuma don kina son ALI NA'IBI ne! Tunda kin maido son gareni na miki alkawarin zama mai kirki fiye da Yayanki ALIYU HAIDAR NA'IB A.B GIWA!" Na dago kaina ido sharkaf da hawaye. "Ko baka canza ba INA SON KA HAKA! I go along with the people I love da halinsu...". Dariya yayi, "Da can dinma bakya ki na, bacin ranki kike expressing' na bakanta miki da nayi. Da kina ki na da kinbi shawarar dana baki a RIVER NIGER". Na dunkule hannu na bugi kirjinshi da shi. "Kai ne baka iya kishin ba ai, kishi na mugunta?" Na sake bugunshi, "Ba'a nuna KISHI da KIYAYYAH... Ga wanda aka yimawa KIYAYYAH NE. Ka daina kishi da Yaya Aliyu don Allah, dan uwanka ne, kuma surukinka. Na so yaya Aliyu, kasancewar shi wani mutum da ya wahalta mini, da gangar jikinsa, da zuciyarsa, da aljihunsa da lokacin shi a kaina. Ya shiga kunci a lokacin da ya rasa ni. Kai da ka samu bai yi kishinka ba ya bada kyakkyawar gudunmawa wurin ganin na hakura na rungumi aurenka Yaya Fa'iz. Aliyu ne ya sani yin zuciyar da na tsaya nayi karatu na shiga sahun dalibai nagartattu a lokacin da nake cikin shagaltattu. Don me ba zan so shi ba a wancan lokacin tunda an halicci zuciya ne da soyayyar mai kyautata mata? Ina son shi ne a lokacin, amma wani irin so irin wanda nake yiwa BABA NA ban taba kimsawa zuciyata sha'awar tarayya a tare dashi ba sai so na 'KAUNA' da mutuntawa hadi da ganin kimar juna. Amma wannan son da nake ji a yanzu akan Hafizin Hajjah? Wani iri ne da harshe ba zai iya bayyanawa ba, kwakwalwa ba zata iya fassarawa ba, da ya gagari fahimtar mutum sai dai zuciya ta jishi amma ba zata iya bayyanawa ba. Haka nan zuciya da kwakwalwa basa iya daukar shi ba tare da sun nuna gazawa ba saboda GIRMANSA! Daban yake dana YAYA ALIYU kazalika NAZIR SANI GALADANCI. A kansu duka, banji irin wannan lullubabben son da nake yiwa FA'EEZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA BA!!!". "Barni haka... kada ki kasheni da raina". "Ya fadi ne a galabaice, cikin tsananta rungumar da yayi min. "Allah Ya bani tsawon ran da zan ninka farantawar da Aliyu yayi miki, Allah Ya bani tsawon ran da zan nuna miki bakiyi asarar Yaya Aliyu ba! Nayi alkawari Fa'izah zan nuna miki so da kulawa fiye dana Yaya Aliyu. Ko da can din ban samu dama bane, babu kuma hanyar da zan samu damar. Sai dai kisa a ranki, na rantse ALIYU BAI FINI SONKI BA... DAMA YA FINI SAMU!" Ni kadai nasan halin rudun da na shiga a lokacin da kike neman hallaka kanki don kiyayyata, sai ko abokina Maajid. Kada ki kara sawa a ranki wai bana son ki. Kisa a ranki Fa'eez naki ne KE KADAI". Shudewar mintuna masu tsayi cikin wasu al'amura masu tsayawa a rai, da zuciyar wanda ake mawa. Na nemi ji na da ganina na wucin gadi na rasa. Fa'eez ya daukeni ya kai wata duniya ta daban irin ta Adamu da Hauwa'u da ma'aurata kadai ke zuwa kwatankwacinta. Ya manta da yunwar cikinsa na manta da tawa, da kyar muka rarrafa zuwa cikin gidanmu muka dangana ga dakin baccinmu. A can komai ya kwance, al'amuran suka sauya taku, baga Fa'iz ba, ba ga Fa'izar ba, kowanne so yake ya nunawa dan uwansa ya fishi so da kaunar kansa. Ina rokon Allah Ya tsawaita rayuwarmu, Ya kara soyayyar junanmu cikin zukatanmu, ya bamu 'ya'ya masu albarka da biyayya ga iyaye. Bana burin in haifi da mai irin halina na kafiya, riko da taurin zuciya. Addu'a nake, Allah Ya bani Da ko 'YA mai hali irin na Ubansa/ubanta, mai yakanah irin ta Ubana da Baban Kaduna, mai son zumunci da kyautatashi irin HAJJAH. Mai tsaftattar zuciya irin ta MOMI na ma'abociyar rungumar kaddarorin UBANGIJI. (Ku ce Ameen, makarantan TAKORI). * * * Kwanaki bakwai da suka biyo baya, babu abinda ke wanzuwa a gidan sai amarci zallah, na a buga a jarida. Babu inda Fa'iz ke zuwa daga gida sai masallacin wani gida makwabtanmu, sai gidansu a Jabi Road shima duk dadewarsa baya wuce rabin awa. Ranar da ya cika kwana goma sha hudu ya ce in shirya zamu je zaga dangi daga nan mu wuce Giwa wajen Hajjah, sun dawo daga Jeddah ita da Baba Na'ibi da Aunty Zainab inda aka kaita asibiti tsayin sati biyu. 'Yan uwa dake kewayen Kaduna muka fara zagewa, su Aunty Hauwa Maman Ummi, sai Jabi Road. Mama dai hadiyeni ne kawai bata yi kullum sai zuba mana albarka, haka Baban Kaduna albarka suke saka mana babu kakkautawa a duk lokacin da kafafun mu suka taka gidajensu. Da kara jan hankalinmu kan riko da ZUMUNCI. Su kan ce. "Ko babu aure mu 'yan uwan juna ne, don haka hakuri da junanmu ya zama dole don cigaba da (maintaining) burin Abubakar Bamalli, ya cigaba da ganin abinsa can inda yake, suna rokonmu ko bayan ransu...kada mu warware wadannan igiyoyi da suke kukkullawa a tsakaninmu kan kannenmu da 'ya'yayenmu, jikoki da tattaba-kunne. Mun dauko hanyar Zaria bayan mun baro Kaduna, bayan motarmu shake da tsarabar su Walida (trolly) guda da Fa'iz yayo musu. Amma cikin rashin sa'a bamu same su a gidan ba. Walida tana makarantar WTC Soba tana shirin zana jarrabawar fita (SSCE) yayin da Abdallah ke makarantar horas da sojoji a Jaji (National Defence Academy). Kausar na S.S I a Sarauniya Amina, inda Walid autan Momi ya shiga shekararsa ta farko a karamar sakandire. Babana Prof. Ahmadu A.B da Momina Maimunatu A.B, sun rasa ina suka-saka-ina-suka aje damu don farin ciki. A fili Baba ya daga hannu yana yiwa Allah godiya a cewarsa da Ya nuna masa wannan rana, wadda Hajjah har kullum ke ce da su tana zuwa! Yayi addu'a Allah Ya karawa Hajjah lafiya da tsawon kwana., Ya jikan ABUBAKAR BAMALLI. Gaba daya muka shafa da amsawa da "Ameen". Fa'eez ya tafi cikin city ya barni, ya ce zai je yaga Surajo ya dawo. Bayan fitarsa ne Baba ya dubeni yana murmushi yake fadin. "Yo ko ke fa Fa'izata?" Na dago kai na dube shi nina murmushin nake yi. Rabon da inga yana walwala irin haka tun muna kanana sanda yake kaimu (Nursery) 'staff school'. Yana tuki yana mana tatsuniya har muje makaranta. Idan ya debo mu akan hanya zai tsaya ne ya sai mana dafaffen kwai da gishiri ni da Walida da Abdallah. Kullum ne ranar Allah sai ya sai mana dafaffen kwai da zuma wai suna kara kwanyar karatu. Idona ya ciko da kwallah da na tuno wahalar da na bashi 'in return' "Na ce ko kefa? Dubi yadda kika yi kyau, kika ciko, da kika kwantar da hankalin ki. Amma watannin baya baki ga irin takaicin da kike sanya ni ba. Kullum idan na daga ido na dubeki a gidan nan wai na kasa lankwasa ki, wani abu ne ke tokareni a kahon zuci. Kullum tunanina wai 'yar da na haifa tafi karfina, tafi karfin UWATA da yayye na, a duk sanda nayi tunanin haka, na duba na hanga naga cewa babu wanda keda irin wannan dan cikin A.B ... sai inyi dakacen dama ba ni na haife ki ba!!!'. Da rarrafe na isa ga Babana, kuka sosai nake har da majina. "Ka yafe min Babana, ka dubi Allah kayi min afuwa, kuskure ne da aikin shaidan ina rokon Allah Ya kara nisantani da shi. Duk abinda nayi nayi ne a bisa kuskure da rashin fahimta. Na roki afuwar yaya Fa'iz tuni ya yafe mini... Ina rokon ku kuma ku dubi Allah da nadamata ku yafe mini ko na cigaba da ganin haske a rayuwata... Ku taya ni rokon Hajjaty ta yafe mini...". Baba yasa hannu ya dago ni, "Tuni na yafe miki Fa'izah, ina gaya miki halin da na shiga a baya ne ba don ban yafe miki ba. Allah Yayi muku albarka, Ya kyautata gabanku da bayanku, Ya baku zuri'a masu albarka!!!". Ya sanya hannu ya janyo 'brief-case' dinshi ya fiddo wasu takardu, ya duba sannan ya miko mini. "(Share) ne na banki na saya muku dukkanin ku, ke kuma na hada da bude miki 'account' da bankin JA'IZ don saukakawa mijinki wasu daga cikin lalurorinki. Na kuma bude shi ne da niyyar duk wata idan na dau albashi zan sanya miki wani abu a ciki, haka kason ku na wata-wata da ake baiwa duk wani da na A.B shi kuma na bude mishi 'account' daban da Bankin 'Fidelity' ga (details) dinnan ki adana a wurinki ko ki bawa mijinki ya adana miki". Hannu biyu nasa na karba ina godiya. Na kare da cewa. "Baba Allah Ya bar min kai!". Murmushi yayi, "Nima Allah Ya bar min ke". Momin tayi dariya tana jinmu bata ce komai ba, dana juya gareta sai naga ta sunkuyar da kai hawaye na diga daga idanunta. Wato wannan din wata irin soyayya ce ta da da mahaifi da ita bata samu ba! Kaico da iyayen dake haifar 'ya'yan su zubda su ko masu sacewa su raba su da iyayensu, saboda cimma wata manufa ta duniya. Ya Allah ka barmu da iyayenmu har karshen rayuwarmu, Ka kara musu lafiya da tsawon kwana, Ka basu ikon kula da hakkokinmu, muma Ka bamu iko da zuciyar yi musu BIYAYYAH don gamawa da duniya lafiya (Ameenm summa Ameen). Dai-dai lokacin da Fa'eez yayi sallama shi da Surajo, Surajo ya gaida Baba da Momi ya koma tsokanata. "Yau sati biyu kacal cikin takaba amma aka rangada kwalliya?" Na galla masa harara Baba kuwa dariya yayi suka shiga hira na abinda ya shafi aikin Surajon (Banking), tashin zabuwar 'Doller' da 'sterling pounds' abin babu dadin ji. Sun dade suna hirar, tare da yiwa kasar mu addu'a. Muka yi sallama dasu muka dauko hanyar Giwa, shi kuma Surajo suka yi hannu ya shige motarsa ya koma cikin city inda gidan iyayensa yake. Har zuwa yanzun bai yi auren fari ba, na dai ji jiya Fa'iz na fadin ya kai kudin aure. Muna tafe akan hanyar Giwa, sanyin na'urar sanyaya mota na ratsa kasusuwa zuwa bargon mu, sautin Abdurrahman Sudaith na tashi cikin Suratul Tagabun, Nake gayawa Fa'iz. "Ko kasan rabon da kalami mai dadi ya hadani da Momi da Baba irin na yau, tun ranar da tsinkayi labarin daurin aurenmu? Na rasa wane irin so kafatanin A.B ke maka, kana da wata ilhama ta musamman da duk cikin zuri'armu babu mai ita. 'I salute!" Na kai hannu na gefen goshi na daga. Gaisuwar girmamawa irinta bature. Dariya na bashi sosai yayi harda bugun sitiyari. "The salute best suits you! Yarinyar da ta gasawa kafatanin A.B gyada a hannu. Ta nuna musu JIYA BA YAU BA... GABA DA GABANTA WAI ALJANI YA TAKA WUTA... I salute too!!!". Ya daga hannu a goshi, ya kankantar da ido cikin kallona. Murmushi nayi cikin jin kaina yayi girma kamar fanteka. Na mika hannu na rike nasa, ya ce. "Kinga matsa, kar kisa in watsar damu tun ban ajiye mai ce min BABA ba". Dariya ta kamani sosai saboda yadda yayi maganar cikin zare ido da barazana launin idonsa na canzawa. "To Baba Abubakar, direban zuciyata, the pilot that drives me crazy...". Kuuu!!! Ya ja wani irin birki a tsakiyar titi, saura kadan ya yiwa wani mai babur diban albarka, motar tayi gaba tayi baya kamar zata hantsila. Kafin ayi haka kankame nake dashi ina shahada, idan mutuwarce ta zo ta daukemu tare ko yanzu ne na shirya mata. A hankali ya gangara muka sauka a gefen titi. Rikon da yayi min mai tsauri ne da saida kasusuwana suka amsa. Idan al'amuranshi suka birkita bana iya doje su a ko'ina ne. Ko nayi kokarin hakan bana cin nasara. Al’amuran soyayyarsa unimaginable, unabandonable' ne a gareni, and also, irresistible. "Yaa Allah ka barni da Fa'iz, ka makantar da duk 'yan matan duniya daga kan mijina Fa'izu Abubakar, ka munanta shi a idanunsu ya zamo ni kadai nake ganin kyansa. "You are my life Yaya Fa'iz... I'll always keep on loving you..." "To say I love you Fa'izah, is not a way to express the feelings. .....!!!". Muryarshi har bata fita, kuma kalaman, yana fadinsu ne tun daga karkashin zuciyarsa. Bamu isa Giwa ba, sai karfe shidda na yamma. *** MURFI Hajjah na kwance tsakiyar falonta, 'yan kananan jikokinta zagaye da ita lokacin da muka shiga tana ta faman bari-barinta data saba daga kwance. Hannuna cikin na Fa'iz muka yi mata sallama a falon. Allah Sarki Hajjah! Mikewa tayi zaune daga kishingiden da take akan tuntu tana kyafta 'yan makyabtanta amma bata iya ta gane ko su waye ba. Hakika tsufa ya zo, amma mai tafe tare da nutsuwa wadda riko da addini ke haifarwa a shekarun tsufa, hakoranta duka rabi sun zube, gilashin take lalube don ya kara ma ganinta karfi ta gane mu. Kasancewar bayan sallama da mukayi kasa-kasa, daga ni har Fa'izun babu wanda ya sake magana balle ta shaida muryarmu. A tare muka isa ni da Fa'iz zuwa ga akwatin gilashin nata wanda yayi gefe guda, hannuna ne ya riga na Fa'iz sauka akan akwatun gilashin. Don haka ni na dauka na sanya mata. Kallon-kallo ake tsakanin Hajjah Hadiza Giwa, da jikokinta Fa'izah da Fa'izu. A nasu fatar bakin, murmushi ne. A nata kuma cewa tayi cikin raunin murya. "Abin tamkar a mafarki, ranar dana dade ina jira. Ranar da Fa'izu zai zo min tare da Fa'izah a matsayin matarsa, suna masu farin ciki da juna... suna annuri a fuska da zuci...". Na zame hannuna daga na Fa'iz na runtuma na rungume Hajjaty.... "Yau ga ranar Hajjah... Ki yafe min Hajjah kuskure ne, ajizanci ne irin na dan Adam!" Ta rungume ni sosai a jikinta tana dariya ina kuka. "Daina kuka Fa'izan Hajjah, ni ai nasan wannan ranar na nan zuwa, ni ai nasan dama shirmenki kike da tarin kuruciya ke haifarwa. Fa'izu nawa! Mijina na kaina, Abubakar Saddiku... akwai gaular data isa tace bata son sa? Ai sai dai ta fada don kawai taji dadin bakinta". Murmushi Fa'iz yayi, ya zauna a gefen ta yana kada 'yan mukullayen shi. "Hajjah tawa! Hajjaty!". Duk sai suka bani dariya, su basu yadda ba mata da mijin ne. Ina dariya mai cakude da hawaye na ce, "Tsinkayenki dai dai ne. Hasashenki bai zama a banza ba. Ki yafe min Hajjah kuskure ne wanda babu dan Adam din da ya isa ya kauce masa. Na yarda na amince ko iyayenda suka haifeni basu fiki so na ba, sai dai su ce su suka haifeni. Ina kira ga 'yan mmatan zamani su nutsu, su dawo cikin hayyacin su daga tasirin ilmin zamani, wajen akida da al'ada. Su daina kallon zurfin iliminsu da wayewarsu wani mataki na fin karfin iyayensu, sanin ciwon kansu ko abinda yake dai-dai ga rayuwarsu. Muna jarabtuwa da son abu alhalin shi din ba alkhairi bane a garemu, haka mu kan ki abu karshen ki a yayinda shi ne alherinmu. Mafi a'ala shi ne mu baiwa Allah ZABI a dukkan lamuranmu musamman 'AURE' mu daina bin soye-soyen zuciya da baiwa soyayya muhimmanci idan aka zo magana ta aure. Mu yiwa iyayenmu biyayya shine mafita. Soyayya ta kwarai a hankali ake samunta ba farat daya take samuwa ba. Ba ina nufin babu 'Love at first sight' ba, 'a'ah, 'it is normally not a geniune one'. Kuma bata da karko. Na gaba har gobe na gaba ne, haka iyaye har gobe iyaye ne koda a kungurmin daji suke zaune karewar rashin wayewar kai. Ina rokon Allah Ya barni da ku Hajjaty! Ya kara muku lafiya da tsawon rai. Ya bani ikon yi muku biyayyah koda ta wuta kuka hura ganga-ganga kuka ce in shiga anan gaba. Hajjah Allah Ya bar mana ke!!!". Murmushi tayi, wanda ya fadada zuwa dariya, ya fiddo wawulon da ya kara fadi a bakinta a dalilin faduwar hakora uku a bayan rabuwa ta da ita. Amma bata ce komai ba. [26/02 8:44 AM] Sumayya Takori: Fa'iz ya ce, "Hajjah me ya sami wayarki ne? In an bugo bata shigowa". Ta ce, "Kai don Allah rabani da wayar nan, kubi ku ishi mutum da kararraki, ko sallah yake ba zaku barshi yayi ta cikin nutsuwa ba. Ku dai ku kira mutum kiranma maras dalili. Na bude na cire batirin don ku kyaleni na huta ku da ubanninku da uwayenku". Yayi dariya ya ce, "Haba Hajjah, ai muna jin muryarki cikin koshin lafiya dadi muke ji musamman in muna nesa. Hankalin mu na kwanciya mu cigaba da fafutukar rayuwa cikin kwanciyar hankali Hajjah". Hajjah ta ce, "Idan ta zama dole ku kira Barau, sai ya kawo min muyi maganar a tashi amma ni ba zan iya ba. Tunda na cire batirin nan na jefa bayan gado kunnuwana suka huta na samu nutsuwar gabatar da ibadu na". Ya ce, "Talbijin fa? Don me ba'a kunnawa alhalin abar taya hira ce? Kina kallon mutane koyaushe suna gilmawa kina kuma jin muryoyin su yafi zama shiru". Ta ce, "Rediyo na ta isheni, in murdo tashar Kaduna in koma sashen Hausa na BBC, duk abinda ake fadi ina ji na kuma san 'yan uwana ne Hausawa Musulmi ba wadannan jajayen fatar da ba jin me suke fada nake ba". Da alama ta bashi dariya amma bai yi dariyar ba, ya ce. "Shi kenan Hajjah, yadda kike so haka za'ayi". Ta ce, "Yo dama mana? Ayi ba yadda nake so din ba a gani in zan yarda, ga jikoki ashirin, tattaba kunne goma sha biyar, kullum suna zagaye dani muna hirarmu, kuje ku ku kadai nake jira ku karo in roki Ubangiji na Ya dau raina haka. Duk wani burina da na marigayi na cika shi, da taimakon Allah da taimakon babanninku 'ya'yan albarka, wadanda har yawun bakina ya bushe ba zan daina sanya musu albarka ba. Bana jiran komai sai fatan cikawa da imani". Ta mike cikin dafa bango da taimakon Ya Fa'iz, ta nufi uwar dakinta tana fadin. "Yau tunda na tashi da safe jikina yake bani zaki zo gareni Fa'izah, don haka na sanya aka yi miki dambun naman kaza cikin katuwar samira, aka kuma yi miki gashin naman rago irin yadda kike so da ruwa-ruwanshi, yana nan cikin magashi (oven) bude ki dauko, dambun na kai daki na boye don in Na'ibi ya shigo ya gani sai ya kwashe rabi". Ina dariya cikin jin dadi na ce, "Allah ko Hajjaty? Sakallahu khairan". Ta dakata a kofar dakin nata tadan yi murmushi. "Irin wanda nayi miki ranar kamun ki, ranar da kika ja kafa kika gujeni baki kara waiwayata ba". Tausayin Hajjah ya kamani, na mike na bita na amso dambun cikin samira. Muka zauna a tare a gefen Ya Fa'iz mun sanyashi a tsakiya, na bude na diba na kai bakina ragowar nace. "To bude wawulon bakinki in zuba miki". Ta bude bakin tana dariya na sanya mata lomar dambun naman mai dadin da baya misaltuwa. "Nayi-na yi kimanta kin ki ko Hajjaty? Ni fa ban gudu na barki ba, naje inga Momi ne". Ta harareni ta ce, "Nono kika je sha ba ganin Momi ba". "Kenan baki yafe min ba Hajjah? Baki yarda kuskure ne ba? Idan baki yafe min ba Hajjah ina zani? In samo irin sanyin da nake samu a cinyoyin ki? Baki yarda ina son Hafizin ki ba kamar koma fiye da yadda nake son kaina? Yaya Fa'iz don Allah ka fada mata 'how much I love you'". Dauke kai yayi ya cigaba da danna wayarsa kamar bai san bikin da muke yi ba. Wani tunani yazo min, ya zanyi in goge wannan tabo a zuciyar Hajjah na cewa ina son Hafizin nata yanzun? Wata zuciyar ta ce. "Show her in another way". Sannu a hankali na tashi daga mazaunina na koma gaban Ya Fa'iz. Na zube gwiwoyina na sumbaci goshinsa zuwa labbansa, sumba mai tsayi da zurfi. Ya bude ido cikin barazana yana zazzare su. "Ke Fa'izah, meye haka? A gaban hajjahhh?" Hajjah ta fashe da kuka, wanda a cewarta, "Na farin ciki ne". "Na yafe miki Fa'izah, Allah Ya yafe mana baki daya". Muna takawa a hankali a harabar gidan zuwa bakin mota, Hajjah a tsakiyarmu ta yo mana rakiya muna 'yan hirarraki wadanda duk akan 'yan uwa ne, masu haihuwa, masu aure da masu karatu. Su Indo, Inna Kubra suka biyomu da tsarabar Hajjah (dambun nama) basu barni na rike ba. Don haka da muka fito kofar gida nayi musu ihsanin da zasu jima basu manta ba. Har mun kai jikin mota zamu bude Hajjah ta ce, "Au, Hafizi?" Fa'eez ya juyo ya dakata da bude motar. "Na'am Hajjah". Ta karaso garemu. Sai ta kama hannuna ta kamo nasa, ta hada ta dunkule. Da wani irin murmushin kauna a gefen bakinta, ta ce. "Sai ina kuma kuka yi yanzun?" Ya ce, "Gida zamu koma Hajjah. Gobe da safe kuma zamu bi jirgi zuwa Lagos wajen su Yaya Aliyu. Da mun dawo za muyi kaura zuwa (Wales) can inda nake aiki don jaurar tayi min sauki, in samu nutsuwar gabatar da ayyuka na Hajjah da Fa'izahta a gefe na, duk karshen shekara zamu zo mu ganku kuma ku ganmu. Ko in aikowa Baban Giwa tikiti ya kai min ke duk lokacin da naji son ganinki. Hakan yayi Hajjah?" Murmushi tayi, wani irin murmushi da ban taba ganin Hajjah tayi irinsa ba. "Nayi ta zama a duniyar kenan Hafizi kuna ganina kuna jin dadi? Ai mun iso gangara, me yayi saura Hafizi bayan fatan cikawa da imani? Ga amanar Fa'izah a hannunka, na roke ka ka kyautata mata muddin rayuwar ka. Baku sani ba, kuma ban taba fada ba koda ga iyayenku, yadda nake sonka haka nake sonta ko a cikin jikokina ku na daban ne. Ina rokon ku ku hada kanku, ku kaunaci juna saboda Allah!". Fa'iz ya sake damke hannuna cikin nasa, ya lumshe idonsa. "Na yi miki wannan alkawarin Hajjah". Har muka shiga motar ya tayar, Hajjah bata koma cikin gida ba. Ta sake matsowa jikin tagar da yake ta russuna dai-dai kunnensa, ta ce. "Kayi tukin a hankali". Sannan ta dago ta dubeni nima, "Fa'eezah ga amanar maigidana, Hafizina Abubakar Saddiku, ki bishi, ki yi masa biyayya kinji Fa'izah? Ki dawo min da mai sunansa in kin tashi dawowa ko mai sunana. Ina kulafucin ganin 'ya'yanku wanda nasan DA KYAR NE...". Jikina yayi wani irin sanyi da al'amarin Hajjaty a yau. Magana take kamar mai yin wasicci kuma kamar mai hango gobe. Ko dan yatsana na kasa motsawa haka shima Hafizin. Na kasa amsawa sai kallon Yaya Fa'iz, shi kuma sai ya sadda kai kasa bai ce komai ba. Da kyar na iya na ce, "Insha Allah Hajjah". Ya yi ribas da motar gate din A.B Houses Hajjah na daga mana hannu. Ni kam mai raguwar zuciya sai nasa kuka, kuka nayi ta yi ba dan kadan ba. Kalaman Yaya Fa'iz ya kara tunzura kukan nawa, cewa yayi. "Yau Hajjah duk ta kashe min jiki da kalamanta, ban san me yasa ba, gata dai lafiyarta kalau... Don Allah ki daina kukan nan Fa'izah, kina kara tayar min da hankali, kina sawa inji tamkar Hajjah mutuwa zata yi kafin mu kai Kaduna". Na tsagaita da kukan amma ban daina ajiyar zuciya da sauke numfashi ba har muka zo gida. A daren shima bai yi wani isasshen barci ba. Sau uku yana bugawa Aunty Maryam Maman Yaya Aliyu da Baba Na'ibi waya yana tambayar yadda Hajjah take har suka yi mamaki. Suka ce lafiyarta kalau, yanzu haka girki take yi wai zata yi sahur dashi, sannan ya samu ya rintsa sama-sama. *** Jirgin 'Aric' muka bi zuwa Lagos a washegari, 'already su Zanirah sun san da zuwan mu. Don haka muka same su a filin jirgin saman sunzo tarbar mu da yaransu Fa'izah da Amra mai sunan Hajjah. Yaya Aliyu yayi kiba har da tumbi tabbacin hutu ya zauna, kazalika itama Zanirar, Zannura inji Hajjah tayi kiba mul-mul da ita, tayi haske na tsabar hutu, daliba a jami'ar Lagos (UNILAG) tana karantar likitancin kashi. Suka tarbemu da farin cikin da baya misaltuwa. Ni da Zanirah muka rungume juna, haka Fa'iz da Yaya Aliyu. Tun daga (Airport) labari ke cin kowannenmu har cikin gida bakinmu bai yi shiru ba ni da Zanira. Na kasa shiru da irin daular da naga yaya Aliyu da iyalinsa ciki, na ce. "Shin wai Zanirah ba aikin kamfani Yaya Aliyu ke yi ba?" Zanirah tayi dariya ta ce, "Da kenan. Ai Yaya Aliyu likkafa ta mugun ci gaba. Yana daya daga cikin mamallaka kamfanin sarrafa gilashi tsura dake Japan. Sannan yana safarar tagogi da kofofi na gilashi daga kamfanin zuwa gida Nigeria". Na ce, "Na fahimta. Allah Ya kara arziki mai albarka takowanne fanni". Anyi zumunci wanda aka dade ba'ayi ba. Diyar Zanirah ta biyu mai sunan Hajjah da suke kira Amrah kamar Ya Fa'iz ya haifeta saboda kamanninsu. Kwananmu uku a Lagos muka juyo gida Kaduna, muka fara shirye-shiryen tafiya Wales. *** A CARDIFF (WALES) Gidan da Abubakar Mukhtar Giwa yake zaune yana Cardiff, wata irin rayuwa ce muka tsinci kanmu, wadda ba zan iya bayyanawa ba. Ubangijin da Ya halicce mu, Ya kuma yo mu jini daya, Ya sanya wata irin soyayya da shaquwa a tsakanin mu da biro ba zai iya rubutawa ba. Abinda zan iya cewa kawai shi ne aurenmu tattare yake da albarkar iyaye wadda ita ce komai. Ita ke haifar da komai, ita ke bude hanyar kowanne alheri cikin rayuwar dan Adam. Ko wata uku bamu rufa a Cardiff (Wales ) ba Yaya Fa’iz ya samar min ‘admission’ a jami’ar Cardiff University of Cardiff ). Ala dole na sauya layi kasancewar turai basa yin ‘course’ dina. Na soma karantar (Civil Law). Watanninmu Shidda a Wales muka ji kira daga gida Nigeria. Wani irin kiran waya mafi muni a rayuwarmu da dukkan zuri'ar Abubakar Bamalli. Wato mu zo gida Hajjah babu lafiya, jikinta ya rikice kuma mu kadai ne a bakinta. Haka Ya Fa'iz ya tattara hidimomin nemansa ya ajiye a gefe muka taho gida. A lokacin ina da cikin fari dan wata hudu. Ashe Hajjah sa'i yayi, kwananmu uku a Giwa Allah Ya yiwa Hajjah rasuwa tana mai sa mana albarka da mu da iyayenmu baki daya, da alfahari da haihuwar su. Tana addu'ar da rokon su ko bayan ranta, su cigaba da daura igiyoyin data bari na aurarraki a tsakanin jininta. Mutuwar Hajjah ta girgiza ta kuma dimauta baki dayan A.B, wata irin girgizawa da ba'ayi irinta ko lokacin mutuwar Abubakar Bamalli ba. Babu wanda bai gigice ya fita hayyacinsa ba, kada Abubakar Fa'iz ya ji labari. Wanda sai da aka yi da gaske kafin ya koma bakin aikinsa. Hatta abinci yasan Hafizi ya rasa Hajjah, tunda shima ya rasa Hafizin na lokaci mai tsawo. Watanni biyar da rasuwar Hajjah na haifi yaro namiji, Fa'iz ya cika burin Hajjah ya mayar mata da maigidanta kuma takwaransa muna kiransa Sadiq. Bayan haihuwar Sadiq da shekaru biyu na haifi Mukhtar, a lokacin karatuna yayi nisa sosai. Ahmad ya biyo baya muna kiranshi (Khazrajy), sai haihuwata ta hudu ne Ubangiji (S.W.T) Ya nufe ni da cika burin Hajjah na samu 'ya mace. Gaba daya daga mu har 'yan uwa HAJJATY muke kiranta. Allah ya dauki son Hajjaty ya sanya a zuciyar Yaya Fa’iz. Su Mukhtar sai suka zama ‘yan kallon sha’anin Daddy da Hajjaty. Gashi ta yo kamannin Hajjah sosai da dan banzan wayau. Haihuwar Hajjaty ta zo mana da sabon sauyi. Rana daya naga Yaya Fa'iz yana tattara 'belongies' dinsa daga kasar Birtaniya, ya aje aiki da 'British Airways' akan kashin kansa ba da son ransu ba, a cewarsa lokaci yayi da zai bada gudummuwarsa ga jiragenmu na gida Najeriya wanda rashin kishin kasa namu na ‘yan Nigeria yasa har gobe suke koma baya, British Airways suka yi mishi tukuici mai yawa wanda koda bai koma aiki ba nan da shekaru ashirin a gaba, a rayuwa dai ta dan Nigeria, Nigeriar ma Arewa, kuma dan asalin garin kauyen Giwa, ta ishe shi shida iyalansa su kasance cikin rufin asirin Ubangiji. Gidanmu na Malali aka sabunta aka fadada shi don walwalar yaranmu. Muka dawo Kaduna ina dauke da cikin kanin-ko-kanwar Hajjaty. Ya debi samarin dukkaninsu ya zuba a British International School dake Lagos, Yaya Aliyu ke kula dasu a can. Gidan daga ni sai Hajjaty, itama da cikina ya shiga watanni takwas Maman Kaduna ta dauketa. Ranar da na haifi MAIMUNATU ranar Yaya Fa'iz ya fara aiki da 'Aric’. Duk yadda dan Adam ke burin rayuwa zan iya cewa mun sameta. Ba zamu gushe ba face muna masu godewa Ubangijin Halitta. Mai azurta wanda Yaso, a kuma lokacin da Yaso. Ya talauta wanda yaso, ba don baya son shi ba sai don ya jarraba imaninsa. Rayuwa mai cike da so da kauna, irin wadanda basa 'fading' (kodewa) har muka fara furfura. A lokacin da nake da mukamin babbar Lauyar Gwamnatin Tarayya a Federal High court reshen jihar Kaduna, ina rokon Allah Ya kara soyayyar juna a zukatanmu, yarda, aminci da arziki mai albarka, ya raya mana yaranmu cikin tarbiyyar islama har zuwa ranar da muka daina numfashi. MASHA ALLAHU LA-QUWWATA ILLA-BILLAH!!!! Nan na kawo karshen littafin ZUMUNTAR KENAN! Da fatan za'a dauki darussan da littafin ke koyarwa muyi amfani dasu cikin rayuwar mu ta yau da kullum. Taku har abada Sumayyah AbdulQadir (Takori ).